1A cikin farko, Allah ya hallici sammai da duniya.2Duniya bata da siffa, sarari ce kawai. Duhu kuma ya rufe dukkan zurfafa. Ruhun Allah kuma yana kewayawa a bisa fuskar ruwaye.3Allah yace, "Bari haske ya kasance, haske kuwa ya kasance."4Allah kuma ya ga hasken, ya kuma ƙayatar. Sai ya raba haske da duhu.5Allah ya kira haske "yini," duhu kuma ya ce da shi "dare." Wannan shi ne safiya da dare, a rana ta ɗaya.6Allah yace, "Bari a sami fili tsakanin ruwaye, Sai ya rarraba tsakanin ruwaye."7Allah yayi tsakani ga ruwayen dake ƙarƙas da kuma ruwayen dake sammai. Haka kuma ya kasance.8Allah ya kira tsakanin "sararin sama." Wannan shi ne maraice da safiya, rana ta biyu kenan.9Allah yace, ruwayen dake ƙarƙashin sammai su tattaru wuri ɗaya, kuma sandararriyar ƙasa ta bayyana," haka kuma ya faru.10Allah ya kira sandararriyar ƙasa "duniya," ruwayen da suka tattaru kuma ya kira su "tekuna" ya kuma ga suna da kyau.11Allah yace, "Duniya ta fitar da ciyayi da itatuwa masu fitar da iri da kuma 'ya'ya waɗanda ke cikin 'ya'yan, kowanne bisa ga irinsa." Haka kuma ya kasance.12Ƙasa ta fitar da ganyayyaki, da itatuwa masu bada iri kowanne bisa ga irinsa, da kuma itatuwa masu bada 'ya'ya dake cikinsu, kowanne bisa ga irinsa. Allah kuma ya ga yana da kyau.13Wannan ce safiya da maraice, rana ta uku.14Allah yace, "Haske ya kasance a sararin sama domin ya raba tsakanin haske da duhu, su kuma zama alamu na yanayi, domin ranaku da shekaru.15Sai su zama haske a sararin sama domin su haskaka duniya." Haka kuwa ya kasance.16Allah yayi manyan haskoki guda biyu, babban hasken yayi mulkin yini, ƙaramin hasken kuma yayi mulkin dare. Ya kuma yi taurari.17Allah ya shirya su a sama domin su bada haske ga duniya,18su kuma yi mulki kan yini da kuma dare, su kuma raba tsakanin haske da duhu. Allah kuma ya ga yana da kyau.19Wannan ce safiya da yammaci, rana ta huɗu.20Allah yace, "Ruwaye su kasance da manyan halittu masu rai, ya kuma bar tsuntsaye suyi ta firiya a saman duniya a sararin sama."21Allah ya hallici manyan hallittu na tekuna, da kuma sauran halittu kowanne bisa ga irinsa, da masu tafiya da kuma waɗanda suka cika ruwaye a ko'ina, da kuma dukkan tsuntsaye masu fukafukai, kowanne bisa ga irinsa. Allah kuma ya ga yana da kyau.22Allah ya albarkace su, cewa, "Ku ruɓanɓanya, ku hayayyafa, ku cika ruwaye a cikin tekuna. Ya ce tsuntsaye su ruɓanɓanya a duniya."23Wannan ne asubahi da yammaci, rana ta biyar.24Allah yace, "Ƙasa ta bada hallittu masu rai, kowanne bisa ga irinsa, dabbobin gida, masu rarrafe dana daji kowanne bisa ga irinsa." Haka kuma ya kasance.25Allah kuma ya yi dabbobin duniya kowanne bisa ga irinsu, dabbobin gida kowanne bisa ga irinsa da duk masu jan jiki a ƙasa kowanne bisa ga irinsa. Ya kuma ga suna da kyau.26Allah yace "Bari muyi mutum cikin kamanninmu, bisa surarmu. Su yi mulkin kifaye na tekuna, da tsuntsayen sararin sama, da dabbobi, da kuma dukkan duniya, da dukkan abu mai rarrafe a bisa duniya."27Allah ya hallici mutum cikin kamanninsa. Cikin kamanninsa ya hallice shi. Mace da namiji ya hallice su.28Allah ya albarkace su ya ce da su,"Ku hayayyafa ku kuma ruɓaɓɓanya. Ku cika duniya ku nome ta. Kuyi mulkin kifaye na tekuna da tsuntsayen sama, da kuma duk abu mai rai dake tafiya bisa duniya."29Allah yace, "Duba na baka kowanne tsiro dake bada iri wanda yake a fuskar duniya, da dukkan bishiyoyi dake da iri a cikinsu. za su zama abinci a gare ku.30Ga kowacce dabba ta duniya, da kuma dukkan tsuntsaye na sammai, da kowanne abu mai rarrafe a doron duniya, da kuma dukkan halittu masu numfashin rai na baku kowanne irin koren ganye domin abinci." Haka kuma ya kasance.31Allah kuma ya ga dukkan abin da ya halitta na da kyau. Wannan ne asubahi da yammaci, rana ta shida.
"Wannan na maganar yadda Allah ya halici sama da duniya tun farko." Wannan maganar ya taƙaita sauran surar. Waɗansu harsuna sun juya wannan haka "Tun zamanin dã Allah ya halici sama da duniya." juya wannan ta hanyar da zai nuna cewa haƙiƙa wannan ya faru ba tatsuniyar waiwai ba.
Wannan na nufin a farkon duniya da komai da komai da ke cikin ta.
"sararin sama, ƙasa, da duk abin da ke cikin su"
Anan, wannan na nufin sararin sama.
Allah baya shirya duniyan ba tukunna.
"ruwan" ko "zurfin ruwa" (UDB) ko "babban ruwa"
"ruwan" ko "farfajiyan ruwa"
Wannan umurni ne. Ta wurin umurnin cewa haske ya kasance, Allah kuwa ya sa hasken ya kasance.
"Allah ya dubi hasken kuma ya faranta masa." "Kyau" anan na nufin "farantawa" ko "dacewa."
"raba haksen da duhu" ko "mayar da shi haske a wani loto, duhu kuma a wani lokaci." Wannan na nufin halitar Allah na yini da dare .
Allah ya yi waɗannan abubuwa a kwanan farko da duniya ya kasance.
Wannan na nufin rana ɗaya. Marubucin na magana game da rana ɗaya kamar ranar na rabe a sashi. Rana a al'adar Yahudawa na farawa a fadiwan rana ne.
Waɗannan umurnai ne. Ta wurin umurtar cewa sarari ya kasance, ya kuma raba tsakanin ruwaye, Allah ya sa haka ya faru ya kuwa raba ruwayen.
"babban fili tsakanin." Yahudawa sun gane sarari a matsayin wani abu ne mai siffer zobe ko cikin kwano da aka juya kasa.
"cikin ruwan"
"Ta wannan hanyar ne Allah ya halici sararin da ya kuma raba ruwayen." Sa'ad da Allah yayi magana, abin da ya fada ya faru. Wannan jimlar na bayana abin da Allah ya yi a sa'ad da yayi magana.
"Ya faru kamar yadda ya ke" ko "haka abin ya faru." Abin da Allah ya umurta ya faru, haka kuwa ya faru.Wannan maganar ya kasance a wurare dayawa a wannan surar kuma yana da ma'ana ɗaya ne a duk inda ya kasance.
Wannan na nufin rana ɗaya. Marubucin na magana game da rana ɗaya kamar ranar na rabe a sashi. Rana a al'adar Yahudawa na farawa a fadiwan rana ne.
Wannan na nufin kwana na biyu kenan da kasancewar duniya. Duba yadda ka juya "kwana na farko" a Farawa 1:3 sai a yanke shawara ko za a juya wannan ta hanyar.
Ana iya fassara wannan tare da aikatau. Wannan umurni ne. Ta wurin umurtar ruwaye su tattaru, Allah ya sa sun tattaru. AT: "Bari ruwayen ... tattaru" ko "Bari ruwaye ... zo wuri ɗaya"
Ruwan ya rufe ƙasa. Ruwan zai tattaru a gefe, sa'anan ƙasa ya kasance. Wannan umurni ne. Ta wurin umurta sandararriyar ƙasa ya kasance, Allah ya sa shi ya kasance. AT: "Bari a ga sandararriyar ƙasa" ko "bari sandararriyar ƙasa ya kasance a fili" ko "bari ƙasar ya zama a fili"
Wannan na nufin ƙasa ne da ruwa baya rufe ba. Ba ana nufin cewa ƙasar ta bushe da ba za a iya noman ta ba.
"Haka ya faru" ko "abin da ya faru kenan." Abin da Allah ya umurta ya faru kamar yadda ya ce.Wannan maganar ya kasance a wurare dayawa a wannan surar kuma yana da ma'ana ɗaya ne a duk inda ya kasance.
"ƙasa" ko " filin ƙasa"
"Yana" anan na nufin ƙasar da teku. dubi yadda aka juya wannan cikin Farawa 1:3.
Wannan umurni ne. Ta wurin ba da umurnin cewa tsire-tsire so fito daga ƙasa, Allah ya sa hakan ya faru. AT: "Bari tsire-tsire su fito daga ƙasa" ko "Bari tsire-tsire su girma daga ƙasa"
"tsire-tsire, kowani shuka mai ba da tsaba da kowani itace mai ba da 'ya'ya" ko "tsire-tsire. Su zama shuka masu tsaba, da kuma itatuwa masu ba da 'ya'ya." An yi amfani da kalmar "tsire-tsire" a nufin kowani shuka da itatuwa.
Waɗannan 'yan tsire-tsire ne ba kamar manyan itatuwa ba.
"itatuwa masu ba da 'ya'ya da ke da ƙwaya a cikinsu"
Ƙwayar za su haifar da itatuwa irin wadda suka fito. ta wurin haka kuwa itatuwa za su "haifar da kansu" (UDB).
"Haka ya faru" ko "abin da ya faru kenan." Abin da Allah ya umurta ya faru kamar yadda ya ce.Wannan maganar ya kasance a wurare dayawa a wannan surar kuma yana da ma'ana ɗaya ne a duk inda ya kasance.
Anan "na" na nufin tsire-tsiren, shuka, da itatuwa. dubi yadda aka juya wannan a cikin Farawa 1:9.
Wannan na nufin rana ɗaya ne. Marubucin na magana game da rana ɗaya kamar ranar na rabe a sashi. Rana a al'adar Yahudawa na farawa a fadiwan rana ne. dubi yadda aka juya wannan a cikin Farawa 1:3.
Wannan na nufin kwana na uku kenan da kasancewar duniya. duba yadda ka juya "kwana na farko" a Farawa 1:3 sai a yanke shawara ko za a juya wannan ta hanyar.
Wannan umurni ne. Ta wurin umurtar haskoki su kasance, Allah kuwa ya sa sun kasance.
"abubuwan da suke haskakawa a cikin sarari" ko "abubuwan da suke kawo haske a cikin sarari." Wannan na nufin rana, wata, da ta taurari.
"cikin sararin sama" ko "a babban sararin sama"
"su raba yini da dare." Wannan na nufin "su taimake mu bambanta tsakanin yini da dare." Rana na nuna yini, wata da taurari kuwa na nuna dare.
Wannan umurni ne. Ta wurin umurtar cewa su zama alamu, Allah kuwa ya sa sun zama alamu. AT: "Bari su kasance alamu" ko "su kuma nuna"
Wannan na nufin wani abu ne da ke bayyanar da wani abu.
"yanayin shekara" na nufin lokaci da aka keɓe domin bukukuwa da wasu abubuwan da mutane ke yi.
Rana, wata, da taurari na nuna yadda lokaci ke wucewa. Wannan na bamu damar sani aukuwar kowani mako, watani, ko shekara.
Wannan umurni ne. Ta wurin umurta cewa su haskaka duniya, Allah kuwa sa sun haskaka duniya.
"su kawo haske a duniya" ko "su sa haske a duniya." Duniya ba ta hasken kanta amma ana haskakata ne, sai ta kuma maimaita hasken.
"Haka ya faru" ko "abin da ya faru kenan." Abin da Allah ya umurta ya faru kamar yadda ya ce.Wannan maganar ya kasance a wurare dayawa a wannan surar kuma yana da ma'ana ɗaya ne a duk inda ya kasance. Dubi yadda aka juya wannan a Farawa 1:6.
"Ta haka kuwa Allah ya yi manyan haskoki biyun." The jimlar na bayana abin da Allah ya yi a sa'ad da ya yi magana.
"haskoki biyu mas girma" ko "hasken biyu masu haskakawa." Manyan haske biyun sune rana da wata.
"ya shugabanci yini kamar yadda shugaba ke tafiyad da mutane" ko "ya ba da alamar lokaci na yini"
Wannan na nufin iyakar sa'a da rana ke haskakawa.
"haske mara girma" ko "ƙaranci haske"
"cikin samai" ko "a sarari sama"
"ya raba haksen da duhu" ko "mayar da shi haske a wani loto, duhu kuma a wani lokaci." Dubi yadda aka juya wannan a Farawa 1:3.
"yana" na nufi rana, wata, da taurari. Dubi yadda aka juya wannan a Farawa 1:3.
Wannan na nufin rana ɗaya ne. Marubucin na magana game da rana ɗaya kamar ranar na rabe a sashi. Rana a al'adar Yahudawa na farawa a fadiwan rana ne. dubi yadda aka juya wannan a cikin Farawa 1:3.
Wannan na nufin kwana na huɗu kenan da kasancewar duniya. duba yadda ka juya "kwana na farko" a Farawa 1:3 sai a yanke shawara ko za a juya wannan ta hanyar.
Wannan umurni ne. Ta umurtar cewa halitu masu rai su cika ruwaye, Allah ya sa haka ya kasance. wasu harsuna na iya samun kalma ɗaya wa kowani irin kifi da dabbobin ruwa. AT: "Bari ruwayen su cika da abubuwa da yawa masu rai" ko "Bari dabbobi da suke ninƙaya su rayu a cikin teku"
Wannan umurni ne. Ta umurtar cewa tsuntsaye su riƙa tashi, Allah ya sa haka ya kasance.
"dabbobin da suke tashi" ko "abubuwan da suke tashiwa"
"a sarari" ko "a sama"
"Ta haka ne Allah ya halicci"
"manya manyan dabbobi da suke zama a cikin teku"
Abubuwa masu rai iri ɗaya na kamar waɗanda suka fito a gare su.
"kowani abu mai fifike da ke tashi." zai fi saukin ganewa a wasu harsuna idan an yi amfani da kalmar "kowani tsuntsu", tun da yake dukka tsuntsaye na da fifike.
"yana" anan na nufi tsuntsaye da kifi. Dubi yadda aka juya wannan a Farawa 1:3.
"albarkace dabbobin da ya halitta"
Wannan albarkan Allah ne. Ya ce da dabbobin tekun su haifar da wasu dabbobin teku irin su domin su zama dayawa a cikin tekuna. Kalmar "riɓaɓɓanya" na bayana yadda ya kamata su "hayayyafa."
"ƙaru sosai" ko "su zama da yawa"
Wannan umurni ne. Ta wurin umurtar cewa tsuntsaye su riɓaɓɓanya, Allah ya sa tsunstaye sun riɓaɓɓanya.
"dabbobin da suke tashi" ko "abubuwan da suke tashiwa."
Wannan na nufin rana ɗaya ne. Marubucin na magana game da rana ɗaya kamar ranar na rabe a sashi. Rana a al'adar Yahudawa na farawa a fadiwan rana ne. dubi yadda aka juya wannan a cikin Farawa 1:3.
Wannan na nufin kwana na biyar kenan da kasancewar duniya. duba yadda ka juya "kwana na farko" a Farawa 1:3 sai a yanke shawara ko za a juya wannan ta hanyar.
"Bari ƙasa ta fid da abubuwa masu rai" ko "Bari dabbobi dayawa masu rai su rayu a duniya." Wannan umurni ne. Ta wurin umurtar duiya ta fid da masu rai, Allah ya sa duniya ta fid da masu rai.
"domin kowani dabba ta haifar da irin ta"
Wannan na nuna cewa Allah ya halicci dukka irin dabbobi. Idan harshe ku na da yadda kuke kiran tarin dabbobi, kuna iya amfani da shi, ko kuma kuna iya amfani da wannan.
"dabbobin da mutane ke kiwo"
"ƙananan dabbobi"
"dabbobin jeji" ko "dabbobi masu haɗari"
"Ya faru kamar yadda ya ke" ko "haka abin ya faru."Abin da Allah ya umurta ya faru, haka kuwa ya faru.Wannan maganar ya kasance a wurare dayawa a wannan surar kuma yana da ma'ana ɗaya ne a duk inda ya kasance.
"Ta haka ne Allah ya halicci dabbobin"
"yana" anan na nufi abubuwa masu rai a duniya.
Kalmar "mu" anan na nufin Allah ne. Allah na faɗin abin da ya ke niyar yi. Yana iya yiwuwa cewa dalilin da sa an yi amfani da kalmar "mu" shi ne 1) jam'in na iya ba da ra'ayin cewa Allah na magana ne da mala'iku da suke a tare a cikin sama ko 2) jam'in na nuna cewa Allah ɗaya ne a cikin uku, yadda aka gane a sabon alkawari. Wasu sun juya wannan cewa "Bari in yi" ko "zan yi." idan ku juya haka, to a tabbatar an sharihinta cewa wannan kalmar na jam'i ce.
"'yan adam" ko "mutane." Ba maza ne kadai wannan kalman ke nufi ba.
Waɗannan kalmomi biyu na da nufi ɗaya ne, kuma yana jadada cewa Allah ya halicci mutum ya zama kamar shi. Wannan ayar bai bayana hanyar da mutane ke kama da Allah ba, kuma Allah ba shi da jiki. haka ya nuna cewa ba kamani jiki ne mutane suke da shi da Allah ba. AT: "kasance cikin gaskiyar kamani Allah"
"mulki bisa" ko "samu iko akan"
Waɗannan jimla biyun na nufin abu ɗaya ne, kuma yana jadada cewa Allah ya halicce mutum a cikin siffan shi.
Ba yadda Allah ya halacci sauran abubuwa bana ya halicci mutum. Ka da a ambaci cewa ya halicci mutum ta wurin maganar baki kamar yadda ya ke a ayoyin baya.
Kalmar "su" na nufin na mijin da macen da Allah ya halitta.
Allah ya ce da na mijin da macen su haifar da wasu mutane kamar su, domin a samu irin su dayawa. Kalmar "riɓaɓɓanya" na bayana yadda ya kamata su "hayayyafa."
cika duniya da mutane.
Allah ya ci gaba da magana.
"dukka tsuntsaye da tashi a sararin sama"
"da ke numfashi" (UDB). Wannan na jadada cewa rayuwan dabbobin dabam ne da na tsire-tsire. tsire tsire ba su numfashi, kuma za su amfana wajen zama abinci wa dabbobin. "Rayuwa" na nufin samun rai na zama.
"Ya faru kamar yadda ya ke" ko "haka abin ya faru."Abin da Allah ya umurta ya faru, haka kuwa ya faru.Wannan maganar ya kasance a wurare dayawa a wannan surar kuma yana da ma'ana ɗaya ne a duk inda ya kasance.
"Haƙĩƙa." Kalmar "gã shi" anan na jadada maganar da ke zuwa.
Allah ya ga dukka abubuwa da ya yi na da kyau ƙwarai.
Wannan na nufin rana ɗaya ne. Marubucin na magana game da rana ɗaya kamar ranar na rabe a sashi. Rana a al'adar Yahudawa na farawa a fadiwan rana ne. dubi yadda aka juya wannan a cikin Farawa 1:3.
Wannan na nufin kwana na shida kenan da kasancewar duniya. duba yadda ka juya "kwana na farko" a Farawa 1:3 sai a yanke shawara ko za a juya wannan ta hanyar.
1To an kammala sammai da duniya, da duk abubuwa masu rai da suka cika su.2A rana ta bakwai Allah ya kammala aikinsa da ya yi, domin haka sai ya huta a rana ta bakwai daga dukkan aikinsa.3Allah ya albarkaci rana ta bakwai ya kuma tsarkaketa, domin a cikinta ya huta daga dukkan aikinsa na halitta da ya yi.4Waɗannan sune al'amuran da suka shafi sammai da duniya, a lokacin da aka hallice su, a ranar da Yahweh ya yi sammai da duniya.5Ba wani filin daji kuma a duniya, ba tsire-tsire kuma a cikin filaye, domin Yahweh bai sa a yi ruwa ba tukuna a duniya, kuma ba mutumin da zai nome ƙasa.6Amma raɓa ta sauka a ƙasa ta jiƙe dukkan ƙasar.7Yahweh Allah ya halitta mutum daga cikin ƙasa, ya kuma hura masa numfashin rai a cikin kafafen hancinsa, sai mutum ya zama rayayyen taliki.8Yahweh ya yi lambun itatuwa a bangon gabas a cikin Aidan, a can ya sa mutumin daya halitta.9Daga cikin ƙasa Yahweh Allah ya sa ko waɗanne irin itatuwa masu ƙayatarwa da abinci su tsiro. Wannan ya haɗa da itacen rai wanda ke a tsakiyar gonar, da kuma itacen sanin nagarta da mugunta.10Rafi ya bi ta tsakiyar lambun Aidan domin ya jiƙa lambun. Daga can ne ya rabu ya zama rafuka huɗu.11Sunan na farko shi ne Fishon. Shi ne wanda ya malala a dukkan ƙasar Habila, inda akwai zinariya. Zinariyar wannan ƙasar tana da kyau.12Akwai kuma itatuwa masu ƙamshi da kyawawan duwatsu.13Sunan rafi na biyun shi ne Gishon. Wannan shi ne wanda ya malala zuwa Kush.14Sunan rafi na ukun shi ne Tigris, wanda ya malala gabashin Asshur. Rafi na huɗu shi ne Yufaretis.15Yahweh Allah ya ɗauki mutumin ya sa shi a lambun Aidin domin ya nome shi ya kula da shi.16Yahweh Allah ya umarci mutumin, da cewa, "Daga kowanne irin 'ya'yan itace na cikin lambun kana da 'yancin ci.17Amma ba za ka ci daga cikin itace na sanin nagarta da mugunta ba, domin ranar daka ci daga cikinsa, tabbas za ka mutu."18Yahweh Allah yace, "ba shi da kyau mutumin ya zauna shi kaɗai. Zan yi masa mataimakiyar da ta dace da shi."19Daga cikin ƙasa ne Yahweh Allah ya siffatta kowacce irin dabba ta saura da kuma tsuntsun sararin sama. Sai ya kawo su wurin mutumin domin ya ga yadda zai kira su. Duk abin da mutumin ya kira kowacce halitta sunanta kenan.20Mutumin ya ba dukkan dabbobi suna da kuma dukkan tsuntsayen sararin sama. Amma ga mutumin ba a sami mataimakin da ya dace da shi ba.21Yahweh Allah ya sa barci mai nauyi ya kwashe mutumin domin haka mutumin ya yi barci. Yahweh Allah ya cire ɗaya daga cikin haƙarƙarinsa ya yi mace ya kuma kawo ta ga mutumin22Da haƙarƙarin da Yahweh ya ciro daga jikin mutumin, ya yi mace da shi ya kuma kawo ta ga mutumin.23Sai mutumin yace, "A wannan lokacin, wannan ƙashi ne na ƙasusuwana, tsoka ce daga tsokata. Za a kira ta 'mace,' saboda daga jikin mutum aka ciro ta."24Domin haka mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, zai zama haɗe da matarsa, kuma za su zama jiki ɗaya.25Dukkan su biyu tsirara suke, mijin da matar, amma ba su jin kunya.
"sararin"
"da dukkan abubuwa da yawa masu rai da ke cikin su" ko "da duk taron rayayyu da ke cikin su"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ya gama halittar su"
Allah ba ya yi kowani aiki ba a kwana na bakwai
Wannan karin magana ne. AT: "ya gama"
"ba ya yi aiki ba a wannan ranar"
Mai yiwuwa ana nufi 1) Allah ya sarrafe kwana na bakwai da sakamako mai kyau, ko 2) Allah ya ce kwana na bakwan na da kyau.
"ya kuma keɓe shi" ko "ya kuma kira ranar na shi"
"a cikinsa bai yi aiki ba"
Sauran Farawa sura biyun na magana game da yadda Allah ya halicci mutane a cikin kwana na shida.
"Wannan shi ne tarihin sama da duniya" ko "Wannan shi ne labari game da sama da duniya." Mai yiwuwa ana nufi 1) wannan taƙaitaciyar labari ne da aka bayar a Farawa 1:1-2:3 ko 2) Na gabatar da abin da ke faruwa a Farawa 2. in mai yiwuwa ne, juya a hanyar da mutane za su fahimce dukka.
"Allah Yahweh ya halicce su." A sura 1 marubucin na ambatar Allah da sunar sa "Allah", amma a sura 2 yana kiran shi "Allah Yahweh."
"a sa'ad da Allah Yahweh ya halicci." Kalmar "rana" na nufin iyakar lokacin halitta, ba wani kwana ɗaya ba.
Wannan shi ne sunar da Allah ya bayyanar wa mutanen sa a cikin Tsohon Alkawari. Duba translationWord domin sanin yadda aka juya kalmar Yahweh.
ba tsire-tsiren da ke girma a jeji domin dabbbobi su ci
ba shuka masu ganyayyeki kamar kayan lambu da mutane da dabbobi za su iya ci
a yi duk abin da ake bukatan yi domin shuka ta yi girma da kyau
Mai yiwuwa ana nufi 1) wani abu kamar hazo, ko 2) bubbugowar ruwa daga rafi.
duniya dukka
"shafi" ko "kera" ko "halicce"
"ɗan adam mai rai ... ɗan adam" ko " mutum ... mutumin" ba lalle na miji ba
"hancinsa"
"numfashin da ke sa abubuwa su rayu." Anan "rai" na nufin kasance rayyaye a duniya.
Wannan na iya zama gonar itatuwa masu 'ya'ya ko wani wuri da ke da kowani irin itatuwa.
"a gabas"
"itace da ke ba mutane rai"
Wannan na nufi "rai madawwami" ko rai mara iyaka.
"itacen da ke ba mutane ikon fahimtar nagarta da mugunta" ko "itace da ke sa mutune su san abubuwa masu kyau da mugayen abubuwa idan an ci 'ya'yan ta"
Wannan karin magana ne da ke nufi sanin farko da iyakar abu da komai da cikin abun. AT: "komai, na nagari da mugunta"
"a tsakiyar gonar." Mai yiwuwa Itatuwa biyun ba a tsakiyar gonar suke ba.
Gonar na Aidan. Kogin ya ci gaba da malalowa har wa jen Aidan. AT: "Wani kogi ya malalo a cikin Aidan ya shayar da gonar."
Anan kadai ne aka ambaci wannan kogin a Littafi Mai Tsarki. .
"iyakar ƙasar da a kira Hawila." Yana nan ne a wani wuri a Hamadar Larabawa. .
Wannan maganar na ba da bayani ne gama da Hawila. Wasu harsuna na iya sa shi a wani jimla dabam. AT: "Akwai zinariya a Hawila"
Kalmar "akwai" na farkon jimlar domin jadada maganar. AT: "Anan ne kuma mutane ke iya samun duwatsu masu daraja"
Wani abu ne mai da ƙamshi da ke fitowa a wani irin itace. Yana mannewa kuma yana iya konewa.
"duwatsu masu daraja." Wani wani irn dutse ne mai kyau.
Anan kadai ne aka ambaci wannan kogin a Littafi Mai Tsarki.
Kogin bai rufe ƙasar gaba daya ba, amma ya kewaye wurare dayawa a ƙasar.
"iyakar ƙasar da ake kira Kush"
"wanda yake malala a cikin ƙasar da ke gabashin birnin Assurh" KoginTigiris na malala daga arewa zuwa kudu. Kalmomin "wanda ke malala gabashin Asshur" na bayana inda Kogin Tigiris ya ke. wasu harsuna za su wannan a wani jimla dabam. AT: "kuma yana malala gabashin Asshur"
"gonar da ke a cikin Aidan"
"ya nome ta." Wannan na nufin cewa ya yi duk abun da ake bukata domin tsire-tsiren su yi girma da kyau.
ya kiyaye gonar daga kowace muguwar abu da ke so ya faru a cikin ta
" 'ya'yan kowance itace da ke a gonar"
Wannan wakilin suna ne.
A wasu harsu a akan fara irin wannan maganar da ambacin wanda ba a so mutum ya aikata kamin wanda zai iya aikatawa.
"na iya ci ba tare da hani ba"
itacen da ke ba mutane ikon fahimtar nagarta da mugunta" ko "itace da ke sa mutune su san abubuwa masu kyau da mugayen abubuwa idan an ci 'ya'yan ta."
"ba zan ba ka izinin ci ba" (UDB) ko "ba za ka ci ba"
"Zan yi masa mai taimakon da ke dai-dai masa"
Maganganu nan "ta filin ƙasa" da kuma "na sararin sama" na faɗin inda ake samun dabbobi da tsuntsu ne. AT: "dukka irin dabbobi da tsuntsaye."
"dukka dabbobin da mutane ke kiwon su"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: " babu abokin hira da ya dace da shi"
"sa mutumin yin barci mai zurfi." ba a iya ta da mai zurfi barci a cikin sauki ba.
"daga haƙarƙarin ... ya kera mace." Haƙarƙarin ne abun da Allah ya yi macen da shi.
"A karshe dai, ƙasusuwan wannan kamar nawa ne, naman ta kuwa kamar nama na." Bayan neman abokin zama daga dabbobin bai kuma samu ba, yanzu dai a karshe ya ga wani mai kama da shi kuma na iya zama abokinsa. Mai yiwuwa mutumin na nuna gamsuwarsa da murna.
Wannan na nufi jikin mutum kamar fata da tsoka.
Mai juya wannan na iya sharihinta cewa "kalmar "mace' na kusa da kalmar 'miji' a Ibraniyanci.
Sauran magana daga marubucin littafin ne ba mutumin da aka halitta ba.
"Don wannan ne"
"mutum zai rabu da gidan mahaifinsa da mahaifiyarsa." Wannan maganar ga maza ne dukka. Ba wa wani takamamen mutum a wani lokaci ba.
Wannan ƙarin maganar na bayana cewa jikinsu da ke tare a jima'i na zama jiki ɗaya ne. AT: "jikinsu biyun zasu zama ɗaya"
Kalmar "su" na nufin na mijin da ta macen da Allah ya hilitta.
"ba tare da sa tufafi ba"
"ba su jin kunyar kasancewa a tsiraice" (UDB)
1To maciji ya fi dukkan sauran dabbobin saura da Yahweh yayi wayau. Sai ya ce da macen, "Ko da gaske ne Allah yace ba zaku taɓa ci daga kowanne 'ya'yan itacen dake cikin lambun ba?"2Sai matar ta ce da macijin, "Ma iya ci daga cikin itatuwan lambun,3amma game da itacen dake tsakiyar lambun, Allah yace, 'Ba zaku ci shi ba, ba kuma zaku taɓa shi ba, in ba haka ba, zaku mutu."'4Sai maciji yace da macen, "Hakika ba zaku mutu ba.5Domin Allah ya san cewa a ranar da kuka ci idanunku zasu buɗe, zaku kuma zama kamar Allah, kuna sanin nagarta da mugunta."6Da matar ta duba ta ga itacen yana da kyau domin abinci, yana kuma ƙayatar da idanu, kuma itacen abin marmari ne yana sa mutum ya zama mai hikima, sai ta tsinki waɗansu daga cikin 'ya'yan ta ci shi. Sai ta bada waɗansu ga mijinta, shi kuma ya ci.7Idanun dukkan su biyun suka buɗe, sai suka gane tsirara su ke. Sai suka ɗinka ganyayyakin ɓaure suka yi wa kansu sutura.8Sai suka ji motsin Yahweh Allah ya na tafiya cikin lambun da sanyin yamma, domin haka mijin da matar suka ɓuya a cikin itatuwan lambun daga fuskar Yahweh Allah.9Sai Yahweh Allah ya kira mutumin yace da shi, "Ina ka ke?"10Mutumin yace "Na ji ka a cikin lambun, na kuma ji tsoro, domin tsirara na ke. Domin haka na ɓoye kaina."11Allah yace, "Wane ne ya faɗa maka cewa tsirara ka ke? Ko ka ci 'ya'yan itacen da na dokace ka kada ka ci daga cikinsa ne?"12Sai mutumin yace, "Macen daka ba ni ta kasance tare da ni, ta ba ni 'ya'yan itacen, na kuwa ci shi."13Yahweh Allah yace da matar, "Me ki ka yi kenan?" Sai macen ta ce, "Maciji ne ya yi mini ƙarya, na kuwa ci."14Yahweh Allah yace da maciji, "Saboda ka yi wannan, kai kaɗai ne la'ananne a cikin dukkan dabbobin saura da dukkan dabbobin sama. A kan cikinka za ka yi tafiya, kuma ƙasa za ka ci dukkan kwanakin ranka.15Zan sa magaftaka tsakaninka da matar, da kuma tsakanin zuriyarka da zuriyarta. Zai ƙuje kanka, kai kuma za ka ƙuje diddigensa."16Ga macen yace, "Zan ninka shan wuyarki sosai a samun 'ya'ya; a cikin shan wuya za ki haifi 'ya'ya. Duk marmarinki zai zama domin mijinki, amma zai yi mulkin ki."17Ga Adamu yace, "Domin ka saurari muryar matarka, ka ci daga cikin itacen da na dokace ka cewa, 'Kada ka ci daga cikinsa,' saboda kai na la'anta ƙasa; ta wurin aiki mai zafi za ka ci daga cikinta dukkan kwanakin ranka.18Za ta fitar da ƙaya da sarƙaƙƙiya domin ka, za ka kuma ci tsire-tsiren ƙasar.19Ta wurin zufarka za ka ci gurasa, har sai randa ka koma turɓaya, domin daga cikinta aka ciro ka. Domin kai ƙura ne, ƙura kuma za ka koma."20Mutumin ya kira sunan matarsa Hauwa ita ce mahaifiyar dukkan rayayyu.21Yahweh Allah ya yi wa Adamu da matarsa sutura ta fatu ya rufe su.22Yahweh Allah yace, "Yanzu mutumin ya zama kamar ɗaya daga cikinmu, yana sane da mugunta da nagarta. To yanzu ba za mu taɓa barinsa ya sa hannunsa, ya tsinka daga itacen rai ba, ya ci, ya kuma rayu har abada."23Saboda haka Yahweh Allah ya fitar da shi daga cikin lambun Aidin, domin ya noma ƙasa wanda daga ita aka ciro shi.24To sai Allah ya kori mutumin daga lambun, ya sa kerubim a gabashin lambun Aidin da kuma takobi mai walƙiya dake jujjuyawa ta kowanne fanni, domin su yi tsaron hanya ta zuwa itacen rai.
Marubucin na fara wani sabon sashin labari.
"fi wayo" (UDB) ko "mai kaifin baki domin ya sanu abun ya ke so, ta wurin faɗin karya"
Macijin na wayancewa yana mamaki wai Allah ya ba da wannan doka. Ana iya fassara wannan tambayar ta lafazi a matsayin sanarwa. AT: "Ina makaki wai Allah ya ce, "Ku ... gona'"
Kalmar "ku" na nufin namijin da ta macen.
"muna da izinin ci" ko "an yarda mana mu ci"
Kalmar "ku" na nufin namijin da ta macen.
"Ba za ku ci ba" ko "kada ku ci"
"ba za ku kuma taɓa shi ba" ko "kuma kada ku taɓa"
Wannan na nufin namijin da ta mace su biyu.
"idanunku zai buɗe." Wannan karin magana na nufin cewa "za ku san abubuwa" ko "za ku fahimci sabobin abubuwa." Ana iya bayana wannan a fili. AT: "Zai kasance kamar cewa idanunku sun buɗe"
Anan "nagarta da mugunta" karin magana ne da ke nufi sanin farko da iyakar abu da komai da ke cikin abun. Dubi yadda aka juya "sanin nagarta da mugunta" a Farawa 2:9. AT: "sanin komai, na nagari da na mugunta"
"itacen na da kyau a duban idanu" ko "na da sha'awan kallo" ko "na da kyau ƙwarai" (UDB)
"ta kuma so 'ya'yan itacen domin ya na iya ba wa mutum hikima" ko "ta kuma so 'ya'yan domin 'ya'yan na iya sa ta fahimci abin da ke dai-dai da mumunar abu kamar yadda Allah ya sani"
"Sai idanunsu suka buɗe" ko "Suka sani" ko "Sun fahimta." Dubi yadda aka juya "idanunku za su buɗe" a cikin Farawa 3:4.
"lazimta" ko "ƙulle"
Idan mutane ba su san kamanin ganyayen ɓaure ba, ana iya juya wannan haka "manyan ganyayen daga itacen ɓaure" ko kuwa "manyan ganyaye." kawai
Sun yi haka domin su na kunya. Ana iya mayar da wannan magana a cikin sauki, idan ana bukata yin haka kamar a cikin UDB. AT: "suka kuma yi wa kansu sutura domin suna kunya"
"a lokacin iska mai sanyi na ranar"
"daga fuskar Allah Yahweh" ko "don kada Allah Yahweh ya iya ganin su" (UDB) ko "daga Allah Yahweh"
"Me ya sa ka na ɓuya daga gare ni?" (UDB). Allah ya san inda mutumin ya ke. Da mutumin ya amsa, ba ya faɗa inda ya ke ba daidai dalilin da da ya sa ya ɓuya.
A aya 9 da 11, Allah na magana da mutumin ne.
"Na ji motsin zuwar ka"
Allah ya san amsar wannan tambayan. Ya yi tambayan domin ya tilasta Adamu ya furta rashin biyayyar sa ga Allah.
Kuma, Allah ya san cewa haka ya faru. A juya wannan ta hanyar da zai nuna cewa Allah na dora wa Adamu laifin rashin biyayya. AT: "haƙika ka ci ... daga."
Allah ya riga ya san abin da macen ta aikata. Da yake tambayan nan, yana ba ta damar ta faɗa masa da kuma yana nuna rashin jin dadi abin da ta aikata. Harsuna da yawa na morar tambaya domin tsautawa. In akwai yadda za a nuna rashi jin dadin a yi amfani da shi. Ana iya fassara wannan tambayar ta lafazi a matsayin sanarwa. AT: "Kin aikata mummunar abu."
"kai kaɗai aka la'anta." Kalman "la'anta" ya fito a farkon maganar a harshen Ibraniyanci domin jadada bambancin albarkan da Allah ya sa wa dabbobin da wannan la'anta da ke akan macijin. Haka aka "saba la'anta", ko yadda ake faɗin kalmar la'antawa. Ta ambacin wannan la'ananci, Allah ya sa haka ya faru.
"duk dabbobin da ake kiwo a gida da na jeji"
"da ciki za ka dinga tafiya a ƙasa." Maganar "da cikin ka" ya zo a farkon maganar domin a jadada bambanci tsakanin yadda sauran dabbobi za su yi tafiya da kafafunsu amma macijin kuwa rub da ciki zai yi. Wannan na yadda a ka saba la'anta ne.
"ƙura za ka ci." "Turɓaya ne" ya zo a farkon maganar domin nuna bambancin tsire-tsire da sauran dabbobi za su ci da kuma datti da ƙurar da ke ƙasa da macijin zai ci. Wannan ma na yadda aka saba la'anan ne.
Wannan na nufin cewa macijin da macen za su zama abokan gãba.
Kalmar "zuriya" na nufin abin da na miji ya ke sa a cikin mace domin yaro ya girma a cikin ta. yadda kalmar yake, ya na iya nufin mutum ɗaya ne ko fiye. A nemi kalmar da zai iya bayana zuriya na iya zama ɗaya ko fiye ɗaya.
Kalmar "shi" da "sa" na nufin zuriyar matar. Idan kalmar "zuriya" na jam'i ne, ana iya juya shi haka "za su ƙuje ... diddigensu"; in ya kasance haka, ana iya sharihinta cewa "su" wakilin suna ne da nufin mutum ɗaya.
"murkushe" ko "boga" ko "farmaki"
"Zan ƙara zafin nuƙudarki" ko "Zan sa zafin naƙudarki ya zama da tsanani"
"ta haifan 'ya'ya" ko "a sa'ad da ki ke haifan 'ya'ya" (UDB)
"za ki kasance da matukar sha'awa ga mijinki." Mai yiwuwa ana nufi 1) "Za ki bukaci dayawa a gare mijinki" ko 2) "Za ki so ki sarrafa mijinki"
"zai kasance uban gidan ki" ko "zai yi sarrafa ki"
Adamu da "na miji" na da kalma ɗaya ne a harshen Ibraniyanci. Wasu juya na amfani da "Adamu" wasu kuma "na mijin." Ana iya amfani da kowane domin ana nufin mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "ka yi biyayya da abin da matar ka ta faɗa"
Ana iya faɗin abin da suka ci. AT: "ci daga 'ya'yan itacen" ko "ci daga wasu 'ya'yan itace"
Kalmar "la'anta" na zuwa a farkon maganar domin a jadada cewa, ƙasar da Allah ya ce na kyau a baya, na karkashin la'ana yanzu. AT: "Ina la'antar ƙasa"
"ta wurin aiki tuƙuru"
Kalmar "ta" na nufin ƙasa ne, kuma yana bayana sashin amfanin gona da ke girma a cikin ƙasa da mutane ke ci. AT: "za ka ci daga abin da ya girma a cikinta"
Mai yiwuwa ana nufi 1) "tsire-tsiren da ka ke nomar ta a gonar ka" ko 2) "tsire-tsiren da ke girma a filin jeji."
"Za ka yi zuffa da aiki tuƙuru"
Anan "gurasa" na nufi kowani irin abinci. AT: "za ka ci abinci"
"har mutuwarka, a kuma sa jikin ka a cikin ƙasa." Wasu al'adu na sa jikin wanda suka mutu a rami a cikin ƙasa. Wahalar aikin mutum ba ta karewa har sai lokacin mutuwarsa da biso.
"Da turɓaya ne na yi ka, haka kuma jikin ka zai zama turɓaya."
Wasu juyi sun ce "Adamu."
"ba wa matarsa suna Hauwa" ko "sa wa matarsa suna Hauwa" (UDB)
Masu juya wannan na iya sharihinta cewa "sunar Hauwa na kamar kalmar Ibraniyanci da ki nufi 'rayuwa.'"
Kalmar "rayayyu" na nufin mutane ne. AT: "dukka mutanen"
"kayansawa daga fatar dabbobi"
Mai yiwuwa ana nufi 1) Allah magana game da mutum ɗaya ne, na mijin, ko 2) Allah na magana game da mutane dukka, wato na miji da matan shi. Ko da mutum ɗaya ne Allah ke magana da, abin da ya faɗa ya shafe su dukka biyu.
"kamar mu." Wakilin sunan nan "mu" jam'i ce. Duba yadda aka juya "Bari mu yi" a Farawa 1:26.
Anan "nagarta da mugunta" ƙarin magana ne da ke nufin iyakar farko da karshen kowani abu da duk abin da ke tsakani. Dubi yadda aka juya "sanin nagarta da mugunta" a cikin Farawa 2:9. AT: "sanin komai, da nagarta da mugunta"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba zan yarda mi shi ba"
"itace da ke ba da rai."
"ƙura, dommin daga ƙura ya fito." Wannan baya nufin wani takamamen ƙasa ne da Allah a ɗauko mutumin.
"Allah ya tilasta mutumin ya bar cikin gonar." Wannan na bayana abin da ya faru a Farawa 3:22, inda ya ce " Allah Yahweh ya kori mutumin daga gonar Aidan." Ba wai Allah ya kori mutumin na biyu ba ne.
Wannan na nufin yin aikin da a ake bukata domin amfanin gona ta girma da kyau. juya wannan kamar a 2:4.
"domin ya tsayad da mutane daga zuwa itacen rai"
Mai yiwuwa ana nufi 1) takobi da ke da harshen wuta akai, ko 2) harshen wuta da kamar siffar takobi. harsuna da ba su da takobi na iya amfani da makami kamar mashi.
1Mutumin ya kwana da matarsa, sai ta yi ciki ta haifi Kayinu. Ta ce,"Na haifi mutum da taimakon Yahweh."2Sai ta sake haifar ɗan'uwansa Habila. Sai Habila ya zama makiyayi, amma Kayinu ya zama manomi.3Sai ya zamana wata rana Kayinu ya kawo wani sashe daga cikin amfanin gonar da ya noma daga ƙasa a matsayin baiko ga Yahweh.4Shi kuma Habila, sai ya kawo waɗansu 'ya'yan fari daga cikin garkensa da kuma sashe na kitse. Yahweh ya karɓi Habila da baikonsa,5amma Kayinu da baikonsa bai karɓa ba. Domin haka Kayinu ya fusata sosai, ya kuma ɓata fuska.6Yahweh yace da Kayinu, "Meyasa ka yi fushi meyasa fuskarka ta ɓaci haka?7In da ka yi abin dake nagari, da ba a karɓe ka ba? Amma in ba ka yi abin dake nagari ba, zunubi na ƙwanƙwasa ƙofa kuma marmarinsa shi ne ya mallake ka, amma dole ne ka yi mulkinsa."8Sai Kayinu ya yi magana da ɗan'uwansa Habila. Sai ya zamana a lokacin da suke cikin saura, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya kashe shi.9Daga nan Yahweh yace da Kayinu, "Ina ɗan'uwanka Habila?" Ya ce, "Ban sani ba. Ni makiyayin ɗan'uwana ne?"10Yahweh yace, "Me ka yi kenan? Jinin ɗan'uwanka yana kira na daga ƙasa.11Yanzu kai la'ananne ne daga ƙasar da ta buɗe baki ta karɓi jinin ɗan'uwanka daga hannunka.12Daga yanzu duk lokacin daka noma ƙasa, ba za ta baka issashen amfaninta ba. Za ka zama mai yawo barkatai a cikin duniya."13Kayinu yace da Yahweh, "Horona ya yi girma fiye da yadda zan iya ɗauka.14Hakika ka kore ni waje yau daga wannan ƙasa, zan kuma riƙa ɓuya daga fuskarka. Zan zama mai yawo barkatai a cikin duniya, kuma duk wanda ya same ni zai kashe ni."15Yahweh yace da shi, In har wani ya kashe Kayinu za ayi masa ramako har niki bakwai." Daga nan Yahweh ya sa alama a jikin Kayinu, domin in wani ya gan shi kada wannan mutumin ya kai masa hari.16Sai Kayinu ya tafi daga fuskar Yahweh ya zauna a ƙasar Nod, a gabashin Aidin.17Kayinu ya kwana da matarsa sai ta yi ciki ta haifi Enok. Ya gina birni ya bashi sunan ɗansa Enok.18Ga Enok sai aka haifa masa Irad. Irad ya zama mahaifin Mehuyawel. Mehuyawel ya zama mahaifin Metushawel. Metushawel ya zama mahaifin19Lamek. Lamek ya aura wa kansa mata biyu: sunan ɗayar Ada, ɗayar kuma sunanta Zilla.20Ada ta haifi Yabal. Shi ne mahaifin masu zama a cikin rumfuna waɗanda ke da dabbobi.21Ɗan'uwansa shi ne Yubal. Shi ne mahaifin makaɗan molo da algaita.22Ita kuma Zilla, ta haifi Tubal Kayinu, shi ne mai samar da kayayyaki na jan ƙarfe. 'Yar'uwar Tubal Kayinu ita ce Na'ama.23Sai Lamek yace da matansa, Ada da Zilla, ku saurari muryata; ku matan Lamek, ku saurari abin da na ce. Domin na kashe mutum saboda ya yi mani rauni, saurayi domin ya ƙuje ni.24In an saka wa Kayinu sau bakwai, to za a saka wa Lamek sau saba'in."25Sai Adamu ya sake kwana da matarsa, sai ta sake haifar wani ɗan. Sai ta kira sunansa Set, ta kuma ce, "Allah ya bani wani ɗan a madadin Habila, domin Kayinu ya kashe shi."26Aka haifa wa Set ɗa, sai ya kira sunansa Enosh. A wancan lokacin ne mutane suka fara kiran bisa sunan Yahweh.
"mutumin" ko "Adamu" (UDB)
Harshen ku na iya samun wata hanyar faɗin wannancikin ɗa'a. Wasu tsohon juyi sun amfani da "sani."
Kalmar "miji" na bayana mutum da ya yi girma, ba ɗan jariri ko yaro ba. Idan juya wannan haka zai kawo rikicewa, ana iya juya shi haka "yaro na miji" ko "yaro" "jariri na miji" ko "ɗa."
Masu juya na iya sharihinta cewa "sunar Kayinu na kamar kalmar da ke nufi a 'haifar' a harshen Ibraniyanci. Hauwa ta bashi sunar Kayinu domin ta haife shi ne."
Bamu da cikakiyar sanin sawon lokacin da ke tsakanin haifuwar Kayinu da Habila. Suna iya kasance tagwaye ne, ko kuma an haifi Habila bayan Hauwa'u ta sake ɗaukan ciki. In zai yiwu, a amfani da maganar da ba zai ba da takamamen tsawon lokaci ba tsakaninsu.
Wannan na nufin cewa yana yin duk abin da ake bukatar yi domin amfanin gona ta girma da kyau.
Wannan jimlar na sa alama ce wa farkon sashi na labarin. Idan harshen ku na da yadda ku ke faɗin wannan, kuna iya yin amfani da shi anan.
Mai yiwuwa ana nufin 1) "bayan tsawon wani lokaci" ko 2) "a dai-dai lokacin"
Wannan na nufin abinci da tsire-tsiren gonar ta haifar. AT: "girbi"
Wannan na nufi da sashin namar rago kitse ko ƙiba da ya kashe, bangare ne ma fi kyau a dabba. AT: "bangare mai ƙiba"
"kula" ko "ya gamsu da"
Wasu harsuna na da yadda suke bayana wannan kamar "zafi/ƙona" ko "ƙonewa da hushi."
Wannan na bayana yadda fuskar sa ya nuna hushinsa da kishi. Wasu harsuna na da yadda suke bayana fuskar wanda ya ke hushi.
Allah ya yi amfani da wannan tambayoyi domin ya nuna wa Kayinu cewa ba dai-dai ba ne ya husata ya kuma sa tsikar jikinsa ta tashi. Mai yiwuwa kuma suna ba wa Kayinu zarafi ne ya furta cewa ya yi laifi ne.
Allah ya yi amfani da wannan tambaya domin ya tunashe Kayinu game da abin da yakamata a ce ya sani. AT: "Ka san cewa in da ka aikata abin da ya ke daidai, ai da na karɓe ka"
Allah na magana game da zunubi kamar wani mutum ne. AT: "Amma idan ba ka bidar aikata abin da ke dai-dai, to za ka bida ka aikata zunubi, kuma za ka yi abin da ke na zunubi. Tilas ne ka ki yin biyayya da shi"
Ana magana game da zunubi anan kamar wani mugun dabba jeji ne da fakon kai hari wa Kayinu. AT: "Za ka cika da hushi har za ka gagara kin aikata zunubi"
Harsuna da ba su da suna da ke bayana "zunubi" na iya juya wannan kamar "sha'awar aikata zunubi" ko "mumunar abubuwan da ka ke so ka yi."
Yahweh na magana game da sha'awar aikata zunubi da Kayinu ke yi kamar wani mutum ne da Kayinu zai yi mulkin shi. AT: "dole ka mallake shi domin kar ka yi zunubi"
Wasu harsuna na iya bukatar takamamen bayanin abin da Kayinu ya ce wa ɗan'uwansa game da tafiyarsu ciki saura.
Habila ƙanin Kayinu ne. Wasu harsuna za su bukaci amfani da kalmar "ƙani."
"kai hari"
Allah ya san cewa Kayinu ka kashi Habila, amma ya tambayeshi domin ya amsa.
Kayinu ya yi amfani da tambaya domin ya guje wa faɗin gaskiya. AT: "Ni ba makiyayin ɗan'uwana ba ne!" ko "Aikina ba kiwon ɗan'uwana bane!"
Allah ya yi amfani tambaya domin ya tsauta wa Kayinu. AT: "Ka aikata mumunar abu!"
Jinin Habila na matsayin mutuwar sa, kamar mutum ne na kiran Allah ya horar da Kayinu. AT: "Jinin ɗan'uwanka na kira kamar mutum ne da ya ke so in horar da mutumin da ya kashe shi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ina la'ance ka, ba za ka iya nomar abinci daga ƙasa ba"
Allah na magana game da ƙasar kamar wani mutum ne da zai iya shan jinin Habila. AT: "da ke jike da jinin ɗan'uwanka"
Allah na magana game da hannun Kayinu kamar hannun ya zuba jinin Habila a "bakin" ƙasa. AT: "da ya zub a sa'ad da ka kashe shi" ko "daga gare ka"
Wannan na nufin yin duk abin da ake bukata domin amfanin gona ta girma da kyau.
An yi maganar ƙasa kamar mutum ne da karfinsa na kasawa. AT: "ƙasar ba za ta ba ka abinci ba"
Ana iya haɗa waɗannan kalmomin tare. AT: "Mai yawo barkatai mara gida"
Kalmar "fuskarka" na nuna gaban Allah. AT: "ba zan iya magana da kai ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "zan ɗau ramako akan shi sau bakwai" ko "Zan hukunta mutumin sau bakwai fiye da hukuncin ka"
"ba zai kashe Kayinu ba"
Koda yake Yahweh yana ko'ina, wannan maganar na nuna kamar cewa Kayinu ya tafi wani wuri mai nisa. AT: "tafi daga inda Yahweh yayi masa magana"
Mai juya wannan na iya sharihinta cewa "Kalmar Nod na nufin "yawo barkatai."
Harshen ku na iya samun wata hanyar faɗin wannancikin ɗa'a. Wasu tsohon juyi sun amfani da "sani."
"Kayinu ya gina birni"
Wannan na nuna cewa Enok ya girma kuma ya aure wata mace. AT: "Enok ya girma kuma ya yi aure, sanan ya haifi ɗa wanda ya kuma kira shi Irad"
"Irad ya haifi ɗa ya kuma kira shi Mehuyawel"
Waɗannan sunayen mata ne
Mai yiwuwa ana nufi 1) "Shi ya zama na farko da ke zama a cikin rumfuna" ko 2) " Shi da zuriyarsa sun zauna a cikin rumfuna."
mutanen da suke zama cikin alfarwa suna kuma kiwon dabbobi
Mai yiwuwa ana nufi 1) "shi ne ya zama na farkon zama makaɗin molo da algaita" ko 2) "Shi da zuriyarsa ne suka zama makaɗan molo da algaita."
"Tubal-Kayinu. Shi ne maƙeran tagulla da kayayyakin ƙarfe"
Wannan wani ƙarfe ne mai karfi wanda ake amfani wajen yin kayayyakin ƙarfe, da makamai.
Lamek ya faɗa wannan sau biyu domin ya jadada abin da ya ce. Muryar na nufin shi gaba ɗaya. AT: "saurare ni a hankali"
Lamek ya kashe mutum ɗaya.
"domin ya yi mini rauni ... ya kuma buge ni" ko "domin ya ji mini ciwo"
Lamek ya san cewa Allah zai rama wa Kayinu sau bakwai. AT: "Da shike Allah zai hukunta sau bakwai duk wanda ya kashe Kayinu, Lamek"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah zai hukunta sau saba'in da bakwai, duk wanda ya kashe ni"
"77"
Harshen ku na iya samun wata hanyar faɗin wannancikin ɗa'a. Wasu tsohon juyi sun amfani da "sani."
Wannan shi ne dalilin da ya sa ta kira sunansa Set. AT: "ta kuma bayana cewa "Allah ya sake ba ni ɗa."
Masu juya na iya sharihinta cewa "Wannan sunan na kamar kalmar da ke nufi "an bayar" a harshen Ibraniyanci."
Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "matar Set kuwa ta haifar masa ɗa"
A wannan lokacin ne mutane suka fara kiran Allah da sunan Yahweh. Ana iya sa wannan a sarari cewa. AT: "yi wa Allah sujada ta wurin kiran sa Yahweh"
1Wannan shi ne lissafin zuriyar Adamu. A ranar da Allah ya hallici mutum, ya yi su a cikin kamanninsa.2Namiji da mace ya hallice su. Ya albarkace su ya basu suna mutane a lokacin da ya hallice su.3Da Adamu ya yi shekaru130 sai ya zama mahaifin ɗa a cikin kamanninsa sai ya kira sunansa Set.4Bayan Adamu ya haifi Set, ya yi rayuwa tsawon shekaru ɗari takwas. Sai ya zama mahaifin waɗansu 'ya'ya maza da mata masu yawa.5Adamu ya yi rayuwa har shekaru 930 daga nan ya mutu.6Da Set ya yi shekaru 105, sai ya haifi Enosh.7Bayan ya haifi Enosh, ya rayu har tsawon shekaru 807 ya zama mahaifin 'ya'ya maza da mata da yawa.8Set ya rayu har shekaru 912 daga nan ya mutu.9Bayan Enosh ya rayu na tsawon shekaru tasa'in, sai ya haifi Kenan.10Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya rayu na tsawon shekaru 815. Sai ya haifi waɗansu 'ya'ya maza da mata masu yawa.11Enosh ya rayu tsawon shekaru 905 daga nan ya mutu.12Da Kenan ya yi shekaru saba'in, sai ya haifi Mahalalel.13Bayan ya haifi Mahalalel, Kenan ya yi shekaru 840. Sai ya haifi sauran waɗansu 'ya'ya maza da mata.14Kenan ya rayu na tsawon shekaru 910, daga nan ya mutu.15Mahalalel ya rayu shekaru sittin da biyar, sai ya haifi Yared,16Mahalalel yana da shekaru 830. Sai ya haifi sauran 'ya'ya maza da mata masu yawa.17Mahalalel ya rayu na tsawon shekaru 895, daga nan ya mutu.18Da Yared ya yi shekaru 162, sai ya haifi Enok.19Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru ɗari takwas. Sai ya haifi waɗansu 'ya'ya maza da mata.20Yared ya rayu na tsawon shekaru 962, daga nan ya mutu.21Da Enok ya yi shekaru sittin da biyar, sai ya haifi Metusela.22Enok ya yi tafiya tare da Allah shekaru ɗari uku daga nan ya haifi Metusela, ya kuma haifi waɗansu 'ya'ya maza da mata.23Enok ya yi shekaru ɗari uku da sittin da biyar.24Enok ya yi tafiya tare da Allah, daga bisani ya tafi, domin Allah ya fyauce shi.25Da Metusela ya yi shekaru 187, ya haifi Lamek.26Bayan ya haifi Lamek, Metusela ya yi shekaru 782. Sai ya haifi waɗansu 'ya'ya maza da mata.27Metusela ya rayu na tsawon shekaru 965 daga nan ya mutu.28Bayan ya yi shekaru182, sai ya haifi ɗa.29Sai ya kira sunansa Nuhu, yana cewa, "Wannan zai bamu hutu daga aikinmu daga kuma aikin hannuwanmu mai wuya, da zamu yi saboda Allah ya la'anta ƙasa."30Lamek ya yi shekaru 595 daga nan ya haifi Nuhu. Daga nan ya haifi sauran 'ya'ya maza da mata.31Lamek ya rayu na tsawon shekaru 777, daga nan ya mutu.32Bayan Nuhu ya yi shekaru ɗari biyar, sai ya haifi Shem, da Ham, da Yafet.
Wannan shi ne farin jerin zuriyar Adamu
Wannan jimlar na nufin Allah ya yi mutum ya zama kamar shi. Wannan ayan bai faɗa ko ta wace hanya ne mutane suke kama da Allah ba. Ba a nufin cewa muna kamar shi a jiki domin Allah ba shi da jiki. AT: "kasance cikin gaskiyar kamanin mu." Duba yadda aka juya "cikin kamaninmu" a Farawa 1:26.
Ana iya sanya wannan aiki. AT: "sa'ad da ya halicce su"
Masu juyi na iya rubuta lamba "130" da "800" ko kuma a cikin kalma "ɗari da talatin" da "ɗari takwas."
"yana da ɗa"
Waɗannan kalmomi na nufin abu ɗaya ne. An yi amfani da su ne domin a tunin cewa Allah ya yi mutum cikin siffarsa. Duba yadda aka juya irin wannan maganar a Farawa 1:26.
"Ya sami 'ya'ya maza da mata"
za a yi ta maimaita wannan maganar a cikin wannan surar. Yi amfani da kalmar da aka fi sanin "mutuwa."
Mutane na da tsawon shekaru a wancan lokacin. Yi amfani da kalmar da aka saba wa "shekaru." AT: "Iyakar rayuwa Adamu shi ne shekara 930"
"Mahaifi" anan na nufin asalin mahaifinsa, ba kakanshi ba. AT: "Ya sami ɗansa Enosh."
"ya kuma kara samin 'ya'ya maza da mata"
"Iyakar rayuwar Set shi ne shekara 912"
Za a yi ta maimaita wannan maganar a cikin wannan surar. Yi amfani da kalmar da aka fi sanin "mutuwa."
Abubuwan da aka rubuta a cikin Farawa 5: 6-27 suna da tsari iri ɗaya. Fassara su gwargwadon bayanan da ke cikin Farawa 5: 6
Abubuwan da aka rubuta a cikin Farawa 5: 6-27 suna da tsari iri ɗaya. Fassara su gwargwadon bayanan da ke cikin Farawa 5: 6
Abubuwan da aka rubuta a cikin Farawa 5: 6-27 suna da tsari iri ɗaya. Fassara su gwargwadon bayanan da ke cikin Farawa 5: 6
Abubuwan da aka rubuta a cikin Farawa 5: 6-27 suna da tsari iri ɗaya. Fassara su gwargwadon bayanan da ke cikin Farawa 5: 6
"ya sami ɗansa Metusela"
Wannan sunan na miji ne.
Yin tafiya tare da wani na bayana kusancewar dangantakar su tare. AT: "Enok ya kusance Allah" ko "Enok ya yi zama zumunta da Allah"
"Ya kara samun 'ya'ya maza da mata"
"Iyakar rayuwar Enok shi ne shekara 365"
Kalmar "ya" na nufin Enok. Ba ya nan a duniya kuma.
Wannan na nufin cewa Allah ya ɗauke Enok zuwa wurin sa (Allah).
Abubuwan da aka rubuta a cikin Farawa 5: 6-27 suna da tsari iri ɗaya. Fassara su gwargwadon bayanan da ke cikin Farawa 5: 6 .
"ya sami ɗa"
Masu juya wannan na iya sharihinta cewa "Wannan sunan na kamar kalmar da ke nufi "hutu" a Ibraniyanci." .
Lamek ya maimaita wannan domin ya jadada irin wahalar aikin. AT: "daga aiki wahala da hunnuwanmu"
"Iyakar rayuwar Lamek shi ne shekara 777"
"ya sami 'ya'yansa maza." Wannan bai bayana mana ko an haife 'ya'yan a rana ɗaya ne ko shekaru dabam dabam.
Ba lalle ne wai an jera sunayen 'ya'ya bisa ga haifuwarsa ba. Akwai bambancin ra'ayi game da wanene babba. A kauce wa juya wannan ta hanyar da zai nuna kamar jerin na bisa shekaran su.
1Sai ya zamana da mutane suka fara ruɓamɓanya a duniya aka kuma haifa masu 'ya'ya mata,2sai 'ya'yan Allah suka ga 'ya'yan mutane na da ban sha'awa. Sai suka auri mata daga cikinsu, dukkan su da suka zaɓa.3Yahweh yace "Ruhuna ba zai dawwama a cikin mutum ba har abada, domin su jiki ne. Za su rayu shekaru 120 ne."4A waɗancan kwanakin akwai ƙarfafan mutane sosai, kuma haka ya faru ne bayan 'ya'yan Allah sun auri 'ya'ya mata na mutane, sun kuma sami 'ya'ya tare da su. Waɗannan sune manyan mutanen dã can, mutane masu jaruntaka.5Yahweh ya ga muguntar mutum ta haɓaka a duniya, kuma dukkan tunane-tunanen zuciyarsa kullum mugunta ce.6Yahweh ya yi takaicin halitar mutum a duniya, kuma abin ya dame shi a zuciyarsa.7Domin haka Yahweh yace,"Zan shafe mutum wanda na halitta daga fuskar duniya; mutum da manyan dabbobi, da abubuwa masu rarrafe da tsuntsayen sammai, domin na yi takaici dana halicce su."8Amma Nuhu ya sami tagomashi a idanun Yahweh.9Waɗannan sune abubuwa game da Nuhu. Nuhu adalin mutum ne, kuma ba shi da abin zargi a cikin mutanen kwanakinsa.10Nuhu yayi tafiya tare da Allah. Nuhu ya haifi 'ya'ya uku: Wato Shem da Ham da Yafet.11Duniya ta ƙazanta a gaban Allah, ta kuma cika da hargitsi.12Allah ya ga duniya; duba, ta gurɓanta, domin dukkan mutane sun ɓata tafarkinsu a duniya.13Allah yace da Nuhu, Na ga cewa lokacin ƙarshen dukkan hallita ya yi domin duniya ta cika da hargitsi ta wurin su, hakika, zan hallaka su tare da duniya.14Ka yi wa kanka jirgi da itacen sida ka yi ɗakuna a cikin jirgin, ka rufe shi ciki da waje.15Ga fasalin yadda zaka yi shi: tsawon jirgin kamu ɗari uku, faɗinsa kamu hamsin, bisansa kamu talatin.16Ka yi wa jirgin rufi, ka kuma kammala shi ka dalaye shi daga sama har ƙasa. Ka sa ƙofa ta gefen jirgin, ka yi masa matakala, ƙarama, da ta biyu, da kuma matakala ta uku.17Ka saurara, Na kusa kawo ambaliyar ruwa a duniya domin in hallakar da dukkan masu rai dake da numfashi rai dake a ƙarƙashin sama. Duk abin dake a duniya zai mutu.18Amma zan kafa alƙawarina da kai. Zaka shiga cikin jirgin, da kai da 'ya'yanka da matarka da matan 'ya'yanka tare da kai.19Da dukkan hallitu masu rai, kowanne iri biyu dole ne kuma ka shigar dasu cikin jirgin, ka ajiye su, su tsira tare da kai, dukkan su namiji da mace.20Da tsuntsaye bisa ga irinsu, da manyan dabbobi bisa ga irinsu, dukkan wani abu mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinsu, biyu daga cikin kowanne iri daga cikinsu za su zo tare da kai, domin ka tsirar da rayukansu21Ka kuma yi wa kanka tanadin kowanne irin abinci na ci ka adana shi, domin ya zamar maka abinci da kuma dominsu."22Sai Nuhu ya yi wannan. Bisa yadda Allah ya umarce shi, haka ya yi.
An yi amfani da wannan maganar domin ba da alamar wani sabon sashi na labarin. Idan akwai yadda harshenku ke faɗin wannan, ana iya yanke shawaran amfani da shi anan.
Wannan na iya zama mai aiki. AT: "matan suka haifi 'ya'ya mata"
Masu juya wannan na iya sharihinta cewa: "Ba a bayana a fili ko wannan na nufi 'yan Adam ne ko halittu sama. Ko da wannene, duk dai Allah ne ya halicce su." Wasu sun gaskanta cewa waɗannan fadadun mala'iku ne da suka yi wa Allah tawaye, watu, mugayen ruhohi ko aljanu. Wasu na tunanin cewa ana nufin manya masu ikon mulki, wasu kuma suna tunani ana nufin da zuriyar Set ne.
Anan Yahweh na magana game da kan shi da ruhunshi, wato Ruhun Allah.
Wannan na nufi da jikin mutum ne mai mutuwa.
Mai yiwuwa ana nufi 1) zaman rayuwan mutane zai ragu zuwa shekara 120. AT: "kwanakin su ba zai haye shekara 120" ko 2) cikin shekara 120 kowa za mutu. AT: "Iyakar kwanakin rayuwarsu she ni shekara 120"
manyan mutane, masu tsayi
"An haifi manya manyan mutanen domin"
"Wadannan ƙarfafan sune ƙarfafan da suka rayu dã can" ko "wadannan yaran ne suka girma suka zama mayaƙa da suka rayu dã can"
maza masu kwarin gwiywa da nasara cikin yaƙi
"shahararun mutane"
"hali" ko "dabi'a"
Marubucin na maganar zuciya kamar shi ne yanki daga cikin mutum da yin tunani. Harsheku na iya amfani da wani yanki jiki da ke sa mutane tunani ba dole sai "zuciya" ba. AT: "cikin sirri tunaninsu"
Marubucin na maganar zuciya kamar shi ne sashin jiki mutum da ke yin baƙin ciki.Harshenku na iya amfani da wani yanki jiki domin nuna yadda mutum ke ji. AT: "ya yi baƙin ciki kwarai da gaske game da haka"
Marubucin na maganar yadda Allah zai hallakar da mutane kamar Allah na share datti daga kan shimfiɗaɗɗe abu. AT: "Zan hallakar da mutum ... ba za a sami ko mutum ɗaya ba a fuskar duniya"
Wasu harsuna na iya bukacin a juya wannan a jimla biyu. AT: Na halicce mutum. Zan kuma shafe su"
"hallakar dukka." Ana maganar "shafewa" anan ta mumunar hanya, domin Allah na maganar hallakar da mutane domin zunuban su.
Nuhu ya sami alfarma a gaban Yahweh" ko "Yahweh ya ji daɗin Nuhu" (UDB)
"idannu" anan na matsayin gani ko tunani. AT: "A wurin Yahweh" ko "a zuciyar Yahweh"
Wannan ne farkon labarin Nuhu, da ya ci gaba har zuwa sura 9.
"Wannan shi ne labarin Nuhu"
Juya wannan kamar yadda aka yi a cikin Farawa 5:21.
"Nuhu ya sami 'ya'ya uku" ko "matar Nuhu na da 'ya'ya uku"
Masu juya wannan na iya sharihinta cewa "ba a bisa girman 'ya'ya ne aka rubuta sunayen su ba."
Mai yiwuwa ana nufi 1) mutanen da suka kasance a duniya, ko 2) "ƙasan duniyar kanta."
An yi magana game da mutanen da suke aikata mugunta kamar abincin da ya ɓace. AT: "ya ɓace" ko "cika da mugunta"
Mai yiwuwa ana nufi 1) "a fuskar Allah" ko 2) "A fuskar Yahweh" kamar a cikin Farawa 4:16.
Marubucin na maganar mugunta kamar wani abu da ake iya zuba a cikin bokiti, duniya kuma kamar ita ce bokitin. AT: akwai kuma mugayen mutane cike a duniyan" ko "domin tana cike da mutanen da suka wa juna mugunta"
Kalmar "ga shi" na jawo hankalin mu ne domin sauraron abin mamaki da zai biyo.
Mai yiwuwa ana nufi 1) dukka 'yan Adam, ko 2) duk rayayu, mutane da dabbobi.
An yi magana game da yadda halin mutane yake kamar wani hanya. AT: "daina rayuwa yadda Allah yake so" ko "aikata hanyar mugunta" (UDB)
"dukka mutanen da suke a duniya mugaye ne"
"Zan hallakar da su, har kuma da duniya" ko "Zan hallakar da su a sa'ad da ina hallakar da duniya"
Wannan na nufin babban akwati da zai iya tafiya akan ruwa ko da bakin ƙwarya. "babban kwalekwale" ko "babban jirgin ruwa"
Mutane ba su san asalin ko wace irin itace ba ne wannan. "itacen da ake gina jirgin ruwa" ko "itace mai kyau"
"yaɗa ƙaro a akai" ko "shafa kwalta akai." Ana iya bayana dalilin yin haka a fili cewa: "domin ya hana ruwa shiga"
Wannan wani mai ne da kauri yana kuma mannewa, mutane na sa wa jirgin ruwa domin hana ruwa shiga tsakanin tazarar itacen.
wannan ma auni ne da ya ka sa rabin mita.
"mita ɗari da talatin da takwas." Ana iya amfani da yadda Ibraniyawa suke awo a ULB ko tsarin awo a UDB, ko kuma in harshenku na da yadda ku ke auna abu kuma za iya kwatantawa da tsarin awo. Ana iya sharihinta cewa: "kafa ɗari huɗu na kusan mita ɗari da talatin da takwas."
"mita ashirin da uku"
"mita goma sha huɗu"
Wannan na iya yiwuwa shimfiɗaɗɗe jinka ko mikakke. An yi haka ne domin hana ruwa shigan jirgin daga kowani hanya.
"hawa na ƙasa, na tsakiya, da na sama" ko "hawa uku a ciki" (UDB)
"kan ɗaki" ko "hawa"
Allah ya faɗi haka domin ya jadada cewa zai aikata abin da so faɗa. "saurara" ko "ka ji abin da nake faɗi"
"Ina shirin kawo ambaliyan ruwa" ko "Ina shirin in sa ambaliya"
Wannan na matsayin dukka rayayu, da mutane da dabbokin
Anan "numfashi" na matsayin rai. AT: "da ke rayaye"
sa alƙawari tsakaninka da ni"
da Nuhu
"Zaka shiga jirgi." Wasu fassarar sun ce "Za ku shiga cikin jirgi."
"Lalle ne ka shigar da kowane irin halitta mai rai cikin jirgin, su biyu biyu"
dabban da Allah ya halitta
"na kowani iri"
Wannan na nufin 'yan kananan dabbobin da suke motsi a ƙasa (UDB).
Wannan na nufin biyu biyu a cikin kowani irin tsuntsaye da dabbobi.
"domin ka rayar da su"
Waɗannan na nufin Nuhu ne shi kadai.
"abincin da mutane da dabbobi suke ci"
Waɗannan jimla biyun na nufin abu ɗaya ne. na farkon na kara bayana na biyu da kuma jadada cewa Nuhu ya yi biyayya da Allah. Ana iya mayar da wannan jimla ta wata hanya. AT: "Nuhu kuwa ya yi dukka abin da Allah ya umurce shi ya yi"
1Yahweh yace da Nuhu, "Ka zo, da kai da dukkan gidanka, zuwa cikin jirgin, domin na ga kai mai adalci ne a gabana a wannan tsara.2Da dukkan dabbobi masu tsarki tare da kai, maza bakwai mata bakwai. Daga dukkan dabbobi marasa tsarki ka ɗauko biyu-biyu.3Hakanan daga tsuntsayen sararin sama, ka kawo maza bakwai da mata bakwai daga cikinsu, domin a tanadi irinsu a faɗin duniya.4Domin a rana ta bakwai zan sa a yi ruwa a dukkan duniya har kwana arba'in dare da rana. Zan hallakar da dukkan masu rai dana halitta daga fuskar duniya"5Nuhu ya yi dukkan abin da Yahweh ya umarce shi.6Nuhu yana da shekaru ɗari shida a lokacin da aka yi ruwan tsufana a duniya.7Da Nuhu, da 'ya'yansa maza, da matarsa, da matan 'ya'yansa maza suka shiga jirgin saboda ruwan tsufana.8Dabbobi masu tsarki da tsuntsaye da duk abu mai rarrafe a ƙasa,9biyu-biyu, namiji da mace, suka zo wurin Nuhu suka shiga akwatin, kamar yadda Allah ya umarci Nuhu.10Sai ya zamana bayan kwanaki bakwai, ruwan tsufana ya sauko a duniya.11A shekaru ɗari shida na Nuhu, a wata na biyu, a ranar sha bakwai ga wata, a dai wannan ranar, sai dukkan taskoki na zurfafa suka buɗe suka fashe, sakatun sama suka buɗe,12Ruwa ya fara sauka a duniya har kwanaki arba'in dare da rana.13A wannan ranar dai Nuhu da 'ya'yansa, Shem da Ham da Yafet da matar Nuhu, da matan 'ya'yan Nuhu uku na tare da su, suka shiga jirgin.14Suka shiga tare da dukkan dabbobin jeji kowanne bisa ga irinsa, da kuma kowacce irin dabba ta gida bisa ga irinta, da kuma duk abu mai rarrafe da kowaɗanne irin tsuntsaye bisa ga irinsu, da dukkan wata hallitta mai fuka-fukai.15Biyu daga dukkan hallitar dake da numfashin rai suka shiga jirgin tare da Nuhu.16Dabbobi da dukkan hallitun da suka shiga sun shiga ne kamar yadda Allah ya umarce shi. Sai Yahweh ya kulle ƙofar bayan sun shiga.17Sai ruwan tsufana ya sauko a duniya kwanaki arba'in, ruwan kuma ya ƙaru ya ɗaga akwatin sama da ƙasa.18Ruwa ya rufe duniya gaba ɗaya jirgin kuma yana ta lilo a saman ruwa.19Ruwa ya tumbatsa sosai a duniya har ya rufe dukkan duwatsu dake ƙarƙashin sama.20Ruwan ya kai har taki shida a bisa duwatsu21Dukkan halittu dake motsi bisa duniya suka mutu; tsuntsaye, da dabbobin gida dana daji, dukkan dabbobi dake da yawa waɗanda ke duniya da kuma dukkan mutane.22Da dukkan hallitun dake bisa ƙasa, waɗanda ke da numfashin rai a hancinsu, suka mutu.23Kowanne abu mai rai dake bisa duniya an shafe su, daga mutane ya zuwa manyan dabbobobi, da duk masu rarrafe, ya zuwa tsuntsayen sama. Dukkan su an hallakar da su daga duniya. Sai Nuhu da waɗanda ke tare da shi ne suka rage.24Ruwan bai janye daga ƙasa ba har kwanaki ɗari da hamsin.
Abubuwan da suka faru a wannan surar na bayan da Nuhu ya gina jirgin ruwan, ya tara abinci, ya kuma sa a cikin jirgin.
"shiga ... cikin jirgin ... ɗauki." Yawancin fassara sun karanta "Ku tafi ... cikin jirgin ... ɗauki."
kalmar "ka" na nufin Nuhu ne shi kadai.
"iyalinka"
Wannan na nufin da cewa, Allah ya ga cewa Nuhu adali ne.
Wannan na nufi dukkan mutane da suke a raye a waccan lokacin. AT: "a cikin dukka mutane da suke a raye yanzu"
Wannan dabba ne da Allah ya yaddar wa mutanen sa su ci, su kuma yi hadaya.
Wannan dabbobi ne da Allah baya yaddar wa mutane sa su ci ba ko su yi hadaya da su.
"domin su sami irinsu da zasu rayu" ko "domin bayan ambaliyan, dabbobi su ci gaba da rayuwa"
Wannan na nufin kwanaki arba'in. Ba wai kwanaki tamanin ba ne in a hada. AT: "yini da dare arba'in"
Wannan na nufin jiki mai rai.
Ayoyi na 6-12 sun maimaita a karo na biyu kuma suna ba da ƙarin haske game da yadda Nuhu ya shiga cikin jirgi tare da iyalinsa da dabbobin a cikin Farawa 7: 1-5. Wannan ba sabon abu bane.
"faru" ko "zo a duniya"
"domin ambaliyan ruwa da ke zuwa" ko "guje wa ambaliyan ruwan"
Ayoyi na 6-12 sun maimaita a karo na biyu kuma suna ba da ƙarin haske game da yadda Nuhu ya shiga cikin jirgi tare da iyalinsa da dabbobin a cikin Farawa 7: 1-5. Wannan ba sabon abu bane.
Waɗannan dabbobi ne da Allah ya yaddar wa mutanen sa su ci, su kuma mika masa hadaya
Wannan dabbobi ne da Allah baya yaddar wa mutane sa su ci ba ko su yi hadaya da su.
Dabbobin suka shiga jirgin biyu-biyu, na miji da ta mace.
Ana amfani da wannan maganar domin a ba da alama ne a cikin labarin: farin ambaliyan. Idan harshenku na da hanya yin wannan, ana iya yin amfani da shi a nan.
"bayan kwanaki bakwai"
Bayyanin wannan maganar a fili shi ne, "aka fara ruwan sama"
Ayoyi 6-12 na maimaita sau na biyu ne da kuma ba da bayyani filla-filla game da yadda Nuhu ya shiga jirgin da iyalinsa da kuma dabbobin a cikin 7:1. Wannan ba sabon aukuwa ba ne.
"A sa'd da Nuhu na shekaru 600"
Tun da shike Musa ne marubucin wannan littafi, ya yiwu yana nufin wata na biyu a kalanda Ibraniyawa, amma ba a tabbatar da wannan ba.
Wannan na nufin takamamen ranar da ruwan ta fara. Wannan maganar na nanata yadda waɗannan abubuwan suka faru nan da nan a sa'ad da lokaci ya kai.
"ruwayen karkashin duniya suka gaggauto zuwa farfajiyar saman duniya"
Wannan na nufin teku da ake tsammanin na karkashin duniya.
Wannan na nufin ruwan sama. Wannan na bayana sararin sama kamar rufi ne da ke hana ruwan da ke sama daga saukowa a duniya. A sa'ad da tagogi ko kofofin da sararin sama suka buɗe, sai ruwa ta sauko ta cikin su. AT: "sararin sama ta buɗe" ko "kofofin sama suka buɗe"
Idan harshenku na da kalma wa ambaliyan ruwa, zai dace a nan.
Ayoyi na 6-12 sun maimaita a karo na biyu kuma suna ba da ƙarin haske game da yadda Nuhu ya shiga cikin jirgi tare da iyalinsa da dabbobin a cikin Farawa 7: 1-5. Wannan ba sabon abu bane.
"a ainihin ranan nan." Wannan na nufin ranar da aka fara ruwan. Ayoyi 13-16 na faɗin abin da Nuhu ya yi nan da nan kafin ruwan ta fara.
Waɗannan kungiyoyi huɗu na nuna cewa dukka dabbobi na ciki. Idan harshen ku na da wata hanyar kasa dabbobi a sashi sashi ana iya amfani da shi, ko a yi amfani da wannan kashi. dubi yadda aka juya wannan a Farawa 1:24.
Wannan na nufin dabbobin da suke jan jiki a ƙasa kamar, jaba, ƙwaro, kaɗangare, da maciji.
"domin kowace irin dabba ta iya haifar da irinta." Duba yadda aka fassara wannan a cikin Farawa 1:24.
Ayoyi na 13-18 sun maimaita a karo na uku kuma sun ba da ƙarin haske game da yadda Nuhu ya shiga cikin jirgi tare da iyalinsa da dabbobi a cikin Farawa 7: 1-5. Wannan ba sabon abu bane.
A nan "nama" a nufin dabbobi ne.
A nan "numfashi" na nufin rai. AT: "da ke raye"
Ana iya fassarar kalmar "zo" kamar "tafi."
A nan "halittu" na nufin dabbobi. AT: "na kowace irin dabba"
Cikakiyar ma'anar wannan na bayane a fili. AT: bayan suka shiga jirgin"
Ayoyi na 13-18 sun maimaita a karo na uku kuma sun ba da ƙarin haske game da yadda Nuhu ya shiga cikin jirgi tare da iyalinsa da dabbobi a cikin Farawa 7: 1-5. Wannan ba sabon abu bane.
Wannan ya faru ne lokacin da ruwan ya cigaba da zuwa a kwanaki arba'in. "ruwan kuwa ya yi zurfi"
"ya kuma sa jirgin yana lilo"
"sa jirgin ya taso a sama ya bar ƙasa" ko "jirgin na ta lilo a saman ruwan mai zurfi"
"Ruwan ya mamaye duniyan gaba ɗaya"
"gantali" ko "yawo"
Wannan na nufin dukka garkin dabbobi da suke yawo a ƙasa.
A nan "hanci"na matsayin dukka dabbobi da mutane. AT: "kowa da kowa da ke numfashi"
Kalmomin nan "numfashi" da "rai" da matsayin ikon sa mutane da dabbobi su kasance a raye.
Wannan na nufin mutuwa ta jiki.
Idan ya cancanta, ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kowane abu mai rai ... sun hallaka" ko "Ambaliyan ya hallakar da kowane abu mai rai gaba ɗaya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ya hallakar da su dukka"
"ba su nan kuma a duniya"
"da mutanen da dabbobin da suke tare da shi"
"ragowa" ko "rayu" ko "rage da rai" (UDB)
"Zurfin ruwan ya maimaye dukka duniya" ko " ruwan ya kasance a duniya" (UDB)
1Sai Allah ya yi la'akari da Nuhu, da dukkan dabbobin jeji, da dukkan dabbobin gida dake tare da shi a cikin jirgin ruwan. Allah ya sa iska ta hura a kan ƙasa, sai ruwaye suka fara sauka ƙasa.2Maɓuɓɓugai na ƙarƙas da sakatun sama aka rufe su, ruwa kuma ya ɗauke.3Ambaliyar ruwa kuma ta kwanta sannu a hankali daga ƙasa, bayan kuma kwanaki ɗari da hamsin, sai ruwa ya yi ƙasa.4Sai jirgin ruwan ya sami sauka a wata na bakwai, a ranar sha bakwai ga wannan watan, a kan duwatsun Ararat.5Ruwan ya ci gaba da sauka har wattanni goma. A rana ta farko ta watan, sai ƙonƙolin duwatsu suka bayyana.6Sai ya zamana bayan kwanaki arba'in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin ruwan da ya yi.7Ya aiki hankaka ya yi ta kai da komowa har sai da ruwa ya tsane daga duniya.8Daga nan sai ya aiki kurciya ta ga yadda ruwan ya tsane daga ƙasa,9amma kurciyar ba ta sami wurin sauka ba, sai ta koma gare shi cikin jirgin ruwan, domin har ya zuwa lokacin ruwa na rufe da ƙasa baki ɗaya. Sai ya miƙa hannunsa ya kamo ta ya shigar da ita cikin jirgin ruwan tare da shi.10Sai ya jira na tsawon ƙarin kwanaki bakwai, sa'an nan sai ya sake aiken kurciyar daga cikin jirgin ruwan.11Kurciyar ta koma wurinsa da yamma. Duba! a cikin bakinta ta tsinko sabon ganyen zaitun. Daga nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga ƙasa12Sai ya ƙara jira na waɗansu kwanaki bakwai, sai ya sake aiken kurciyar. Ba ta sake komawa wurinsa ba.13Sai ya zamana a shekara ta ɗari shida a farkon shekara, a wata na farko, a ranar farko ta wata, sai dukkan ruwa ya bushe daga dukkan ƙasa. Nuhu ya buɗe rufin jirgin ruwan, ya dudduba ya ga ƙasa ta bushe.14A cikin wata na biyu, a ranar ashirin da bakwai ga wata, ƙasa ta bushe.15Sai Allah yace da Nuhu,16"Ka fito daga cikin jirgin ruwan da kai da matarka da 'ya'yanka da matan 'ya'yanka tare da kai.17Ka kuma kwaso kowacce halitta mai rai dake tare da kai, da tsutsaye, da dabbobi da duk abin da ke rarrafe a doron ƙasa - domin su hayayyafa, su zama babbar runduna ta masu rai a ko'ina a duniya, su hayayyafa, su ruɓamɓanya a cikin duniya."18Sai Nuhu ya fita tare da 'ya'yansa, da matarsa da matan 'ya'yansa.19Da kowacce irin hallitta dake tare da shi da dukkan masu rarrafe da dukkan tsuntsaye da duk wani abu mai motsi bisa duniya, bisa ga irinsu, suka fito daga cikin jirgin ruwan.20Nuhu ya gina bagadi ga Yahweh. Ya ɗauki waɗansu daga cikin dabbobi masu tsarki da tsuntsaye masu tsarki ya miƙa hadaya ta ƙonawa da su akan bagadin.21Yahweh ya shaƙi ƙanshin hadayar sai ya ce a cikin zuciyarsa, "Ba zan sake la'anta ƙasa saboda mutum ba, koda yake nufe-nufen mutane a zukatansu mugunta ne tun daga yarantakarsu. Ba zan ƙara hallakar da duk masu rai ba kamar yadda na yi.22Muddin duniya tana nan, lokacin iri da lokacin girbi, sanyi, da zafi, bazara da damuna, dare da rana ba za su taɓa ƙarewa ba."
"tuna" ko "tunani game da"
Wannan na nufin babban akwati da zai iya tafiya akan ruwa ko da bakin ƙwarya. "babban kwalekwale" ko " Babban Jirgin ruwa." juya wannan kamar a cikin Farawa 6:13.
"Ruwan ya daina fitowa daga ƙasa, ruwan sama kuma ya daina faɗowa." Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ya rufe maɓuɓɓugai zurfafa da tagogin sama"
"ruwa daga ƙarƙashin duniya." Dubi yadda aka fassarar wannan a cikin Farawa 7:11.
Wannan na nufin ruwan ya daina. Wannan na bayana sararin sama kamar rufi ne da ke hana ruwan da ke sama daga saukowa a duniya. A sa'ad da tagogi ko kofofin da sararin sama suka buɗe, sai ruwa ta sauko ta cikin su. AT: "sararin sama ta buɗe" ko "kofofin sama suka buɗe." Dubi yadda aka juya "tagogin sama" a cikin Farawa 7:11.
"sauka akan doran ƙasa" ko "tsaya a doron ƙasa"
Domin Musa ne ya rubuta wannan littafi, mai yiwuwa ana nufin watan bakwai da na goma na kalandar Ibraniyawa, amma ba tabbacin wannan.
"A rana ta farko ga watan goma"
Ana iya bayana wannan a fili: "bayyana a bisa fuskar ruwan."
Ana amfani da wannan maganar domin sa alama a farkon wani sabon sashi labari. Idan harshenku na da wani hanya faɗin haka, ana iya yanke shawarar amfani da shi a nan. AT: "Ya kasance cewa"
Maganar "da ya yi" na magana game da tagar. Wasu harsuna na iya bukaci a raba wannan maganar zuwa wani jimla: "Nuhu ya yi taga a jirgin ruwan. "sai ya zama bayan kwanaki arba'in sai ya buɗe tagar"
wani bakin tsuntsu ne da ya ke cin zanlar nama da dabbobin da sun mutu
Wannan na nufin hankaka ya yi ta barin cikin jirgin ya je ya dawo.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "sai da iska ya busher da ruwan" ko "har sai ruwan ya bushe"
"saukowa" ko " sauka." Ya na nufin sauka aka wani abu domin a huta daga shawagi a sama.
Marubucin na amfani da kalmar "kurciya" a matsayin mace. Ana iya juya waɗannan maganganu ta wannin wakilin sunan " ta ...ita ..." ko "shi ...ka ..." bisa ga yadda harshenku ke kiran kurciya.
Idan ana amfani wakilin suna na maza wa "kurciya", za a bukaci a sa sunar Nuhu a nan domin a kauce wa rikicewa: "Nuhu ya aike kurciyar," Nuhu ya miƙar da hannunsa," etc.
"Jawo hankalin" ko "Wannan na da muhimminci"
"ganyen da ta tsinko daga itacen zaitun"
"yanke daga abu"
"Ya kuma jira na kwanaki bakwai"
Ana iya bayana dalilin a fili idan mutane ba za su fahimta ba: "Ba ta sake komawa wurinsa ba domin ta sami wurin hutawa."
Ana amfani da wannan maganar domin ba da alama na farkon wani sabon sashin labarin. Idan harshenku na da wani hanya faɗin haka, ana iya yanke shawarar amfani da shi a nan.
"sa'ad da Nuhu na shekara 601"
Domin Musa ne ya rubuta wannan littafi, mai yiwuwa ana nufin watan farko na kalandar Ibraniyawa ne, amma ba tabbacin wannan.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki AT: "ruwan da ya rufe ƙasa ya bushe" ko "iska ta busher da ruwan da ya rufe ƙasa" .
Wannan na nufin abin da aka sa domin hana ruwan sama shiga cikin jirgin.
Kalmar "ga shi" na jawon hankalin mu ne ga muhimmin sakon da ke zuwa nan gaba.
"rana ta ashirin da bakwai ga watan biyu." Wannan mai yiwuwa ana nufin wata na biyu na kalandar Ibraniyawa ne, amma ba tabbacin wannan.
"ƙasar ta bushe gaba ɗaya" (UDB)
"bar ... ɗauki." Wasu fassarar an karanta "zo waje ... kawo"
"kowacce irin halitta mai rai." Duba yadda aka juya "kowacce halitta" a Farawa 6:11.
Wannan karin magana ne. Duba yadda aka juya wannan a Farawa 1:28. Allah na so mutane da dabbobi su sake haifuwa, domin so kasance dayawa.
Wasu fassarar sun karanta "Nuhu ya fito."
"tare da irin su"
"gina bagadi, ya keɓe wa Yahweh" ko "gina bagadin sujada ga Yahweh." Mai yiwuwa ya gina shi da duwatsu ne.
"tsarki" a nan na nufin cewa Allah ya yarda a yi amfani da waɗannan dabbobin domin hadaya. Ba a amfani da wasu dabbbobi wajen miƙa hadaya, ana kiran su "mara tsarki."
Nuhu ya kashe dabbobin, sai ya ƙona su kurmus a matsayin baiko ga Allah. AT: "ƙona dabbobin a matsayin baiko ga Yahweh"
Wannan na nufin ƙanshi mai kyau daga gasashen nama.
"tun daga farkon shekarunsu, sun kasnace da nufin aikata mugunta" ko "tun suna ƙuruciya, suna son aikata mugayen abubuwa"
"muddin jurewa duniya" ko "muddin kasancewa duniya"
"lokacin da ake yin shuki"
Wannan maganar na nufin yanayi lokaci biyu da suke a shekara.
1Sai Allah ya albarkaci Nuhu da 'ya'yansa, ya ce da su, "Ku ruɓanɓanya ku hayayyafa, ku cika duniya.2Tsoronku da tsoratarwarku za ta zama a kan dukkan dabbobi masu rai dake duniya, da kowanne tsuntsu dake sararin sama, da duk wani abu dake motsi bisa ƙasa, da dukkan kifayen teku. An bada su a hannunka.3Dukkan wani abu mai motsi dake rayuwa zai zama abinci a gare ku. Na baku koren ganyayyaki, yanzu na ba ku kowanne abu.4Amma ba za ku ci naman da jininsa da ransa ke cikinsa ba.5Amma a bisa jininka, da ran dake cikin jininka, zan bukaci diyya. Daga dukkan dabbobi zan bukace ta. Daga hannun kowanne mutum, wato, mutumin da ya aikata kisan kai ga ɗan'uwansa,6zan bukaci bada lissafi na wannan mutum. Duk wanda ya zubar da jinin mutum ta wurin mutum za a zubar da jininsa, domin cikin kammanin Allah aka hallici mutum.7Ku kuma, ku hayayyafa, ku ruɓanɓanya, ku warwatsu a ko'ina a duniya, ku ruɓanɓanya a cikinta."8Sai Allah ya yi magana da Nuhu da 'ya'yansa dake tare da shi cewa,9Amma, "Ka saurara! Zan tabbatar da alƙawarina da ku da zuriyarku dake biye da ku, da kuma10dukkan halittu masu rai dake tare da ku, da tsuntsaye, da dabbobin gida, da kowacce halitta ta duniya dake tare da ku, da kuma duk abin da ya fito daga cikin jirgin, da kuma dukkan halittu masu rai dake duniya.11Na tabbatar da alƙawarina da ku, cewa ba zan ƙara hallakar da dukkan halittu da ruwa ba, ba za a sake yin ruwan da zai hallaka duniya ba."12Allah yace, "Wannan ce alamar alƙawarin da nake yi tsakanina da ku da dukkan halittun dake tare da ku, domin kuma dukkan tsararraki masu zuwa:13Na sa bakangizona a cikin girgije, zai kuma zama alamar alƙawarina da ku da kuma duniya.14Zai kuma zamana a lokacin da na sauko da girgije a kan duniya aka kuma ga bakangizo a cikin girgijen,15to zan tuna da alƙawarina da ku da dukkan halitta mai rai. Ruwaye ba zasu ƙara zama abin hallakarwa ga mutane ba.16Bakangizon zai kasance a cikin girgije, zan kuma gan shi, domin in tuna da alƙawarina madawwami, tsakanin Allah da dukkan halittu masu rai a duniya.17"Sai Allah yace da Nuhu, "Wannan ita ce alamar alƙawarin da na tabbatar tsakanina da dukkan masu rai na duniya."18'Ya'ya maza na Nuhu da suka fito daga cikin jirgin sune Shem, Ham, da kuma Yafet. Ham shi ne mahaifin Kan'ana.19Waɗannan guda uku sune 'ya'yan Nuhu, daga waɗannan ne aka sami dukkan mutanen duniya.20Nuhu ne ya fara zama manomi, ya kuma shuka garkar inabi.21Sai ya sha waɗansu 'ya'yan inabin, ya kuma bugu. Yana kwance a cikin rumfarsa tsirara.22Sai Ham mahaifin Kan'ana, ya ga tsiraicin mahaifinsa, ya kuma faɗawa 'yan'uwansa guda biyu a waje.23Sai Shem da Yafet suka ɗauki mayafi suka ɗora a kafaɗunsu, suka tafi da baya suka rufe tsiraicin mahaifinsu. Fuskokinsu na fuskantar wani bangon, domin haka ba su ga tsiraicin mahaifinsu ba.24Da Nuhu ya tashi daga mayensa, sai ya gane abin da ɗansa ƙarami ya yi masa.25Domin haka ya ce, "Kan'ana zai zama la'annanne. Ya zama baran barorin 'yan'uwansa."26Hakan nan ya ce, "Yahweh Allah na Shem, ya zama da albarka, Kan'ana kuma ya zama baransa.27Allah ya faɗaɗa abin mulkin Yafet, ya kuma sa gidansa a cikin rumfunan Shem. Kan'ana kuma ya zama baransa."28Bayan ruwan tsufana, Nuhu ya yi shekaru ɗari uku da hamsin.29Dukkan kwanakin Nuhu shekaru ɗari tara ne da hamsin, daga nan ya mutu.
Wannan albarkan Allah ne. Ya ce wa Nuhu da 'ya'yan sa su haifar da wasu mutane kamar kansu, domin a su zama da yawa. Kalmar "ruɓanɓanya" na bayana yadda za su "hayayyafa." Dubi yadda aka fassarar wannan umarnin a Farawa 1:28.
Marubucin na maganar tsoro da tsoratarwa kamar wani abu ne da ke iya kasance a kan dabbobin. AT: "Kowani dabba mai rai ... da dukkan kifayen teku za su ji tsoron ka"
Wannan ne farko jeri guda na dabbobi da marubucin ya rubuta, ba wai an takaita ambacin sauran dabbobin da aka ambaci su a nan gaba ba.
Wannan suna ne na dukka abubuwa da suke tashi sama. Dubi yadda aka fassara wannan a Farawa 1:20.
Wannan ya haɗa kowani irin kananan dabbobi. Dubi yadda aka fassara wannan a Farawa 1:24.
Hannun yana wakiltar sarrafawa. Ana iya sanya wannan aiki. AT: "An ba su su cikin ikonku" ko "Na sanya su ƙarƙashin ikonku"
Allah ya ci gaba da magana da Nuhu da 'ya'yansa.
Masu fassara na iya ƙara alamun rubutu kamar haka: "Jini alama ce ta rayuwa." Wataƙila za su iya ƙara alamar ƙwallon ƙafa da ke faɗi abu kamar haka: "Allah yana umartar mutane kada su ci nama yayin da jini ke cikinsa. Dole ne su fara fitar da jinin da farko."
Allah ya ci gaba da magana da Nuhu da 'ya'yansa.
Wannan na banbanta jinin mutum da jini dabbobi (Farawa 9:1).
Wannan na nuna cewa a zubar da jini. AT: "Idan wani ya sa jinika ya zuba" ko "Idan wani ya zubar da jinika" ko " Idan wani ya kashe ka"
Wannan na nufin rayuwa a zahiri
Wannan biyan na nufin mutuwar mai kisa, ba kuɗi ba. AT:"zan buƙaci duk wanda ya kashe ka ya biya"
A nan kalmar "hannun" na nufin wanda ya zama sanaɗin faruwar abin.
"zan buƙaci kowacce dabba da ta dauki ranka ta biya"
"Zan bukaci duk wanda ya ɗauki ran wani mutum ya biya"
Wannan na nufin mutum. AT:"daga wannan mutumin"
A nan an yi amfani da "dan uwa" a matsayin dangi, kamar yan ƙabila daya, dangi, or ƙungiya.
Zubar da jini na nufin kisan wani. Wannan na nufi idan wani mutum ya kashe wani, to tilas ne wani mutum ya yi kisan sa. Duk da haka "jini" na da muhimminci a wannan yankin rubutun, in ya yiwu a yi amfani da kalmar a juyi. Fassarar "zubar da jini" da kalmar da zai nuna yawan jini da a ka rasa na sa mutuwa.
"domin Allah ya yi mutum ya zama kaman shi" ko "domin na yi mutum a cikin kamani na"
Wannan albarkar Allah ce. Ya ce wa Nuhu da iyalin sa su hayayyafa, don suyi yawa. Kalmar "ku ruɓanɓanya" ta bayyana yadda zasu zama da "albarka". Duba yadda aka fasara a Farawa 1:28.
Da ma tun can Allah na magana da su. Wannan maganar na ba da alamar cewa Allah zai canja abin da yake magana a kai. AT: Allah ya ci gaba da magana wa Nuhu da 'ya'yansa" ko "Sai Allah ya ci gaba da cewa"
An yi amfani da wannan jimlar da Turanci domin a nuna canzawa daga lokacin da Allah ke magana da Nuhu da 'ya'yan sa zasu yi zuwa abin da Allah zai yi
"sa alkawari tsakanin na da kai." Fassarar wannan kamar Farawa 6:18.
Allah ya ci gaba da magana da Nuhu da 'ya'yansa.
"Ta wurin faɗin wannan, Ina sa alƙawari tare da kai." Dubi yadda a juya kalmomi mai kamar wannan a cikin Farawa 6:18.
Mai yiwuwa ana nufin 1) dukka mutane ko 2) dukka rayayu da ake gani, da mutane da dabbobi.
"Ba za a ƙara hallakar da duniya da ambaliya ba." Za a yi ambaliya, amma ba zai hallakar da dukkan duniya.
Wannan na tunashewa da abin da aka alkawatar.
Alkawarin ya shafi Nuhu da iyalinsa har ma da dukkan tsararraki masu zuwa.
Allah ya ci gaba da magana da Nuhu da 'ya'yansa.
"kowani lokaci." Abu ne wanda zai ci gaba da faruwa loto loto.
Ba a bayana ko wanene zai ga bakangizo, amma tun da shike alƙawari na sakanin Yahweh ne da mutane, kuma in ya zama lalle a faɗa ko wanene da wanene za za su ga bakangizon, zai fi kyau a cewa Yahweh ne da mutane. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Ni da mutane za mu ga bakangizo"
Wannan bai nuna cewa Allah zai manta ba ne. AT: "Zan yi tunani game da alƙawarina"
Kalmar "kai" biyu ne. Allah na maganar Nuhu da 'ya'yansa.
"kowani irin abu mai rai"
Allah ya ci gaba da magana da Nuhu da 'ya'yansa.
"saboda in tuna" ko "domin in yi tunani game"
Allah ke magana anan. AT: "tsakanin na da kowani halitta mai rai"
Allah ya riga yana magana da Nuhu. Wannan magana na ba da alama ce na karshen sashin abin da Allah yake cewa. AT: "Allah ya gama magana da Nuhu" ko "Sai Allah ya ce wa Nuhu"
Ayoyi 18-19 na gabatar da 'ya'yan Nuhu su uku, wanda suke da muhimminci a sashin labari da ke gaba.
Ham shi ne asalin mahaifin Kan'ana.
"mai noma ƙasa"
"ya sha 'ya'yan inabin da yawa"
Nassin bai fayyace nawa jikin Nuhu ya buya yayin da yake cikin maye ba. 'Ya'yansa maza halayen sun nuna mana cewa abin kunya ne.
Wannan na nufin Nuhu ne.
A cikin ayoyi 25-27 Nuhu ya la'anci ɗan Ham kuma ya albarkaci 'yan'uwan Ham. Abin da Nuhu ya faɗa game da su kuma ya shafi zuriyarsu, kamar yadda aka nuna a cikin UDB.
ULB yayi wannan tare da waƙoƙi a cikin la'anar Nuhu da albarka a cikin ayoyi 25-27. Wasu fassarar suna saita kowane layi na waƙa nesa da dama fiye da sauran rubutun don sauƙaƙe karatu.
"ya warware"
Wannan na nufin Ham ne. AT: "ƙaramin ɗansa, Ham"
"Na la'anci Kan'ana" ko "Bari mugayen abubuwa su faru ga Kan'ana"
Wannan ɗaya ne daga 'ya'yan Ham. AT: "ɗan Ham, Kan'ana"
"mafi ƙarancin bawan 'yan'uwansa" ko "mafi ƙanƙantar bawan' yan'uwansa"
Wannan na iya nufin 'yan'uwan Kan'ana ko kuma danginsa gaba ɗaya.
Idan za a iya sa waɗanan ayoyin kamar waka domin masu karatu su gane cewa waka ne.
"Yabo ya tabbata ga Yahweh, Allahn Shem," ko "Yahweh, Allahn Shem, ya isa yabo" ko "Na yabe Yahweh, Allahn Shem" (UDB)
"Kan'ana kuma ya zama baran Shem." Wannan ya shafi zuriyar Kan'ana da zuriyar Shem.
Mai yiwuwa ana nufin 1) "Allah ya sa ƙasar Yafet ya yi girma" (UDB) ko 2) "Allah ya sa Yafet ya sami zuriya mai yawa."
"ya kuma yi zaman salama da Shem." Wannan ya shafi zuriyar Yafet da zuriyar Shem.
"bari Kan'ana kuma ya zama baransa." Wannan na nufin zuriyar Kan'ana da Yafet
1Waɗannan sune zuriyar 'ya'yan Nuhu maza, wato Shem da Ham da Yafet. An haifa masu 'ya'ya maza bayan ruwan tsufana.2'Ya'yan Yafet maza sune Gomar, Magog, Madai, Yaban, Tubal, Meshek da Tiras.3'Ya'yan Gomar maza sune Ashkenaz, Rifhat da Togarma.4'Ya'yan Yaban maza sune Elisha, Tarshish, Kittim da Dodanim.5Daga waɗannan ƙasashe mutane suka watsu suka tafi ƙasashensu, kowanne da nasu harshe bisa ga kabilarsu, da kuma janhuriyunsu.6'Ya'yan Ham maza sune Kush, Mizraim, Fut da Kan'ana.7"Ya'yan Kush maza sune Seba, Habila, Sabta, Ra'ama da Sabteka. 'Ya'ya maza na Ra'ama sune Sheba da Dedan.8Kush ya zama maihaifin Nimrod, wanda shi ne ya fara mamaye duniya.9Shi riƙaƙƙen maharbi ne a fuskar Yahweh. Wannan ya sa ake cewa "Kamar Nimrod riƙaƙƙen maharbi a fuskar Yahweh."10Wurin mulkinsa na farko shi ne Babila, Erek, Akkad, da Kalne a ƙasar Shinar.11Daga cikin ƙasar ya fita zuwa Assiriya ya gina Nineba da Rehobot Ir, Kala,12da Resen wadda take a tsakanin Nineba da Kalash. Ita babban birni ce.13Mizraim ya zama mahaifin Ludatiyawa, Anamitiyawa, da Lehabiteyawa, Naftuhitawa,14Fatrusitiyawa da Kasluhiyatawa (waɗanda daga cikinsu ne Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftoriyawa.15Kan'ana ya zama mahaifin Sidom, ɗansa na fari, da kuma Het,16har kuma da Yebusawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,17Hibiyatawa, da Arkittawa, da Sinitawa,18da Arbaditiyawa, da Zemaritiyawa, Hammatiyawa. Bayan haka kabilar Kan'aniyawa ta yaɗu waje.19Kan iyakar Kan'ana tana daga Sidon, wajen Gerar har zuwa Gaza da kuma kamar mutum zai yi wajen Sodom, da Gomara, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.20Waɗannan sune 'ya'yan Ham bisa ga kabilarsu, da kuma harsunansu, a cikin ƙasarsu, da al'ummarsu.21Hakanan an haifawa Shem 'ya'ya maza, babban ɗan'uwan Yafet. Shem shi ne kãkan dukkan mutanen Eber22'Ya'yan Shem maza sune Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da kuma Aram.23'Ya'yan Aram maza kuwa sune Uz, Hul, Gezar, da Meshek.24Arfakshad ya zama mahaifin Shela, Shela kuma ya haifi Eber.25Eber na da 'ya'ya biyu sunan ɗayan shi ne Feleg, domin a cikin kwanakinsa aka raba duniya. Ɗan'uwansa shi ne Yoktan.26Yoktan ya zama mahaifin Almodad, Shelef, Hazamabi, Yerah,27Hadoram, Uzal, Diklah28Obal, Abimawel, Sheba,29Ofir, Habila, da Yobab. Duk waɗannan 'ya'ya maza ne na Yoktan.30Iyakarsu ta kama daga Mesha, har ya zuwa hanyar Sefhar da tsauni na gabas.31Waɗannan sune 'ya'yan Shem maza, bisa ga kabilarsu da harsunansu, a cikin ƙasashensu, bisa ga al'ummarsu.32Waɗannan sune kabilar 'ya'yan Nuhu, bisa ga ƙididdigar asali, ta hanyar janhuriyarsu. Daga waɗannan janhuroriyoyi suka rarrabu suka shiga ko'ina a duniya bayan ruwan tsufana.
"Wannan shine asalin 'ya'yan Nuhu." Wannan jimlar na gabatar da asalin zuriyar Nuhu a Fara 10:1-11 :9.
"Ya'yan Yaban maza da zuriyar suka rabu, su ka je ƙasashe"
Wannan na nufin mutanen da suke zama a tsibiri.
"ƙasashensu na asali." Waɗannan wurare ne da mutane suka koma zama.
"Kowanne mutane suna furta harshensu" ko "Mutanen suka raba kansu zuwa harshensu"
Mizrayim ƙasar "Masar" ne a harshen Ibraniyanci.
Mai yiwuwa ana nufin 1) "babban mayaƙi" ko 2) "babban jarumi" ko 3) "ikon mulki."
Mai yiwuwa ana nufin 1) "a gaban Yahweh" ko 2) "da taimakon Yahweh"
Wannan na gabatar da karin magana. Mai yiwuwa harshenku na da yadda ku ke gabatar da karin magana ta wani hanya. AT: "Wannan shine dalilin da ya sa mutane su ke cewa
Mai yiwuwa ana nufin 1) wurin da fara mulkinsa, ko 2) muhimmin birane
"Nimron ya tafi zuwa Asiriya"
Jerin sunayen zuriyar Nuhu ya ci gaba.
Mizrayim ɗaya ne daga cikin 'ya'yan maza na Ham. Zuriyarsa ne suka zama mutanen Masar. Mizrayim kalmar Ibraniyanci ne na Masar.
Wannan sunayen na nufin babban taron mutanen zuriyar Kan'ana
"yankin ƙasa" ko "iyakar ƙasar su"
Idan ya kasance ana bukatar gamsashen bayani game da yankin kudu. AT: "daga arewacin birnin Sidon har zuwa kudunci garin Gaza, wanda ke kusa da Gerar"
Idan ya kasance ana bukatar gamsashen bayani game da yankin da ke fuskantar "gabas" ko "nesa daga teku." AT: "sai gabas wajejen garuruwan Sodom, Gomara, Adma, da Zeboyim har zuwa Lasha" (Duba: Assumed Knowledge da Implicit Information)
Kalmar "waɗannan" na nufin mutanen da jera sunayensu a Farawa 10:6.
"suka rabu bisa ga harsunansu dabam dabam"
"cikin ƙasashensu na asali"
Arfakshad ɗaya ne daga 'ya'yan Shem.
Masu fassara na iya ƙara bayanin takaice na rubutu da ke cewa: "ma'anar sunan Feleg kuwa shine 'rabuwa.'"
Ana iya sanya wannan aiki. AT: "mutanen duniya suka raba kansu" ko "mutanen duniya suka rabu daga tsakanin su" ko "Allah ya raba mutanen duniya"
Yoktan ɗaya ne daga 'ya'yan Eber.
Anan "waɗannan" na nufin 'ya'ya maza na Yoktan.
"ƙasar da suke da iko akai" ko "ƙasar da suke zama"
Kalmar "waɗannan" na nufin zuriyar Shem (Farawa 10:21).
Wannan na nufin dukka jerin mutane da aka kira daga Farawa 10:1.
"jeri bisa"
"Daga waɗannan kabilun ne janhuroriyoyi suka rarrabu a ko'ina a duniya" ko "Waɗannan kabilun suka rarrabu a tsakaninsu suka zama janhuroriyoyi na duniya"
Ana iya bayana wannan a fili da gamsashen bayani. AT: "bayan ambaliyan ruwan ya hallakar da duniya"
1To dukkan duniya sun yi magana da harshe ɗaya, kalmominsu kuma ɗaya ne.2Da suka yi tafiya zuwa gabas a hayin filin Shinar suka zauna a can.3Suka ce da juna, "Zo mu yi tubula mu gasa su sosai." Suka yi aiki da tubali a madadin dutse, katsi kuma a maimakon yunɓu,4"Suka ce, "Ku zo, mu gina wa kanmu birni da kuma hasumiya wadda tsawonta zai kai har sararin sama, kuma mu yi wa kanmu suna. In ba mu yi ba, za a warwatsu mu a fuskar duniya dukka."5Sai Yahweh ya zo daga sama domin ya ga birnin da hasumiyar da zuriyar Adamu suka gina.6Yahweh yace "Duba su mutane ɗaya ne da harshe ɗaya, kuma sun fara yin wannan! Ba da jimawa ba zasu iya yin duk wani abin da suka yi niyya, ba abin da zai gagare su.7Zo, mu sauka mu rikirkitar da harshensu a can, domin kada su fahimci juna."8Sai Yahweh ya warwatsa su daga can zuwa ko'ina a duniya, sai kuma suka dena ginin birnin.9Domin haka sunansa ya zama Babila, domin a can ne Yahweh ya rikirkitar da harsunan duniya baki ɗaya, kuma daga can ne Yahweh ya watsa mutane ko'ina a sararin duniya.10Waɗannan sune zuriyar Shem, Shem na da shekaru ɗari, sai ya zama mahaifin Arfakshad shekaru biyu bayan ruwan tsufana.11Shem ya rayu har shekaru ɗari biyar bayan ya haifi Arfakshad. Hakanan ya haifi 'ya'ya maza da mata ma su yawa.12Da Arkfashad ya yi shekaru talatin da biyar, sai zama mahaifin Shela.13Arkfashad ya rayu na tsawon shekaru 403 bayan ya haifi Shela. Hakanan ya haifi waɗansu sauran 'ya'ya maza da mata.14Da Shelah ya kai shekaru talatin, ya haifi Ebar.15Shelah ya rayu har shekaru 403 bayan ya haifi Ebar. Hakanan ya haifi sauran waɗansu 'ya'ya maza da mata.16Da Ebar ya yi shekaru talatin da huɗu sai ya haifi Felag.17Ebar ya yi shekaru 430 bayan ya haifi Felag, Hakanan ya haifi sauran waɗansu 'ya'ya maza da mata.18Da Felag ya yi shekaru talatin, sai ya haifi Reu,19bayan Felag ya haifi Reu ya rayu har shekaru 209, ya kuma haifi sauran waɗansu 'ya'ya maza da mata.20Da Reu ya kai shekaru 32 sai ya haifi Serug.21Reu ya yi shekaru 207 bayan ya haifi Serug. Hakanan ya haifi sauran waɗansu 'ya'ya maza da mata.22Da Serug ya kai shekaru talatin sai ya haifi Nahor.23Bayan Serug ya haifi Nahor, ya rayu na tsawon shekaru ɗari biyu sai kuma ya haifi sauran waɗansu 'ya'ya maza da mata.24Bayan Nahor ya rayu shekaru ashirin da tara, sai ya zama mahaifin Tera.25Nahor ya rayu shekaru 119 bayan ya haifi Tera. Hakanan ya zama mahaifin waɗansu 'ya'ya maza da mata.26Bayan Tera ya rayu na tsawon shekaru saba'in sai ya zama mahaifin Abram, da Nahor, da Haran.27To waɗannan sune zuriyar Tera, Tera ya haifi Ibram, Nahor, Haran, Haran kuma ya haifi Lot.28Haran ya mutu a fuskar mahaifinsa Tera a ƙasar haihuwarsa, a Ur ta Kaldiyawa.29Ibram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Ibram Sarai matar Nahor kuma sunanta Milka, 'yar Haran wanda shi ne mahaifin Milka da Iskah.30To Sarai bakarariya ce; ba ta da ɗa.31Tera ya ɗauki ɗansa, da Lot ɗan ɗansa Haran, da kuma surukarsa Sarai matar ɗansa Ibram, tare suka bar Ur ta Kaldiyawa, zuwa ƙasar Kan'ana. Amma suka zo Haran suka zauna a can.32Tera ya rayu shekaru 205 daga nan ya mutu a Haran.
Wannan kalmar na nuna cewa marubucin na shirin fara wani sabon sashi ne na labarin.
dukka mutanen duniya
Waɗannan magana na nufin abu ɗaya ne, kuma na jadada cewa dukkan mutane sun yi magana da harshe ɗaya ne.
"ƙaura" ko "tafiya wurare"
Mai yiwuwa ana nufi 1) "cikin gabas" ko 2) daga gabas" ko 3) "zuwa gabas". Zaɓin da aka fi so shi ne "a gabas" saboda Shinar yana gabas inda malamai ke gaskata jirgin ya tsaya.
daina tafiya daga wuri zuwa wuri aka kuma kasance a wuri ɗaya ana rayuwa
Idan harshen ku na da yadda ake iza, ko umurtar mutane ga yin aiki kamar yadda Turanci ke amfani da "ku zo!", kuna iya amfani da shi a nan.
Mutane na yin tubali daga yinɓu sai a gasa su sosai domin su kasance da karfin gaske.
wani abu ne mai kauri, da ke mannewa, baƙi mai ruwa-ruwa da ke fitowa daga ƙasa
Wannan wani abu ne mai kauri da ake yin ta daga garin siminti, lãka, garin kasa da ruwa wanda ake amfani wajen hada tubali ko duwatsu waje gini.
"mu yi wa kanmu martaba mai girma"
"martaba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "za mu rarrabu daga tsakanin mu kuma kasance a wurare dabam dabam"
"mutanen"
Ana iya ba da gamsashen bayani game da inda ya sauko: "sauko daga sama." Wannan baya bayana yadda ya sauko ba. Yi amfani da kalmar gama gari ma'ana "ta sauko."
"a kiyaye" ko "a duba sosai"
Mai yiwuwa ana nufi 1) sun riga sun fara aikata wannan," manufar cewa sun fara gina hasumiya amma basu karasa ba, ko 2) "Wannan abu ne farko da suka yi," ko ma'anar shi ne nan gaba za su yi manyan abubuwa.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "kowani abin da suka yi niyyar aikatawa mai yiwuwa ne a gare su"
Kalmar "mu" jam'i ne ko da yake yana nufin Allah ne. Wasu sun juya shi cewa "bari in sauka" ko "zan sauka." Idan an yi haka, ana iya tunanin sharihinta cewa wakilin sunan jam'i ce. Duba bayanin "Bari mu yi" a Farawa 1:26.
Ma'anar wannan shi ne Yahweh zai sa mutanen dukka duniya su daina amfani da harshe ɗaya. AT: "jujjuya harshensu"
Wannan ne dalilin rikirkitar da harshensu. AT: "ta yadda ba za su iya fahimtar abin da juna ke faɗi ba"
"daga birnin"
sunan Babel na kamar kalmar da ke nufin "rikirkita." Masu juya na iya sharihinta game da wannan.
Ma'anar wannan shi ne Yahweh zai sa mutanen dukka duniya su daina amfani da harshe ɗaya. AT: "jujjuya harshen duniya gaba ɗaya"
Sauran suran nan na ba da jerin zuriyar Shem zuwa Ibram.
Wannan jimlar ya fara jerin zuriyar Shem.
Wannan ita ce rigyawa daga zamanin Nuhu lokacin da mutane suka zama mugaye har Allah ya aiko da ambaliyar duniya ta rufe duniya.
"samu ɗan sa Arfakshad " ko "aka haifi ɗansa Arfakshad"
Wannan sunan namiji ne
Masu juya na iya rubuta wannan cikin kalmomi ko adadi "100," "2," da "500." )
"an haifi ɗan sa Shela"
Wannan sunan namiji ne
Abubuwan da aka rubuta a cikin Farawa 11:12-25 suna da tsari iri ɗaya. Duba yadda ka fassara su a cikin Farawa 11:12-13.
Abubuwan da aka rubuta a cikin Farawa 11:12-25 suna da tsari iri ɗaya. Duba yadda ka fassara su a cikin Farawa 11:12-13.
Abubuwan da aka rubuta a cikin Farawa 11:12-25 suna da tsari iri ɗaya. Duba yadda ka fassara su a cikin Farawa 11:12-13.
Abubuwan da aka rubuta a cikin Farawa 11:12-25 suna da tsari iri ɗaya. Duba yadda ka fassara su a cikin Farawa 11:12-13.
Abubuwan da aka rubuta a cikin Farawa 11:12-25 suna da tsari iri ɗaya. Duba yadda ka fassara su a cikin Farawa 11:12-13.
Abubuwan da aka rubuta a cikin Farawa 11:12-25 suna da tsari iri ɗaya. Duba yadda ka fassara su a cikin Farawa 11:12-13.
Ba mu san jerin haifuwar 'ya'yan sa ba.
Wannan jimlar na gabatar da labarin zuriyar Tera. Farawa 11:27-25:11 na managa game da zuriyar Tera musamman ɗan sa Ibrahim. AT: "Wannan ne jerin asalin zuriyar Tera"
Wannan na nufin cewa Haran ya mutu yayin da mahaifinsa na nan da rai. AT: "Haran ya mutu yayin da mahaifinsa Tera, na tare da shi"
"aure mata"
Wannan sunan mace ne.
Ana amfani da wannan kalmar wajen gabatar da sabon bayani game da Sarai da zai zama da muhimminci a surori na gaba.
Wannan kalmar na bayana macen da ba ta iya haifuwa ba ko yin ciki ba.
A nan kalmar "ya" na nufin Tera.
"surukarsa Sarai, wanda itace matan ɗansa Ibram"
Waɗannan sunaye biyu ne dabam dabam kuma ana rubuta su dabam dabam a Ibraniyanci. Ɗayan sunan mutum ne, ɗayan kuma sunan birni ne. Kuna iya rubuta su dabam dabam a harshen ku domin nuna wannan bambanci.
1Sai Yahweh yace da Ibram "Ka tashi ka bar ƙasarka da danginka, da kuma ƙasar mahaifinka, zuwa ƙasar da zan nuna maka,2zan maishe ka babbar al'umma, zan albarkace ka in kuma sa sunanka ya yi girma, kuma za ka zama albarka.3Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, zan kuma la'anta duk wanda ya tozarta ka. Ta wurin ka dukkan al'ummar duniya za ta sami albarka."4To Ibram ya tafi, kamar yadda Yahweh ya faɗa masa ya yi, Lot kuma ya tafi tare da shi. Ibram yana da shekaru saba'in da biyar a lokacin da ya tafi ya bar Haran.5Ibram ya ɗauki matarsa Sarai, da Lot ɗan ɗan'uwansa da dukkan mallakarsu da suka tara, da kuma dukkan mutanen da suka samu a Haran. Suka tafi zuwa ƙasar Kan'ana, suka kuwa isa ƙasar Kan'ana.6Ibram ya wuce ƙasar har zuwa Shekem, zuwa al'ul na Moreh. A wancan lokacin Kan'aniyawa na zaune a ƙasar.7Yahweh ya bayyana ga Ibram, ya ce, "Ga zuriyarka Zan ba da wannan ƙasa." Daga nan Ibram ya gina bagadi domin Yahweh, wanda ya bayyana a gare shi.8Daga can ya tafi zuwa ƙasar duwatsu a gabashin Betal, inda ya kafa rumfarsa, ga Betal a yammaci, Ai kuwa a gabashi. A can ya kafa bagadi domin Yahweh, ya kuma yi kira bisa sunan Yahweh.9Daga nan Ibram ya ci gaba da tafiya, zuwa wajen Negeb.10A kwai yunwa a cikin ƙasar, don haka Ibram ya gangara zuwa Masar ya zauna domin yunwar ta tsananta sosai a cikin ƙasar.11Da ya kusa shiga Masar sai ya ce da matarsa Sarai, "Duba na san ke mace ce kyakkyawa.12In Masarawa suka gan ki za su ce, 'Wannan matarsa ce; za su kuma kashe ni, amma za su bar ki da rai.13Ki ce ke 'yar'uwata ce, domin komai ya yi mani dai-dai saboda ke, don a bar ni in rayu saboda ke."14Sai ya zamana bayan Ibram ya shiga cikin Masar, Masarawa suka ga cewa Sarai kyakkyawa ce.15'Ya'yan sarki suka gan ta, suka kuma yaba mata a gaban Fir'auna, sai aka ɗauki matar zuwa gidan sarki.16FIr'auna ya kyautatawa Ibram saboda ita, ya ba shi tumaki, takarkarai, da jakai maza da mata da bayi maza da mata da kuma raƙuma.17Sai Yahweh ya bugi gidan Fir'auna da annoba mai zafi saboda Sarai matar Ibram.18Fir'auna ya kira Ibram ya ce da shi me kenan ka yi mini? Meyasa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ba ce?19Meyasa ka ce ita 'yar'uwarka ce; don in ɗauke ta ta zama matata? To yanzu ga matarka nan. Ka ɗauke ta ku tafi."20Sai Fir'auna ya bada umarni game da shi daga nan suka sallame shi ya tafi, tare da matarsa da duk abin da yake da shi.
Ana amfani da wannan kalmar domin nuna alamar sabon sashin labari.
"Ka tafi daga ƙasarka, daga iyalika"
"ka" a nan na nufin Ibram ne, amma Ibram na wakiltar zuriyar sa. AT: "Zan fara babbar al'umma ta wurin ka" ko "Zan mai da zuriyarka babbar al'umma"
Kalmar "suna" tana wakiltar mutuncin mutum. AT: "kuma maishe ka shaharare"
An fahimci waɗannan kalmomin "zuwa wasu mutane." AT: "za ka zama albarka ga wasu mutane"
"zan la'anta duk wanda ya rena ka" ko "idan wani ya mayar da kai abin banza, zan la'ance shi"
Ana iya sanya wannan aiki. AT: "Zan albarkace al'umman duniya dukka ta wurin ka"
""Saboda ka" ko "Domin na albarkace ka"
Wannan ya kunshi dabbobi da dukiya mara rai.
Mai yiwuwa ana nufi 1) "bayin da suka tara" (UDB) ko 2) "mutanen da suka tara su kasance tare da su."
An kira Ibram ne kadai domin shine kan gidan. Allah ne ya bashi umurni ya tashi da iyalinsa su kuma tafi wurin. AT: "Sai Ibram da iyalinsa suka wuce cikin ƙasar"
"ƙasar Kan'ana"
Mai yiwuwa "Moreh" sunan wani wuri.
"Yahweh, domin ya bayyana a gare shi"
Ibram na da mutane dayawa tare da shi sa'ad da yana tafiya. Mutanen da suke tafiya wurare dabam dabam na zama a rumfar ne. AT: "suka kafa rumfarsu"
"sun yi addu'a cikin sunan Yahweh" ko "yi wa Yahweh sujada"
"Sai Ibram ya ɗauki rumfarsa ya kuma ci gaba da tafiya."
"ta yankin Negeb" ko "ta wajen kudu" ko "kudu zuwa hamadan Negeb" (UDB)
Amfanin gona bai girma da kyau ba a wancan kakar. Ana iya ba wannan gamsashen bayani cewa. AT: "Ana ƙarancin abinci"
"cikin yankin" ko "a ƙasar da Ibram ke zama"
Mai yiwuwa ana nufin 1) "kara gaba zuwa kudu" (UDB) ko 2) "ya tafi daga Kan'anan zuwa." Zai fi kyau a juya wannan da kalmar da aka saba amfani da shi waje tafiya daga wuri mai tudu zuwa ƙasa.
Ana iya ba gamsashen bayana game da dalilin da zai sa a kashi Ibram: "za su kashe ni domin su aure ki"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: domin saboda ke, ba za su kashe ni ba"
Mai yiwuwa ana nufin 1) An yi amfani da wannan kalmomin a nan domin sa alamar inda aka fara abu, kuma idan harshenku na da hanyar yin wannan, ana iya yin yan ke shawarar amfani da shi a nan, ko 2) "haka kuma ya faru" (UDB).
"Jami'an Fir'auna su ka ga Sarai" ko "ma'aikacin Fir'auna suka gan shi" (UDB)
AT: "Fir'auna ya ɗauke ta zuwa cikin gidansa" ko "Fir'auna da sojojinsa sun ɗauke ta zuwa cikin gidansa"
Sarai
Mai yiwuwa ana nufin 1) "iyalin Fir'uan", wato a matsayin mata, ko 2) "gidan Fir'auna" ko "fadar Fir'auna," ana nufin Fir'auna ya maishe ta ɗaya a cikin matan shi.
"saboda Sarai" ko "saboda ita"
Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "domin Fir'auna na da nufin ɗaukan Sarai, matar Ibram, ta zama matar sa"
"Fir'auna ya kira Ibram" ko "Fir'auna ya umarci Ibram ya zo wurinsa"
Fir'auna yayi amfani da wannan tambaya ta zance don ya nuna fushin sa game da abin da Ibram ya yi masa. Hakanan za'a iya bayyana azaman tsawa. AT: "Kun yi min mummunan abu!"
"Sai Fir'auna ya umarci ma'aikatan sa game da Ibram"
"sai ma'aikatan suka sallame Ibram daga wurin Fir'auna, da matar sa da kuma dukka mallakarsa"
1Sai Ibram ya bar Masar ya tafi Negeb, shi da matarsa da duk abin da ya mallaka. Lot ya tafi tare da su.2Ibram ya wadata sosai ta fannin dabbobi da zinariya da azurfa.3Ya ci gaba da tafiya daga Negeb har zuwa wurin da ya kafa rumfarsa a dã baya, tsakanin Betal da Ai.4Ya tafi har zuwa inda ya kafa rumfa a baya. A nan ya fara kiran sunan Yahweh.5To Lot wanda ke tare da Ibram shi ma yana da garke da sauran bisashe da rumfuna.6Ƙasar kuma ta yi masu kaɗan, su da mallakarsu domin suna da mallaka da yawa, saboda haka ba su iya tsayawa a wuri ɗaya ba.7Hakanan akwai rashin jituwa tsakanin makiyayan dabbobin Ibram da kuma makiyayan dabbobin Lot. Feriziyawa da Kan'aniyawa ne ke zama a wannan ƙasar a wancan lokacin.8Sai Ibram yace da Lot, "bai kamata a sami rashin jituwa tsakanina da kai ba, ko kuma tsakanin makiyayan dabbobina da makiyayan dabbobinka.9Fiye ma da haka mu dangi ne, duba ba fili ne nan gabanka ba? Ka zaɓi duk inda kake so, in ka zaɓi hagu, ni sai in zaɓi dama, in ka zaɓi dama ni sai in zaɓi hagu"10Sai Lot ya duba yankin Yodan, ya kuma gan shi kore shar har zuwa yankin Zowar, kamar lambun Yahweh, kamar kuma ƙasar Masar. Haka yake kafin a hallaka Sodom da Gomora.11Sai Lot ya zaɓi wannan filin na Yodan ya tafi gabas, dangin suka rabu da juna.12Ibram ya zauna a ƙasar Kan'ana Lot kuma ya zauna a biranen filin ƙasa. Ya kakkafa rumfunansa har zuwa Sodom,13To mutanen Sodom miyagu ne sosai, masu yi wa Yahweh zunubi ne.14Yahweh yace da Ibram bayan Lot ya rabu da shi. "Duba daga inda kake tsayuwa zuwa arewa, kudu da gabas da yamma.15Dukkan wannan ƙasar da ka ke gani, na bada ita ga zuriyarka har abada.16Zan haɓaka zuriyarka ta zama kamar turɓayar ƙasa, domin in har mutum zai iya ƙirga turɓayar ƙasa to zai iya ƙirga zuriyarka.17Tashi ka kewaya faɗin ƙasar da tsawonta, domin zan bada ita gare ka.18Sai Ibram ya tashi ya ɗauki rumfarsa ya je ya zauna kusa da itatuwan rimayen Mamre, wanda ke a Hebron. A can ya kafa bagadi domin Yahweh.
"hagu" ko "tashi daga"
Negeb wani hamada ne kudu da Kan'ana, a yammacin Masar. Ana iya ba da gamsashen bayana wannan. AT: "komo zuwa hamadan Negeb"
"Ibram na da dobbobi masu yawa, zinariya da azurfa masu yawa ƙwarai"
"dabbobin gida" fo "shanu"
Ibram da iyalinsa suna bin tafiyar daga wani wuri zuwa wani wuri. Ana iya ba da gamsashen bayani. AT: "Suka ci gaba da tafiyarsu"
Masu fassarawa na iya ƙara ƙarin bayani na ɗan ƙasan da ke cewa "Duba Farawa 12:8." Lokacin tafiyarsa zai iya zama bayyane. AT: "zuwa wurin da kafa rumfarsa kafin ya tafi zuwa Masar"
"sum yi addu'a a cikin sunan Yahweh" ko "sujada ga Yahweh." Duba yadda aka juya wannan a Farawa 12:8.
Ana amfani da wannan kalman wajen nuna cewa bayanin da ke zuwa na ba da ƙarin haske ne, domin ya taimake masu karatu wajen fahimtar aukuwar da ke zuwa.
Babu isashen wurin kiwo da ruwa domin dukka dabbobin su.
Wannan ya ƙunshi dabbobi ma, da suke bukatar wurin kiwo da kuma ruwa.
"basu iya zama tare ba"
Wannan ma wani dalili ne da ya sa ƙasar ta kasa musu dukka.
"kar muyi jayayya"
"takun saƙa" ko "hargitsi" ko "husuma"
"mu kuma hana makiyayan dabbobin mu jayayya"
"domin mu dangi ne"
Ana iya juya wannan tambayan a wata hanya mai kyau. AT: "dukka filin na nan domin ka."
Ibrahim na magana da Lot, yana kuma karfafa shi ya yi abin da zai taimake su tare. "Mu rabu."
Ma'ana mai yiwu 1) "In ka bi wani hanya, ni sai in bi ɗayan" 2) "In ka yi arewa, ni sai in yi kudu." Ibram ya bar Lot ya zaɓi iyakar fili da yake so, sai shi Ibram kuma ya ɗauki abin da ya rage.
Wannan na nufin iyakar yankin Kogin Urdun.
"akwai ruwa sosai"
"kamar gonar Yahweh ko kamar ƙasar Masar." Waɗannan wurare dabam ne guda biyu.
Wannan wani suna na gonar Aidan.
Wannan yana tsammanin wani abu da zai faru daga baya. Yana da mahimmanci a nan saboda ya bayyana dalilin da ya sa Lot ya zauna a yankin da daga baya ba ta da amfani.
"yan'uwa" ko "iyalan." Wannan na nufin Lot da Ibram da kuma gidajensu.
"kasance" ko "tsaya"
"ƙasar Kan'anawa"
Ma'ana mai yuwa 1) "Ya kakkafa rumfunansa kusa da Sodom" (UDB) ko 2) "Ya matsar da rumfanansa zuwa wani wuri da ya kai har zuwa Sodom."
"bayan Lot ya bar Ibrahim"
"ka kewaya dukka ƙasar"
Wannan sunan mutumin da yake da itacen rimin.
Wannan sunan wuri ne.
"badadin yi wa Yahweh sujada"
1Sai ya zamana a kwanakin Amrafel, sarkin Shinar, Ariyok sarkin El'asar, Kedorlaoma sarkin Elam, da Tidal sarkin Goyim,2suka kai yaƙi kan Bera sarkin Sodom, Birsha, sarkin Gomora, Shinab, sarkin Adma, Shemebar, Sarkin Zeboyim, da sarkin Bela (wato wanda ake kira Zowar).3Waɗancan sarakuna na baya suka taru a kwarin Siddim (wanda kuma ake kira Tekun Gishiri).4Suka bautawa Kedorlawoma shekaru sha biyu, amma a shekara tasha uku suka yi tayawe.5A shekara ta sha huɗu kuma, da sarakunan dake tare da shi suka zo suka kawo hari kan Rafaim a Ashterot Karnaim, da Zuzim a Ham, na Emim a Shaba Kiriataim,6da Horitiyawa a ƙasar duwatsu ta Se'ir, har zuwa El Faran dake kusa da hamada.7Daga nan sai suka juyo suka zo En Mishfat (wadda kuma ake kira Kadesh), suka cinye dukkan ƙasar Amelikawa, da kuma ta Amoriyawa waɗanda ke zama a Hazazon Tamar.8Daga nan sai sarkin Sodom, da sarkin Gomora, da sarkin Admah da sarkin Zeboim da sarkin Bela (da ake kira Zowar) suka je suka yi shirin yaƙi9găba da Kedorlawomar sarkin Elam, Tidal, sarkin Goim, Amrafel sarkin Shinar, Ariok, sarkin Ellasar; sarakuna huɗu găba da biyar.10To kwarin Siddim ya cika da ramukan yaƙi, da sarakunan Sodom da Gomora suka gudu sai suka faɗa cikinsu a can. Waɗanda suka rage suka gudu kan duwatsu.11Domin haka maƙiya suka kwashe dukkan kayayyakin Sodom da Gomora suka tafi abin su12Da suka tafi, suka kame Lot, ɗan ɗan'uwan Ibram, wanda ke zama a Sodom tare da dukkan malakarsa.13Wani da ya tsira ya zo ya gaya wa Ibram Ba'ibirane. Yana zama a gefen rimin Mamre Ba'amore, ɗan'uwan Eshkol da Aner, Waɗanda dukkansu abokan Ibram ne.14To da Ibram ya ji maƙiya sun kame ɗan'uwansa, sai ya jagoranci horarrun mazajensa guda 318 waɗanda aka haifa a gidansa ya bi su har zuwa Dan.15Ya rarrraba mazajensa găba da su a wannan daren ya kai masu hari, ya bi su har zuwa Hoba wadda ta ke arewa da Damaskus.16Daga nan ya dawo da dukkan mallakar, ya kuma dawo da ɗan'uwansa Lot da duk kayansa, da mataye da sauran mutane.17Bayan Ibram ya dawo daga yin nasara da Kedorlawoma da sarakunan dake tare da shi, sarkin Sodom ya tafi ya tare shi a kwarin Shabe (Wanda kuma ake kira Kwarin Sarki)18Melkizedek, sarkin Salem ya kawo gurasa da ruwan inabi. Shi firist ne na Allah Maɗaukaki.19Ya albarkace shi cewa, Mai albarka ne Ibram ta wurin Allah Mafi Ɗaukaka, Mahallicin sama da duniya.20Albarka ta tabbata ga Allah Mafi Ɗaukaka, wanda ya bada maƙiyanka a hannunka." Sai Ibram ya ba shi kaso ɗaya bisa goma na komai.21Sarkin Sodom yace da Ibram, "Ka bani mutane, ka ɗauki kayayyakin domin kanka.22"Ibram yace da sarkin Sodom, "Na ɗaga hannunna sama zuwa ga Yahweh, Allah Maɗaukaki, Mahallicin sama da duniya,23cewa ba zan ɗauki koda tsinkin zare ko takalmi ko dukkan wani abu dake naka ba, domin kada ka ce, 'Na sa Ibram ya azurta,'24Ba zan ɗauki komai ba sai abin da matasa samari suka ci da kuma rabon mazajen dake tare da ni. Let Aner, Eshkol, da Mamre su ɗauki nasu kason."
Biranen da aka kira a Farawa 14:1 su na da 'yancin kansu.
Ana amfani da wannan maganan wajen fara wani sabon sashi ne na labarin. Idan harshen ku na da yanda a ke faɗin wannan kuna iya amfani da shi nan.
"a lokacin"
"suka tafi yaƙi" ko "suka fara yaƙi" ko "suka yi shirin yaƙi"
Bayanai cewa sojojinsu suna tare dasu ana iya bayyane. AT: "Waɗannan sarakuna biyar na ƙarshe da rundunarsu sun haɗu wuri ɗaya"
Abubuwan da suka faru a ayoyi 4-7 sun faru ne kafin aya ta 3. Yarenku na iya samun hanyar nuna wannan.
Mai yiwu suna biyan haraji a warin shi, suna kuma bauta a matsayin sojojin shi. AT: "suna karkashin mulkin Kedorlawoma"
"sun ƙi bauta masa" ko "sun daina yi masa hidima"
Waɗannan sunayen kungiyar mutanne ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Ayoyi 8 da 9 sun maimaita abin da aka faɗa a cikin Farawa 14: 3 kuma ta ci gaba da ba da labarin abin da ya faru lokacin da sarakuna suka taru don yaƙi.
Kalmar "su" na nufin sarakuna hudun da suka zo domin su kai farmaki a yankin Kan'ana. Sunayen kuwa Amrafel, Ariok, Kedorlawomar, da Tidal. AT: "suka juyo su ka je"
Wannan maganar na bayana wani mutane Amoriyawa ne aka ci da yaƙi. Akwai waɗansu mutanen Amoriyawa da suka kasance a wasu wurare.
Birnin Bela ana iya kira Zowar. Ana iya faɗin wannan maganar a karshen jimla. "da sarkin Bela suka fati da shirin yaƙi. Bela kuma ana iya ce ita Zowar."
"na da ramukan yaƙi dayawa." Waɗannan ramuka ne a ƙasa da akwai kwalta a ciki.
Anan sarakuna suna wakiltar kansu da sojojinsu. AT: "sarakunan Sodom da Gomora da rundunarsu"
Ma'ana mai yiwuwa 1) wasu sojojinsu su ka faɗa cikin ramukan kwalta, ko 2) sarakuna da kansu su ka faɗa a cikin ramukan da ke da kwalta. Tunda yaki 14:17 ya bayana cewa sarkin Sodom a je ya sami Ibram, to mai yiwuwa ma'ana na farko ne ke dai-dai.
Waɗanda ba su mutu ba waje yaƙi kuma basu faɗa a cikin ramukan ba"
Wannan na nufin sarki Kedorlawomar da sauran sarakuna da suke tare da kuma sojojinsu wadda suke tare a kai wa Sodom da Gomora farmaki.
"Sodom" da "Gomora" na nufin mutanen da su ka zama a waɗannan biranen. AT: "dukiyar mutanen Sodom da Gomora" ko " mallakar mutanen Sodom da Gomora"
Wannan maganar "ɗan ɗan'uwan Ibram" da kuma "wanda ke zama a Saduma" na tunar da masu karatu game da abubuwan da aka rubuta game da Lot a baya. AT: "suka kuma ɗauki Lot da dukka mallakarsa. Lot ɗan ɗan'uwan Ibram ne kuma ya na zama a Sodom a wacan lokacin"
"Wani mutum da gudo daga yaƙin ya zo"
"Ibram yana zama." Wannan yana gabatar da bayanan baya.
"wanda sun kulla yarjejeniya da Ibram" ko "suna kulla zama salama da Ibram"
Wannan na nufin da Lot, yaron ɗan'uwan Ibram.
:mazajen da suka horu wajen yaƙi"
"mazajen da aka haifa a cikin gidan Ibram." 'Ya'yan bayin Ibram ne.
"bi su a guje"
Mai yiwuwa wannan na nufin dabarar yaƙi ne. "Ibram ya rarraba mazajen kashi-kashi, suka kuma kai ma maƙiyansu hari ta hanyoyi dabam-dabam" (UDB)
Wannan na nufin abubuwan da maƙiyan suka sato daga birnin Sodom da Gomora.
"da mallakar Lot wadda maƙiyan suka sato daga wurin Lot"
"tare da mataye da sauran mutanen da sarakuna hudu su ka kama"
Bayanin da aka nuna game da inda yake dawowa zai iya zama bayyane. AT: "an koma inda yake zaune"
Wannan ne farkon da ambaci wannan sarki.
Mutane sun saba cin gurasa da ruwan inabi. Duba yadda aka fassara "gurasa" a Farawa 3:17 da kuma "ruwan inabi" a Farawa 9:20.
Sarki Melkizedek ya albarkace Ibram
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari Allah Mafi Ɗaukaka, Mahallicin sama da duniya ya albarkace Ibram"
"Allah Mafi Ɗaukaka domin ya ba da." Maganar ya fara da "wanda ya ba da" ya na faɗa mana wani abu ne gae da Allah Mafi Ɗaukaka.
Wannan hanyar yi wa Allah yabo ne. Duba yadda aka fassara "albarka ta tabbata" a Farawa 9:26.
"a mulkin ka" ko "cikin ikon ka"
"Mutanen" na iya nufin mutanen Sodom wanda maƙiya su ka kama. Ibram ya cece su a sa'ad da ya cece Lot.
Wannan na nufi "Na ɗauki ranstuwa" ko "Na yi alkawari."
"Iyakar abin da matasana samarai suka ci shi ne a karba a gare ka." Ibram ya ki ya karba komai domin kansa, amma ya amince cewa sojojinsa sun riga sun ci daga abin da ke akwai a sa'ad da suna dawowa Sodom daga yaƙi.
Ana iya ba da ma'anar wannan maganar a gamsashen bayani. AT: "rabo daga mallakar da ke na mazajen da suka taimaka mini samun su"
Waɗannan abokan yaƙi ne na Ibram (Duba Farawa 14:13). Domin su abokan yaƙin Ibram ne, su na zuwa yaƙi tare da shi. Ana iya ba da cikakiyar ma'anar wannan maganar haka. AT: "Abokai na Aner, Eshkol, da Mamre"
1Bayan waɗannan abubuwa sai maganar Yahweh ta zo wurin Ibram a wahayi, cewa, "Ibram kada ka ji tsoro ni ne garkuwarka da kuma babban ladanka."2Ibram yace, ya Ubangiji Yahweh, me za ka bani tunda yake har yanzu bani da ɗa. Magajin gidana kuma Eliyazar ne daga Damaskus,"3Ibram yace, da yake baka bani zuriya ba, duba, ɗan aikin gida ne ya zama magajina.4Sai ga maganar Yahweh ta zo gare shi, cewa "Ba wannan mutumin ne zai gaje ka ba, amma wanda zai fito daga cikin jikinka ne zai zama magajinka."5Daga nan sai ya fito da shi waje ya ce, "Duba sama, ka kuma ƙidaya taurari, in za ka iya ƙirga su. Daga nan ya ce da shi, haka zuriyarka za ta zama."6Ya yi imani da Yahweh, sai ya lisafta masa shi a matsayin adalci.7Ya ce da shi, "Ni ne Yahweh, wanda ya fito da kai daga Ur ta Kaldiyawa, domin in baka wannan ƙasar ka gãje ta."8Ya ce ya Ubangiji Yahweh, ta yaya zan sani cewa zan gãje ta?"9Daga nan ya ce da shi, "Ka kawo mini bijimi ɗan shekara uku da kuma akuya 'yar shekara uku da kurciya, da tantabara."10Ya kawo masa dukkan waɗannan ya kuma datsa su biyu-biyu ya kuma ajiye kowanne tsagi a gefen ɗayan, amma bai raba tsuntsayen ba.11Lokacin da tsuntsayen dake yawo suka zo wurin mushen sai Ibram ya kore su.12Daga nan bayan rana ta kusa faɗuwa, Ibram ya yi barci mai nauyi, sai ga wani babban duhu mai ban razana ya sha kan shi.13Daga nan Yahweh yace da Ibram, hakika ka san cewa zuriyarka zasu yi baƙunci a ƙasar da ba tasu ba, za a kuma bautar da su, a tsananta musu har tsawon shekaru ɗari huɗu.14Zan hukunta waccan al'ummar da zasu bauta wa, bayan haka kuma zasu fita da mallaka mai yawa.15Amma za ka je wurin ubanninka da salama, kuma za a yi maka jana'iza a shekaru ma su kyau.16A cikin tsara ta huɗu zasu sake zuwa nan kuma, saboda muguntar Amoriyawa ba ta kai iyakarta ba tukuna."17Da rana ta faɗi dare kuma ya yi, sai ga hayaƙin wuta da kuma harshen wutar tukunya da tartsatsi suka wuce a tsakanin yankin naman.18A wannan lokaci Yahweh ya yi yarjejeniya da Ibram cewa ga zuriyarka zan bada wannan ƙasa tun daga kogin Masar zuwa babban kogin Yuferetis-19da Kan'aniyawa da Kanizitawa20da Hitiyawa da Feriziyawa da Refatiyawa,21da Amoriyawa da Kan'aniyawa da Girgashiyawa da Yebusiyawa."
"Waɗannan abubuwa" na nufin lokacin yaƙin sarakunan da kuma ceton da Ibram ya wa Lot.
Wannan na nufin cewa Yahweh ya yi magana. AT: "Yahweh ya faɗa saƙonsa"
Anan "magana" na wakiltar saƙon Yahweh ne. AT: "saƙon Yahweh"
Allah yayi amfani da waɗannan kalmomi domin ya bayana wa Ibram halinsa da kuma dagantakarsa da Ibram.
"biya." Wani na nufin biyan da wani ya cancanta. mai yiwuwa ma'ana biyu ne 1) "Ni ne kadai ka ke bukata" ko 2) Zan ba ka dukka abin da ka ke bukata."
"Ibram ya ci gaba da cewa, da ya ke ka ba ni"
Kalamar "gashi" na jadada cewa kalmar Yahweh ta sa ke zuwa ga Ibrahim.
Wannan na nufin Eliyaza ne daga Damaskus.
"wanda za ka zama mahaifinsa" ko "asalin ɗan ka." Ɗan Ibram zai zama magajin sa.
'ƙirga taurari"
Kamar yanda Ibram ba zai iya ƙidaya taurari ba, haka nan ba zai iya ƙidaya zuriyarsa ba domin za su kasance da yawa.
Wannan na nufi ya amince cewa abin da Yahweh ya faɗa gaskiya ne.
"Yahweh ya lisafta imanin Ibram a kan adalci" ko "Yahweh ya ɗauke Ibram adali ne domin Ibram ya gaskanta da shi"
Yahweh na tunar da Ibrahim game da abin da ya riga ya yi domin Ibrahim ya san cewa Yahweh na da ikon ba wa Ibram abin da ya alkawatar masa.
"same ta" ko "domin ka mallake ta"
Ibram na tambaya domin ya kara samun tabbaci cewa Yahweh zai ba shi kasar.
"jikin dabbobi da tsunstayen da suka mutu"
"Ibram ya kore tsuntsayen." Ya tabbatar cewa tsuntsaye ba su ci dabbobin da suka mutu ba.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "Ibrahim ya yi barci mai zurfi"
"matsananciyar duhu da ta razanar da shi"
"mamaye shi"
"'yan ƙasan waje" ko "wanda ba 'yan gida ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "masu ƙasar kuwa za su maishe zuriyarka bayi, su kuma tsananta musu"
Yahweh ya ci gaba da yi wa Ibram maganar sa'ad da Ibram yana cikin mafarkin.
Anan "hukunta" na nufin abin da zai faru bayan Allah ya yi shari'a. AT: "Zan azabtar"
Wannan karin magana ne. AT: "mallaka mai matuƙan yawa" ko "wadatar dukiya"
Wannan wata hanya ɗabi'a ne na cewa "za ku mutu."
"za ku tsufa kafin ku mutu, iyalinku kuwa su yi muku jana'iza"
Tsara ɗaya a nan na nufi tsawon shekaru ɗari. "bayan shekaru ɗari huɗu"
"zuriyarka za su sake dawo nan." Zuriyar Ibrahim za su sake komowa ƙasar da Ibram ke zama, da kuma ƙasar da Yahweh ya alkawatar ma sa.
"bai cika ba" ko "sai ya yi muni kafin zan hukunta su"
Allah ya yi wannan domin ya nuna wa Ibram cewa ya na yin yarjejeniya tare shi.
"wuce tsakanin layin naman dabba"
Ta faɗin wannan, Allah na ba da ƙasa wa zuriyar Ibram. Allah na yin haka a wacan lokacin amma zuriyar ba za su shiga ƙasar ba sai bayan shekaru da yawa.
kogin Yuferetis mai girma.
Waɗannan sune sunayen kungiyar mutanen da suke zama a ƙasar. Allah a yardar wa zuriyar Ibrahim su ci nasara yaƙi da waɗannan mutane, su kuma ɗauki ƙasar.
1To Sarai, matar Ibram, ba ta haifa masa 'ya'ya ba tukuna, amma tana da baiwa, mutumiyar Masar, sunanta Hajara.2To sai Sarai ta ce da Ibram, "Duba Yahweh ya hana mani 'ya'ya, ka je ka kwana da baiwata. Watakila na sami 'ya'ya ta wurinta." Ibram ya saurari muryar Sarai.3Bayan Ibram ya yi shekaru goma a Kan'ana ne Sarai ta miƙa baiwarta Hajara ga Ibram a matsayin mata.4Sai ya yi tarayya da Hajara ta kuwa yi juna biyu. Da taga ta yi juna biyu sai ta fara duban uwargijiyarta da reni.5Daga nan Sarai ta ce da Ibram, "Wannan kuskuren a kaina saboda kai ne. Na bada baiwata gare ka, kuma bayan ta ga ta yi juna biyu, sai aka sayar da ni a idonta. Bari Ubangiji ya shari'anta tsakanina da kai."6Amma Ibram yace da Sarai, "Duba ita baiwarki ce, tana ƙarƙashin ikonki, ki yi mata abin da kike tunanin ya fi kyau," Sai Sarai ta takura mata sosai, sai ta gudu daga gare ta7Sai mala'ikan Yahweh ya same ta a maɓulɓular ruwa a jeji, wannan maɓulɓular dake kan hanya zuwa Shur.8Ya ce da ita, Hajara baiwar Sarai daga ina ki ka zo kuma ina za ki? sai ta ce "ina gujewa uwargijiyata ne Sarai."9Mala'ikan Yahweh yace da ita, "Ki koma wurin uwargiyarki, ki miƙa kai ga shugabancinta."10Sai mala'ikan Yahweh yace da ita, "Zan ruɓanɓaya zuriyarki sosai, domin su zama da yawa, su wuce ƙirge."11Hakanan mala'ikan Yahweh yace da ita, Duba kina ɗauke da juna biyu na ɗa namiji, kuma za ki kira sunansa Isma'ila, saboda Yahweh ya ji ƙuncinki.12Zai zama jakin jeji, zai yi magaftaka da dukkan mutane, dukkan mutane kuma na gãba da shi, zai kuma zauna a ware da 'yan, uwansa."13Sai ta bada wannan sunan ga Yahweh wanda ya yi magana da ita, "Kai Allah ne mai ganina," domin ta ce, "Ko zan ci gaba da gani, bayanda ya gan ni?"14Saboda haka ake kiran rijiyar Beyer Lahai Roi; tana nan tsakanin Kadesh da Bered.15Hajara ta haifa wa Ibram ɗa namiji ta ba shi suna Isma'ila.16Ibram na da shekaru tamanin da shida a lokacin da Hajara ta haifi Isma'ila.
Ana amfani da wannan kalmar a cikin Turanci don gabatar da sabon ɓangaren labarin da bayanan asali game da Sarai.
"baiwa." Wacennan baiwa za ta bauta wa matan gidan.
"daga haifan 'ya'ya"
"Zan ta da iyalina ta wurinta"
"Ibram ya yi abin da Sarai ta ce"
"ta raina uwargijiyarta" ko "ta dubi kan ta da daraja fiya da uwargijiyarta"
Ana nufin da Sarai ne a nan. AT: "mai mallakarta" ko "Sarai"
"Wannan rashin adalcin da na yi"
"hakin ka ne" ko "laifin ka ne"
Sarai na nufi cewa ya kwana da baiwarta. AT: "Na ba ka baiwa ta domin ka kwana da ita"
Wannan na iya zama mai aiki. AT: "ta na kiyayya da ni" ko " ta fara tsane ni" ko "ta dubi kan ta da daraja fiye da ni"
"Ina so Yahweh ya faɗa ko tsakani na kai wa ye da laifi" ko " Ina so Yahweh ya yanke shawara tsakanin mu biyu wa ya yi daidai. Maganar "shari'anta tsakani" na nufin yanke shawara a kan wanda ya aikata daidai tsakanin su.
"Saurare ni" ko "Kawo hankalin ki"
ƙarƙashin izni ki"
Sarai ta nuna wa Hajara mumunar hali"
"sai Hajara gudu daga gare Sarai"
Ma'ana mai yiwuwa 1) Yahweh ya mayar da kanshi a kamanin mala'ika, ko 2) wannan wani mala'ikan Yahweh ne, ko 3) wannan ɗan saƙo ne daga Allah na musamman (wasu malamai na tunani wai Yesu ne). Tunda shike ba'a fahimci wannan maganar ba, ya fi kyau a juya wannan cewa "mala'ikan Yahweh."
Yankin jeji da ta je hamada ne. AT: "hamada"
Wannan sunan wani wuri ne kuduncin Kan'ana da kuma gabacin Masar.
Ana nufi da Sarai ne a nan. Uwargiji na da iko a kan baiwarta. AT: "mamalaki." Duba yadda aka fassara "mai mallakarta" a Farawa 16:1.
"Mala'ikan Yahweh yace da Hajara"
Duba bayanin kula game da wannan jimlar a cikin Farawa 16: 7.
Sa'ad da ya ce "Zan," yana game da Yahweh ne. A sa'ad da ana fassara wannan maganar, a yi amfani da kalmar "Zan" wa Yahweh kamar yadda mala'ikan Yahweh ya yi.
"Zan ba ki zuriya ma yawa ƙwarai"
"sosai, da ba wanda zai iya ƙirgawa"
"Saurara" ko "Kula"
"haifuwan ɗa namiji"
"Za ki kira sunansa." Kalmar "ki" na nufi da Hajara.
Masu fassarar wannan na iya sharihinta cewa "ma'anar sunar 'Isma'ila' shine "Allah ya ji.'"
Ta sha ƙuncin da wahala
Wannan ba zagi ba ne. Yana yiwuwa Isma'ila zai kasance da yanci da kuma ƙarfi kamar jakin jeji. AT: "Zai kasance kamar jakin jeji a cikin mutane"
"Zai zama maƙiyin kowani mutum"
Ma'anar wannan na iya zama "zai yi zaman rashin jituwa da wasu."
"Yahweh, domin ya yi magana da ita"
Hajara ta yi amfani da tambaya ta nuna mamakin cewa tana nan a raye kodayake ta ga Allah. Mutane na tsammanin cewa zasu mutu in sun ga Allah. AT: "Ina mamaki ina a raye har yanzu, ... ni"
Masu fassarar wannan na iya sharihinta cewa ma'anar "Beyer Lahai Roi" ita ce "rijiyar rayaye, wanda yaki gani na."
Wannan na nufin cewa marubucin da masu karatu sun san wuri da ake magana a kai. AT: "ba shakka tana tsakanin Kadesh da Bered"
Ana iya ba da gamsashen bayani cewa Hajara ta dawo wurin Sarai da Ibram. AT: "Sai Hajara ta koma, ta kuma haifi"
Hajara ta sa wa ɗansa suna" ko "sunar ɗansa da Hajara"
Wannan na ba da ƙarin haske ne game da shekarar Ibram sa'ad da waɗannan abubuwa sun faru. Mai yiwuwa harshenku na da yadda ake ba da irin wannan ƙarin hasken.
Ma'anar wannan shine "ta haifi wa Ibram ɗa, Isma'ila." An maida hankali a kan cewa Ibram na da ɗa.
1Da Ibram ya kai shekaru tasa'in da tara, lokacin da Yahweh ya bayyana a gare shi ya kuma ce masa, "Ni ne Allah mai iko dukka. Ka yi tafiya a gabana ka zama da rashin laifi.2Daga nan zan cika alƙawarina tsakani na da kai, zan kuma kuma ruɓanɓanya ka sosai."3Ibram ya sunkuyar da fuskarsa ƙasa sai Allah ya yi magana da shi cewa,4"Ni kam, duba, alƙawarina na tare da kai. Zaka zama uban al'ummai masu yawa.5Ba za a ƙara kiran sunanka Ibram ba, amma sunanka zai zama Ibrahim - domin na zaɓe ka ka zama uban al'ummai masu yawa.6Zan sa ka ruɓanɓanya sosai, daga cikinka kuma zan samar da al'ummai, daga cikinka kuma za a sami sarakuna.7Zan kafa alƙawarina tsakanina da kai da kuma zuriyarka dake biye da kai, a dukkan tsararrakinsu domin alƙawari na har abada, in zama Allah a gare ka da kuma zuriyarka dake biye da kai.8Zan bada ƙasar da kake zama gare ka da kuma zuriyarka, dukkan ƙasar Kan'ana domin ta zama mallakarka ta har abada, zan kuma zama Allahnsu."9Sai Allah yace wa Ibrahim, "Amma kai dole ka kiyaye alƙawarina, da kai da zuriyarka dake biye da kai a dukkan tsararrakinsu.10Wannan shi ne alƙawarina da dole zaka kiyaye, tsakanina da kai da dukkan tsararrakin dake biye da kai:11Dole ka yi wa kanka kaciya, kuma wannan nan zai zama alamar alƙawarina da kai.12Kowanne ɗa namiji a cikinku da ya kai shekaru takwas, dole ne a yi masa kaciya, a dukkan tsararrakin mutanenka. Wannan ya haɗa da wanda aka haifa a gidanka, da kuma wanda aka saya da kuɗinka daga kowanne irin bãƙo wanda ba ya cikin zuriyarka.13Da wanda aka haifa maka da wanda ka saya dole ne ayi masa kaciya. Da haka alƙawarina zai kasance a jikinka domin zama alƙawari na har abada.14Duk wani namiji wanda ba shi da kaciya za a fitar da shi daga cikin mutanensa. Ya karya alƙawarina."15Allah yace da Ibrahim, "Game da Sarai matarka kuma Kada ka ƙara kiranta Sarai. A maimakon Sarai za a kira sunanta Saratu.16Zan albarkace ta, kuma za ta zama uwar al'ummai. Sarakunan mutane za su fito daga cikinta."17Daga nan sai Ibrahim ya sunkuyar da fuskarsa ƙasa ya yi dariya, a cikin zuciyarsa ya ce, "Ko za a haifa wa ɗan shekara ɗari ɗa? Ta yaya Saratu wadda ta kai shekaru tasa'in za ta iya haifar ɗa?"18Ibrahim yace da Allah, "Ah Isma'ila zai zauna tare da kai!"19Allah yace, "A 'a, amma Saratu matarka za ta haifa maka ɗa, kuma za ka ba shi suna Ishaku. Zan kafa alƙawarina da shi wato alƙawari na har abada da zuriyarsa dake biye da shi.20Shi kuma Isma'ila na ji ka. Duba na sa masa albarka, zan kuma ruɓaɓɓanya shi zan wadata shi sosai. Zai zama uban kabilu goma sha biyu. Zan kuma mai da shi babbar al'umma.21Amma alƙawarina zan kafa shi da Ishaku, wanda Saratu za ta haifa maka baɗi war haka."22Da ya gama yi masa magana, sai Allah ya rabu da Ibrahim.23Sai Ibrahim ya ɗauki Isma'ila ɗansa, da duk waɗanda aka haifa a cikin iyalinsa, da duk waɗanda ya saya da kuɗinsa da dukkan mazaje na mutanensa duk suka yi kaciya a rana ɗaya kamar yadda Allah ya faɗa masa.24Ibrahim yana da shekaru tasa'in da tara lokacin da ya yi kaciya.25Ɗansa Isma'ila kuma yana da shekaru sha uku a lokacin da aka yi masa kaciya.26A wannan ranar aka yi wa Ibrahim da ishaku kaciya a rana ɗaya.27Aka yi masa kaciya tare da dukkan mazajensa, da waɗanda aka haifa masa da waɗanda ya saya da kuɗi daga bãƙi.
Ana amfani da wannan magana a nan domin ba da alama ce na sabon sashin labarin. Idan harshen ku na da wata hanya yin haka, to ana iya amfani da ita.
"Allah wanda ke da iko duka"
Tafiya na nufin rayuwa ne a nan, kuma "a gabana" na nufin biyayya. AT: "Yi rayuwar da na ke so" ko "Yi ma ni biyayya"
"Zan ba da alƙawarina" ko " Zan cika alƙawarina"
A wannan ne Allah ya yi alƙawarin albarkace Ibram, amma ya na bukatan Ibram ya yi biyayya a gare shi.
"zan ƙara yawan zuriyarka ƙwarai" ko "zan ba zuriya masu yawa ƙwarai"
"Ibram ya fadi, fuskarsa kuma a ƙasa" ko "Nan da nan Ibrahim ya sa furkarsa a ƙasa" .Ya yi haka ne domin ya nuna girmar da ya ba Allah, kuma zai yi masa biyayya.
Allah yayi amfani da wannan maganar domin ya gabatar da abin da zai yi wa Ibram daga na shi bangaren alƙawarinsa da Ibram.
Kalmar "duba" a nan na bayana tabbacin abun da zo nan gaba: "haƙika alƙawarina na tare kai."
"uban al'ummai masu yawa ƙwarai" ko "al'ummai da yawa zasu sami sunansu daga gare ka"
Masu fassarar wannan na iya sharihinta cewa, ma'anar sunan "Ibram" kuwa shi ne "uba mai daraga" sunan "Ibrahim" kuma na kamar "uban dangi masu yawa."
"Zan sa ka sami zuriya masu yawa"
"Zan sa zuriyarka su zama al'umma da yawa"
"daga cikin zuriyarka za a sami sarakuna" ko "wasu daga zuriyarka za su zama sarakuna"
Allah ya ci gaba da yi Ibrahim magana.
"na kowani tsara"
"a matsayin alkawari da zai kasance har abada"
"in zama Allahn ka da na zuriyarka"
Kan'ana, a matsayin mallakarka har abada" ko "Kan'ana, ka mallaka har abada"
Wannan maganar na gabatar da abin da Ibram ke bukatar yi a na shi matsayin a sashi alƙawarin shi da Allah.
"kula da alƙawarina" ko "yi biyayya da alƙawarina"
"Wannan ita ce sharaɗin alƙawarina." Wannan jimlar na gabatar da bangaren alƙawarin ne da dole Ibram ya kiyaye.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. 'Dole ne ka yi wa kowani na miji a cikinku kaciya"
Wasu al'ummomin na iya son ƙaramin bayanin kwatanci kamar "Dole ne a yi muku kaciya." Idan fassarar ku ta "a kaciya" ta riga ta ƙunshi kalmar don "kaciyar fata", ba kwa buƙatar maimaita ta. Ana iya sanya wannan aiki. AT: "Dole ne ku yi wa kowane ɗa namiji kaciya"
"alamar da ke nuna cewa akwai alƙawarin"
Ma'ana mai yiwuwa 1) "alamar" ko 2) "wani alama." Na farko na nufin cewa iyakar alamar kenan gode ɗaya, na biyun kuma na nufi cewa alamar na iya kasance fiye da ɗaya. Kalmar "alama" a nan na ba da tuni ne na abin da Allah ya alƙawatar.
Allah ya ci gaba da yi wa Ibrahim magana.
"cikin kowani tsara"
Wannan na nufin bayi ne. AT: "kowani na miji da ka saya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "za ka sa alamar alƙawarina a jikinka"
"zama madawwamen alƙawari." Domin alamar a jiki ya ke, ba wani mai iya sharewa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki, kuma kuna iya barin kalmomin da zasu ba da ma'ana mara kyau a yarenku. AT: "namijin da ba ka yi wa kaciya ba"
Ma'ana mai yiwuwa 1) "Zan yanke kowani namiji marasa kaciya ... daga mutanensa" ko 2) "Ina so ka yanke kowani namiji mara kaciya ... daga mutanensa"
"Baya kiyaye umurnin alƙawarina ba." Wannan ne dalilin da za a yanke shi daga mutanensa.
Kalmar "game da" in gabatar da mutumin da Allah ke magana a kai, da ke zuwa nan gaba.
"Zan sa ta haifar maka ɗa"
"za ta kasance kakar al'umai" (UDB) or "zuriyar ta za su zama al'ummai"
"Sarakunan mutane za su sauko daga gare ta." ko "Wasu zuriyar ta za su zama sarakunan mutane"
"a cikin tunanin sa" ko "ya ce da kansa a cikin zuciyarsa"
Ibrahim ya yi amfani da tambaya domin ya nuna rashin amincewa wai haka zai iya faruwa. AT: "haƙiƙa mutum mai shekara ɗari ba zai iya haifan ɗa ba!"
Ibrahim ya yi amfani da tambaya domin ya nuna rashin amincewa wai haka zai iya faruwa. Maganar "wadda ke shekara tasa'in" ya nuna dalilin da ya sa Ibrahim baya amince cewa Sarai za ta iya haifa ɗa ba. AT: "Shekaru Sarai tasa'an ne, za ta iya haifan ɗa?" ko "shekarar Sarai tasa'in ne, tabbas ne ba za ta iya haifan ɗa ba!"
"Ina roƙo, bari Isma'ila ya gaji alƙawari da ka tsakani na da kai" ko "ko zai yiwu Isma'ila ya gaji alƙawarin albarkar ka." Ibrahim ya ba da sharawarar abin da tabbata zai iya faruwa.
Allah ya faɗa wannan domin ya canja wa Ibrahim tunaninsa na cewa Sarai baza ta iya samin ɗa ba.
Kalmar "ka" na nufi Ibrahim ne.
Wannan ƙarin magana ne da ke nufi "zan sa ya sami 'ya'ya dayawa."
"shugabanni" ko "masu mulki." Waɗannan ubanne ba 'ya'ya goma sha biyu da jikokin Yakubu ba ne da zasu shugabanci kabila goma sha biyu na Isra'ila.
Allah ya koma ga maganar alƙawarin sa da Ibrahim, ya kuma jadada cewa da Ishaku ne zai cika alƙawarin ba Isma'ila ba.
"Da Allah ya gama magana da Ibrahim"
"Allah ya bar Ibrahim"
"kowani mutum namiji da ke gidan Ibrahim." Wannan na nufi dukka mutane maza na kowani shekara: jarirai, yara, da maza.
"Wannan ya kunshi waɗanda aka haifa a gidansa da kuma waɗanda ya saya a wurin bãƙi"
Wannan na nufi da bayi ne.
1Yahweh ya bayyana ga Ibrahim a gefen itatuwan rimi na Mamre a lokacin da yake zaune a ƙofar rumfa da tsakar rana.2Ya duba sama, sai ga mutane uku na tsaye kewaye da shi. Da ya gan su, sai ya ruga daga ga ƙofar rumfar domin ya gamu da su, ya sunkuya ƙasa.3Ya ce, "Ubangiji, in na sami tagomashi a wurin ka, kada ka wuce ka rabu da bawanka.4Sai a kawo maku ɗan ruwa, ku wanke ƙafafu, ku kuma shaƙata a ƙarƙashin itace.5Sai in kawo maku abinci domin ku sami ƙarfi tun da kun zo wurin bawanku. "Suka amsa, Ka yi kamar yadda ka ce."6Sai Ibrahim ya yi hanzari ya shiga rumfa wurin Saratu, ya ce, "Hanzarto ki samo awo uku na gãri ki cuɗa shi ki yi gurasa."7Sai Ibrahim ya ruga garke ya ɗauko ɗan maraƙi ƙosasshe ya ba bayinsa su yi sauri su gyara shi.8Ya ɗauki curin da madara da maraƙin da aka gyara ya kai musu ya tsaya a gefensu a lokacin da suke ci.9Suka ce da shi, "Ina Saratu matarka?" Ya amsa, Ta na can, cikin rumfa,"10Ya ce, hakika zan komo wurinka baɗi war haka, kuma duba, Saratu matarka za ta sami ɗa." Saratu tana ji a bakin ƙofa cikin rumfa dake bayansa.11To Ibrahim da Saratu sun tsufa, shekarunsu sun yi nisa sosai, Saratu kuma ta wuce lokacin da mata ke iya haifar 'ya'ya.12Domin haka Saratu ta yi wa kanta dariya, tana cewa da kanta, "Bayan na tsufa, shugabana kuma ya tsufa, ko zan sami wannan jin daɗin?"13Yahweh yace da Ibrahim, "Meyasa Saratu ta yi dariya ta kuma ce, "Ko hakika zan iya haifar ɗa Yanzu dana tsufa"?14Ko akwai abin da ke da wuya ne ga Yahweh? A daidai lokacin dana sa, kamar war haka, zan komo wurinka a shekara mai zuwa Saratu za ta sami ɗa,"15Sai Saratu ta yi musu, ta ce "Ban yi dariya ba domin tana jin tsoro. Ya amsa mata ya ce, "A'a, kin yi dariya."16Sai mutanen suka tashi suka tashi suka duba wajen Sodom. Sai Ibrahim ya tafi tare dasu ya raka su a kan hanyarsu.17Amma Yahweh yace "Ko zan ɓoye wa Ibrahim abin da zan aikata,18da yake Ibrahim zai zama babbar al'umma kuma dukkan al'umman duniya zasu sami albarka ta wurinsa?19Domin na zaɓe shi domin ya umarci 'ya'yansa da gidansa dake biye da shi domin su bi tafarkin Yahweh, su aikata adalci da aikin adalci, domin Yahweh ya cika abin da ya faɗa wa Ibrahim zai aikata a gare shi."20Daga nan sai Yahweh yace, "Saboda kukan Sodom da Gomora ya yi yawa, kuma zunubinsu ya haɓaka,21Yanzu zan sauka in ga kukan da ake yi a kan su wanda ya zo gare ni, ko hakika sun aikata al'amarin. In ba haka ba zan sani."22To sai mazajen suka juya daga can, suka nufi wajen Sodom, amma Ibrahim ya tsaya a gaban Yahweh.23Sai Ibrahim ya matso ya ce "Ko zaka share adalai tare da mugaye?24In a ce za a sami adalai hamsin a cikin birnin. Ko zaka hallaka shi ba tare da la'akari da adalan nan hamsin ba dake can?25Ba zai yiwu ba ka yi haka wato ka kashe adalai tare da miyagu, domin a hori adalai kamar yadda aka hori miyagu. Ba zai yiwu ba mai hukunta duniya ya yi abin da ke dai-dai?"26Yahweh yace, "In na sami adalai hamsin a cikin birnin Sodom, to zan kuɓutar da dukkan birnin saboda su."27Ibrahim ya amsa ya ce, "Duba na jawo wa kaina magana da Ubangijina, koda yake ni ƙura ne kawai da toka!28To in ace adalan sun gaza hamsin ba mutum biyar? Zaka hallaka birnin saboda rashin biyar?" Daga nan sai ya ce, "Ba zan hallaka shi ba, in na sami mutane arba'in da biyar."29Sai ya sake yi masa magana, ya ce "To a ce za a sami arba'in a can fa?" Ya amsa, "Saboda mutane arba'in ɗin ba zan yi ba."30"Ya ce, "Har yanzu dai ina roƙo Ubangiji kada ka yi fushi in na yi magana. To in a ce za a sami talatin a can fa." Ya amsa ba zai yi hakan ba, in a kwai mutane talatin a can."31Ya ce "Ga shi na dage in yi magana da Ubangijina! In a ce za a sami ashirin a can fa." Ya amsa "Saboda mutane ashirin ɗin ba zan hallakar da shi ba."32Ya ce, "Ina roƙo kada ka yi fushi, Ubangiji, zan sake faɗin wannan karo na ƙarshe. In a ce za a sami goma fa a can." Sai ya ce, "Ba zan hallaka shi ba saboda mutane goman nan."33Sai Yahweh ya tafi a lokacin da ya gama yin magana da Ibrahim, shi kuma Ibrahim ya koma gida.
Wannan sunan mutumin mai itacen rimi..
"a ƙofar rumfar ko alfarwa"
"zafin rana"
"Ya duba sama, sai ga mutane uku suna tsaye"
"kur kusa" ko "wurin." suna kusa da shi, amma da dan nisa da zai iya gudu zuwa wurin sa.
Wannan na nufi nuna ban girma da tawali'u, da kuma daraja wani.
Wannan laƙani ne na ban girma. Ma'ana mai yiwuwa sune 1) Ibrahim ya san cewa ɗaya daga cikin mutanen Allah ne, ko 2) Ibrahim ya san waɗannan mutanen wakilan Allah ne.
Ibrahim na magana da wani a tsakanin mutanen.
"kada ka ci gaba da tafiya"
"ni." Ibrahim na nufin da kansa ne haka domin ya nuna ban girma wa bãƙonsa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari in kawo muku ruwa" ko "Bari bawa na ya kawo muku ruwa"
"ruwa ... abinci." Ambacin "ɗan" wata hanyar nuna karimci. Ibrahim za ba su ruwa da abinci fiye da abun da suke bukata.
Wannan al'ada ne na taimakon matafiya ne koren gajiya bayan tafiya mai nisa.
kamar lita 22
"bawan ya ruga guje"
"a yanka a kuma gasa shi"
Wannan sashin madara ne da ke daskare.
"maraƙin da aka gasa"
"Sa'annan suka ce da Ibrahim"
Kalmar "Ya" na nufi da mutumin da Ibrahim ya kira shi "Ubangiji" a Farawa 18:3.
"idan wannan lokacin ya zo shekara ta gaba" ko "game da wannan lokacin shekara mai zuwa"
Kalmar "duba" na jan hankalin mu ne ga lura da bayani mai ban mamaki da ke zuwa.
Zai iya yiwuwa a kara cewa "jin daɗi na samin ɗa"
Ma'anar wannan shine "tunda yake miji na ma ya tsufa."
Wannan laƙanin ban girma ne da Sarai ta ba wa mai gidan ta Ibrahim.
Allah yayi amfani da tambaya domin ya nuna wa Ibrahim cewa ya san abin da Sarai ke tunani a zuciyar ta, kuma baya ji dadi ba. Ha maimaita tambayar da Sarai ta yi a Farawa18:11 da wasu kalmomi dabam. AT: "Sarai ba ta yi daidai ba da yin dariya ta kuma ce, "ba zan iya haifar ɗa ba domin na tsufa sosai!"
"Ko akwai abin da ba zai iya yi ba? Yahweh na magana game da kanshi kamar yana maganar wani ne, domin ya tunashi Ibrahim cewa, Shi, Yahweh, mai girma ne kuma zai iya yin komai. AT: "Ba abin da ni, Yahweh ba zan iya yi ba!"
"A lokacin da na zaba, kamar war haka"
"Sai Sarai ta yi musu ta na cewa"
"Yahweh ya amsa"
"I, kin yi dariya." Ma'anar wannan ita ce "A'a, ba gaskiya ba; haƙiƙa kin yi dariya."
"ya sa su a hanyarsu" ko " domin ya yi bankwana da su". Ya kasance mai ladabi a ɗan yi nisa tare da baƙi yayin da suke barin.
Allah yayi amfani da tambaya a nuna cewa zai yi wa Ibrahim magana game da wani muhimmin abu, kuma zai fi kyau ya yi haka. AT: "Bai kamata in ɓoye wa Ibrahim abin da na ke shirin yi ba, kuma ba zan ɓoye ba ... shi." ko " Ya kamata in faɗa wa Ibrahim abin da na ke shirin yi, kuma zan faɗa ma shi... shi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan albarkaci dukka al'uman duniya ta wurin Ibrahim"
"cewa zai shiryar" ko "don ya umarta"
Yahweh na magana game da kanshi kamar wani ne dabam. AT: "domin kiyaye abin da ni, Yahweh na ke so ... Ni, Yahweh, zan kawo ... na faɗa"
Wannan na faɗin yadda za a kiyaye hanyar Yahweh.
"domin Yahweh ya albarkace Ibrahim kamar yadda ya ce zai yi." Wannan na nufin alkawarin albarkar Ibrahim na mayar da shi babban al'uma.
Ana iya juya waɗannan kalmomi domin a nuna cewa kalmar "kuka" na nufin "zargi" ne. AT: "Mutane dayawa na zargin 'yan Sodom da Gomora akan aikata mugayen abubuwa"
"sun aikata zunubi da yawa"
"Yanzu zan sauka zuwa Sodom da Gomara"
Yahweh na magana kamar ta wurin zargin da ke zuwa daga mutanen da suka wahala ne ya san abin da yake faruwa. AT: "muguntar ya kai yadda mutanen da suke zargin su ke faɗi"
"bar inda Ibrahim ya ke"
"Ibrahim suka tsaya tare da Yahweh"
"matso wurin Yahweh"
Ibrahim na maganar hallakar da mutane kamar sharar da ake yi da tsin-tsiya. AT: "hallakar"
"adalan mutane tare da mugayen mutane"
Ibrahim ya ci gaba da magana da Yahweh.
Ibrahim na begen cewa Yahweh zai ce, "Ba zan hallakar da shi ba." AT: "I tsamanin ba za hallakar da shi ba, ta dalilin adalai hamsin da su ke can"
"Ba zan taba so ka yi abu irin wannan ba" ko "Bai kamata ka so aikata abu irin wannan ba"
"abu haka kamar kisa"
Wannan za a iya bayyana a cikin aikatau. AT: "ka bi da adalai dai-dai da yadda za ka bi da mugaye"
Ibrahim ya yi amfani da tambaya domin ya bayana abin da ya ke tsamani Allah ya yi. AT: "Na tabbata Mai Hukuncin duniya zai yi adalci" ko "Tun da ya ke kai ne mai hukuta dukka duniya, tabas za ka yi abin da ke dai-dai!"
Kalmar "Duba" a nan na jawo hankalin mu ne ga maganar da ke zuwa a gaba.
"Gafarce ni domin ƙarfin zuciyar da na ɗauka wajen managa da kai" or "Garfarce rashin tsoro na wajen yin magana"
Ibrahim na nuna bangirman da ya ke da shi ga Yahweh ta wurinmagana kamar yana yi da wani dabam. AT: "a gare ka, ya Ubangijina"
Wannan ƙarin magana ne da bayana Ibrahim a matsayin mutum da zai mutu ya kuma zama ƙura da toka. AT: "mutum kawai mai mutuwa" ko "marasa muhimminci kamar ƙura da toka"
"adalai arba'in da biyar kawai"
"in ya ka sa da adalai mutum biyar"
"Ibrahim ya yi magana da Yahweh"
Ma'anar wannan shine "A ce ka sami adalai guda arba'in a Sodom da Gomora."
"Yahweh ya amsa"
"Ba zan hallakar da biranen ba, in na sami adalai mutum arba'in a can"
"adalai mutum talatin" ko "mutanen kirki guda talatin"
"Gafarce ni domin ƙarfin zuciyar da na ɗauka wajen managa da kai" or "Garfarce rashin tsoro na wajen yin magana"
"adalai mutum ashirin" ko "mutanen kirki guda ashirin"
"Wataƙila fa ka sami adalai mutum goma a can"
"adalai mutum goma" ko "mutanen kirki guda goma"
"Sai Yahweh ya amsa"
"Idan na sami mutane goma adalai a can"
"Yahweh tashi daga wurin" ko "Yahweh ya tafi"
1Mala'ikun guda biyu suka zo Sodom da yamma, a lokacin da Lot ke zaune a ƙofar Sodom. Da Lot ya gan su sai ya tashi ya tare su, ya sunkuyar da fuskarsa har ƙasa.2"Ya ce, "Ya shugabannina, ina roƙon ku daku biyo ta gidan baranku, ku kwana ku wanke ƙafafunku. Da safe sai ku tashi ku yi tafiyarku." Suka amsa, "A'a za mu je mu kwana a kwararo."3Amma ya yi ta roƙon su, sai suka tafi tare da shi, suka shiga gidansa. Ya shirya musu abinci ya kuma soya musu gurasa marar gami suka ci.4Amma kafin su kwanta, mazajen birnin, wato mazajen Sodom, suka kewaye gidan, da tsofaffinsu da matasansu, da dukkan mazajen birnin.5Suka kira Lot, suka ce da shi, "Ina mutanen da suka zo gidanka yanzu? Fito da su gare mu, domin mu kwana da su."6To sai Lot ya fita wajen ƙofa ya kulle ƙofar a bayansa.7Ya ce da su, "Ina roƙon ku 'yan'uwana, kada ku yi aikin mugunta irin wannan.8Duba ina da 'ya'ya mata guda biyu da ba su taɓa kwana da maza ba. Ina roƙon ku in kawo muku su, ku yi duk abin da kuka so da su. Amma kada ku yi wa mazajen nan komai, domin suna nan ne a ƙarƙashin kulawata9Suka ce, "Ka tsaya can!" Haka kuma suka ce, "Shi da ya zo baƙunta, yanzu kuma ya zama alƙalinmu! Yanzu za mu ci mutuncika fiye da yadda za mu yi musu." Suka matsa wa Lot da kuma mutanen, suka zo kusa da ƙofar domin su ɓarke ta.10Amma sai mutanen suka miƙa hannuwansu suka shigo da Lot ciki suka kulle ƙofar.11Sai bãƙin na Lot suka bugi mutanen da makanta, wato mutanen dake wajen ƙofar gidan, duk da matasansu da tsofaffinsu duk ƙarfinsu ya ƙare a lokacin da suke ƙoƙarin ɓarke ƙofar12Sai mutanen suka ce da Lot, "Ko kana da wani naka a nan? Ko surukai, ko 'ya'ya maza da mata da duk wanda kake da shi a cikin birnin, ka fitar da su daga birnin nan.13Domin mu na gab da hallaka wannan wurin, saboda zargin da ake yi wa birnin a gaban Yahweh ya yi yawa shi ya sa ya aiko mu domin mu hallaka shi."14Sai Lot ya tafi ya yi magana da surukansa, wato mazajen da suka yi alƙawari zasu auri 'ya'yansa mata, ya ce "Ku hanzarta, ku fita daga wannan wurin, domin Yahweh na gab da hallaka birnin." Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.15Da safiya ta yi, mala'ikun suka hanzarta Lot, "Ka fito da kai da matarka da 'ya'yanka mata guda biyu dake a wannan wuri, domin kada a share ku tare a cikin wannan hukunci na birni."16Amma ya yi jinkiri. Sai mazajen suka kama hannuwansa, da hannun matarsa, da hannuwan 'ya'yansa mata guda biyu, saboda Yahweh ya yi masa jinƙai. Suka fitar dasu bayan birnin.17Da suka fitar dasu waje, ɗaya daga cikin mazajen ya ce, "Ku tserar da rayukanku! Kada ku waiga baya, ko kuma ku tsaya a wannan filin. Ku gudu kan duwatsu domin kada a hallakar da ku."18Lot yace da su, "A'a shugabannina ina roƙon ku!19Baranku ya sami tagomashi a wurinku, kuma kun nuna mini kirki sosai da kuka ceci raina, amma ba zan iya kai wa kan duwatsu ba, masifar za ta same ni, kuma zan mutu.20Duba ga wani birni can, ya isa in je can domin tsira, kuma ƙarami ne, ina roƙo ku bar ni in je can in tsira (ba ɗan ƙarami ba ne?), rayuwata kuma za ta cetu."21Ya ce da shi, "Shikenan, na biya maka wannan buƙata, kuma ba zan hallaka birnin da ka faɗa ba.22Ka yi hanzari ka gudu can, domin ba zan yi wani abu ba sai ka isa can." Shi ya sa ake kiran wurin Zowar.23Rana ta ɗaga bisa duniya a lokacin da Lot ya isa Zowar.24Sai Yahweh ya saukar da ruwan wuta da matsanancin zafi bisa Sodom da Gomora.25Ya hallaka waɗannan biranen, da filayen, da duk mazauna biranen da tsire-tsire da suka yi girma a ƙasa.26Amma matar Lot dake bayansa, ta waiwaya baya, sai ta zama umudin gishiri. Ibrahim ya tashi da sassafe ya je wurin da ya tsaya tare da Yahweh.27Ya duba wajen Sodom da Gomora da kuma dukkan filayen.28Da ya duba sai ya ga hayaƙi na tashi daga filin kamar na hayaƙin matoya.29To lokacin da Allah ya hallakar da biranen da filayen, Allah ya tuna da Ibrahim Ya fitar da Lot daga wannan hallakarwar a lokacin da ya hallaka biranen da Lot ya zauna.30Amma Lot ya fita daga Zowar zuwa duwatsu tare da 'ya'yansa mata guda biyu, domin yana jin tsoron zama a Zowar. Sai ya zauna a cikin kogon dutse, shi da 'ya'yansa mata guda biyu.31Babbar ta ce da ƙaramar, "Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wanda zai kwana damu bisa ga tsarin dukkan duniya.32Ki zo, mu sa mahaifinmu ya sha ruwan inabi ya bugu, sai mu kwana da shi, domin mu wanzar da sunan mahaifinmu."33Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi ya bugu a wannan daren. Sai babbar ta je ta kwana da mahaifinta, bai ma san lokacin da ta kwanta ba, bai kuma san lokacin da tashi ba.34Washegari Sai babbar ta ce da ƙaramar, "Kin ga, jiya na kwana da mahaifina. Yau kuma sai mu sa shi ya sake buguwa da ruwan inabi, ke kuma sai ki je ki kwana da shi, domin mu wanzar da sunan mahaifinmu."35Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi ya bugu, sai ƙaramar ta je ta kwana da shi. Bai san lokacin da ta kwanta ba haka kuma bai san lokacin da ta tashi ba.36Ta haka 'ya'yan Lot guda biyu suka yi juna biyu ta wurin mahaifinsu.37Ta farin ta haifi ɗa namji ta sa masa suna Mowab. Shi ne ya zama uban Mowabawa a yau.38Ita ma ƙaramar 'yar ta haifi ɗa namiji sai ta ba shi suna Ben Ammi. Shi ne ya zama uban mutanen Ammon na yau.
A Farawa 18 an bayana cewa mutane biyu sun tafi Spdom. A nan a bayana mana cewa mala'iku ne. (Duba: Farawa 18:22)
"hanyar shigar birnin Saduma." Akwai ganuwa kewaye da birnin, lalle ne mutane su bi ta ƙofar kafin su shiga. Wannan muhimmin wurin ne a birni. Muhimman mutane ne suke zama a wurin.
Ya sa gwiywar sa a ƙasa, sai goshinsa da hancinsa kuma na ƙasa.
Wannan kalmar bangirma ne da Lot ya ba wa mala'ikun.
"Na roƙe ku, ku tsaya a gidan bawanku"
Mutanen na son wanke ƙafafunsu bayan tafiya.
Lokacin da mala'ikun suna magana, suna magana game da su biyu ne ba tare da Lutu ba. Su biyun sun shirya su kwana a kwararo. Wasu harsuna na iya amfani da "mu" a nan.
Wannan a nufi filin gari ne, na jama'a.
"suka juya su tafi tare da shi"
"kafin mutanen gidan Lot su kwanta su yi barci"
"mazajen birni, wato, mazajen Sodom" ko kuma "mazajen birnin Sodom"
"daga kananan matasan zuwa tsofaffi." Ma'anar wannan shine "mazaje na kowa ne shekara" na Sodom, suka kuma kewaye gidan Lot.
"wancan ya shiga gidan ka
"mu yi jima'i da su." Mai yiwuwa harshenku na wata hanyar faɗin wannan cikin da'a. AT: "mu san su ta wurin kwana da su"
"bayan ya fita" ko "bayan ya wuce"
"kada ku aikata wani mummunan abu haka" ko "kar kuyi irin wannan mummunan abu"
"duk abinda kuke so" ko "duk abinda kuke tunani dai-dai ne"
Mutane biyun baƙi a gidan Lot, kuma lalle ne ya kare su. Kalmar "rufa" na matsayin gidan Lot ne, da kuma tsare su da Lutu zai yi. AT: "a cikin gida na, kuma Allah ya bukace ni in kare su"
"ma sa gefe!" ko "tashi mana a hanya!" (UDB)
"Wannan da ya zo daga waje" ko "Wannan baƙon da ya zo zama a nan"
"Lot." Mutane na magana a tsakanin su. Idan wannan magana ba a fili ya ke ba a harshenku, kuna iya ambata cewa mutanen na magana game da Lot ne a nan, kamar a UDB.
"yanzu yana tunani cewa ya na da yanci ya gaya mana abin da ke daidai da wanda ba dai-dai ba" ko "ba za mu yarda masa ya zo ya hana mu aikata abin da mu ke so ba"
"kuma ba shi wani dalili mai kyau na yin haka, shi"
"Domin ka na gaya mana cewa abin da mu ke yi ba daidai ba, mu"
Mazan sun yi fushi da Lot domin ya ce, "kada ku aikata wannan muguntar" (Farawa 19:6), to yanzu suna yi ma sa barazana cewa za su aikata muguntar fiye da yadda ya ke tunani a farko. AT: "za mu aikata mugunta a gare ka fiye da yadda zamu yi musu"
Ma'ana mai yiwuwa shi ne 1) "suka ci gaba da zuwa kurkusa da mutumin, wato Lot, har sun kai kusa da inda za su iya ɓarke kofar" ko 2) suka ture Lot zuwa bango, ko ƙofar gidan, suna shirin ɓarke ƙofar.
"Amma bãƙi biyun na gidan Lot" ko "Amma mala'iku biyun"
Harshenku na iya bukaci a ambata cewa mutanen sun buɗe kofar tukunna. AT: "mutanen suka buɗe kofar domin su iya mika hannayensu su jawo... su, sai suka kulle"
Kalmar "bugi da makanta" ba ya nufi cewa bãƙin sun dau hannu ko wanni abu suka bugi mutanen kamar yadda muka gane kalmar "bugi" ba. AT: "bãƙin na Lutu suka makantar da mutanen" ko "sun hana su iya gani"
"mutane na kowani shekara." Wannan na jadada cewa bãkin sun makantar the dukka mazan. Wannan na iya nuna matsayin mutum maimakon shekaru. AT: "da manya da kanana"
"Sai mutane biyun suka ce" ko "Sai mala'iku suka ce"
"Akwai wani da ke na gidanka kuma a cikin birnin?" ko "Kana da wani ɗan iyalinka a wannan wurin?"
"wani daga iyalinka da ke zama a birnin"
Wannan kalmar "mu" na nufin mala'ikun ne su biyu kadai zasu hallakar da birnin, ba tare da Lot ba. Idan harshenku na da yadda za a iya bayana haka, to a yi amfani da shi a nan.
Ana iya canja kalmomin nan ta wani hanya domin a bayana kalmar "zargi." AT: "mutane da yawa sun kawo kuka cewa mutanen birnin nan na aikata mugunta" da kuma yadda aka fassara waɗannan kalmomin a Farawa 18:20
"Don haka Lot ya bar gidan"
Kalmomin "mazajen da suka yi alkawarin aure 'ya'yansa mata" na bayana kalmar "surukai" ne. AT: "mazajen da za su aure 'ya'yansa mata" ko "samaran 'ya'yansa mata"
"kafin tashiwan rana"
"tashi yanzu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "domin kada Yahweh ya hallakar da kai sa'ad da yana hukunta mutanen wannan birnin"
"Birnin" a nan na nufin mutanen ne.
"Amma Lot ya ɗan dakata" ko "Amma Lot ba ya fara tafiya"
"sai mazaje biyun suka kama" ko "sai mala'iku suka kama"
ya ji tausayin Lot." Ana bayana Yahweh a matsayin "mai jinƙai" domin ya kare Lot da iyalinsa ba tare da hallakar da su ba tare da mutanen Sodom ba.
"Sa'ad da da maza biyun suka fitar da Lot da iyalinsa waje"
Wannan wani hanyar faɗa masu cewa su tafi a guje domin kar su mutu. AT: "ku tafi a guje domin ceton rayuwanku!"
A fahimci cewa ana magana game da birnin ne. AT: "Kada ku juya baya ku dubi birnin" ko "Kada ku juya baya ga Sodom"
Wannan na nufin filin wajajen Kogin Yodan.
A fahimci cewa za a share su da mutanen birnin. AT: "ko Allah ya hallakar da ku tare da mutanen birnin"
Ana magana game da "gamshe" wani kamar 'tagomashi" wani abu ne da ake iya samuwa."a wurinku" kuma na wakilce tunani ko ra'ayi mutum. AT: "Kun sami gamsuwa a gare ni"
AT: "kun yi mini kirki sosai ta wurin ceton raina"
Ana maganar yadda Lot ba zai iya barin Sodom ba kafin Allah ya hallakar da birnin kamar "masifar" wani mutum ne da zai bi Lot a guje har ya kama shi. AT: "Lalle ne ni da iyalina mu mutu idan Allah na hallakar da mutanen Sodom domin duwatsun na da nisa, ba za su iya kai wurin ba a cikin lafiya"
Ana iya ba da gamsashen bayani game da roƙon Lot a haka. AT: "maimakon hallakar da wancan birnin, bari in gudu zuwa wurin domin tsira"
Wannan na nufin cewa Lot da iyalinsa za su cetu. AT: "domin in kasance a raye" ko "domin in rayu"
"Zan yi abin da ka tambaya"
Ana iya ba da gamsashen bayani wannan. AT: "ba zan hallakar da sauran biranen ba"
Masu juya wannan na iya sharihinta cewa "sunan Zowar na kamar kalmar da ke nufi 'ƙarami' a Ibraniyanci. Lutu ya kira wannan garin 'ƙarami' a Farawa 19:20."
"Rana ta tashi bisa duniya." Ana iya barin wannan maganar "bisa duniya" ba tare wani bayani ba kamar yadda ya ke a UDB.
An nuna cewa dangin Lutu suna tare da shi. AT: "lokacin da Lutu da iyalinsa suka isa Zowar"
Jimlar "daga Yahweh" na nuna ikon Allah wajen sa farar wuta da wuta mai zafi su sauko a birnin. AT: "Yahweh ya sa farar wuta da kuma wuta mai zafi su sauko da sama a Sodom da Gomora"
Ana amfani da waɗannan kalmomin guda biyu tare don bayyana abu ɗaya. AT: "konewar sulfur" ko "ruwan sama mai zafi"
Wannan na nufi Sodom da Gomora ne musamman, amma kuma da wasu garuruwa guda uku.
"mutanen da suke zama a biranen"
"ta zama gunkin gishiri" ko "gikin ta ya zama kamar dutsen gishiri." Domin ta yi wa mala'ikan rashin biyayya wajen juya baya, Allah ya sa ta zama wani abu kamar gunki da aka yi da gishiri.
Kalmar nan "duba" na jawo hankali ga maganar mai ban mamaki da ke zuwa.
Wannan na nuna cewa hayaƙin na da yawa. AT: "kamar hayaƙi daga babban wuta"
Aya 29 ya taƙaita wannan sura.
Wannan na bayana dalilin da ya sa Allah ya ceci Lot. Wannan bai nuna cewa Allah ya manta da Ibrahim ba ne a baya, amma ya dubi Ibrahim ya kuma nuna masa jinƙai. AT: "Allah yayi tunani game da Ibrahim sai ya kuma nuna masa jinƙai"
"daga hallakar" ko "daga hatsari"
An yi amfani da maganar cewa "fita daga" domin Lot ya tafi inda yake da tudu a duwatsun ne.
"'yar farin Lot"
"ƙaramar 'yar" ko "kanwar ta"
"Duniya" a nan na nufi mutanen ne. AT: "kamar yadda mutane ke yi a koina"
Ana iya ba da gamsashen bayani cewa manufar su shine su sa shi ya bugu. AT: "sha ruwan inabi har sai ya bugu"
Wannan na maganar ba wa Lot zuriya kamar iyalinsa na jere ne kuma ana ƙokarin kara tsayi. AT: "domin mu iya haifar da 'ya'ya da za su zama zuriyar mahaifinmu"
"bai san komai da ya faru ba" ko "bai ma san cewa ta kwanta da shi ba"
A fassara waɗannan kalmomi kamar yadda aka yi a Farawa 19:31.
Ana iya ba da gamsashen bayani cewa manufar su shine su sa shi ya bugu. AT: "sha ruwan inabi har sai ya bugu"
Wannan na maganar ba wa Lot zuriya kamar iyalinsa na jere ne kuma ana ƙokarin kara tsayi. AT: "domin mu iya haifar da 'ya'ya da za su zama zuriyar mahaifinmu"
"bai san komai da ya faru ba" ko "bai ma san cewa ta kwanta da shi ba"
"suka ɗauki ciki ta wurin mahaifinsu"
"Shi ne"
"mutanen Mowab da suke a raye yanzu"
Kalmar "a yau" na nufin lokacin da marubicin littafin Farawa na a raye ne. An haifi marubucin wannan littafi da lokacin da yayi wannan rubutu shekaru da yawa ne bayan rayuwar Lot da iyalinsa sun mutu.
Wannan sunan namiji ne.
"zuriyar Ammon"
1Ibrahim ya bar wurin ya gangara zuwa Negeb, ya zauna tsakanin Kadesh da Shur. Shi baƙo ne mazaunin Gerar.2Ibrahim yace game kuma da Saratu matarsa, "Ita 'yar'uwata ce" Sai Abimelek sarkin Gerar ya aika mazajensa suka ɗauko Saratu.3Amma Allah ya zo wurin Abimelek a mafarki da duhu, ya ce da shi, "Duba kai mataccen mutum ne saboda matar daka ɗauko, domin ita matar mutumin ce."4Abimelek kuma bai kusance ta ba ya ce, "Ubangiji ko zaka kashe har ma al'umma mai adalci? Ashe ba shi da kansa ne ya ce da ni 'ita 'yar'uwataba ce?'5Har ma ita da kanta ta faɗa, cewa 'Shi ɗan'uwana ne.' Na yi wannan bisa nagartar zuciyata, da kuma rashin laifofin hannuwana."6Sai Allah yace da shi a cikin mafarki, I nima na sani ka yi haka ne bisa ga nagartar zuciyarka, Ni ma kuma na hana ka yi mini zunubi. Saboda haka ne ban bar ka ka taɓa ta ba.7Saboda haka ka mayar wa mutumin matarsa domin shi annabi ne. Zai yi maka addu'a kuma za ka rayu. Amma in ba ka mayar da ita ba, ka sani tabbas kai da dukkan abin da ke naka zaku hallaka."8Abimelek ya tashi da asuba ya kira dukkan bayinsa gare shi. Ya faɗa musu duk waɗanna abubuwa, sai mazajensa suka firgita.9Sai Abimelek ya kira Ibrahim yace da shi, "Me kenan ka yi mana? Yaya nayi maka laifi, da ka jawo wa mulkina da ni kaina wannan zunubi? Ka yi mini abin da bai kamata a yi ba."10Abimelek yace da Ibrahim, "Meyasa ka yi wannan abin?"11Ibrahim yace, domin na yi tsammanin cewa hakika babu tsoron Allah a wannan wurin, kuma zasu kashe ni saboda matata.'12Bayan haka kuma hakika ita 'yar'uwata ce, 'yar mahaifina ce, amma ba 'yar mahaifiyata ba, sai kuma ta zama matata.13Lokacin da Allah ya sa na bar gidan mahaifina in yi tafiya daga wannan wuri zuwa wancan wuri, na ce da ita dole ne ki nuna mini wannan aminci a matsayin matata: A duk inda muka je ki faɗi haka game da ni, "Shi ɗan'uwana ne.""14Sai Abimelek ya kwashi tumaki da takarkari da maza da mata na bayi ya bada su ga Ibrahim. Daga nan ya mayar da Saratu, matar Ibrahim a gare shi.15Abimelek yace, "Duba, wannan ƙasar tawa tana gabanka. Ka zauna a duk inda ya yi maka kyau."16Ga Saratu kuma ya ce, duba, na ba ɗan'uwanki azurfa dubu. Wannan domin ya shafe duk wani laifi dana yi maku ne a fuskarku dukka, da kuma a gaban kowa da kowa, hakika kun yi abin da ke dai-dai."17Sai Ibrahim ya yi addu'a sai Allah ya warkar da Abimelek, da matarsa, da bayinsa mata domin su iya haifar 'ya'ya.18Domin Yahweh yasa dukkan matan gidan Abimelek su zama marasa haihuwa baki ɗaya, Saboda Saratu matar Ibrahim.
Wannan wani hamada ne gabashin iyakar yankin masar
"ya sa mazajensa su je su kawo masa Sarai"
"Allah ya bayyana a wurin Abimelek
kalmar "duba" na kara jadada game da abin da zai biyo baya. "Saurare ni" (UDB)
Wannan wani mumunar hanya ce na cewa sarkin zai mutu. AT: "lalle ne ka kusan mutuwa" ko "Za ɗauke ran ka"
"matar aure ce"
Ana amfani da wannan kalmar wajen sa alamar canja labari zuwa bayani game da Abimelek.
Wannan wani hanyar cewa ne bai yi jima'i da ita ba. AT: "Abimelek bai kwana da Sarai ba" ko "Abimelek bai taba Sarai ba"
"al'umma" a nan na nufi mutanen ne. Abimelek ya damu cewa ba shine kadai Allah zai hukunta ba, har da mutanen sa. AT: "har ma da mutanen da basu da laifi"
Wannan yana da ambato cikin zance. Ana iya bayyana su azaman maganganun kai tsaye. AT: "ba shi da kansa ne ya ce da ni wai 'ita 'yar'uwarsa ba ce? Har ita ma kanta ta ce shi ɗan'uwanta ne"
Anan "zuciya" na nufin tunaninsa ko ƙudurisa. "hannu" kuma na nufi abun da ya aikata. AT: "Na aikata wannan da nufin mai kyau" ko "Na yi wannan ba tare da nufin aikata mugunta ba"
"Allah ya ce da Abimelek"
Wannan maganar na nufi yin jima'i da Sarai. AT: "ka kwana da ita"
"matar Ibrahim"
"Zan bar ka ka rayu"
"dukkan mutanen ka"
"Ya faɗa musu dukka abubuwan da Allah yace da shi"
Abimelek na amfani da tambaya ya tuhume Ibrahim. AT: "Ka aikata mana mumunar abu!" ko "Duba abin da ka yi mana!"
Abimelek na amfani da tambaya ya tunashe Ibrahim cewa bai yi masa zunubi ba. AT: "Ban yi maka laifin komai ba da har za ka kawo ... zunubi"
Ana maganar sa mutum ya aikata laifi kamar wani abu ne da ake iya ɗaura wa wani a kai. AT: "da zaka ɗaura wa ni da mulkina aikata irin wannan mumunar zunubi"
"mulki" a nan na nufi mutane ne. AT: "a bisa mutanen da nake mulki"
"Bai kamata ka yi mini haka ba"
"Me yasa ka yin wannan?" ko "Me dalilin da yasa ka aikata wannan?" Ana iya ba da gamsashen bayanin abin da Ibrahim ya aikata. AT: "Me yasa ka ce da ni Sarai 'yar'uwarka ce?"
AT: "Domin na ni tunanin cewa babu wani mai tsoron Allah a nan, wani na iya kashe ni domin ya ɗauki mata ta."
Anan "wuri" yana nufin mutane. AT: "babu wani a nan Gerar da ke tsoron Allah"
"Amma da gaske ma Sarai 'yar'uwata ce" ko "har ila yau, lalle Sarai 'yar'uwata ce"
"Mahaifin ɗaya ne, amma mahaifiyar dabam ne"
A aya 13 Ibrahim ya ci gaba da ba Abimelek amsa.
Anan "gidan" na nufin iyalin Ibrahim. AT: "mahaifina da sauran iyali na"
AT: "Na ce da Sarai, ina so duk inda muka je ta nuna min aminci wajen faɗin cewa ni ɗan'uwanta ne"
"Abimelek ya kawo wasu" (UDB)
"Abimelek ya cewa Ibrahim"
Wannan wani hanyar cewa "Ina mika dukka ƙasa tawa a gare ka"
"Yi zama a inda ka ke so"
"1, 000"
Ana maganar bayar da kudi domin nuna cewa ba ta da laifi kamar wani marufi ne da aka rufe laifi domin ka da kowa ya gani. AT: "Ina ba shi wannan, domin duk waɗanda su ke tare su san cewa ba ka aikata wani laifi ba"
Ana iya bayana "yin abin da ke dai-dai" ta wani hanya. AT: "kowa da kowa zai san cewa ba ka da laifi"
"ba za su iya samun 'ya'ya ba baki ɗaya"
Ana iya ba da gamsashen bayani haka. AT: "domin Abimelek ya ɗauki matar Ibrahim Sarai"
1Yahweh ya saurari Saratu kamar yadda ya ce zai yi, Yahweh kuwa ya yi wa Saratu kamar yadda ya alƙawarta.2Saratu kuwa ta yi juna biyu ta haifa wa Ibrahim ɗa a cikin kwanakin tsufansa, a daidai lokacin da Yahweh ya yi masa magana.3Ibrahim kuma ya raɗa wa ɗansa suna, wato wannan ɗa da aka haifa masa, wannan da Saratu ta haifa masa wato Ishaku.4Ibrahim ya yi wa ɗansa Ishaku kaciya da yayi kwana takwas, kamar dai yadda Allah ya umarce shi.5Ibrahim na da shekaru ɗari a lokacin da aka haifa masa Ishaku.6Saratu ta ce, "Allah ya sa ni dariya, duk wanda ya ji zai yi dariya tare da ni."7Wane ne zai ce da Ibrahim cewa Saratu za ta yi masa renon 'ya'ya, kuma duk da haka na haifa masa ɗa a kwanakin tsufansa!"8Yaron ya yi girma aka yaye shi, Ibrahim ya yi babbar liyafa a ranar da aka yaye Ishaku.9Saratu ta ga ɗan Hajara Bamasariya, da ta haifa wa Ibrahim, na ba'a.10Saboda haka ta ce da Ibrahim, "Ka kori wannan baiwar matar da ɗanta: domin ɗan wannan baiwar ba zai ci gãdo, tare da ɗana Ishaku ba."11Wannan abin ya yi wa Ibrahim zafi a rai saboda ɗansa.12Amma Allah yace da Ibrahim, "Kada ka damu saboda yaron, da kuma saboda wannan matar baiwarka. Ka saurari kalmominta kan duk abin da ta faɗa maka kan wannan al'amari, saboda ta wurin Ishaku ne za a kira zuriyarka.13Hakanan zan sa ɗan baiwar matar ya zama al'umma, domin shi zuriyarka ne."14Ibrahim ya ta shi da asuba, ya ɗauki gurasa da goran ruwa, ya ba da shi ga Hajara ya ɗora shi a kafaɗarta. Ya ba ta ɗan ya sallame ta ta tafi. Ta tafi ta yi ta yawo cikin jejin Beyersheba.15Da ruwan da ke cikin goran ruwan ya ƙare, sai ta yashe da ɗan a gindin wasu ciyayi.16Sai ta tafi ta zauna can nesa dai-dai harbin kibiya, domin ta ce, "Kada in ga mutuwar ɗana." Da ta zauna daura da shi sai ta ta da murya ta yi kuka.17Allah ya ji kukan ɗan, sai mala'ikan Allah ya kira Hajara daga can sama, ya ce da ita, "Me ke damun ki, Hajara? Kada ki ji tsoro, domin Allah ya ji kukan ɗan a inda yake.18Tashi ki ɗauki yaron, ki ƙarfafa shi, domin zan maishe shi babbar al'umma."19Sai Allah ya buɗe idanunta, sai ta ga rijiyar ruwa. ta je ta cika gorar da ruwa, ta ba ɗan ya sha.20Allah na tare da ɗan, ya kuma yi girma. Ya yi rayuwa cikin jeji sai ya zama mafarauci.21Ya yi rayuwa a jejin Faran, mahaifiyarsa kuma ta aura masa mata daga ƙasar Masar22Sai ya zamana a lokacin da Abimelek da Fikol shugaban sojojinsa ya yi magana da Ibrahim, cewa, "Allah na tare da kai a cikin dukkan al'amuranka.23Yanzu sai ka rantse mini cewa ba zaka yi mini ƙarya ba, haka kuma 'ya'yana, da zuriyata. Ka nuna mini da kuma ƙasar da kake zaune a ciki irin wannan alƙawari mai aminci da na nuna gare ka."24Ibrahim yace "Na rantse."25Ibrahim kuma ya miƙa kukansa ga Abimelek game da rijiyar ruwa da bayin Abimelek su ka ƙwace daga wurinsa.26Abimelek yace "Ban san wanda ya yi wannan abu ba. Ba ka faɗa mini ba tuntuni; Ban ji al'amarin ba sai yau."27Sai Ibrahim ya ɗauki tumaki da shanu ya ba Abimelek, su biyun suka yi yarjejeniya.28Sai Ibrahim ya ware raguna bakwai na garken da kansu.29Abimelek yace da Ibrahim, "Mene ne ma'anar waɗannan matan tumakin daka shirya su da kansu?"30Ya amsa, waɗannan matan tumakin guda bakwai zaka karɓa daga hannuna, domin su zama shaida domina, cewa ni na haƙa wannan rijiya."31Sai ya kira wannan wurin Biyasheba, saboda a can ne dukkan su suka yi rantsuwa.32Suka yi yarjejeniya, Daga nan sai Abimelek da Fikol, shugaban sojojinsa, ya koma ƙasar Filistiyawa.33Ibrahim ya dasa itacen sabara a Biyasheba. a can ya yi sujada ga Yahweh, Allah madawwami.34Ibrahim ya zauna a matsayin baƙo a ƙasar filistiyawa na kwanaki masu yawa.
Kalmar "saurari" a nan na nufin cewa Yahweh ya taimakawa Sarai wajen samun ɗa. AT: "Yahweh ya taimakawa Sarai"
"ta haifa ɗa wa Ibrahim"
"sa'ad da Ibrahim ya tsufa kwarai"
"a dai-dai lokacin da Allah yace da shi zai faru"
"Ibrahim ya sa wa ɗan jariri da aka haifa masa, wanda Sarai ta haifa, Ishaku" ko "Ibrahim ya ba sunan ɗan su Ishaku"
"Sa'ad da Ishaku ɗansa na kwana ta takwas, Ibrahim ya yi masa kaciya"
"ya umarce Ibrahim ya yi"
"100"
Sarai na dariya domin tana murna da kuma mamaki. Ana iya bayana wannan haka. AT: "Allah ya sa ni farin ciki"
Ana iya ba da gamsashen bayani game da abin da mutane za su ji. AT: "duk wanda ya ji abin da Allah ya yi mini" (UDB)
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Ba wanda zai ce da Ibrahim, Sarai za ta reno 'ya'ya"
Wannan wata hanya ne cikin da'a da ake nufi da shayas da 'ya'ya. AT: "shayas da jariri da nono ta"
"yaye" a nan hanya ce mai ladabi na cewa yaron ya gama da nono. AT: "Ishakuya girma kuma baya bukatar shan nono mahaifiyarsa. Ibrahim ya yi babbar liyafa"
Ana iya ambaci sunan ɗan Hajara. AT: "Isma'ila ɗan Hajara na Masar da Ibrahim"
Ana iya bayana cewa ya na yi wa Ishaku ba'a. AT: "yi wa Ishaku dariya"
"Sarai ta cewa Ibrahim
"salleme" ko "cire" (UDB)
Wannan na nufin Hajara ne da Isma'ila. Mai yiwuwa Sarai ba ta ambaci su da sunayen su domin tana fushi da su.
"tare da ɗa na Ishaku"
"Ibrahim bai ji dadin abin da Sarai ta faɗa ba"
"domin ta magana game da ɗan sa." Ana nufin da ɗan sa, Isma'ila.
"Kada ka yi fushi game da yaron da baiwarka"
AT: "Ka yi duk abin da Sarai ta ce da kai game da su"
Kalmar "za a kira" na nufin cewa waɗanda aka haifa ta wurin Ishaku ne Allah zai yi amfani da su a matsayin zuriyar alkawari da Ibrahim. AT: "Ishaku ne zai kasance kakan zuriyar da na alkawatar ma ka"
Kalmar "al'umma" a nufin cewa Allah zai ba shi zuriya mai girma da za su zama babban jama'a. AT: "Zan sa ɗan baiwar ma ya zama uban babban al'umma"
Ma'ana mai yiwuwa 1) wannan na nufi kowani irin abinci, ko 2) gurasa ne musamman.
"jakar ruwa." Ana yin gorar ruwa da fatar dabba.
"da ruwan gorar ya ƙare" or "da su ka sha ruwar dukka"
Ma'anar wannan shine, nesa kamar harbin kibiya. Wannan na kamar mita 100.
AT: "Ba na so in ga yadda yaron zai mutu"
Anan "murya" tana tsaye don sautin kukanta. AT: ta ta da babban murya ta yi kuka" ko "ta yi kuka da karfi"
"muryar yaron." Anan "murya" na nufin karar kuka or maganar yaron. AT: "muryar Isma'ila"
"sama" a nan na nufin inda Allah ya kasance.
"Don me ki na kuka"
Anan "murya" tana tsaye don sautin yaron yana kuka ko magana. AT: "muryar yaron a kwance a wurin"'
"taimake yaron ya tashi tsaye"
Ma'anar maishe Isma'ila babbar al'umma shine zuriyarsa za su zama babbar al'umma. AT: "Zan mai da zuriyarsa babban al'umma"
An yi maganar yadda Allah ya sa Hajara ta ga rijiyar kamar ya ɗau hannunsa ne ya buɗe idanunta. AT: " Allah ya sa Hajara ta ga" ko "Allah ya nuna mata"
"gorar fata" ko "jaka"
"yaron" ko "Isma'ila"
Ma'anar wannan maganar "tare da" shi ne Allah ya taimakawa ko ya sa wa ɗan albarka. AT: "Allah ya kulla da yaron" ko "Allah ya sa wa yaron albarka"
"gwanancewa a amfani da baka da kibiya"
"samo masa mata"
Wannan maganar na nuna farkon wani sabon sashin labarin ne. Idan harshenku na da yadda kuke faɗin wannan, ana iya amfani da shi a nan.
Wannan sunan namiji ne.
Wannan maganar "tare da kai" na ma'anar cewa Allah ya taimake ko albarkaci Ibrahim. AT: "Allah ya albarkaci ayyukan ka"
Wannan kalmar "yanzu" baya ni "a dai-dai wannan lokacin", amma an yi amfani da shi ne wajen jawo hankali ga maganar da ke zuwa. AT: "Saboda haka"
Ma'anar wannan shi ne rantsuwa da babban iko, a wannan wurin kuma, Allah ne. AT: "yi mini alkawari a gaban Allah"
"cewa ba za kayi mun karya ba"
Mutane biyun suna da alkawari a tsakanin su. AT: "kasance da aminci a gare ni da kuma kasar, kamar yadda na yi a gare ka"
Anan "ƙasar" na wakiltar mutane. AT: "ga mutanen ƙasar"
Ana iya bayyana wannan tare da bayanan da aka fahimta. AT: "Na rantse zan yi maka aminci da mutanenka kamar ya ka ke mini"
Ma'ana mai yiwuwa 1) Ibrahim na kokawa game da abin da ya faru, ko 2) "Ibrahim kuma ya tsawata wa Abimelek"
"domin bawan Abimelek ya karbawa Ibrahim rijiyarsa"
"Yau ne farkon da nake ji game da wannan"
Wannan alamar alkawarin abokantaka ne da Ibrahim ya yarda ya yi da Abimelek.
"Ibrahim ya cire raguna guda bakwai daga garken"
"Me ya sa ka ware waɗannan raguna bakwan daga tumakin?"
"za ka ɗauke"
Anan "hannu" na nufin Ibrahim ne. AT: "daga wuri na"
Ana iya sa wannan kalmar "sheda" a matsayin "tabbaci." AT: "domin tabbaci a gaban kowa da kowa"
"Ibrahim ya kira wacan wurin"
Masu fassarar wannan na iya sharihinta cewa "ma'anar Biyasheba na iya zama "rijiyar alkawari" ko "rijiyar bakwai."
"Ibrahim da Abimelek"
Wannan itaciya ce wacce ba ta da ƙwari da za ta iya girma cikin hamada. Ana iya bayyana shi gaba ɗaya. AT: "wani itace"
"Allah rayaye har abada"
Wannan na nufi tsawon lokaci mai yawa.
1Sai ya zamana bayan waɗannan abubuwa Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce da shi, "Ibrahim" Ibrahim yace, "Ga ni nan,"2Sai Allah yace, "Ka ɗauki ɗanka, tilon ɗanka, wanda kake ƙauna, Ishaku, sai ku je ƙasar Moriya. A can za ka miƙa shi baiko na ƙonawa akan ɗaya daga cikin duwatsun dake can, wanda zan faɗa maka game da shi."3Sai Ibrahim ya tashi da asuba ya ɗaura wa jakinsa sirdi, ya kuma ɗauki biyu daga cikin matasan mazajensa tare da shi, haɗe kuma da Ishaku ɗansa. Ya sassari itace domin baiko na ƙonawa, daga nan ya kama hanyarsa zuwa inda Allah ya faɗa masa.4A rana ta uku Ibrahim ya duba sama sai ya hangi wurin daga nesa.5Sai Ibrahim yace da matasansa, "Ku tsaya nan da jakin, ni da yaron zamu haura can. Za mu yi sujada daga nan sai mu dawo wurinku."6Sai Ibrahim ya ɗauki itace domin hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa Ishaku ɗansa. Sai ya ɗauki wuƙa da wuta a hannunsa; sai kuma suka tafi tare.7Ishaku ya yi magana da Ibrahim mahaifinsa ya ce, "Babana," sai ya ce, "Ga ni nan ɗana." Ya ce, Ga wuta anan da itace, amma ina ɗan ragon baikon ƙonawa?"8Ibrahim yace, "Ɗana Allah da kansa zai tanada ɗan rago domin baikon ƙonawa." Sai suka ci gaba da tafiya tare su dukka.9Sa'ad da suka zo wurin da Allah ya faɗa masa, Sai Ibrahim ya gina bagadi a can ya zuba itace a kansa. Sai ya ɗaure ɗansa Ishaku, ya ɗora shi akan bagadin bisa itacen.10Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauko wuƙa domin ya yanka ɗansa.11Sai mala'ikan Yahweh ya kira shi daga sama ya ce, "Ibrahim, Ibrahim!" sai ya ce, "Ga ni nan."12Ya ce, "Kada ka ɗora hannunka a kan yaron, kar ka yi duk wani abu da zai cutar da shi, domin yanzu na sani kana tsoron Allah, ganin cewa ba ka hana mini ɗanka ba, tilon ɗanka."13Ibrahim ya duba sama, sai ga ɗan rago a sarƙafe da ƙahonsa. Ibrahim ya ɗauki ɗan ragon ya miƙa shi baiko na ƙonawa a maimakon ɗansa.14Saboda haka Ibrahim ya kira wurin, "Yahweh zai tanada," haka kuma ake kiran wurin har yau,"A kan tsaunin Yahweh za a tanada shi."15Mala'ikan Yahweh ya kira Ibrahim daga sama a karo na biyu16ya ce - wannan shi ne furcin Yahweh - na yi rantsuwa da kaina cewa da yake ka yi wannan abu, ba ka hana ɗanka ba tilon ɗanka,17Hakika zan albarkace ka zan kuma ruɓanɓanya zuriyarka kamar taurarin sammai, kamar kuma yashin dake gaɓar teku; zuriyarka kuma zasu mallaki ƙofar maƙiyansu.18Ta wurin tsatsonka za a albarkaci dukkan al'ummar duniya, saboda ka yi biyayya da muryata."19Sai Ibrahim ya koma wurin barorinsa, suka tafi Beyarsheba tare sai ya zauna a Beyarsheba.20Ya zamana bayan waɗannan abubuwa sai, aka ce da Ibrahim "Milka ta haifi 'ya'ya, haka kuma ɗan'uwanka Nahor."21Su ne Uz ɗansa na fari, Buz shi ne ɗan'uwansa, Kemuwal shi ne mahaifin Aram, da22Kesed da Hazo, da Fildash da Yidlaf da Betuwel.23Betuwel ya haifi Rebeka. Waɗannan sune 'ya'ya takwas da Milka ta haifa wa Nahor, ɗan'uwan Ibrahim.24Ƙwarƙwararsa mai suna Reuma ita ma ta haifi Tebah da Gaham Tahash da Ma'aka.
Ana amfani da wannan a sa alama a farkon sashin labarin ne. Idan harshen ku na yadda ake faɗin wannan, yana iya yiwuwa a yi amfani da shi a nan.
Wannan kalmar na nufin abin da ya faru a Farawa Sura 21 ne.
An nuna cewa Allah yana gwada Ibrahim don ya sani ko Ibrahim zai kasance da aminci a gare shi. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "Allah ya gwada amincin Ibrahim"
"Na'am, ina saurara"
Wannan na nuna cewa Allah ya san wai Ibrahim na da wani yaro, Isma'ila. Wannan na jadada cewa Ishaku ne ɗan alkawarin da Allah ya ba wa Ibrahim. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "tilon ɗanka da na alkawatar"
Wannan na jadada ƙaunar da Ibrahim ya ke da shi ga ɗansa Ishaku.
"ƙasar da ake kira Moriya"
"ɗaura wa jaki kaya" ko "sa kayan da ya ke bukata domin tafiyar a kan jaki"
"bayi" (UDB)
"fara tafiyar sa" (UDB)
AT: "bayan tafiya na tsawon kwanaki uku"
"ya hangi daga nesa inda Allah ya faɗa"
Kalmar "mu" na nufi Ibrahim da Ishaku kawai.
"komo gare ku"
"ya sa Ishaku, ɗansa ya ɗauka"
"A hannunsa" na jadada cewa Ibrahim ya ɗauka waɗannan abubuwan da kansa. AT: "Ibrahim da kansa ya ɗauki"
Anan "wuta" na nufin kwano da garwashin wuta a ciki ko fitila. AT: "wani abu da ake wura wuta"
"suka tafi tare" ko "suka tafi tare su biyu"
Wannan hanya ce da ɗa ke maganar da mahaifinsa cikin ƙauna.
"Na'am, ina saurara" ko "Na'am, me ya faru?"
Wannan hanya ce da mahaifi ke magana da ɗansa cikin ƙauna.
"ragon da za ka mika baikon ƙonawar?"
"Kansa" a nan na jadada cewa Allah ne zai tanada ragon.
"zai ba mu"
"Sa'ad da Ibrahim da Ishaku su ka iso wurin"
"a bisa itacen da ke kan bagadi"
"ɗauki wuƙa"
Ma'ana mai yiwuwa 1) Yahweh ya mayar da kansa a kamanin mala'ika, ko 2) wannan ɗaya ne daga cikin mala'ikun Yahweh, ko 3) wannan da aika ne daga Allah na musamman (Wasu masu karatu na tunani Yesu ne). Tunda shike maganar ba fili ta ke, zai fi kyau a juya yadda ya ke "mala'ikan Yahweh" kamar yadda aka saba amfani da kalmar "mala'ika." Duba Farawa 16:7.
Kalmar "kada ka ɗore hannunka a kan" wata hanyar cewa "kada ka cutar." Allah na maimata abu ɗaya sau biyu domin ya jadada cewa kada Ibrahim ya yi wa Ishaku illa. AT: "kada ka cutar da yaron ta kowani hanya"
Kalmomi "Na" da "Ni" na nufin Yahweh ne. A sa'ad da ana fassara wannan, sai a yi shi kamar yadda mala'ikan Yahweh ya yi amfani da kalmomin "Na' da "Ni" wajen nufin Yahweh.
Wannan na nufin ba da girma ga Allah da kuma nuna wannan girmar wajen yin biyyaya a gare shi.
"domin na ga cewa"
"ba ka hana ɗanka ba ... daga gare ni." AT: "kana shirye ka miƙa ɗanka ... a gare ni"
Kalmar "duba" na jawo hankalin mu ne ga bayani da ke zuwa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ɗan rago da ƙahonsa ya makale a daji" ko "ragon da ya makale da daji"
"Ibrahim ya je ya ɗauki ragon"
A amfani da kalma ɗaya da aka yi amfani da shi a Farawa 22:7.
"har yanzu." Ma'anar wannan shine har zuwa lokacin da marubucin ke rubuta wannan littafin.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "zai tanada"
Kalmar "na biyu" ita ce ƙa'ida ta biyu. AT: "sake"
"faɗa saƙon nan daga Yahweh" ko "furta waɗannan kalmomin daga Yahweh." Wannan na nufin cewa maganar ta zo daga Yahweh ne kai tsaye.
"Na yi alkawari kuma ni ne shaida." Kalmar "rantsuwa da" na da ma'anar wani abu ko wani mutum da shine tushi ko na da iko bisa alkawarin da aka yi. Ba wani abu da ke da iko fiye da Yahweh da zai yi rantsuwa da shi.
"ka yi mini biyyaya"
"Zan sa zuriyarka su yi ta karuwa" ko "Zan sa zuriyar ka su yi yawa"
Allah na kamanta yawan zuriyar Ibrahim da taurari da yashi. Kamar yadda mutane ba za su iya kirga taurari ko yashi ba, haka zuriryar Ibrahim za su yawa da mutane ba za su iya kirga wa ba. AT: "fiye da abun da za ka iya kirgawa"
"sammai" a nan na nufin dukka abun da ke sama da duniya, da rana, wata, da kuma taurari.
Anan "ƙofar" na wakiltar birnin gaba ɗaya. "mallaki ƙofar maƙiyansu" na ma'anar hallakar da aƙiyansu. AT: "samu cikaken nasara bisa maƙiyansu"
Mala'ikan Yahweh ya ci gaba da magana da Ibrahim.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ni, Ubangiji, zan albarkaci duk mutanen da ke zaune a ko'ina"
Anan "murya" na nufin abun da Allah ya faɗa. AT: "ka yi biyyaya da abun da na faɗa" ko "ka yi mini biyyaya"
An ambata sunan Ibrahim ne kadai domin shine uban, amma a nufin cewa ɗansa ya koma tare da shi. Ana iya ba da cikakiyar ma'anar wannan maganar a fili. AT: "Ibrahim da ɗansa suka koma"
"suka bar wacan wurin"
An ambaci Ibrahim shi kadai domin shine shugaban iyalinsa da barorinsa, amma a nufin cewa suna tare da shi ne. Cikakiyar ma'anar wannan magana na a fili haka. AT: "Ibrahim da mutanen sa suka zauna a Biyasheba"
"Bayan waɗannan abubuwan." Maganar "waɗannan abubuwa" na nufin aukuwar Farawa 22:1-19.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Wani ya ce da Ibrahim"
"Milka ma ta haifi 'ya'ya"
"Sunan ɗansa na fara shi ne Uz, sunan sauran 'ya'yansa kuma Buz ne ɗan'uwansa"
Waɗannan sunayen maza ne. Juya waɗannan yadda za a gane a fili cewa dukka waɗannan 'ya'yan Nahor ne da Milka, banda Aram.
"Daga baya Betuwel ya zama mahaifin Rebeka"
"Waɗannan takwas sune 'ya'yan Milka da Nahor ɗan'uwan Ibrahim."
"Ƙwarƙwarar Nahor"
Wannan sunan mace ce.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
1Saratu ta rayu tsawon shekaru ɗari da ashirin da bakwai. Waɗannan sune shekarun Saratu.2Saratu ta mutu a Kiriyat Arba wato Hebron, a ƙasar Kan'ana. Ibrahim ya yi makoki da kuka domin Saratu.3Sai Ibrahim ya tashi ya bar wurin da matarsa ta mutu, ya yi magana da 'ya'yan Het, cewa.4"Ni bãƙo ne a cikin ku Ina roƙo ku bani mallakar wurin maƙabarta a cikinku domin in bizne matattuna."5Sai 'ya'yan Het suka amsa wa Ibrahim cewa,6"Ka saurare mu shugabana. Kai yariman Allah ne a cikin mu. Bizne matattunka a duk inda ka zaɓa a maƙabartunmu, ba wanda zai hana maka maƙabartarsa domin ka bizne matattunka."7Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna wa mutanen ƙasar, ga "ya'yan Het.8Ya yi musu magana cewa, "In kun yarda cewa in bizne matacciyata, sai ku saurare ni ku roƙi Ifron ɗan Zohar domi na.9Ku tambaye shi ya sayar mini da kogon Makfela, wadda ya mallaka, wadda yake a ƙarshen filinsa. Domin cikakken farashi ya kuma sayar mini da shi a gaban mutane domin ya zama mallakata, da maƙabarta."10Ifron kuma na zaune a cikin 'ya'yan Het, sai Ifron Bahitte ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan 'ya'yan Het maza da kuma duk waɗanda suka zo ƙofar birninsa, cewa,11"A'a shugabana, ka saurare ni. Na baka filin da kuma kogon dake cikinsa. Na baka shi a gaban 'ya'yan mutanena maza. Na baka shi domin bizne matacciyarka."12Sai Ibrahim ya sunkuyar da kansa ƙasa a gaban mutanen ƙasar.13Ya yi magana da Ifron a kunnen mutanen ƙasar cewa. "Amma in ka amince, inka yarda ka saurareni. Zan biya kuɗin filin. Ka karɓi kuɗi daga wuri na, ni kuma zan bizne mattaciyata a can."14Ifron ya amsa wa Ibrahim, da cewa,15"Ina roƙo, ya shugabana, ka saurare ni. Ɗan yankin ƙasa na shekel ɗari huɗu na azurfa, mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka bizne mamaciyarka."16Ibrahim ya saurari Ifron, ya auna shekel ɗari huɗu kamar yadda Ifron ya ambata a kunnuwan dukkan 'ya'yan Het maza, mudu ɗari huɗu na zinariya, bisa ga mizanin ma'aunin fatake.17Domin haka filin Ifron dake a Makfela wanda ke gaban Mamre, wato da filin da kogon dake cikinsa, da duk itatuwan dake cikin filin, da dukkan iyakarsa,18aka ba Ibrahim tawurin sayarwa a gaban 'ya'yan Het maza, da kuma duk waɗanda suka zo ƙofar birninsa.19Bayan wannan Ibrahim ya bizne Saratu matarsa a cikin kogon filin Makfela, wanda ke gaba da Mamre wato Hebron, a cikin ƙasar Kan'ana.20Domin haka da filin da kogon dake cikinsa aka miƙa su ga Ibrahim daga 'ya'yan Het maza domin ya zama maƙabarta.
"Sarai ta yi rayuwa shekaru 127"
Wasu juyi basu da wannan maganar.
Wannnan sunan wani birni ne.
"Ibrahim ya yi bakin cikin, ya yi kuka domin Sarai ta mutu"
"ya tashi ya bar ganga jikin matarsa"
Anan "'ya'ya" na nufin 'yan zuriyar da zo ta wurin Het. AT: "zuriyar Het"
Ana iya bayana wannan maganar a matsayin wuri. "a ƙasar ku" ko "a nan"
"Sayar mun da fili" ko "Yardar mun in saya wani fili"
AT: "mata ta da ta mutu"
An yi amfani da wannan domin a martaba Ibrahim.
Wannan karin magana ne. Ma'anar wannan mai yiwu shine "mutum mai karfin iko"
Ana iya sa wannan a sauki haka "mata." AT: "matarka da ta mutu" ko"matarka"
"inda ya fi kyau a maƙabartunmu"
"hana ka da wurin bizina"
Ma'anar wannan shine durƙusawa ƙasa cikin tawali'u domin nuna bangirma da daraja ga wani.
"ga 'ya'yan Het da suke zama a wurin"
Waɗannan sunayen maza ne.
"kogon da ke a ƙarshen filinsa a Makfela"
"kogon da ke Makfelah." Makfelah sunan wani wuri ne. Ifron na da fili a Makfelah, kogon kuma na cikin filin ne.
"sayar mini da shi a bainar mutane"
"zama fili na da zan iya amfani da ita a matsayayin nawa"
Wannan ƙarin haske ne ko bayani game da Ifron.
Ana iya bayyana kalmar ta "ji" a matsayin "sauraro." AT: "domin dukka 'ya'yan Het su ji ni" ko "sa'ad da 'ya'yan Het su na saurara"
Wannan na bayana su wanene a cikin 'ya'yan Het su ka saurari maganar. AT: "duk waɗanda su ka tataru a ƙofar birninsa"
A ƙofar birni ne shugabanen birnin ke zama su ɗauki muhimmin shawarwari.
Anan "gaba" na nufin mutanen da suka zama shaidu ne. AT: "da 'yan ƙasana a matsayin shaiduna"
"Na ba ka. Ka bizne mataccenka"
Ma'anar wannan shine durƙusawa ƙasa cikin tawali'u domin nuna bangirma da daraja ga wani.
"mutanen da suke zama a yankin"
Kalmar "amma" na nuna banbancin magana. Ifron na so ya ba wa Ibrahim fili; Ibrahim kuma na so ya biya kuɗin filin. AT: "A'a, In ka yarda" ko "A'a, amma in ka yarda da wannan"
"Zan ba ka kuɗin filin"
"Ka ji ni, ya shugabana" ko "Ka saurareni mallam"
Ifron na nufin cewa tundashike shi da Ibrahim masu arziki ne, shekel 400 ƙaramin kuɗi ne. AT: "kuɗin filin shekel ɗari hudu ne. Wannan ai ba komai ba ne a gare ni da kai."
Wannan a kimanin kilo 4.5 na azurfa.
Ibrahim ya auna wa Ifron dai-dai shekel da ya ambata" ko "Ibrahim ya auna wa Ifron iyakar azurfan"
"kimanin azurfa da Ifron ya ambata"
"amfani da mizanin ma'aunin fatake." Ana iya sa wannan a wa ta sabon jimla. AT: "Ya auna azurfan kamar yadda fatake suke auna wa"
Wannan maganar ya bayana abun da marubucin ke ma'ana da "filin Ifron." Ba filin kadai ba, amma har da kogon da itatuwan da ke filin.
"Ya zama mallakar Ibrahim bayan ya saye ta shi" ko "zama na Ibrahim bayan da ya saya"
Anan "gaba" na matsayin yadda mutanen suka zama shaidu. AT: "da mutane Het suna kallo a matsayin shaidu"
Wannan na magana game da 'ya'yan Het wanda su ka Ibrahim lokacin da ya ke sayan mallakar.
"birnin da ya ke zama." Wannan maganar na nuna cewa Ifron na waccan birnin ne. Ba wai birnin mallakar sa ba ne.
"Bayan ya saya filin"
"kogon da ke filin"
"filin cikin Makfela"
Ma'ana mai yiwuwa sune 1) Mamre wani suna ne na Hebron, ko 2) A baya ana kira Hebron da sunar Mamre, ko 3) Mamre na ku sa da babban birnin Hebron, shiyasa mutane su ka saba kira Hebron.
"ya zama mallakar Ibrahim na binza, a sa'ad da ya saye ta daga 'ya'yan Het maza"
1Ya zamana kuma Ibrahim ya tsufa ainun, kuma Yahweh ya albarka ce shi a cikin komai.2Sai Ibrahim yace da baransa, wanda ya fi daɗewa da kuma ke kula da komai da ya mallaka, ya ce "Sa hannunka a ƙarƙashin cinyata,3zan sa ka ka rantse da Yahweh, Allah na sama da kuma Allah na duniya, cewa ba zaka auro wa ɗana mata daga cikin Kan'aniyawan da nake zama a cikinsu ba.4Amma zaka je cikin ƙasata da dangina ka auro wa ɗana Ishaku mata daga can."5Sai baran yace da shi, "To yaya kenan, in matar ta ce ba za ta biyo ni zuwa wannan ƙasar ba fa? Ko ya zama tilas in mayar da ɗanka zuwa ƙasar da ka baro?"6Ibrahim yace da shi, "Ka tabbata cewa ba ka komar da ɗana can ba!7Yahweh Allah na sama, wanda ya ɗauko ni daga gidan mahaifina da kuma ƙasar dangina, wanda kuma ya yi mini tabbataccen alƙawari cewa, 'Ga zuriyarka zan bada wannan ƙasa,' zai aiko mala'ikansa a gabanka, kuma zaka samo wa ɗana mata daga can.8Amma in matar ba ta son ta biyo ka, to ka kuɓuta daga rantsuwata, kada ka komar da ɗana can,"9Sai baran ya sa hannunsa a ƙarƙashin cinyoyin Ibrahim shugabansa, ya yi masa rantsuwa game da wannan al'amari.10To sai baran ya ɗauki raƙuma goma na shugabansa ya tafi. Haka nan ya ɗauki duk waɗansu kyaututtuka da suka kamata daga wurin shugabansa ya tafi da su yankin Aram Naharaim zuwa birnin Nahor.11Ya sa raƙuman suka kwakkwanta a gefen rijiyar ruwa. Da yamma ne daidai lokacin da mata ke fita ɗiban ruwa.12Daga nan sai ya ce, "Yahweh, Allah na shugabana Ibrahim, ka ba ni nasara a yau ka kuma nuna amintaccen alƙawarinka ga shugabana Ibrahim.13Duba yanzu ina tsaye a bakin ƙoramar ruwa, kuma 'yan'matan mutanen birnin suna fitowa domin su ɗibi ruwa.14Ka sa abin ya kasance kamar haka. In na ce da budurwar ina roƙon ki ki saukar da abin ɗiban ruwanki domin in sha; sai kuma ta ce da ni, ka sha, zan kuma shayar da raƙumanka ma; to bari ta zama matar daka nufa ta zama matar bawanka Ishaku. Da haka zan sani cewa ka nuna amintaccen alƙawarinka ga shugabana."15Sai ya zamana kafin ma ya gama magana sai ga Rebeka ta zo da abin ɗiban ruwanta a kafaɗarta. Rebeka 'yar Betuwel ce ɗan Milka, matar Nahor, ɗan'uwan Ibrahim.16Budurwar kyakkyawa ce kuma ba ta ɓata budurcinta ba. Ba mutumin da ya taɓa kwana da ita. Sai ta tafi ƙoramar ta cika abin ɗiban ruwanta, ta hauro.17Sai baran ya yi gudu domin ya gamu da ita ya ce, "Ina roƙo ki sam mani ruwa in ɗan sha daga cikin abin ɗiban ruwanki."18Ta ce ya shugabana ka sha sai ta yi sauri ta sauke abin ɗiban ruwan ƙasa a hannunta ta ba shi ya sha.19Bayan ta gama ba shi ya sha, sai ta ce, "Zan ɗebowa raƙumanka ma su sha har sai sun kammala sha."20Sai ta yi sauri ta juye abin ɗebo ruwan, ta yi gudu ta sake komawa rijiyar domin ta ɗebo ruwa domin dukkan raƙumansa.21Sai mutumin ya dube ta a natse domin ya gani ko Yahweh ya ba tafiyarsa nasara ko kuwa a'a.22Bayan raƙuman sun gama shan ruwan, sai mutumin ya ciro zoben zinariya na hanci mai nauyin rabin ma'auni, da ƙarau guda biyu na azurfa na sawa a dantse wanda ya kai nauyin ma'auni goma,23sai ya tambaya, "Ke "yar wane ne? Ina roƙon ki ki faɗa mini, ko akwai masauki a gidan mahaifinku da za mu kwana?"24Ta ce da shi, "Ni 'yar Batuwel ce ɗan Milka wanda ta haifawa Nahor."25Ta kuma ce da shi muna kuma da ciyawa da abincin dabbobi da kuma ɗaki domin ku kwana."26Sai mutumin ya sunkuya ƙasa ya yi sujada ga Yahweh.27Ya ce, "Albarka ta tabbata ga Yahweh, Allah na shugabana Ibrahim, wanda bai yashe da alƙawarinsa mai aminci ba da kuma amincinsa ga shugabana. Ni da kaina Yahweh ya bi da ni kai tsaye zuwa gidan dangin shugabana."28Sai budurwar ta yi gudu ta je ta faɗa wa iyalin gidan mahaifiyarta duk abin da ya faru dangane da waɗannan al'amura.29Rebeka kuma tana da ɗan'uwa, sunansa Laban. Sai Laban ya ruga zuwa wurin mutumin wanda ke can kan hanyar ƙoramar.30Da ya ga wannnan zobe na hanci da ƙarau na dantse a dantsen 'yar'uwarsa, kuma bayan ya ji duk abin da Rebeka 'yar'uwarsa ta faɗa, "Wannan shi ne abin da mutumin ya ce da ni," sai ya tafi wurin mutumin, sai ga shi a tsaye a gefen raƙuma a wurin ƙoramar.31Sai Laban yace, "Zo, kai mai albarka na Yahweh. Meyasa kake tsayuwa a waje? Na shirya gida da kuma wuri domin raƙuman."32Sai mutumin ya zo gidan ya kuma sauke wa raƙuman kaya. Sai aka ba raƙuman ciyawa da abincin dabbobi aka kuma tanadi ruwa domin ya wanke ƙafafunsa da kuma na mutanen dake tare da shi.33Suka kawo masa abinci domin ya ci, amma ya ce, "Ba zan ci ba sai na faɗi abin da zan faɗa. "Sai Laban yace to faɗi abin da zaka faɗa."34Ya ce, "Ni baran Ibrahim ne.35Yahweh ya albarkaci shugabana sosai ya kuma yi girma sosai. Ya ba shi garkuna da dabbobi da zinariya da azurfa, da bayi maza da mata da raƙuma da jakuna.36Saratu matar shugabana ta haifi ɗa ga shugabana a lokacin da ya tsufa, ya kuma bayar da duk abin da ya mallaka gare shi.37Shugabana ya sa na rantse, cewa, 'Ba za ka auro wa ɗana mata daga cikin 'yanmatan Kan'aniyawa ba, waɗanda a ƙasarsu na yi gidana.38Maimakon haka dole ka je wajen dangin mahaifina, cikin 'yan'uwana ka samo wa ɗana matar aure.'39Na ce da shugabana, in a ce matar ba zata biyo ni ba fa.'40Amma ya ce da ni, Yahweh wanda nayi tafiya a gabansa, zai aiko mala'ikansa ya kasance tare da kai ya kuma baka nasara bisa tafiyarka, domin ka auro wa ɗana mata daga cikin dangina da kuma iyalin mahaifina.41Amma zaka kuɓuta daga rantsuwata in ka zo wurin 'yan'uwana in ba su baka ita ba. To zaka kuɓuta daga rantsuwata.'42To da na kawo wurin ƙorama, na ce, 'Ya Yahweh, Allah na shugabana Ibrahim, ina roƙon ka, in har ka so ka ba tafiyata nasara-43gani nan a tsaye a bakin ƙorama-ka sa budurwar da ta zo ɗiban ruwa, wato macen da zan ce, "Ina roƙo ki ɗan san mani ruwa in sha daga abin ɗiban ruwanki,"44macen da ta ce da ni, "Sha, zan kuma shayar da raƙumanka"_Bari ta zama macen da kai, Yahweh, ka zaɓa domin ɗan shugabana.'45Tun ma kafin in gama magana a cikin zuciyata, sai ga, Rebeka ta zo da abin ɗiban ruwanta a kafaɗarta sai ta gangara ƙoramar ta ɗebo ruwa. Sai na ce da ita, 'Ina roƙo ki bani ruwa in sha.'46Sai ta yi sauri ta sauko da abin ɗiban ruwan daga kafaɗarta ta ce, 'Ka sha, zan kuma shayar da raƙumanka.' Sai na sha, ta kuma shayar da raƙuman.47Na tambaye ta cewa, 'Ke 'yar wane ne?' Ta ce, 'Yar Betuwel, ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.' Daga nan sai na sa zoben a hancinta da kuma ƙarau a damtsenta.48Sai na sunkuya na yi sujada ga Yahweh, na albarkaci Yahweh Allah na shugabana Ibrahim, wanda ya bishe ni a madaidaiciyar hanya domin in sami 'yar dangin shugabana domin ɗansa.49Yanzu kuma, in kuna shirye ku nuna zumunci mai aminci da amana, ku faɗa mini. Amma in ba haka ba, ku faɗa mini, domin in bi dama ko hagu."50Sai Laban da Betuwel suka amsa suka ce, Al'amarin daga Yahweh ya zo; ba zamu iya ce maka ya yi kyau ko bai yi kyau ba.51Duba Rebeka na gabanka. Ɗauke ta ku tafi, domin ta zama matar ɗan shugabanka, kamar yadda Yahweh ya faɗa."52Da baran Ibrahim ya ji maganarsu, sai ya sunkuyar da kansa ƙasa ga Yahweh.53Sai baran ya fito da kayayyaki na zinariya da azurfa da sutura ya miƙa su ga Rebeka. Hakanan ya bada kyautai masu daraja ga ɗan'uwanta da kuma mahaifiyarta.54Daga nan shi da mazajen dake tare da shi suka ci, suka sha. Suka kwana har gari ya waye, bayan sun tashi da safe, ya ce "Ku sallame ni zuwa gun shugabana."55Ɗan'uwanta da mahaifiyarta suka ce, "Bari budurwar ta ɗan yi waɗansu 'yan kwanaki kamar goma tukuna. Bayan nan za ta iya ta tafi."56Amma ya ce da su kada ku hana ni da yake Yahweh ya sa tafiyata ta yi nasara. Ku sallame ni domin in koma wurin shugabana."57Suka ce za mu kira budurwar mu tambaye ta."58Sai suka kira Rebeka suka tambaye ta, "Za ki tafi tare da wannan mutumin?" Ta amsa "zan tafi."59Sai suka aika 'yar'uwarsu Rebeka, tare da baranyarta, a cikin tafiyarta tare da baran Ibrahim da mazajensa.60Suka albarkaci Rebeka, suka ce da ita, "Yar'uwarmu, muna addu'a ki zama uwar dubun dubbai goma, da ma zuriyarki ta mallaki ƙofar maƙiyansu."61Sai Rebeka ta tashi, ita da barorinta mata suka hau raƙuma, suka bi mutumin. Da haka baran ya ɗauki Rebeka ya yi tafiyarsa.62Ya zamana Ishaku na zama a Negeb, ya dawo kenan daga Beyerlahairoi.63Ishaku ya fita domin yin nazari a saura da yammaci. Da ya duba tudu, ya hanga, sai ya ga raƙuma na tafe!64Rebeka ta duba, da ta ga Ishaku sai ta diro daga kan raƙumin.65Ta ce da baran, "Wane ne wancan dake tafiya a cikin saura domin ya tarbe mu?" Baran yace, "'Shugabana ne." Sai ta ɗauki gyale ta yi lulluɓi.66Baran ya zaiyana wa Ishaku dukkan abin da ya yi.67Sai Ishaku ya kawo ta rumfar mahaifiyarsa Saratu ya ɗauki Rebeka, ta zama matarsa, ya kuma ƙaunace ta. Da haka Ishaku ya ta'azantu bayan mutuwar mahaifiyarsa.
An yi amfani da wannan kalmar ne anan don nuna dan tsaiko a cikin labarin. A nan marubucin ya fara bayyana sabon sashi na labarin.
Ibrahim na shirin roƙon bawansa ya rantse zai yi wani abu. Sa hannun sa ƙarƙashin cinyar Ibrahim na nufin yana da tabbacin zai yi abin da ya rantse zai yi.
Za'a iya bayyana wannan a matsayin umarni. AT: "rantse"
Kalmar "rantse da" na nufin yin amfani da sunan wani ko wani abu a matsayin ginshiƙin ko ikon da aka kafa rantsuwar. "yi mani alkawari da Yahweh a matsayin sheda"
"Allah na sama da kuma Allah na duniya." Kalmomin " sama" da "ƙasa" an yi amfani da su tare ne domin nuna duk abin da Allah ya halitta. AT: "Allahn komai da komai na sama da ƙasa"
Wannan na nufin wurin da Allah yake
"mata daga cikin Kan'aniyawa" ko "daga Kan'aniyawa." Wannan na nufin matan Kan'aniyawa.
"da nake zama a cikinsu." A nan "nake" na nufin Ibrahim da iyalin sa da barorinsa. AT: "da nake zama a cikinsu"
Za'a iya furta wannan a matsayin umarni. AT: "rantse da cewa za ka tafi" ko "amma tafi"
"iyalina"
"me zan yi idan"
"ba za ta biyo ni ba" ko " ta ƙi mu dawo tare"
"Ko in mayar da ɗanka zuwa ƙasar da ka baro"
Jimlar "ka tabbbata" ta ingiza umarnin da ya biyo baya. "Ka tabbata cewa ba ka komar da ɗana can ba" ko "Ka da ka yarda ka komar da ɗana can ba"
A nan "gida" na nufin mutanen da iyalinsa. AT: "wanda ya ɗauko ni daga gidan mahaifina da sauran iyalinsa"
"ya yi tabbataccen alƙawari gare ni"
Wannan magana ce cikin baka a wata baka. Za'a iya furta wannan a fakaice. AT: "ya cewa ga zuriyarka zan bada wannan ƙasa"
Kalmar "zai" da "sa" na nufin Yahweh
Aya 8 ci gaba ne na ka'idodin da Ibrahim ya ba bawansa
"Amma in matar ba ta son ta biyo ka." Ibrahim na amsa tambayar bawansa daga Farawa 24:5.
"ka kuɓuta daga rantsuwata da ka yi mani." Rashin cika alkawari an bayyana shi kamar mutum ya kujewa wani abin da ya kamata. AT: "ba sai ka yi mini abin da ka rantse mini ba"
Wannan na nuna tabbbacin zai yi abin da ya rantse.
"ya yi masa rantsuwa"
"game da bukatar Ibrahim" ko "zai yi abin da Ibrahim ya buƙace shi"
Jimlar ta fara da "haka nan ya ɗauki" ta bada ƙarin bayani game da abin da bawan ya ɗauka lokacin tafiya. Ya tattarasu kafin ya tafi.
Wannan na nufin ya ɗauki abubuwa masu kyau da yawa da shugaban sa ke so ya baiwa iyalin matar.
"ya kama hanya ya tafi" ko " ya kama hanya yayi tafiyar sa"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "birnin da Nahor ya zauna" ko 2) "birnin da ake kira Nahor." Idan zaka fasara shi ba tare da zaɓar ma'ana ba, ka iya yin haka.
Rakuma dabbobi ne masu bisa da dogayen ƙafafu. Ya sa suka kwankwanta a kan ƙasa. "Ya sa raƙuman sun kwankwanta ƙasa"
"rijiyar ruwa" ko "rijiya" (UDB)
"samo ruwa" (UDB)
"Sai bawan ya ce "
Za ka iya furta wanna da kalmar "ta wurin." Wannan ya nuna a zahiri yadda bawan ya ke son Allah ya cika alkawarin sa. AT: "ka nuna amintaccen alƙawarinka ga shugabana Ibrahim ta wurin bani nasara yau"
"ka ba ni nasara." Bawan na so ya samarwa yaron Ibrahim mata nagari. Kalmar "nasara" zata iya zama aikatau. AT: "ka taimake ni don inyi nasara" ko "ka bani ikon yin abin da ya kawo ni nan"
Wannan aminci ne saboda alkawarin da Allah ya yi da Ibrahim. Kalmar "amintaccen" za'a iya cewa "ka yi aminci." AT: "ka nuna amintaccen alƙawarinka ga shugabana Ibrahim"
A nan kalmar "duba" ta ƙara armashi ga abin da ya biyo.
"ƙoramar ruwa" ko "rijiya"
"'yan'matan birnin"
"Ka sa abin ya kasance kamar haka" ko "bari haka ya kasance"
Wannan magana ce a bakã cikin wata bakã. Za'a iya bayyana hakan a fakaice. AT: "In na ce da budurwar ina roƙon ki ki saukar da abin ɗiban ruwanki domin in sha"
Matan suna ɗaukar abin ɗibar ruwa a kafaɗa. Sai ta saukar kafin ta ba namiji ruwa in ya bukata.
Wata matsakaiciyar gora ce da ake yi da yinbu domin ajiye ko zuwa abu ruwa-ruwa
Kalmar "amintacce" za a iya cewa "zama da aminci". AT: "ka nuna amintaccen alƙawarinka ga shugabana"
Wannan jimlar an yi amfani da ita ne a nuna inda aikin ya fara. idan harshenka na da wata hanyar yin wannan, zaka iya duba yiwuwar amfani da shi a nan.
Kalmar "duba" a nan na ankarar da mu muyi la'akari da bayanin banmamaki da zai biyo baya.
Wata matsakaiciyar gora ce da ake yi da yinbu domin ajiye ko zuwa abu ruwa-ruwa. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 24:12
"Uban Rebeka ne Betuwel. Iyayen Batuwel ne Milka da Nahor. Nahor ɗan'uwan Ibrahim ne"
Betuwel uba ne wurin Rebeka. Duba yadda aka fassara wannan suna a Farawa 22:20.
Wannan sunan namiji ne. Duba yadda aka fassara sunan a Fassara 11:22.
Milka matar Nahor ce kuma uwa ga Betuwel. Duba yadda aka fasara wannan suna a Farawa 11:29.
Ƙoramar na ƙasa da inda bawa ya tsaya
"ya sami budurwar"
"dan ruwa kadan"
Wata matsakaiciyar gora ce da ake yi da yinbu domin ajiye ko zuwa abu ruwa-ruwa. Duba yadda aka fassara wannan a Fawara 24:12
"shugabana". A nan matar ta yi amfani da wannan kalmar bangirman ga mutumin, duk da ba baiwar shi bace.
"sai ta yi sauri ta sauke abin ɗiban ruwan." Tana dauke da abin ɗibar ruwan a kafaɗar ta. Ta saukar da shi domin ta bada ruwa ga baran.
"zan samo ruwa"
"Sai ta yi sauri ta juye abin ɗebo ruwan"
"kwamin shan ruwa" (UDB). Kwami wani dogon buɗaɗɗen mazibin ruwane wanda ake zubawa dabbobi su sha.
"Baran" (UDB)
"ya dubi Rebeka" ko "ya dubi yar budurwar"
Koyon wani abu akan dube shi kamar gani. AT: "a sani"
"ya ba tafiyarsa nasara" ko " ya sa tafiyarsa da nasara." Za ka iya bayyana abin da baran ya kudurta. AT: "yana nuna masa wadda zata zama matar Ishaku"
Kuna iya bayyana cikakken bayanin da aka fahimta. AT: "ko bai yi nasara a tafiyarsa ba"
"zoben zinariya na hanci mai nauyin giram shida"
"ƙarau guda biyu na azurfa na sawa a dantse domin ta da yakai giram 110." Nauyin na nuna girma da darajar su. AT: "ƙarau guda biyu na azurfa domin dantse ta"
"Wanene mahaifin ki"
"ko akwai wuri a gidan mahaifinku"
Da alamu wadansu mutanen sun tafi tare da baran Ibrahim. A nan "mu" na nufin baran da wadanda suke tafiya tare da shi. (Duba:
"mu kwana a nan" ko "mu kwana"
"Rebeka ta ce" ko "budurwar ta ce"
"ga baran"
"Batuwel ubana ne, iyayen shi kuma sune Milka da Nahor"
An fahimta cewa ciyawa anbincin raƙuma ne. Zaka iya bayyana wannan bayani. AT: "muna kuma da ciyawa da abincin dabbobi"
"domin ku kwana" ko "inda zaku tsaya daren nan"
A nan "ku" na nufin baran da waɗanda suke tafiya tare.
"baran" (UDB)
Wannan alama ce ta ƙasƙantar da kai gaban Allah.
"bai yashe da alƙawarinsa mai aminci ba da kuma amincinsa ga shugabana." Kalmar "amincinsa" da "alherinsa" za su iya zama "zama da aminci da alherinsa." AT: "ya ci gaba da zama da aminci da alherin sa domin alƙawarinsa ga shugabana"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT: "ya ci gaba da nuna"
"iyali" ko "dangi"
A nan "iyalin" na nufin duk mutanen da ke gidan mahaifiyarta. AT: "ta yi gudu ta je ta faɗa wa mahaifiyarta da duk waɗanda suke nan"
"duk abin da ya faru"
An yi amfani da wannan kalmar ne domin nuna dan tsaiko cikin labarin. A nan marubucin ya yi bayani akan Rebeka. Marubucin ya gabatar da dan'uwan ta, Laban, a labarin.
Waɗannan abubuwa sun faru ne kafin ya ruga wurin mutumin. Wannan ya nuna dalilin da yasa Laban ya ruga wurin mutumin.
Wannan zai iya zama magana ce a fakaice. AT: "bayan ya ji duk abin da Rebeka 'yar'uwarsa ta faɗa"
"da gaske." Kalmar "duba" a nan ta ƙara armashi ga abin da ya biyo baya.
"Zo ciki" ko "Shigo"
"kai wanda Yahweh ya sawa albarka"
A nan kalmar "kai" na nufin baran Ibrahim.
Laban yayi amfani da wannan tambaya ya gayyaci baran Ibrahim zuwa gidan sa. Za'a iya juya wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "baka buƙatar zama a waje."
Kalmar "ya zo" za'a iya fasara ta a matsayin "ya tafi".
Ba'a fayyace wanda yayi wannan aikin ba. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "baran Laban ya sauke wa raƙuma kaya"
Wannan bai bayyana wanda yayi aikin ba. Idan ka bayyana wannan a zahiri yi amfani da "baran Laban" a matsayin batun magana. AT: "baran Laban ya ba raƙuman ciyawa da abincin dabbobi, aka kuma tanaɗi ruwa"
"ga baran Ibrahim da mutanen da suke tare da shi su wanke ƙafafun su"
A nan, kalmar "su " na nufin iyalin Laban ko na baran gidan
"kawo abinci ga baran"
"sai na faɗi abin da zan faɗa" ko "faɗa maku dalilin zuwa na nan"
A nan kalmar "ya" na nufin Ibrahim
"ya zama mai dukiya ƙwarai"
Kalmar "ya" na nufin Yahweh
Baran Ibrahim ya ci gaba da magana ga iyalin Rebeka
"ta haifi ɗa"
"shugabana ya bashi ... ga ɗan sa"
"Shugabana ya sa na rantse cewa zan yi duk abin da ya buƙaci in yi. Ya ce"
Wannan na nufin matan Kan'aniyawa. AT: "daga matan Kan'aniyawa" ko "daga Kan'aniyawa"
"waɗanda na girma cikin su." A nan "na" na matsayin Ibrahim da duk iyalin sa da barorin sa. AT: "waɗanda tsakanin su na girma"
"ga dangi"
Baran Ibrahim ya ci gaba da magana ga iyalin Rebeka
Wannan abu ne da zai iya faruwa. AT: "in a ce matar ba zata biyo ni ba fa." ko "Me zan yi idan matar ba zata biyo ni?"
Bautawa Yahweh an yi maganar sa ne kamar Ibrahim na tafiya da kasancewar Yahweh. AT: "wanda nake bautawa"
"zai mai da hanyoyin ka da nasara"
"iyali"
Wannan misalin yanayi ne da Ibrahim bai tsammaci zai faru ba. Mai yiwuwa ma'anar kan zan 1) "Akwai hanya ɗaya tak da zaka iya yantuwa daga rantsuwa ta: Idan ka zo ga dangi na suka ƙi baka ita, to zaka yantu daga rantsuwa ta" ko, 2) ginawa kan aya 40, "Idan ka je wurin iyalin babana ka kuma nemi yarin ya, ka yi abin da na buƙaci kayi ke nan. Idan ba zasu baka ita ba, to zaka yantu daga alkawarin da ka rantse mani."
"zaka kuɓuta daga rantsuwata da ka yi mini." Rashin cika alkawari an bayyana shi kamar mutumin ya yantu daga wani abu da ya daure shi. AT: "ba sai kayi abin da ka rantse mani zakayi ba"
Harsuna na amfani da kalmomin zo da tafi dabam-dabam.AT: "idan ka je wurin yan'uwa na" ko "idan ka je gidan yan'uwa na"
Baran Ibrahim ya ci gaba da yin magana ga iyalin Rebeka
"rijiya"
Baran ya yi kutse ga abin da yake roƙon Allah yayi ta wurin ankaras da Allah inda yake a tsaye
Baran ya koma wajen bayyana buƙatar sa, kuma yana da abu uku da zai faɗa game da macen da yake da begen zata zo.
"ta sami ruwa"
Wata matsakaiciyar gora ce da ake yi da yinbu domin ajiye ko zuwa abu ruwa-ruwa. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 24:12
Baran ya gama bayyyana buƙatar sa
Baran Ibrahim ya ci gaba da yin magana ga iyalin Rebeka
An bayyana yin addu'a a cikin zuciyar mutum kamar yin magana cikin zuciya. Kalmar "zuciya" na nufin tunanin sa da zuciyarsa. AT: "addu'a
"da gaske" ko "nan take." Kalmar "ku ji" a nan na ankaras da mu ga maida hankali ga bayanan banmamaki da suka biyo.
Wata matsakaiciyar gora ce da ake yi da yinbu domin ajiye ko zuwa abu ruwa-ruwa. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 24:12
Jimlar "je wajen" an yi amfani da ita ne saboda ƙoramar na wani wuri ne ƙasa da inda baran ke tsaye.
"rijiya"
"ta bada ruwa ga raƙuman"
Baran Ibrahim ya ci gaba da yin magana ga iyalin Rebeka
"Betuyel mahaifi na ne. Iyayen sa kuma Nahor da Milka ne"
a wannan labarin, duk waɗannan abubuwan an yi sune da zinariya. Duba yadda aka fassara su a Farawa 24:21
Wannan alama ce ta ƙaskanci wurin Allah.
"ya kawo ni nan"
Kalmar "bishe ni" zata iya nuna dalilin da yasa baran ya yi sujada ga Allah. AT: "saboda Yahweh ya bishe ni"
Wannan na nufin Betuyel, yaron ɗan'uwan Ibrahim.
Baran Ibrahim ya ci gaba da yin magana ga iyalin Rebeka
"Yanzu" (UDB). A nan "yanzu" ba tana nufin "nan take ba", amma an yi amfani da ita ne domin jan hankali ga batutuwa masu amfani da suka biyo.
Yadda zasu nuna aminci da amana a fili ya ke. AT: "ku faɗa mini in kuna shirye ku nuna zumunci mai aminci da amana ga shugabana ta wurin ba shi Rebeka ta zama matar ɗan sa"
Kalmar " kai" na nufin Laban da Betuyel
Waɗannan kalmomi za'a iya bayyana su kamar "aminci da amana."
Bayanai da aka fahimta ka iya zama a fayyace. AT: "Amma in baku a shirye ku nuna zumunci mai aminci da amana ga shugabana"
Mai yiwuwa ma'anar ta hada da 1) yanke shawarar abin da za'a yi an bayyana shi ne kamar mutum zai juya wani sashin ko wani. AT: "domin in san matakin da zan dauka" ko 2) baran na so ya san ko akwai buƙatar ya tafi wani wurin. AT: "domin in ci gaba da tafiya ta"
Wannan shine mahaifin Laban da Rebeka
"Yahweh ya sa duk wadannan abubuwa su faru"
Suna cewa basu da yancin yin zaɓi ko abin da Allah yayi mai kyau ne ko mara kyau. AT: "bai kamata mu shara'anta abin da Yahweh ke yi"
Kalmar "duba" a nan ta ƙara armashi ga abin da zai biyo baya
"Ga Rebeka nan"
"Kalaman Laban da Betuyel." A nan "kalmomi" na a matsayin abin da suka faɗi. AT: "abin da Laban da Betuyel suka ce"
Sunkuyar da kai gaban Allah alama ce ta sujada gare shi.
"kayan zinariya da azurfa" ko "kayayyaki da aka yi da zinariya da azurfa "
"kyautai masu tsada" ko "kyautai masu tamani"
"Baran Ibrahim da mutanen sa"
"suka yi barci a wannan dare"
"sun tashi safiya ta gaba"
"ku bar ni in tafi in koma"
"akalla ta ƙara kwana goma"
"10"
"Daga nan"
"Baran Ibrahim ya ce"
"ga yan'uwan Rebeka da mahaifiyar ta"
"Kada ku ɓata man lokaci"(UDB) ko "Kada ku sani in jira"
A nan "tafiyata" na nufi baƙuntar sa. AT:"Yahweh ya sa tafiyata ta yi nasara"
"Ku barni in tafi"
"iyalin suka tura Rebeka"
Rebeka yar'uwar Laban ce.AT: "dangin su" ko "yar'uwar Laban"
Wannan na nufin baiwar da ta kula da Rebeka tun tana ƙarama, ta lura da ita tun tana ƙarama, har yanzu tana bauta mata.
Rebeka ba yar'uwa bace ga kowa a iyalin ta. Amma suna kiranta haka su nuna suna ƙaunarta. AT: "Kaunatacciyar mu Rebeka"
A nan "uwar" na nufin kakanni. AT: "muna addu'a ki zama uwar dubun dubbai goma" ko "bari ki samu ziri'a mai yawa sosai"
Wannan na nufin lamba mai yawa ko wadda bata iya ƙirguwa.
Sojoji kan karya ganuwar biranen maƙiyansu su kuma ci mutanen da yaƙi. AT: "bari zuriyarki su yi nasara akan maƙiyanki gaba ɗaya"
"Sai Rebeka ta tashi, ita da barorinta mata suka hau raƙuma"
"Ta wannan hanyar baran Ibrahim ya dauki Rebeka tare da shi ya koma inda ya fito"
Wannan kalmar ta kawo canji cikin labarin. Tana magana kan yadda baran ya samo mata, yanzu kuma zata yi magana ka Ishaku
Wannan sunan wata rijiyar ruwa ce a Negeb. Duba yadda aka fasara ta a cikin Farawa 16:13.
"Da yammacin wata rana Ishaku ya fita filidomin yin tunani." Wannan zai yiwu dogon lokaci ne bayan da baran da Rebeka suka baro gidan iyayenta tunda dole suyi tafiya mai nisa.
Kalmar "duba" a nan ta ankaras da mu ga mai da hankali ga bayani mai banmamaki da ya biyo baya, "Da ya duba tudu, ya hanga, yayi mamakin ganin raƙuma na tafe"
"Rebeka ta duba sama"
"sai ta sakko daga kan raƙumin da sauri"
"Sai ta ɗauki gyale ta yi lulluɓi ta rufe fuskarta." Wannan alama ce ta bangirma da kamun kai ga mijin da zata aura.
yadin tufa da ake amfani da shi a rufe kai, kafaɗa da fuska
Duka jimlolin na nufin Ishaku ya auri Rebeka. AT: "ya auri Rebeka" ko "ya ɗauki Rebeka, ta zama matarsa"
Za'a iya bayyyan wannan da gabgaɗi. AT: "Rebeka ta ta'azantar da Ishaku"
1Sai Ibrahim ya auro wata mata mai suna Ketura.2Ta haifa masa Zimra, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak, da Shuwa.3Yokshan ya haifi Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Asiriya, da mutanen Letush, da mutanen Leyum.4'Ya'yan Midiyan sune Efa, Efer, Hanok, Abida, da Elda'ah. Duk waɗannan sune zuriyar Ketura.5Ibrahim ya mallaka duk abin da yake da shi ga Ishaku.6Duk da haka, a lokacin da yake raye ya ba da kyautai ga 'ya'yan ƙwaraƙwaransa ya aika su ƙasar gabas nesa da ɗansa Ishaku.7Waɗannan sune kwanakin shekarun rayuwar Ibrahim da ya yi shekaru, 175.8Ibrahim ya yi numfashinsa na ƙarshe ya mutu a cikin kyakkyawan tsufa, tsohon mutum mai cike da kuzari, sai aka tattara shi ga mutanensa.9Ishaku da Isma'ila, 'ya'yansa suka bizne shi a kogon Makfela, a filin Ifron ɗan Zohar Bahitte, wadda ke kusa da Mamre.10Wannan filin Ibrahim ya saya daga'ya'yan Het maza. A can aka bizne Ibrahim da matarsa Saratu.11Bayan mutuwar Ibrahim Allah ya albarkaci ɗansa Ishaku, Ishaku ya zauna kusa da Beyer Lahai Roi.12To Waɗannan sune zuriyar Isma'ila ɗan Ibrahim, da Hajara Bamasariya baiwar Saratu, ta haifa wa Ibrahim.13Waɗannan sune sunayen 'ya'yan Isma'ila bisa ga tsarin haihuwarsu: Nebaiyot - shi ne ɗan fari na Isma'ila, da Kedar, da Adbe'el, da Mibsam,14da Mishma, da Massa,15Hadad, da Tema, da Yetur, da Nafish, da Kedema.16Waɗannan su ne 'ya'yan Isma'ila, kuma waɗannan sune sunayensu bisa ƙauyukansu, suna kuma da sarakuna sha biyu bisa ga kabilarsu.17Waɗannan su ne shekarun rayuwar Isma'ila, shekaru, 137 ya yi numfashinsa na ƙarshe sa'an nan ya mutu, sai aka tattara shi ga mutanensa.18Sun yi rayuwa daga Habila zuwa Ashur, wadda take kusa da Masar, ɗaya kuma ya nufi Asiriya. Sun yi zaman tankiya da juna.19Waɗannan su ne al'amura game da Ishaku, ɗan Ibrahim: Ibrahim ya haifi Ishaku.20Ishaku nada shekaru arba'in a lokacin da ya ɗauki Rebeka a matsayin matarsa, 'yar Betuwel mutumin Aramiya ta Faddan Aram, 'yar'uwar Laban na Aramiya.21Ishaku ya yi addu'a ga Yahweh domin matarsa saboda ba ta da ɗa, Yahweh kuma ya amsa addu'arsa, Rebeka matarsa kuma ta yi juna biyu.22'Ya'yan na ta fama tare tun daga cikinta, sai ta ce, "Meyasa wannan ke faruwa da ni?" Ta je ta tambayi Yahweh game da haka.23Yahweh yace da ita, "Al'umma biyu ce a mahaifarki, mutane biyu kuma zasu rabu daga gare ki. Ɗaya jama'ar za ta fi ɗayar ƙarfi, babban kuma zai bauta wa ƙaramin."24Da lokacin haihuwarta yayi, sai ta kasance da 'yan biyu a mahaifarta.25Na farkon ya fito da gargasa a ko'ina kamar tufafin gashi. Suka kira sunansa Isuwa.26Bayan haka, ɗan'uwansa ya fito hannuwansa na riƙe da diddigen Isuwa. Sai aka kira shi Yakubu. Ishaku na da shekaru sittin lokacin da matarsa ta haifa masa su.27Samarin suka yi girma, Isuwa ya zama shahararren mafarauci mai yawo a saura; amma Yakubu mai shiru-shiru ne, wanda ya kashe lokacinsa cikin runfofi.28Sai ishaku ya ƙaunaci Isuwa domin yakan ci namomin jejin da ya harbo, amma Rebeka ta ƙaunaci Yakubu.29Yakubu ya shirya ɗan dage-dage. Isuwa ya zo daga saura, ya kuma raunana saboda yunwa.30Isuwa yace da Yakubu, "Ka ciyar da ni da dage-dagenka mana. Ina roƙonka ƙarfina ya ƙare!" Shiyasa aka kira sunansa Idom.31Yakubu yace, "Da farko ka sayar mani da matsayinka na ɗan fari tukuna."32Isuwa yace, "Duba, Na kusa mutuwa. Wanne amfani ne matsayin ɗan fari ke da shi a gare ni?"33Yakubu yace, "Da farko sai ka rantse mani" ta haka Isuwa ya yi rantsuwa kuma ta haka Isuwa ya sayar da matsayinsa na ɗan fari ga Yakubu.34Yakubu ya ba Isuwa dage-dagen wake da gurasa. Ya ci ya sha, daga nan ya tashi ya tafi abinsa. Ta wannan hali Isuwa ya banzantar da matsayinsa na ɗan fari.
Wannan na nufin mutane da ake ambata a aya 2-4.
"Ishaku ya gãji dukka mallakar Ibrahim." Dai-dai ne uba ya raba tarin dukiyarsa lokacin da ya tsufa, ba ya bari bayan mutawarsa wasu su yi ba.
"Ibrahim ya rayu shekaru 175"
"Ibrahim ya yi nunfashinsa na ƙarshe sanan ya mutu." "nunfashinsa na ƙarshe" da "mutuwa" na da ma'ana ɗaya ne. AT: "Ibrahim ya mutu"
Waɗannan magana biyun na nufin abu ɗaya ne, kuma ana jadadda cewa Ibrahim ya yi rayuwa har ya tsufa. AT: "Da ya yi rayuwa sosai har ya tsufa kwarai kuwa"
Ma'anar wannan shi ne, bayan Ibrahim ya mutu ruhun sa ya je inda ruhun 'yan'uwansa wadda su ka mutu kafin shi. AT: "Ya sadu da 'yan iyalinsa wadda su ka riga su ka mutu"
Ifron na da fili a Makfela da kogon da ke filin. Ibrahim ya saya filin a wurin Ifron.
"Ibrahim ya saya wannan fili"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Su ka bizne Ibrahim"
Ma'anar wannan sunar shine "rijiyar rayayye wanda ya ke kallo na." Duba yadda aka juya sunan wannan wurin a Farawa 16:13,
Ana amfani da wannan kalmar a Turanci wajen gabatar da sabon sashin labari da kuma ba da bayani game da Isma'ila.
Za'a iya bayyana wadannan a jimla guda biyu. "Wadannan sune sunayen 'yayan Isma'ila goma sha biyu. Sun jagoranci ƙabilun da aka basu sunna su, kuma kowannen su na da garinsu da ƙauyukansu."
"12"
A nan kalmar "yarima" na nufin mutanen ke shugabanci ko jagorancin ƙabilu, ba wai yana nufin su yayan sarakuna bane.
"Isma'ila ya rayu shekaru 137"
Kalmar "yayi numfashinsa na ƙarshe" da "ya mutu" na nufin kusan abu ɗaya. AT: "mutu"
Wannan na nufin bayan Isma'ila ya mutu, an kai jikin sa wurin yan'uwansa da suka mutu kafin shi. Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT: "ya sadu da iyalin sa da suka riga suka mutu"
"zuriyar sa ta zauna"
"tsakanin Habila da Shur"
Habila na wani wuri ne a Hamadar yankin Larabawa. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 2:11
"ya fuskanci"
Ma'anonin zasu iya zama 1) "basu zauna da salama a tsakanin su ba" (UDB), ko 2) "sun gujewa sauran danginsu."
Wannan jimlar ta gabatar da labarin zuriyar Ishaku na cikin Farawa 25:19-35:29. AT: "Wannan shi ne labarin zuriyar Ishaku, ɗan Ibrahim"
"shekaru 40"
"lokacin da ya auri Rebeka"
Betuyel mahaifin Rebeka ne. Duba yadda aka fassara wannan sunan a Farawa 22:20.
Wannan wani suna ne na yankin Mesofotamiya, wadda take a daidai wurin da ƙasar Iraƙi ta yanzu take.
"bata iya dauƙar juna biyu"
A bayyane yake cewa Rebeka ta yi juna biyu dauke da yara biyu a lokaci ɗaya. AT: "Rebeka, matarsa, ta sami juna biyu na 'yan biyu"
"yaran na cikin ta na bugun junan su" ko "Yaran ka yi turereniya a cikin ta"
Rebeka na da juna biyu dauke da 'yan biyu.
"Ta je ta tambayi Yahweh game da haka." Ba cikakken bayanin inda ta je. Mai yiwuwa ta je wani keɓeɓɓen wurin ne ta yi addu'a, ko ta je wani wuri ne domin miƙa hadaya.
"yace da Rebeka"
Wannan yaren waƙa ne. Idan harshen ka na da tanadi domin waƙa, zaka iya yin amfani da wannan a nan.
A nan "al'umma biyu" na nufin yara biyun. Kowannan yaro zai zama uba ga al'umma. AT: "al'umma biyu zata fito daga yan biyun da ke tare da ke"
A nan "mutane biyu" na matsayin yara biyun. Kowanne zai zama uba ga al'umma. Za'a iya fasara wannan da aikatau. AT: "yayin da kika haifi wadannan yaran zasu yi gaba da juna"
Ma'anar Wannan sune 1) "babban yaro zai bautawa ƙaramin yaro" ko 2) "zuriyar babban zata bautawa zuriyar ƙaramin." Idan zai yiwu, a fassara shi yadda mutane zasu fahimci kowacce ma'ana.
Kalmar "gashi" a nan na ƙara jadada abun zai biyo. "haƙĩƙa"
Ma'anar Wannan sune 1) fatar sa ja ne da gashi mai yawa a jikinsa, ko 2) yana da jar gashi a jikin sa. AT: "ja da kuma gashi kamar tufafin gashi"
Masu fassara na iya ƙara sharihinta cewa "Sunar Isuwa na kamar kalmar da ke nufin "gargashi."
"riƙe bayar tafin kafar Isuwa"
Masu fassara na iya ƙara sharihinta cewa "Ma'anar sunar Yakubu shi ne "ya riƙe diddigen."
"shekaru 60"
"zama mai farauta, ya na kashe dabbobi domin abinci"
"mutum mai salama"
Wannan na magana game da lokaci kamar wani abu ne wanda za'a iya kashi. AT: "ya kasance a runfofi yawacin lokaci"
An yi amfani da wannan a ba da alaman canjin magana, zuwa ba da ƙarin haske game da Ishaku da Rebekah.
Ma'anar kalmar "ƙauna" a nan shine "rahama" ko "fĩfĩta"
"domin ya na cin namomin da Isuwa ya harbo" ko "domin a jin dadin naman jeji da Isuwa ke kamowa"
Tunda ya ke wannan shine farkon labari game da wani abu da ya faru a wani lokaci, wasu masu juya wannan na iya farawa a cewa "Wata rana, Yakubu ya dafa" kamar yadda ya ke a UDB.
"shirya taushe" ko "dafa miya." Wannan taushen an shirya shi da wake ne. (Duba: Farawa 25:31)
"ƙarfinshi ya ƙare domin yana jin yunwa" ko Yana jin yunwa"
"ƙarfin na ya ƙare da yunwa" ko "Ina jin yunwa"
Masu fassara na iya sharihinta cewa "ma'anar sunar Idom shine "ja.'"
"damarka ta ɗan fari na gadon mallakar ubanmu" (UDB)
Isuwa ƙara azama a maganar sa domin ya jadada irin yunwan da yake ji. AT: "Ina jin yunwa kamar zan mutu"
Isuwa ya yi amfani da tambaya domin ya jadada cewa cin abinci ya fi muhimminci mishi da damar ɗan fari. AT: "Gado ba shi da amfani a gare ni idan na mutu da yunwa!"
Ana iya ba da gamsashen bayani a fili abun da Yakubu ke so Isuwa ya rantse a kai. AT: "A farko ka rantse mini za ka sayar mun da damarka na ɗan fari"
Wannan wani irin wake ne kanana.
"Isuwa ya nuna cewa bai daraja matsayinsa na ɗan fari ba."
1Sai aka yi yunwa a ƙasar, bayan wacce aka yi ta fari a kwanakin Ibrahim, Ishaku ya tafi wurin Abimelek, sarkin Filistiyawa a Gerar.2Sai Yahweh ya bayyana gare shi ya ce, "Kada ka gangara Masar; ka zauna a ƙasar dana ce ka zauna a ciki.3Ka zauna a wannan ƙasar, zan kasance tare da kai, in kuma albarkace ka; domin a gare ka da zuriyarka ne zan bayar da ƙasashen al'ummai, kuma zan cika alƙawarin dana yi wa Ibrahim mahaifinka.4Zan ruɓanɓanya zuriyarka kamar taurarin sama zan kuma bada waɗannan ƙasashe ga zuriyarka. Ta wurin al'ummarka dukkan ai'umman duniya zasu sami albarka.5Zan yi wannan domin Ibrahim ya yi biyayya da muryata ya kuma kiyaye dokokina, da farillaina, da shari'una. da ka'idodina."6Don haka Ishaku ya zauna a Gerar.7Da mutanen wurin suka tambaye shi game da matarsa, sai ya ce, "Ita 'yar'uwata ce". Ya ji tsoro ya ce, "Ita matata ce," saboda ya yi tunanin cewa, mutanen zasu kashe ni su ɗauke Rebeka domin ita kyakkyawa ce."8Bayan Ishaku ya daɗe a can, sai Abimelek sarkin Filistiyawa ya duba ta taga. Sai ya ga Ishaku na shafa Rebeka, matarsa.9Abimelek ya kira Ishaku gare shi ya ce, "Duba hakika ita matarka ce. Don me ka ce, ita 'yar'uwata ce'?" Ishaku yace da shi, "Saboda na yi tsammanin wani zai iya ya kashe ni don ya same ta."10Abimelek yace, "Me kenan ka yi mana? Da kuwa wani ya kwana da matarka cikin sauƙi, da kuma ka jawo mana laifi."11Sai Abimelek ya gargaɗi mutene ya ce, "Duk wanda ya taɓa mutumin nan ko matarsa hakika za a kashe shi."12Ishaku ya shuka hatsi a waccan ƙasar, ya kuma yi girbi a wannan shekara, ya sami riɓi ɗari, saboda Yahweh ya albarkace shi.13Mutumin ya azurta, ya dinga bunƙasa sosai har sai da ya yi girma sosai.14Yana da tumakai masu yawa da dabbobi, da iyalai masu yawa. Filistiyawa suka yi kishinsa.15To dukkan rijiyoyin da barorin mahaifinsa suka haƙa a kwanakin Ibrahim mahaifinsa, Filistiyawa suka cike su da ƙasa.16Abimelek yace da Ishaku, "Ka tafi ka ba mu wuri, domin ka fi mu ƙarfi."17Sai Ishaku ya bar garin ya koma Kwarin Gerar ya zauna a can.18Haka kuma Ishaku ya tone rijiyoyi na ruwa waɗanda aka haƙa a kwanakin Ibrahim mahaifinsa. Filistiyawa suka ɓata su bayan mutuwar Ibrahim. Ishaku ya kira rijiyoyin da ainihin sunan da mahaifinsa ya kira su.19Bayan barorin Ishaku sun yi tono a cikin kwarin, sai suka sami wata rijiya mai fitar da ruwa a can.20Makiyayan Gerar suka yi faɗa da makiyayan Ishaku suka ce, "Wannan ruwan namu ne." Domin haka Ishaku ya kira rijiyar "Esek" wato rikici, saboda sun yi rikici da shi.21Sai suka sake haƙa wata rijiyar, sai suka sake yin rikici akan itama wannan rijiyar, sai ya ba ta suna "Sitnah."22Sai ya bar wurin ya ƙara haƙa wata rijiyar, amma ba su yi rikici kan wannan ba. Don haka ya kira ta Rehobot, ya ce, "Yanzu Yahweh ya samar mana masauki, kuma za mu wadata a cikin ƙasar."23Sai Ishaku ya haura daga can zuwa Bayersheba.24Yahweh ya bayyana a gare shi a cikin wannan daren ya ce, "Ni ne Allah na Ibrahim mahaifinka. Kada ka ji tsoro, domin ina tare da kai zan kuma albarkace ka in ruɓanɓanya zuriyarka, saboda barana Ibrahim."25Ishaku ya gina bagadi ya yi kira bisa sunan Yahweh. A can ya kafa rumfarsa, barorinsa kuma suka haƙa rijiya.26Sai Abimelek ya je wurinsa daga Gerar, tare da Ahuzat, abokinsa, da Fikol, jagoran sojojinsa.27Ishaku yace da su, "Meyasa kuke zuwa gare ni, tun da yake kun ƙi ni, kun kuma kore ni daga wurinku?"28Sai suka ce, "Zahiri mun ga Yahweh na tare da kai. Shi yasa muka ga ya fi kyau a sami rantsuwa tsakaninmu, i, tsakaninmu da kai, To in ka yarda sai mu yi yarjejeniya da kai,29cewa ba zaka wahalshe mu ba, kamar yadda muka yi maka muka sallame ka cikin lumana, hakika Yahweh ya albarkace ka."30Sai ishaku ya shirya liyafa domin su, suka ci suka sha.31Suka tashi da asuba suka yi rantsuwar alƙawari da juna. Daga nan Ishaku ya sallame su, suka bar shi cikin salama.32A wannan ranar dai barorin Ishaku suka zo suka ba shi labari game da rijiyar da suka haƙa. Suka ce, Mun sami ruwa."33Ya kira rijiyar da suna Shiba, shi ya sa a ke kiran wannan birni da suna Bayersheba har ya zuwa yau.34Da Isuwa ya kai shekaru arba'in, ya auri mata mai suna Yudit 'yar Be'eri Bahitte, da kuma Basemat "yar Elon Bahitte.35Suka kawo baƙinciki ga Ishaku da Rebeka.
An yi amfani da wannan kalmar ne anan domin a nuna sabon sashi na labarin
"an yi yunwa" ko "an yi wata yunwa"
Za ka iya fayyace ƙasar da wannan ke nufi. AT: "a ƙasar da Ishaku da iyalin sa suke rayuwa"
Kalmar "a kwankin" na nufin lokacin da Ibrahim ya rayuwa. AT: "wanda ya faru a kwanakin rayuwar Ibrahim"
Yahweh ya fara magana da Ishaku
"ya bayyana ga Ishaku"
Abin da aka saba faɗi ne barin ƙasar alƙawari kamar "ficewa" zuwa wani wuri.
"domin a gare ka da zuriyarka ne zan bayar da ƙasashen"
"zan tabbatar da alƙawarin dana yi wa Ibrahim mahaifinka"
Yahweh ya ci gaba da magana ga Ishaku
"Zan sa zuyirarka ta zama da yawa"
Wannan na magana kan yawan zuriyar Ishaku kamar yawan taurarin sama. Duba yadda aka fasara wannan a Farawa 22:15.
Wannan na nufin duk abin da muke gani a sama, har da rana, wata, da taurari.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɖi. AT: "Zan albarkaci dukkan ai'ummai duniya"
Jimlar "ya yi biyayya da murya ta" da "ya kiyaye dokokina,da farillaina, da shari'una da ka'idodina" na nufin kusan abu ɗaya. AT: "Ibrahim ya yi biyayya gareni tare da yin duk abin da na umarce shi"
A nan "murya" na nufin Yahweh. AT: "biyayya gare ni"
Ishaku ne kadai aka ambata domin shi ne shugaban iyalin, amma dukan iyalin sa na tare da shi. AT: "Don haka Ishaku da iyalinsa ya zauna a Gerar"
A nan "tsoro" na nufin rashin tabbas da mutum ke fuskanta lokacin da ya fahimci wani hatsari a gare shi ko wasu. "Ya ji tsoro ya ce"
"domin ya dauƙi Rebeka"
Kalmar "ya duba" ta nuna abin da Abimelek ya gani ya bashi mamaki"
Ma'anonin zasu iya zama 1) yana taɓa ta kamar yadda maigida ke taɓa matar sa ko 2) yana dariya tare da magana da ita yadda maigida ke magana da matar sa.
Mai yiwuwa Abimelek ya aiki wani ya faɗawa Ishaku cewa ya son ganin sa. AT: "Abimelek ya aiki wani ya kirawo Ishaku wurin sa" (Duba: fighs_metonymy)
Wannan na nufin magana a baka cikin wata baka. Za'a iya cewa magana a fakaice. AT: "Don me ka ce, ita 'yar'uwata ce'?"
"don ya same ta."
Abimelek yayi amfani da wannan tambaya don ya ƙalubalanci Ishaku. AT: "Da baka yi mana haka ba!"
Wannan na nufin sa wani ya zama mai laifi kamar "laifi" wani abune da ake ɗorawa wani. AT: "da kuma ka jawo mana laifi na ɗaukar matar wani"
A nan "mu" na nufin Abimelek da mutanen sa.
A nan "taɓawa" na nufin a taɓa mutum ta hanyar da zai cutar da shi. AT: "duk wanda ya cutar da mutumin nan"
Mai yiwuwa Abimelek yayi tunanin Faɗawa wani ya kashe duk wanda zai cutar da Ishaku ko Rebeka. Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT: "Zan kashe shi" ko "Zan umarci mutane na su kashe shi"
Wannan ya fara wani sabon sashi na labarin. Ya canza daga bayani kan yadda Ishaku ke kiran Rebeka yar'uwar sa, ya fara da faɗin yadda Ishaku ya zama da arziƙi har Filistiyawa na masa baƙin ciki.
"a Gerar"
Wannan na nufin "ninki ɗari na abin da ya shuka." Za'a iya fasara ta da "hatsi mai yawa"
"Ishaku ya zama da arziƙi" ko "ya yi arziƙi"
"ya dinga bunƙasa sosai har sai da ya yi girma sosai"
Wannan zai kunshi harma da awaki.
A nan "iyalai" na nufin ma'aikata ko barori. AT: "barori da yawa"
A nan wannan kalmar ba tana nufin "a wannan lokacin" ba. Tana nuna inda abin da ake magana a labarin ya fara. Za'a iya fasara ta da kalmar "Don" a nuna cewa wannan sakamako ne na abin da ya faru a Farawa 26:12.
Jimlar "a kwanakin" na nufin lokacin mutum. AT: "lokacin Ibrahim, mahaifin sa, yana rayuwa"
Ma'anonin zasu iya zama 1) wannan wani abune da zai matsawa Ishaku da Iyayensa su tafi. AT: "Sai Abimelek yace" ko "A karshe Abimelek yace" ko 2) Abimelek ya yi wannan kudiri domin ya lura mutanen sa na kishi tare da nuna zafin rai ga Ishaku. AT: "Saboda haka sai Abimelek yace"
"kana da ƙarfi fiye da yadda muke"
Ishaku kaɗai aka ambata saboda shi ne sugaba, amma iyalinsa da barorin sa sun tafi tare da shi. AT: "Saboda haka Ishaku da iyalin sa suka tafi"
A nan "Ishaku" na nufin Ishaku da barorin sa. AT: "Ishaku da barorin sa sun tona"
"Wadda barorin Ibrahim suka tona"
Jimlar "a kwanakin" na nufin lokacin mutum. AT:"lokacin Ibrahim, mahaifin sa, yana rayuwa" . Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 26:15
Wannan ne dalilin da ya sa Ishaku ya tona su. Wasu hanyoyin da za'a iya fsasara wannan ya ƙunshi 1) Tun sa'adda wannan ya faru da farko, wannan jimlar zata iya zuwa kafin jimlar game da Ishaku ya tone su, kamar a UDB, ko 2) Wannan jimlar zata iya farawa da "Ishaku yayi wannan saboda Filistiyawa sun ɓata su."
"sun cika su da ƙasa"
Wannan na nufin ruwan da suka samo lokacin da suke tona sabuwar rijiya. Ya nuna cigaba da fitar sabon ruwa mai daɗ. AT: "sabon ruwa"
"mutanen da ke kiwon dabbobi"
A nan "namu" na nufin makiyayan Gerar
Masu fassarar zasu iya ƙara dan bayani a ƙasa "Sunan Esek na nufin "rikici" ko "gardama."
"Sai barorin Ishaku suka sake haƙa " (UDB)
"makiyayen Gerar suka yi gardama da makiyayen Ishaku"
"saboda haka Ishaku ya dada"
Masu fassarar zai iya bada dan bayani da zai ce "sunan Sitna na nufin 'banbanta' ko 'ƙalubalanta.'"
Masu fassarar zai iya bada dan bayani da zai ce "Sunan Rehobot na nufin 'bada dama domin' ko 'wurin da ba komai.'"
Ishaku na magana game da kansa da iyalinsa.
A nan "haura" mai yiwuwa na nuna tafiya arewa. Ka furta ya haura yadda harshen ka ya bada dama. AT: "Ishaku ya haura daga can zuwa Biyasheba"
"zai ruɓanɓanya zuriyarka" ko "za sa zuriyar ka ta ƙaru kwarai"
"saboda barana Ibrahim" ko ka mai da ma'anar a zahirance. AT: "saboda na yiwa bawa na Ibrahim alkawari hakan zan yi"
Zaka iya gane dalilin da ya sa Ishaku ya gina bagadi. AT: "Ishaku ya gina bagadi a can domin yin hadaya ga Yahweh"
A "kira" na nufin yin addu'a ko sujada. A nan "sunan" na nufin Yahweh. AT: "Ya yi addu'a ga Yahweh" ko "yin sujada ga Yahweh"
"ya je wurin Ishaku"
Wannan sunan namiji ne.
Ma'anonin zasu iya zama 1) "abokin Abimelek" ko 2) "Masu ba Abimelek shawara."
Wannan sunan namiji ne. Duba yadda aka fasara shi a Farawa 21:22.
Wannan na nufin Abimelek, Ahuzat, da Fikol. Ɗayan su ne ya yi magana, sai sauran su ka amince. Ba wai sun yi maganar tare ne a lokaci guda ba. AT: "ɗayan su ya ce"
"mun sa ni" ko "muna da tabbaci"
"don haka muna so muyi yarjejeniya"
Ana iya sa wannan kamar sabon jimla. "Kirki ne kadai mu ka nuna maka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya sa maka albarka"
Ci da sha tare na cikin alkawari tsakanin juna.
"su" na nufin "Abimelek, Ahuzat, da Fikol." AT: "dukkan su su ka ci" (UDB)
"suka farka da asuba"
"Don haka, ya kira rijiyar Shiba." Masu fassarar na iya sharihinta cewa "Kalmar Shiba na kamar kalmar da ke ma'anar 'rantsuwa'".
Masu fassarar na iya sharihinta cewa "ma'anar Biyasheba na iya zama "rijiyar rantsuwa" ko "rijiyar bakwai." (Duba Farawa 21:31)
Yawancin Farawa 26 game da Ishaku ne. Waɗannan ayoyin suna magana ne akan babban ɗansa Isuwa.
"40"
"ya yi aure." Ana iya bayana a fili cewa ya aure mata biyu. AT: "ya auri mata biyu"
Waɗannan sunayen matan Isuwa ne.
Waɗannan sunayen maza ne.
"zuriyar Het"
Anan "su" na nufin Yudit da Basemat. Ana maganar baƙin ciki kamar wani abu ne da wani ke ba wa wani dabam. AT: "Suka sa Ishaku da Rebeka baƙin ciki" ko "Ishaku da Rebeka suka yi baƙin ciki sabili da su"
1Da Ishaku ya tsufa har ta kai ga ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa, babban ɗansa, ya ce da shi, "Ɗana." Ya ce da shi "Ga ni."2Ya ce, "Gashi yanzu, na tsufa. Ban kuma san ranar mutuwata ba.3Domin haka, ka ɗauki kwarinka da bakanka da makamanka, ka je daji ka yiwo mini farauta.4Ka yi mani dage-dage, irin wanda nake ƙauna, ka kawo shi gare ni domin in ci in albarkace ka kafin in mutu."5Sai Rebeka ta ji lokacin da Ishaku ke magana da Isuwa ɗansa. Isuwa ya tafi daji domin ya yiwo farauta ya kawo.6Sai Rebeka ta yi magana da Yakubu ɗanta ta ce, "Duba, na ji mahaifinka ya yi magana da Isuwa ɗan'uwanka. Ya ce,7'Ka farauto mani nama ka shirya mani dage-dage domin in ci in albarkace ka a gaban Yahweh kafin mutuwata.'8Yanzu fa ɗana, ka yi biyayya da muryata kamar yadda zan umarce ka.9Ka je garke, ka kawo mini "yan awaki guda biyu; zan kuma shirya dage-dage mai daɗi da su domin mahaifinka, kamar yadda yake ƙauna.10Zaka kai shi wurin mahaifinka, domin ya ci, ya albarkace ka kafin ya mutu."11Yakubu yace da Rebeka mahaifiyarsa, "Gashi, Isuwa ɗan'uwana gargasa ne, ni kuma sulɓi ne.12In mahaifina ya taɓa ni, na kuma zama mayaudari a gare shi. Zan jawo wa kaina la'ana ba albarka ba."13Mahaifiyarsa ta ce da shi, "Ɗana, bari duk wata la'ana ta auko mani. kai dai ka yi biyayya da muryata, ka je ka kawo su wurina."14Sai Yakubu ya tafi ya samo 'yan awaki guda biyu ya kawo su ga mahafiyarsa, mahaifiyarsa kuwa ta shirya dage-dage, kamar yadda mahaifinsa ke ƙauna.15Sai Rebeka ta ɗauki tufafin Isuwa babban ɗanta, mafi kyau, wanda ke tare da ita a gida, sai ta sa wa Yakubu, ƙaramin ɗanta.16Sai ta sa fatar 'yan awaki a hannunsa da kuma tattausan sashen wuyansa.17Sai ta sa dage-dagen mai daɗi da gurasar da ta shirya a hannun ɗanta Yakubu.18Sai Yakubu ya tafi wurin mahaifinsa ya ce, "Mahaifina." Ya ce,"Ga ni nan; Wane ne kai ɗana?"19Yakubu yace da mahaifinsa, "Ni ne Isuwa ɗanka na fari; Na yi kamar yadda ka ce da ni. Yanzu sai ka tashi ka zauna ka ci ɗan dage-dagen, domin ka albarkace ni."20Ishaku yace da ɗansa, "Ɗana yaya aka yi ka samo shi da sauri haka?" Ya ce, "Domin Yahweh Allanka ya kawo su wurina".21Ishaku yace da Yakubu, "Ɗana ka matso kusa da ni, domin in taɓa ka, domin in san ko kai ɗana ne."22Yakubu ya matsa ga Ishaku mahaifinsa, Ishaku kuma ya taɓa shi ya ce, "Muyar kamar ta Yakubu ce, amma jikin na23Isuwa ne." Ishaku bai iya gane shi ba, domin hannuwansa gargasa ne kamar na hannuwan ɗan'uwansa Isuwa, domin haka Ishaku ya albarka ce shi.24Ya ce "Kai ne ɗana Isuwa kuwa?" Ya amsa "Ni ne."25Ishaku yace, "Kawo abincin wurina, zan ci in kuma albarkace ka. Yakubu ya kawo abincin gare shi. Ishaku ya ci, Yakubu kuma ya kawo masa ruwan inabi, ya kuwa sha.26Sai babansa Ishaku yace da shi, "Ɗana ka zo nan kusa ka sumbace ni."27Yakubu ya matso kusa ya sumbace shi' ya sunsuni ƙamshin suturarsa ya albarkace shi. Ya ce, "Duba, ƙamshin ɗana yana kama da ƙamshin ganyayyakin da Yahweh ya sa wa albarka.28Allah ya baka rabo na raɓar sama, rabo na sashin ƙasa mafi dausayi, ya baka hatsi da ruwan Inabi mai yawa.29Mutane da al'ummai kuma su rusuna maka. Ka zama shugaban 'yan'uwanka maza, 'ya'yan mahaifiyarka maza kuma su rusuna maka. Duk kuma wanda ya la'ance ka ya zama la'annanne, duk wanda kuma ya albarkace ka ya zama mai albarka."30Ishaku na gama sa wa Yakubu albarka kenan, bayan ya fita daga wurin mahaifinsa Ishaku, sai ga Isuwa ɗan'uwansa ya shigo daga wurin farautarsa.31Shi ma ya shirya dage-dagen, abinci mai daɗi ya kawo shi wurin mahaifinsa. Ya ce da mahaifinsa, "Mahaifina, ka tashi ka ci irin dage-dagen ɗanka, domin ka albarkace ni."32Ishaku mahaifinsa ya ce da shi, "Kai wane ne?" Ya ce, "Ni ne ɗan farinka, Isuwa.33Ishaku ya gigice sosai ya ce, "Wane ne ya yiwo farauta ya kawo mani dage-dage? Na ci a gabanin zuwanka, na kuma albarkace shi. Hakika, zai zama da albarka."34Bayan Isuwa ya ji kalmomin mahaifinsa, ya yi kuka da baƙinciki matuƙa, ya ce da mahaifinsa, "Ni ma ka albarkace ni mana, mahaifina."35Ishaku yace, "Ɗan'uwanka ya zo cikin yaudara ya karɓe albarkarka."36Isuwa yace, "Ashe ba haka ta sa aka ba shi suna Yakubu ba? Domin ya zambace ni sau biyu. Ya karɓe matsayina na ɗan fãri, kuma duba yanzu ya karɓe albarkata." Daga nan ya ce, "Ba ka rage wata albarka domina ba?"37Ishaku ya amsa ya ce da Isuwa, "Duba, na maishe shi ya zama shugabanka, kuma na ba shi dukkan 'yan'uwansa maza su zama bayinsa, na kuma ba shi hatsi da sabon ruwan inabi. Me kuma zan yi maka, ɗana?"38Isuwa yace da mahaifinsa, "Ko albarka ɗaya ba ka rage mani ba mahaifina? Ka albarkace ni nima mahaifina." Isuwa yayi kuka da ƙarfi.39Ishaku mahaifinsa ya amsa masa cewa, "Duba, wurin da zaka zauna zai zama da nisa daga wadatar duniya, nesa kuma da raɓar sararin sama.40Ta wurin takobinka zaka rayu, kuma zaka bautawa ɗan'uwanka. Amma lokacin da kayi tayarwa, zaka kawar da karkiyarsa daga wuyanka."41Isuwa ya ƙi Yakubu saboda albarkar da mahaifinsa ya ba shi. Isuwa yace a cikin zuciyarsa, "Kwanakin makokin mahaifina sun kusa wucewa, bayan wannan zan kashe ɗan'uwana Yakubu."42Sai aka faɗa wa Rebeka kalmomin da babban ɗanta ya faɗa. Domin haka ta aika a kira Yakubu ƙaramin ɗanta ta ce da shi, "'Duba, ɗan'uwanka na tunanin yadda zai kashe ka.43Saboda haka, ɗana, yanzu sai ka yi biyayya da muryata, ka gudu wurin Laban ɗan'uwana a Haran.44Ka zauna tare da shi na ɗan lokaci,45har sai fushin ɗan'uwanka ya huce daga gare ka, ya kuma manta abin da kayi masa. Daga nan zan aika a dawo da kai daga can. Don me zan rasa ku dukka a rana ɗaya?46Rebeka ta ce, "Na gaji da rayuwa saboda 'ya'yan Het. In Yakubu ya auri 'yanmata irin waɗannan mataye, waɗansu daga cikin 'yan matan ƙasar, wanne abu ne mai kyau zai zama a rayuwata?"
Wannan yana magana game da kusan makaho kamar idanun fitila ne kuma haske ya kusan fita. AT: "ya kusa makance"
"ya kuma cewa Isuwa"
"Ina nan" ko "Ina sauraro." Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Farawa 22:1.
"Sai Ishaku yace"
Maganar "duba nan" na jadadda abin da ke zuwa a gaba. AT: "saurare ni a hankali"
Ma'anar wannan shi ne Ishaku ya san cewa ya kusa mutuwa. AT: "Ina iya mutuwa a kowani rana"
Wannan na nufin mutuwa ta jiki.
Ishaku ya ci gaba da ba da umarni ga babban ɗansa Isuwa.
"ƙayan farauta"
Kibiya kwalliya ce ta rike kibiyoyi. AT: "Kibar kibanku"
"ka yi mini farautar naman jeji"
Kalmar "dage-dage" na nufin abin da ke da dandano mai dadi. AT: "dafa mun naman mai dandano da na ke ƙauna"
A zamani Littafi Mai Tsarki, mahaifi kan sa wa 'ya'yansa albarka na musamman.
"Rebeka ta ji Ishaku yana magana da ɗansa Isuwa"
Ana iya kara kalmar "sai" domin a nuna cewa Rebeka na wa Yakubu magana domin abin ta ji ne, kuma lokacin da ta ke masa magana Isuwa ya tafi. AT: " Sa'ad da Isuwa ya tafi ... ya kawo,"
Isuwa da Yakubu dukkasu 'ya'yan Ishaku da Rebeka. Ake kira su "ɗansa" da "ɗanta" domin a jadada cewa ɗaya a cikin iyayan na son ɗayan ɗa fiye da ɗayan.
Wannan ambaton ne a cikin zance. Ana iya bayyana shi azaman zance na kai tsaye. AT: "Ya ce da Isuwa ya 'farauto naman jeji, ya kuma shirya nama mai dandano da ya ke ƙauna.' Ishaku zai albarkaci Isuwa a gaban Yahweh, kafin ya mutu.
"kawo mini naman jejin da ka farauto"
"dafa mini nama mai dandano da na ke so."
Rebeka ta yi magana da karamin ɗanta Yakubu.
Ma'anar wannan ba shi ne "a wannan lokaci" ba, an yi amfani da shi ne domin a jawo hankali zuwa maganar da ke zuwa.
Rebeka tace "muryata" a nufin abin da ta ke faɗa. AT: "Ka yi mini biyayya waje aikata abin da na faɗa ma ka"
Kalmar "dage-dage" na nufin wani abu ne da ke da dandano mai daɗi. Dubi yadda aka juya makamacin wannan jimlar a Farawa 27:3.
"Sai ka kai wa mahaifinka"
"bayan ya ci sai ya albarkace ka"
"kafin mutuwarsa"
"Ni mutum da jiki mai santsi" ko " ba ni da gargasa"
"zai kuma yi tunani cewa ni makaryaci ne" ko "zai san cewa ina yaudarar shi ne"
An yi maganar sa la'ana ko albarka kamar su wani abu ne da ake iya sa a bisan wani. AT: "Ta dalilin haka kuma, zai la'ance ni, ba albarkace ni ba"
"bari la'anarka ya kasance a gare ni, ɗa na." AT: "bari mahaifinka ya la'ance ni a maimakonka, ɗa na"
Rebeka tace "muryata" don nufin abin da take faɗa. AT: "yi abun da na faɗa maka" ko "yi mini biyayya"
"kawo mini ɗan akuya"
fatar akuyan na nan da gashin a kai.
"Ta ba wa ɗanta Yakubu dage-dagen da ta shirya da gurasa"
"mahaifinsa kuma ya ce" ko "Ishaku ya amsa" (UDB)
"I, ina saurara" ko " na am, mene ne?" Duba yadda ka fassara wannan a Farawa 22:1.
"Na yi abin da ka mini in yi"
Kalmar "farauto" na nufin namomin jeji da wani ya farauto ya kashe. Duba yadda aka fassara "farauto" a Farawa 27:3.
"Yakubu amsa"
Wannnan karin magana na nufin cewa Allah ne ya sa wanna ya faru. AT: "taimake ni in yi nasara wurin farauta
"in kai asalin ɗana ne Isuwa"
"Yakubu ya maso wurin Ishaku mahaifinsa'
Anan Ishaku yayi magana game da muryar Yakubu kamar wakiltar Yakubu. AT: "muryarka kamar na Yakubu"
Anan Ishaku yayi maganar hannayen Isuwa a matsayin wakiltar Isuwa. AT: "amma hannayenka na kamar na Isuwa"
Ishaku ya yi wannan tambayar kafin ya albarkace ɗansa. AT: "Amma Ishaku ya tambaya"
Kalmar "farauto" na nufin naman jeji da mutane ke yin farauta su kuma kashe. Duba yadda aka juya "farauto" a Farawa 27:5.
"Ishaku ya kuma sha"
Ana iya bayana a fili cewa suturar na ƙamshin na Isuwa. AT: "ya sunsuna suturarsa, su ka kuma yi ƙamshi kamar suturar Isuwa, sai Ishaku ya albarkaceshi"
"Ishaku kuma ya sunsuna"
"ya kuma sa masa albarka." Wannan na nufin yadda mahaifi ke sa wa 'ya'yansa albarka cikin hanya na ƙwarai.
Ana amfani da kalmar "duba" a bayyananniyar ƙarin magana da ke da ma'anar "gaskiya ne." AT: "Gaskiya, ƙamshin ɗana"
Anan kalmar "mai-albarka" na nufin cewa Yahweh ya sa kyawawan abubuwa sun faru ga filin kuma ya zama mai amfani. AT: "da Yahweh ya sa shi ya wadata"
Wannan albarkar Ishaku ne. Ya na tunanin cewa da Isuwa ya ke magana, amma da Yakubu ya ke magana.
A nan "ka" na nufin Yakubu ne kadai. Amma albarka zai bi har zuriyar Yakubu.
"raɓar" shi ne digon ruwa wanda yake fitowa akan tsiro cikin dare. Ana iya bayyana wannan a bayyane a cikin fassarar. AT: "raɓa da dare daga sama domin ba wa abinci gona ruwa"
Ana maganar ƙasa mai kyau domin amfanin gona kamar ƙasar na da ƙiba ko arziki. AT: "ƙasa mai kyau domin abinci gona"
Idan "hatsi" da "giya" ba a san su ba, ana iya bayyana wannan gaba ɗaya. AT: "abinci and abin sha da yawa"
Anan waɗannan karin magana suna ɗaya ɗaya kuma suna nufin Yakubu. Amma albarkar ta shafi zuriyar Yakubu.
Ishaku na sa Yakubu albarka, amma yana nufi har ma da zuriyarsa da zasu mulkance zuriyar Isuwa da kuma zuriyar sauran 'yan'uwan da mai yiwuwa Yakubu ya ke da su.
"'ya'yan mahaifiyarka maza kuma rusuna maka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ya la'ance duk wanda ya la'ance ka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ya albarkace duk wanda ya albarkace ka"
"ya fita daga rumfar mahaifinsa Ishaku"
"ɗanka" a nan wata hanya ne cikin da'a da ya ke nufin abinci da ya shirya.
Wannan na nufin yadda mahaifi ke sa wa 'ya'yansa albarka cikin hanya na ƙwarai.
"ya ce da Isuwa"
"Ishaku ya fara rawan jiki"
baƙin cikin Isuwa na kamar an ɗanɗana wani abu ne marasa daɗi. AT: "ya yi kuka da karfi"
Wannan ƙarin magana ne mai ma'anar cewa Yakubu ya karɓi da ke na Isuwa. AT: "Na albarkace shi a maimakon ka"
Isuwa ya yi amfani da tambaya ya jadada fushinsa da Yakubu. AT: "Sunar Yakubu ne ya dace da ɗan'uwana!"
Masu fassarar na iya sharihinta cewa "ma'anar sunar Yakubu shi ne "ya riƙe diddige." Sunan kuma na kamar sunar da ke ma'ana "ya yaudare" a harshen asalin.
Wannan yana magana ne game da matsayin ɗan fari kamar abu ne wanda mutum zai iya ɗauka. AT: "Ya yaudare ne, na ba shi ka shi biyu daga gadon da yakamata in karɓa a matsayin ɗan fari!"
An yi maganar albarka kamar wani abu ne da mutum ke iya karɓa. AT: "yanzu ya yaudare ka wajen sa masa albarka a maimako na"
Isuwa ya san cewa ba zai yiwu ba mahaifinsa ya albarkace shi da abubuwa da albarkace Yakubu da su ba. Isuwa na tambaya ko akwai wani abu da Ishaku zai ce da shi, wadda bai ambata ba a sa'ad da ya ke albarkace Yakubu.
Ishaku ya yi tambaya domin ya jadada cewa ba shi da wani abu kuma da zai iya yi. AT: "Ba wani abu kuma da zan iya yi maka!"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. "Maihaifina, ka na da ko albarka ɗaya domina"
"ce da Isuwa"
Wannan karin magana ne da ke nufin ƙasa mai kyau. AT: "nesa da ƙasa mai kyau"
A cikin Farawa 27: 39-40 waɗannan karin magana ɗaya ne kuma suna nufin Isuwa, amma abin da Ishaku ya ce ya shafi zuriyar Isuwa" .
"raɓar" shi ne digon ruwa wanda yake fitowa akan tsiro cikin dare. Ana iya bayyana wannan a bayyane a cikin fassarar. AT: "raba da dare daga sama domin ba wa amfanin gona ruwa"
A nan "takobi" na nufi hargitsi. AT: "Za ka yi fashi da kisan mutane kafin ka sami abun da ka ke bukata na zaman rayuwa"
Wannan na magana game da wani da ke da maigida kamar ikon maigidan a kan mutumin wani karkiya ne da mutum ya ɗauka. AT: "za ka yantar da kanka daga mulkin shi" (UDB)
A nan "zuciyarsa" na wakiltar Isuwa da kansa. AT: "Isuwa ya ce wa kansa"
Wannan na nufin iyakar kwanakin da mutum ke makoki idan wani ɗan iyali ya mutu.
"kalmomi" a nan na matsayin abin da Isuwa ya faɗa. AT: "Sai wani ya faɗa wa Rebeka game da shirin Isuwa"
"Saurara" ko "Mayar da hankali"
"yana sa kansa ya ji daɗi"
Ma'anar wannan ba wai "a wannan lokaci" ne, amma an yi amfani da shi domin a jawo hankalin ga muhimmin maganar da ke zuwa.
"ma za ka bar nan, ka kuma ta fi wurin Laban"
"na wani lokaci"
"sai ɗan'uwanka ya huce da fushinsa"
Ba a yin magana da fushi yanzu kamar fushin ya juya zuwa wata hanyar dabam daga mutumin. AT: "har sai ya daina fushi da kai"
Rebeka ta yi amfani da tambaya ta jadada damuwarta. AT: "ba na so in rasa ku dukka a rana ɗaya!'
Rebeka namagana haka domin ta jadada yadda take jin haushin matan Hittiyawa da Isuwa ya aura. AT: "Ina cike da baƙin ciki"
"waɗannan matan Hittiyawa" ko "zuriyar Het"
Maganar "'ya'yan ƙasar" na nufin matan ƙasar. AT: "kamar waɗannan matan da su ke zama a wannan ƙasar"
Rebeka ta yi amfani da tambaya ta jadada yadda baƙin ciki zai zama idan Yakubu ya aure matan Hittiyawa. AT: "Rayuwata za ta munana!"
1Ishaku ya kira Yakubu, ya albarkace shi, ya kuma dokace shi, "Tilas ba zaka ɗauki mata daga cikin matan Kan'aniyawa ba.2Ka tashi, ka tafi Faddan Aram, zuwa gidan Betuwel mahaifin mahaifiyarka, ka kuma ɗauki mata daga can, ɗaya daga cikin 'ya'ya mata na Laban, ɗan'uwan mahaifiyarka.3Bari Allah mai iko dukka ya albarkace ka, yasa kayi 'ya'ya, ka kuma ruɓanɓanya, yadda zaka zama mutane tururu.4Bari ya bada albarkar Ibrahim, gare ka, da zuriyarka a bayanka, domin ka iya gãdon ƙasa inda ka ke zama, wadda Allah ya ba Ibrahim."5Sai Ishaku ya sallami Yakubu, Yakubu ya tafi Faddan Aram, zuwa ga Laban ɗan Betuwel Ba'aramiye, ɗan'uwan Rebeka, mahaifiyar Yakubu da Isuwa.6Yanzu Isuwa ya ga Ishaku ya albarkaci Yakubu ya kuma sallame shi zuwa Faddan Aram, ya ɗauko mata daga can. Ya kuma ga cewa Ishaku ya albarkace shi ya kuma dokace shi, cewa, "Tilas ba za ka ɗauki mata daga matan Kan'aniyawa ba."7Isuwa kuma ya ga cewa Yakubu ya yi biyayya da mahaifinsa da mahaifiyarsa, ya kuma tafi Faddan Aram.8Isuwa ya ga cewa matan Kan'aniyawa ba su gamshi Ishaku mahaifinsa ba.9Sai ya tafi wurin Isma'ila, ya ɗauko, baya ga matan da yake da su, Mahalat ɗiyar Isma'ila, ɗan Ibrahim, 'yar'uwar Nebayot, ta zama matarsa.10Yakubu ya bar Bayesheba ya tafi zuwa Haran.11Ya iso daidai wani wuri ya kuma tsaya wurin dukkan dare, saboda rana ta fãɗi. Ya ɗauki ɗaya daga cikin duwatsun wurin, ya sa ƙarƙashin kansa, ya kuma kwanta a wurin domin ya yi barci.12Ya yi mafarki ya kuma ga hawan bene an kafa bisa duniya. Ƙololuwarsa ta kai cikin sama kuma mala'ikun Allah suna hawa suna sauka a kansa.13Duba, Yahweh ya tsaya a bisansa ya kuma ce, "Ni ne Yahweh, Allah na Ibrahim mahaifinka, da Allah na Ishaku. Ƙasar inda kake kwance, zan bayar gare ka ga kuma zuriyarka.14Zuriyarka zasu zama kamar turɓayar ƙasa, kuma zaka bazu nesa zuwa yamma, zuwa gabas, zuwa arewa, zuwa kuma kudu. Ta wurin ka da ta wurin zuriyarka dukkan iyalan duniya zasu yi albarka.15Duba, Ina tare da kai, kuma zan kiyaye ka ko'ina ka tafi. Zan sake kawo ka cikin wannan ƙasa; gama ba zan barka ba. Zan yi dukkan abin dana yi alƙawari a gare ka."16Yakubu ya tashi daga barci, ya kuma ce, "Tabbas Yahweh yana wannan wurin, kuma ban sani ba."17Ya ji tsoro ya kuma ce, "Wurin nan mai ban tsoro ne! Wannan ba wani wuri ba ne wanda ya wuce gidan Allah. Wannan ƙofar sama ce."18Yakubu ya tashi da sassafe ya kuma ɗauki dutsen da ya sa ƙarƙashin kansa. Ya kafa shi a matsayin ginshiƙi ya kuma zuba mai a kansa.19Ya kira sunan wannan wuri Betel, amma asalin sunan wannan birni Luz ne.20Yakubu ya yi wa'adi, cewa, "Idan Allah zai kasance tare da ni ya kuma kiyaye ni a cikin wannan hanya dana ke tafiya, ya kuma ba ni gurasa in ci, da suturar sanya wa,21yadda zan dawo lafiya zuwa gidan mahaifina, daga nan Yahweh zai zama Allah na.22Daga nan wannan dutse dana kafa a matsayin ginshiƙi zai zama tsarkakakken dutse. Daga kowanne abin da ka bani, babu shakka zan bayar da kashi ɗaya cikin goma a gare ka."
"kada ka ɗauki"
"tafi yanzu"
Wannan wani sunane kuma na yankin Mesofotamiya wanda a yau na ƙasar Iraki. Duba yadda aka juya wannan a Farawa 25:19.
Wannan na nufin zuriyar wani ne ko 'yan dangin AT: "iyali"
Betuwel shi ne mahaifin Rebeka. Duba yadda ka juya wannan sunan a Farawa 22:20.
"kakanka"
"daga 'ya'ya mata"
"kawu"
Ishaku ya ci gaba magana da Yakubu
Kalmar nan "ninka" ta bayyana yadda Allah zai sa Yakubu ya yi 'ya'ya. AT: "ba ka 'ya'ya da yawa da zuriyar"
Wannan yana magana ne game da albarkar wani kamar wata ni'ima abu ce da mutum zai iya bayarwa. AT: Allah ya albarkace ka da zuriyarka kamar yadda ya albarkace Ibrahim" ko "Allah ya ba ka da zuriyarka abin da ya alkawartar wa Ibrahim"
An yi maganar yadda Allah zai ba Yakubu da zuriyarsa ƙasar kamar wani ɗa ne da ke gãdan kuɗi da mallaka a wurin mahaifinsa.
"ƙasar da ka kasance a ciki"
"wadda Allah ya alkawatar wa Ibrahim"
Betuwel mahaifin Rebeka ne. Duba yadda ka fassara wannan a cikin Farawa 22:20.
Labarin ya canja daga Yakubu zuwa Isuwa
Ana amfani da wannan a nan domin sa alamar canji daga labarin zuwa bayanin ba da haske game da Isuwa.
"ya ɗauki mata wa kansa"
"Isuwa ya ga cewa Ishaku ya riga ya albarkace Yakubu"
"ka da ka ɗauki"
"'ya'ya mata na Kan'ana"
Wannan na ci ga ba da ba da ƙarin haske game da Isuwa.
"Isuwa ya ga ne"
"mahaifinsa Ishaku bai amince da matan Kan'ana ba"
"Sabili da haka"
"a haɗe da matan da ya ke da su"
Wannan sunan ɗaya a cikin 'yar Isma'ila.
Wannan sunan ɗaya daga cikin 'ya'yan Isma'ila maza
Labarin ya koma game da Yakubu
"Ya iso wani wuri, sai ya zauna a dukkan dare domin rana ta fãɗi"
"Yakubu ya yi mafarki"
"karshen da ke taɓa kasa"
"Wannan na nufi wurin da Allah ya ke
Kalmar "duba" a nan na jawo hankali zuwa bayanin ban mamaki da ke zuwa a gaba.
Ma'ana mai yiwuwa 1) "Yahweh na tsaye a saman hanyar hawan bene" ko 2) "Yahweh na tsaye a gaba da Yakubu"
Ma'anar "mahaifi" a nan shi ne "kaka." AT: "Ibrahim kakanka"
Allah ya ci gaba da magana da Yakubu a mafarki.
Allah ya kwatanta yawan zuriyar Yakubu da ƙurar ƙasa domin ya jadada girmar yawan su. AT: "Za ka sami zuriya fiye da abun da za ka iya kirgawa"
Anan kalmar "ka" a nan na nufin mutum ɗaya ne, amma a nufin zuriyar Yakubu ne. Ana magana da Yakubu shi kadai domin shi ne kan iyalin. AT: "zuriyarka kuma zasu bazu zuwa yamma"
Ma'anar wannan shine mutanen za su wuce iyakar ƙasarsu su mamaye yankin ƙasar.
Ma'anar wannan maganar maganar shi ne "a kowani gyefe." AT: "a kowani gyefe"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan albarkaci dukka iyalin duniya ta wurin ka da zuriyarka"
"gama ba zan barka ba sai na yi dukka"
"zan kiyaye ka daga matsala" ko "Zan kare ka"
"Zan sa ke kawo ka wannan ƙasar"
Maganar "ƙofar sama" na bayana cewa wannan wurin ne a shigar "gidan Allah" da "shigar idan Allah ya ke."
Ana maganar shigar inda Allah ya ke kamar wani masarauta da ke da ƙofa wadda wani ke buɗe wa mutane su shiga cikin.
Wannnan ginshiƙin na tunawa ne, wato wani babban dutsen a aka kafa.
Aikata wannan na nuna cewa Yakubu ya ƙebe ginshiƙin ga Allah. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "zuba mai a kai domin ya ƙeɓe ginshiƙin ga Allah"
Masu fassarar wa na iya sharihinta cewa "Ma'anar sunanBetel shi ne 'gidan Allah."
Wannan sunan wani birni ne.
"ɗau alkawari da Allah"
Yakubu yana magana da Allah a cikin mutum na uku. Ana iya bayyana wannan a cikin mutum na biyu. AT: "Idan za ka ... sai kai, Yahweh, za ka zama Allahn da zan bauta wa"
Wannan na maganar tafiyar Yakubu ne zuwa nema mata, ya kuma koma gida. AT: "a wannan tafiya"
Anan "gurasa" na wakiltar kowani abinci.
Anan "gida" na wakiltar iyalin Yakubu. AT: "ga mahaifina da sauran 'yan iyali"
Wannan na nufin cewa dutsen na alamar inda Allah ya bayyana mishi kuma zai kasance inda mutane za su bauta wa Allah. AT: "gidan Allah" ko "wurin Allah"
1Daga nan Yakubu ya kama tafiyarsa ya zo cikin ƙasar mutanen gabas.2Yayin da ya duba, sai ya ga rijiya a saura, kuma, duba, garkunan tumaki uku na kwance a gefen ta. Domin daga wannan rijiyar za su yi wa garkunan ban ruwa, kuma dutsen dake bakin rijiyar ƙato ne.3Sa'ad da dukkan garkunan suka taru a nan, makiyayan zasu gangarar da dutsen daga bakin rijiyar su kuma yi wa tumakin ban ruwa, sai kuma su mai da dutsen bakin rijiyar, daidai wurinsa.4Yakubu yace masu, "Yan'uwana, daga ina ku ke?" Suka maida amsa, "Daga Haran muke."5Ya ce masu, "Kun san Laban ɗan Nahor?" Suka ce, "Mun san shi."6Ya ce masu, "Yana nan lafiya?" Suka ce, "Yana nan lafiya, kuma, duba can, Rahila ɗiyarsa na zuwa tare da tumaki."7Yakubu yace, "Duba, yanzu rana tsaka ne. Lokaci bai yi ba da za a tattara garkuna tare. Kuyi wa tumakin ban ruwa daga nan ku tafi ku kai su kiwo."8Suka ce, "Ba za mu iya yi masu banruwa ba har sai dukkan garkunan sun tattaru tare. Daga nan mazan zasu gangarar da dutsen daga bakin rijiyar, sai kuma mu yi wa tumakin banruwa."9Yayin da Yakubu ke magana tare da su, Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, domin ita ke kiwon su.10Sa'ad da Yakubu ya ga Rahila, ɗiyar Laban, ɗan'uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, ɗan'uwan mahaifiyarsa, Yakubu ya zo kusa, ya gangarar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma yi wa garken Laban ɗan'uwan mahaifiyarsa banruwa.11Yakubu ya sumbaci Rahila ya yi kuka da ƙarfi.12Yakubu ya gaya wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne, kuma cewa shi ɗan Rebeka ne. Daga nan ta ruga ta gaya wa mahaifinta.13Sa'ad da Laban ya ji labarin Yakubu ɗan 'yar'uwarsa, ya ruga domin ya same shi, ya rungume shi, ya sumbace shi, ya kuma kawo shi cikin gidansa. Yakubu ya gaya wa Laban dukkan waɗannan abubuwa.14Laban yace masa, "Tabbas kai ƙashina ne da namana." Daga nan Yakubu ya zauna tare da shi har wajen wata ɗaya.15Daga nan Laban ya cewa Yakubu, "Kã bauta mani a banza saboda kai ɗan dangina ne? Gaya mani, mene ne zai zama ladanka?"16Yanzu dai Laban na da 'ya'ya mata biyu. Sunan babbar Liya, sunan ƙaramar kuma Rahila.17Idanun Liya tausasa ne amma Rahila na da kyakkyawar siffa.18Yakubu ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, "Zan bauta maka shekaru bakwai domin Rahila, ƙaramar ɗiyarka."19Laban yace, "Gwamma in bayar da ita a gare ka, maimakon in bayar da ita ga wani mutumin. Ka yi zamanka da ni."20Sai Yakubu ya yi bauta shekaru bakwai domin Rahila; sai kuma suka yi masa kamar kwanaki kaɗan, domin ƙaunar da yake yi mata.21Daga nan Yakubu ya cewa Laban, "Ka bani matata, domin kwanakina sun kammalu - domin in aure ta!"22Sai Laban ya tattara dukkan mutanen wurin ya kuma yi biki.23Da maraice ya yi, Laban ya ɗauki ɗiyarsa Liya ya kuma kawo wa Yakubu, wanda ya kwana da ita.24Laban ya ɗauki baiwarsa Zilfa ya ba ɗiyarsa Liya, ta zama baiwarta.25Da safe, da ya duba, sai ya ga ashe Liya ce! Yakubu ya cewa Laban, "Mene ne wannan ka yi mani? Ba domin Rahila na bauta maka ba? To me ya sa ka yaudare ni?"26Laban yace, "Ba al'adarmu ba ce mu bayar da ƙaramar ɗiya kafin ta fãrin.27Ka kammala satin amarcin wannan ɗiyar, za mu kuma baka ɗayar a sakamakon sake bauta mani na wasu shekarun bakwai."28Yakubu ya yi haka, ya kammala satin Liya. Daga nan Laban ya ba shi Rahila ɗiyarsa a matsayin matarsa.29Laban kuma ya bayar da Bilha ga ɗiyarsa Rahila, ta zama baiwarta.30Haka kuma Yakubu ya kwana da Rahila, amma ya ƙaunaci Rahila fiye da Liya. Sai Yakubu ya bauta wa Laban na wasu shekaru bakwai.31Yahweh ya ga cewa ba a ƙaunar Liya, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ba ta da ɗa.32Liya ta ɗauki ciki ta haifi ɗa, ta kuma kira sunansa Ruben. Domin ta ce, "Saboda Yahweh ya dubi azabata; babu shakka yanzu mijina zai ƙaunace ni."33Daga nan ta sake ɗaukan ciki ta haifi ɗa. Ta ce, "Saboda Yahweh ya ji cewa ba a ƙauna ta, saboda haka ya bani wannan ɗan kuma," ta kuma kira sunansa Simiyon.34Daga nan ta sake ɗaukan ciki ta haifi ɗa. Ta ce, "Yanzu a wannan lokacin mijina zai haɗe da ni, saboda na haifa masa 'ya'ya maza uku." Saboda haka a ka kira sunansa Lebi.35Ta sake ɗaukar ciki ta kuma haifar ɗa. Ta ce, "Wannan lokacin zan yabi Yahweh." Saboda haka ta kira sunansa Yahuda; Daga nan ta tsaya da haihuwar 'ya'ya.
Wannan na nufin mutanen Fadan Aram, ƙasar na gabancin ƙasar Kan'ana.
Kalmar "duba" na matsayin alama ne a farkon wani aukuwa a babban labari. Mai yiwuwa harshenku na da wani hanyar yin wannan.
"domin daga waccan rijiyar." Wannan maganar na ba da alamar canji ne da ga labarin zuwa bayanin ƙarin haske ne game da yadda makiyaya ke shayar da dabbobin.
"makiyayan za su shayar" ko "masu kulla da tumakin za su shayar"
Anan "bakin" a hanya ce ta nufin buɗewa. AT: "buɗe rijiyar"
"Yakubu ya cewa mikiyayan"
Wannan wani hanyar gai da baƙo ne cikin da'a.
Anan "ɗa" na nufin ɗa namiji. Wata ma'ana mai yiwuwa ita ce "Laban jikan Nahor." (UDB)
"Duba! Rahila ɗiyarsa na zuwa da tumaki"
"rana na haske sosai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "domin ka tattara dabbobin"
Ma'anar wannan shine a tattarasu a shinge domin da dare. Ana iya bayana ma'anar wannan a fili.
"su ci ciyawa a fili."
"Dole ne mu jira mu shayar dasu."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "sai sauran makiyayan dabbobin sun tattara dabbobinsu"
"sa'annan zamu shayar da tumakin"
"kawunsa"
Anan "bakin" a hanya ce ta nufin buɗewa. AT: "rijiyar"
A tsohuwar Gabas ta Tsakiya, sananniya ce a gaishe da dangi da sumba. Koyaya, ana yin shi tsakanin maza. Idan yarenku yana da kyakkyawar gaisuwa ga dangi, yi amfani da hakan. Idan ba haka ba, yi amfani da abin da ya dace.
Yakubu ya yi kuka, domin murna. Ana iya ba da cikaken ma'anar wannan magana a fili.
"mai dangantaka da mahaifinta"
"sai Yakubu ya faɗa wa Laban dukka abun da ya gaya wa Rahila"
Wannan jumlar tana nufin suna da alaƙa kai tsaye. AT: "dangina" ko "ɗan iyalina"
Laban yayi amfani da tambaya ya fifita cewa ya kamata ya sakawa Yakubu don aikin da ya yi masa. Za'a iya fasara wannan tambayar kamar bayani. Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT: "Ya kamata in saka maka domin aikin da kayi mini ko da yike kai dan uwana ne"
Kalmar "yanzu" an yi amfani da ita anan ne domin alamar canji daga labari zuwa matashiyar bayanin game da Laban da 'ya'yan sa mata.
Ma'anonin zasu iya zama 1) "Idanun Liya tausasa ne" ko 2) "Idanun Liya a fili suke"
A nan kalmar "kaunaci" na nufin sha'awar jiki tsanin namiji da mace.
"maimakon in bayar da ita ga wani mutum"
"amma lokacin yayi masa kamar kwanaki kaɗan"
"domin ƙaunar da yake yi mata" ko "saboda ƙaunar da yake yi mata"
A nan "kwanaki" na nufin dogon lokaci. Jimlar "kwanaki na sun kammalu" za a iya bayyana shi da gabagaɗi. AT:"Ka bani Rahila domin in aure ta, domin na yi maka aikin shekara bakwai!"
"shirya bikin aure." Mai yiwuwa Laban ya sa wasu suka shirya bikin. AT:"ya samu wasu su shirya bikin"
Ya nuna Yakubu bai san yana tare da Liya ba saboda dare yayi baya kuma gani. Cikakkiyar maganar nan a bayyane take.
A nan mai rubutun ya bada matashiya game da yadda Laban ya ba da Zilfa ga Liya. Mai yiwuwa ya bada Zilfa ga Liya kafin aure.
Wannan sunan baranyar Liya ne
"Yakubu yayi mamakin ganin Liya kan gado tare da shi." Kalmar "ashe" a nan na nuna Yakubu yayi mamaki da abin da ya gani.
Yakubu yayi amfani da tambaya ya bayyana fushin sa da mamakin sa. AT: "Ba zan iya gaskata cewa kun yi mini wannan ba!" Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa.
Yakubu yayi amfani da wannan tambayar ya bayyana illar wasa da hankalin da Laban yayi masa. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Na bauta maka shekara bakwai domin in auri Rahila!"
"A iyalin mu ba ma bayar da"
"Ka kammala satin amarcin Liya"
Cikakkiyar ma’anar ana iya bayyana ta a sarari. AT: "sati mai zuwa zamu baka Rahila"
"Yakubu yayi abin da Laban ya buƙata, ya gama satin amarcin Liya"
Wannan sunan baranyar Rahila ne.
Wannan hanya ce ta nuna sun yi dangantakar auratayya a fakaice. AT: "Yakubu ya auri Rahila"
Wannan na nufin kaunar jiki tsakanin namiji da mace.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yakubu baya kaunar Liya"
Wannan na fayyace yadda Yakubu ke kaunar Rahila fiye da Liya. AT: "ba'a kaunar ta kamar Rahila!"
Allah ya ba Liya damar ta dauki ciki an bayyana shi kamar an buɗe mahaifarta.
"bata iya ɗaukan ciki"
"Liya ta ɗauki ciki ta haifi ɗa"
Masu fassara zasu iya sa dan bayani da zai ce: "Sunan Ruben na nufin 'duba, ɗa'"
Liya na dandana aƙuba domin Yakubu ya yashe ta. Kalmar "azatarwa" za ta iya zama aikatau. AT: "Yahweh ya dubi azabata"
"Sai Liya ta samu ciki"
"ta haifi ɗa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya ji cewa mai gidana ba ya ƙauna ta"
Masu fassara zasu iya gara dan bayani da zai ce "sunan Simiyon na nufin 'Ji."
"mijina zai rungume ni"
"na haifi 'ya'ya maza uku"
Masu fassara zasu iya gara dan bayani da zai ce "Sunan Lebi na nufin 'haɗewa"
"Liya ta sake daukar ciki"
"ta haifi ɗa"
Masu fassara zasu iya gara dan bayani da zai ce "Sunan Yahuda na nufin 'yabo."
1Da Rahila ta ga cewa ba ta haifa wa Yakubu 'ya'ya ba, sai Rahila ta ji kishin 'yar'uwarta. Ta ce wa Yakubu, "Ba ni 'ya'ya, ko in mutu."2Fushin Yakubu ya yi ƙuna gãba da Rahila. Ya ce, "Ina a madadin Allah ne, wanda ya hana ki samun 'ya'ya?"3Ta ce, "Duba, wannan baiwata ce Bilha. Ka kwana da ita, saboda ta haifi 'ya'ya bisa gwiwoyina, kuma in sami 'ya'ya ta wurin ta."4Sai ta bayar da baiwarta Bilha a matsayin mata, Yakubu kuma ya kwana da ita.5Bilha ta ɗauki ciki ta haifa wa Yakubu ɗa.6Daga nan Rahila ta ce, "Allah ya baratar da ni, ya kuma ji muryata ya kuma bani ɗa." Domin wannan dalili ta kira sunansa Dan.7Bilha, baiwar Rahila, ta sake ɗaukar ciki ta haifa wa Yakubu ɗa na biyu.8Rahila ta ce, "Da kokowa mai girma na yi kokowa da 'yar'uwata na kuma yi nasara." Ta kira sunansa Naftali.9Sa'ad da Liya ta ga cewa ta tsaya da haihuwar 'ya'ya, ta ɗauki Zilfa, baiwarta, ta bayar da ita ga Yakubu a matsayin mata.10Zilfa, baiwar Liya, ta haifa wa Yakubu ɗa.11Liya ta ce, "Wannan rabo ne!" Sai ta kira sunansa Gad.12Daga nan Zilfa, baiwar Liya, ta haifa wa Yakubu ɗa na biyu.13Liya ta ce, "Na yi murna! domin 'ya'ya mata zasu kira ni murna." Sai ta kira sunansa Asha.14Ruben ya fita a lokacin yankan alkama ya kuma samo 'ya'yan itacen manta'uwa daga saura. Ya kuma kawo su wurin mahaifiyarsa Liya. Daga nan Rahila ta ce wa Liya, "Ki ba ni daga cikin 'ya'yan itacen manta'uwa na ɗanki."15Liya ta ce mata, "Ƙaramin al'amari ne a gare ki, cewa kin ɗauke mani miji? Ki na so yanzu ki ɗauke 'ya'yan manta'uwa na ɗana, kuma?" Rahila ta ce, "To zai kwana dake a daren nan, a matsayin musanya domin 'ya'yan manta uwa na ɗanki."16Yakubu ya dawo daga gona da yamma. Liya ta fita ta same shi ta ce, "Tilas ka kwana da ni a daren nan, domin nayi hayar ka da 'ya'yan manta'uwa na ɗana." Sai Yakubu ya kwana da Liya a wannan daren.17Allah ya saurari Liya, ta kuma ɗauki ciki ta haifa wa Yakubu ɗa na biyar.18Liya ta ce, "Allah ya bani ladana, saboda na bayar da baiwata ga mijina." Sai ta kira sunansa Issaka.19Liya ta sake ɗaukan ciki ta haifa wa Yakubu ɗa na shida.20Liya ta ce, "Allah ya bani kyauta mai kyau. Yanzu mijina zai girmama ni, saboda na haifa masa 'ya'ya maza shida." Ta kira sunansa Zebulun.21Daga baya ta haifi ɗiya ta kuma kira sunanta Dina.22Allah ya tuna da Rahila ya kuma saurare ta. Ya sa ta ɗauki ciki.23Ta ɗauki ciki ta haifi ɗa. Ta ce, "Allah ya ɗauke kunyata."24Ta kira sunansa Yosef, cewa, "Yahweh ya ƙara mani wani ɗan."25Bayan da Rahila ta haifi Yosef, sai Yakubu yace wa Laban, "Ka sallame ni saboda in tafi nawa gidan da ƙasata.26Ka bani matayena da 'ya'yana waɗanda domin su na yi maka bauta, bari kuma in tafi, gama ka san hidimar dana yi maka."27Laban yace masa, "Idan yanzu na sami tagomashi a gaban ka, ka jira, saboda ta wurin amfani da sihiri na gane cewa Yahweh ya albarkace ni saboda kai."28Daga nan ya ce, "Ka faɗi ladanka, zan kuma biya su."29Yakubu yace masa, "Ka san dai yadda na bauta maka, da yadda dabbobinka suka kasance tare da ni.30Domin 'yan kaɗan kake da su kafin in zo, kuma sun ƙaru a yalwace. Yahweh ya albarkace ka a duk inda na yi aiki. Yanzu yaushe zan samar wa nawa gidan shi ma?"31Sai Laban yace, "Me zan biya ka?" Yakubu yace, "Ba zaka bani komai ba. Idan zaka yi wannan domina, zan sake ciyar da dabbobinka in kiwata su kuma.32Bari in ratsa cikin dukkan dabbobinka a yau, zan ware daga cikin su duk wasu tumaki dabbare-dabbare da masu ɗigo, da waɗanda ke baƙaƙe daga cikin tumakin, da masu ɗigo da kyalloli daga cikin awakin. Waɗannan ne zasu zama ladana.33Amincina zai yi shaida game da ni daga bisani, sa'ad da zaka zo ka duba ladana. Duk wadda ba kyalla ba ce ko mai ɗigo daga cikin awaki, da baƙa daga cikin tumaki, duk wadda a ka samu a wurina, a ɗauke shi a matsayin sata."34Laban yace, "Na yarda. Bari ya kasance bisa ga maganarka."35A wannan rana Laban ya ware dukkan bunsurai masu zãne da masu ɗigo, da dukkan awaki kyalloli da masu ɗigo, duk wata mai fari a jikinta, da dukkan baƙaƙe daga cikin tumaki, ya kuma bayar da su cikin hannun 'ya'yansa.36Laban kuma ya sa tafiya ta kwana uku tsakaninsa da Yakubu. Sai Yakubu ya ci gaba da kiwon sauran dabbobin Laban.37Sai Yakubu ya ɗauko ɗanyun tsabgun auduga, da rassan itacen almond da rassan itacen durumi, ya kuma fera fararen zãne a kan su, ya sanya fararen itatuwan dake cikin ƙiraren su bayyana.38Daga nan ya jera ƙiraren da ya feffere a gaban dabbobin, a gaban kwamamen ruwa in da suke zuwa su sha. Suna ɗaukar ciki sa'ad da suka zo shan ruwa.39Dabbobin suka yi ta barbara a gaban ƙiraren; dabbobin kuma suka yi ta haihuwar 'ya'yai masu zãne, da kyalloli, da masu ɗigo.40Yakubu ya ware waɗannan 'yan raguna, amma ya sanya sauran su fuskanci dabbobin masu zãne da dukkan baƙaƙen tumaki a garken Laban. Daga nan sai ya ware nasa dabbobin domin kansa kaɗai ba ya kuma haɗa su tare da dabbobin Laban ba.41A duk sa'ad da ƙarfafan tumakin ke barbara, sai Yakubu ya shimfiɗa ƙiraren nan a cikin kwamamen ruwan nan a gaban idanun dabbobin, saboda su ɗauki ciki a tsakiyar ƙiraren.42Amma idan dabbobi marasa ƙarfi daga cikin garken suka zo, ba ya sanya ƙiraren a gabansu. Sai ya zama dabbobin marasa ƙarfi na Laban ne, ƙarfafan kuma na Yakubu ne.43Mutumin ya zama wadatacce sosai. Yana da manyan garkuna, bayi mata da bayi maza, da raƙuma da jakuna.
"Lokacin da Rahila ta fahimci cewa ta kasa daukar ciki"
"Ka sa ni in yi ciki"
Rahila tana wuce gona da iri don nuna bacin ranta game da rashin yara. AT: "Zan ji ba ni da daraja kwata-kwata"
An yi maganar fushin Yakubu kamar wuta ne. AT: "Yakubu ya yi fushi da Rahila"
Yakubu ya yi amfani da wannan tambayar ne ya tsauta wa Rahila. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Ni ba Allah ba ne, Ba ni ba ne na ke hana ki samun 'ya'ya!"
"Rahila yace"
A wancan lokacin, wannan hanya ce karɓaɓɓiya ga mace bakarariya ta sami 'ya'yan waɗanda doka za ta iya zama nata. Cikakkiyar ma’anar wannan na iya zama bayyane.
Wannan wata hanyar faɗin cewa ɗan da Bilha ta haifa zai zama na Rahila. AT: "mini"
"ta haifi ɗa na miji wa Yakubu"
"Rahila ta sanya masa suna"
Masu fassarar wannan na iya sharinhinta cewa "ma'anar sunan Dan shi ne 'ya shari'anta.'"
"Bilhah ... ta sake samun ciki"
An yi amfani da maganan nan "kokawa na yi kokawa" domin a jadada maganar, an kuma yi maganar koƙarin da Rahila ta yi ta sami 'ya'ya kamar 'yar uwarta, kamar tana fada na jiki ne da Liya. AT: "Na yi fama mai girma domin in sami 'ya'ya kamar babar 'yar uwata Liya" (UDB)
Masu fassarar wannan na iya sharihinta cewa "ma'anar sunan Naftali shine 'gwagwarmayata.'"
"Lokacin da Liya ta san da hakan"
"ta ba da Zilfa, baiwarta, ga Yakubu a matsayin mata"
"Wannan sa'a mai kyau ne"
Masu fassarar wannan na iya sharihinta cewa "Ma'anar sunan Gad shine 'rabo.'"
Masu fassarar wannan na iya sharihinta cewa "Ma'anar Asha shi ne 'farin ciki.'"
Wannan 'ya'yan itace ne da ake cewa ya na ba da karfin ba da 'ya'ya da marmarin kwana da masoyi. AT: "kwayar soyaya"
"Ba ki damu ba ... miji na? Wannan tambaya ne domin tsautawa Rahila.Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "munin ya yi haka ... miji na.?
"To Yakubu zai kwana" ko "To zan bar Yakubu ya kwana"
"don farashin manta'uwa ɗana." Duba ya aka juya "manta'uwa" a Farawa 30:14.
An yi maganar yadda Allah ya ba Liya lada kamar yadda wani ubangida na biyan ma'aikaci ne da ya yi masa aiki. AT: "Allah ya yi mani sakamako"
Masu fassara wannan na iya sharihinta cewa: "Ma'anar sunan Issaka shine 'akwai sakamako.'"
Masu fassara wannan na iya sharihinta cewa: "Ma'anar sunan Zebulun shine 'daraja.'"
Wannan sunar ɗiyar Liya ce.
Maganar "kira zuwa ga tunani" na nufin tunawa. Wannan baya nufin Allah ya manta da Rahila. Yana nufin ya yi la’akari da bukatarta. AT: "Allah ya duba Rahila, ya kuma ba ta abin da ta ke so"
Ana magana game da Allah da ya sa Rahila ta daina jin kunya kamar “kunya” wani abu ne da mutum zai iya ɗauka daga wani. Ana iya bayyana kalmar ta "kunya" a matsayin "abin kunya". AT: "Allah ya sa ban daina jin kunya ba"
Masu fassara wannan na iya sharihinta cewa: "Ma'anar sunan Yosef shine 'bari ya kara.'"
'Ya'ya fari na Rahila daga baiwarta ce Bilha.
"Da Rahila ta haifi Yosef"
"domin in tafi"
Yakubu na tunar da Laban shirin da su ka yi
Idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. AT: "Idan na sami tagomashi a gare ka"
"Na gano ta ruhaniya da sihiri ayyuka"
Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "Ka faɗa mini nawane zan biya ka domin ka zauna a nan"
"lafiyar dabbobinka tun da na fara kiwon su"
"amma yanzu wadatarka sun karu sun kuma yi girma"
"garkenku sun kasance kadan kafin na yi muku aiki"
"Yanzu wani lokaci ne zan fara lura da nawa iyalin?" Yakubu ya yi tambaya ne domin ya jadada cewa shi ma ya na so ya fara tanadi wa iyalinsa. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Yanzu ina so in lura da iyalina!"
"Me zan iya biya muku" ko "Me zan iya ba ku." Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "Me zan iya biya muku don ku tsaya ku yi min aiki"
"in kuma ware kowani tumaki mai ɗigo, dukka baƙaƙe, da kuma kowani akuya mai ɗigo"
"Wannan ne sakamakon zama na a nan"
Kalmar nan "aminci" na nufin "gaskiya." Wannan yana magana ne game da mutunci kamar dai mutum ne wanda zai iya ba da shaida game da wani ko kuma game da shi. AT: "Daga baya kuma za ka sani ko na yi maka aminci ko ba haka ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Idan ka sami wani akuya mara ɗigo ko tumaki da ba baƙaƙe ka ɗauke su a matsayin sata"
AT: "Ya kasance yadda ka faɗi" ko "za mu yi kamar yadda ka faɗa"
"kowani akuya da ke da fari a jikinta"
"Hannu" a nan na matsayin iko ko kula. AT: "ba 'ya'yansa su kula da su"
Dukka waɗannan itatuwan masu farin katako ne.
"ya kuma fera bawon domin fararen zãnen itatuwan su nuna"
dogayen buɗaɗɗun buɗaɗɗun ruwa don dabbobi su sha
"Dabbobin suka haifu"
haifar 'ya'ya masu zãne, da ɗigo"
"ya ware dabbobin sa wani gyefe"
"idanu" a nan na nufi "kalo". AT: "domin dabbobin su kuma kale su"
"a gaban ƙiraren"
"Don haka raunanan zuriyar sun kasance na Laban, yayin da zuriyar ta fi ta Yakubu." Kuna iya bayyana wannan har ma a bayyane. AT: "Don haka raunanan zuriya ba su da ratsi ko tabo don haka na Laban ne, yayin da zuriya mafi ƙarfi ke da ratsi ko tabo don haka na Yakubu ne"
"Yakubu"
"ɓunkasa ƙwarai" ko "ya zama mai arziki sosai"
1Yanzu Yakubu ya ji maganganun 'ya'yan Laban maza, cewa sun ce, "Yakubu ya ɗauke dukkan abin dake na mahaifinmu, kuma daga mallakar mahaifinmu ne ya samo dukkan wannan dukiyar."2Yakubu ya kalli yanayin fuskar Laban. Ya ga cewa halinsa zuwa gare shi ya canza.3Daga nan Yahweh ya cewa Yakubu, "Ka koma ƙasar ubanninka da danginka, zan kuma kasance tare da kai."4Yakubu ya aika a ka kira Rahila da Liya zuwa saura a garkensa5ya kuma ce masu, "Na ga halin mahaifinku zuwa gare ni ya canza, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.6Kun san cewa da dukkan karfina ne na bautawa mahaifinku.7Mahaifinku ya ruɗe ni ya canza ladana sau goma, amma Allah bai ba shi damar cutar da ni ba.8Idan ya ce, "Dabbobin kyalloli zasu zama ladanka,' daga nan dukkan garken suka haifi jarirai kyalloli. Idan ya ce, "Ma su zãne zasu zama ladanka,' daga nan dukkan garken suka haifi 'ya'ya masu zãne.9Ta wannan hanya Allah ya ɗauke dabbobin mahaifinku ya kuma bayar da su a gare ni.10Sau ɗaya a lokacin yin barbara, na gani a mafarki cewa bunsuran na barbara da dabbobin. Bunsuran masu zãne ne, da kyalloli, da masu ɗigo.11Mala'ikan Allah yace da ni a cikin mafarkin, 'Yakubu.' Na ce, 'Ga ni nan.'12Ya ce, 'Ka ɗaga idanunka ka ga dukkan bunsuran dake barbara da dabbobin. Masu zãne ne, da kyalloli, da masu ɗigo, gama na ga dukkan abin da Laban yake yi maka.13Ni ne Allah na Betel, in da ka yi wa ginshiƙi shafewa, in da ka ɗaukar mani wa'adi. Yanzu ka tashi ka bar wannan ƙasar ka kuma koma ƙasar haihuwarka."'14Rahila da Liya suka amsa suka ce masa, "Akwai kuma wani rabo ko gãdo dominmu a gidan mahaifinmu?15Ba kamar bãre ya maida mu ba? Gama ya sayar da mu kuma ya lanƙwame kuɗinmu gabaɗaya.16Domin dukkan arzikin da Allah ya ɗauke daga wurin mahaifinmu yanzu na mu ne da 'ya'yanmu. To yanzu duk abin da Allah yace maka, sai ka yi."17Daga nan Yakubu ya tashi ya ɗora 'ya'yansa da matayensa bisa raƙumma.18Ya kora dukkan dabbobinsa gaba da shi, tare da dukkan kaddarorinsa, har da dabbobin da ya samu a Faddan Aram. Daga nan ya kama tafiya zuwa wurin mahaifinsa Ishaku a cikin ƙasar Kan'ana.19Sa'ad da Laban ya tafi yi wa tumakinsa sausaya, Rahila ta ɗauke allolin gidan mahaifinta.20Yakubu shi ma ya ruɗi Laban Ba'aramiye, ta wurin ƙin gaya masa cewa zai tashi.21Sai ya tsere da dukkan abin da yake da shi, nan da nan kuma ya wuce ƙetaren Kogi, ya kuma doshi zuwa ƙasar tudu ta Giliyad.22A rana ta uku a ka gaya wa Laban cewa Yakubu ya gudu.23Sai ya ɗauki danginsa ya kuma bi shi na tsawon tafiyar kwana bakwai. Ya sha kansa a ƙasar tudu ta Giliyad.24Sai Allah ya zo wurin Laban Ba'aramiye a cikin mafarki da dare ya kuma ce masa, "Ka yi hankali kada kayi magana da Yakubu mai kyau ko marar kyau."25Laban ya sha kan Yakubu. Yanzu Yakubu ya kafa rumfarsa a ƙasar tudu. Laban shi ma ya kafa sansani tare da danginsa a ƙasar tudu ta Giliyad.26Laban ya cewa Yakubu, "Mene ne ka yi, da ka ruɗe ni ka kuma ɗauke 'ya'yana mata kamar kamammun yaƙi?27Meyasa ka tsere a asirce ka kuma yi mani dabara ba ka kuma gaya mani ba? Da na sallame ka da biki da waƙe-waƙe, tare da tambari da garayu.28Ba ka bar ni na yi sumbar sallama ga jikokina da 'ya'yana ba. Yanzu ka aikata wawanci.29A cikin ikona ne in cutar da kai, amma Allah na mahaifinka ya yi magana da ni a daren da ya wuce ya ce, 'Ka yi hankali kada ka yi magana da Yakubu mai kyau ko marar kyau.'30Yanzu ka gudu saboda kana marmarin ka koma gidan mahaifinka. Amma me ya sa ka sace allolina?"31Yakubu ya amsa kuma ya ce wa Laban, "Saboda na ji tsoro kuma na yi tunanin za ka karɓe 'ya'yanka mata da ƙarfi daga gare ni sai na gudu a asirce.32Duk wanda ya sace allolinka ba zai ci gaba da rayuwa ba. A gaban dangoginmu, ka tantance abin da ke naka tare da ni ka ɗauka." Gama Yakubu bai san cewa Rahila ta sace su ba.33Laban ya shiga cikin rumfar Yakubu, cikin rumfar Liya, da cikin rumfar bayi matan biyu, amma bai gan su ba. Ya fita daga rumfar Liya ya shiga cikin rumfar Rahila.34A she Rahila ta ɗauki allolin gidan, ta sanya su a sirdin raƙumi, ta kuma zauna a bisansu. Laban ya bincike rumfar gabaɗaya, amma bai same su ba.35Ta ce wa mahaifinta, "Kada ka ji haushi, shugabana, cewa ba zan iya tashi ba a gabanka, domin ina cikin al'adata." Sai ya bincike amma bai ga allolin gidansa ba.36Yakubu ya husata ya yi gardama da Laban. Ya ce masa, "Mene ne laifi na? Mene ne zunubi na, da ka runtumo ni da zafi?37Gama ka duba dukkan mallakata. Me ka samu daga dukkan kayayyakin gidanka? Ka fito da su yanzu a gaban dangoginmu, sai su shar'anta a tsakanin mu biyu.38Shekaru ashirin ina tare da kai. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuma ci wani rago ba daga garkunanka.39Abin da bisashe suka yayyage ban kawo maka ba. Maimako, na ɗauki asararsa. Ko yaushe kana sa in biya duk wata dabbar da ta bace, ko wadda a ka sace da rana ko wadda a ka sace da dare.40Nan ni ke; da rana zafi na cinye ni, da dare cikin sanyin dusar ƙanƙara; na yi tafiya kuma babu barci.41Waɗannan shekaru ashirin ina cikin gidanka. Na yi maka aiki shekaru sha huɗu domin 'ya'yanka biyu mata, shekaru shida kuma domin dabbobinka. Ka canza ladana sau goma.42Idan ba domin Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim, da wanda Ishaku ke tsoro, yana tare da ni ba, tabbas da yanzu ka kore ni hannu wofi. Allah ya dubi tsanantawata da aiki tuƙuru dana yi, ya kuma tsauta ma ka a daren jiya."43Laban ya amsa ya ce wa Yakubu, "'Ya'yan mata 'ya'yana ne, jikokin jikokina ne, dabbobin kuma dabbobina ne. Dukkan abin da kake gani nawa ne. Amma me zan iya yi a yau game da waɗannan 'ya'ya matan nawa, ko kuma game da 'ya'yansu da suka haifa?44To yanzu, bari mu ɗauki alƙawari, kai da ni, bari kuma ya zama domin shaida tsakanin kai da ni."45Sai Yakubu ya ɗauki dutse ya kuma dasa shi a matsayin ginshiƙi.46Yakubu ya cewa danginsa, "Ku tattara duwatsu." Sai suka ɗebo duwatsu suka tattara su.47Laban ya kira shi Yagar Saha Duta, amma Yakubu ya kira shi Galid.48Laban yace, "Wannan tarin shaida ne tsakani na da kai a yau." saboda haka a ka kira sunansa Galid.49A na kuma kiransa Mizfa, saboda Laban yace, "Bari Yahweh ya duba tsakanin ka da ni, yayin da muka ɓace daga juna.50Idan ka wulaƙanta 'ya'yana mata, ko kuma ka auri wasu matan baya ga 'ya'ya na, ko da yake babu wanda ke tare da mu, duba, Allah ne shaida tsakanin ka da ni."51Laban ya cewa Yakubu, "Dubi wannan tarin, ka kuma dubi ginshiƙin, wanda na kafa tsakanin ka da ni.52Wannan tarin shaida ne, ginshiƙin kuma shaida ne, cewa ba zan ƙetare gaba da wannan tarin ba zuwa gare ka, kai kuma ba zaka ƙetare gaba da wannan tarin ba da wannan ginshiƙin zuwa gare ni ba, domin cutarwa.53Bari Allah na Ibrahim, da allahn Naho, da allolin mahaifinsu, su shar'anta tsakaninmu." Yakubu ya rantse da tsoron mahaifinsa Ishaku.54Yakubu ya miƙa hadaya a bisa tsaunin ya kuma kira danginsa su ci abinci. Suka ci suka zauna tsawon dare a tsaunin.55Tun da sassafe Laban ya tashi, ya sumbaci jikokinsa da 'ya'yansa mata ya albarkace su. Daga nan Laban ya tafi ya koma gida.
Wannan kalmar an yi amfani da ita ne a nuna tsaiko a cikin labarin. A nan marubucin ya fara bayyana sabon sashe na labarin.
A nan "maganganun" na nufin abin da suke faɗi. AT: "Yakubu ya ji cewa 'ya'yan Laban sun ce"
'Ya'yan Laban na yaya abin saboda sun yi fushi. AT: "duk abin da Yakubu ya dauka na mahaifin mu ne"
Waɗannan jimla guda biyun na ma'anar abu ɗaya ne. Na biyun na bayana fuskar Laban ne. AT: "Yakubu ya lura cewa Laban baya jin daɗinsa kuma"
"mahaifin ku Ishaku da kakan ku Ibrahim"
Yakubu ya aika a kira Rahila da Liya su same shi a fili inda yake tare da tumaki"
Za'a iya bayyana wannan ajimloli biyu. AT :"a garkensa. Ya kuma ce masu"
"Na lura mahaifinka baya farin ciki da ni yanzu"
Kalmar "kun" na nufin Rahila da Liya. AT: "Ku ma da kanku ku san yadda na bautawa mahaifinku da dukka karfina"
"ya yi mani ƙarya" ko "baya yi mani adalci ba"
"abin da ya ce zai biya ni"
Ma'anonin zasu iya zama 1) illa a fili (UDB) ko 2) ya sa Yakubu ya sha wuya a kowacce hanya.
"Dabbobi masu dabbura-dabbura"
"garken suka haifi"
"dabbobi masu zãne"
"Ta haka ne Allah ya ba da dabbobin mahaifinku a gare ni"
Yakubu ya ci gaba da ba wa matansa labari, Liya da Rahila.
"Lokacin barbara"
A nan "dabbobin" na nufin matan awakin. AT: "barbara da matan awakin na dabbobin"
"masu zãne ne, da kyalloli, da masu ɗigo"
Ma'anonin zasu iya zama 1) Allah da kansa ya bayyana a siffar mutum, ko 2) ɗaya daga cikin yan saƙon Allah ya bayyana. Tunda ba'a fahimci jimlar ba, ya fi sauki a fasara shi da "mala'ikan Allah."
"sai na amsa"
"I, ina jinka" ko "I, menene?" Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 22:1.
Mala'ikan Allah ya ci gaba da yin magana ga Yakubu.
Wannan wata hanya ce ta cewa "kalli sama."
A nan "dabbobin" na nufin matan awakin. AT: "barbara da matan awakin na dabbobin"
"masu zane da dabbura-dabbura"
Yakubu ya kwara mai a kan ginshiƙin domin ya miƙa shi ga Allah.
"ƙasar da aka haife ka"
Wannan ba yana nufin sunyi magana tare ba. Yana nuna sun yarda da juna.
Rahila da Liya sunyi amfani da tambaya su tabbatar da cewa babu wani abu da ya rage mahaifinsu ya bayar. AT: "Babu sauran abinda ya rage da zamu gada wurin mahaifin mu!"
Sun yi amfani da tambaya su nuna fushin su kan yadda mahaifin su yake yi masu. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mahaifin mu ya maishe mu kamar bare maimakon yaya!"
Za'a iya bayyana wannan. AT: "ya sayau da mu don ribar sa"
Laban yana amfani da kuɗin da ya kamata ya ba 'ya'yansa mata gaba ɗaya ana magana da shi kamar dai shi dabbar daji ce wacce ta ci kuɗin kamar abinci. AT: "ya gama amfani da kuɗinmu gaba ɗaya"
"na mu ne da 'ya'yanmu"
A nan "yanzu" ba tana nufin "a wannan lokacin ba" amma ana amfani da shi ne don jawo hankali ga bayanai masu mahimmanci da zasu biyo baya.
"ku yi duk abin da Allah ya ce kuyi"
Yakubu ya dauki dukan 'ya'yansa. An anbaci yayan sa ne domin sune magadan sa. AT: "ya'yansa"
"Ya kora dukkan dabbobinsa" A nan "dabbobinsa" na nufin dukan dabbobin gidansa.
"har da sauran dabbobin da ya samu lokacin da yake Fadan Aram"
"Ya tafi aƙsar Kan'ana inda mahaifinsa yake"
"Lokacin da Laban ya tafi don yanke gashin hisan tumakinsa"
Wannan na nufin Kogin Yuferatis.
"yayi tafiya zuwa"
"tsauninkan Giliyad" ko "tsaunin Giliyad"
Al'adar Yahudawa ce su fara ƙirga ranar tafiya a matsayin ranar farko. AT:"kwana biyu bayan sun barshi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT:"wani ya faɗawa Laban"
Yakubu kadai aka ambata domin shine shugaban iyalin. A bayyane yake cewa iyalin sa sun tafi tare da shi. AT:"Yakubu ya gudu da matansa da 'ya'yansa"
"sai Laban ya ɗauki"
"ya bi Yakubu"
Laban yayi tafiyar kwana bakwai do ya taras da Yakubu.
"ya same shi"
Kalmar "sai" an yi amfani da ita anan domin nuna alamar canji daga labarin zuwa gabatarwa gama da Laban. AT: "a daren nan Allah ya zo wurin Laban a mafarki"
Jimlar "mai kyau ko mara kyau" an yi amfani da su ne da nufin "komai." AT: "kada ka ce wani abu domin ka hana Yakubu tafiya"
Kalmar "yanzu" an yi amfani da ita anan domin nuna alamar canji daga labarin zuwa gabatarwa akan Yakubu da Laban. AT: "Lokacin da Laban ya taras da Yakubu, Yakubu ya kafa rumfarsa a ƙasar tudu. Laban shi ma ya kafa sansani tare da danginsa a ƙasar tudu ta Giliyad"
Laban yayi magana kan ƙoƙarin Yakubu na daukar iyalin sa su koma ƙasar Kan'ana kamar Yakubu ya dauke su a matsayin kamammun yaƙi kuma yana matsa masu su tafi tare da shi. Laban na yayatu saboda yayi fushi yana kuma son Yakubu ya yadda cewa yayi laifi domin abin da yayi.
"gudu a asirce"
"da farin ciki"
Kayan bushe-bushen na nufin kaɗe-kaɗe. AT: "tare da kaɗe-kaɗe"
a bin kiɗa ne mai kai kamar ganga da za'a iya bugawa tare da kuma ƙarafuna zagaye da ke bada amo idan an girgiza shi
A nan "jikoki" sun ƙunshi jikoki maza da mata. AT: "na yi sumbar sallama ga jikokina"
"Yanzu kayi aikin wawanci"
Wannan ba wai yana nufin "wannan lokacin ba,"amma an yi amfani da shi ne don jan hankali ga amfanin abin da ya biyo baya.
Kalmar "kai" na nufi duk wanda suke tare da Yakubu. AT: "Ina da isassun mutanen da zasu cutar da kai"
"ka" na nufin Yakubu kaɗai.
A nan "gidan" na nufin iyali. AT: "ka zauna gida tare da mahaifi da sauran iyali"
"gumaka na"
"na gudu a asirce saboda na ji tsoro kuma na yi tunanin za ka karɓe 'ya'yanka mata da ƙarfi daga gare ni"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "zamu kashe du wanda ya saci allolinka"
Kalmar "mu" na nufin dangin Yakubu da ya haɗa da dangin Laban. Dukan dangin zasu kula su tabbatar cewa komai na tafiya dai-dai.
"ka tantance abin da ke naka tare dani ka ɗauka"
Wannan ya canza daga labari zuwa matashiya akan Yakubu.
Wannan na nufin Zilfa da Bilha
"bai sami gumakan sa ba"
Kalmar "ashe" anyi amfani da ita ne don nuna canji daga labarin zuwa matashiya akan Rahila.
wuri ne a bayan raƙumi da mutum ke hawa
Kiran wani "shugabana" hanya ce ta girmama shi.
"domin ba zan iya tsayawa a gabanka ba"
Wannan na nufin lokaci a wata da mace ke zubar da jini daga mahaifarta.
"Yakubu ya cewa Laban"
Jimlar "menene laifi na" da "menene zunubi na" na nufin kusan abu ɗaya. Yakubu na tambayar Laban ya faɗa masa abin da yayi ba dai-dai ba. AT: "Me nayi ba dai-dai ba da zaka taso mini haka?"
A nan kalmar "da zafi" na nufin Laban ya tunkari Yakubu da hanzari da nufin ya kama shi.
"Me ka samu da yake kayan gidanka?"
A nan kalmar "mu" na nufin dangin Yakubu da na Laban. AT : "Ka fito da duk abin da ka samu gaban danginmu"
A nan "mu biyun" na nufin Yakubu da Laban. Jimlar "su shara'anta mu" na nufin a sansance mai gaskiya a cikin wata rashin jituwa. AT: "zasu shara'anta tsakanin mu biyun"
Yakubu ya ci gaba da magana ga Laban
"shekaru 20"
macen tumaki
Wannan na nufin basu taɓa ɓarin ciki ko haifar mataccen da ba.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Lokacin da naman jeji ya kashe daya daga cikin dabbobin ka ban kawo maka ba"
Ga Yakubu don ƙidaya matattun dabbobin Laban a matsayin asara daga garken nasa an yi maganarsa kamar yana da nauyi da zai ɗauka a kafaɗunsa. AT: "Maimakon na kirga ta a matsayin asara daga garkenku, sai na dauke ta a matsayin asara daga garkena"
Shan wahala cikin yanayin zafi da sanyi an bayyana shi kamar yanayin dabba cde da ke cin Yakubu. AT: "Ina tare da dabbobin ka da rana zafi da dare cikin sanyin dusar ƙanƙara"
Yakubu ya ci gaba da magana da Laban
"shekaru 20 na karshe"
"shekaru 14"
"Ka canza abin da ka ce zaka biya ni sau goma." Duba yadda aka fasara "lada na" a Farawa 31:7.
Yakubu na magana kan Allah ɗaya ne ba uku ba. AT: "Idan ba domin Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim, da wanda Ishaku ke tsoro, yana tare dani ba"
A nan kalmar "mahaifi" na nufin iyaye, Ishaku.
A nan kalmar "tsoro" na nufin "tsoron Yahweh," wanda ke nufin ka matuƙar girmama shi tare da nuna haka ta wurin yi masa biyayya
Wannan na nufin rashin komai. AT: "ba tare da komai ba"
Za'a iya bayyana "tsanantuwa" a matsayin "tsanani." AT: "Allah ya dubi yadda nayi aiki tuƙuru da yadda ka tsananta mini"
Laban yayi amfani da tambaya ya nuna ba abin da zai iya yi. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "amma, babu abin da zan iya yi don in dawo da yaya na mata da jikokina tare da ni."
A nan kalmar "shaida" ba tana nufin mutum ba, amma tana nufin alkawarin da Yakubu da Laban suka yi. Anyi maganar alkawarin kamar mutum ne wanda yana wurin lokacin da suka yi yarjejeniyar aiwatar wa cikin salama ga juna.
Wannan na nufin ƙaton dutse aka sa a ƙarshen ta don a yi sheda a wurin da wannan mahimmin abu ya faru
"a ɗora kan yan uwansu"
Cin abinci tare sashi ne na yin alkawarin ga juna.
Mai fassara zai iya ƙara dan bayani a ƙasa cewa: "Sunan Yagar Saha Duta na nufin 'tarin shaidu' a yaren Laban."
Mai fassara zai iya ƙara dan bayani a ƙasa cewa: "Sunan Galid na nufin "tarin shaidu' a yaren Yakubu.
Duwatsu basa shaida kamar mutum a zahirance. AT: "tarin zai zama abin tunawa tsakani na da kai"
Mai fassara zai iya ƙara dan bayani a ƙasa cewa: "Sunan Galid na nufin "tarin shaidu' a yaren Yakubu. Duba yadda aka fasara wannan a Farawa 31:45
Mai fassara zai iya ƙara dan bayani a ƙasa cewa: "Sunan Mizfa na nufin 'wakin gini.'"
A nan "ɓace ga juna" na nufin in bama tare. AT: "idan bama tare da juna"
A nan "mu" na nufin Laban da Yakubu. AT: "ko da ba wanda ke ganin mu"
"tunawa." Wannan ya ƙara armashi ga abin da aka faɗa a gaba.
Wannan tarin duwatsu zasu zama tuni ne da kuma iyaka ga Laban da Yakubu game da alƙawarin su. Sun yi maganar su kamar mutane shaidu.
Ibrahim kakan Yakubu ne. Naho kakan Laban ne. Mahaifin Ibrahim da Naho Tera ne. Ba dukan su ke sujada ga Yahweh ba.
Kalmar "tsoro" na nufin Yahweh, wanda Ishaku ke matukar girmamawa ta wurin yi masa biyayya.
Cin abinci tare alama ce ta yin alƙawari da juna.
Aya 55 ita ce ayar farko ta sura 32 a cikin ainihin juya Ibraniyanci, amma ayar sura 31 a yawan ci Littafi Mai Tsarki na wannan lokacin. Mun shawarci a bi tsarin yadda aka shirya Littafi Mai Tsarki na yaren ku.
Wannan na nufin marmarin abu mai kyau zai faru ga wani
1Yakubu shima ya tafi hanyarsa, mala'ikun Allah suka same shi.2Sa'ad da Yakubu ya gan su, ya ce, "Wannan sansanin Allah ne." sai ya kira sunan wannan wuri Mahanayim.3Yakubu ya aiki manzanni gaba da shi zuwa ga ɗan'uwansa Isuwa a cikin ƙasar Seyir, a cikin lardin Idom.4Ya dokace su, cewa, "Ga abin da zaku cewa shugabana Isuwa: Ga abin da bawanka Yakubu yace: 'Ina zaune tare da Laban, na kuma yi jinkirin dawowata har zuwa yanzu.5Ina da shanu, da jakkai, da garkunan tumaki, da awaki, bayi maza da bayi mata. Na aiko da wannan saƙon ga shugabana, domin in sami tagomashi a idanunka."'6Manzannin suka dawo wurin Yakubu suka kuma ce, "Munje wurin ɗan'uwanka Isuwa. Yana zuwa ya same ka, da mutane ɗari huɗu tare da shi."7Daga nan Yakubu ya tsorata kuma ya ji haushi. Sai ya raba mutanen dake tare da shi ya yi sansani biyu, da garkunan tumaki, da awaki, da garkunan shanu, da raƙumma.8Ya ce, "Idan Isuwa ya zo ga sansani ɗaya ya kawo mana hari, daga nan sansanin da ya rage zasu kuɓuce."9Yakubu yace, "Allah na mahaifina Ibrahim, da Allah na mahaifina Ishaku, Yahweh, wanda ya ce mani, 'Ka koma ga ƙasarka da danginka, zan kuma wadata ka,'10Ban cancanci dukkan ayyukanka na alƙawarin aminci ba da dukkan yarda da ka yi domin bawanka ba. Domin da sandana kawai na ƙetare wannan Yodan, yanzu kuma na zama sansanai biyu.11Ina roƙonka ka cece ni daga hannun ɗan'uwana, daga hannun Isuwa, domin ina jin tsoronsa, cewa zai kawo mani hari tare da iyaye matan da 'ya'yan.12Amma ka ce, 'Babu shakka zan sa ka wadata. Zan maida zuriyarka kamar rairayin teku, waɗanda ba za a iya lissafawa ba domin yawansu."'13Yakubu ya zauna nan a wannan daren. Ya ɗauki wasu daga cikin abin da yake da su a matsayin kyauta domin Isuwa, ɗan'uwansa:14awaki ɗari biyu da bunsuru ashirin, tumaki ɗari biyu da raguna ashirin,15raƙuma talatin masu shayarwa da 'ya'yansu, shanu arba'in, bijimai goma, jakkai mata ashirin da jakkai maza goma.16Waɗannan ya bayar dasu cikin hannun bayinsa, kowanne garke daban. Ya cewa bayinsa, "Ku tafi gaba da ni, ku sanya tazara tsakanin kowanne garken."17Ya umarci bawa na farko, cewa, "Idan Isuwa ɗan'uwana ya gamu da kai ya tambaye ka, cewa, 'Kai na wane ne? Ina za ka je? Dabbobin wane ne waɗannan da ke gabanka?'18Daga nan za ka ce, 'Na bawanka ne Yakubu. Kyauta ce a ka aiko wa shugabana Isuwa. Duba, shi ma yana zuwa bayanmu."'19Yakubu ya sake bada umarnai ga ƙungiya ta biyu, ta uku, da dukkan mutanen da suka bi garkunan. Ya ce, "Zaku faɗi abu iri ɗaya ga Isuwa idan kuka same shi.20Tilas kuma ku ce, 'Bawanka Yakubu yana zuwa bayanmu."' Gama ya yi tunani, "Zan tausar da shi da kyaututtukan da nake aikawa da su a gabana. Sai daga baya, sa'ad da zan gan shi, wataƙila zai karɓe ni."21Sai kyaututtukan suka tafi gaba da shi. Shi kuwa da kansa ya tsaya a wannan daren a cikin sansani.22Yakubu ya tashi da daddare, ya kuma ɗauki matayensa biyu, da matayensa barori su biyu, da 'ya'yansa maza sha ɗaya. Ya aika da su ƙetaren kududdufin Yabbok.23Ta wannan hanyar ya aika da su ƙetaren rafin tare da dukkan mallakarsa.24A ka bar Yakubu shi kaɗai, wani mutum kuwa ya yi kokowa da shi har wayewar gari.25Sa'ad da mutumin ya ga cewa ba zai kayar da shi ba, sai ya mazge shi a kwankwaso. Sai kwankwason Yakubu ya goce sa'ad da yake kokowa da shi.26Mutumin yace, "Bari in tafi, domin gari yana wayewa." Yakubu yace, "Ba zan bar ka ka tafi ba sai ka albarkace ni."27Mutumin yace masa, "Yayã sunanka?" Yakubu yace, "Yakubu."28Mutumin yace, "Ba za a sake kiran sunanka Yakubu ba, amma Isra'ila. Gama ka yi gwagwarmaya tare da Allah tare da mutane ka kuma yi nasara."29Yakubu yace masa, "Ina roƙon ka, ka faɗi mani sunanka." Ya ce, "Meyasa kake tambayar sunana?" Daga nan ya albarkace shi a wurin.30Yakubu ya kira sunan wurin Feniyel, gama ya ce, "Na ga Allah fuska da fuska, kuma rayuwata ta kuɓuta."31Rana ta taso bisa Yakubu sa'ad da yake wuce Feniyel. Yana ɗangyashi saboda kwankwasonsa.32Shi ya sanya har wa yau mutanen Isra'ila ba su cin jijiyoyin kwankwaso waɗanda suke mahaɗin kwankwaso, saboda mutumin ya yi wa jijiyoyin rauni sa'ad da ya sa kwankwason Yakubu ya goce.
Mai fassara zai iya ƙara dan bayani cewa "sunan Mahanayim na nufin 'sansani biyu.'"
Wannan yanki ne mai duwatsu a cikin yankin Idom.
Wannan na da baka cikin baka. Wato magana cikin magana. AT: "Wannan ne abin da nake so ka faɗawa shugabana Isuwa. Ku shaida masa cewa ina ... a idanun sa."
Yakubu na amfani da kalmomi masu tsabta yana kwatanta dan'uwansa a matsayin "shugaba na."
Yakubu na amfani da kalmomi masu tsabta yana kwatanta kansa a matsayin "bara"
A nan "idanunka" na nufin tunanin mutum ko ra'ayin sa. AT: "domin in sami tabbacin ka"
"mutum 400"
Wannan wani yanayi ne na mara daɗi da mutum ka tsinci kansa lokacin da akwai hatsarin da ke fuskantar sa ko wasu.
"damuwa:" ko "mawuyacin hali"
A nan "sansani" na nufin mutane. AT: "ya kawo mana hari a sansani ɗaya, daganan sansanin da ya rage zasu kuɓuce"
Wannan ba yana nufin alloli da yawa ba, amma ga Allah daya da suke yiwa sujada. AT: "Yahweh, wanda shine Allahn kaka na Ibrahim da baba na Ishaku"
Wannan magana ce cikin magana. AT: "Yahweh, Kai wanda ka ce in koma ƙasa ta da dangi na, ka kuma ce zaka wadata ni"
"da ga iyalinka"
"Zan yi alheri gare ka" ko "za yi maka yin kyau"
Kalmar "amincewa" da "dukkan yarda" zasu iya zama "aminci" da "biyayya." Ban cancanci ka ci gaba da zama da aminci gareni ba ko ka zama da yarda gare ni, bawan ka"
Wannan hayar cewa "ni" da ladabi ce
A nan "na zama" na nufin abin da yake da shi yanzu. AT: "gashi yanzu ina da mutane, danbbobi, da abin hannu da ke tare da ni domin in yi sansani biyu"
"cece ni"
A nan kalmar "hannu" na nufin iko. Jimloli biyun mai yiwuwa nada ma'ana ɗaya. Ta biyun ta bayyana mana yadda dan'uwan da Yakubu ke ƙudiri shine Isuwa. AT: "daga ikon dan'uwana, Isuwa" ko "daga dan'uwana, isuwa"
"I na sakkar zai yi"
Wannan magana ce cikin magana. AT: "Amma ka ce mani zaka wadata ni, za kuma ka maishe da zuriyata ... yawansu"
"yi maka alheri" ko "kulawa da kai"
Wannan na magana akan zuriyar Yakubu mai ɗinbin yawa kamar rairai na bakin teku.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda ba mai iya ƙirgawa saboda yawan su"
"200"
"20 ... 30 ... 40 ... 0"
"da kana nan su"
A nan "cikin hannun" na nufin a bada iko a kansu. AT: "Ya raba su zuwa ƙananun garke, ya ba kowanne baran sa iko akan garke"
"Bari a sami tazara tsakanin kowanne garken"
"ya bada umarni"
Wannan magana ce cikin magana. AT: "duk wanda ya tambaya ka shugabanka, ina zaka je, ko kuma wa ya mallaki wadannan dabbobin da ke gaban ka"
"wanene shugaban ka?"
"dabbobin wane ne waɗannan da ke gabanka?"
Wannan magana ce cikin magana. AT: "Ina so ga shaida masa cewa dukan wadannan na Yakubu ne, da baransa, kuma zai ba Isuwa shugaban sa. Bayan nan ka faɗa masa Yakubu na kan hanya zai same shi"
Yakubu na nuna kansa a matsayin baran Isuwa cikin natsuwa
Yakubu na nuna Isuwa a matsayin shugaban sa cikin natsuwa.
A nan "mu" na nufin baran da ke magana da sauran barorin da ke kawowa Isuwa kargunan.
"ya umarci ƙungiya ta biyu"
Ma'anonin zasu iya zama cewa: 1) "Kuma zaku ce, 'baran ka Yakubu"' ko 2) "za ku ce, 'baranka Yakubu.'"
"Zan tausar da shi " ko "Zan sa fushin sa ya tafi"
"zai amshe ni da zuciya ɗaya"
A nan "kyaututtuka" na nufin baran da ke kai kyaututtukan.
A nan "dakansa" na bayyana cewa Yakubu bai tafi tare da baran ba.
"barorin matayensa su biyu." Wannan na nufin Zilfa da Bilha
wuri mara zurfi a rafi wanda ke da saukin hayewa
Wannan sunan kogi ne.
"dukkan abin da yake da shi"
"har wayewar gari" (UDB)
"ƙugu." Wannan wani wuri ne inda ƙashin ƙafar sama ya haɗu da kwankwaso.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutumin ya goce wa Yakubu kwankwaso yayin da suke kokowa da shi"
"rana zata fito da sauri"
A nan "albarka" na nufin a furta abin kirki akan wani tare da yi masa fatan alheri.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Tabbas bazai yiwu ba! sai ka albarkace ni, kafin in barka ka tafi"
Masu fassara zasu iya ƙara wani dan bayani mai cewa "sunan Isra'ila na nufin 'yayi gwagwarmaya da Allah.'"
A nan "mutane" na nufin mutane gaba ɗaya
"Ya ce, ' Me yasa kake tambayar sunana?"' Wannan tambayar da bata buƙatar amsa an yi ta ne domin ta bada mamaki, tsokaci da sa Yakubu yin binbini akan abin da ya faru tsakanin sa da wancan mutumin da yayi gwagwarmaya da shi. AT: "Kada ka tambayeni suna na!"
Masu fassara zasu iya ƙara wani dan bayani mai cewa "sunan Feniyel na nufin 'fuskar Allah.'"
"fuska da fuska" na nufin mutum biyu na ganin juna a zahiri, a kusa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "duk da haka ya barni da rai"
Wannan ya canza labarin zuwa matashiya ga zuriyar Isra'ila.
Wannan na nufin harwa yau da marubucin ke rubuta wannan.
Wannan na nufin tsokar da ke hade ƙashin kwankwaso da mahadar sa
"ƙugu"
"yayin ƙoƙarin"
1Yakubu ya hango, kuma, duba, Isuwa na zuwa, tare da shi kuma mutane ɗari huɗu. Yakubu ya raba 'ya'yan tsakanin Liya, Rahila, da matayen biyu barori.2Daga nan ya sanya matayen barori da 'ya'yansu a gaba, a biye kuma Liya da 'ya'yanta, a biye kuma Rahila da Yosef na ƙarshen su dukka.3Shi da kansa kuma ya tafi gaba da su. Ya rusuna zuwa ƙasa sau bakwai, har sai da ya zo kusa da ɗan'uwansa.4Isuwa ya rugo ya same shi, ya rungume shi, ya rungumi wuyansa, ya sumbace shi kuma. Daga nan suka yi kuka.5Sa'ad da Isuwa ya hanga, sai ya ga matayen da 'ya'yan. Ya ce, "Su wane ne waɗannan mutanen tare da kai?" Yakubu yace, "'Ya'yan da Allah ta wurin alherinsa ya ba bawanka ne."6Daga nan bayi matan suka zo gaba tare da 'ya'yansu, suka kuma rusuna.7Sai Liya ita ma da 'ya'yanta suka zo gaba suka rusuna. A ƙarshe kuma Yosef da Rahila suka zo gaba suka rusuna.8Isuwa yace, "Mene ne kake nufi da dukkan waɗannan ƙungiyoyi da na tarar?" Yakubu yace, "Domin in sami tagomashi a gaban shugabana ne."9Isuwa yace, "Ina da isassu, ɗan'uwana. Ka ajiye abin da kake da shi domin kanka."10Yakubu yace, "A'a, ina roƙon ka, idan na sami tagomashi a idanunka, to ka karɓi kyautata daga hannuna, gama babu shakka, na ga fuskar ka, kuma kamar ganin fuskar Allah ne, kuma ka karɓe ni.11Ina roƙon ka ka karɓi kyautata da a ka kawo maka, saboda Allah ya aiwatar da alheri zuwa gare ni, saboda kuma ina da isassu." Haka nan Yakubu ya lallashe shi, Isuwa kuma ya karɓe su.12Daga nan Isuwa yace, "Mu kama hanya. Zan tafi gaba kafin kai."13Yakubu yace masa, "Shugabana yasan cewa yaran ƙanana ne, kuma tumakin da garken dabbobin suna renon ƙananansu. Idan a ka kora su da ƙarfi a rana ɗaya, dukkan dabbobin zasu mutu.14Ina roƙon ka bari shugabana ya tafi gaba da bawansa. Zan yi tafiya a hankali, bisa ga saurin dabbobin dake a gabana, bisa kuma ga saurin yaran, har sai na zo ga shugabana a Seyir."15Isuwa yace, "Bari in bar maka wasu daga cikin mutane na dake tare da ni." Amma Yakubu yace, "Meyasa zaka yi haka? Bari in sami tagomashi a idanun ubangijina."16Sai Isuwa a wannan ranar ya fara tafiya bisa hanyarsa ta komawa Seyir.17Yakubu ya tafi Sukkot, ya gina wa kansa gida, ya yi wa dabbobinsa kuma wurin zama. Saboda haka sunan wannan wuri ana kiransa Sukkot.18Sa'ad da Yakubu ya zo daga Faddan Aram, ya isa lafiya a birnin Shekem, wanda ke a cikin ƙasar Kan'ana. Ya kafa sansani kusa da birnin.19Daga nan ya sayi filin da ya kafa rumfarsa daga hannun 'ya'yan Hamo, mahaifin Shekem, a kan jimillar azurfa ɗari.20A nan ya kafa bagadi, ya kuma kira shi El Elohi Isra'ila.
"mutane 400"
Wannan ba yana nufin Yakubu ya raba yayan daidai ba. Yakubu ya raba yayan yadda kowanne ya ko ta tafi tare da mahaifiyarta.
"barorin mata." Wannan na nufin Bilha da Zilfa.
A nan "dakansa" na nuna Yakubu ya tafi shikadai a gaban wasu.
A nan kalmar "rusuna" na nufin duƙawa don nuna ƙasƙanci tare da bangirma ga wani.
"tarar da shi"
Za'a iya fasara wannan zuwa sabon jimla. AT: "Isuwa ya sa kafadarsa a kan Yakubu, ya rungume shi, ya kuma sumbace shi"
Ana iya fassara wannan a sarari. AT: "Sai Isuwa da Yakubu suka yi kuka saboda suna cike da farin cikin sake ganin juna"
"ya ga mata da yaran da ke tare da Yakubu"
Jimlar "bawanka" hanyar bangirma ce da Yakubu ya dubi kansa. AT: "wadannan ne ya'yan da Allah ta wurin alherinsa ya ba bawanka."
"barorin mata." Wannan na nufin Bilha da Zilfa.
A nan kalmar "rusuna" na nufin duƙawa don nuna ƙasƙanci tare da bangirma ga wani.
Maganar "dukkan wadannan ƙungiyoyin" na nufin kungiyoyin barorin da Yakubu ya aika su kai kyautai ga Isuwa. AT: "Me ya sa ka aiko duk wadan nan kungiyoyin su zo wuri na?"
A nan "gaban" na nufin tunanin mutum ko ra'ayin sa. AT: "Domin ka, ya shugaba na, ka gamsu da ni"
Jimlar "shugaba na" hanyar bangima ce ta nuna Isuwa.
Kalmar "dabbobi" ko "kaya" an fahimce ta. AT: "I na da isassun dabbobi"
A nan "idanunka" na nufin tunani ko ra'ayin mutum. AT: " idan na sami tagomashi a idanunka"
A nan "hannu" na nufin Yakubu. AT: "wadan nan kyaututtuka da na ke baka"
Za'a iya fasara wannan a matsayin sabuwar jimla. "hannu na. Domin tabbas"
Ma'anar wannan batu nada dan duhu. Mai yiwuwa ma'anar ta zama 1) Yakubu na murna cewa Isuwa ya gafarta masa kamar yadda Allah ya gafarta masa ko 2) Yakubu na mamakin sake ganin dan'uwansa kamar yadda yayi mamakin ganin Allah ko 3) Yakubu ya natsu domin zuwa gaban Isuwa kamar yadda ya natsu a gaban Allah.
A nan "fuska" na nufin Isuwa. Yana da kyau a fasara "fuska" saboda amfanin kalmar a nan da "fuskar Allah" da "fuska da fuska" a Farawa 32:29.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda bayina suka kawo maku"
"Allah yayi mani da kyau" ko "Allah ya albarkace ni sosai"
Abin da aka saba ne aƙi amsar kyauta da farko, amma sai a amsa kafin mai badawa ya yi fushi.
Wannan wata hanya ce ta bangirma da Isuwa ke wa kansa . AT: "kai,shugabana, ka sani"
Ana iya bayyana ma'anar a bayyane. AT: "yaran sun yi ƙanƙantar da bazasu iya tafiya da sauri ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Idan a ka kora su da ƙarfi a rana ɗaya"
Wannan wata hanya ce ta bangirma da ake wa Yakubu. AT: "Shugaba na, Ni baranka ne. Ina roko ka tafi gaban baranka"
"bisa ga saurin dabbobin da na ke kulawa zasu iya tafiya"
Wannan wani yanki ne mai tsaunika a Edom. Dubi yadda aka fassara wannan a 32:3
Yakubu yayi amfani da tambaya ya nuna Isuwa bai kamata ya bar mutane ba. AT: "Kada kayi haka!" ko "bai kamata kayi haka ba!"
Wannan wata hanya ce ta bangirma da ake wa Isuwa. AT: "kai, shugabana, ka" .
Masu fassara zasu iya ƙara dan bayani cewa, "Sunan Sukkot na nufin 'mahalli'"
Akawai alamun gidan harda iyalin sa. AT: "ya gina wa kansa gida da iyalinsa"
"domin dabbobin da yake kulawa"
Wannan ya fara sabon sashi na labarin. Marubucin ya nuna abin da Yakubu yayi bayan ya huta a Sukkot.
"Bayan Yakubu ya bar Fadan Aram"
An faɗi Yakubu ne saboda shi ne shugaban iyalin. Wannan ya nuna iyalinsa na tare da shi.
"Ya kafa sansani kusa da"
"filin ƙasa"
Wannan sunan mutum ne.
Shekem sunan wani gari ne da kuma sunan wani mutum
Mai fassara zai iya ƙara dan bayani mai cewa: "sunan El Elohi Isra'ila na nufin Allah, Allahn Isra'ila."
1Sai Dinah, ɗiyar Liya wadda ta haifawa Yakubu, ta fita ta tafi wurin 'yanmatan ƙasar.2Shekem ɗan Hamo Bahibiye, yariman ƙasar, ya ganta ya kuma cafke ta, ya ɓata ta, ya kuma kwana da ita.3Ya shaƙu da Dinah, ɗiyar Yakubu. Ya ƙaunaci yarinyar, ya kuma yi mata magana mai taushi.4Shekem ya yi magana da mahaifinsa, cewa, "Ka samo mani wannan yarinyar a matsayin mata."5Yanzu Yakubu ya ji cewa ya lalata ɗiyarsa Dina. 'Ya'yansa kuma na tare da dabbobinsa a saura, sai Yakubu ya kame bakinsa har sai da su ka zo.6Hamo mahaifin Shekem ya tafi wurin Yakubu domin ya yi magana da shi.7'Ya'yan Yakubu suka dawo daga saura sa'ad da suka ji batun al'amarin. Mutanen ransu ya ɓaci. Suka fusata sosai saboda ya kunyatar da Isra'ila ta wurin tilasta kansa bisa ɗiyar Yakubu, domin bai kamata a aiwatar da irin haka ba.8Hamo ya yi magana da shi, cewa, "Ɗana Shekem na ƙaunar ɗiyarka. Ina roƙon ka. ka bayar da ita a gare shi a matsayin mata.9Ku yi auratayya da mu, ku bayar da 'ya'yanku mata a gare mu, ku kuma ɗauki 'ya'yanmu mata domin kanku.10Zaku zauna tare da mu, za a buɗe ƙasar kuma a gare ku domin ku zauna ku kuma yi sana'a a ciki, ku kuma mallaki kaddarori."11Shekem yace wa mahaifinta da 'yan'uwanta maza, "Bari in sami tagomashi a idanunku, duk kuma abin da kuka ce mani zan bayar.12Ku tambaye ni komai yawan sadakin da kyautar da kuke so, kuma zan bayar da duk abin da kuka ce, amma dai ku bani yarinyar a matsayin mata."13'Ya'yan Yakubu suka amsa wa Shekem da Hamo mahaifinsa tare da zamba, saboda Shekem ya ɓata Dina 'yar'uwarsu.14Suka ce masu, "Ba za mu iya yin wannan abu ba, mu bayar da 'yar'uwarmu ga duk wani wanda ba shi da kaciya; domin zai zama abin kunya a gare mu.15Sai dai a kan wannan matakin kaɗai za mu yarda da ku: Idan zaku zama masu kaciya kamar mu, idan kowanne namiji a cikin ku an yi masa kaciya.16Daga nan ne za mu bayar da 'ya'yanmu mata a gare ku, mu kuma zamu ɗauki 'ya'yanku mata a gare mu, mu kuma zauna daku mu zama mutane ɗaya.17Amma idan baku saurare mu ba kuka zama masu kaciya, daga nan zamu ɗauki 'yar'uwarmu kuma za mu tashi."18Maganganunsu suka gamshi Hamo da ɗansa Shekem.19Saurayin bai ɓata lokaci ba wurin yin abin da suka ce, saboda yana jin daɗin ɗiyar Yakubu, saboda kuma shi ne taliki mafi daraja a dukkan gidan mahaifinsa.20Hamo da ɗansa Shekem suka tafi ƙofar birninsu suka kuma yi magana da mutanen birninsu, cewa,21"Mutanen nan suna zaman salama da mu, bari su zauna cikin ƙasar su kuma yi sana'a a ciki domin, tabbas, ƙasar na da isasshen girma domin su. Bari mu ɗauki 'ya'yansu mata a matsayin matayen aure, bari kuma mu bayar da 'ya'yanmu mata a gare su.22A wannan matakin kaɗai mutanen za su yarda su zauna da mu kuma mu zama mutane ɗaya. Idan a ka yi wa kowanne namiji a cikin mu kaciya, kamar yarda suke da kaciya.23Ba dukkan dabbobinsu da kaddarorinsu - dukkan dabbobinsu zasu zama namu ba? Don haka mu yarda da su, zasu kuma zauna a cikinmu."24Dukkan mutanen birnin suka saurari Hamo da Shekem, ɗansa. Kowanne namiji a ka yi masa kaciya.25A rana ta uku, sa'ad da suke cikin zafi tukuna, 'ya'yan Yakubu biyu (Simiyon da Lebi 'yan'uwan Dina), kowannen su ya ɗauki takobinsa suka kuma kai hari ga birnin dake da tabbacin tsaro, suka kuma kashe dukkan mazajen.26Suka kashe Hamo da ɗansa Shekem ta kaifin takobi. Suka ɗauke Dina daga gidan Shekem suka yi tafiyar su.27Sauran 'ya'yan Yakubu suka zo wurin gawawwakin suka washe birnin, saboda mutanen sun ɓata 'yar'uwarsu.28Suka ɗauki garkunan tumakinsu dana awaki, da garkunan shanunsu, da jakkansu, da duk wani abu dake cikin birnin da gonakin dake kewaye tare da29dukkan dukiyarsu. Dukkan 'ya'yayensu da matayensu, suka kame. Suka ma ɗauke kowanne abu dake cikin gidajen.30Yakubu ya cewa Simiyon da Lebi, "Kun kawo mani matsala, domin kun sa in yi ɗoyi ga mazaunan ƙasar, da Kan'aniyawa da Feriziyawa. Ni kima ne a lissafi. Idan suka tattara kansu tare gãba da ni, su kuma kawo ma ni hari, daga nan zan hallaka, ni da gidana."31Amma Simiyon da Lebi suka ce, "Ya kamata Shekem ya yi da 'yar'uwarmu kamar karuwa?"
A nan amfanin wannan kalmar shine na alamar sabon sashi na labarin
Wannan sunan 'yar Liya ne. Duba yadda aka fassara wannan sunan a Farawa 30:19.
Wannan sunan wani kungiyar mutane ne. Duba yadda aka fassara wannan sunan a Farawa 10:15.
Wannan Hamor ne ba Shekem ba. Kuma, "yarima" a nan ba yana nufin dan sarki ba. Yana nufin Hamor ne shugaban mutane a wannan yankin
Shekem yayi wa Dina fyaɗe.
"Ta dauke masa hankali"
Wannan na nufin yana yi mata magana mai sosa zuciya don ya gamsar da ita yana son ta haka kuma yana son ta kaunace shi.
"Yanzu" an yi amfani da ita a nan don nuna canji daga labari zuwa matashiya game da Yakubu.
Kalmar "ya" na nufin Shekem
Wannan yana nufin cewa Shekem ya ƙasƙantar da Dina sosai ta hanyar tilasta mata ta kwana da shi.
Wannan hanya ce ta cewa Yakubu bai ce ko yi wani abu kan matsalar ba.
"Hamor ... ya tafi wurin Yakubu"
"mutanen sun fusata"
Wannan zai iya zama maganar da dan Yakubu yayi, kamar yadda ya ke a UDB. (Duba:
A nan kalmar "Isra'ila" na nufin dukan iyalin Yakubu. Isra'ila a matsayin mutane sun kunyata. AT: "ya ƙasƙantar da iyalin Isra'ila" ko "ya kawo abin kunya ga mutanen Isra'ila"
"cin zarafin yarinyar Yakubu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "domin bai kamata a aiwatar da irin haka ba"
"Hamor ya yi magana da Yakubu da 'ya'yan sa"
Kalmar "kaunar" na nufin son da ke tsakanin namiji da mace. AT: "kaunar ta da son auren ta"
A wasu al'adun, iyaye kan zaɓa wa yayan su wadanda zasu aura.
A yi auratayya na nufin auren wanda ba asalin ku ɗaya ba. AT: "barin auratayya tsakanin mutanen ku da mutanen mu"
"za a buɗe ƙasar a gare ku"
"Shekem ya ce wa mahaifin Dina wato Yakubu"
A nan "idanun" na matsayin tunani ko ra'ayin mutum. AT: "idan zaka amince mini, to zan baka duk abinda kake buƙata"
A wasu al'adun, akan buƙaci namiji ya bada kuɗi, kadara, dabbobi, da wasu kyaututtuka ga iyalin budurwar a lokacin aure.
Kalmar "zamba" zata iya komawa "karya". AT: "Amma yaran Yakubu sun yi wa Shekem da Hamor ƙarya lokacin da suka amsa masu"
Wannan yana nufin cewa Shekem ya ƙasƙantar da Dina sosai ta hanyar tilasta mata ta kwana da shi. Duba yadda kuka fassara "ƙazantacce" a cikin Farawa 34:4.
"'Ya'yan yakubu suka cewa Shekem da Hamor'"
"Ba zamu yarda mu bada Dina aure ba"
"domin zai zama abin kunya a gare mu." A nan "mu" na nufin 'ya'yan Yakubu da dukkan mutanen Isra'ila.
Wannan na nufin zasu bar wani daga cikin iyalin Yakubu ya auri wani mazaunin ƙasar Hamor.
A nan "kalmar" na nufin abin da aka faɗa. AT: "Hamor da ɗansa suka yarda da abinda 'ya'yan Yakubu suka faɗa"
"su yi kaciya"
"Yarinya Yakubu Dina"
Za'a iya fasara wannan a matsayin sabuwar jimla. Mai yiwuwa Shekem ya san cewa sauran mutanen zasu yarda a yi masu kaciya domin suna girmama shi sosai. AT: "Shekem ya san cewa duk mutanen da ke gidan sa zasu yarda da shi domin an fi darajanta shi a tsakanin su"
Abin da aka saba gani ne shugabanni su haɗu a ƙofar birni domin yanke shawara a hukumance.
"Yakubu, 'ya'yan sa, da kuma mutanen Isra'ila"
A nan "mu" ta ƙunshi Hamor, ɗansa da dukkan mutanen da suka yi magana dasu a ƙofar birnin.
"bari su zauna cikin ƙasar su yi kasuwanci a ciki "
Shekem yayi amfani da kalmar "tabbas" domin ƙara armashi ga batun. "saboda, tabbas, ƙasar na da isasshen girma domin su" ko "saboda, da gaske, akwai isasshen fili domin su"
Wannan na nufin aure tsakanin matan wata ƙabila da mazan wata ƙabila. Duba yadda aka fasara makamantan jimloli a cikin Farawa 34:8
Hamor da ɗansa Shekem sunci gaba da magana ga dattawan gari.
"Sai dai ƙadai idan a ka yi wa kowanne namiji a cikin mu kaciya, kamar yarda mutanen Isra'ila ke da kaciya, za su yarda su zauna da mu kuma mu zama mutane ɗaya"
Shekem yayi amfani da tambaya don tabbatar cewa dabbobi da kadarorin Yakubu zasu zama na mutanen Shekem. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Dukkan dabbobin su da kadarorinsu zasu zama namu."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Don haka Hamor da Shekem suka sami wanda ya yiwa dukan maza kaciya"
"uku" lamba ce ta uku. Za a iya cewa. AT: "Bayan kwana biyu"
"sa'ad da mutanen garin ke cikin zafi tukuna"
"suka ɗauki takubban su"
A nan "birnin" na nufin mutane. AT: "sun kai hari ga mutanen birnin"
Za a iya fasara wannan a matsayin sabuwar jimla. "tsaro. Simiyon da Lebi suka kashe dukkan mazajen birnin"
A nan "kaifin" na nufin kaifin takobi. AT: "ta wurin kaifin takobin su" ko "da takobin su"
"gawarwakin Hamor, Shekem, da mutanen su"
"suka sace duk wani abu mai kyau dake birnin"
Shekem kadai ya ci zarafin Dinah, amma 'ya'yan Yakubu sun dauki iyalin Shekem da duk mazaunin garin a matsayin masu hannu a ciki
"'ya'yan Yakubu suka ɗauki garkunan"
"duk abin da suka mallaka da kuɗi"
"suka ɗauke dukkan 'ya'yayensu da matayensu"
Kawowa wani matsala an bayyana shi kamar matsala wata aba ce da ake kawowa tare da dorawa akan wani. AT: "Kun kawo mani matsala babba"
Sa mutanen garin su nuna ƙiyayya kan Yakubu an bayyana shi kamar yayan Yakubu sun mai dashi yana ɗoyi a zahiri. AT: "kun maishe ni abin kwatanci ga mutanen gari"
A nan kalmar "Ni" da "mani" na nufin iyalan gidan Yakubu. Yakubu yace "Ni" ko "mani" kawai saboda shi ne shugaba. AT: "Gidana kima ne ... gãba da mu, su kuma kawo mana hari, daganan zamu hallaka"
"su kafa runduna su kawo mani hari" ko "su kafa runduna su kawo mana hari"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "zasu hallaka ni" ko "zasu hallaka mu"
Simiyon da Lebi sun yi amfani da tambaya wajen tabbatar da cewa Shekem yayi mugun abu da ya cancanci mutuwa. AT: "Bai kamata Shekem ya yi wa 'yar'uwarmu kamar ita karuwa ce!"
1Allah ya cewa Yakubu, "Ka tashi, ka nufi sama zuwa Betel, ka kuma zauna a can. Ka ginawa Allah bagadi a wurin, wanda ya bayyana a gare ka sa'ad da kake gujewa Isuwa ɗan'uwanka."2Daga nan Yakubu ya cewa gidansa da dukkan waɗanda ke tare da shi, "Ku fitar da bãƙin alloli dake a tsakaninku, ku tsarkake kanku, ku kuma canza suturarku.3Daga nan mu bar nan, mu nufi sama zuwa Betel. Zan ginawa Allah bagadi a can, wanda ya amsa mani a ranar ƙuncina, kuma ya kasance tare da ni dukkan inda na nufa."4Sai suka ba Yakubu dukkan bãƙin alloli da suke a hannunsu, da zobban da suke a kunnuwansu. Yakubu ya bizne su a ƙarƙashin rimi dake kusa da Shekem.5Yayin da suke tafiya, Allah ya sanya tsoronsu ya fãɗo a bisa biranen dake kewaye da su, domin haka waɗannan mutane ba su runtumi 'ya'yan Yakubu ba.6Sai Yakubu ya iso Luz (wato, Betel), wadda ke cikin ƙasar Kan'ana, shi da dukkan mutanen dake tare da shi.7Ya gina bagadi a nan ya kira sunan wurin El Betel, saboda a wurin ne Allah ya bayyana kansa a gare shi, sa'ad da yake gudu daga ɗan'uwansa.8Debora, mai kula da Rebeka, ta mutu. A ka bizne ta a gangare daga Betel ƙarƙashin itacen rimi, domin haka ana kiran wurin Allon Bakut.9Sa'ad da Yakubu ya zo daga Faddan Aram, Allah ya sake bayyana a gare shi ya kuma albarkace shi.10Allah yace masa, "Sunanka Yakubu, amma ba za a sake kiran sunanka Yakubu ba. Sunanka zai zama Isra'ila ne." Sai Allah ya kira sunansa Isra'ila.11Allah yace masa, "Ni ne Allah Mai Iko Dukka. Ka hayayyafa ka kuma ruɓanɓanya. Ƙasa da ƙungiyar ƙasashe zasu fito daga gare ka, kuma sarakuna zasu kasance cikin zuriyarka.12Ƙasar dana bayar ga Ibrahim da Ishaku, zan bayar a gare ka. Ga zuriyarka bayanka kuma zan bayar da ƙasar."13Allah ya tafi daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.14Yakubu ya kafa ginshiƙi a wurin da Allah ya yi magana da shi, ginshiƙin dutse. Ya zuba baikon sha a bisansa ya kuma zuba mai a kansa.15Yakubu ya kira sunan wurin inda Allah ya yi magana da shi, Betel.16Suka kama tafiya daga Betel. Yayin da suke da 'yar tazara daga Efrat, Rahila ta fãra naƙuda. Ta yi naƙuda mai wuya.17Yayin da take cikin azabar naƙuda, unguwar zomar ta ce mata, "Kada ki ji tsoro, domin yanzu za ki sami wani ɗan."18Yayin da take mutuwa, da numfashinta na mutuwa ta raɗa masa suna Ben-Oni, amma mahaifinsa ya kira shi da suna Benyamin.19Rahila ta mutu a ka kuma bizne ta a kan hanyar zuwa Efrat (wato, Betlehem).20Yakubu ya kafa ginshiƙi bisa kabarinta. Shi ne shaidar kabarin Rahila har ya zuwa yau.21Isra'ila ya ci gaba da tafiya ya kafa rumfarsa a gaba da hasumiyar tsaron garke.22Yayin da Isra'ila ke zaune a wannan ƙasa, Ruben ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra'ila kuma ya ji labari. Yakubu dai na da 'ya'ya maza sha biyu.23'Ya'yansa maza daga Liya su ne Ruben, ɗan fãrin Yakubu, da Simiyon, Lebi, Yahuda, Issaka, da Zebulun.24'Ya'yansa maza daga Rahila su ne Yosef da Benyamin.25'Ya'yansa maza daga Bilha, baiwar Rahila, sune Dan da Naftali.26'Ya'ya maza na Zilfa, baiwar Liya, su ne Gad da Asha. Dukkan waɗannan 'ya'yan Yakubu ne waɗanda a ka haifa masa a Faddan Aram.27Yakubu ya zo wurin Ishaku a Mamri a Kiriyat Arba (ita ce dai Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.28Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin.29Ishaku ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu, a ka kuma tattara shi ga kakanninsa, tsohon mutum cike da kwanaki. Isuwa da Yakubu, 'ya'yansa, suka bizne shi.
An yi amfani da kalmar "sama" saboda Betel na yankin da ke tudu fiye da Shekem.
Allah yai magana da kan sa a fakaice. AT: "Ka gina bagadi a can domina, Allahn ka"
"ya ce wa iyalin sa"
"Ku jefar da gumakan ku" ko "ku watsar da allolin karya dake tare da ku"
Wannan al'adar da aka saba ce ta yin tsarki kafin a wajen yin sujada ga Allah.
Sa sababbin tufafi alama ce ta nuna cewa sun maida kan su da tsarki kafin tunkarar Allah.
Ma'anonin "ranar" zasu iya zama 1) ranar da Yakubu ya gujewa Isuwa, ko 2) "ranar" na nufin lokacin da Yakubu ya shiga cikin ƙunci. AT: "lokacin da nake cikin mawuyacin hali" ko "lokacin da nake cikin matsala"
"saboda haka dukkan iyalan gidan Yakubu sun bada" ko "dukkan iyalin sa da barorin sa sun bayar"
A nan "a hannun su" na nufin abin da suka mallaka. AT: "da suka mallaka" ko "da suke dashi"
"zobban su" (UDB). Ma'anar na iya zama 1) zinariyar da ke kunnuwansu za'a iya amfani da su wajen yin wasu allolin, ko 2) suka dauki yan kunnen daga birnin Shekem bayan sun kai masa hari sun kashe dukan mutanen. Zobban zasu tuna masu da zunuban su.
Allah ya zubawa mutanen garin tsoron Yakubu da iyalin sa anyi maganar sa kamar tsoro wani abu ne da ke faɗowa kan mutane. Kalmar "tsoron" zata iya zama "fargaba." AT: "Allah ya sanya tsoronsu ya fãɗo a bisa biranen"
A nan "biranen" na nufin mutanen da suka rayu a garin.
Ya nuna babu mai yaƙar wani tsakanin iyalin Yakubu. Amma 'ya'yansa biyu, Simiyon da Lebi sun yaƙi yan'uwan Shekem Kan'aniyawa bayan ya ci zarafin ɗiyar Yakubu. Yakubu na tsoron zasu dauki fansa a Farawa 34:30. AT: "iyalin Yakubu" ko "gidan Yakubu"
Wannan sunan birni ne. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 28:18.
Mai fassara zai iya ƙara dan bayani mai cewa: "Sunan El Betel na nufin 'Allahn Betel.'"
"a wurin Allah ya bayyana kansa ga Yakubu"
Wannan sunan mace ne.
Mai jiya wata mace ce dake lura da yaron wata matar. Ana girmama mai jiyar sosai don tana da tasiri ga iyalin.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "A ka bizne ta a gangare daga Betel"
Jimlar "gangare daga" an yi amfani da ita ne domin an bizne ta a wurin da yake bai kai bisar yankin Betel ba.
Mai fassara zai iya ƙara dan bayani mai cewa: "Sunan Allon Bakut na nufin 'itacen rimi inda ake kuka."
Za a iya tabbatarwa cewa suna Betel. AT: "Sa'ad da Yakubu ya zo daga Fadan Aram, yayin da yake a Betel"
A nan "albarka" na nufin a bayyana abubuwa masu kyau akan wani da yi masa fatan alheri.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "amma ba za a sake kiran sunanka Yakubu ba"
"Allah ya cewa Yakuba"
Allah ya fadawa Yakubu ya hayayyafa don su mamaye duniya. Kalmar "hayayyafa" na bayyana yadda zai zama da "albarka." Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 1:22.
A nan "al'umma" da "al'ummai" na nufin zuriyar Yakubu wanda zasu gina ƙasashen.
A nan "tafi daga" an yi amfani da ita ne domin akan yi tsammanin Allah na zama a sama ko saman duniya. AT: "Allah ya bar shi"
Wannan ginshiƙin tunatarwa ne wanda a taƙaice na nufin babban dutse da aka kafa a karshen sa.
Wannan alama ce cewa yana miƙa ginshiƙin ga Allah.
Masu fassara zasu iya ƙara dan bayani mai cewa "Sunan Betel na nufin 'gidan Allah'"
Wannan wani suna ne na garin Betlehem.
"ta na samun matsaloli wajen wajen haihuwa"
"Lokacin da naƙudar tayi tsanani"
wani da ke taimakon mace yayin haihuwa
"numfashin mutuwa" numfashin karshe ne kafin mutum ya mutu. AT: "kafin ta mutu, yayin da take numfashin ta na karshe"
Mai fassara zai iya ƙara dan bayani mai cewa: "Sunan Benoni na nufin 'dan tausayi.'"
Mai fassara zai iya ƙara dan bayani mai cewa: "Sunan Benyamin na nufin 'dan hannun dama.'" Jimlar "hannun dama" na nuna wurin jinkai na musamman.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "sai aka bizne ta"
"a gefen hanya" (UDB)
"Alamar kabarin Rahila ne har wa yau"
"har zuwa yanzu." Wannan na nufin har lokacin da marubucin ke rubuta wannan.
Wannan ya nuna iyalin Isra'ila da barorinsa na tare da shi. Cikakkiyar ma'anar wannan bayani za a iya fayyace shi.
Wannan sunan baranyar Rahila ce. Duba yadda aka fassara wannan sunan a Farawa 29:28
Wannan ta fara sabon batu, wanda ya ci gaba a ayoyin da ke biye.
"'ya'ya maza 12"
Wannan ya nuna ba Benyamin cikin su wanda aka haifa a ƙasar Kan'ana kusa da Betlehem. An faɗi Fadan Aram ne saboda yawancin su a can aka haife su. AT: "waɗanda a ka haifa masa a Fadan Aram, in banda Benyamin da aka haifa a ƙasar Kan'ana"
A nan "zo" kan iya zama "je."
Wannan wani suna ne na birnin Hebron. Mai yiwuwa an sa sunan ne don martaba Mamri, abokin Ibrahim wanda ya zauna can. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 13:16.
Wannan sunan wani gari ne. Duba yadda aka fasaara wannan a Farawa 23:1
"shekaru 180"
"Ishaku ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu." Jimlar "ya yi numfashin sa na ƙarshe" da "mutu" na nufin kusan abu ɗaya. Duba yadda aka fasara irin wannan jimlar a Farawa 25:7. AT: "Ishaku ya mutu"
Wannan hanya ce ta cewa mutum ya mutu da taushin rai. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 25:7.
Wannan na nufin Ishaku ya mutu, ruhun shi ya tafi wurin da magabatan sa suka tafi. AT: "ya je wurin iyalin sa da suka mutu"
Jimlar "tsohon mutum" da "cike da kwanaki" na nufin kusan abu ɗaya. Sun bayyana Ishaku ya yi rayuwa ta dogon lokaci. AT: "bayan yayi rayuwa ta dogon lokaci ya kuma tsufa sosai"
1Waɗannan ne zuriyar Isuwa (wanda kuma a ke kira Idom).2Isuwa ya ɗauki matayensa daga Kan'aniyawa. Waɗannan ne matayensa: Ada ɗiyar Elon Bahittiye; Oholibama ɗiyar Ana, jikar Zibiyon Bahibbiye;3da Bashemat, ɗiyar Isma'il, 'yar'uwar Nebayot.4Ada ta haifi Elifaz da Isuwa, Bashemat kuma ta haifi Ruwel.5Oholibama kuma ta haifi Yewish, Yalam da Kora. Waɗannan ne 'ya'yan Isuwa waɗanda a ka haifa masa a ƙasar Kan'ana.6Isuwa ya ɗauki matayensa, da 'ya'yansa maza, da 'ya'yansa mata, da mutanen dake gidansa, da dabbobinsa - dukkan dabbobinsa, da dukkan mallakarsa, wadda ya tattara a ƙasar Kan'ana, ya tafi cikin wata ƙasa nesa da ɗan'uwansa Yakubu.7Ya yi haka ne saboda mallakarsu ta yi yawan da ba zasu iya zama tare ba. Ƙasar da suka zauna ba za ta iya ɗaukar su ba saboda yawan dabbobinsu.8Sai Isuwa, wanda kuma a ka sa ni da Idom, ya zauna a ƙasar tudu ta Seyir.9Waɗannan ne zuriyar Isuwa, kakan Idomawa a ƙasar tudu ta Seyir.10Waɗannan ne sunayen 'ya'ya maza na Isuwa: Elifaz ɗan Ada, matar Isuwa; Ruwel ɗan Bashemat, matar Isuwa.11'Ya'ya maza na Elifaz sune Teman, Omar, Zefo, Gatam, da Kenaz.12Timna, wata ƙwarƙwarar Elifaz, ɗan Isuwa, ta haifi Amalek. Waɗannan ne jikoki maza na Ada, matar Isuwa.13Waɗannan ne 'ya'ya maza na Ruwel: Nahat, Zera, Shamma, da Mizza. Waɗannan ne jikoki maza na Bashemat, matar Isuwa.14Waɗannan ne 'ya'ya maza na Oholibama, matar Isuwa, wadda ita ce ɗiyar Ana da jikar Zibiyon. Ta haifa wa Isuwa Yewish, Yalam, da Kora.15Waɗannan ne kabilu a cikin zuriyar Isuwa: Zuriyar Elifaz, ɗan fãrin Isuwa: Teman, Omar, Zefo, Kenaz,16Kora, Gatam, da Amalek. Waɗannan ne dangogin da suka fito daga Elifaz a ƙasar Idom. Su ne jikoki maza na Ada.17Waɗannan ne dangogi daga Ruwel, ɗan Isuwa: Nahat, Zera, Shamma, Mizza. Waɗannan ne dangogin da suka fito daga Ruwel a cikin ƙasar Idom. Su ne jikokin Bashemat, matar Isuwa.18Waɗannan ne dangogin Oholibama, matar Isuwa: Yewish, Yalam, Kora. Waɗannan ne dangogin da suka fito daga matar Isuwa Oholibama, ɗiyar Ana.19Waɗannan ne 'ya'ya maza na Isuwa (wanda a ka sa ni da Idom), kuma waɗannan ne hakimansu.20Waɗannan ne 'ya'ya maza na Seyir Bahorite, mazauna ƙasar: Lotan, Shobal, Zibiyon, Ana,21Dishon, Eza, da Dishan. Waɗannan ne dangogin Horitiyawa, mazauna Seyir a cikin ƙasar Idom.22'Ya'ya maza na Lotan su ne Hori da Heman, kuma Timna 'yar'uwar Lotan ce.23Waɗannan ne 'ya'ya maza na Shobal: Alban, Manahat, Ebal, Shefo, da Onam.24Waɗannan ne 'ya'ya maza na Zibiyon: Aiya da Ana. Wannan Ana shi ne ya gano maɓulɓular ruwa mai zafi a jeji, yayin da yake kiwon jakkan Zibiyon mahaifinsa.25Waɗannan ne 'ya'yan Ana: Dishon da Oholibama, ɗiyar Ana.26Waɗannan ne 'ya'ya maza na Dishon: Hemdan, Eshban, Itran, da Keran.27Waɗannan ne 'ya'ya maza na Eza: Bilhan, Za'aban, da Akan.28Waɗannan ne "ya'ya maza na Dishan: Uz da Aran.29Waɗannan ne dangogin Horitiyawa: Lotan, Shobal, Zibiyon, da Ana,30Dishon, Eza, Dishan: Waɗannan ne dangogin Horitiyawa, bisa ga dangoginsu da aka lissafa a ƙasar Seyir.31Waɗannan ne sarakunan da suka yi mulki a ƙasar Idom kafin wani sarki ya yi mulki a bisa Isra'ilawa:32Bela ɗan Beyor, ya yi mulki a Idom, sunan birninsa kuma Dinhaba ne.33Sa'ad da Bela ya mutu, daga nan Yobab ɗan Zera da Bozra, ya yi mulki a gurbinsa.34Sa'ad da Yobab ya mutu, Husham wanda ke daga ƙasar Temanawa, ya yi mulki a gurbinsa.35Sa'ad da Husham ya mutu, Hadad ɗan Bedad wanda ya ci Midiyanawa da yaƙi a ƙasar Mowab, ya yi mulki a gurbinsa. Sunan birninsa Abit ne.36Sa'ad da Hadad ya mutu, daga nan Samla na Masreka ya yi mulki a gurbinsa.37Sa'ad da Samla ya mutu, daga nan Shawul na Rehobot ta gefen kogi ya yi mulki a gurbinsa.38Sa'ad da Shawul ya mutu, daga nan Ba'al Hanan ɗan Akbor ya yi mulki a gurbinsa.39Sa'ad da Ba'al-hanan ɗan Akbo, ya mutu, daga nan Hadar ya yi mulki a gurbinsa. Sunan birninsa Fawu ne. Sunan matarsa Mehetabel, ɗiyar Matred, jikar Me Zahab.40Waɗannan ne sunayen shugabannin kabilu daga zuriyar Isuwa, bisa ga dangoginsu da lardunansu, bisa ga sunayensu: Timna, Alba, Yetet,41Oholibama, Ela, Finon,42Kenaz, Teman, Mibzar,43Magdiyel, da Iram. Waɗannan ne shugabannin dangogin Idom, bisa ga mazaunansu a cikin ƙasar da suka mallaka. Wannan ne Isuwa, mahaifin Idomawa.
"Waɗannan sune zuriyar Isuwa, wanda ake kira Idom." Wannan ya kawo bayanin zuriyar Isuwa a Farawa 36:1-8. AT: "Wannan labarin zuriyar Isuwa, wanda ake kira Idom."
Waɗannan sunayen matan Isuwa.
"Elon Bahittiye" ko "Elon zuriyar Hittiyawa." Wannan sunan namiji ne. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 26:34.
Wannan sunan maza ne.
Wannan na nufin kungiyar mutane da yawa. Duba yadda aka fassara a Farawa 10:15.
Wannan sunan ɗăya daga cikin matan Isuwa ne. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 26:34.
Wannan sunan ɗaya daga cikin yayan Isma'ila ne. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 28:8.
Waɗannan sunayen matan Isuwa ne. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 36:1
Waɗannan sunayen 'ya'yan maza Isuwa ne.
Wannan na nufin dukkan abubuwan da ya tara lokacin da yake rayuwa a ƙasar Kan'ana. AT: "wanda ya tara lokacin zaman sa a ƙasar Kan'ana"
Wannan na nufin ka tafi wani wuri ka zauna can. AT: "ya tafi cikin wata ƙasa "
"mallakar Isuwa da Yakubu"
ƙasar bata da girma sosai da zata iya daukar dukan dabbobin Isuwa da Yakubu suka mallaka. AT: "ba za ta iya ɗaukar su ba saboda yawan dabbobinsu" ko "bata da girman da zata iya daukar dabbobin Isuwa da Yakubu"
Kalmar "zauna" na nufin matsawa zuwa wani wuri don a rayu a can. AT: "in da suka koma"
Wannan na gabatar da labarin zuriyar Isuwa a Farawa 36: 9-43. AT: "Wannan bayani ne kan zuriyar Isuwa"
Wannan na nufin sun rayu a ƙasar tudu ta Seyir. AT: "waɗanda suka rayu a ƙasar tudu ta Seyir"
Waɗannan sunayen yayan Isuwa ne. Duba yadda aka fassara wadannan sunayen a Farawa 36:4.
Waɗannan sunayen matan Isuwa ne. Duba yadda aka fassara wadannan sunayen a Farawa 36:1.
Waɗannan sunayen 'ya'yan maza Elifaz ne.
Wannan sunan farkar Elifaz ne.
Waɗannan sunayen 'ya'yan maza Isuwa ne. Duba yadda aka fassara wadannan sunayen a Farawa 36:4.
Waɗannan sunayen 'ya'yan maza Ruwel ne.
Waɗannan sunayen maza ne.
Waɗannan sunayen matan Isuwa ne. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 36:1
Wannan sunan ɗan Isuwa ne. Duba yadda aka fassara waɗannan sunayen a Farawa 36:4.
Waɗannan sunayen 'ya'yan maza Elifaz ne.
Wannan sunan ɗaya daga cikin matan Isuwa ne. Duba yadda aka fassara wannan sunan a Farawa 36:1.
Waɗannan sunayen 'ya'yan maza Isuwa ne. Duba yadda aka fassara waɗannan sunayen a Farawa 36:4.
Waɗannan sunayen yayan Ruwel ne. Duba yadda aka fassara waɗannan sunayen a Farawa 36:13
Wannan na nufin sun rayu a ƙasar Idom. AT: "wanda suka rayu a ƙasar Idom"
Waɗannan sunayen matan Isuwa ne. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 36:1
Wannan sunan namiji ne. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 36:1
Kalmar "Seyir" sunan wani mutum ne da wata ƙasa.
Kalmar "Horitiyawa" na nufin wasu kungiyar mutane. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 14:3
"mazauna ƙasar Seyir, wanda ake kira Idom"
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan sunan mace ne.
Waɗannan sunayen maza ne. Duba yadda aka fassara waɗannan sunayen a Farawa 36:20.
Waɗannan sunayen maza ne.
Waɗannan sunayen maza ne. Duba yadda aka fassara waɗannan sunayen a Farawa 36:20.
Wannan sunan mace ne.
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan sunayen wasu kungiyar mutane. Duba yadda aka fassara wannan a Farawa 14:3.
Waɗannan sunayen maza ne. Duba yadda aka fassara waɗannan sunayen a Farawa 36:20-21.
Wannan na nufin sun rayu a ƙasar Seyir. AT: "waɗanda suka rayu a ƙasar Seyir"
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan na nufin wannan birnin ya rayu. AT: "sunan birnin da ya rayu"
Waɗannan sunan wurare ne.
Wannan sunan namiji ne. Duba yadda aka fassara wannan sunan a Farawa 36:31.
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan na nufin Husham ya rayu a ƙasar Temanawa. AT: "Husham wanda ke daga ƙasar Temanawa"
Wannan sunan wurare ne.
"zuriyar Teman"
Wannan na nufin wannan birnin ya rayu. AT: "Wannan sunan birnin da ya rayu ne"
Wannan sunan namiji ne. Duba yadda aka fassara wannan sunan a Farawa 36:34.
Shawul ya rayu a Rehobot. Rehobot na wajen Kogin Yufiretis. AT: "sai Shawul yayi mulki a maimakon sa. Daga Rehobot yake daura da Kogin Yufiretis"
Waɗannan sunayen maza ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Za a iya ƙara bayanin da ya ɓata. AT:"ɗiyar Matred da jikar Me Zahab"
Wannan sunan mace ne.
"shugabannin kabilu"
Aka sanya sunayen kabilan da yankuna bisa ga shugabannin kabilan. AT: "sunayen danginsu da kuma yankunan da suka zauna sunansu. Waɗannan sunayensu ne"
Waɗannan sunayen mutane ne.
"wuraren zaman su" ko "wuraren da suka zauna"
An jera wannan jerin "ya zama" Isuwa, ma'ana wannan shi ne dukka jerin zuriyarsa. AT: "Waɗannan su ne jerin zuriyar Isuwa"
1Yakubu ya zauna ƙasar da mahaifinsa ke zama, a cikin ƙasar Kan'ana.2Waɗannan ne al'amura game da Yakubu. Yosef, wanda ke saurayi ɗan shekaru sha bakwai, yana kiwon tumaki da awaki tare da 'yan'uwansa. Yana tare da 'ya'yan Bilha da 'ya'yan Zilfa, matan mahaifinsa. Yosef yana kawo labarai marasa daɗi game da su wurin mahaifinsu.3Isra'ila dai yana ƙaunar Yosef fiye da dukkan 'ya'yansa maza saboda shi ɗan tsufansa ne. Ya yi masa wata riga mai kyau.4'Yan'uwansa suka ga cewa mahaifinsu na ƙaunarsa fiye da dukkan 'yan'uwansa maza. Suka ƙi jininsa, kuma ba su maganar alheri da shi.5Yosef ya yi wani mafarki, ya kuma gaya wa 'yan'uwansa game da mafarkin. Suka ƙara ƙin jininsa.6Yace masu, "Ina roƙon ku da ku saurari wannan mafarkin da na yi.7Duba, muna ta ɗaurin dammunan hatsi a gona, gashi kuwa, sai damina ya tashi ya kuma tsaya a tsaye, sai kuma, dammunanku suka zo a kewaye suka rusuna wa damina."8'Yan'uwansa suka ce masa, "Lallai zaka yi sarauta a kanmu? Lallai kuwa zaka yi mulki a kanmu?" Suka ƙara ƙin jininsa saboda mafarkansa saboda kuma maganganunsa.9Ya sake yin wani mafarkin ya gaya wa 'yan'uwansa. Yace, "Duba, Na yi wani mafarkin: Rana da wata da taurari sha ɗaya sun rusuna mani."10Ya gaya wa mahaifinsa kamar yadda ya gaya wa 'yan'uwansa, mahaifinsa kuma ya tsauta masa. Yace masa, "Wanne irin mafarki ne ka yi haka? Ko hakika mahaifiyarka da Ni da 'yan'uwanka maza za mu zo mu rusuna ƙasa a gare ka?"11'Yan'uwansa suka yi kishin sa, amma mahaifinsa ya ajiye al'amarin a rai.12'Yan'uwansa suka tafi kiwon dabbobin mahaifinsu a Shekem.13Isra'ila ya cewa Yosef, "Ba 'yan'uwanka na kiwon dabbobin a Shekem ba? Zo, zan kuma aike ka wurin su." Yosef yace masa, "Na shirya."14Yace masa, "Ka tafi yanzu, ka duba ko 'yan'uwanka na lafiya ko dabbobin kuma na lafiya, sai ka kawo mani magana." Sai Yakubu ya aike shi daga Kwarin Hebron, Yosef kuma ya tafi Shekem.15Wani mutum ya sami Yosef. Duba, Yosef yana ta gararanba a saura. Mutumin ya tambaye shi, "Me kake nema?"16Yosef yace, "Ina neman 'yan'uwana ne. Ka gaya mani, ina roƙon ka, inda suke kiwon dabbobin."17Mutumin yace, "Sun bar nan wurin, domin na ji suna cewa, 'Bari mu tafi Dotan."' Yosef ya bi bayan 'yan'uwansa ya kuma same su a Dotan.18Suka hange shi daga nesa, kafin kuma ya iso kusa da su, suka shirya makirci gãba da shi su kashe shi.19'Yan'uwansa suka ce wa junansu, "Duba, mai mafarkin nan yana tafe.20Ku zo yanzu, saboda haka, bari mu kashe shi mu kuma jefa shi cikin ɗaya daga cikin ramukan. Za mu ce, 'Naman jeji ya cinye shi.' Za mu ga abin da zai fãru da mafarkansa."21Ruben ya ji labari, kuma ya ceto shi daga hannunsu. Ya ce, "Kada mu ɗauki ransa."22Ruben yace masu, "Kada ku zubar da jini. Ku jefa shi cikin wannan ramin dake cikin jeji, amma kada ku ɗora hannu a kansa" - domin ya ceto shi daga hannunsu ya maida shi wurin mahaifinsa.23Sai ya kasance da Yosef ya iso wurin 'yan'uwansa, suka tuɓe masa kyakkyawar rigarsa.24Suka ɗauke shi suka jefa shi cikin ramin. Ramin ba komai a ciki babu ma ruwa a ciki.25Suka zauna, su ci abinci. Suka ɗaga idanuwansu suka duba, kuma, duba, zangon Isma'ilawa na tafe daga Giliyad, tare da raƙummansu ɗauke da kayan yaji da man ƙanshi da kayan ƙanshi. Suna tafiya zasu kai su Masar.26Yahuda ya cewa 'yan'uwansa, "Ina ribar da ke ciki idan muka kashe ɗan'uwanmu muka kuma rufe jininsa?27Ku zo, mu sayar da shi ga Isma'ilawa, kada dai mu ɗora hannunmu a kansa. Gama shi ɗan'uwanmu ne, jikinmu." 'Yan'uwansa suka saurare shi.28Midiyawan fatake suna wuce wa. 'Yan'uwan Yosef suka jawo shi, suka fito da shi daga rijiyar. Suka sayar da Yosef ga Isma'ilawa a kan azurfa ashirin. Isma'ilawa suka ɗauki Yosef zuwa cikin Masar.29Ruben ya dawo ga ramin, kuma, duba, Yosef ba shi cikin ramin. Ya yage tufafinsa.30Ya dawo wurin 'yan'uwansa ya ce, "Yaron ba shi a wurin! Ni kuma, ina zan tafi?"31Suka yanka akuya, daga nan kuma suka ɗauki rigar Yosef suka tsoma a cikin jinin.32Sa'an nan suka kawo ta wurin mahaifinsu suka ce, "Mun tsinci wannan. Muna roƙon ka, ka duba ko rigar ɗanka ce ko a'a."33Yakubu ya gane ta ya ce, "Rigar ɗana ce. Naman daji ya cinye shi. Babu shakka an yayyaga Yosef gutsu-gutsu."34Yakubu ya yayyage tufafinsa, ya sanya tsummokara a kwankwasonsa. Ya yi makokin ɗansa kwanaki da yawa.35Dukkan 'ya'yansa maza da 'ya'yansa mata suka tashi domin su ta'azantar da shi, amma ya ƙi ya ta'azantu. Ya ce, "Tabbas zan gangara zuwa Lahira cikin makoki domin ɗana." Mahaifinsa ya yi kuka domin sa.36Midiyawa kuwa suka saida shi a Masar ga Fotifa, wani maƙaddashin Fir'auna, hafsan masu tsaro.
"A cikin ƙasar Kan'ana inda mahaifinsa ya yi zama"
Wannan jumla ta gabatar da labarin 'ya'yan Yakubu a cikin Farawa 37:1-50: 26. Anan "Yakubu" yana nufin duka iyalinsa. AT: "Wannan shi ne lissafin dangin Yakubu"
"shekaru 17"
Wannan sunan baiwar Rahila. Duba yadda zaka fassara wannan sunan a cikin Farawa 29:28.
Wannan sunan baiwar Liya. Duba yadda zaka fassara wannan sunan a cikin Farawa 29:23.
Wannan yana nuna cewa an haifi Yosef okacin da Isra'ila ta kasance dattijo. AT: "wanda aka haife shi lokacin da Isra'ila dattijo"
"Isra'ila sun yi Yosef"
"kyakkyawar tufafi"
"bai iya magana da shi da ladabi ba"
Wannan shi ne taƙaita abubuwan da zasu faru a cikin Farawa 37: 6-11.
"Kuma 'yan'uwan Yosef sun ƙi shi fiye da yadda suka ƙi shi a gabani"
"Ina roƙon ku a saurari wannan mafarkin da na yi"
Yosef ya gaya wa 'yan'uwansa mafarkin sa.
Kalmar "gani" a nan tana faɗakar da mu mu mai da hankali ga bayanin abin mamakin da ya biyo baya.
Kalmar "mu" tana nufin Yosef kuma ya hada da duka 'yan'uwansa.
Lokacin da aka girbe hatsi an ɗaura shi cikin ɓoye kuma a ɗaure shi har sai lokaci ya yi da za a raba hatsi da ciyawar.
Anan guraben alkama suna tsaye suna durƙusa kamar dai mutane ne. Waɗannan kunshin suna wakiltar Yosef da 'yan'uwansa.
Duk waɗannan jumlolin suna nufin abu ɗaya ne. 'Yan'uwan Yosef suna amfani da tambayoyi don yi wa Yosef ba'a. Ana iya rubuta su azaman kalamai. AT: "Ba za ku taɓa kasancewa sarkinmu ba, kuma ba za mu taɓa rusuna muku ba."
"Yosef ya sake yin wani mafarkin"
"taurari 11"
"Isra'ila ta tsawatar masa, yana cewa"
Isra'ila ta yi amfani da tambayoyi don gyara Yosef. Ana iya rubuta wannan azaman kalamai. AT: "Wannan mafarkin da kuka yi ba gaskiya bane. Mahaifiyarku, 'yan'uwanku, kuma ba zan yi sujada a gabanku ba!"
Wannan yana nufin yin fushi saboda wani yayi nasara ko mafi mashahuri.
Wannan yana nufin cewa ya ci gaba da yin tunani game da ma'anar mafarkin Yosef. AT: "ci gaba da tunani game da abin da mafarkin na iya ma'ana"
Isra'ila ta yi amfani da tambaya don fara tattaunawa. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Ya ku 'yan'uwa kuna kiwon garken a Shekem."
A nan ana nuna cewa Isra'ila tana neman Yosef ya shirya kansa don ya tafi ya tafi ya ga 'yan'uwansa. AT: "Shirya"
Ya shirya ya tafi. "A shirye nake in tafi"
"Isra'ila yace wa Yosef"
Isra'ila tana son Yusufu ya dawo ya gaya masa yadda ɗan'uwansa da kuma garkensa suke yi. AT: "zo ka faɗa mini abin da ka gano" ko "ba ni rahoto"
"daga kwarin"
"Wani mutum ya sami Yusufu yana yawo a gona"
"Me ake nema?"
Wannan shi ne sunan wurin da ke nisan kilomita 22 daga Shekem.
"'Yan'uwan Yosef sun gan shi tun yana nesa"
"sun yi shirin kashe shi"
"ga wanda yazo da mafarkin"
Waɗannan kalmomin sun nuna cewa ’yan’uwa sun bi abin da aka tsara. AT: "Yanzu a yanzu"
"dabba mai haɗari" ko "dabba mai tsoron"
to da gaske sun ci
'Yan’uwansa sun yi niyyar kashe shi, don haka ba abin mamaki ba ne su faɗi mafarkinsa na zuwa, tunda zai mutu. AT: "Ta hakan za mu tabbatar da cewa mafarkansa bai cika ba"
"jin abin da suke cewa"
Kalmomin "hannayensu" yana nufin 'yan'uwa "" shirin kashe shi. AT: "daga gare su" ko "daga shirye-shiryensu"
Kalmomin "ɗauki ransa" magana ce ta kisan wani. AT: "Kada mu kashe Yosef"
"zubar da jini" tsoka ne don kisan wani. AT: "Kada a zub da jini" ko "Kada ku kashe shi"
Ana iya fassara wannan azaman sabon jumla: "Ruben ya faɗi wannan don ya ceci Yosef"
"mayar masa"
Wannan kalmar ana amfani da ita anan don nuna alama mai mahimmanci a cikin labarin. Idan harshenku yana da hanyar yin wannan, zaku iya tunanin amfani da shi anan.
"suka yaye masa kyakkyawar rigarsa"
"kyakkyawa tufafi." Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Farawa 37:3.
"Gurasa" yana wakiltar abinci gaba ɗaya. AT: "Sun zauna su ci abinci" ko "'Yan'uwan Yosef sun zauna su ci"
Anan ana maganar sama sama kamar wanda mutum ya ɗaga idanunsa a zahiri. Hakanan, kalmar "duba" ana amfani da ita anan don jawo hankalin mai karatu game da abin da mazan suka gani. AT: "Da suka ɗaga kai sai suka ga vanyari"
"Kawo da su Masar." Ana iya yin wannan dalla-dalla. AT: "kawo su Masar don sayar da su"
Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Ba mu cin riba ta hanyar kashe ɗan'uwanmu da rufe jininsa"
Wannan karin magane ne na nufin kan ɓoye mutuwar Yosef. AT: "ɓoye kisan sa"
"ga waɗannan mutanen zuriyar Isma'il"
Wannan yana nufin kada a cutar da shi ko cutar da shi. AT: "kada ku cuce shi"
Kalmar “jikin” wata ce da ke nuni ga dangi. AT: "shi danginmu ne na jini"
"'Yan'uwan Yahuda sun saurare shi" ko kuma "' yan'uwan Yahuda sun yarda da shi"
Duk sunayen biyu suna nuni da kungiyar yan kasuwar da 'yan'uwan Yosef suka hadu da su.
"akan farashin azurfa 20"
"ya tafi da Yosef zuwa Masar"
"Sai Ruben ya koma wurin ramin, ya yi mamakin ganin Yosef bai nan." Kalmar "duba" a nan ta nuna cewa Ruben ya yi mamakin gano Yosef ya tafi.
Wannan aiki ne na baƙin ciki da makoki. Ana iya rubuta wannan a sarari. AT: "Ya yi baƙin ciki har ya kyakketa tufafinsa"
Ruben ya yi amfani da tambayoyi don ƙarfafa matsalar da Yosef ya ɓace. Ana iya rubuta waɗannan azaman kalamai. AT: "Yaron ya tafi! Ba zan iya komawa gida yanzu!"
Wannan yana nufin kyakkyawar tufar da mahaifinsa yayi masa.
"jinin akuya"
"sun kawo rigar"
"aika ci shi"
Yakubu yana tunanin cewa dabbar daji ta tsinke jikin Yosef. AT: "Haƙiƙa ya tsage Yosef"
Wannan aiki ne na baƙin ciki da makoki. Ana iya rubuta wannan a sarari. AT: "Yakubu ya yi baƙin ciki har da ya kyakketa tufafinsa"
Anan "tsummoki" yana nufin tsakiyar sashin jiki ko kugu. AT: "saka tsummoki"
A nan ana maganar 'ya' ya zuwa ga mahaifinsu a matsayin "tashi." AT: "ya zo wurinsa"
Wannan nuna cewa zai sa ya kasance yana baƙin ciki tun daga yanzu har zuwa lokacin da ya mutu. AT: "Tabbas idan na mutu har zuwa ganina zuwa lahira zan kasance cikin makoki"
"Midiyanawa sun sayar da Yosef"
"shugaban sojojin da suka tsare sarki"
1Sai ya kasance a wannan lokaci Yahuda ya bar 'yan'uwansa ya je ya zauna da wani Ba'addulmiye, mai suna Hira.2Ya haɗu da wa ta ɗiyar wani mutum Bakananiye mai suna Shuwa. Ya aure ta ya kuma kwana da ita.3Ta ɗauki ciki ta sami ɗa, a ka sa masa suna Er.4Ta sake ɗaukar ciki ta sami ɗa. Ta kira sunansa Onan.5Ta sake samun wani ɗan ta kira sunansa Shela. A Kezib ne wurin da ta haife shi.6Yahuda ya samar wa Er mata, ɗan fãrinsa. Sunanta Tama ne.7Er, ɗan fãrin Yahuda, mugu ne a idanun Yahweh. Yahweh ya kashe shi.8Yahuda ya cewa Onan, "Ka kwana da matar ɗan'uwanka. Ka yi aikin ɗan'uwan miji a gare ta, ka samar wa ɗan'uwanka ɗa."9Onan ya san cewa ɗan ba zai zama na shi ba. Duk lokacin da ya kwana da matar ɗan'uwansa, sai ya zubar da maniyin a ƙasa domin kada ya samar wa ɗan'uwansa ɗa.10Abin nan da ya yi kuwa mugunta ce a idanun Yahweh. Yahweh ya kashe shi shima.11Daga nan Yahuda ya cewa Tama, surukarsa, "Ki yi zaman gwauruwa a gidan mahaifinki har sai Shela, ɗana, ya girma." Gama ya ji tsoro, "Shi ma wataƙila ya mutu, kamar 'yan'uwansa." Tama ta tashi ta kuma koma da zama gidan mahaifinta.12Bayan lokaci mai tsawo, ɗiyar Shuwa, matar Yahuda, ta mutu. Yahuda ya ta'azantu ya kuma tafi wurin sausayar tumakinsa a Timna, shi da abokinsa Hira Ba'addulmiye.13Aka gaya wa Tama, "Duba, surukinki zai tafi Timna domin sausayar tumakinsa."14Sai ta tuɓe tufafin gwaurancinta ta rufe kanta da gyale ta kuma lulluɓe jikinta. Ta zauna a ƙofar Enayim, wadda ke kan hanyar zuwa Timna. Domin ta ga Shela ya girma, amma ba a bayar da ita ba a gare shi a matsayin mata.15Sa'ad da Yahuda ya ganta ya zaci cewa karuwa ce saboda ta lulluɓe fuskarta.16Ya je wurin ta a bakin hanya ya kuma ce, "Zo, ina roƙon ki bari in kwana da ke" - domin bai san cewa surukarsa ba ce - sai kuma ta ce, "Mezaka bani domin ka kwana da ni?"17Ya ce, "Zan aiko maki da 'yar akuya daga garke." Ta ce, "Zaka bani diyya har sai ka aiko da ita?"18Ya ce, "Wacce irin diyya zan ba ki?" Ta maida amsa, "Zoben hatiminka da ɗamararka, da sandar dake a hannunka." Ya bayar dasu a gare ta ya kuma kwana da ita, sai ta sami ciki daga gare shi.19Ta tashi ta yi tafiyarta. Ta tuɓe lulluɓinta ta sanya tufafin gwaurancinta.20Yahuda ya aika da 'yar akuyar ta hannun abokinsa Ba'addulmiye saboda ya karɓo diyyar daga hannun matar, amma bai same ta ba.21Sai Ba'addulmiyen ya tambayi mutanen dake wurin, "Ina karuwar asiri dake zaune a Enayim a bakin hanya?" Suka ce, "Babu wata karuwar asiri dake zaune a nan."22Ya dawo wurin Yahuda yace, "Ban same ta ba. Kuma, mutanen wurin sun ce, 'Babu wata karuwar asiri dake zaune a nan."'23Yahuda yace, "Bari ta ajiye abubuwan, domin kada mu sha kunya. Tabbas, na aika da 'yar akuyar nan, amma ba ka same ta ba."24Sai ya kasance bayan wajen wata uku, sai a ka gaya wa Yahuda, "Tama surukarka ta aikata karuwanci, kuma tabbas, ta sami ciki ta haka." Yahuda yace, "Ku kawo ta nan bari a ƙona ta kuma."25Sa'ad da aka fito da ita, sai ta aika wa surukinta da saƙo, "Ta wurin mutumin dake da waɗannan nake da ciki." Ta ce, "Ina roƙon ka da ka gano mani waɗannan na waye, zoben tambarin da ɗamarar da sandar."26Yahuda ya gane su ya kuma ce, "Ta fi ni adalci, tunda ban bayar da ita ba a matsayin mata ga Shela, ɗana." Bai sake kwana da ita ba kuma.27Sai ya kasance da lokacin haihuwarta ya kai, duba, tagwaye ne ke cikin mahaifarta.28Sai ya kasance a lokacin da take haihuwar ɗaya ya fito da hannunsa waje, unguwar zomar ta ɗauki jan zare ta ɗaura masa a hannu ta kuma ce, "Wannan ne ya fãra fitowa."29Amma daga nan sai ya maida hannunsa, kuma, duba, sai ɗan'uwansa ya fito farko. Unguwar zomar ta ce, "Ya ya ka faso waje!" Sai aka sa masa suna Ferez.30Daga nan ɗan'uwansa ya fito, wanda yake da jan zare a hannu, aka kuma sa masa suna Zera.
Wannan yana gabatar da sabon sashi na labarin wanda ya mayar da hankali kan Yahuda.
Hirah sunan wani mutum ne da ya rayu a ƙauyen Adullam.
Shuwa wata Bakan'aniya ce, ta auri Yahuda.
Wannan wata cuta ce. AT: "ya yi jima'i da ita"
"Matar Yahuda ta yi ciki"
Ana iya rubuta wannan cikin tsari mai aiki. AT: "Mahaifinsa ya sa masa suna Er"
Waɗannan sunayen 'ya'ya maza na Yahuda.
Wannan shi ne sunan wurin.
Kalmomin "a idahun" yana nufin Yahweh yana ganin muguntar Er. AT: "mugu ne ga Yahweh kuma ya gan shi"
Yahweh ya kashe shi saboda muguntarsa. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Don haka Yahweh ya kashe shi"
Wannan wata cuta ce. AT: "Ku yi jima'i da matar ɗan'uwanku"
Wannan yana nufin al'ada ce wacce idan 'yan' uwan ya mutu kafin shi da matarsa su haifi ɗa, 'yan'uwan na gaba zai yi aure ya yi jima'i da bazawara. Lokacin da gwauruwa ta haifi ɗa na fari, ana ɗaukar wannan ɗa ɗan ɗan farin kuma zai sami gādon ɗan'uwan na farko.
Kalmomin "a idanun" yana nufin Yahweh yana ganin mugunta ne Onan.AT: "mugunta ce kuma Yahweh ya gani"
Yahweh ya kashe shi saboda abin da ya yi. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Don haka Yahweh ya kashe shi"
"matar tsohon ɗansa"
Wannan yana nufin ta zauna a gidan mahaifin nan. AT: "kuma ka zauna a gidan mahaifinka"
Yahuda ya yi niyyar Tamar ya auri Shela idan ya girma. AT: "kuma idan yayana, Shela ya girma, zai iya aurenta"
Yahuda ya ji tsoron cewa idan Shela ta auri Tamar ma zai mutu kamar yadda 'yan'uwansa suka yi. AT: "Gama ya ji tsoro," fIdan ya aure ta to shi ma yana iya mutuwa kamar yadda 'yan'uwansa suka yi "
"A lokacin da Yahuza ba baƙin ciki, ya"
"Timna, inda mutanensa suke kiwon tumaki"
Waɗannan sunayen wurare ne.
"Abokin Hira, daga Adullam, ya tafi tare da shi"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Wani ya gaya wa Tamar"
"mahaifin mijinki"
wani siririn kayan wanda aka yi amfani dashi domin rufe mate kai da fuska
Wannan yana nuna cewa ta ɓoye kanta da suturarta don kada mutane su gane ta. A bisa ga al'ada, wani ɓangare na suturar mata manyan kayayyaki ne da suke manne da su. AT: "ta lulluɓe kanta a jikin rigarta don kada mutane su gane ta"
"matan da mazansu suka mutu"
"a kan hanya"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Yahuda bai ba ta a ƙwace Shela ba"
Kalmar “ganta” anan tana nufin Tamar, amma mai karatu yakamata ka fahimci cewa Yahuda bai san macen da yake nema Tamar ba ce.
Yahuda ba ta tunanin karuwa ce kawai saboda fuskarta rufe amma kuma domin tana zaune a ƙofar. AT: "saboda ta rufe kanta kuma ta zauna inda karuwai ke zaune sau da yawa"
Tamar kuwa tana zaune a bakin hanya. AT: "Ya tafi inda ta ke zaune a bakin hanya"
"zo da ni"
"daga garken awaki"
“Hatiminka” yana kamar da tsabar kuɗin da aka zana akan sa, wanda aka yi amfani da shi don narkar da kakin zuma. An sanya "igiyar" ta cikin hatimi na yadda mai shi ya iya sa shi a wuyan wuyansa. Ma'aikaci dogon katako ne wanda ya taimaka wajen tafiya akan kasa mai tsauri.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "mayar da jingina"
Anan "hannun" yana jaddada cewa sun kasance a nan mallaka. Hannun matar tana nufin matar. AT: "daga matar"
"wasu mutanen da suka rayu a can"
"karuwai wanda yake aiki a haikali"
Da mutane suka ga abin da ya faru, za su yi wa Yahuda ba'a da dariya. Ana iya bayyana wannan a bayyane kuma a bayyane a cikin aiki mai aiki. AT: "in ba haka ba mutane za su yi mana dariya idan sun gano abin da ya faru"
Ana amfani da wannan kalmar anan don nuna alamar sabon ɓangaren labarin.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "wani ya fada wa Yahuda"
Anan kalmar "haka" tana nufin "karuwanci" da ta aikata. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "ya sanya ta yi ciki" ko "tana da ciki"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Zamu ƙone ta har ya mutu"
Wannan wata cuta ce. AT: "ba ta sake yin jima'i da ita ba"
Kalmar "dubai" tana faɗakar da mu abin mamakin cewa Tamar tana ɗauke da tagwaye, waɗanda ba a sani ba a baya.
"ɗaya daga cikin jariran ya fitar da hannunsa"
"a kusa da wuyan hannursa"
Wannan ya nuna mamakin ungozoma ta ga jariri na biyu ya fito da farko. AT: "Don haka wannan shine yadda kuka fara fitar da hanyarku da farko!" ko "Kun riga kun farko!"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "ta raɗa masa suna"
Wannan sunan ɗan yaro. Masu fassara na iya ƙara ɗan littafin rubutu wanda ke cewa: "Sunan Ferez yana nufin "watse daga."
Wannan sunan ɗan yaro. Masu fassara na iya ƙara ɗan littafin rubutu wanda ke cewa: "Sunan Zera yana nufin "ja mai haske. "
1Aka kawo Yosef zuwa Masar. Fotifa, maƙaddashin Fir'auna kuma hafsan masu tsaro kuma Bamasare, ya sawo shi daga Isma'ilawa, waɗanda suka kawo shi nan.2Yahweh yana tare da Yosef ya kuma zama wadataccen mutum. Yana zaune cikin gidan ubangidansa Bamasare.3Ubangidansa ya ga cewa Yahweh na tare da shi kuma Yahweh na wadata kowanne abu da ya yi.4Yosef ya sami tagomashi a idanunsa. Ya bautawa Fotifa. Fotifa ya maida Yosef shugaban gidansa, da kowanne abu da ya mallaka, ya sanya ƙarƙashin lurarsa.5Sai ya kasance tun lokacin da ya maida shi shugaba bisa gidansa da bisa kowanne abu da ya mallaka, sai Yahweh ya albarkaci gidan Bamasaren saboda Yosef. Albarkar Yahweh tana bisa kowanne abu da Fotifa yake da shi a cikin gida da gona.6Fotifa ya sanya kowanne abu da yake da shi a ƙarƙashin lurar Yosef. Ba ya buƙatar ya yi tunani game da komai sai dai kawai abincin da zai ci. Shi dai Yosef kyakkyawa ne gwanin sha'awa kuma.7Sai ya kasance bayan wannan matar ubangidansa ta yi sha'awar Yosef. Ta ce, "Ka kwana da ni."8Amma ya ƙi, ya kuma ce wa matar ubangidansa, "Duba, ubangidana ba ya kulawa da abin da nake yi a cikin gidan nan, kuma ya sanya kowanne abu da yake da shi a ƙarƙashin lura ta.9Babu wanda ya fi ni girma a cikin gidan nan. Bai hana mani komai ba sai dai ke, saboda ke matarsa ce. Ta yaya daga nan zan yi wannan irin babbar mugunta da zunubi gãba da Allah?"10Ta dinga magana da Yosef rana bayan rana, amma ya ƙi ya kwana da ita ko ya kasance tare da ita.11Sai ya kasance wata rana, Yosef ya shiga cikin gidan domin ya yi aikinsa. Babu ko ɗaya daga cikin mutanen gidan dake cikin gidan.12Ta kama shi ta tufafinsa ta ce kuma, "Ka kwana da ni." Ya bar tufafinsa a hannunta, ya tsere, ya fita waje kuma.13Sai ya kasance, sa'ad da taga cewa ya bar tufafinsa a cikin hannunta ya kuma tsere waje,14sai ta kira mutanen gidanta ta ce masu, "Duba, Fotifa ya kawo Ba'ibraniye ya wulaƙanta mu. Ya shigo wurina ya kwana da ni, na kuwa yi ihu.15Sai ya kasance sa'ad da ya ji ina ihu, sai ya bar tufafinsa tare da ni, ya tsere, ya kuma fita waje."16Ta ajiye tufafinsa a kusa da ita har sai da ubangidansa ya zo gida.17Ta faɗi masa wannan bayyani, "Ba'ibraniyen nan bawa wanda ka kawo mana, ya shigo domin ya wulaƙanta ni.18Sai ya kasance sa'ad da nayi ihu, ya bar tufafinsa tare da ni ya kuma tsere waje."19Sai ya kasance, sa'ad da ya ji bayanin da matarsa ta faɗi masa, "Wannan ne abin da bawanka ya yi mani," sai ya fusata sosai.20Ubangidan Yosef ya ɗauke shi ya saka shi cikin kurkuku, wurin da a ke tsaron 'yan kurkukun sarki. Ya na nan a cikin kurkukun.21Amma Yahweh na tare da Yosef ya kuma nuna alƙawarin aminci a gare shi. Ya kuma ba shi tagomashi a idanun shugaban kurkukun.22Shugaban kurkukun ya bayar da dukkan 'yan kurkukun dake cikin kurkukun cikin hannun Yosef. Duk abin da suka yi a nan, Yosef ne ke shugabancin sa.23Shugaban kurkuku ba ya kulawa da kowanne abu dake cikin hannunsa, saboda Yahweh na tare da shi. Duk abin da ya yi Yahweh na wadatar da shi.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Isma'ilawa sun tafi da Yosef zuwa Masar"
Wannan ya nuna cewa Yahweh ya taimaki Yosef kuma ya kasance tare da shi koyaushe. AT: "Yahweh ya jagoranci Yusufu kuma ya taimaka masa"
Anan marubucin yayi magana akan aiki a gidan maigidan kamar yana zaune a gidan maigidan. Manyan amintattun bayin kawai ne aka basu izinin yin aiki a gidan maigidan nasu. AT: "ya yi aiki a gidan"
Yosef bawan Fotifa ne.
Wannan yana nufin cewa maigidan ya ga yadda Yahweh yake taimakon Yosef. AT: "Maigidansa ya ga cewa Yahweh yana taimakonsa"
"Yahweh ya sa duk abin da Yosef ya yi nasara"
"Sami tagomashi" yana nufin amincewa da wani. Magana “a gabansa” tana nufin hukuncin mutum ne. Ma’anar mai yiwuwa su ne 1) AT: “Fotifa ya gamsu da Yosef” ko 2) AT: “Yahweh ya gamsuda Yosef”
Wannan yana nuna cewa shi bawan Fotifa ne.
"Fotifa ya naɗa Yosef a gidansa, da duk abin da yake na Fotifa"
Lokacin da aka “sanya wani abu a karkashin kulawar wani,” hakan na nuna cewa mutumin yana da alhakin kulawarsa da kuma amintaccen tsaro. AT: "ya kasance yana kula da Yosef"
Wataƙila kuna buƙatar amfani da kalmomin "Yosef" da "Bamasaren" kafin amfani da kalmar sihiri don magana a kansu. AT: "Bamasaren" ya naɗa Yosef mai lura da gidansa da dukan abin da ya mallaka. Daga lokacin da Yahweh ya sa wa gidan Bamasaren albarka saboda Yusufu.
Wannan yana nufin gidansa da amfanin gonakinsa da dabbobinsa. Ana iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayanin a bayyane. AT: "Gidan Fotifa da dukkan amfanin gonakinsa da dabbobinsa"
Lokacin da aka “sanya wani abu a karkashin kulawar wani,” hakan na nuna cewa mutumin yana da alhakin kulawarsa da kuma amintaccen tsaro. AT: "Don haka Fotifa ya sa Yosef ya lura da duk abin da yake da shi"
Za a iya wannan azaman sanarwa tabbatacce. AT: "Fotifa ne kawai ya yi tunani game da abin da yake son ci"
Dukkan kalmomin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. Sun yi magana a kan kyawawan halayen Yosef. Wataƙila kyakkyawa ne kuma mai ƙarfi. AT: "kyakkyawa ce kuma mai ƙarfi"
"Sai mai." Ana amfani da wannan kalmar anan don alamar sabon abin da ya faru.
Wannan wata karin magana ne. AT: "ku yi jima'i da ni"
"maigidana bai kula da gidansa ba." Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa tabbatacce. AT: "maigidana ya amince da ni tare da iyalinsa"
Lokacin da aka “sanya wani abu a karkashin kulawar wani,” hakan na nuna cewa mutumin yana da alhakin kulawarsa da kuma amintaccen tsaro. AT: "shi ne ya ɗora ni a kan duk abin da ke nasa" (Duba: metaphor)
Za a iya wannan azaman sanarwa tabbatacce. AT: "Ya ba ni komai in banda ku"
Yosef yayi amfani da tambaya don girmamawa. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Tabbas ba zan iya yin irin wannan mugunta ba kuma nayi zunubi ga Allah."
Wannan yana nuna cewa ta ci gaba da roƙonsa ya kwana da ita. Ana iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayanin a bayyane. AT: "Ta ci gaba da roƙon Yosef ya kwana da ita"
"Babu wani daga cikin sauran mutanen da suka yi aiki a gidan"
"da sauri ya fita waje" ko "da sauri ya fice daga gidan"
Anan matar Fotifa tana zargin Yosef da kokarin kama ta kuma ta yi zina da ita. AT: "Ya zo cikin dakina domin yin lalata da ni"
"Lokacin da ya ji ni na yi kururuwa, sai ya." An yi amfani da kalmar "ya kasance" a nan don yiwa alama ta gaba a cikin labarin.
"Maigidan Yosef." Wannan yana nufin Fotifa.
"Ta bayyana hakan kamar haka"
Kalmar "mu" tana nufin Fotifa, matarsa, kuma ya haɗa da sauran mutanen gidan.
"ya ji matarsa tana yi masa bayani." Kalmar "nasa" da "shi" a nan na nufin Fotifa.
"Fotifa ya yi fushi sosai"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "wurin da sarki ya sa fursunonin sa"
"Yosef ya sauka a wurin"
Wannan ya nuna yadda Yahweh ya kula da Yosef kuma ya kyautata masa. AT: “Amma Yahweh ya yi wa Yosef alheri” ko “Amma Yahweh ya kula da Yosef”
Ana nuna kalmar 'amincin' a matsayin "mai aminci" ko "da aminci". AT: "ya kasance mai aminci ga alƙawarin da ya yi da shi" ko "ya ƙaunace shi da aminci"
Wannan yana nufin Yahweh ya sa mai kula da kurkukun ya amince da Yosef kuma ya kula da shi da kyau. AT: "Yahweh ya sa mai kula da kurkukun ya yi farin ciki da Yosef"
"manajan kurkukun" ko "mutumin da ke kula da kurkukun"
Anan "hannun" yana wakiltar ikon Yosef ko amintacce. AT: "ka sa Yosef a madadin" (Duba:
"Yosef shi ne mai lura da abin da suka aikata a wurin"
Wannan ya nuna yadda Yahweh ya taimaki Yosef ya kuma bishe shi. AT: "saboda Yahweh ya jagoranci Yosef"
"Yahweh ya sa duk abin da Yosef ya yi nasara"
1Sai ya kasance bayan waɗannan abubuwa, mai riƙon ƙoƙon sha na sarkin Masar da mai toye-toye na sarki suka ɓata wa ubangidansu, sarkin Masar rai.2Fir'auna ya ji haushin ofisoshinsa biyu, da shugaban ma su riƙon ƙoƙon sha da shugaban masu toye-toye.3Ya sa aka tsare su a cikin gidan shugaban masu tsaro, a cikin wannan kurkuku inda aka tsare Yosef.4Shugaban masu tsaron ya miƙa Yosef a gare su, ya kuma yi masu hidima. Suka ci gaba a tsare na wani lokaci.5Dukkan su biyu sai suka yi wani mafarki - mai riƙon ƙoƙon sha da mai toye-toye na sarkin Masar waɗanda ke tsare a kurkukun - kowanne mutum ya yi nasa mafarki a dare ɗaya, kuma kowanne mafarkin da tasa fassarar.6Yosef ya zo wurin su da safe ya kuma gan su. Duba, suna cikin baƙinciki.7Ya tambayi ofisoshin Fir'auna waɗanda ke tare da shi a tsare a cikin gidan ubangidansa, ya ce, "Meyasa kuke baƙinciki a yau?"8Suka ce masa, "Dukkan mu biyu munyi wani mafarki kuma babu wanda ya iya fassara su." Yosef yace masu, "Fassarori ba ta Allah ba ce?" Ku faɗa mani, ina roƙon ku."9Shugaban masu riƙon ƙoƙon sha ya gaya wa Yosef mafarkinsa. Ya ce masa, "A cikin mafarkina, duba, itacen inabi na gabana.10A itacen inabin akwai rassa uku. Suka tsiro, suka yaɗu da 'ya'ya nan da nan inabin kuma suka nuna.11Ƙoƙon Fir'auna yana hannuna. Na ɗauki 'ya'yan inabin na matse su cikin ƙoƙon Fir'auna, sai kuma na miƙa ƙoƙon cikin hannun Fir'auna."12Yosef yace masa, "Wannan ce fassarar sa. Rassan uku kwanaki uku ne.13A cikin kwanaki uku Fir'auna zai ɗaga kanka ya kuma mai da kai wurin aikinka. Za ka sanya ƙoƙon Fir'auna cikin hannunsa, kamar dai sa'ad da kake mai riƙon ƙoƙon shansa.14Amma ka tuna da ni sa'ad da komai ya tafi lafiya da kai, ina roƙon ka kuma ka nuna mani alheri. Ka ambace ni wurin Fir'auna a fito da ni daga wannan kurkuku.15Domin tabbas an sato ni ne daga ƙasar Ibraniyawa. A nan kuma banyi wani abu ba da zai sanya su su sani cikin wannan rami ba."16Sa'ad da shugaban masu toye-toye ya ga cewa fassarar ta yi daɗi, ya cewa Yosef, "Ni ma nayi mafarki, kuma, duba, kwanduna uku na gurasa suna bisa kaina.17A cikin kwandon na sama akwai kowanne irin kayan toye-toye domin Fir'auna, amma tsuntsaye suka cinye su daga cikin kwandon a bisa kaina."18Yosef ya amsa ya ce, "Wannan ce fassarar sa. Kwandunan uku kwanaki uku ne.19A cikin kwanaki uku Fir'auna zai ɗaga kanka daga gare ka zai kuma sarƙafe ka bisa itace. Tsuntsaye kuma zasu cinye namanka daga gare ka."20Sai ya kasance a rana ta uku ranar tunawa da haihuwar Fir'auna ce. Sai ya yi wa dukkan bayinsa biki. Sai ya ɗaga kan shugaban masu riƙon ƙoƙon sha da shugaban masu toye-toye, daga cikin bayinsa.21Ya maido da shugaban masu riƙon ƙoƙon sha ga hidimarsa, ya kuma sake sanya ƙoƙon cikin hannun Fir'auna.22Amma ya sargafe shugaban masu toye-toye, kamar yadda Yosef ya yi masu fassara.23Duk da haka shugaban masu riƙon ƙoƙon shan bai tuna da Yosef ba, amma ya manta da shi.
Wannan shi ne mutumin da ya kawo wa sarki sha.
Wannan shi ne mutumin da ya ba sarki abinci.
"haushi da maigidan nasu"
"babban shugaban shayarwa da shugaban masu tuya"
"Ya saka su a kurkukun da ke cikin gidan wanda ke nan da shugaban rundunonin tsaro"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "A wannan kurkuku ne Yosef ya kasance" ko "Wannan gidan yarin ne Fotifa ya sa Yosef a ciki"
"Sun daure a kurkuku na dogon lokaci"
"Yosef ya zo wurin masu shayarwa da mai tuya"
Kalmar "duba" a nan ta nuna cewa abin da Yosef ya yi ya ba shi mamaki. AT: "Ya yi mamakin ganin sun yi baƙin ciki"
Wannan yana nufin mai shayarwa ne da mai yin gasa.
"A cikin kurkuku a gidan maigidan." "Maigidansa" yana nufin maigidan Yosef, shugaban masu tsaro.
Yosef yayi amfani da tambaya don girmamawa. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Fassara na Allah ne!" ko "Allah ne zai iya ba da ma'anar mafarkai!"
Yosef ya nemi su gaya masa mafarkinsu. AT: "Ku faɗa mini mafarkan, don Allah"
Mafi mahimmanci mutumin da ya kawo abin sha ga sarki. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Farawa 40: 2.
"A mafarkina, na ga itacen inabi a gabana!" Mai shayarwa ya yi amfani da kalma “duba” a nan don nuna cewa abin da ya gani ya yi mamakin abin da ya gani a mafarkinsa kuma ya faɗakar da Yosef ya mai da hankali.
"gunguran reshensu sun zama 'ya'yan inabi."
Wannan yana nuna cewa ya matso ruwan a cikin su. AT: "matsi ruwan 'ya'yansu daga gare su"
"Ga abinda mafarkin ke nufi"
"Rassan ukun suna wakiltar kwana uku"
"Cikin kwana ukun"
Anan Yosef yayi maganar Fir'auna ya saki mai shayarwa daga kurkuku kamar dai Fir’auna yake sa shi ya ɗaga kansa kai. AT: "zai sake ku daga kurkuku"
"zai dawo maka da aikin ka"
"kamar yadda kayi lokacin da"
"ina roƙon ka ka tausaya min"
Yosef yana nufin mai shayarwar ya gaya wa Fir'auna game da shi domin Fir'auna zai sake shi daga kurkuku. AT: "Ka taimake ni ka fita daga wannan gidan kurkuku ta hanyar gaya wa Fir'auna game da ni"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Lallai mutane sun ɗauke ni" ko "Tabbas mutanen Isma'il sun ɗauke ni"
"ƙasar da Ibraniyawa suke zama"
"kuma a lokacin da nake nan a Masar, ban aikata wani abin da ya cancanci a saka ni kurkuku ba"
Wannan yana nufin jagoran da ya kawo abinci ga sarki. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Farawa 40: 2.
"Na kuma yi mafarki, a cikin mafarkina"
"kwanduna uku na abinci a kaina!" Mai shayarwa ya yi amfani da kalmar "gani" a nan don nuna cewa abin da ya gani ya yi mamakin abin da ya gani a cikin mafarkinsa kuma ya faɗakar da Yosef ya mai da hankali.
"Ga abinda mafarkin ke nufi"
"Kwandunan uku suna wakiltar kwana uku"
Yosef ya kuma yi amfani da kalmar “za ta ɗaga kan ku” lokacin da ya yi magana da mai shayarwa a cikin Farawa 40:12. Anan yana da ma'ana daban. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) "za su ɗaga kanka sama don saka igiya a wuyan wuyanka" ko 2) "zai ɗaga kanka sama don yanke shi."
Anan "nama" a zahiri yana nufin ƙwayar laushi a jikin mutum.
"Bayan haka, a rana ta uku." An yi amfani da kalmar "ya kasance" a nan don alamar wani sabon abin aukuwa a labarin.
"Yana da liyafa"
"Hakkin shugaban masu shayarwa" yana nufin aikinsa na shugaban masu shaye-shaye ne. AT: "Ya bai wa shugaban masu shayarwa aikin sa"
AT: "Amma ya ba da umarnin a rataye shugaban masu toye-toye" ko kuma "Amma ya umarci masu tsaronsa su rataye shugaban masu toye-toye"
Wannan yana nufin lokacin da Yosef ya fassara mafarkinsu. AT: "kamar yadda Yosef ya faɗi cewa zai faru lokacin da ya fassara mafarkan mutanen biyu"
1Sai ya kasance bayan shekaru biyu cur Fir'auna ya yi wani mafarki. Duba, yana tsaye bakin Nilu.2Duba, sai ga wasu shanu bakwai sun fito daga Nilu, masu ban sha'awa da ƙiba, suna kuma kiwo a cikin iwa.3Duba, ga wasu shanun bakwai sun fito bayan su daga cikin Nilu, marasa ban sha'awa ramammu kuma. Suka tsaya gefen waɗancan shanun a bakin kogin.4Daga nan shanun marasa ban sha'awa ramammu kuma suka cinye shanun masu ban sha'awa da ƙiba. Daga nan Fir'auna ya farka.5Daga nan kuma ya sake yin barci ya kuma sake yin mafarki karo na biyu. Duba, kawunan hatsi bakwai sun fito bisa kara ɗaya, cikakku masu kyau kuma.6Gashi, kawuna bakwai, ƙanana waɗanda kuma iskar gabas ke kakkaɓewa, suka fito bayan su.7Ƙananan kawunan suka haɗiye kawunan cikakku masu kyau kuma. Fir'auna ya farka, kuma, duba, ashe mafarki ne.8Sai ya kasance da safe ruhunsa ya damu. Ya aika aka kira dukkan 'yan dabo da masu hikima na Masar. Fir'auna ya gaya masu mafarkansa, amma babu wani da ya iya fassara su ga Fir'auna.9Daga nan shugaban masu riƙon ƙoƙon sha ya ce wa Fir'auna, "A yau ina tunani game da laifuffukana.10Fir'auna ya yi fushi da bayinsa, ya kuma sanya ni cikin tsaro a cikin gidan shugaban masu tsaro, shugaban masu tuya tare da ni.11Muka yi mafarki a cikin dare ɗaya, shi da ni. Muka yi mafarki kowanne mutum bisa ga fassarar mafarkinsa.12Tare da mu a can akwai wani saurayin mutum Ba'ibraniye, bawan shugaban masu tsaro. Muka faɗi masa kuma ya fassara mana mafarkanmu. Ya fassara wa kowannen mu bisa ga mafarkinsa.13Sai ya kasance kamar yadda ya fassara mana, haka ya faru. Fir'auna ya maido ni bisa aikina, amma ɗayan ya sarƙafe shi."14Daga nan Fir'auna ya aika aka kuma kirawo Yosef. Nan da nan suka fito da shi daga ramin. Ya kuma yi aski, ya canza sutura, ya kuma fito zuwa wurin Fir'auna.15Fir'auna ya cewa Yosef, "Na yi mafarki, amma babu mai fassara. Amma na ji labarinka, cewa idan ka ji mafarki kana iya fassara shi."16Yosef ya amsawa Fir'auna, cewa, "Ba ni ba ne. Allah zai amsawa Fir'auna da tagomashi."17Fir'auna ya yi magana da Yosef, "A cikin mafarkina, duba, ina tsaye a bakin Nilu.18Gashi, shanu bakwai suka fito daga cikin Nilu, masu ƙiba da ban sha'awa, suna kuma kiwo cikin iwa.19Gashi, wasu shanun bakwai suka fito bayan su, marasa ƙarfi, marasa ban sha'awa, ramammu kuma. A cikin dukkan ƙasar Masar ban taɓa ganin wani abin rashin ban sha'awa ba kamar su.20Shanun marasa ƙiba da rashin ban sha'awa suka cinye shanun na farko masu ƙiba.21Sa'ad da suka cinye su, ba za a ma san cewa sun cinye su ba, domin sun kasance marasa ban sha'awa kamar dã. Daga nan na farka.22Na duba a cikin mafarkina, kuma, duba, kawuna bakwai na hatsi suka fito bisa kara ɗaya, cikakku masu kyau.23Gashi kuwa, ƙarin kawuna bakwai - busassu, ƙanana, waɗanda kuma iskar gabas ke kakkaɓewa - suka fito bayansu.24Ƙananan kawunan suka haɗiye kawunan bakwai masu kyau. Na faɗi waɗannan mafarkai ga masu dabo, amma babu wani da zai yi bayyanin su a gare ni."25Yosef ya cewa Fir'auna, "Mafarkan Fir'auna ɗaya ne. Abin da Allah ke gaf da aiwatar wa, ya bayyana wa Fir'auna.26Shanun masu kyau guda bakwai shekaru bakwai ne, kawunan hatsin bakwai kuma shekaru bakwai ne. Mafarkan iri ɗaya ne.27Shanun bakwai ramammu marasa ban sha'awa da suka fito bayan su shekaru bakwai ne, haka nan kuma kawunan hatsin ƙanana da iskar gabas ke kakkaɓe wa shekaru ne bakwai na yunwa.28Wannan batun ne na faɗawa Fir'auna. Abin da Allah ke gaf da aiwatar wa ya bayyana wa Fir'auna.29Duba, shekaru bakwai na yalwa zasu zo cikin dukkan ƙasar Masar.30Shekaru bakwai na yunwa zasu zo bayan su, za a kuma manta da dukkan yalwar da aka yi a ƙasar Masar, kuma yunwar za ta lalata ƙasar.31Ba za a tuna da yalwar ba a cikin ƙasar saboda yunwar da za ta biyo baya, domin za ta zama da tsanani sosai.32Cewa an maimaita wa Fir'auna mafarkin saboda Allah ya tabbatar da al'amarin ne, kuma Allah zai aiwatar ba da daɗewa ba.33Yanzu bari Fir'auna ya nemi wani mutum mai fahimta da hikima, ya kuma ɗora shi bisa ƙasar Masar.34Bari Fir'auna ya zaɓi shugabanni bisa ƙasar, bari kuma su ɗauki kashi biyar na dukkan amfanin Masar a cikin shekaru bakwai na yalwa.35Bari su tattara dukkan abincin waɗannan shekaru masu kyau dake zuwa su kuma ajiye hatsi a ƙarƙashin ikon Fir'auna, domin abincin da za a yi amfani da shi a cikin biranen. Su adana shi.36Abincin zai zama abin wadatar wa domin ƙasar domin kuma shekaru bakwai na yunwa da zasu kasance a ƙasar Masar. Ta wannan hanyar ƙasar ba zata lalace ba ta wurin yunwar."37Wannan shawara ta yi kyau a idanun Fir'auna da idanun dukkan bayinsa.38Fir'auna ya cewa bayinsa, "Za mu iya samun wani mutum kamar wannan, wanda Ruhun Allah ke cikinsa?"39Sai Fir'auna ya cewa Yosef, "Tunda Allah ya nuna maka dukkan waɗannan abubuwa, babu wani mafi fahimta da hikima kamar kai.40Zaka kasance bisa gidana, kuma bisa ga maganar ka za a yi mulkin dukkan mutanena. A bisa kursiyi ne kawai zan fi ka girma."41Fir'auna ya cewa Yosef, "Duba, na sanya ka bisa dukkan ƙasar Masar."42Fir'auna ya cire zoben hatiminsa daga hannunsa ya sanya a hannun Yosef. Ya yi masa sutura da suturar linin mai laushi, ya kuma sanya sarƙar zinariya a wuyansa.43Ya sanya shi ya tuƙa karusarsa ta biyu da ya mallaka. Mutane suka yi sowa a gabansa, "Gwiwa a durƙushe." Fir'auna ya sanya shi bisa dukkan ƙasar Masar.44Fir'auna ya cewa Yosef, "Ni ne Fir'auna, baya gare ka kuma, babu mutumin da zai ɗaga hannunsa ko ƙafarsa a cikin dukkan ƙasar Masar."45Fir'auna ya kira Yosef da suna "Zafenat-Faniya." Ya ba shi Asenat, ɗiyar Fotifera firist na On, a matsayin mata. Yosef ya fita bisa ƙasar Masar.46Yosef yana da shekaru talatin sa'ad da ya tsaya a gaban Fir'auna, sarkin Masar. Yosef ya fita daga gaban Fir'auna, ya kuma tafi cikin dukkan ƙasar Masar.47A cikin shekaru bakwai na yalwa ƙasar ta fitar da amfani a yalwace.48Ya tattara dukkan abinci na shekaru bakwai dake cikin ƙasar Masar ya kuma sanya abincin a cikin biranen. Ya sanya a cikin kowanne birni abincin gonakin dake kewaye da shi.49Yosef ya ajiye hatsi kamar rairayin teku, da yawan gaske har ya daina ƙirgawa, saboda ya zarce ƙirgawa.50Yosef ya haifi 'ya'ya biyu kafin zuwan shekarun yunwa, waɗanda Asenat, ɗiyar Fotifa firist na On, ta haifa masa.51Yosef ya kira sunan ɗan fãrinsa Manasse, domin ya ce, "Allah ya sa na manta da dukkan damuwata da dukkan gidan mahaifina."52Ya kira sunan ɗan na biyu Ifraim, domin ya ce, "Allah ya maida ni mai bada 'ya'ya a cikin ƙasar wahalata."53Shekaru bakwai na yalwa da suka kasance a ƙasar Masar suka kawo ƙarshe.54Aka fãra shekaru bakwai na yunwa, kamar yadda Yosef ya faɗa. Aka yi yunwa a cikin dukkan ƙasashen, amma a cikin dukkan ƙasar Masar akwai abinci.55Sa'ad da dukkan ƙasar Masar suka fãra yunwa, mutanen suka kira ga Fir'auna da ƙarfi domin abinci. Fir'auna ya cewa dukkan Masarawa, "Ku je wurin Yosef ku kuma yi abin da ya ce."56Yunwa tana bisa dukkan fuskar ƙasar. Yosef ya buɗe dukkan gidajen ajiya ya sayar wa da Masarawa. Yunwa ta yi tsanani a ƙasar Masar.57Dukkan duniya na zuwa Masar su sayi hatsi daga wurin Yosef, saboda yunwar ta yi tsanani a dukkan duniya.
Shekaru biyu sun shuɗe bayan Yosef ya fassara fassarar mafarkin mai shayarwa da mai toye-toye, wanda ya kasance tare da Yosef a kurkuku.
"Fir'auna na tsaye"
"lafiya da mai"
"suna cin ciyawa a gefen kogin"
"mara lafiya da bakin ciki"
"kusa da rafin" ko "rafin kogi." Wannan shi ne mafi girman ƙasa a gefen kogin.
"farka"
Wani bangare ne na masara mai shuka da irin shuka ke tsiro.
"girma a kan tushe ɗaya."
"a ɗaya tushe kuma sun kasance lafiya da kyau"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "waɗanda suke bakin ciki da ƙonewa saboda iska mai zafi daga gabas"
Iska daga gabas ta shiga cikin hamada. Jin zafi na gabas yana yawan lalata.
"girma" ko "haɓaka"
"ci abinci." Fir'auna yana mafarki cewa masara mara lafiya zata iya cin masara ta lafiya kamar yadda mutum yake cin abinci.
"ya yi mafarki"
Anan kalmar "ruhu" yana nufin kasancewarsa ta ciki ko kuma motsin zuciyar sa. AT: "ya damu da kasancewarsa" ko "ya damu"
Sarakuna da shugabanni na da da in da suka yi amfani da bokaye da masu hikima a matsayin masu ba da shawara.
An yi amfani da kalmar "Yau" don girmamawa. Laifin nasa "shi ne yakamata a fadawa Fir'auna wani abu tun da farko amma bai yi hakan ba. AT: "Na gano cewa na manta ne in gaya muku wani abu"
"ka sanya shugaban masu toye-toye da ni a kurkuku inda shugaban masu gadin yake." Anan "gidan" yana nufin kurkuku.
"A wani dare muna duka mafarki"
"Mafarkanmu na da ma'anoni daban-daban"
Shugaban masu shayarwa ya ci gaba da magana da Fir’auna.
"A kurkuku muna tare da mu"
Anan "nasa" yana nufin masu shayarwa da masu toye-toye ne daban-daban, baya ga wanda ke fassara mafarkin. AT: "Ya bayyana abin da zai faru tsakaninmu"
"abin da ya yi bayani game da mafarki shi ne abin da ya faru daga baya"
Anan ne mai shayarwar ya yi amfani da taken Fir'auna wajen yin magana da shi a matsayin hanyar girmama shi. AT: "Ka ba ni damar komawa bakin aikina"
Anan "ya" yana nufin Fir'auna. Kuma, yana tsaye ga sojojin da Fir'auna ya umarta a rataye shugaban masu toye-toye. AT: "kun umarci sojojinku su rataye"
An fahimci cewa Fir'auna ya aiki bayin. AT: "Fir'auna ya aiki bayinsa su sa Yosef"
Ya zama al'ada gama aske fuska da gashin kai yayin shirya su tafi gaban Fir'auna.
Anan "fito" za'a iya bayyana shi azaman "ya tafi." AT: "ya tafi gaban Fir'auna"
"Ba ni bane wanda zai iya bayyana ma'anar"
"Allah zai amsa wa Fir'auna da alheri"
Fir'auna ya fara ba da labarin Yosef game da mafarkansa
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "ba wanda zai iya faɗi cewa bakin ciki shanun sun ci shanun"
Fir'auna ya ci gaba da gaya wa Yosef mafarkansa.
Yana nuna cewa ma'anar iri ɗaya ce. AT: "Mafarkai biyu suna nufin abu ɗaya"
Yosef ya yi magana da Fir'auna a cikin mutum na uku. Wannan wata hanya ce ta nuna girmamawa. Ana iya bayyana shi a cikin mutum na biyu. AT: "Allah yana nuna maka abin da zai aikata nan ba da jimawa ba"
Yosef ya ci gaba da fassarar mafarkin Fir'auna
Yosef ya yi magana da Fir'auna a cikin mutum na uku. Wannan wata hanya ce ta nuna girmamawa. Ana iya bayyana shi a cikin mutum na biyu. AT: "Waɗannan abubuwan zasu faru kamar yadda na faɗa muku ... ya Fir'auna, wanda aka bayyana maka"
Wannan yana magana game da shekarun wadata kamar idan lokaci wani abu ne wanda yake tafiya kuma yazo wani wuri. AT: "za a yi shekara bakwai a cikin wadatar abinci a ƙasar Masar"
Yosef ya ci gaba da fassara mafarkin Fir'auna.
Wannan yayi magana game da shekaru bakwai na yunwa kamar dai wani abu ne wanda yake tafiya kuma yana zuwa wani wuri. AT: "To, za a yi shekara bakwai lokacin da ƙarancin abinci yake"
Yosef ya bayyana ra'ayi a hanyoyi biyu don jaddada mahimmancinta.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah ya baku mafarkai biyu don ya nuna muku cewa lalle zai sa waɗannan abubuwan su faru"
Yosef ya yi magana da Fir'auna a cikin mutum na uku. Wannan wata hanya ce ta nuna girmamawa. Ana iya bayyana shi a cikin mutum na biyu. AT: "Kai Fir'auna, ya kamata ka duba"
Kalmomin "saka shi" yana nufin ba wani iko ko izni. AT: "ka ba shi iko bisa masarautar Masar" ko "ka sa shi ya zama mai mulkin masarautar"
Kalmar "na biyar" ƙunshi juzu'i ne. AT: "Bari su raba kayan masarufin zuwa kashi biyar daidai yake, sannan a ɗauki ɗayan waɗannan sassan"
"a cikin shekaru bakwai ɗin da ake samun wadatar abinci"
Bayanin "a karkashin ikon Fir'auna" yana nufin Fir'auna ya ba su iko. AT: "yi amfani da ikon Fir'auna don adana hatsin"
Anan "ƙasa" tana nufin mutane. AT: "abincin nan zai kasance ga mutane"
Anan "ƙasa" tana tsaye ga mutane. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ta haka ne mutane ba za su matsananciyar yunwar yayin yunwar ba"
Idanu suna wakiltar gani, da gani suna wakiltar tunani ne ko hukunci. AT: "Fir'auna da bayinsa suna tsammani wannan kyakkyawan shiri ne"
Wannan yana nufin jami'an Fir'auna.
"mutum kamar wanda Yosef ya bayyana"
"wanda a cikinsa Ruhun Allah ke zaune"
"Babu wanda ya isa ya yanke shawara."
Anan "gidan" yana tsaye ne ga gidan Fir'auna da mutanen da ke cikin gidan. Kalmomin "zai kare" na nufin Yosef zai sami iko a kansa. AT: "Za ku kasance a madadin kowa a fada na"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Za ku mallaki jama'ata kuma za su aikata abin da kuka umarta"
Anan “kursiyi” na wakiltar sarautar Fir’auna a matsayin sarki. AT: "Kawai a matsayina na sarki"
Duk waɗannan ayyukan suna nuna cewa Fir'auna ya ba Yosef ikon yin duk abin da Yosef ya shirya.
Wannan zobe yana da hatimin Fir'auna a jikinshi. Wannan ya ba Yusufu iko da kuɗin da ake buƙata don aiwatar da tsare-tsarensa.
Wannan abin da ya yi ya bayyana wa mutane cewa Yosef na biyu ne na Fir'auna.
"Ku yi ruku'u, ku girmama Yosef." Rage gwiwa da ruku'u alama ce ta girmamawa da girmamawa.
Anan "hannun" da "ƙafa" suna tsaye don ayyukan mutum. AT: "Ba wani mutum a Masar da zai yi komai ba tare da izininka ba" ko kuma "kowane mutum a Masar dole ne ya nemi izininka kafin su yi wani abu"
Masu fassara na iya ƙara wa ɗan littafin rubutun mai zuwa: Sunan Zafenat-Faniya yana nufin "mai siye da asirai."
Firistoci a ƙasar Masar su ne mafi girma kuma mafi kyawon ɗabi'a. Wannan aure yana nuna matsayin Yosef na daraja da gata.
On wani birni ne, wanda kuma ake kira Heliopolis, wanda shi ne "Birnin Rana" da kuma tsakiyar bautar gunkin rana Ra.
Anan "ya tsaya a gaban" tsaye ga Yosef wanda ya fara hidimar Fir’auna. AT: "lokacin da ya fara bauta wa Fir'auna"
"A cikin shekarun nan bakwai kyawawa"
Wannan yana kwatanta hatsi da yashi na teku don ƙarfafa babban adadinsa. AT: "Hatsi da Yosef ya adana ya kasance mai yawa kamar yashi a bakin teku"
Wannan yana magana game da shekaru kamar dai wani abu ne wanda yake tafiya kuma yana zuwa wani wuri. AT "kafin shekara bakwai na yunwar ta fara"
Masu fassarar na iya ƙara shafin rubutu da ke cewa, "Sunan 'Manasse' yana nufin 'sanadin abin da ake mantawa.'"
Masu fassara na iya ƙara rubutun cikin rubutu da ke cewa, "Sunan 'Ifraim' yana nufin 'mai 'ya 'ya' ko 'da 'ya'ya.'"
A cikin duk al'umman da suke kewaye da Masar, har da ƙasar Kan'ana.
Kalmar "fuska" tana nufin saman ƙasar. AT: "Yunwar ta bazu ko'ina cikin ƙasar"
Anan "Yosef" yana tsaye ne ga bayin Yosef. AT: "Yosef ya sa bayinsa su buɗe shago kuma sayar da hatsi ga Masarawa"
Anan "ƙasa" tana wakiltar mutane daga kowane yanki. AT: "Mutane suna ta zuwa Masar daga dukkan yankuna kewaye"
1Yanzu Yakubu ya sami sani cewa akwai hatsi a Masar. Ya ce wa 'ya'yansa maza, "Meyasa kuke kallon juna?"2Ya ce, "Ku saurara, Na ji cewa akwai hatsi a Masar. Ku gangara can ku sawo domin mu dagacan domin mu rayu kada kuma mu mutu."3'Yan'uwan Yosef goma suka gangara domin su sawo hatsi daga Masar.4Amma Benyamin, ɗan'uwan Yosef, Yakubu bai aike shi ba tare da 'yan'uwansa, saboda ya ji tsoron cewa wani bala'i na iya afko masa.5'Ya'yan Isra'ila na cikin waɗanda suka zo saye, domin akwai yunwa a cikin ƙasar Kan'ana.6Yanzu dai Yosef shi ne gwamna a ƙasar. Shi ne ke saida wa dukkan mutanen ƙasar. 'Yan'uwan Yosef suka zo suka kuma rusuna masa da fuskokinsu ƙasa.7Yosef ya ga 'yan'uwansa ya kuma gãne su, amma ya ɓadda masu kamarsa ya kuma yi magana da su da zafi. Ya ce masu, "Daga ina kuka fito?" Suka ce, "Daga ƙasar Kan'ana domin mu sayi abinci."8Yosef ya gãne 'yan'uwansa, amma su basu gãne shi ba.9Daga nan Yosef ya tuna da mafarkan da ya yi game da su, ya kuma ce masu, "Ku 'yan leƙen asirin ƙasa ne! kun zo ku ga sassan ƙasar da basu da tsaro."10Suka ce masa, "A'a, shugabana. Bayinka sun zo sayen abinci ne.11Dukkan mu 'ya'yan mutum ɗaya ne. Mu mutane ne masu gaskiya. Bayinka ba 'yan leƙen asirin ƙasa ba ne."12Ya ce masu, "A'a, kun zo ku ga sassan ƙasar da ba su da tsaro."13Suka ce, "Mu bayinka 'yan'uwa sha biyu ne, 'ya'yan mutum ɗaya a cikin ƙasar Kan'ana. Duba, ƙaramin mu a yau yana tare da mahaifinmu, ɗayan ɗan'uwan kuma baya da rai."14Yosef yace masu, "Abin da na ce maku ke nan; ku 'yan leƙen asirin ƙasa ne.15Ta haka za a gwada ku. Da ran Fir'auna, ba zaku bar nan ba, sai idan ƙaramin ɗan'uwanku ya zo nan.16Ku aiki ɗaya daga cikin ku ya je ya zo da ɗan'uwanku. Zaku zauna a kurkuku, domin a gwada maganganunku, ko akwai gaskiya a cikin ku."17Ya sa dukkan su a ka kulle su har kwana uku.18A rana ta uku Yosef yace masu, "Ku yi haka kuma ku rayu, domin ina tsoron Allah.19Idan ku mutane ne masu gaskiya, bari ɗaya daga cikin 'yan'uwanku a tsare shi a kurkuku, amma ku ku tafi, ku ɗauki hatsi domin yunwar gidajenku.20Ku kawo mani ƙaramin ɗan'uwanku domin a tabbatar da maganganunku kuma ba za ku mutu ba." Sai suka yi haka.21Suka cewa juna, "Babu shakka mun yi laifi game da ɗan'uwanmu yadda muka ga ƙuncin ransa sa'ad da ya roƙe mu, amma muka ƙi sauraron sa. Saboda haka wannan ƙunci ya zo bisanmu."22Ruben ya amsa masu, "Ban gaya maku ba, 'Kada kuyi zunubi game da saurayin, amma baku saurare ni ba? Yanzu, duba, ana neman jininsa daga hannunmu."23Basu san cewa Yosef ya fahimce su ba, domin akwai mai fassara a tsakanin su.24Ya juya daga gare su ya yi kuka. Ya kuma dawo gare su ya yi magana da su. Ya ɗauki Simiyon daga cikin su ya ɗaure shi a gaban idanunsu.25Daga nan Yosef ya umarci bayinsa su cika buhunan 'yan'uwansa da hatsi, kuma su maida wa kowa kuɗinsa cikin buhunsa, su kuma basu kayan masarufi domin tafiyarsu. A ka yi haka domin su.26Suka ɗora wa jakunansu hatsi suka kuma yi tafiyar su daga wurin.27Yayin da ɗaya daga cikin su ya buɗe buhunsa domin ya ciyar da jakinsa a wurin hutawar su, ya ga kuɗinsa. Duba, suna bakin buhunsa.28Ya cewa 'yan'uwansa, "An maida mani kuɗina, ku dube su; suna bakin buhuna." Zukatansu suka nitse, suka kuma juya suna rawar jiki ga junansu, suna cewa, "Mene ne haka da Allah ya yi mana?"29Suka tafi wurin Yakubu, mahaifinsu a cikin ƙasar Kan'ana suka kuma gaya masa dukkan abin da ya faru da su. Suka ce,30"Mutumin, ubangijin ƙasar, ya yi magana da mu da zafi ya zaci cewa mu 'yan leƙen asirin ƙasa ne.31Muka ce masa, "Mu mutane ne masu gaskiya. Ba 'yan leƙen asirin ƙasa bane.32Mu 'yan'uwa ne sha biyu, 'ya'ya maza na mahaifinmu. Ɗaya baya da rai, ƙaramin kuma yau yana tare da mahaifinmu a ƙasar Kan'ana.'33Mutumin, ubangijin ƙasar, ya ce mana, 'Ta haka zan sani cewa ku mutane ne masu gaskiya. Ku bar ɗaya daga cikin 'yan'uwanku tare da ni, ku ɗauki hatsi domin yunwar dake gidajenku, ku kuma yi tafiyarku.34Ku kawo ƙaramin ɗan'uwanku wuri na. Daga nan zan sani cewa ku ba 'yan leƙen asirin ƙasa ba ne, amma ku mutane ne masu gaskiya. Daga nan zan saki ɗan'uwanku a gare ku, kuma zaku yi sana'a a ƙasar."'35Sai ya kasance yayin da suka zazzage buhunansu, duba, kowanne mutum jakkar azurfarsa na cikin buhunsa. Sa'ad da su da mahaifinsu suka ga jakkunan azurfarsu, sai suka tsorata.36Yakubu mahaifinsu ya ce masu, "Kun salwantar mani da 'ya'yana. Yosef ba shi da rai, Simiyon kuma ya tafi, kuma zaku ɗauke Benyamin. Waɗannan abubuwa dukka gãba suke da ni."37Ruben ya yi magana da mahaifinsa, cewa, "Kana iya kashe 'ya'yana biyu idan ban maido maka da Benyamin ba. Ka sanya shi cikin hannuwana, kuma zan sake maido maka da shi."38Yakubu yace, 'Ɗana ba zai tafi tare da ku ba. Domin ɗan'uwansa ya mutu shi kaɗai kuma ya rage. Idan wani bala'i ya zo masa a hanyar da zaku tafi, daga nan zaku kawo furfurata da baƙinciki zuwa Lahira."
Yakubu ya yi amfani da tambaya ya tsawata wa 'ya'yansa saboda rashin yin komai game da hatsin. AT: "Kada ku zauna kawai!"
A nan "Masar" yana nufin mutanen da ke sayar da hatsi. AT: "daga masu siyar da hatsi a Masar"
Benyamin da Yosef suna da uba ɗaya da uwa ɗaya, mahaifiyarsu ta bambanta da iyayen sauran 'yan'uwan. Yakubu bai so yin haɗarin aika ɗan Rahila na ƙarshe ba.
Ana iya fassara kalmar "ya zo" a matsayin "ya tafi." Hakanan, kalmomin "hatsi" da "Masar" an fahimta. AT: "'Ya'yan Isra'ila suka tafi tare da hatsi tare da wasu mutanen da suka tafi Masar"
Wannan wata hanya ce ta nuna girmamawa.
"A lokacin da Yusufu ya ga 'yan'uwansa, ya gane su"
"ya yi aiki kamar ba ɗan'uwansu bane" ko kuma bai bar su su san cewa shi ɗan'uwansu ne ba
Wannan ba karamar magana ba ce duk da cewa Yosef ya san amsar. Yana daga cikin zaɓaɓɓen nasa don kiyaye asalinsa daga 'yan'uwansa.
'Yan leƙen asirin mutane ne waɗanda suke ƙoƙarin neman bayani game da wata ƙasa don taimakawa wata ƙasa.
Wannan wata hanya ce da za a koma zuwa wani don girmama su.
'Yan'uwa suna kiran kansu “barorinku”. Wannan ita ce hanya madaidaiciyar magana da wani da ke da babban iko. AT: "Mu bayin ku, muna da" ko "Muna da"
"Yosef ya ce wa 'yan'uwansa"
Ana iya bayyana cikakkiyar ma'ana a sarari. AT: "A'a, kun zo ne don gano inda ba mu tsaron ƙasarmu domin ku iya kawo mana hari"
"Yanzu yan uwanmu yana tare da mahaifin mu"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ta haka zan gwada ku"
Wannan magana tana nuna rantse mai kauri. AT: "Na rantse da ran Fir'auna"
"Ku zaɓi ɗaya daga cikin ku don ku nemi ɗan'uwanku"
"Sauranku zasu ci gaba da kasancewa a kurkuku"
Bayanin da aka fahimta za a iya bayyana shi a sarari. AT: "Idan zaku yi abin da na faɗi, zan bar ku ku rayu"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "A bar ɗaya daga cikin 'yan'uwanku a nan cikin kurkuku"
Anan "gidaje" suna tsaye ga iyalai. AT: "kai hatsi gida don taimaka wa danginku a lokacin wannan yunwar"
Kalmar nan "kurwa" tana wakiltar Yosef. AT: "saboda mun ga yadda Yosef ya wahala sosai" ko "saboda mun ga cewa Yosef yana wahala"
Ana iya bayyana sunan "baƙin ciki" a zaman kalmar aikatau "wahala." AT: "Abin da ya sa muke wahala haka yanzu"
Ruben ya yi amfani da tambaya don tsauta wa 'yan'uwansa. AT: "Na ce kada ku cuci yaron, amma ba za ku kasa kunne ba!"
Anan "jini" yana wakiltar mutuwar Yosef. 'Yan'uwansa sun yi zaton Yosef ya mutu. Jumlar "ana buƙatar mu" yana nufin dole ne a hukunta su saboda abin da suka aikata. AT: "Muna samun abin da ya cancanci mutuwarsa" ko "muna shan wahala saboda mun kashe shi"
Wannan ya canza daga layin babban labari zuwa bayanan baya wanda ya bayyana dalilin da yasa 'yan uwan suke tunanin Yosef bai iya fahimtar su ba.
An ɗauka cewa Yosef ya yi kuka domin yana cikin nutsuwa bayan ya ji abin da 'yan'uwansa suka faɗi.
Anan mutane suna wakilta ta "idanunsu" don jaddada abin da suke gani. AT: "ɗaure shi a idanunsu" ko "ɗaure shi yayin da suke kallo"
"Lokacin da suka tsaya a wani wuri da daddare, wani daga cikin 'yan'uwa ya bude jakarsa don neman abinci ga jakinsa. A cikin buhu ya ga kudinsa!"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Wani ya mayar da kuɗata"
Don tsoro, ana magana kamar an ce zuciyoyinsu suna ruɗewa. Anan "zukata" suna tsaye don ƙarfin hali. AT: "Sun tsorata sosai"
"ubangijin Masar"
"yi magana da ƙarfi"
Wannan yana da ambaton cikin ambato. Ana iya bayyana shi azaman magana kai tsaye. AT: "Mun gaya masa cewa mu masu gaskiya ne ba 'yan leken asiri ba."
AT: "Mun ce 'yan uwanmu goma sha biyu ne, 'ya'yan mahaifinmu, kuma ɗan'uwanmu baya nan ... ƙasar Kan'ana"
An fahimci kalmar "ɗan'uwana". AT: "ɗaya 'yan'uwanmu baya raye"
Anan "gidaje" suna tsaye ga "dangi." AT: "ɗauki hatsi don taimakawa danginku yayin yunwar"
"koma gida" ko "tafi"
"kun hana ni 'ya'yana" ko "kun sa ni rasa biyu daga cikin' ya'yana"
"Duk waɗannan abubuwan sun cuce ni"
Wannan roƙon ne don Ruben ya tafi da Benyamin tare da kula da shi yayin tafiya. AT: "Ka sanya shi a madadinsa" ko "Bari in kula da shi"
AT: "Ɗana Benyamin, ba zai tafi tare da ku zuwa Masar ba"
Ana iya bayyana cikakkiyar ma'ana. AT: "Gama matata, Rahila, ta haifi 'ya'ya biyu. Yosef ya mutu, amma Benyamin guda kaɗai ya rage"
''Saukar da ... zuwa cikin Lahira" hanya ce da za su sa shi ya mutu kuma ya tafi Lahira. Yayi amfani da kalmar "ƙasa" saboda galibi an yi imani da cewa Sheol wani wuri ne ƙarƙashin ƙasa. AT: "to, za ka sa ni, dattijo, ya mutu saboda baƙin ciki"
1Yunwa ta yi tsanani a ƙasar.2Sai ya kasance sa'ad da suka cinye hatsin da suka kawo daga Masar, mahaifinsu ya ce masu, "Ku sake komawa; ku sayo mana ɗan abinci."3Yahuda yace masa, "Mutumin ya yi mana kashedi sosai, 'Ba za ku ga fuskata ba har sai ɗan'uwanku na tare da ku.'4Idan ka aika ɗan'uwanmu tare da mu, to za mu gangara mu je mu sayo maka abinci.5Amma idan ba ka aika da shi ba, ba za mu tafi ba. Domin mutumin ya ce mana, 'Ba za ku ga fuskata ba har sai ɗan'uwanku na tare da ku."'6Isra'ila yace, "Meyasa kuka yi mani mummunan abu haka ta wurin gaya wa mutumin cewa kuna da wani ɗan'uwan?"7Suka ce, "Mutumin ya yi tambaya dalla-dalla game da mu da iyalinmu. Ya ce, 'Mahaifinku yana nan da rai? Kuna da wani ɗan'uwan? Muka amsa masa bisa ga waɗannan tambayoyi. Ta yaya zamu san cewa zai ce, 'Ku kawo ɗan'uwanku nan?"'8Yahuda ya cewa Isra'ila mahaifinsa, "Ka aiki saurayin tare da ni. Zamu tashi mu tafi domin mu rayu kada kuma mu mutu, dukkanmu, da kai, da kuma 'ya'yanmu dukka.9Ni zan tsaya domin sa. Zaka riƙe ni hakkinsa. Idan ban dawo maka da shi ba na kuma tsaida shi a gabanka ba, daga nan bari in ɗauki laifin har abada.10Domin idan da ba mu yi jinkiri ba, tabbas da yanzu mun dawo karo na biyu.11Mahaifinsu Isar'ila yace masu, "Idan haka abin yake, yanzu kuyi haka. Ku ɗauki mafi kyau daga cikin amfanin ƙasar a cikin jakkunanku. Ku tafi da su kyauta ga mutumin - su man shafawa da zuma, kayan yaji da ƙaro, tsabar 'ya'yan itace dana almond.12Ku ɗauki kuɗi ka shi biyu a hannunku. Kuɗaɗen da aka maido maku da aka buɗe buhunanku, ku ɗauka a cikin hannunku. Wataƙila kuskure ne.13Ku ɗauki ɗan'uwanku kuma. Ku tashi ku sake tafiya wurin mutumin.14Bari Allah maɗaukaki ya baku jinƙai a gaban mutumin, domin ya sakar maku ɗaya ɗan'uwanku da Benyamin. Idan na rasa 'ya'yana, na rasa su."15Mutanen suka ɗauki kyautar, a hannunsu kuma suka ɗauki kuɗi kashi biyu, tare da Benyamin. Suka tashi kuma suka tafi suka gangara zuwa Masar suka je suka tsaya kuma a gaban Yosef.16Sa'ad da Yosef yaga Benyamin tare da su, ya cewa ma'aikacin gidansa, "Ka kawo mutanen cikin gida, ka yanka dabba ka shirya ta, domin mutanen zasu ci tare da ni da rana."17Ma'aikacin ya yi yadda Yosef ya ce. Ya kawo mutanen cikin gidan Yosef.18Mutanen suka tsorata saboda an kawo su cikin gidan Yosef. Suka ce, "Saboda kuɗaɗen da aka maido mana cikin buhunanmu a zuwanmu na farko aka kawo mu ciki, domin ya sami zarafin gãba da mu. Zai iya ɗaure mu ya ɗauke mu a matsayin bayi, ya kuma karɓe jakkunanmu."19Suka kusanci ma'aikacin gidan Yosef,20suka kuma yi magana da shi a bakin ƙofar gidan, cewa, "Shugabana, mun zo karo na farko sayen abinci.21Sai ya kasance, da muka isa wurin hutawa, sai muka buɗe buhunanmu, kuma, duba, kuɗin kowanne mutum na bakin buhunsa, kuɗaɗenmu kuma nada nauyinsu dai-dai. Mun sake kawo su a hannuwanmu.22Mun sake kuma kawo wasu kuɗaɗen domin mu sayi abinci. Ba mu san wanda ya sanya kuɗaɗenmu cikin buhunanmu ba."23Ma'aikacin yace, "Salama a gareku, kada ku ji tsoro. Allahnku da Allahn mahaifinku ne ya sanya kuɗaɗenku a buhunanku. Na karɓi kuɗaɗenku." Daga nan ma'aikacin ya fito da Simiyon wurinsu.24Ma'aikacin ya kai mutanen cikin gidan Yosef. Ya basu ruwa, suka kuma wanke ƙafafunsu. Ya ciyar da jakkunansu.25Suka shirya kyaututtukan domin zuwan Yosef da rana, domin sun ji cewa zasu ci abinci a nan.26Sa'ad da Yosef ya zo gida, suka kawo kyaututtukan dake hannuwansu cikin gidan, suka kuma rusuna a gabansa har ƙasa.27Ya tambayi lafiyarsu ya kuma ce, "Mahaifinku na nan lafiya, tsohon da kuka yi maganar sa? Har yau yana nan da rai?"28Suka ce, "Bawanka mahaifinmu yana nan lafiya lau. Har yau yana nan da rai." Suka kwanta kuma suka rusuna har ƙasa.29Sa'ad da ya ɗaga idanunsa ya kalli Benyamin ɗan'uwansa, ɗan mahaifiyarsa, sai ya ce, "Wannan ne ƙaramin ɗan'uwanku da kuka yi mani maganarsa?" Daga nan ya ce, "Allah ya yi maka alheri, ɗana."30Yosef ya yi hanzari ya fita daga ɗakin, saboda ya motsu sosai game da ɗan'uwansa. Ya nemi wurin da zai yi kuka. Ya tafi ɗakinsa ya yi kuka a can.31Ya wanke fuskarsa ya kuma fito. Ya kame kansa, ya ce, "A raba abincin."32Bayin suka yi wa Yosef hidima shi kaɗai, suka kuma yi wa 'yan'uwan hidima su kaɗai. Masarawan suka ci tare da shi su kaɗai, saboda Masarawa ba zasu ci abinci tare da Ibraniyawa ba, domin yin haka abin ƙyama ne ga Masarawa.33'Yan'uwan suka zauna a gabansa, na farko bisa ga matsayin haihuwarsa, ƙaramin kuma bisa ga samartakarsa. Mutanen suka yi mamaki tare.34Yosef ya aika masu kaso daga abincin dake gabansa. Amma kason Benyamin ya yi sau biyar fiye dana 'yan'uwansa. Suka sha suka kuma yi murna tare da shi.
An fahimci kalmar "Kan'ana". Ana iya yin bayanin wannan a bayyane. AT: "Yunwar ta yi tsanani a ƙasar Kan'ana"
Anan "mu" yana nufin Yakubu, 'ya'yansa, da sauran dangi.
Wannan yana nufin Yosef, amma 'yan'uwa ba su san shi Yosef ba ne. Sun kira shi "mutumin" ko kuma "mutumin, ubangijin ƙasa" kamar yadda a cikin Farawa 42:29.
Yahuza yayi amfani da wannan magana sau biyu cikin Farawa 43: 3-5 don jaddada wa mahaifinsa cewa ba za su iya komawa Masar ba tare da Benyamin. Kalmomin "fuskata" tana nufin mutumin, wanda yake Yosef. AT: "Ba za ku gan ni ba"
"Me yasa kika jawo min matsala sosai"
"Mutumin ya yi tambayoyi da yawa"
"Mun amsa tambayoyin da ya yi mana"
Ya'yan sun yi amfani da wata tambaya suna jaddada cewa mutum bai san abin da mutumin zai gaya musu ba. Wannan tambaya za a iya fassara a matsayin bayani. AT: "Ba mu san zai faɗi ba ... ƙasa!"
Kalmomin "muna iya rayuwa" kuma "ba mutu" suna nufin abu ɗaya. Yahuda yana nanata cewa lallai ne su sayi abinci a Masar don su rayu. AT: "Yanzu za mu tafi ƙasar Masar mu sami hatsi don danginmu su rayu"
Ana iya amfani da kalmar 'garanti' azaman kalmar aikatau "alƙawari". AT: "Zan yi alkawarin dawo da shi"
Yadda Yakubu zai riƙe Yahuda alhakin za a iya bayyana a sarari. AT: "Za ku ba ni amsa a kanku game da abin da ya faru da Benyamin"
Wannan yana magana game da "zargi" kamar dai abu ne wanda mutum ya kamata ya ɗauka. AT: "zaku iya zarge ni"
"da mun dawo sau biyu"
"Idan wannan shine zabin mu, to yi shi"
Anan "hannun" yana tsaye ga mutum gaba ɗaya. AT: "ɗauki ninki biyu tare da ku"
Anan "hannun" yana tsaye ga mutum gaba ɗaya. Ana iya bayyana kalmar "da aka mayar" a cikin aiki mai aiki. AT: "koma ƙasar Masar kuɗin da wani ya saka a cikin jakarku"
"Riƙi Benyamin"
Ana iya bayyana sunan "rahama" a zaman ma'anar "nau'in". AT: "Allah Madaukakin ya sa mutumin ya yi muku alheri"
"Simiyon"
"Idan na rasa 'ya'yana, to, na rasa' ya'yana." Wannan yana nuna cewa Yakubu ya san dole ne ya yarda da duk abin da ya faru da 'ya'yansa.
"Benyamin tare da manyan 'yan'uwan Yosef"
“Mai hidimar” ya kasance yana kula da ayyukan gidan Yosef.
"Yan'uwan Yosef sun ji tsoro"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ma'aikacin gidan yana kawo mu cikin gida saboda kuɗin da wani ya sake sanyawa cikin kayanmu"
Ana iya fassara wannan azaman sabon jumla. AT: "Yana jiran zarafi ya tuhume mu, domin ya kama mu"
‘Yan’uwan sun ci gaba da magana da ma'aikacin gidan.
"lokacin da muka je wurin da za mu tsaya a daren"
"kowanenmu ya sami cikakkiyar adadin kuɗinsa a cikin taikinsa"
Anan "hannaye" suna tsaye ga mutum gaba ɗaya. AT: "Mun dawo da kuɗin tare da mu"
Anan "hannun" yana tsaye ga mutum gaba ɗaya. AT: "Mun kuma kawo ƙarin kuɗi don siyan abinci"
Ana iya bayyana sunan "Salama" a matsayin fi'ili. AT: "Huta" ko "kwantar da kanku"
Ma'aikacin gidan din ba yana magana game da alloli biyu ne daban-daban ba.AT: "Allahnku, Allahn mahaifinku yana bauta"
Wannan al'ada ta taimaka wa matafiya waɗanda suka gaji don yin annashuwa bayan sun yi tafiya mai nisa. Ana iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayanin a bayyane.
Anan "hannun" yana tsaye ga mutum gaba ɗaya. AT: "'yan'uwan sun kawo kyaututtukan da suke tare da su"
Suna kiran mahaifinsu da “Bawanka” don nuna girmamawa. AT: "Mahaifinmu wanda yake yi maka aiki"
Waɗannan kalmomin suna nuna dai-dai ne. Sun kwanta a gaban mutumin don nuna masa girmamawa. AT: "Sun sunkuya a gabansa"
Wannan yana nufin "ya duba sama."
Ana iya fassara wannan da sabon jumla. AT: "ɗan mahaifiyarsa, ko kuma Yosef yace"
Ma'anan iya ma'ana sune 1) Da gaske ne Yosef yana yin tambaya don tabbatar da cewa wannan mutumin Benyamin ne, ko 2) tambaya ce mai magana. AT: "To, wannan shi ne ƙanen kuku ... ni."
Wannan hanya ce ta abokantaka wanda mutum zai yi magana da wani mutum mai ƙarancin daraja. AT: "saurayi"
"da sauri na fice daga dakin"
Kalmomin nan "ya motsa sosai" yana nufin samun ƙarfin ji ko motsin rai yayin da wani abu mai mahimmanci ya faru. AT: "saboda yana da tsananin tausayin ɗan'uwansa" ko "saboda yana da ƙaunar ɗan'uwansa"
Wannan yana nufin cewa Yosef, 'yan'uwan, da kuma sauran Masarawa suna cin abinci a wurare uku a cikin wannan ɗakin. AT: "Barorin sun bauta wa Yosef shi kaɗai da 'yan'uwan su kaɗai da kuma Masarawa waɗanda suke cin abinci tare da shi, su da kansu"
Ana iya fassara wannan azaman sabon jumla: "Sun yi wannan ne saboda Masarawa suna tsammani abin kunya ne a ci tare da Ibraniyawa"
An ɗauka cewa Yosef ya shirya inda kowane ɗan'uwan zai zauna. Kuna iya bayyana bayyanannen bayanin. AT: "'Yan'uwan sun zauna a gefen mutumin, gwargwadon yadda ya tsara wuraren su"
Ana amfani da “firstbornan fari” da “ƙarami” tare domin nufin cewa duk ’yan’uwan sun zauna bisa tsari bisa ga shekarunsu.
"Mutanen sun yi matukar mamaki lokacin da suka fahimci hakan"
Ana iya faɗi kalmar "sau biyar" a gaba ɗaya. AT "Amma Benyamin ya sami rabo wanda ya fi girma fiye da abin da 'yan'uwansa suka karɓi"
1Yosef ya umarci ma'aikacin gidansa, ya ce, "Ka cika buhunan mutanen da abinci, iya yadda zasu iya ɗauka, ka kuma maida wa kowannen su kuɗinsa cikin bakin buhunsa.2Ka sanya kofina, kofin azurfa, cikin bakin buhun ƙaramin, da kuɗinsa na hatsi." Ma'aikacin ya yi yadda Yosef ya ce.3Da asuba, aka kuma sallami mutanen, su da jakkunansu.4Sa'ad da suka fice daga birnin ba su riga sun yi nisa ba, Yosef ya cewa ma'aikacinsa, "Tashi, ka bi bayan mutanen, idan kuma ka sha kansu, ka ce masu, 'Meyasa kuka maida mugunta domin nagarta?5Wannan ba kofin da maigidana ke sha bane, kofin da yake amfani da shi domin sihiri? Kun yi mugunta, wannan abin da kuka yi."'6Ma'aikacin ya sha kansu ya kuma faɗi waɗannan maganganu a gare su.7Suka ce masa, "Meyasa shugabana yake faɗin waɗannan maganganu haka? Bari ya yi nesa daga bayinka da zasu aikata irin wannan.8Duba, kuɗaɗen da muka samu a bakin buhunanmu, mun sake kawo maka su daga ƙasar Kan'ana. Ta yaya daga nan zamu yi sãtar azurfa ko zinariya daga gidan shugabanmu?9Duk wanda aka same shi a wurinsa daga cikin bayinka, bari ya mutu, mu kuma zamu zama bayin shugabana."10Ma'aikacin yace, "Yanzu kuma bari ya kasance bisa ga maganganunku. Shi wanda aka sami kofin a wurinsa zai zama bawana, ku kuma sauran zaku fita daga zargi."11Daga nan kowanne mutum ya yi hanzari ya sauko da buhunsa ƙasa, kowanne mutum kuma ya buɗe buhunsa.12Ma'aikacin ya bincike. Ya fãra da babban ya kuma ƙarashe da ƙaramin, aka kuma sami kofin a buhun Benyamin.13Daga nan suka kece tufafinsu. Kowanne mutum ya ɗora kaya a jakinsa suka kuma dawo cikin birni.14Yahuda da 'yan'uwansa suka zo gidan Yosef. Har yanzu yana nan, suka kuma rusuna a gabansa har ƙasa.15Yosef yace masu, "Mene ne kuka yi haka? Ba ku san cewa mutum kamar ni ina aikata sihiri ba?"16Yahuda yace, "Me za mu cewa shugabana? Me za mu faɗa? Ko yaya zamu baratar da kanmu? Allah ya gãno laifin bayinka. Duba, mu bayin shugabana ne, dukkan mu da wanda aka iske kofin a hannunsa." Yosef yace,17"Bari yayi nesa da ni da in aikata haka. Mutumin da aka iske kofin a hannunsa, wannan taliki zai zama bawana, amma game da ku sauran, ku tafi cikin salama ga mahaifinku."18Daga nan Yahuda ya matso kusa da shi ya kuma ce, "Shugabana, na roƙe ka bari bawanka ya faɗi magana cikin kunnuwan shugabana, bari kuma fushinka ya yi ƙuna gãba da bawanka, domin kamar dai Fir'auna kake.19Shugabana ya tambayi bayinsa, cewa, 'Kuna da mahaifi ko ɗan'uwa?'20Muka cewa shugabana, 'Muna da mahaifi, tsohon mutum, kuma da ɗan tsufansa, ƙarami ne. Amma ɗan'uwansa ya mutu, shi kaɗai kuma ya rage ga mahaifiyarsa, kuma mahaifinsa na ƙaunarsa.'21Daga nan ka cewa bayinka, 'Ku kawo shi nan a gare ni domin in gan shi.'22Bayan haka, muka cewa shugabana, 'Yaron ba zai iya barin mahaifinsa ba. Domin idan har ya bar mahaifinsa to mahaifinsa zai mutu.'23Daga nan ka cewa bayinka, 'Har sai ƙaramin ɗan'uwanku ya zo tare da ku, ba zaku sake ganin fuskata ba.'24Daga nan ya kasance sa'ad da muka tafi wurin bawanka mahaifina, muka faɗi masa maganganun shugabana.25Mahaifinmu yace, 'Ku sake komawa, ku sawo mana ɗan abinci.'26Daga nan muka ce, 'Ba za mu iya komawa ba. Idan ƙaramin ɗan'uwanmu yana tare da mu, daga nan zamu gangara mu tafi, domin ba za mu iya ganin fuskar mutumin ba har sai ƙaramin ɗan'uwanmu yana tare da mu.'27Bawanka mahaifina ya ce mana, 'Kun san cewa matata ta haifa mani 'ya'ya maza biyu.28Ɗaya daga cikin su ya fita daga gare ni kuma na ce, "Tabbas an yage shi gutsu-gutsu, ban sake ganin sa ba kuma tuni."29Yanzu idan kuka sake ɗauke wannan daga gare ni, kuma bala'i ya zo masa, zaku gangarar da furfurata da baƙinciki zuwa Lahira.'30Yanzu, saboda haka, sa'ad dana koma wurin bawanka mahaifina, kuma saurayin baya tare da mu, tun da rayuwarsa ɗaure take da rayuwar yaron,31zai kasance, sa'ad da ya ga yaron ba ya tare da mu, zai mutu. Bayinka zasu gangara da furfurar bawanka mahaifinmu da baƙinciki zuwa Lahira.32Gama bawanka ya zama wanda ya tsaya domin yaron ga mahaifina na kuma ce, 'Idan ban maido maka da shi ba, daga nan zan ɗauki laifin ga mahaifina har abada."33Saboda haka yanzu, ina roƙon ka bari bawanka ya tsaya a maimakon yaron a matsayin bawan shugabana, bari kuma yaron ya tafi tare da 'yan'uwansa.34Gama ta yaya zan tafi wurin mahaifina idan yaron ba ya tare da ni? Ina tsoron in ga mugun abin da zai zo bisa mahaifina."
Wannan yana fara sabon abu a cikin labarin.
Ƙuɗinsu shi ne tsabar kuɗi na azurfa wataƙila a cikin karamar jaka.
"Saka kofin azurfina"
An fahimci kalmar "ɗan'uwana". AT: "a cikin ƙaramar ɗan'uwanmu"
"Hasken safe ya nuna"
Ana amfani da wannan tambayar don zagin 'yan'uwa. AT: "Kun cutar da mu, bayan mun kyautata muku!"
Ana amfani da wannan tambayar don zagin 'yan'uwa.AT: "Kun dai san cewa wannan shi ne kofin da maigidana yake amfani da shi don sha da kuma sa'ar da gaya!"
"Ya yi magana da abin da Yusufuosef ya ce masa"
Anan "kalmomi" suna tsaye ne ga abin da aka faɗa. 'Yan'uwan sun ambaci wakilin a matsayin "maigidana." Wannan ita ce hanya madaidaiciyar magana da wani da ke da babban iko. Ana iya bayyana shi a cikin mutum na biyu. AT: "Me yasa kake faɗi haka, ya shugabana?"
'Yan uwan suna kiran kansu a matsayin "barorinku" da "su." Wannan ita ce hanya madaidaiciyar magana da wani da ke da babban iko. AT: "Ba za mu taɓa yin irin wannan abin ba!"
"mun zo muku da shi daga ƙasar Kan'ana"
'Yan uwan suna amfani da wata tambaya don jaddada cewa ba za su sace daga hannun ubangijin Masar ba. AT: "Don haka ba za mu taɓa ɗaukar komai daga gidan maigidanka ba!"
Ana amfani da waɗannan kalmomin tare tare da ma'ana cewa ba za su sace komai ba.
'Yan'uwa suna kiran kansu “barorinku”. Wannan ita ce hanya madaidaiciyar magana da wani da ke da babban iko. Ana iya bayyana shi a cikin mutum na farko. Hakanan, "an samo shi" za a iya bayyana shi a cikin tsari mai aiki. AT: "Idan kun gano cewa ɗayanmu ya saci ƙoƙon"
Kalmomin "maigidana" yana nufin wakilin ne. Ana iya bayyana wannan a cikin mutum na biyu. AT: "Kuna iya ɗauka mu ku bayi ku"
"saukar da buhu"
Ana iya fassara wannan azaman sabon jumla kuma cikin tsari mai aiki. AT: "Ma'aikacin sami ƙoƙon a cikin buhun Benyamin"
Kalmar "su" tana nufin 'yan'uwa. Wanke tufafin alama ce ta babban bakin ciki da baƙin ciki.
"Har yanzu dai Yosef yana wurin"
"suka fadi a gabansa." Wannan alama ce ta ‘yan’uwa da ke son ubangiji ya ji ƙansu.
Yosef yayi amfani da tambaya don tsauta wa 'yan'uwansa. AT: "Tabbas kun san cewa mutum kamar ni zai iya koyan abubuwa ta hanyar sihiri!"
Duk tambayoyin guda uku suna nufin dai-dai ne abu ɗaya. Suna amfani da waɗannan tambayoyin don jaddada cewa babu wani abin da za su iya faɗi don bayyana abin da ya faru. AT: "Ba mu da abin da za mu ce, ya shugabana. Ba za mu iya faɗi komai mai mahimmanci ba. Ba za mu iya baratar da kanmu ba."
Anan "gano" ba yana nufin Allah ne kawai ya gano abin da 'yan'uwa suka aikata ba. Wannan yana nufin Allah yana azabta su saboda abin da suka aikata. AT: "Allah yana yi mana horo game da zunubanmu na baya"
Anan "hannun" yana tsaye ga mutum gaba ɗaya. Hakanan, "an samo" za'a iya bayyana shi a cikin tsari mai aiki. AT: "wanda ya sami ƙoƙon ku"
Anan "hannun" yana tsaye ga mutum gaba ɗaya. Hakanan, "an samo" za'a iya bayyana shi a cikin tsari mai aiki. AT: "Mutumin da yake da ƙoƙo na"
"matso kusa"
Yahuda yana kiran kansa "bawanka." Wannan ita ce hanya madaidaiciyar magana da wani da ke da iko. Ana iya bayyana wannan a cikin mutum na farko. AT: "Bari ni, bawanka"
Kalmar "kunne" yana wakiltar mutum gaba ɗaya. AT: "yi magana da kai, maigidana"
Ana magana da fushi kamar ana cin wuta ne. AT: "ina roƙe ka kada ka yi fushi da ni, ni bawanka"
Yahuda ta kamanta maigidan da Fir’auna don ƙarfafa babbar ikon da ubangijin yake da shi. Hakanan yana nuna cewa yana son maigidan ya yi fushi kuma ya kashe shi. AT: "gama kai mai ƙarfi ne kamar Fir'auna kuma zai iya cewa sojojinka su kashe ni"
Wannan shi ne zance a cikin zance ne. Ana iya bayyana shi azaman magana kai tsaye. AT: "Kuma muka ce maigidana cewa muna da uba ... mahaifinsa yana ƙaunarsa"
Wannan shi ne zance a cikin zance ne. Ana iya bayyana shi azaman magana kai tsaye. AT: "Kuma ka ce wa bayinka cewa za mu zo da ƙaninmu dan uwanka domin ku gan shi"
Wannan shi ne zance a cikin zance ne. Ana iya bayyana shi azaman magana kai tsaye. AT: "A cikin mayar da martani, mun ce wa maigidana cewa saurayin ba zai iya ... uba zai mutu ba"
An ɗauka cewa mahaifinsu zai mutu saboda baƙin ciki.
Wannan shi ne zance a cikin zance ne. Ana iya bayyana shi azaman magana kai tsaye. AT: "Sai da kuka ce wa bayinku cewa sai dai idan autanmu ya zo tare da mu, ba za mu ƙara ganin ku ba."
Yahuda ya kira Yosef a matsayin "maigidana." AT: "mun fada masa abin da kuka ce, ya shugabana"
Wannan shi ne zance a cikin zance ne. Ana iya bayyana shi azaman magana kai tsaye. AT: "Sai muka ce masa ba za mu iya gangara zuwa Masar ba. Mun gaya masa cewa idan autanmu yana tare da mu ... yana tare da mu"
Anan "fuska" tana tsaye ga mutumin gaba ɗaya. AT: "don ganin mutumin"
Faɗin matakin uku wanda ya fara a aya ta 27 yana ci gaba. Yahuda ya ci gaba da ba da labarins ta Yosef.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Dabba na daji ya tsage shi"
Bayanin matakin uku wanda ya fara a aya ta 27 ya ƙare anan.
Faɗin matakin uku wanda ya fara da kalmomin "Bawanka ... ya ce mana," Kun san ... sonsa twoa biyu "a cikin aya ta 27 kuma ya ci gaba da kalmomin "sai na ce, Tabbas ... tunda" a cikin aya ta 28 ta ƙare a nan. Wataƙila kuna buƙatar canza ɗaya ko fiye da waɗannan matakan zuwa abubuwan da ba kai tsaye ba. AT: "Ga abin da bawanka mahaifina ya ce mana:" Kun dai san matata ta haifa mini 'ya'ya biyu. Wani daga cikinsu ya fita daga wurina sai na ce hakika ya tsage, kuma ban gan shi ba tun yanzu. Yanzu idan kai ma ka ɗauke wannan guda ɗaya daga wurina, har wata cuta ta same shi, za ka saukar da gashina da baƙin ciki zuwa cikin Sheol." ko kuma "Bawanka mahaifina ya gaya mana cewa mun san cewa matarsa ta haifa masa 'ya'ya maza guda biyu. Ɗaya daga cikinsu ya fita daga gare shi, sai ya ce lalle wannan ɗan an ragargaza shi, kuma bai gan shi ba tun daga can sai ya ce idan har muka ɗauke wannan ɗin daga wurinsa, kuma wata masifa ta same shi, za mu zai saukar da launin toka da baqin ciki zuwa lahira."
Wannan yana wakiltar Yakubu kuma yana jaddada tsufarsa. AT: "ni, dattijo"
"Yaron ba ya tare da mu"
Mahaifin yana cewa zai mutu idan ɗansa ya mutu ana maganar kamar ransu biyu da ɗaure a zahiri. AT: "tunda ya ce zai mutu idan yaron bai dawo ba"
''Saukar da ... zuwa cikin Lahira" hanya ce da za su sa shi ya mutu kuma ya tafi Lahira. Yayi amfani da kalmar "ƙasa" saboda galibi an gaskata cewa Lahira wani wuri ne ƙarƙashin ƙasa. AT: "Kuma za mu sa tsohon mahaifinmu ya mutu da bakin ciki"
Ana ɗauka cewa mutum mai laifi ne kamar "laifi" wani abu ne da mutum yake ɗauka. AT: "sannan mahaifina zai iya zarge ni"
Yahuda ya yi amfani da tambaya don ƙarfafa baƙin cikin da zai samu idan Benyamin bai koma gida ba. AT: "Ba zan iya komawa wurin ubana ba idan saurayin ba ya tare da ni."
Ana magana da mutumin da ke fama da bala'i kamar "mugunta" abubuwa ne da ke kan mutum. AT: "Ina jin tsoron ganin mahaifina zai wahala"
1Daga nan Yosef bai iya kame kansa ba a gaban dukkan bayin dake tsaye a gefensa. Ya ce da ƙarfi, "Kowa ya bar ni tilas. "Babu bawan da ya tsaya a gefensa sa'ad da Yosef ya sanar da kansa ga 'yan'uwansa.2Ya yi kuka da ƙarfi, Masarawa suka ji, gidan Fir'auna kuma suka sami labari.3Yosef ya cewa 'yan'uwansa, "Ni ne Yosef. Har yanzu mahaifina nada rai?" 'Yan'uwansa ba su iya amsa masa ba, domin sun gigice a gabansa.4Daga nan Yosef ya cewa 'yan'uwansa, "Ku zo kusa da ni, ina roƙon ku." Suka zo kusa da shi. Ya ce, "Ni ne Yosef ɗan'uwanku, wanda kuka sayar zuwa cikin Masar.5Kada kuyi baƙinciki ko kuji haushin kanku saboda kun sayar da ni zuwa nan, domin Allah ya aiko ni ne gaba da ku saboda a ceci rai.6Domin shekaru biyu kenan yunwa na cikin ƙasar, har yanzu kuma akwai shekaru biyar inda ba za a yi huɗa ko girbi ba.7Allah ya aiko ni gaba da ku domin ya adana ku a matsayin ragowa a duniya, ya kuma ajiye ku da rai ta wurin babbar kuɓutarwa.8Saboda haka yanzu ba ku ne kuka aiko ni nan ba amma Allah ne, kuma ya maida ni uba ga Fir'auna, shugaban dukkan gidansa, kuma mai mulki a cikin dukkan ƙasar Masar.9Ku yi hanzari ku tafi wurin mahaifina ku ce masa, 'Wannan ne abin da ɗanka Yosef yace, "Allah ya maida ni shugaban dukkan Masar. Ka gangaro zuwa gare ni, kada ka yi jinkiri.10Zaka zauna a ƙasar Goshen, zaka kuma kasance kusa da ni, kai da 'ya'yanka da 'ya'yan 'ya'yanka, da garkunan tumakinka dana awaki da garkunan shanunka, da dukkan abin da kake da shi.11Zan biya buƙatunka a can, domin har yanzu akwai shekaru biyar na yunwa, domin kada ku kai ga talaucewa, kai, da gidanka, da dukkan abin da kake da shi."'12Duba, idanunku sun ga ni, da idanun ɗan'uwanku Benyamin, cewa bakina ne ya yi magana da ku.13Zaku gayawa mahaifina game da dukkan ɗaukakata a Masar da dukkan abin da kuka gani. Zaku yi hanzari ku kawo mahaifina a nan."14Ya rungume wuyan ɗan'uwansa Benyamin ya kuma yi kuka, Benyamin kuma ya yi kuka a wuyansa.15Ya sumbaci dukkan 'yan'uwansa kuma ya yi kuka a kansu. Bayan wannan 'yan'uwansa suka yi magana da shi.16Aka faɗi labarin al'amarin a gidan Fir'auna: "'Yan'uwan Yosef sun zo." Abin ya gamshi Fir'auna da bayinsa sosai.17Fir'auna ya cewa Yosef, "Ka cewa 'yan'uwanka, 'Ku yi haka: Ku yi wa dabbobinku kaya ku kuma tafi ƙasar Kan'ana.18Ku ɗauko mahaifinku da gidanku dukka ku kuma zo wurina. Zan baku nagartar ƙasar Masar, kuma zaku ci dausayin ƙasar.'19Yanzu an umarce ku, 'Ku yi haka, ku ɗauki kekunan shanu daga ƙasar Masar domin 'ya'yanku domin matayenku kuma. Ku kuma ɗauko mahaifinku ku zo.20Kada ku damu da mallakokinku, domin nagartar dukkan ƙasar Masar taku ce."'21'Ya'ya maza na Isra'ila suka yi haka. Yosef ya basu kekunan shanu, bisa ga dokar Fir'auna, ya kuma basu guzuri domin tafiyar.22Ga dukkan su ya ba kowanne mutum canjin tufafi, amma ga Benyamin ya bayar da azurfa ɗari uku da canjin tufafi biyar.23Ya aika wannan domin mahaifinsa: jakuna goma ɗauke da kyawawan abubuwan Masar; da matan jakuna goma ɗauke da hatsi, gurasa, da sauran kayan masarufi domin mahaifinsa domin tafiyar.24Sai ya sallami 'yan'uwansa suka kuma yi tafiyarsu. Ya ce masu, "Ku tabbatar cewa ba ku yi faɗa ba a kan hanya."25Suka tafi daga Masar suka zo ƙasar Kan'ana, ga Yakubu mahaifinsu.26Suka gaya masa cewa, "Yosef yana nan da rai, kuma shi ne shugaba bisa dukkan ƙasar Masar." Zuciyarsa ta yi mamaki, domin bai gaskata da abin da suka faɗa masa ba.27Suka gaya masa dukkan maganganun Yosef da ya faɗi masu. Sa'ad da Yakubu ya ga kekunan shanun da Yosef ya aiko su da su, ruhun Yakubu mahaifinsu ya farfaɗo.28Isra'ila yace, "Ya isa. Yosef ɗana yana nan da rai. Zan tafi in gan shi kafin in mutu."
Wannan yana nufin bai iya sarrafa motsin zuciyar sa ba. Ana iya bayyana shi da kyau. AT: "yana shirin fara kuka"
"kusa da shi"
Anan "gidan" yana tsaye ga mutane ne a gidan Fir'auna. AT: "kowa a gidan Fir'auna"
"firgita da shi"
Ana iya bayyana ma'anar ma'ana sosai. AT: "wanda kuka sayar a matsayin bawa ga dan kasuwar da ya kawo ni ƙasar Masar"
"kada ku damu"
Ana iya bayyana ma'anar ma'ana sosai. AT: "da kuka sayar da ni a matsayin bawa, kun aiko ni nan ƙasar Masar"
Anan "rayuwa" tana wakiltar mutanen da Yosef ya ceci daga mutuwa lokacin yunwar. AT: "don haka zan iya ceci rayukan mutane da yawa"
"za a yi shekara biyar ba tare da an shuka girbi ko girbi ba." A nan "ba ya yin huɗa ko girbi" tabbatacce ne cewa har yanzu albarkatun gona ba za su yi girma ba saboda yunwar. AT: "kuma yunwar za ta ƙara shekaru biyar"
"don kada kai da danginku ku halaka gaba ɗaya daga duniya" ko kuma ku tabbata cewa zuriyarsu za su rayu "
AT: "don kiyaye ku da rai ta hanyar cetarku cikin ƙarfi"
Yosef yana ba da shawara da taimakon Fir'auna ana magana kamar dai Yosef mahaifin Fir'auna ne. AT: "ya maishe ni jagora zuwa ga Fir'auna" ko "ya maishe ni mai ba da shawara a kan Fir'auna"
Anan "gidan" yana tsaye ga mutanen da suke zaune a fadarsa. AT: "na gidansa duka" ko "na gidansa duka"
"AT: "Ku koma wurin mahaifina"
Wannan shi ne zance a cikin zance ne. Ana iya bayyana shi azaman magana kai tsaye. AT: "Ka faɗa masa cewa ɗansa Yosef ya ce Allah ya maishe shi ubangijin duka Masarawa, saboda haka dole ne ya gangara zuwa wurin Yosef ba da jinkiri ba. Zai zauna a ƙasar Goshen, zai kuma kasance kusa da Yosef, shi da 'ya'yansa, da garkunansa, da garkunansa, da abin da yake da shi.
Wannan yana magana game da "talauci" kamar dai makoma ne. AT: "ɓacewa" ko "matsananciyar yunwa"
Kalmar "idanu" tana tsaye ne ga mutumin. AT: "Duk ku da Benyamin za ku iya gani"
Kalmar “baki” tana tsaye ne ga dukan mutumin. AT: "Ni ne Yosef, zan yi magana da ku"
"yadda jama'ar Masar suka girmama ni"
AT: "Mahaifina anan gare ni"
"Yosef ya rungumi ɗan'uwansa Benyamin, dukansu kuma suka yi kuka"
A tsohuwar Gabas ta Tsakiya, abu ne na yau da kullun gaishe dangi da sumba. Idan yarenku yana da gaisuwa mai nuna soyayya ga dangi, yi amfani da hakan. Idan ba haka ba, yi amfani da abin da ya dace.
Wannan yana nufin Yosef yana kuka yayin da ya sumbace su.
A da, sun ji tsoron yin magana. Yanzu suna jin za su iya magana da yardar rai. Ana iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayanin a bayyane. AT: "Bayan haka 'yan uwansa sun yi magana da shi kyauta"
Wannan shi ne zance a cikin zance ne. Ana iya bayyana shi azaman magana kai tsaye. Hakanan za'a iya bayyana shi a cikin tsari mai aiki. AT: "Dukkanin gidan Fir'auna sun ji cewa 'yan'uwan Yusufu sun zo."
Wannan yana nufin fadar Fir'auna.
"Zan ba ku ƙasar mafi kyau a Masar"
Mafi kyawun abincin da ƙasa ke samarwa ana magana da ita kamar dai ƙashin ƙasar ne. AT: "Za ku ci abinci mafi kyau a cikin ƙasa"
Fir'auna ya ci gaba da gaya wa Yosef abin da zai faɗa wa 'yan'uwansa.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Na kuma umurce ku da ku faɗa musu" ko "kuma in gaya masu"
"Sarurrukan motoci" kekunan ne masu ƙafafun biyu ko huɗu. Dabbobi suna jan kekunan.
"ya basu abinda suke bukata domin tafiya"
Kowane mutum ya sami rukunin tufafi banda Benyamin da ya karɓi riguna 5.
"azurfa guda 300"
An hada jakuna a matsayin wani ɓangare na kyautar.
Ma'anar mai yiwuwa sun hada da 1) "kada ku yi jayayya" da 2) "kada ku firgita"
A nan "ƙasar Masar" tana tsaye ne ga mutanen Masar. AT: "Yana mulkin duka mutanen Masar"
Anan "zuciya" tana tsaye ga mutum gaba ɗaya. AT: "ya yi mamaki" ko "ya yi mamaki sosai"
"bai yarda cewa abin da suka fada gaskiya ne ba"
"Sun gaya wa Yakubu"
"Duk abin da Yosef ya faɗa musu"
Kalmar "ruhu" tana tsaye ne ga dukan mutum. AT: "Yakubu mahaifinsu ya murmure" ko "mahaifinsu Yakubu ya yi matukar farin ciki"
1Isra'ila ya kama hanyarsa da dukkan abin da yake da shi, ya kuma tafi Bayersheba. A can ya miƙa hadayu ga Allah na mahaifinsa Ishaku.2Allah ya yi magana da Isra'ila a cikin wahayi da dare, cewa, "Yakubu, Yakubu." Ya ce, "Ga ni nan."3Ya ce, "Ni ne Allah, Allah na mahaifinka. Kada ka ji tsoron gangarawa zuwa Masar, domin a can zan maida kai babbar al'umma.4Zan gangara da kai zuwa cikin Masar, kuma tabbas zan sake hawo da kai kuma Yosef zai rufe idanunka da hannunsa."5Yakubu ya taso daga Bayersheba. 'Ya'yan Isra'ila suka tafi da Yakubu mahaifinsu, 'ya'yansu, da matayensu, a cikin kekunan shanun da Fir'auna ya aiko a ɗauke shi.6Suka ɗauki dabbobinsu da mallakarsu da suka tattara a ƙasar Kan'ana. Suka zo cikin Masar, Yakubu da dukkan zuriyarsa tare da shi.7Ya taho Masar tare da 'ya'yansa maza da 'ya'yan 'ya'yansa maza, da 'ya'yansa mata da 'ya'yan 'ya'yansa mata, da dukkan zuriyarsa.8Waɗannan ne sunayen 'ya'yan Isra'ila waɗanda suka zo Masar: Yakubu da 'ya'yansa, Ruben, ɗan fãrin Yakubu;9'ya'yan Ruben, Hanok, Fallu, Hezron, da Karmi;10'ya'yan Simiyon, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar, da Shawul, ɗan Bakan'aniya;11'ya'yan Lebi kuma, Gashon, Kohat, da Merari.12'Ya'yan Yahuda su ne Er, Onan, Shela, Ferez, da Zera, (amma Er da Onan sun mutu a ƙasar Kan'ana). 'Ya'yan Ferez su ne Hezron da Hamul.13'Ya'yan Issaka su ne Tola, Fuwa, Lob, da Shimron;14'ya'yan Zebulun sune Sered, Elon, da Yalil15Waɗannan ne 'ya'yan Liya waɗanda ta haifa wa Yakubu a Faddan Aram, tare da ɗiyarsa Dina. Lissafin 'ya'yansa maza da mata talatin da uku.16'Ya'yan Gad su ne Zefon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi, da Areli.17'Ya'yan Asha su ne Imna, Ishba, Ishbi, da Beriya; kuma Sera ce 'yar'uwarsu. 'Ya'yan Beriya su ne Heba da Malkiyel18Waɗannan ne 'ya'yan Zilfa, wadda Laban ya bayar ga ɗiyarsa Liya. Waɗannan 'ya'ya ta haifa wa Yakubu - sha shida dukka dukkansu.19'Ya'yan Rahila matar Yakubu su ne Yosef da Benyamin.20A Masar Asenat ɗiyar Fotifera firist na On, ta haifa wa Yosef Manasse da Ifraim.21'Ya'yan Benyamin su ne Bela, Beka, Ashbel, Gera, Na'aman, Ehi, Rosh, Muffim, Huffim, da Ard.22Waɗannan ne 'ya'yan Rahila da aka haifa wa Yakubu - sha huɗu dukkan su.23Ɗan Dan shi ne Hushim.24'Ya'yan Naftali su ne Yaziyel, Guni, Yeza, da Shillem.25Waɗannan ne 'ya'yan da Bilha ta haifa wa Yakubu, wadda Laban ya bayar ga Rahila ɗiyarsa - bakwai dukka dukkansu.26Dukkan waɗanda suka tafi Masar tare da Yakubu, waɗanda ke zuriyarsa, ba a ƙidaya da matayen 'ya'yan Yakubu ba, su sittin da shida ne dukkansu.27Tare da 'ya'yan Yosef maza biyu da aka haifa masa a Masar, yawan iyalinsa da suka tafi Masar su saba'in ne dukkansu.28Yakubu ya aiki Yahuda zuwa ga Yosef saboda ya nuna masa hanya a gabansa ta zuwa Goshen, suka kuma zo ƙasar Goshen.29Yosef ya shirya karusarsa ya kuma tafi domin ya sami Isra'ila mahaifinsa a Goshen. Ya gan shi, ya rungumi wuyansa, ya kuma yi kuka na dogon lokaci bisa wuyansa.30Isra'ila yace wa Yosef, "Yanzu bari in mutu, tunda na ga fuskarka, cewa kana nan da rai."31Yosef ya cewa 'yan'uwansa da gidan mahaifinsa, "Zan tafi in gaya wa Fir'auna, cewa, "Yan'uwana da gidan mahaifina, waɗanda suke a ƙasar Kan'ana, sun zo wurina.32Mutanen makiyaya ne, domin suna kiwon dabbobi ne. Sun kawo garkunan tumakinsu dana awakinsu, da garkunan shanunsu, da dukkan abin da suke da shi.'33Zai kasance, sa'ad da Fir'auna zai kira ku ya yi tambaya, 'Mene ne sana'arku?'34To zaku ce masa, 'Bayinka masu kiwon dabbobi ne tun daga ƙuruciyarmu har zuwa yanzu, dukkanmu, da ubanninmu.' Ku yi haka domin ku zauna a ƙasar Goshen, domin kowanne makiyayi haramtacce ne ga Masarawa."
"ya zo Biyasheba"
"Ee, Ina sauraro"
Kalmar “ku” yana nufin Yakubu. Anan Yakubu yana nufin zuriyarsa waɗanda zasu zama babbar al'umma. AT: "Zan ba ku zuriya masu yawa, kuma za su zama babbar al'umma"
"zuwa Masar"
Kalmomin "rufe idanunka da nasa hannun" wata hanya ce ta cewa Yosef zai kasance lokacin da Isra'ila ta mutu kuma Yosef ne zai rufe idanun Yakubu a lokacin mutuwarsa. AT: "Yosef zai kasance tare da ku a lokacin mutuwarku"
"tashi daga"
"sun samo" ko "sun sami"
"Yakubu ya kawo tare da shi"
Wannan yana nufin sunayen mutanen da marubucin ke shirin lissafawa.
Waɗannan duk sunayen mutane ne.
Waɗannan duk sunayen mutane ne.
Wanna sunan mace.
A nan "'ya' ya 'da' ya 'mata" suna nufin' ya'yan Yakubu, 'ya'yansa mata, da jikokinsu waɗanda ke da dangantaka da Liya. AT: "Gaba ɗaya yana da 'ya'ya maza 33, mata, da jikoki 33"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan sunan mace. (Duba: translate names)
Wannan sunan mace.
Waɗannan 'ya'ya ta haifa wa Yakubu - sha shida dukka dukkansu
Wannan sunan mace.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan yana nufin 'ya'ya maza 14 da jikokin da suke da alaƙa da Rahila.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan sunan mace.
Wannan yana nufin yara 7 da jikokinsu waɗanda ke da alaƙa da Bilhah.
"nuna musu hanyar Goshen"
Anan "Yosef" yana tsaye ga bayinsa. AT: "Barorin Yosef sun shirya karusarsa kuma Yusufu ya hau"
An yi amfani da kalmar "hau" saboda Yosef yana tafiya zuwa hawa mafi girma don saduwa da mahaifinsa. AT: "ya haɗu da Isra'ila"
"yafa hannun mahaifinsa, yayi ta kuka tsawon lokaci"
"Yanzu na shirya don mutu" ko "Yanzu zan mutu cikin farin ciki"
Anan "fuska" tana tsaye ga mutumin gaba ɗaya. Yakubu yana bayyana farin ciki da ganin Yosef. AT: "tunda na sake ganinku da rai"
Anan "gidan" yana tsaye ga danginsa. AT: "dangin mahaifinsa" ko "gidan mahaifinsa"
Ya zama ruwan dare gama amfani da kalmar "hau sama" yayin da kake nufin wani zaiyi magana da wani mai iko.AT: "Zan je in gaya wa Fir'auna"
Ana amfani da wannan kalmar anan don nuna alama ga wani muhimmin abin da zai faru a cikin labarin. Idan harshenku yana da hanyar yin wannan, zaku iya tunanin amfani da shi anan.
Wannanzance a cikin zance ne. Ana iya bayyana shi azaman magana kai tsaye. AT: "lokacin da Fir'auna ... ya tambaya menene sana'arku, da za ku iya cewa kun kasance masu kiwon dabbobi tun ƙuruciyarku har zuwa yau, ku da ubanninku."
AT: "Masarawa suna tunanin makiyaya abin ƙyama ne"
1Daga nan Yosef ya shiga ya gaya wa Fir'auna, "Mahaifina da 'yan'uwana, da garkunan tumakinsu da na awaki, da garkunan shanunsu, da dukkan abin da ke nasu, sun iso daga ƙasar Kan'ana. Duba, suna ƙasar Goshen."2Ya ɗauki biyar daga cikin 'yan'uwansa ya kuma gabatar da su ga Fir'auna.3Fir'auna ya cewa 'yan'uwansa, "Mene ne sana'arku?" Suka cewa Fir'auna, "Bayinka makiyaya ne, kamar kakanninmu."4Daga nan suka cewa Fir'auna, "Mun zo ɗan zama ne a ƙasar. Babu makiyaya domin garkunan bayinka, saboda yunwar ta yi tsanani a ƙasar Kan'ana. To yanzu, muna roƙonka bari bayinka su zauna a ƙasar Goshen."5Daga nan Fir'auna ya yi magana da Yosef, ya ce, "Mahaifinka da 'yan'uwanka sun zo wurinka.6Ƙasar Masar na gabanka. Ka zaunar da mahaifinka da 'yan'uwanka a lardi mafi kyau, ƙasar Goshen. Idan ka san maza ƙwararru daga cikinsu, ka sanya su kiwon dabbobi na."7Daga nan Yosef ya shigo da Yakubu mahaifinsa ya kuma gabatar da shi ga Fir'auna. Yakubu ya albarkaci Fir'auna.8Fir'auna ya cewa Yakubu, "Tsawon rayuwarka nawa?"9Yakubu ya cewa Fir'auna, "Shekarun yawace-yawace na ɗari ne da talatin. Shekarun rayuwata kima ne kuma cike da wahala. Ba su kai yawan na kakannina ba."10Daga nan Yakubu ya albarkaci Fir'auna ya kuma fita daga gabansa.11Daga nan Yosef ya zaunar da mahaifinsa da 'yan'uwansa. Ya ba su gunduma a ƙasar Masar, yankin ƙasar mafi kyau, a ƙasar Ramesis, kamar yadda Fir'auna ya umarta.12Yosef ya wadata abinci domin mahaifinsa, da 'yan'uwansa, da dukkan gidan mahaifinsa, bisa ga lissafin masu dogara da su.13Yanzu dai babu abinci a dukkan ƙasar; domin yunwar ta yi tsanani. Ƙasar Masar da ƙasar Kan'ana suka lalace saboda yunwar.14Yosef ya tattara dukkan kuɗaɗen dake ƙasar Masar da ƙasar Kan'ana, ta wurin sayar da hatsi ga mazaunan. Daga nan Yosef ya kawo kuɗaɗen fãdar Fir'auna.15Sa'ad da aka gama kashe dukkan kuɗaɗen dake ƙasashen Masar da Kan'ana, dukkan Masarawa suka zo wurin Yosef suka ce, "Ka bamu abinci! Ya ya zamu mutu a gabanka saboda kuɗaɗenmu sun ƙare?"16Yosef yace, "Idan kuɗaɗenku sun ƙare, ku kawo dabbobinku ni zan kuma baku abinci misanya domin dabbobinku."17Sai suka kawo dabbobinsu wurin Yosef. Yosef ya basu abinci misanya domin dawakai, domin garkunan tumaki da awaki, domin garkunan shanu, domin kuma jakuna. A wannan shekarar ya ciyar dasu da abinci a misanyar dukkan dabbobinsu.18Sa'ad da shekara ta ƙare, suka zo wurinsa a shekara ta gaba suka kuma ce masa, "Ba zamu ɓoye ba daga shugabanmu cewa kuɗaɗenmu sun tafi, kuma garkunan shanun na shugabanmu ne. Babu abin da ya rage a idanun shugabana, sai jikkunanmu kawai da ƙasarmu.19Yaya zamu mutu a gaban idanunka, dukkanmu da ƙasarmu? Ka saye mu da ƙasarmu a musanya domin abinci, mu da ƙasarmu mu zama bayi ga Fir'auna. Ka bamu iri domin mu rayu kada mu mutu, kada kuma ƙasar ta zama kufai."20Saboda haka Yosef ya saye wa Fir'auna dukkan ƙasar Masar. Domin kowanne Bamasare ya sayar da gonarsa, saboda yunwar ta yi tsanani sosai. Ta wannan hanya, ƙasar ta zama ta Fir'auna.21Game da mutanen, ya mayar dasu bayi daga ƙarshen kan iyakar Masar zuwa ɗaya ƙarshen.22Ƙasar firistoci ce kawai Yosef bai saya ba, saboda ana ba firistocin albashi. Suna ci daga kason da Fir'auna yake ba su. Saboda haka basu sayar da gonarsu ba.23Daga nan Yosef ya cewa mutanen, "Duba, na saye wa Fir'auna ku da ƙasarku. Yanzu ga iri domin ku, zaku kuma noma ƙasar.24Da kaka tilas ku bada kaso biyar ga Fir'auna, kashi huɗu kuma zai zama naku, domin iri na gonaki domin kuma abinci domin gidajenku da 'ya'yanku."25Suka ce, "Ka ceci rayukanmu. Bari mu sami tagomashi a idanunka. Zamu zama bayin Fir'auna."26Sai Yosef ya maida haka doka mai aiki har wayau a ƙasar Masar, cewa kashi biyar na Fir'auna ne. Ƙasar firistoci ce kawai ba ta zama ta Fir'auna ba.27Saboda haka Isra'ila ya zauna a ƙasar Masar, a ƙasar Goshen. Mutanensa suka sami mallakar wurin. Suka hayayyafa suka ruɓanɓanya sosai.28Yakubu ya zauna a ƙasar Masar shekaru sha bakwai, saboda haka shekarun rayuwar Yakubu ɗari da arba'in da bakwai ne.29Sa'ad da lokaci ya kusato da Isra'ila zai mutu, ya kira ɗansa Yosef yace masa, "Yanzu idan na sami tagomashi a idanunka, ka sanya hannunka a ƙarƙashin cinyata, ka kuma nuna mani aminci da yarda. Ina roƙon ka kada ka bizne ni a Masar.30Sa'ad da na yi barci da ubannina, zaka ɗauke ni ka fitar da ni daga Masar ka kuma bizne ni a maƙabartar kakannina." Yosef yace, "Zan yi yadda ka ce."31Isra'ila yace, "Ka rantse mani," Yosef kuma ya rantse masa. Daga nan Isra'ila ya rusuna a bisa kan gadonsa.
"Barorinka suna kiwon garken"
"mu da ubanninmu" ko "mu da kakanninmu"
"Mun zo don mu jima a Masar"
"Babu ciyawa da za ku ci"
"Ƙasar Masar ta buɗe muku" ko kuma "Duk ƙasar Masar tana wurin ku"
"Ku zaunar da mahaifinku da 'yan'uwanku a ƙasar Goshen, wurin da ya fi kyau."
Anan "mai albarka" yana nufin nuna sha'awar abubuwa masu kyau da fa'ida don faruwa ga wannan mutumin.
"Shekaranku nawa?"
Kalmomin "shekarun tafiya na" yana nufin tsawon lokacin da ya rayu a duniya yana tafiya daga wuri zuwa wani. AT: "Na yi tafiya cikin ƙasa tsawon shekaru 130"
Yakubu yana nufin rayuwarsa takaice idan aka kwatanta da rayuwar Ibrahim da Ishaku
"A sa'an nan Yosef ya kula da mahaifinsa da 'yan'uwansa, ya taimaka musu su kafa inda za su zauna"
Wannan shi ne wani sunan ƙasar Goshen.
Anan, kalmar "dogara" tana nufin ƙananan yara a cikin dangi. AT: "gwargwadon yawan yaran da ke cikin danginsu"
Wannan kalmar ana amfani da ita anan don alamar hutu a cikin babban labarin labarin. Anan marubucin ya fara ba da sabon ɓangaren labarin.
Wannan yana nufin mutanen da ke zaune a waɗannan ƙasashe. AT: "Mutanen Masar da mutanen Kan'ana"
"ya zama na bakin ciki da rauni"
"Mutanen Masar da na Kan'ana sun kashe dukiyoyinsu don siyan hatsi daga hannun Yosef"
Anan "filaye" suna wakiltar mutanen da suke zaune a ƙasashe. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Lokacin da mutanen Masar da na Kan'ana suka yi amfani da dukiyoyinsu"
Mutanen sun yi amfani da wata tambaya don nuna irin tsananin tsananin son sayen abinci. Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin bayani. AT: "Mu na roƙon ka, kada ka bari mu mutu saboda mun cinye kuɗinmu duka!"
Anan "burodi" yana tsaye ga abinci gaba ɗaya. AT: "Ya ba su abinci" ko "Ya ba su abinci"
"mutane suka zo wurin Yosef"
Mutanen suna kiran Yosef a matsayin "maigidana." Wannan ita ce hanya madaidaiciyar magana da wani da ke da babban iko. Ana iya bayyana shi a cikin mutum na biyu. AT: "Ba za mu ɓoye muku ba, maigidanmu" ko "Ba za mu ɓoye muku ba"
Anan “gani” yana wakiltar Yosef da kansa. AT: "Ba mu da wani abin da za mu ba ka, ya maigidanmu"
Kalmar "idanu" tana nufin kallon Yosef. Mutanen sun yi amfani da wata tambaya don jaddada irin tsananin tsananin son sayen abinci. Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin bayani. AT: "Mu na roƙon ka, kar a yi tsaro kamar yadda muke mutuwa kuma ƙasarmu ta lalace!"
"Ƙasar ta zama tiwan Fir'auna"
"Amma bai sayi ƙasar firistoci ba"
“albashi” adadin kuɗi ne ko abinci da wani yakan bayar wa wani mutum a kai a kai. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Fir'auna ya bai wa firistoci abinci na abinci kowace rana"
"Sun ci daga abin da Fir'auna ya basu"
"domin ku yi shuka"
Kalmar "na biyar" ƙunshi juzu'i ne. AT: "A lokacin girbi za ku rarraba amfanin gonan zuwa kashi biyar. Kuna ba da kashi ɗaya ga Fir'auna don biyan kuɗi kuma kashi huɗu ɗinku na kanku ne"
Kuna iya bayyana a sarari bayanin da aka fahimta. AT: "don abinci ga gidajenku da abinci don yaranku"
Anan, idanu suna wakiltar gani, da gani suna wakiltar tunani ko hukunci. AT: "Ka yi farin ciki da mu"
"a kan ƙasar Misira" ko "a ko'ina cikin Misira"
Wannan yana nufin zuwa lokacin da marubucin yake rubuta wannan.
Kalmar "ya ninka" yayi bayanin yadda suke 'ya' ya 'ya. AT: "Suna da yara da yawa"
"shekaru 17"
"saboda haka Yakubu ya yi shekara 147"
Wannan yana magana game da lokaci kamar dai yana tafiya ya isa wani wuri. AT: "Lokacin da kusan Isra'ila ta mutu"
Anan “idanun” kalmomi ne don gani, kuma “gani” yana tsaye ne ga tunani ko ra'ayoyi. AT: "Idan na sami yardar ku" ko "Idan na gamsu ku"
Wannan aiki alamu ne na yin alkawari. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Farawa 24: 2.
Ana iya fassara sunayen sunaye "amincin" da "gaskene" azaman manufofi. AT: "bi da ni cikin aminci da aminci"
Kalmar nan "Ina roƙon ka" yana ƙara ƙarfafawa ga wannan buƙata.
Anan "barci" hanya ce mai ladabi don ma'anar mutuwa. AT: "Lokacin da na mutu kuma in shiga cikin dangi na waɗanda suka mutu a gabana"
"Ku yi mini alƙawarin" ko "Ku yi mini rantsuwa"
"yi masa alƙawarin" ko "yi masa rantsuwa"
1Sai ya kasance bayan waɗannan abubuwa, sai wani ya cewa Yosef, "Duba, mahaifinka bai da lafiya." Sai ya ɗauki 'ya'yansa maza biyu tare da shi, Manasse da Ifraim.2Sa'ad da aka gaya wa Yakubu, "Duba, ɗanka Yosef ya iso ya ganka," Isra'ila ya ƙoƙarta kuma ya zauna bakin gado.3Yakubu ya cewa Yosef, "Allah maɗaukaki ya bayyana a gare ni a Luz cikin ƙasar Kan'ana.4Ya albarkace ni ya kuma ce mani, 'Duba, zan sa ka hayayyafa, ka kuma ruɓanɓanya. Zan maida kai taron al'ummai. Zan bayar da wannan ƙasar ga zuriyarka a matsayin madawwamiyar mallaka.'5Yanzu 'ya'yanka biyu maza, waɗanda aka haifa maka a ƙasar Masar kafin in zo wurinka a Masar, nawa ne. Ifraim da Manasse zasu zama nawa, kamar yadda Ruben da Simiyon suke nawa.6'Ya'yan da zaka haifa bayan su zasu zama naka; za a lissafa su ƙarƙashin sunayen 'yan'uwansu a cikin gãdonsu.7Amma game da ni, sa'ad dana zo daga Faddan, cikin baƙincikina Rahila ta mutu a ƙasar Kan'ana a kan hanya, yayin da da sauran tazara a isa Ifrat. Na bizne ta a nan a kan hanyar zuwa Ifrat" (wannan ce, Betlehem).8Sa'ad da Isra'ila ya ga 'ya'yan Yosef maza, ya ce, "Na wane ne waɗannan?"9Yosef yace wa mahaifinsa, "'Ya'yana ne, waɗanda Allah ya bani a nan." Isra'ila yace, "Kawo su wurina, domin in sa masu albarka."10Yanzu dai idanun Isra'ila na kasawa saboda shekarunsa, har baya iya gani. Sai Yosef ya kawo su kusa da shi, kuma ya sumbace su ya kuma rungume su.11Isra'ila ya cewa Yosef, "Banyi tsammanin zan sa ke ganin fuskarka ba, amma Allah ya bar ni inga 'ya'yanka ma."12Yosef ya fito da su daga tsakanin guiwoyin Isra'ila, Daga nan kuma ya rusuna da fuskarsa ƙasa.13Yosef ya ɗauke su biyun, Ifraim a hannun damansa zuwa hannun hagun Isra'ila, Manasse kuma a hannun hagunsa zuwa hannun damar Isra'ila, ya kuma matso da su kusa da shi.14Isra'ila ya miƙa hannunsa na dama ya kuma ɗora bisa kan Ifraim, wanda shi ne ƙarami, hannun hagunsa kuma bisa kan Manasse. Ya gitta hannuwansa, domin Manasse shi ne ɗan fãri.15Isra'ila ya albarkaci Yosef, yana cewa, "Allah wanda a gabansa ubannina Ibrahim da Ishaku suka yi tafiya, Allah wanda ya lura da ni har ya zuwa yau,16mala'ikan da ya kiyaye ni daga dukkan bala'i, bari ya albarkaci waɗannan samari. Bari a raɗa sunana a sunansu, da sunan ubannina Ibrahim da Ishaku. Bari su yaɗu su yi tururu a bisa duniya."17Sa'ad da Yosef ya ga cewa mahaifinsa ya ɗora hannunsa na dama bisa kan Ifraim, bai ji daɗi ba. Ya ɗauke hannun mahaifinsa domin ya matsa da shi daga bisa kan Ifraim zuwa bisa kan Manasse.18Yosef yace wa mahaifinsa, "Ba haka ba, babana; domin wannan shi ne ɗan fãrin. Ka ɗora hannunka na dama bisa kansa."19Mahaifinsa ya ƙi ya kuma ce, "Na sani, ɗana, Na sani. Shi ma zai zama jama'a, shima kuma zai zama babba. Duk da haka ƙanensa zai fi shi girma, kuma zuriyarsa zasu zama al'ummai tururu."20Isra'ila ya albarkace su a wannan rana da waɗannan maganganu, "Mutanen Isra'ila zasu furta albarku da sunayenku suna cewa, 'Bari Allah ya maida ku kamar Ifraim kamar Manasse kuma'." Ta wannan hanya, Isra'ila ya sanya Ifraim gaba da Manasse.21"Isra'ila ya cewa Yosef, "Duba, ina gaf da mutuwa, amma Allah zai kasance tare da ku, zai kuma maida ku ƙasar ubanninku.22Game da kai, a matsayin wanda aka ɗora sama da 'yan'uwansa, Na baka gangaren tsaunin dana karɓe daga hannun Amoriyawa da takobina da kuma bakana."
Ana amfani da wannan kalmar anan don nuna alamar sabon ɓangaren labarin.
"Saboda haka Yosef ya karɓi"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Lokacin da wani ya gaya wa Yakubu"
"ɗanka Yosef ya zo wurinka"
Anan marubucin yayi magana akan Isra'ila tana gwagwarmayar zama akan gado kamar dai tana tara "ƙarfi" kamar yadda wani yake tara ainihin abubuwan. AT: "Isra'ila ta yi ƙoƙari sosai don zaune a kan gado" ko "Isra'ila ta yi fama yayin da yake zaune a kan gado"
Wannan sunan birni ne. Ka ga yadda ka fassara sunan wannan birni a cikin Farawa 28:18.
Kalmomin "ya ninka ku" ya yi bayani game da yadda Allah zai sa Yakubu ya sami ''ya 'yantu". AT: "Zan ba ku zuriya mai yawa"
A nan "ku" yana nufin Yakubu, amma yana wakiltar zuriyar Yakubu. AT: "Zan sa zuriyarka cikin al'ummai da yawa"
"mallaka ce ta dindindin"
Yankin Ifraimu da na Manassa kowanne zai sami kashi ɗaya daga cikin 'yan'uwan Yosef.
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) 'Ya'yan Yosef kuma su sami gādo bisa ga wani ɓangare na kabilan Ifraim da na Manasse ko 2) Za a ba Yosef rabe rabe tare da Ifraim da Manasse, sauran' ya'yan Yosef kuma za su gāji ƙasar. AT: "Game da gādonsu, za ku lissafa su a ƙarƙashin sunayen 'yan'uwansu"
Wannan wani suna ne na garin Betlahem. Ka ga yadda ka fassara sunan wannan birni a cikin Farawa 35:16.
'Ya'yan wa?
"Isra'ila ta sumbace su"
Anan "fuska" tana tsaye ga mutumin gaba ɗaya. Wani fassarar: "don sake ganin ku"
Lokacin da Yosef ya ɗora 'ya'yansa a cinyar Isra'ila ko gwiwowi alama ce da ke nuna cewa Isra'ila ta karbe su. Wannan ya ba wa yara haƙƙoƙin musamman na Yakubu.
Yosef ya sunkuyar da kansa don girmama mahaifinsa.
Yosef ya sa yaran a madadin Isra'ila ta sa hannun dama na Manasse. Manasse shi ne ɗan'uwan ɗan'uwansa, kuma daman ita ce alama ce za ta sami babbar albarka.
Anan "Yosef" kuma yana wakiltar Ifraim da Manasse. Tunda Yosef uba ne, shi kaɗai ne aka ambata anan.
Bautar Allah ana magana da ita kamar tana tafiya a gaban Allah. AT: "Allah wanda kakana Ibrahim da mahaifina Ishaku suka bauta wa"
Allah ya kula da Isra’ila kamar makiyayi yakan kula da tumakinsa. AT: "wanda ya lura da ni kamar makiyayi yana kula da dabbobinsa"
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) wannan yana nufin mala'ikan da Allah ya aiko don kare Yakubu ko 2) wannan yana nufin Allah wanda ya bayyana a cikin surar mala'ika don kare Yakubu.
"tsĩrar da ni"
Anan "suna" yana tsaye ne ga mutumin. Kalmomin "suna na a cikin su" wata karin managa ne na nufin ana ambaton mutum saboda wani. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Mutane su tuna da Ibrahim, da Ishaku, da ni saboda Ifraim da Manasse"
Anan "su" yana nufin Ifraim da Manasse, amma yana wakiltar zuriyarsu. AT: "Zasu sami zuriya da yawa waɗanda zasu rayu ko'ina cikin duniya"
Hannun dama alama ce ta babbar albarka da ɗan farin zai samu
A nan "Shi" yana nufin Manasse, amma yana wakiltar zuriyarsa. AT: "sonanka mafi tsufa zai sami zuriya masu yawa, kuma za su zama babbar jama'a"
"ran nan, yana cewa"
"Mutanen Isra'ila za su faɗi sunayen ku lokacin da suke sa wa wasu albarka"
Wannan zance a cikin zance ne. Ana iya bayyana shi azaman magana kai tsaye. AT: "ta sunayen ku. Za su roki Allah ya yi wasu kamar Ifraim da na Manasse"
Ana ambatar baiwa Ifraim babbar albarka da kuma fifita shi fiye da na Manasse kamar dai Isra'ila ta zahiri ta sanya Ifraim a gaban Manasse.
Wannan karin magana ne na nufin Allah zai taimaka kuma ya albarkaci jama'ar Isra'ila. AT: "Allah zai taimake ka" ko "Allah zai albarkace ka"
Anan "kawo" za'a iya fassara shi azaman "ɗauka."
"ƙasar kakanninku"
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) Yosef yana da fifiko da iko fiye da 'yan'uwansa kamar dai yana sama da su ne. AT: "A gare ku, wanda ya fi 'yan'uwanku girma, na ba da rafin dutsen" ko 2) Yakubu yana nufin yana ba Yosef ƙasa fiye da yadda yake baiwa' yan'uwan Yosef. AT: "A gare ku, Na ba ɗayan dutse guda ɗaya fiye da wanda na bai wa 'yan'uwanku. Na ba ku gangaren tsauni"
Anan "takobi" da "baka" suna tsaye don faɗa a cikin yaƙi. AT: "ƙasar da na yi gwagwarmayar karɓa daga hannun Amoriyawa"
1Daga nan Yakubu ya kirawo 'ya'yansa maza, ya kuma ce: "Ku tattara kanku tare, domin in gaya maku abin da zai faru daku a gaba.2Ku tattara kanku ku kuma saurara, ku 'ya'yan Yakubu. Ku saurari Isra'ila, mahaifinku.3Ruben, kai ne ɗan fãrina, ƙarfina, da farkon ƙarfina, ka yi fice wajen jamali, ka kuma yi fice wajen iko.4Marar kamewa kamar ruwan dake ambaliya, ba zaka yi muhimmanci ba, saboda ka hau bisa gadon mahaifinka. Daga nan ka gurɓata shi; ka hau bisa gadona.5Simiyon da Lebi 'yan'uwa ne. Makaman ta'addanci ne takubbansu.6Ya raina, kada ka zo cikin shawararsu; kada ka shiga cikin taruwarsu, domin zuciyata ta fi haka daraja sosai. Domin cikin fushinsu sun kashe mutane. Saboda annashuwa ne suka turke shanu.7Bari fushinsu ya la'ana, domin mai zafi ne - hasalarsu kuma domin mai tsanani ce. Zan rarraba su a Yakubu in kuma warwatsa su a Isra'ila.8Yahuda, 'yan'uwanka zasu yabe ka. Hannunka zai kasance bisa wuyan maƙiyanka. 'Ya'yan mahaifinka za su rusuna a gabanka.9Yahuda ɗan zaki ne. Ɗana, ka haura daga kamammunka. Ka duƙa, ka rarrafa kamar zaki, kamar zakanya. Wa zai kuskura ya tada kai?10Sandan sarauta ba za ta fita daga Yahuda ba, ko sandar mulki daga tsakanin ƙafafunsa, har sai Shilo ya zo. Al'ummai zasu yi masa biyayya.11Yana ɗaure jakinsa ga kuringar inabinsa, da ɗan jakinsa ga zaɓaɓɓiyar kuringar inabinsa, ya wanke tufafinsa cikin ruwan inabi, da alkyabbarsa cikin jinin inabi.12Idanunsa zasu yi duhu kamar ruwan inabi, haƙoransa kuma farare kamar madara.13Zebulun zai zauna a gaɓar teku. Zai zama masaukin jiragen ruwa, kuma kan iyakarsa za ta zarce har zuwa Sidon.14Issaka jaki ne mai ƙarfi, yana zaune a tsakiyar turakun tumaki.15Yana ganin wurin hutawa mai kyau da ƙasa mai gamsarwa. Zai sunkuyar da kafaɗarsa domin kaya ya kuma zama bawa domin hidimar.16Dan zai hukunta mutanensa a matsayin ɗaya daga cikin kabilun Isra'ila.17Dan zai zama maciji a gefen hanya, maciji mai dafi a tafarki dake cizon kofaton doki, saboda mahayinsa ya fãɗi ta baya.18Ina jiran cetonka, Yahweh.19Gad - mahaya zasu kai masa hari, amma zai kai masu hari ta diddigensu.20Abincin Asha zai zama wadatacce, zai kuma bayar da girke-girken sarauta.21Naftali sakakkiyar barewa ce; zai haifi kyawawan 'ya'ya.22Yosef mai hayayyafa ne, mai bayar da 'ya'ya ne, mai bayar da 'ya'ya dake gefen ƙorama wanda rassansa ke hawan katanga.23Maharba zasu kai masa hari, su kuma harbe shi, su firgita shi.24Amma bakansa zai tsaya dai-dai, kuma hannayensa zasu ƙware saboda hannayen Mai Iko na Yakubu, saboda sunan Makiyayi, Dutsen Isra'ila.25Allah na mahaifinka zai taimakeka kuma Allah Mai Iko Dukka zai albarkace ka da albarkun sararin sama, albarkun zurfafa dake kwance ƙarƙashin ƙasa, da albarkun nonna da mahaifa.26Albarkun mahaifinka sun fi albarkun duwatsun zamanin dã ko abubuwan marmari na tuddan dã. Bari su kasance bisa kan Yosef, har bisa rawanin dake kan yariman 'yan'uwansa.27Benyamin damisa ne mayunwaci. Da safe zai lanƙwame kamammensa, da yamma kuma zai raba ganimarsa."28Waɗannan ne kabilu sha biyu na Isra'ila. Wannan ne abin da mahaifinsu ya ce masu sa'ad da ya albarkace su. Kowannen su ya albarkace shi bisa ga albarkar da ta dace.29Daga nan ya umarce su ya ce masu, "Ina gaf da tafiya ga mutanena. Ku bizne ni tare da kakannina a kogon dake cikin gonar Ifron Bahittiye,30a cikin kogon dake cikin gonar Makfela, wadda ke kusa da Mamri a ƙasar Kan'ana, gonar da Ibrahim ya saya a matsayin maƙabarta daga hannun Ifron Bahittiye.31A nan ne aka bizne Ibrahim da matarsa Saratu; a nan ne suka bizne Ishaku da matarsa Rebeka; a nan ne kuma na bizne Liya.32Gonar da kogon dake cikin ta an saye su ne daga mutanen Het."33Da Yakubu ya gama waɗannan umarnai ga 'ya'yansa, ya ja ƙafafunsa cikin gadonsa, ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma tafi wurin mutanensa.
Wannan ya fara daga albarka na karshe ga Yakubu. Wannan ya ci gaba ta hanyar Farawa 49:27. An rubuta albarkun Yakubu cikin tsari na waƙa.
Dukkan jimlolin suna faɗi abu ɗaya ne don girmamawa. AT: "Ku zo ku saurari mahaifinka da kyau"
Yakubu yana nufin kansa ne a cikin mutum na uku. Ana iya bayyana shi a cikin mutum na farko. AT: "sonsa'ana. Ku saurare ni, mahaifinku"
Kalmomin "ɗan fari na, ƙarfina" da kuma “farkon ƙarfina” suna nufin abu ɗaya ne. Kalmomin "ƙarfin" da "ƙarfi" suna wakiltar ikon Yakubu ne na haihuwar yara. Kalmomin "ɗan fari" da "fara" yana nufin cewa Reuben ɗansa ne na fari. AT: "ɗan fãrina na farko bayan na zama mutum"
Ana iya bayyana wannan azaman sabon jumla. AT: "Kai ne kan gaba a daraja da ƙarfi" ko "Ka fi kowa girma cikin girma da iko"
Yakubu ya gwada Reuben da ruwa a cikin wata mai ƙarfi don tabbatar da cewa ba zai iya kame fushinsa ba kuma ba shi da kwanciyar hankali.
"Ba za ku kasance farkon cikin 'yan'uwanku ba"
Anan "gado" da "babban kujera" suna tsaye da ƙwarƙwarar Yakubu, Bilha. Yakubu yana magana ne lokacin da Ruben ya kwana da Bilha
Wannan baya nufin 'yan uwan juna ne ta hanyar haihuwa. Yakubu yana jaddada cewa sun yi aiki tare don kashe mutanen Shekem.
"Suna amfani da takobinsu su ji rauni kuma su kashe mutane"
Yakubu ya yi amfani da kalmomin "raina" da "zuciya" don nuna kansa kuma yana cewa wasu mutane, kuma wataƙila Allah ma, girmama shi sosai cewa ba ya son shiga tare da waɗanda suke yin niyyar mugunta.
Waɗannan jumla guda biyu suna ma'ana dai-dai ne. Yakubu ya hada su don jaddada cewa shi baya son shiga cikin mugayen tsare-tsarensu. AT: "Ba zan shiga tare da su don yin wani shiri ba"
Wannan yana nuni ga Simiyonu da Lebi masu lalata garkunan shanu kawai don nishaɗi.
Allah yana la'antar Simiyon da Lebi kamar ana zagin Allah da fushinsu. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ubangiji ya ce, ''Ni zan la'ane su saboda fushinsu mai zafi da kuma tsananin zafin fushinsu'' ko kuma "Ni, Ubangiji, zan la'ancesu saboda zafin fushinsu da tsabar zafin fushinsa”
Kalmar "Ni" tana nufin Allah. Kalmar "su" tana nufin Simiyon da Lebi amma sun kasance ma'anar kalmomin zuriyarsu. Kalmomin "Yakubu" da "Isra'ila" isharar suna daidai ne ga duka jama'ar Isra'ila. AT: "Zan rarrabe zuriyarsu kuma in warwatsa su cikin dukan mutanen Isra'ila"
Waɗannan maganganu guda biyu suna ma'ana abu ɗaya ne.
Wannan wata hanya ce ta "Za ku yi nasara a kan maƙiyanku."
Yakubu ya yi magana game da Yahuda kamar ɗan zaki ne. Yakubu yana ƙarfafa ƙarfin Yahuda. AT: “Yahuda kamar ɗan zaki ne”
"Kai ɗana, ka dawo daga cin abincikinka"
Yakubu ya yi amfani da tambaya don nuna yadda Yahuda ke tsoro ga sauran mutane. AT: "Ba wanda yake so ya tashe shi."
“Sandar” da “ma’aikatan” dogayen sanduna ne wadanda sarakuna suka kwashe su. Anan sune maganganu waɗanda suka tsaya ga ikon yin sarauta. “Yahuda” yana wakiltar zuriyarsa. AT: "Ikon sarauta zai kasance tare da zuriyar Yahuda koyaushe"
Ma'anar mai yiwuwa sune 1) "Shiloh" ma'ana "haraji." AT: "har sai al'ummai su yi masa biyayya kuma su kawo masa haraji" ko 2) "Shiloh" yana nufin garin Shilo. AT: "har sai mai mulki ya zo Shilo. Al'ummai za su yi masa biyayya" Mutane da yawa suna ɗaukar wannan annabci game da Almasihu, wanda yake daga zuriyar Sarki Dauda. Dauda ɗan zuriyar Yahuda ne
Anan "al'ummai" suna nufin mutane. AT: "Al'ummai za su yi masa biyayya"
Kalmomin biyu suna ma'ana abu ɗaya ne. An nuna cewa 'ya'yan inabine suna cike da'ya'yan inabin har ubangijin bai damu cewa jakin sa yana cin wasunsu ba.
Kalmomin biyu suna ma'ana abu ɗaya ne. Yana nuna cewa akwai inabi da yawa da zasu iya wanke tufafinsu a cikin ruwan 'ya'yan itace.
Wannan yana nufin launin idanun mutum zuwa launin jan giya. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) idanu masu duhu suna nufin idanuwa masu kyau ko 2) idanun mutane zasu yi ja daga shan giya mai yawa.
Wannan yana kwatanta launin hakoran mutum da farin launi na madara. Wannan ya nuna cewa za a sami wadatattun shanu masu ƙoshin lafiya za su sami madara da yawa da za su sha.
Wannan yana nufin zuriyar Zabaluna. AT: "Zuriyar Zebulun za su rayu"
Anan "Zai" yana tsaye ne ga biranen teku waɗanda mutanen Zebulun za su zauna ko gini. Waɗannan biranen za su ba da mafaka ga jiragen ruwa.
Yakubu yayi magana game da Issaka da zuriyarsa kamar dai jakai ne. Wannan ya nanata cewa za su yi aiki tuƙuru. AT: "'Ya'yan Issaka za su zama kamar jaki mai ƙarfi"
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) "kwance tsakanin fakitin da suke ɗauke da su" ko 2) "kwance tsakanin alƙalum tumakin." Ko yaya dai, Yakubu ya yi magana game da zuriyar Issaka kamar dai jakai ne waɗanda suka yi wahala kuma suna kwance don hutawa.
"wurin hutawa mai kyau ne, ƙasa kuma mai daɗi ce"
Kalmomin "tanƙwara kafada da ɗaukar nauyi" wata hanya ce da ke cewa "ku yi aiki tukuru don ɗaukar kaya"
"Zai yi aiki ga waɗansu a matsayin bayi"
Anan "Dan" yana tsaye ga zuriyarsa. AT: "Zuriyar Dan za ta yi hukunci a kan mutanenta"
Yakubu yayi magana game da Dan da zuriyarsa kamar dai macizai ne. Duk da cewa maciji karami ne, yana iya saukar da mahaya daga kan dokinsa. Don haka Dan duk da cewa ƙarami ne, yana da haɗari ga maƙiyanta. AT: "'Ya'yan Dan za su zama kamar maciji a gefen hanya"
Ana amfani da kalmar nan "ceto" azaman "adanawa." AT: "Ina jiran ka, Yahweh, ka cece ni
Anan "Gad" yana tsaye ga zuriyarsa. Anan "diddigensu" tana tsaye ga mayaƙan da ke tserewa daga zuriyar Gad.
Anan "Asha" yana tsaye ga zuriyarsa. Anan "mai arziki" wata hanya ce ta "mai daɗi."
A nan "Naftali" yana tsaye ga zuriyarsa. Yakubu ya yi magana game da zuriyar Naftali kamar dai bareyin mata ne wanda ke da 'yanci. Wannan na iya nanata cewa za su kasance masu saurin aika sakonni ne. AT: "'Ya'yan Naftali za su zama kamar barewa"
Anan "Yosef" yana tsaye ga zuriyarsa. Yakubu yayi magana game da su kamar suna reshe na itacen da ke ba da 'ya'ya da yawa. Wannan ya nanata cewa zasu ƙaru da yawa. AT: "Zuriyar Yosef ɗan riɓi ne mai riba"
Rassan da suka girma kuma suka fadada akan bango ana magana dasu kamar suna hawa.
Yakubu ya ci gaba da sa wa Yosef da zuriyarsa albarka.
Mutumin da yake riƙe baka da tsayayyiyar an yi maganarsa kamar an ɗaga baka zai ci gaba da zama. Hakan yana nuna yana riƙe ta har abada kamar yadda ya yi niyya ga maƙiyansa. AT: "Zai riƙe baka a tsaye kamar yadda ya nufa a kan maƙiyinsa"
Anan mutum yana wakiltar mutum da "hannayen" tunda an yi amfani dasu don riƙe baka. AT: "hannayensa za su yi ƙarfi yayin da yake burin bakansa"
Hannun "hannayen" suna bayyana ikon Yahweh. AT: "ikon Mai Iko"
Anan "suna" yana nufin mutum gaba ɗaya. AT: "saboda Makiyayi"
Yakubu yayi magana game da Yahweh kamar "Makiyayi ne." Wannan ya nanata cewa Ubangiji yana yi musu jagora kuma yana kiyaye mutanensa.
Yakubu ya yi maganar Yahwehkamar dai shi “Dutsen” ne da mutane za su hau hawa don neman lafiya daga maƙiya. Wannan ya nanata cewa Yahweh yana kiyaye mutanensa.
Yakubu ya ci gaba da sa wa Yusufu da zuriyarsa albarka.
Anan "ku" yana nufin Yosef wanda yake wakiltar zuriyarsa. AT: "ka taimaki zuriyarka ... ka sa musu albarka"
Anan "sama" na tsaye ne ga ruwan sama wanda ke taimakawa amfanin gona su yi girma.
A nan "mai zurfi" yana tsaye ga ruwa a ƙarƙashin ƙasa wanda ke ba da koguna da rijiyoyin.
Anan "ƙirji da mahaifa" suna tsaye don iyawar uwa suyi yara kuma su ciyar da su madara. :
Ma'anar asalin yare ba shi da tabbas. Wasu fassarorin Littafi Mai Tsarki suna da “kakana” maimakon “tsoffin tsauni”.
Anan "su" yana nufin albarkun mahaifinsa.
Yakubu yana so a ba da waɗannan albarkatu ga mafi mahimmancin zuriyarsa. AT: "a kan mahimmancin zuriyar Yosef"
"mafi mahimmancin 'yan'uwansa"
Anan "Benyamin" ma'anar magana ce ga zuriyarsa. Yakubu yayi magana game da zuriyar Benyamin kamar kyarkeke yake. Wannan ya nanata cewa za su zama mayaƙa masu zafin rai. AT: "'Ya'yan Benyamin za su zama kamar karnuka kishirwa"
"Waɗannan" suna nufin 'ya'yan Yakubu da aka ambata a cikin Farawa 49: 1-27. Kowane ɗa ya zama shugaban kabilarsa.
Anan kalmar "mai albarka" tana nufin magana ta albarka mai zuwa.
"Ya yi wa kowane ɗa yabon da ya dace"
"ya umurce su"
Wannan ita ce hanyar ladabi da ya ce yana gab da mutuwa. AT: "Zan kusan mutu"
Wannan sunan mutum ne. "Hittiyawa" na nufin "zuriyar Heth." Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Farawa 23: 8.
Wannan shi ne wani sabon abu domin birnin Hebron. Wataƙila an ba shi suna ne bayan Mamri, abokin Ibrahim da ya zauna a can. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Farawa 13: 16.
Yakubu ya ci gaba da magana da yaransa.
Za'a iya bayyana sayan a bayyane. AT: "a cikin Ibrahim aka sayo shi"
"daga Hittiyawa"
"sun gama koyar da 'ya'yansa maza" ko kuma "sun gama umarnin' ya'yansa maza"
Yakubu kuwa yana zaune a bakin gado. Yanzu, Yakubu ya juya ya saka ƙafafunsa a kan gado domin ya kwanta.
Wannan ita ce hanya mai ladabi na cewa mutum ya mutu.
Bayan Yakubu ya mutu, mutumin cikin shi ya tafi dai-dai da wurin danginsa waɗanda suka mutu a gabaninsa.
1Daga nan Yosef ya rikice, ya faɗi bisa fuskar mahaifinsa, ya kuma yi kuka a bisansa, ya kuma sumbace shi.2Yosef ya umarci bayinsa masu ilimin magani su nannaɗe mahaifinsa. Masu ilimin maganin suka nannaɗe Isra'ila da maganin hana ruɓewa.3Suka ɗauki kwana arba'in, domin wannan ne tsawon lokaci idan an naɗe gawa. Masarawa suka yi masa kuka na kwana saba'in.4Da kwanakin makoki suka cika, Yosef ya yi magana da gidan Fir'auna, cewa, "Idan yanzu na sami tagomashi a idanunku, ina roƙonku ku yi magana da Fir'auna, ku ce,5'Mahaifina yasa in yi rantsuwa, cewa, "Duba, ina gaf da mutuwa. Ka bizne ni a kabarin dana gina domin kaina a ƙasar Kan'ana. A can zaka bizne ni." Yanzu bari in haye in tafi, in kuma bizne mahaifina, daga nan kuma zan dawo."'6Fir'auna ya amsa, "Ka tafi ka bizne mahaifinka, kamar yadda yasa ka yi rantsuwa."7Yosef ya haye ya tafi bizne mahaifinsa. Dukkan 'yan majalisar Fir'auna suka tafi tare da shi - dattawan gidansa, dukkan manyan masu gari na ƙasar Masar,8tare da dukkan gidan Yosef da 'yan'uwansa, da gidan mahaifinsa. Amma 'ya'yansu, da garkunan tumakinsu, dana awaki, da garkunan shanunsu aka bari a ƙasar Goshen.9Karusai da mahaya dawaki suka tafi tare da shi. Babbar ƙungiyar mutane ce sosai.10Sa'ad da suka iso bakin masussukar Atad a ɗayan gefen Yodan, suka yi makoki da babban makoki da baƙinciki mai tsanani. A can Yosef ya yi makokin kwana bakwai domin mahaifinsa.11Sa'ad da mazauna ƙasar, Kan'aniyawa, suka ga makokin a masussukar Atad, suka ce, "Wannan taro ne na baƙinciki sosai ga Masarawa." Shi yasa ake kiran wurin da suna Abel Mizrayim, wanda ke tsallaken Yodan.12Daga nan 'ya'yan Yakubu suka yi masa kamar yadda ya umarta.13'Ya'yansa suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan'ana suka kuma bizne shi a kogon cikin gonar Makfela, kusa da Mamri. Ibrahim ya sayi kogon tare da gonar a matsayin maƙabarta. Ya saya ne daga Ifron Bahittiye.14Bayan da Yosef ya bizne mahaifinsa, sai ya koma cikin ƙasar Masar, shi, tare da 'yan'uwansa, da dukkan waɗanda suka raka shi bizne mahaifinsa.15Sa'ad da 'yan'uwan Yosef suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, suka ce, "To idan Yosef ya riƙe mu da fushi gãba da mu fa, kuma yana so ya yi mana cikakkiyar sakayya domin dukkan muguntar da muka yi masa?"16Sai suka umarci kasancewar Yosef, suka ce, "Mahaifinka ya bada umarni kafin ya mutu, cewa,17'Ku gaya wa Yosef haka, "Mu na roƙonka ka gafarta laifin 'yan'uwanka da zunubinsu sa'ad da suka yi maka mugunta."' Yanzu muna roƙonka ka gafartawa bayin Allah na mahaifinka. Yosef ya yi kuka sa'ad da suka yi masa magana.18'Yan'uwansa kuma suka zo suka kwanta fuska ƙasa a gabansa. Suka ce, "Duba, mu bayinka ne."19Amma Yosef ya amsa masu, "Kada ku ji tsoro. Ina gurbin Allah ne?20Game da ku, kun yi niyyar mugunta a gare ni, amma Allah ya yi niyyar alheri ne, saboda a adana rayuwar mutane da yawa, kamar yadda kuka gani a yau.21Saboda haka, yanzu kada ku ji tsoro. Zan tanada maku da ƙananan 'ya'yanku." Ya ta'azantar dasu ta wannan hanyar ya kuma yi maganar mutunci ga zukatansu.22Yosef ya zauna a Masar, tare da iyalin mahaifinsa. Ya yi rayuwa shekaru ɗari da goma.23Yosef ya ga 'ya'yan Ifraim har zuwa tsara ta uku. Ya kuma ga 'ya'yan Makir ɗan Manasse, waɗanda aka sanya a gwiwoyin Yosef.24Yosef ya cewa 'yan'uwansa, "Ina gaf da mutuwa; amma tabbas Allah zai zo gare ku, ya kuma bida ku hayewa daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya rantse zai ba Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu."25Daga nan Yosef ya sa mutanen Isra'ila suka rantse da alƙawari. Ya ce, "Tabbas Allah zai zo gare ku. A wannan lokacin tilas ku ɗauki ƙasusuwana daga nan."26Sai Yosef ya mutu, da shekaru 110. Aka nannaɗe shi da maganin hana ruɓa, kuma aka ajiye shi cikin akwati.
Kalmar "ya rushe" karin magana ne don cin nasara. AT: "ya fadi kan mahaifinsa cikin baƙin ciki"
"bayinsa waɗanda suka kula da gawawwakin"
Zuwa "nannaɗe" hanya ce ta musamman wacce take kiyaye wata gawa kafin a binne ta. AT "shirya jikin mahaifinsa don binnewa"
"Sun ɗauki kwana 40"
"ranakun makoki domin shi" ko "ranakun kuka da shi"
A nan "gidan Fir'auna" yana wakiltar wakilai waɗanda ke cikin gidan sarauta na Fir'auna. AT: "Yosef ya yi magana da shugabannin Fir'auna"
Kalmomin "neman alfarma" kalma ce wanda ke nuna yarda da wani. Hakanan, idanu suna wakiltar gani, da gani suna wakiltar tunani ko hukunci. AT: "Idan na sami tagomashi a wurin ku" ko "Idan kun gamshe ni"
Wannan shi nezance a cikin zance. Wannan fassarar za a iya fassara ta azaman magana kai tsaye. "Mahaifina ya yi mini rantsuwa, yana cewa lalle zai mutu kuma zan binne shi a cikin kabarinsa wanda ya haƙa wa kansa ƙasar Kan'ana. In binne shi a can. Yanzu dai bari na haura ... Zan koma."
An ɗauka cewa membobin kotun sun yi magana da Fir’auna, yanzu Fir’auna yana mayar da martani ga Yosef.
Duk manyan shugabannin Fir'auna sun halarci wurin jana'izar.
Ana iya fassara wannan azaman sabon jumla: "Gidan Yosef, da 'yan'uwansa, da gidan mahaifinsa su ma sun tafi tare da shi"
"Taro ne babba."
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) kalmar "Atad" tana nufin "ƙaya" kuma yana iya nufin wurin da ɗimbin yawa na ƙaya ya girma, ko 2) yana iya zama sunan mutumin da ya mallaki masussukar.
"sun yi matukar bakin ciki kuma sun yi baƙin ciki mai yawa"
"Makokin Masarawa suna da yawa"
Mai fassara zai iya ƙara ɗan rubutu wanda ya ce: "Sunan Abel Mizrayim na nufin "makokin Masar."
"kamar yadda ya umurce su"
"'Ya'yan nasa sun karɓi gawarsa"
Anan ana magana da fushi kamar wani abu ne na zahiri wanda Yusufu zai iya riƙe hannunsa. AT: "Idan har Yosef har yanzu yana fushi da mu"
Samun ɗaukar fansa a kan wanda ya cutar da shi ana magana ne kamar dai mutumin yana biyan wasu bashin ne abin da ake bin sa. AT: "yana son ɗaukar fansa kan munanan ayyukan da muka yi masa"
Yakubu shi ne mahaifin 'yan'uwa duka. Anan suka ce "mahaifinka" don jaddadka cewa Yusufu yana buƙatar kulawa da abin da mahaifinsa ya faɗi. AT: "Kafin mahaifinmu ya mutu ya ce"
'Yan'uwan suna ambaton kansu “bayin Allah na ubanku”. Ana iya bayyana wannan a cikin mutum na farko. AT: "muna roƙonka ku gafarta mana, bayin Allah na ubanmu"
"Yosef ya yi kuka lokacin da ya ji wannan saƙo"
Sun kwanta tare da fuskokinsu ƙasa. Wannan alama ce ta tawali'u da girmamawa ga Yosef.
Yosef ya yi amfani da tambaya don ta'azantar da 'yan'uwansa. AT: "Ba ni cikin inda Allah yake." ko "Ba ni ne Allah ba."
"Don haka kada ku ji tsoro ni"
"A koyaushe zan tabbatar da cewa kai da 'ya'yanku sun isa samun abinci"
A nan "zukata" yana nufin 'yan'uwa. Maimaita fassarar: "Ya ta'azantar da su ta yin magana da su da kirki"
"Ya yi rayuwa shekaru 110"
"'Ya'yan Ifraim da jikoki"
Wannan sunan jikan Yosef ne.
Wannan magana tana nufin cewa Yosef ya auro wa 'ya'yan Makir a matsayin ɗiyan kansa. Wannan yana nufin suna da haƙƙoƙin mallaka na musamman daga wurin Yosef.
A cikin Farawa 50: 24-26 kalmar "ku" tana nufin 'yan'uwan Yosef, amma kuma yana ga zuriyarsu.
AT: "fito da ku daga wannan ƙasa zuwa kanku zuwa ƙasar"
"nannaɗe" hanya ce ta musamman wacce take kiyaye wata gawa kafin a binne ta. Duba yadda zaka fassara a cikin Farawa 50:1.
"a kirji" ko "a cikin wani yanayi." Wannan akwati ne da aka sanya mamaci a ciki.
1Ga sunanyen 'ya'yan Isra'ila da suka zo cikin Masar tare da Yakubu, kowannen su tare da iyalansa:2Ruben, da Simiyon, da Lebi, da kuma Yahuda,3da Issaka, da Zebulun da kuma Benyamin,4da Dan, da Naftali, da Gad, da Asha.5Dukkan zuriyar Yakubu su saba'in ne. Yosef yana nan a Masar.6Sai Yosef, dukkan 'yan uwansa, da duk wannan tsãra suka mutu.7Isra'ilawa suka yi albarka, suka riɓaɓɓanya, da kuma ƙara ƙarfi sosai; ƙasar kuma ta cika da su.8Yanzu dai sai wani sabon sarki ya taso a Masar, wanda bai san da Yosef ba.9Ya cewa mutanensa, "Ku duba, Isra'ilawan sun fi mu yawa da kuma ƙarfi.10Ku zo, bari mu bi da su cikin hikima, idan ba haka ba za su ci gaba da haɓɓaƙa, idan yaƙi ya taso, za su haɗa kai da maƙiyanmu, su yaƙe mu, su kuma bar ƙasar."11Sai suka ɗora shugabannin aikin tilas a bisansu domin su wahalshe su da bauta mai zafi. Isra'ilawan suka gina wa Fir'auna biranen ajiya: Fitom da Ramesis.12Amma sa'ad da Masarawan suke ƙuntata masu, da haka Isra'ilawa ke ƙaruwa suna kuma yaɗuwa. Don haka Masarawan suka fara tsorata da Isra'ilawa.13Masarawan suka sa Isra'ilawa su yi aiki mai tsanani.14Suka sa rayukan su suka yi ɗaci cikin hidimarsu a kwaɓa ƙasa da ginin tubali, da kuma dukkan ayyuka a cikin filaye. Dukkan aikin da ake so suyi masu wuya ne.15Sai sarkin Masar ya yi magana da mataye unguwarzoma na Ibraniyawa; ɗaya sunanta Shifra, ɗayan kuma Fuwa.16Ya ce, "Lokacin da kuke taimaka wa matan Ibraniyawa a kujeran haihuwa, ku kula da lokacin da suka haihu. Idan ɗa namiji ne, to sai ku kashe shi; amma idan mace ce, to tana iya rayuwa."17Amma matan unguwarzoma suka ji tsoron Allah ba su kuma aikata yadda sarkin Masar ya umarce su ba; a maimakon haka, suka bar 'ya'ya maza su rayu.18Sarkin Masar ya kirawo mataye unguwarzoman ya ce masu, "Don me kuka yi haka, da kuka bar 'ya'ya maza su rayu?"19Unguwarzoman suka ce wa Fir'auna, "Matayen Ibraniyawa ba kamar matayen Masar ba ne. Suna da ƙarfi kuma kamin mu iso gare su sun rigaya sun haihu."20Allah kuma ya tsare waɗannan mata unguwarzoma. Mutanen kuma suka riɓaɓanya suka zama da ƙarfi sosai.21Domin mataye unguwarzoman sun ji tsoron Allah, sai ya ba su iyalai.22Sai Fir'auna ya ba dukkan mutanensa doka, "Dole ku jefa kowanne ɗan da aka haifa cikin kogi, amma kowacce ɗiya ku bar ta da rai."
Wannan na nufin dukkan mutanen da ke zama a gida tare, yawanci babban iyali ne a haɗe da barorin da ke gidan.
"70"
"Yusufu ya fara zama a Ƙasar Masar kamun 'yan'uwansa"
Wannan na haɗe ne da yayunsa 10 da kanin sa guda ɗaya.
AT: "sun sami 'ya'ya da yawa" ko kuma "sun haifi 'ya'ya da yawa"
"sun cika ƙasar"
Kalmar nan "su" na nufin Isra'ilawa.
"ya fara mulkin mutanen Ƙasar Masar"
"Sarkin ya ce wa mutanensa"
Wato mutanen da ke zama a Ƙasar Masar kenan, Masarawa.
"Kalmar nan "mu" na dukka ne, kuma yana nufin sarkin da kuma mutanensa, Masarawa.
Anan ana maganar yaki kamar wani mutum ne da ke iya yin wani abu.
"bar Masar"
wato wasu Masarawa kenan da ke tilasta Isralawa da aiki masu wuya. wato Masarawa da ke da nawayan tilasta Isra'ilawa su yi aiki kenan.
"don su tilasta Isra'ilawan ga aiki mai wuya wa Masarawa"
Wato wuraren da shugabannin ke zuba abince da wasu abubuwa masu amfani dd kyau kenan.
"suka sa ... aiki ƙwarai" ko kuma "suka sa su aiki ... matsanani"
Ana maganar rayuwar Isra'ilawa ne kamar wani abinci mai ɗaci da ke da wuyan ci.
...
"Marasawan sun sa su ayyuka masu tsanani" ko kuma "Marsarawan sun tilasta su da ayyuka masu tsanani"
Ana kiran sarkin Masar Fir'auna.
Waɗannan su ne matan da ke taimaka wa mace a lokacin haifuwa.
Waɗannan sunayen Yahudawa ne mata kuma.
Mata sukan zauna a wata gajeren kujera a lokacin haifuwa. Sobada haka, ba a raba su da haifuwa. AT: "yayin da suke haifuwa"
Waɗannan su ne matan da ke taimaka wa mace a lokacin haifuwa. Duba yadda ka juya wannan a 1:15)
Fir'auna yayi wannan tambayan ne domin yă tsauta wa ungozomai ɗin saboda barin 'ya'ya mazan da rai. Ana iya sanar da wannan tambayan gangancin a wata hanya da ba tambaya ba? AT: "Kun yi rashin biyayya da umarni ta wurin barin 'ya'ya mazan nan da rai!"
Ungozomai ɗin su amsa Sarkin da hikima ne domin su kwantar wa Fir'auna da hushinsa.
Allah ya sa Fir'auna bai kashe ungozomain ba.
Waɗannan su ne matan da ke taimaka wa mace a lokacin haifuwa. Duba yadda ka juya wannan a 1:15
"Isra'ilawan kuwa suka riɓanya"
"suka girmama Allah" ko kuma "suna da tsoron Allah"
"ya bar su sun samu 'ya'ya"
An ba da wannan umarnin ne domin a bar ruwa ya hallaka 'ya'yan. Anan iya kara haske a ma'annan wannan. AT: "Dole ku ... cikin kogi don su mutu a ruwa"
1To akwai wani mutum daga kabilar Lebi wanda ke auren wata mace mutumiyar Lebi.2Macen ta yi juna biyu ta kuma haifi ɗan yaro. Da ta ga cewa yaron lafiyayye ne, sai ta ɓoye shi har wata uku.3Amma da ya kai wani lokacin da ta ga ba za ta iya ɓoye shi ba, sai ta ɗauki kwandon iwa ta dalaye shi da katsi da ƙaro. Sai ta sanya jaririn ciki ta kuma saka shi cikin ruwan a cikin ciyayin bakin teku.4'Yar'uwarsa na tsaye daga nesa don ta ga abin da zai faru da shi.5Ɗiyar Fir'auna ta gangaro zuwa kogin domin ta yi wanka yayin da kuyanginta na tafiya a gefen kogin. Sai ta hango kwandon cikin ciyayi sai ta aika kuyanginta su kawo shi.6Da ta buɗe, sai ta ga jaririn. Duba, jaririn na kuka. Sai ta yi juyayinsa ta kuma ce, "Wannan lallai ɗaya daga cikin 'ya'yan Ibraniyawa ne."7Sai 'yar uwar jaririn ta ce ma ɗiyar Fir'auna, "In je in nemo maki mai reno daga cikin matan Ibraniyawa?"8Sai ɗiyar Fir'auna ta ce ma ta, "Je ki." Sai yarinyar ta tafi ta kuma samo uwar jaririn.9Sai ɗiyar Fir'auna ta cewa uwar jaririn, "Ɗauki jaririn nan ki yi mani renon sa, ni kuma zan biya ki albashi." Sai matar ta ɗauki jaririn ta yi renon sa.10Da jaririn ya yi girma, sai ta kawo shi wurin ɗiyar Fir'auna, sai ya zama ɗanta. Ta raɗa masa suna Musa ta kuma ce, "Domin na tsamo shi daga ruwa."11Da Musa ya yi girma, ya tafi wurin mutanensa ya kuma lura da nawayarsu. Sai ya ga wani Bamasare na bugun Ba'ibrane, ɗaya daga cikin mutanensa.12Sai ya waiga nan da can, da ya ga babu kowa a wurin, sai ya kashe Bamasaren ya kuma binne jikinsa cikin yashi.13Washegari ya sake fita, kuma, gashi kuwa, biyu daga cikin mazajen Ibraniyawa suna faɗa da juna. Ya cewa wanda shi ke da rashin gaskiya, "Me ya sa kake dukan ɗan'uwan ka?"14Amma mutumin yace, "Waye ya sanya ka shugaba da mai shari'a bisanmu? Ko kana shirin kashe ni kamar yadda ka kashe wancan Bamasaren?" Sai Musa ya ji tsoro ya kuma ce, "Abin da na yi tabbas ba a ɓoye yake ga sauran ba."15Ya zama kuma da Fir'auna ya ji abin da ya faru, sai ya yi ƙoƙarin kashe Musa. Amma Musa ya tsere daga gaban Fir'auna zuwa ƙasar Midiyan. A nan ya zauna a bakin wata rijiya.16Ya zama cewa firist na Midiyan na da 'yan mata guda bakwai. Suka zo, su ɗebi ruwa, su cika kwamayensu don su shayar da garkunan mahaifinsu.17Sai wasu makiyaya suka zo suka yi ƙoƙarin korar su, amma Musa ya tashi ya taimake su. Sai kuma ya shayar da dabbobinsu.18Da 'yan matan suka komo wurin Ruwel mahaifinsu, ya ce, "Me ya sa kuka yi saurin dawo wa gida yau?"19Suka ce, "Wani Bamasare ne ya kuɓutar da mu daga hannun makiyayan. Har ma ya jawo mana ruwa ya shayar da garken."20Sai ya ce da 'yan matansa, "To ina yake? Don me kuka bar mutumin? Ku kira shi domin ya ci abinci tare da mu."21Sai Musa ya yarda da ya zauna tare da mutumin, shi ma sai ya ba shi ɗiyarsa Ziffora ya aura.22Ta haifa masa ɗan yaro, sai Musa ya kira shi da suna Gashom; yana cewa, "Na zama mai baƙonci a cikin baƙuwar ƙasa."23Bayan lokaci mai tsawo, sai sarkin Masar ya mutu. Isra'ilawa suka yi nishi saboda aikin bautarsu. Suka yi kukan neman taimako, sai kuma roƙon su ya kai ga Allah saboda bautarsu.24Sa'ad da Allah ya ga ƙuncinsu, Allah ya tuna da alƙawarinsa da Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu.25Allah ya ga Isra'ilawa, ya kuma fahimci matsalarsu.
An yi amafini ne da wannan kalmar "Sai" domin a dakatar da ainihin labarin da ake kan bayarwa. Anan marabucin ya fara ba da wata sabuwar bangaren labarin ne. Idan kuna da wata hanyar yin haka a harshen ku, kuna iya amfani da ita anan.
"3"
Wannan wata kwando ne da aka saƙa ta da wata ciyawa mai tsayi da ke girma a gefen kogin Nilu a kasar Masar.
Kuna iya kara haske a wannan bayanin cewa an yi hakka ne domin a hana ruwa shiga. AT: "yafa kwalta ton kada ruwa yă iya shiga ciki"
A nan "yaɓe" na nufin ta sa abu mai tsare ruwa.
Wani abu ne da kauri kamar tuwo da ake yin ta da fetur. Ana iya amfini da shi a tsare ruwa. AT: "tar"
Wannan wani abu ne da kauri ja ko baki da ake iya yin ta daga ruwan wata bishiya ko fetur. Saboda haka, "kwalta" anan na iya zama a haɗe da wasu ruwan itace. Ana iya amfani de shi ma a tsare ruwa. AT: "tar" ko kuma "wani irin ruwan ƙaro"
Waɗannan "iwa" wasu irin ciyawa ne masu tsayi da ke girma a fili, wuraren da ke jike.
Wannan na nufin cewa ta tsaya da nesa kenan domin kada wani yă san cewa tana wurin, amma dai tana wurin da za iya duban kwandon.
"bayin"
Kalmar nan "sai" na ba da alamar wani labarin ban mamaki ne da ya biya baya.
"shayar"
"'yar Bayahudiyar ta kai shi"
"ya zama tallafaffen ɗan gidan diyar Fir'auna"
Masu juyi na iya karin bayani a kasa da ke cewa "Sunan nan "Musa na nan kamar kalmar Ibraniyance da ke nufin "ja."
"ja shi"
"kwaɗa" ko kuma "dũkan"
Waɗannan kalamu biyun na nufin "ko'ina." AT: "Ya waiwaya ko ina"
"Musa ya fito"
Kalmar nan "sai kawai" na ba da alamar wani labarin ban mamaki ne da ya biya baya. Kuna iya amfani da wata kalma a harshenku da zai ba da wannan ma'annan.
Wannan wata hanya ce na cewa "wanda ya ta da fadan." AT: "Wanda ke da laifin ta da fadan"
Mutumin nan na amfami ne da wannan tambayan domin yă tsauta wa Musa daga shiga tsakaninsu. AT:"Kai ba shugabanmu bane kuma ba ka da 'yanci ka ka shar'anta mu!"
Mutumin ya yi wannan tambayan domin gatse ne. AT: "Mu na da sanin cewa ka kashe wani Bamasara jiya. To kada ma ka kashe ni!"
Ana amfani ne da kalmar nan "Da" a nan domin a dakatar da labarin. A nan, marubucin ya cigaba da faɗin wata sabuwar bangaren abinda ya faru ne.
Ana amfani ne da kalmar nan "Da" anan domin a dakatar da labarin. A nan, marubucin yana magganar wasu sabobin mutane ne a labarin.
Wato su diba ruwa daga rijiya kenan.
wata doguwar, tsiririn, buɗadiyar kwano kenan da dabbobi ke ci da sha a ciki.
"watsar da su"
"ya cece su"
Wannan tambayan na ɗan tsauta wa ne kadan ga 'yan matan domin basu gayyaci Musa zuwa gidansu yadda marabtan baki na al'adan su ke wajaba. AT: "Ai da ba ku bar mutumin a bakin rijiyan ba!"
"Musa kuwa ya yarda yă yi zama tare da Reyuwel"
"Wato diyar Reyuwel kenan.
Wato ɗan Musa kenan.
"ni baƙo ne a baƙuwar ƙasa"
Su yi haka ne saboda baƙin ciki da azaba da suke ciki. AT: "yi juyayi"
Ana maganar koke kokensu kamar mutum ne da ke iya tafiya sama har gun da Allah ya ke. AT: "Allah ya ji kukansu"
Wannan wata hanya ce na cewa Allah ya yi tunani game da alkawarin da ya yi. AT: "Allah ya yi tunanin alkawarin da yayi"
1Yanzu dai Musa yana ta kiwon garken Yetro surukinsa, firist na Midiyan. Musa ya kai garken har iyakar sashen hamada ya kuma iso Horeb, tsaunin Allah.2A nan mala'ikan Yahweh ya bayyana gare shi cikin harshen wuta mai ci a kurmi. Sai Musa ya duba, ga shi, kurmin na ci da wuta, amma kurmin bai ƙone sarai ba.3Sai Musa yace, "Zan juya nan inga wannan abin ban mamaki, don me kurmin bai cinye ƙurmus da wutar ba."4Sa'ad da Yahweh ya ga cewa ya juya garin ya duba, sai Allah ya yi kira gare shi daga cikin kurmin ya ce, "Musa, Musa." Musa yace, "Ga ni nan."5Allah yace, "Kada ka iso nan! Ka kwaɓe takalmanka daga kafafun ka, gama inda kake tsaye ƙasa ce keɓaɓɓiya a gare ni."6Ya kuma ce, "Ni ne Allahn mahaifinka, Allahn Ibrahim, da na Ishaku, da kuma na Yakubu." Sai Musa ya rufe fuskarsa, gama yana tsoron duban Allah.7Yahweh yace, "Na ga azabar mutanena da suke a Masar. Na ji kururuwarsu sabili da shugabanninsu na aikin tilas, gama ina sane da wahalarsu.8Na sauko domin in kuɓutar da su daga ikon Masarawa in kuma fito da su daga wannan ƙasa zuwa ƙasa mai kyau, mai girma, ƙasa mai ɓulɓulo da madara da zuma; zuwa ƙasashen Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Ferizziyawa, da Hibiyawa, da kuma Yebusiyawa.9Yanzu dai kururuwar mutanen Isra'ila ta hau zuwa gare ni. Fiye da haka, na ga zaluncin da Masarawa suke gwada masu.10Ga shi yanzu, zan aike ka wurin Fir'auna domin ka fito da mutanena, Isra'ilawa, daga cikin Masar."11Amma Musa ya cewa Allah, "Ni, wane ne, har da zan tafi wurin Fir'auna in kuma fito da Isra'ilawa daga cikin Masar?"12Allah ya amsa, "Ni zan kasance tare da kai tabbas. Wannan zai zama maka alama da cewa Ni na aike ka. Yayin da ka fito da mutanen daga Masar, za ku yi mani sujada a kan wannan n."13Sai Musa ya cewa Allah, "Sa'ad da na tafi wurin Isra'ilawa na kuma ce masu, 'Allah na kakanninku ya aiko ni gare ku,' in kuma suka ce mani, 'Mene ne sunansa?' to me zan amsa masu?"14Sai Allah ya cewa Musa, "NI NE DA NAKE NI NE." Allah yace, "Dole ka faɗi wa Isra'ilawa, 'NI NE ya aiko ni gare ku."'15Allah ya kuma ce wa Musa, "Dole ka gaya wa Isra'ilawa, 'Yahweh, Allah na kakanninku, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu, ya aiko gare ku. Wannan ne sunana har abada, kuma da haka za a tuna da ni cikin dukkan tsararraki.16Ka tafi ka tara shugabannin Isra'ila tare. Ka ce masu, 'Yahweh, Allah na kakanninku, Allah na Ibrahim, na Ishaku, kuma da na Yakubu, ya bayyana gare ni ya ce, "Lallai na kula da ku na kuma ga abin da aka yi maku a Masar.17Na yi alƙawarin in fito da ku daga zaluncin Masar zuwa ƙasar Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Feriziyawa, da Hibiyawa, da kuma Yebusiyawa, ƙasa mai zubo da madara da kuma zuma."'18Za su saurare ka. Da kai da shugabannin Isra'ila dole ku je wurin sarkin Masar, dole kuma ku faɗi masa, 'Yahweh, Allah na Ibraniyawa, ya gamu da mu. Saboda haka yanzu bari mu yi tafiyar kwana uku cikin jeji, domin mu yi hadaya ga Yahweh Allahnmu.'19Amma na san da cewa sarkin Masar ba zai bar ku ku tafi ba, sai in an tilasta hannunsa.20Zan miƙa hannuna in kuma kai wa Masarawa farmaki da dukkan al'ajiban da zan aikata a tsakaninsu. Bayan haka, zai ƙyale ku ku tafi.21Zan bai wa mutanen nan tagomashi daga Masarawa, don haka lokacin da kuka fito, ba za ku fita hannu wofi ba.22Kowacce mace za ta roƙi ƙarafan azurfa da zinariya da kuma tuffafi daga maƙwabtansu Masarawa da kuma kowacce mace dake zama gidan maƙwabtanta. Za ku sanya su bisa 'ya'yanku maza da mata. Da haka za ku washe Masarawa."
Wannan Yahweh ne da kansa yana ya bayyana a matsayin Mala'ika, ba wai mala'ikan da Yahweh ya aika kawai ba. "Yahweh ya bayyana da kamanin mala'ika" (UDB).
Wannan suna ne na Allah da ya bayyana wa mutanensa a Tsohon Alkawali. Duba shafi na translationWord kame da Yahweh da kuma yadda ake juya wannan.
Kalmar nan "sai" a nan na nuna cewa Musa ya ga wani abu ne da ya banbanta da abinda yake sammani.
"tsatsarka"
Dukkan waɗannan mutanen suna bauta wa Allah ɗaya.
Wannan na iya nufin 1) "tsofofinka" ko kuma 2) "na ubanka" Idan yana nufin "kakanka," to jimlar da ke biye na ba da bayyani wadda shi ne "ubanka" ke nufi: yana nufin Ibrahim, Ishaku, da Yakubu. Idan yana nufin "ubanka", to yana nufin uban Musa da kansa.
wato wasu Masarawa kenan da ke tilasta Isralawa da aiki masu wuya. wato Masarawa da ke da nawayan tilasta Isra'ilawa su yi aiki kenan.
"ƙasa da madara da zuma ke gudana." Allah yana maganar ɗacewar ƙasar ne ga dabbobi da shuke-shuke kamar madara da zuma daga waɗannan dabbobi da shuke-shuken suna gudana a ƙasar. AT: "ƙasar da ke da kyau a kiwon dabbobi da noma abinci"
"cike da" ko kuma "da yalwar"
Dashike ana samun madara daga shanu da dawakai ne, wannan na nufin abincin da dabbobi ke bayarwa. AT: "abinci daga dabbobi"
Dashike ana samun zuma daga furannin itace ne, wannan na nufin abincin da 'ya'yan itace ke bayarwa.
A nan maganar "kuka" anan ne kamar wasu mutane ne da ke iya tafiya da kansu. AT: ""Na ji kuke-kuken jama'ar Isra'ila"
Musa yana amfani ne da wannan tambayan don yă gaya wa Allah cewa shi ba komai ba ne kuma ba wanda zai saurare shi. AT: "Ni ban isa har in je gaban Fir'auna ... Masar ba!"
Wannan shi ne amsar da Allah ya ba wa Musa game da tambaya da ya yi akan sunan Allah. Ana iya kara haske a wannan. AT: "Allah ya ce wa Musa, "ka ce masu Allah ya ce sunansa shi ne, 'NI NE NI."
Wannan na iya nufin 1) duka jimlar nan sunaye Allah ne ko kuma 2) Ba faɗin sunan Allah ne yake yi anan ba, amma wani abu game da kansa. Ta wurin faɗin haka, Allah yana koyar cewa shi madawami ne; yana nan tun dã kuma zai cigaba da kasancewa a kodayaushe.
Harsuna da basu da kalma kamar "ne" na iya amfani da "RAYE" ko kuma "INA NAN."
Allah ya ci gaba da magana da Musa.
Ibrahim, Ishaku da Yakubu sune kakkannnin Musa. Dukansu sun bauta wa Allah ɗaya ne.
Kalmar nan "ku" na nufin jama'ar Isra'ila.
"ƙasa da madara da zuma ke gudana." Allah yana maganar ɗacewar ƙasar ne ga dabbobi da shuke-shuke kamar madara da zuma daga waɗannan dabbobi da shuke-shuken suna gudana a ƙasar. Duba yadda aka juya wannan a 3:7. AT: "ƙasar da ke da kyau a kiwon dabbobi da noma abinci"
"cike da" ko kuma "da yalwar"
Dashike ana samun madara daga shanu da dawakai ne, wannan na nufin abincin da dabbobi ke bayarwa. AT: "abinci daga dabbobi"
Dashike ana samun zuma daga furannin itace ne, wannan na nufin abincin da 'ya'yan itace ke bayarwa
"Kalmar nan "ka" na nufin Musa. AT: "Dattawan za su saurare ka"
Allah ya cigaba da magana da Musa.
Wannan na iya nufin 1) "sai dai in ya ga cewa ba shi da ikon yin wani abu kuma"
A nan "hannu" na nufin ikon Allah. AT: "zan buge shi da iko"
A nan amfani ne da kalmar nan "hannun wofi" domin a nanata wani abu da ban da wanda ake nufi. AT: "za ku tafi da hannayen ku cike da abubuwa masu kyau" ko kuma "za ku tafi da abubuwa masu daraja ƙwarai"
"duk mataye Masarawa da ke zama a gidajen maƙwatan ta Bamasara"
1Sai Musa ya amsa, "Amma idan basu gaskata da ni ko su saurare ni ba amma suka ce a maimako, 'Yahweh bai bayyana gare ka ba'?"2Yahweh yace masa, "Menene wannan a hannunka?" Musa yace, "Sanda ce.3Yahweh yace, "Jefa ƙasa." Sai Musa ya jefar da ita ƙasa, sai ta zama maciji. Sai Musa ya guje masa.4Yahweh ya cewa Musa, "Ka miƙa hannu ka riƙe wutsiyar." Sai ya miƙa hannu ya kuma kama macijin. Sai ta sake zama sanda cikin hannunsa.5"Wannan ya faru domin su gaskata da Yahweh, Allahn kakanninsu, Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yakubu, ya bayyana gare ka."6Yahweh ya sake ce masa, "Yanzu ka sanya hannun ka cikin rigarka." Sai Musa ya sanya hannunsa a cikin rigarsa. Da ya fito da shi, gashi kuwa, hannunsa ya kama kuturta, fari fat kamar ƙanƙara.7Yahweh yace, "Ka sake maida hannunka cikin riga, kuma da ya fito da shi, sai ya ga cewa an maido da lafiyarsa kuma, kamar sauran sashen fatarsa.8Yahweh yace, "Idan basu gaskanta da kai ba - idan har basu kula da alama ta ikona na farko ba ko su gaskanta da ita ba, to za su gaskanta da alama ta biyun.9Idan kuma basu gaskanta da dukka waɗannan alamu biyu na ikona ba, ko su saurare ka, sai ka ɗebo ruwa daga kogi ka kuma tsiyaye shi a busasshiyar ƙasa. Ruwan daka ɗebo zai zama jini a bisa busasshiyar ƙasar."10Sai Musa ya cewa Yahweh, "Ubangiji, ban taɓa iya magana da kyau ba, ko a dã ko tun lokacin daka yi magana da bawanka. Ni ba mai magana da sauri ba ne kuma harshena mai nauyi ne."11Yahweh yace dashi, "Wanene ya yi bakin mutum? Wa ke maida mutum bebe ko kurma ko mai gani ko makaho? Ba Ni ba ne, Yahweh?12Saboda haka yanzu ka tafi, Ni kuma zan kasance da kai in kuma koya maka abin da za ka faɗi."13Amma Musa yace, "Ubangiji, na roƙe ka ka aika da wani, duk wanda ka so ka aika."14Sai Yahweh ya yi fushi da Musa. Yace, "To Haruna fa, ɗan'uwanka, Ba'lebi? Na san da cewar ya iya magana da kyau. Ga shi ma, yana fitowa don ya tarye ka, kuma sa'ad da ya ganka, zai yi murna cikin zuciyarsa.15Za ka yi magana dashi ka kuma sanya maganganun da zai faɗi a bakinsa. Zan kasance da bakinka da kuma bakin sa, kuma zan bayyana maku ku biyun abin da za ku yi.16Shi za ya yi magana ga mutanen a madadin ka. Zai zama bakinka, kai kuma za ka zama gareshi kamar ni, Allah.17Za ka ɗauki wannan sanda a hannunka. Da ita za ka aiwatar da alamun."18Sai Musa ya komo wurin Yetro surukinsa ya kuma ce dashi, "Bari in tafi domin in koma ga dangina da su ke a Masar in kuma ga ko suna nan da rai." Sai Yetro ya cewa Musa, "Ka tafi cikin salama."19Yahweh ya cewa Musa cikin Midiyan, "Tafi, ka koma Masar, gama dukkan mazajen dake neman su ɗauke ranka sun mutu."20Musa ya ɗauki matarsa da 'ya'yansa ya ɗora su bisa jaki. Ya dawo zuwa ƙasar Masar, ya kuma ɗauki sandar Allah cikin hannunsa.21Yahweh ya cewa Musa, "Lokacin da ka iso Masar, ka tabbata ka aikata a gaban Fir'auna dukkan abubuwan banmamaki da na sanya cikin ikonka. Amma zan taurare zuciyarsa, ba kuwa zai bar mutanen su tafi ba.22Dole ka cewa Fir'auna, 'Ga abin da Yahweh yace: Isra'ila ɗana ne, ɗan fãrina,23kuma ina ce maka, "Ka bar ɗana ya tafi, domin ya yi mani sujada." Amma tunda ka ƙi ka bar shi ya tafi, lallai zan kashe ɗanka, ɗanka na fãri.'"24Yayin da suke kan hanya, da suka tsaya don su kwana a daren nan, Yahweh ya gamu da Musa ya kuma yi ƙoƙarin ya kashe shi.25Sai Ziffora ta ɗauki wuƙa mai kaifi ta yanke loɓar fatar ɗanta, ta taɓa shi da ita ga sawayensa. Sai ta ce, "Tabbas kai ango ne a gare ni ta wurin jini."26Sai Yahweh ya ƙyale shi. Ta ce, "Kai angon jini ne" sabili da kaciyar.27Yahweh yace da Haruna, "Tafi cikin jeji ka gamu da Musa." Haruna ya tafi, ya gamu dashi a tsaunin Allah, ya yi masa sumba.28Sai Musa ya faɗa wa Haruna dukkan maganganun Yahweh da ya aike shi ya faɗi da dukkan alamu na ikon Yahweh da ya umarce shi ya aikata.29Sai Musa da Haruna suka tafi suka tãra dukkan dattawan Isra'ila.30Haruna ya faɗi dukkan maganganun da Yahweh ya faɗa wa Musa. Ya kuma yi alamun na ikon Yahweh a gaban mutanen.31Mutanen suka gaskanta. Lokacin da suka ji cewa, Yahweh ya lura da Isra'ilawa kuma da cewa ya ga ƙuncinsu, sai suka sunkuyar da kansu suka kuma yi masa sujada.
"idan Isra'ilawa basu gaskanta ba"
"ɗauka shi ta wutsiyarsa" ko kuma "cafke shi daga wutsiyar"
"ya canza zuwa sanda" ko kuma "ya juya zuwu sanda"
Ibrahim, Ishaku da Yakubu ne kakkaninsu guda uku. Duk kum sun bauta wa Allah ɗaya.
Ana amfani ne da wannan kalmar anan motasin rai, a nuna mamaki.
Kalmar nan "kamar" anan na kwatanta kamanin Musa ne. Ciwon kuturta na sa fatan jikin mutum yă yi fari. Mai yiwuwa ba ku da kalmar snow a harshen ku, don haka, kuna iya tunanin wani abu da ake iya bayyana fari sa shi. AT: "fari fat kamar auduga"
"amince" ko "yarda"
"shahararren mai magana"
Jimlar nan "nauyin baki" da nauyin harshe" a takaice da ma'ana guda. Musa yana amfani ne da su domin yă nanata cewa shi ba iya magana da kyau ba.
A nan "harshe" na nufin yanayin iya maganar Musa. AT: "rashin iya magana da kyau"
Yahweh yana amfani ne da wannan kalmar yă nanata cewa shi ne Mahallici da ke sa mutum iya magana. AT: "Ai Ni ne Yahweh mai hallitan bakin ɗan adam, mai kuma sa mutum iya magana!"
Yahweh yana amfani ne da wannan tambayan domin yă nanata cewa shi ne ke iya sa mutum iya magana da kuma jin magana, da kuma iya gani. AT: "Ai ni ne Yahweh mai iya sa mutane magana, ko ji, ko su gani ko su zama makafai!"
Yahweh yana amfani ne da wannan tambayan domin yă nanata cewa shi kadai ke iya ɗaukan waɗannan ra'ayin. AT: "Ni, Yahweh, ni ne mai yin wannan!"
AT: " Ni zan sa ka iya magana"
A nan "zuciya" na nufin tunanin mutum. AT: "za zama da farin ciki"
Ana maganar magana anan ne kamar su wasu abubuwa ne da ake iya sa a bakin mutum. Anan "magana" na nufin sako. AT: "ka bashi sakon da zai je yă maimaita"
Kalmar nan "baki" na nufin kalamun da Haruna zai mora. AT: "Zan ba shi daidai kalamun da da zai furta"
Kalmar nan "baki" na nufin maimaita abinda Musa ya faɗa masa. AT: "Zai faɗi abinda ka ce yă faɗa"
Kalmar nan "kamar" a nan na nufin cewa Musa zai tsaya a iko ga Haruna kamar yaddda Allah da kansa ya yi wa Musa. AT: "ka kuwa za ka yi magana da Haruna da irin ikon da nake maka magana da shi"
suruki na nufin Mahaifin matar Musa.
A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. Anan maganar taurin kansa ne kamar zuciyarsa ne ya taurara. AT: "sa Fir'auna yă taurara"
Kalmar nan "Isra'ila" anan na nufin dukkan jama'ar Isra'ila. AT: "Jama'ar Isra'ila dukka 'ya'ya na ne"
A nan ana maganar jama'ar Isra'ila ne kamar su 'ya'yan fãri ne masu sa farin ciki da fahariya. AT: "suna kamar ɗa na na fãri ne"
"Kalmar nan "shi" na nufin jama'ar Isra'ila a matsayin ɗan Allah. AT: "ka ki ka bar ɗa na yă tafi"
Kalmar nan "ɗa" anan na nufin ainihin ɗan Fir'auna.
Wannan na iya zama haka ne domin Musa bi yi wa ɗansa kaciya ba.
Wannan ne suna matar Musa.
Wannan wani wuka ne mai ci sosai.
Mai yiwuwa "kafa" anan wata hanya ce da ke nufin azzakarinsa.
Ba haske a ma'annan wannan karin magana. Amma mutanen al'addun su sun fahimci maganar da kyau. AT: "jini ya hada ni da ke" ko kuma "kai mai gida na ne ta wurin jini"
...
Mai yiwuwa wannan na nufin dutsen Sina'i amma, ayan bai ambaci haka ba.
Kalmar nan "ya" na nufin Yahweh ne, sa'annan "shi" yana nufin Musa.
"a gaban mutanen"
ya damau akan Isra'ilawan
Wannan na iya nufin 1) "suka saukar da kawunansu don ban girma" ko kuma "2) suka durkusa da bangirma"
1Bayan waɗannan abubuwan sun faru, sai Musa da Haruna suka je wurin Fir'auna suka kuma ce, "Ga abin da Yahweh, Allah na Isra'ila, yace: 'Ka bar mutane na su tafi, domin suyi ma ni biki a cikin jeji.'"2Fir'auna yace, "Wane ne Yahweh? Don me zan saurari muryarsa har da zan bar Isra'ila ya tafi? Ban san Yahweh ba; don haka, ba zan bar Isra'ila ya tafi ba."3Suka ce, "Allah na Ibraniyawa ya gamu da mu. Ka bar mu mu yi tafiyar kwana uku cikin jeji mu kuma yi hadaya ga Yahweh Allahnmu domin kada ya kawo mana farmaki da annoba ko takobi."4Amma sarkin Masar yace ma su, 'Musa da Haruna, don me kuke ɗauke mutanen nan daga aikinsu? Ku koma ga aikinku."5Ya kuma ce, "Gashi yanzu akwai mutane Ibraniyawa dayawa a cikin ƙasarmu, kuma kuna sasu su daina aikinsu."6A wannan ranar, Fir'auna ya bada umarni ga shugabannin aikin tilas da masu jagorar mutanen. Ya ce,7Ba kamar dã ba, ba za ku bada tattaka ga mutanen ba domin yin tubula. Bari su tafi su tarawa kansu budu.8Duk da haka, za ka buƙaci tubula daga garesu dai dai kamar yadda ka buƙata a dã. Kada ku karɓi abin da ya gaza yadda aka sãba, domin ƙyuya gare su. Shi yasa suke kira da cewar, 'Bari mu je mu yi hadaya ga Allahnmu.'9Ku ƙara wa mazajen aiki don su duƙufa cikinsa har da ba za su saurari maganganun yaudara ba."10Sai shugabannin aikin tilas da masu jagorar mutanen suka fita suka yi magana da mutane. Suka ka ce, "Ga abin da Fir'auna yace: 'Ba zan ƙara baku wani budu ba.11Ku da kanku dole ku je ku kuma samo budu duk inda ake samunsa, amma aikin ku ba zai ragu ba.'"12Don haka sai mutanen suka barbazu a ko'ina cikin ƙasar Masar domin su tãra yayi don budu.13Sai 'yan gandu suka ci gaba da tsananta masu suna cewa, "Ku gama aikin ku, kamar yadda dã ake baku tattaka."14Shugabannin aikin tilas na Fir'auna suka dinga bugun masu jagorar Isra'ilawa, waɗanda aka sanya bisa sauran ma'aikata. Shugabannin aikin tilas suka dinga tambayarsu, "Don me yasa baku yi dukkan ãdadin tubula da ake buƙata ba, ko na jiya da kuma na yau, kamar yadda kuka sãba a baya?"15Sai masu jagora na Isra'ilawa suka shiga wurin Fir'auna da kuka gare shi. Suka ce, "Meyasa kake yi da bayinka haka?16Babu wata tattakar da ake ba bayin ka kuma, duk da haka suna ce mana, 'Ku yi tubula!' Mu ma, bayin ka, yanzu bugun mu ake yi, duk da haka laifin mutanen ka ne."17Amma Fira'auna yace, "Kuna da ƙyuya! Kuna da ƙyuya! Kun ce, 'Ka barmu mu je mu yi hadaya ga Yahweh.'18Saboda haka yanzu ku koma ga aiki. Ba za a ba ku tattaka ba, amma dole ne ku cika ãdadin tubulan ku."19Sai masu jagorar Isra'ilawa suka ga cewa suna cikin matsala lokacin da aka ce da su, "Ba za ku rage tubula na kowace rana ba."20Sai suka sami Musa da Haruna, a wannan lokaci suna tsaye a wajen fãdar, sa'ad da suke fitowa daga wurin Fir'auna.21Suka cewa Musa da Haruna, 'Bari Yahweh ya dube ku ya kuma hore ku, domin kunsa mun zama abin kyama a gaban Fir'auna da kuma bayinsa. Kun sanya takobi a hannunsu don su kashe mu."22Sai Musa ya komo ga Yahweh ya kuma ce, "Ubangiji, meyasa ka kawo wahala ga mutanenka? Meyasa ka aiko ni tun da farko?23Tun lokacin da na iso wurin Fir'auna domin in yi magana da shi a sunanka, ya jawo wa mutanen nan wahala, kuma baka ƙubutar da mutanenka ba sam-sam."
Ba san takamaimain yawan lokacin da ya ɗauki Musa da Haruna suka kira har lokacin da suka tashe zuwa gun Fir'auna ba.
Wannan wata biki ce ta musamman domin yi wa Yahweh sujada.
Fir'auna yana amfani ne da wannan tambaya domin ya nuna cewa bai san da wani Yahweh a matsayin Allah ba. AT: "Ban sa Yahweh ba"
Fir'auna yana amfani ne da wannan tambayan yă ya nuna da cewa ba ya da wani marmarin yi wa Yahweh biyayya ko ma yă bar 'ya'yan Isra'ila so je su yi masa biyayya. AT: "Shi ba kome bane a gare noi, kuma ba zan taba ba 'ya'yan Isra'ila su tafi ba!"
kalmar nan "muryarsa" na nufin" na nufin maganar da Allah ya fada. AT: "saurari abin da ya fada"
Ana iya ce wa wannan Allah na Isra'ilawa ko kuma Yahweh.
A nan "takobi" na nufin yaƙi ko kuma kawo hari daga abokan gãba. AT: "ko kuma sa abokan gãbanmu su kawo mana hari"
Fir'auna yana amfani ne da wannan tambayan ya nuna bacin ran shi da Musa da kuma Haruna domin suna hana 'Isra'ilawa yin aikinsu. AT: "ku daina daomun mutanen daga yin aiki!"
wato wasu Masarawa kenan da ke tilasta Isralawa da aiki masu wuya. wato Masarawa da ke da nawayan tilasta Isra'ilawa su yi aiki kenan. Duba yadda ka juya wannan a 1:11.
Kalmar nan "ku" an waɗannan na nufin shugabannin aiki ne.
wato wasu Masarawa kenan da ke tilasta Isralawa da aiki masu wuya. wato Masarawa da ke da nawayan tilasta Isra'ilawa su yi aiki kenan. Duba yadda ka juya wannan a 1:11.
...
A nan "da kanku" na nanata cewa Masarawan ba za su taimake su kuma ba.
AT: "za ku cigaba da yin yawan tubula yadda kuka saba yi da"
Wannan maganan faɗaɗawane kuma ana amfani da shi ne domin a nuna yawan kokarin da Isra'ilawa suke yi don cika burin Fir'auna. AT: "yanki mai yawa"
wato wasu Masarawa kenan da ke tilasta Isralawa da aiki masu wuya. wato Masarawa da ke da nawayan tilasta Isra'ilawa su yi aiki kenan. Duba yadda ka juya wannan a 1:11
tushiya ta bayan girbi.
shugabannin aikin suna amfani ne da tambayan yă nuna cewa suna fushin karancin tubalin. AT: "ba kwa yin isashen tubalin, a jiya ko a yau, kamar yadda ku ka yi a da ba!"
"yi ƙara"
A nan "su" na nufin shugabanni Masarawa.
AT: "da Fir'auna ya ce masu"
Wannan wata babban gida ce da sarki ke zama.
Masarawan suna amsa wa Isra'ilawan kamar yadda za su yi sa'adda suka ji warin wani abo. AT: "kun sa sun ƙi mu"
A nan "takobi" na nufin samun daman hallaka abokan gãba. AT: "ka basu hujja su kashe mu" (UDB)
Wannan tambayan na nuna masanan rashin jin dadin sa da ganin yadda Masarawa ke bi da Isra'ilawa da tsanani ma yanzu. AT: "Ubangiji, ban ji dadin masifar da ka sauka wa mutanennan ba"
Wannan tambayan na nuna rashin jin dadin Musa da yadda Allah ya aiko shi Masar. AT: "Da ma baka tabba aika na zuwa nan ba"
Kalmar nan "suna" a nan na nufin sakon Allah. AT: "in ba shi sakonka"
1Daga nan Yahweh ya cewa Musa, "Yanzu ne za ka ga abin da zan yi wa Fir'auna. Za ka ga wannan, gama zai barsu su tafi sabili da hannuna mai ƙarfi. Sabili da hannuna mai ƙarfi, zai kore su daga ƙasarsa."2Allah ya yi magana da Musa ya kuma ce masa, "Ni ne Yahweh.3Na bayyana ga Ibrahim, ga Ishaku, ga Yakubu kuma a matsayin Allah Mai Iko Dukka; amma da sunana, Yahweh, basu san Ni ba.4Na kuma kafa alƙawari na da su, domin in ba su ƙasar Kan'ana, ƙasar da suka zauna a matsayin baƙi, ƙasar da suka yi yawo a ciki.5Bugu da ƙari, na ga ƙuncin 'ya'yan Isra'ila waɗanda Masarawa suka bautar, kuma na tuna da alƙawarina.6Saboda haka, ka gaya wa Isra'ilawa, 'Ni ne Yahweh. Zan fito da ku daga bautar Masarawa, kuma zan fishe su daga ƙarƙashin ikon su. Zan kuɓutar da ku ta wurin nuna ikona, tare da manyan ayyukan hukunci.7Zan ɗauke ku a gare ni a matsayin mutane na, zan kuma zama Allahnku. Za ku sani Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito da ku daga bautar Masarawa.8Zan kawo ku cikin ƙasar da na rantse in ba Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu. Zan bada ita gareku abin mallaka. Ni ne Yahweh."'9Da Musa ya faɗi wannan ga Isra'ilawa, sai suka ƙi su saurare shi saboda karayar zucinsu sabili da bautarsu mai zafi.10Sai Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,11"Tafi ka faɗi wa Fir'auna, sarkin Masar, ya bar mutanen Isra'ila su tafi daga ƙasarsa."12Sai Musa ya cewa Yahweh, "To idan har Isra'ilawa ba su saurare ni ba, don me Fir'auna zai saurare ni, tunda ban ƙware a magana ba?"13Yahweh ya yi magana da Musa da kuma Haruna. Ya ba su umarni domin Isra'ilawa domin kuma Fir'auna, sarkin Masar, su fito da Isra'ilawa daga ƙasar Masar.14Waɗannan su ne shugabannin gidajen kakanninsu: 'Ya'yan Ruben, ɗan fari na Isra'ila, su ne Hanok, da Fallu, da Hezron, da kuma Karmi. Waɗannan su ne kakannin kabilar Ruben.15'Ya'yan Simiyon su ne Yemuwel, da Yamin, da Ohad, da Yakin, da Zohar, da kuma Shawul - ɗan wata mace Bakan'aniya. Waɗannan su ne kakannin kabilar Simiyon.16Ga jerin sunayen 'ya'yan Lebi, tare da zuriyarsu. Sune Gashon, da Kohat, da kuma Merari. Lebi ya yi rayuwa har shekaru 137.17'Ya'yan Gashon su ne Libni da Shimei.18'Ya'yan Kohat su ne Amram, da Izhar, da Hebron, da kuma Uzziyel. Kohat ya yi rayuwa har ya kai shekaru 133.19'Ya'yan Merari su ne Mahli da Mushi. Waɗannan suka zama kakannin kabilar Lebiyawa, tare da zuriyarsu.20Amram ya auri Yokebeb, 'yar'uwar mahaifinsa. Ta haifar masa Haruna da Musa. Amram ya yi rayuwa har tsawon shekaru 137 sai kuma ya mutu.21'Ya'yan Izhar su ne Korah, da Nefeg, da Zikri.22'Ya'yan Uzziyel su ne Mishyel, da Elzafan, da kuma Sitri.23Haruna ya auri Elisheba, ɗiyar Amminadab, 'yar uwar Nahshon. Ta haifar masa Nadab da Abihu, da Eliyeza da kuma Itamar.24'Ya'yan Kora su ne Assir, da Elkana, da kuma Abiyasaf. Waɗannan su ne kakannin kabilar Korahawa.25Eliyeza, ɗan Haruna, ya auri ɗaya daga cikin 'ya'ya matan Futiyel. Ta haifa masa Finehas. Waɗannan su ne shugabannin gidajen ubanni a cikin Lebiyawa, tare da zuriyarsu.26Waɗannan mutanen biyu su ne Haruna da Musa a gare su ne Yahweh yace, "Ku fito da 'ya'yan Isra'ilawa daga ƙasar Masar, bisa ga ƙungiyoyinsu na mayaƙa."27Sai Haruna da Musa suka yi magana da Fir'auna, sarkin Masar, da ya barsu su fito da Isra'ilawa daga Masar. Waɗannan dai Musa da Harunan ne.28Da Yahweh ya yi magana da Musa a cikin ƙasar Masar,29ya ce masa, "Ni ne Yahweh. Ka ce wa Fir'auna, sarkin Masar, dukkan abin da zan faɗa maka."30Amma Musa ya cewa Yahweh, "Ban ƙware ba wurin magana, don haka ta yaya Fir'auna zai saurare ni?"
Kalmar nan "hannu" a nan na nufin ayyukan Allah. AT: "ikon da zan nuna cikin ayyukanna"
Na nuna kaina ga Ibrahim, ga Ishaku, ga kuma Yakubu"
AT: "Ba su san da ni ba"
Wato gunaguni ta dalilin tsanani da azaba.
Wannan umarni ne daga Yahweh zuwa ga Musa. AT: "Yahweh ya ce wa Musa ya fada wa Isra'ilawa."
"na alkawarta" ko kuma "na ce zan"
Musa yana wannan tambayan da begen cewa Allah zai canza zuciya akan amfani da Musa. AT: "Tunda Isra'ilawa basu saurare ni ba, Fir'auna ma ba zai saurare ni ba, domin ba ni da lafazi!"
A nan "shugabanni" nan nufin ainihin zuriyan kakkannin su. AT: "zuriyan kakkanni"
Waɗannan sunayen maza ne.
Waɗannan sunayen maza ne.
Waɗannan sunayen maza ne.
Waɗannan sunayen maza ne.
Waɗannan sunayen maza ne.
Waɗannan sunayen maza ne.
Waɗannan sunayen maza ne.
AT: "Waɗannan su ne shugabannin iyalen."
"kabila ɗaya a lokaci" ko kuma "iyali ɗaya bayan ɗaya"
Musa yana wannan tambayan ne da zaton canza wa Allah zuciya. AT: "Ina da matsala ... ba shakka Fir'auna ba zai saurare ni ba!"
1Yahweh ya cewa Musa, "Duba, Na maishe ka kamar wani allah ga Fir'auna. Haruna ɗan'uwanka zai zama annabi dominka.2Za ka faɗi dukkan abin da na dokace ka ka faɗa. Haruna ɗan'uwanka zai yi magana da Fir'auna don ya bar mutanen su tafi daga ƙasarsa.3Amma zan taurare zuciyar Fir'auna, kuma zan bayyana alamu masu yawa na iko na, abubuwa masu ban mamaki, cikin ƙasar Masar.4Amma Fir'auna ba zai saurare ku ba, saboda haka zan saukar da hannuna bisa Masar in kuma kawo ƙungiyoyin mayaƙana, mutanena, zuriyar Isra'ila, daga cikin ƙasar Masar da manyan ayyuka na shara'antawa.5Masarawa zasu sani Ni ne Yahweh sa'ad da na miƙa hannuna bisa Masar na kuma fito da Isra'ilawa daga cikin su."6Sai Musa da Haruna suka aikata haka; suka yi dai-dai kamar yadda Yahweh ya dokace su.7Musa yana da shekara tamanin, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku a lokacin da suka yi magana da Fir'auna.8Yahweh ya cewa Musa da Haruna,9"Idan Fir'auna yace maku, 'Ku yi abin al'ajibi,' sai ka ce wa Haruna, 'Ka ɗauki sandarka ka kuma jefa ta ƙasa a gaban Fir'auna, domin ta zama maciji.'"10Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir'auna, sai kuma suka yi kamar yadda Yahweh ya umarce su. Haruna ya jefar da sandarsa ƙasa a gaban Fir'auna da bayinsa, sai ta zama maciji.11Sai Fir'auna shima ya kira masu hikimarsa da masu duba. Sai su ma suka yi haka ta wurin sihiri.12Kowanne mutum ya jefar da sandarsa ƙasa, sai sandunan suka zama macizai. Amma sai macijin Haruna ya haɗiye macizansu.13Amma zuciyar Fir'auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar yadda Yahweh ya faɗa tun dã.14Yahweh ya cewa Musa, "zuciyar Fir'auna ta yi tauri, kuma ya ƙi ya bar mutanen su tafi.15Ka tafi wurin Fir'auna da safe lokacin da ya fita wurin ruwan. Ka tsaya daga bakin kogin don ka tarye shi, ka kuma ɗauki sandarka a hannunka sandar da ta zama maciji.16Ka ce masa, 'Yahweh, Allah na Ibraniyawa, ya aike ni gare ka in ce maka, "Ka bar mutanena su tafi, don su yi mani sujada cikin jeji. Har yanzu baka saurara ba."17Yahweh ya faɗi wannan: "Ta haka zaka sani Ni ne Yahweh. Zan bugi ruwa na Kogin Nilu da sandar dake a hannuna, sai kuma ruwan ya zama jini.18Kifayen da suke a cikin kogin za su mutu, kuma kogin zai yi ɗoyi. Masarawa ba za su iya shan ruwa daga kogin ba.'""19Sai Yahweh yace da Musa, "Ka ce wa Haruna, 'Ka ɗauki sandarka ka miƙa ta zuwa ga ruwayen Masar, da kuma zuwa ga kogunansu, da rafufukansu, da kududdufansu, da kuma dukkan tafkunansu, domin ruwayensu sun zama jini. Ka yi wannan domin a sami jini cikin dukkan ƙasar Masar, har ma da randunan itace da na duwatsu.'"20Sai Musa da Haruna suka yi kamar yadda Yahweh ya umarta. Haruna ya miƙa sandar ya kuma bugi ruwan kogin, a gaban Fir'auna da bayinsa. Sai dukkan ruwaye na kogunan suka zama jini.21Kifayen kogin suka mutu, sai kogin ya fara ɗoyi. Masarawa ba su iya shan ruwa daga kogin ba, kuma sai jinin ya bazu ko'ina a cikin ƙasar Masar.22Amma masu sihiri na Masar suka yi haka dai-dai da dabonsu. Amma zuciyar Fir'auna an taurare, sai kuma ya ƙi ya saurari Musa da Haruna, kamar yadda Yahweh ya faɗi zai faru.23Sai Fir'auna ya juya ya koma gidansa. Bai ma ba da hankalinsa ga wannan ba.24Dukkan Masarawa suka haƙa rami a gefen kogin don su sami ruwa su sha, amma ba su iya shan ruwan kogin da kansa ba.25Kwana bakwai suka wuce bayan da Yahweh ya kai farmaƙi ga kogin.
"Zan sa Fir'auna ya ɗauke ka kamar wani allah ne kai"
A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. Ana maganar taurin kansa kamar zuciyar sa ne ya yi tauri. Duba yadda aka juya wannan a 4:21. AT: "Fir'auna zai zama da taurin kai"
Kalamun nan "alamu" da "mu'ajjizai" a takaice na nufin abu ɗaya ne. Allah yana amfani ne da su yă nanata yawan abinda zai yi a Masar.
Kalamun nan "hannuna" na nufin Yawan Ikon Allah. AT: "yi amfine da iko na gãba da ku ...nuna ayyukan iko na gãba da"
AT: "Idan Fir'auna ya ce ku yi wani al'ajibi, sai ka ce wa Haruna yă ɗauki sandarsa yă jefa shi ƙasa a gaban Fir'auna, domin yă zama maciji"
"cinye"
A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. Anan maganar taurin kansa kamar zuciyarsa ne ta taurara. AT: "Zuciyar Fir'auna ya yi kanta"
A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. Ana maganar taurin kansa kamar zuciyarsa ne ta taurara. Duba yadda aka fasara wannan a 7:11. AT: "Fir'auna na da taurin kai"
A nan iya kara haske ga wannan bayanin. AT: "da ya fito zuwa kogin Nilu"
"ka ce wa Fir'auna"
...
"a kowane yankin"
Anan "zuciya" na nufin Fir'auna. Ana maganar taurin kansa kamar zuciyarsa ne ta taurara. Duba yadda aka fasara wannan a 7:11. AT: "Fir'auna ya zama da taurin kai"
Ana iya fadin sunan wannan kogin. AT: "a cikin kogin Nilu"
Wannan maganan faɗaɗawane kuma ana amfani da shi ne domin a nuna tsananin matsalar. AT: "Masarawa da dama"
1Sai Yahweh ya yi magana da Musa, "Ka tafi wurin Fir'auna ka kuma ce masa, 'Yahweh ya faɗi wannan: "Ka bar mutanena su tafi domin suyi mani sujada.2Idan ka ƙi ka barsu su tafi, zan azabtar da dukkan ƙasarka da ƙwaɗi.3Kogunan za su cika da kwaɗi. Za su fito su shiga gidajenku, da ƙuryar ɗakinku, da kan gadonku. Za su shiga cikin gidajen bayinku. Za su kai ga mutanenka, cikin murhunka, da kuma cikin makwaɓan ƙullunka.4Kwãɗin za su hau kanka, da mutanenka, da kuma dukkan bayinka.""'5Yahweh ya cewa Musa, "Ka ce wa Haruna, 'Miƙa hannun ka tare da sandarka bisa kogunan, da rafufuka, da kuma kududdufai, ka kawo kwãɗi bisa ƙasar Masar."'6Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwayen Masar, sai kwãɗin suka zo suka rufe dukkan ƙasar Masar.7Amma bokayen suka aikata irin haka da dabonsu; suka kawo kwãɗi bisa ƙasar Masar.8Sai Fir'auna ya kirawo Musa da Haruna ya kuma ce, "Ku yi addu'a ga Yahweh don ya kawar da kwãɗin daga gare ni da mutanena. Sa'an nan zan bar mutanen su tafi, domin su yi masa hadaya."9Musa ya cewa Fir'auna, "Kana iya samun zarafin gaya mani in yi maka addu'a, da bayinka, da kuma mutanenka, don a kawar da kwãɗin daga gare ku da gidajenku su kuma tsaya a cikin kogin kawai."10Fir'auna yace, "Gobe." Musa yace, "Bari shi zama yadda ka faɗa, don ka san cewa babu wani kamar Yahweh, Allahnmu.11Kwãɗin za su bar ka, da gidajenka, da bayinka, da kuma mutanenka. Za su tsaya cikin kogi ne kawai."12Sai Musa da Haruna su ka fito daga gaban Fir'auna. Sai Musa ya yi kuka ga Yahweh game da kwãɗin da ya kawo bisa Fir'auna.13Yahweh ya aikata kamar yadda Musa ya roƙa: Sai kwãɗin suka mutu cikin gidajen, daga shirayi, da filaye.14Sai mutanen suka tara su tuli-tuli, sai kuma ƙasar ta yi ɗoyi.15Amma da Fir'auna ya ga cewa akwai sauƙi, sai ya taurare zuciyarsa bai kuma saurari Musa da Haruna ba, kamar yadda Yahweh yace zai yi.16Yahweh ya cewa Musa, "Ka ce da Haruna, 'Ka miƙa sandarka ka bugi ƙurar ƙasa, don ta zama kwarkwata cikin dukkan ƙasar Masar."'17Suka aikata haka: Haruna ya miƙa hannunsa da sandarsa. Ya bugi ƙura a ƙasa. Sai kwarkwata masu yawa suka zo bisa mutum da dabba. Dukkan ƙurar ƙasa ta zama kwarkwata cikin dukkan ƙasar Masar.18Sai bokayen su ma suka gwada da sihirinsu domin su fito da kwarkwata, amma ba su iya yin haka ba. Aka sami kwarkwata a bisa mutane da kuma dabbobi.19Sai bokayen suka ce wa Fir'auna, "Wannan yatsan Allah ne." Amma zuciyar Fir'auna ta taurare, don haka bai saurare su ba. Dai-dai ne ga yadda Yahweh ya faɗi cewa Fir'auna zai yi.20Yahweh ya cewa Musa, "Ka tashi da sauri da safe ka kuma tsaya a gaban Fir'auna yayin da ya fito zuwa kogi. Ka ce da shi, 'Yahweh ya faɗi wannan: "Ka bar mutanena su tafi don suyi mani sujada.21Amma idan baka bar su sun tafi ba, zan aiko da cin-cirindon ƙudaje gareka, zuwa ga bayinka, da kuma mutanenka, da kuma cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da cin-cirindon ƙudaje, har ma da ƙasar da suke tsayawa za ta cika da ƙudaje.22Amma a wannan ranar zan bambanta ƙasar Goshen, ƙasar da mutanena suke zama, don kada a sami wani cin-cirindon ƙudaje a nan. Wannan zai faru domin ka san cewa Ni ne Yahweh da nake tsakiyar wannan ƙasa.23Zan bambanta tsakanin mutanena da mutanenka. Wannan alama ce ta ikona zai faru gobe.""'24Yahweh ya yi haka, sai kuma cin-cirindon ƙudaje mai kauri suka aukawa gidan Fir'auna da kuma gidajen bayinsa. Cikin dukkan ƙasar Masar, ƙasar ta lalace ta dalilin cin-cirindon ƙudajen.25Sa'an nan Fir'auna ya kira Musa da Haruna yace, "Ku tafi, ku yi hadaya ga Allahnku a cikin ƙasarmu."26Musa yace, "Bai yi dai-dai ba muyi haka, gama hadayar da muke yi ga Yahweh Allahnmu abar ƙyama ce ga Masarawa. Idan muka miƙa hadayar suna gani abin ƙyama ga Masarawa, ba zasu jejjefemu ba?27Ba haka ba, tafiyar kwana uku ce cikin jeji da ya kamata muyi, domin muyi hadaya ga Yahweh Allahnmu, kamar yadda ya umurce mu."28Fir'auna yace, "Zan bar ku don ku tafi ku yiwa Allahnku hadaya cikin jeji. Sai dai kada ku tafi da nisa sosai. Ku yi mani addu'a.29Musa yace, "Da zarar na fita daga gare ka, zan yi roƙo ga Yahweh domin cin-cirindon ƙudaje su bar ka, Fir'auna, da bayinka da kuma mutanenka gobe. Amma kada ka ƙara yin yaudara ta wurin ƙin barin mutanenmu su tafi su yiwa Yahweh hadaya."30Sai Musa ya fita daga gaban Fir'auna ya kuma yi roƙo ga Yahweh.31Yahweh ya yi yadda Musa ya roƙa; ya kuma janye cin-cirindon ƙudaje daga Fir'auna, da bayinsa, da mutanensa. Babu wanda ya rage32Amma Fir'auna ya taurare zuciyarsa wannan lokaci kuma, ya kuma ƙi barin mutanen su tafi.
"kogin Nilu
Waɗannan su ne kwanukan da ake hada gurasa.
...
...
...
...
...
"Sai Fir'auna ya kirawo Musa da Haruna"
"Kana iya zaban lokacin da zan yi maka addu'a" ko kuma "Kana iya zaben lokacin da zan maka addu'a"
...
"Fir'auna ya taurare zuciyarsa." Anan "taurare" na nufin cewa ya zama da taurin kai.
kamar yadda Yahweh ya ce Fir'auna zai yi"
...
...
...
Kalmar nan "aiki" anan na nufin ikon Allah. AT: "Ai wannan aikin ikon Allah ne"
A nan "zuciya" na nufin. A nan maganar taurin kansa kamar zuciyarsa ne ta taurara. Duba yadda aka juya wannan a 7:11.AT: "Zuciyar Fir'auna ya yi kanta"
"ka je gaban Fir'auna"
"Ka ba mutane na yanci"
Yahweh ya cigaba da magana da Fir'auna ta bakin Musa.
Wannan wata hanya ce na cewa "a gaban mutum." AT: "a gabansu"
Musa yana wannan tambayan ne domin a nuna wa Fir'auna cewa Masarawa ba za su yarda wa Isra'ilawa su yi wa Yahweh sujada ba. AT: "lallai za su jejefe mu!"
AT: "ka yi mana gaskiya, ka bar mu da jama'ar mu mu tafi"
"Kada ka yauɗare mu ko kuma "kada ka ruɗe mu"
A nan "zuciya" na nufin. A nan maganar taurin kansa kamar zuciyarsa ne ta taurara. Duba yadda kuka juya wannan a 7:11. AT: "Zuciyar Fir'auna ya yi kanta"
1Sa'an nan Yahweh yace da Musa, "Jeka wurin Fir'auna ka ce masa, 'Yahweh, Allah na Ibraniyawa, ya faɗi wannan: "Bar mutanena su tafi domin suyi mani sujada."2Amma idan baka yarda ka bar su ba, idan ka hana su,3daganan hannun Yahweh zai kasance bisa garken shanunka cikin filaye da kuma bisa dawakai, da jakuna, da raƙuma, garkunan dabbobi, da garkunan tumaki da awaki, kuma zai yi sanadiyar cuta mai banrazana.4Yahweh zai bambanta garken Isra'ilawa da ta Masarawa kuma babu dabbar dake ta Isra'ilawa da za ta mutu.5Yahweh ya tsayar da lokaci; ya riga yace, "Gobe ne zan aikata wannan abin cikin ƙasar.""'6Yahweh ya yi wannan washegari: Dukkan garkunan shanun Masar suka mutu, amma babu dabbar da ke ta Isra'ila da ta mutu, ko dabba ɗaya.7Fir'auna ya yi bincike, kuma, duba, ko da ɗaya na dabbar Isra'ilawa bata mutu ba. Amma zuciyarsa ta taurare, don haka bai yadda mutanen su tafi ba.8Sai Yahweh ya cewa Musa da Haruna, "Ku ɗebo toka daga murhu. Kai, Musa, dole ka watsa tokar sama cikin iska yayin da Fir'auna na gani.9Za su zama ƙura mai laushi bisa dukkan ƙasar Masar. Za su yi sanadiyar gyambuna da kuma marurai su addabi mutane da dabbobi cikin dukkan ƙasar Masar."10Sai Musa da Haruna suka ɗebo toka daga murhu suka kuma tsaya a gaban Fir'auna. Sai Musa ya watsar da tokar cikin iska. Tokar ta yi sanadiyar gyambuna da marurai da suka addabi mutane da dabbobi.11Bokayen ba su iya tsayayya da Musa ba sabili da gyambunan, domin gyambunan sun kama su da sauran Masarawa.12Yahweh ya taurare zuciyar Fir'auna, don haka Fir'auna bai saurari Musa da Haruna ba. Wannan kamar yadda Yahweh ya riga ya gaya wa Musa ne cewa Fir'auna zai yi.13Sai Yahweh yace wa Musa, "Ka tashi da sassafe, ka tsaya a gaban Fir'auna, ka kuma ce masa, 'Yahweh, Allah na Ibraniyawa, ya faɗi wannan: "Ka bar mutanena su tafi domin suyi mani sujada.14Gama a wannan karon zan aiko da dukkan annobaina a kanka, a bisa bayinka da mutanenka. Zan aikata wannan domin ka san cewa babu wani mai kama da ni cikin dukkan duniya.15Ko a yanzu da na miƙa hannuna in kai maka farmaki da mutanenka da cuta, kuma da yanzu an kawar da kai daga ƙasar.16Amma sabili da wannan dalili ne na bar ka ka tsira: Domin in nuna maka ikona, domin a shaida sunana a cikin dukkan duniya.17Har yanzu kana ɗaukaka kanka gãba da mutanena da har yanzu baka barsu su tafi ba.18Ka saurara! Gobe warhaka zan kawo ruwa da ƙanƙara mai ƙarfi, irin wadda ba a taɓa gani ba a cikin ƙasar Masar ba tun lokacin da aka kafa ta zuwa yau.19Yanzu dai, ku aika mazaje su dawo da garken ku da dukkan abin da kuke da shi a cikin gonaki zuwa ga mafaka. Kowanne mutum da dabba dake a gona da ba a shigo da su gida ba - ƙanƙarar zata faɗo masu, za su kuma mutu.""'20Sa'an nan wasu daga cikin bayin Fir'auna waɗanda suka gaskanta da saƙon Yahweh suka yi hanzari suka dawo da bayinsu da kuma garkensu cikin gidaje.21Amma waɗanda ba su ɗauki maganar Yahweh da wani mahimmanci ba suka bar bayinsu da garken su cikin gonaki.22Sai Yahweh yace wa Musa, "Miƙa hannunka zuwa sararin sama don a yi ƙanƙara cikin dukkan ƙasar Masar, bisa mutane, bisa dabbobi, da kuma dukkan itatuwan cikin gonaki a dukkan ƙasar Masar."23Sai Musa ya miƙa sandarsa zuwa sararin sama, sai Yahweh ya aiko da aradu, ƙanƙara, da walkiya a ƙasar. Ya kuma kwararo ruwan ƙanƙara a bisa ƙasar Masar.24Saboda haka aka yi ƙanƙara da walƙiya gauraye da ƙanƙarar, mai tsananin gaske, irin da ba a taɓa yi ba cikin dukkan ƙasar Masar tun lokacin da ta zama al'umma.25A dukkan ƙasar Masar kuwa, ƙankaran ta bugi kowanne abu cikin gonaki, da mutane da kuma dabbobi. Ta bugi kowacce shuka dake a gonaki ta kuma karya kowanne itace.26A ƙasar Goshen ne kaɗai, inda Isra'ilawa ke zama, babu ƙanƙara.27Daga nan sai Fir'auna ya aika da mutane su kawo Musa da Haruna. Ya ce masu, "Na yi zunubi dai yanzu. Yahweh mai adalci ne, ni kuwa da mutanena mugaye ne.28Ku yi addu'a ga Yahweh, domin waɗannan tsawa mai ƙarfi da kuma ƙanƙara sun yi yawa. Zan barku ku tafi, ba kuma zaku zauna nan ba."29Musa yace masa, "Da zarar na fita daga birnin, zan buɗe hannuwana ga Yahweh. Tsawar aradun zata tsaya, kuma babu sauran ƙanƙara. Ta haka zaka sani cewa duniyar ta Yahweh ce.30Amma game da kai da bayinka, Na san da cewa har yanzu baka rigaya ka girmama Yahweh Allah ba da gaske."31Yanzu dai da hatsi da kuma riɗi an lallatar da su, gama riɗi ta yi ido, hatsi kuma tana fidda kai.32Amma alkama da gero ba a ji masu rauni ba domin ba su yi girma ba tukuna.33Bayan da Musa ya bar Fir'auna da kuma birnin, ya miƙa hannuwansa ga Yahweh; tsawa da ƙanƙara suka tsaya, sai kuma ruwan sama bai sake saukowa ba.34Sa'ad da Fir'auna ya ga cewa ruwan sama ya tsaya, da ƙanƙarar, da tsawar aradun sun tsaya, sai ya sake yin zunubi ya taurare zuciyarsa, duk da bayinsa.35Zuciyar Fir'auna ta taurare, don haka bai bar mutanen Isra'ila su tafi ba. Yadda Yahweh ya riga ya faɗa wa Musa cewa Fir'auna zai aikata.
Yahweh ya cigaba da magana da Musa game da Fir'auna da Fitowar 'yan Ibraniyawa daga Masar.
Waɗannan jimlar suna da ma'ana ɗaya ne a takaice. Za su nanata wa Fir'auna abinda zai idan Fir'auna ya yi haka. AT: "Idan ka cigaba da hana su tafiya"
Kalmar nan "hannu" a nan na nufin Ikon Yahweh da ke iya sa wa dabbobin cuta. AT: "to, ikon Yahweh zai auko bisa dabbobin ku da cuta"
Kalmar nan "ku" anan na nufin jama'ar Masar da ke da shanikai.
A nan "Isra'ila" na nufin jama'ar Isra'ila. AT: "shanikan da ke na jama'ar Isra'ila"
A nan "Masar" na nufin jama'ar Masar. AT: "shanikan jama'ar Masar"
"sa lokaci" ko kuma "kaɓe lokaci"
Ana faɗin wannan ne domin a nanata tsanani wannan yanayin. AT: "shanikai da yawa a Masar sun mutu"
A nan "Masar" na nufin jama'ar Masar. AT: "shanikan jama'ar Masar"
Fir'auna ya nemi dukkan shadodi game da zancen.
"sai ga" a nan yana nuna mamakin da Fir'auna ya yi da abinda ya gani.
"A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. AT: "ya ƙi yă canza zuciyarsa"
wutar makera
"ƙanana sosai" ko kuma "kura"
"su bullo a bisa"
A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. Ana maganar taurin kansa kamar zuciyarsa ne ta taurara. Duba yadda aka juya wannan a 7:11. AT: "Zuciyar Fir'auna ya yi kanta"
Wannan na nufin Fir'auna da kansa ma zai ju zafin duk annoba da Allah zai aiko.
Kalmar nan "haka" na nufin su annoban da Musa ya yi wa Fir'auna magana akai.
A nan "hannu na" na nufin Ikon Allah. AT: "yi amfani da iko na in buge ka"
AT: "domin jama'a na ko ina sun san cewa ni mai girma ne"
Ana maganar hamayyar Fir'auna ne ta wurin hana 'ya'yan Isra'ila tafiya su yi wa Allah sujada kamar yana girmama kansa ne ta wurin zama masu cikas.
"Ku sa hankali ga wannin abu mai muhimmanci da zan gaya maku"
"kira"
"Musa ya ce wa Fir'auna"
"Wannan wata alama ce ta addu'a. AT: "yaɗa hannaye na in yi addu'a ga Yahweh"
"Darajanta Yahweh ya kunshe yi masa biyayya da kuma rayuwa a hanyar da ke nuna girmar sa.
Wannan wata tushe ce ca ke da jijiyoyi da ake iya yin kayyayakin lilin da su.
Wannan wata irin hatsi ce da ake yin gurasa da ita; shanaki ma na iya ci.
Wannan wata irin alkama ce.
A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. Ana maganar taurin kansa kamar zuciyarsa ne ta taurara. AT: "Zuciyar Fir'auna ya yi kanta"
A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. Ana maganar taurin kansa kamar zuciyarsa ne ta taurara. Duba yadda aka juya wannan a 7:11. AT: "Zuciyar Fir'auna ya yi kanta"
1Yahweh ya cewa Musa, "Ka tafi wurin Fir'auna, gama na taurare zuciyarsa da zuciyar bayinsa. Na yi haka ne domin in nuna waɗannan alamun ikon ƙarfina a cikin su.2Na kuma yi haka ne domin ku gaya wa 'ya'yanku da jikokinku abubuwan dana yi, yadda na fusata bisa Masar, da kuma yadda na nuna alamu daban-daban na ƙarfin ikona a tsakaninsu. Da haka zaku sani Ni ne Yahweh."3Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir'auna suka kuma ce masa, "Yahweh, Allah na Ibraniyawa, ya faɗi wannan: 'Har yaushe zaka ƙi ka ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin suyi mani sujada.4Amma idan ka ƙi ka bar mutanena su tafi, ka saurara, gobe zan kawo fãri cikin ƙasarka.5Za su rufe fuskar ƙasa har babu wanda zai iya ganin ƙasa. Za su chinye kowanne abin da ya tsira daga ƙanƙara. Za su kuma cinye kowanne itacen da ya tsiro domin ka cikin gonaki.6Za su cika gidajenka, da na bayinka, da na dukkan Masarawa - abu ne wanda mahaifinka da kakanka basu taɓa gani ba, abin da ba a taɓa gani ba tun daga ranar da suke cikin duniya har wa yau.'" Daga nan Musa ya fita ya kuma bar Fir'auna.7Sai bayin Fir'auna suka ce masa, "Har yaushe wannan mutum zai zama mana bala'i? Ka bar Isra'ilawan su tafi domin su yi wa Yahweh Allahnsu sujada. Ko ba ka fahimci cewa an hallakar da Masar ba?"8Aka kawo Musa da Haruna kuma a gaban Fir'auna, sai yace masu, "Ku tafi ku yiwa Yahweh Allahnku sujada. Amma waɗanne mutane ne za su tafi?"9Musa yace, "Za mu tafi tare da ƙanananmu da kuma tsofofinmu, tare da 'ya'yanmu maza da 'ya'ya mata. Zamu tafi da tumakanmu da garkenmu, gama dole ne muyi buki ga Yahweh."10Fir'auna yace masu, "Bari Yahweh lallai ya kasance tare da ku, idan har na barku ku tafi tare da 'yan ƙanananku. Duba, kana da wata mugunta a cikin zuciya.11Ba haka ba! Ku tafi, mazaje kawai na cikinku, ku yiwa Yahweh sujada, gama abin da kuke so kenan." Sa'an nan aka kori Musa da Haruna daga fuskar Fir'auna.12Sai Yahweh ya cewa Musa, "Ka miƙa hannunka bisa ƙasar Masar zuwa ga fãrin, domin su abko wa ƙasar Masar su kuma cinye dashe-dashen cikin ta, dukkan sauran abubuwan da ƙanƙara ta rage."13Musa ya miƙa sandarsa bisa Masar, Yahweh kuwa ya aiko da iskar gabas bisa ƙasar dukkan wannan rana da dare. Sa'ad da safiya ta yi, iskar gabas ta riga ta kawo fãrin.14Fãrin suka shiga dukkan ƙasar Masar suka kuma cutar da dukkan sassanta. Ba a taɓa yin irin wannan cin-cirindon fãri cikin ƙasar ba, ba kuma za a sake mai kamannin haka ba.15Suka rufe fuskar dukkan ƙasa har wuri ya yi duhu. Suka cinye dukkan dashe-dashe da ke cikin ƙasa da dukkan 'ya'yan itatuwan da ƙanƙara ta rage. A cikin dukkan ƙasar Masar, babu koren tsiro mai rai da ta ragu, ko wani itace ko dashe a cikin gonaki.16Sa'an nan Fir'auna ya kirawo Musa da Haruna ya kuma ce, "Na yi zunubi ga Yahweh Allahnku, da gare ku kuma.17Yanzu dai, ku gafarta zunubi na wannan kãron, kuyi addu'a ga Yahweh Allahnku don ya ɗauke wannan mutuwa daga gare ni."18Don haka Musa ya fita daga gaban Fir'auna ya yi addu'a ga Yahweh.19Yahweh ya kawo babbar iskar yamma mai ƙarfi da ta kwashe fãrin ta kora su cikin Jan Teku; babu fãrar da ta rage cikin dukkan lardunan Masar.20Amma Yahweh ya taurare zuciyar Fir'auna, kuma Fir'auna bai bar Isra'ilawa su tafi ba.21Sai Yahweh ya cewa Musa, "Ka miƙa hannunka zuwa sararin sama, don a yi duhu bisa ƙasar Masar, duhun da za a iya taɓawa."22Sai Musa ya miƙa hannunsa zuwa sama, sai aka yi wani gaggarumin duhu bisa dukkan ƙasar Masar har na kwana uku. Babu wanda ya iya ganin wani;23Babu wanda ya bar gidansa har kwana uku. Duk da haka, dukkan Isra'ilawa suna da haske a wurin da suke zaune.24Sai Fir'auna ya aika aka kawo Musa sai yace, "Ku tafi ku yi wa Yahweh sujada. Har da iyalanku na iya tafiya tare da ku, amma garkunan ku na tumaki dole ku bar su nan."25Amma Musa yace, "To dole ka ba mu dabbobin da zamu yi hadaya ga Yahweh Allahnmu.26Garkunan mu dole mu tafi da su; babu ko ƙofaton su da zai rage a baya, gama dole ne mu tafi da su domin yin sujada ga Yahweh Allahnmu. Gama ba mu san da mene ne za mu yi sujada ga Yahweh ba, sai mun isa can."27Amma sai Yahweh ya taurare zuciyar Fir'auna, har da ba zai bar su su tafi ba.28Fir'auna ya cewa Musa, "Ka fita daga gare ni! Kayi hankali da abu ɗaya, cewa kada ka ƙara gani na, gama duk ranar da ka ga fuskata, za ka mutu."29Sai Musa yace masa, "Kai da kanka ka faɗa. Ba zan ƙara ganin fuskarka ba."
Yahweh yana maganar taurara zukatan Fir'auna da na barorinsa ne kamar yana sa zukatansu su yi tauri ne.
"da ban-da ban"
Wannan kalmar yana kara nanata maganar da ya biyo baya ne. AT: "Ku sa hankali ga wannin abu mai muhimmanci da zan gaya maku"
Ƙanƙara wata ruwa ce da ke a daskare yayin da yake faduwa daga gajimare.
AT: "abinda ba wanda ya taɓa gani"
...
Fir'auna yana wannan tambayan ne domin ya nuna irin hallaka da bala'i da ya sauko a ƙasar Masar. Wannan tambayan ganganci ne. AT: "Ba za mu bar wannan mutumin yă cigaba da jawo mana bala'i ba!"
Barorin Fir'auna suna wannan tambayan ne domin su sa Fir'auna ya gane abinda ya ki gani. A nan iya sanar da wannan tambayn gangancin a wata hanya da ba tambaya ba. AT: "Yakama ka gane da cewa Masar ta lalace!"
AT: "cewa waɗannan annoban sun lalatar da Masar" ko kuma "cewa Allahn su ya lalatar da Masar"
Fir'auna yana faɗin wannan ne domin yă nanata cewa ba zai bar Musa su ɗauki 'ya'yansu zuwa wurin sujada ga Yahweh ba.
AT: "Sai Fir'auna ya kore Musa da Haruna daga gabansa" ko kuma "Sai Fir'auna ya sa barorinsa su kore Musa da Haruna daga gabansa"
Fara sun cika ƙasar ne har ko ina ta yi duhu. AT: "har sun duhunta ƙasar" ko kuma "har ƙasar ya zama da duhu"
"kuma"
Kalmar nan "mutuwa" a nan na nufin lalacin da farar suka jawo gonakin Masar, wadda zai kai ga mutuwar mutanen domin ba za a samu abinci a gonaki kuma ba. A nan iya kara haske a wannan bayani. AT: daina wannan hallaka da zi kai mu ga mutuwa"
"ta hura farar"
A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. Ana maganar taurin kansa kamar zuciyarsa ne ta taurara. Duba yadda aka juya wannan a 9:11 . AT: "Zuciyar Fir'auna ya yi kanta" (Dubi: and )
Yahweh yana maganar matuƙar duhu ne kamar ya yi ƙauri ne da har mutane za su iya cafkewa a hannayensu. AT: "duhu na tinjim da mutane ke iya cafkewa da hannayen su"
A nan kalmar nan "kofato" na nufin dabban gabaɗaya. AT: "ba za mu iya barin ko dabba guda ba"
A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. Ana maganar taurin kansa kamar zuciyarsa ne ta taurara. Duba yadda aka juya wannan a 9:11. AT: "sa zuciyar Fir'auna ta yi kanta"
"Fir'auna ba zai bar su su tafi ba"
"Ka dai tabbatar da abu ɗaya"
A nan kalmar nan "fuska" na nufin mutumin gabaɗaya. AT: "ka ganni"
Da waɗannan kalamu ne Musa ya nanata cewa Fir'auna yana faɗin gaskiya. AT: "Abinda ka faɗa gaskiya ne kam"
1Daga nan Yahweh ya cewa Musa, "Akwai sauran annoba guda ɗaya da zan kawo bisa Fir'auna da Masar. Bayan wannan, zai barku ku tafi daga nan. Sa'ad da a ƙarshe ya barku kuka tafi, zai kore ku gaba ɗaya.2Ka umarci mutanen cewa kowanne mutum da kowacce mace su roƙi maƙwabcinsa ko maƙwabciyarta kayayyakin azurfa da kayayyakin zinariya."3Yanzu dai Yahweh ya sa Masarawa suyi ɗokin farantawa Isra'ilawa rai. Bugu da ƙari, mutumin nan Musa ya birge sosai a gaban barorin Fir'auna da mutanen Masar.4Musa yace, "Yahweh ya faɗi wannan: 'Wajen tsakar dare zan ratsa cikin dukkan Masar.5Dukkan 'ya'yan fãri cikin ƙasar Masar za su mutu, daga ɗan fãrin Fir'auna, wanda ke zaune bisa kursiyinsa, zuwa ɗan fãrin baiwa wanda ke bayan dutsen niƙa tana niƙa, da dukkan 'ya'yan fãrin dabbobi.6Daga nan za a yi babban makoki cikin dukkan ƙasar Masar, irin wanda ba a taɓa yi ba kuma ba za a ƙara yi ba.7Amma babu ko kare da zai yi haushi ga ko ɗaya daga cikin mutanen Isra'ila, ko ga mutum ko dabba. Ta wannan hanya za ku sani cewa ina nuna bambanci tsakanin Masarawa da Isra'ilawa.'8Dukkan waɗannan bayin naka, Fir'auna, za su sauko zuwa gare ni su rusuna mani. Za su ce, 'Ka tafi, kai da dukkan mutanen da suka biyo ka!' Bayan wannan zan fita." Daga nan ya fita daga wurin Fir'auna da babban fushi.9Yahweh ya cewa Musa, "Fir'auna ba zai saurare ka ba. Wannan ya zama haka ne domin in aiwatar da abubuwan ban mamaki masu yawa a cikin ƙasar Masar."10Musa da Haruna suka yi dukkan waɗannan al'ajibai a gaban Fir'auna. Amma Yahweh ya kangarar da zuciyar Fir'auna, Fir'auna kuma bai bar mutanen Isra'ila suka fita daga ƙasarsa ba.
Duk inda akayi amfani da kalmar nan "ku" a wannan aya ana maganar Musa ne da sauran Isra'ilawa.
Wato ƙarfe 12 na dare kenan.
"ɗan farin" na nufin 'yan fari na dabbobi da mutane.
Wannan jimlar na nufin Fir'auna.
"wadda ke niƙa a wurin dutsen niƙa" ko kuma "wadda ke niƙa hatsi a wurin niƙa"
Wannan na nufin Musa da jama'ar Isra'ila za su bar Masar. AT: "Daga nan zan fita daga nan" ko kuma "Daga nan zan fita daga Masar"
A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. Ana maganar taurin kansa kamar zuciyarsa ne ta taurara. Duba yadda aka juya wannan a 9:11. AT: "Zuciyar Fir'auna ya kara yin kanta"
1Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna a cikin ƙasar Masar. Ya ce,2"Game da ku, wannan wata zai zama farawar watanni, watan farko na shekara a gare ku.3Ka faɗa wa taron Isra'ila, 'A ranar goma ga wannan watan dole ne kowannen su ya ɗauki ɗan rago ko ɗan akuya domin kansu, kowanne iyali na yin wannan, ɗan rago domin kowanne gida.4Idan gidan ya yi ƙanƙanta sosai domin ɗan rago, mutumin da makwabcinsa zasu ɗauki naman ɗan rago ko ɗan akuya wanda zai isa domin adadin mutanen. Ya kasance ya isa domin kowanne mutum ya ci, saboda haka dole su ɗauki isasshen nama domin dukkan su su ci.5Ɗan ragonku ko ɗan akuyan dole ya zama marar aibi, ɗan shekara ɗaya m. Kuna iya ɗaukar ɗaya daga cikin tumaki ko awaki.6Tilas ku ajiye ta har sai ranar sha huɗu ga wata. Daga nan dukkan taron Isra'ila tilas su yanka waɗannan dabbobi da hasken asuba.7Tilas ku ɗiba daga cikin jinin ku kuma sanya a dokin ƙofa gefe biyu da saman ginshiƙan ƙofofin gidajen inda zaku ci naman.8Tilas ku ci naman a wannan daren, bayan an gasa da farko a bisa wuta. A ci shi da gurasa da akayi ba da gami ba, tare da ganye mai ɗaci.9Kada ku ci shi ɗanye ko dafaffe cikin ruwa. A maimako, ku gasa shi bisa wuta tare da kansa, kafafunsa da kayan cikinsa.10Tilas ba za ku bar wani daga cikinsa ba ya rage har safiya. Tilas ku ƙone duk abin da ya rage har safiya.11Ga yadda tilas zaku ci shi: tare da ɗamararku a ɗaure, takalmanku bisa tafin ƙafarku, da sandarku a hannunku. Tilas ku ci shi da hanzari. Ƙetarewa ne na Yahweh.12Yahweh ya faɗi wannan: zan ratsa ta cikin ƙasar Masar a wannan dare zan kuma kai hari ga dukkan 'ya'yan fãri na mutum da na dabba a cikin ƙasar Masar. Zan kawo horaswa ga dukkan allolin Masar. Ni ne Yahweh.13Jinin zai zama alama ne bisa gidajenku domin zuwa na a gare ku. Idan naga jinin, Zan ƙetare ku sa'ad da na kai hari ga ƙasar Masar.14Wannan annoba ba za ta zo bisan ku ba ta kuma hallaka ku. Wannan rana zata zama abar tunawa domin ku, wadda tilas ku kiyaye a matsayin bikin Yahweh. A koyaushe zai kasance shari'a a gare ku, cikin dukkan tsararrakin mutanenku, cewa tilas ku kiyaye wannan rana.15Zaku ci gurasa ba tare da gami ba a lokacin kwanakin bakwai. A rana ta farko zaku cire gami daga gidajenku. Duk wanda yaci gurasa mai gami daga ranar farko zuwa rana ta bakwai, wannan taliki tilas a datse shi daga Isra'ila.16A rana ta farko za ayi taro da za a keɓe a gare ni, a rana ta bakwai kuma za a sake yin wani irin wannan taron. Babu wani aikin da za ayi a cikin waɗannan kwanaki, sai dai girki domin kowa ya ci. Wannan ne kaɗai aikin da tilas ya zama mai yiwuwa a gare ku.17Tilas ku kiyaye wannan biki na gurasa marar gami saboda a wannan rana ce na fito da mutanenku, ƙungiya, ƙungiya na mayaƙa, daga cikin ƙasar Masar. Saboda haka tilas ku kiyaye wannan rana cikin dukkan tsararrakin mutanenku. Wannan a koyaushe zai zama shari'a a gare ku.18Tilas ku ci gurasa marar gami tun daga hasken asuba na ranar sha huɗu ga watan farko na shekara, har zuwa hasken asuba na ranar ashirin da ɗaya ga watan.19A lokacin waɗannan kwanaki bakwai, tilas kada a sami wani gami cikin gidajenku. Duk wanda ya ci gurasa da aka yi da gami tilas a datse shi daga cikin gundumar Isra'ila, koda wannan taliki baƙo ne ko kuma wanda aka haifa a cikin ƙasar.20Tilas ba zaku ci wani abin da akayi da gami ba. Duk inda kuka zauna, tilas ku ci gurasa da akayi ba tare da gami ba."'21Daga nan Musa ya yi sammace ga dukkan dattawan Isra'ila ya kuma ce masu, "Kuje ku zaɓi 'yan raguna ko 'yan awaki waɗanda za su isa ku ciyad da iyalanku sai ku kuma yanka su a matsayin ɗan ragon Ƙetarewa.22Daga nan sai ku ɗauki curin soso ku tsoma cikin jinin da zai kasance cikin kwano. Sai ku shafa jinin a bisa ginshiƙin ƙofa da dokin ƙofofi biyu. Kada waninku ya fita daga ƙofar gidansa har sai da safe.23Domin Yahweh zai ratsa ta ciki ya kai hari ga Masarawa. Idan yaga jinin a bisa ginshiƙin ƙofar da dokin ƙofa biyun, zai ƙetare ƙofarku kuma ba zai bada izini ga mai lalatarwa ba ya shigo cikin gidajenku ya kawo maku hari.24Tilas ku kiyaye wannan al'amari. Wannan a koyaushe zai zama shari'a domin ku da zuriyarku.25Idan kuka shiga ƙasar da Yahweh zai baku, kamar yadda ya yi alƙawari zai yi, tilas ku kiyaye wannan aikin sujada.26Idan 'ya'yanku suka tambaye ku, 'Mene ne ma'anar wannan aikin sujada?'27daganan tilas ku ce, 'hadayar Ƙetarewa ce ta Yahweh, saboda Yahweh ya ƙetare gidajen Isra'ilawa a Masar sa'ad da ya kai hari ga Masarawa. Ya 'yantar da gidajenmu."' Daga nan mutanen suka rusuna suka kuma yi sujada ga Yahweh.28Isra'ilawa suka tafi suka yi dai-dai yadda Yahweh ya umarci Musa da Haruna.29Ya kuwa faru a tsakar dare Yahweh ya kai hari ga dukkan 'ya'yan fãri dake cikin ƙasar Masar, daga ɗan fãrin Fir'auna, wanda ya zauna bisa kursiyi, har ya zuwa ɗan fãrin talikin dake cikin kurkuku da dukkan 'ya'yan fãrin dabbobi.30Fir'auna ya tashi da dare - shi, dukkan bayinsa, da dukkan masarawa. Akwai makoki mai ƙara a Masar, domin babu wani gida inda ba wanda ba a rasa wani da ya mutu ba.31Fir'auna ya yi sammace ga Musa da Haruna da dare ya kuma ce, "Ku tashi, ku fita daga cikin mutanena, ku da Isra'ilawa. Ku tafi, kuyi sujada ga Yahweh, kamar yadda kuka ce kuna so kuyi.32Ku ɗauki garken tumakinku dana awakinku da garken shanunku, kamar yadda kuka ce, ku kuma tafi, sai ku kuma albarkace ni."33Masarawa suna cikin babban hanzari su fitar dasu daga ƙasar, gama sun ce, "Dukkanmu zamu mutu."34Sai mutanen suka ɗauki ƙullinsu ba tare da sun ƙara wani gami ba. Kwanonin markaɗensu sun riga sun ɗaure cikin kayansu da bisa kafaɗunsu.35Yanzu mutanen Isra'ila sun yi yadda Musa yace masu. Suka roƙi Masarawa domin kayayyakin azurfa, da kayayyakin zinariya, da sutura.36Yahweh yasa Masarawa ɗokin farantawa Isra'ilawa rai. Sai masarawa suka basu komai game da abin da suka roƙa. Ta wannan hanyar, Isra'ilawa suka washe Masarawa.37Isra'ilawa suka yi tafiya daga Remasis zuwa Sukkot. Lissafinsu kimanin mazaje 600,000, baya ga ƙarin mataye da yara.38Gaurayen taron waɗanda ba Isra'ilawa ba ma suka tafi tare da su, tare da garkunan tumaki da awaki da na shanu, babban lissafin dabbobi.39Suka gasa gurasa marar gami daga cikin ƙullin da suka kawo daga Masar. Ya zama marar gami ne saboda an kore su daga Masar ba zasu kuma yi jinkirin shirya abinci ba.40Isra'ilawa sun yi zama a cikin Masar har shekaru 430.41A ƙarshen shekaru 430, a dai-dai wannan rana, dukkan ƙungiyoyin mayaƙan Yahweh suka fita daga ƙasar Masar.42Wannan dare ne na tsayawa a faɗake, domin Yahweh ya fito da su daga ƙasar Masar. Wannan daren Yahweh ne da za a kiyaye ga dukkan Isra'ilawa cikin dukkan tsararrakin mutanensu.43Yahweh ya cewa Musa da Haruna, "Wannan ne ka'ida domin Ƙetarewa: babu wani bare da mai yiwuwa yaci daga cikin sa.44Duk da haka, kowanne bawan Ba-isra'ile, da aka sawo da kuɗi, yana iya ci bayan kun yi masa kaciya.45Bare da bayin haya tilas ba za su ci wani daga cikn abincin ba.46Tilas a ci abincin cikin gida ɗaya. Tilas ba za ku ɗauki wani daga cikin abincin ba ku fita da shi waje, tilas kuma ba za ku karya wani ƙashi ba daga cikin sa.47Dukkan gundumar Isra'ila tilas su kiyaye wannan biki.48Idan bare yana zaune tare daku kuma yana so ya kiyaye Ƙetarewar ga Yahweh, dukkan danginsa maza tilas a yi masu kaciya. Daga nan zai yiwu su zo su kuma kiyaye shi. Zai zama kamar mutanen da aka haifa cikin ƙasar, Duk da haka, babu wani taliki marar kaciya da mai yiwuwa ya ci wani abu daga cikin abincin.49Wannan irin dokar za a zartar ga haifaffen garin da kuma bare dake zaune cikin ku.50Sai dukkan Isra'ilawa suka yi dai-dai yadda Yahweh ya umarci Musa da Haruna.51Sai ya kasance a dai-dai wannan rana ce Yahweh ya fito da Isra'ila daga ƙasar Masar a ƙungiyoyin mayaƙansu.
Waɗannan jimla na nufin abu ɗaya ne kuma suna nanata ne cewa watan da waɗannan abubuwa wannan sura suka auku za su zama farkon kalandar su a shekara.
Wata na farko a shekara a kalandar Yahudawa ya haɗa da watan uku, da kuma farkon watan huɗu na kalandar kasashen yammaci. Yana nuna alamar lokacin da Yahweh ya fanshe Isra'ilawa daga Masarawa.
Wannan na nufin idan iyalin ba su da yawa da za su iya cinye tunkiya ɗungum ba. AT: "Idan babu isheshen mutane a iyali da zau su iya cin tunkiya dungum"
A nan "mutumin" na nufin shugaban iyalin.
Wato da yamma kenan bayan faduwar rana amma dai da sauran haske.
"a gefe da kuma samman ƙofar shiga cikin gida"
AT: "da gurasa da aka yi babu yisti a ciki"
Waɗannan wasu shuke-shukemasu ɗaci da kuma rashin ɗadi.
"Kada ku ci tunkiyar ko akuyan ɗanye"
yă kai safiya"
Wato wata tsiri na fata ko masana'anta da ake ɗaurawa kewaye da kwankwaso.
"ku ci shi da sauri-sauri"
Wato cin dabban a rana ta goma ga wata kenan. AT: "Wannan farillar na ƙeterewa na Allah ne"
AT: "Zan horas da dukkan allolin Masar"
Wannan na nuna kenan cewa Yahweh zai ga jinin da ke nuna gidan ba Isra'ila. AT: "wannan zan gani yayin da na zo gare ku.
Wannan kalma "ƙetere" wata hanya ce na nuna cewa ba za a ziyarce ko shiga gidan ba a al'adun su. AT: "ba zan shiga gidan ku ba"
"a gareku da dukkan mutanen zuriyar ku"
Wannan maganar na da ma'anna uku a kalla 1) "lallai ne jama'ar Isra'ila su kori wannan mutum" 2) "ba zan gan shi a matsayin ɗaya daga cikin jama'ar Isra'ilawa ba" 3) "ya zama tilas jama'ar Isra'ila su ɗauki ransa."
AT: "wani taro tas musamman da aka keɓe mani"
AT: "Ba za ku yi wani aiki a waɗannan kwanaki ba"
AT: "Wannan ne kadai aikin da ya zama tilas ku yi"
Wannan kalmar na nufin runduna sojoji ko kuma sojoji masu yawa. Duba yadda aka juya wannan a 12:5.
Wato da yamma kenan bayan faduwar rana amma dai da sauran haske.
Wannan ne wata na farko a kalandar Yahudawa. Kwana ta gomasha haɗun yana kusa ne da farkon watan huɗu a kalandar Yammaci.
rana ta farko na wata- "kwana ta farko ga watan farko." Wato kusa da tsakar watan huɗu a kalandar yammaci.
AT: "ko kaɗan ba za a sami yisti a gidajenku ba"
Wannan maganar na da ma'anna uku a kalla 1) "lallai ne jama'ar Isra'ila su kori wannan mutum" 2) "ba zan gan shi a matsayin ɗaya daga cikin jama'ar Isra'ilawa ba" 3) "ya zama tilas jama'ar Isra'ila su ɗauki ransa." Duba yadda aka juya wannan a 12:15
Duba yadda aka juya wannan a 12:5.. AT: "gurasa da aka yi babu yisti a cikinsa" (Dubi: Active or Passive)
"kira"
...
"a gefe da kuma samman ƙofar shiga cikin gida" Duba yadda aka juya irin wannan a 12:5.
A nan kalmar nan "ƙofa" na nufin gidan gabaɗaya. Wannan na nufin cewa Allah zai kyale jama'ar Isra'ila da ke gidajen da aka sa jini a ƙofofin. AT: "ƙetere gidajenku"
Waɗannan jimlar suna nufin ƙeterewa ko kuma shagalin Gurasa Marar yeast. Yin wannan Ƙeterewar wata hanya ce na yi was Yahweh sujada.
Wannan na nufin Yaweh ya kyale 'yan fari maza na Isra'ila. AT: "Bai ƙashe 'yan farin mu maza a gidajenmu ba"
"duk abinda Yahwen ya ce wa Musa da Haruna su yi"
"a tsakiyar dare"
A nan "'yan fãri" na nufin babban ɗa na miji. Duba yadda aka juya irin wannan a 11:4.
Wato Fir'auna.
"zuwa 'yan fãrin talikan da ke kurkuku." Wato 'yan kurkuku, gaba ɗaya, ba wai ga wani mutum ta musamman a kurkuku ba.
AT: "Dukkan Masarawa suka yi kuka da ƙarfi"
AT: "domin an yi rashi a kowane gida"
Masarawan sun yi amfani da wannan maganar ne somin su nanata cewa haƙika za su mutu idan Isra'ilawa ba su bar ƙasar Masar. AT: "Ai za mu mutu idan ba ke tafi ba"
AT: "Sun riga sun kimsa kwanonin markaɗensu sun ɗaure a cikin kayansu, a bisa kafaɗunsu kuma"
Wannan wata babbar birni ce a Masar da ake tara hatsi. Dubi yadda aka juya wannan a 1:11.
"Jimilansu mazaje ya kama 600,000"
...
AT: "Masarawan sun kore su daga Masar"
Wato kabilun Isra'ila kenan. Duba yadda aka juya wannan "ƙungiyoyin mayaƙan" a 12:17.
AT: "da sukkan Isra'ilawan suka kiyaye"
"dukkan Isra'ilawan da dukkan tsararrakin zuriyar su"
Wakilin sunan nan "sa" na nufin Abinci Ƙeterewar.
"ko ma wani bawa na Isra'ila"
AT: "da Ba-isra'ile ya sawo da kuɗi"
AT: "Dole ne ko wane iyalin Isra'ila su ci abincin a gida ɗaya"
"ba za ku taɓa karya ko kashi ɗaya daga cikin sa ba." A nan kalmar nan "sa" na nufin tunkiyar da Iyalin Isra'ilan za su ci.
AT: "dole wani ya yi wa 'yan mazan danginsa kaciya"
A nan kalmar man "ƙasar" na nufin ƙasar Kan'ana. Furcin nan "haifa a ƙasar" na nufin mutumin da ke Ba-isra'ila ne daga haifuwa. AT: "mutanen da ke Isra'ilawa ta wurin haifuwa"
AT: "masu kaciya ne kaɗai zai iya ci"
"dukkan abubuwan da Yahweh ya ce wa Musa da Haruna su yi"
Ana amfani ne da wannan jimlar domin a datsa aya ga wani abu mai muhimmance da ya auku a labarin. Idan harsen ku na da wata hanya ta musamman na yin haka, kuna iya moran ta a nan.
Wannan kalmar na nufin runduna sojoji ko kuma sojoji masu yawa. Duba yadda aka juya "kungiyan mayaƙa" a 12:17.
1Yahweh ya yi magana da Musa ya kuma ce,2"Ka keɓe mani dukkan 'ya'yan fãri, kowanne ɗan fãri namiji daga cikin Isra'ilawa, duk da na mutane da dabbobi. 'Ya'yan fãrin nawa ne."3Musa ya cewa mutanen, "Ku tuna da wannan rana, ranar da kuka fito daga Masar, daga gidan bauta, domin ta hannun Yahweh mai ƙarfi ya fito daku daga nan wurin. Babu wata gurasa mai gami da zai yiwu a ci.4Za ku fita daga Masar a wannan ranar, a cikin watan Abib.5Sa'ad da Yahweh ya kawo ku cikin ƙasar Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Hibbiyawa, da kuma Yebusiyawa, ƙasar da ya rantse wa kakanninku zai baku, ƙasar dake malala da madara da zuma - daganan tilas ku kiyaye wannan aikin sujada a cikin wannan watan.6Gama kwanaki bakwai tilas za ku ci gurasa marar gami; a ranar kwana na bakwai za ayi bikin girmama Yahweh.7Gurasa marar gami tilas za a ci cikin dukkan kwanakin bakwai; babu wata gurasa mai gami da zai yiwu a gani a cikin ku. Babu wani gami da zai yiwu a gani tare daku a cikin kowanne kan iyakokinku.8A wannan rana zaku cewa 'ya'yanku, 'Wannan saboda abin da Yahweh ya yi domina ne sa'ad da na fito daga Masar.'9Wannan zai zama abin tunawa domin ka a bisa hannu, abin tunawa kuma a bisa goshi. Wannan saboda shari'ar Yahweh ta kasance a bakinka, domin tare da hannu mai ƙarfi Yahweh ya fito da kai daga Masar.10Saboda haka tilas ka kiyaye wannan shari'a a lokacin da aka zaɓa daga shekara zuwa shekara.11Sa'ad da Yahweh ya kawo ku cikin ƙasar Kan'aniyawa, kamar yadda ya rantse maku da kakanninku zai yi, kuma sa'ad da ya bayar da ƙasar a gare ku,12tilas ku keɓe ga Yahweh kowanne yaro ɗan fãri da ɗan farko na dabbobinku. Mazajen dukka za su zama na Yahweh.13Kowanne ɗan fãrin jaki tilas ku saye shi da ɗan rago. Idan baku saye shi ba, daga nan tilas ku karya wuyansa. Amma kowanne ɗan fãri namiji daga cikin dukkan 'ya'yanku maza - tilas ku sake sayen su.14Idan ɗan ka yayi maka tambaya daga bisani, 'Mene ne ma'anar wannan?' Daga nan sai ka gaya ma shi, 'Ta wurin hannun Yahweh mai ƙarfi ne aka fito damu daga Masar, daga gidan bauta.15Sa'ad da Fir'auna da taurin kai ya ƙi ya bar mu mu tafi, Yahweh ya kashe dukkan 'ya'yan fãri na ƙasar Masar, duk da 'ya'yan fãrin mutane da 'ya'yan fãrin dabbobi. Shi ya sa nake hadaya ga Yahweh na ɗan fãri namiji na kowacce dabba, shi yasa kuma nake sake sayen 'ya'yan fãri na mazaje.'16Wannan zaya zama abin tunawa a hannunku, abin tunawa kuma a bisa goshinku, domin ta hannu mai ƙarfi Yahweh ya fito damu daga Masar."17Sa'ad da Fir'auna ya bar mutanen su tafi, Allah bai bida su ta hanyar ƙasar Filistiyawa ba, koda yake wannan ƙasar tana kurkusa. Domin Allah yace, "Watakila mutanen za su canza ra'ayinsu sa'ad da suka fuskanci yaƙi daganan kuma su koma Masar."18Sai Allah ya bi da mutanen su kewaya ta cikin jeji zuwa Tekun Iwa. Isra'ilawa suka fita daga ƙasar Masar shirye domin yaƙi.19Musa ya ɗauki ƙasusuwan Yosef tare da shi, domin Yosef yasa Isra'ilawa suka yi rantsuwa ya kuma ce, "Babu shakka Allah zai ceto ku, kuma tilas ku ɗauke ƙasusuwana tare daku."20Isra'ilawa suka yi tafiya daga Sukkot suka kuma yi sansani a Itam a bisa gaɓar jeji.21Yahweh ya shiga gabansu da rana ta inuwar girgije domin ya bida su ta hanyar da zasu bi. Da dare ya tafi ta inuwar wuta domin ya basu haske. Ta wannan hanyar suna iya tafiya da rana da kuma dare.22Yahweh bai ɗauke kuma daga gaban mutanen da rana inuwar girgije ba da dare kuma inuwar wuta ba.
Allah ya umurta cewa a keɓe masa kowane ɗan fãri.
AT: "Ku tuna ku kuma yi bikin wannan rana"
Musa yana maganar Masar ne kamar wani gida ne da mutane ke ijiye barori. AT: "wurin da kuke barori"
A nan "kalmar nan "hannu" na nufin iko. Duba yadda kuka juya "hannu ... mai ƙarfi" a 6:1.
AT: "Kada ku kuskura ki ci gurasa mai yisti"
Wannan shi ne sunan wata na farko a kalandar Yahudawa. Abib shi ne ta ƙarshen watan uku da kuma farkon watan huɗu a kalandar Yammaci.
Da shike ana samun madara daga shanikai ne da awakai, "madara" na nufin abincin da dabbobi ke bayarwa. Tunda ana samun zuma daga furen itace, "zuma" na nufin abincin da shuƙe-shuƙe ke bayarwa. Duba yadda kuka juya irin wannan a 3:7. AT: "abinci daga dabbobi da kuma shuƙe-shuƙe"
Idan sun bar ƙasar Kan'ana , ya zama tilas ne su yi bikin Ƙeterewa a wannan rana a ko wace shekara. Duba yadda kuka juya wannan jimla a 12:24)
Musa ya cigaba da magana da Jama'ar Isra'ila.
"Gama kwanaki 7"
AT: "ba za ku taɓa cin gurasa marar yisti ba"
AT: "Ba za a same ku da wani gurasa mai yisti a cikinku ba"
AT: "Kada a same ku da yisti ko kadan"
...
AT: "A wannan rana za ku ce wa 'ya'yanku cewa wannan sabouda abinda Yahweh ya yi maku ne sa'ad da kuka fito daga Masar"
Waɗannan wasu irin hanyoyi ne daban daban ta jiki domin kada mutane su manta da wani abu mai huhimmanci.
Musa yana maganar bikin wannan shagalin kamar ɗaura wani abu ne a bisa hannayensu domin yă tunashe su da abinda Yahweh ya yi. AT: "kamar wani abu ne da ke kewaye a hannun ku a matsayin tunashewa"
Musa yana maganar bikin wannan shagalin kamar ɗaura wani abu ne a bisa goshi domin yă tunashe su da abinda Yahweh ya yi. AT: "kamar wani abu ne da ke ɗaure a kai a matsayin tunashewa"
Kalamun nan "a bakinka" a nan na nufin maganganun da za su yi. AT: "saboda ka riƙa maganar shari'ar Yahweh a kowace lokaci"
Kalmar nan "hannu" a nan na nufin ayyukan Allah. AT: "ikon da na nuna a ayyuka na"
"kuma sa'ar da ya bayar da ƙasar Kan'ananiyawa a gareku"
Ana ba wa Isra'ilawa zaɓin kashi ɗan fãrin jaki ko kuma su saye ta da tunkiya.
Dukkan jama'ar Isra'ila da ke da 'yan fãri maza, ya zama tilas su sake siye shi.
AT: "Idan ɗan ka yayi maka tambaya nan gaba ma'annar wannan, sai ka ce masa"
Kalmar nan "hannu" a nan na nufin ayyukan Allah. AT: "ikon da na nuna a ayyuka na." Duba yadda kuka juya wannan a 6:1.
Musa yana maganar Masar ne kamar wani gida ne da mutane ke ijiye barori. Duba yadda kuka juya wannan a 13:3. AT: "Wurin da kuke masu bauta"
Wannan na nuna hanyoyi biyu na tunawa da muhimmancin Idin Ƙeterewa. Duba yadda kuka juya wannan a 13:8.
"kusa da wurin da suke"
Da shike Isra'ilawa sun yi bauta ne dukkan ran su. Sun fi sabuwa da salama fiye da yaƙi kuma za su iya zaba su koma bautar su da a ce su yi yaƙi.
Itam yana kudancin hanyar da ke zuwa Filistiyawa, a iyakacin jeji.
Allah yana tare da su a inuwar da rana kuma a wutar da dare.
1Daga nan Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"Ka gaya wa Isra'ilawa cewa su juya su kuma yi sansani kafin Fi Hahirot, tsakanin Magdol da teku, kafin Ba'al Zifon. Za ku yi sansani a gefen teku akasi da Fi Hahirot.3Fir'auna zai ce game da Isra'ilawa, 'Su na yawo a cikin ƙasar. Jeji ya rufe bisan su.'4Zan taurare zuciyar Fir'auna, kuma zai runtume su. Zan sami girmamawa saboda Fir'auna da dukkan mayaƙansa. Masarawa zasu sani cewa Ni ne Yahweh." Sai Isra'ilawa suka yi sansani kamar yadda aka umarce su.5Sa'ad da aka gaya wa sarkin Masar cewa Isra'ilawa sun tsere, sai ra'ayin Fir'auna da bayinsa suka juya gãba da mutanen. Suka ce, "Me muka yi? Mun saki Isra'ila daga bauta ma na?"6Daga nan sai Fir'auna ya shiryo karusansa ya kuma ɗauki mayaƙansa tare da shi.7Ya ɗauki zaɓaɓɓun karusai ɗari shidda da dukkan sauran karusan Masar, da shugabanni a bisa dukkansu.8Yahweh ya taurare zuciyar Fir'auna, sarkin Masar, sarkin kuma ya runtumi Isra'ilawa. Yanzu dai Isra'ilawa sun yi tafiyarsu cikin nasara.9Amma Masarawa suka runtume su, tare da dukkan dawakansa da karusai, mahayan dawakansa, da mayaƙansa. Suka sha kan Isra'ilawa da suka yi sansani a gefen teku a gefen Fi Hahirot, kafin Ba'al Zifon.10Sa'ad da Fir'auna ya iso kusa, Isra'ilawa suka duba sama suka kuma yi mamaki. Masarawa suna tattaki bayan su, suka kuma firgita. Isra'ilawa suka yi kuka ga Yahweh.11Suka ce wa Musa, "Saboda babu kaburbura ne a Masar, shi yasa ka ɗauko mu domin mu mutu a jeji? Meyasa ka yi haka da mu, ka fito da mu daga Masar?12Ba wannan muka gaya maka ba a Masar? Muka ce maka, 'Ka ƙyale mu, domin mu yiwa Masarawa aiki.' Ya gwammace mana muyi aiki domin su maimakon mu mutu cikin jeji."13Musa ya cewa mutanen, "Kada kuji tsoro. Ku tsaya cik ku kuma ga ceton da Yahweh zai wadata domin ku a yau. Domin ba zaku sake ganin Masarawan da kuka gani ba a yau.14Yahweh zai yi yaƙi domin ku, kuma tsayawa kawai za kuyi cik."15Daga nan Yahweh ya cewa Musa, "Meyasa kai, Musa, ka ke ci gaba da kira a gare ni? Ka gaya wa Isra'ilawa su tafi gaba.16Ka ɗaga sandarka, ka miƙa hannunka bisa tekun ka kuma raba ta biyu, saboda mutanen Isra'ila su bi ta tekun bisa busasshiyar ƙasa.17Ka sani cewa zan taurare zukatan Masarawa saboda su biyo bayansu. Zan sami daraja saboda Fir'auna da dukkan mayaƙansa, karusansa, da mahaya dawakansa.18Daga nan Masarawa zasu sani cewa Ni ne Yahweh sa'ad da Na samo daraja saboda Fir'auna, karusansa, da mahaya dawakansa."19Mala'ikan Allah, wanda ya tafi gaban Isra'ilawa, ya matsa ya kuma je bayansu. Inuwar girgijen ta matsa daga gabansu ta kuma koma ta tsaya bayansu.20Girgijen ya zo tsakanin sansanin Masar da sansanin Isra'ila. Girgije mai duhu ne ga Masarawa, amma ya haska daren domin Isra'ilawa, sai gefe ɗaya basu zo kusa da ɗayan ba dukkan dare.21Musa ya miƙar da hannunsa bisa tekun. Yahweh ya maida tekun baya da babbar iskar gabas dukkan wannan dare ya kuma maida tekun zuwa busasshiyar ƙasa. Ta haka ruwayen suka rabu.22Isra'ilawa suka tafi ta cikin teku bisa busasshiyar ƙasa. Ruwayen suka yi katanga domin su a hannun dama da hannun hagu.23/ Masarawa suka runtume su. Suka tafi bayansu cikin tsakiyar teku - dukkan dawakan Fir'auna, da karusai, da mahaya dawakai.24Amma a sa'o'in farkon safiya, Yahweh ya duba ƙasa bisa mayaƙan Masarawa ta wurin umudin wuta da girgije. Ya sanya firgita tsakanin Masarawa.25Keken karusansu suka cije, mahayan dawakan suka yi tuƙi da wahala. Sai masarawa suka ce, "Bari mu tsere daga Isra'ila, gama Yahweh yana yaƙi domin su gãba da mu."26Yahweh ya cewa Musa, "Ka miƙar da hannunka bisa tekun domin ruwayen su dawo bisa Masarawa, karusansu, da mahaya dawakansu."27Sai Musa ya miƙar da hannunsa bisa tekun, kuma ya koma yadda ya ke da safiya ta bayyana. Masarawa suka tsere cikin teku, Yahweh kuma ya kora Masarawa zuwa cikin tsakiyarsa.28Ruwayen suka dawo suka rufe karusan Fir'auna, mahayan dawakai, da dukkan mayaƙansa dasu ka bi karusan zuwa cikin teku. Babu wanda ya tsira.29Duk da haka, Isra'ilawa suka yi tafiya bisa busasshiyar ƙasa cikin tsakiyar teku. Ruwayen suka zama katanga domin su a hannun damansu da hagunsu.30Sai Yahweh ya ceto Isra'ila a wannan rana daga hannun Masarawa, Isra'ila kuma suka ga matattun Masarawa bisa gaɓar teku.31Sa'ad da Isra'ila suka ga babban iko da Yahweh ya yi amfani da shi gãba da Masarawa, mutanen suka girmama Yahweh, suka kuma amince da Yahweh da kuma bawansa Musa.
Waɗannan garurruka ne a iyakacin gabacin Masar.
Wato Musa da Isra'ilawa kenan.
AT: "Fir'auna zai ce Isra'ilawa suna yawo ne a ƙasar, ga kuma jeje ya rufa a bisansu"
Fir'auna yana maganar Jeji kamar wani mutum ne da ya kama su a tarko.
Yahweh ya cigaba da umurtan Musa game da wurin da za su je da wbinda Yahweh zai yi.
A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. Ana maganar taurin kansa kamar zuciyarsa ne ta taurara. Duba yadda aka juya wannan a 9:11. AT: "Zuciyar Fir'auna ya yi kanta"
"Fir'auna zai runtume Isra'ilawa"
"Mutane za su girmama ni"
Masarawan za su fahimci cewa ni ne Yahweh, Allah makaɗaici"
AT: "Sai Isra'ilawa suka yi sansani kamar yadda Yahweh ya umarce su"
AT: "Da wani ya gaya wa sarkin Masar "
Wato Fir'auna kenan.
"sun tafi"
A nan kalmar nan "ra'ayi" na nufin halinsa ga Isra'ila ya canza. AT: "Fir'auna da mutanensa sun canza halinsu game da Isra'ila"
Sun yi wannan tabayan ne domin su nuna cewa sun yi wawanci. AT: "Mun yi wawanci da barin mutanen Isra'ila su tafi haka kurum!"
"ɗauki karusai 600 mafi kyau"
A nan "zuciya" na nufin Fir'auna. Ana maganar taurin zuciyarsa ne kamar zuciyarsa ya taurara. Duba yadda aka juya irin wannan a 9:11. AT: "Yahweh ya sa zuciyar Fir'auna ya yi kanta"
Waɗannan garurruka ne a iyakacin gabacin Masar. Duba yadda aka juya irin wannan a 14:1.
Kalmar nan "Fir'auna" na nufin rundunar mayakan Masar. AT: "Sa'ad da Fir'auna da mayakansa suka maso kusa"
"Isra'ilawa suka yi mamaki"
Isra'ilawan sun yi wannan tambayan ne domin su nuna takaicisu da kuma tsoro mutuwa da suke ji. AT: "Akwai kaburbura da yawa a Masar da za a iya birne mu a ciki ai. Ba sai ka kai mu jeji ba kamun mu mutu!"
Isra'ilawan sun yi wannan tambayan ne domin su tsauta wa Musa da fito da su zuwa jeji su mutu da yayi. AT: "Da ba yi mana haka ba ta wurin fito da mu da Masar da ka yi!"
Isra'ilawan sun yi wannan tambayan ne domin su nanata cewa abinda suka gaya wa Musa kenan. AT: " Ai haka muka gaya maka tun muna Masar."
AT: "Mun ce maka ka bar mu domin mu yi wa Masarawa aiki."
Musa ya amsa tsoron mutanen.
Wakilin sunan nan "ku" na nufin Isra'ilawa.
Musa yana amfani ne da wata hanya mai saki na ce wa Allah zai hallaka mayakan Masarawa. AT: "Gama Allah zai kashe Masarawa"
A bayane yake cewa Musa Yana ta addu'a ga Allah shi yasa Allah yana amfani da wannan tambayan yă karfafa abinda Musa yake yi. AT: "Kada ka kira gare ni kuma, Musa"
"raba tekun bangare biyu"
...
A nan "zukata" na nufin Masarawan kansu., Ana maganar hain taurin kan su ne kamar zukatansu sun yi tauri. Duba yadda aka juya irin wannan jimlar a 9:11. AT: "Zan sa Masarawan su ƙara kanta"
"saboda Masarawan su biyo Isra'ilawan cikin tekun"
"mayakan Masar da jama'ar Isra'ila" (UDB)
Wannan na nufin cewa Masarawan da Isra'ilawan basu kusa da juna ba sam.
Iskar gabas yana tasowa ne daka gabar ya huro zuwa yamma.
wurin da rana ke tasowa
AT: "Yahwen ya raba ruwayen"
"a kowane gefen su" ko kuma "a kowane gefensu"
sun tsorata har sun kãsa tunani daidai.
AT: "Laka ya cije keken karusansu" ko kuma "Keken karusansu ya makale a laka"
AT: "Yahweh ya ce wa Musa yă miƙa hannunsa bisa tekun domin ruwayen su dawo su rufe masarawan, karusansu, da mahaya dawakansu."
"faɗa bisa"
Dashike tekun yana rufuwa ne a bisa Masarawan, a maimakon guje was, suna kara guduwa ne can cikin ruwan.
...
Duk wurin da aka sa "Isra'ila" na nufin Jama'ar isra'ila. AT: "Jama'ar Isra'ila" ko kuma "Isra'ilawa"
A nan "kalmar nan "hannu" na nufin iko. AT: "daga ikon Masarawa"
"a bakin tekun"
1Daga nan Musa da mutanen Isra'ila suka raira wannan waƙa ga Yahweh. Suka raira, "Zan raira ga Yahweh, gama ya yi ɗaukakakkiyar nasara; doki da mahayinsa ya watsar cikin teku.2Yahweh ne ƙarfina da waƙata, ya kuma zama mai cetona. Wannan ne Allahna, kuma zan yabe shi, Allah na mahaifina, zan kuma ɗaukaka shi.3Yahweh mayaƙi ne; Yahweh ne sunansa.4Ya watsar da karusan Fir'auna da mayaƙansa cikin teku. Zaɓaɓɓun hafsoshin Fir'auna sun nutse cikin Tekun Iwa.5Zurfafa sun rufe su; sun tafi ƙasa cikin zurfafa kamar dutse.6Hannunka na dama, Yahweh, ɗaukakakke ne cikin iko; hannunka na dama, Yahweh, ya rugurguza maƙiyi.7Cikin babban girma ka kayar da waɗanda suka taso gãba da kai. Ka aika da hasalarka; ta cinye su kamar haki.8Da hucin kafofin hancinka ruwaye suka jera; ruwayen dake malala suka tsaya tsaye suka yi tsibi; ruwa mai zurfi ya daskare a cikin zuciyar teku.9Maƙiyi yace, 'Zan runtuma, zan sha kai, zan rarraba ganima; marmarina zai ƙoshi a kansu; zan zaro takobina; hannuna zai hallakar dasu.'10Amma ka busa da iskarka, teku kuma ya rufe su; suka nutse kamar baƙin ƙarfe cikin manyan ruwaye.11Wane ne kamar ka, Yahweh, a tsakanin alloli? Wane ne kamar ka, girma cikin tsarki, daraja cikin yabo, mai aikata al'ajibai?12Ka miƙa hannun damanka, ƙasa kuma ta haɗiye su.13A cikin alƙawarin amincinka ka bida mutanen ka ceto su. A cikin ƙarfinka ka bida su zuwa wuri mai tsarki inda kake zaune.14Mutane zasu ji, zasu kuma yi rawar jiki; fargaba zai afko wa mazaunan Filistiya.15Daga nan shugabannin Idom zasu ji tsoro; sojojin Mowab zasu girgiza; dukkan mazaunan Kan'ana zasu narke.16Tsoro da fargaba zai fãɗo masu. Saboda ikon damtsenka, zasu tsaya cik kamar dutse har sai mutanenka sun wuce, Yahweh - har sai mutanen da ka ceto sun wuce.17Za ka kawo su ka dasa su bisa tsaunin gãdonka, wurin da, Yahweh, ka yi domin ka zauna a ciki, wuri mai tsarki, Ubangijinmu, wanda hannuwanka suka gina.18Yahwah zai yi mulki har abada abadin."19Gama dawakan Fir'auna suka tafi tare da karusansa da mahaya dawakansa cikin teku. Yahweh ya maido da ruwayen teku bisansu. Amma Isra'ilawa suka yi tafiya bisa busasshiyar ƙasa a tsakiyar teku.20Miriyam annabiya, 'yar'uwar Haruna, ta ɗauki kacau-kacau, dukkan mataye kuma suka fita da kacau-kacau, suna rawa tare da ita.21Miriyam ta raira masu waƙa: "Ku raira ga Yahweh, domin ya yi ɗaukakakkiyar nasara. Doki da mahayinsa ya jefar cikin teku."22Daga nan Musa ya bida Isra'ila gaba daga Tekun Iwa. Suka tafi zuwa cikin jejin Shur. Suka yi tafiya kwana uku cikin jeji basu kuma sami ruwa ba.23Daga nan suka iso Mara, amma basu iya shan ruwan wurin nan ba saboda yana da ɗaci. Sai suka kira sunan wannan wuri Mara.24Sai mutanen suka yi gunaguni ga Musa suka kuma ce, "Me zamu sha?"25Musa ya yi kuka ga Yahweh, sai Yahweh ya nuna masa wani itace. Musa ya jefa shi cikin ruwan, ruwan kuma ya zama da daɗin sha. A wannan wurin ne Yahweh ya basu shari'a mai tsauri, a wannan wurin ne kuma ya gwada su.26Ya ce, "Idan a hankali kuka saurari muryar Yahweh Allahnku, kuka kuma yi abin dake dai-dai a idanunsa, idan kuma kuka kasa kunne ga umarninsa kuka kuma yi biyayya da dukkan shari'unsa - ba zan sanya maku ko ɗaya daga cikin cututtukan dana sanya wa Masarawa ba, gama Ni ne Yahweh dake warkar da ku."27Daga nan mutanen suka iso Elim, inda akwai maɓuɓɓugan ruwa sha biyu da itatuwan dabino saba'in. Suka yi sansani a nan bakin ruwa.
Wannan waƙa ne game da abubuwan da suka far a 14:26.
Musa ya yi waka ne game da yadda Allah ya sa teku ya rufa ya kuma hallaka dawakai da mahayin su kamar Allah ya watsar da su ne cikin teku. AT: "ya sa teku ya rufa doki da mahayinsa" ko kuma "ya sa doki da mahayinsa su hallaka cikin teku.
Wato duk ko kuma dawakan Masarawa da mahayinsa masu yawa da ke koran Isra'ilawa.
mutumin da ke zama a bisa doki ko ke tafiya a keken da doki ke ja.
Wannan na iya nufin 1) Yahweh ne mai ba ni ƙarfi" ko 2) "Yahweh ne mai ƙarfi da ke mini kariya."
Musa yana ce da Yahweh waƙarsa domin waƙarsa game da Yahweh ne. AT: "da kuma wanda nake waƙa dominsa"
Musa yana ce da Allah cetonsa domin Allah ya cece shi ne. AT: "ce cece ni" ko kuma "shi ne wanda ya cece"
Musa yana ce da Allah mayaƙi na ne domin Allah ya yi yaƙi da iƙo ga Masarawa kuma yayi nasara. AT: "Yaweh kamar mayaƙi ne"
Musa yana waƙa game da yadda Allah ya sa tekun ta rufa Karusan Fir'auna da mayakansa kamar Allah ya watsar da su ne cikin teku. AT: "ya sa tekun ya rufa karusan Fir'auna da mayakansa" ko kuma "Ya sa mahayan karusan Fir'auna da mayakansa sun nutsa a tekun"
kamar yadda dutse bata taso kan ruwa amma saidai ya nutse zuwa kasan teku, abokan gãba mayakan sun nutse zuwa kasan teku. AT: "sun tafi cikin zurfafar ruwa kamar dutse da ke nutsewa zuwa kasan teku"
Musa yana maganar Allah kamar Allah yana da hannu ne. Hannun damar Allah na nufin Ikon Allah ko kuma abubuwad da Allah ke yi da iko. AT: "Yahweh, ikon ka ɗaukakakke ne" ko kuma "Yahweh, abin da ka yi ɗaukakakke ne cikin ikon"
Musa yana maganar Allah kamar Allah yana da hannu ne. Hannun damar Allah na nufin ikon Allah. AT: "Yahweh, ikon ka ya rugurguza makiyi" ko kuma "Yahweh, ta wurin ikon ka, ka rugurguza makiyi"
Musa yana maganar maƙiyi kamar wani abu ne mai saukin fashewa da zai iya rugurguzawa kamar gilashi ko tukwance. AT: "ya hallaka maƙiyi gabaɗaya"
Ana maganar tawaye da Allah ne kamar tayarwa ne da shi. AT: "waɗanda suka tayar maka" maƙiyanka"
Musa yana maganar hasalar kamar wani bare ne da Allah ya aika ya yi wani abu. AT: "ka nuna hasalarka" ko kuma " ka yi bisa hasalarka"
Musa yana maganar hasalar Allah ne kamar wuta ne da ke iya cinye abubuwa gabaɗaya. Maƙiyin sun hallalaka kamar ciyawa da a wuta. AT: "ya hallaka maƙiyanka ne kamar wuta ne da ke ƙona ƙara"
Musa yana maganar Allah ne kamar Allah yana da hanci, kuma kamar yana maganar nunfashi ne kamar Allah ya hura nunfashi ne daga hancinsa. AT: "ku hura bisa tekun da" (UDB).
AT: "zan ƙosar da marmari na a kansu" ko kuma "zan ƙarbi dukkan abinda nake so daga garesu"
Maƙiyan suna maganar hallakar da Isra'ilawan da ikon hannayensu ne kamar hannayensu ne zai hallakar da su. AT: "Zan hallakar da su da hannaye na"
Musa yana maganar yadda Allah ya sa iskarsa ya hura kamar Allah ya hura iskar da hancinsa ne ko kuma da baki. AT: "Amma ka sa iskar ya hura"
baƙin ƙarfe wata ƙarfe ne mai nauyi da ake amfani da shi a sa abubuwa su nutse a cikin ruwa. Ana wannan maganar ne a nuna yana maƙiyan Allah sun nutse ne a ruwa nan da nan sun hallaka. AT: "nutse da nan tãke kamar baƙin ƙarfe"
Musa yana amfani ne da wannan tambayan domin nuna girmar Allah. AT: "O Yahweh, ba wani allah mai kama da kai!
Musa yana amfani ne da wannan tambayan ya nuna girman Allah. AT: "Babu kamar ka. Babu mai girma cikin tsarki, babu mai daraja cikin yabbai kamar ka, babu kuma mai aikata al'ajibai kamar kai!
Jimlar nan "hannun dama" na nufi ƙarfin ikon Allah. AT: "da ƙarfin ikonka"
Musa yana maganar yadda Allah yana sa abu yă fãru ne kamar Allah ya miƙa hannunsa ne. AT: "Da ƙarfin ikon Allah ya sa shi ya fãru"
Musa yana maganar ƙasa ne kamar zai iya haɗiye ko hallaka da baƙinsa. AT: "ƙasa kuma ta hallakasu"
Wato kaɗuwa domin tsoro.
Musa yana maganar fargaba kamar wani mutum ne da ke iya cafke mutum da ƙarfi ya riƙe shi har ya sa mutum mutuƙar tsoro. AT: "mazaunan Filistiya za su tsaurata"
Musa yana maganar yadda mutane ke iya rauni ne domin tsoro kamar narkewa. AT: "za su yi rauni domin tsoro" ko kuma "za su tsorota su suma"
Musa ya cigaba ne da waƙa game da yadda jama'ar wasu kasashe za su ji yayin da sun ga mutanen Allah.
Duka kalamun nan na nufin cewa tsoro zai fãɗo masu. AT: "Tsoro zai auko masu"
Tsoron nan kwa babban juyayi ne da tashin hankali game da wani abu da zai faru or zai iya faruwa.
Hannun Allah na nufin matuƙar ƙarfin Allah. AT: "Saboda matuƙar karfinka"
Wannan na iya nufin 1) Za su tsaya shuru kamar dutse" ko kuma 2) Zasu kasa motsi kamar dutse"
Ana iya kara haske akan wurin da Allah zai kawo su. Da shike Musa bai shigo Kan'anan ba tukuna, wasu harsuna suna iya amfani da "kai" a maimakon "kawo." AT: "zaka kai mutanenka Kan'anan"
Musa yana magana ne game da yadda Allah zai ba wa mutanensa ƙasar zama kamar su wani bushiya ne da Allah ke shukawa. AT: "shirya su a bisa dutse" ko kuma "bar su su rayu a bisa dutse"
Wato Dutsen Sihiyona kenan a ƙasar Kan'anan.
Musa yana magana ne game da alkawarin da Allah ya yi domin ba wa mutanensa dutsen har abada kamar yana basu shi ne a matsayin gãdo. AT: "da ka basu a matsayin gãdo"
Jimlar nan "hannuwanka" na nufin ikon Allah. AT: "da ka gina ta wurin ikonka"
Miriyam ce ke gaba da Musa da Haruna.
Wannan wata kayar kida ne kamar wata karamin ganga da ke da wani gefen ƙarfe a kewaye da shi domin yă sa shi ƙara.
"ɗaukakakkiyar nasara a bisa maƙiyansa"
Miriyam na magana ne game da yadda Allah ya sa tekun ya rufe ya kuma hallakar da doki da mahayinsa kamar Allah ya jefar da su cikin teku ne. Duba yadda aka juya wannan a [15:1]. AT: "Ya sa doki da mahayi sun hallaka cikin teku"
Kalmar nan "Isra'ila" na nufin jama'ar Isra'ila. AT: "Musa ya shugabanci jama'ar Isra'ilaa"
Ba mu san daidai wuraren da waɗannan wuraren suke ba.
"suka yi baƙin cikii suka ce wa Musa" ko "da bacin rai suka ce wa Musa"
Yahweh yana magana ne game da nashu muryar. AT: "murya ta"
Jimlar nan "a idanunsa" na nufin abinda Allah ke tunani ko ya zaɓa. AT: aikata abinda Yahweh ke gani dai-dai ne"
Allah yana maganar sa mutane su kamu da cututtuka ne kamar sanya masu cututtuka ne. AT: "Ba zan sa ko ɗaya daga cikinkuyă kamu da cututtuka"
Wannan wani ɗan wurin dausayi ne a tsakiyar hamada, wuri da ke da ruwa da kuma itattuwa da ke ba da inuwa.
"12"
"70"
1Mutanen suka kama hanya daga Elim, kuma dukkan taron jama'ar Isra'ila suka iso jejin Sin, wanda ke tsakanin Elim da Sinai, a ranar sha biyar ga watan biyu bayan barowarsu daga ƙasar Masar.2Dukkan taron jama'ar Isra'ila suka yi gunaguni gãba da Musa da Haruna a cikin jejin.3Isra'ilawa suka ce masu, "Da ma kawai mun mutu ta hannun Yahweh a ƙasar Masar sa'ad da muke zama gefen tukwanen nama muke kuma cin gurasa mu ƙoshi. Domin ka fito da mu cikin wannan jeji ka kashe dukkan taron jama"armu da yunwa."4Daga nan Yahweh ya cewa Musa, "Zan yi ruwan gurasa daga sama domin ku. Mutanen zasu fita su tattaro ta yini ɗaya kowacce rana saboda in gwada su in gani ko zasu yi ko kuwa ba zasu yi tafiya cikin shari'a ta ba.5Za ya kasance a rana ta shida, zasu tattaro riɓi biyu na yawan yadda suke tattarawa kowacce rana a baya, sai kuma su dafa abin da suka ɗebo."6Daga nan Musa da Haruna suka cewa dukkan mutanen Isra'ila, "Da maraice zaku sani cewa Yahweh ne ya fito da ku daga ƙasar Masar.7Da safe zaku ga ɗaukakar Yahweh, domin ya ji gunaguninku gãba da shi. Mu su wane ne da zaku yi gunaguni gãba da mu?"8Musa ya sake cewa, "Zaku san wannan sa'ad da Yahweh ya baku nama da maraice da gurasa da safe ku ƙoshi - domin ya ji gunagunan da kuka furta gãba da shi. Su wane ne Haruna da ni? Gunagunanku ba gãba damu ba ne; gãba da Yahweh ne."9Musa ya cewa Haruna, "Ka cewa dukkan taron jama'ar mutanen Isra'ila, 'Ku zo kusa a gaban Yahweh, domin ya ji gunagunanku."'10Sai ya kasance, yayin da Haruna yake magana da dukkan taron jama'ar mutanen Isra'ila, sai suka kalli zuwa jeji, kuma, duba, ɗaukakar Yahweh ta bayyana a girgije.11Daga nan Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,12"Na ji gunagunan mutanen Isra'ila. Ka yi magana dasu ka ce, 'Da maraice zaku ci nama, da safe kuma zaku cika da gurasa. Daga nan zaku sani cewa Ni ne Yahweh Allahnku."'13Sai ya kasance da maraice makwarwai suka taso suka rufe sansanin. Da safe raɓa ta kwanta kewaye da sansanin.14Da raɓar ta tafi, a nan birbishin jejin sai ga wasu falle-falle kamar dusar ƙanƙara a ƙasa.15Sa'ad da mutanen Isra'ila suka gan ta, suka ce da juna, "Mene ne wannan?" Ba su san ko mene ne ba. Musa yace masu, "Gurasar da Yahweh ya baku ce ku ci.16Wannan ne umarnin da Yahweh ya bayar: 'Tilas ku tattaro, kowannen ku, adadin da kuke buƙata ku ci, awon kowanne taliki bisa ga lissafin mutanenku. Ga yadda zaku tattara ta: Ku tattara isasshe domin ci ga kowanne taliki dake zaune a rumfarku."'17Mutanen Isra'ila suka yi haka. Wasu suka tãra da yawa, wasu suka tãra kaɗan.18Sa'ad da suka auna da awon gwangwani, waɗanda suka tãra da yawa basu rage komai ba, waɗanda kuma suka tãra kaɗan basu rasa komai ba. Kowanne taliki ya tãra dai-dai da biyan buƙatarsu.19Daga nan Musa yace masu, "Dole ba wanda zai bar komai daga cikin ta har safiya."20Duk da haka, basu saurari Musa ba. Waɗansu suka rage daga cikin ta har safiya, sai ta haifar da tsutsotsi ta kuma yi wãri. Daga nan Musa ya fusata da su.21Suka tattara ta safiya bayan safiya. Kowanne taliki ya tãra isassar wanda zai ci domin wannan ranar. Sa'ad da rana ta yi zafi, ta narke.22Sai ya kasance a rana ta shida kowannensu ya tãra riɓi biyu na gurasar, gwangwani biyu domin kowanne taliki. Dukkan shugabannin jama'ar suka zo suka faɗi wa Musa.23Ya ce masu, "Wannan ne abin da Yahweh yace: 'Gobe hutun nadama ne, Asabar mai tsarki cikin girmama Yahweh. Ku gasa abin da kuke so ku gasa, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Duk abin da ya rage, sai ku ajiye shi gefe domin kanku har sai da safe."'24Sai suka ajiye ta gefe har sai da safe, kamar yadda Musa ya bada umarni. Ba ta zama da wãri ba, ko kuma a sami wata tsutsa a cikinta.25Musa yace, "Ku ci wannan abin cin yau, domin yau rana ce wadda aka keɓe a matsayin Asabaci na girmama Yahweh. Yau ba zaku same ta ba a gonaki.26Zaku tattara ta cikin kwanaki shida, amma rana ta bakwai Asabaci ce. A ranar Asabar babu manna."27Sai ya kasance a rana ta bakwai waɗansu mutane suka fita su tattaro manna, amma ba su sami komai ba.28Daga nan Yahweh ya cewa Musa, "Har yaushe zaku ƙi kiyaye umarnai na da shari'u na?29Duba, Yahweh ya baku Asabaci. Don haka a rana ta shida yana baku gurasa domin kwanaki biyu. Kowannen ku tilas ya tsaya a wurinsa; tilas babu wanda zai fita daga wurin shi a rana ta bakwai."30Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.31Mutanen Isra'ila suka kira wannan abinci "Manna." Ita fara ce kamar tsabar riɗi, ɗanɗanon ta kuma kamar wainar da aka yi da zuma.32Musa yace, "Wannan ne Yahweh ya umarta: 'A ajiye gwangwanin manna cikin dukkan tsararrakin mutanenku saboda zuriyarku su ga gurasar dana ciyar da ku a jeji, bayan da na fito daku daga ƙasar Masar."'33Musa ya cewa Haruna, "Ka ɗauki tukunya ka sa gwangwani ɗaya na manna a cikin ta. Ka adana ta gaban Yahweh domin a ajiye ta cikin dukkan tsararrakin mutanen."34Kamar yadda Yahweh ya umarci Musa, Haruna ya ɓoye ta bayan alƙawarin dokoki a cikin akwatin alƙawari.35Mutanen Isra'ila suka ci manna shekaru arba'in har sai da suka zo ƙasar dake da mazauna. Ita suka ci har sai da suka zo kan iyakokin ƙasar Kan'ana.36Yanzu dai gwangwanin kashi ɗaya ne cikin goma na mudu.
Kalmar nan "Sin" anan shine sunan wannan jejin a Yahudanci. Ba "sin" na turanci ba ne.
Wannan lokacin ya kasance daidai ne da ƙarshen watan huɗu da farkon watan biyar a kalandar Yamma. AT: "a rana ta 15 ga watan biyu"
"Dukkan Isra'ilawa." Wannan gamammiyar kalma ce. Musa da Haruna ba su yi gunaguni ba. AT: "Iasr'ilawa"
"suka yi magana a fushi ba"
Wannan wata hanya ne na cewa da ma sun mutu kawai. AT: "Da ma mun mutu kawai ma"
Jimlar nan "hannun Yahweh" na nufin aikin Yahweh. AT: "ta aikin Yahweh"
Allah yana maganar abinci daga sama ne kamar ruwan sama. AT: "zan sauko maku da gurasa kamar ruwan sama" ko kuma "zan sa gurasa su faɗo gareku daga sama"
Allah yana maganar abincin da zai turo daga sama kamar gurasa ne abincin. Isra'ilawan za su ci wannan abinci a kowace rana ne, kamar yadda suke cin gurasa kullum kamun wannan tanaɗi. AT: "abinci" ko kuma "abinci kamar gurasa"
Allah yana maganar biyayya da shari'arsa ne kamar tafiya ne a cikin ta. AT: "biyayya ga shari'a ta" ko kuma "rayuwa bisa ga shari'a ta"
"umarni na"
AT: "A rana ta shidda"
"a rana ta 6"
"sau 2"
Musa da Haruna sun yi amfani ne da wannan tambayan domin su nuna wa mutanen cewa wauta ne su yi gunaguni gãba da su. AT: "Ai ba mu da cikakken iko da har za ku yi gãba da mu." ko kuma "Ai wauta ne ku yi gunaguni gãba da mu, domin ba mu iya yin abinda kuke so ba."
Musa yana maganar abincin da zai turo daga sama kamar gurasa ne abincin. Isra'ilawan za su ci wannan abinci a kowace rana ne, kamar yadda suke cin gurasa kullum kamun wannan tanaɗi. Duba yadda kuka juya wannan a 16:4. AT: "abinci" ko kuma "abinci kamar gurasa"
Musa yana amfani ne da wannan tambayan domin yă nuna wa mutanen cewa shi kansa da Haruna basu da iko su basu abinda suke so. AT: "Haruna dai da ni ba za mu iya baku iyakar abinda kuke so ba"
Mutanen suna gunaguni gãba da Musa da Haruna, wadda bayin Yahweh ne su. Don haka, ta wurin yin gãba da su, mutanen suna gunaguni gãba ne da Yahweh ainun. AT: "Gunagunanku ba ma gãba da mu bane; gãba ne dai da Yahweh, domin mu dai bayinsa ne"
Wannan jimlar tana sa alamar wata abu mai muhimmanci ne a labarin. Abu mai muhimmancin a nan dai shi ne yadda mutanen suna ganin ɗaukakar Allah. Idan harshen ku tana da wata hanya ta musamman na yin haka, kuna iya moransa anan.
Kalmar nan "Ga shi" anan na nuna cewa mutanen sun ga wani abin ban sha'awa.
Allah yana maganar abincin da zai turo daga sama kamar gurasa ne abincin. Isra'ilawan za su ci wannan abincin a kowace rana ne, kamar yadda suke cin gurasa kullum kamun wannan tanaɗi. Duba yadda kuka juya wannan a 16:4. AT: "gurasa" ko kuma "abinci kamar gurasa"
Anyi amfani ne da wannan jimlar anan domin a dasa aya ga wani sashi mai muhimmanci a abubuwan da ke faruwa. Idan harshen ku tana da wata hanya ta musamman na yin haka, kuna iya moransa a nan.
Waɗannan wasu ƙananan tsuntsaye ne.
Ainihin masu karatun sun san yadda wannan ƙanƙara take, don haka wannan jimlar zai taimake su su fahimci yadda wannan gutsurin yake. Ƙanƙara wani daskararen raba ne da ake iya gani a ƙasa. Yana da kyaun gani sosai. AT: "ƙamar ƙanƙara" ko kuma "da ke da kyaun gani kamar ƙanƙara"
Musa yana maganar abincin da Allah ya turo ne kamar gurasa ne abincin. Isra'ilawan za su ci wannan abincin a kowace rana ne, kamar yadda suke cin gurasa kullum kamun wannan tanaɗi. AT: "abinci" ko kuma "abinci kamar gurasa"
Musa ya cigaba ne da magana da mutanen game da abincin da Allah ke tanadar masu.
"lita biyu"
"basu rasa kome ba" ko kuma "sami isheshe"
Wannan jimla na dasa aya ne domin nuna alamar farkon wata sabuwar sashin labarin. Ayoyi 16:22-30 suna maganar abinda mutanen suka yi gane da Manna a kwana ta shidda da bakwai na mako. Idan harshenku tana da wata hanya ta musamman na nuna alamar wata sabuwar sashi a labari, kuna iya amfani da shi anan.
"a rana ta 6"
"sau 2"
Wato, gurasa da ke bayana kamar kanƙara a kasa a kowace asuba.
...
"bai yi ruɓe yana wari ba"
"yau Asabar ce kuma za'a girmama Yahweh ne kawai a cikinta"
"amma a rana ta bakwai"
Wannan shi ne suna da isra'ilawa suka ba wa gurasa da Yahweh yake tanadar masu a kowace safiya.
"ba su sami Manna ba"
Yahweh yana magana da Musa, amma kalmar nan "ku" yana nufin jama'ar isra'ila ne gabaɗaya.
Allah yana amfani ne da wannan tambayan domin ya tsauta wa mutanen domin basu yi biyayya da shari'un sa ba. AT: "Ku dai baku kiyaye umarnai na da shari'u ta ba har yanzu!"
"ku yi biyayya da umarnai na da shari'u na"
Yahweh yana maganar koya wa mutanen hutu ranar Asabar kamar Asabar ɗin wata kyauta ne. AT: "Ni, Yahweh na koya maku cewa ku huta a ranar Asabar"
"rana ta 6 ... kwana 2 ... kwana ta 7"
Wato, gurasa da ke bayana kamar kanƙara a kasa a kowace asuba.
Wannan shi ne suna da isra'ilawa suka ba wa gurasa da Yahweh yake tanadar masu a kowace safiya. Duba yadda kuka juya wannan a 16:26.
Akan bushar da wannan riɗi a niƙa shi zuwa gari sa'annan sa shi a cikin abinci domin ya ba shi ɗanɗano.
...
"litta 2"
Wato, gurasa da ke bayana kamar kanƙara a kasa a kowace asuba
Mudu ɗaya da ephah ɗaya duk ma'auni ne na kimata yăwa. Ainihin masu karatu ne za su iya kimanta yadda iyakar ephah yake. AT: "Yanzu dai mudu goma shi ne ephah guda"
"litta biyu"
1Ɗaukacin taron jama'ar Isra'ilawa suka yi tafiya daga jejin Sin, biye da umarnan Yahweh. Suka yi sansani a Refidim, amma babu ruwa domin mutane su sha.2Sai mutanen suka ba Musa laifi saboda halin da suke ciki suka kuma ce, "Ka ba mu ruwa mu sha." Musa yace, "Meyasa kuke faɗa da ni? Meyasa kuke gwada Yahweh?"3Mutanen suna jin ƙishi sosai, suka kuma yi gunaguni gãba da Musa. Suka ce, "Meyasa ka fito da mu daga Masar? Don ka kashe mu da 'ya'yanmu da kuma dabbobinmu da ƙishi?"4Daga nan Musa ya yi kuka ga Yahweh, "Me zanyi da waɗannan mutanen? Sun kusa shirya jifa na."5Yahweh ya cewa Musa, "Ka tafi gaba da mutanen, ka tafi kuma tare da wasu dattawan Isra'ila. Ka ɗauki tare da kai sandar daka buga kogi, ka kuma tafi.6Zan tsaya a gabanka can a dutsen Horeb, zaka kuma bugi n. Ruwa zai fito daga cikin sa domin mutanen su sha." Daga nan Musa ya yi haka a gaban dattawan Isra'ila.7Ya kira wannan wuri Massa da Meriba saboda gunagunin Isra'ilawa, saboda kuma sun gwada Ubangiji ta wurin cewa, "Yahweh yana cikinmu ko a'a?"8Daga nan mayaƙan mutanen Amalekawa suka fita suka kuma kai hari ga Isra'ila a Refidim.9Sai Musa ya cewa Yoshuwa, "Ka zaɓi wasu mutane ka fita. Ka yi faɗa da Amalekawa. Gobe zan tsaya bisa tudu tare da sandar Allah a hannuna."10Sai Yoshuwa ya yi faɗa da Amalekawa kamar yadda Musa ya umarta, yayin da Musa, Haruna, da Hor suka hau saman tudu.11Yayin da Musa ke riƙe da hannayensa sama, Isra'ila suna nasara; idan ya sauke hannayensa su huta, sai Amalekawa su fãra yin nasara.12Sa'ad da hannayen Musa suka zama da nauyi, Haruna da Hor suka ɗauki dutse suka sanya ƙasansa domin ya zauna a kai. A dai-dai wannan lokaci, Haruna da Hor suka riƙe hannayensa sama, mutum ɗaya a gefensa ɗaya, mutum ɗaya kuma a ɗayan gefensa. Haka aka riƙe hannayen Musa a tallafe har faɗuwar rana.13Haka Yoshuwa ya kayar da mutanen Amalekawa da takobi.14Yahweh ya cewa Musa, "Ka rubuta wannan cikin littafi ka kuma karanta shi cikin kunnuwan Yoshuwa, saboda da zan share tunawa da Amalekawa kakaf daga ƙarƙashin sammai."15Daga nan Musa ya gina bagadi ya kira shi "Yahweh ne tuta ta."16Ya ce, "Gama an ɗaga hannu sama zu wa kursiyin Yahweh - cewa Yahweh zai ja dagar yaƙi da Amalekawa daga tsara zuwa tsara."
Kalmar nan "Zin" a nan shine sunan wannan jejin a Yahudanci. Ba "Zin" na turanci ba ne. Duba yadda kuka juya wannan a 16:1 (Dubi: )
Wannan na nufin "wurin hutu," wani wuri ne na huta daga tafiya mai nesa a cikin jeji.
Musa yana amfani ne da wannan tambayan domin ya tsauta wa mutanen. AT: "Kada ku yi mini faɗa! Kada ku gwada Yahweh!"
Mutanen sun yi amfani ne da wannan tambayan domin yi zargi Musa da son yă kashe su. AT: "Ai ka kawo mu nan domin ka kashe mu ne kawai, da 'ya'yan mu da dabbobinmu ta wurin hana mu samun ruwan sha!"
wannan wani wuri ne a jeji da sunarsa ke da ma'ana "gwadawa"
wannan wani wuri ne a jeji da sunarsa ke da ma'ana "gunaguni"
Wannan na nufin "wurin hutu," wani wuri ne na huta daga tafiya mai nesa a cikin jeji.
Yoshuwa na nufin Isra'ilawa da ya jagorance su a yaƙi. AT: "Sai Yoshuwa da mazajen da ya zaɓa suka yi yaƙi da Amalekawa"
Hor abokin Musa da Haruna ne.
Kalamun nan "Isra'ila" da "Amalek" na nufin kungiyoyin mayaƙan. AT: "mayakan Isra'ila suna nasara ... mayakan Amalekawa za su fãra cin nasara"
...
Kalmar nan takobi na nufin yaƙi. AT: "a yaƙi"
Allah yana maganar hallakar da Amalek ne kamar zai cire labarin Amalek. Yayin da aka hallakar da zuriyar mutane gabaaɗya, babu wani abu kuma da za a tunashe sauran jama'a game da su. AT: "Zan hallakar da Amalek gabaɗaya"
Mutane sukan daga hannayensu sama yayin da suke ɗaukan alkawari, don haka daga hannaye sama na nufin ɗaukan alkawari. AT: "an ɗauki alkawari"
AT: "Yahweh ya daga hannunsa sama" ko kuma "Yahweh ya ɗauki alkawari"
Wato Amalekawa. AT: "Amalekawa"
1Yetro, firist na Midiyan, surukin Musa, ya ji dukkan abin da Allah ya yi domin Musa domin kuma Isra'ila mutanensa. Ya ji cewa Yahweh ya fito da Isra'ila daga Masar.2Yetro, surukin Musa, ya ɗauki Ziffora, matar Musa, bayan da ya tura ta gida,3da 'ya'yanta maza biyu; sunan ɗan ɗaya Gashom, domin Musa yace, "Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa."4Sunan ɗayan Eliyeza, domin Musa yace, "Allah na kakannina ne taimako na. Ya cece ni daga takobin Fir'auna."5Yetro, surukin Musa, ya zo tare da 'ya'yan Musa da matarsa a wurin Musa a cikin jeji inda ya yi sansani a tsaunin Allah.6Ya cewa Musa, "Ni, surukinka Yetro, ina zuwa tare da matarka da 'ya'yanta maza biyu."7Musa ya tafi domin ya tarbi surukinsa, ya rusuna ƙasa, ya kuma sumbace shi. Suka tambayi lafiyar juna daganan kuma suka tafi cikin rumfa.8Musa ya gaya wa surukinsa dukkan abin da Yahweh ya yi wa Fir'auna da Masarawa saboda Isra'ila, game da dukkan wahalhalun da suka afko masu a kan hanya, da yadda Yahweh ya cece su.9Yetro ya yi farinciki game da dukkan nagartar da Yahweh ya yi wa Isra'ila, yadda ya cece su daga hannun Masarawa.10Yetro yace, "Bari a yabi Yahweh, domin ya cece ka daga hannun Masarawa daga kuma hannun Fir'auna, ya kuma kuɓutar da mutanen daga hannun Masarawa.11Yanzu na sani cewa Yahweh babba ne fiye da dukkan alloli, saboda sa'ad da Masarawa suka wulaƙanta Isra'ilawa da gadara, Allah ya ceci mutanensa."12Yetro, surukin Musa, ya kawo baikon ƙonawa da hadayu ga Allah. Haruna da dukkan dattawan Isra'ila suka zo su ci abinci a gaban Allah tare da surukin Musa.13Washegari Musa ya zauna domin yi wa mutane hukunci. Mutane suka tsaitsaya kewaye da shi daga safe har yamma.14Sa'ad da surukin Musa yaga dukkan abin da ya yi domin mutanen, ya ce, "Mene ne haka kake yi tare da mutanen?" Meyasa kake zaunawa kai kaɗai kuma dukkan mutanen ke tsayawa kewaye da kai daga safe har yamma?"15Musa ya cewa surukinsa, "Mutanen suna zuwa wurina ne su tambayi bishewar Allah.16Sa'ad da suka sami saɓani, suna zuwa wurina. Ina ɗaukar matsayi tsakanin taliki ɗaya da wani, kuma ina koyar da su farillan Allah da shari'unsa."17Surukin Musa yace masa, "Abin da kake yi bai da kyau sosai.18Tabbas zaka gajiyar da kanka, kai da mutanen dake tare da kai. Wannan ƙangi ya yi maka nauyi sosai. Ba zaka iya yin shi ba kai kaɗai.19Ka saurare ni. Zan baka shawara, kuma Allah zai kasance tare da kai, saboda kai ne a madadin mutane ga Allah, kuma kai ke kawo rikice-rikicensu gare shi.20Dole ka koya masu farillansa da shari'unsa. Dole ka nuna masu hanyar da zasu yi tafiya da kuma aikin da zasu yi.21Gaba da haka, dole ka zaɓi mutane tsayayyu daga cikin mutanen, mutane masu girmama Allah, mutane masu gaskiya masu ƙin ƙazamar riba. Dole ka sanya su bisa mutane su zama shugabannin dubbai, da ɗarurruka, da hamsin-hamsin, da goma-goma.22Za su yi hukunci tsakanin mutane a dukkan al'amuran yau da kullum, amma al'amura masu wuya sai su kawo maka. Game da dukkan ƙananan al'amura kuwa, zasu hukunta waɗannan da kansu. ta wannan hanyar zai yi maka sauƙi, za su kuma ɗauki nauyin tare da kai.23Idan ka yi wannan, idan kuma Allah ya umarce ka kayi haka, daganan zaka iya jurewa, kuma dukkan mutanen zasu iya tafiya gida a barace."24Sai Musa ya saurari maganganun surukinsa ya kuma yi dukkan abin da ya ce.25Musa ya zaɓi tsayayyun mutane daga dukkan Isra'ila ya kuma maida su shugabannin mutanen, shugabanni masu lura da dubbai, da ɗarurruka, da hamsin-hamsin, da goma-goma.26Suka hukunta mutane a al'amura masu sauƙi, al'amura masu wuya kuma suka kawo wa Musa, amma su da kansu suka hukunta dukkan ƙananan al'amura.27Daga nan Musa ya bar surukinsa ya tafi, Yetro kuma ya koma cikin ƙasarsa.
surukin* - Na nufin mahaifin matar Musa.
Wannan na iya nufin 1) Yetro ya kai Ziffora da 'ya'yanta maza biyu wurin Musa, ko kuma 2) Yetro tun can ya marabci Ziffora da 'ya'yanta maza biyu.
Abinda Musa ya yi kenan tun can. Ana iya kara haske a ma'anan wannan. AT: "bayan da Musa ya aiko ta gida wurin iyayenta
Wannan ɗan Musa da Ziffora kenan, wadda sunar sa na nufin "baƙo"
Wannan ma wani ɗan Musa da Ziffora ne, wadda sunan sa na nufin "Allah ne mai taimako na."
Wannan na nufin da Fir'auna ko mayakan Fir'auna sun kashe shi. AT: "na mutu ta hannun Fir'auna" ko kuma "na mutu ta hannun mayakan Fir'auna"
AT: "inda ya yi sansani da Isra'ilawa"
Waɗannan wasu hanyoyi ne na yau da kullum da suke nuna ban girma da dakufa a al'adan su.
Kalmar nan "Isra'ila" na nufin jama'ar Isra'ila. AT: "domin a tallafe wa jama'ar Isra'ila"
Musa yana maganar wahalhalun da suka sha ne kamar wahalhalun sun zo masu ne. AT: "dukkan wahalhalun da suka faru da su" ko kuma "dukkan wahalhalun da suka dandana"
Hannu na nufin ikon da mutum ke da shi ya yi wani abu. AT: "ikon Masarawa ... ikon Fir'auna" ko kuma "abinda Masarawa Masarawa ke yi maku ... abinda Fir'auna ke yi maku"
Yetro yana amfani ne da wannan tambayan domin yă nuna cewa abinda yake yi ba kyau. Ana iya juya wannan tambayan gangancin zuwa furci. AT: "Kada ka riƙa wannan duka da mutanen!"
Yetro yayi amfani ne da wannan tambayan domin yă nuna wa Musa cewa abinda yake yi ya yi yawa. Ana iya juya wannan tambayan ganganci zuwa furci. AT: "Kada ka zauna kai kadai ... daga safe har yamma!"
Kalmar nan "zauna" a nan na nufin "shari'a." Alkalawa sukan zama domin su saurare kararrakin mutane. AT: "kana yanke shari'a kai kadai" ko kuma "kai ne kadai kake yanke wa mutanen shari'a"
"ya za sa kanka ka gaji sosai"
Yetro yana maganar kuzarin aiki da Musa ke yi ne kamar wani kangi ne na jiki da Musa ke ɗauke da shi. AT: "Ai wannan aiki ya yi maka yawa"
...
Yetro yana maganar taimakon da Allah zai yi wa Musa ne kamar Allah zai kasance da shi ne. AT: "Allah zai taimake ka" ko kuma "Allah zai ba ka hikima"
Yetro yana maganar yadda Musa zai faɗa wa Allah saɓannin su ne kamar Musa yana kai saɓannin ne a wurin Allah. AT: "'ka yi magana da Allah game da saɓanninsu" ko kuma "ka yi wa Allah magana gane da muhawaransu"
Yetro yana magana rayuwa ko nuna hali ne kamar bi na. AT: Dole ka nuna masu yadda za su tafiyar da rayuwa" ko kuma "Dole ka nuna masu yadda za su tafiyar da halinsu"
Yetro ya ci gaba ne da magana da Musa.
"bugu da kari, dole ka zaɓa" ko kuma "Dole kuma ka zaɓa"
Yetro yana maganar basu iko ne kamar sanya su ne a bisa mutanen. AT: "Dole ka kuma ba su iko a bisa mutane"
"taron 1,000, taron 100, taron 50, taron 10"
...
Wannan na nufin cewa sai a faɗa wa Musa al'amura masu wuya. AT: "sai su faɗa maka game da al'amura masu wuya" ko kuma "idan an samu al'amura masu wuya, sai a faɗa maka domin kai ya yanke shari'a a kansu"
AT: "za su yi ayyuka masu nauyi tare da kai" ko kuma "za su taimake ka yi aiki masu wuya"
Ana iya kara haske game da aninda za su jure da shi. AT: "jurewa da nawayan aikin"
AT: "shugabannin mutanen"
Ana iya kara haske a kan abinda su ke iya zam tsayayyu a kai. AT: "mutane da ke iya shugabanta" ko kuma "mutanen da ke iya yanke shari'a"
"yanayi"
Wato su faɗa wa Musa. AT: "al'amura masu wuyan kuma suka faɗa wa Musa" ko kuma "yayin da suka samu al'amura masu wuya, sai su faɗa wa Musa domin yă yanke masu shari'a"
...
1A cikin wata na uku bayan da mutanen Isra'ila suka fito daga ƙasar Masar, a wannan ranar, suka zo jejin Sinai.2Bayan da suka bar Refidim suka kuma zo jejin Sinai, suka yi sansani a jejin a gaban tsaunin.3Musa ya hau zuwa wurin Allah. Yahweh ya kira shi daga tsaunin ya kuma ce, "Tilas ka gaya wa gidan Yakubu, mutanen Israi'la;4Kunga yadda na yiwa Masarawa, yadda na ɗauko ku bisa fikafikan gaggafa na kuma kawo ku a gare ni.5To yanzu, idan da biyayya kuka saurari muryata kuka kuma kiyaye alƙawarina, daganan zaku zama mallakata ta musamman daga cikin dukkan mutane, domin dukkan duniya tawa ce.6Zaku zama masarautar firistoci da al'umma mai tsarki domina. Waɗannan maganganun ne tilas ka faɗe su ga mutanen Isra'ila."7Daga nan Musa ya zo ya sammaci shugabannin mutanen. Ya faɗi a gabansu dukkan waɗannan maganganun da Yahweh ya umarce shi.8Dukkan mutanen suka amsa tare suka ce, "Za muyi dukkan abin da Yahweh yace." Daga nan Musa ya zo ya kawo rahoton maganganun mutanen ga Yahweh.9Yahweh ya cewa Musa, "Zan zo gare ka cikin girgije mai kauri saboda mutanen su iya ji sa'ad da zan yi magana tare da kai, su kuma gaskata da kai har abada." Daga nan Musa ya faɗi maganganun mutanen ga Yahweh.10Yahweh ya cewa Musa, "Ka tafi wurin mutanen. Yau da gobe Tilas ka keɓe su a gare ni. ka kuma sanya su su wanke tufafinsu.11Ku shirya domin rana ta uku, gama a rana ta uku Yahweh zai sauko bisa Tsaunin Sinai.12Tilas ka sanya kan iyakoki domin mutanen a dukkan kewayen tsaunin. Ka ce masu, 'Ku kula da cewa baku hau zuwa tsaunin ba koku taɓa kan iyakarsa. Duk wanda ya taɓa tsaunin tabbas za a kashe shi.'13Kada hannun wani ya taɓa irin wannan taliki. A maimako, babu shakka tilas za a jefe shi ko a harbe shi. Ko mutum ne ko dabba tilas a kashe shi. Sa'ad da aka busa ƙaho mai dogon amo, suna iya zuwa gindin tsaunin."14Daga nan Musa ya tafi ya gangara daga tsaunin zuwa ga mutanen. Ya keɓe mutanen ga Yahweh suka kuma wanke tufafinsu.15Ya cewa mutanen, "Ku shirya a rana ta uku; kada ku kusanci matayenku."16A rana ta uku, sa'ad da safiya ta yi, aka yi cida da wurge-wurgen walƙiya da girgije mai kauri a bisa tsaunin, da ƙarar kaho mai ƙarfi sosai. Dukkan mutanen dake cikin sansanin suka yi rawar jiki.17Musa ya fito da mutanen daga cikin sansanin su gamu da Allah, suka kuma tsaya a gindin tsaunin.18Tsaunin Sinai kuwa an lulluɓe shi ɗungum da hayaƙi saboda Yahweh ya sauko bisa kansa cikin wuta da hayaƙi. Hayaƙin kuwa ya yi sama kamar hayaƙin tanderu, tsaunin kuma gabaɗaya ya yi mummunar girgiza.19Da ƙarar ƙahon ta ci gaba da ƙaruwa bisa ƙaruwa, Musa ya yi magana, Allah kuma ya amsa masa da murya.20Yahweh ya sauko bisa Tsaunin Sinai, bisa ƙololuwar tsaunin, ya kuma sammaci Musa zuwa sama. Sai Musa ya haye sama.21Yahweh ya cewa Musa, "Ka gangara ka dokaci mutanen da kada su faso gareni su kalla, ko dayawa daga cikin su su hallaka.22Bari firistocin suma dake kusantata su keɓe kansu - su shirya kansu domin zuwa na - saboda kada in kai masu hari."23Musa ya cewa Yahweh, "Mutanen ba zasu iya zuwa har Tsaunin Sinai ba, domin ka dokace mu: 'Ku sanya kan iyakoki kewaye da tsaunin ku kuma keɓe shi ga Yahweh."'24Yahweh yace masa, "Tafi, ka gangara daga tsaunin, ka kuma kawo Haruna tare da kai, amma kada ka bar firistocin da mutanen su faso shingen su hawo zuwa gare ni, ko in kai masu hari."25Sai Musa ya gangara zuwa ga mutanen ya yi magana da su.
Wannan na nufin cea sun iso jejin a rana ta farko na wata kamar yadda suka bar Masar a rana ta farko ga wata. Rana ta farko a watan uku a kalandar Yahudawa ya kusa da watan biyar ne a kalandar Yammaci. AT: "A watan uku ... a rana ta farko ga wata"
"sun bar"
Wannan wani wuri ne a karshen jejin Sinai da mutane Isra'ila suka yi sansani. Duba yadda a kuka juya wannan sunan a 17:1
Kalmar nan "gida" na nufin iyalin da kuma zuriyar Yakubu. AT: "zuriyar Yakubu"
Jimlar nan "mutanen Isra'ila" da bayana abinda "gidan Yakubu" ke nufi.
Kalmar nan "ku" a nan na nufin Isra'ilawa. Yahweh yana gaya wa Musa abinda faɗa wa Isra'ilawa.
Wato yadda ya lura da su a tafiyan da suke yi. AT: "Na taimake ku a tafiyanku kamar yadda gaggafa ke ɗaukan ''ya'yansu a fikafikan ta"
biyayya anan kalmar aikatau ne. AT: "ku saurari murya ta ku kuma yi mini biyayya"
Muryar Allah na nufin abinda ya faɗa. AT: "abinda na faaɗ" ko kuma "kalamu na"
"kiyaye abinda alƙawarina ya bida ku yi"
...
Wato jama'ar Allah. AT: "al'umma keɓaɓɓiya da suke kamar firistoci" ko kuma "al'ummar mutane da ke yin abinda firistoci ke yi"
...
kalmar nan "maganganu" na nufin abinda Yahweh ya faɗa. AT: "dukkan abinda Yahweh ya umarce shi"
Ana iya kara haske akan inda Musa ya je. AT: "Musa ya koma kan dutsen da rohoton"
Kalmar nan "maganganu" anan na nufin abinda mutanen suka ce. AT: "abinda mutanen suka ce"
Wannan na iya nufin "ka ce masu su miƙa su a gare ni" ko kuma "ka ce masu su tsarkake kansu a gare ni."
"kayan sawa"
Wannan umarni ne ga mutanen Isra'ila.
Yahweh ya cigaba da magana da Musa.
"yi iyakoki." Wannan wata alama ce ta iyaka.
AT: "Dole ne a kashi duk wanda ya taɓa dutsen"
"Duk mutumin da ya taɓa"
"mutumin da ya yi haka" ko kuma "mutumin da ya taɓa wannan dutse"
...
Wannan na nufin kashe mutum da masu kori da baka ke iya yi ko harbi da duwatsu daga gofa ko majajjawa.
"dogon amo, mai ƙara"
Wannan wata hanye ce na cewa kada su yi jima'i da matayensu. AT: "kada ku yi jima'i da matayenku"
"yi rawar jiki don tsoro"
...
Wannan na nuna cewa hayaki mai yawan gaskiye kenan. AT: "kamar hayaki ne daga wuta mai yawa sosai"
wani murhu ne da ake iya sa wutarta ta zama da zafi ƙwarai.
sun cigaba da ƙaruwa
Kalmar nan "murya" anan na nufin ƙaran da Allah ya yi. Wannan na nufin 1) ta wurin magana da ƙarfi ƙamar tsawa" ko kuma 2) "ta wurin magana" 3) ta wurin sa tsawa ya yi ƙara"
"ya umarci Musa yă hauro sama"
Wato kada su ketere iyakar kenan. Duba yadda kuka juya wannan a 19:12. AT: "kada su ketere iyakar" ko kuma "kada su wuce iyakar"
"ka sauka"
Wato su ketere iyakar kenan. Duba yadda kuka juya wannan a 19:19. AT: "su ketere iyakar" ko kuma "su faso shigen"
1Allah ya furta dukkan waɗannan maganganu,2"Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito daku daga ƙasar Masar, daga gidan bauta.3Tilas ne ba zaku yi wasu alloli ba baya ga ni.4Ba zaku yi wa kanku sassaƙaƙƙen siffa ba ko kamannin wani abu dake can cikin sama, ko a ƙarƙashin ƙasa, ko a cikin ruwaye.5Dole ne ba zaku rusuna masu ba koku yi masu sujada, gama Ni, Yahweh Allahnku, Allah ne mai kishi. Ina horon muguntar kakanni ta wurin sauko da horo bisa zuriyarsu, har zuwa tsararraki na uku da na huɗu na waɗanda ke ƙi na.6Amma ina nu na alƙawarin aminci ga dubban waɗanda ke ƙaunata suke kuma kiyaye dokokina.7Dole ne ba zaku ɗauki sunan Yahweh Allahnku ba, a wofi, domin ba zan riƙe shi marar laifi ba duk wanda ya ɗauki sunana a wofi.8Ku tuna da ranar Asabaci, ku keɓe ta domina.9Dole kuyi aiki tuƙuru ku kuma yi dukkan aikinku a ranaku shida.10Amma rana ta bakwai Asabaci ce ga Yahweh Allahnku. A wannan rana baza kuyi wani aiki ba, koku, ko 'ya'yanku maza, ko 'ya'yanku mata, ko bayinku maza, ko bayinku mata, ko garken shanunku, ko baƙon da yake cikin ƙofofinku.11Domin a cikin ranaku shida Yahweh ya yi sammai da duniya, da teku, da dukkan abin dake cikin su, sai kuma ya huta a rana ta bakwai. Saboda haka Yahweh ya albarkaci ranar Asabaci ya kuma keɓe ta.12Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, saboda ka rayu na dogon lokaci a cikin ƙasar da Yahweh Allahnka yake baka.13Tilas ba zaka kashe kowa ba.14Tilas ba zaka yi zina ba.15Tilas ne ba zaka yi sata ba daga wani.16Tilas ne ba zaka bada shaidar ƙarya ba gãba da maƙwabcinka.17Tilas ne ba zaka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka ba; tilas ne ba zaka yi ƙyashin matar maƙwabcinka ba, bawansa namiji, baiwarsa mace, sansa, jakinsa, ko dukkan wani abu dake na maƙwabcinka."18Dukkan mutanen suka ga cidar da walƙiyar, suka kuma ji muryar ƙahon, suka kuma ga tsaunin na hayaƙi. Sa'ad da mutanen suka ga haka, suka firgice suka kuma tsaya daga nesa.19Suka cewa Musa, "Ka yi magana da mu, zamu kuma saurara; amma kada ka bari Allah ya yi magana da mu, ko kuwa za mu mutu."20Musa ya cewa Mutanen, "Kada kuji tsoro, domin Allah ya zo ya gwada ku saboda girmamawarsa ya kasance cikin ku, saboda kuma kada kuyi zunubi."21Sai mutanen suka tsaya nesa, Musa kuma ya kusanci duhun mai kauri inda Allah ya ke.22Yahweh ya cewa Musa, "Wannan ne tilas ka gayawa Isra'ilawa: 'Ku da kanku kunga cewa nayi magana da ku daga sama.23Kada ku yiwa kanku wasu alloli tare da ni, allolin azurfa ko allolin zinariya.24Tilas ku gina mani bagadin ƙasa, dole kuma ku yi hadayar baye-baye na ƙonawa a kansa, baye-baye na zumunta, tumaki, da shanu. A cikin dukkan inda nasa a girmama sunana, zan zo gare ku in albarkace ku.25Idan kuka yi mani bagadin dutse, ba zaku gina shi ba da dutsen da aka yanko, domin idan kuka yi amfani da kayan aikinku a kansa, kun riga kun gurɓata shi.26Tilas ne ba za ku hau bisa bagadina ta matakala ba, saboda kada tsirancinku ya bayyana."'
"wurin dă da kuke barori"
"Ba za ku yi ibada ga wasu alloli ba sai dai ni"
"kuma ba zai yi abu mai kamanni"
Kalmar nan "su" na nufin sifa da aka sassaƙa ko gumki.
Allah yana son mutane si yi wa shi kadai ne ibada.
Allah zai horas da mutane saboda zunuban iyayensu.
"tsararraki na 3 da 4.
"saboda alƙawari na, Ina da aminci ga dubban" ko kuma "Ina ƙaunar dubbai da aminci"
"tsrarraki dubbai"
"yi amfani da sunana"
"a banza" ko kuma "ba tare da ban girma ba"
"Ko kadan ba zan taɓa ɗaukan shi mai laifi ba" ko kuma "Ba shakka zan horas"
"ku yi dukkan abubuwan da kun saba yi"
Garurruka suna da ganuwa kewaye da su domin tsare magabta, da kuma kofofi domin shiga da fita. AT: cikin al'ummominku" ko kuma "a cikin garinku"
...
Wannan na iya nufin 1) Allah ya sa ranar Asabar din ta ba da amfani mai kyau, 2) Allah ya ce ranar Asabar rana ce mai kyau.
"keɓe ta domin wata manufa ta musamman"
"Kada ku yi jima'i da kowa da ba matarka matarka ko mai gidanki ba"
"bada rohoton ƙarya ba" ko kuma "ba za ka faɗi ƙarya akan wani ba"
"ba za ka yi matuƙar marmari ka sami" ko kuma "ba za ka so ta ƙarɓi"
"ƙara"
"hayaƙi na fitowa daga duwatsun"
"suka yi rawar jiki da tsoro"
"suka tsaya can"
"saboda ku girmama shi kaa kuma ku yi zunubi"
"suka je kusa da"
"Ka gaya wa Isra'ilawa cewa"
"Ga shi ku ji ina magana da ku daga sama"
"Ba za ku kuskura ku yi wa kanku wasu alloli in banda ni ba"
"alloli da aka yi su da azurfa ko zinariya" ko kuma "gumakai da aka kera su daga azurfa ko zinariya"
bagadi da akayi da wasu abubuwa daga kasa kamar su duwatsu, kasa ko laƙa.
AT: "na zaɓa maku ku ku giramamani"
"Kada ku yi bagadi mai mataka"
nuna tsirancin jikinku"
1To waɗannan su ne sharuɗan da zaka sa a gabansu:2Idan ka sayi bawa Ba'ibrane, zai yi bauta shekara shida, a ta bakwai zai tafi 'yantacce ba tare da ya biya kome ba.3Idan shi kaɗai ya zo, sai ya tafi shi kaɗai, idan kuma ya zo da mata, zata zama 'yantarta ta tafi tare da shi.4Idan ubangijinsa ne ya yi masa aure, da matar da 'ya'yanta zasu zama na ubangijinsa, shi kuwa zai zama 'yantacce ya tafi shi kaɗai.5Amma idan bawan da kansa ya ce, "Ina ƙaunar ubangijina da matata da 'ya'yana; ba zan zama 'yantacce in tafi ba,"6Dole ubangijinsa ya kawo shi wurin Yahweh, dole ubangijinsa zai kawo shi ƙofa ko bakin ƙofa, kuma dole ubangijinsa zai huda kunnensa da allura. Daga nan zai zama bawa har iyakar rayuwarsa.7Idan mutum ya sayar da ɗiyarsa mace ta zama baiwa, ba zata tafi haka nan kamar yadda bayi maza suke yi ba.8Idan ba ta gamshi ubangijinta wanda ya ajiye ta domin kansa ba, to dole ne a fanshe ta. Ba zai sayar da ita ga waɗan su baƙin mutane ba. Ba shi da wannan damar saboda ya yaudare ta.9Idan ubangijinta ya bada ita ga ɗansa ta zama matarsa, sai ya ɗauke ta kamar ɗiyarsa.10Idan ya ɗauko wata matar, kada ya hana ta abinci ko tufafi ko kuwa 'yancinta na aure.11Amma idan bai ba ta waɗannan abubuwa uku ba, to sai ta tafi a matsayin 'yantarta, ba tare da ta biya wasu kuɗi ba.12Ko wane ne ya doki wani mutum har ya mutu, shima sai a kashe shi.13Idan mutumin bada manufa ya yi ba, amma ya yi da kuskure ne, zan tanada wurin da zai gudu.14Idan wani mutum ya kaiwa maƙwabcinsa hari, ya yaudare shi har ya kashe shi, zaka ɗauke shi, koda yana kan bagadin Yahweh, domin a kashe shi.15Dukkan wanda ya doki mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole za a kashe shi.16Dukkan wanda ya yi garkuwa da mutum - ko wanda ya yi garkuwa da mutumin ya sayar da shi, ko kuwa an same shi a hannun mai garkuwar - dole ne a kashe mai yin garkuwar.17Dukkan wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole za a kashe shi.18Idan mutane suka yi faɗa, ɗaya ya bugi ɗayan da dutse ko ya naushe shi, kuma mutumin bai mutu ba, amma ya kwanta saboda dukan da ya yi masa;19idan mutumin ya samu ya tashi, har yana tafiya yana dogara sanda, shi wanda ya doke shi zai biya shi diyyar lokacin da ya ɓata; dole mutumin ya biya kuɗin jinyar sa har ya warke. Amma mutumin bai tserewa laifin kisan kai ba.20Idan mutum ya doki bawansa ko baiwarsa da sanda, har bawan ya mutu sanadiyar wannan duka, dole ne za a hori mutumin. Duk da haka,21idan bawan ya rayu kwana ɗaya ko biyu, ba za a hori mutumin ba, saboda ya sha wuyar rashin bawansa.22Idan mutane suka yi faɗa suka yi wa mace mai ciki rauni, har ta yi ɓari amma ba wani rauni a jikinta, mai laifin zai biya tara yadda mijinta ya bukata, dole ya biya abin da alƙali ya ce ya biya.23Amma idan akwai rauni mai muni, sai a bada rai maimakon rai,24ido maimakon ido, haƙori maimakon haƙiri, hannu naimakon hannu, ƙafa maimakon ƙafa,25ƙuna maimakon ƙuna, rauni maimakon rauni, ƙujewa maimakon ƙujewa.26Idan mutum ya bugi bawansa ko baiwarsa a ido har idon ya mutu, bawan zai zama 'yantacce ya tafi maimakon idonsa ko idonta.27Idan ya buge wa bawansa ko baiwarsa haƙori har ya cire, bawan ko baiwar zai zama 'yantacce ya tafi maimakon haƙorinsa ko haƙorinta.28Idan să ya soki mutum namiji ko mace har ya mutu, dole za a jejjefe san, kuma ba za a ci namansa ba; amma mai san zai zama baratacce.29Amma idan san ya kan soki mutane dama, kuma an yi wa mai san gargaɗi bai kuwa ɗaure san ba, idan san ya soki wani mutum ko wata mace har ga mutuwa, za a jejjefe san, mai san ɗin shima za a kashe shi.30Idan kuwa an ce a biya diyya domin ransa, to, dukkan abin da aka bukata a biya haka zai biya.31Idan san ya soki ɗan wani ko ɗiyar wani, mai san zai yi kamar yadda wannan ka'ida ta bukaci ya yi.32Idan san ya soki bawan wani mutum na miji ko mace, mai san zai biya azurfa talatin, san kuma za a jejjefe shi.33Idan mutum ya buɗe rami ko ya gina rami bai rufe shi ba, idan să ko jaki ya faɗa cikin sa,34wanda ya yi ramin zai biya diyya. Dole zai biya mai dabbar kuɗi, matacciyar dabbar kuma za ta zama asararsa.35Idan san wani ya yi wa san wani rauni har ya mutu, za a sayar da san mai rai sai su raba kuɗin, su kuma raba san wanda ya mutu.36Amma idan dama san ya saba yin haka, kuma an yiwa mai san gargaɗi amma bai ɗaure sansa ba, zai biya să maimakon să matacciyar dabbar kuma za ta zama ta sa.
Yahweh ya cigaba da wa Musa magana.
"dole ka basu" ko kuma "dole ka ce masu"
Yahweh ya gaya wa Musa dokokinsa ga mutanen Isra'ila.
Ana iya kara haske ga bayyanin "shi kadai" a nan. Wasu harsuna na iya su buƙaci wasu karin bayyani da ke nuna cewa ya yi aure tun yana bauta ne. AT: "Idan ya zama bare tun ba shi da mata, sa annan kuma idan ya yi aure tun yana bauta ne, shugabansa zai buƙaci yă sake mutumin"
"ba tare da mata ba"
"idan yana da aure kamin ya zama bare" ko kuma "idan ya zo a matsayin mai aure"
ya faɗa kai tsaye
Ba na son shugabanna ya bani 'yanci"
"a saka rami a kunnensa"
wani abu ne da ake amfani da shi domin yin rami
"har rayuwarsa ta kare" ko kuma "har ma yă mutu"
"ya zaɓa"
AT: "lallai ne ya bar mahaifin ta ya sãke fansan ta
"ba shi da iƙo ya sayar"
...
"ya zaɓe ta"
AT: "lallai ne yă ba wa matarsa na farko abinci, da tufafi a 'yancin ta na aure iri ɗaya"
"rage"
Wannan yana haɗe da hakin mai gida ga matarsa, har ma da kwana da ita. AT: "kuma lallai ne yă cigaba da kwana da ita kamar yadda yăke dã"
...
AT: "lallai ne a kashe wannan mutumin" ko kuma "ya zama dole a kashe wannan mutumin"
...
AT: "Zan tanada wurin da mutumin zai iya gudu domin tsira"
"bayan ya yi tunani da kyau akai"
Kalmar nan "shi" na nufin mutumin da ya kashe makwabtansa.
AT: "domin ka kashe shi"
AT: "Idan wani ya gugi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole ne ku tabbatar ku kashe shi" ko kuma "Ku tabbatar kun kashe duk wanda ya bugi mahaifinsa ko mahaifiyarsa"
...
"tare da shi"
AT: "dole ku tabbatar kun kashe mai yin garkuwar"
...
AT: "bai iya tasuwa a gado kuma ba"
ya samu sawwuƙi"
Wato sandar da mutum ke iya jingina a kai domin yă yiya taimake shi a tafiya.
Wannan na nufin yanayin da mutum ba zai iya aiki yă samu kuɗi. Kuna iya juya wannan da haske a yanda za ku juya shi. AT: "lokacin da bai iya ya yi aiki ba"
"biyar kuɗin kiwon lafiyar sa" ko kuma "biyyar kuɗin jiyyar sa har warkewa" (UDB)
"ta dalilin jin wannan rauni" ko kuma "domin mai gidansa ya buge shi"
AT: "lalle ne ku tabbatar kun hukunta wannan mutumin"
Kuna iya sanar a fili cewa bawarsa yana da amfani gareshi. AT: "domin ya riga ya rasa bawarsa da ke da muhimmanci a gare shi"
"jaririn da ke cikin ta ya warke" ko kuma "ta haife jaririn da ke cikinta kamun lokaci har ya mutu"
AT: "lalle ne ku tabbatar kun ci mai laifin da tãra" ko kuma "lalle ne mai laifin yă biya"
...
Wato idan ta ji rauni, lalle ne mutumin da ya ji mata raunin ya ji rauni shi ma. AT: "lalle ne yă ba da nasa rai domin nata rai, idonsa kuma domin nata ido"
A nan "wani" na nufin mai bawa.
"a matasyin biya." 'Yanta abinda mutum ke iya yi wa wani ne ko yă ba wa wani ya yi domin biyan rashin da ya jawo.
"ya ji rauni da kafonsa"
AT: "lalle ne a jejjefe san har mutuwa"
AT: "kada ku kuskura ku ci namansa ba"
AT: "mai san kuwa zai kuɓuta"
AT: "dole ku kashe mai san"
Mai san na iya biyan tara domin ya ceci rasan, sa'annan zai biya duk abinda alkalawa suka zatas. AT: "idan mai bijimin zai iya biyan tara domin yă ceci ransa, lallai ne yă biya cikakken kuɗin da alkalai suka sa yă biya"
"ya ji rauni da kafonsa"
"giram 330 na azurfan." Kowane Shekel ɗaya yana da giram gomashaɗaya.
AT: "lalle ne ku kashe san da jejjefa"
"ya buɗe rami a kasa"
Lalle ne a biya mai san diyya domin rashin dabbarsa. AT: "a biya mai mataccen dabbar"
Mutumin da ya biya diyyar ɓataccen dabbar zai zama mai dabbar, yă kuma yi duk abinda yake son yă yi da shi. Ana iya bayana ma'anar wannan maganar a fili. AT: "zai zama na mai ramin"
"raba kuɗin" ko kuma "raba kuɗin da sun karɓa"
AT: "idan mutane sun san" ko kuma "idan mais shi ya sani"
"ya ji wa wasu dabbobi rauni da ma"
Wato mai san bai tsare sansa a wata danga ba. AT: "mai san bai sa san a wata danga ba"
Mai san da ya yi kisa zai ba wa mutumin da ya rasa nasa să wani să. AT: mai să da ya yi kisa zai tabatar ya ba da rayayyen să ga wanda san sa ya mutu
1Idan mutum ya saci bijimi ko tinkiya, ya kashe ko ya sayar, zai biya da bijimai biyar a kan bijimi ɗaya, ko tinkiya huɗu a kan tinkiya ɗaya.2Idan aka kama ɓarawo yana fasa gida, aka buge shi har ya mutu, ba za a kama kowa da laifin kisan kai a kansa ba.3Amma idan rana ta fito kamin ya fasa ya shiga, za a kama wanda ya kashe shi da laifin kisan kai. Dole ɓarawo ya biya diyya. Idan kuwa ba shi da komi, sai a sayar da shi saboda satar sa.4Idan an sami dabbar da ya sata a wurin sa, ko bijimi ne ko jaki ko tinkiya, dole ya biya riɓi biyu na abin da ya sata.5Idan mutum yana kiwo, ya bar dabbarsa ta kwance ta yi kiwo a gonar wani, dole ya biya diyya daga gonarsa mafi kyau ko daga garkarsa mafi kyau.6Idan wuta ta ƙwace ta shiga cikin ƙayoyi har ta tarar da hatsi, ko an girbe ko kuwa yana tsaye har ta cinye gonar, dole wanda ya kunna wutar ya biya diyya.7Idan mutum ya ba maƙwabcinsa ajiyar kuɗi ko kaya, sai aka sace abin a gidansa, idan aka kama ɓarawon dole zai biya diyyar abin da ya sata riɓi biyu.8Amma idan ba a kama ɓarawon ba, sai mai gidan ya zo wurin alƙali a gani ko ya ɗauki wani abu cikin kayan maƙwabcinsa.9Gama kowacce jayayya game da wani abu, ko bijimi ko jaki ko tinkiya ko kayan sawa, ko kowanne abin da ya ɓace wani ya ce, "Wannan nawa ne," dole a zo wurin alƙali da masu jayayyar. Wanda a ka samu da laifi zai biya maƙwabcinsa diyya riɓi biyu.10Idan mutum ya ba maƙwabcinsa ajiyar jaki ko bijimi ko tinkiya ko kowacce irin dabba, sai ta mutu ko aka ji mata rauni ko aka ɗauke ta ba wanda ya gan ta,11dole su biyun suyi rantsuwa domin a gane wani bai ɗauki kayan maƙwabcinsa ba. Sai mai abin ya yarda da haka kuma ɗayan ba zai biya diyya ba.12Amma idan sacewa aka yi, sai mutumin ya biya diyya ga mai shi.13Idan kuma an yayyaga dabbar ne, sai mutumin ya kawo dabbar shaida. Ba zai biya dabbar da aka yayyaga ba.14Idan mutum ya yi aron dabba a wurin maƙwabcinsa, sai aka yi wa dabbar rauni ko ta mutu ba a wurin mai ita ba, dole ɗaya mutumin ya biya diyya.15Amma idan dabbar tana wurin mai ita, ɗaya mutumin ba zai biya ba; idan hayar dabbar aka yi sai a biya kuɗin hayar.16Idan mutum ya ruɗi budurwa wadda ba a yi riƙon ta ba, har ya kwana da ita, dole yasa ta zama matarsa ta wurin biyan dukiya yadda aka bukaci ya biya.17Idan mahaifinta ya ƙi ba shi ita, to dole ya biya dukiya dai-dai da ta budurwa.18Dole ne ba zaka bar mayya ta rayu ba.19Dukkan wanda ya kwana da dabba dole za a kashe shi.20Dukkan wanda ya yi hadaya ga wani allah in ba Yahweh ba dole za a hallaka shi.21Dole ne ba zaku yi wa baƙo laifi ba ko kuwa ku ƙware shi, domin dă ku baƙi ne a Masar.22Kada ka wulaƙanta gwauruwa ko maraya.23Idan ka ƙware su, suka yi kira gare ni, babu shakka zan ji kiran su.24Fushina zai yi, ƙuna kuma zan kashe ka da kaifin takobi; matanka zasu zama gwauraye, 'ya'yanka kuma su zama marayu.25Idan ka bada rancen kuɗi cikin mutanena matalauta, kada ka zama kamar mai bada kuɗi da ruwa, ba zaka sa riba ba.26Idan ka karɓi rigar maƙwabcinka da alƙawari, dole ka dawo masa da ita kafin rana ta faɗi,27gama ita kaɗai ce abin rufarsa; ita ce rigar da zai sa jikinsa. Da me zai rufa? Sa'ad da ya kira gare ni, zan ji kiransa gama ni mai tausayi ne.28Kada ka yi mani saɓo, Allah, ko ka zagi mai mulkin mutanenka.29Kada ku hana baye-baye daga amfanin gonarku ko ruwan inabinku. Dole ku bani nunar fari ta 'ya'yanku.30Dole kuma ku yi haka da bijimanku da tumakinku. Gama kwana bakwai za su yi da iyayensu, a rana ta takwas za ku bada su gare ni.31Za ku zama mutane keɓaɓɓu gare ni. Kada ku ci kowanne abin da naman daji ya kashe a gona. Sai dai, ku jefa wa karnuka shi.
Yahweh ya cigaba da gaya wa musa shari'u ga jama'ar Isra'ila.
AT: "Duk wanda ya kama ɓarawo"
...
AT: "Duk wanda ya buge shi har ya mutu"
...
"idan ko ina na da haske kamun ya shiga" ko kuma "idan ya fashe ya shiga kuma bayan rana ya haura ne"
...
"ya biya abinda ya sata"
AT: "dole ku sayar da shi a matsayin bawa domin ku yi biyyar abinda ya sata"
AT: "Idan an iske cewa yana da dabbar da ya sata yana raye"
zai biya dabbobi biyu na kowane dabba ɗaya da ya sata
...
"yi barna a bonar"
"dole ya biya mai gonar"
"Idan wani ya sa wuta har ta shiga cikin kayoyi"
"ta kama kasa har bushsashen ciyawa"
Wato hatsi da aka girɓe aka tara. "tararren hatsi" ko kuma "girbaɓen hatsi"
Hatsi da ba a girɓe ba, amma ya kai na girɓi.
"wuta ta cinye gonar" ko kuma "wuta ta cinye filin"
dole ne yă biya hatsin da wuta ta batar"
"ya lura da shi" ko kuma "ya ajiye shi da kyau"
AT: "idan wani ya sace shi"
wanda ya saci abu
AT: "Idan kun sami ɓarawon"
"zo gaban alƙamlai domin su bincika ko ya"
Wannan karin magana ne. Idan kuna da wata hanayar faɗin wannan a harshenku, kuna iya amfani da shi anan. AT: "ya saci kayan maƙwabcinsa"
Dole ne alkalai su saurare mutum biyu da ke cewa abun nasune kamun alkalain su san wanene da laifi.
Mutumin da ake zargi da sata ne kadai zai ɗauki rantsuwa. Kuma sai mai bataccen dabbar ya amince da rantsuwar. AT: "har sai mai kiwon dabbar ya ɗauki rantsuwa a gaban Yahweh tukuna kamun mai shi yă amince da rantsuwar"
AT: "Amma idan sani ne ya saci dabbar daga gare shi"
...
AT: "Ba zai biya dabbar da dabbobin jeji suka yayyaga din ba"
"dole ne ya biya da wani dabba" ko kuma "dole ne a biya mai dabbar"
AT: "Idan wani ne dai ya karɓi hayar dabbar"
Ba lalle ne shi da ya yi hayar dabbar yă ya biya ainihin mai dabbar fiye da kuɗin hayar dabbar ba. Kuɗin zai kai na biyar bataccen dabbar. AT: "Kuɗin da aka biya na hayar dabbar zai biya na asaran dabbar"
"kuɗin da aka biya domin hayar dabbobin"
"lallashe"
"ba a yi mata alkawarin aure ba"
Wato idan ya yi jima'i da ita kenan. AT: "idan ya yi jima'i da ita"
"kudin sadaki"
Waɗannan wakilan suna na nufin mutumin da ya lallashe budurwa."
A nan "kwana da dabba" na nufin yin jima'i da dabba. AT: "Lallai ne ku tabbatar ku kashe mutumin da ya yi jima'i da dabba"
AT: "Yahweh, dole ku hallakar da wannan mutumin gaba ɗaya"
"wulaƙanta baƙo" ko kuma "cuce baƙo"
AT: "Wajibi ne ku bi da duk gwamraye da 'ya'ya mara uba da kirki"
"mace da mai gidanta ya ratsu"
"maraya" ko kuma " 'ya da basu da iyaye"
A kashe mutum "da takobi" karin magana ne da ke nufin cewa mutumin zai mutu da ƙarfi, ko kuma a cikin yaƙi. AT: "za ku mutu da ƙarfi"
"mai ba da rancen kuɗi"
"chaje shi wani kuɗi a kan aron da yayi" ko kuma "chaje shi wani kuɗi a kan rancen da yayi"
...
"kaday rigar da zai sa yă ju dumi"
Wannan tambayan yana kara nanaci ne. Ana ma iya kara ƙarfinsa. AT: "To ai ba zai samu abinda zai rufu da shi ba sa'an da ya kwanta barci!"
"jinkai" ko kuma "mai alheri"
"Kada ku zagi Allah" ko kuma "Kada ku faɗi mugun magana game da Allah"
"kuma kada ku roƙi Allah ya yi wa mai muki abubuwa marar kyau"
AT: "Lalle ne ku kawo dukka baye-bayenku"
"ku miƙa 'ya'yanku ta fãri gareni"
"miƙa mini 'ya'yanku na fãri"
AT: "Gama kwana 7 da haifuwa"
AT: "rana ta 8 ga kirge.
"ku miƙa su gareni"
1Kada ku ba da shaidar ƙarya game da wani. Kada ku haɗa kai da mai mugunta ku zama maƙaryatan shaidu.2Kada ku bi rububi domin ku yi mugunta, ko ku goyi bayan rububi ku yi shaida domin ku ɓata adalci.3Kada ku nuna wa matalauci fifiko idan a na yi ma sa shari'a ko kaɗan.4Idan ka gamu da bijimin maƙiyinka ko jakinsa ya ɓace, dole ka dawo masa da shi.5Idan ka ga jakin wanda yake ƙin ka ya faɗi, kaya ya danne shi, kada ka bar shi shi kaɗai. Dole ka taimake shi ka tada jakinsa.6Kada ka yar da adalci gefe sa'ad da ake yi wa matalaucinka shari'a.7Kada ka haɗa kai da waɗan su ku yi zargi a kan ƙarya, kada ku kashe marar laifi ko mai adalci, gama ba zan 'yantar da mai mugunta ba.8Kada ku karɓi toshi ko kaɗan, gama toshi ya kan sa masu gani su makance, ya hana maganar masu aminci aiki.9Kada ku cuci baƙo, da yake ka san rayuwar baƙo, gama da kuma baƙi ne a Masar.10Shekaru shida za ka shuka iri a gonakinka ka sami amfaninsa.11Amma a shekara ta bakwai za ka bar ta ba za ka noma ba, domin matalauta na cikin ku su ci abinci. Abin da suka rage namun daji za su ci. Haka kuma za ku yi da gonakinku da garkunan inabinku.12Cikin kwanaki shida za ku yi aiki, amma a rana ta bakwai dole za ku huta. Ku yi haka domin bijimanku da jakinku su huta, domin 'ya'yan bayinka da kowanne baƙo ya huta ya wartsake.13Ku yi lura da dukkan abin da na gaya maka. Kada ku ambaci sunayen waɗansu alloli, ko ku bari a ji sunayensu daga bakinku.14Dole ku je ku yi mani biki sau uku a kowacce shekara.15Za ku yi bikin gurasa marar gami. Kamar yadda na umurce ku, za ku ci gurasa marar gami kwana bakwai. A wannan lokaci, za ku zo gabana a watan Abib, wanda aka tsaida domin yin haka. A cikin wannan wata ne kuka fito daga Masar. Amma kada ku zo gabana hannu wofi.16Dole za ku yi Bikin Kaka, na nunar fari na irin da kuka shuka a gonakinku. Kuma dole ku yi Bikin Tattarawa a ƙarshen shekara, sa'ad da kuka tattara amfanin gonakinku gida.17Dole mazajenku dukka su zo gaban Ubangiji Yahweh sau uku a shekara18Dole ba za ku miƙa mani jinin hadayunku da gurasa wadda take da gami ba. Kitsen hadayun idodina ba zai wuce dukkan dare ya kai safiya ba.19Dole ku kawo zaɓaɓɓar nunar fari na gonakinku gidana, gidan Yahweh Allahnka. Ba za ka dafa 'yar burguma mai shan nonon uwarta ba.20Zan aiko da mala'ika ya yi maku jagora a kan hanya, ya kawo ku wurin da na shirya.21Ku saurare shi ku yi masa biyayya. Kada ku cakune shi domin ba zai gafarta laifofinku ba. Sunana yana kansa.22Idan kuka yi biyayya da muryarsa kuka yi dukkan abin da na faɗa maku, zan zama maƙiyi ga maƙiyanku in tayar wa masu tayar maku.23Mala'ikana zai shiga gabanku ya kawo ku wurin Amoriyawa da Hittiyawa da Firizziyawa da Kan'aniyawa da Hibiyawa da Yebusiyawa. Zan hallaka su.24Kada ku rusuna wa allolinsu, ku yi masu sujada, ko ku yi kamar yadda suke yi. Maimakon haka, dole ku kaɓantar da su dukka, ku ragargaza ginshiƙan duwatsunsu rugu--rugu.25Dole Yahweh Allahnku za ku yiwa sujada, kuma zai albarkaci gurasarku da ruwanku. Zan kawar da ciwo daga cikin ku.26Ba matar da za ta zama bakarariya ko ta yi ɓarin jariri a ƙasarku. Zan baku tsawancin kwana.27Zan sa tsoro a cikin waɗanda kuke shiga ƙasarsu. Zan kashe dukkan mutanen da kuka gamu da su. Zan sa dukkan maƙiyanku su juya maku baya a wurin yaƙi.28Zan aiko da zirnaƙo ya kori Hibiyawa da Kan'aniyawa da Hittiyawa daga gabanku.29Ba zan kore su a cikin shekara ɗaya ba domin kada ƙasar ta zama ba kowa, kada namun daji su yi maku yawa ƙwarai.30Maimakon haka zan kore su da kaɗan-kaɗan har ku yi yawa ku gaji ƙasar.31Zan sa iyakokinku daga Tekun Iwa zuwa Tekun Filistiyawa, kuma daga jejin Kogin Yuferatis. Zan baku nasara a kan dukkan mazunan ƙasar. Za ku kore su daga gabanku.32Kada ku yi amana da su koda allolinsu.33Kada su zauna a ƙasarku, domin kada su sa ku yi zunubi a gare ni. Idan kuka yi sujada ga allolinsu, babu shakka zai zama tarko a gare ku."'
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila.
Wannan ɗaya yake da ƙarya ko maƙaryatan shaidu.
"kuma kada kuma ku yi magana"
Wannan maganar yana bayyana yadda mutum na iya keterewa ne yă haɗa hannu da taron mutane. AT: "aikata abinda yawancin muutane ke so" ko kuma "yarda da yawancin mutane"
ƙetere doka ko haramtacce ayyuka da ke jawo rashin adalci ga mulki
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila
"Kada ku yi duk abinda ba zai kawo sakamako da ke daidai ba" da zai jawo yanci ga mai laifi ko hukunci ga marar laifi.
A wannan jimlar, wannan na nufin shari'ar gaskiya, da ke daidai
"muhawara"
"Ba zan iske mugu marar laifi ba" ko kuma "Ba zan ce da mugayen mutane marar laifi ba"
A nan ana maganar "toshi" kamar wani mutum ne. AT: "toshi yankan ƙasƙantar ... rushe"
"irin rayuwar baƙo an ƙasar baƙonci"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila
"amfanin gona"
...
"yadda yake" ba amfanin ba da wani abu"
Matalauta suna iya samu cu ci duk wani abinda ya tsira a gonar ba ba'a nome ta ba. AT: "Domin matalauta a cikinku su girba su kuma ci duk abincin da ya tsira da kansa an wanan gona"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila.
"ku yi biyayya da"
"dabbobin aikinku"
AT: "ko wanne baƙo yă huta yă kuma samu ƙarfin jikinsa"
A nan "sunaye" na nufin yin addu'a ga sauran alloli. AT: "Kada ku yi addu'a ga sauran alloli"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila.
Wannan shi ne wannan wata na fãri a kalandar Yahudawa. Abib shi ne ta karshen watan Uku da kuma farkon watan huɗu a kalandar kasashen Yamma. Duba yadda kuka juya wannan a 13:3.
hannu-wannan na nanata cewa lallai ne Isra'ilawa su bayyana a wurin Yahweh da bayaswar da ya ɗace. AT: "Ko zo gare ni da bayaswar da ya cancanta" ko kuma "ku riƙa kawo mini bayaswa"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila.
"Dole ku girmamma" ko kuma "Dole ku yi bikin"
Wannan shagablin biki ne na girbin dukkan amfanin gona na shekara.
"A nan "zo" na nufin tattaruwa domin sujada. AT: "Dole ne dukkan mazajenku su taru su yi mini sujada"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila.
An ƙone kitsen ne a matsayin bayaswa ga Yahweh amma ba za a ci ba sam.
"mafi kyau kuma nunar fari daga girbinku"
Wannan ayyukan sihirin haifuwa ne da Kan'aniyawa ke yi, don haka Allah bai yarda wa Isra'ilawa su sa hannu ba.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila.
...
"Idan kun cakune shi, ba zai gafarta"
A nan "suna" na nufin Iƙon Allah. AT: "Yana da iƙo na"
Anan "murya" na nufin abinda mala'ikar ke faɗi. AT: "Idan kuka yi biyayya da abinda yake faɗi"
Waɗannan jimla biyun suna da manufa guda ne, kuma suna nanata abu ɗaya ne.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila.
Isra'ilawan ba za su yi rayuwa kamar yadda mutanen da suke bauta wa wasu alloli ba. AT: "Kada ... ku yi rayuwa kamar yadda waɗanda suke bauta wa wasu alloli"
Wannan na nufin ci da shanku. AT: "Zan albarkaci ci da shanku" ko kuma "Zan albarkace ku ta wurin ba ku abinci da ruwan sha"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila.
AT: "Kowacce mace za ta iya ɗaukar ciki har tă haife 'ya'ya masu lafiya"
zuban ciki
Wasu kwari ne masu firiya da ke iya harbin mutane har yă sa su ji za fi.
"domin ba kowan da zai zauna a cikin ƙasar"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila.
Wannan na nufin bautar wasu alloli zai jawo mutanen Isra'ila ga hallaka kamar baddar da aka kama a tarkon mafarauci.
1Sa'an nan Yahweh yace da Musa, "Ku hawo wuri na-kai, da Haruna, da Nadab, da Abihu, da dattawa saba'in na Isra'ila, ku yi mani sujada daga nesa.2Musa kaɗai ne zai zo kusa da ni. Sauran ba zasu zo kusa ba, mutanen ba zasu hawo tare da shi ba."3Musa ya je ya faɗa wa mutanen Isra'ila dukkan maganganun Yahweh da farillai. Dukkan mutanen suka amsa da murya ɗaya suka ce, "Za mu yi dukkan abin da Yahweh yace,"4Sa'an nan Musa ya rubuta dukkan maganganun Yahweh. Tun da sassafe, Musa ya gina bagadi a kusa da tsaunin ya shirya duwatsu goma sha biyu, domin duwatsun goma sha biyu su zama a madadin kabilu goma sha biyu na Isra'ila.5Ya aiki waɗansu samarin Isra'ila su miƙa baye-baye na ƙonawa da hadaya ta baye-bayen zumunta na bijimai ga Yahweh.6Musa ya ɗauki rabin jinin ya sa cikin darurruka; ya yayyafa sauran rabin a bisa bagadin.7Ya ɗauki littafin Alƙawarin ya karanta shi da murya ga mutanen. Suka ce, "Za mu yi dukkan abin da Yahweh ya faɗi. Za mu zama masu biyayya."8Sa'an nan Musa ya ɗauki jinin ya yayyafa shi a kan mutanen. Ya ce, "Wannan shi ne jinin alƙawarin da Yahweh ya yi daku sa'ad da ya baku alƙawari da dukkan waɗannan maganganun."9Sa'an nan Musa da Haruna da Nadab da Abihu, da dattawa saba'in na Isra'ila suka hau bisa tsaunin.10Suka ga Yahweh na Isra'ila. A ƙarƙashin ƙafafunsa a kwai wani dakali wanda aka yi kamar da n safire, yana sheƙi kamar sararin sama.11Yahweh bai ɗora hannu don fushi a kan dattawan Isra'ila ba. Suka ga Yahweh, suka ci suka sha.12Yahweh yace da Musa, "Ka hawo wurina a kan tsaunin ka tsaya a can. Zan baka alluna na dutse da doka da dokokin da na rubuta, domin ka koya masu."13Sai Musa ya shirya, shi da mataimakinsa Yoshuwa suka hau tsaunin Yahweh.14Musa yace da dattawan, "Ku tsaya nan ku jira har sai mun dawo wurin ku. Haruna da Hor suna tare da ku. Idan wani yana da damuwa, ya je wurin su."15To sai Musa ya hau tsaunin, girgije ya rufe tsaunin.16Darajar Yahweh ta sauko a kan Tsaunin Sinai, girgije ya rufe shi har kwana shida. A rana ta bakwai ya kira Musa daga cikin girgijen.17Baiyanuwar darajar Yahweh ta yi kama da wuta mai ci a idanun Isra'ilawa a kan tsaunin.18Musa ya shiga cikin girgijen ya hau kan tsaunin. Yana can kan tsaunin har kwana arba'in da yini arba'in.
Waɗannan sunayen mutane maza ne. Duba yadda kuka juya waɗannan sunaye a 6:23.
dattawa 70 na Isra'ila
Wannan wata karin magana ne da ke nufin mutanen dukka sun amince. AT: "tare" ko kuma "da amincewa"
"gindin dutsen"
Musa ya karɓi rabin jinin a darurruka domin yă yafa su a bisa mutanen a 24:7. Wannan zai tabbatar da haɗa hunnun mutanen a ɗaukar alkawari tsakanin mutanen Isra'ila da kuma Allah.
A nan bagaɗin na wakilcin Allah. Wannan zai tabbatar da haɗa hunnun mutanen a ɗaukar alkawari tsakanin mutanen Isra'ila da kuma Allah.
AT: "Za mu yi biyayya da kome"
Wannan na nufin jinin da Musa ya zuba a kwanuka. AT: "Sai Musa ya ɗauki jinin da ke kwanukan"
Waɗannan sunayen mutane maza ne. Duba yadda kuka juya wannan a 6:23.
Wannan na maganar Allah ne kamar yana da tsawo irin ta mutum.
...
wurin tafiya ne mai ƙarfi sosai
Wannan karin magana ne. AT: "da sheƙi kamar sararin sama idan babu haɗari"
Wannan na nufin bai Allah bai yi masu lahani ba. AT: "Allah bai yi wa dattawan Isra'ila lahani ba"
Allah ya rubuta doka da dokoki a allunan dutse. AT: "allunan dutse biyu da na rubuta dukkan dokokin
"tare da Yoshuwa wanda ya taimake shi" ko kuma "tare da Yoshuwa wanda ya taimaka masa"
ku jira ni da Yoshuwa"
Hur abokin Musa da Haruna ne. Duba yadda kuka juya wannan a 17:8.
Wannan na nufin kwanyarsar hasken kasancewar Allah. AT: "Kwanyarsar hasken da ke nuna kasancewar Allah"
Wannan na nufin cewa ɗaukakar Yahweh yana nan babba kuma yana ci da haske kamar wuta. AT: "kamar babbar wuta da ke ci"
A nan "gabar" na nufin tunaninsu da kuma abinda suka gani. AT: "ga Isra'ilawa"
kwana 40 da yini 40"
1Yahweh yace da Musa,2"Ka ce da Isra'ilawa, duk mutumin da ya ji yana da niyya a zuciyarsa ya kawo mani baiko. Sai ka karɓi waɗannan baye-baye domi na.3Ga baye-bayen da za ka karɓa daga wurin su: zinariya, da azurfa, da tagulla;4da shuɗi, da shunayya, da jăn kaya; da leshe mai kyau; da gashin awaki;5da fatar rago da aka yiwa jan rini da fatar ragon ruwa; da itacen ƙirya;6da mai domin fitilu na haikali; da kayan yaji saboda mai na shafewa da turare mai ƙanshi da duwatsun7oniks da sauran duwatsu masu daraja da za a manna a alkyabba da ɗamara ta ƙirji.8Sai su yi mani haikali domin in zauna a cikin su.9Sai ka yi dai-dai yadda zan nuna maka tsarinsa da dukkan kayayyakinsa.10Za su yi akwati na itacen ƙirya. Ratarsa za ta zama kamu biyu da rabi; faɗinsa zai zama kamu ɗaya da rabi; tsayinsa zai zama kamu ɗaya da rabi.11Sai ka shafe shi da zinariya tsantsa ciki da waje, dole ka kewaye shi da rawanin zinariya a bisansa.12Sai ka yi ƙawanyu huɗu na zubi da zinariya domin sa, kasa su a ƙafafu huɗu na akwatin, da ƙawanyoyi biyu a ɗaya gefen.13Sai ka yi sanduna na itacen ƙirya ka shafe su da zinariya.14Sai kasa sandunan a cikin ƙawanyoyi na gefen akwatin alƙawarin, yadda za a iya ɗaukar sa.15Za a bar sandunan jikin akwatin; kada a cire su.16Sai ka sa ka'idodi na alƙawarin da zan baka a cikin akwatin.17Sai ka yi marfi na zinariya tsantsa. Ratarsa za ta zama kamu biyu da rabi, faɗinsa kuma kamu ɗaya da rabi.18Sai ka yi sifofi biyu na kerubim da gogaggiyar zinariya saboda gefe biyu na marfin kafara.19Ka yi kerub ɗaya saboda gefe ɗaya na marfin kafara, ɗaya kerub ɗin kuma saboda ɗaya gefen. Za ka yi su dai-dai kamar abu ɗaya da marfin kafara.20Fukafukan kerubobin su miƙe tsaye su yi sama su yiwa marfin kafara inuwa. Kerubobin su dubi juna su kalli tsakiyar marfin kafara.21Sai ka sa marfin kafara a kan akwatin, kuma kasa ka'idodi na alƙawari da zan ba ka a ciki.22A wurin akwatin ne zan sadu da kai. Zan yi magana da kai a inda nake a bisa marfin kafara. Zai zama daga tsakanin kerubobin biyu a bisa akwatin na shaida zan yi magana da kai game da dukkan ka'idodi da zan baka domin Isra'lawa.23Sai ka yi teburi na itacen ƙirya. Ratarsa za ta zama kamu biyu; faɗinsa kamu ɗaya, tsayinsa zai zama kamu ɗaya da rabi.24Sai ka shafe shi da zinariya tsantsa ka yi masa ado da dajiya ta zinariya a sama kewaye da shi.25Sai kayi dajiya ta kewaye shi mai faɗin tafin hannu ɗaya, ka kuma yiwa bakinsa ado da bugaggen zinariya.26Sai ka yi masa ƙawanyoyi na zinariya guda huɗu ka liƙa ƙawanyoyin a kusurwoyinsa huɗu, inda ƙafafun nan huɗu suke.27Sai ka liƙa ƙawanyoyin a wuri domin sandunan, yadda za a iya ɗaukar teburin.28Sai ka yi sandunan da itacen ƙirya ka shafe su da zinariya domin a iya ɗaukar teburin tare da su.29Sai ka yi tasoshinsa da cokulansa da butocinsa da akusoshinsa domin zuba baye-baye na sha. Sai ka yi su da zinariya zalla.30Za ka riƙa ɗora gurasa ta kasancewa a bisa teburin a gabana.31Sai ka yi wurin ɗora fitila da gogaggiyar zinariya. Wurin ɗora fitilar za kayi da wurin zamansa. Kofinansa da leɓunansa da furanninsa za kayi su tare kamar abu ɗaya.32Rassa shida za su fito daga gefunansa-rassa uku daga gefe ɗaya, rassa uku kuma na wurin ɗora fitilar su zarce a ɗaya gefen.33Reshe na farko zai zama da kofuna uku kamar an yi su da lingaɓin itacen almond, da baki mai kamar ganye da fure, kofuna uku kuma an yi su kamar lingaɓin itacen almond a ɗaya reshen, da baki kamar ganye da fure. Dukkan su shida za su zama dai-dai da juna, su zarce daga abin ɗora fitilar.34A kan abin ɗora fitilar kansa, a tsakiyarsa, zai kasance da kofuna huɗu masu kama da lingaɓin itacen almond, da kamannin ganye da furanni.35Tagwayen rassa biyu na farko za su zama da baki kamar ganye-an yi su tare kamar abu ɗaya, tagwayen rassa na biyu kuma an yi su da kamar ganye abu ɗaya tare. Haka kuma tagwayen rassa na uku za a yi su da kamannin ganye sai ka ce abu ɗaya. Haka dukkan rassan shida za su zama su zarce wurin ɗora fitilar.36Bakunansu masu kama da ganye za su zama abu ɗaya, an yi shi da bugaggiyen aikin curin zinariya tsantsa.37Za ka yi abin ɗora fitilar da fitulunsa guda bakwai, kasa fitilun a bisansa domin su bada haske daga wurinsa.38Hantsukan da tasoshin a yi su da zinariya tsantsa.39A yi amfani da awo ɗaya na zinariya a yi wurin ɗora fitilar da kayayyakinsa.40Ka tabbata ka yi su kamar yadda aka nuna maka a kan tsaunin.
Wannan wata karin magana ne da ke nuna alamar marmarin mutum ya yi bayaswa. AT: "mutumin da yake son yayi bayaswa"
Kalmar nan "ku" na nufin Musa da shigabannin.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa shari'unsa ga mutanen Isra'ila.
Wannan na iya nufin 1) kaya da aka yi masa rina shuɗi, da shunayya, da jă," mai yiwuwa zaren ulu ko kuma 2) da shuɗi, da shunayya, da jăn rini" a yi rinin lilin.
...
wani babbar dabba da ke zama a ruwa yana cin shuke shuke
basheshun shuke shuke da akan niƙa zuwa gari sai a sa a mai ko abinci domin ba da kanshi mai kyau.
wani dutse ne mai daraja da ke da yadudduka fari da baki, ja ko launin ruwan kasa.
AT: "duwatsu masu daraja da wani zai shirya"
...
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
A nan waɗannan kamomi na da ma'ana ɗaya.
A nan "ka" na nufin Musa da Jama'ar Isra'ila.
A nan "ka" na nufin Musa kenan,
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
"kuma 2.5 ... kamu 1.5
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Ƙawayoyi wata hanya ce na narkar da zinariya, da aka zuba ta a wani abu mai kamanin zobe aka bar ta ta kama.
"domin ku iya ɗaukar akwatin alkawarin"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Wannan wat murfi ne da ke bisa akwatin alkawarin, a wurin da ake tsantsa.
"kamu 2.5 ... kamu 1.5"
...
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Wannan wat murfi ne da ke bisa akwatin alkawarin, a wurin da ake tsantsa. Duba yadda kuka juya wannan a 25:15.
AT: "Dole sa su"
A nan "ka" na nufin Musa da Mutanen Isra'ila ne.
Yawheh ya cigaba da wa Musa magana.
""Zan same ka a wurin akwatin." A 25:22 kalmar nan "ka" na nufin Musa ne.
Wannan wat murfi ne da ke bisa akwatin alkawarin, a wurin da ake tsantsa. Duba yadda kuka juya wannan a 25:15
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
"kamu 2 ... kamu 1 ... kamu 1.5"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
aunin santimita 7 zuwa 8
"wa taburin ado"
...
...
"don ku iya ɗaukar"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
AT: "Domin ku ɗauki taberun tare da su"
AT: "Domin ku yi amfani da su ku zuba baye-bayen sha"
"Gurasar na wakilcin kansacewar Allah.
... Duba yadda kuka juya wannan a 25:15.
AT: "Za ka yi wurin ɗora fitilan"
AT: "Ka sa kofinansa, leɓunansa, da furanninsa dukka kamar abu ɗaya"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi. Yahweh yana yin bayani ne game da maɗorin fitilan. (Dubi: 25:31).
fure mai kala fari ko ruwan hoda da ke da kunnen fure
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi. Yahweh yana yi bayani ne game da maɗorin fitilan. (Dubi: 25:31)
AT: "Sa ka yi su da kamanin ganye ɗaya sai kace abu ɗaya ne da maɗorin fitilan"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
"domin su haska daga wurinsa"
AT: "Ka yi hantsykan da tasoshin da zinariya tsantsa"
Awo ɗaya yana da nauyi kimamun kilo 34
hantsukan da tasoshin da su tire
AT: "Nake nuna maka a bisa dutsen"
1Rumfar taruwa kuma za ka yi ta da labule goma da aka yi su da lilin mai kyau da shuɗi da shunayya da jan ulu mai zanen cerubim. Wanda gwanin mai aikin hannu ya yi.2Tsawon kowanne labule zai zama kamu ashirin da takwas, faɗi kuma kamu huɗu. Labulen dukkan su su kasance girmansu ɗaya.3Labule biyar su zama haɗe da juna, sauran biyar kuma su zama haɗe da juna.4Kashi ɗaya na labulen za ka yi masa abin ratayewa na shuɗi daga ƙarshensa. Kashi na biyu ma haka za ka yi masu daga ƙarshe.5Kashi na farko za ka yi masu wurin ratayewa hamsin, kashi na biyu ma za ka yi masu wurin ratayewa hamsin. Ka yi haka domin wurin ratayewar labulen su dubi junansu.6Sai ka yi kayan adon labule na zinariya guda hamsin ka haɗa labulen tare da juna domin rumfar sujadar ta zama a haɗe.7Za ka yi labule na gashin awaki domin rumfa ta bisan rumfar sujada. Za ka yi labule guda goma sha ɗaya.8Tsawon kowanne labule zai zama kamu talatin, faɗin kowanne labule kuma kamu huɗu. Labulen nan goma sha ɗaya girmansu ya zama ɗaya.9Labule biyar sai ka haɗa su da juna sauran shida kuma ka haɗa su da juna. Sai ka gwama labule na shida wanda yake a gaban rumfar.10Sai ka yi maratayi hamsin a gefen labule jeri na farko, maratayi hamsin kuma a gefen labulen da ya haɗa jeri na biyu.11Sai ka yi abin maƙalawa hamsin na tagulla ka sa su a maratayin. Sa'an nan ka haɗa rumfar tare ta zama abu ɗaya.12Rabin labulen da ya rage, wato wanda ya zarce ya ragu daga labulen rumfar, sai ka bar shi yana lilo a bayan rumfar sujada.13Zai zama kamu ɗaya na labulen a gefe ɗaya, kamu ɗaya kuma na labulen a ɗaya gafen-wato abin da ya ragu na labulen rumfar a bar shi ya na lilo a gefen rumfar sujada a sashi ɗaya domin ya rufe ta.14Sai ka yi wa rumfar sujadar abin rufewa da fatun rago waɗanda a ka jeme mai rinin jă, wani marfin kuma na fata mai kyau ka sa ya rufe wannan.15Sai ka yi wa rumfar sujadar diraku na itacen ƙirya a kafa su a tsaye.16Ratar kowacce dirka zai zama kamu goma, faɗin ta kuma kamu ɗaya da rabi.17Sai a yi wa dirakun turaka biyu na katako domin su haɗa su da juna. Haka za ka yi dukkan dirakun rumfar sujada.18Sa'ad da ka yi dirakun rumfar sujadar, sai ka yi guda ashirin saboda sashi na kudu.19Sai ka yi darurruka arba'in na azurfa a ƙarƙashin dirakun nan ashirin. Darurruka biyu za su zama matashin dirka ta farko, darurruka biyu kuma za su zama matashin dirakun guda biyu.20Sashi na biyu na rumfar sujada, wato daga arewa, za ka yi masa diraku ashirin21da darurrukansu guda arba'in na azurfa. Dirka ta farko za ta kasance da darurruka biyu, biyu kuma a ta gaba, har a gama su dukka.22Bayan rumfar sujada kuma daga sashin yamma, sai ka yi ma sa diraku shida.23Sai ka yi diraku biyu saboda kusurwar rumfar sujada ta baya.24Waɗannan dirakun ba za a haɗa su daga ƙasa ba, amma daga sama za a haɗa su da ƙawanya ɗaya. Haka kusurwoyi biyu na baya za su zama.25Za su zama diraku takwas, tare da darurrukansu na azurfa. Za a sami darurruka goma sha shida, darurruka biyu a ƙarƙashin dirka ta farko, darurruka biyu kuma a ta gaba, har a gama.26Dole ka shirya katakai da zasu gitta da itacen ƙirya-biyar saboda sashi ɗaya na dirakun rumfar sujada,27katakai biyar na gittawa kuma saboda ɗaya sashin na dirakun rumfar sujada, katakai biyar na gittawa kuma saboda dirakun sashin rumfar sujada na baya wajan yamma.28Katakon da yake tsakiyar dirakun, zai kai daga wannan ƙarshe zuwa wancan ƙarshen.29Sai ka shafe dirakun da zinariya. Za kuma ka yi zobbansu da zinariya, domin su riƙe katakan da aka gitta, na gittawar ma za ka shafe su da zinariya.30Dole ka tsara rumfar sujada ta wurin bin yadda aka nuna maka a kan tsaunin.31Sai ka kayi labule na shuɗi, da shunayya, da jan ulu, da leshe mai kyau da zanen kerubim, wanda ƙwararren mai aikin hannu zai yi.32Sai dole ka rataye shi a kan ginshiƙai na itacen ƙirya shafaffu da zinariya. Waɗannan ginshiƙai za a yi ma su ƙugiyoyi na zinariya a kan darurruka huɗu na azurfa.33Sai kuma dole ka sa labulen a wurin ratayewarsa, sai kuma ka kawo akwatin a ciki. Labulen zai raba tsakanin wuri mai tsarki da wuri mafi tsarki.34Sai kasa marfi na kafara a bisa akwatin shaida, wanda yake a cikin wuri mafi tsarki. Sai kasa teburin a waje daga labulen.35Sai kasa wurin ɗora fitilar ya dubi teburin daga sashin kudu na rumfar sujada. Teburin ya kasance daga sashin arewa.36Sai kuma dole ka yi maratayi a ƙofar shiga rumfar. Sai kuma dole ka yi shi da shuɗi, da shunayya, da jan ƙyalle, da leshe mai kyau, murɗaɗɗe wanda mai iya zane a kan tufa ya yi.37Wurin ratayewar za ka yi masa ginshiƙai biyar na ƙirya shafaffu da zinariya. Ƙugiyoyinsu su zama na zinariya, ka yi darurruka biyar na zubi da tagulla.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi. (Dubi: 25:1)
Yahweh yana magana da Musa ne. Yana iya yiwuwa Yahweh yana gaya wa Musa wannan ne domin ya faɗa wa ainihin wanda zai yi aikin, amma hakin Musa shi ne ya tabbatar cewa an yi aikin yadda ya kamata. "Ka wa ma'aikacin yă yi"
...
ulu da aka rina ta ja wur
mutumin da ya gwaninta a sana'ar sa na kera abubuwa da kyau.
"kamu 28 ... kamu 4." Kamu 46 yana da sentimeter 46 ne.
AT: "A ɗinka labule biyar a wuri ɗaya domin su zama kashe ɗaya. sa'annan a ɗinka sauran labule biyar ɗin ma tare a sake yin wani kashi"
Abin ratayewan yana haɗe ne daidai da adon da ke riƙe labulen tare.
"kashi ɗaya na labule biyar"
"kashi ta biyu na labule biyar"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
"11 ... 30 ... 4"
Kamu shi ne sentimeta 46.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Abin ratayewan yana haɗe ne daidai da adon da ke riƙe labulen tare. Duba yadda kuka juya wannan a 26:4.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Kamu ɗaya yana da santimita 46.
"launi"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Wannan na nufin rumfa ko bangarori da suka yi ta wurin haɗa 'yan kananan katakai.
"kamu 10 ... kamu 1.5"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Waɗannan wasu tabulan azurfa ne da ke da rami a cikinsu domin su tsare katakon.
Dirakun azurfan ne ya raɓa katakon da kasa.
"Ku saka daruruka biyu"
Wannan na nufin cewa an yi da sauran katakan dukka yadda aka yi da katakai biyu na fari. AT: "da daruruka biyun wa dukka sauran katakan"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
AT: "A raɓa waɗannan dirakun a kasa, amma a haɗa su a sama"
Waɗannan wasu tabulan azurfa ne da ke da rami a cikinsu domin su tsare katakon.Duba yadda kuka juya shi a 26:19.
"jimila"
Wannan na nufin cewa an yi da sauran katakan dukka yadda aka yi da katakai biyu na fari. AT: "da daruruka biyun wa dukka sauran katakan"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Katakan suna ba ginin zama da kyau.
Gaban rumfar sujada da ke fuskantar gabas.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
"wanda za su riƙe katakan da aka gitta" ko kuma "saboda za su rike katakan da aka gitta"
Katakan suna ba ginin zama da kyau. Duba yadda kuka juya shi a 26:26.
AT: "da na nuna maka an nan kan dutse"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa yadda za a kera alfarwar.
Yahweh yana yana magana da Musa. Yana iya yiwuwa cewa Yahweh yana son Musa ya gaya wa ainihin wanda zai yi aikin, amma Musa ne ke da hakin tabbatar cewa ain yi aikin daidai. AT: "Ka ce wa mai aikin hannu ya yi." Duba yadda kuk juya shi a 26:1.
Wato wurin ratayar labulen. Duba yadda kuka juya wannan a 26:4.
Akwatin shaidar shi ne akwatin da ke ɗauke da dokokin. AT: "sai ka kawo akwatin da ke ɗauke da dokokin"
AT: "Labulem za raɓa wuri mai tsarkin"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda za su yi.
Wannan wat murfi ne da ke bisa akwatin alkawarin, a wurin da ake tsantsa. Duba yadda kuk juya shi a 25:15.
"a bisa akwatin da ke ɗauke da dokokin"
Wannan shi ne teburin da ke riƙe da gurasar da ke wakilcen kasancewar Allah. AT: "Ka sa teburin gurasar kasancewar Allah a sashin arewa"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa yadda za a kera alfarwar.
wato labule
Wannan na iya nufin 1) kaya da aka yi masa rina shuɗi, da shunayya, da jă," mai yiwuwa zaren ulu ko kuma 2) da shuɗi, da shunayya, da jăn rini" a yi rinin lilin. Duba yadda kuka juya shi a 25:3.
da leshi da aka sassaƙa da kyau."
"mai iya ɗinki da zane a kan kaya"
1Sai ka yi bagadi na itacen ƙirya, ratarsa kamu biyar faɗinsa ma kamu biyar. Bagadin zai kasance kamu dai-dai kowanne gefe da tsawonsa kamu uku.2Za ka sa kusurwoyinsa su zarce da kamannin ƙahonin bijimi. Bagadin da ƙahonin za su zama tare kamar abu ɗaya, zaka shafe su da tagulla.3Za ka yi kayan aiki domin bagadin: wato tukunya saboda zuba toka da kuma cebur da darori da cokulan tsamo nama da kasake na tuya. Dukkan waɗannan kayan aikin za kayi su da tagulla.4Za ka yiwa bagadin makari na tagulla da răgă. Za ka yi zobba na tagulla guda huɗu domin kowacce kusurwa.5Za ka sa makarin ƙasa da bagadin, ya kai rabin sa daga ƙasa.6Za ka yiwa bagadin sanduna na itacen ƙirya, ka shafe su da tagulla.7Sandunan za ka sa su shiga cikin zobban, a sassa biyu na bagadin, domin a iya ɗaukar sa.8Za kayi bagadin ba kome a cikinsa, da katakai. Za kayi shi kamar yadda a ka nuna maka a kan tsaunin.9Za ka yi wa rumfar sujada haraba. Za a yi wuraren rataye-rataye a harabar a sashin kudu, ragayu na leshe mai kyau saƙaƙƙe mai ratar kamu ɗari.10Za ka yi diraku ashirin domin ragayun, da darori ashirin na tagulla. Za a yi ƙugiyoyi liƙe da dirakun da sanduna na azurfa.11Haka kuma a sashin arewa, za ka yi ragayu guda ɗari tare da diraku ashirin da darori ashirin na tagulla da ƙugiyoyi liƙe da dirakun da sandunan azurfa.12A sashin yamma na harabar za ka yi labule kamu hamsin. Za ka yi diraku goma da darori goma.13Haraba za ta zama kamu hamsin daga sashin gabas.14Ragayoyi na wurin shiga ratarsa za su zama kamu hamsin. Za su zama da diraku uku da darori uku.15Ɗaya sashin ma zai zama da ragayu kamu goma sha biyar. Da dirakunsu uku da darorinsu uku.16Ƙofar shigowa harabar za ta zama da labule mai ratar kamu ashirin. Za a yi labulen da shuɗi da shunaiya da jăn ƙyalle da saƙaƙƙen leshe mai kyau, wanda ƙwararren mai aikin hannu ya yi. Zai zama da diraku huɗu da darori huɗu.17Dukkan dirakun harabar za su zama da sandunan azurfa da ƙugiyoyin azurfa da darorin tagulla.18Ratar harabar za ta zama kamu ɗari, da faɗin kamu hamsin da tsawon kamu biyar da ragaya ta saƙaƙƙen leshe mai kyau da darori na tagulla.19Dukkan kayan aikin rumfar sujada, da abubuwan kamawar na harabar za a yi su da tagulla.20Za ka umurci mutanen Isra'ila su kawo man zaitun, mai tsabta, domin fitilun su yi ta ci ba fasawa.21A rumfa ta taruwa, bayan labulen rumfar sujada inda akwatin shaida ya ke, Haruna da 'ya'yansa za su sa fitilun suyi ta ci tun daga yamma har zuwa safiya a gaban Yahweh. Mutanen Isra'ila za su lura da wannan ka'idar a dukkan zamanu.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi. (Dubi: EXO 25:1)
"tsawon meta 2.2 a kowane gefe"
"Bagadin zai kasance gefe da kumu 1.3 a tsayi"
Kamu guda yana da santimeta 46.
"Za ku sa tsinkaya su yi kamar ƙahohin bijimi a dukka gefe huɗu"
"Za ku sa ƙahohin"
"za ku shafe bagaden da ƙahohin"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
"darori"
Wannan wasu farati ne da ke rike gawayi mai zafi daga bagadin.
wasu kayan aiki masu amfani.
...
wani firam da ke riƙe da katakon yayin da yake wutan ke ci
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Ana sa wannan makarin a cikin bagadin. AT: "Za ka saka makarin a ragar bagadin, a cikin bagadin"
wani firma da ke riƙe da katakon yayin da yake wutan ke ci. Duba yadda kuka juya wannan a 27:3.
Sandunan ne za su taimaka a ɗaukan bagaadin. AT: "Za ka yi sanduna na itance domin ɗaukar bagadin"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
...
...
AT: "Da na nuna maka a kan wannan dutse"
...
... Duba yadda kuka juya wannan a 26:36.
an saƙa su ne domin su yi ƙarfi.
"mita 44"
AT: "Za ka haɗa kugiyoyi ... dirakun"
Wani katako mai ƙarfi da ke tokarewa.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Ga 27:11, duba yadda kuka juya irin wannan kalamun a 27:9.
Ana iya juya wannan a matsayin umarni.
Ana iya juywa wannan a matsayin umarni.
Ana iya jua wannan a matsayin umarni.
Ana iya juya wannan a matsayin umarni.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi
Wato was manyan labule ne da aka yi su da Yaduna. Duba yadda kuka juy irin wannan a 26:36.
Wani katako mai ƙarfi da ke tokarewa. Duba yadda kuka juya wannan a 27:9.
... Duba yadda kuka juya wannan a 26:19.
kimamun mita bakwai
Ana iya juya wannan a matasyin umarni.
AT: "Ƙwrarren mai aikin hannu ne zai yi wannan labulen ... saƙaƙƙen leshe mai kyau"
...
mutum mai ɗinkida zane-zane a kan kaya
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
"kamu 100." Kamu ɗaya yana da santimita 46.
An saƙa su ne domin su yi ƙarfi. Duba yadda kuka juya wannan a 26:36.
AT: "sa'annan a yi duk abubuwan kamawar alfarwar da kuma harabar daga tagulla"
wasu abubuwane da ake yin su ko da katako ko karafuna da sinin baki domin a kama gefe-gefen buka a kasa.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Wannan wani suna ne na alfarwa.
Wannan yana ɗauke ne da duwatsu ne wanda Yahweh ya rubuta dokoki goma a bisa su.
"Ina son mutane su riƙa yin haka har dukkan zamanai"
1Ka kira Haruna ɗan'uwanka da 'ya'yansa maza- wato, Nadab, da Abihu, da Eliyeza, da Itama - daga cikin Isra'ilawa domin su yi mani hidima a matsayin firistoci.2Ka yi wa Haruna, ɗan'uwanka rigunan keɓaɓɓu gare ni. Waɗannan riguna za su zama domin ya fita da kyau da kwarjini.3Ka yi magana da mutane masu hikima a zuciya, waɗanda na cika su da ruhun hikima, domin su yi wa Haruna riguna a keɓe shi domin ya yi mani hidima a matsayin firist.4Rigunan da za suyi su ne, ɗamara ta sawa a ƙirji da alkyabba, da taguwa, da riga mai aiki, da rawani, da ɗamara. Za su yi waɗannan tufafi keɓaɓɓu gare ni. Za su zama saboda Haruna ɗan'uwanka da 'ya'yansa domin su yi mani hidima a matsayin firistoci.5Ma su aikin hannu za su yi amfani da leshe mai kyau mai launin zinariya, da shuɗi, da shunayya, da jã.6Sai su yi alkyabba da launin zinari, da shuɗi, da shunayya, da jan ulu, da leshe mai kyau mai aiki. gwani ne zai yi aikin.7A kusurwoyi biyu za ta kasance da ƙyallayen da za'a sa a kafaɗa.8A yi mata saƙa mai kyau ɗamarar ta zama kamar alkyabbar; kuma a yi su tare da falmarar, ayi su da leshe mai kyau mai aiki da launin zinari da shuɗi da shunaiya da ja.9Ka ɗauki duwatsu biyu na oniks ka rubuta sunayen 'ya'yan Isra'ila goma sha biyu.10Sunaye shida a kan dutsen ɗaya, sauran shidan kuma a kan ɗaya dutsen, bisa ga yadda aka haife su.11Mai iya rubutu a kan dutse ne zai yi rubutun kamar yadda ake rubuta hatimi, ka rubuta sunayen 'ya'yan Isra'ila goma sha biyu a kan duwatsun guda biyu. Ka ɗora duwatsun a kan kasko na zinariya.12Za ka ɗora duwatsun biyu a ƙyallen kafaɗa na falmara, su zama duwatsun tuna wa Yahweh da 'ya'yan Isra'ila. Haruna zai ɗauki sunayensu a gaban Yahweh bisa kafaɗunsa biyu su zama abin tunawa a gare shi.13Sai kayi kasake na zinariya14za kayi sarƙoƙi biyu na zinariya kamar tsarkiyoyi, ka liƙa sarƙoƙin a jikin kasaken.15Za ka yi ƙyalle na ƙirji domin yin shawara, ka sami gwani ya tsara shi kamar alkyabba. A yi shi na zinariya, da shuɗi, da shunayya, da jan ulu, da linin mai kyau.16Ya zama murabi'i. Ƙyallen na ƙirji za ka sa shi riɓi biyu. Ratarsa za ta zama taki ɗaya faɗinsa ma taki ɗaya.17Ka yi jere huɗu na duwatsu masu daraja a jikinsa. Dole jeri na farko a sa rubi, da tofez, da kuma ganet..18A jeri na biyu kuma dole a sa emerald, da saffiya, da lu'u-lu'u.19Jeri na uku kuma dole kasa yasint, da agat, da kuma ametis.20Jeri na huɗu za ka sa beril da oniks, da yasfa. A sa su a kan kasaken zinariya.21Za a jera duwatsun bisa ga sunayen 'ya'yan Isra'ila goma sha biyu, bi da bi a jere. A zana su kamar yadda a ke yin hatimi da zobe, kowanne suna ya zama a madadin kabilu goma sha biyu.22Ƙyalle na ƙirjin ya zama sarƙa kamar tsarkiya, saƙaƙƙe na zinariya tsantsa.23Za ka yi wa ƙyallen zobba biyu liƙe da juna a kusurwoyinsa biyu.24Ka liƙa sarƙoƙin nan biyu a jikin ƙyalle na ƙirji.25Za ka liƙa ƙarshen sarƙoƙin nan biyu a jikin kasaken. Sa'an nan ka liƙa su a jikin ƙyallen kafaɗa na falmara a gaba.26Za ka yi zobba na zinariya guda biyu, ka sa su a ɗaya gefe na ƙyallen na ƙirjin, a ƙarshen kalmasa ta ciki kusa da haɓar.27Dole zaka yi waɗansu zobba na zinariya guda biyu, ka liƙa su jikin ƙyalle na kafaɗar falmara daga ƙasa, a bisa ɗamarar nan ta kyakkawan leshe na falmarar.28Su haɗa ƙyallen nan na ƙirji da zobban falmarar nan masu launin shuɗi, domin su haɗu saƙaƙƙiyar ɗamarar nan ta falmarar. Domin kada ƙyallen na ƙirji ya zama a ware da falmarar.29Sa'ad da Haruna yake shiga cikin wuri mai tsarki, zai ɗauki sunayen mutanen Isra'ila a bisa zuciyarsa cikin ƙyallen nan na ƙirji domin ɗaukar shawara, za ayi ta yin haka domin ya zama abin tunawa a gaban Yahweh.30Zaka sa Urim da Tummim a cikin ƙyalle na ƙirjin domin ɗaukar shawara, domin su zama a bisa zuciyar Haruna sa'ad da yake shiga gaban Yahweh. Ta haka Haruna zai riƙa ɗaukar abin ɗaukar shawara domin mutanen Isra'ila bisa zuciyaarsa a gaban Yahweh.31Rigar wato falmara zaka yi ta duka da shuɗi.32Za a yi mata wurin sa kai a tsakiya. Dole ayi wa wurin sa kai ɗin saƙa domin kada ya yage. Dole a sami mai saƙa ya yi aikin.33Za ka yi wa haɓar rigar, ado na 'yan tutoci da shuɗi, da shunayya, da jan ulu ya kewaye dukka.34Ka yi ƙararrawa ta zinariya ta zagaya dukka a tsakanin tutocin. A sa ƙararrawa ta zinariya da tuta, sai kuma ƙararrawa ta zinariya sai kuma tuta - da sauransu - kewaye tufar dukkan ta.35Haruna zai sa wannan tufar sa'ad da zai yi hidima, domin a iya jin ƙararta sa'ad da yake shiga wuri mai tsarki gaban Yahweh da sa'ad da yake fita. Wannan domin kada ya mutu ne.36Dole ka yi faranti na zinariya ka yi zane a kan sa, kamar zanen hatimi, "Tsarki ga Yahweh."37Za ka liƙa wannan farantin da shuɗiyar iggiya a jikin rawanin.38Haruna zai sa shi a kansa; zai ɗauki laifi da ake yi game da baye-baye masu tsarki na Isra'ilawa waɗanda aka keɓe domin Yahweh. Dole rawanin ya kasance a kansa domin Yahweh ya karɓi baye- bayensu.39Dole ka yi alkyabba da linin mai kyau, da rawani na linin mai kyau. Kuma zaka sa mai zane ya yi masa ado.40Zaka yi riguna saboda 'ya'yan Haruna, da ɗammaru, da abin ɗaurawa a kansu saboda daraja da kwarjini.41Dole ka suturta Haruna ɗan'uwanka, da 'ya'yansa. Dole ka shafe su, ka naɗa su, ka keɓe su domi na, domin su yi mani hidima a matsayin firistoci.42Dole ka yi masu wuyan wanduna na sawa a ciki domin su rufe tsiraicin jikinsu, ya rufe su daga kwankwaso zuwa cinya.43Haruna da 'ya'yansa za su riƙa sa waɗannan tufafi sa'ad da suke shiga wurin taruwa da sa'ad da suke fuskantar bagadi su yi hidima a wuri mai tsarki. Dole su yi haka domin kada su zama da kuskure in ba haka ba za su mutu. Wannan zaunanniyar doka ce domin Haruna da zuriyarsa a bayansa.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi. (Duba: 25:1)
A nan "ka" na nufin Musa.
Waɗannan dukka sunayen maza ne.
A nan "ka" na nufin mutanen.
AT: "riguna da za ka keɓe mani"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
"wani riga da aka saka da zane-zane har cikinta"
Wannan wani marufin kai ne da aka sakawa sai saka a kai .
Wannan kuma wani kaya ne da mutane ke ɗaura a kwankwason su or kuma a kewaye da kirjinsu.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
... Duba yadda kuka juya wannan a 26:36.
Mutumin da ka yin abubuwa masu kyau da hannuwansa.
...
Waɗannan wasu duwatsu ne masu amfani kwarai kuma suna da zane-zane na fari da baki, ko kuma jah ko launin ruwan kasa a ciki. Duba yadda kuka juya wannan a 25:3.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
"Kamar yadda mutum ke rubutu a hatimi"
Mutumin da ke iya zane-zane a bisa abu mai ƙarfi kamar su katako, dutse, ko ƙarfe.
dutse da aka zana ana kuma amfani da shi a matasyin hatimi.
...
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
... Duba yaddak kuka juya shi a 28:10.
...
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
"Mai aikin da ya gwaninta zai tsara shi kamar alkyabba"
Faɗi ɗaya santimita 22 ne.
Launin da aka yi amafani da su anan na iya banbantawa da waɗanda ke a cikin UDB.
Duba yadda kuka juya shi a 25:3.
Waɗannan ma dudwatsu masu daraja ne.
Wannan wani dutse mai daraja ne da ke da launin shuɗe. Duba yadda kuka juya shi a 24:9.
wani dutse ne mai daraja da ke da yadudduka fari da baki, ja ko launin ruwan kasa. Duba yadda kuka juya shi a 25:3.
AT: "Ku saka su akan kasaken zinariya"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
AT: "Zaku jera duwatsun"
A nan, an saka dutsen ne akan zoben. Duba yadda kuka juya wannan "hatimi" a 28:10.
"Ana yin sarƙa da tsantsa zinariya ne sa'annan a saƙa su zuwa igiya." (Duba yadda kuka juya irin wannan jimlar a 28:13.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
"sarƙokin da aka tsaika." Duba yadda kuka juya wannan a 28:13.
Akwai kasake biyu da suka ƙulla duwatsun. AT: "kasake biyun da suka ƙulla duwatsun"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Duba yadda kuka juya wannan a 28:6.
AT: "Domin ku haɗa shi"
AT: "ƙyallen na kirjin zai haɗu da alkyabba"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Wannan na nufin sunayen kabilun da aka sassaƙa a bisa duwatsu goma sha biyun yadda aka bayana a 28:17.
"a bisa zuciyar Haruna" ko kuma "a bisa kirjin Haruna"
Kaman jimla na biyun na bayana amfanin Urim da Tummim ne.
Ba haske ko menene waɗannan. Wasu abubuwa ne dai, mai yiwuwa duwatsu, da Firist ke mafani da su domin dai iya sanin nufin Allah.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Ana iya sanar da wannan a matsayin umarni. AT: "Mai saƙa ne lallai ake buƙata yayi wannan aikin"
"mutumin da ke yin tufafi da ulu"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Tuta wani 'yan itace ne mai jan launi.
An maimaita wannan jimlar ne domin a nuna irin zanen da za'a yi a bisa tufafin.
AT: "Lallai ne Haruna yă saka wannan tufafi sa'ada yake hidima"
AT: "domin kararrawar su yi kara"
Ana iya ɗaukan cewa zai mutu ne domin bai yi wa Yahweh biyayya ba. AT: "Don haka, zai iya mutuwa saboda rashin biyayya da umarnina"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
"Ka yi rubuta a kan sa kamar yadda mutum ke iya rubuta a kan hatimi." Duba yadda kuka juya irin waɗannan kalamun a 28:10.
Wannan wani marufin kai ne da aka sakawa sai saka a kai . Duba yaddaa kuka juya wannan na 28:4.
...
AT: "Dole ne Haruna yă riƙa sa rawanin a kansa"
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Wannan wani marufin kai ne da aka sakawa sai saka a kai . Duba yaddaa kuka juya wannan na 28:4.
Duba yadda kuka juya wannan a 28:4.
Mutum mai ɗinki da zane-zane a kan kaya. Duba yadda kuka juya wannan a 26:36.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Duba yadda kuka juya wannan a 28:4.
...
Haruna yaya ne ga Musa. AT: "Ka saka wa yayanka Haruna waɗannan tufafan
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
...
Wannan wata suna ce na alfarwa. Duba yadda aka juya wannan a 27:20.
"doka ce da ba ta da ƙarshe"
1Ga abin da za ka yi domin ka keɓe su yadda za su iya yi mani hidima a matsayin firistoci. Ka ɗauki ɗan bijimi da raguna biyu marasa cikas da,2gurasa marar gami, da waina marar gami gauraye da mai. Ka kuma ɗauki wainar alkama marar gami ka shafe da mai. wadda aka yi da kyakkyawar alkama. Wadda ake ci da zuma.3Dole ka sa su a cikin kwando ɗaya, ka kawo su a cikin kwandon, ka miƙa su tare da bijimin da ragunan nan biyu.4Dole ne ka miƙa Haruna da 'ya'yansa a ƙofar shiga rumfar ta taruwa. Za ka yi wa Haruna da 'ya'yansa wanka da ruwa.5Dole ka ɗauki rigunan da alkyabba ka sa wa Haruna da maratayin falmara da falmara da ƙyalle na ƙirjin da ɗamara ta leshe mai kyau tare da falmara ka yafa masa.6Ka naɗa rawanin a kansa da kambi na tsarki a bisa rawanin.7Sa'an nan ka ɗauki mai na shafewa ka zuba a kansa, da haka za ka shafe shi.8Dole ka kawo 'ya'yansa su ma ka sa masu alkyabbobi.9Za ka sa wa Haruna da 'ya'yansa ɗammaru da ƙyalle na ado a kansu. Aikin firist zai zama nasu kullum bisa ga doka. Ta haka za ka tsarkake Haruna da 'ya'yansa domin su yi mani hidima.10Dole dukkan ku za ku kawo bijimin a wurin rumfa ta taruwa, Haruna da 'ya'yansa za su sa hannayensu a kan bijimin.11Zaka yanka bijimin a ƙofar rumfar ta taruwa a gaban Yahweh.12Dole ka ɗauki jinin bijimin da yatsarka ka sa a kan ƙahon bagadin, sai ka ɗauki sauran jinin ka zubar da shi a dakalin bagadin.13Dole ka ɗauki kitse na marfin ciki da wanda ya lulluɓe hantar da ƙodojin biyu da kitsen da yake kansu; ka ƙona a kan bagadin.14Amma naman bijimin da fatarsa da sauran abin da ya rage jikinsa, dole ka ƙone su a waje. Za ya zama baiko na zunubi.15Dole ka kuma ɗauki rago ɗaya, Haruna da 'ya'yansa su ɗora hannuwansu a kansa.16Dole ka yanka ragon, ka yayyafa jininsa a kowanne sashi na bagadin.17Dole ka yanka ragon gunduwa--gunduwa da ƙafafunsa, ka sa 'yancikinsa tare da gunduwoyin tare da kansa,18a bisa bagadin. Sa'an nan ka ƙone ragon dukkan sa. Zai zama baiko na ƙonawa ga Yahweh, baiko mai daɗin ƙanshi wanda aka yi domin Yahweh.19Sa'an nan dole ka ɗauki ɗaya ragon, Haruna da 'ya'yansa su ɗora hannuwansu a kansa.20Sa'an nan dole ka yanka ragon ka ɗauki jininsa. Ka sa shi a bisa kunnen Haruna na dama, da bisa kan kunnuwan 'ya'yansa na dama, da kan babban yatsansu na dama, da babban yatsan kowannen su na dama na ƙafa. Sa'an nan ka yayyafa jinin a jikin bagadin a kowanne sashe.21Dole ka ɗauka daga jinin da yake kan bagadi da mai na shafewa, ka yayyafa a kan Haruna da tufafinsa, da kuma kan 'ya'yansa da tufafinsu. Sa'an nan Haruna zai zama keɓaɓɓe domi na, da kuma tufafinsa da 'ya'yansa da tufafinsu tare da shi.22Dole ka ɗauki kitsen ragon da kitsen bindin da kitsen da ya rufe kayan cikin da wanda ya lulluɓe hantar, da ƙodojin biyu da kitsen dake kansu, da cinyar dama-wannan ragon na keɓewar firistoci ne a gare ni.23Ka ɗauki dunƙule ɗaya na gurasa da wainar da aka yi da mai, guda ɗaya da wainar alkama ɗaya daga cikin kwandon wadda bata da gami wadda ke gaban Yahweh.24Dole ka sa waɗannan a cikin hannuwan Haruna da hannuwan 'ya'yansa ka ɗaga su a gabana domin baiko na ɗagawa a gaban Yahweh.25Sa'an nan dole ka ɗauke abincin daga hannuwansu ka ƙone shi a kan bagadin tare da baiko na ƙonawa. Zai kawo ƙanshi mai daɗi a gare ni; zai zama baikon da aka yi mani da wuta.26Dole ka ɗauki haƙarƙarin ragon da aka yanka saboda keɓe Haruna ka ɗaga shi ka karkaɗa shi sama domin ya zama baiko na ɗagawa ga Yahweh, shi ne kuma zai zama rabonka.27Dole ka keɓe ƙirjin da aka karkaɗa a sama domi na, cinyar da firistoci suka kawo gudummuwa-ƙrjin da aka karkaɗa da cinyar da aka kawo gudummuwa saboda Haruna da 'ya'yansa.28Wannan zai zama zaunanniyar ka'ida saboda Haruna da 'ya'yansa. Zai zama gudummuwar da mutanen Isra'ila suka ba Yahweh baye-baye na salama.29Za a ajiye tufafin Haruna masu tsarki saboda 'ya'yansa a bayansa. Za a shafe su a cikin waɗannan tufafi a keɓe su gare ni a cikin su.30Firist ɗin da ya gaje shi daga cikin 'ya'yansa, wanda ya zo rumfa ta taruwa domin ya yi mani hidima a wuri mai tsarki, zai sa waɗannan tufafi har kwanaki bakwai.31Dole ka ɗauki ragon na rantsar da firistoci ka dafa namansa a cikin wuri mai tsarki.32Haruna da 'ya'yansa ne za su ci naman ragon da gurasar dake cikin kwando a ƙofar shiga rumfa ta taruwa.33Dole su ci naman da gurasar da aka bayar domin a yi masu kafara a kuma naɗa su, domin a keɓe su domina. Ba wanda zai ci wannan abincin, saboda zai zama abin da aka tsarkake saboda ni.34Idan naman keɓewar da aka bayar ko gurasar sun rage har sun kai safiya, za ka ƙone shi. Ba za a ci shi ba saboda an riga an keɓe shi saboda ni.35Haka za ka yi, ka bi umarnin dana baka, ka yi wa "ya'yan Haruna haka. Ka shirya su har kwana bakwai.36Kowacce rana zaka miƙa bijimi domin baiko na zunubi damin kafara. Dole ka tsarkake bagadin ta wurin yin kafara domin sa, zaka shafe shi domin ya zama a keɓe domi na.37Dole ka yi kwana bakwai kana yin hadaya saboda bagadin kana keɓe shi saboda Yahweh. Sa'an nan bagadin zai zama keɓaɓɓe saboda ni. Dukkan abin da ya taɓa bagadin zai zama keɓaɓɓe na Yahweh.38Dole ka riƙa miƙa ɗan rago bana ɗaya kowacce rana.39Dole ka miƙa ɗan rago ɗaya da safe, ɗaya ɗan ragon kuma ka miƙa shi da yamma.40Tare da ɗan rago na fari, za a miƙa mudu biyu na garin alkama mai laushi wanda aka kwaɓa da man zaitun kwalba biyu, da ruwan inabi shi ma kwalba biyu baiko na sha.41Rago na biyu tilas ka miƙa shi da faɗuwar rana. Dole ka sa gari kamar yadda ka sa da safe, haka kuma baiko na sha. Waɗannan za su zama da ƙamshi mai daɗi a gare ni; za su zama baiko da aka yi mani da wuta.42Waɗannan za su zama baiko na ƙonawa a cikin dukkan tsararrakinku, a ƙofar shiga rumfa ta taruwa a gaban Yahweh, inda zan sadu da kai in yi magana da kai a can.43A nan ne zan sadu da Isra'ilawa; darajata za ta keɓe rumfar. Zan keɓe rumfar ta taruwa da bagadin domin su nawa ne ni kaɗai.44Zan kuma keɓe Haruna da 'ya'yansa domin su yi mani hidima a matsayin firistoci.45Zan zauna a cikin Isra'ilawa zan zama Allahnsu.46Za su sani Ni ne Yahweh, Allahnsu wanda ya fito da su daga Masar domin in zauna a cikin su. Ni ne Yahweh Allahnsu.
Kalmar nan "yanzu" na nuna alama ce na cangin zance da aka yi, wato daga zancen turfafun firistoci zuwa zancen Kaɓe Firistoci.
"A nan "ka" na nufin Musa ne.
"domin ka keɓe Haruna da 'ya'yansa"
A nan "ni" na nufin Yahweh.
saniya
...
Waɗannan abinci ne iri daban daban da aka yi su da gari.
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
"Dole ka sa gurasar, da wainar, da wainar alkama"
A nan "miƙa" na nufin a ba da hadaya. AT: "sa'annan ka miƙa mani su yayin da ka ba da hadayan bijimin da kuma ragunan biyu"
Wannan wata suna ce ta alfarwa. Duba yadda kuka juya wannan a 27:20.
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
Duba yadda kuka juya wannan a 28:4.
Duba yadda kuka juya wannan a 28:6.
Wannan wani marufin kai ne da aka sakawa sai saka a kai. Duba yaddaa kuka juya wannan na 28:4.
An yi bayanin wannan kambi a 29:5 da cewa yana ɗauke da kalamau "keɓabbe ga Yahweh" (UDB) an kuma kera ta daga zinariya ne tsantsa.
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
"kawo 'ya'yan Haruna maza"
Duba yadda kuka juya wannan a 28:4.
Duba yadda kuka juya wannan a 28:4.
Duba yadda kuka juya wannan a 28:40.
"nawayan zama firistoci"
Nawayan zaman firisoci za zama na 'ya' maza na zuriyar Haruna. AT: "zai zama nasu da na zuriyarsu"
"doka marar karshe." Duba yadda kuka juya wannan a 28:42.
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
Wannan wata suna ce ta alfarwa. Duba yadda kuka juya wannan a 27:20.
Musa ne zai kashe hadayar bijimim, ba firsitoci ba, a kofar shiga by a cikin rumfa ta taruwar ba.
Dashike ayoyin nan sun faɗa abinda za a yi da jinin bijimin, sai ku yi amfani da kalmar da zai nuna cewa za a yanke wuyan saniyar ne domin a iya tara jinin a wani daro
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
Wannan wata suna ce na alfarwa. Duba yadda kuka juya wannan a 27:20
Musa ne zai yanka bijimin, ba firistocin ba, a kofar shiga ne kuma, ba a cikin rumfa ta taruwar ba.
Dashike ayoyin da sun biya baya za su fada mana abin da za a yi da jinin, sau ku yi amfani da kalmar da zai nuna cewa za a yanke bijimin ne har ma a tara jinin a daro.
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
Duba yadda kuka juya wannan a 27:1.
"jinin da ya rage"
"ya lullube gabobin"
Waɗannan gabobi ne da ke cikin jikin.
"Amma dai sauran gabobin bijimin"
Dashike wannan hadayun keɓe firistoci ne, Musa ne da kansa zai yanka dabbobin ba Haruna ko 'ya'yansa ba.
Ba kamar hadayan bijimi da aka ƙona a wajen rumfa ba, na ragunan za a ƙona su ne a bagadi na ciki.
"gabobin cikinsa." Duba yadda kuka juya wannan a 29:12
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
Za a kashe ragon ne ta wurin yanke wuyansa. AT: "Sa'annan ka yanka wuyan ragon"
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana
AT: "Ta wurin yin haka, zaka miƙa mini Haruna kenan"
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana
Wannan na nufin gabobin da ke cikin jikn. Duba yadda kuka juya wannan a 29:12.
Don 29:23, Duba yadda kuka juya irin waɗannan kalamun a 29:1.
AT: "da ka saka a gabana"
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana
Anan "waɗannan" na nufin sauran gobobuwan hadayan da aka ambata a ayoyin baya.
AT: "ka ƙona mini a matsayin baiko"
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
"ragon da ka miƙa" ko kuma "ragon da ka yanka"
"ragon da ka mora domin miƙa Haruna"
...
"zai zama na har'abada cewa waɗannan"
AT: "da za a ɗauka daga bayaswan Isra'ilawa"
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana
Tufafan sun zama na firistanci ne amma ba tufafan Haruna na sakawa haka kawai ba. AT: "Lallai ne Haruna ya ajiye tufafan sa masu tsarki wa 'ya'yansa a bayansa"
AT: "Lallai ne su saka waɗannan tufafi masu tsarki yayi da za ka shafe 'ya'yansa ka keɓe su a gare ni"
Wannan wata suna ce ta alfarwa. Duba yadda kuka juya wanna a 27:20.
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana
"ragon da ka yanka yayin da kake rantsar da firistocin"
Wannan ba ɗaya yake da wuri ma tsarki da ke wajen wuri mafi tsarki ba. AT: "a ƙofar shiga rumfar ta taruwar"
Wannan wata suna ce ta alfarwa. Duba yadda kuka juya wanna a 27:20.
...
AT: "Kada kowa yă ci shi"
...
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
"Na umurce ka ka yi wa Haruna da 'ya'yansa haka"
"Sa'annan bagadin zai zama mafi tsarki" (UDB)
"shi ma zai zama da tasarki sosai"
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
"Dole ne ku riƙa miƙa haday kullum a bisa bagadin"
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
"1/10 ... 1/4"
Mudu ɗaya shi ne lita 22.
Zaitun kwalba ɗaya shi ne lita 3.7.
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
AT: "Za su zama ƙonennen hadaya a gare ni"
"a cikin dukkan tsararrakin zuriyarku." Duba yadda kuka juya wannan a 12:12.
Wannnan wata suna ce ta alfarwa. Duba yadda kuka juya wannnan a 27:20.
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa.
AT: "Kasancewata zai kallafad da rumfar a gare ni"
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
1Tilas ka yi bagadi na ƙona turare. Tilas ka yi shi da itacen ƙirya.2Ratarsa za ta zama kamu ɗaya, faɗinsa kamu ɗaya. Tilas ka yi shi murabbi'i, tsawonsa kamu biyu. Tilas ka yi shi tare da ƙahonninsa.3Tilas ka shafe bagadin da zinariya tsantsa-bisansa, da sassansa, da ƙahoninsa. Tilas ka kewaye gefensa da zinariya.4Tilas ka yi zobba biyu na zinariya liƙe da shi a kusa da shi daga ƙasa suna duban sa a sassa biyu. Zobban za su zama wurin zura sandunan riƙewa da za a iya ɗaukar bagadin.5Tilas ka yi sandunan da itacen ƙirya, ka shafe su da zinariya.6Tilas ka sa bagadin turaren a gaban labulen dake kusa da akwatin shaida. Zai zauna a gaban marfin kafara na zunubi a bisa akwatin shaida, inda zan sadu da kai.7Tilas Haruna ya ƙona turare mai ƙamshi kowacce safiya. Zai ƙona shi sa'ad da yake gyara fitilun,8da yamma kuma Haruna zai kunna fitilun domin turaren ya riƙa ƙonewa koyaushe a gaban Yahweh, a dukkan tsararraki.9Amma kada ka miƙa wani turaren a kan bagadin turaren, ko wani baiko na ƙonawa ko baiko na hatsi. Kada ka zuba wani baiko na sha a kansa.10Tilas Haruna ya yi hadaya ta zunubi a kan ƙahonninsa sau ɗaya a shekara. Da jinin baikon na zunubi zai yi hadaya ta zunubi sau ɗaya a shekara a dukkan tsararrakinku. Keɓaɓɓe ne sarai saboda Yahweh."11Sa'an nan Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,12"Sa'ad da ka ƙidaya Isra'ilawa, kowanne mutum zai kawo abin fansa domin ransa ga Yahweh. Sa'ad da ka ƙidaya su dole ne ka yi haka. Domin kada annoba ta auko a cikin su sa'ad da kake ƙidaya su.13Dukkan wanda aka ƙidaya cikin yin ƙidayar zai biya rabin awo na azurfa, bisa ga kuɗin da ake amfani da su a wuri mai tsarki (awon dai-dai yake da abin da ake auna nauyin ƙaramin abu). Wannan rabin awo baiko ne domin Yahweh.14Dukkan wanda aka ƙidaya, daga shekara ashirin zuwa gaba, dole ya bada wannan baikon gare ni.15Lokacin da mutane suke bada wannan baiko domin fansar rayukansu, masu arziki ma ba zasu bada fiye da rabin awon nan ba, matalauta kuma ba zasu bada abin da bai kai rabin awon nan ba.16Dole ka karɓi wannan kuɗin fansa daga Isra'ilawa ka sa su cikin aikin rumfa ta taruwa. Dole ya zama abin tunawa ga Isra'ilawa a gare ni, su miƙa abin kafara domin rayukansu.17Sa'an nan Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,18"Zaka yi babban bangaji na tagulla da wurin zamansa na tagulla, bangajin wanke-wanke. Tilas ka sa shi tsakanin rumfa ta taruwa da bagadi, ka zuba ruwa a cikin sa.19Haruna da 'ya'ansa za su wanke hannuwansa da ƙafafunsu da ruwan dake cikin sa.20Sa'ad da suke shiga rumfa ta taruwa da sa'ad da suke zuwa kusa da bagadi su yi mani hidima ta ƙona baiko, dole su wanke da ruwa domin kada su mutu.21Dole su wanke hannuwansu da ƙafafunsu domin kada su mutu. Dole wannan ta zama dawwamammar doka ga Haruna da zuriyarsa a dukkan tsararrakin mutanensa.22Sa'an nan Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,23"Ka ɗauki waɗannan kayan yaji masu kyau: da murr mai zubowa na awo ɗari biyar, da sinamon mai ƙanshi mai daɗi na awo 250, da kayan yaji mai ƙanshi na awo 250,24da kayan yaji mai ƙanshi na kasiya na awo ɗari biyar, wanda aka auna bisa ga ma'aunin wuri mai tsarki, da kwalba ɗaya ta man zaitun.25Dole da waɗannan kayan haɗi za ka sa maiyin turare ya yi mai na shafewa mai tsarki. Zai zama man tsarki na shafewa, ajjiyayye saboda ni.26Dole da wannan mai na shafewa za ka shafe rumfa ta taruwa da akwati na shaida,27sai kuma teburin da kayan aikinsa da abin ɗora fitilar da kayanta da sanduƙin turare,28sai kuma bagadin ƙona baye--baye da dukkan kayansa da bangajin da wurin ɗora shi.29Tilas ka keɓe su saboda ni su zama masu tsarki domi na. Dukkan abin da ya taɓa su zai zama mai tsarki.30Tilas ka keɓe Haruna da 'ya'yansa domin su yi mani hidima a matsayin firistoci.31Dole kace da Isra'ilawa, 'Wannan mai na shafewa ne da aka keɓe domin Yahweh a dukkan tsararrakin mutanenku.32Dole mutane ba za su shafa shi a jikinsu ba, kuma ba za ka yi wani mai da kamar yadda ka yi shi ba, saboda keɓaɓɓe ne saboda Yahweh. Dole ka lura da shi ta wannan hanya.33Dukkan wanda ya yi turare irin sa, ko ya shafa wa wani shi, za a datse shi daga cikin mutanensa."'34Yahweh yace da Musa, "Ka ɗauki kayan yaji - wato su-stakte da onika da galbanum-kayan yaji masu ƙanshi tare da lubban tsantsa, ka auna su dai-dai wa daida.35Ka yi su kamar turaren yadda maiyin turare ya haɗa, gyararre da gishiri, mai tsafta keɓaɓɓe.36Ka yi masa haɗi mai kyau ka niƙa. Ka ɗiba cikinsa ka sa a shaida, wanda yake a cikin rumfa ta taruwa, inda zan sadu da kai. Ka ɗauke shi da tsarki sosai a gare ni.37Wannan turaren da zaka yi, ba zaka yi wani irin sa domin kanka ba. Zai zama mai tsarki sosai a gare ka.38Dukkan wanda ya yi turare irin sa ya yi anfani da shi za a datse shi daga cikin mutanensa."
Musa ya cigaba da gaya wa Musa yadda za a gina Masujadan.
A nan "ka" na nufin Musa da Mutanen Isra'ila.
Duba yadda kuka juya wannan a 27:1.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda Mutanen za su yi.
"bagadin ƙona"
AT: "da za ka haɗa shi da bagadin"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda Mutanen za su yi.
Sandukin akwati ne da ke ɗauke da dokokin. Duba yadda kuka juya wannan a 26:31. AT: "akwatin da ke ɗauke da dokokin"
Duba yadda kuka juya wannan a 25:15.
A nan "kai" na nufin Musa.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda Mutanen za su yi.
a dukkan tsararrakin zuriyar ku." Duba yadda kuka juya wannan a 12:12.
Kodashike kalmar nan "ka" na nufin Musa ne, amma dokar musamman ga Haruna ne da zuriyarsa game da lokaci da kuma abinda za su ba da hadaya a bagadin.
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
Duba yadda kuka juya wannan a 27:1.
"a dukkan tsararrakin zuriyarku" Duba yadda kuka juya wannan a 12:12.
Wannan na iya nufin: 1) "ka" na nufin Musa kadai ko kuma 2) "ka" na nufin Musa da shigabannin Isra'ila na nan gaba idan an ƙidaya.
"Shugabannin suna kirga Isra'ilawa maza ne kawai.
Suna ƙirga maza ne kawai. AT: "Dukkan wanda ka ƙidaya" ko kuma "Duk namijin da ka ƙidaya"
"1/2 awo na azurfa." Masu juyi na iya amfani da ma'aunin da mutanensu sun fi gane da shi. "Giram 5.5 na zaurfa" ko kuma "Giram 6 na azurfa"
Wannan kam a bayane yake cewa dai azurfa fiye da ɗaya ne a wannan lokaci. Wannan na ba da daidai wanda za a mora.
"gera 20." Gera wani ma'auni ne da mutane ke amfani da shi su auna abinda babu yawa ko kadan.
Akan ɗaukan cewa mayan lambobi suna gaba ne da kanana. AT: "daga shekara ashirin ko fiye" ko kuma "wadda ke shekara ashirin ko fiye da haka"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda Mutanen za su yi.
Maza ne kawai ke miƙa wannan hadaya.
Masu juyi na iya amfani da ma'aunin da mutanensu sun fi gane da shi. "Giram 5.5 na zaurfa" ko kuma "Giram 6 na azurfa." Duba yadda kuka juya wannan a 30:11.
Wannan na iya nufin 1) "Zai tunashe Isra'ilawan su miƙa abin gafara domin rayukansu" ko kuma 2) "Zai tunashe Isra'ilawa cewa sun miƙa abin dagara domin rayukansu."
A nan "ka" na nufin Musa da Mutanen Isra'ila.
"daro" ko kuma "
A bisa wannan ne za a dora banjajin wanke-wanken.
Wannan jimlar na bayana abinda firistoci ke amfani da babban daron su yi.
bagadin hadaya
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda Mutanen za su yi.
"ruwan da ke daron"
"ga Haruna da dukkan sararrakin zuriyarsa." Duba yadda kuka juya irin wannan jimlar a 12:12.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda Mutanen za su yi.
Duba yadda kuka juya wannan a 25:3.
"awo 500 ... awo 250." Shekel ɗaya na da kusa giram 11. Masu juyi na iya amfani da ma'aunin da mutanensu sun fi gane da shi. "Kilo 5.7 ...kilo 11.4 ... ko kuma "kilo shida ... kilo uku"
Waɗannan kayan yaji ne masu dadi.
Duba yaddak kuka juya wannan a 30:11.
Masu juyi na iya amfani da ma'auna da mutanensu sun fi sani; "lita 3.7" ko kuma "lita hudu"
...
Wannan na iya nufin 1) Musa zai samo mai yin turare ya yi ko kuma 2) Musa zai yi aikin da kansa yadda mai yin turare zai yi.
Mutumin da ya gwaninta a haɗa kayan kanshi su mai.
Yahweh ya cigaba da wa Musa magana.
A nan "ka" na nufin Musa.
Akwatin na ɗauke ne da dokokin. Duba yadda kuka juya wannan a 26:31. AT: "akwatin da ke ɗauke da dokokin."
"bagadin da ake ƙona hadaya a kai"
Yahweh ya cigaba da wa Musa magana.
Wannan na nufin kayayyakin da aka lisafta a 30:26.
"dukkan dukkan tsararrakin zuriyar mutanenku. Duba yadda kuka juya wannan a 12:12.
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
AT: "Ba za ku shafa man shafewa da aka miƙa ga Yahweh a jikin kowa ba"
"da kayan hadin da ka yi shi"
Wannan karin magana "datse" na iya nufin abubuwa uku ne a kalla. 1) "Ba zan ɗauke shi a matsayin mutumin Isra'ila kuma ba" 2) "Dole jama'ar Isra'ila su kori wannan mutumin" 3) "Dole jama'ar Isra'ila su kashe shi."
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi. Yahweh ya ba da waɗannan umarni ga Musa ne kawai: don haka kalmar nan "ka" na nufin Musa ne. Kalamun nan "haɗin mai yin turare" na iya nufin cewa Musa ne zai samo mai yin turaren ya bashi kayan yajin, ya haɗa su, ya nika su, sa'annan yă ba wa Musa don haka Musa na iya sa wasu haɗin a gaban awaktin, kamar yadda yake a UDB.
Waaɗannan duka kayan yaji ne.
AT: "Dole ne mai yin turare ya haɗa su zuwa irin wannan turare"
Wannan na iya nufin 1) Musa zai nema mai yin turare ne yă yi wannan aikin ko kuma 2) Musa da kansa ne zai yi wannan aikin daidai yadda ma yin turare zai yi shi. Duba yadda kuka juya wannan a 30:22.
"Zaka nika shi." Anan "ka" na nufin Musa.
A nan "ku" na nufin Musa ne da dukkan jama'a. (Dubi:
Yahweh ya cigaba da faɗa wa Musa abinda mutanen za su yi.
Kalmar nan "ku" na nufin jama'ar Isra'ila.
"da irin kayan haɗi ɗaya" Duba yadda kuka juya wannan a 30:32.
"Za ku ɗauke shi da mafi tsarki"
...
Wannan karin magana "datse" na iya nufin abubuwa uku ne a kalla. 1) "Ba zan ɗauke shi a matsayin mutumin Isra'ila kuma ba" 2) "Dole jama'ar Isra'ila su kori wannan mutumin" 3) "Dole jama'ar Isra'ila su kashe shi."Duba yadda kuka juya wannan a 30:32.
1Sai Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,2"Duba, na kira sunan Bezalel ɗan Uri ɗan Hour, daga kabilar Yahuda.3Na kuma cika Bezalel da Ruhuna, ya ba shi hikima, basira da ilimi, da dukkan kayayyakin ayyukan hannuwa,4don ya yi fasalin abubuwa da aikin zinariya da azurfa da tagulla;5ya kuma yanka da jera duwatsu da sassaƙa itace -- ya yi kowanne irin aikin fasahar hannu.6Tare da shi, na zaɓi Oholiyab ɗan Ahisamak, daga kabilar Dan. Na sa fasaha a zukatan dukkan masu hikima don su yi dukkan abin dana umarce ka. Wannan ya haɗa da7rumfar taruwa, da akwatin shaida, da abin tuba da yake kan akwatin, da dukkan kayayyakin dake cikin rumfar-8teburi da kayayyakinsa da tsantsa alkuki tare da dukkan kayayyakinsa, da turaren bagadi da9bagadin hadayar konawa da dukkan kayayyakinsa da babbar kwatarniya tare da mazaunin ta.10Wannan ya haɗa da ƙyakkyawan - sakakkun riguna - tsarkakkun tufafin domin Haruna firist da 'ya'yansa maza, na ajiye su domin na, saboda su yi aikin firistoci.11Wannan ya haɗa da man shafewa da turare domin wuri mai tsarki. Waɗannan masu sana'ar hannu dole ne su yi dukkan waɗannan abubuwa kamar yadda na umarce ku."12Sai Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,13"Faɗa wa Isra'ilawa: 'Dole ku kiyaye ranakun Asabar na Yahweh, domin dukkan waɗannan za su zama alama tsakanin shi da ku acikin dukkan zuriyar mutanenku har abada don ku sani shi ne Yahweh, wanda ya keɓe ku domin kansa.14Saboda haka dole ku kiyaye Asabar, don ku lura da ita da tsarki, ya keɓe ta dominsa. Duk wanda ya tozarta ta babu shakka kashe shi za a yi. Duk wanda ya yi aiki ranar Asabar, wannan mutum babu shakka za a yanke shi daga mutanensa.15Ku yi aiki a kwana shida kaɗai, amma a rana ta bakwai ranar Asabar ce ku huta, tsattsarka ga Yahweh. Duk wanda ya yi aiki a ranar Asabar babu shakka za a kashe shi.16Saboda haka Isra'ilawa dole su kiyaye Asabar. Dole su kiyaye ta a dukkan tsararrakin mutanensu za ta zama dawwamammar doka.17Asabar za ta zama a kullum alama tsakanin Yahweh da Isra'ilawa, gama a cikin kwana shida Yahweh ya yi sama da ƙasa, a rana ta bakwai kuma ya huta da yin komai.'"18Sa'ad da Allah ya gama magana da Musa a kan Tsaunin Sinai, ya ba shi alluna biyu na alƙawarin ka'idodi, da aka yi da dutse, rubutattu da hannunsa.
Allah na maganar zaɓen da ya yi kamar kiran su da sunan su ne. AT: "Na zaɓa"
Waɗannan sunayen maza ne.
Allah ya cigaba da wa Musa magana.
Yahweh yana maganar ba wa Bezalel Ruhunsa kamar Bezalel wani randa ne sa'annan Ruhun Allah kuma ruwa. AT: "Na ba wa Bezalel Ruhuna"
AT: "domin yă iya yin dukkan irin abubuwan da ake yi da hannu"
Allah ya cigaba da wa Musa magana
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan na nufin Allah ya sa iya yin abubuwa a zukatansu. AT: "Na ba da hikima ga dukkan masu hikima" ko kuma "Na sa dukkan masu hikima su iya yin abubua da kyau"
Wannan wata suna ce ta alfarwa. Duba yadda kuka juya wannan a 27:20.
Akwatin yana ɗauke da dokokin. Duba yadda kuka juya wannan a 26:31. AT: "akwatin da ke ɗauke da dokokin"
Wannan murfin yana bisa akwatin a wurin da ake miƙa hadaya. Duba yadda kuka juya wannan a 25:15.
"bagani ƙona turare." Duba yadda kuka juya wannan a 30:3.
"Bagaden da ake ƙona hadaya." Duba yadda kuka juya wannan a 30:26.
Allah ya cigaba da yi wa Musa magana.
Duba yaddak kuka juya irin wannan jimlar a 28:6.
"Waɗannan da suka gwaninta a yin abubuwa masu kyau"
Wato su yi biyayya da ka'idodin Asabar kenan. AT: "Dole ku kiyaye ka'idodin Yahweh game da Asabar"
Duba yadda kuka juya wannan a 12:12.
Wato ya keɓe mutanensa wa kansa kenan. AT: "wanda ya zaɓe ku ku zama mutanensa"
AT: "dole ku kiyaye shi da tsarki"
Wato duk wanda ya raina ta. AT: "Duk wanda ya kiyaye Asabar da raini" ko kuma "Duk wanda bai kiyaye dokokin Asabar ba"
"Dole a kashe shi." AT: dole ku kashe"
Wannan karin magana "datse" na iya nufin abubuwa uku ne a kalla. 1) "Ba zan ɗauke shi a matsayin mutumin Isra'ila kuma ba" 2) "Dole jama'ar Isra'ila su kori wannan mutumin" 3) "Dole jama'ar Isra'ila su kashe shi."
Yahwweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda zai fada wa mutanen Isra'ila.
Wato su kiyaye umarnin Sa game da Asabar kenan. AT: "dole su kiyaye umarnin Yahweh game Asabar"
"Su da dukkan tsararrakin zuriyar su za su kiyaye shi." Duba yadda kuka juya wannan "dukkan tsararrakin mutanensu" a 12:12.
"dokar da ba ta da karshe." duba yadda kuka juya wannan a 28:42.
AT: da Yahweh ya rubuta da hannunsa"
1Da mutanen suka ga Musa ya yi jinkirin dawowa daga tsaunin, sai suka taru kewaye da Haruna, suka ce masa, "Zo, ka yi mana gunki da zai wuce gaban mu. Domin wannan Musa, mutum wanda ya fito damu daga ƙasar Masar, bamu san abin da ya faru da shi ba."2Sai Haruna yace masu, "Ku tuttuɓe zobbanku na zinariya waɗanda suke a kunnuwan matayenku da kunnuwan 'ya'yanku maza da mata ku kawo su gare ni."3Dukkan jama'a suka tuttuɓe zobban da suke a kunnuwansu, suka kawo su wurin Haruna.4Ya karɓi zinariyar daga wurinsu, ya narkar da su, ya mai da shi siffa ta ɗan maraki. Sai mutanen suka ce, "Isra'ila, wannan shi ne allahnku wanda ya fito da ku daga ƙasar Masar."5Sa'ad da Haruna ya ga wannan, ya gina bagadi a gaban siffar marakin ya yi shela; ya ce, "Gobe akwai bikin girmama Yahweh."6Mutane suka tashi da asussuba kashegari suka miƙa hadayu na konawa da bayarwar zumunta. Sai suka zauna suka ci suka sha, sa'an nan suka tashi suna shagalin shashanci.7Sai Yahweh ya yi magana da Musa, "Tafi da sauri, gama mutanenka, waɗanda ka fito da su daga ƙasar Masar, sun ƙazantar da kansu.8Sun yi saurin ƙyale hanyar dana umarce su. Sun yi wa kansu ɗan maraki suna yi masa sujada, suna miƙa masa hadaya. Sun kuma ce, Isra'ila, wannan shi ne allahnka wanda ya fito daku daga ƙasar Masar.'"9Sai Yahweh ya faɗa wa Musa, "Na ga wannan jama'ar. Duba, mutanen nan suna da taurinkai.10Yanzu dai, kada ka yi ƙoƙarin hana ni. Fushina ya yi ƙuna a kansu, saboda haka zan hallaka su. Sai in yi wata babbar al'umma daga gare ka."11Amma Musa ya yi ƙoƙarin roƙon Yahweh Allahnsa. Ya ce, "Yahweh, me ya sa ka husata da mutanenka, waɗanda ka fito da su daga ƙasar Masar da ƙarfin iko da babban hannu?12Me ya sa za ka sa Masarawa su ce, 'Ya sa su sun fito da mugun nufi, don ya kashe su cikin duwatsu ya kuma shafe su daga fuskar duniya?' Ka janye daga zafin fushinka, ka ji tausayi daga wannan hukunci a kan mutanenka.13Ka tuna da Ibrahim da Ishaku da Isra'ila, bayinka, waɗanda kai da kanka ka rantse ka ce, 'Zan riɓaɓɓanya zuriyarka kamar taurarin sammai, in kuma ba zuriyarku dukkan wannan ƙasa wanda na yi maganar ta. Za ku gaje ta har abada.'"14Sai Yahweh ya huce ya janye daga hukuncinsa da ya ce zai sa masifa a kan mutanensa.15Musa kuwa ya juyo ya sauko daga kan tsaunin, yana ɗauke da allunan biyu na shaidar ka'idodi a hannunsa. Allunan rubutattu ne ciki da waje, gaba da baya.16Allunan kuma aikin Allah ne, rubutun kuwa na Allah ne, da ya zana a kan allunan.17Sa'ad da Yoshuwa ya ji hayaniyar mutane kamar suna ihu, ya cewa Musa, "Akwai hargowar yaƙi a zangon."18Amma Musa yace, "Ai ba amon nasara ba ce, ba kuma amon mutanen da aka ci nasara a kansu bane, amma hayaniyar waƙa nake ji."19Sa'ad da Musa ya kusato zangon ya ga siffar ɗan maraki mutane kuma na ta rawa. Ya harzuka da haushi. Ya watsar da allunan da suke hannunwansa suka farfashe a gindin tsaunin.20Ya ɗauki siffar ɗan marakin da mutane suka yi, ya kone ta, ya nike ta zama gari, ya barbada a cikin ruwa. Sa'an nan ya sa mutanen Isra'ila su sha ta.21Musa ya cewa Haruna, "Me waɗannan mutane suka yi maka, da ka jawo babban zunubi a kansu?"22Haruna yace, "Kada ka bar fushinka ya yi ƙuna, ya shugabana. Ka san waɗannan mutane, yadda suke a kan yin mugunta.23Sun ce da ni, 'Ka yi mana allah wanda zai wuce gabanmu. Gama Musa, mutumin da ya fito da mu daga ƙasar Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba.'24Ni kuwa nace da su, 'Duk wanda yake da zinariya, bari ya tuɓe ya kawo ta.' Suka ba ni zinariya ni kuwa na zuba su cikin wuta, daganan wannan maraki ya fito."25Musa ya ga mutanen sun gagara (gama Haruna ya barsu sun fi karfin a shawo kansu, suna sa abokan gãbarsu su yi masu ba'a).26Sai Musa ya tsaya a ƙofar zango ya ce, "Duk wanda yake wajen Yahweh, ya zo wurina." Dukkan Lebiyawa suka tattaru a wurinsa.27Ya ce masu, "Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: 'Bari kowanne mutum ya rataya takobinsa a gefensa da bayansa ya tafi ya dawo daga ƙofa zuwa ƙofa cikin zango kowa kuma ya kashe ɗan'uwansa, ya kashe abokinsa da kuma makwabcinsa.'"28Lebiyawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarta. A ranan nan mutane dubu uku suka mutu.29Musa ya cewa Lebiyawa, "Ku bada kanku cikin aikin Yahweh yau, gama kowannenku ya yi gãba da ɗansa da ɗan'uwansa, saboda Yahweh ya iya baku albarka yau."30Washegari Musa ya cewa mutanen, "Kun aikata babban zunubi. Yanzu zan tafi wurin Yahweh. Watakila zan iya yin kafara domin zunubanku."31Musa ya koma wurin Yahweh yace, "Aiya, waɗannan mutane sun aikata zunubi mai girma, sun yi wa kansu gunkin zinariya.32Amma yanzu, idan ka yarda ka gafarta zunubansu; amma idan ba za ka yi ba, ka shafe sunana daga cikin litafin daka rubuta."33Yahweh ya cewa Musa, "Duk wanda ya yi mani zunubi, shi ne kuwa zan shafe sunansa daga cikin littafina.34Saboda haka yanzu ka tafi, ka bida mutanen zuwa wurin da zan faɗa maka. Duba, mala'ikana zai wuce gabanka. Amma a ranar da zan hukuntasu, zan hukuntasu saboda zunubinsu."35Yahweh ya aika da annoba ga mutanen domin sun yi ɗan marakin, da Haruna ya yi.
Wato suka gane. AT: "mutanen su gane"
Kalmar nan "zo" yana nanata karfin umarnin. Mutanen suna neman Haruna ya yi masu gunki.
"jagorance mu" ko kuma "zama shugabanmu"
Kalmar nan "su" na nufin su zobbanku na zinariya.
Wannan na nufin dukkan mutanen da suka ƙi Musa a matsayin shugabansu da kuma Allahn Musa a matsayin Allahnsu.
Haruna ya narkar da zinariyar ya zuɓa ta cikin mazubi da ke da siffar ɗan maraki. Da zinariyar ta kama, sai ya cire mazubin, sa'annan kammamen ziniriyar ta ba da kamanin ɗan maraki.
"Da Haruna ya ga abinda mutanen suka yi"
Akwai alamar cewa mutanen sun yi fasikanci a cikin shagalin.
Wato rashin biyaya da abinda ya umarce su su yi kenan. AT: "daina yin abinda na umarce su kada su yi" ko kuma "sun daina yi abinda na umarce su su yi"
"Sun yi wa kansu gunkin zinariya mai kamanin ɗan maraki"
A nan Yahweh yana kwatanta sanin mutanen da ganinsu. AT: "Na san waɗannan mutanen"
AT: "mutane masu taurinkai"
An yi amfani ne da kalmar nan "yanzu" domin ba da alamar dakatar da maganar da Musa yake gaya wa Musa. AT: "Yahweh ya fada abinda zai yi wa mutanen.
Wato Yahweh yana maganar fushinsa kenan kamar wani wuta ne mai zaafi. AT: "Fushi na a kansu zai yi muni" ko kuma "Ina fushi ƙwarai da su"
Kalmar nan "ka" na nufin Musa.
Musa ya yi amfani ne da wannan tambayar domin ya lallashe Yahweh kada ya yi fushi da mutanensa. Ana iya juya wannan tambayan gangancin zuwa magana. AT: "Kada ka bar fushin ka ya sauko a bisa mutanenka" ko kuma "Kada ka yi fushi da mutanenka haka"
Waɗannan jimlar biyun na da ma'ana kusan ɗaya, an yi afani ne da su domin nanaci.
A nan kalmar nan "hannu" na nufin abubuwan da Yahweh ya yi. AT: "da dukkan mayan abubuwan da ka aikata.
Musa ya cigabda wa Allah magana kada yă hallaka Isra'ila.
Musa ya yi amfani ne da wannan tambayar domin ya lallashe Yahweh kada ya yi fushi da mutanensa. Ana iya juya wannan tambayan gangancin zuwa magana. AT: "Idan ka hallaka mutanenka, ai Masarawa suna iya ce, 'Ya sa sun fito ...don yă shafe su daga fuskar duniya'
"daga duniya"
"kada daina fushi haka"
Musa yana maganar fushin Allah kamar wani wuta ne mai ƙuna. AT: "mummunan fushinka"
"Ka yi tunanin Ibrahim"
"yi alkawali" ko kuma "ka ɗauki alkawari"
Wato za su mallaki kasar kenan. AT: "Za su mallaki kasar har'abada"
Waɗannan duwatsu biyu ne da Allah ya sassaƙa dokokinsa a kai.
Waɗannan jimla biyun suna da ma'ana kusan ɗaya. Na biyun yana bayana yadda duwatsun sun zama "aikin Allah."
Ana ɗaukan cewa Yoshuwa ya same Musa yayin da Musa yana koma cikin sansani.
"duwatsun da Yahweh ya yi rubuta akai"
AT: "Sai Musa ya tambaye Haruna abinda mutanen suka yi masa da har ya jawo masu irin wannan babban zunubin"
AT: "ka sa su sun aikata munmunan zunubi"
Haruna yana maganar fushin Musa kamar wani wuta ne da ke iya ƙuna. "Kada ka yi fushi"
Sun kuduru su yi zunubi. AT: "sun kudura su aikata mugunta"
"Kalamun nan "shi wannan" da aka saka kamu Musa alama ce ta raini. Sai ya zama kamar Musa din wani mutum ne da basu sani ba ko ma su gaskanta da shi.
AT: "Ni kuwa na ce da su duk wanda yake da zinariya ya tuɓe ya kawo ta"
A maimakon amincewa shi na ya yi ɗan marakin, Haruna yana cewa ɗan marakin ya fito daga wutan ne da ikon allahntaka.
"ba su kame kansu ba"
AT: "Sai Musa ya tasaya a ƙofar shiga ya ce duk wanda yana wajen Yahweh ya zo wurinsa"
Musa na maganar biyayya da Yahweh ne a matsayin zuwa wajensa ne. AT: "Duk wanda ke biyayya da Yahweh" ko kuma "Duk wanda zai bauta wa Yahweh"
"ya shiga ci ya fita daga wani kofar sansani zuwa wani kofar"
"mutane 3000"
Wannan na nufin "An zaɓe ku ku bauta wa Yahweh" ko kuma "Kun zama barorin Yahweh."
Ana iya bayana a fili cewa sun yi wannan ne cikin biyayya da Allah. AT: "gama ku yi biyayya da Yahweh kun kashe 'ya'yanku maza da 'yan uwanku"
Sun bauta wa gunki.
Musa yana maganar lallasan Allah ya gãfarta masu ne kamar zai iya yin kafaradomin zunubansu. AT: "Watakila zan iya lallashe Yahweh ya gãfarta maku"
Kalmar nan "na" na nufin Musa. AT: "ka goge suna na daga littafin"
Ana iya bayana a fili abinda Allah ya rubuta a littafin. AT: littafin da ka rubuta sunayen mutanenka"
Jimlar nan "shine" na nufin "sunan mutumin." AT: "Za goge sunan wannan mutumin daga litafina"
Wannan na nufin littafin Yahweh da Musa ya yi maganarsa a 32:30.
A ranar da Allah ya zaɓa ya hukuntasu, zai zama a fili cewa Allah ne ke hukunta su.
Mai yiwuwa wannan annoban wani rashin lafiya mai tsanani ne. AT: "Yahweh ya sa mutanen sun yi wata tsananin rashin lafiya"
Kodashike Haruna ne ya yiăn marakin, mutanen ma suna da laifi domin sune suka ce wa Haruna ya yi shi. AT: "sune suka ce wa Haruna yayi ɗan marakin"
1Sai Yahweh ya yi magana da Musa. "Tafi, daganan, kai da mutane waɗanda ka fito da su daga ƙasar Masar. Tafi zuwa ƙasar dana rantse wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, da na ce, 'Zan bada ita ga zuriyarku.'2Zan kuma aiki mala'ika a gabanka, zan kori Kan'aniyawa, da Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hibiyawa, da Yebusiyawa.3Tafi zuwa ƙasar, wanda ke fitar da madara da zuma, amma ba zan tafi tare da ku ba, gama ku mutane ne masu taurinkai. Don zan iya hallaka ku a hanya."4Sa'ad da mutane suka ji waɗannan maganganu masu tada hankali, suka damu suka yi nadama babu wanda ya sa kayan ado.5Yahweh yace da Musa, "Faɗa wa Isra'ilawa, 'Ku mutane ne masu taurin kai. Idan na tafi tare daku ɗan lokaci kaɗan, zan hallaka ku. Domin haka yanzu, ku tuɓe kayan adonku don zan iya yin abin dana shawarta da ku.'"6Saboda haka Isra'ilawa ba su sa kayan ado daga Tsaunin Horeb ba har zuwa gaba.7Musa ya ɗauki rumfar ya kafa ta a bayan zango. Ya kuma kira ta da suna rumfar taro. Duk wanda yake neman Yahweh da kowanne abu sai ya tafi rumfar taruwa, wajen zangon.8Duk sa'ad da Musa ya fita daga zango, dukkan mutane nan za su tashi tsaye a ƙofar rumfarsu su kalli Musa har sai ya shiga ciki.9Duk sa'ad da Musa ya shiga rumfa, al'amudin girgije yakan sauko ya tsaya bisa ƙofar rumfar, Yahweh kuwa ya yi magana da Musa.10Duk lokacin da dukkan mutane suka ga al'amudin girgijen nan na tsaye a kofar rumfar, sai su tashi su yi sujada, kowanne mutum a ƙofar rumfarsa.11Yahweh kuwa zai yi magana da Musa fuska da fuska, kamar mutum ne ke magana da abokinsa. Musa kuwa zai koma cikin zango, amma baransa Yoshuwa ɗan Num, saurayin mutum, zai tsaya a rumfar.12Musa ya cewa Yahweh, "Duba, ka faɗa mani cewa, 'Ka fita da mutanen nan a tafiyarsu,' amma ba ka bar ni in san wanda za ka aika tare da ni ba. Ka ce, 'Na san ka ta wurin sunanka, ka kuma sami tagomashi a idanuwana.'13Yanzu idan har na sami tagomashi a idanunka, ka nuna mani hanyoyinka domin in san ka in kuma cigaba da samun tagomashi a idanunka. Ka tuna wannan al'umma mutanenka ne."14Yahweh kuwa ya amsa, "Zan tafi tare da kai, zan kuma baka hutawa."15Musa yace da shi, "Idan ba za ka tafi tare da mu ba, kada ma ka ɗaga mu daga nan.16Domin in ba ta haka ba, ƙaƙa za a sani na sami tagomashi a idanunka, ni da mutanenka? Ba sai ka tafi tare da mu ba, domin ni da mutanenka a ga bambanci daga dukkan sauran jama'ar da suke fuskar duniya?"17Yahweh ya cewa Musa, "Zan kuma yi wannan abu yadda ka roƙa, gama ka sami tagomashi a idanuna, na kuma san ka da suna."18Musa kuwa ya ce, "Idan ka yarda ka nuna mani darajarka."19Yahweh yace, "Zan sa dukkan ɗaukakata ta wuce a gabanka, zan kuma yi alheri ga wanda na yi wa alheri, zan kuma nuna jinkai ga wanda na yi wa jinkai.20Amma Yahweh yace, "Ba za ka iya ganin fuskata ba, gama babu wanda zai gan ni ya rayu."21Yahweh yace, "Duba, a nan ga wani wuri kusa da ni; inda za ka tsaya bisa wannan dutsen.22Sa'ad da ɗaukakata take wucewa, zan sa ka a tsaguwar dutsen, in rufe ka da hunnuna har sai na wuce.23Sa'an nan zan ɗauke hannuna, za ka ga bayana, amma ba za ka ga fuskata ba."
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da fushinsa.
Ƙasar na da kyau a yi kiwon dabbobi a kuma nome abinci. Duba yadda kuka juya wannan a 3:7. AT: "ƙasar da ke da kyau a kiwon dabbobi da noma abinci"
"ka cike da" ko kuma "ke da yawar"
Dashike ana samun madara daga shanaye ne da kuma awakai, wannan na nufin abincin da ake samu daga dabbobi"
Dashike ana samun zuma daga furen itace ne, wannan na nufin abincin da ake samu daga amfanin gona. AT: "abinci daga amfanin gona"
"mutanen da sun ƙi su canja"
kayan ado masu kyau sosai da su sarkoki da zoɓe da ke da jauhari a cikinsu.
"mutanen da sun ƙi su canja." Duba yadda kuka juya wanna a 33:1.
Girgijen na da siffar al'amudi. Duba yadda kuka juya wannan a 13:19. AT: "girgijen da ka da siffar al'amudi"
Ana iya bayana a fili wurin da ya fito. AT: "yakan sauko daga sararin sama"
Yana magana da shi a fili a maimakon ta wurin mafarkai da wahayi ne ake fadi kamar Musa da Allah suna kallon fuskar juna ne yayin da suke magana. AT: "Yahweh yakan yi magana da Musa kai tsaye"
wanda ya kai ya zama soja (17:8), amma yă kasa da musa a shekaru
"Gani!" ko kuma "Kă ji!" ko kuma "Ka mai da hankali ga abinda zan gaya maka."
A san mutum da sunansa na nufin a sanshi sosai. AT: Na sanka sosai"
Wannan na cikin abinda Allah ke gaya wa Musa. AT: "Ni ji daɗi da kai" ko kuma "Na amince da kai"
Wannan na cikin abubuwan da Musa ke gaya wa Allah. AT: "To idan ka ji daɗi da ni" ko kuma "To idan ka amince da ni"
Wannan na iya nufin 1) "ka nuna mani abinda kake son ka yi nan gaba" ko kuma 2) "ka nuna mani yadda mutane ke iya faranta maka rai."
Kasancewar Allah na nufin shi kansa. AT " Zan tafi"
Kalmar nan "ka" na nufin Musa.
"Zan barka ka huta"
"Domin idan kasacewarka bai tafi tare da mu ba"
AT: "ta yaya mutane za su sani"
Musa yana amfani ne da wannan tambayan domin ya nanata cewa idan Allah bai tafi tare da su ba, ba wanda zai san cewa Musa ya sami tagomashin Allah.
"Ba za a sani idan"
Idan Yahweh ya ce "ka" a wannan aya, yana nufin Musa ne.
Wannan karin magana ne da ke nufin cewa Allah ya ji daɗinsa. Duba yadda kuka juya wannan a 33:12.. AT: "Na ji daɗinka" ko kuma "na amince da kai"
A san mutum da suna shi ne a san shi sosai. Duba yadda kuka juya wannan a 33:12. AT: "Na san ka sosai"
Allah na maganar tafiya yă wuce Musa domin Musa yă iya ganin alherinsa zai wuce ga Musa. AT: "Zan motsa i wuce ka domin ka gan alherina"
"Găni!" ko kuma "Ka ji!" ko kuma "Ka mai da hankali ga abinda zan fada maka."
Wannan domin Yahweh zai wuce yă tafi ne daga wurin Musa.
...
1Yahweh ya cewa Musa, "Ka datse allunan biyu na dutse kamar allunan farkon. Zan rubuta kalmomin a kan waɗannan allunan yadda suke cikin allunan farkon, allunan da ka farfasa.2Ka yi shiri da safe, ka zo kan Tsaunin Sinai, ka gabatar da kanka gare ni a kan saman tsaunin.3Babu wani da zai zo tare da kai. Kada ka bari a ga wani a ko'ina a kan tsaunin. Kada a bar garken tumaki ko awaki, su yi kiwo a gaban tsaunin."4Sai Musa ya sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ya tashi da sassafe, ya hau kan Tsaunin Sinai, kamar yadda Yahweh ya umarce shi. Musa ya rike allunan na dutse a hannunsa.5Yahweh kuwa ya sauko cikin girgije ya tsaya tare da Musa a can, ya yi shelar sunansa "Yahweh." Yahweh ya wuce ta gabansa ya yi shelar Yahweh,6Yahweh, Allah mai jinkai, mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan kauna, mai gaskiya,7mai kiyaye alƙawarin aminci ga dubban tsarraraki, mai gafarta mugunta da laifuffuka da zunubai. Gama ba zai kuɓutar da mai mugunta ba. Zai hukunta 'ya'ya da jikoki har tsara ta uku da tsara ta hudu saboda zunubin iyaye."8Musa ya hanzarta ya sukunyar da kansa ƙasa ya yi sujada.9Sai ya ce, "Idan na sami tagomashi a idanunka, Ubangijina, ina roƙonka ka tafi tare da mu, gama waɗannan mutanen suna da taurinkai. Gafarta mana laifinmu da zunubinmu, ka ɗauke mu abin gãdonka."10Yahweh yace, "Duba na kusan yin alƙawari. Gaban dukkan mutanenka, zan aikata al'ajabi irin wanda ba a taba yi ba a cikin dukkan duniya ko a cikin wata al'umma. Dukkan mutanen dake cikinku za su ga aikina, gama abin bantsoro nake yi da ku.11Ku kiyaye abin dana umarce ku yau. Na kusa korar maku Amoriyawa da Kan'aniyawa da Hittiyawa da Ferizziyawa da Hibiyawa da Yebusiyawa.12Ku lura da kada ku yi alƙawari tare da mazaunan ƙasar inda za ku tafi, ko su zama tarko a cikinku.13A maimakon haka dole ku rurrushe bagadansu, ku farfashe al'amudansu na dutse, ku sassare gumakansu.14Gama ba za ku yi wa wani allah sujada ba, domin Yahweh, wanda sunansa mai Kishi, Allah mai kishi ne.15Saboda haka kuyi hankali kada ku ƙulla alƙawari tare da mazaunan ƙasar, domin sun karuwantar da kansu ga allolinsu, kuma suka miƙa hadaya ga allolinsu. Sa'an nan wani daga cikinsu zai gayyace ku kuma za ku ci daga cikin hadayarsa,16sa'an nan kuma za ku ɗauka daga cikin 'ya'yansa mata domin "ya'yanku maza, 'ya'yansa mata za su karuwantar da kansu ga allolinsu, za su kuma sanya 'ya'yanku maza su karuwantar da kansu ga allolinsu.17Kada ku yi wa kanku alloli na zuɓi.18Dole ku kiyaye Bukin Abinci Marar Gami. Kamar yadda na umarce ku, ba za ku ci gurasa marar gami ba har kwana bakwai a kan lokacin da aka sa a watan Abib, gama a watan Abib kuka fito daga cikin Masar.19Dukkan ɗan farin nawa ne, koda ɗan farin mutum ne ko na dabba, dukkan 'ya'yan farin dabbobinku, wato na saniya da tunkiya.20Za ku fanshi ɗan farin jaki da ɗan rago, amma idan kuwa ba za ku fanshi ɗan rago ba, sai ku karya wuyansa. Dole za ku fanshi kowanne ɗan fari 'ya'ya mazanku. Kada wani ya zo gabana da hannu wofi.21Za ku iya yin aiki kwana shida, amma a kan rana ta bakwai dole sai ku huta. Koda lokacin noma ne da lokacin girbi dole ku huta.22Dole ku kuma kiyaye Bukin Makwanni tare da amfanin fari na alkama da kuka cire, kuma dole ku kiyaye bukin Tattarawa a karshen shekara.23Sau uku a cikin shekara dukkan mazajenku dole su hallara a gaban Ubangiji Yahweh, Allah na Isra'ila.24Gama zan kori al'ummai daga gabanku, in faɗaɗa kan iyakokinku. Babu wani da zai yi ƙyashin ƙasarku kamar na su a lokatan da kuka tafi ku bayyana a gaban Yahweh Allahnku sau uku a shekara.25Ba za ku miƙa jinin hadayata tare da wani abu mai gami ba, ko wani nama daga hadaya ta Bikin Ƙetarewa wanda za a bari har zuwa safiya.26Dole ku kawo mai kyau ta nunar farin amfanin gonakinku a cikin gidana. Kada ku yarda ku dafa ɗan akuya da yake shan nonon uwarsa."27Yahweh ya cewa Musa, "Rubuta waɗannan maganganu, gama dai-dai suke da maganganu alƙawarin da ni na ɗauka da Isra'ila."28Musa kuwa yana tare da Yahweh yini arba'in da dare arba'in; bai ci kowanne abinci ba ko ya sha ruwa ba. Ya rubuta maganganun alƙawarin a kan allunan, Dokoki Goma.29Lokacin da Musa ya sauko daga Tsaunin Sinai tare da alluna biyu na alƙawarin a hannunsa, bai sani ba, fuskarsa tana annuri lokacin da yake magana tare da Allah.30Sa'ad da Haruna da Isra'ilawa suka ga fatar fuskar Musa tana annuri, sai suka ji tsoro suka ka sa zuwa kusa da shi.31Amma Musa ya yi magana da Haruna da dukkan shugabannin jama'a su zo gare shi. Musa kuwa ya yi magana da su.32Bayan wannan, dukkan mutanen Isra'ila suka zo wurin Musa, ya faɗa masu dukkan umarnin da Yahweh ya ba shi a Tsaunin Sinai.33Sa'ad da Musa ya gama magana tare da su, sai ya sa mayafi ya rufe fuskarsa.34Duk lokacin da Musa ya je gaban Yahweh ya yi magana da shi, sai ya cire lullubin, har sai ya fito. Idan ya fito, zai faɗawa Isra'ilawa abin da aka umarce shi ya faɗa.35Da Isra'ilawa suka ga fuskar Musa tana haske, sai ya lullube fuskarsa kuma har sai ya koma don ya yi magana tare da Yahweh.
"shimfiɗaɗɗen dutsen." Duba yadda kuka juya wannan a 31:18
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
Wato ganin wani abu na nufin yin haka. AT: "Kada ka bar kowa a koina a wannan dutse"
"Ko ma garken tumaki ba za ka bari su zo kusa da dutsen ma su ci ciyawa ba."
"ya tsaya tare da Musa a kan dutsen"
Wannan na iya nufin 1) ya kira sunan "Yahweh" ko kuma 2) "ya shela wanene "Yahweh"
Allah na magana game da kansa ne. AT: "Ni, Yahweh, Ni ne Allah, kima Ni mai jinkai ne, mai alheri kuma"
"mai nuna aminci a alkawaransa da gaskiyansu a koda yaushe"
"mai aminci da alkawarinsa a kodayaushe. Duba yadda kuka juya wannan a 20:4.
"mai gaskiya a kodayaushe"
Yahweh yana magana game da kansa ne. AT: "Amma zan"
Yahweh yana magana game da kansa ne. AT: "ba zan kuɓutar da mai mugunta ba"
"ba zai taba kubutar da mai mugunta ba" ko kuma " ba zai taba ce da mai lafi marar laifi ba" ko kuma "ba zai taba kubutar da mugayen mutane ba"
AT: "Zai hukunta 'ya'yan saboda zunuban iyayensu"
Kalmar nan "'ya'ya" na nufin zuriya. AT: "zuriyarsu"
Ana maganar sa mutum yă ji daɗi ne kamar samun tagomashi ne a garesu.Duba yadda kuka juya wannan a 33:12. AT: "To idan har ka ji daɗi da ni" ko kuma "To idan ka amince da ni"
Kalamun nan "laifi" a takaice na nufin abu ɗaya ne, an dai haɗa su haka ne domin nanaci. AT: "dukkan zunubanmu"
Wato yă mallake su har abada kenan. AT: "ka ɗauke mu a matsayin mutanen da ka mallaka har abada" ko kuma "ka karɓe mu a matsayin mutanenka na har'abada"
A nan "ka" na nufin Musa.
Abin tsoro abu ne da ke sa mutane su ji tsoro. A Wannan hali, mutane za su ji tsoron Allah yayin da sun gan abinda yake yi. AT: "Abinda nake yi zai sa mutane su ji tsoro na"
A nan "ku" na nufin Musa da mutanen Isra'ila.
Yahweh ya cigaba da wa Musa magana. Anan, ya fada abinda Musa da mutanen za su yi.
Ana maganar masu jarabtan wasu ga zunubi ne kamar su tarko ne. AT: "za su jarabce ku ga zunubi"
Kalmar nan "suna" anan na nufin Halin Allah. AT: "Ni, Yahweh, mai kishi ne a ko da yaushe" ko kuma "Ni, Yahweh, ina mai kishi a kodayaushe"
Kalmar nan "kishi" anan na nufin cewa Allah na kula da darajarsa. Idan mutanensa sun bauta wa wasu alloli, ya rasa darajarsa kenan, domin idan mutanensa basu daraja shi ba, sauran mutane ba za su daraja shi ba. AT: "Ni, Yahweh, ina kare daraja na a kodayaushe"
Yahweh ya cigaba da fada wa Musa yadda mutanensa za su be da kansu a gaban bare.
Allah yana maganar yadda mutanensa ke bautar wasu alloli ne kamar su karuwai ne ga sauran maza. AT: "domin sun bauta wa wasu alloli" ko kuma "domin sun bauta wa wasu alloli kamar karuwai da ke zuwa wurin wasu maza"
Ana iya ba da sakamakon cin abincin da aka miƙa hadaya ga wani allah daban. AT: "kuma za ku ci wasu hadayarsa ku kuma zama da laifin bauta wa allolinsa" ko kuma "kuma za ku karuwantar da kanku ga allahnsa ta wurin ci daga hadayarsa"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda mutanen za su yi.
"kwana 7"
Wannan ne suna wata na farko a kalandar Yahudawa. Abib yana ta karshen watan uku da kuma farkon watan huɗu a kalandar yammaci. Duba yadda kuka juya "Abib" a 13:3.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda mutanen za su yi.
'Yan fari maza da na jakuna na Yahweh ne, amma Yahweh baya son a miƙa masa hadayarsu. A maimakon haka, Isra'ilawan za su ba da hadaya ɗan tunkiya a madadinsu. Ta haka ne Isra'ilawana ke iya fansa jakunan da ''yan su maza daga wurin Yahweh.
AT: "Dole ne duk mai zuwa wurina yă zo mani da hadaya"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda mutanen za su yi.
"Ko da kuna shirin no ma ne ko girbin amfanin gona"
An san da wannan bukin ma da Bukin Mafaka ko kuma Bukin Bukkoki. Tunanin ya zo ne daga yadda manoma sukan zama a 'yan bukka domin su yi gadin gonar har sai amfanin gonar ya nuna. Kalmar nan "Tattarawa" na nufin yayin da sun yi girbi amfanin gonar.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda mutanen za su yi.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda mutanen za su yi.
Ana iya sanar a fili cewa jinin na dabba ne. AT: "jinin dabbar da ka miƙa mani hadaya"
AT: "tare da gurasa mai gami a cikinsa"
"Musa kuwa yana kan dutsen"
"yini 40"
"har kwana arba'in, da yini da dare"
"Musa ya rubuta"
"ta fara ƙyali"
"su kusance shi" ko kuma "sun je wurinsa." Ba su hauro kan dutsen ba.
AT: "dukkan umarcni da Yahweh fada masa" ko kuma "kome da Yahweh ya umarce shi"
sai Musa ya cire"
AT: "abinda Yahweh ya umarce shi"
1Musa ya tattara dukkan jama'ar Isra'ilawa ya ce da su, "Waɗannan su ne abubuwan da Yahweh ya umarce ku da yi.2A rana ta shida za ku yi aiki, amma dominku, rana ta bakwai za ku maida ita rana mai tsarki, ranar Asabar ce ku huta sosai, mai tsarki ta Yahweh. Duk wanda ya yi wani aiki a ranar lalai zai mutu.3Ba za a hura wuta a kowanne gida ba a ranar Asabar."4Musa kuwa ya yi magana da dukkan jama'ar Isra'ilawa, cewa, "Wannan shine abin da Yahweh ya umarta.5Ku karɓi baiko domin Yahweh, dukkan ku wanda ya yi niyya a zuciya. Ku kawo baikon ga Yahweh--zinariya da azurfa da tagulla6da zane shudi da shunayya da mulufi da lallausan zaren lilin da gashin awaki da7fatun raguna da aka rina suka zama ja da fatun awaki da itacen kirya8da man fitila da kayan yaji domin man keɓewa da turaren konawa9da duwatsu masu tamani da duwatsun da za a mammanne a alkyabba da kyallen makalawa a kirji."10Kowanne mutum da yake da fasaha a cikinku ya zo ya yi wani abu ga Yahweh ya umarta-11rumfar sujada da rumfarta, da murfinta da maratayai da katakanta da sandunanta da dirkokinta da kwasfanta12da kuma akwati da sandunansa, da marfin kafara, da labule domin rufewa.13Suka kawo tebur da sandunansa da dukkan kayayyakinsa, kuma da gurasa ta kasancewa,14da alkuki don haske, tare da kayayyakinsa da fitilunansa da man fitilu15da bagadin turaren ƙonawa da sandunansa da man keɓewa mai ƙanshi da turaren ƙonawa da labulen ƙofar rumfa ta sujada16bagadin baye-baye na ƙonawa da ragarsa ta tagulla da sandunansa da kuma kayayyakinsa da babban daro da gammonsa.17Suka kawo labulen domin harabar tare da dirkokinsa da kwasfansu da labulen don ƙofar harabar18da kuma turakun maratayin rumfar da turakun farfajiyar tare da igiyoyinsu.19Suka kawo saƙaƙƙun tufafi na yin aiki a wuri mai tsarki da tsarkakkun tufafi domin Haruna firist da tufafin 'ya'yansa maza na aikin firistoci."20Sai dukkan kabilun Isra'ila suka tashi daga gaban Musa.21Kowanne zuciyarsa ta kada shi da wanda ruhunsa ya iza shi ya yi niyya kawo wa Yahweh baiko domin yin rumfa ta sujada, da dai dukkan ayyuka cikinta da kuma tsarkakkun tufafi.22Suka zo, maza da mata, dukkan waɗanda suke da niyya a zuciya. Suka kawo kayayyakin ƙawanya wato su 'yan kunne da ƙawane da mundaye da kayayyakin dukkan zinariya iri iri. Dukkansu suka bada baikon zinariya kamar su baye-bayen kaɗawa ga Yahweh.23Kowanne mutum da yake da shuɗi ko shunayya ko mulufi ko lallausan lilin ko gashin awaki ko fatun raguna da aka rina suka zama ja ko fatun awaki ya kawo su.24Kowanne ne wanda ya iya yin baikon azurfa da tagulla ga Yahweh, da kowanne wanda aka same shi yana da itacen ƙirya wanda zai zama da amfani a cikin aikin ya kawo shi.25Kowace mace mai fasaha da ta kaɗa zare da hannuwanta ta kawo zaren da ta kaɗa na shuɗi da shunayya da mulufi da lallausan lilin.26Dukkan mataye waɗanda zukatansu suka iza su, suka kaɗa zare da gashin awaki.27Shugabanai suka kawo duwatsu masu daraja da za a jera a kan alkyabba da kyallen makalawa a kirji;28suka kuma kawo kayan yaji da mai don fitilu da mai domin keɓewa da turare mai kanshi don ƙonawa.29Sai Isra'ilawa suka kawo bayarwar yardar rai ga Yahweh; kowanne mutum da mace waɗanda zuciyarsu ta iza su da niyya suka kawo kayayyaki domin dukkan aikin da Yahweh ya umarta ta wurin Musa aka yi shi.30Musa ya cewa Isra'ilawa, "Duba Yahweh ya kira Bezalel ɗan Uri ɗan Hur da sunansa, daga kabilar Yahuda.31Ya cika Bezalel da Ruhunsa, domin ya ba shi hikima da basira da sani da ilimi, don ya iya dukkan kowanne irin aiki,32ya ƙirƙiro zane-zane da aikin zinariya da azurfa da tagulla33da kuma wajen sassaƙar duwatsu na jerawa da sassaƙar itace-ya yi dukkan kowanne irin zane-zane na gwaninta.34Ya sa masa a cikin zuciyarsa ya koyar, shi da Oholiyab dan Ahisamak, daga kabilar Dan.35Ya cika su da fasaha ta yin kowanne irin aiki, da aiki kamar na sassaƙa dana zane-zane dana yin ɗinke-ɗinke da shuɗi da shunayya da mulufi da lallausan lilin dana yin saƙa. Sun iya yin kowanne irin aiki da yin zane-zane.
"ranar Asabar"
AT: "Dole ku kashe duk wanda ya yi wai aiki a wannan ranar"
Musa yana gaya wa Isra'ila cewa su yi abubuwan da Yahweh ya umarce shi a 25:3.
...
A nan "zuciya" na nufin mutumin da ke yin bayaswa. AT: "duk wanda yake da niya"
Musa ya cigaba da fada wa mutanen abinda Allah ya umarce su su yi.
"Duk mutum da ke da fasaha"
Duba yadda kuka huya wannan a 26:4.
Waɗannan wasu abubuwa ne da ke ajiye a kasa suna kuma hana abubuwan da aka haɗasu tafiya. Duba yadda kuka juya wannan a 25:31.
Wannan wat murfi ne da ke bisa akwatin alkawarin, a wurin da ake tsantsa. Duba yadda kuka juya wannan a 25:15.
"Jama'ar Isra'ila suka kawo"
Wannan gurasar na wakiltan kasacewar Allah. Duba yadda kuka juya wannan a 25:28.
wani firam da ke riƙe da katakon yayin da yake wutan ke ci. Duba yadda kuka juya wannan a 27:3.
Duba yadda kuka juya wannan a 26:36.
Wani katako mai ƙarfi ne da ke tokarewa. Duba yadda kuka juya wannan a 27:9.
Waɗannan wasu abubuwa ne da ke ajiye a kasa suna kuma hana abubuwan da aka haɗasu tafiya. Duba yadda kuka juya wannan a 26:19.
wasu abubuwane da ake yin su ko da katako ko karafuna da sinin baki domin a kama gefe-gefen buka a kasa. Duba yadda kuka juya wannan a 27:17.
...
Wannan na nufin mutane kabilun. AT: "mutane dukkan kabilun Isra'ila"
A nan "zuciya" na nufin mutumin. Ana maganar zuciyar da ta saurari Allah ne kamar ruwa ne da guguwa ta kaɗa ta. AT: "wanda sun saurari Allah"
A nan "ruhu" na nufin mutumin. AT: "wanda ke da niyya" ko kuma "wanda ke son ya"
A nan "zuciya" na nufin mutumin. AT: "dukkan wada ke da niyya"
Wannan dukka kayan ado ne kala kala.
Domin 35:23. Duba yadda kuka juya yawancin kalamun nan a 25:3
Wannan na iya nufin 1) "kaya da aka rina shuɗi da shunayya da mulufi," mai yiwuwa ulu. Ko kuma 2) "rina shuɗi da rina shunayya da mulufi" domin a rina lilin. Duba yadda kuka juya wannan a 25:3.
A nan "zuciya" na nufin matayen. Ana maganar matayen da sun saurare Allah ne kamar ruwa ne da goguwa da kaɗa. AT: "wanda suka saurare Allah"
Domin 35:27-29, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 25:1 da 25:3
A nan "zuciya" na nufin mutanen. AT: "waɗanda ke da marmari"
A nan maganar Ruhun Allah da ya ba Bezelel iyawa ne kamar wani abu ne da ya cika Bezalel.
Domin 35:30-33, Duba yadda kuka juya yawancin kalamun nan a 31:1 and 31:3.
Musa ya cigaba da yi wa mutanen magana.
A nan "zuciya" na nufin Bezalel. Ana maganar iya koyarsa wani abu ne kamar wani abu ne da ake iya saka wa a zuciya. AT: Ya ba wa Bezalel iya koyarwa"
Ana maganar fasaha na iya yi abubuwa masu kyau ne kamar wani abu ne da ke iya cika mutum. AT: "ya ba su gwaninta"
"Oholiyab" da "Ahissamach" sunayen maza ne. Duba yadda kuka juya wannan a 31:6.
Mutumin da ke iya yi zane-zane a kan abubuwa masu karfi kamar su katako, dutse, ko karfe.
Mai yin zane-zane a kan kaya.
masu yi abubuwa masu kyau da hannuwansu
masu yin kaya da zare
mai yi kaya da abubuwa masu kyau
1Bezalel da Oholiyab da kowanne mutum mai fasaha waɗanda Yahweh ya ba su fasaha da basira na sanin yin kowanne irin aikin wuri mai tsarki bisa ga dukkan yadda Yahweh ya umarta."2Musa ya kirawo Bezalel da Oholiyab da kowanne mutum mai fasaha wanda Yahweh ya ba shi fasaha a zuciya da dai dukkan wanda zuciyarsa ta iza shi ya zo ya yi aikin.3Su kuwa sun karɓa daga wurin Musa dukkan baye-bayen da Isra'ilawa suka kawo domin aikin wuri mai tsarki. Duk da haka mutane suna kawo baye-bayen yardar ransu kowacce safiya ga Musa.4Sai dukkan mutane masu fasaha suke yin aiki a wuri mai tsarki suka zo daga aikin da suke ta yi.5Masu aikin hannu suka faɗa wa Musa, "Mutane suna ta kawo wa fiye da abin da ake buƙata domin aikin da Yahweh ya umarta a yi."6Sai Musa ya umarce su kada wani a cikin zango ya sake kawo baiko don aikin wuri mai tsarki.7Saboda haka mutane suka dena bada waɗannan kyaututtuka. Sun bada fiye da kayayyakin da ake buƙata domin yin dukkan aikin.8Sai dukkan gwanayen mutane a cikin ma'aikatan suka yi rumfa da labule goman da aka yi daga lallausan zanen lilin da shudi da shunayya da mulufi da kuma zanen kerubim. Wannan shine aikin Bezalel, mai babbar fasahar sassaƙa.9Tsawon kowanne labule kamu ashirin da takwas, faɗinsa kuma kamu hudu ne. Dukkan labule girmansu ɗaya ne.10Bezalel ya haɗa labule biyar ga kowanne ɗayan, sa'an nan kuma ɗayan labule biyar ya kuma haɗa kowanne da ɗan'uwansa.11Ya sa maratayai shuɗi a gefen karshen labule na layin, ya sake yin haka har sau biyu.12Ya sake sa hantuna hamsin a karbun labule na fari, haka kuma ya sa na biyun. Saboda haka dukkan maratayan suna daura da juna.13Ya kuma yi maɗauri hamsin na zinariya, ya harhaɗa labulen da juna da maɗauran saboda rumfar sujadar ta zama ɗaya.14Bezalel ya yi labulai da gashin awaki domin a rufe rumfar; ya yi waɗannan labulai goma sha ɗaya.15Tsawon kowanne labule kamu talatin, faɗinsa kuma kamu huɗu ne. Kowanne ɗaya daga cikin labule goma sha ɗayan girmansu ɗaya ne.16Ya harhaɗa labule biyar wuri ɗaya, labule shida kuma ya harhaɗa su wuri ɗaya da juna.17Sai ya yi hantuna hamsin ya sa a gefe na bisa na labule na farin, haka kuma ya sa maratayai hamsin a gefen sama na labule na biyu.18Bezalel ya yi hamsin maɗaurai da tagulla waɗanda zai harhaɗa maratayan da su domin rumfar ta zama ɗaya.19Ya yi wa rumfar marufi da fatun raguna da aka rina ja, ya kuma sake yin wani abin rufewa na fata mai kyau ya hau sama da shi.20Bezalel ya yi katakan rumfar da itacen ƙirya.21Tsawon kowanne katako kamu goma ne, kaurinsa kuwa kamu ɗaya da rabi ne.22Kowanne katako an feƙe bakinsa biyu domin a harhaɗa su tare. Ya yi wannan domin dukkan katakan rumfar.23Ya yi katakan rumfar ne ta wannan hanya: ya kafa katakai ashirin domin gefen kudu.24Bezalel ya yi kwasfa arba'in da azurfa su shiga ƙarƙashin katakai ashirin. Akwai kuma katako da yana da kwasfa biyu don bakinsa biyu da aka feƙe.25Gama na biyun yana wajen arewa da rumfar, ya kafa katakai ashirin,26kwasfa arba'insu na azurfa. Akwai katako da yake da kwasfa biyu a ƙarƙashin katakon gaba.27Domin bayan rumfar a gefen yamma, Bezalel ya yi tsaikoki shida.28Ya yi kuma katakai biyu don kusurwar baya ta rumfar.29Waɗannan katakai an raba su tun daga ƙasa, amma an haɗa su a sama a ƙawanya ta fari. Haka ya yi da su kusurwoyin nan biyu.30Akwai katakai takwas da kwasfansu na azurfa guda goma sha shida dukkansu, kowanne katako yana ƙarƙashin na fari, katakai biyu kuma suna ƙarƙashin kwasfa ta gaba.31Bezalel ya yi sanduna na itacen ƙirya-sanduna biyar domin katakan gefe ɗaya na rumfar,32sanduna biyar kuwa don katakan ɗaya gefen na rumfar, biyar kuma domin katakan da yake bayan rumfar wajen yamma.33Ya sa sandan da yake a tsakiya ya wuce daga ƙarshe zuwa ƙarshe. Ya dalaye katakan da zinariya.34Ya yi masu ƙawanne na zinariya, don su yi aikin riƙe sarƙafa sandunan, ya kuma dalaye sandunan da zinariya.35Bezalel ya yi labule da shuɗi, da shunayya da mulufi da lallausan zaren lilin, ya kuma yi wa labulen zanen kerubim na aikin gwaninta.36Ya yi wa labulen dirkoki huɗu da itacen ƙirya, sai ya dalaye su da zinariya. Ya kuma yi masu maratayai da zinariya don dirkokin kwasfa huɗu da azurfa.37Ya yi wa ƙofar rumfar labule da shuɗi da shunayya da mulufi da lallausan zaren lilin ya yi wa labulen ado sosai.38Ya kuma haɗa labulen da dirkokinsa biyar. Ya dalaye kawunansu da maɗauransu da zinariya. Kwasfansu guda biyar an dalaye su da tagulla.
Musa ya cigaba da yi wa mutanen Magana.
Wanan sunan namiji ne. Duba yadda kuka juya wannan a 31:1.
Wannan suna namiji ne. Duba yadda kuka juya wannan a 31:6.
A nan ana maganar fasaha da basira kamar wani abu ne da Yahweh ke iya sakawa a cikin mutum.
"kamar yadda Yahweh ya umurta"
Wanan sunan namiji ne. Duba yadda kuka juya wannan a 31:1.
Wannan suna namiji ne. Duba yadda kuka juya wannan a 31:6.
A nan "ziciya" na nufin mitumin da Yahweh ya mai da shi mai fasaha. AT: "wanda Yahweh ya bashi fasaha"
A nan "zuciya" na nufin mutumin. Anan maganar yadda zuciyar mutum na iya sauraron Allah ne kamar ruwa ne da goguwa ya kaɗa. AT: "wanda ya saurare Allah"
AT: "Masu aikin hannun sun fada wa Musa cewa mutanen suna kawo fiye da abinda ake buƙata domin yin aikin da Yahweh ya umurcesu su yi"
"Mutanen da suke aikin wurin mai tasarkin suka faɗa wa Musa"
Domin 38:8-10, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 26:1
A haɗa waɗannan labulen ne domin a iya rataya su su haɗa bukka.
Wannan sunan namiji ne. Duba yadda kuka juya wannan a 31:1.
Domin 36:11-13. Duba yadda kuka juya yawancin wa kalamun a 26:4.
...
Duba yadda kuka juya wannan a 26:1.
A nan "ya" na nufin Bezalel, ammam ya shafe dukkan ma'aikatan wuri mai tsarkin.
"maɗauri na zinariya 50"
Domin 36:14-17, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan a 26:7 and 26:10.
"ya yi 11"
"kamu 30"
"hantuna 50"
Domin 36:18-19, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 26:10 and 26:12.
"hantuna ta tagulla 50"
Domin 36:20-23, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 26:15.
"kamu 10 ... kamu 1.5"
...
Domin 36:24-26, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 26:19.
"kwafsa 40 na azurfa"
"katakai 20"
Za a samu kwafsa biyu kuma a karkashin kowane katakai.
Domin 36:27-28, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 26:22.
a gefen da ke yamma
...
Domin 36:29-30, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 26:22.
"kwasfansu ... 16 dukkansu"
Za a samu kwafsa biyu kuma a karkashin kowane katakai.
Domin 36:31-34, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan a 26:26 and 26:29.
a gefen yamma
daga wannan gefen alfarwar zuwa wancan gefen
Domin 36:35-36, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 26:31.
Domin 36:37-38, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 26:36.
A nan "ya" na nufin Bezalel da waɗanda suke masa aiki. "Bezalel da mutanen sa sun yi"
...
1Bezalel ya yi akwati da itacen ƙirya, tsawonsa kamu biyu da rabi, faɗinsa kamu ɗaya da rabi, tsayinsa kamu ɗaya da rabi.2Ya dalaye shi da zinariya tsantsa ciki da waje, ya kuma yi masa dajiya da zinariya kewaye har sama.3Ya sa ƙawanya huɗu ta zinariya domin kafafunsa huɗu, kawanne biyu a gefensa ɗaya, biyu kuma a ɗaya gefen.4Ya yi sandunan da itacen ƙirya ya kuma dalaye su da zinariya.5Ya zura sandunan cikin ƙawayun da suke a gefen akwatin don ɗaukarsa.6Ya yi murfin kafara da zinariya tsantsa. Tsawonsa kamu biyu da rabi faɗinsa kuma kamu ɗaya da rabi.7Bezalel ya ƙera siffofin kerubobin biyu da zinariya domin ƙarshen kafara biyu.8Kerub ɗaya don ƙarshen kafara, ɗaya kerub kuma domin ƙarshen gefen. An yi su kamar guntu ɗaya ne na murfin.9Kerubobin suka buɗe fikafikansu sama, suka inuwanta murfin da fikakansu. Kerubobin suna fuskantar juna, suna kallon tsakiyar murfin kafara.10Bezalel ya yi tebur da itacen ƙirya. Tsawonsa kamu biyu, faɗinsa kamu ɗaya ne, tsayinsa kamu ɗaya da rabi.11Ya dalaye shi da zinariya tsantsa, ya kuma yi masa dajiya da zinariya tsantsa a kewayan samansa.12Ya yi masa dajiya mai faɗin tafin hannu kewaye da shi, ya kuma yi wata dajiya da zinariya a kewaye da ita.13Ya yi ƙawanye huɗu na zinariya, ya kuma manna kowanne a kursuwoyi huɗu na ƙafafunsa.14Kowannensu na kusa da dajiyar inda za a zura sanduna na ɗaukar teburin.15Ya yi sanduna da itacen ƙirya, ya kuma dalaye su da zinariya domin ɗaukar teburin.16Ya yi kayan da za a ɗora a kan teburin-kwanonin da cokula da kwanonin tuya da butoci waɗanda za ayi baye-baye da su. Ya yi su da zinariya tsantsa.17Ya yi alkuki da zinariya tsantsa. Ya yi alkuki a gindinsa da gorar jikinsa, ƙoƙunan da mahaɗansa da furanninsa dukkansu a haɗe aka yi da ita.18Akwai rassa guda shida daga cikin kowanne gefen-rassa uku daga cikin ɗaya gefen, sa'an nan rassa uku na alkukin daga wancan gefen.19Reshe na fari ya yi da ƙoƙuna uku an yi su kamar tohon almond tare da mahaɗai da furanni da kofuna guda uku wanda aka yi kamar almond ya yi fure a kan reshe da mahaɗan furannin. Tana kamar dukkan rassa shidan daga wajen alkuki.20A bisa alkukinsa, a tsakiyar ƙyauran, akwai kofuna guda huɗu da aka yi su kamar tohon almond da mahaɗai da furanni.21Akwai mahaɗi a ƙarƙashin kowanne reshe biyu biyu-an yi su kamar ɗaya da ita, a ƙarƙashin rassa na biyu biyu-haka nan kuma an yi kamar guda ɗaya a haɗe. Ta wannan hanyar akwai mahaɗi a ƙarƙashin rassa na uku, an yi da maɗauri ɗaya. Haka aka yi don dukkan rassa shida daga cikin alkukin.22Ganyensu da rassan an yi dukka a maɗauri ɗaya, da ƙerarriyar zinariya tsantsa aka yi kome.23Bezalel ya yi alkuki da fitilunsa bakwai da hantsuka da farantansa da zinariya tsantsa.24Ya yi alkuki da kayayyakinsa tare da talanti ɗaya da zinariya tsantsa.25Bezalel ya yi bagadin ƙona turare. Ya yi ta da itacen ƙirya. Tsawonsa kamu ɗaya, faɗinsa kamu ɗaya, murabba'i tsayinsa kuma kamu biyu. Ƙahoninsa an yi su kamar ɗaya ne da shi.26Ya dalaye bagadin da zinariya tsantsa-bisansa da gefensa da ƙahoninsa. Ya kuma kewaye shi da dajiya ta zinariya.27Ya yi masa ƙawanne biyu wanda za a haɗa su da ita a ƙarƙashin dajiya daura da juna. Kowannen su yana riƙe da sandunan da za a ɗauki bagadin.28Ya kuma yi sanduna na itacen ƙirya, ya kuma dalayesu da zinariya.29Ya yi tsattsarkan mai na keɓewa da kuma tsantsa turare mai ƙanshi yadda mai yin turare ya kan yi.
Wannan sunan namiji ne. Duba yadda kuka juya wannan a 31:1.
"kamu 2.5 ... kamu 1.5"
Ana maganar katakai huʊɗu da ke tokare sandukin ne kamar kafafun mutum ne ko na dabba.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Domin 37:4-6, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 25:12 and 25:15.
Kodashike "ya" na nufin Bezalel, "ya" na iya zama a haɗe da dukkan ma'aikatan da ke taimaka masa.
"kamu 2.5 ... kamu 1.5"
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Domin 37:7-9, duba yadda kuk juya yawancin waɗannan kalamun a 25:15 and 25:19.
AT: "Ya yi su ne kamar guntu ɗaya"
Bezalel ya saka siffar Kerubim ne kamar su ainihin Kerubim ne da fukafukansu a yaɗe, suna kuma inuwanta marfin.
Bezalel ya saka siffar Kerubim ne kamar su ainihin Kerubim ne da fukafukansu a yaɗe, suna kuma inuwanta marfin.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Domin 37:10-13, duba yadda kuka juwa yawancin waɗannan kalamun a 25:23 and 25:25.
"kamu 2 ... kamu 1 ... kamu 1.5"
Faɗin hannun mutum da yatsun a yaɗe.
Ana maganar katakai huɗu da ke tokare sandukin ne kamar kafafun mutum ne ko na dabba.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Domin 37:14-16, duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 25:25 and 25:28.
AT: "Bezalel ya haɗa Zobban"
Ana amfani da kwanoni da butoci ne a yi baye-baye. ...
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Domin 37:17-19, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 25:31 da 25:33.
AT: "Ya yi gorar jikinsa, kofunan jikinsa, da furanninsa a haɗe da alkuki"
"sa'annan ya yi kofuna 3 sun yi kamar tahon furanni"
...
Domin 37:20-22, duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 25:33 da 25:35.
AT: "akwai kofuna 4 da Bezalel ya yi da sun yi kamar tahon almond"
AT: "wanda ya yi su kamar ɗaya da ita alkukin"
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Domin 37:23-24, duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 25:37.
Wani abinda ɗaukan kayan aiki ne.
"kilo 34"
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Domin 37:25-26, duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 30:1 and 30:3.
Kamu ɗaya na da santimita 46.
AT: "Ya yi Ƙahohinsa kamar ɗaya ne da shi"
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Domin 37:27-28, duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 30:3 and 30:5.
AT: "Wanda za a haɗa su da bagadin"
Mutumin da ya gwaninta a haɗa kayan kanshi su mai. Dub a yadda kuka juya wannan a 30:22.
1Bezalel ya yi bagadin ƙona baye-baye da itacen ƙirya. Tsawonsa kamu biyar faɗinsa kamu biyar - murabba'i ne nan - tsayinsa kuwa kamu uku ne.2Ya yi masa zankaye a kusurwoyinsa huɗu siffar kamar ƙahonnin takarkari. An yi ƙahonnin su haɗe tare da bagadin, ya dalaye shi da tagulla.3Ya yi dukkan kayayyakin domin bagadin-tukwane da cokula da daruna da cokula masu yatsotsi da farantan wuta. Ya kuma yi dukkan kayayyakin da tagulla.4Ya yi raga domin bagadin, an yi aikin ne da tagulla aka sa a ƙarƙashin kanta, yasa ta daga ƙasa zuwa sama.5Ya sa ƙawanyoyi huɗu domin kusurwoyi huɗu na ragar tagulla don zura sandunan.6Bezalel ya yi sanduna da itacen kirya ya kuma dalaye su da tagulla.7Sai ya zura sandunan cikin ƙawanne na gefen bagadin, don ɗaukar shi. Ya yi bagadin da itace sa'an nan ya raba cikinsa.8Bezalel ya yi daron wanka da tagulla da gammonsa na tagulla. Ya yi gammuna daga madubai na mata masu yin aiki a ƙofar rumfar taro.9Ya kuma yi haraba. Ya yi labulenta na gefen kudun harabar da lallausan zaren lilin, tsawonsu kamu ɗari ne.10Labulai suna da dirkokinsu ashirin, tare da tagulla a ƙarƙashin kwasfan ashirin. Akwai maratayan dirkoki, da maɗaurai da aka yi da azurfa.11Kamar yadda yake gefen arewa, akwai labule kamu ɗari da sanduna masu kamu ashirin na tagulla, maɗauran sanduna ƙarafuna na azurfa.12Labule na gefen yamma kamu hamsin ne, dirkokinsa kuwa guda goma ne. Maɗaurai da dirkokin ƙarafuna na azurfa ne.13Tsawon harabar kamu hamsin ne wajen gabas.14Labulai na gefe ɗaya na ƙofar kamu goma sha biyar ne. Suna da dirkoki guda uku tare da kwasfan dirkoki uku.15A gefen ƙofar farfajiyar akwai labule masu tsawo kamu goma sha biyar da dirkoki uku da kuma kwasfan uku.16Dukkan labulai da suke kewaye da harabar an yi su da lallausan zaren lilin.17An yi kwasfan dirkoki da tagulla. Maratayan dirkoki da maɗauransu an yi su ne da azufa. Dukkan dirkokin farfajiyoyin an dalaye su da azurfa, kuma marufan dirkokin suma an yi su da azurfa. Dukkan harabar dirkokan an dalaye su da azurfa.18Labulan ƙofar harabar kamu ashirin tsayinsa. Labulen an yi su da shudi da na shunayya da na mulufi da na lallausan zaren lilin.19Tsawonsa kamu ashirin, tsayinsa kamu biyar dai-dai da labulen haraba. An yi dirkokin labulen guda huɗu da kwasfan dirkoki na azurfa. An dalaye kawunansu da maɗauransu da azurfa.20Dukkan turakun rumfa da harabar an yi su da tagulla,21Wannan shi ne lissafin abubuwan da aka yi na rumfa, rumfar alƙawarin ka'idodi, kamar yadda aka yi bisa ga yadda Musa ya yi umarni. Wannan aikin Lebiyawa ne a ƙarƙashin jagorancin Itamar ɗan Haruna firist.22Bezalel ɗan Uri ɗan Hur daga kabilar Yahuda, an yi dukkan abin da Yahweh ya umarci Musa.23Oholiyab ɗan Ahisamak daga kabilar Dan, wanda ya yi aiki tare da Bezalel gwani ne, cikakken ma'aikacin zane-zane da ɗinki na shuɗi, da na shunayya da na mulufi da na lallausan zaren lilin.24Dukkan zinariya da aka yi aikace-aikacen da ita don wannan aiki, a cikin dukka aikin wanda ya haɗa da wuri mai tsarki - zinariya daga baikon bankwana - talanti ashirin da tara ne da awo 730 bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi.25Azurfar da aka samu ta wurin taron mutane awonsa talanti ɗari ne da awo 1,775, bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi,26ko kowanne mutum da aka ƙidaya ya bada rabin awo. Wannan adadin abin da aka samu bisa kowanne mutum wanda aka ƙidaya ta ƙasa, waɗanda sun kai 603,550 daga shekara ashirin zuwa gaba manya da tsoffafi na dukkan maza.27An yi amfani da azurfa talanti ɗari domin yin kwasfa don wuri mai tsarki da labule-an yi kwasfa ɗari da talanti ɗaya don kowanne kwasfa.28Sauran 1,775 na awon azurfa, Bezalel yayi maratayan dirkokin, ya dalaye saman maratayan dirkoki ya kuma yi da ƙarafuna dominsu.29Tagulla daga abin da aka bayar kuwa talati saba'in da awo 2,400.30Tare da wannan ya yi kwasfa domin ƙofar rumfar taruwa, da tagullar bagadi, da tagulla aka yi ragarsa, da dukkan kayayyakin bagadin,31Kwasfa domin harabar, da kwasfa don ƙofar harabar, da dukkan turakun don rumfar sujada da na dukkan turakun harabar.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Domin 38:1-3, duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 27:1 and 27:3.
Kamu ɗaya shi ne santimita 46.
AT: "Ya yi ƙahohin a haeɗ ne da bagadin"
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Domin 38:4-5, duba duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 27:3 da 27:5.
AT: "da suka sa a ƙarƙashin kanta"
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 27:7.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Gammon ne ke riƙe da daron wanka ta tagullan. Duba yadda kuka juywa wannan a 30:17.
An samu tagullan ne daga madubai. AT: "Tagullan sun zo ne daga maduban"
...
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
Domin 38:9-10, Duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 27:9.
"100 ... 20"
Kamu ɗaya na da santimita 46.
Domin 38:11-12, duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 27:11.
"100 ... 20 ... 50 ... 10"
Kamu ɗaya na da santimita 46.
Domin 38:13-16, duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 27:11 da 27:14.
"50 ... 15 ... 3"
Kamu ɗaya na da santimita 46.
AT: "Bezalel da abokan aikinsa sun yi dukkan labulai na suke kewaye da harabar da lallausan zaren lilin"
Domin 38:17-20, duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 27:14 da 27:17.
AT: "Bezalel da abokan aikinsa sun yi kwafsan dirkokin da tagulla ne"
Suka dalaye dukkan dirkokin farfajiyoyin da azurfa, sa'annan marufan dirkokin suma da azurfa.
AT: "Suka rufa harabar dirkokin da azurfa"
"20 ... 5 ... 4"
Kamu ɗaya na da santimita 46.
"Suka yi labulan da"
AT: Suka dalaye kawunansu da maɗaurinsu da azurfa"
AT: "Suka yi dukkan turakan rumfa da haraba da tagulla"
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
AT: "dă Musa ya umarci Lewiyawa su rubuta"
Wannan sunan namiji ne. Duba yadda kuka juya wannan sunan a 6:23.
"Bezalel" da "Uri" sunayen maza ne. Duba yadda kuka juya waɗannan a 31:1.
"kowane abinda Yahweh ya ce wa Musa ya yi"
"Oholiyab" da Ahisamach" sunayen maza ne. Duba yadda kuka juya wannan a 31:6.
"a matsayin gwani cikakken ma'aikaci a zane-zane da ɗinki"
AT: "Dukkan zinariya da mutanen suka yi aikace-aikacen"
talanti tara ... talanti ɗari- "talanti 29 ... talanti 100." Talanti guda kilo 34 ne.
Awo ɗaya giram 11 ne.
Akwai ma'aunin awo daban daban a lokacin. Amma ba a san wannene za a yi amfani da shi ba. Duba yadda kuka juya wannan a 30:11
AT: "Azurfar da taron mutanen suka bayar"
Beka ɗaya shi ne awo 1/2.
"awo 1/2"
An kidaya duk mutumin da ke da shekaru ashirin ko fiye ne, kuma ana bukatan yă ba da rabin awo.
"shekara 20"
Talantin ɗaya kilo 34 ne. AT: "Ma'aikatam sun yi amfani da talanti 100 na azurfa ne" ko kuma " Ma'aikatan sun yi amfani da kilo 3,400 na azurfa ne"
"100 ... 70"
Kowane awo giram 11 ne.
Wannan sunan namaji ne. Duba yadda kuka juya wannan a 31:1.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da gina alfarwar da kayan ɗakin.
wani firam da ke riƙe da katakon yayin da yake wutan ke ci. Duba yadda kuka juya shi a 27:3.
wasu abubuwane da ake yin su ko da katako ko karafuna da sinin baki domin a kama gefe-gefen buka a kasa. Duba yadda kuka juya wannan a 27:17.
1Tare da shuɗi da shunayya da mulufi, suka ɗinka tufafi masu kyau domin aiki a wuri mai tsarki. Sun yi wa Haruna tsarkakun tufafi domin wuri mai tsarki, kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.2Bezalel ya yi falmarar da zinariya, da shuɗi da shunayya da mulufi da lallausan lilin.3Suka buga zinariya falle-falle, suka yanyanka ta zare-zare don su yi aikin saƙa da ita tare da zane na shuɗi da shunayya da mulufi da kuma na lallausan lilin, aikin gwani mai fasaha ne.4Suka yi aikin kafaɗu domin falmara, sa'an nan suka haɗa su a gefenta biyu na sama.5An yi anfani da ɗamarar falmarar ta saƙa mai kyau; da irin kayan da aka saƙa falmara ne aka saƙa su da zinariya da shuɗi da shunayya da mulufi da zane lallausan lilin, kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.6Sun gyaggyarta duwatsu masu daraja aka jera su a tsaiko, aka zana sunayen 'ya'yan Isra'ila goma sha biyu.7Bezalel ya sa a kan kafaɗun falmarar don su zama duwatsun tunawa da Isra'ila, kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.8Ya kuma yi ƙyallen maƙalawa a ƙirji, an yi amfani da gwaninta kamar yadda aka yi wa falmarar. Ya yi ta da zinariya da shuɗi da shunayya da mulufi da lallausan lilin.9Tana nan murabba'i. An yi ƙyallen maƙalawa a kirji riɓi biyu. tsawonsa da faɗinsa kamu ɗaya ne.10Suka sa jeri huɗu na duwatsu masu daraja a bisansa. Jeri na fari aka sa yakutu da tofaz da ganat.11A jeri na biyu aka sa emeral da saffir da lu'u-lu'u.12A jeri na uku aka sa yakinta da idon mage da ametis.13A jeri na huɗu aka sa beril da onis da yasfa. Duwatsun an yi masu maɗauki da zinariya.14An jera duwatsun bisa sunayen 'ya'yan Isra'ila goma sha biyu, kowanne bisa ga yadda sunansa yake. Suna kamar yadda a kan yi hatimin zoɓe, kowanne suna ya tsaya domin ɗaya daga cikin kabilu goma sha biyu.15A kan kirjin sai suka yi tukakkun sarƙoƙi kamar igiyoyin amara da aikinsa zinariya tsantsa.16Sai suka yi tsaiko biyu na zinariya da ƙawanyu biyu na zinariya, suka sa ƙawanen nan biyu a gefe biyu na ƙyallen maƙalawa a ƙirji.17Suka kuma zura sarkokin nan biyu na zinariya a kowannen biyu na ƙyallen maƙalawa a ƙirji.18Sai suka maƙala waɗancan a bakin sarƙoƙin biyu. Sa'an nan suka rataya su a kafaɗun falmarar daga gaba.19Suka yi ƙawanne biyu na zinariya, suka sa su a gefe biyu na kyallen maƙalawa a ƙirji daga ciki kusa da falmaran.20Suka yi waɗansu ƙawanne biyu na zinariya, suka maƙala su kusa a gaban kafaɗu biyu na falmarar kusa da mahaɗin a bisa abin damarar falmarar.21Sai suka ɗaure ƙawanyun kyallen maƙalawa a ƙirji a ƙawanyun falmarar da shuɗiyar igiya saboda kyallen maƙalawa a ƙirji ya kwanta lif a bisa kan abin damarar. An yi wannan don kada falmarar ya kwance daga ƙirjin falmarar. Wannan ya faru ne kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.22Bezalel ya saka taguwa ta falmaran da shuɗi ga baki ɗaya, aikin masaƙi ne.23An yi wa taguwar wuya wurin sa kai a tsakiya. An yi wa wayan saƙa saboda kada ta yage.24A ƙasan taguwar, sai suka yi fasalin 'ya'yan rumman da shuɗi, shunayya, da mulufi da lallausan lilin.25Suka yi kararrawa da zinariya tsantsa, suka sa su a tsakankanin rumman dukka kewaye a ƙasa da bakin igiyar, tsakanin rumman --26an sa ƙararrawa da rumman, ƙararrawar da rumman -- a bakin igiya domin Haruna ya yi hidima a ciki. Wannan bisa ga yadda Yahweh ya umarci Musa.27Suka saƙa janfofi da lallausan zaren lilin saboda Haruna da 'ya'yansa.28Suka kuma yi rawani da lallausan lilin, da huluna da mukura da lallausan lilin, da mukurai da lallausan lilin.29Sun kuma yi abin damara da lallausan lilin mai launin shuɗi da shunayya da mulufi, an yi mata dinkin ado. Wannan an yi shi kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.30Suka yi allo tsattsarka da zinariya tsantsa suka zana rubutu a kan ta, irin na hatimi a kanta, "Mai Tsarki ga Yahweh."31Suka ɗaura shi da shuɗiyar igiya a gaban rawanin. Wannan an yi shi yadda Yahweh ya umarci Musa.32Haka kuma aka yi aikin rumfar sujada, da rumfar taruwa, kuma an gama ta. Mutanen Isra'ila suka yi shi dukka. Suka bi dukkan umarnin da Yahweh ya ba Musa.33Suka kawo wa Musa rumfar sujada - rumfar da dukkan kayayyakinta, maratayanta da katakanta da sandunanta da dirkokinta da kwasfanta34da murfi na jan fatun raguna da na awaki da labulen rufewa35da akwatin alƙawari da sandunansa da murfin kafara.36Suka kawo tebur da dukkan kayayyakinsa da gurasar ajiyewa37da alkuki na zinariya tsantsa da fitilunsa, tare da kayayyakinsa da mai domin fitilu38da bagadin zinariya da mai na keɓewa da turare mai ƙanshi da labulen ƙofar rumfar sujada39da bagadin tagulla da ragarsa ta tagulla da sandunansa da kayayyakinsa da daro da gammonsa.40Suka kawo labulen harabar da dirakunta da kwasfanta da labulen ƙofarta da igiyoyinta da turakunta da dukkan kayayyaki don aiki a rumfar sujada da rumfar taruwa.41Suka kawo tufafin ado na aiki a wuri mai tsarki da tsarkakan tufafin domin Haruna firist da tufafin 'ya'yansa maza, domin su yi aiki a matsayin firistoci.42Mutanen Isra'ila suka yi dukkan wannan aiki yadda Yahweh ya umarci Musa.43Musa ya duba dukkan aikin, duba, sun yi shi dai-dai. Yadda Yahweh ya umarta, ta wannan hanya suka yi shi. Sai Musa ya sa masu albarka.
Abokan aikin Bezalel sun koma yin tufafan firist.
Kalmar nan "su" na nufin Bezalel, da Oholiyab, da sauran ma'aikatan.
"dai-dai yadda Yahweh ya ce wa musa yayi"
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist.
Wannan sunan namiji ne. Duba yadda kuka juywa shi a 31:1.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist.
AT: "sun yi shi ne kamar abu daya da saƙaƙƙen lallausan lilin"
"kamar yadda Yahweh ya ce wa Musa yăyi." Duba yadda kuka juya shi a 39:1.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist.
Duba yadda kuka huya shi a 28:10.
"''ya'ya 12"
"kamar yadda Yahweh ya ce wa Musa ya yi. Duba yadda kuka juya shi a 39:1.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist.
"Bezalel ya yi" ko kuma "Bezalel da ma'aikata sun yi"
Kamu ɗaya na da santimita 23.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist.
"Ma'aikatan sun sa ƙyallen maƙalawa a kirji"
Wasu harsuna basu da kalamu domin kowannen waɗannan duwatsun. Abin muhimmanci anan dai shin suna da daraja kuma sun bambanta da juna. Duba yadda kuka juya su a 28:17.
AT: "Sun yi masu duwatsun a tsaiko na zinariya"
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist.
AT: "Ma'aikatan sun jera duwatsun"
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist.
"sarkokin da aka yi su da zinariya tsantsa aka kuma tuƙa su kamar igiya." Duba yadda kuka juya shi a 28:13.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist da aka umarta a 28:25 da 28:27.
saƙaƙƙen damarar falmara - Duba yadda kuka juya shi a 28:6.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist da aka umarta a 28:27.
AT: "Saboda a iya maƙale shi"
"falmaran yă zama a haɗe da ƙirjin falmaran"
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist kamar yadda aka umarta a 28:31 da 28:33.
Wannan sunan namiji ne. Duba yadda kuka jiya shi a 31:1.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist kamar yadda aka umarta a 28:33.
Waɗannan wasu ƙananan kararrawa ne.
Haka ne yakamata a cigaba da maimaita adon dukka har kashen rigar.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist.
Domin 39:27-29, duba yadda kuka juya yawancin waɗannan kalamun a 28:39 da 28:40 da 28:42.
Wannan wani abin rufa kai ne da aka yi shi da wani dogon tsiri da maza ke ɗaurawa a kai.
Wannan wani tufa ne da ake sakawa a ciki haɗe da jiki bayan tufafi na waje. AT: "tufafi"
Wannan wata doguwar tufai ne da ake sakawa a kan kafada ko kuma kewaye da kwankwaso.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da yi tufafan firist kamar yadda aka umarta a 28:36.
Wannan wata kwarzanannen rawani ne da aka yi ta da zinariya. Duba yadda kuka juya shi a 29:5.
'Ya'yan Isra'ila sun gama yin abubuwan da Yahweh ya umurta a 35:4 da 35:10.
"Alfarwar" da "rumfar taruwa " na nufin abu ɗaya ne. AT: "Sai mutanen Isra'ila suka gama dukkan ayyukan alfarwar"
Abin ratayewan yana haɗe ne daidai da adon da ke riƙe labulen tare. Duba yadda kuka juya waɗannan a 26:4.
Duba yadda kuka juya shi a 25:31.
Wannan wat murfi ne da ke bisa akwatin alkawarin, a wurin da ake tsantsa. Duba yadda kuka juya shi a 25:15.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da miƙa wa Musa dukkan abubuwan da suka yi.
Wannan gurasar ya wakilci kasancewar Allah. Duba yadda kuka juya shi a 25:28.
wani firam da ke riƙe da katakon yayin da yake wutan ke ci. Duba yadda kuka juya shi a 27:3.
Abokan aikin Bezalel sun cigaba da miƙa wa Musa dukkan abubuwan da suka yi.
"Mutanen Isra'ila suka kawo"
Dukkan su wurin ɗaya ne.
"Sai mutanen"
Kalmar nan "ga shi" yana jan hankali ne zuwa sanarwa da ya biyo baya.
"Sun yi shi a yadda Yahweh ya umarce su"
1Sai Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"A kan rana ta fari a wata na fari a sabuwar shekara dole ka kafa rumfar sujada, rumfar taruwa.3Ka sa akwatin alƙawari a cikin ta sa'an nan ka kare akwatin da labule.4Ka shigar da tebur, ka shirya shi yadda ya kamata da kayayyakinsa dai-dai. Ka kuma shigar da alkukin da fitilu a bisansa.5Ka ajiye bagadi na zinariya na ƙona turare a gaban akwatin alƙawari, sa'an nan ka rataya labulen ƙofar rumfar sujada.6Ka ajiye bagadi na yin baikon ƙonawa a gaban ƙofar rumfar taruwa.7Ka kuma ajiye daro tsakanin rumfar taruwa da bagadin sa'an nan ka zuba ruwa a cikin shi.8Ka yi harabar ka kewaye ta, sa'an nan ka rataya labulen ƙofar harabar.9Ka ɗauki man keɓewa, ka shafa wa rumfar sujada da kome dake cikinta. Ka tsarkake ta da dukkan kayayyakinta gare ni, ta kuma zama tsarkakkiya.10Ka shafe bagadin domin ƙona hadaya da dukkan kayayyakinsa. Za ka tsarkake bagadin a gare ni, zai zama mafi tsarki gare ni.11Ka shafa wa daron tagulla da mazauninsa man keɓewa a gare ni.12Ka kawo Haruna da 'ya'yansa maza a ƙofar rumfar taruwa, kuma dole ka yi masu wanka da ruwa.13Sa'an nan ka sa wa Haruna tufafi masu tsarki ka shafa masa man domin ka tsarkake shi ya yi mani aikin firist.14Ka kawo 'ya'yansa maza, ka kuma sa masu taguwoyi.15Sa'an nan ka shafe su da mai kamar yadda ka shafe mahaifinsu saboda su yi mani aiki a matsayin firistoci. Shafe su da man zai sa su zama firistoci din-din din cikin dukkan tsararrakin mutanen su.16Wannan shine abin da Musa ya yi; ya bi dukkan umarnin da Yahweh ya ba shi. Ya yi dukkan waɗannan abubuwa.17Sai aka kafa rumfar sujadar a kan rana ta fari a wata na fari a sheka ta biyu.18Musa ya kafa rumfar sujadar, ya kafa kwasfanta, ya jera katakanta, ya sa mata sandunanta, ya kakkafa dirkokinta.19Sa'an nan ya baza shinfiɗa a bisa rumfar sujadar ya sanya rumfa a bisan ta, kamar yadda Yahweh ya umarce shi.20Sai ya ɗauki dokokin alƙawaran ka'idodi ya sa a cikin akwatin. Ya kuma zura sandunan a ƙawanen akwatin, sa'an nan ya sa murfin kafara a bisansa.21Ya kawo akwatin a cikin rumfar sujada. Sa'an nan ya sa labulen domin kare akwatin alƙawari yadda Yahweh ya umarce shi.22Ya sa teburin cikin rumfar taruwa, a wajen gefen arewa na rumfar sujada, a wajen labulen.23Sai ya jera gurasa a kan teburin a gaban Yahweh, yadda Yahweh ya umarce shi.24Ya kuma sa alkukin a cikin rumfar taruwa, daura da gaban tebur, a wajen kudu na rumfar sujada.25Ya kunna fitilu a gaban Yahweh, yadda Yahweh ya umarce shi.26Sai ya sa zinariyar turaren bagadi a cikin rumfar taruwa a gaban labule.27Ya ƙona turare a kanta, yadda Yahweh ya umarce shi.28Ya sa labule a ƙofar rumfar sujada.29Ya kuwa sa bagadi domin ƙona hadaya a ƙofar rumfar sujada da rumfar taruwa. Ya kuma miƙa hadaya ta ƙonawa da hadayar gari, yadda Yahweh ya umarce shi.30Ya sa daro a tsakanin rumfar taruwa da rumfar sujada, ya kuma sa ruwa a cikinta domin wankewa.31Musa da Haruna da 'ya'yansa maza su kan wanke hannuwansu da ƙafafuwansu daga daron,32sa'ad da suke shiga cikin rumfar taruwa, da sa'ad da su kan tafi bisa bagadi, yadda Yahweh ya umarci Musa.33Musa kuwa ya yi haraba kewaye da rumfar sujada da bagadin. Ya sa labulen ƙofar harabar. Ta wannan hanya, Musa ya gama aikin.34Sa'ad da girgije ya rufe rumfar taruwar, sai ɗaukakar Yahweh ta cika rumfar sujada.35Musa kuwa bai iya shiga rumfar taruwa ba gama girgijen yana zaune a bisanta, kuma saboda ɗaukakar Yahweh ta cika rumfar sujadar.36Duk lokacin da aka ɗauke girgijen daga kan rumfar sujadar, mutanen Isra'ila su kan kama hanya domin tafiya.37Amma idan girgijen bai tashi daga rumfar sujadar ba, mutanen ba za su iya tafiya ba. Za su tsaya har ranar da ya tashi.38Gama girgijen Yahweh yana bisa kan rumfar sujada da rana, haka nan wutarsa ta na bisan shi da dare, wannan ya sa dukkan mutanen Isra'ila suka yi tafiyarsu ko'ina.
Wannan na nuna lokacin da Allah ya ceci mutanensa daga Masar. Wannan yakan faru ne a tsakiyar watan uku a kalandar yammaci.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda mutanen za su yi.
"sa akwatin alkawarin na umuni da ke cikin akwati mai tsarki"
"ka sa akwatin a bayan labulen"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda mutanen za su yi.
Wannan na nufin "akwati mai tsarki" (UDB).
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abinda mutanen za su yi.
"dukkan abubuwan da ke a haɗe da shi"
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
Musa ne zai yi waɗannan abubuwan da kansa.
AT: "da ka keɓe mani"
Yahweh ya cigaba da yi wa Musa magana.
"cikin dukkan tsararrakin zuriyarsu." Duba yadda kuka juya irin wannan jimlar a 12:12.
AT: "Sai mutanen suka kafa rumfar sujada"
Wannan na nufin daidai bayan shekara ɗaya da Allah ya ceci mutanensa daga kasar Masar. Wannan ya faru ne a irin su tsakiyar watan uku a kalandar yammaci. Duba yadda kuka juya shi a 40:1.
Wato shekara ta biyu kenan bayan Yahweh ya ciro mutanensa daga kasar Masar.
Musa shi ne shugaban. Mutanen sun tamaka masa ne da kafa akwatin.
"wani tace ne mai karfi da aka kafa shi zuwa sama ana kuma amfani da shi domin a tare
Musa ne shugaban. Yana da ma'aikata masu taimakonsa.
"a gaban"
Musa ya umurce ma'aikatansa to masar da alkukin. AT: "Abokan aikin Musa sun kafa alkukin a cikin rumfa mai tsarkin"
Labulen ne aka yi amfani da shi aka raɓa wuri mai tsarki daga wuri mafi tsarki. AT: "a gaban labulen da ya raɓa wuri mai tsarki da wurin da ke mafi tsarki"
Sun wanke ne da ruwar da ke daron. AT: "suka wanke hannayensu da kafafuwansu da ruwar da ke daron"
"Don haka"
"Darajar asancewar Yahweh Yahweh ya cika"
AT: "ya taso daga"
AT: "sa'ada ya taso"
1Yahweh ya kira Musa ya yi masa magana daga cikin rumfar taruwa, ya ce,2"Ka yi wa mutanen Isra'ila magana ka gaya masu cewa, 'Sa'ad da waninku ya kawo baiko ga Yahweh, sai ya kawo baikon dabbar daga cikin dabbobinsa, daga garken shanu ko kuma na tumaki.3Idan baikonsa baiko ne na ƙonawa daga garken shanu, dole ya miƙa namiji marar lahani. Zai miƙa shi a ƙofar rumfar taruwa, domin ya zama karɓaɓɓe a gaban Yahweh.4Zai ɗibiya hannunsa a kan baiko na ƙonawar, sa'an nan za a karɓa daga gare shi a yi masa kaffara domin shi kansa.5Dole ne ya yanka bijimin a gaban Yahweh. 'ya'yan Haruna maza, firistoci, zasu miƙa jinin su yayyafa shi a kan bagadi wanda ya ke a bakin ƙofar rumfar taruwa.6Sa'an nan dole ya feɗe baikon ƙonawar ya kuma yanyanka shi gunduwa-gunduwa.7Sa'an nan 'ya'ya maza na Haruna firist zasu kunna wuta a kan bagadin su sa itace domin iza wutar.8'Ya'yan Haruna maza, firistoci zasu jera gunduwa-gunduwar nan, za su sa kan da fari sa'an nan kitsen a jere haka a kan itacen da ke bisa wutar da ke kan bagadi.9Amma kayan cikinsa da ƙafafuwansa dole ya wanke su da ruwa. Sa'an nan firist zai ƙona dukka a kan bagadi a matsayin baiko na ƙonawa. Zai ba da ƙamshi mai daɗi a gare ni; zai zama baikon da aka yi mani da wuta.10Idan baikonsa domin baiko na ƙonawa ne daga cikin garke, ɗaya daga cikin tumaki ko ɗaya daga cikin awaki, dole ya miƙa namiji marar lahani.11Dole ya yanka shi a arewacin bagadin a gaban Yahweh. 'Ya'yan Haruna maza, firistoci, zasu yayyafa jinin a kowanne gefen bagadin.12Sa'an nan dole zai yanka shi gunduwa-gunduwa, tare da kansa, da kuma kitsensa, firist zai jera su dai-dai akan itace da ke kan wuta, wadda take kan bagadi, amma kayan ciki da ƙafafun dole ya wanke su da ruwa.13Sa'an nan firist zai miƙa dukka, ya ƙona shi a kan bagadin. baiko na ƙonawa ne, zai bada ƙamshi mai daɗi ga Yahweh; zai zama baikon da aka yi masa da wuta.14Idan baikonsa ga Yahweh zai zama baiko na ƙonawa na tsuntsaye, to dole ya kawo baikon kurciya ko 'yar tantabara.15Dole firist ya kawo shi ga bagadi, ya murɗe kansa, ya ƙona shi a kan bagadin. Sa'an nan dole a tsiyaye jininsa a gefen bagadin.16Dole ya cire ƙururunsa da abin da ke cikinsa, ya jefar da shi a gabashin bagadin a gefe, wurin da ake zuba toka.17Dole ya tsaga shi biyu ya buɗe shi daga fukafukansa, amma ba zai raba shi biyu ba. Sa'an nan firist zai ƙona shi a kan bagadin, a kan itacen da ke kan wuta. Zai zama baiko na ƙonawa, kuma zai bada ƙamshi mai daɗi ga Yahweh; zai zama baiko da aka yi masa da wuta.
Wannan sunan na Allah ne wanda ya bayyana wa mutanen Tsohon Alkawali.
Yahweh ya fara magana da mutumin a nan. Maganan nan ya kare a sura ta 3:17. Za a iya juya wannan ba tare da magana a kan magana ba. AT: "daga cikin rufar taruwar ne ya kuma gaya wa Musa cewa ya gaya wa mutanen Isra'ila wannan: 'Idan mutum"
"Sa'ad da waninku" ko "Idan wanin ku"
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa abin da dole ne mutanen za su yi domin hadayar su ya zama abin ƙarbuwa ga Yahweh.
A nan, "sa" ko "shi" na nufin mutumin da yake kawo baiko wa Yahweh. AT: 1:1 "Idan baikon ka ... dole ka mika" (Dubi:|First, Second or Third Person)
AT: "Domin Yahweh ya karba" (Dubi:|Active or Passive)
Wannan kalmar aiki ne da ke nuna mutumin da dabban da zai mika. Ta yin haka ne mutumin ke mika kansa ta wurin dabban nan wa Yahweh, saboda Allah ya gafarce zunuban mutumin indan suka yanka dabban nan. (Dubi:|Symbolic Action)
AT: "sa'annan Yahweh zai karba ya kuma yafe zunuban sa" (Dubi:|Active or Passive)
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da abubuwan da mutanen za su yi.
A nan "ya" na nufin mutumin da ke kawo baikon. AT: "sa'annan dole ka yanka bijimin "
"A gaban Yahweh"
Na nufin cewa firist din zai ṭare jinin a kwano yayen da jinin na fita daga dabban. Sa'annan za su kawo daron tare da jinin a cikin ta su kuma mika ta wa Yahweh a bagadi.
Kammar yadda aka nuna a sura ta 1:9, dole ne mutumin ya wanke cikin kafaffu dabban da ruwa. Mutumin zai yi haka ne kafin ya mika su wa firistocin sa'annan su kuma ajiye sun akan bagadin.
A nan "shi" na nufin mutumin da ke kawo baikon
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da abubuwan da mutanen za su yi.
Wannan na iya nufin cewa firistocin sun ajiye gawayi masu zafi a kan bagadin sa'annan suka daura itace a kan gawayin. AT: "saka itace a kan bagadin in kuma ketta wuta"
Wannan ƙarin magana ne da ke nufin cigaba da saka itace a cikin wuta. AT: "domin wutar ya cigaba da ci"
Mutumin zai yi wannan kafin ya mika kyallen ga firist domin ya dora akan bagaden.kana iya furta wannan a karshen: 1:5.
Wannan ciki ne da kuma hanji.
A nan "shi" yana nufin wanda ya ke yin baikon.
Yahweh ya ji daɗin amincin mai sujadar ana furta shi anan cewa Yahweh ya ji daɗin ƙamshin haɗayar
Yahweh ya na magana da Musa cewa baye-bayen dole a ƙona su da wuta, ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT: " haɗaya ta ƙonawa domina"
Yahweh ya cigaba a gaya wa Musa game da abin ya zama dole ne mutanen zasu yi.
"A gaban Yahweh"
Yahweh ya cigaba a gaya wa Musa game da abin ya zama dole ne mutanen zasu yi.
AT: 1:7.
AT: 1:5-6 "Sa'annan dole ku yanka shi"
"Sa'annan firist din zan ƙona komai da ke kan bagadin"
A nan a na magana game da cewa Yahweh yana gamsuwa da mai sujadar gaskiya da yake kuma mika haɗaya kamar Allah ya gamsu ne da ƙamshin haɗayar da aka ƙona. AT: 1:7
Yahweh ya gaya wa Musa cewa ya zama dole ne firist din ya ƙona baikon su da wuta. AT: " zai zama baiko da aka ƙona mani ne" ko "zai zama baikon da aka ƙona wa Yahweh ne"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da ya zama dole ne mutanen zasu yi,
"Murɗe kansa"
AT: "Sa'annan dole ne firist din ya tsiyaye jininsa"
"Dole ne firist din zai"
Ƙururu wata abi ce kamar 'yar jaka a maƙogoron tsuntsu, inda abincin da bai rigaya ya narke ba ke tsayawa.
"Shi" a nan na nufin ƙururu da kuna jakar ta ne.
AT: 1:12-13 ko 1:7
AT: 1:12-13
1Sa'ad da wani ya kawo baikon hatsi ga Yahweh, dole ne baikonsa ya zama na gari mai laushi, kuma ya zuba mai a kai ya sa turare a kai.2Zai kai baikon ga 'ya'yan Haruna maza firistoci, a can firist zai ɗibi tafi guda na garin mai laushi tare da mai da turare da ke kansa. Sa'an nan firist zai ƙona baikon a kan bagadin baiko na tunawa kenan. Zai ba da ƙamshi mai daɗi ga Yahweh; zai zama baikon da aka yi masa da wuta.3Duk ragowar baiko na garin hatsi zai zama rabon Haruna da 'ya'yansa maza. Mafi tsarki ne sosai ga Yahweh domin daga baye-baye ne da aka yi wa Yahweh da wuta.4Sa'ad da kuka miƙa baiko na garin hatsi da babu gami da aka toya a tanda, dole ya zama waina mai laushi da aka yi da lallausar gari cuɗe da mai, ko waina mai tauri da bata da gami, da aka yayyafa mata mai.5Idan baikonku na garin hatsi an toya shi a tandar ƙarfe ne, dole ya zama gari mai laushi marar gami cuɗaɗɗe da mai.6Za ku yanyanka shi gunduwa-gunduwa a zuba mai a kai. Wannan shi ne baiko na hatsi.7Idan baikonku na garin hatsi an dafa a tukunyar tuya ne, dole a yi shi da gari mai laushi da mai.8Dole ku kawo baiko na garin hatsi da aka yi su daga waɗannan abubuwa ga Yahweh, za a kuma miƙa su ga firist, wanda zai kawo su wurin bagadi.9Sa'an nan firist zai ɗauki wasu daga baiko na garin hatsin domin ya zama baikon madadi, zai kuma ƙona su a kan bagadin. Zai zama baikon da aka yi da wuta, zai bada ƙamshi mai daɗi ga Yahweh.10Ragowar baikon garin hatsi zai zama na Haruna da 'ya'yansa maza. Abu ne mafi tsarki ga Yahweh daga cikin baye-baye da aka yi ga Yahweh da wuta.11Kada baiko na garin hatsi da za ku miƙa wa Yahweh ya zama da gami, gama ba za ku ƙona gami ba, ko zuma, a baikon da aka yi da wuta ga Yahweh.12Za ku miƙa su ga Yahweh a madadin baikon nunar fari, amma ba za a yi amfani da su don su bada ƙamshi mai daɗi a kan bagadi ba.13Dole kowanne baye-bayenku na garin hatsi a sa masa ɗanɗanon gishiri. Kada ku fasa sa gishiri na alƙawari na Allahnku a cikin baikonku na garin hatsi. Cikin dukkan baye-bayenku dole ku miƙa gishiri.14Idan kuka miƙa baikon hatsin nunar fari ga Yahweh, ku miƙa sabon hatsi wanda aka gasa da wuta sa'an nan aka ɓarza,15Sai ku sa mai da turare a kai. Wannan shi ne baiko na garin hatsi.16Sa'an nan firist zai ƙona wasu daga cikin ɓarzajjen hatsin da mai da turare sun zama baiko na madadi. Wannan baiko ne da aka yi da wuta ga Yahweh.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da ya zama dole ne mutanen zasu yi.
"Ya zama gari mafi kyau"
Gari da aka yi da alkama
"Ya zama dole ya kai"
"Ya ɗibi abin da zai iya rikewa a hannuwarsa"
Hatsi da aka ɗiba na nuna gabadayar hatsin da aka mika. Wannan na nufin cewa hatsin gabadaya na Yahweh ne.
AT: 1:7
AT: "zai zama baikon da aka kona ne wa Yahweh"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da ya zama dole mutane da kuma firist za su yi domin baikon su ya zama ƙarɓɓaɓe garesa.
AT: "da kuka toya ta a cikin tanda"
Mai yiwuwa wannan murhu ne da aka gina da laka. Wuta na ci a ƙarkashi tandan, sai kuma zafin wutar zai toya kullun da ke cikin tandar.
An iya gane cewa babu yisti a cikin waina mai laushi.
AT: da mai a kan wainan"
AT: "Idan kun toya baikonku na garin hatsi a tandar ƙarfe"
Wannan kwano ne mai ƙauri da aka gyara ta da laka ko ƙarfe. Ana iza kwanon a wuta, sa'annan kullun zai dafu a bisa kwanon.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da ya zama dole mutane da kuma firist za su yi domin baikon su ya zama ƙarɓɓaɓe garesa.
A nan "shi" na nufin baikon hatsin da aka dafa shi a kwano na ƙarfe.
AT: Idan kun dafa baikon ku na kwayar hatsi"
Tukunya kwano ne na ƙarfe. A na daura ƙunllun ne a kwanon a kuma dafa shi a wuta.
AT: "dole ne ku yi shi"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da ya zama dole mutane da kuma firist za su yi domin baikon su ya zama ƙarɓɓaɓe garesa.
AT: "da kuka yi da garin da kuma main"
AT: "zaku mika su"
AT: 2:1-10
AT: 1:7
AT:daga cikin baye-baye da aka ƙona ga Yahweh
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da ya zama dole mutane da kuma firist za su yi domin baikon su ya zama ƙarɓɓaɓe garesa.
AT: "kada ku yi amfani da yisti a baikon ku na garin hatsi da zaku mika wa Yahweh"
AT: "baikon da aka ƙona"
"Zaku mika baikon hatsin da aka yi da gami da kuma zuma"
AT: "ba za ku yi amfani da su don su bada ƙamshi mai daɗi a kan bagadi ba" ko "ba za ku ƙona su a kan bagadin ba"
Ana nufin cewa gishirin alama ce da ke nuna alƙawarin da Allah
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da ya zama dole mutane da kuma firist za su yi domin baikon su ya zama ƙarɓɓaɓe garesa.
AT: "da kuka dafa a kan wuta, sa'anan kuma kuka ɓarza"
AT: 2:1.
AT: "Wannan baiko ne da aka ƙona da wuta wa Yahweh"
1Idan wani ya miƙa hadayarsa wanda baiko ne na zumunta na dabba daga garken shanu, ko namiji ko mace, dole ya miƙa dabbar da ba ta da lahani a gaban Yahweh.2Zai ɗibiya hannusa a kan baikonsa ya yanka ta a ƙofar rumfar taruwa. Sa'an nan 'ya'yan Haruna maza firistoci zasu yayyafa jinin kewaye da bagadin.3Mutumin zai miƙa hadayar baiko na zumunta da wuta ga Yahweh. Ƙitsen da ya rufe ko kuma da ke haɗe da kayan ciki,4da ƙodoji biyu, da ƙitsen da ya ke kansu a wajen kwiɓi, da na taiɓar hanta, tare da ƙodoji - zai cire dukkan waɗannan.5'Ya'yan Haruna maza zasu ƙona wannan a kan bagadi tare da baiko na ƙonawa, wanda ya ke a kan itacen da ya ke kan wuta. Wannan zai bada ƙamshi mai daɗi ga Yahweh; zai zama baikon da aka yi masa da wuta.6Idan hadayar mutumin baikon zumunta ne ga Yahweh daga cikin garken tumaki; namiji ko mace, dole ya miƙa hadaya marar lahani.7Idan ya miƙa ɗan rago domin hadaya, to dole ya miƙa shi a gaban Yahweh.8Zai ɗibiya hannunsa a kan hadayar ya yanka shi a gaban rumfar taruwa. Sa'an nan 'ya'yan Haruna maza zasu yayyafa jinin kewaye da bagadin.9Mutumin zai miƙa hadayar baye-bayen zumunta domin baiko da aka yi da wuta ga Yahweh. Kitsen, dukkan kitse na wajen wutsiya da aka yanke kusa da ƙashin baya, da kitsen da ya rufe kayan ciki da dukkan kitsen da ke kusa da kayan ciki,10da kuma ƙodojin biyu da kitsen da ke tare da su, wanda ke kusa da kwiɓi, da na taiɓar hanta, tare da ƙodoji - zai cire duk waɗannan.11Sa'an nan firist zai ƙona su dukka a kan bagadi ya zama baiko na ƙonawa na abinci ga Yahweh.12Idan baikon mutumin akuya ce, to zai miƙa ta a gaban Yahweh.13Dole ya ɗibiya hannunsa a kan akuyar ya yanka ta a gaban rumfar taruwa. Sa'an nan 'ya'yan Haruna maza za su yayyafa jinin kewaye da bagadi.14Mutumin zai miƙa hadayarsa da ya yi da wuta ga Yahweh. Zai cire kitsen da ya rufe kayan ciki, da kuma dukkan kitsen da ke kusa da kayan cikin.15Zai kuma cire ƙodojin biyu da kitsen da ke tare da su, wanda ke wajen kwiɓi, da wajen taiɓar hanta tare da ƙodoji.16Firist zai ƙona dukkan waɗannan a kan bagadi ya zama baiko na ƙonawa na abinci, da zai bada ƙamshi mai daɗi. Duk kitsen ya zama na Yahweh.17Zai zama madawwamin farilla ga dukkan tsararrakin jama'arku a ko'ina da kowanne wuri da kuka maida shi mazauninku, cewa ba za ku ci kitse ba ko jini.'"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen game da abin da Allah yake so suyi.
"A gaban Yahweh" ko "wa Yahweh"
AT: 1:3
A na nufin cewa kafin nan su yafa jinin, zasu tare jinin a kwano yayyen da suke tsiyaye jinin daga dabban.
Wannan ciki ne da kuma hanji.
Ana samun wannan sashi na jiki a gefen ƙashin baya, yana tsakannin haƙarƙari ne da kashin kwankwaso.
Wannan ce lankwasa ko zagaya ta hanta.wannan ake ɗauka mafi kyaun ɓangaren hanta.
Yahweh yana jin dadin yarda da bawan da yake ba da sadaka da haɗaya,amma Allah yana jin dadin ƙonawar hadayar ta ƙonawa.Duba yadda aka juya wannan a 1:7
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki.AT:'haɗaya ce ta ƙonawa ga Yahweh'
'Mika ta a gaban Yahweh' ko 'mika wa Yahweh'
Wannan hadayar alama ce domin gane mutumin da ke miƙa dabbar domin haɗaya.Ta haka mutumin ke miƙa kansa ga Yahweh ta wurin dabbar.
Ya nuna cewa kamin su watsa jinin,zasu riƙe jinin cikin ƙoƙon yayinda yake tsiyayewa daga dabbar.
Ana iya fadin wannan a fasalin aiki.AT:'kamar haɗaya ta ƙonawa'
Faɗan nan,zai cire dukan wannan,za a iya sa shi a farkon nassin.AT:'zai cire dukan kitsen,dukkan kitsen...da kodar'
Wannan shine tumbi da kuma hanji
Ana iya fara sabuwar nassi a nan.AT:'wanda ke kusa da kayan ciki.Dole ya cire ƙodar
Wannan shine lankwasa ko zagayayyar gefen ƙoda.'wannan ne kashi mafi kyau na ci a ƙoda'
Ka juya shi a hayar da zai nuna a fili Yahweh baya cin wannan abincin.AT:'za a ƙona wadanan abubuwan akan bagade kamar haɗaya ga Yahweh.Wadannan abubuwan zasu fito ne daga yalwar abincin ku(UDB)
'A gaban Yahweh' ko 'ga Yahweh'
Wannan aikin,alama ce ta gane mutumin da ke da dabbar domin haɗaya.Ta haka mutumin na mika kansa haɗaya ga yahweh ta wurin dabbar.duba yadda za a juya wannan a 1:3
Wannan na nuna kamim su yayyafa jinin zasu kama ƙoƙon jinin yayinda yake tsiyayewa daga dabbar.
Wannan ana iya furta shi ckin yanayin aiki.AT:'zai mika hadayar sa da wuta' ko 'zai ƙona hadayar sa'
Anan, "shi" ana nufin mutumin dake mika hadayar
Juya wannan yadda zai nuna Yahwah ba shi ne ke cin abincin ba.AT:"zai kone komi kan bagaden hadaya ga Yahweh.Zai zama kamar abinci da ka ba wa Yahweh"(UDB)
Yahweh na farinciki da shesheki mai kamshi ta nama idan yana farinciki da amincin mai sujadar.Duba yadda za a juya wannan a 1:7.
Wannnan na nufin su da tsararrakin su dole su yi biyayya da umurnan nan har abada
"ko cin jini"
1Yahweh ya yi wa Musa magana, ya ce,2"Ka gaya wa mutanen Isra'ila, 'Lokacin da wani ya yi zunubi ba da niyyar yin zunubi ba, ya yi wani abu daga cikin abubuwan da Yahweh ya dokata kada a yi, idan ya yi abin da aka hana, ga abin da dole za a yi.3Idan babban firist ne ya yi zunubin har ya kawo laifi a kan jama'a, domin zunubinsa da ya aikata sai ya miƙa ɗan maraƙi marar lahani ga Yahweh baiko don zunubi kenan.4Dole ya kawo bijimin ƙofar rumfar taruwa a gaban Yahweh, ya ɗibiya hannunsa a kansa, ya yanka shi a gaban Yahweh.5Keɓaɓɓen firist zai ɗiba daga jinin bijimin ya kai rumfar taruwa.6Firist zai tsoma ɗan yatsansa cikin jinin ya yayyafa shi sau bakwai a gaban Yahweh, a gaban labulen wuri mafi tsarki.7Sa'an nan firist zai sa daga jinin a ƙahonnin bagadin na turare mai ƙamshi a gaban Yahweh, wanda ya ke cikin rumfar taruwa, zai kuma zuba dukkan sauran jinin bijimin a gindin bagadi domin baye-baye na ƙonawa, wanda ya ke a ƙofar rumfar taruwa.8Zai yaɗe dukkan kitsen bijimin baiko don zunubi; kitsen da ya rufe kayan ciki, da dukkan kitsen da ke manne da kayan ciki,9da ƙodojin biyu da kitsen da ke bisansu, wanda ke wajen kwiɓi, da taiɓar hanta, tare da ƙodoji - zai yanke duk wannan.10Zai yanke shi dukka, kamar yadda ya yanke shi daga bijimi na hadayar baye-baye ta salama. Sa'an nan firist zai ƙona waɗannan ɓangare akan bagadin baye-bayen ƙonawa.11Fatar bijimin da duk sauran naman, da kan da ƙafafunsa da kayan cikinsa da kashinsa,12da dukkan sauran sashen bijimin - zai ɗauki dukkan waɗannan ya kai bayan sansani wurin da aka tsarkake domina, inda ake zuba toka; zasu ƙona waɗannan a bisa itace. Dole su ƙona waɗannan ragowar bijimin inda suke zubar da toka.13Idan dukkan taron Isra'ila suka yi zunubin da ba na ganganci ba, kuma taron ba su san sun yi zunubi ba idan suka yi wani abu daga cikin abubuwan da Yahweh ya umarta kada su yi, idan sunyi laifin,14sa'annan, yayin da zunubin da suka aikata ya zama sananne, dole taron su miƙa ɗan bijimi baiko wato baiko don zunubi a kuma kawo shi gaban rumfar taruwa.15Dattawan taro zasu ɗibiya hannuwansu a bisa kan bijimin a gaban Yahweh, za a yanka bijimin a gaban Yahweh.16Keɓaɓɓen firist zai kawo daga jinin bijimin zuwa rumfar taruwa,17firist kuma zai tsoma yatsansa cikin jinin ya yayyafa shi sau bakwai a gaban Yahweh, a gaban labule.18Zai sa daga jinin a ƙahonnin bagadin da ke gaban Yahweh, wanda ya ke cikin rumfar taruwa, zai kuma zuba jinin dukka a gindin bagadin baye-baye na ƙonawa, wanda ya ke a kofar rumfar taruwa.19Zai ɗebe dukkan ƙitsen daga gare shi ya ƙona a kan bagadi.20Wannan shi ne abin da zai yi dole da bijimin. Kamar yadda ya yi da bijimin baiko don zunubi, haka kuma zai yi da wannan bijimin, firist kuma zai yi kaffara domin mutane, za a kuma gafarta masu.21Zai ɗauki bijimin ya kai shi bayan zango ya ƙona kamar yadda ya ƙona bijimi na farko. Wannan shi ne baiko don zunubi saboda taron.22Sa'ad da shugaba ya yi zunubi ba dagangan ba, har ya yi ɗaya daga cikin dukkan abubuwan da Yahweh Allahnsa ya umarta ka da a yi, kuma ya yi laifin,23sai aka sanar da shi a kan zunubin da ya aikata, dole ya kawo hadayarsa ta akuya, bunsuru marar lahani.24Zai ɗibiya hannunsa a kan bunsurun ya yanka shi inda aka yanka baiko na ƙonawa a gaban Yahweh. Wannan shi ne baiko domin zunubi.25Firist zai tsoma ɗan yatsansa cikin jinin baiko domin zununbi ya sa shi a ƙahonnin bagadin domin baye-baye na ƙonawa, sai ya kuma zuba jinin a gindin bagadin baiko na ƙonawa.26Zai ƙona dukkan kitsen a kan bagadi, dai-dai kamar na kitsen hadayar baye-baye na salama. Firist zai yi kafara domin shugaban game da zunubinsa, za a kuwa gafarta wa shugaban nan.27Idan wani talaka ya yi zunubi ba dagangan ba, sai ya yi wani abu daga cikin abubuwan da Yahweh ya umarta kada a yi, idan ya gane laifinsa,28sa'an nan za a bayyana masa zunubinsa, sai ya kawo akuya domin hadayarsa, ta mace marar lahani, domin zunubin da ya aikata.29Zai ɗibiya hannunsa a kan baiko domin zunubi ya kashe baikon don zunubin a wurin yin baiko na ƙonawa.30Firist zai lakuto daga jinin a yatsansa ya sa a ƙahonnin bagadi domin baye-baye na ƙonawa. Zai zuba dukkan sauran jinin a gindin bagadin.31Zai yaɗe dukkan kitsen, dai-dai kamar yadda ya yaɗe kitsen da ke kan hadayar baye-baye na salama. Firist zai ƙona su a kan bagadi domin ya bada ƙamshi mai daɗi ga Yahweh. Firist zai yi kaffara domin mutumin, za a kuwa gafarta masa.32Idan mutumin ya kawo ɗan rago domin hadayarsa ta baiko domin zunubi, zai kawo mace marar lahani.33Zai ɗibiya hannunsa a kan baiko domin zunubi sai kuma a yanka ta saboda baiko domin zunubi a inda aka yanka baiko na ƙonawa.34Firist zai ɗiba daga jinin baiko domin zunubi a ɗan yatsansa yasa su a kan ƙahonnin bagadi domin baye-baye na ƙonawa, zai zuba dukkan jinin a gindin bagadi.35Zai yaɗe dukkan kitsen, kamar yadda aka yaɗe kitsen ɗan rago daga hadayar baye-bayen salama, firist zai ƙona shi a kan bagadi a bisa baye-bayen Yahweh da aka yi da wuta. Firist zai yi kaffara saboda shi domin zunubin da ya aikata, za a kuwa gafarta wa mutumin.
Wannan na da nassi a cikin wani nassin.Nassi na kai tsaye za iya fadinsa kai tsaye.AT:"Yahweh yayi magana da musa ya kuma gaya masa ya gaya wa mutanen Isa'illa cewa:Lokacin da wani yayi zunubi"
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatau.AT:"wato,Yahweh ya dokaci mutane kada su yi"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatau.AT:"Idan yayi anin da Yahweh ya hana"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatau.AT:"he must do the following"
Bayanin dake a dunƙule,na iya zama a bayyane.AT:Domin zama sanadin laifi ga mutane.
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa abinda mutanen za su yi
"Babban firist dole ya kawo bijimi"
Wannan alama ce ta nuna mutumin da dabbar da yake miƙawa.Ta haka mutumin na miƙa kansa wurin yahweh ta wurin dabbar.Duba yadda ka juya wannan a 1:3.
Wannan ya nuna cewa firist zai kama jinin a ƙoƙon sa'ad da jinin ke tsiyayewa daga dabbar.
"Ɗiga kaɗan" ko "warwatsa kaɗan"
Wannan na nufin kusuryoyin bagaden.Suna da siffar ƙahon bijimi.AT:"doron da ke kusuryoyin bagaden"(UDB)
"Zuba duka sauran jinin"
"A kalkashin bagaden"
"Firist zai yaɗe dukkan"
Wannan furcin"zai yaɗe dukkan"na iya zama a farkon kalmomin.AT:zai yaɗe dukkan kitsen da ya rufe kayan ciki...da ƙodojin"
Wannan furcin"zai yanke duka".AT:"zai yanke dukkan kitsen da ya rufe kayan ciki...da ƙodojin"
Wannan tumbi ne da hanji
Wannan gaɓan jiki ne na gefen ƙashin baya da ke tsakanin haƙarƙari da ƙashin cinya
Wannan ne lanƙwasa ko zagaya na hanta.wannan shine gaɓa mafi kyau na ci.AT:"Gaɓa mafi kyau na hanta
Wannan furcin:"zai ɗauki dukkan gaɓoɓin"na iya zama a farkon kalmomin.AT:"Firist zai ɗauki fatar...gaɓoɓin bijimim waje"
Wurin da kulayaumi ke a tsarkake da ya dace domin bautar Ubangiji ana fadin sa kamar tsabtatacce a fili.(Duba:figa_metaphor)
A nan "su" na nufin firistoci, da "ni" na nufin Yahweh.
"Bai sani ba"
Ana iya fadin wannan a yanayin aikatau.AT:"ka dokace su kada su yi
"Kuma sun yi laifin" ko "kuma ya kamata Allah ya hukunta su
Ana iya fadin wannan a yanayin aikatau.AT:"Idan sun gane sun yi zunubi"
Wannan alama ce da ta bayyana mutanen da dabbobin da suke mikawa.ta haka mutanen suna mika kansu ga Yahweh ta wurin dabbar.duba yadda ka juya irin wannan nassin a 1:3.
Ana iya furta wannan a yanayin aikatau.AT"kuma za su yanka bijimin"
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa abinda dole mutanen za su yi
Ya na nufin firist ya kama jinin daga ƙoƙon yayinda jinin ke tsiyayewa daga bijimin.
Wannan na nufin wannan ne labulen da ke a gaban wuri maitsarki.
"Firist zai sa"
Wannan na nufin gindin bagaden.an sifanta su kamar kaho na bijimi.duba yadda ka juya a 4:6
"Zai watsa sauran jinin"
"Dukkan kitsen daga bijimin zai ƙona kitsen"
"Dole firist ya yi"
Ana iya furta kalman "kaffara"a cikin yanayin aikatau.AT:"shi firist zai yi kaffara domin zunubin mutane"
Ana iya furta wannan a cikin yanayi na aikatau.AT:"Yahweh zai gafarta masu"
Ana iya furta wannan cikin yanayin na aikatau.AT:"Yahweh Allah ya umurta wa mutane kada su yi"
Ana iya furta wannan a cikin yanayi na aikatau.AT:"sai ya gane ya yi zunubi"
"Mai mulkin zai ɗibiya"
Wannan alama ce da ke nuna mutumin da ke da dabbar domin miƙawa.Ta haka mutumin na miƙa kansa ga yahweh ta wurin dabbar.Duba yadda ka juya a 1:3
"Inda firist ya yanka"
"A gaban Yahweh" ko "ga Yahweh"
Yana nuna shi firist zai tsoma yatsar sa cikin jinin da ke a ƙoƙon yayin da jinin ke tsiyayewa daga bunsurun.
Wannan na nufin gindin bagaden.An sifanta su kamar ƙahon bijimi.Duba yadda ka juya wannan a 4:6
"Firist zai kona"
Wannan kalman "kaffara" ana iya furta shi cikin yanayi na aikatau.AT:"Firist zai yi kaffara domin shugaba"
Ana iya furta wannan a ckin yanayi na aikatau.AT:"Yahweh zai gafarta zunubin shugaba"
Dukkan mutanaen Isra'ila an umurce da ka da su yi zunubi.Ana iya furta wannan a cikin yanayi na aikatau.AT:"Yahweh ya umurci mutanen kada su yi
Ana iya fadin wannan cikin yanayi na aikatau.AT:"ya gane yayi zunubi"
Wannan alama ce da ke nuna mutumin da dabbar da ya ke miƙawa.ta haka mutumin na mika kansa ga yahweh ta wurin dabbar.Duba yadda ka juya a 1:3.
Wannan na nufin firist zai lakuto jinin daga ƙoƙon yayin da jinin ke tsiyayewa daga dabbar.
Wannan na nufin gindin bagaden,wanda ke da siffar kahon bijimi.Duba yadda ka juya shi a 4:6
"Ɗukkan jinin da ya rage a ƙoƙon"
A nan "zai" na nufin mutum wanda ke ba da haɗayar
Ana iya furta wannan a yanayin Aikatau.AT:"kammar yadda mutumin ke yaɗe kitsen"
"Zai ƙona kitsen"
Yahweh cikin murna da amincin mai miƙa hadayar ana fadin shi kamar Allah na murna da ƙamshin hadayar ta konawa.Duba yadda ka juya wannan a 1:7
Wannan kalman "kaffara" ana iya furta shi kamar aikatau.AT:"Firist zai yi kaffara domin zunuban mutumin"
Ana iya furta wannan a yanayi na aikatau.AT:"Yahweh zai gafarta zunuban mutumin"
Wannan alama ce da ke nuna mutumin da dabbar da yake miƙawa.Ta haka mutumin yana miƙa kansa ga Yahweh ta wurin dabbar.Duba yadda ka juya wannan a 1:3
"Inda firist ya yanka"
Wannan na nufin ƙahonnin bagaden.An sifanta su kamar ƙahon bijimi.Duba yadda ka juya wannan a 4:6.
"Zai zuba sauran jinin"
A nan "zai"na nufin mutumin mai miƙa haɗayar
Ana iya furta wannan a yanayi na aikatau.AT:"kamar yadda mutum ke yaɗe kitsen ragon"
"Firist zai ƙona kitsen"
Ana iya furta wannan a yanayi na aikatau:AT:"hadaya ta konawa ta Yahweh"
Kalman na kaffara ana iya furta shi a yanayi na aikatau.AT:"zai yi kaffara domin zunubin da ya yi"
Ana iya furta wannan a yanayi na ailkatau.AT:"Yahweh zai gafarta zunuban da mutumin yayi"
1Idan wani ya yi zunubi domin bai bada shaida ba sa'ad da ya ga wani abu game da abin da yakamata ya yi shaida, ko ya gani, ko kuwa yaji akan abin, za a kama shi da laifi.2Ko wani ya taɓa wani abin da Allah ya haramta shi marar tsarki, ko mushen haramtacciyar dabbar jeji ko ta gida da ta mutu, ko dabba mai rarrafe, ko da mutumin bai yi niyyar taɓa ta ba, ya ƙazamtu, ya kuma zama da laifi.3Ko kuma idan ya taɓa ƙazamtar wani mutum, ko ma mene ne ƙazamtar, idan har bai sani ba, zai zama da laifi bayan an sanar da shi.4Ko kuma wani ya yi rantsuwa da garaje da bakinsa zai yi mugunta, ko ya yi nagari, ko mene ne mutum ya rantse da garaje, ko ma dai da rashin saninsa, idan an sanar da shi, zai zama da laifi a cikin abubuwan nan.5Idan wani yana da laifi ko da guda ɗaya ne daga cikin waɗannan abubuwa, dole ya furta kowanne zunubi da ya aikata.6Dole ya kawo wa Yahweh baiko na laifi domin zunubin da ya aikata, dabba mace daga cikin garke ko ɗan rago ko akuya, domin baiko na zunubi, firist kuma zai yi kaffara dominsa game da zunubinsa.7Idan ba zai iya sayan ɗan rago ba, sai ya kawo baikonsa na laifi domin zunubinsa kurciyoyi biyu ko 'yan tantabarai biyu ga Yahweh, ɗaya domin baiko na laifi ɗaya kuma domin baiko na ƙonawa.8Dole ya kawo su ga firist, wanda zai miƙa ɗaya domin baiko domin zunubi da fari - zai murɗe kan daga wuya amma ba zai cire shi ɗungum daga jikinsa ba.9Sa'an nan zai yayyafa kaɗan daga cikin jinin baikon domin zunubi a gefen bagadi, sauran jinin zai tsiyayar a gindin bagadi. Wannan shi ne baiko domin zunubi.10Sa'an nan dole ya miƙa tsuntsu na biyu domin baiko na ƙonawa, kamar yadda aka bayyana a cikin farillai, sai firist kuma ya yi masa kaffara domin zunubin da ya aikata, za a kuwa gafarta wa mutumin.11In kuwa ba zai iya sayan kurciyoyi biyu ko 'yan tantabarai biyu ba, sai dole ya kawo hadaya domin zunubinsa tiya biyu na gari mai laushi saboda baiko domin zunubi. Ba zai sa mai ko turare a kai ba, saboda baiko ne domin zunubi.12Dole ne ya kawo shi ga firist, firist kuma zai ɗiba dai-dai tafin hannu ya zama baiko domin tunawa Sa'an nan zai ƙona shi a kan bagadi, a bisa baye-baye da aka yi da wuta domin Yahweh. Wannan baiko domin zunubi kenan.13Firist zai yi kaffara domin kowanne zunubin da mutumin ya aikata, za a kuwa gafarta wa mutumin nan. Duk ragowa daga baikon zai zama rabon firist, kamar dai baiko na hatsi.'"14Sa'an nan Yahweh ya yi wa Musa magana, cewa,15"Idan wani ya yi zunubi ya aikata rashin aminci game da abubuwan da ke na Yahweh, amma ba dagangan ba, to dole ya kawo baiko domin laifi ga Yahweh. Wannan baiko dole ya zamana rago marar lahani daga garken tumaki; za a lisafta tamaninsa da ma'aunin azurfar - ma'auni na masujada - domin baiko na laifi.16Dole ya gamshi Yahweh domin abin da ya yi marar kyau game da abu mai tsarki, dole kuma ya ƙara kashi ɗaya cikin biyar a kai domin ya ba firist. Sa'an nan firist zai yi masa kafara da ragon baiko na laifi, za a kuwa gafarta wa mutumin nan.17Idan wani ya yi zunubi har ya yi wani abin da Yahweh ya bada doka kada a yi, idan ma bai ankara da yinsa ba, duk da haka ya yi laifi dole ne ya amsa laifinsa.18Dole ya kawo rago marar lahani daga cikin garke, dai-dai tamanin kuɗinsa a yanzu, domin baiko domin laifi ga firist. Sa'an nan firist zai yi masa kaffara game da zunubin da ya aikata, wanda ya yi da rashin sani, za a kuwa gafarta masa.19Baiko ne domin laifi, kuma hakika yana da laifi a gaban Yahweh."
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa abinda dole ya yi.
Dokokin Yahudawa da shugabanin su duka na buƙatar mutane su shaida, ko su shaidu ne ga laifi.Ana iya fadin wannan a yanayi na aikatau.AT:"Wani abinda alkali na bukatarsa ya yi shaida"
Wani abinda Allah ya bayyana shi haramtacce domin mutane su taɓa, ko su ci, ana faɗinsa ne kamar abin da ya ƙazamtu a fili
"Mushen"
Mutumin da ba shi da karɓuwa domin hidimar Allah ana faɗin sa ne kamar wanda ya ƙazamtu a fili.
Wannan kalman "Kazamta"ana iya furta shi a ƙarin bayani.AT:"idan ya taɓa wani abu da ke ƙazamtar da mutum"
Wani abu da Yahweh ya furta shi haramtacce domin a taɓa ko a ci ana furta shi haramtacce a fili.
"Har shi bai sani ba" ko "shi bai san da shi ba"
A nan "baki" na nufin mutum gabaki daya.AT:"idan wani yayi rantsuwa da garaje"
Wannan na nufin yin rantsuwa kan alƙawali batare da yin la'akari ba.Yana nuna bayan mutumin yayi rantsuwar wanda ba zai iya cika ta ba ko kuma ya ki ya aikata
Yahweh ya ci gaba da faɗa wa Musa abinda zai yi dole
Wannan ƙalman "kaffara" ana iya furta ta a yanayi na aikatau.AT:"firist zai yi kaffara domin shi"
"Idan bashi da isassan kudi domin sayan dan rago"
"Zai yanka shi ta murɗe kansa da kuma karya wuyarsa,amma ba zai cire kansa ba"
Ana iya furta wannan a yanayi na aikatawa.AT:"Kamar yadda Yahweh ya umurta"
Wannan kalman "Kaffara" ana iya furta shi a yanayi na aikatau.AT:"firist zai yi kaffara domin zunubin da mutumin ya aikata"
Ana iya furta wannan a yanayi na aikatawa.AT:"Yahweh zai gafarta wa mutumin"
tiya biyu dai dai yake da lita 22.tiya biyu na gari mai laushi misalin lita biyu ne,
Wannan kashi ɗaya ne cikin goma.
"dole ya kawo gari mai laushi"
dai-dai tafin hannunsa da firist firist ya ƙona wannan baiko ne domin dukkan mutane.Wannan na nufin baiko ne na Yahweh.Duba yadda aka juya a 2:1.
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatau.AT:"akan haɗaya ta ƙonawa domin Yahweh"
Wannan kalman kaffara ana iya furta shi a yanayi na aikatau.AT:"zai yi kaffara"
Ana iya fadin wannan kai tsaye.AT: "Yahweh zai gafarta zunubin mutumin"
Wannan ya na nufin mutumin yayi zunubi ta wurin rashin baiwa Yahweh abinda Yahweh ya umurta a bashi.AT:"Zunubi ta wurin rashin baiwa Yahweh abinda ke na Yahweh"
Aana iya furta wannan cikin yanayin aikatawa.AT:"dole ya auna shekel nawa dan ragon yake"
Wannan na nuna watakila akwai ma'auni biyu na shekel.wannan na nufin kwatanta yadda firist na masujadan ke auna shekel.AT:" ma'aunin gwaji yarjajje na masujada mai tsarki"(UDB)
Wannan wani suna ne na masujada mai tsarki
Ta biyar-wannan na nufin dole mutumin ya biya ƙari na biyar a yawan abinda Yahweh ke binsa.
Biyar-wannan na nufin kashi ɗaya cikin biyar,madaidaita.(Duba:translation_fraction)
Wannan kalman "kaffara"ana iya furta shi cikin yanayi na aikatau.AT:"Firist zai yi kaffara dominsa"
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"Yahweh zai gafarta wa mutumin".
Ana iya furta wannan a yanayi na aikatawa.AT:"ya umurta mutanen kada su yi"
Ana furta zunubin mutumin kamar wani kaya ne da mutumin ke dauke da shi.Anan kalman "laifi" yana nufin horo na laifin.AT:"hakkin laifinsa na kansa" ko kuma "Yahweh zai hore shi domin zunubinsa"
Wannan na nufin mutumin zai kwatanta yawan shekel da ya cancanci ɗan ragon da ma'auni na wurin sujada mai-tsarki.Duba5:14
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"Yahweh zai garfarta wa mutumin"
"Hakika yana da laifai agaban Yahweh"
1Yahweh ya yi wa Musa magana, cewa,2"Idan wani ya yi abin rashin aminci gãba da Yahweh ta wurin yaudarar makwabcinsa game da wani abin da aka bashi riƙon amana, ko game da wani abin da aka sace, ko dai ya yi ta zaluntar makwabcinsa,3ko ya tsinci abin da makwabcinsa ya ɓatar ya yi musu a kansa, ya kuma rantse a kan ƙaryar, ko duk dai cikin abubuwa makamantan haka da mutane ke zunubi,4idan ya zamana ya yi zunubi, har aka same shi mai laifi ne, dole ne ya mayar da abin da ya karɓe da ƙwace ko ta hanyar zalunci, ko ta ajiyar da aka bashi riƙon amana ko ta abin da ya ɓace ya kuma tsinta.5Bugu da ƙari, a cikin kowanne al'amari da ya rantse a kan karya, dole ya mayar cif yadda ya ke ya kuma ƙara kashi ɗaya cikin biyar na tamanin abin da ya biya dukka ga mai ita a ranar da aka kama shi da laifi.6Sa'an nan zai kawo wa Yahweh baiko na laifinsa, rãgo marar lahani daga cikin garke wanda tamaninsa haka ya ke a kasuwa, domin baiko na laifi ga firist.7Firist zai yi masa kaffara a gaban Yahweh, za a kuma gafarta masa game da duk wani laifi da ya yi."8Sa'an nan Yahweh ya yi wa Musa magana, cewa,9"Ka dokaci Haruna da 'ya'yansa maza, cewa, 'Wannan ita ce dokar baiko na ƙonawa: Dole baiko na ƙonawa ya kasance a kan garwashin wutar bagadi dukkan dare har safiya, kuma wutar bagadin za a dinga izata tayi ta ci.10Firist zai sanya rigunansa na lilin, zai kuma sa ƙananan kaya 'yan ciki na lilin. Zai kwashe tokar da ta rage bayan wuta ta cinye baiko na ƙonawa da ke kan bagadi, zai kuma sa tokar a gefen bagadin.11Zai tuɓe rigunansa ya sa wasu rigunan domin ya kai tokar bayan zango a wuri mai tsabta.12Wutar da ke kan bagadi za a dinga iza ta. Ba za a barta ta mutu ba, firist zai yi ta ƙona itace a kanta kowacce safiya. Zai shirya baiko na ƙonawa yadda ya kamata a bisansa, a kansa zai ƙona kitsen baye-baye na salama.13Dole a sa wuta ta yi ta ci a kan bagadin ba fasawa. Kada a bari ta mutu.14Wannan ita ce shari'a ta baiko na hatsi. 'Ya'yan Haruna maza zasu miƙa shi a gaban Yahweh a gaban bagadi.15Firist zai ɗibi tafin hannu na lallausar gari daga cikin baiko na garin hatsi da na mai da kuma turare wanda ya ke a kan baiko na garin hatsi, zai ƙona shi a kan bagadin domin ya bada ƙamshi mai daɗi domin baiko na madadi.16Haruna da 'ya'yansa maza zasu ci duk abin da ya rage daga baikon. Dole a ci shi ba gami a wuri mai tsarki. Za su ci shi a harabar rumfar taruwa.17Ba za a toya shi da gami ba. Na ba su wannan kason ya zama nasu rabon daga nawa baye-baye da aka yi mani da wuta. Abu ne mafi tsarki, kamar baiko domin zunubi da baiko domin laifi.18Domin dukkan lokatai masu zuwa dukkan tsararrakin mutanenku, kowanne ɗa namiji daga zuriyar Haruna zai iya cin rabonsa, daga baye-baye ga Yahweh da aka yi da wuta. Duk wanda ya taɓa su zai tsarkaka.'"19Sai Yahweh ya sake yin magana da Musa, cewa,20"Wannan shi ne baikon Haruna da 'ya'yansa maza, wanda zasu miƙa wa Yahweh a ranar da aka keɓe kowanne ɗa: kashi ɗaya cikin goma na garwar lallausar gari domin baiko na hatsi koyaushe, rabinsa da safe rabi kuma da maraice.21Za a yi shi da mai a kaskon tuya. Sa'ad da aka jiƙa shi, za ku kawo shi ciki. A toye curi-curi za ku miƙa baiko na garin hatsi domin ya bada ƙamshi mai daɗi ga Yahweh.22Ɗan babban firist wanda zai gaji babban firist daga cikin 'ya'yansa zai miƙa shi. Kamar yadda aka umarta har abada, za a ƙona shi dukka ga Yahweh.23Kowanne baiko na garin hatsi na firist za a ƙona shi ƙurmus. Ba za a ci shi ba."24Yahweh ya sake yin magana da Musa, cewa,25"Ka yi wa Haruna da 'ya'yansa maza magana, cewa, "Wannan ita ce dokar baiko domin zunubi: Dole a kashe baiko domin zunubi inda aka kashe baiko na ƙonawa a gaban Yahweh. Abu ne mafi tsarki.26Firist da ya miƙa shi don zunubi zai ci shi. Dole a ci shi a wuri mai tsarki a harabar rumfar taruwa.27Duk abin da ya taɓa naman zai zama da tsarki, kuma idan aka yayyafa jinin akan wata riga, dole ku wanke ta, wannan shashen da ya ɗiga a kai, a wuri mai tsarki.28Amma tukunyar yunɓun da aka dafata a ciki dole a fashe ta. Idan an dafa ne a tukunyar ƙarfe, dole ne a kankare ta a ɗauraye ta cikin ruwa mai tsabta.29Kowanne ɗa namiji daga cikin firistoci zai iya ci daga ciki domin mafi tsarki ne.30Amma kowanne baiko domin zunubi wanda aka kawo jininsa a rumfar taruwa domin a yi kaffara a wuri mai tsarki ba za a ci shi ba. Dole ne a ƙona shi.
"Karya ɗaya daga cikin dokokin Yahweh
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"yin karya akan abin da makwabcinsa ya bashi aro"
A nan "makwabci" ya na nufin bayahude,ba kowane mutumin dake zama a kusa ba
Ana iya furta wannan a yana yi na aikatawa.AT:"rashin mayar da abinda ya yi aro".
"Cike" ko "gabaki daya"
Ta biyar-wannan na nufin mutumin zai mayar da duk abinda ya ara ya kuma biya ƙari kashi ɗaya cikin biyar na abinda ya karba.Duba yadda ka juya wannan a 5:14.
Ana iya juya wannan a yanayi na aikatawa.AT:"ya biya mutumin da ya karɓi aro"
Mutumin da yayi sata za a kawo shi a gaban alkali wanda zai furta shi mai laifi.Ana iya fadin wannan a yanayi na aikatawa:"Alkalin zai furta shi mai laifi"
Wannan na nufin mutumin zai a'una dai dai tamanin ɗan ragon da ma'auni na masujada mai tsarki. Kana iya sa bayanin yadda za' a fahimta.duba yadda aka juya wannan a 5:14
Wannan kalman "kaffara"ana iya furta ta cikin yanayi na aikatau.AT: "Firist zai yi kaffara dominsa"
"A gaban Yahweh"
Wannan na nufin yahweh zai garatawa mutumin ba firist ba.Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"Allah zai gafarta masa"
Wannan na da furci cikin furci.furci na kai tsaye ana iya fadinsa kamar ba furci na kai tsaye ba ne.AT:" sai Yahweh yayi magana da Musa ya kuma ce masa ka umurci Haruna da ƴaƴansa maza cewa,"wannan shine dokar"
"Dole ya kasance a kan bagaden"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"dole a dinga iza wutar bagaden tayi ta ci"
Lilin farin tufafi ne.AT:"farin tufaffinsa"
"Zai kwashe tokar"
Ƙonawar wutar gaba daya na hadayar ana fadinsa ne kamar wutar ta cinye, ko an gama haɗayar ta ƙonawa
Wurin da ya dace ayi hidima ta ubangiji ana faɗinsa ne kamar wuri mai tsabta.
Ana iya juya wannan a yanayi na aikatawa.AT:"firist zai ci gaba da iza wutar bagaden"
Ana iya furta wannan a yanayi na aikatawa.AT:"a kansa kamar yadda Yahweh ke buƙata"
Yahweh ya yi farin ciki da baikon mai sujadar da ya miƙa baikon ana fadinsa ne kamar Allah na farin ciki da ƙamshin baikon.Duba yadda ka juya a 1:7.
Tafin hannu na laulausar gari nä kwatancin baikon hatsi.wannan ya na nufin dukkan baikon na Yahweh ne. Duba yadda ka juya a 2:1.
ana iya juya wannan a yanayi na aikatawa.AT"dole su ci"
ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"Ka da a toya shi da gami"
Ana iya furta wannan a yanayi na aikatawa.AT:"baiko ta ƙonawa"
Wannan kashedi ne ga duk wanda ba daga zuriyar Haruna maza ba, ka da su taɓa baikon.Cikakkiyar ma'anar na iya zama a bayyane.
Wannan ya na nuna za'a keɓe su idan sun zama firistoci.Cikkakiyar ma'anar na iya zama a baiyane.Ana iya furta wannan a yanayi na aikatawa.AT:"idan ya keɓe kowane ɗa,ya maishe su firistoci"
Ephah lita ashirin da biyu ne.kashi ɗaya bisa goma ya na daidai da lita biyu.
wannan kashi ɗaya ne na kashi goma dake daidai.
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"za a yi shi"
Wannan kasko ne mai kauri wanda aka yi da yumɓu ko karfe.An ɗora kaskon akan wuta,an toya wainar akan kaskon.duba yadda ka juya "kaskon karfe mai fadi" cikin 2:4
"Sa'ad da aka jiƙa gari mai laushi cikin mai"
A nan "za ku" na nufin mutumin da ke ba da baikon.
Yin farin cikin Yahweh da amincin mai yin sujadar wanda ya miƙa baikon ana faɗinsa kamar Ubangiji yayi murna da sheƙi mai-kamshi na baikon.duba yadda ka juya wannan a 1:7
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"kamar yadda yahweh ya umurta"
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"dole ya kona su duka"
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"Kada wani ya ci shi"
Akwai kalamai cikin kalamai.kalamai na kai tsaye ana iya faɗinsu kamar kalamai wanda ba na kai tsaye ba.AT:Yahweh ya yi magana da Musa kuma ya ce masa yi magana da Haruna da ƴaƴansa cewa,"wannnan itace dokar"
Yahweh ya na magana da Haruna da ƴaƴansa,amma wannan dokar ya shafi kowane firist wanda ke yin hidima da baiko.Cikkakaiyar ma'anar kalmomin na iya zama da fahimta sarai.
A bayyana shi a fili domin nuna cewa wannan yana nufin bangare na arewa na bagaden.Duba 1:10
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"Dole ne ka kashe baikon na haɗayar zunubi"
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"inda kuka kashe dabar domin haɗaya ta ƙonawa"
"Ga Yahweh"
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:" dole ne ya ci shi"
Wannan kashedi ne cewa babu wanda zai taɓa naman, na baikon zunubi sai dai firistoci.Cikakkiyar ma'anan ya na a baiyane.
Ana iya juya wannan a cikin yanayi na aikatawa.AT:"idan an yayyafa jinin a kan"
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa. AT:"dole a fase tukunyar yunbun wanda aka tafasa naman"
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:" idan an dafa ne da tukunyar ƙarfe,dole ne a kankare ta a ɗauraye ta cikin ruwa mai tsabta"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"ka da wani ya ci baikon na zunubi"
ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"daga cikin wanda ya ɗauki jinin cikin rufar taruwa"
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:" Dole ne firist ya ƙone shi"
1Wannan ita ce dokar baiko domin laifi. Mafi tsarki ne.2Dole a kashe baiko domin laifi a mayankarsa, dole kuma su yayyafa jininsa a kowanne gefen bagadi.3Dukkan kitsen da ke cikinsa za a miƙa shi: kitsen wutsiya, da kitsen da ke a kan kayan ciki,4da ƙodojin biyu da kitsen da ke bisan su, wanda ke kusa da kwiɓi, da wanda ya rufe hanta, tare da ƙodoji - duk wannan dole a cire su.5Dole firist ya ƙona waɗannan sassa a kan bagadin shi ne baikon da aka yi da wuta ga Yahweh. Wannan shi ne baiko domin laifi.6Kowanne namiji daga cikin fistoci zai iya ci daga wannan baikon. Dole ne a ci shi a wuri mai tsarki domin mafi tsarki ne.7Baiko domin zunubi kamar baiko domin laifi ya ke. Doka guda ce domin su biyun. Za su zama na firist wanda ya ke yin kaffara da su.8Firist wanda ya miƙa wa wani baikonsa na ƙonawa zai iya ɗaukar wa kansa fatar wannan baikon.9Kowanne baiko na garin hatsi da aka toya a cikin tanda, da kowanne makamancin baiko da aka dafa a tukunya ko a kaskon tuya zai zama na firist da ya miƙa baikon.10Kowanne baiko na garin hatsi, ko busasshe ko kwaɓaɓɓe da mai, za su zama rabon dukkan zuriyar Haruna dai-dai wa dai-da.11Wannan ita ce shari'ar hadayar baye-baye na salama wadda mutane za su miƙa ga Yahweh.12Idan wani ya miƙa shi domin ya yi godiya, to dole ya miƙa shi da hadayar waina da aka yi ba a sa gami ba, amma kwãɓe da mai, waina da aka yi ba gami, amma an shafa masu mai, waina da aka yi ta da lallausar gari da aka kwaɓa da mai.13Kuma domin dalilin miƙa godiya, dole ya miƙa baikonsa na salama tare da wainar gurasa da aka yita da gami.14Zai miƙa guda ɗaya na kowanne irin waɗannan hadayu ya zama baikon da aka miƙa ga Yahweh. Zai zama rabon firist wanda ya yayyafa jinin baye-baye na salama a kan bagadi.15Mutumin da ke miƙa baiko na salama domin nuna godiya dole ya ci naman baikonsa a ranar yin hadayar. Kada ya bar ragowar har kashegari da safe.16Amma idan hadayar baikonsa domin wa'adi ne, ko kuma domin bayarwar yardar rai, dole a ci naman a ranar da ya miƙa hadayar, amma duk abin da ya rage a ciki za a iya cinsa kashegari.17Amma, kowanne ragowar naman hadaya a rana ta uku dole a ƙone shi.18Idan aka ci naman hadayar wani na baikon salama a rana ta uku, ba za a karɓa ba, ba kuma za a lisafta shi ga mai miƙa wa ba. Zai zama abin ƙyama, kuma mutumin da ya ci shi zai ɗauki laifin zunubinsa.19Duk naman da ya taɓa abin da ba tsarki ba za a ci shi ba. Dole a ƙona shi. Game da sauran naman, duk wanda ya ke da tsarki zai iya cin shi.20Amma fa, mutum marar tsarki wanda ya ci wani nama daga hadayar baiko na salama wanda ya ke na Yahweh ne- wannan mutum dole a datse shi daga mutanensa.21Idan wani mutum ya taɓa wani abu marar tsarki - ko ƙazamtar mutum ne, ko na ƙazamin dabba, ko na wani abu marar tsarki na ban ƙyama, sa'an nan kuma ya ci daga naman hadayar baiko na salama wanda ya ke na Yahweh ne, wannan mutumin dole a datse shi daga mutanensa.'"22Sai Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,23"Yi magana da mutanen Isra'ila ka ce, 'Ba za ku ci kitsen sã ko na tunkiya ko na akuya ba.24Kitsen dabba mushe da ba a yi hadaya da ita ba, ko kitsen dabbar da namomin jeji suka yayyaga, za a iya yin amfani da su domin wani abu, amma kada ku kuskura ku ci su.25Ko wane ne ya ci kitsen dabbar da mutane zasu iya miƙa ta hadaya ta ƙonawa ga Yahweh, wannan mutumin dole a datse shi daga mutanensa.26Ba za ku ci jini ba daɗai a gidajenku, ko daga tsuntsu ya ke ko dabba.27Duk wanda ya ci jini, dole a datse wannan mutum daga mutanensa.'"28Sai Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,29"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce, 'Wanda duk ya ke miƙa hadayar baiko na salama ga Yahweh dole ya kawo wani sashen hadayar ga Yahweh.30Baiko domin Yahweh da za a yi da wuta, mai ita ne zai kawo da hannunsa. Dole ya kawo kitsen tare da ƙirjin, saboda a kaɗa ƙirjin ya zama baiko don kaɗawa a gaban Yahweh.31Dole ne firist ya ƙona kitsen a kan bagadi, amma ƙirjin zai zama na Haruna da zuriyarsa.32Dole a bada cinyar ƙafar dama ga firist a matsayin baikon da aka miƙa daga cikin hadayarku ta baye-baye na salama.33Firist, ɗaya daga cikin dangin Haruna, wanda ya miƙa jinin baye-baye na salama da kitsen - shi zai ɗauki cinyar ƙafar dama rabonsa kenan na baikon.34Gama na ɗauka daga mutanen Isra'ila, ƙirjin baiko na kaɗawa, da cinya su zama bayarwarsu, an rigaya an ba Haruna firist da 'ya'yansa maza waɗannan su zama rabonsu koyaushe.35Wannan ne rabon Haruna da zuriyarsa daga baye-bayen da aka yi wa Yahweh da wuta, a ranar da Musa ya miƙa su su yi wa Yahweh hidima a cikin aikin firist.36Wannan rabon ne da Yahweh ya umarta a ba su daga mutanen Isra'ila, a ranar da ya keɓe firistoci. Kullum zai zama rabonsu har dukkan tsararraki.37Wannan shi ne shari'ar baiko na ƙonawa, da baiko na hatsi, da baiko domin zunubi, da baiko domin laifi, da baiko na keɓewa, da na hadayar baye-baye na salama,38wanda Yahweh ya ba da umarnai ga Musa a kan Tsaunin Sinai a ranar da ya umarci mutanen Isra'ila su miƙa hadayunsu ga Yahweh a jejin Sinai.'"
Yahweh ya ci gaba da fada wa Musa abinda zai fadawa Haruna da yayansa
Ana iya bayyana shi cewa wannan ya na nufin wurin da dabbobin domin hadayar ake konawa. duba 1:10
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"dole ne firist ya mika duka kitsen"
Wannan tumbi ne da hanji
Juya wannan yadda ka juya 3:3.
Wannan gaɓan jiki ne kusa da ƙashin baya tsakanin haƙarƙari da ƙashin cinya. Duba yadda ka juya a 3:3
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"dole ne firist ya cire duka wannan"
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"Baikon konawa"
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"dole su ci shi"
"Dokar daya ce domin su biyun"
Ana iya furta wannan kalman "kaffara" cikin yanayi na aikatau:AT:" domin shi firist wanda ya mika hadaya ta kaffara domin zunuban wani"
Gashi ko fatar dabbar
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"Cewa wani ya yi tuya a tanda...wani yayi girki a kaskon tuya"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:" Wani ya yi tuya a tanda...wani yayi dahuwa a kaskon tuya"
Wannan kasko ne na karfe mai zagayeyyen gaɓa.An ɗora masar a kaskon tuya and dafa akan wuta.yadda ka juya "kaskon tuya" a 2:6.
Wannan kasko ne da aka yi da yunɓu ko karfe.an ɗora kaskon akan wuta,an toya wainar akan tandar.duba yadda ka juya "kaskon tuya buɗadɗe" a 2:4.
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"wainar da ba a sa gami ba amma an cura da mai".
A nan "waina" yana nufin gurasa mai kauri.
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:" wainar mara kauri da ya yi babu gami amma an shafe ta da mai".
anan "waina" ya na nufin gurasa mara kauri
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"wainar da yayi da gari mai laushi da aka cura da mai"
A nan "waina" ya na nufin gurasa mai kauri.kusan dai dai yake da na farko sai dai an yi wannan ne da gari mai kyau, mai laushi.
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:" waina ta gurasa da ka yi da gami".
Wannan ya na nufin gurasa mai kauri.
"Mutumin da ya miƙa"
Wannan kalman "godiya" ana iya furta ta a yanayi na aikatau:AT:" Domin nuna godiya ga Yahweh"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"dole ya ci namar...wataƙila ya ci namar"
Rana ta uku ƙayyadaden lamba ce ta uku.AT:"bayan kwana biyu"
Ana iya juya wannan cikin yanayi ta aikatawa.AT:"Mutumin dole ya ƙona shi"
Ana iya juya wannan cikin yanayi ta aikatawa.AT:"idan wani ya ci naman,naman baiko ta salama a rana ta uku"
Ana iya furta wannan a yanayi ta aikatawa.AT:"Yahweh ba zai karɓa ba"
Ana iya furta wannan cikin yanayi ta aikatawa.AT:"Yahweh ba zai girmama baikon da mutumin ya miƙa ba"
Ana magana ne game da mutumin da ya aikata zunubin kamar zai ɗauki nauyin zunubin ne a kansa a fili.
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"ka da wani ya ci naman da ya taɓa abu mara tsarki
Abin da Yahweh ya furta shi mara tsarki ko kuma, ka da a taɓa ko a ci a na fadar sa ne kamar abu mara tsarki ne a fili.
Ana iya juya wannan a yanayi na aikatawa.AT:"dole ne a ƙona shi"
Mutumin da ke karɓabɓe domin aikin Allah na fadar sa ne kamar wanda yake da tsarki a fili.
Mutumin da Allah bai karɓe shi ba, domin hidimarsa ana fadin sa ne kamar mutumin ba shi da tsarki a fili.
Mutumin da aka hukumta shi cikin alumma ana fidin sa ne kamar wanda aka datse,daga mutanensa,kamar yadda ake yanke tufafi, ko kuma ake datse reshen itace.Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"Wannan mutumin ba zai sake zama cikin mutanensa ba" ko "dole ne a ware shi daga cikin mutanensa"
Abin da Yahweh ya furta shi mara tsarki ka da a taba ko ka da aci ana fadar sa ne kamar marar taski ne a fili.
Anan "Mutum" ya na nufin muatane baki daya.AT:" ko na mutum ko dabba"
"Ko na wani abu na ban kyama ga Yahweh"
Mutumin da aka cire shi daga cikin al'ummar sa ana faɗar sa ne kamar wanda aka yanke shi daga cikin mutanen sa,kamar yadda ake yanke tufafi ko datse reshen itace.Ana iya juya wannan cikin yanayi ta aikatawa.Duba yadda ka juya a 7:19.
Wannan ya na da magana cikin magana.Magana na kai tsaye ana iya fadar sa kamar Magana da ba na kai-tsaye ba.AT: "Sai Yahweh ya yi magana da Musa ya ce ma sa, ka gaya wa yayan Israila wannan: "ka da ku ci kitse"
"Ya mutu ba a mika shi haɗaya ba"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT: " kitse na dabbar da namomin daji suka kashe"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT: "ana iya anfani da shi"
Ana iya furta wannan cikin yanayi na aikatawa.AT: "Hadaya ta Konawa"
Mutumin da aka datse shi daga al'ummar sa ana fadar sa ne kamar an datse shi daga mutanensa,kamar yadda ake yanke tufafi ko kuma datse reshen itace.Ana Iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.Duba yadda ka juya wannan cikin 7:19.
"Ba za ku ci jini ba"
"A gidajenku" ko "a duk in da ku ka zauna"
Wannan magana ce ta kai tsaye.Magana ta kai tsaye ana iya fadar ta kamar magana wanda ba ta kai tsaye ba.AT: "Sai Yahweh ya yi magana da Musa ya ce ka gaya wa mutanen Israila ka ce: "duk wanda ya mika"
Kalmomin nan " dole hannunsa ya kawo shi" ana iya sa shi a farkon maganar.Kalmomin nan " za a yi da wuta" ana iya fadar sa a yanayi na aikatawa.AT: "shi da kansa zai kawo baikon da ya shirya domin haɗaya ta ƙonawa ga Yahweh"
A nan "hannunsa" na nufin mutumin gaba ɗaya.AT: " dole ya kawo shi da kansa"
Bangaren jikin dabbar ta gaba,ƙarkashin wuyar sa
Ana iya juya wannan ckin yanayi na aikatawa.AT: " domin firist ya miƙa shi ga Yahweh haɗaya ta juyawa"
Miƙa haɗayar alama ce ta nuna mutumin yana miƙa haɗayar sa ga Yahweh.
Bangaren sama na ƙafa,sama da gwiwa
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT: " a kuma miƙa shi baiko"
A nan "Ni" ya na nufin Yahweh.
"Da aka bayar baiko"
Ana iya juya wannan cikin yanayi ta aikatawa.AT: " haɗayar ta ƙonawa domin Yahweh"
Ana iya furta wannan cikin yanayi ta aikatawa.AT: " Yahweh ya umarta a ba su daga mutanen isra'ila"
"Da Musa ya keɓe firistocin"
Juya wannan kalmomin kamar yadda ka juya 3:15
Wannan itace karshen maganar da aka fara a 7:28
1Yahweh ya yi magana da Musa, cewa'2"Ka ɗauki Haruna da 'ya'yansa maza tare da shi, da riguna, da man ƙeɓewa, da bijimi domin baiko na zunubi, da raguna biyu, da kwandon waina marar gami.3Ka tara dukkan taron a ƙofar rumfar taruwa."4Sai Musa ya yi yadda Yahweh ya umarce shi, dukkan taron suka tattaru a ƙofar rumfar taruwa.5Sai Musa ya cewa taron, "Ga abin da Yahweh ya umarta a yi."6Musa ya kawo Haruna da 'ya'yansa maza ya wanke su da ruwa.7Ya sa wa Haruna riga 'yarciki ya ɗaura masa ɗamara a ƙugunsa, ya sa masa taguwa ya kuma sa masa falmara, sa'an nan ya ɗaura masa falmarar da wata ƙasaitacciyar ɗamara mai kyan ɗinki ya zagaya ƙugunsa da ita ya ɗaure.8Ya sa masa ƙyallen ƙirji, a kan ƙyallen kuma ya sa Urim da Tumim.9Ya naɗa masa rawani a kansa, a kan rawanin, a goshi, ya kafa masa tasar zinariya, kambi mai tsarki, kamar yadda Yahweh ya umarce shi.10Musa ya ɗauki man ƙeɓewa, ya keɓe rumfar da dukkan abin da ke cikinta ya keɓe su ga Yahweh.11Ya yayyafa man a kan bagadi sau bakwai, ya shafe bagadin da dukkan kayan aikinta, da daron wanki da maɗorinta, saboda a keɓe su domin Yahweh.12Ya zuba wasu man keɓewa akan Haruna ya shafe shi don a keɓe shi.13Musa ya kawo 'ya'yan Haruna maza ya suturta su da su riguna 'yanciki. Ya ɗaura masu ɗamara kewaye da ƙugunsu ya ɗaura masu rawanin ƙyallen lilin a kawunansu, kamar yadda Yahweh ya umarce shi.14Musa ya kawo bijimin na baiko domin zunubi, sai Haruna da 'ya'yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan bijimin da suka kawo saboda baiko domin zunubi.15Ya yanka shi, sai ya ɗauki jinin ya sa a kan ƙahonnin bagadin da ɗan yatsansa, ya tsarkake bagadin, ya zuba jinin a ƙarƙashin bagadin, ya keɓe shi ga Yahweh domin ya yi kaffara domin shi.16Ya ɗauki dukkan kitsen da ke kan kayan ciki, da wanda ya rufe hanta, da ƙodojin biyu da kitsensu, sai Musa ya ƙona su dukka a kan bagadi.17Amma bijimin, da fatarsa, da namansa, da kashinsa ya ƙona su a bayan sansani, kamar yadda Yahweh ya umarce shi.18Musa ya miƙa rãgon domin baiko na ƙonawa, kuma Haruna da 'ya'yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan rãgon.19Ya yanka shi ya yayyafa jininsa a kowanne gefen bagadin.20Ya yanka rãgon gunduwa gunduwa ya ƙona kan da yankakkun naman da kuma kitsen.21Ya wanke kayan cikin da ƙafafun da ruwa, ya kuma ƙona rãgon ɗungum a kan bagadi. Baiko ne na ƙonawa mai bada ƙamshi mai daɗi, baiko ne da aka yi da wuta ga Yahweh kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.22Sa'an nan Musa ya miƙa ɗaya ragon, ragon tsarkakewa, Haruna da 'ya'yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan rãgon.23Sai Haruna ya yanka shi, Musa kuma ya ɗiba daga jinin ya sa su a leɓatun kunnen dama na Haruna, da bisa babban yatsansa na hannun damansa da bisa babban yatsan ƙafarsa ta dama.24Ya kawo 'ya'yan Haruna maza, ya sa daga jinin a kan leɓatun kunnuwansu na dama, da kan manyan yatsan hannuwansu na dama, da kan manyan yatsansu na ƙafafun dama. Sa'an nan Musa ya yayyafa jinin a kowanne gefen bagadin.25Ya ɗauki kitsen, kitsen wutsiya, dukkan kitsen da ke bisa kayan ciki, da wanda ya rufe hanta, da ƙodojin biyu da kitsensu, da cinyar dama.26Daga cikin kwandon gurasa da bata da gami da ke gaban Yahweh, ya ɗauki curi guda na marar gami, da curi guda na gurasa da aka shafe ta da mai, da waina guda, sai ya ɗibiya su bisa kitsen da kuma kan cinyar dama.27Ya sa su dukka a hannuwan Haruna da kuma hannuwan 'ya'yansa maza kuma ya kaɗa su a gaban Yahweh domin baiko na kaɗawa.28Sa'an nan Musa ya karɓe su daga hannunsu ya ƙona su a kan bagadi domin baiko na ƙonawa. Baiko ne na keɓewa ya kuma bada ƙamshi mai daɗi. Baiko ne da aka yi da wuta ga Yahweh.29Musa ya ɗauki ƙirjin ya kaɗa su don su zama baikon kaɗawa ga Yahweh. Wannan shi ne rabon Musa daga rãgon domin naɗa firist, kamar yadda Yahweh ya umarce shi.30Musa ya ɗiba daga man keɓewa da jinin da ke kan bagadi; ya yayyafa su a kan Haruna, da kan rigunansa, da kan 'ya'yansa maza, da kan rigunan 'ya'yansa maza tare da shi. Da haka ne ya keɓe Haruna da rigunansa, da 'ya'yansa maza da rigunansu ga Yahweh.31Sai Musa ya cewa Haruna da 'ya'yansa maza, "Ku dafa naman a ƙofar shiga rumfar taruwa, ku ci a can da gurasar da ke cikin kwandon tsarkakewa, kamar yadda na umarta, cewa, 'Haruna da 'ya'yansa maza za su ci shi.'32Duk abin da ya rage daga naman da gurasar dole a ƙona.33Ba za ku fita daga ƙofar rumfar taruwa ba har kwana bakwai, sai kwanakin naɗinku sun cika. Domin Yahweh zai tsarkake ku kwana bakwai.34Mene ne aka rigaya aka yi yau - Yahweh ya umarta a yi domin a yi maku kaffara.35Za ku zauna dare da rana har kwana bakwai a ƙofar rumfar taruwa, ku yi biyayya da umarnin Yahweh, domin kada ku mutu, domin wannan ne aka umarce ni.36Sai Haruna da 'ya'yansa maza suka yi dukkan abubuwan da Yahweh ya umarce su ta wurin Musa.
Ă sura ta takwas, Musa ya naɗa Haruna da 'ya'yan sa maza a matsayin firisti bisa ga umurnin Yahweh da Musa ya rubuta a litafin Firistoci.
"Tufafin firistoci" ko "kayakin da firistoci suke sakawa"
"Yahweh ya umurce mu mu yi"
Wannan na nuna aikin ne. Wannan tsarki ne na al'ada da ake masu domin su zama firistoci
Ɗamara da aka yi da saƙa- Wannan taguwa ce na musamman da Yahweh ya umurce mutanen su yi wa firistocin.
Dogon tufafi da ake ɗaurawa a ƙwanƙwaso ko ƙirji
"Ɗaura masa"
"Musa ya maƙala wa Haruna ƙyallen maƙalawa"
Waɗannan tufafi ne na musamman da Yahweh ya umurce mutane suyi wa firistoci.
Waɗannan abubuwan basuwa nan a bayyane. Abubuwan nan wata hanya ce da firistocin suna amfani da shi domin su gane nufin Allah.
Wannan dogon tufafi ne da ake naɗewa a ƙan mutum
Ƙalamu biyun nan suna nufin abu ɗaya ne. Wannan allon zinariya ne da ya ke tare da rawanin.
Waɗannan ne dukan tukwane, kwanon rufi, shebur, da kuma cokali mai yatsa da aka yi amfani da su akan bagaden.
Tagulla daron nan ne aka samu a tsakanin bagade da kuma alfarwa.
Wannan tsayayen tagulla ce wadda aka ajiye daron.
"Musa ya zuba"
Wannan jam'i ne na "ɗamara." AT: 8:6
Wannan ya nuna yadda Haruna da 'ya'yan sa maza tare da dabban da suka mika. Ta haka, suna mika kawunansu wa Yahweh ta wurin dabban. AT: 1:3
Wannan na nufin gabobin bagaden. An ƙera su ne kamar ƙahon bijimin. AT: 4:6.
"Shirya bagaden wa Allah"
A nan "kafara" na nufin gyara bagadi domin bautar Allah. AT: "domin yă zama wurin da ya dace a kona hadayan zunubi"
Wannan ciki ne da kuma hanji. AT: 1:7.
AT: 3:3
Gashi ko fatar garkin dabbobi
Wannan ya nuna yadda Haruna da 'ya'yan sa maza tare da dabban da suka mika. Ta haka, suna mika kawunansu wa Yahweh ta wurin dabban. AT: 1:3
"Musa ya yanka ragon"
A nan ana magane akan Yahweh yana gamsuwa da hadayar mai sujadar gaskiya kamar Allah ya gamsu da ƙamshin hadayar da aka ƙona. AT: 1:7.
AT: "hadaya da ya ƙona wa Yahweh"
Kalman nan "tsarkakewa" yana bayyana wani yanayi wanda ba ra'ayin mutum bane. AT: "ragon da za yi amfani da shi domin a keɓe Haruna da ya'yan sa maza domin aikin Allah"
Wannan kalmar aikin na nuna Haruna da 'ya'yan sa maza tare da dabban da suke mikawa. Ta yin haka, suna mika ƙansu ga Yahweh tawurin wannan dabban. AT: 1:3.
Wannan na nufin cewa Musa ya tare jinin a cikin kwano da jinin na zubowa daga jikin dabban. Za ă iya yin bayanin kalman nan a fili.
kayan ciki - Wannan na nufin ciki da hanji. AT: 1:7.
AT: 3:3.
Cinya yana saman kafa ne a bisa gwiwa. AT: 7:31.
Wannan baya nufin wurin da aka ajiye kwandon abincin. Yana nufin cewa wannan ne abincin da Musa ya mika wa Yahweh.
A nan "hannunuwa" ya na nufin Mutum gaba ɗaya.AT: "mika shi duka ga Haruna da kuma 'ya'yansa maza"
Wannan ya na nufin Haruna da kuma ƴaƴansa suna wakiltar baikon.Ana iya samun asalin ma'anar wannan.AT: "sun kaɗa shi a gaban Yahweh baiko na kaɗawa"
Wannan alama ce ta miƙa baikon ga Yahweh.
A nan "su" ya na nufin kitse,cinya,da kuma dukkan gurasar
A nan "hannuwa" ya na nufin mutum gaba daya.AT:"daga Haruna da yayansa"
"Ya ƙona su a kan bagaden domin baiko na ƙonawa domin keɓe Haruna da kuma ƴaƴansa domin hidimar Yahweh"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT: "Haɗaya ta konawa ga Yahweh"
Farin cikin Yahweh da amincin mai sujada wanda ya miƙa hadayar sa ana fadar sa kamar Allah ya jin ɗaɗin ƙamshin haɗayar ta ƙonawa.Duba yadda ka juya a a baya cikin kalmomin 1:7.
Gaɓa ta gaba ta jikin dabbar da ke kalkashin wuya.
Buki ta musamman na keɓe mutum ya zama firist
Musa annabi ne da kuma shugaban mutanen Isra'ila na fiye da shekaru arbain. lokacin da Musa yake jariri iyayen sa suka sa shi a cikin kwando a cikin zaborin kogin Nile domin su boye shi da ga fir'auna na ƙasar Masar.ƴar'uwan Musa Miryam ita ce ta ke lura da shi a can.Musa ya tsira da ran sa lokacin da ɗiyar fir'auna ta samo shi ta kuma ɗauke shi ta kai shi cikin fadar sarki domin ta rene shi a matsayin ɗan ta Allah ya zabi Musa domin ya kubutar da Isra'ilawa daga kangin bauta ta ƙasar Masar ya kuma kai su ƙasa mai tsarki. Bayan Isra'ilawa sun kubuce daga ƙasar Masar kuma bayan su na ta yawo a cikin jeji,Ubangiji ya ba wa Musa allo na duwatsu biyu wanda aka rubuta dokoki goma a kan su kusa da ƙarshen rayuwar sa.Musa ya ga ƙasar alƙawari,amma bai shi ga cikin ta ba domin rashin biyayya ga Allah.
Miriyam ƙasar alƙawari Dokoki goma
wannan kalma "keɓewa" ya na nufin shafa ko kwara mai a kan mutum ko wani abu.wani lokaci ana garwaya turaren kamshi,domin ba da sheƙi mai daɗi,na turare.wannan kalman ana iya anfani da shi a yanayi na kwatanci ga Ruhu mai tsarki ya zaba ko ya sabko a kan wani. A cikin tsohon alƙawari,firistoci da sarakuna da annabawa su ne ake shafewa da mai domin a keɓe su domin yin wani hidima ga Allah. abubuwa kamar bagadi da kuma rufar sujada,su ma ana shafe su da mai domin a nuna an keɓe su domin yi wa Allah sujada da kuma domin daukakar Ubangiji. A cikin Sabon Alƙawari an rubuta sau biyu cewa mace ta shafe yesu da mai domin ÿa warƙar da ita. Sabon Alƙawari ya bayyana sau biyu mace ta shafe shi da mai mai-kamshi,wanda ke nuna halin sujada.A wani lokaci yesu ya furta ya ce ta haka ta na shirya shi ne domin ranar bizinan sa. Bayan yesu ya mutu,abokan sa sun shirya gawar sa domin bizinewa ta shafe jikin sa da mai da kuma kayan kamshi. wannan sunan "Al'masihu"(yahudanci) da kuma "kristi"(helenanci) ya na nufin "shafeffe". Yesu al'masihu shi ne wanda ya ke zaɓaɓɓe da kuma annabi,babban firist da kuma sarki. Shawara a kan yadda za a juya ya danganta ga ma'anar,kalman "shafe"ana iya juya shi "kwara mai a kan" ko "zuba mai a kan" ko "kwara mai mai- ƙamshi a kan".
tsarkakewa
Mai ya na da kauri,abu ruwa ruwa mai haske da ake samu daga ƴa'ƴan itatuwa.A lokacin littafi mai tsarki mai ana samun ta ne daga itacen olifs. mai na olifs ana anfani da ita ce domin girki,shafewa,haɗaya,yin fitila,da kuma magani. a zamanin ḍa,mai na olifs ya na da tsada sosai kuma duk wanda ya mallaki mai na olifs ana kwatanta shi da dukiya. ka tabbata ka juya wannan kalmomin da nufin nuna mai da ake anfani da ita domin girki ba mai na motar hawa ba.Wasu yarururka suna da kalmomi iri iri da suke nu na mai.
Olif Haɗaya,baiko
Kalman "Jini" ya na nufin abu ja ruwa-ruwa wanda ke fitowa daga fatar jikin mutum idan an sami rauni.Jini ya na bada abubuwan rai ga mutum da jikinsa gaba ɗaya. Jini na nuna rai,kuma idan an zubar da ita,ta na nuna karewar rai ko mutuwa. idan mutane sun miƙa haɗaya ga Allah,su kan kashe dabbar, su kuma zuba jinin akan dabbar a kan bagadi.wannan ya na nuna haɗayar ta ran dabbar domin biyan zunbubai na mutane. Ta wurin mutuwar sa akan giciye,jinin Yesu ya nuna tsarkake mutane daga zunuban su ya kuma biya hukumci da ya kamata a yi wa mutane domin zunuban su. Furcin nan "nama da jini" ya na nufin yan adam. Furcin nan "nama na da jini na" ya na nufin mutane ƴan'uwa ta jini. Shawara domin Juya wa ana iya juya wannan da kalman da yake nufin jini a cikin yaren da ake juyawa. furcin nan "nama da jini" ana iya juya shi ya zama "mutane" ko "ƴan adam". ya danganta ga ma'anar,furcin nan "nama na da jini na" ana iya juya shi kamar haka "iyali na" ko "ƴan'uwa na" ko "mutane na". Idan akwai furci a yaren da ake juya wa wanda ake anfani da wannan maanar, ana iya juya wannan furcin haka "nama da jini".
nama
Bagadi gini ne wanda aka ɗaga wanda Isra'ilawa suke ƙona dabbobi da hatsi domin baiko ga Allah. A zamanin littafi mai tsarki,ana yin bagadi cikin sauki da laka ko jerin duwatsu wanda aka shirya ya zama kamar ǧado. ana yin wasu akwatuna ta musamman da katako shirye da karfe akai na gol,tagulla da azurfa. wasu mutane da ke zama kusa da Isra'ilawa su ma suna yin bagadi domin bautar allolin su.
Bagadin turare allolin karya,allolin wasu kasa,allah,alloli mata baikon hatsi
Kalman nan "keɓewa" yana nufin a ware daga wani abu domin yin wani muhimmin aiki. 'Ya'yan Isra'ila an keɓe su domin yin hidima ga Allah. Ruhu mai tsarki ya umarce krista a Antakiya su keɓe Bulus da Barnabas domin aikin da ubangiji ya ke buƙatar su su yi mai bi wanda aka"keɓe" domin hidimar Allah an "mika" shi ne domin cika nufin Allah. wata ma'anar kalman nan "tsarki" ita ce domin keɓewa ga Allah da kuma fita daga hanyar zunubi ta duniya. kalman nan "tsarkake" ya na nufin a keɓe mutum domin aikin Allah. Shawara domin juya wa hanyoyin juya "keɓewa" na iya zama,"zaɓe ta musamman" ko "warewa daga cikin su" ko "ajiyewa domin aiki ta musamman" a "keɓe" ana iya juya wa haka "a ware"
tsarki, tsarkakewa yin tsarki, tabatar da tsarki zaɓa, zaɓaɓɓe
Haruna shine wan Musa.Allah ya zabi Haruna ya zama babban firist na farko a mutanen Isra'ila. Haruna ya taimaka wa Musa domin yin magana da fir'auna saboda ya sa ki mutanen sa Israila su tafi. Yayin da Israilawa suke tafiya cikin jeji,Haruna yayi zunubi ta wurin yin gunki domin mutane su yi masa sujada. Allah kuma ya zabi Haruna da ƴa'ƴansa na zuriyarsa domin su zama firistoci(../kt/priest.md)firistoci domin mutanen Isra'ila.
firist,firistoci Musa Isra'ila,Isra'ilawa,kasar Isra'ila
Idan ana anfani da ita ta misali a cikin littafi mai tsarki,"sanya riga" ya na nufin cika ko zuba wani abu.sa "riga" ya na nufin ga mutum ya na iya zama da wata hali. kamar yadda ake sa riga a waje kowa ya gani haka ne idan "ka sa" wata hali ana iya gani da wuri."ka sanya wa kanka halin kirki" yana nufin ka nuna halin ka na kirki domin kowa ya gani. ka "sami" iko daga sama ya na nufin an ba ka iko wannan furcin ana anfani da ita ce domin fadar abinda ba shi da kyau wato "ka sha kunya" ko "ka sha azaba" Shawara domin juya wa idan ya yiwu a bar kalman yadda yake"sa wa kanka abin".wata hanyar juya wa ya na iya zama "ka sa" idan ya na nufin sa riga idan bai bada ma'anar ba wasu hanyar juya "ya sa" ya na iya zama "nuna" ko "kasancewa da" furcin nan "ka sanya wa kanka" ana iya juya shi haka "ka rufe kanka da" ko "ka nuna hali da ya zama"
furcin nan "ɗa"ya na nufin ɗa namiji yaro ko namiji babba mai dangantaka da iyayensa.Yana iya zama zuri'a ta namiji ko ɗan riko. "ɗa" ana yawan anfani da shi ne a cikin littafi mai tsarki domin nuna zuri'a namiji kamar jika ko tattaɓa kunne maza. kalman nan "ɗa" ana iya anfani da shi a hanyar sauƙi zuwa ga yaro ko namiji babba. wani lokaci "ƴaƴan Allah" ana anfani da shi a cikin sabon alkawari ga masu bin yesu kristi. Allah ya kira Isra'ila ɗansa "ɗan fari".Wannan ya na nufin zaben Allah a kan kasar Isra'ila su zama mutanen sa muhimmai.Ta wurin su ne Allah zai aiko da saƙon fansa da ceto.Da kuma ta haka dukkan sauran mutane su zama ƴa'ƴan Allah na ruhu. Furcin nan "ƴa'ƴan" kusan kullum ya na da ma'ana ta misali,"kasancewa da halayen".Misalai su na kamar haka,"ƴa'ƴan haske" "ƴa'ƴan rashin biyayya" "ɗan salama" da kuma "ɗan tsawa". furcin nan "ɗan" ana iya anfani da shi domin nuna ko wanene ubansa.Ana anfani da wannan a jerin zuri'a da wurare. Yin anfani da "ɗan"domin ba da suna ga uban ya na taimaka wa wajen kawo banbanci na mutane da ke da suna iri ɗaya misali "Azariya dan Zadok" da kuma Azariya dan Nathan" 1 Sarakuna 4,da "Azariya,dan Amaziya a 2 Sarakuna 15 maza ne daban da ban. Shawara domin Juya wa bisa ga yawan kalmomin nan yana da kyau ka juya shi haka "ɗa" ta wurin yin anfani da yadda yaren su ke kiran ɗa. idan za a juya kalman "ɗan Allah",sai ayi anfani da sunan da yaren suke anfani da shi domin juya kalman nan "ɗa". idan za a yi anfani da zuri'a fiye da ɗa,kalman nan "zuri'a" idan ana nufin Yesu shi zuri'ar Dauda" ko cikin jerin zuri'a inda wani lokaci "ɗa"ya na nufin dangi namiji amma ba ɗa na haifuwa ba. wani lokaci "ƴa'ƴa" ana iya juya su kamar "yara",idan dukkan maza da mata ne ake kiran su.Misali,"ƴa'ƴan Allah".ana iya juya su "ƴa'ƴan Allah"da shike wannan furcin ya ƙunshi ƴammata da Mata. Wannan furcin na, misali "ƴa'ƴan" ana iya juya wa a ce "wani wanda ya ke da halayen" ko " wani wanda yake" ko "wani wanda yana da shi" ko "wanda ya ke yi kamar"
Azaraya zuri'a zuri'ar da ka fito kaka,kakanni,iyayenku na dă ɗan fari ɗan Allah,ɗan,ɗa ya'yan Allah
wannan ya na nufin kwandon ya ƙunshi baye-baye na naɗin Haruna da ƴaƴansa maza.AT:"kwandon"
wannan ya na da magana cikin magana.Ana iya furta magana na kai tsaye kamar magana wanda ba na kai tsaye ba.AT: "kamar yadda na umurce ku ku yi"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:" sai dai kun cika kwanakin naɗinku"
wannan hidima ce ta musamman ta naɗin firist.duba yadda ka juya a 8:28
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"mu, mu yi"
ana iya furta wannan kalman "kaffara" a cikin yanayi na aikatau.AT:" domin yin kaffara domin zunuban ka"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"wannan shi ne abin da ya umurce ni"
1A rana ta takwas Musa ya kira Haruna da 'ya'yansa maza da dattawan Isra'ila.2Ya cewa Haruna, "Ka ɗauki ɗan maraƙi daga garke domin baiko na zunubi, da rago marar lahani domin baiko na ƙonawa, ka miƙa su a gaban Yahweh.3Dole ka yi wa mutanen Isra'ila magana ka ce, 'Ku ɗauki bunsuru domin baikon zunubi da kuma ɗan maraƙi da ɗan rãgo, dukka biyun bana ɗaya kuma marasa lahani, domin baiko na ƙonawa;4kuma ka ɗauki sã da rãgo domin baiko na salama a yi hadaya ga Yahweh, da baiko na garin hatsi cuɗaɗɗe da mai, domin yau Yahweh zai bayyana a gare ku.'"5Sai suka kawo dukkan abin da Yahweh ya umarta zuwa rumfar taruwa, sai dukkan taron Isra'ila suka matso suka tsaya a gaban Yahweh.6Sai Musa ya ce, "Wannan shi ne Yahweh ya umarce ku kuyi domin ɗaukakarsa ta bayyana a gare ku,"7Musa ya cewa Haruna, "Ka matso kusa da bagadi ka miƙa baikonka domin zunubi da na ƙonawa, ka yi wa kanka kaffara domin mutane kuma, ka kuma miƙa hadaya domin mutane domin a yi masu kaffara kamar yadda Yahweh ya umarta."8Sai Haruna ya tafi kusa da bagadi ya yanka ɗan maraƙin domin baikon zunubi wanda domin kansa ne.9'Ya'yan Haruna suka miƙa masa jinin, sai ya tsoma yatsansa cikinsa ya sa a ƙahonnin bagadin; sa'an nan ya zuba jinin a gindin bagadin.10Amma, ya ƙona kitsen, da ƙodojin da wanda ya rufe hanta a kan bagadi domin baikon zunubi, kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.11Da naman da fatar ya ƙona su a bayan sansani.12Haruna ya yanka baiko na ƙonawa, 'ya'yansa maza suka bashi jinin, wanda ya warwatsa a kowanne gefen bagadi.13Sa'an nan suka miƙa masa baiko na ƙonawa, gunduwa-gunduwa, tare da kan, sai ya ƙona su a kan bagadi.14Ya wanke kayan cikin da ƙafafuwan ya ƙona su a kan baiko na ƙonawa a kan bagadi.15Haruna ya miƙa hadayar mutanen - bunsuru, sai ya ɗauke shi domin hadayar zunubansu ya yanka shi; ya miƙa hadayar ne domin zunubi, kamar yadda ya yi da bunsuru na fari.16Ya miƙa baiko na ƙonawa ya miƙa kamar yadda Yahweh ya umarta.17Ya miƙa baiko na garin hatsi; ya cika tafin hannunsa da ita ya ƙona ta a kan bagadi, tare da baikon ƙonawa na safe.18Ya kuma yanka san da rãgon, hadaya domin baiko na salama, saboda mutanen. 'Ya'yan Haruna maza suka ba shi jinin, wanda ya yayyafa a kowanne gefen bagadi.19Amma, suka yanke kitsen bijimin da na rãgon, da kitsen wutsiyar, da kitsen da ya rufe kayan ciki, da ƙodoji, da wanda ya rufe hanta.20Suka ɗauki sassan da aka yanka suka ɗibiyasu a kan ƙirjin, sa'an nan Haruna ya ƙona kitsen a kan bagadi,21Haruna ya kaɗa ƙirjin da cinyar ƙafar dama domin baiko na kaɗawa a gaban Yahweh, kamar yadda Musa ya umarta.22Sa'an nan Haruna ya ɗaga hannuwansa yana fuskantar mutane ya albarkace su; sai ya dawo daga miƙa baiko na zunubi, baiko na ƙonawa, da baiko na salama.23Musa da Haruna suka shiga rumfar taruwa, suka sake fitowa kuma suka albarkaci mutanen, sai ɗaukakar Yahweh ta bayyana ga dukkan mutane.24Wuta ta fito daga Yahweh ta cinye baikon ƙonawar da kitsen da ke kan bagadin. Da dai dukkan mutane suka ga haka, sai suka yi ihu suka kwanta fuskokinsu a ƙasa.
kalman na "takwas" keɓaɓɓiyar lamba ce ta takwas.
"ga Yahweh" ko "a gaban Yahweh"
Musa ya ci gaba da magana da Haruna.
Musa ya ci gaba da magana da Haruna.wannan na da magana cikin magana.Ana iya furta magana kai tsaye,kamar maganar da ba kai tsaye ba.AT:"kuma ka fada wa mutanen Israila su dauki bunsuru...zai bayyana ga dukan mutanen".
"shakaru goma sha-biyu na haifuwa"
"domin yin haɗaya ga Yahweh"
Ana "ku" ya na nufin mutanen Israila.
A nan "daukaka" ya na a madadin kasancewar Yahweh.AT: "domin ya nuna maku kasancewar daukakarsa"
Wannan haɗayar kashi biyu ne, daban daban.Haɗaya ta farko domin yin kaffara domin zunubai na babban firist.Idan babban firist ya yi zunubi ta shifi kowane mutum.(duba: 4:1).haɗayar ta biyu domin yin kaffara saboda zunuban da mutane su ka yi da kansu.
Wannan ya na nuna sun kawo jinin a cikin akushi yayin da jinin na tsiyayewa daga dabbar.Cikakkiyar ma'anar wannan furcin na iya zama a bayyane.
Wannan ya na nufin gafen bagadin.An sifanta su kamar ƙahonnin bijimi.Duba yadda ka juya shi a 4:6.
"A gindin bagadin"
"Haruna ya ƙona"
juya wannan kalmomin kamar yadda ka yi a 3:3
wannan gashin ko fatar dabbar ne.Duba yadda ka juya shi a 7:7.
wannan ya na nuna sun kawo jinin cikin akushi yayin da jinin ke tsiyayewa daga dabbar.Cikakkiyar ma'anar wannan furcin na iya zama a bayyane.
kayan ciki- wannan ita ce tumbi da kuma hanji.Duba yadda ka juya shi a 1:7
kalman "farko" keɓaɓɓiyar lamba ce ta ɗaya.AT:" Bunsurun domin na sa baikon"
wannan ya na nufin haɗaya ta farko ta kowace rana.Firist zai miƙa hadaya ta ƙonawa da safe kafin ya miƙa wasu haɗayun.Cikakkiyar ma'anar wannan kalmomin ya na iya zama a baiyane.
"Haruna ya kashe"
wannan ya na nuna jinin ya na cikin akushin.cikakiyar ma'anar wannan ya na iya zama a bayyane.
wannan tumbi ne da hanji.Duba yadda ka juya shi a 1:7
ka juya kalmomin na kamar yadda ka yi a 3:3
'ya'yan Haruna maza suka ɗauki sassan"
kalman "waɗannan" ya na nufin kitse da kayan ciki da aka lisafata su a baya.
wannan gaɓar jikin dabbar ce ta gaba ta karkashin wuya.duba yadda ka juya a 7:28
wannan gaɓa ce ta kafa sama da gwiwa.duba yadda ka juya a 7:31.
"Ga Yahweh"
kalma "sauko ƙasa" ana yin anfani ne da shi domin wurin bagadin ya na sama da inda mutanen ke tsaye
anan "daraja" ya na a madadin kasancewar Yahweh.AT:"Yahweh ya nuna wa dukkan mutanen darajar kasancewar sa"
"Yahweh ya sauko da wuta ta cinye su"
wutar ta cinye haɗayar duka ana fadar sa ne kamar wutar ta cinye ko ta gama baikon ta ƙonawa.
"kwanciya da fuskoki a ƙasa".wannan alama ce ta bangirma da daraja.
1Sai Nadab, da Abihu 'ya'yan Haruna maza, kowannensu ya ɗauki farantinsa ya sa wuta a ciki, da kuma turare. Sa'an nan suka miƙa haramtacciyar wuta a gaban Yahweh, wanda bai dokace su su miƙa ba.2Saboda haka wuta ta fito daga gaban Yahweh ta hallaka su, suka kuwa mutu a gaban Yahweh.3Sai Musa ya cewa Haruna, "Wannan shi ne Yahweh ya ke magana a kai sa'ad da ya ce, "Zan bayyana tsarkina ga waɗanda suka matso gare ni. Za a ɗaukaka ni a gaban dukkan mutane.'" Haruna bai ce komai ba.4Musa ya kira Mishayel da Elzafan, 'ya'ya maza na Uziyel kawun Haruna, ya ce masu, "Ku zo nan ku ɗauki 'yan'uwanku daga cikin sansani daga gaban rumfar taruwa."5Sai suka matso kusa suka ɗauke su, suna saye da rigunansu na firistoci, zuwa bayan sansani, kamar yadda Musa ya umarta.6Sai Musa ya ce da Haruna da Eliyazar da kuma Itamar 'ya'yansa maza, "Kada ku bar gashin kanku da tsawo, kada kuma ku kekketa tufafinku, domin kada ku mutu, kuma domin kada Yahweh ya yi fushi da dukkan taro. Amma ku bari 'yan'uwanku wato dukkan gidan Isra'ila, su yi makoki domin waɗanda wutar Yahweh ta babbake.7Ba za ku fita daga ƙofar rumfar taruwa ba, ko kuwa ku mutu, gama man shafewa na Yahweh yana kanku." Sai suka aikata bisa ga umarnin Musa.8Yahweh ya yi magana da Haruna, cewa,9"Kada ka sha ruwan inabi ko barasa, da kai, da 'ya'yanka maza da ke tare da kai, yayin da kuka shiga rumfar taruwa, domin kada ku mutu. Wannan zai zama tsayayyar ka'ida dukkan tsararrakin mutanenku,10domin a faiyace mai tsarki da marar tsarki, tsakanin ƙazamtacce da tsarkakke,11domin ka koyar da mutanen Isra'ila dukkan farillan da Yahweh ya umarta ta wurin Musa."12Musa ya yi magana da Haruna da Eliyazar da kuma Itamar, 'ya'yansa maza da suka rage, "Ku ɗauki baiko na hatsi da ya ragu daga baye-bayen Yahweh da aka yi da wuta, ku ci bada gami ba kusa da bagadi, gama mafi tsarki ne.13Dole ka ci shi a wuri mai tsarki, domin rabonku ne da kuma rabon 'ya'yanku maza baye-bayen da aka yi wa Yahweh da wuta, gama wannan ne aka umarce ni in faɗa maku.14Ƙirjin da aka kaɗa da cinyar da aka miƙa wa Yahweh, dole ku ci a wuri mai tsabta karɓaɓɓe ga Yahweh. Da kai da 'ya'yanka maza da 'ya'yanka mata tare da kai za ku ci waɗannan rabon, gama an bada su domin su zama rabonka da na 'ya'yanka maza daga cikin hadayu na baye-baye na zumunta na mutanen Isra'ila.15Cinyar da aka miƙa da ƙirjin da aka kaɗa, dole ne su kawosu da baye-baye na kitse da aka yi da wuta, domin a kaɗa su a gaban Yahweh. Za su zama naka da na 'ya'yanka maza rabonku ne har abada, kamar yadda Yahweh ya umarta."16Sa'an nan Musa ya tambaya game da bunsurun baiko na zunubi, sai ya ga an ƙone shi kurmus. Saboda haka ya yi fushi da Eliyazar da Itamar, sauran 'ya'ya maza na Haruna; ya ce,17"Me ya sa ba ku ci baiko na zunubi a harabar rumfar sujada ba, tunda shike mafi tsarki ne, kuma tun da Yahweh ya bada shi gare ku domin a ɗauke laifin taro, domin a yi masu kaffara a gabansa?18Duba, ba a kawo jininsa cikin rumfar sujada ba, yakamata lallai da kun ci shi a harabar rumfar sujada, kamar yadda na umarta."19Sai Haruna ya amsa wa Musa, "Duba, yau sun miƙa baikonsu na zunubi da baiko ta ƙonawa a gaban Yahweh, kuma ga wannan abu ya faru da ni yau. In da na ci baiko na zunubi yau, da zai zama da kyau kenan a idon Yahweh?"20Da Musa ya ji wannan, sai ya gamsu.
wannan sunan ya'yan Haruna ne maza.
faranti mara zurfi na karfe wanda firistoci ke amfani da shi domin ɗiban garwashin wuta ko turare
"sa garwashin wuta a ciki"
"amma Yahweh bai karɓi baikon su ba, domin ba su miƙa bisa ga umarnan da ya dokace su, su mika"
"haramtacciyar wuta ga Yahweh"
"sai Yahweh ya aiko da wuta"
"ta fito daga Yahweh"
wutar ta cinye mazan duka ana furta shi ne kamar wutar ta gama da su ko ta cinye su duka.
"sun mutu a gaban Yahweh"
wannan yana da magana cikin magana.Magana kai tsaye na iya zama maganar da ba kai tsaye ba.AT:"wannan shi ne Yahweh yake magana a kai da ya ce zai bayyana tsarkinsa...wanda ya matso gareni za a daukaka shi...mutane"
Kalmomin nan "wanda ya matso gare ni" ya na nufin firistoci wanɗanda ke yi wa Yahweh hidima."zan nuna wa waɗanda su ka matso kusa domin su yi mani hidima cewa ni mai tsarki ne" ko "waɗanda suka matso gare ni domin yi mun hidima dole su yi da tsarki"
sashi na biyu na maganar Yahweh ya shafi firistoci,ma su matsowa ku sa da Yahweh.Ana iya juya wannan a yanayi na aikatawa.AT:"Dole su girmama ni a gaban mutane" ko "Dole su girmama ni a idanun dukkan Jama'a
wannan sunayen maza ne.
wannan ba yana nufin ƴan'uwa na ciki ba.Anan ƴan'uwa na nufin dangi ko ƴa'ƴan kawu
"sai Mishayel da Elzafa su ka matso kusa"
daukan gangar jikin Nadab da Abihu,wanda suke anye da rigunan firistoci a jikinsu
wannan sunayen ƴa'ƴan Haruna ne maza.
Yahweh ya na gaya wa Haruna da ƴaƴansa maza kada su nuna makokinsu a fili.
"domin kada ku mutu"
Anan "taro" ya na nufin dukkakan jama'ar Isra'ila,ba shugabanni kadai ba.AT:kada yayi fushi da dukkan mutane na Israila
Anan "gida" yana nufin dukkan jama'ar Israila.AT:"Dukkan mutanen Isra'ila"
"waɗanda Yahweh ya kashe su da wuta"
Anan "wannan"ya na nufin umarni ga firistoci da kada su sha ruwan giya ko ruwan sa maye kafin su shiga rufar taruwa.
ka juya waɗannan kalmomin kamar yadda ka yi a 3:15
kana iya fara sabuwar kalmomi anan."dole ka yi wannan domin ka bambanta"
keɓaɓɓen kalmar bayani "mai tsarki"da kuma "marar tsarki" ana iya fadarsa a kalmar bayani.AT:"tsakanin abin da ke da tsarki da marar tsarki"ko "tsakanin abin da an keɓewa Allah da kuma wanda ba a keɓe ba"
kalman bayani "kazamtacce" da kuma "mai tsabta" ana iya fadar sa a kalmar bayani.AT:"tsakanin kazamtacce da mai tsabta" ko tsakanin abin da Allah zai karɓa da wanda bai zai karɓa ba"
Mutum ko wani abu wanda Yahweh ya furta shi kazamta kuma kada a taɓa, ana fadar sa ne kamar abin da ke kazamtacce.
Mutum ko wani abu wanda Yahweh ya furta shi mai tsabta ne don taɓawa,ana fadar sa ne kamar abin da ke da tsabta.
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"Haɗaya ta ƙonawa ga Yahweh"
"domin baikon hatsi mafi tsarki ne"
Ana iya juya wannan a yanayi na aikatawa.AT:"wannan shine Yahweh ya umarce ni in gaya maku"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"kirjin da cinyar aka kaɗa an kuma mika wa Yahweh"
gabar jikin dabbar na gaba a kalkashin wuya
gabar sama ta kafa da ke sama da gwiwa
wurin da ya yi kyau domin yi wa Allah hidima ana fadar sa ne kamar wuri ne mai tsabta a fili.
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT:"domin Yahweh ya ba su rabonsu"
Anan "ka" yana nufin Haruna.
Ka juya wannan domin a gane cewa kason na Haruna ne da ƴa'ƴansa maza.AT:"wannan kason zai kasance kullayomi domin ka da ƴa'ƴanka maza"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT: "firist ya koneshi kurmus"
Ka juya wannan sunayen yadda ka juya a 10:5
Musa ya mori tambaya ya ƙwabi Eliyaza da Itamar.Wannan tambayar rashin amsar ana iya juya ta kamar kalmomi.AT:"Da ka ci...a gababn sa".
" da shike baikon na zunubi mai tsarki ne"
Sa Yahweh ya gafarta zunuban mutanen Isra'ila ana furta shi ne kamar zunubi ya zama wani abu ne da Yahweh yake dauke wa mutane.
" a gabansa"
Ana iya juya wannan cikin yanayi na aikatawa.AT: " Baku kawo jininsa ba"
Haruna ya na magana ne akan mutuwar yayansa maza biyu
za a ci haɗayun nan da murna da farin ciki.Haruna ya yi tambaya ne domin jaddada cewa Yahweh ba zai yi farin ciki da haɗayar sa ba domin yana makokin mutuwar ƴaƴansa maza.wannan tambayar ana iya juya ta kamar kalmomi.AT:" Haƙiƙa Yahweh ba zai ji dadi ba"
1Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna, cewa,2"Ka yi wa mutanen Isra'ila magana, ka ce, 'Waɗannan su ne masu rai da za ku ci daga cikin dukkan dabbobin da ke a duniya.3Za ku ci kowacce dabba da ke da rababben kofato tana kuma tuƙa.4Amma fa, wasu dabbobin suna tuƙa, ko kuma suna da rababbun kofatai, ba za ku ci su ba, dabbobi kamar su raƙumi, domin yana tuƙa, amma ba shi da rababben kofato. Saboda haka raƙumi marar tsarki ne a gare ku.5Haka ma rema, domin tana tuƙa amma ba ta da rababben kofato, ita ma marar tsabta ce a gare ku.6Zomo yana tuƙa, amma ba shi da rababben kofato, saboda haka marar tsabta ne a gare ku.7Alade, koda shike yana da rababben kofato, ba ya tuƙa, marar tsabta ne a gare ku.8Ba za ku ci namansu ba, ko ku taɓa gawawakinsu. Marasa tsabta ne a gare ku.9Dabbobin da ke zaune cikin ruwa da za ku ci su ne duk waɗanda ke da ƙege ko kamɓori, ko a cikin teku ko cikin koguna.10Amma duk rayayyun hallitu da ba su da ƙege ko kamɓori a cikin teku da koguna, har da ma dukkan masu yawo a ruwa da dukkan hallitu da ke cikin ruwa - dole za su zama abin ƙyama a gare ku.11Tun da ya zama dole ku ƙyamace su, ba za ku ci daga namansu ba; kuma, dole ku ƙyamaci gawawakinsu.12Dukkan abin da ba shi da ƙege ko kamɓori a cikin ruwa dole ku ƙyamace su.13Ga tsuntsayen da za ku ji ƙyama kuma ba za ku ci su ba su ne: gaggafa, da ungulu,14da shirwa, da kowacce irin mikiya,15da kowanne irin hankaka,16jimina, da mujiyar dare, da shaho, da kowacce irin shirwa.17Za ku kuma ƙyamaci mujiya, da babba da ƙarama, da zalɓe,18da kazar ruwa, da kwasakwasa, da ungulu,19da shamuwa, da jinjimi, da burtu, da jemage.20Dukkan ƙwari masu fukafukai da ke tafiya a kan ƙafa huɗu abin ƙyama ne a gare ku.21Amma za ku iya cin ƙwari masu tashi suna kuma tafiya a kan ƙafafu huɗu idan ƙafafunsu suna da mahaɗi don tsalle a ƙasa.22Za ku iya cin kowacce irin fara, da gara mai fukafukai da gyare, ko fara.23Amma duk ƙwari masu tashi masu ƙafa huɗu abin ƙyama ne a gare ku.24Za ku ƙazantu har faɗuwar rana ta wurin waɗannan dabbobi idan kun taɓa mushen ɗaya daga cikinsu.25Duk wanda ya ɗauki ɗaya daga cikin gawawakinsu dole ya wanke tufafinsa ya ƙazantu har ya zuwa faɗuwar rana.26Duk dabbar da ke da rababben kofato kuma bata tuƙa zai zama ƙazantacce a gare ku. Duk wanda ya taɓa ta zai ƙazantu.27Duk abin da ke tafiya a kan daginsa a cikin dukkan dabbobi da suke tafiya a kan ƙafafu huɗu, ƙazantattu ne a gare ku. Duk wanda ya taɓa mushensu zai ƙazantu zuwa maraice.28Duk wanda ya ɗauki gawarsa dole ya wanke tufafinsa ya ƙazantu har ya zuwa maraice. Waɗannan dabbobi za su zama ƙazantattu a gare ku.29Cikin dabbobi masu rarrafe a ƙasa, waɗannan dabbobi za su zama ƙazantattu a gare ku: da murɗiya, da ɓera, da kowanne irin babban ƙadangare,30da tsaka, guza, da ƙadangare, da damo da hawainiya..31A cikin dukkan dabbobi masu rarrafe, waɗannan ne dabbobin da za su zama ƙazantattu a gare ku. Duk wanda ya taɓa mushensu zai ƙazantu har maraice.32Idan waninsu ya mutu ya kuma faɗi a kan wani abu, wannan abin ya ƙazantu, ko an yi shi da itace, ƙyalle, fata, ko tsumma, Ko mene ne shi kuma ko mene ne ake amfani da shi, dole a sa shi cikin ruwa; zai zama ƙazamtacce har maraice. Sa'an nan zai zama tsarkakakke.33Duk tukunyar yumɓun da ƙazantacciyar dabbar ta faɗa ciki, duk abin da ke cikin tukunyar ya ƙazanta, dole ku fasa tukunyar.34Duk abinci da za a iya ci amma yana da ruwa a bisansa wannan tukunya ba ta da tsabta. Duk abin sha da ya ke cikin tukunyar ya ƙazantu.35Duk abin da mushe ya faɗi a kansa ya ƙazantu; ko tanderu ne ko ƙaramin murhu ne, dole a farfasa su mitsi-mitsi. Ba su da tsarki kuma dole su kasance marasa tsarki a gare ku,36Maɓuɓɓugar ruwa ko daron ɗibar ruwa zai zama da tsabta; amma duk wanda ya taɓa mushensu ya ƙazantu.37Idan wani shashen mushen ya faɗa kan iri domin shuka, waɗannan irin yana da tsabta.38Amma idan an zuba ruwa akan wannan iri, kuma wani sashe na mushen ya faɗi a kansa, za ya zama ƙazantattu a gare ku.39Idan dabbar da ya kamata ku ci ta mutu, sai shi wanda ya taɓa gawar ya ƙazantu har sai maraice.40Duk wanda ya ci wannan mushen dole ya wanke tufafinsa ya ƙazantu har faɗuwar rana. Wanda duk ya ɗauki wannan gawa zai wanke tufafinsa ya ƙazantu har maraice.41Kowacce dabba da ke rarrafe a ƙasa za ku ƙyamace ta; ba za ku ci su ba.42Duk abin da ke jan ciki, da duk abin da ke tafiya akan ƙafafu huɗu, ko mai ƙafafu da yawa - dukkan dabbobi masu rarrafe a ƙasa, ba za ku ci waɗannan ba, domin abin da za a ji ƙyama ne.43Ba za ku ƙazantar da kanku da kowacce hallita mai rai wanda ya ke jan ciki ba; ba za ku ƙazantar da kanku da su ba, har da za ku zama marasa tsarki da su.44Gama ni ne Yahweh Allahnku. Za ku ƙeɓe kanku da tsarki, saboda haka, kuma ku zama da tsarki, domin ni mai tsarki ne. Ba za ku ƙazantar da kanku da kowacce irin dabbar da ke tafiya a fuskar ƙasa ba.45Domin ni ne Yahweh, wanda ya fitar daku daga ƙasar Masar, domin in zama Allahnku. Saboda haka dole ne ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne,46Wannan ita ce dokar da ta shafi dabbobi, da tsuntsaye, da dukkan rayayyun hallitu da ke yawo cikin ruwaye, da kowacce hallita da ke rarrafe a fuskar ƙasa,47waɗanda za a sa bambanci tsakanin marasa tsarki da masu tsarki, da tsakanin abubuwa masu rai da za a iya ci, da abubuwa masu rai da ba za a ci su ba.'"
"daga kowace irin dabba"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da abin da ya ba mutanen izini su ci da kuma abin da haramtas kada su ci.
Wannan na nufin kafato da ya raɓu zuwa kashi biyu a maimakon ya zama guda daya kachal.
Wannan na nufin dabban da take fittad da abinci daga cikĩ ta kuma sake ci kuma.
Wato, suna yin guda a ciki, amma ba duka biyu ba.
An yi magana game da rashin tsabtar rakumin domin mutanen su ci kamar tsabtar jiki ne.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da abin da ya ba mutanen izini su ci da kuma abin da haramtas kada su ci.
ƙaramar dabba ce da take zama a duwatsu
An yi magana game da dabbobin nan da Allah ya ya bayyana cewa haramtacce ne wa mutane su ci kamar basu da tsabtar jiki ne.
wata ƙaramar dabba mai dogon kunnuwa da an cika samu a rami cikin kasa
"ko kuwa taba gawar su ba"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da abin da ya ba mutanen izini su ci da kuma abin da haramtas kada su ci.
abu mara ƙauri da yake jikin ƙifi suna amfani da shi domin suyi tafiya a cikin ruwa
ƙaramar abu mai tsifar faranti da take a jikin ƙifi
"dukkan hallita da ke raye a cikin teku ko ƙoguna da ba su da ƙege ko kamɓori"
Yahweh ya umurce mutanen su tsane cin waddanan hallitun. AT: "dole ku yi kyamar su" ko "dole ne ku ki su gabaɗaya"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da abin da ya ba mutanen izini su ci da kuma abin da haramtas kada su ci.
"kyama" shine a tsane abu. AT: "Da shike ku ji kyamar su" ko " Da shike ya zama dole ne ku ji kyamar su gabaɗaya"
AT: "dole ne ku tsane gawar su" ko "kada ku taba gawar su"
"Kowane abu da ke a cikin ruwa da ba shi da ƙege ko kamɓori"
AT: "dole ku ji kyamar" ko "dole ku tsane su gabaɗaya"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da abin da ya ba mutanen izini su ci da kuma abin da haramtas kada su ci.
Waddanan tsusayen ne suke a farke cikin dare ko
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da abin da ya ba mutanen izini su ci da kuma abin da haramtas kada su ci.
dukkan wadannan tsuntsaye ne wanda suke cin bera da kwari kuma ba sa barci da dare.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da abin da ya ba mutanen izini su ci da kuma abin da haramtas kada su ci.
Kalman nan "ƙazamtattce" za a iya bayyana shi da kalmar aiki. AT: "Za ku yi kyamar dukkan ƙwairai masu fikafiki wanda suke kuma tafiya da ƙafafu huɗu"
Kalmomin nan "ƙafa huɗu" ƙarin magana ne da yake ma'anar yi rarrafe a kasa, a kuma raba waddanan kwarin daga sauran abubuwa masu tafiya a sama kamar tsunsu, wanda suke a kafafu biyu kachal. AT: "kwarai masu rarrafe a kasa"
Waddanan ƙananan kwarai ne, su na cin shuki, suna kan iya tashiwa sama kuma.
"kwarai ma su tafiya a sama wanda suke da ƙafa huɗu"
Yahweh ya fara gaya wa Musa da Haruna game da irin dabban da yakamata mutane su gani a matsayin ƙazamtacce.
AT: "Gawar waddanan dabbobin za su ƙazamttad da ku idan kun taba wanin su"
A nan, ana magana game da mutumin da ya zama mara ƙarbaɓe domin nufin Allah ba domin ya taɓa ɗaya daga cikin mattaccen dabbobin nan kamar mutumin ba shi da tsabta ta jiki ne.
Wannan na nufin dabbobin da yake kokarin jerawa a surorin da ke biye.
Yahweh ya fara gaya wa Musa da Haruna game da irin dabban da yakamata mutane su gani a matsayin ƙazamtacce.
A nan, ana magana game da dabbobin nan da Allah ya ayyana su a matsayin mara ɗacewa ga mutane su ci kamar suna da datti ta jiki.
AT: 11:3...
AT: 11:3...
A nan, ana magana game da mutumin da ya zama mara ƙarbaɓe domin nufin Allah ba domin ya taɓa ɗaya daga cikin mattaccen dabbobin nan kamar mutumin ba shi da tsabta ta jiki ne.
dabbobin da ake ciyes da su da ƙambori
"har faɗiwar rana"
Yahweh ya fara gaya wa Musa da Haruna game da irin dabban da yakamata mutane su gani a matsayin ƙazamtacce.
A nan, ana magana game da dabbobin nan da Allah ya ayyana su a matsayin mara ɗacewa ga mutane su ci kamar suna da datti ta jiki.
ƙaramar dabba wanda ke da gashi mai launin ruwan kasa, wanda yake cin tsunsaye da kuma ƙananan dabbobi a matsayin abinci.
Waddannan hallitu masu rarrafe dabam dabam ne, masu kafafu huɗu.
"kaɗangaren ƙasa"
Yahweh ya fara gaya wa Musa da Haruna game da irin dabban da yakamata mutane su gani a matsayin ƙazamtacce.
AT: 11:29 - 30 ...
AT: 11: 26 - 28 ...
"har faɗiwar rana"
Abin da Allah ya ayyana ya zama mara ɗacewa ga mutane su taba domin mattaccen dabbobin nan sun faɗo ne, ana magana game da su kamar rashin tsabtar jiki ne. Ana magana akai kamar tsabta ta jiki bayan an wanke ta.
Ana magana game da abin da Allah ya ayyana ya zama mara ɗacewa ga mutane su taba bayan da aka wanke shi kamar yana da tsabta ta jiki ne.
AT: "ko yaya aka yi amfani da shi, dole ku saka shi cikin ruwa"
A nan, an yi magana game da abincin da Allah ya ayyana cewa ya ɗace mutanen su ci kamar yana da tsabta ta jiki ne.
AT: "domin ku ci"
A nan ana magana game da abincin da bai ɗace wa mutane su ci ba domin ƙazamtaccen ruwa ya faɗi akai kamar ba shi da tsabtar jiki ne. (Dubi: )
AT: "za ku iya sha"
"na gawar"
AT: "Dole ku farfasa su mitsi-mitsi" ko "Dole ku farfasa su"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da irin dabbobin da mutanen za su gani a matsayin ƙazamtacce.
Ruwan da aka ba wa mutane izini su sha daga maɓuɓɓugar ruwa ko daro, ana magana akai kamar yana da tsabta ta jiki ne.
AT: "daron da ake ɗeba ruwan sha"
Ana magana game da gawar dabban da Allah ya ayyana ya zama mara ɗacewa domin mutane su taɓa kamar ba shi da tsabta ta jiki ne. (Dubi: )
AT: 11:26 - 28
"iri da kake tunanin shuka"
Ana magana game da iri da Allah ya yarda wa mutanen su shuka kamar suna da tsabta ta jiki ne, kuma waddanda ba yarda masu ba kamar ƙazamtattu ne.
AT: "Amma, idan kun saka ruwa akan irin"
AT: 11:26-28...
"sai faɗiwar rana"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da irin dabbobin da mutanen za su gani a matsayin ƙazamtacce.
AT: "dole ku yi kyaman" ko "dole ku ki"
AT: "kada ku ci"
AT: 11:41
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da irin dabbobin da mutanen za su gani a matsayin ƙazamtacce.
Yahweh ya yi amfani da dabaran nan sau biyu domin ya ƙarfafa su game da umurnen da ya basu cewa kada su ci ƙazamtattcen dabba.
AT: 11:26-28...
AT: "domin kada ku zama marasa tsarki saboda su"
Yahweh ya gama gaya wa Musa da Haruna game da abin da ya ba wa mutanen izini su ci da kuma abin da ya haramtad kada su ci.
AT: "waɗanda za ku sa bambanci tsakanin"
AT: 11:24... 11:26...
AT: "da za ku ci ..da ba za ku ci ba"
1Yahweh ya cewa Musa,2"Ka yi wa mutanen Isra'ila magana, cewa, "Idan mace ta yi ciki ta haifi ɗa namiji, za ta ƙazantu har kwana bakwai, kamar yadda ta ƙazantu a kwanakin watan hailarta.3A rana ta takwas dole a yi wa ɗan yaron kaciya.4Sa'an nan tsarkakewar uwar daga zubar jini zai ci gaba har kwana talatin da uku. Ba zata taɓa wani abu mai tsarki ba ko ta shiga harabar haikali har sai kwanakin tsarkakewarta sun cika.5Amma idan ta haifi 'ya mace, za ta ƙazantu sati biyu, kamar yadda take kwanakin hailarta. Sa'an nan kwanakin tsarkakewar uwar zai ci gaba har kwana sittin da shida.6Lokacin da kwanakin tsarkakewarta suka cika, domin ɗa na miji ko mace, dole ta kawo ɗan tunkiya bana ɗaya, domin baiko na ƙonawa, da ɗan kurciya ko tattabara domin baiko na zunubi, zuwa ƙofar rumfar taruwa, zuwa ga firist.7Sa'an nan zai miƙa shi a gaban Yahweh ya yi kaffara domin ta, sa'an nan za ta tsarkaka daga zubar jininta. Wannan ita ce doka game da matar da ta haifi ɗa ko ɗiya.8Idan ba ta iya ba da tunkiya ba, to sai ta ɗauko kurciyoyi biyu ko 'yan tantabarai biyu, ɗaya domin baikon ƙonawa, ɗayan domin baiko na zunubi, sa'an nan firist zai yi kaffara domin ta; sa'an nan za ta tsarkaka.'"
Ana magana game da matar da sauran jama'a ba za su taba ba domin ta na zubar da jini daga cikin ta kamar ba ta da tsabtar jiki ne.
Wannan na nufin lokacin watan da mata tana 'yo'yo daga cikin ta.
Fristin ne kawai zai iya yin wannan aikin. AT: "dole ne fristin ya yi wa yaron kaciya"
kwana uku - Wannan na nufin cewa matar za ta zama da rashin tsarki har kwanaki talatin da uku.
kwana uku - "kwanki 33"
AT: 12:1-3...
"har kwanaki goma sha huɗu"
AT: 12:1....
kwana shida - "kwanaki 66"
"Lokacin da kwanakin tsarkakewar uwar suka cika"
Wannan na nufin lambar kwanaki dabam dabam na tsarkakewarta, bisa ga haifuwar ɗa na miji ko na mace.
AT: "sa'annan wannan zai tsarkake ta daga zubar jinin a lokacin haifuwa"
AT: "Idan ba ta da ishashen kuɗi ta saya tunkiya" Domin mika hadayan...
Ana mag game da matar da sauran jama'a za su iya taba ta ba kamar ba ta da tsabtar jiki ne.
1Yahweh ya yi magana da Musa da kuma Haruna, ya ce,2"Sa'ad da wani yana da kumburi ko ɓamɓaroki ko tabo mai haske a fatar jikinsa, har ya kamu da cuta kuma akwai cutar fata a jikinsa, dole a kawo shi ga Haruna babban firist, ko ga ɗaya daga cikin 'ya'yansa maza firistoci.3Firist zai dudduba cutar a fatar jikinsa. Idan gashin da ke cikin cutar ya zama fari, kuma idan an ga cutar ta yi zurfi fiye da fatar jiki, to cuta ce mai yaɗuwa. Bayan da firist ya dudduba shi, dole ya furta shi marar tsarki.4Idan tabon mai haske a jikinsa fari ne, kuma ba aga cutar ta yi zurfin data zarce fatar jikin ba, kuma idan gashin da ke cikin cutar bai rikiɗa fari ba, to dole firist ya ware wannan mai cutar shi kaɗai har kwana bakwai.5A rana ta bakwai, dole firist ya duba shi idan a ganinsa cutar ba ta ƙara muni ba, in kuma ba ta bazu a cikin fatar ba. Idan ba ta bazu ba, sai dole firist ya ƙara tsare shi wasu kwanaki bakwai kuma.6Firist zai sake bincike shi a rana ta bakwai ya ga ko cutar ta yi sauƙi, bata kuma ƙara bazuwa a fatar ba. Idan bata bazu ba, sai firist ya furta shi tsarkakakke. Ƙuraje ne. Dole ya wanke tufafinsa, sai ya tsarkaka.7Amma idan ɓamɓaroki ya yaɗu a cikin fatar bayan ya nuna kansa ga firist domin tsarkakewarsa, sai dole ya sake nuna kansa ga firist kuma.8firist zai sake duba shi ya ga ko ɓamɓarokin ya ƙara yaɗuwa a fatar jikin. Idan ya yaɗu, dole firist ya furta shi marar tsarki. Cutar fata ce mai bazuwa.9Idan cutar fata mai yaɗuwa tana jikin wani, dole a kawo shi wurin firist.10Firist zai duba shi ya ga ko akwai farin kumburi a fatar jikinsa, idan gashin ya rikiɗa ya zama fari, ko kuma akwai buɗaɗɗen ƙurji a kumburin.11Idan akwai, to lallai akwai riƙaƙƙiyar cutar fata mai yaɗuwa, dole firist ya furta shi marar tsarki. Ba zai ware shi ba kaɗai, gama ya rigaya ya ƙazantu.12Idan cutar ta bazu barkatai a cikin fata kuma ta mamaye duk fatar jikin mutumin daga kansa har zuwa kafafunsa, bisa ga ganin firist,13sai dole firist ya dudduba shi domin ya ga ko cutar ta rufe dukkan jikinsa. Idan kuwa haka ne, sai firist dole ya furta cewa mutumin nan mai cutar tsarkakke ne. Idan ta rikiɗa ta zama fari, to tsarkakakke ne.14Amma idan akwai buɗaɗɗen ƙurji a kansa, to ya ƙazantu.15Dole firist ya duba miƙin jikin ya furta cewa ya ƙazantu domin miƙin fatar ƙazantacce ne. Cuta ce mai yaɗuwa.16Amma idan miƙin fatar ya koma kuma ya zama fari, dole mutumin ya tafi wurin firist.17Firist zai dudduba shi ya ga ko fatar ta koma fari. Idan ya koma, sai firist ya furta wannan mutum tsarkakke ne.18Idan mutum yana da maruru a fatar jikinsa amma ya warke,19kuma a tabon marurun nan sai ga wani farin kumburi ko fata mai ƙyalli, ja da fari, to fa dole a nuna wa firist.20Firist zai dudduba ya ga ko ya shiga cikin fata sosai, kuma idan gashin wurin ya rikiɗa ya zama fari. Idan haka ne, dole firist ya furta shi marar tsarki. Cuta ce ta fata mai saurin yaɗuwa, idan ya girma a inda kumburin ya ke.21Amma idan firist ya dudduba ya ga ba farin gashi a ciki, kuma zurfin bai zarce fata ba amma ya dushe, dole firist ya ware shi da bam har kwana bakwai.22Idan ta bazu ta mamaye fatar, dole firist ya furta shi marar tsarki. Cuta ce mai yaɗuwa.23Amma idan fata mai haske ta kassance wuri guda bai bazu ba, to tabon maruru ne, dole kuma firist ya furta shi tsarkakakke.24Idan fata tana da ƙuna kuma wani buɗaɗɗen ƙurji ya fito a wurin da launi jaja-jaja fari-fari ko farin ɗigo,25sai firist ya dudduba shi ya ga ko gashin wurin ya zama fari, in kuma zurfinsa ya wuce fata. Idan haka ne, to cuta ce mai yaɗuwa. Ya ɓullo ne akan tabo, dole ne firist ya furta shi marar tsarki. Cuta ce mai yaɗuwa.26Amma idan firist ya dudduba shi ya ga babu farin gashi a wurin, kuma bai zarce fata ba amma ya dushe, sai dole firist ya ware shi shi kaɗai har kwana bakwai.27Sa'an nan ɗole firist ya dudduba shi a rana ta bakwai. Idan ya yaɗu ya mamaye fatar, dole firist ya furta shi marar tsarki. Cuta ce mai yaɗuwa.28Idan cutar ta tsaya wuri guda ba ta yaɗu cikin fatar ba amma ta dushe, to kumburi ne daga ƙuna, dole firist ya furta shi tsarkakakke, saboda ba wani abu ba ne, sai dai tabo ne daga ƙuna.29Idan namiji ko mace na da cuta mai yaɗuwa a kã ko a haɓa,30sai dole firist ya dudduba mutumin saboda cutar da ke yaɗuwa domin a ga ko ta zarce fatar jikin, idan aka ga gashi ruwan ɗorowa, kuma siriri a cikinsa. Idan akwai shi, to dole firist ya furta shi marar tsarki. Ƙaiƙai ne. Cuta ce mai yaɗuwa a kã ko a haɓa,31Idan firist ya dudduba cuta mai ƙaiƙayi ya ga babu ita ƙarƙashin fata, kuma ba baƙin gashi a ciki, to sai firist ya ware mutumin nan mai cutar ƙaiƙayi shi kaɗai har kwana bakwai.32A rana ta bakwai firist zai duba cutar ya ga ko ta bazu. Idan babu gashi mai kalar ruwan ɗorowa, kuma idan cutar ba ta zarce zurfin fata ba, sai dole a yi masa aski,33amma ba za a aske wajen cutar ba, kuma dole firist ya ware mutumin nan mai cutar ƙaiƙayi shi kaɗai kimamin wasu kwana bakwai.34A rana ta bakwai firist zai dudduba cutar ya ga ko ta dena bazuwa a cikin fatar, Idan an ga bata zarce zurfin fata ba, sai dole firist ya furta shi tsarkakakke. Dole mutumin ya wanke tufafinsa, sa'an nan za ya zama tsarkakakke,35Amma idan cutar ƙaiƙayin ta bazu da yawa a cikin fatar bayan firist ya ce ya tsarkaka,36sai dole firist ya sake dudduba shi kuma. Idan cutar ta bazu a cikin fatar, firist bai buƙatar ya nemi gashi mai launin rawaya. Mutumin ya kazantu.37Amma idan a ganin firist cutar ƙaiƙayi ta dena bazuwa kuma baƙin gashi ya toho a wurin, to cutar ta warke. Ya zama tsarkakakke, dole firist ya furta shi tsarkakakke.38Idan namiji ko mace na da farin tabbuna a fata,39sai dole firist ya dudduba mutumin ya ga ko tabbunan ba farare sosai ba ne, wannan ƙuraje ne kawai da suka farfashe a cikin fatar. Shi tsarkakakke ne.40Idan gashin namiji ya zube daga kansa, yana da saiƙo, amma yana da tsarki.41Idan gashinsa suka zube daga gaban kansa, idan goshinsa na da saiƙo, shi tsarkakakke ne.42Amma idan akwai wani ƙurji jaja-jaja fari-fari akan saiƙonsa ko goshinsa, wannan cuta ce mai yaɗuwa da ta faso.43Saboda haka dole firist ya dudduba shi ya ga ko kumburin cutar inda take a kan saiƙo ko goshinsa ya yi jaja-jaja fari-fari, da kuma kamannin cuta mai yaɗuwa ce a cikin fata.44Idan ita ce, to yana da cuta mai yaɗuwa kuma ba shi da tsarki. Tabbas kuma dole ne firist ya furta shi marar tsarki saboda cutarsa da ke a kansa.45Mutumin da ke da cuta mai yaɗuwa dole ya sa yagaggun tufafi, ya bar gashin kai ba gyara, dole kuma ya rufe fuskarsa har hanci yana kira da ƙarfi, 'Marar tsarki, marar tsarki.'46Dukkan kwanakin da ya ke da wannan cuta mai yaɗuwa zai kasance marar tsarki. Domin ya ƙazantu da cuta mai yaɗuwa, dole ya zauna shi kaɗai. Dole ya zauna a bayan sansani.47Rigar data ƙazantu da kuturta ko ta ulu ce ko rigar lilin ce,48abin da aka saƙa ko aka ɗinka daga ulu ko lilin, ko fata, ko mene ne dai da aka yi shi daga fata -49idan akwai wani kore-kore ko jaja-jajar ƙazanta a taguwar, fatar, da saƙa ko ɗinkakken yadi, ko mene ne dai da aka yi daga fata, to wannan kuturta ce data yaɗu; dole a nuna wa firist.50Dole firist ya dudduba kayan don kuturta; dole ne ya kulle duk abin da ke da kuturta har kwana bakwai.51Zai sake duba kuturtar nan a rana ta bakwai. Idan ta bazu a tufar da aka saƙa ko aka ɗinka daga ulu ko yadin lilin ko fata ko wani abu da aka yi amfani da fata, to wannan kuturta ce mai cutarwa, wannan abu ya ƙazantu.52Dole ya ƙona wannan tufar, ko sakakkiya ko ɗinkakkiyar abin da aka yi da ulu ko yadin lilin, ko fata, ko wani abin da aka yi daga fata, dukkan abin da aka sami kuturta mai cutarwa a ciki, gama zai iya kaiwa ga cuta, Dole a ƙona wannan abin ƙurmus.53Idan firist ya dudduba abin ya ga kuturta amma bata bazu cikin tufa ba ko cikin abin da aka ɗinka da yadi ko aka saƙa da ulu ko lilin, ko kayayyakin da aka yi su da fata,54sa'an nan zai umarce su su wanke kayan da aka sami kuturta a ciki, dole kuma zai kulle shi wasu kwana bakwai kuma.55Sa'an nan firist zai duba abin bayan an wanke wannan kayan mai kuturta. Idan kuturtar bata sauya launin ba, koda shike bata bazu ba, ƙazamtacce ne. Dole a ƙona wannan abin, ko ma a ina kuturtar ta ƙazamtar da shi.56Idan firist ya duba wannan abin, idan kuturtar ta dushe bayan an wanke ta, dole ya yage wannan ƙazantaccen wuri daga tufar ko fatar, ko daga saƙaƙƙe ko ɗinkakken yadi.57Idan kuturta ta sake bayyana a taguwar ko a cikin saƙaƙƙe ko ɗinkakken yadi, ko wani abin da aka yi da fata, bazuwa take yi. Dole ku ƙona duk wani abin da ke da kuturta.58Riga ko wani abin da aka saƙa ko aka ɗinka daga ulu ko yadin lilin, ko fata, ko wani abin da aka yi da fata - idan kun wanke abin kuma kuturtar ta fita, sai kuma dole ku wanke wannan abin karo na biyu, sa'an nan zai zama da tsarki.59Wannan ita ce shari'a game da kuturta a tufar ulu ko lilin, ko kowanne abin da aka saƙa ko ɗinka daga ulu ko yadin lilin, ko fata ko ko mene ne da aka yi shi da fata, domin ku furta shi mai tsarki ko marar tsarki."
AT: "dole ne wani ya kawo shi"
"ga ɗaya daga cikin 'ya'ya maza na Haruna"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da abin da ya zama dole mutanen su yi.
A nan "sa" na nufin mutumin da cutar na fatar jikinsa.
cuta da ke iya bazuwa nan da nan daga jikin mutum zuwa wani..............
"dole ne firistin ya furta mutumin mara tsarki." Ana magana game da mutumin da sauran jama'a ba za su iya taba shi ba kamar ba shi da tsabtar jiki ne.
"har kwana 7"
A nan "shi" na nufin mutmin da yake da cutar a jikinsa.
Wannan na nufin cewa idan cutar jikin bai ƙaru ko ya koma zuwa wani sashi na jiki.
"Bakwain" na nuna matsayin lamba na 7. AT: "kwana ta 7th"
"kwana 7"
Ana magana game da mutumin da sauran jama'a za su iya taba shi kamar yana da tsabtar jiki ne.
Wannan wani wuri a jikin da ke da kyama, amma ƙurajen ba za su bazu wa sauran jama'a ba.
Wannan na nufin mutumin da ya ke da cutar a jikin sa.
AT: 13:5-6
AT: 13:3
Firist din ne ke yarda ko cutar na yaɗuwa. AT: "sai wani ya kawo shi wurin firist"
A nan "buɗaɗɗen ƙurji" na iya nufin buɗaɗɗen ciwo a fatar ko sabuwar fata da ke fita, amma wurin na nan da cutar. Ko dai ɗaya daga cikin su na nuna cewa cutar bai warke da kyau ba.
Wannan cutar na cigaba har na tsahon lokaci.
AT: 13:5
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da abin da ya zama dole mutanen su yi.
AT: 13:5-6
A nan "na nufin mutumin da ke da cutar fata
Juya waɗannan kalmomin a yadda ka yi a 13:9.
An yi maganar mutumin wanda wasu mutane zasu iya taɓawa kamar yana tsabtar jiki.
Yahweh ya ji gaba da gaya wa Musa and Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani ya ke da cutar fata.
wani wuri mai zafi a fata da ya kamu
Za'a iya juya wan a aikace. AT: "sa'an nan dole ne ya nuna shi wa firist"
an yi maganar mutumin wanda wasu mutane dole kada su taɓa shi kamar ba shi da sabtar jiki
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa da Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani yake da cutar fata.
A nan "shi" na nufin farin gumburi ko tabo mai haske a fatar.
An yi maganar mutumin wanda wasu mutane dole kada su taɓa kamar ba ya da tsabtar jiki.
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa da Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani yana da cutar jiki.
Juya wannan kalmomin a yadda ka yi a 13:3.
An yi maganar mutumin wanda wasu mutane dole kada su taɓa shi ba kamar ba su da tsabtar jiki
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa da Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani yana da cutar jiki.
A nan "shi" na nufin unar da ke a fatar mutumin.
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa da Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani yana da cutar jiki.
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa da Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani yana da cutar jiki.
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa da Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani yana da cutar jiki.
Za'a iya juya wannan a aikace. AT: "mutumun dole ne ya aske gashin da ke kusa da ciwon amma ba gashin da ke a ciwon ba"
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa da Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani yana da cutar jiki.
A nan "Cutar" na nufin cutar da ke a kan ko haɓar mutumin.
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa da Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani yana da cutar jiki.
An yi maganar mutumin wanda wasu mutane dole kada su taɓa kamar ba ya da tsabtar jiki
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa da Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani yana da cutar jiki.
Juya wannan kalma kamar yadda kayi a 13:5.
"Wancan mutumin na da tsabta"
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa da Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani yana da cutar jiki.
An yi maganar mutumin wanda wasu mutanemai yiwu wa kada su taɓa kamar ba shi da tsabtar jiki
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa da Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani yana da cutar jiki.
An yi maganr mutumin wanda wasu mutane mai yiwu wa ba za su taɓa ba kamar ba shi da tsabtar jiki.
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Musa da Haruna abin da mutane dole su yi a lokacin da wani yana da cutar jiki.
Sansanin shi ne wurin da mafi yawn Isra'ilawa suka zauna. Ba a ba mutum mara tsabta izini ya zauna a cikin su ba domin cutar shi zata iya kama sauran mutanen.
"Rigar da ke da hunhuna a kai" ko "Rigar da ke hunfuna
naman gwari, sau da yawa fari a launi, da ke girma a abubuwa da ke ɗanye ko da laima
Za'a iya juya wannan a aikace. AT: dole ne mai shi ya nuna wa firist" (UDB) (Dubi:
"kwana 7"
"ta bakwai" ita ce lambar da ta nuna matsayin 7. AT: "ranar 7th"
Za'a iya juya wannan a aikace. AT: "duk wani abu da mutum yayi anfani da fata"
Funfuna mai cutarwa zai iya samar da cuta a mutum wanda yayi cuɗanya da abun.
"sa'an nan first zai umurce masu shi" A nan firist ɗin na gaya wa mutanen abin da zasu yi da abubuwan iyali da ke kame da cutar.
Za'a iya iya juya wannan a aikace. AT: "bayan sun wanke abin da ke da hunhuna"
A nan "ka" baya nufin firist a musamman. Kawai yana nufin dole wani ya ƙone abun.
Za'a iya juya wannan a aikace. AT: "bayan da mai shi ya wanke shi"
Za'a iya juya wannan a aikace. AT: "idan mai shi ya wanke shi"
An yi maganar abun da Allah ya furta ya zama ya dace wa mutane su taɓa kamar yana da tsabtar jiki.
Juya waɗannan kalmomin kamar yadda kayi a 13:47.
"domin in ya yiwu firsit ya furta shi"
1Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"Wannan ce shari'a domin mutum mai cuta a ranar tsarkakewarsa. Dole ne a kawo shi ga firist.3Firist zai fita daga cikin zango domin ya dudduba mutumin ya ga ko cutar mai yaɗuwa a fata ta warke.4Sa'an nan firist zai bada doka cewa wanda za a tsarkake ya ɗauki tsuntsaye biyu masu rai, masu tsabta, da itacen sida. da jan zare, da ɗaɗɗoya.5Firist zai umarce shi ya kashe ɗaya daga cikin tsuntsayen a kan ruwa mai tsabta da ke cikin tukunyar yumɓu.6Firist zai ɗauki tsuntsun mai rai da itacen sida, da jan zare da ɗaɗɗoyar, yatsoma dukkan waɗannan abubuwa, har ma da tsuntsun nan mai rai, a cikin jinin tsuntsun da aka kashe a kan ruwa mai tsabta.7Sa'an nan firist zai yayyafa wannan ruwa sau bakwai a kan mutumin da za a tsarkake daga cutar, sa'an nan firist zai furta cewa ya tsarkaka. Sa'an nan firist zai saki tsuntsun mai rai ya yi tafiyarsa jeji.8Mutumin da ake tsarkakewa zai wanke tufafinsa, ya aske dukkan gashinsa, ya yi wanka da ruwa, sa'an nan zai tsarkaka. Bayan wannan dole ya dawo cikin zango. amma ba zai zauna a cikin rumfarsa ba sai bayan kwana bakwai.9A rana ta bakwai dole ya yanke dukkan gashin kansa, kuma dole ya aske gemunsa da girar idonsa. Dole ya aske dukkan gashinsa, kuma dole ya wanke tufafinsa ya yi wanka da ruwa; sa'an nan zai zama da tsarki.10A rana ta takwas dole ya ɗauki 'yan raguna biyu marasa lahani, da 'yar tunkiya bana ɗaya marar lahani, da kashi uku bisa goma na mudun lallausar gari cuɗaɗɗe da mai domin baiko ta hatsi, da moɗar mai ɗaya.11Firist da ya tsarkake shi zai tsaida wanda za a tsarkake, tare da waɗannan abubuwa, a gaban Yahweh a ƙofar rumfar taruwa.12Firist zai ɗauki ɗaya daga cikin 'yan ragunan ya miƙa shi baiko domin laifi, tare da moɗar mai; zai kaɗa su domin baiko na kaɗawa a gaban Yahweh.13Dole ya yanka ɗan ragon a inda suke yanka baye-baye na zunubi da baye-baye na ƙonawa, a harabar haikali, domin baiko na zunubi rabon firist ne, haka ma baiko na laifi, domin mafi tsarki ne.14Firist zai ɗauki kaɗan daga cikin jinin baikon domin laifi ya sa shi a leɓatun kunnen dama na mutumin da za a tsarkake, da kan babban yatsan hannun damansa, da kan babban yatsan ƙafarsa ta dama.15Sa'an nan firist zai ɗauki mai daga moɗar ya zuba shi a tafin hannun hagunsa,16ya tsoma yatsansa na dama a cikin man da ke tafin hannunsa na hagu, ya yayyafa daga man da yatsansa sau bakwai a gaban Yahweh.17Firist zai sa ragowar man a hannunsa a kan leɓatun kunnen dama na mutumin da za a tsarkake, da a kan babban yatsan hannunsa na dama, da a kan babban yatsan ƙafarsa ta dama. Dole ya sa wannan mai a kan jinin baiko domin laifi.18Game da sauran man da ke hannun firist, zai sa shi a kan mutumin da za a tsarkake, firist kuma zai yi kaffara dominsa a gaban Yahweh.19Sa'an nan firist zai miƙa baiko na zunubi ya yi kaffara domin wanda za a tsarkake saboda rashin tsarkinsa, bayan wannan zai yanka baiko na ƙonawa.20Sa'an nan firist zai miƙa baiko na ƙonawa da kuma baiko na hatsi a kan bagadi. Firist zai yi kaffara domin wannan mutumin, sa'an nan zai zama da tsarki.21Amma, idan mutumin matalauci ne har ba zai iya ba da waɗannan hadayu ba, to sai ya ɗauki ɗan rago ɗaya domin baiko na laifi saboda a kaɗa shi, a yi kaffara dominsa, da awon garwa na gari mai laushi da aka kwaɓa da mai domin baiko na hatsi, da mai a moɗa,22tare da kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu, iyakar dai abin da ya iya samu; tsuntsu ɗaya zai zama na baikon zunubi ɗayan kuma baiko na ƙonawa.23A rana ta takwas dole ya kawo su domin tsarkakewarsa ga firist, zuwa ƙofar shiga rumfar taruwa, a gaban Yahweh.24Firist zai ɗauki ragon domin baiko, zai ɗauke shi tare da moɗar man zaitun, sai ya ɗaga su sama sosai sa'ad da ya ke miƙa wa Yahweh.25Zai yanka ɗan ragon baiko domin laifi, zai ɗauki ɗan jinin baiko domin laifi ya sa su a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsarkake, da kan babban yatsan hannun dama, da kan babban yatsan ƙafar damansa.26Sa'an nan firist zai zuba daga cikin man a tafin hannunsa na hagu,27kuma ya yayyafa da ɗan yatsansa na dama daga cikin man da ke tafin hannunsa na hagu sau bakwai a gaban Yahweh.28Firist zai sa daga man da ke tafin hannunsa a kan leɓatun kunnen dama na wanda za a tsarkake, da kan babban yatsan hannun damansa, da kuma kan babban yatsan ƙafar damansa, a nan wuraren da ya sa jinin baiko domin laifi.29Zai sa sauran man da ke hannunsa a kan wanda za a tsarkake, domin a yi kaffara dominsa a gaban Yahweh.30Dole ya miƙa ɗaya daga cikin 'yan kurciyoyin ko 'yan tantabarai, gwargwadon abin da mutumin ya iya samowa -31ɗaya domin baikon zunubi ɗaya kuma domin baiko na ƙonawa, tare kuma da baiko na garin hatsi. Sai firist ya yi kaffara domin wanda za a tsarkake a gaban Yahweh.32Wannan ita ce doka domin mutumin da ke da cutar fata mai yaɗuwa, wanda ya gaza bayarwa bisa ga ka'idodin baye-baye domin tsarkakewarsa."33Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna, cewa,34"Sa'ad da kuka shiga cikin ƙasar Kan'ana wanda na ba ku ta zama mallakarku, idan na sa kuturta mai yaɗuwa a cikin gida cikin ƙasar mallakarku,35sai dole mai wannan gida ya tafi ya faɗa wa firist. Dole ne ya ce, 'Ni a gani na akwai wani abu kamar kuturta a cikin gidana.'36Sa'an nan firist zai umarta a fitar da komai daga cikin gidan kafin ya shiga ya duba ya tabbatar akwai kuturtar, domin kada a ƙazamtar da dukkan abin da ke gidan. Bayan wannan firist zai shiga ya duba cikin gidan.37Dole ya dudduba kuturtar ya ga ko tana bangayen gidan, ya duba ko yana da kore-koren launi ko jaja-jaja cikin zurfin bangayen.38Idan akwai kuturta a gidan, sai firist ya fita daga gidan ya rufe ƙofar gidan har kwana bakwai.39Sa'an nan firist zai sake dawowa a rana ta bakwai ya dudduba shi domin ya ga ko kuturtar ta bazu a bangayen gidan.40Idan ta bazu, sai firist ya umarta a cire duwatsun da aka tarar da kuturta a jefar da su a wuri marar tsabta a bayan birni.41Zai sa a kankare dukkan bangayen cikin gidan, dole kuma a kwashe dukkan ƙazamtattun kayayyakin da aka kankare a kai su can bayan birni a zuba su a wuri marar tsabta.42Dole su ɗauki wasu duwatsu su cike gurbin waɗancan duwatsun da aka cire, dole kuma su yi amfani da sabuwar ƙasa su yaɓe gidan.43Idan kuturta ta sake ɓullowa cikin gidan da aka ciccire duwatsun bangayen aka kakankare su aka kuma yi sabon shafe,44sai dole firist ya shiga ciki ya dudduba gidan ya ga ko kuturtar ta bazu a cikin gidan. Idan ta bazu, to kuturtar mai cutarwa ce, gidan kuma ya ƙazantu.45Dole ne a rushe gidan nan. Da duwatsun, da katakan, da dukkan shafen cikin gidan dole a kwashe su daga cikin birni zuwa wuri marar tsabta.46Bugu da ƙari, duk wanda ya shiga cikin gidan a lokacin da aka kulle gidan zai zama marar tsarki har maraice.47Duk wanda ya kwana a cikin gidan dole ya wanke tufafinsa, kuma duk wanda ya ci a cikin gidan dole ya wanke tufafinsa.48Idan firist ya shiga domin ya dudduba ya ga ko kuturtar ta yaɗu a cikin gidan bayan an yi wa gidan yaɓe, sa'an nan, idan kuturtar ta tafi, sai ya furta wannan gida tsarkakakke.49Sai dole firist ya ɗauki tsuntsayen biyu domin tsarkake gidan, da itacen sida, da shuɗin zare, da ɗaɗɗoya.50Sai ya kashe ɗaya tsuntsun a bisa ruwa mai tsabta cikin tukunyar yumɓu.51Zai ɗauki itacen sida, da ɗaɗɗoyar, da shuɗin zaren da kuma tsuntsun mai rai, ya tsoma su cikin jinin ɗaya tsuntsun da aka kashe, cikin ruwan nan mai tsabta, ya yayyafa gidan sau bakwai.52Zai tsarkake gidan da jinin tsuntsun da ruwan nan mai kyau, tare da tsuntsun nan mai rai, da itacen sida, da ɗaɗɗoya, da kuma jan zare.53Amma zai bar tsuntsun mai rai ya fita daga cikin birni ya tafi jeji. Ta haka ne dole zai yi kaffara domin gidan, zai kuma zama da tsarki.54Wannan ita ce shari'a domin dukkan irin cutar fata mai yaɗuwa, da abubuwan da ke sa irin wannan cuta, ko ƙaiƙayi,55da kuma kuturta a cikin tufafi da cikin gida,56da kumburi, da ƙuraje, da kuma tabo,57domin a tabbatar da lokacin da makamantan haka ba tsarki ko da tsarki. Wannan ita ce shari'a a kan cututtukan fatar jiki mai yaɗuwa da kuma kuturta.
Yahweh ya gaya wa Musa da Haruna abin da mutanen dole su yi a lokacin da aka warkar da wani daga cutar fata.
Wannan na nufin ranar da firist bayyana mutumin ya zama mai tsabta bisa ga al'ada.
Za'a iya juya wannan a aikace. AT: "DOle ne wani ya kawo shi wurin firist" ko "Dole ne ya je wurin firist"
Yahweh ya cigaba da gaya wa musa da Haruna game da ya zama dole mutane za su yi idan aka tsarkake mai cutar fatar jiki.
AT: 13:3.
AT: "mutumin da zai tsarkake" (Dubi:
AT: 13:3
"da jan zare"
AT: "mutumin da zai tsarkake"
Yahweh ya cigaba da gaya wa musa da Haruna game da ya zama dole mutane za su yi idan aka tsarkake mai cutar fatar jiki.
AT: "tsunsu da mutumin ya ƙashe"
AT: 14: 1-3
Yahweh ya cigaba da gaya wa musa da Haruna game da ya zama dole mutane za su yi idan aka tsarkake mai cutar fatar jiki
Yahweh ya cigaba da gaya wa musa da Haruna game da ya zama dole mutane za su yi idan aka tsarkake mai cutar fatar jiki
AT: "Mutumin da firit ke tsarkakewa"
Mutumin da ake tsarkakewa
A nan "shi" na nufin matumin da aka tsakake.
mudun lallausa ɗaya shine lita 22
moɗa ɖaya shine lita0.31 (Dubi:
AT: "Mutumin da yake tsarkakewa"
moda ɗaya shine lita 0.31.
Dole ya yanka ɗan ragon a inda suke yanka baye-baye
AT:14:10-11
moɗa ɗaya shine lita 0.31.
ya yayyafa wasu man da yatsansa sau bakwai a gaban Yahweh.
"sauran man da ke a hannun sa"
AT: 14:10-11
"a gaban Yahweh"
AT: 14:16-18
AT:14:16-18
Yahweh ya cigaba da gaya wa musa da Haruna game da ya zama dole mutane za su yi idan aka tsarkake mai cutar fatar jiki.
"ba shi da isasshen ƙudin da zai saya"
Za'a iya juya shi a aikace. AT: "cewa firist kaɗa hannunsa... don shi"
...
moɗa ɗaya shine lita ɗaya.
...
14:18-20
Yahweh ya cigaba da gaya wa musa da Haruna game da ya zama dole mutane za su yi idan aka tsarkake mai cutar fatar jiki.
zai zuba daga cikin man a tafin hannunsa
AT: 14:15
"Dole ne firist ya mika"
AT: 14:11-15
AT: 13:3.
AT: "wWanda ba shi da ishashen kudi domin ya saya"
A nan "ku" na nufin mutanen Isra'la ne.
AT:13:47
Kalmar nan "mallaka" kalmar aiki ce.
Da zaran da firist ya .........
Dole ya dudduba kuturtar ya ga ko tana bangayen gidan
Wannan na nufin cewa firist din ne zai zaɓa ko kuturtar ya yi zurfi ko yana bisa bangon ne.
AT: "inda aka samu kuturtan"
inda mutane ba za su iya zamna ba
A nan "Shi" yana nufin firist.
Za'a iya juya wannan a aikace. AT" "cewa mai gidan ya kankare duka bangon gidan"
Wannan na nufin kayan da ke da fumfuna a kai. Za'a iya juya wannan a aikace. AT: "gurɓatattun kayan da aka kankare
Wurin da bai dace mutane su zauna ko an yi maganar anfani domin manufar Allah kamar mara tsabta ta jiki.
Za'a iya juya wannan a aikace. AT: "duwatsun da suka cire"
"dole ne su rufe duwatsun da sabon lãka"
Za'a iya juya wannan a aikace. AT: "a cikin gidan bayan mai gidan ya ɗauke duwatsun, ya kankare bangon, kuma ya rufe sabon duwatsun da lãka"
an yi maganar gidan da bai chanchanta mutane su zauna ba kamar bai da tsabtar jiki.
Za'a iya juya wannan a aikace. AT: Dole ne su rushe gidan"
Za'a iya juya wannan a aikace. AT: Dole ne su ɗauke duwatsun, katakon, da kuma duka shafen da ke a cikin gidan"
Mutum wanda wasu mutane mai yiwu wa bha zasu taɓa ba kuma wanda ba karɓabɓe ba ne domin manufar Allah domin ya shiga cikin gidan da aka yi magana kamar mutumin bai da tsabtar jiki.
AT: "mai shi ya saka laka a kan dutsen"
Inda mutane zasu zamna
AT: 14:3
AT: "jinin tsuntsun da aka kashe"
...
AT: 14:42
AT: 13:3
AT: 13:47
AT: 13:5
AT: 14:15
1Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna, cewa,2"Ka yi magana da mutanen Isra'ila, ka ce masu, "Yayin da kowanne mutum ya ke da ruwan da ke fitowa daga cikin jikinsa, ya zama ƙazantacce.3Ƙazantarsa sakamakon wannan cutar ruwan ce. Ko jikinsa yana zubar da ruwan ko ya tsaya, kazantacce ne.4Kowanne gadon da ya kwanta akai zai ƙazantu, duk abin da ya zauna akansa kuma zai ƙazantu.5Duk wanda ya taɓa gadonsa dole ya wanke tufafinsa kuma ya yi wanka cikin ruwa, kuma ya ƙazantu har yamma.6Duk wanda ya zauna akan kowanne abin da da mutum mai cutar zubar ruwan nan ya zauna akai, wannan mutum dole ya wanke tufafinsa ya kuma yi wanka cikin ruwa, kuma zai zama marar tsabta har yamma.7Duk wanda ya taɓa jikin mai cutar zubar ruwa dole ya wanke tufafinsa kuma ya yi wanka cikin ruwa, ya ƙazantu har yamma.8Idan mutumin nan mai cutar zubar ruwa ya tofa miyau a bisa wani mai tsabta, daga nan wannan mutumin dole ya wanke tufafinsa ya yi wanka cikin ruwa, kuma ya ƙazantu har yamma tayi.9Kowanne sirdi da mai zubar ruwan ya hau kai zai zama ƙazantacce.10Duk wanda ya taɓa kowanne abin da ke ƙarƙashin mutumin zai ƙazantu har yamma, kuma wanda ya ɗauki waɗannan abubuwan dole ya wanke tufafinsa ya yi wanka cikin ruwa; ya ƙazantu har yamma ta yi.11Duk wanda mai cutar zubar ruwan ya taɓa ba tare da ya ɗauraye hannuwansa da farko cikin ruwa ba, mutumin da aka taɓa dole ya wanke tufafinsa ya yiwa kansa wanke cikin ruwa, kuma zai zama marar tsabta har yamma ta yi.12Kowacce tukunyar yumɓun da mai irin wannan zubar ruwan ya taɓa dole a fasata, kuma kowanne akushin itace dole a ɗauraye shi cikin ruwa.13Sa'ad da shi mai zubar ya tsarkaka daga zubar tasa, daga nan sai ya ƙirgawa kansa kwana bakwai domin tsarkakewarsa; daga nan dole ya wanke tufafinsa ya kuma yi wanka cikin ruwa mai gudu. Daga nan zai tsarkaka.14A rana ta takwas dole ya ɗauki "yan kurciyoyi biyu ko 'yan tantabarai guda biyu ya zo gaban Yahweh a ƙofar shiga rumfar taruwa; a can dole ya bada tsuntsayen ga firist.15Dole firist ɗin ya miƙa su, ɗaya a matsayin hadayar zunubi ɗaya a matsayin ƙonanniyar hadaya, kuma dole firist ya yi kaffara domin sa a gaban Yahweh domin zubarsa.16Idan kowanne mutum yana da fitaccen maniyyi, daga nan dole ya wanke dukkan jikinsa cikin ruwa; zai zama marar tsabta har yamma.17Kowacce riga ko tufar fata inda akwai maniyyin dole a wanke ta da ruwa; zata zama marar tsarki har yamma.18Idan mace da miji suka kwanta tare kuma akayi canjin maniyyi zuwa gare ta, dole dukkansu su yi wanka cikin ruwa; zasu zama marasa tsarki har yamma.19Idan mace tana haila, rashin tsarkinta zai ci gaba har kwana bakwai, kuma duk wanda ya taɓata zai ƙazantu har yamma ta yi.20Kowanne abin data kwanta akai lokacin al'adarta zai zama marar tsarki; kowanne abin data zauna akansa kuma zai zama marar tsarki.21Duk wanda ya taɓa gadonta dole ya wanke tufafinsa kuma ya wanke kansa cikin ruwa; wannan mutumin zai zama marar tsarki har yamma.22Duk wanda ya taɓa kowanne abin data zauna a kansa dole ya wanke tufafinsa ya kuma yi wanka cikin ruwa; wannan mutumin zai ƙazantu har yamma.23Ko akan gado ko akan kowanne abin da ta zauna akai, idan ya taɓa shi, wannan mutumin zai zama marar tsarki har yamma.24Idan kowanne mutum ya kwana da ita, kuma idan zubar rashin tsarkinta ya taɓa shi, zai zama marar tsarki har kwana bakwai. Kowanne gadon da ta kwanta kai zai zama marar tsarki.25Idan mace tana zubar jini kwanaki da yawa wanda ba cikin kwanakin hailarta bane, ko idan tana zuba fiye da kwanakin hailarta, lokacin dukkan kwanakin zubar rashin tsarkinta, zata zama kamar tana cikin kwanakin hailarta. Marar tsarki ce.26Kowanne gadon data kwanta akai dukkan kwanakin zubar jininta zai zama a gareta kamar gadon data kwanta akai lokacin hailarta, kuma duk abin data zauna akai zai ƙazantu, kamar rashin tsarkin ta na haila.27Duk wanda ya taɓa kowanne ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan zai zama marar tsarki; dole ya wanke tufafinsa ya kuma wanke kansa cikin ruwa, kuma ya zama marar tsarki har yamma tayi.28Amma idan ta tsarkaka daga zubar jininta, daga nan sai ta lisafta wa kanta kwanaki bakwai, bayan wannan ta tsarkaka.29A rana ta takwas za ta ɗauki 'yan'kurciyoyi guda biyu ko 'yan' tantabarai guda biyu za ta kawo su wurin firist a ƙofar rumfa ta taruwa.30Firist zai miƙa tsuntsu ɗaya a matsayin hadaya ta zunubi, ɗayan kuma domin ƙonanniyar hadaya, kuma zai yi kaffara domin ta a gaban Yahweh domin zubar jininta.31Ta haka za ku keɓe mutanen Isra'ila daga ƙazantarsu, domin kada su mutu ta wurin ƙazantarsu, ta wurin ɓata rumfar sujadata, in da nake zama a tsakiyar su.32Waɗannan su ne ka'idodi domin duk wanda ya ke zubar ruwa, domin kowanne mutum da maniyinsa ya fita daga gare shi ya sa shi ya zama marar tsarki,33ga kowacce mace da ke haila, da duk wanda ya ke zubar ruwa, ko namiji ko mace, da kuma duk wanda ya kwana da matar da ta ƙazanta.'"
Wannan na nufin jikin mutum.
AT: 14:15
"jikinsa ya zama ƙazantacce" ko " ya zama ƙazantacce"
Kowanne gadon da ya kwanta akai zai ƙazantu, duk abin da ya zauna akansa kuma zai ƙazantu.
AT: 14:15
"har faɗiwar rana"
AT: 15:4
"har faɗiwar rana"
"Duk wanda ya taɓa jikin"
AT: 14:15
AT: 14:15
Sirdi kujerar leda ne da mutum ke sakawa a bayan doki domin ya iya tuka ta.
Ana magana game da abin da Yahweh ya furta cewa a taba kamar ba shi da tsabtar jiki ne.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa da Haruna game da mutanen zasu yi domin guje wa cutar.
Wannan na nufin mutumin da ya kama cutar.
AT: 14:15
AT: 15:4-5
"Duk wanda mai cutar zubar ruwan"
AT: "mutumin da ya taɓa"
AT: "Sai wani ya fasa tukunyar lakar da mutumin da ke da zuɓar ruwan ya taba"
AT: "Sai wani ya ɗauraye akushin itace cikin ruwa"
Ana magana game da mai zubar ya warke daga cutar kamar ya zama da tsabta ta jiki ne. AT: "Ya warke daga zubar tasa"
Ana magana game da mutumin da mutane zasu iya tabawa kamar suna da tsabtar jiki ne.
AT: 15:8.
AT: 15:8
AT: "dole a wanke ta da ruwa"
Dukkan waddanan na nufin idan jini na zuɓa daga cikin mace.
"za ta cigaba da zama marasa tsarkaka"
Ana maga game da mutane da abubuwan da sauran jama'a baza su taba ba kamar basu da tsabtar jiki ne.
Wannan na nufin matar da take hailar.
AT: 19:20
AT:15:8
"zubar rashin tsarkinta" ko "jini daga cikin ta"
An magana da abubuwab da sauran jama'a baza su taba ba kamar ba su da tsabtar jiki ne.
Wannan na nufin cewa idan matan ta na zubar da jini daga cikin ta ă kowane lokaci fiye da ainihin lokacin hailar ta, za ta zama kuma marasa tsarki kamar lokacin hailar ta.
Ana magana game da mutanen da sauran jama'a baza su iya taɓa su ba kamar basu da tsabtar jiki ne.
A nan ana magana game da abubuwa da sauran jama'a ba za su iya taɓawa ba kamar basu da tsabtar jiki ne.
Ƙalman nan "ta" na nufin matar da take hailar.
A nan ana magana game da matar da samun sauki daga zubar jinin ta kamar ta zama da tsabtar jiki ne. AT: "ta warke daga zubar jinin ta"
A nan ana magana game da matar da sauran jama'a zasu iya taɓa ta kamar tana da tsabtar jiki ne.
"zata ɗauki da kanta"
"zubar jinin ta da ya mayad da ita mara tsarkaka"
Yahweh yana magana game da hana mutanen nan yin ƙazamta kamar yana keɓe su ne daga ƙazamtar su. AT: "Ta haka ne za ku keɓe mutanen Isra'ila daga ƙazamta"
A nan ana magana game da mutanen da sauran jama'a baza su taɓa ba, waddanda basu dace da nufin Allah ba kamar basu da tsabtar jiki ne.
"Waddanan abubuwan ne sun zama dole a yi su"
A nan ana magana game da mutanen da sauran jama'a baza su taɓa ba kamar basu da tsabtar jiki ne.
"wadda take haila" ko "wadda take zuba daga cikin ta"
1Yahweh ya yi magana da Musa -- wannan bayan mutuwar 'ya'yan Haruna guda biyu, lokacin da suka kusato Yahweh kuma suka mutu.2Yahweh ya ce da Musa. "Ka yi magana da Haruna ɗan'uwanka ka ce masa kada kowanne lokaci ya riƙa shiga wuri mai tsarki cikin labule, a gaban mazaunin jinƙai wanda ke bisa kan akwatin al̀ƙawari. Idan ya yi haka, zai mutu, saboda ina bayyana cikin girgije a bisa mazaunin jinƙai.3Don haka ga yadda Haruna zai shiga wuri mafi tsarki. Dole ya shiga da ɗan bijimi domin hadaya ta zunubi, da rago domin hadaya ta ƙonawa.4Dole ya sanya riga mai tsarki, kuma dole ya sa riga 'yarciki a jikinsa, kuma dole ya sa ɗamarar linin da rawanin linin. Waɗannan su ne riguna masu tsarki. Dole ya wanke jikinsa cikin ruwa daga nan ya shirya kansa da waɗannan rigunan.5Dole ya karɓi bunsura biyu daga taron jama'ar Isra'ila a matsayin baikon zunubi da rago ɗaya domin ƙonanniyar hadaya.6Daga nan dole Haruna ya miƙa bijimi domin baikon zunubi, wanda ya ke domin kansa, zai yi kaffara domin kansa da iyalinsa.7Daga nan dole ya ɗauki bunsura biyun ya ajiye su gaban Yahweh a ƙofar shiga rumfar taruwa.8Daga nan dole Haruna ya jefa ƙuri'a domin bunsuran biyu, ɗaya domin Yahweh, ɗaya a matsayin refataccen bunsuru.9Daga nan dole Haruna ya miƙa bunsurun da ƙuri'a ta faɗa wa ga Yahweh, kuma ya miƙa bunsurun a matsayin baikon zunubi.10Amma bunsurun da ƙuri'a ta faɗa wa a matsayin refataccen bunsuru dole a kawo shi da rai gaban Yahweh, domin kaffara ta wurin aikar da shi a matsayin refataccen bunsuru cikin jeji.11Daga nan dole Haruna ya miƙa bijimi domin baikon zunubi, wanda zai zama domin kansa. Dole ya yi kafara domin kansa da kuma domin iyalinsa, dole ya yanka bijimi a matsayin baikon zunubi domin kansa.12Dole Haruna ya ɗauki kasko cike da garwashin wuta daga bisa bagadi gaban Yahweh, hannuwansa kuma cike da gyararren garin turare mai ƙanshi, ya kuma kawo waɗannan abubuwan cikin labule.13A can dole ya ɗibiya turare akan wuta gaban Yahweh domin hayaƙi daga turaren ya rufe marfin kaffara a bisa dokokin alƙawarin. Dole ya yi haka domin kada ya mutu.14Daga nan dole ya ɗauki jinin bijimi ya yayyafa shi da yatsansa a gaban marfin kaffara. Dole ya yayyafa sauran jinin da yatsansa sau bakwai gaban mazaunin jinƙai.15Sa'an nan dole ya yanka bunsuru domin hadayar zunubi wanda ya ke domin jama'a ya kawo jininsa cikin labule. A can dole ya yi da jinin kamar yadda ya yi da jinin bijimin: Dole ya yayyafa shi a bisa murfin kafara da kuma gaban murfin kafara.16Dole ya yi kafara domin wuri mai tsarki saboda ƙazantar ayyukan mutanen Isra'ila, da kuma domin tayarwarsu da dukkan zunubansu. Dole kuma ya yi haka kuma domin rumfar taruwa, inda Yahweh ke zama cikinsu, a gaban ƙazantattun ayyukansu.17Ba wanda zai kasance a rumfar taruwa sa'ad da Haruna ya shiga domin ya yi kaffara cikin wuri mafi tsarki, har lokacin da ya fito ya kuma gama yin kaffara domin kansa da kuma iyalinsa, da kuma dukkan taron Isra'ila.18Dole ya fita zuwa bagadin da ke gaban Yahweh domin ya yi kaffara domin sa, kuma dole ya ɗibi jinin bijimi da jinin akuyar ya sa shi a bisan ƙahonnin bagadi ko'ina kewaye.19Dole ya yayyafa daga cikin jinin a kai da yatsansa sau bakwai ya tsabtace shi ya keɓe shi ga Yahweh, nesa daga ƙazantar ayyukan mutanen Isra'ila.20Sa'ad da ya gama yin kaffara domin wuri mafi tsarki, rumfar taruwa, da bagadi, dole ya miƙa bunsurun mai rai.21Dole Haruna ya ɗibiya hannayensa a kan bunsurun mai ran ya furta dukkan muguntar mutanen Isra'ila, dukkan tayarwarsu, da dukkan zunubansu. Daga nan dole ya sa zunubansu a kan bunsurun ya sallami bunsurun ta wurin kulawar mutumin da ya shirya ya jagoranci bunsurun zuwa cikin jeji.22Dole bunsurun ya ɗaukarwa kansa dukkan muguntar mutane zuwa wurin da ba kowa. A can cikin jeji, mutumin zai saki bunsurun ya tafi hakanan.23Daga nan dole Haruna ya koma cikin rumfar taruwa ya tuɓe rigunansa na linin waɗanda ya sa kafin ya shiga wuri mafi tsarki, kuma dole ya bar rigunan can.24Dole ya wanke jikinsa a cikin ruwa cikin wuri mai tsarki, ya sa tufafinsa da ya saba; daga nan dole ya fito ya miƙa baikonsa na ƙonawa da baikon ƙonawa domin jama'a, ta haka zai yi kaffara domin kansa kuma domin jama'a.25Dole ya ƙone kitsen baikon zunubi a bisa kan bagadi.26Mutumin da ya bar refataccen bunsuru ya tafi dole ya wanke tufafinsa ya kuma yi wanka cikin ruwa; bayan haka, zai iya dawowa cikin sansani.27Bijimi domin baikon zunubi da bunsurun domin baikon zunubi, wanda aka kawo jininsu domin kaffara cikin wuri mai tsarki, dole a ɗauke su waje bayan sansani. A can dole su ƙone fatarsu, namansu, da kashinsu.28Mutumin da ya ƙone waɗannan sassan dole ya wanke tufafinsa ya wanke jikinsa cikin ruwa; bayan haka, zai iya dawowa cikin sansani.29Zai zama farilla a gare ku kullum a cikin wata na bakwai, a bisa rana ta goma, dole ku ƙasƙantar da kanku kada ku yi aiki, ko wanda aka haifa ɗan gari ko bãƙo wanda ya ke zama a cikinku.30Saboda a ranar nan za ayi kaffara domin ku, a tsarkake ku daga dukkan zunubanku domin ku tsarkaka a gaban Yahweh.31Assabat ta musamman ta hutawa domin ku, dole kuma ku ƙasƙantar da kanku kada ku yi wani aiki. Wannan zai zama farilla a gare ku kullum.32Babban firist, wanda za a zuba masa mai a keɓe shi ya zama babban firist a madadin mahaifinsa, dole ya yi wannan kaffarar ya sa tufafin linin, wato, tufafi masu tsarki.33Zai yi kaffara domin wuri mafi tsarki; dole ya yi kaffara domin rumfar taruwa da kuma domin bagadi, kuma dole ya yi kaffara domin firistoci kuma domin dukkan taron jama'a.34Wannan zai zama farilla a gare ku koyaushe, a yi kaffara domin mutanen Isra'ila saboda dukkan zunubansu, sau ɗaya a cikin shekara." An yi haka kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.
Wannan na nufin Nadab da Abihu. Sun mutu domin sun kawo wutar da Yahweh bai yarda da shi ba. (Dubi: 10:1)
"Ga yadda"
"rigar ciki." Wannan riga ce da ake sakata kusa da fatar jiki a ƙarkashin ainihin kayan.
Ɗan kayan da ake ɗourawa a kwanƙwaso ko kirji
Wannan ɗan kaya ne da ake dourawa a kai.
"daga taron jama'ar "
"baikon zunubi domin kansa"
"akuyar da aka ƙora." Yakamata Haruna ya saka wani ya saki akuyan cikin jeji.
"wanda aka shirya domin kuri'ar"
AT: "Amma, yazama dole ne Haruna ya kawo bunsurun ... da rai a gaban Yahweh"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da dole ne Haruna zai yi a ranar kafarar
Haruna zai tăre jinin bajimin nan a kwano domin nan gaba ya iya 'yafa ta a marfin kafarar. Za a iya bayyana ma'anar kalman nan a fili.
ɗan gongonin wuta da turare da firistoci suke amfani da shi
"turare mai ɗadin ƙamshi." Wannan na nufin ƙamshi, ba ɗandano turaren ba.
Wannan jinin da Haruna ya tare da kwano ne AT: 16:11.
Ya yi amfani da yatsansa domin ya yafa jinin.
Ya saka jinin a saman marfin. Ya sake saka ta a gefen marfin da ke fuskantar sa a yayen da yake shigowa wuri mafi tsarkin.
Ma'ana mai yiwuwa 1) "a kasan marfin kaffaran a ta ƙirjin" ko 2) "a kasa a gaban marfin kaffaran."
AT: 16:11
AT: 16:14
Zunuban mutanen Isra'ila ya ƙazamtad da wuri mai tsarkin.
Waddanan kalaman suna nufin abu ɗaya ne. Suna nanata cewa mutanen sun aikata zubai dayawa.
A nan ana magana game da ayukan zunubai da suke mayad da mutane da rashin ɗachewa ga Yahweh kamar su ƙazamtaccen ayuka ne na jiki.
Kalaman nan "ƙazamtattun ayukansu" na nuna mutane biyun nan da suka aikata ayukan zunubai"
Wannan bagadi ne dake cikin haikali.
Kamar wuri mai tsarki da kuma dakin taro, bagadin ya zama da rashin tsarki domin zunuban mutanen.
"a gabobin bagadin" (UDB). Wannan na nufin gabobin bagadin. Suna kama da tsifar ƙahon ..... AT: 4:6.
A nan ana magana game da bagadin da ya dace domin aikin Allah kamar yana da tsabta ta jiki ne.
A nan ana magana game da bagadin da aka mika wa Yahweh kamar an raɓa shi ta jiki ne daga zunuban mutane.
A nan ana magana game da ayyukan ƙazanta da suke sa mutane su zama da rashin ƙarbuwa ga Yahweh kamar ƙazantar ayyukan jilki ne.
Ana kiran akuyan nan refatacciyar akuya. AT: 16:8.
"ya furta akan akuyan"
Ayyukan Haruna anan alamar canji ne na zunuban mutanen nan zuwa ga akuyan, a matsayin cewa akuyan nan ne zai ɗauki horon laifin su.
Dukkan waddanan abubuwan, suna nufin abi ɗaya ne. Haruna yana furta kowace irin zububai da mutanen suka aikata.
Waddanan riga ne na mussamam da Haruna ke sakawa idan ya shiga wuri mafi tsarki.
A nan "wuri mai tsarki" baya nufin wurin taro. Wannan wuri ne dabam da aka keɓe masa domin ya wanke kansa.
Waddanan tufafin ne Haruna ke sakawa a sauran ayukkan sa.
"Dole Haruna zai ƙona"
Mutumin ya ƙazamtu domin ya taɓa refatacciyar akuya nan da ke ɗauke da zunuban mutanen.
"akuyan da aka ƙora." AT: 16:8.
AT: "wanda Haruna ya kawo jininsu"
AT: "dole wani ya ɗauke shi"
" fatarsu." A nan "su" na nufin bajimin da kuma akuyan.
Kalman nan "ku" jam'i ne kuma na nufin mutanen Isra'ila.
Wannan wata na bakwai ne a kalandar.
AT: Haruna zai yi kafara domin ku"
A nan ana magana game da mutanen da suka dace ga nufin Allah kamar suna da tsabta ta jiki ne.
Wannan ba irin assabat da suke kiyayewa ba ne a kowace kwana ta bakwai na mako. Wannan assabat ce na musammam a rana ta kafara.
AT: "wanda za su zuba masa mai su kuma keɓe shi"
Idan babban firist ya mutu, daya daga cikin 'ya'yan sa maza zai gaje shi.
Waddanan kaya ne na musammam da ya zama dole babban firist zai saka idan zai shiga wuri mafi tsarki.
"domin dukkan mutanen Isra'ila"
Yahweh ya gama gaya wa Musa game da abin da ya zama dole ne mutanen za su yi a Ranar Kafara.
AT: "Sai Musa ya yi yadda Yahweh ya Umarta" ko "Sai Haruna ya yi yadda Yahweh Ya umurci Musa"
1Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"Ka yi magana da Haruna da 'ya'yansa, da dukkan mutanen Isra'ila. Ka faɗa masu abin da Yahweh ya umarta:3'Duk mutumin da ke daga gidan Isra'ila wanda ya kashe sã, rago ko akuya a cikin sansani, ko wanda ya kashe shi a bayan sansani, domin ya miƙa shi hadaya -4idan bai kawo shi a ƙofar rumfar taruwa ya miƙa shi hadaya ga Yahweh a gaban mazaunin sa ba, wannan mutum ya zama da laifin zubar da jini. Ya zubar da jini, wannan mutum dole a datse shi daga cikin jama'arsa.5Dalilin wannan dokar shi ne domin mutanen Isra'ila su kawo hadayunsu ga Yahweh a ƙofar rumfar taruwa, wurin firist domin hadaya a matsayin baikon zumunta ga Yahweh, maimakon baikon hadayun da suke miƙawa a fili.6Firist zai yayyafa jinin a bisa bagadin Yahweh a ƙofar rumfar taruwa, zai ƙona kitsen domin ya bada ƙanshi mai daɗi domin Yahweh.7Nan gaba mutanen ba za su ƙara miƙa hadayunsu ga gumakan bunsuru ba, domin sun aikata kamar karuwai. Wannan zai zama farilla ta din-din din a gare su ga dukkan tsararsu.'8Dole ka ce masu, 'Kowanne mutumin Isra'ila, ko kowanne baƙon da ke zaune a cikinsu, wanda ya miƙa baikon ƙonawa ko hadaya9kuma bai kawo ta a ƙofar rumfar taruwa domin a miƙa ta ga Yahweh ba, wannan mutumin dole a fitar da shi daga jama'arsa.10Idan wani mutumin gidan Isra'ila, ko wani baƙon da ke zaune a cikin su ya sha kowanne irin jini, zan sa fuskata gãba da wannan mutum da ya sha jini kuma zan datse shi daga cikin jama'arsa.11Gama ran dabba yana cikin jininsa. Na bada jininsa gare ku domin ku yi kaffara a bisa bagadi domin rayukanku, saboda jini ne ke yin kaffara, gama jini ke yin kaffara domin rai.12Domin wannan na ce da mutanen Isra'ila ba wani a cikinku da zai ci jini, ko kowanne bãƙo da ke zaune a cikinku ya ci jini.13Kowanne mutumin Isra'ila, ko baƙin da ke zaune a cikinsu, wanda ya yi farauta ya kashe dabba ko tsuntsun da za a iya ci, dole wannan mutumin ya zubar da jinin sa'an nan ya rufe jinin da ƙasa.14Gama ran dukkan halitta yana cikin jininta. Shi ya sa na ce da mutanen Isra'ila, "Ba za ku ci jinin kowacce halitta ba, gama ran kowacce halitta yana cikin jininta. Duk wanda ya ci ya zama dole a datse shi."15Kowanne mutumin da ya ci dabbar data mutu ko wadda namomin jeji suka yayyaga, ko mutumin nan haifaffen gida ne ko baƙon da ke zama a cikinku, dole ya wanke tufafinsa ya kuma yi wanka cikin ruwa, zai zama ƙazantacce har yamma. Sa'an nan zai tsarkaka.16Amma idan bai wanke tufafinsa ba ko ya wanke jikinsa ba, daga nan dole ya ɗauki alhakin laifinsa.'"
"a gaban mazaunin Yahweh"
A nan, ana magana game mutumin da ake hana shi shiga cikin jama'a kamar an yanke shi ne daga mutanen sa, kamar yadda ake yanke gutsuri kaya ko a yanke rashe daga itace. AT: 7:9
AT: "wurin firist domin ya yi hadayar su"
Ana magana game da rashin amincin mutanen ga Yahweh ta wurin bauta wa allohlin ƙarya kaman su na yi mutumin da ya ci amanar matarsa ta wurin aikata zina. AT: "domin sun yi rashin aminci ga Yahyeh"
AT: 3:15.
AT: 17:1-4
Kalman nan "fuska" na nufin mutumin. Ƙarin maganan nan na nufin ki wani ko abu. AT: "Zan sa kai na gãba da wannan mutum" ko "Zan ki wannan mutum"
AT: 17:1-4 "Ba zan yarda wannan mutumin ya zauna tare da mutanen sa kuma ba" ko "zan raɓa mutumin nan daga mutanen sa"
Wannan na nufin cewa Allah na amfani da kafara domin zunuban mutane domin jinin rai ne. Kada mutanen su ci jinin domin yana da aiki ne na musamman.
A nan "na" na nufin Yahweh ne.
"ba wani a cikinku da zai iya cin nama dake da jini akai"
AT: "da na ce za a iya ci"
"sa'annan ya rufe jinin da datti"
Wannan na nufin cewa jinin ne na saka hallitun nan su rayu. AT: "kowace hallita na iya rayu domin jinin jininsa"
AT: 17:1-4 "Duk wanda ya ci jini, ba zai iya zama cikin mutanen sa ba" ko "Dole ku raɓa duk wanda ya ci jinin daga mutanen sa"
Yahweh ya ci gaba da yin magana.
A nan ana magana game da dabban da namomin jeji suka kashe kamar namomin jejin sun yayyaga shi ƙanana ne. AT: "da namomin jejin suka kashe"
A nan ana magana game da mutumin da sauran jama'a baza su taba ba kaman shi ƙazantacce ne ta jiki sa'annan mutumin da sauran jama'a za su iya taɓa kaman shi tsarkakke ne ta jiki.
"har faɗiwar rana"
A nan ana magana game da alhakin mutum kamar abi ne ta jiki da mutumin ke ɗaukawa. A nan, kalmar "alhaki" na wakilcin horo ne domin alhakin nan. AT: "Sa'annan shi ke ɗauki da hukuncin laifin sa" ko "Sa'annan Zan hukunta shi domin zunuban sa"
1Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce masu, 'Ni ne Yahweh Allahnku.3Ba za ku yi abubuwan da mutane ke yi a Masar ba, in da kuka taɓa zama. Ba za ku yi abubuwan da mutane ke yi a Kan'ana ba, ƙasar da nake kai ku. Kada ku bi al'adunsu.4Shari'una su ne za ku yi dole, dokokina kuma su ne za ku kiyaye dole, domin ku yi tafiya cikinsu, saboda ni ne Yahweh Allahnku.5Don haka dole ku kiyaye umarnaina da shari'una. Idan mutum ya yi biyayya da su, zai rayu saboda su. Ni ne Yahweh.6Ba wanda zai kwanta da kowanne dangi na kusa domin ya buɗe tsiraicinsa. Ni ne Yahweh.7Kada ka ƙasƙantar da mahaifinka ta wurin kwanciya da mahaifiyarka. Ita mahaifiyarka ce! Kada ka ƙasƙantar da ita.8Kada ka kwana da kowacce matar mahaifinka; kada ka ƙasƙantar da mahaifinka kamar haka.9Kada ka kwana da kowacce 'yar'uwarka, ko ita ɗiyar mahaifinka ce ko ɗiyar mahaifiyarka, ko a gidan ku ta girma ko a wani gida na nesa da kai. Kada ka kwana da 'yan'uwanka mata.10Kada ka kwana da ɗiyar ɗanka ko ɗiyar 'yarka. Wannan zai zama abin kunya gare ka.11Kada ka kwana da ɗiyar matar mahaifinka, wadda mahaifinka ya haifa. Ita 'yar'uwarka ce, kuma kada ka kwana da ita.12Kada ka kwana da 'yar'uwar mahaifinka, Ita 'yar'uwar mahaifinka ce ta kusa.13Kada ka kwana da 'yar'uwar mahaifiyarka. Ita 'yar'uwar mahaifiyarka ce ta kusa.14Kada ka ƙasƙantar da ɗan'uwan mahaifinka ta wurin kwana da matarsa. Kada ka yi kusa da ita akan wannan dalili; ita bãbarka ce.15Kada ka kwana da matar ɗanka. Ita matar ɗanka ce; kada ka kwana da ita.16Kada ka kwana da matar ɗan'uwanka; kada ka ƙasƙantar da shi ta wurin yin haka.17Kada ka kwana da mace da ɗiyarta kuma, ko ɗiyar ɗanta ko ɗiyar 'yarta. Su danginta ne na kusa, kwana da su zai zama mugunta.18Ba zaka auri 'yar'uwar matarka a matsayin kishiyarta ba kuma ka kwana da ita yayin da matarka ta farko na da rai.19Kada ka kwana da mace a lokacin hailarta. Ba ta da tsarki a wannan lokacin.20Kada ka kwana da matar maƙwabcinka kuma ka ƙazantar da kanka da ita ta wannan hanya.21Kada ka bada ko ɗaya daga cikin 'ya'yanka a sa su cikin wuta, domin ka miƙa su hadaya ga Molek, saboda ba za ka tozarta sunan Allahnka ba. Ni ne Yahweh.22Kada ka kwana da wasu maza kamar yadda ake yi da mace. Wannan zai zama mugunta.23Kada ka kwana da kowacce dabba ka kuma ƙazantar da kanka da ita. Ba wata mace da zata kwana da kowacce dabba. Wannan zai zama keta doka.24Kada ka ƙazantar da kanka ta kowanne irin waɗannan hanyoyi, gama ta cikin irin waɗannam hanyoyi ne al'ummai suka ƙazantu, al'umman da na kora daga gaban ku.25ƙasar ta ƙazantu, na hukunta zunubansu, ƙasar ta amayar da mazaunanta.26Domin haka, ku, dole ku kiyaye dokokina da umarnaina, kuma ba za ku aikata ko ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan banƙyama ba, ko haifaffen Ba - Isra'ile ko bãƙon da ke zaune a cikinku.27Gama wannan ita ce muguntar da mutanen cikin ƙasar da suka rigaye ku suka aikata, waɗanda suka zauna nan kafin ku, yanzu kuma ƙasar ta ƙazantu.28Don haka sai ku yi hankali don kada ƙasar ta amayar da ku bayan da kun ƙazantar da ita, kamar yadda ta amayar da mutanen da suka rigaye ku.29Duk wanda ya aikata kowanne ɗaya daga cikin abubuwan banƙyamar nan, mutanen da suka yi waɗannan za a datse su daga cikin jama'arsu.30Don haka dole ku kiyaye dokata kada ku aikata ko ɗaya daga cikin waɗannan al'adun mãsu banƙyama waɗanda aka aikata a nan a gaban ku, domin kada ku ƙazantar da kanku ta wurin su. Ni ne Yahweh Allahnku.'"
Waddanan kalaman suna nufin abu daya ne, suna kuma nanata cewa dole ne mutanen za su yi biyayya ga duk abin da Yahweh ya umurce su su yi. AT: "Dole ne ku kiyaye dokokina da kuma umurni na"
A nan ana magana game da kiyaye dokokin Yahweh kamar dokokin hanya ce da mutun ke iya tafiya akai. AT: "domin ku yi ayukan ku bisa ga su"
Wasu lokatai, mutane su kan aure mace fiye da daya. Allah bai ba da izini ɗa ya kwana da matar uɓan sa ba.
Wannan na nufin cewa kada wani ya kwana da 'yar'uwar sa idan sun fito daga iyaye daya ko ma idan ta fito daga uwa ko uɓa dabam.
AT: " ko a gidan ku ta girma a nesa da ku"
AT: "Kada ku kwana da 'yar'uwar ku ko na uɓa ko uwa dabam" (UDB). A nan mutumin ba shi da uwa ko uɓa daya da matan. Sun zama dan'uwa da 'yar'uwa idan iyayen su sun yi aure.
"Kada ka yi kusa da ita domin ka kwana da ita"
Yahweh ya sake yin wannan domin ya nanata game da umarnin.
Wannan lokaci ne wanda mace tana zubad da jini daga cikin ta.
A nan ana magana game da matar da mutane ba za su iya taɓa ta ba kamar ba ta da tsabtar jiki ne.
"matar wani"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da bai kamata mutanen su yi ba, wanda zai ƙazantar da su.
Kalman nan "wuce cikin wuta" na nufin a ƙona abi da wuta a matsayin hadaya. AT: "kada ku ƙona 'ya'yan ku da rai"
Kalman nan "tozarta" na nufin rashin ba da girma. Kalman nan "suna" na nufin Allah ne da kansa". "kada ku ki girmama Allahn ku"
A nan "ƙeta doka" na nufin rashin ƙetare dokar hallita da Yahweh ya nufa su faru.
Wannan na nufin mutanen d suke zama a ƙasar Kan'ana. AT: "mutanen ƙasar sun ƙazantad da kansu"
"Mutane sun ƙazantad da ƙasar"
A nan ana magana game da Yahweh ya tilasta mutanen su fita daga ƙasar kamar ƙasar mutum ne da ke amayar da mutane waje. AT: "Na tilastad da cire mutanen daga ƙasar, kamar mutumin da ya ke amayar da abinci"
" ko ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan banƙyama ba"
Wannan na nufin "abubuwan banƙyaman na."
"Don haka sai ku yi kula domin ku yi mani biyayya"
AT: 18:24
Yahweh ya gama gaya wa Musa game da ya zama dole ne mutanen za su yi.
AT: 17:10-11
AT: "wanda mutanen suka yi a nan kafin ku zo"
A nan "su" na nufin al'adun bankyama.
1Yahweh ya yi magana da Musa cewa,2"Ka yi magana ga dukkan taron jama'ar Isra'ila ka ce masu, "Dole ku zama da tsarki, gama ni Yahweh Allahnku mai tsarki ne.3Kowanne dole ya girmama mahaifiyarsa da mahaifinsa, kuma dole ku kiyaye assabataina. Ni ne Yahweh Allahnku.4Kada ku juya ga gumakai marasa amfani, ko ku yi wa kanku alloli na ƙarfe. Ni ne Yahweh Allahnku.5Sa'ad da ka miƙa hadaya ta zumuntar baye-baye ga Yahweh, dole ka miƙa ta yadda za a karɓe ka.6Dole a cinye ta a ranar da aka miƙa ta, ko kuma washegari. Idan wani abu ya rage har rana ta uku, dole a ƙone shi da wuta.7Idan anci ta ko kaɗan a kan rana ta uku, naman ya zama marar tsarki; ba za a karɓe ta ba,8kuma duk wanda ya ci dole ya ɗauki alhakin laifinsa saboda ya ƙazantar da abin da ke mai tsarki na Yahweh, wannan mutum dole a datse shi daga jama'arsa.9Sa'ad da kuka girbe amfanin ƙasarku, ba za ku girbe kusurwowin gonarku dukka ba, ba kuma za ku tattara dukkan amfanin girbin ku ba.10Ba za ku tattara kowanne inabi daga garkar inabin ba, ko ku tattara inabin da ya faɗi a ƙasa cikin garkar. Dole ku bar su domin matalauta kuma domin bãƙi. Ni ne Yahweh Allahnku.11Kada ku yi sata. Kada ku yaudari juna.12Kada ku rantse da sunana kan ƙarya kuma ku tozarta sunan Allahnku. Ni ne Yahweh.13Kada ka zalunci makwabcinka ko ka yi masa fashi. Haƙin bawan da aka yi hayarsa kada ya kwana wurinka har safiya.14Kada ka la'anta kurma ko ka sa abin tuntuɓe gaban makaho. Maimakon haka, dole ku ji tsoron Allah. Ni ne Yahweh.15Kada ka aikata rashin gaskiya cikin shari'a. Kada ka nuna tãra ga wani saboda shi talaka ne, kuma kada ka nuna tãra ga wani saboda muhimmancinsa. Maimakon haka, ka shari'anta makwabcinka bisa ga adalci.16Kada ka yi tafiyar yawon ɓatanci a cikin mutanenka, amma ka nemi kare ran makwabcinka. Ni ne Yahweh.17Kada ka ƙi ɗan'uwanka a zuciyarka. Dole ka tsauta wa maƙwabcinka akan gaskiya domin kada zunubinsa ya shafe ka.18Kada ka ɗaukar wa kanka fansa ko ka riƙe shi da ƙiyayya gãba da wani cikin mutanenka, amma maimakon haka sai ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka. Ni ne Yahweh.19Dole ku kiyaye dokokina. Kada ku bar dabbobinku su yi barbara da wasu irin dabbobi dabam. Kada ku cuɗa iri biyu lokacin da kuke shuka a gonarku. Kada ku sa tufafin da aka yi da ke da haɗe-haɗe iri biyu tare.20Duk wanda ya kwana da yarinyar da take baiwa wadda aka alƙawarta wa miji, amma ba a fanshe ta ba ko 'yanta ta ba, dole a hukunta su. Ba za a kashe su ba saboda ba a 'yanta ta ba.21Sai mutumin ya kawo baikon laifinsa ga Yahweh a ƙofar shiga rumfar taruwa - rago domin hadayar laifi.22Daga nan firist zai yi kaffara domin sa da rago domin baikon laifi a gaban Yahweh, domin zunubin da ya aikata. Daga nan za a gaffarta masa zunubin da ya yi.23Sa'ad da kuka zo cikin ƙasar kuma kuka dasa ko waɗanne irin itatuwa domin abinci, sai ku maida 'ya'yan itatuwansu haramtattu gare ku har shekaru uku. Ba za ku ci su ba.24Amma a cikin shekara ta huɗu dukkan amfaninsu za su zama mãsu tsarki, baikon yabo ga Yahweh.25A cikin shekara ta biyar za ku iya cin amfanin, domin kun jira saboda itatuwan su ƙara ba da 'ya'ya da yawa. Ni ne Yahweh Allahnku.26Kada ku ci kowanne irin nama tare da jininsa a cikinsa. Kada ku tuntuɓi ruhohi game da abin da zai faru nan gaba, kada ku nemi ku mulki waɗansu ta wurin manyan ikoki ko duba.27Ba za ku aske gashin kanku a kewaye ko ku aske ƙarshen gemunku ba.28Kada ku yanke jikinku domin matattu ko ku yi tsaga a jikinku. Ni ne Yahweh.29Kada ka kunyatar da ɗiyarka ta wurin sa ta karuwanci, ko ƙasar ta faɗa cikin karuwanci ƙasar kuma ta cika da mugunta.30Dole ku kiyaye Assabataina ku girmama mazaunina mai tsarki. Ni ne Yahweh.31Kada ku juya wurin waɗanda suke magana da matattu ko da ruhohi, kada ku neme su, domin za su ƙazantar da ku. Ni ne Yahweh Allahnku.32Dole ku tashi tsaye gaban wanda ya ke da furfura kuma ku gimama kasancewar dattijo. Dole ku ji tsoron Allah. Ni ne Yahweh.33Idan bãƙo na zaune a wurinku cikin ƙasarku, kada ku cutar da shi.34Bãƙon da ke zaune tare da ku dole ya zama kamar haifaffen Ba-Isra'ile wanda ya ke zama a cikin ku, kuma dole ka ƙaunace shi kamar kanka, saboda dã ku bãƙi ne a cikin ƙasar Masar. Ni ne Yahweh Allahnku.35Kada ku yi awo da ma'aunin ƙarya lokacin auna tsawo, nauyi ko yawa.36Dole ku yi amfani da ma'auni, madaidaici, kwanon gaskiya kofi na gaskiya. Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fitar da ku daga ƙasar Masar.37Dole ku kiyaye dukkan farillaina da dokokina, kuma ku aikata su. Ni ne Yahweh.'"
" kiyaye assabataina" ko "girmama ranar hutu na"
A nan ana magana game da sujada ga gumakai kamar sun juya zuwa wurin su. AT: " Kada ku fara yin bautar gumakai marasa anfani"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da ya zama dole ne mutanen za su yi.
Ma'ana mai yiwuwa 1) AT:Yahweh zai karɓi baikon hadayar mutumin. "dole ku mika ta da kyau domin in karɓe ku" ko 2) Yahweh zai karɓi hadayar mutumin. AT: "dole ku mika ta da kyau domin in karɓi hadayar ku"
AT: "Dole ku cinye ta"
AT: "dole ku ƙone shi"
AT: "Idan ku ka ci ko ɗaya daga cikin ta"
Allah ya hana cin baikon bayan lokacin da aka shirya domin ya kan ƙara akan laifi da yakamata baikon ya rufe. AT: "Ba za ku yarda a shi domin a ci ba"
A nan ana magana game da laifin mutum kamar abu ne da mutumin ya ɗauka "laifi" na nufin hukuncin laifin. AT: duk wanda ... ya na ɗauki da laifin sa" ko "Yahweh zai hukunta duk wanda ... domin zunuban sa"
AT: 7:19
"A lokacin da ku ka tattara anfanin gonar ku, kada ku tara nata kusurwar gonar ku"
Wannan na nufin komawa na biyu zuwa gonan domin a tăre kowace anfanin gona da ta rage a bayan da an rigaya an kwashe da farko. AT: "kuma kada ku koma ku kuma kwashe wanda kuka bari a baya"
"Kada ku yi anfani da sunana domin rantsuwa akan abin da ba na gaskiya ba"
A nan "makwabci" na nufin "wani." AT: "Kada ka yi zalunci ko yi wa wani fashi.
Yahweh ya yi umarni cewa kowa ya biya waddanan su ka yi wa aiki a ranar.
AT: "Yi shari'ar gaskiya a kowace lokaci"
Kalaman nan "talaka" da "muhimminci" dabam ne, .... wanda tare suna ma'anan "wani." AT: "Kada ka nuna tãra ga wani saboda yawan kuɗin da yake da shi"
"ka shari'anta kowa bisa ga abin da ke daidai"
"kada ka yi tafiyar yawon ɓatanci ga sauran jama'a"
A nan ana maganar cigaba da kin wani kamar ka ki mutum ne daga zuciyar ka. AT: "Kada ka cigaba da kin ɗan'uwanka"
"Dole ka gyara mutumin da ke yin zunubi"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da ya zama dole ne mutanen za su yi.
AT: "tufafin da wani ya yi da ke haɗe-haɗe iri biyu"
AT: "AT: "wanda aka alƙawarta wa wani domin suyi aure"
AT: "amma wanda mijin ta mai zuwa nan gaba bai fanshe ta ba ko 'yanta ta ba"
AT: "dole ku hukunta baiwar nan tare da wanda ya kwana da ita"
AT: "Ba za ku kashe su ba"
"Sai mutumin ya kawo rago a matsayin hadayar laifi ga Yahweh a ƙofar shiga rumfar taruwar"
AT: ´"Yahweh zai gafarta zunuban da ya aikata"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da ya zama dole ne mutanen za su yi.
Yahweh ya sake hana domin nuna cewa dole ne itacen ta haifi 'ya'ya a farkon shekara na ukun. AT: "hakika ba za ku ci 'ya'yan itacen nan ba a sheƙaru uku farko"
AT: "ku mai da 'ya'yan itatuwansu a matsayin abin da na rigaya haramta shi a gare ku"
AT: "Na haramtad da 'ya'yan ittatuwan nan a gare ku"
AT: " Ba za ku ci su ba"
Kalaman nan "ƙasa" na nufin jama'an da ke zama cikin ta ne. Ana magana game da mutane dayawan da ke aikata karuwanci da sauran munanan ayuka kamar sun faɗa cikin ko suna yin waddanan abubuwan ne. AT: "mutanen za su fara aikata karuwanci da kuma munanen abubuwa dayawa"
AT:1) "mattatu" da "ruhohi" ababai dabam ne ko 2) na nufin "ruhohin mutanen da suka mutu"
"Kada ku nemo mutanen nan. Idan kun yi, zasu ƙazamtar da ku"
Tashiwa a gaban wani alamar bangirma ne.
wanda yake da furfura - Wannan na nufin mutumin da ya yi furfura a gashin sa, ko "mutumin da ya tsufa."
Wannan ya hana aikin ganganci da na'urori da ba su da kyau idan ana auna abubuwa.
Wannan awu ne na hatsi.
Wannan awu ne na ruwa.
Waddanan kalaman na nufin abi ɗaya ne, suna kuma nanata umarnin biyayya.
1Yahweh ya yi magana da Musa cewa,2"Ka faɗa wa mutanen Isra'ila 'Duk wanda ke daga cikin jama'ar Isra'ila, ko bãƙon da ke zaune a cikin Isra'ila ya miƙa ɗaya daga cikin 'ya'yansa ga gunkin nan Molek, dole a kashe shi. Dole mutanen cikin ƙasar su jejjefe shi da duwatsu.3Zan kuma sa fuskata gãba da wannan mutumin in kuma datse shi daga cikin mutanensa domin ya miƙa ɗansa ga Molek, domin ya ƙazantar da wurina mai tsarki ya kuma muzanta sunana mai tsarki.4Idan jama'ar ƙasar suka kulle idanunsu ga wannan mutumin a lokacin da ya ke miƙa ɗaya daga cikin 'ya'yansa ga Molek, Idan suka ƙi kashe shi,5Sa'an nan Ni da kaina zan sa fuskata gãba da wannan mutumin da danginsa, zan kuma datse shi da kuma dukkan wanda ya shiga karuwanci domin ya aikata karuwaci tare da Molek.6Mutum wanda ya juya ga waɗanda suke magana da matattu, ko ga waɗanda ke magana da ruhohi don ya yi karuwanci tare da su, Zan sa fuskata gãba da wannan mutumin; Zan datse shi daga cikin mutanen sa.7Don haka ku tsarkake kanku ku kuma zama da tsarki, domin Ni ne Yahweh Allahnku.8Dole ku kiyaye umarnaina ku kuma aikata su. Ni ne Yahweh wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka.9Duk wanda ya la'anta mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi. Ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, to ya yi laifi kenan ya kuma cancanci mutuwa.10Mutumin da ya yi zina da matar wani, wato, dukkan wanda ya yi zina da matar maƙwabcinsa - mazinacin da mazinaciyar dole ne a kashe su.11Idan mutum ya kwana da matar mahaifinsa, ya buɗe tsiraicin mahaifinsa. Da ɗan da matar mahaifinsa dole a kashe su. Alhakin jininsu na kansu.12Idan mutum ya kwana da matar ɗansa, dukkan su dole ne a kashe su, sun aikata abin ƙyama. Masu laifi ne sun kuma cancanci mutuwa.13Idan mutum ya kwana da namiji, yadda ake yi da mace, dukkansu sun aikata mummunan abin ƙyama. Hakika tilas ne a kashe su. Masu laifi ne sun kuma cancanci mutuwa.14Idan mutum ya auri mace ya kuma auri mahaifiyarta, wannan mugunta ce. Dole ne a ƙone su, shi da matar dukka, domin ya zama babu mugunta a tsakiyarku.15Idan mutum ya kwana da dabba, dole ne a kashe shi, dole kuma ku kashe dabbar.16Idan mace ta kusanci kowacce dabba domin ta kwana da ita, dole ku kashe macen da dabbar. wajibi ne ku kashe su. masu laifi ne sun kuma cancanci mutuwa.17Idan mutum ya kwana da 'yar'uwarsa, ɗiyar mahaifinsa ko ɗiyar mahaifiyarsa, ya kuma buɗe tsiraicinta, ita kuma ta ga tsiraicinsa, abin kunya ne. Dole a datse su daga gaban jama'arsu, saboda ya kwana da ƴar'uwarsa. Dole ya ɗauki alhakin sa.18Idan mutum ya kwana da mace a lokacin jinin al'adarta har ya kwana da ita, har ya buɗe jinin da ke gudanowa daga jikinta, maɓulɓular jininta. Da mutumin da matar dole a datse su daga cikin jama'arsu.19Ba za ka kwana da 'yar'uwar mahaifiyarka ba, ko kuma da 'yar'uwar mahaifinka, domin zaka ƙasƙantar da danginka na kusa. Wajibi ne ka ɗauki alhakinka.20Idan mutum ya kwana da bãbarsa, ya ƙasƙantar da kawunsa. Za su ɗauki hakkin zunubinsu, za su kuma mutu babu 'ya'ya.21Idan mutum ya auri matar ɗan'uwansa sa'ad da ɗan'uwansa ke da rai, wannan ƙasƙanci ne. Ya ƙasƙantar da ɗan'uwansa, kuma zan ɗauke wa 'ya'yansu duk wata mallaka da suka gada daga iyayensu.22Saboda haka wajibi ne ku kiyaye dukka farillaina da dukkan dokokina; Dole ku yi biyayya da su domin kada ƙasar da Na ke kai ku domin ku zauna a ciki ta amayar da ku daga cikinta.23Ba za ku yi tafiya cikin al'adun al'umman da nake kora daga gabanku ba, domin sun aikata duk waɗannan abubuwan, kuma na ƙyamace su.24Na faɗa maku, "Za ku gãji ƙasarsu; Zan ba ku ita ku mallaketa, ƙasa mai ɓulɓulo da madara da zuma. Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya keɓe ku daga sauran mutane.25Dole ne ku bambanta tsakanin dabbobi masu tsarki da marasa tsarki, da kuma tsakanin tsuntsaye marasa tsarki da masu tsarki. Wajibi ne ku ƙaurace wa ƙazantar da kanku da dabbobi ko tsuntsaye ko da kowacce irin halitta mai rarraffe akan ƙasa, wanda Na keɓe su a matsayin ƙazamtattu daga gare ku.26Dole ne ku zama da tsarki, gama Ni, Yahweh, Mai Tsarki ne, kuma Na keɓe ku daga sauran mutane, saboda ku nawa ne.27Mutum ko matar da ke yin magana da matacce ko suke yin magana da ruhohi dole ne a kashe su. Dole jama'a su jejjefe su da duwatsu. masu laifi ne sun kuma cancanci mutuwa.'"
Waddanda suka bauta wa Molek sun mika hadayar 'ya'yansu tawurin wuta. AT: "ƙashe ɗaya daga cikin 'ya'yansa wa Molek"
AT: "dole mutanen ƙasar su jefe shi har ga mutuwa"
Kalman nan "sa fuskata gãba" ƙarin magana ne dake nufin "a ƙi" AT: "Ni ma zan ƙi shi" .....
"ya miƙa hadayar ɗansa"
"ta yin haka kuma, ya ƙazantar da wurina mai tsarki ya kuma muzanta sunana mai tsarki"
Sunar Allah na nufin sunan Allah da kuma muhimmincin sa. AT: "rashin girmama sunana" ko "rashin girmama ni" ...
Kalman nan "a kulle idanunsu" na nufin "ba suwa iya gani" kuma yana nufin rashin iya ganewarsu. AT: "ƙyale" (UDB)
Wannan kalman na kwatanta marasa adalci ga Yahweh da karuwai. AT: "marasa adalci ga Yahweh"
Wannan kalman na kwatanta mutane marasa adalci da karuwai. AT: ta yin haka, suna neman shawarware daga ruhohin nan amma ba daga ni ba"
AT: 20:3
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da ya zama dole ne mutanen za su yi.
Kalaman nan "kiyaye" da kuma "aikata su" na nufin abi ɗaya ne. Ana anfani da su tare domin a nanata cewa dole ne mutanen nan za su yi biyayya ga Allah.
AT: "dole ku kashe shi"
AT: "Mutumin da ya yi zina da matar wani"
AT: "dole ku kashe dukkansu"
Wannan wata hanya ce da take faɗi cewa ya kwana da matar mahaifin sa. Wasu ƙabilu suna anfani da kalaman nan kamar "ya kwana da matar mahaifinsa."
A nan Allah ya ƙira mutunin da ya ke kwana da matar ɗansa "ƙyama", zunubi mai nauyi.
Wannan wata hanya ce da take faɗi cewa ya kwana da matar wani. Wasu ƙabilu suna anfani da waddanan kalaman "wani ya kwana da"
Yadda ya yi da mutumin nan haka zai yi da macen nan. AT: "haka zai yi da macen nan"
"abin kunya" ko "abu mai ƙyama"
AT: "Dole ne ku karkashe su"
AT: "Dole ku ƙone macen nan da mijin nan har ga mutuwa"
AT: "dole ne ku kashe shi"
Dukkan ƙarin maganan nan na nufin abi ɗaya ne. Su na nanata cewa dole ne a kashe matan nan da kuma dabban nan.
"Dole ne ku kashe su"
Wannan wata hanya ce da take cewa ya kwana da 'yar'uwarsa. Wasu harshe suna anfani da wasu kalamai kamar "wani mutumin ya kwana da."
Wannan na nufin mutum ba zai kwana da 'yar'uwarsa ba. AT: "ko asalin 'yar'uwarsa ko daga uwa ko uɓa dabam"
AT: 7:9
Wannan kalman na nufin mutumin ne zai ɗauki alhakin zunubin sa. AT: Shi ne zai ɗauki alhakin zunubin sa" ko "dole ne ku hukunta shi"
lokacin da matar za ta zubar da jini daga cikin ta
Wannan kalmar tana kwatanta kwana da mace a lokacin hailar ta da kau da abin yakamata yana boye. AT: "ya yi abin kunya tawurin buɗe zubar jinin ta"
AT: "Domin sun yi wannan abin kunyan, dole ne a datse mutumin nan da kuma macen nan"
Wannan wata hanya ce da take cewa ya kwana da innan sa. Wasu harshen suna anfani da kalmar nan kaman "kwana da"
Ƙarin maganan nan "ɗauki alhakin ka" na nufin "kai za ka ɗauka alhakin zunubin ka" ko "zan hukunta ka"
Wasu littatafan masu tsarkin sun juya wannan a matsayi " za su kasance mara 'ya'ya har ga mutuwa." ...
AT: 18:24 "ba za a ƙi ku a ƙasar da zan kai ku ba"
A nan ana magana game da aikata aikin masu bauta wa gumakai kamar tafiya kaman su ne. AT: "Dole ne ku bi"
"cire"
Kalman nan "ƙasa mai ɓulɓulo da madara da zuma" na nufin "mai arziki da kuma ba da ishashen abinci ga kowa." AT: "ƙasar da take da ƙyau wa shanukai da kuma noma" ko "ƙasa mai haifar da 'ya'ya"
"Na bam-bamta ku" ko "Na keɓe ku"
"koƙarin magana da"
AT: "dole ne a kashe su"
1Yahweh ya cewa Musa: "Ka yi magana da firistoci, 'ya'ya maza na Haruna, ka ce masu, 'Kada a sami wani a cikinku da zai ƙazantar da kansa da gawar wanda ya mutu daga cikin mutanensa,2sai dai idan shi dangi ne na kusa - mahaifiyarsa, mahaifinsa, ɗansa, 'yarsa, ɗan'uwansa,3ko 'yar'uwarsa budurwa wadda ya ke rike da ita, tunda ya ke bata da miji - saboda ita yana iya ƙazantar da kansa.4Amma kada ya ƙazantar da kansa saboda waɗansu dangi ta haka ya kuma ɓata kansa.5Firistoci ba za su aske kansu ko su aske gefen gemun su, ko su yanka jikkunnansu ba.6Dole su zama tsarkaka ga Allahnsu, kada kuma su ƙasƙantar da sunan Allahnsu, gama firistoci ke miƙa hadayun Yahweh na abinci, gurasa ta Allahnsu. Don haka wajibi ne firistoci su zama da tsarki.7Ba za su auri kowacce mace wadda take karuwa ba da wadda aka ɓata, Kuma ba za su auri mace wadda mijinta ya sake ta ba, domin su keɓaɓɓu ne ga Allahnsu.8Za ku keɓe shi, domin shi ne mai miƙa gurasa ga Allahnku. Dole ya zama da tsarki gare ku, domin Ni, Yahweh wanda ya tsarkake ku, Mai Tsarki ne.9Duk wata ɗiya ta firist da ta ƙazantar da kanta ta wurin zama karuwa ta ƙasƙantar da mahaifinta. Dole a ƙone ta.10Wanda ya ke shi ne babban firist daga cikin "yan'uwansa, wanda aka zuba mai na keɓewa a kansa, wanda kuma aka tsarkake domin ya sa rigar babban firist, ba zai kwance gashin kansa ko ya keta tufafinsa ba.11Ba zai je wurin da akwai gawa ba ya kuma ƙazantar da kansa, ko da mataccen mahaifinsa ne ko mahaifiyarsa ce.12Babban firist ba zai bar harabar haikali ko ya ƙazantar da haikalin Allahnsa ba, domin an keɓe shi a matsayin babban firist ta wurin man keɓewa na Allahnsa. Ni ne Yahweh.13Wajibi ne babban firist ya auri budurwa a matsayin matarsa.14Ba zai auri gwauruwa, ko sakakkiyar mace, ko mace wadda take karuwa ba. Ba zai auri irin waɗannan matan ba. Zai iya auren budurwa daga cikn jama'arsa,15domin kada ya ƙazantar da 'ya'yansa daga cikin jama'arsa, domin Ni ne Yahweh, wanda ya maishe shi tsarkakakke.'"16Yahweh ya yi magana da Musa, ya ce,17"Ka yi magana da Haruna ka faɗa masa, 'Dukkan wanda aka samu da wata nakasar jiki cikin zuriyarka a dukkan tsararrakinsu, ba zai matso kusa domin ya miƙa abinci ga Allahnsa ba.18Kowanne mutum da ke da nakasa a jiki kada ya kusanci Yahweh, irin wannan makahon ko mutumin da bai iya tafiya, shi da ya ke da nakasa a jiki ko fuskar,19mutumin da ke da nakasa a hannu ko a ƙafa,20mutumin da ke da ƙusumbi a bayansa ko shanyayye ko wãda, ko mutumin da ke da hãkiya a idanunsa, ko ya ke da cuta, gyambo, ƙurji, ko rauni a mazakutta.21Ba wani mutum daga cikin zuriyar Haruna firist mai nakasa a jikinsa da zai matso kusa domin ya miƙa baye-bayen da ake miƙawa da wuta ga Yahweh. Irin wannan mutumin mai naƙasa a jiki; kada ya zo kusa domin ya miƙa gurasar Allahnsa.22Ya iya cin abincin Allahnsa, ko daga cikin mafi tsarki ko kuma daga cikin mai tsarki.23Duk da haka, Ba zai shiga daga cikin labulen ko ya zo kusa da bagadi ba, saboda yana da naƙasa a jikinsa, domin kada ya ƙazantar da tsattsarkan wurina, gama Ni ne Yahweh, wanda ya tsarkake su."'24Haka Musa ya faɗawa Haruna waɗannan maganganu, ga 'ya'yansa, da kuma ga dukkan mutanen Isra'ila.
A nan ana magana game da mutumin da ba karbaɓe domin nufin Uɓangiji ba kamar shi ƙazantacce ne.
"cikin Isra'ilawa"
AT: "budurwa"
"gyefe" (UDB) ko "kowace sashi"
"Dole a keɓe su"
Kalman nan "suna" ana anfani da shi domin nuna halayen Yahweh. AT: "kada su kasƙantar da sunan Allahnsu"
A nan "gurasa" na nufin abinci ne. Yahweh bai ci waddanan baikon ba. Manufar baikon abincin nan ne ke gamshe Allah.
"Firistocin ba za su"
"domin an keɓe su" (UDB)
"dole ku mutane ku bi da firist din a matsayin tsarkakka"
A nan "gurasa" na nufin abinci. Yahweh bai ci baikon ba. Wannan na nufin cewa "Yaweh bai ci abincin da baƙin sa ba".
AT: "Dole ku gan shi da tsarki"
AT: "Dole ku ƙone ta har ga mutuwa"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da ya zama dole firist din zai yi.
A nan ana ba da missalin mai na keɓewa ne da ake anfani da shi idan ana bukin tsarkakewan sabon babban firist.
AT: "wanda aka zuba mai na keɓewa a kansa, aka kuma tsarkake shi"
Kwance gashi da kuma keta tufafi alama ce na makoki. ...
Wannan ba ya nufin cewa babban firist din ba zai bar wurin ba. Allah bai bar shi ya bar wurin ba domin ya ti baƙin cikin wanda ta mutu.
"daga cikin ƙabilarsa, ƙabilar firistoci"
Ta wurin auren mace mara tsarki da marasa bin Allah, firist din zai samu 'ya'yan da basu cancanta su zama firsit ba. AT: "cewa ba zai samu 'ya'yan da basu cancanta ba tawurin auren macen da ba ta bin Allah"
AT: "ba zai zo domin ya ƙona baikon abinci a bagadin Allah ba"
Yakamata firist ya da ishashen lafiya kafin nan ya kusanci Yahweh. Wannan baya nufin cewa naƙasassun ne da laifi ba ko cewa dukkan naƙassasun ba za su kusanci Yahweh ba.
"wanda shi nakasasse ne a jiki ko fuska"
A nan "gurasa" na nufin abinci ne. AT: "a miƙa baikon abinci a bagadin Allah"
A nan "ya" na nufin firist mai nakasassen jiki.
"cin baikon abinci na Allahnsa." Sauran hadayar na firist ne kuma za a iya cin ta.
Wannan ma na nufin abincin da aka miƙa hadayar ta. AT: "wasu hadayar da aka miƙa su a wuri mafi tsarki ko wasu hadayar da aka miƙa a wuri mai tsarki"
"ga 'ya'ya maza na Haruna"
1Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"Ka yi magana da Haruna da 'ya'yansa maza, ka faɗa masu su kiyaye kansu daga kayayyaki masu tsarki na mutanen Isra'ila, waɗanda suka keɓe gare ni. Ba za su ƙasƙantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Yahweh.3Ka faɗa masu, 'Idan wani daga cikin zuriyarku cikin dukkan tsararrakinku ya kusanci kayayyaki masu tsarki da jama'ar Isra'ila suka keɓe ga Yahweh, a sa'ad da ya ke marar tsarki, wannan mutumin dole a datse shi daga gabana: Ni ne Yahweh.4Kada wani daga cikin zuriyar Haruna wanda ke da cutar fata, ko mai miki da ke zubar da ruwa daga jikinsa, ya ci ko ɗaya daga waɗannan hadayun da aka miƙa ga Yahweh har sai ya tsarkaka. Dukkan wanda ya taɓa wani abu marar tsarki ta wurin taɓa gawa, ko ta wurin taɓa mutum mai zub da maniyyi,5ko kowacce dabba mai rarrafe data ƙazantar da shi, ko kowanne mutum ɗaya maida shi marar tsarki, ko dai kowacce irin ƙazanta ta zama-6daga nan firist wanda ya taɓa kowanne abu marar tsarki zai zama marar tsarki har maraice. Ba zai ci duk wani abu mai tsarki ba, har sai ya wanke jikinsa a cikin ruwa.7Sa'ad da rana ta faɗi, zai zama tsarkakakke. Bayan rana ta faɗi ya iya ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa, domin su abincinsa ne.8Ba zai ci duk abin da aka same shi matacce ba ko abin da naman jeji ya kashe, wanda ta wurin haka zai ƙazantar da kansa. Ni ne Yahweh.9Wajibi ne firistoci su bi umarnaina, domin kada su yi zunubi, su mutu domin muzanta ni. Ni ne Yahweh wanda ke tsarkake su.10Kada wanda ba daga iyalin firist ya ke ba, duk da baƙon da ya sauka a gidan firist ko barorinsa, ya ci duk abin da ya ke tsatstsarka.11Amma idan firist ya sayi wani bawa da kuɗinsa, wannan bawan na iya ci daga cikin abin da aka keɓe ga Yahweh. Iyalan gidan firist da kuma bayin da aka haifa a gidansa, za su iya cin waɗannan abubuwan tare da shi.12Idan ɗiyar firist ta auri wani mutum wanda ba firist ba, ba za ta ci ko ɗaya daga cikin baye-bayen gudunmuwa mai tsarki ba.13Amma idan ɗiyar firist ɗin gwauruwa ce, ko kuma sakakkiya, kuma idan bata da ɗa, kuma idan ta koma ta zauna a gidan mahaifinta kamar a lokacin ƙuruciyarta, za ta iya ci daga cikin abincin mahaifinta. Amma kada wani wanda ba daga cikin iyalin firist ya ke ba yaci abincin firist.14Idan mutum yaci abinci mai tsarki ba da sani ba, dole ya biya firist abin da ya ci; wajibi ne ya ƙara kashi ɗaya bisa biyar akan abin ya kuma maida wa firist.15Mutanen Isra'ila ba za su ƙazantar da abubuwa masu tsarki waɗanda suka ɗaga sama suka miƙa ga Yahweh ba.16Su jawowa kansu ɗaukar zunubin da zai sa su yi laifin cin abinci mai tsarki, gama Ni ne Yahweh wanda ya ke tsarkake su."17Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,18"Ka yi magana da Haruna shi da 'ya'yansa maza, da dukkan mutanen Isra'ila. Ka faɗa masu, 'Duk Ba-Israi'le, ko bãƙon da ke zaune cikin Isra'ila, lokacin da suka kawo hadaya- kodai ta cika wa'adi, ko ta bayarwar yadda rai, ko idan sun kawo hadayar ƙonawa ga Yahweh,19Idan za ta zama karɓaɓɓiya, dole su miƙa dabba namiji marar aibu daga cikin garken shanu, tumaki, ko awaki.20Amma kada ku miƙa duk wani abu mai aibu. Ba zan karbe su a maimakon ku ba.21Kowanne mutum da ya miƙa hadaya ta salama daga cikin garke ko tumaki ga Yahweh don cika wa'adi, ko a matsayin bayarwar yardar rai, dole ta zama marar aibu kafin a karɓe ta. Kada a sami nakasa cikin dabbar.22Ba zaku miƙa mani dabbobi makafi ba, ko guragu, ko naƙasassu, ko masu kirci, ko masu ƙuraje, ko tabbai. Ba za ku miƙa waɗannan ga Yahweh a matsayin hadaya ta ƙonawa a kan bagadi ba.23Zaku iya miƙa bayarwar yardar rai da sã, ko da ɗan rago da ke da naƙasa ko ƙanƙane, amma bayarwa irin wannan ba za ta karɓu domin cika wa'adi ba.24Kada ku miƙa wa Yahweh kowacce dabbar da ke da ƙurji, gurzajje, yayyagagge, ko dandaƙaƙƙe ba. Ba za ku yi wannan a cikin ƙasarku ba.25Kada kubar baƘo ya miƙa maku gurasa ga Allahnku. Waɗannan dabbobin naƙasassu ne suna kuma da aibu a cikin su, ba za'a karɓe su a madadinku ba."26Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,27"Sa'ad da aka haifi ɗan maraki, ko ɗan tunkiya ko ɗan akuya, dole ya zauna tare da mahaifiyarsa har kwana bakwai. A kwana na takwas, a iya karbar shi a matsayin hadayar ƙonawa da wuta ga Yahweh.28Ba za ku kashe saniya ko tunkiya tare da ƙananunsu, dukka a rana ɗaya ba.29Duk sa'ad da kuke miƙa hadaya ta godiya ga Yahweh, dole ku miƙa ta ta karɓaɓɓiyar hanya.30Dole ku cinye naman hadayar a ranar da aka miƙa ta. Ba za ku rage komai daga ciki zuwa safiya ba. Ni ne Yahweh.31Dole ne ku kiyaye dokokina ku kuma aikatasu dukka. Ni ne Yahweh.32Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole ne a san ni a matsayin mai tsarki ta wurin jama'ar Isra'ila. Ni ne Yahweh mai tsarkake ku,33wanda ya fishsheku daga ƙasar Masar domin in zama Allahnku: Ni ne Yahweh.
"faɗa masu lokacin da zasu kiyaye kansu daga kayyataki masu tsarki." Yahweh yana bayanin irin yanayin da firist zai kasance da rashin tsarki kuma ba za yarda ya taɓa kayyayaki masu tsarki ba.
Kalman nan "ƙasƙantar" na nufin rashin ba da girma. Kalman nan "suna" na nufin halayen Yahweh. AT: "ƙasƙantar da suna na" ko "ƙasƙantar da ni"
"daga yanzu"
A nan ana magana game da mutumin da ba yarda da shi domin ya aikata nufin Allah ba kamar shi ƙazamtacce ne.
A nan ana magana game da firist da ba yarda ya bauta wa Yahweh ba kamar an datse shi ne daga gaban Yahweh, kamar yadda wani zai datse tufafi ko ya datse rashi daga itace. AT: "cewa mutumin ba zai iya aiki a matsayin firist ba"
cuta a fata kan iya yaɗuwa daga mutum zuwa sauran jama'a
"cutar fatar jiki"
Wannan na nufin gabar mutum. AT: 15:1"daga gabar sa" ...
A nan ana magana game da mutumin da aka yarda da shi domin aikin Allah kamar shi tsarkakke ne.
A nan ana magana game da abin Yahweh ya ce bai cancanta a taɓa ba kamar ƙazamtacce ne.
"ta wurin taɓa gangar jiki"
AT: "hadayun da wani ya miƙa wa Yahweh"
AT: "ko wanda shi ƙazamtacce ne ta wurin taɓa dabbobi masu rarrafe ko daga taɓa ƙazamtaccen mutum"
A nan ana magana game da mutumin da ba yarda mashi ya aikata nufin Allah ba kamar mutumin ƙazamtacce ne.
"har faɗiwar rana"
"za a gan firist din da tsarki." A nan ana magana game da mutumin da an yarda mashi yayi aikin nufin Allah kamar mutumin tsarkakke ne.
AT: "wanda a same shi matacce ko wanda naman jeji ua kashe"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin dole ne 'ya'yan maza na Haruna za su yi.
Kalman nan "gudunmuwa" AT: "baiko mai tsarki da mutane suka ba da gudunmawa"
bisa biyar akan abin AT:1) cewa mutumin zai mayad da irin abincin da ya rigaya ya ci ko2) cewa mutumin zai biya kuɗi wa firist domin abincic da ya rigaya ya ci.
biyar- Wannan sashi ɗaya ne cikin sashoshi biyar.
AT: "dole ne su bi da abubuwa masu tsarki da tsarki"
Kalaman nan "ɗaga sama" alamar biyayya ne da ke nufin baikon abu ga Yahweh. Suna nufin abu daya ne da "miƙa." AT: "wanda suka miƙa"
A nan ana magana game da zunubi kamar abu ne da mutane kan ɗauka. Ma'ana mai yiwuwa 1) su ne zasu ɗauki zunuban kuma su zama da laifi. AT: "za su zama masu laifi domin zunuban da suka aikata" ko 2) kalman nan "zunubi" ƙarin magana ne na hukuncin zunuban da suka aikata. "zasu karɓi hukuncin domin laifin su"
"wani baƙo"
AT: "idan Yahweh zai karɓe shi" ko "idan Ni, Yahweh, zan yarda da shi"
AT: "domin in karɓe shi" ko "domin Yahweh ya karɓe shi"
Kalaman nan na nufin lahani da aka samu ta wurin tsautsayi.
Wannan na nufin cutar jiki iri-iri.
AT: "Ba zan karɓa ba" ko "Yahweh ba zai karɓa ba"
Waddanan kalaman na nufin lahani da dabbobin nan suka samu tun haifuwa.
A nan "gurasa" na nufin abinci. Allah bai ci baikon da baƙi ba. Firistocin ne suke miƙa hadayar a kan bagadin Allah, kuma suna ci daga cikin naman. AT: "ba za a miƙa dabban a matsayin hadayar abinci ga Allahn ku"
Kalman nan "hannu" na nufin mutumin ne gabaɗaya. A na nufin cewa Isra'ilawan ba za su iya anfani da dabbobi a matsayin hadaya ga Allah idan baƙo ne ya kawo, domin baƙi suna yi wa dabbobin su ƙachiya da ke saka su zama mara ƙarɓaɓɓe ga Allah. "wanda baƙo ya ba ku, domin sun yi wa dabbobin su ƙachiya"
AT: "Yahweh ba zai karɓe su ba daga ku"
AT: "za ku iya karɓe shi"
AT: " a matsayin hadayar konawa"
AT: "Dole ne ku ci"
AT: "wanda kuka yi hadayar"
Kalaman nan "kiyaye" da kuma "aikata su" na nufin abi ɗaya ne. Sun nanata cewa dole ne mutanen su yi biyayya ga umarnin Allah. AT: "yi biyayya ga umarnai na"
A nan, kalman "suna na nufin Yahweh da kansa da kuma .... AT: "Kada ku ƙasaƙntar da sunana"
AT: "Dole ne mutanen Isra'ila su ce da mai tsarki"
1Yahweh ya faɗa wa Musa:2"Ka yi magana da mutanen Isra'ila, kace masu, 'waɗannan su ne ƙayyadaddun bukukuwanku ga Yahweh, waɗanda dole ku shaida su a matsayin tattaruwa mai tsarki; su ne bukukuwana na yau da kullum.3Za ku iya yin aiki kwanaki shida, amma rana ta bakwai asabar ce ta cikakken hutu, tattaruwa mai tsarki. Ba za ku yi wani aiki ba domin asabar ce ta Yahweh a cikin dukkan wuraren da kuke zaune.4Waɗannan su ne ƙayyadaddun bukukuwa na Yahweh, tattaruwa mai tsarki da dole ku sanar a ƙayyadaddu lokuttansu:5A wata na farko, a rana ta goma sha huɗu ga wata washegari, ranar bukin ƙetarewa ne na Yahweh.6A rana ta goma sha biyar ga wannan watan ranar za ta zama ranar bukin gurasa marar gami ga Yahweh. Dole za ku ci gurasa marar gami har tsawon kwana bakwai.7A rana ta farko za ku keɓe kanku domin ku taru wuri ɗaya; ba za ku yi kowanne irin aiki da kuka saba yi ba.8Za ku miƙa bayarwar abinci ga Yahweh har kwana bakwai. Kwana na bakwai tattaruwa ce keɓaɓɓiya ga Yahweh, kuma a wannan rana wajibi ne ba za ku yi kowanne aiki da kuka saba yi ba.9Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,10"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce masu, 'Lokacin da kuka shiga cikin ƙasar da zan ba ku, Sa'ad da kuka yi girbi, wajibi ne ku kawo dami na nunar fari na hatsin ga firist.11Shi zai ɗaga damin hatsin a gaban Yahweh ya kuma miƙa shi gare shi, domin a karɓe shi a maimakon ku. A kwana ɗaya bayan assabacin firist zai ɗaga abin ya kuma gabatar da shi gare ni.12A ranar da kuka ɗaga damin hatsin kuka kuma miƙa shi gare ni, wajibi ne ku miƙa ɗan rago mai shekara ɗaya kuma marar naƙasa hadaya ta ƙonawa ga Yahweh.13Hadaya ta gari wajibi ne ta zama kashi biyu bisa goma na lallausan gari da aka gauraya da mai, bayarwar da aka yi da wuta ga Yahweh. Domin ta bada ƙamshi mai daɗi, kuma tare da ita hadaya ta abin sha, awo huɗu na ruwan inabi.14Ba za ku ci gurasa, ko gasashshen nama, ko ɗanyen hatsi ba, har sai ranar da kuka kawo sadakar ga Allahnku ta kewayo. Wannan farilla haka zata zama din-din din cikin dukkan tsararrakin jama'arku, a cikin dukkan wurin da kuke zaune.15Tun daga kwana ɗaya bayan ranar asabaci-Wannan ce ranar da ku ka kawo damin hatsi a matsayin sadaka ta ɗagawa - ku ƙirga makonni bakwai cikakku.16Dole ku ƙirga kwanaki hamsin, wanda zai kasance rana bayan asabar ta bakwai. Wajibi ne ku miƙa bayarwar sabon hatsi ga Yahweh.17Dole ku ɗibo curi biyu daga cikin gidajenku da aka yi da kashi biyu bisa goma na garwa. Wajibi ne a yi su da lallausan gari da aka yi da gami; zasu zama bayarwar nunar fari ta ɗagawa ga Yahweh.18Za ku miƙa gurasar tare da 'yan raguna bakwai masu shekara ɗaya marasa aibu, ɗan maraƙi ɗaya, da raguna biyu. Dole su zama hadaya ta ƙonawa ga Yahweh, tare da hadayar garin da hadaya ta sha, bayarwar da aka yi da wuta mai kuma bada ƙanshi ga Yahweh.19Za ku miƙa bunsuru ɗaya domin hadaya ta zunubi, ku kuma miƙa 'yan raguna biyu masu shekara ɗaya hadaya, a matsayin hadaya ta zumunci.20Wjibi ne firist ya kaɗa su tare da gurasar nunar fari a gaban Yahweh, ya kuma miƙa su gare shi a matsayin bayarwa tare da 'yan raguna biyu. Za su zama baye-baye masu tsarki na Yahweh domin firist.21Dole kayi shaida a wannan ranar. Za'a haɗa taro mai tsarki, kuma kada kuyi aikin da kuka saba yi. Wannan zai zama farilla na din-din din cikin dukkan tsararrakin jama'arku a cikin dukkan wuraren da kuke zaune.22Lokacin da kuka girbe amfanin gonarku, baza ku girbe har ƙurewar gonakinku ba, ba kuma za ku yi kalar gonakinku ba. Dole ne ku rage wa matalauta da baƙi su. Ni ne Yahweh Allahnku'".23Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,24"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka faɗi masu, 'A wata na bakwai, ranar farko ta wannan watan zata zama ranace ta cikakken hutu gare ku, ranar tunawa tare da busa sarewa, da kuma ranar taro mai tsarki.25Ba za ku yi wani aiki ba, kuma dole ne ku miƙa hadaya da wuta ga Yahweh."'26Sai Yahweh ya yi magana da Musa, cewa27"Yanzu ranar goma ga wannan wata na bakwai ita ce Ranar Kaffara. Za ta kasance tattaruwa mai tsarki, kuma dole ku ƙasƙantar da kanku ku kuma miƙa baiko da wuta ga Yahweh.28Ba za ku yi wani aiki a wannan rana ba gama Ranar Kaffara ce, ku yi kaffara domin kanku a gaban Yahweh Allahnku.29Dukkan wanda bai ƙasƙantar da kansa a wannan rana ba dole a datse shi daga cikin mutanensa.30Dukkan wanda ya yi wani aiki a wannan rana, Ni, Yahweh, zan hallakar da shi daga cikin mutanensa.31Ba za ku yi kowanne irin aiki a wannan rana ba. Wannan zai zama farilla ta din-din din cikin dukkan tsararrakin mutanenku a dukkan wuraren da kuke zama.32Ranar nan zata zama Assabat ta cikakken hutu gare ku, kuma dole ku ƙasƙantar da kanku a rana ta tara ga watan da maraice. Daga maraice zuwa maraice za ku kiyaye Assabacinku."33Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,34"Ka yi magana da mutanen Isra'ila, cewa, 'Rana ta goma sha biyar ga wata na bakwai zata zama ranar bukukuwan bukkoki ga Yahweh. Za ku kiyaye shi har kwanaki bakwai.35Za ku yi tattaruwa mai tsarki a rana ta fari. Ba za ku yi aikin da kuka saba yi ba.36Tsawon kwana bakwai za ku miƙa hadaya ta wurin wuta ga Yahweh. A rana ta takwas za ku yi taro mai tsarki, kuma dole ne ku miƙa hadaya ta wuta ga Yahweh. Wannan babban taro ne, kuma ba za ku yi aikin da kuka saba yi ba.37Waɗannan su ne ƙayyadaddun bukukuwa ga Yahweh, waɗanda zaku shaida a matsayin tattaruwa mai tsarki ku miƙa hadayu na wuta ga Yahweh, bayarwar ƙonawa da kuma bayarwar gari, hadaya da kuma bayarwar abin sha, kowacce a ranar ta.38Waɗannan bukukuwa ƙari ne ga Assabar ta Yahweh da kuma kyaututtukanku, dukkan alƙawuranku, da kuma dukkan baye-bayenku na yardar rai da kuka ba Yahweh.39Dangane da bukukuwan bukkoki, a ranar goma sha biyar ga wata na bakwai, lokacin da kuka gama tattara albarkun ƙasar, Dole ku kiyaye wannan bukukuwa ga Yahweh har kwana bakwai. Ranar farko zata zama ta cikakken hutu, haka rana ta takwas ma zata kasance ranar cikakken hutu.40A rana ta fari za ku ɗauka daga cikin mafi kyau na 'ya'yan itatuwanku, rassan itatuwan dabino, da rassa masu ganyayyaki na itatuwa masu ƙarfi, da ciyayi masu yaɗo daga rafuka, zaku yi murna a gaban Yahweh Allahnku har kwana bakwai.41Tsawon kwana bakwai a kowacce shekara, wajibi ne ku yi wannan buki ga Yahweh. Wannan zai zama farilla gare ku cikin dukkan tsararrakin mutanenku a dukkan wuraren da kuke zama. Dole ne ku yi bukin nan a wata na bakwai.42Wajibi ne ku zauna cikin bukkoki har kwana bakwai. Dukkan haifaffen gidan Isra'ila dole ya zauna cikin ƙananan bukkoki tsawon kwana bakwai,43domin zuriyarku, daga tsara zuwa tsara, su koyi yadda nasa mutanen Isra'ila suka zauna a cikin irin waɗannan bukkokin lokacin da na jagorance su daga cikin ƙasar Masar. Ni ne Yahweh Allahnku."'44Ta haka fa, Musa ya sanar wa mutanen Isra'ila ƙayyadaddun bukukuwa ga Yahweh.
Waɗɗannan bukukuwan ne wanda Ubangiji ya zaɓi lokacin da za a yi su. A waɗɗannan bukukuwan ne mutane za su yi masa sujada. AT: "bukukuwa na Yahweh" ko "bukukuwan Yahweh"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da dole ne mutanen za su yi a muhimman ranaku da kuma lokatai.
Waɗɗanan abubuwan ne yakamata ya zama jiki ga mutanen. Bayan kowace kwana na shida da suka yi aiki, dole ne su huta a rana ta bakwan.
A nan ana magana game da abin da ake bukata daga tattaruwar mutanen domin yi wa Allah sujada a ranar kaman ranar ne ranan tattaruwar. AT: "rana mai tsarki, da dole ku tattaru a wuri ɗaya domin ku yi mani sujada"
"a ainihin lakutansu"
A wata na farko ga kalandar Ibraniyawa na nuna alamar lokacin da Yahweh ya fitar da Isra'ilawa daga Masar. Rana ta goma sha huɗu da kuma goma sha biyar farkon ranaku ne na watan Aprilu a kalanda na Yamma.
"a faɗiwar rana"
"Dole ne ku keɓe rana ta farkon domin tattaru a wuri ɗaya" ko "Dole ne ku keɓe rana ta farkon ku kuma tattaru a wuri ɗaya"
Za su mika shi ga Yahweh tawurin ƙonawa a kan bagadi.
AT: 23:3 "keɓuwa ga Yahweh na nufin lokacin da suka tattaru, dole ne su yi wa Yahweh sujada. AT: "Kwana na bakwai rana ce da za ku tattaru a wuri ɗaya domin ku yi wa Yahweh sujada"
"dami na farko" ko "damin hatsi na fako." "dami" kurshen hatsi ne da mutum ya ɗaura su tare.
AT: "Domin Yahweh ya karɓe shi" ko "za kuma karɓe shi"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da dole ne mutane za su yi.
Garwan litta 22 ne. AT: "litta huɗu da raɓi"
Awon litta 3.7 ne. AT: "litta ɗaya"
"ko daffafe ko ɗanyen hatsi"
AT: 3:15
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da dole ne mutane za su yi.
"kwanaki 50"
Haka ne ake jeranta lamba ta bakwai.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da dole ne mutane za su yi.
AT: "da ku ka yi da kashi biyu bisa goma na garwar gari sa'annan ku ka yi da gami"
Gaba ɗaya wannan lita 4.5 ne. AT: "lita huɗu da raɓi"
Jin daɗin da Ubangiji ya yi da kamshin nan na wakilcin jin daɗinsa da mutumin da ke ƙona baikon. AT: "Yahweh zai kuma ji daɗin ku" ko "da ya gamshe da Yahwehi"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da dole ne mutane za su yi.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da dole ne mutane za su yi.
"Lokacin da kuka tattare amfanin ganarku, ba za ku tara su har da na ƙurewar gonankinku ba"
AT: 23:4-6
lokaci da aka shirya domin sujada kawai amma ba na aiki ba
Wannan ne kwana na bakwai na kalandar Ibraniyawa. Kwana na farkon ya kusanci sakiyar wata na Satumba a kalanda na yamma.
Wannan wata na bakwai na ga kalandar Ibraniyawa. Kwana na goman ya yi kusa da karshen watar Satumba a kalandar na Yamma.
A wannan rana ta kowace sheƙara, babban firist zai yi haɗaya ga Yahweh domin Yahweh ya gafarta wa dukkan zunuban mutanen Isra'ila. AT: "Ranar haɗayar domin Gafara"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da dole ne mutane za su yi a kowane sheƙara.
AT: 7:19
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da dole ne mutane za su yi a kowane sheƙara.
"a Ranar Kafara"
AT: 3:15.
Wannan ba Assabat da suka saba lura da ita na kowace sati na rana ta bakwai ba ne. Wannan Assabat ce ta mussamman na ranar Kafara.
A wannan yanayi, ƙasƙantar da kansu na nufin cewa ba za su ci abinci ba. AT: "dole ku ƙasƙantar da kanku ba za ku kuma ci abinci ba"
Wannan na nufin wata na bakwai a kalandar Ibraniyawa. Rana ta taran na kusa da ƙarshen watan Satumba a kalandar na Yamma. AT: "a rana ta bakwai na wata ta bakwan"
"Daga faɗiwar rana zuwa faɗiwar rana na washe gari"
Wannan na kusa da farkon wata na October a kalandar Yamma.
Wannan buki ne wanda mutanen Isra'ila suna zama a buka na ɗan karamin lokaci har kwanaki bakwai domin tunawa da lokacin da suka yi a cikin jeji bayan da suka bar Masar.
Yahweh yana ba da umurnai domin Bukukuwan Bukkoki.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da dole ne mutane za su yi a kowane sheƙara.
Wannan na nufin bukukuwan da aka ambata a 23:1-36.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da dole ne mutane za su yi a kowane sheƙara.
AT: 23:33
Wannan ne wata na bakwai a kalandar Ibraniyawa. Kwana na goma sha biyar din ya yi kusa da farkon wata na October a kalandar Yamma.
Kalman nan "ya'yan ittatuwa" na nufin amfanin gona iri-iri. AT: "bayan da kuka tattara amfanin gonar"
Yahweh yana ba da umurnai domin Bukukuwan Bukkoki.
Ma'ana mai yiwuwa 1) a yi wurin zama na ɗan karamin lokaci ko 2) domin su kada su yayen da suke murna a bukin. Za a iya bayyanin na a fili.
Itace mai dogon, matsattsen ganye, da ake samuwa a kusa da ruwa
Yahweh yana ba da umurnai domin Bukukuwan Bukkoki.
"Tsara zuwa tsara" ƙarin magana ne da ke mufin tsara da suka yi rayuwa a bayan wani tsara. AT: "dukkan zuriyarku da ke zuwa nan gaba su koyi" ko "dukkan zuriyarku su yi koyo na harabada"
1Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,2"Ka umurci mutanen Isra'ila su kawo maka mai mai tsabta da aka tatso daga zaitun don a riƙa amfani dashi cikin fitilu, domin su yi ta bada haske ba yankewa.3A wajen labulen a gaban akwatin alƙawari cikin rumfar taruwa, wajibi ne ga Haruna daga maraice zuwa safiya, ya sa fitila ta yi ta ci a gaban Yahweh. Wannan zai zama farillanku na din-din din cikin dukkan tsararrakin jama'arku.4Dole babban firist ya sa fitilu su yi ta ci a gaban Yahweh, fitilun za su kasance a kan maɗorin da aka yi da zinariya tsantsa.5Ka ɗauki lallausan gari ka yi curin gurasa goma sha biyu dashi. Kowanne curi a yi shi da adadin kashi biyu bisa goma na garwa.6Sa'an nan wajibi ne ku jera su a layi biyu, shida a kan kowanne layi, a kan tebur na zinariya mai tsabta a gaban Yahweh.7Wajibi ne ku sa turare mai tsabta a kan kowanne jerin gurasa a maimakon baiko. Wannan turaren za a ƙone shi domin Yahweh.8Kowacce Assabar babban firist ya ajiye gurasa a gaban Yahweh a maimakon mutanen Isra'ila, a matsayin alama ta alƙawari na har abada.9Wannan bayarwar zata zama domin Haruna da 'ya'yansa maza, kuma za su ci gurasar a wurin da ya ke mai tsarki, domin rabo ne daga baye-baye ga Yahweh da aka miƙa ta wuta."10Ya zama fa ɗan wata mata Ba-isra'iliya, wanda mahaifinsa Ba-masare ne, ya tafi tare da mutanen Isra'ila. Wannan ɗan matar Ba-isra'iliya ya yi faɗa da mutumin Isra'ila a cikin zango.11Wannan ɗan matar Ba-isra'iliya ya zagi sunan Yahweh ya kuma la'anta Allah, domin haka jama'a suka kawo shi gaban Musa. Sunan mahaifiyarsa Shelomit, ɗiyar Dibri, daga kabilar Dan.12Suka tsare shi a kurkuku har sai sun ji abin da Yahweh da kansa zai furta nufinsa a kansu.13Daga nan Yahweh ya yi magana da Musa, cewa,14"Ka ɗauki mutumin da ya la'anta Allah bayan sansani. dukkan wanda ya ji shi dole su ɗibiya hannayensu a kansa, daga nan dukkan taron jama'a su jejjefe shi.15Dole ka bayyanawa mutanen Isra'ila ka ce, "Duk wanda ya la'anci Allahnsa dole ya ɗauki alhakin laifinsa.16Shi wanda ya saɓi sunan Yahweh hakika dole a kashe shi. Dukkan taron jama'a dole su jejjefe shi da dutse, ko shi baƙo ne ko haifaffen Ba-Isra'ile. Duk wanda ya yi saɓon sunan Yahweh, dole a kashe shi.17Duk wanda ya bugi wani mutum har ya mutu, lallai dole shi ma a kashe shi.18Idan wani ya bugi dabbar wani har ta mutu, dole ya mayar, rai maimakon rai.19Idan wani ya yi wa maƙwabcinsa rauni, dole ayi masa yadda ya yi wa maƙwabcinsa:20tsaga maimakon tsaga, ido domin ido, haƙori domin haƙori. Kamar yadda ya jawo lahani ga mutum, to haka shi ma za'a yi masa.21Duk wanda ya kashe dabba dole ya biya, kuma duk wanda ya kashe mutum dole shi ma a kashe shi.22Dole ku kasance da doka iri ɗaya domin baƙo da wanda ya ke haifaffen Ba-Isra'ile, gama Ni ne Yahweh Allahnku.'"23Sai Musa ya yi magana da mutanen Isra'ila, mutanen kuma suka fito da mutumin wajen sansani, wanda ya la'anta Yahweh. Suka jejjefe shi da duwatsu. Mutanen Isra'ila suka aiwatar da dokar Yahweh ta hannun Musa.
Allah ya ba wa Musa umurnai game da abubuwan a rumfar taruwar.
"mai mai tsabta na itacen zaitun"
Wannan na nufin fitila ko fitilu a tsarkakiyar alfarwa na Yahweh. AT: "fitilar da ke cikin alfawar na wurin taron"
Allah ya cigaba da ba wa Musa umurnai game da abubuwan a cikin rumfar taruwar.
Maganan nan "akwatin alƙawari" na wakilcin ko dutsen da aka rubuta alƙawarin ko akwatin da aka ajiye dutsen. An ajiye waɗannan abubuwan ne a wuri mai tsarki, a daki ne da ke bayan labule na cikin rumfar taruwan. AT: "Wajen labule da ke gaban dutse da aka yi rubutu a akwatin alƙawarin"
Wannan labule ma ƙauri ne da aka rataya a matsayin bango. Wannan ba irin labule mara ƙaurin na wundo ba ne.
"daga faɗiwar rana zuwa tashiwar rana" ko "dukkan ɗare"
AT: 3:15.
Allah ya cigaba da ba wa Musa umurnai game da abubuwan a cikin rumfar taruwar.
Wannan na misalin lita 4.5 ne. AT: "lita huɗu da raɓi"
Wannan tabur na wuri mai tsarki ne, wanda ke a gaban mafi starki.
Allah ya cigaba da ba wa Musa umurnai game da abubuwan a cikin rumfar taruwar.
Mai yiwuwa wannan turare na gaba ko bayan gurasar ne, ko dai akan gurasar ne. AT: "Dole ne ku saka turare mai tsabta a kan kowane jerin gurasa"
Za a iya bayyana abin da turaren na nufi. AT: "a miƙa gurasar a matsayin baiko" ko "ya zama baiko da ke nufin gurasa"
AT: "Za ku ƙona turaren nan domin Yahweh"
"Gurasar da aka miƙa"
"domin sun dauka ne daga baye-bayen"
"baye-bayen ƙonawa ga Yahweh" ko "baikon da kuka ƙona ga Yahweh"
Kalman nan na nuna sabuwar sashi a littafin.
Kalaman nan duka suna nufin abu ɗaya ne. AT: "la'anta sunan Yahweh tawurin zagin sa" ko "faɗi munanan abubuwa game da Yahweh"
Wannan sunan mace ce.
Wannan sunan mutum na miji ne.
Yakamata su saka hannayensu a kansa domin a nuna cewa shi ne mai laifin.
Allah ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da yakamata su yi da mutumin da ya la'anta sunan Allah.
A nan ana magana game da shan wahala domin zunubi kamar yakamata mutumin ya ɗauka alhakin laifinsa ne. AT: "dole ya sha wahala domin zunubin sa" ko "dole a hukunta shi"
AT: "dole ne mutanen su kashe shi"
Allah ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da yakamata su yi da mutumin da ya la'anta sunan Allah.
AT: "duk wanda ya kashe wani lallai dole shima a kashe shi"
Za a iya bayyana yadda zai mayar a fili. AT: "dole ya mayar tawurin ba shi rayayyen dabba" (Dubi: )
Wannan ƙarin magana na nufin cewa za mayad da rai a maimakon rai. AT: "a mai da ran wani a maimakon wani rai" ko "a mai da rai da ya kashe"
Allah ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da yakamata mutane su yi idan wani ya yi abu mara kyau.
AT: "dole ku yi masa"
Wannan kalman na nanata cewa yakamata a yi illa wa mutum daidai da abin da ya wa wani.
Wannan na nufin ƙaryayyen ƙashi ne. AT: "ƙaryayyen ƙashi a maimakon ƙaryayyen ƙashi" ko "Idan ya ƙarya ƙashin wani, shima a ƙarye ɗaya daga cikin ƙashi shi" ko "Idan ya ƙarye ƙashin wani, za su ƙarye ɗaya daga cikin ƙashin shi"
Wannan na nufin ido da aka yi wa mummunan illa ko aka kwakwulo su waje. AT: "Idan ya ɓata idon wani, shima a ɓata masa ido" ko " Idan ya ɓata wa wani ido, za su ɓata masa ido"
Wannan na nufin haƙori da aka bugo sa daga baƙi. AT: "Idan ya cure haƙorin wani, dole shima a cire ɗaya daga cikin haƙorinsa" ko "Idan ya cire haƙorin wani, za su cire ɗaya daga cikin haƙorinsa shima"
AT: "dole su kashe duk wanda ya kashe wani"
"biyayya da umurnin"
1Yahweh ya yi magana da Musa akan tsaunin Sinai, cewa,2"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce masu, "Sa'ad da kuka zo cikin ƙasa wadda na ba ku, daga nan dole ƙasar za ta kiyaye Assabat domin Yahweh.3Dole ku shuka gonarku shekaru shida, shekaru shida kuma dole ku gyara gonarku ta inabi ku tattara amfaninta.4Amma a cikin shekara ta bakwai, dole a kula da Assabat mai saduda ta hutu, Assabat domin Yahweh. Ba za ku shuka gonar ba ko ku gyara gonar inabinku ba.5Ba za ku shirya girbe duk abin da ya tsiro don kansa ba, kuma ba za ku shirya girbin inabin da ya tsiro a kuringar da baku gyara ba. Wannan za ta zama shekara mai saduda ta hutawa domin ƙasar.6Duk tsiron da ƙasar da baku aikata ba ta bayar lokacin Assabat na ƙasar zai zama abinci domin ku. Ko, 'ya'yanku maza, da bayinku mata, da bayin da aka yi hayarsu, da baƙi da ke zaune tare da ku za ku iya tattara abinci,7dabbobinku kuma da bisashenku za su iya cin amfanin da ƙasar ta bayar.8Dole ku lisafta Assabat guda bakwai na shekaru, wato, bakwai sau shekaru bakwai, wato akwai Assabat bakwai na shekaru, jimilla duka shekaru arba'in da tara ke nan.9Sa'an nan za ku busa ƙaho da ƙarfi ko'ina a rana ta goma a watan bakwai. A ranar kaffara dole ku busa ƙaho ko'ina a cikin ƙasarku.10Dole ku keɓe shekara ta hamsin ga Yahweh kuma ayi shelar 'yanci ko'ina a ƙasar ga dukkan mazaunanta. Zata zama ranar mayarwa domin ku, inda kowacce mallaka da bayi dole za su koma wurin iyalinsu.11Shekara ta hamsin zata zama shekarar mayarwa a gare ku. Ba za ku shuka ko shirya girbi. Ko cin duk abin da ya tsiro da kansa ba, kuma ba za ku tattara inabi da ya tsiro a kuringai da baku gyara ba.12Gama Shekarar 'Yanci ce, wadda za ta zama mai tsarki domin ku. Dole kuci amfanin da ya tsiro don kansa a gonaki.13Dole ku mayar wa da kowanne mutum mallakarsa a shekarar 'Yanci.14Idan ka sayar da gona ga maƙwabcinka ko ka sayi gona a wurin maƙwabcinka, kada ku cuci ko ku zalunci juna.15Idan ka sayi gona daga maƙwabcinka, sai ka yi la'akari da shekaru da amfanin da za a girbe har zuwa shekarar gaba ta 'Yanci. Maƙwabcinka da ke sayar maka da gonar dole ya kula da wannan shi ma.16Yawan shekarun har zuwa shekarun 'Yanci zai ƙara tamanin ƙasar, gwargwadon ƙarancin shekarun za a rage tamanin ta, saboda yawan girbin da ƙasar zata bayar domin sabon mai gonar yana alaƙa da yawan shekaru kafin shekarar 'Yanci ta gaba.17Ba za ku cuci ko ku zalunci juna ba; maimakon haka dole ku girmama Allahnku, gama Ni ne Yahweh Allahnku.18Domin wannan dole ku kiyaye umarnaina, ku kiyaye dokokina, kuma ku aiwatar da su. Daga nan za ku zauna cikin ƙasar lafiya.19ƙasa za ta bada amfaninta, kuma za ku ci ku ƙoshi kuma ku zauna can cikin tsaro.20Za ku iya cewa, "Me zamu ci cikin shekara ta bakwai? Duba, ba dama mu shuka ko mu tattara amfaninmu ba."21Zan umarci albarkata ta zo bisanku a cikin shekara ta shida, kuma zata bada isasshen amfani har shekaru uku.22Za ku shuka cikin shekara ta takwas kuma ku ci gaba da cin abincin da kuka ajiye a shekarun baya. Har lokacin girbi na shekara ta tara ta zo, za ku ci daga tanajin ajiyar da kuka yi a shekarun baya.23Ba za a sayar da ƙasa ga wani ya zama sabon mai ita ta din-din din ba, saboda ƙasa tawace. Dukkanku bãƙi ne masu zama na ɗan lokaci a ƙasa ta.24Dole ku kula da haƙin fansa domin dukkan ƙasar da kuka mallaka; dole ku bari a sake sayen ƙasar ga iyalin daga wanda ya saye ta.25Idan ɗan'uwanka Ba-Isra'ile ya zama talaka kuma akan wannan dalili ya sayar da wata mallaka tasa, daga nan danginsa na kusa zai iya zuwa ya fanshi mallakar da ya sayar maka.26Idan mutum ba shi da ɗan'uwa da zai fãnshi mallakarsa, amma idan ya azurta har zai iya fãnsar ta,27daga nan zai iya lissafta shekaru tun lokacin da aka sayar da ƙasar sai ya biya sauran ga mutumin da ya sayar wa. Daga nan zai iya dawo wa ga mallakarsa.28Amma idan bai iya dawo da ƙasar domin kansa ba, daga nan ƙasar da ya sayar za ta kasance cikin mallakar shi wanda ya saye ta har zuwa lokacin shekarar 'Yanci. A shekarar 'Yanci, ƙasar zata koma ga mutumin da ya sayar da ita, ainihin mai ita kuma zai koma ga mallakarsa.29Idan mutum ya sayar da gidansa a cikin birni mai ganuwa, daga nan zai iya ya fãnshar sa cikin dukkan shekara bayan ya sayar. Gama a cikin cikar shekara yana da 'yancin fãnsa.30Idan ba a fãnshi gidan kamin cikar shekara ba, daga nan gidan da ke cikin birni mai ganuwa zai zama mallaka ta din-din din ga wanda ya saya shi da zuriyarsa. Ba za a mayar da shi cikin shekara ta 'Yanci ba.31Amma gidajen ƙauyukan da ba su da gãnuwa kewaye da su za a yi lissafinsu a matsayin filin ƙasa. Za a iya fãnsarsu kuma dole a dawo da su a shekarar 'Yanci.32Amma, gidajen da Lebiyawa suka mallaka cikin birane za su iya fãnsarsu a kowanne lokaci.33Idan ɗaya daga cikin Lebiyawa bai fãnshi gidan da ya sayar ba, daga nan gidan da aka sayar a cikin birni a inda ya ke dole a dawo da shi cikin shekarar 'Yanci, gama gidajen biranen Lebiyawa mallakarsu ne a cikin mutanen Isra'ila.34Amma filayen da ke kewaye da biranen ba za a sayar da su ba saboda mallakar Lebiyawa ne na din-din din.35Idan ɗan ƙasarku ya zama talaka, yadda ba zai iya biyan buƙatar kansa ba, daga nan dole ka taimake shi kamar yadda za ka taimaki bãƙo ko wani dabam da ke zaune kamar na waje a cikinku.36Kada ka caje shi da ruwa ko ka yi ƙoƙarin samun riba daga gare shi ta kowacce hanya, amma ka girmama Allahnka domin ɗan'uwanka ya ci gaba da zama tare da kai.37Kada ka bashi bashin kuɗi da ruwa, ko ka sayar masa abinci don samun riba.38Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito da ku daga ƙasar Masar, domin in baku ƙasar Kan'ana, kuma in zama Allahnku.39Idan ɗan ƙasarku ya zama talaka har ya sayar da kansa gare ka, kada kasa shi ya yi aiki kamar bawa. Ka kula da shi kamar baran haya.40Dole ya zama kamar wanda ya ke zama da kai na ɗan lokaci. Zai yi hidima tare da kai har zuwa shekarar 'Yanci.41Daga nan zai tafi daga gare ka, shi da 'ya'yansa tare da shi, zai koma wurin iyalinsa da mallakar kakanninsa.42Gama su bayina ne waɗanda na kawo daga ƙasar Masar. Ba za a sayar da su kamar bayi ba.43Kada ku mallake su da tsanani, amma dole ku girmama Allahnku.44Ga zancen bayinku maza da mata, waɗanda za ku samu daga al'umman da ke kewaye da ku, za ku iya sayen bayi daga gare su.45Za ku iya sayen bayi daga bãƙin da ke zaune a wurin ku, wato, daga iyalin da ke tare da ku, 'ya'yan da aka haifa cikin ƙasarku. Sun zama mallakarku.46Za ku iya tanada wa 'ya'yanku irin waɗannan bayi su zama gãdo bayan ku, su riƙe su a matsayin mallaka, su kuma za su zama bayi har abada, amma baza ku yi mulkin 'yan'uwanku cikin mutanen Isra'ila da tsanani ba.47Idan bãƙo ko wani da ke zama cikinku na ɗan lokaci ya azurta, ɗan'uwanku kuma Ba-Isra'ile ya talauce ya sayar da kansa ga bãƙon, ko ga wani cikin iyalin bãƙon,48bayan da an sayi Ba-Isra'ilenku, za a iya fãnsarsa. Wani daga cikin iyalinsa zai iya fãnsar sa.49Zai iya zama kawun mutumin ko ɗan kawunsa, wanda ya fanshe shi, ko wani wanda ya ke kusa da iyalinsa. Ko, idan ya azurta, zai iya fãnsar kansa.50Dole ya yi ciniki da wanda ya saye shi; dole su lisafta shekarun daga shekarar da ya sayar da kansa ga wanda ya saye shi har zuwa shekarar 'Yanci. Farashin da aka fãnshe shi zai zama dai-dai da yawan wanda aka biya baran da akayi hayar sa, zai iya ci gaba da yin aiki har wasu shekaru ga wanda ya sawo shi.51Idan har yanzu akwai sauran shekaru da yawa kafin shekarar 'Yanci, dole ya biya kuɗin domin fãnsarsa bisa ga adadin waɗannan shekaru.52Amma idan shekarun sun ragu kaɗan ga shekarar 'Yanci, daga nan dole ya yi ciniki tare da mai sayensa ya nuna yawan shekarun da suka ragu kafin shekarar 'Yanci, kuma dole ya biya domin fãnsarsa bisa ga yawan shekarun.53Dole a kula da shi kamar mutumin da aka yi hayarsa shekara bayan shekara. Dole ku tabbatar ba a tsananta masa da tsanani ba.54Idan ba a fãnshe shi ta waɗannan hanyoyi ba, daga nan zai ci gaba da bauta har zuwa shekarar 'Yanci, shi da 'ya'yansa tare da shi.55A gare ni mutanen Isra'ila bayi ne. Bayi na ne waɗanda na fisshe su daga ƙăsar Masar. Ni ne Yahweh Allahnku.'"
Ana magana game da ƙasar kamar mutum zai iya yin biyayya ga assabat tawurin hutu. Kamar yadda yakamata mutanen zasu huta a kowace rana ta bakwan, yakamata mutanen su ɗaukaka Allah ta wurin rashin nome gonar a kowce sheƙara ta bakwan. AT: "Dole ku yi biyayya ga doƙar assabat tawurin barin gonar ta huta a kowace shekara ta bakwai domin Yahweh" ko "dole ku yi biyayya ga assabat na Yahweh tawurin rashin nome gonar a kowace shekara ta bakwai"
Gyara gonar ku ta innabi na nufin a yanke rashi da kuringar domin 'ya'yan itacen su yi kyau.
A nan ana magana game da rashin nome gonar kamar barin gonar ta huta ne. AT: "dole ku kula da Assabat mai saduda domin gonar" ko "Dole ku yi biyayya ga doƙar nan ta Assabat tawurin rashin nome gonar a kowace shekara ta bakwai"
A sura ta 25:5-6 Yahweh na nufin cewa ba zai bar mai gonar ya shirya bayinsa domin su girbe gonar kamar yadda ya ke yi a shekaru shidda da suka wuce ba. Amma dai, Yahweh zai bar sauran jama'a su je gonar domin su ɗeba su kuma ci 'ya'yan itacen da suka samu.
Wannan na nufin cewa babu wanda ya gyara kuringar, ya kuma ɗatse su kamar yadda suke yi a sauran shekarun. AT: "kurigar ku da baku gyara ta ba"
"duk abin da ya tsira a gonar da baku yi aikata ta ba"
Yahweh ya cigaba ya gaya wa Musa game da abin da yakamata mutanen zasu yi.
"za a samu shekaru bakwai sau bakwai"
Shekaru tara - "shekaru 49"
Wannan wata na bakwai ne a kalandar Ibriniyawa. Rana ta goma ya kusanci karshen watar September.... a kalanda ta Yamma.
AT: 23:26
Wannan jeren lamba ce. AT: "shekaran 50"
Ranar mayarwa shekara ce da ya zama cewa Yahudawa za su mayar da gona wa ainihin maishi su kuma săke bayin su daga ɓauta. AT: "shekarar gyara gare ku" ko "shekara domin ku mayar da gona da kuma săke bayi daga ɓauta"
AT: "dole ku mayar da mallaka da kuma bayi"
Za a iya yin bayanin waddanda za a mayar masu da gonar AT: "25:10-10"
AT: 25:5-7
"wannan shekara ta gyara" ko " shekaran nan domin a mayar da gona a kuma săke bayi daga ɓauta"
Allah ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da yakamata mutane su yi.
AT: "da za ku girbe"
"a shekara ta gaba na gyara" ko "a shekara ta gaba da za a mayar da gona"
Dukkan waddanan magana suna nufin abi ɗaya ne. Su na nanata cewa dole ne mutane su yi biyyaya ga duk abin da Yahweh ya faɗi.
Wannan na nufin cewa za su ci su koshi har sai cikin su ya cika. AT: "za ku ci har sai kun koshi" ko "za ku ci sosai"
A nan "Ku" na nufin mutanen Isra'ila ne.
Allah ya yi maganar albarkansa kamar mutum ne da zai iya yin biyyaya da shi. AT: "Zan aiko da albarkata a bisanku" ko "Zan albarkace ku"
AT: "daga abincin da kuka yi ajiya"
Yahweh ya cigaba da yin magana.
AT: "Ba za ku sayar da gonar ku din-din din zuwa ga wani mutum ba"
Ƙalman nan "fansa" za a iya faɗe su da kalmar nan ta aiki "sake saya." AT: "Ku tuna cewa ainihin mai shi na da iko ya fanshi gonar a duk lokacin da ya so"
AT: "dole ku bar iyalin wanda kuka saya gonar a gun sa su sake sayar ta"
AT: "ya sayar da gonar"
AT: "biya wa wanda ya saye ta da kudin da da wanda ya saye ta ya amfana"
AT: 25:10.
AT: "wanda ya saye ta zai komar da ita"
"zai koma ga gonar sa"
AT: "bayan da ya sayar da ita"
AT: 25:23-25
AT: "Idan shi ko iyalinsa basu fãnshi gidan ba"
AT: "Ba lallai ba ne mutumin da ya saya gidan ya mayar da shi"
AT: 25:10
Wasu ƙauyuka ba su da gãnuwa a kewaye da su.
AT: "Za ku iya sayan waddanan gidajen kuma waddanda suka saye ta dole su mayar da ita"
AT: 25:10
AT: "gidajen da Lebiyawa suka mallaka cikin biranensu"
AT: Lebiyawan za su iya fãnshe su a kowace lokaci"
AT: "wanda ya saya gida a cikin birni a inda yake dole ya mayar da shi"
AT: 25:10
An raɓa ƙasar Kan'ana wa mutanen Isra'ila ne, amma a wannan ƙasar, an ba wa Lebiyawa biranai guɗa 48 ne kawai da kuma filaye da suke kewaye da su. AT: "sashin ƙasar su da Isra'ilawa suka mallaka" ko "mallakar su a ƙasar Isra'ila"
AT: "Amma, kada Lebiyawan su sayar da filayen dake kewaye da biranensu"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da yakamata mutane za su yi.
"Kada ka sa shi ya biya ka fiye da abin da ka arar masa"
Wannan na nufin cewa yakamata mai shi ya kula da Isra'ilawa da ladabi fiye da yanda zai yi da bayi.
AT: 25:10.
Allah ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da zai faɗa wa mutane.
"mutanen ka bayi na ne"
AT: "Ba za ku sayar da su kamar bayi ba"
"za ku iya sayan bayi daga al'uman nan"
AT: "bayan wa wani dabam ya saya dan'uwan ka Ba-isra'ila, wani daga iyalin Ba-isaila zai iya sayan sa kuma"
Ba-isra'ila zai iya zama bawa har shekarar ta ''Yanci. Waddanan Umurnan na idan Ba-isra'ila ya na so ya saya 'Yancinsa kafin shekarar nan ta 'Yanci ne.
AT: 25:10.
Kalmar aikin nan "dai dai" za a iya bayyana su cikin aiki. AT: "dole ne su san dai-dai farashin fãnsar sa" ko "Dole ne su san ko nawa ne zasu biya Ba-al'uman nan domin su cece Ba-isra'ilan nan"
Idan Ba'isra'ilan ya saya 'yancin sa, dole ne Ba'al'uman nan zai yi hayar bara da zai yi aikin da Ba'isra'ilan nan zai yi amma bai yi ba. Kalmar nan "biya" za a iya faɗin su cikin aiki. AT: "bisa ga abin da wani zai biya domin ya yi hayar bara"
"domin sauran shekaru kafin 'yanci da Ba-isra'ilan zai cigaba da yin aiki amma ba zai yi ba"
"dole ne Ba'isra'ila bawan nan zai biya"
AT: "dole ne Ba-al'uman nan da ya sayo shi a matsayin bawa ya yi da shi"
AT: "kada wani ya tsananta masa"
AT: "Idan wani bai fãnshe shi ta waɗannan hanyoyi ba daga wanda ya sayo shi a mastayi bawa"
Bayin nan Ba'isra'ila da 'ya'yansa za su yi wa Ba'al'uman nan bauta har zuwa shekarar 'Yanci, sa'an nan Ba'al'uman zai sãke Ba'isra'ilan da 'ya'yansa.
"Gama a gare ni ne jama'ar Isra'ila bayi ne." Ta wannan dalilin ne Allah ya so a sãke Isra'ilawa a shekarar 'yanci. Su bayin sa ne. Ba a basu 'yancin su zama bayin wani din-din din ba.
1"Ba za ku yi gumakai ba, kuma ba za ku ɗaga sassaƙaƙƙiyar siffa ko keɓaɓɓen ginshiƙin dutse, kuma ba za ku kafa kowacce irin sassaƙaƙƙiyar siffa ta dutse a cikin ƙasarku da za ku durƙusa masa ba, gama ni ne Yahweh Allahnku.2Dole ku kiyaye assabataina ku girmama rumfar sujadata. Ni ne Yahweh.3Idan kuka yi tafiya cikin umarnaina kuka kiyaye dokokina kuma kuka yi biyayya da su,4daga nan zan ba ku ruwan sama a lokacinsa; ƙasar kuwa zata bada amfaninta, itatuwan gonaki kuma za su bada 'ya'yansu.5Za ku yi ta girbi har lokacin girbin 'ya'yan inabi, girbin inabi kuma zai ci gaba har lokacin shuka. Za ku ci abincinku ku ƙoshi kuma ku zauna lafiya inda kuka yi gida a cikin kasarku.6Zan bada salama cikin ƙasar; za ku kwanta ba abin da zai tsoratar da ku. Zan kawar da mugayen dabbobi daga ƙasar, takobi kuma ba zata ratsa ta ƙasarku ba.7Za ku runtumi maƙiyanku, kuma za su faɗi a gaban ku ta wurin takobi.8Mutum biyar ɗinku za su runtumi ɗari, mutum ɗarinku kuma za su runtumi mutum dubu goma; maƙiyanku za su faɗi a gabanku ta wurin takobi.9Zan dube ku da idon rahama in sa ku hayayyafa in riɓanɓanya ku; zan tabbatar da alƙawarina tare da ku.10Za ku ci abinci ku ajiye shi tsawon lokaci. Za ku fitar da abincin da kuka ajiye saboda kuna buƙatar ɗaki domin ku ajiye sabon hatsi.11Zan kafa mazaunina a tsakiyar ku, ba kuwa zan ƙi ku ba.12Zan yi tafiya tare da ku in kuma zama Allahnku, kuma za ku zama mutanena.13Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, domin kada ku zama bayinsu. Na karya sandunan karkiyarku na sa ku yi tafiya madaidaiciya.14Amma idan ba za ku saurare ni ba, kuma ba za ku yi biyayya da dukkan dokokin nan ba,15idan kuma kuka yi watsi da dokokina kuma kuka ƙi umarnaina, domin kada ku yi biyayya da dukkan dokokina, amma kuka karya alƙawarina -16- idan kuka yi waɗannan abubuwa, daga nan nima zan yi wannan a gare ku: Zan sa tsõro a kan ku, cututtuka da zazzaɓin da zai lalatar da idanunku rayuwa zata zama da wahala. Za ku shuka irinku a banza, amma maƙiyanku ne za su ci amfaninsu.17Zan sa fuskata gãba da ku, maƙiyanku za su fi ƙarfinku. Mutanen da suke ƙin ku za su mallake ku. Za ku yi gudu ko da wani bai kore ku ba.18Idan bayan dukkan wannan baku saurare ni ba, daga nan zan ƙara hukunta ku da tsanani sau bakwai domin zunubanku.19Zan karya gimanku cikin ikonku. Zan sa sama da ke kanku ta zama kamar ƙarfe ƙasarku kuma kamar tagulla.20Ƙarfinku zai zama ba amfani, saboda ƙasarku ba zata bada amfaninta ba, itatuwan ƙasar kuma ba za su bada 'ya'yansu ba.21Idan kuka yi tafiya gãba da ni ba ku saurare ni ba, Zan kawo nushi sau bakwai akan ku, bisa ga yawan zunubanku.22Zan aiko maku da mugayen namomin jeji gãba da ku, waɗanda za su sace 'ya'yanku, su hallaka dabbobinku, su sa ku zama kaɗan. Hanyoyin kuma za su zama ba masu gilmawa.23Idan baya ga waɗannan duk da haka ba ku karɓi gyara na ba kuka ci gaba da tafiya cikin yin adawa da ni,24daga nan ni ma zan yi tafiya cikin yin adawa da ku, kuma Ni da kaina zan hukunta ku sau bakwai saboda zunubanku.25Zan kawo takobi a kanku a kashe ku da ramuwa domin karya alƙawari. Za a tattara ku tare cikin biranenku, can zan aikar da cuta a wurin, za a miƙa ku cikin hannun maƙiyanku.26Idan na datse abincin da kuka tanada, mata goma za su dafa abinci a murhu ɗaya, kuma za su rarraba abincinku bisa ga ma'auni. Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba.27Idan ba ku saurare ni ba duk da waɗannan abubuwan, amma kuka ci gaba da tafiya gãba da ni,28daga nan ni ma zanyi tafiya gãba da ku cikin fushi, kuma zan hukunta ku har sau bakwai sosai saboda zunubanku.29Za ku ci naman 'ya'yanku maza; za ku ci naman 'ya'yanku mata.30Zan lalatar da wurarenku masu tsayi, in datse bagadan ƙona turarenku, in jefar da gawarwakinku akan gawarwakin gumakanku, kuma ni da kaina zan ji ƙyamar ku.31Zan juyar da biranenku su zama kufai in lalatar da masujadanku. Ba zan ji daɗin ƙamshin baye-bayenku ba.32Zan lalatar da ƙasar. Maƙiyanku da ke zaune a ƙasar za su yi mamaki da irin lalatarwar.33Zan warwatsaku cikin ƙasashe, kuma zan zare takobina in fafareku. Ƙasarku za a yashe ta, biranenku kuma za su zama kangaye.34Daga nan ƙasar zata ji daɗin hutunta muddin tana kwance yasasshiya kuma ku kuna ƙasashen maƙiyanku. A wannan lokaci, ƙasar zata huta zata ji daɗin hutunta.35Muddin ƙasar tana kwance kango, zata huta, zai zama hutun da bata samu ba tare da assabatunku, lokacin da kuka zauna cikinta.36Amma ga waɗansun ku da suka ragu cikin ƙasashen maƙiyanku, Zan aikar da tsoro cikin zukatansu yadda motsin kaɗawar ganye cikin guguwa ma zai razanar da ku, za ku sheƙa a guje kamar kuna gujewa takobi. Za ku faɗi, koda ba wanda ke korar ku.37Za ku yi ta karo da juna kamar kuna gujewa daga takobi, kodashike ba mai korar ku. Ba za ku sami ikon tsayawa gaban maƙiyanku ba.38Za ku hallaka cikin al'ummai, ƙasar maƙiyanku kanta za ta haɗiye ku.39Waɗanda suka ragu a cikinku za su lalace cikin zunubansu, a can cikin ƙasashen maƙiyanku, saboda zunubin kakanninsu kuma za su lalace kamar su.40Duk da haka idan suka furta zunubansu da zunubin kakanninsu, da cin amanar su da suka zama da rashin aminci a gare ni, da tayarwar da suka yi mani --41wanda ya sa ni na juya gãba da su na kawo su cikin ƙasar maƙiyansu - idan suka ƙasƙantar da zukatansu marasa kaciya, kuma suka karɓi hukunci domin zunubansu,42daga nan zan tuna da alƙawarina da Yakubu, alƙawarina da Ishaku, da kuma alƙawarina tare da Ibrahim; kuma, zan tuna da ƙasar.43Za su yashe da ƙasar, za ta ji daɗin hutunta yayin da take kwance yasasshiya ba tare da su ba. Za su biya alhakin zunubansu saboda su da kansu sun yi watsi da umarnaina suka yi ƙyamar dokokina.44Duk da haka bayan dukkan waɗannan, sa'ad da suke cikin ƙasar maƙiyansu, ba zan ƙi su ba, ko in ƙyamace su domin in hallaka su gaba ɗaya har in karya alƙawarina da su ba, Gama Ni ne Yahweh Allahnsu.45Amma saboda su zan tuna da alƙawarina tare da kakanninsu, waɗanda na fisshe su daga ƙasar Masar a idon al'ummai, domin in zama Allahnsu. Ni ne Yahweh."46Waɗannan dokoki, umarnai da shari'u waɗanda Yahweh ya yi tsakaninsa da mutanen Isra'ila a Tsaunin Sinai ta hannun Musa.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa game da abin da yakamata mutanen za su yi.
"kiyaye dokokin Assabataina"
Ana nufin abu ɗaya ne ta waddanan hanyoni guda ukun. Sun nanata cewa dole ne mutanen za su kiyaye kowace abu da Allah ya umurce su su yi. AT: "Idan kun kiyaye dokoki na da kuma umurnai na"
A nan ana magana game da yin rayuwa bisa ga umurnai kamar yakamata su yi tafiya bisa ga umurnan ne. "Idan kun bi da halayen ku bisa ga umurnai na" ko "Idan kun yi rayuwa bisa ga umurnaina"
A nan gurasa na nufin abinci ne. "Ga ƙoshia" na nufin har sai cikin su ya cika da abinci. AT: "ci abinci har su ƙoshi
" Zan bada salama cikin ƙasar"
A nan, kalman nan "takobi" na nufin sojojin abokan gaba ko hari na abokan gaba. AT: "sojoji ba za su kawo maku hari ba"
A nan "faɗi" na nufin mutuwa, kuma "takobi" na nufin ko a kai hari da takobi ko yaki ne. AT: "za su mutu idan kun kai masu hari da takobi" ko "za ku karkashesu a wurin yaki"
Wannan na nufi cewa Isra'ilawa za su yi nasara ga maƙiya masu yawa.
"5 ... 1000 ... 10,000"
"Zan maku alheri" ko "Zan albarkace ku" (UDB)
Kalaman nan guda biyu na suna nufin cewa Allah zai saka su su samu zuriya masu yawa saboda su yi yawa.
A nan, Allah na magana game da su cewa za su sami 'ya'ya dayawa kamar su itattuwa ne da za su haifi 'ya'ya dayawa. AT: "saka ku sami 'ya'ya dayawa"
"Za ku sami ishashen abinci da kuka ajiye ku ci na tsawon lokaci" ko "za ku samu ishashen abinci da za ku ajiye ku kuma ci na tsawon lokaci"
"Zan saka mazaunina a cikin ku"
"Zan karbe ku"
Tafiya tare da su na nufin rayuwa cikin su ne. AT: "Zan yi rayuwa tare da ku"
Allah na magana game da bautar su kamar cewa yakamata su saka karkiya a wuya ne domin su yi aiki da kwazo. Karya sandunan karkiya kuma na nufin kubutar da su ne. AT: "Na kubutad da ku daga aiki mai wahala da suka sa ku yi"
Yahweh yana gaya wa Musa game da abin da zai faru idan mutane ba su kiyaye umurnansa ba.
1Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,2"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce masu, 'Idan wani ya yi alƙawari na musamman ga Yahweh, yi amfani da waɗannan tamanin.3Darajar misalin abin da za ka biya domin maza daga shekara ashirin zuwa sittin dole ya zama awo hamsin na tagulla, bisa ga awo na wuri mai tsarki.4Ga mataye masu shekaru iri ɗaya darajar abin da za a biya dole ya zama awo talatin.5Daga shekara biyar zuwa shekara ashirin darajar abin da za a biya domin maza dole ya zama awo ashirin, mataye kuma awo goma.6Daga wata ɗaya zuwa shekara biyar darajar abin da za a biya domin maza dole ya zama awo biyar na tagulla, ga mata awo uku na tagulla.7Daga shekaru sittin zuwa sama ga maza tamanin abin da za a biya dole ya kai awo goma sha biyar, mata kuma awo goma.8Amma idan mutumin da ya yi wa'adi ba zai iya biyan tamanin ba, daga nan mutumin da aka bayar dole a kawo shi gaban firist, firist ɗin zai kimanta tamanin abin da mutumin da ya yi wa'adin zai iya biya bisa ga ƙarfinsa.9Idan wani yana son miƙa hadayar dabba ga Yahweh, kuma idan Yahweh ya karɓe ta, daga nan wannan dabbar za a keɓe ta dominsa.10Kada mutumin ya musanya irin wannan dabbar, mai kyau da marar kyau ko marar kyau da mai kyau. Idan ya musanya ko canza dabbar da wata, daga nan dukkan su biyu da aka musanya da wadda aka musanyar za su zama masu tsarki.11Duk da haka, idan abin da mutumin ya yi wa'adi zai ba Yahweh ta zama marar tsarki, don haka Yahweh ba zai karɓe ta ba, daga nan dole mutumin ya kai dabbar wurin firist.12Firist zai kimanta tamanin ta, bisa ga darajar dabbar. Duk yadda firist ya kimanta dabbar, haka darajarta zata zama.13Idan mai ita yana so ya fãnshe ta, sai ya yi ƙarin kashi biyar na farashin fãnsa.14Idan mutum ya keɓe gidansa a matsayin kyauta mai tsarki ga Yahweh, daga nan sai firist ya kimanta tamaninsa ko da kyau ko ba kyau. Duk yadda firist ya kimanta darajarsa, haka zai zama.15Amma idan mai gidan wanda ya keɓe gidan yana so ya ƒãnshe shi, dole ya ƙara kashi ɗaya cikin biyar na tamanin farashin fansa, gidan kuwa zai zama nasa.16Idan mutum ya keɓe wani sãshe na gonarsa, daga nan tamaninta zai zama kimanin dai-dai da yawan irin da ya kamata a shuka - tiyar bãli tamaninta zai zama a bakin shekel hamsin na azurfa.17Idan ya keɓe gonarsa lokacin shekarar 'Yanci, haka tamaninta zai tsaya.18Amma idan ya keɓe gonarsa bayan shekarar 'Yanci dole firist ya lisafta yawan tamanin ƙasar bisa ga yawan shekarun da suka rage har zuwa shekarar 'Yanci, kuma dole a rage tamaninta.19Idan shi mutumin da ya keɓe gonar yana so ya fãnshe ta, daga nan dole ya ƙara kashi biyar na tamanin, kuma sai ta zama ta sa.20Idan bai fãnshi gonar ba, ko idan ya rigaya ya sayar da gonar ga wani mutum, ba za ta fãnsu ba faufau.21Maimakon haka, idan gonar, an sake ta cikin shekarar 'Yanci, zata zama kyauta mai tsarki ga Yahweh, kamar gonar da aka bayar gaba ɗaya ga Yahweh. Zata zama mallakar firist.22Idan mutum ya keɓe gonar da ya saya, amma wannan gonar bata cikin ƙasar gãdon iyalinsa,23daga nan firist zai kimanta tamaninta har zuwa shekarar 'Yanci, daga nan dole mutumin ya biya tamaninta a ranar a matsayin kyauta mai tsarki ga Yahweh.24A cikin shekarar 'Yanci, sai gonar ta koma ga mutumin wanda daga wurinsa aka saye ta, ga ainihin mai gonar.25Dukkan kowanne tamani dole ya zama bisa ga nauyin awo na wuri mai tsarki. Ƙaramin awo ashirin da ke matsayin awo ɗaya.26Ba wanda zai keɓe ɗan fãri cikin dabbobi, da shike dama na Yahweh ne; ko sã ko tunkiya, na Yahweh ne.27Idan dabbar marar tsarki ce, daga nan mai ita zai iya fãnsar ta bisa ga tamanin, dole ya ƙara kashi biyar akan tamanin. Idan ba'a fãnshi dabbar ba, daga nan sai a sayar da ita bisa ga tamanin da aka sanya.28Amma ba abin da mutum zai bayar ga Yahweh, daga dukkan abin da ya ke da shi, ko mutum ko dabba, ko ƙasar gãdonsa, da za a sayar ko a fãnsar. Duk abin da aka keɓe ya zama mai tsarki na Yahweh.29Ba za a biya kuɗin fãnsa ba ga mutumin da aka keɓe domin hallakarwa. Wannan mutumin dole a kashe shi.30Dukkan zakkar ƙasa, ko ta hatsin da aka noma a ƙasa ko 'ya'yan itatuwa, na Yahweh ne. Mai tsarki ne ga Yahweh.31Idan mutum ya fãnshi kowanne abu na zakkarsa, dole ya ƙara ɗaya bisa biyar na tamaninta.32Ga kowanne ɗaya bisa goma na makiyaya ko dabbobi, ko mene ne ya wuce ta ƙarƙashin sandar makiyaya, dole a keɓe ɗaya bisa goma ga Yahweh.33Kada makiyayin ya nemi mai kyau ko munanan dabbobi, kada ya musanya da wata. Idan har ya canja, daga nan dukkansu da wadda ya canja za su zama tsarkakku ga Yahweh. Ba za a fãnshe su ba.'"34Waɗannan su ne dokokin da Yahweh ya bayar a tsaunin Sinai ga Musa domin mutanen Isra'ila.
1Yahweh ya yi magana da Musa a runfar taruwa a cikin jejin Sinai. Wannan ya fãru ne a rana ta farko a wata na biyu a shekara ta biyu bayan da mutanen Isra'ila suka fito daga ƙasar Masar. Yahweh yace,2"Ka yi ƙidayar dukkan mutanen Isra'ila daga kowanne dangi, a cikin iyalan ubanninsu. Ka ƙidaya su bisa ga sunaye. Ka ƙidaya kowanne namiji, kowanne mutum3wanda ke shekaru ashirin ko fiye. Ka ƙidaya dukkan waɗanda ke iya faɗa a matsayin sojoji domin Isra'ila. Kai da Haruna tilas ku rubuta lissafin dukkan mazaje a rukunonin mayaƙansu.4Mutum daga kowacce kabila, kan dangi, tilas ya yi hidima tare da ku a matsayin shugaban kabilarsa. Kowanne shugaba tilas ya shugabanci mazajen da zasu yi faɗa kabilarsa.5Waɗannan ne sunayen shugabannin waɗanda tilas su yi faɗa tare da ku: Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;6daga kabilar Simiyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;7daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;8daga kabilar Issaka, Netanel ɗan Zuwar;9daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;10daga kabilar Ifraim ɗan Yosef, Elishama ɗan Ammihud; daga kabilar Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;11daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gidiyoni;12daga kabilar Dan, Ahiyeza ɗan Ammishaddai;13daga kabilar Asha, Fagiyel ɗan Okran;14daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Duwel;15kuma daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan."16Waɗannan ne mazajen da aka zaɓa daga mutanen. Suka bida kabilun kakanninsu. Sune shugabannin kabilun a Isra'ila.17Musa da Haruna suka ɗauki waɗannan mutane, waɗanda aka lissafa da sunayensu,18tare da waɗannan mutanen tattaro dukkan mutanen Isra'ila a rana ta farko na wata na biyu. Daga nan kowanne mutum ɗan shekaru ashirin da sama ya tantance asalinsa. Dole ya bada suna ga dangi da iyalan zuriyar daga kakanninsa.19Daga nan Musa ya rubuta lissafinsu a cikin jejin Sinai, kamar yadda Yahweh ya umarce shi ya yi.20Daga zuriyar Ruben, haihuwar fãrin Isra'ila, an yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum kuma ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.21Suka ƙidaya mutane 46,500 daga kabilar Ruben.22Daga zuriyar Simiyon kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum kuma ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen kabilun kakanninsu da iyalansu.23Suka ƙidaya mutane 59,300 daga kabilar Simiyon.24Daga zuriyar Gad kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum kuma ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.25Suka ƙidaya mutane 45,650 daga kabilar Gad.26Daga zuriyar Yahuda kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum kuma ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.27Suka ƙidaya mutane 74,600 daga kabilar Yahuda.28Daga zuriyar Issaka kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.29Suka ƙidaya mutane 54,400 daga kabilar Issaka.30Daga zuriyar Zebulun kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.31Suka ƙidaya mutane 57,400 daga kabilar Zebulun.32Daga zuriyar Ifraim kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.33Suka ƙidaya mutane 40,500 daga kabilar Ifraim.34Daga zuriyar Manasse kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen dangin kakanninsu da iyalansu.35Suka ƙidaya mutane 32,200 daga kabilar Manasse.36Daga zuriyar Benyamin kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen kabilun kakanninsu da iyalansu.37Suka ƙidaya mutane 35,400 daga kabilar Benyamin.38Daga zuriyar Dan kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen kabilun kakanninsu da iyalansu.39Suka ƙidaya mutane 62,700 daga kabilar Dan.40Daga zuriyar Asha kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen kabilun kakanninsu da iyalansu.41Suka ƙidaya mutane 41,500 daga kabilar Asha.42Daga zuriyar Naftali kuma aka yi ƙidayar dukkan sunayen kowanne mutum ɗan shekaru ashirin ko sama wanda ke iya zuwa yaƙi, daga rubuce-rubucen kabilun kakanninsu da iyalansu.43Suka ƙidaya mutane 53,400 daga kabilar Naftali.44Musa da Haruna suka ƙidaya dukkan waɗannan mutane, tare da mutanen sha biyu waɗanda ke shugabancin kabilun sha biyu na Isra'ila.45Haka dukkan mazajen Isra'ila daga 'yan shekaru ashirin zuwa sama, dukkan waɗanda ke iya faɗa a yaƙi, aka ƙidaya su a kowanne iyalansu.46Suka ƙidaya mutane 603,550.47Amma mazajen da suka fito daga zuriyar Lebi ba a ƙidaya su ba,48saboda Yahweh ya cewa Musa,49"Tilas baza ka ƙidaya kabilar Lebi ba ko ka haɗa da su cikin jimillar mutanen Isra'ila.50A maimakon haka, ka sa Lebiyawa lura da runfar alƙawarin dokoki, su kuma lura da dukkan kayayyakin adon runfar da kowanne abu dake cikinta. Tilas Lebiyawa su ɗauki runfar, kuma tilas su ɗauki kayayyakin adon runfar. Tilas su lura da runfar, su kuma yi wa kansu sansani kewaye da ita.51Sa'ad da za a matsa da runfar zuwa wani wuri, tilas Lebiyawa su sauke ta. Sa'ad da za a kafa runfar, tilas Lebiyawa su kafa ta. Duk wani baƙo da ya zo kusa da runfar tilas a kashe shi.52Sa'ad da mutanen Isra'ila zasu kafa runfunansu, kowanne mutum tillas ya yi haka kusa da tutar da take ta ƙungiyar mayaƙansa.53Duk da haka, Lebiyawa tilas su kafa runfunansu kewaye da runfar alƙawarin dokoki kada fushina ya sauko bisa mutanen Isra'ila. Tilas Lebiyawa su lura da runfar alƙawarin dokoki."54Mutanen Isra'ila suka yi dukkan waɗannan abubuwa. Suka yi kowanne abin da Yahweh ya umarta ta wurin Musa.
Wannan sunan Allah ne da ya bayyana wa mutanesa a ciki Tsohon Alkawaro. Dubi shafin transalationWord game da Yahweh yadda ya ka juya wannan.
"rana ta fari a wata na biyu." Wannan shine wata na biyu a kalandar Yahudawa. Rana ta fari kusa ne da da watan huɗu a kalandar ta yammacin duniya.
Wannan na nufin a ƙidaya mazaje ta wurin rubuta sunayensu. AT: "Ƙiɗaya su, ta wurin rubuta sunan kowane na miji"
"shekaru 20"
Wannan na nufin kassafa mazajen ga kungiyan su na sojoji.
...
"taimake ku"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Yahweh ya cigaba da lisafta sunayen shugabannen kabilun ga Musa.
Yahweh ya cigaba da lisafta sunayen shugabannen kabilun ga Musa.
Yahweh ya cigaba da lisafta sunayen shugabannen kabilun ga Musa.
AT: "Mutanen da Yahweh ya zaɓa"
"tara waɗannan mutanen a wurin ɗaya"
AT: "wanɗanda aka rubuta sunayen
Wannan wata ta biyu ne a kalandar Yahudawa. Rana ta fari na tsakiyar watan huɗu a kalandar mutanen da ke zama a yammacin duniya. Duba yadda ku ka juya wannan cikin 1:1.
Jimla na biyu, a takaice, na nufin abu ɗaya ne kamar yadda an ƙara na farkon don samin bayani a fili.
Anan "sunan" na nufin "faɗa". AT:
AT: "sun kirga dukka sunayen"
"wanda zai iya zuwa yaƙi"
"mazaje dubu arbain da shida da dari biyar"
Wannan dogon maganan an maimaita ta a kirgen da aka yi na mutanen. Duba yadda ka juya ta cikin 1:20. AT: "sun kirga sunayen kowane na miji ... kabilai da iyalai"
Wannan dogon maganan an maimaita ta a kirgen da aka yi na mutanen. Dubi yadda ka juya ta cikin 1:20. AT: "sun kirga sunayen kowane na miji ... kabilai da iyalai"
Wannan dogon maganan an maimaita ta a kirgen da aka yi na mutanen. Dubi yadda ka juya ta cikin 1:20. AT: "sun kirga sunayen kowane na miji ... kabilai da iyalai"
Wannan dogon maganan an maimaita ta a kirgen da aka yi na mutanen. Dubi yadda ka juya ta cikin 1:20. AT: "sun kirga sunayen kowane na miji ... kabilai da iyalai"
Wannan dogon maganan an maimaita ta a kirgen da aka yi na mutanen. Dubi yadda ka juya ta cikin 1:20. AT: "sun kirga sunayen kowane na miji ... kabilai da iyalai"
Wannan dogon maganan an maimaita ta a kirgen da aka yi na mutanen. Dubi yadda ka juya ta cikin 1:20. AT: "sun kirga sunayen kowane na miji ... kabilai da iyalai"
Wannan dogon maganan an maimaita ta a kirgen da aka yi na mutanen. Dubi yadda ka juya ta cikin 1:20. AT: "sun kirga sunayen kowane na miji ... kabilai da iyalai"
Wannan dogon maganan an maimaita ta a kirgen da aka yi na mutanen. Dubi yadda ka juya ta cikin 1:20. AT: "sun kirga sunayen kowane na miji ... kabilai da iyalai"
Wannan dogon maganan an maimaita ta a kirgen da aka yi na mutanen. Duba yadda ka juya ta cikin 1:20. AT: "sun kirga sunayen kowane na miji ... kabilai da iyalai"
Wannan dogon maganan an maimaita ta a kirgen da aka yi na mutanen. Duba yadda ka juya ta cikin 1:20. AT: "sun kirga sunayen kowane na miji ... kabilai da iyalai"
Wannan dogon maganan an maimaita ta a kirgen da aka yi na mutanen. Dubi yadda ka juya ta cikin 1:20. AT: "sun kirga sunayen kowane na miji ... kabilai da iyalai"
Wannan dogon maganan an maimaita ta a kirgen da aka yi na mutanen. Duba yadda ka juya ta cikin 1:20. AT: "sun kirga sunayen kowane na miji na Isra'ila ... cikin kiwane iyalansu"
AT: "Musa da Haruna ba su kirga mazajen wanda ke daga zuriyar Lawi ba"
Inda lallai ana bukatan, ana iya rubuta wannan a wata hanya dabam. AT: "wanda suke da zuriyar Lawi"
Anan "kabilan Lawi" na nufin dukkan mazajen da cikin kabilan Lawi. AT: "lallai ba za a kirga mazajen kabilan Lawi ba"
An kira alfarwar da wannan doguwan sunan saboda an sa sanduki da kuma shari'ar Allah a cikin ta.
Anan "ta" na nufin alfarwar.
Aikin su ne su ɗauki alfarwar a sa'adda suke tafiya. AT: "Sa'adda ku ke tafiya, Lallai ne Lawiyawan su ɗauki alfarwar"
Wannan na nufin cewa ya kamata su shirya tantin su kewaye da alfarwar. AT: "shirya tantin su kewaye da ita"
AT: "Sa'adda lokacin ya yi don shirya alfarwar"
AT: "Wani bako ... lallai ne ya mutu" ko "Lallai ne ku kashe kowane bako wanda ya zo kusa da alfarwar"
...
"ƙungiyansan na sojoji"
An kira alfarwar da wannan doguwan sunan saboda an sa sanduki da kuma shari'ar Allah a cikin ta. Dubi yadda ka juya wann cikin 1:50.
Anan Yahweh na magana game da rashin hukuncin Isra'ilawa kamar fushinsa zai sauko a kan su. Maganan nan "sauko kan" na nufin fushinsa a kan su. AT: "don kada in hukunta mutanen Isra'ila cikin fushi na"
Yahweh ya umurce Musa game da kowane abin da ya kamata Isra'ilawa su yi, Musa kuwa ya umurce Isra'ilawan.
1Yahweh ya sake magana da Musa da Haruna. Ya ce,2"Kowanne Ba'isra'ile dole ya yi sansani wajen matsayinsa, tare da tutocin gidan ubanninsa. Za su yi sansani kewaye da rumfar taruwa ta kowanne gefe.3Waɗanda za su yi sansani gabas da rumfar taruwa, inda rana ke fitowa, su ne sansanin Yahuda kuma suna sansani a ƙarƙashin matsayinsu. Nashon ɗan Amminadab shi ne shugaban mutanen Yahuda.4Lissafin mutanen Yahuda 74,600 ne.5Kabilar Issaka tilas su yi sansani a gaba da Yahuda. Netanel ɗan Zuyar tilas ya shugabanci mayaƙan Issaka.6Lissafin bataliyar mutane 54,400 ne.7Kabilar Zebulun tilas su yi sansani a gaba da Issaka. Eliyab ɗan Helon tilas ya shugabanci mayaƙan Zebulun.8Lissafin bataliyarsa 57,400 ne.9Dukkan lissafin sansanin Yahuda 186,400 ne. Sune za su fãra tafiya.10Gefen kudu zai zama sansanin Ruben a wajen matsayinsu. Shugaban sansanin Ruben shi ne Elizur ɗan Shedewur.11Lissafin dake bataliyarsa 46,500 ne.12Simiyon zai yi sansani a gaba da Ruben. Shugaban mutanen Simiyon shi ne Shelumiyel ɗan Zurishaddai.13Lissafin bataliyarsa shi ne 59.300.14Kabilar Gad su ne gaba. Shugaban mutanen Gad shi ne Eliyasaf ɗan Deuyel.15Lissafin bataliyarsa shi ne 45,650.16Lissafin dukkan mutanen da aka bayar ga sansanin Ruben, bisa ga bataliyarsu, shi ne 151,450.17Na gaba, rumfar sansanin tilas ta fita daga sansanin tare da Lebiyawa a tsakiyar dukkan sansanan. Tilas su fita daga sansanin bisa ga tsarin yadda suka shiga sansanin. Kowanne mutum tilas ya tsaya a wurinsa, gefen tutarsa.18Rabe-raben zangon sansanin Ifraim a ƙarƙashin matsayinsu. Shugaban mutanen Ifraim shi ne Elishama ɗan Ammihud.19Lissafin bataliyarsa shi ne 40,500.20Gaba dasu su ne Kabilar Manasse. Shugaban Manasse shi ne Gamaliyel ɗan Fedazur.21Lissafin bataliyarsa shi ne 32,200.22Gaba da su zai kasance kabilar Benyamin. Shugaban Benyamin shi ne Abidan ɗan Gidiyoni.23Lissafin dake bataliyarsa 35,400 ne.24Dukkan waɗanda aka lissafa a sansanin Ifraim 108,100 ne. Su ne na ukun fita.25Daga arewa zai kasance bataliyoyin sansanin Dan. Shugaban mutanen Dan shi ne Ahiyeza ɗan Ammishaddai.26Lissafin dake bataliyarsa 62,700 ne.27Mutanen kabilar Asha suka yi sansani gaba da Dan. Shugaban Asha shi ne Fagiyel ɗan Okran.28Lissafin bataliyarsa 41,500 ne.29Kabilar Naftali su ne gaba. Shugaban Naftali shi ne Ahira ɗan Enan.30Lissafin dake bataliyarsa 53,400 ne.31Dukkan waɗanda aka lissafa a sansanin tare da Dan 157,600 ne. Sune na ƙarshen fita daga sansanin, a ƙarƙashin tutarsu."32Waɗannan ne Isra'ilawa, an lissafa su bisa ga iyalansu. Dukkan waɗanda aka ƙidaya a sansanansu, bisa ga bataliyoyinsu, 603,550 ne.33Amma Musa da Haruna ba su ƙidaya Lebiyawa ba a cikin mutanen Isra'ila. Wannan bisa ga yadda Yahweh ya umarci Musa ne.34Mutanen Isra'ila suka yi kowanne abu da Yahweh ya umarci Musa. Suka yi sansani bisa ga tutocinsu. Suka fita daga sansanin bisa ga dangoginsu, bisa ga tsarin iyalan kakanninsu.
"tuta" kugiyoyi huɗu ne da aka kassa kabilun. An umurci kowane tuta su taru wuri ɗaya. Wannan na wakilcin tuta.
Kowane iyali kuma su na da tuta tare da zangon wanda ke daidai wurin da aka ba su.
...
"tuta" kugiyoyi huɗu ne da aka kassa kabilun. An umurci kowane su taru wuri ɗaya. Wannan na wakilcin tuta. Dubi yadda ka juya "tuta" cikin 2:1.
Ka juya wannan suna na maza daidai kamar yadda ka juya shi a 1:7.
"Dubu saba'in da huɗu da ɗari shida"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa cewa kowane kabila da sojojin ta za su kafa zango kewaye da alfarwa ta sujada.
Juya wannan sunan maza daidai yadda ka yi cikin 1:7.
Wannan kalma ce ta babbar kungiyar sojoji. Kowane kabila ta "rarrabu" a kanta.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa cewa kowane kabila da sojojin ta za su kafa zango kewaye da alfarwa ta sujada.
Juya wannan sunan mazan daidai yadda ka juya shi cikin 1:7.
AT: "mazaje 57,400"
Wannan ta kunshi dukkan mazaje da ke kabilun da suka kafa zangon ƙarƙashin Yahuza. AT: "Lamban mazaje ƙarƙashin Yahuza ita ce 186,400"
Wannan na nufin cewa za su fita da farko a sa'adda Isra'ilawa suna tafiya. AT: "Za su fara tafiya da farko, a sa'adda suna tafiya"
Yahwey ya cigaba da gaya wa Musa inda kowane kabila da sojojin ta za su kafa zangonsu kewaye da alfarwa ta sujada
"tuta" kugiyoyi huɗu ne da aka kassa kabilun. An umurci kowanensu su taru wuri ɗaya. Wannan na wakilcin tuta. Dubi yadda ka juya "tuta" cikin 2:1.
Ka juya wannan suna daidai yadda ka juya a 1:4.
AT: "mazaje 46,500"
Yahwey ya cigaba da gaya wa Musa inda kowane kabila da sojojin ta za su kafa zangonsu kewaye da alfarwa ta sujada
Juya wannan daidai yadda ka juya shi a cikin 1:4.
AT: "mazaje 59,300"
Yahwey ya cigaba da gaya wa Musa inda kowane kabila da sojojin ta za su kafa zangonsu kewaye da alfarwa ta sujada
Juya wannan sunan mazan daidai yadda ka yi cikin 1:12.
AT: "mazaje 45,650
Wannan na haɗe da dukkan mazajen da ke kabilun da ke ƙarƙashin jagorancin Ra'ubainu. AT: "Jimilla dukkan mazajen da sun kafa zango ƙarƙashin jagorancin Ra'ubainu, bisa ga kassafin su, su 151,450"
Wannan na nufin cewa lallai ne Lawiyawa su ɗauki alfarwa ta sujada a tsakanin kabilun a sa'adda suke tafiya.
"Su" na nufin kabilu goma sha biyu.
Ba wai kowane mutum na da tutarsa ba; maimaƙo haka, wannan na nufin tutar kabilarsa. AT: "ta wurin tutar kabilansa"
Yahwey ya cigaba da gaya wa Musa inda kowane kabila da sojojin ta za su kafa zangonsu kewaye da alfarwa ta sujada
"tuta" manyan kungiyoyi huɗu ne da aka kassa kabilun. An umurci kowanensu su kafa zangon su tare. Alamar itace tutar da aka kafa. Dubi Yadda ka juya wannan kalma "tuta" cikin 2:1.
AT: "mazaje 40,500"
Yahwey ya cigaba da gaya wa Musa inda kowane kabila da sojojin ta za su kafa zangonsu kewaye da alfarwa ta sujada
Wannan na nufin cewa kabilan Manassa za fita bayan kabilan Ifraimu.
AT: "mazaje 32,200"
Yahwey ya cigaba da gaya wa Musa inda kowane kabila da sojojin ta za su kafa zangonsu kewaye da alfarwa ta sujada
Ka Juya wannan sunan na miji daida kamar yadda ka juya shi cikin 1:10.
AT: "mazaje 35,400"
Yahwey ya cigaba da gaya wa Musa inda kowane kabila da sojojin ta za su kafa zangonsu kewaye da alfarwa ta sujada
Wannan haɗe ne da dukkan mazajen da ke cikin kabilun da zun kafa zango ƙarƙashin tutar Ifraimu. AT: "Yawan mutanen da ke ƙarƙashin tutar Ifraimu su 108,100"
Yahwey ya cigaba da gaya wa Musa inda kowane kabila da sojojin ta za su kafa zangonsu kewaye da alfarwa ta sujada
Wannan na nufin kashi kashi kabilun Dan, Ashiru da Naftali da ke ƙarƙashin tutar Dan. AT: "kashi kashi zangon da ke ƙarƙashin tutuar Dan"
Ka juya wannan sunan na mijin daidai kamar yadda ka juya shi a cikin 1:12.
AT: "mazaje 62,700"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa inda kowane kabila da sojojin ta za su kafa zangonsu kewaye da alfarwa ta sujada
Ka juya wannan suna na miji daidai yadda ka yi a cikin 1:12.
AT: "mazaje 41,500"
Yahwey ya cigaba da gaya wa Musa inda kowane kabila da sojojin ta za su kafa zangonsu kewaye da alfarwa ta sujada
Ka juya wannan suna na miji daidai yadda ka yi cikin 1:12.
AT: "Mazaje 53,400"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa wurararen da kowane kabila da sojojin ta za su kafa zangon kewaye da alfarwar sujada.
Wannan haɗe ne da dukka mazajen da ke kabilun da sun kafa zangon ƙarƙashin tutar Dan. AT: "Mutanen da aka kiɗaya a ƙarkashin zangon Dan su 157,600"
AT: "Musa da Haruna sun kirga su dukka"
Anan "su" na nufin mutanen Isra'ila.
Wannan na nufin lokacin da suna tafiya zuwa wani wuri kuma. AT: "Lokacin da suna tafiya, sun fita daga zangon"
1Yanzu wannan ne tarihin zuriyar Haruna da Musa sa'ad da Yahweh ya yi magana da Musa a Tsaunin Sinai.2Sunayen 'ya'yan Haruna maza su ne Nadab haihuwar farko, da Abihu, Eliyeza, da Itama.3Waɗannan ne sunayen 'ya'yan Haruna maza, firistoci waɗanda aka shafe aka kuma naɗa su yi hidima a matsayin firistoci.4Amma Nadab da Abihu sun fãɗi sun mutu a gaban Yahweh sa'ad da suka miƙa masa wuta marar karɓuwa a cikin jejin Sinai. Nadab da Abihu ba su da 'ya'ya, sai Eliyeza da Itama ne kawai suka yi hidima a matsayin firistoci tare da Haruna mahaifinsu.5Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,6"Ka kawo kabilar Lebiyawa ka gabatar da su ga Haruna firist domin su taimake shi.7Tilas su aiwatar da ayyuka a madadin Haruna da dukkan jama'a a gaban rumfar taruwa. Tilas su yi hidima a rumfar sujada.8Tilas su lura da dukkan kayan ado na cikin rumfar taruwa, kuma tilas su taimaki kabilun Isra'ila su aiwatar da hidimar rumfar sujada.9Tilas ka bayar da Lebiyawa ga Haruna da 'ya'yansa maza. An bayar da su ɗungun su taimaka masa ya yi hidima ga mutanen Isra'ila.10Tilas ka naɗa Haruna da 'ya'yansa maza a matsayin firistoci, amma duk wani bãre da yazo kusa tilas a kashe shi."11Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,12"Duba, na ɗauki Lebiyawa daga tsakanin mutanen Isra'ila. Na yi haka ne a maimakon ɗaukar kowanne haihuwar fãri namiji wanda aka haifa a cikin mutanen Isra'ila. Lebiyawa nawa ne.13Dukkan haihuwar fãri nawa ne. A ranar dana kai hari ga dukkan haihuwar fãri na ƙasar Masar, na keɓewa kaina dukkan haihuwar fãri cikin Isra'ila, mutane duk da dabbobi. Nawa ne su. Ni ne Yahweh."14Yahweh ya yi magana da Musa a jejin Sinai. Ya ce,15"Ka ƙidaya zuriyar Lebi a kowanne iyali, cikin dangoginsu. Ka ƙidaya kowanne namiji daga wata ɗaya zuwa sama.16"Musa ya ƙidaya su, yana bin maganar Yahweh, kamar yadda dai aka umarce shi ya yi.17Sunayen 'ya'yan Lebi maza su ne Gashon, Kohat, da Merari.18Dangin da suka fito daga 'ya'yan Gashon maza su ne Libni da Shimai.19Dangin da suka fito daga 'ya'yan Kohat maza su ne Amram, Izhar, Hebron, da Uzziyel.20Dangin da suka fito daga 'ya'yan Merari maza su ne Mahli da Mushi. Waɗannan ne dangogin Lebiyawa, aka rubuta dangi zuwa dangi.21Dangin Libniyawa da Shimaiyawa sun fito daga Gashon. Waɗannan ne dangogin Gashonawa.22Dukkan mazaje daga wata ɗaya zuwa sama an ƙidaya su, jimilla 7,500.23Kabiluin Gashonawa tilas su yi sansani gefen yamma da rumfar sujada.24Eliyasaf ɗan Layel tilas ya shugabanci kabilun zuriyar Gashonawa.25Iyalin Gashon tilas su lura da rumfar taruwa duk da rumfar sujada. Tilas su lura da rumfar, da abin rufewar ta, da labulen da ake amfani da shi a shiga rumfar taruwar.26Tilas su lura da masagalen labulen harabar, labulen dake ƙofar harabar - harabar dake kewaye da tsattsarkan wuri da bagadi. Tilas su lura da igiyoyin rumfar taruwa kuma domin kowanne abu dake cikinta.27Waɗannan kabilun sun zo daga Kohat: kabilar Amramiyawa, dangin Izrahiyawa, kabilar Hebroniyawa, da kabilar Uzziyeliyawa. Waɗannan kabilar Kohatawa ne.28Mazaje 8,600 an ƙidaya su shekaru daga wata ɗaya zuwa sama su lura da abubuwan dake na Yahweh.29Dangogin Kohat tilas su yi sansani a gefen kudu da rumfar sujada.30Elizafan ɗan Uzziyel tilas ya shugabanci dangogin Kohatawa.31Tilas su lura da akwatin, da teburin, da abin ajiyar fitila, da bagadai, da abubuwa masu tsarki da ake amfani da su wajen hidimarsu, labule, da dukkan aiki dake kewaye da shi.32Eliyeza ɗan Haruna firist tilas ya shugabanci mutanen dake shugabantar Lebiyawa. Tilas ya kula da mutanen dake lura da wuri mai tsarki.33Dangogi biyu suka zo daga Merari: Dangin Mahliyawa da dangin Mushiyawa. Waɗannan dangogi sun zo daga Merari.34Mazaje 6,200 aka ƙidaya shekara daga wata ɗaya zuwa sama.35Zuriyel ɗan Abihayil tilas ya shugabanci dangogin Merari. Tilas su yi sansani a gefen arewa da rumfar sujada.36Zuriyar Merari tilas su lura da katakan rumfar sujada, da sandunan gittawa, dana dirkoki, dana kafa harsashe, dukkan kaya masu ƙarfi, da duk wani abu da yake tattare dasu, duk da37ginshiƙai da dirkokin harabar dake kewaye da rumfar sujada, tare da kwasfofinsu, turkuna, da igiyoyin.38Musa da Haruna da 'ya'yansu maza tilas su yi sansani a gefen gabas na rumfar sujada, a gaban rumfar taruwa, zuwa tasowar rana. Sune ke da nauyi domin cika ayyukan tsattsarkan wuri da ayyukan mutanen Isra'ila. Duk wani bãre da ya gabato tsattsarkan wuri tilas a kashe shi.39Musa da Haruna suka ƙidaya dukkan mazajen dake cikin dangogin Lebi masu shekaru daga wata ɗaya zuwa sama, kamar dai yadda Yahweh ya umarta. Suka ƙidaya maza dubu ashirin da biyu.40Yahweh ya cewa Musa, "Ka ƙidaya dukkan mazaje haihuwar fãri na mutanen Isra'ila masu shekaru daga wata ɗaya zuwa sama. Ka lissafa sunayensu.41Tilas ka ɗauki Lebiyawa domina - Ni ne Yahweh - maimakon dukkan haihuwar fãri na mutanen Isra'ila, da dabbobin Lebiyawa maimakon haihuwar fãri na dabbobin zuriyar Isra'ila."42Musa ya ƙidaya dukkan haihuwar fãri na mutanen Isra'ila yadda Yahweh ya umarce shi ya yi.43Ya ƙidaya sunan dukkan mazaje haihuwar fãri, shekara daga wata ɗaya zuwa sama. Ya ƙidaya maza 22,273.44Yahweh, ya sake magana da Musa. Ya ce,45"Ka ɗauki Lebiyawa a maimakon dukkan haihuwar fãri daga cikin mutanen Isra'ila, ka kuma ɗauki dabbobin Lebiyawa a maimakon dabbobin mutanen. Lebiyawa nawa ne - Ni ne Yahweh.46Tilas ne ka karɓi shekel biyar domin fansar kowanne ɗaya daga cikin 273 haihuwar fãri na mutanen Isra'ila da suka zarce lissafin Lebiyawa.47Tilas ka yi amfani da shekel na tsattsarkan wuri a matsayin adadin awo. Shekel na dai-dai da awo ashirin na gera.48Tilas ku bayar da kuɗin fansa da kuka biya ga Haruna da 'ya'yansa maza."49Sai Musa ya karɓi biyan fansar daga wurin waɗanda suka zarce lissafin waɗanda Lebiyawa suka fansa.50Musa ya karɓi kuɗin daga haihuwar fari na mutanen Isra'ila ya karɓi shekel 1,365 an auna da shekel na tsattsarkan wuri. Musa ya bayar da kuɗin fansa ga Haruna da 'ya'yansa maza.51Musa ya yi kowanne abu da aka ce masa yayi ta maganar Yahweh kamar yadda Yahweh ya umarce shi.
Anan marubucin ya yi amfani da kalman nan "yanzu" don ya fara faɗi wani sabon tarihi.
"Nadab, wanda shine ɗan fari"
Waɗannan sunayen maza ne.
AT: "firistocin da Musa ya zuba wa mai ya kuma naɗa"
Juya waɗannan sunayen mazan daidai kamar yadda ya yi a cikin 3:1.
Wannan na nufin a gaban Yahweh. Abin nufi kuwa ita ce Yahweh ya ga dukkan abin da ya faru. AT: "a gaban Yahweh"
Anan an yi amfani da kalman nan "wuta" da nufin "ƙona turare." AT: "sun ƙona turare a hanyar da Yahweh bai amince da shi ba"
Anan, kalman nan "kabila" na nufin mazajen da ke kabilan. AT: "Kawo mazajen da ke kabilan Lewi"
"don." Wannan na nufin a yi wani abu ma wani kamar a wakilci su.
Anan "kabilun Isra'ila" na nufin mutanen Isra'ila. AT: "taimaki mutanen Isra'ila"
AT: "lalle ne su taimakin kabilun Isra'ila ta wurin yin hidima a cikin alfarwan"
"aikin alfarwan"
"ka" na nufin Musa.
AT: "Na mika su gabakiɗaya"
AT: "lalle ne ka kashe kowane bako da ya zo kusa" ko "lalle ne kowane bakon da ya zo kusa ya mutu"
Anan iya bayana ma'anan wannan magana a fili. AT: "amma kowane bako da ya do kusa da alfarwar"
"kassa kunne" ko "kassa kunne ga abin da zan faɗa maka"
"Na zaɓi Lawiyawa"
Yahweh yana umurtan Musa ya kiɗaya zuriya, maza kaɗai. AT: "Kiɗaya maza na zuriyan"
Anan "gidajen kakanin" su na nufin "iyalin kakanin" su. Wannan na nufin "kabilun" su. AT: "bisa ga kabilun su"
Waɗannan maganganu a takaice na nufin abu ɗaya ne, kuma an yi amfani da su tare don a nanata cewa ya yi biyayya ga Yahweh.
Wannan sune zuriyar Lewi.
Anan marubucin ya yi magana game da "zuriya" sai ka ce yana "zuwa." AT: "Kabilan da ke daga zuriyar"
Anan marubucin ya yi magana game da "zuriya" sai ka ce yana "zuwa." AT: "zuriya daga Gashon"
"Libnawa" da "Shimaiyawa" sunayen kabilun wanda aka ba su suna bisa ga kan iyalinsu. "Gashonawa" suna ne na mutane daga zuriyar Gashon.
AT: "Musa ya kiɗaya dukkan maza daga mai wata ɗaya har mafi shekaru"
"dubu bakwai da ɗari biyar"
Waɗannan sunaye mazaje ne.
...
"wato, farfajiyan da ke kewaye da alfarwan da bagaden"
Wannan su ne kabilu daga zuriyar Kohat.
Juya wannan sunan namijin daidai kamar yadda ka juya shi cikin 3:17.
AT: "Musa ya kiɗaya mazaje 8,600"
"daga mai wata ɗaya da mafi sufa"
Waɗannan ayoyin na bayani game da kabilu daga zuriyar Kohat.
AT: "abubuwa masu tsarki da firistoci na amfani da shi cikin hidima"
Wannan su ne kabilu daga zuriyar Merari.
AT: "Musa ya kiɗaya mazaje 6,200"
Wannan katake ne da aka harhada na kofa.
Waɗannan sune ke riƙe gini.
dirkoki wani katako da ke riƙe gini.
kwasfan shike riƙe dirkokin.
Wannan na nufin duk abubuwan da aka yi amfani da shi don a haɗa sanduna, da dirkoki da kuma kwasfan, tare.
Anan "su" na nufin "ginshiki da dirkoki."
Waɗannan sune dukka abubuwan da aka yi amfani da su don a tsare ginshikin da dirkokin a wuri ɗaya.
Anan "sa" na nufin Haruna
Wannan shine gabancin alfarwar. AT: a gabasa, inda rana ke fitowa"
AT: "domin su yi aikin da ya kamata su yi"
AT: "Lalle ne ka kashe kowani bako da ya zo kusa da alfarwar" ko "duk wani bako da ya zo kusa da alfarwar zai mutu"
mazaje dubu ashirin da biyu- "mazaje 22,000"
AT: "lalle ne ka karɓa dukkan dabbobin Lawiyawan"
"dukkan ɗa na fari"
AT: "fanshe"
"'yan fari maza na Isra'ila"
Shekel wata ma'auni ne na nauyi da ke kusa giram 11. AT: "kusan giram 55 na azurfa"
Wannan na nufin cewa jimilar 'ya'yan fari maza 273 da ke cikin kabilun Isra'ila ya fi yawan Lewiyawa maza.
Wannan na nufin cewa nauyin shekel din ya zama daidai da waɗanda ke alfarwar. AT: "Lallai ne ka yi amfani da nauyin shekel na alfarawar a matsayin ma'aunin"
"geraf ashirin." geraf guda, ma'auni ne na nauyi da ke kusan kilogram 57.
Anan, kalman nan "kuɗin" na nufin shekel da Musa ya karɓa. AT: "kuɗin da ka karɓa don fansarsu"
1Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna. Ya ce,2"Ka yi ƙidayar mazaje zuriyar Kohat daga cikin Lebiyawa, bisa ga dangoginsu da iyalansu.3Ka ƙidaya dukkan mazan dake shekaru talatin zuwa hamsin. Waɗannan mutane tilas su shiga ayarin hidima a cikin rumfar taruwa.4Zuriyar Kohat tilas su lura da abubuwa mafi tsarki da aka keɓe domina a cikin rumfar taruwa.5Sa'ad da sansanin ya shirya matsawa gaba, Haruna da 'ya'yansa maza tilas su shiga cikin rumfar, su sauke labulen da ya raba tsakanin wuri mafi tsarki da wuri mai tsarki su kuma rufe akwatin alƙawari da shi.6Tilas su rufe akwatin da fãtun saniyar teku. Tilas su baza shuɗiyar sutura a kai. Tilas su sãƙa dirkokin don su ɗauke shi.7Za su baza shuɗiyar sutura bisa teburin gurasa da ke gabansa. A bisan sa tilas su sa kwanonin, da cokulan, da langunan, da kwalaben zubawa. Tilas koyaushe gurasa ta kasance a teburin.8Tilas su rufe ta da jar sutura kuma tare da fãtar saniyar teku. Tilas su sãƙa dirkoki na ɗaukar teburin.9Tilas su ɗauki shuɗiyar sutura su rufe mazaunin fitilar, tare da fitilun, da mamurɗan, da tururrukan, da dukkan kwalaben mai domin fitilun.10Tilas su sanya mazaunin fitilar tare da kayayyakinsa a cikin abin rufewar da aka yi da fãtar saniyar teku, tilas su sanya shi cikin katakon ɗauka.11Tilas su baza sutura shuɗiya bisa bagadin zinariya. Tilas su rufe shi da abin rufewar da aka yi da fãtun saniyar teku, daga nan kuma a sãƙa dirkokin ɗauka.12Tilas su ɗauki dukkan kayayyakin aikin wuri mai tsarki a kuma rufe su da shuɗiyar sutura. Tilas su rufe shi da fãtun saniyar teku a sanya kuma kayayyakin cikin katakon ɗauka.13Tilas su ɗebe toka daga bagadi su kuma shimfiɗa sutura shunayya bisa bagadin.14Tilas su sanya dukkan kayayyaki da suka yi amfani da su wurin aikin bagadi bisa katakon ɗauka. Waɗannan kayayyaki su ne kaskunan wuta, cokula masu yatsu, cebura, kwanuka, da dukkan sauran kayayyaki domin bagadi. Tilas su rufe bagadin da fãtun saniyar teku Daga nan kuma su sãƙa dirkokin ɗauka.15Sa'ad da Haruna da 'ya'yansa maza suka kammala rufe wuri mai tsarki da dukkan kayayyakinsa, sa'ad da kuma sansani ya matsa gaba, Daga nan zuriyar Kohat tilas su zo su ɗauki wuri mai tsarki. Idan suka taɓa kayayyakin aikin masu tsarki, tilas su mutu. Wannan ne aikin zuriyar Kohat, su ɗauki kayayyakin ado na cikin rumfar taruwa.16Eliyeza ɗan Haruna firist zai shugabanci lura da mai domin haskakawa, turare mai daɗi, baikon hatsi da aka saba yi, da mai na shafewa. Zai shugabanci lura da rumfar sujadar gaba ɗaya da dukkan abin dake cikin ta, wuri mai tsarki da kayayyakinsa."17Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna. Ya ce,18"Kada ku bari a cire kabilar dangogin Kohatawa daga cikin Lebiyawa.19Ku kãre su, domin su rayu kada kuma su mutu, ta wurin yin haka. Sa'ad da suka kusanci abubuwa mafi tsarki20tilas ba za su je su duba wuri mai tsarki ba ko dana ɗan taƙi, ko kuwa tilas su mutu. Haruna da 'ya'yansa maza tilas su shiga ciki, Daga nan kuma Haruna da 'ya'yansa maza tilas su sanya kowanne daga cikin Kohatawa ga aikinsa, ga aikinsa na musamman."21Yahweh ya sake magana da Musa, ya ce,22"Ka yi ƙidayar zuriyar Gashon kuma, bisa ga iyalan kakanninsu bisa ga dangoginsu.23Ka ƙidaya waɗanda suke shekaru talatin zuwa shekaru hamsin. Ka ƙidaya dukkan waɗanda za su shiga ayarin su yi bauta a rumfar taruwa.24Wannan ne aikin kabilun Gashonawa sa'ad da suka yi bauta da abin da suka ɗauka.25Tilas su ɗauki labulan rumfar sujada, da rumfar taruwa da abin rufe ta, abin rufe ta na fãtar saniyar teku, da labulan hanyar shiga rumfar taruwa.26Tilas su ɗauki labulan harabar, labule domin hanyar ƙofa ta ƙofar harabar, wadda ke kusa da rumfar sujada kusa kuma da bagadi, igiyoyinsu, da dukkan kayayyakin aiki domin hidimarsu. Duk abin da ya kamata a yi da waɗanan abubuwa, tilas su yi shi.27Haruna da 'ya'yansa maza tilas su bida dukkan hidimar zuriyar Gashonawa, a cikin dukkan abin da suka ɗauko, a cikin kuma dukkan hidimarsu.28Tilas ka sanya su ga dukkan ayyukansu. Wannan ne hidimar dangogin zuriyar Gashonawa domin rumfar taruwa. Itama ɗan Haruna firist tilas ne ya bida su cikin hidimarsu.29Tilas ka ƙidaya zuriya Merari bisa ga dangoginsu, ka kuma shirya su bisa ga iyalan kakanninsu,30daga shekaru talatin zuwa sama har shekaru hamsin. Ka ƙidaya dukkan waɗanda za su shiga ayari su kuma yi bauta a rumfar taruwa.31Wannan ne hakkinsu da aikinsu a cikin dukkan hidima domin rumfar taruwa. Tilas su lura da katakan rumfar sujada, da sandunan gittawa, dirkoki, da mahaɗai,32tare da dirkokin filin harabar dake kewaye da rumfar sujada, mahaɗansu, turkuna, da igiyoyinsu, tare da dukkan kayayyakinsu. Ka lissafa bisa sunan kayayyakin da tilas su ɗauka.33Wannan ne aikin kabilun zuriyar Merari, abin da za su yi domin rumfar taruwa, ƙarƙashin bishewar Itama ɗan Haruna firist."34Musa da Haruna da shugabannin jama'a suka ƙidaya zuriyar Kohatawa bisa ga dangogin iyalan kakanninsu.35Suka ƙidaya su daga shekaru talatin zuwa sama har shekaru hamsin. Suka ƙidaya kowanne da zai shiga ayari ya yi bauta a rumfar taruwa.36Suka ƙidaya mazaje 2,750 bisa ga dangoginsu.37Musa da Haruna suka ƙidaya dukkan mazaje a cikin dangogi da iyalan Kohatawa waɗanda suke bauta a rumfar taruwa. A cikin yin haka, sun yi biyayya da abin da Yahweh ya umarce su suyi ta wurin Musa.38Aka ƙidaya zuriyar Gashon a cikin dangoginsu, ta wurin iyalan kakanninsu,39daga shekaru talatin zuwa shekaru hamsin, kowanne da zai shiga ayari ya yi bauta a rumfar taruwa.40Dukkan mazaje, da aka ƙidaya ta wurin dangogi da iyalan kakanninsu, lissafi 2,630 ne.41Musa da Haruna suka ƙidaya dangogin zuriyar Gashon waɗanda za su yi bauta a cikin rumfar taruwa. A cikin yin haka, sun yi biyayya da abin da Yahweh ya umarce su suyi ta wurin Musa.42Aka ƙidaya zuriyar Merari a cikin dangoginsu ta wurin iyalan kakanninsu,43daga shekaru talatin zuwa shekaru hamsin, kowanne da zai shiga ayari ya yi bauta a cikin rumfar taruwa.44Dukkan mazaje, da aka ƙidaya ta wurin dangoginsu da iyalan kakanninsu, lissafi 3,200 ne.45Musa da Haruna suka ƙidaya dukkan waɗannan mazaje, zuriyar Merari. A cikin yin haka, sun yi biyayya da abin da Yahweh ya umarce su suyi ta wurin Musa.46Sai Musa, Haruna, da shugabannin Isra'ila suka ƙidaya dukkan Lebiyawa ta wurin dangoginsu cikin iyalan kakanninsu47daga shekaru talatin zuwa shekaru hamsin. Suka ƙidaya kowanne da zai yi aiki a cikin rumfar sujada.48Suka ƙidaya mazaje 8,580.49Ta umarnin Yahweh, Musa ya ƙidaya kowanne mutum, yana ajiyar ƙidayar kowanne bisa ga irin aikin da aka ba shi ya yi. Ya ƙidaya kowanne mutum bisa ga irin hakkin da aka ɗora masa ya ɗauka. A cikin yin haka, sun yi biyayya da abin da Yahweh ya umarce su su yi ta wurin Musa.
Juya wannan sunan na mijin daidai yadda ka yi a 3:17.
"shekaru 30 zuwa 50"
Wannan na nufin sauran mutanen da ke aiki cikin alfarwa ta sujada.
AT: "waɗanda na zaɓa musamman don kaina"
Anan "zango" na nufin dukkan mutanen ca ke zangon. AT: "Sa'adda mutanen na shiri"
Wannan na nufin cewa mutanen za su tafi zuwa wani wuri. AT: "su tafi suwa wani wuri"
Kalman nan "shi" na nufin labulen da ya raba tsakanin wurin mafi tsarki daga wurin mai tsarki.
An zura sandunan cikin zoben da suke gefen akwatin alkawarin don a yi amfani da sandunan a dauka akwatin alkawarin. AT: "cusa sandunan a cikin zoben da ke gefe biyu na akwatin alkawarin"
Wannan gurasar na wakilcin kasancewar Yahweh. AT: "gurasar kasancewar Yahweh"
"Anan "shi" na nufin kayan mai launin shuɗi.
Anan iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "kwanoni da butoncin da ake amfani don zuba hadaya ta sha"
Anan "su" na nufin "kwanoni, cokala, tasa, da tuluna."
"Lallai ne a sami gurasa kullum a"
...
An zuraa sandunan cikin zoben da suke kusurwan taburin don a yi amfani da sandunan a ɗauka taburin. AT: "zura sanduna a cikin zoben da ke kusurwan taburin"
"Lallai ne su rufe ... da fatun shanu"
"lallai ne su sa dukkan waɗannan abubuwan da ke kan katakan don ɗaukan su" (UDB)
An zura sandunan cikin zoben da suke gefen bagadin don a yi amfani da sandunan a ɗauka shi. AT: "zura sandunan a cikin zoben da ke gefe biyu na bagadin"
katakan da aka sarafa don a yi amfani da su a ɗauka abubuwa
Kalman nan "aiki" ana iya bayana shi da kalman nan "hidima." AT: "amfani da shi sa'ad da ake hidima gaban Yahweh cikin wurin mai tsarki"
Kalman nan "aiki" ana iya bayana shi da kalman nan "hidima." AT: "sa'ad da ake hidima a gaban bagadin"
An zura sandunan cikin zoben da suke gefen bagadin don a yi amfani da sandunan a ɗauka shi. AT: "zura sandunan a cikin zoben da ke gefe biyu na bagadin"
Anan wuri mai tsarki na nufin dukkan abubuwan ya kunshi wuri mai tsarki da Haruna da 'ya'yansa maza sun rufe da zane da fatun. AT: "ɗauka dukkan abubuwan da ke wuri mai tsarki"
Anan kalman nan "zangon" na nufin dukkan mutanen da ke zangon. AT: "sa'ad da mutanen sun yi gaba"
Juya wannan sunan maza daidai yadda ka yi cikin 3:17.
...
Anan kalman nan "wuta" na nufin "fitilu." AT: "mai don fitilun"
Anan "lura" ana iya bayana shi kamar aikatau. AT: "waɗanda ke lura da"
Wannan na nufin zuriyar Kohat. Juya wannan daidai yadda ka yi cikin 3:27.
Wannan na nufin mutuwar Kohatawan. AT: "a aikata wani abu da zai sa ni in fid da su daga cikin Lawiyawa"
Wannan magana na nufin abin da Yahweh ya faɗa a nan gaba. Musa zai tsare Kohatawan ta wurin hana su zuwa don su ga wuri mai tsarki.
Waɗannan maganganu biyu a takaice na nufin abu ɗaya, an kuma haɗa su don a nanata ne.
Wannan na nufin maza ne kaɗai. AT: "maza daga zuriyar Gershon"
Juya wannan sunan mazan daidai kamar yadda ka yi cikin 3:17.
"shekaru 30 zuwa shekaru 50"
Kalman nan "kungiya" na nufin sauran mutanen da ke aikin cikin alfarwar ta sujada. Duba yadda ka juya wannan magana cikin 4:1.
Wannan jimla bayani ne da ke faɗin abubuwan game da ayoyi da ke gaba.
Wannan na nufin zuriyar Gershon. Juya wannan daidai yadda ka yi cikin 3:21.
Wannan shine abin rufewa da aka sanya a saman alfarwa ta sujada. AT: "abin rufewa da aka yi da fatan shanu an kuma sanya a saman" ko "abin rufewa da aka yi da fatan shanu an kuma rufe shi ta waje"
AT: "Kowane aikin da waɗannan abubuwa ke bukata"
"duba aikin wani"
Anan, kalman nan "aiki" suna ne da ake iya bayana shi cikin aikatau. Anan, kalman nan "Wannan" na nufin abin da Yahweh ya gama faɗa yanzu. AT: "Ga yadda iyalai daga zuriyar Gershonawa za su yi hidima cikin alfarwa ta sujada"
Juya wannan sunan mazan daidai kamar yadda ka yi cikin 3:1.
Wannan na nufin mazaje ne kaɗai. AT: "maza daga zuriyar Merari"
Juya wannan sunan mazaje daidai yadda ka yi cikin 3:17.
"lissafta su"
"shekaru 30 ... shekaru 50"
Kalman nan "kungiya" na nufin sauran mutanen da ke aiki cikin alfarwa ta sujada. Dubi yadda ka juya wannan magana cikin 4:1.
"Wannan" na nufin abin da Yahweh ya faɗa a gaba.
Anan "su" na nufin dirkokin farfajiyan.
Waɗannan duka gabobin alfarwan. Duba yadda ka juya duk waɗannan gabobin cikin 4:31.
"Lisafta sunan kowane na miji da kayan da lallai ne ya ɗauka"
Kalman nan "shugabanci" suna ne da za a iya bayana shi cikin aikatau. AT: "kamar yadda Itamar ɗan Haruna ya shugabanci su"
Juya wannan sunan na miji daidai kamar yadda ka yi cikin 3:1.
Wannan na nufin maza. AT: "maza daga zuriyar Kohatawa"
Wannan na nufin zuriyar Kohat. Juya wannan daidai kamar yadda ka yi ckin 3:27.
"shekaru 30 ... shekaru 50"
Anan, kalman "zai" ba ya nufin cewa mazajen sun "zaɓa" su haɗa kai da kungiyan maimakon haka an "tura" zuwa ga kungiyan. AT: "duk wanda aka tura ya haɗa kai da kungiyan"
Kalman nan "kungiya" na nufin sauran mutanen da ke aiki cikin alfarwa ta sujada. Duba yadda ka juya wannan magana cikin 4:1.
"dubu biyu da ɗari bakwai da hamsin"
Wannan na nufin mazajen. AT: "Mazajen daga zuriyar Gershon"
AT: "Musa da Haruna sun kiɗaya zuriyar Gershon"
"daga mai shekata 30 zuwa 50"
Anan kalman nan "zai" ba wai na nufin cewa mutanen su "zaɓa" su haɗa kai da kungiyan ba, amma maimakon haka an "danka" wa kungiyan. AT: "duk wanda an umurce su su hada kai da kungiyan"
Kalman nan "kungiya" na nufin sauran mutanen da ke aiki cikin alfarwar ta sujada. Dubi yadda ka juya wannan magan cikin 4: 1.
AT: "wand Musa da Haruna ya kiɗaya bisa ga kabilunsu"
"mazaje 2, 630"
Kalman nan "su" na nufin Musa da Haruna.
AT: "Musa da Haruna sun kiɗaya zuriyar Merari"
"daga mai shekara 30 zuwa 50"
Anan kalman nan "zai" ba wai na nufin cewa mutanen su "zaɓa" su haɗa kai da kungiyan ba, amma maimakon haka an "tura" zuwa kungiyan. AT: "duk wanda an tura su su haɗa kai da kungiyan"
Kalman nan "kungiya" na nufin sauran mutanen da ke aiki cikin alfarwar ta sujada. Dubi yadda ka juya wannan magan cikin 4: 1.
AT: "Wadda Musa da Haruna sun kiɗaya bisa ga iyalansu"
Kalman nan "su" na nufin Musa da Haruna.
Wannan na nufn mazaje. AT: "mazaje daga talatin zuwa hamsin"
"daga 30 zuwa 50"
"Kamar yadda Yahweh ya umurta"
Waɗannan maganganu biyun suna ma'ana kusan iri ɗaya, an yi amfani da su tare don nanata yadda Musa ya kiɗaya dukka mazajen.
AT: "bisa ga irin aiki da ak ba su" ko "bisa ga irin aikin da ya ba wa kowane na miji ya yi"
"zai samu"
Anan "su" na nufin Musa da Haruna.
1Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Ka umarci mutanen Isra'ila su kori kowanne mutum daga sansani wanda ke da cutar fãta da ake ɗauka, da kowanne dake da ƙurjin dake fitar da ruwa, da duk wanda ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa.3Ko namiji ko mace, tilas ka kore su daga sansanin. Tilas ne ba za su gurɓata sansanin ba, saboda ina zaune a cikin sa."4Mutanen Isra'ila suka yi haka. Suka kore su daga sansanin, kamar yadda Yahweh ya umarci Musa. Mutanen Isra'ila suka yi biyayya da Yahweh.5Yahweh ya sa ke magana da Musa. Ya ce,6"Ka yi magana da mutanen Isra'ila. Sa'ad da wani mutum ko wata mata suka aikata zunubi irin wanda mutane ke aikatawa ga junansu, kuma ya yi rashin aminci a gare ni, wannan mutum ya yi laifi.7Daga nan tilas ya furta zunubin da ya yi. Tilas ya biya farashin laifinsa gaba ɗaya ya kuma ƙara akan farashin kashi ɗaya cikin biyar. Tilas ya bayar da wannan ga wanda ya yiwa laifin.8Amma idan wanda aka yiwa laifin bai da ɗan'uwa na kusa da zai karɓi biyan, tilas ya biya farashin laifinsa gare ni ta wurin firist, tare da rago na yin kaffara domin sa.9Kowanne baiko na mutanen Isra'ila, abubuwan da aka keɓe aka kuma kawo ga firist ta wurin mutanen Isra'ila, zai zama nasa.10Baye-bayen kowanne taliki zai zama domin firist; idan wani ya bayar da wani abu ga firist, zai zama nasa."11Bugu da ƙari, Yahweh yayi magana da Musa. Ya ce,12"Kayi magana da mutanen Isra'ila. Ka ce da su, 'Ga misali idan matar wani ta kauce hanya ta kuma yi zunubi gãba da mijinta.13Misali a ce wani mutum ya kwana da ita. A wannan al'amari, ta ƙazantu. Ko da mijinta bai gani ba ko kuma ya san da hakan, kuma ko da ba wanda ya kama ta cikin aikata hakan kuma ba bu wanda zai bada shaida gãba da ita,14duk da haka. ruhun kishi zai sanarwa mijin cewa matarsa ta ƙazamtu. Ko da yake, ruhun kishi na ƙarya na iya sauko wa mutum alhali matarsa ba ta ƙazantu ba.15A cikin irin waɗannan al'amura, tilas mutumin ya kawo matarsa ga firist. Tilas mutumin ya zo da baikon da ake buƙata a madadin ta, kashi goma na awon garin bali. Tilas ne kuma ba zai zuba mai a kai ba ko kuma ya zuba turaren ƙonawa a kai ba, saboda baikon hatsi ne na kishi, baikon hatsi domin tunawa, a matsayin abin tunawa da laifin.16Tilas firist ya kawo ta kusa ya miƙa ta gaban Yahweh.17Tilas firist ya ɗauki gorar ruwa mai tsarki ya kuma ɗibi ƙurar ƙasan rumfar sujada. Tilas ya zuba ƙurar cikin ruwan.18Firist zai sa matar gaban Yahweh kuma zai kwance gashin dake kan matar. Zai sanya cikin hannuwanta baikon hatsi na tunawa, wanda shi ne baikon hatsi na zato. Firist zai riƙe a hannunsa ruwa mai ɗaci da zai iya kawo la'ana.19Firist zai sanya matar ƙarƙashin rantsuwa ya kuma ce mata, 'Idan babu mutumin da yayi saduwar jima'i dake, idan kuma baki fita iskanci ba kika kuma aikata rashin tsarki, to zaki 'yantu daga wannan ruwa na ɗaci da zai iya kawo la'ana.20Amma idan ke, mace ƙarƙashin mijinta, kin fita iskanci, idan kin ƙazantu, idan kuma wani mutum daban ya kwana da ke,21daga nan, (tilas firist ya sa matar ta ɗauki rantsuwar da za ta sauko mata da la'ana, daga nan kuma tilas ya ci gaba da magana da matar) 'Yahweh zai maida ke la'ana da za a nuna wa mutanenki ya kasance haka. Wannan zai kasance idan Yahweh ya sa cinyarki ta ruɓe kuma mararki ta kumbura.22Wannan ruwan da zai kawo la'ana zai shiga cikin cikinki ya sa mararki ta kumbura cinyoyinki kuma su ruɓe.' Matar kuma za ta maida amsa, 'I, bari haka ya kasance idan ina da laifi.'23Firist tilas ne ya rubuta waɗannan la'anoni cikin naɗaɗɗen littafi, Daga nan kuma tilas ya wanke rubutattun la'anonin cikin ruwa mai ɗaci.24Tilas firist ya sa matar ta sha ruwa mai ɗaci da zai kawo la'ana. Ruwan dake kawo la'ana zai shiga cikinta ya zama ɗaci.25Firist tilas ya ɗauke baikon hatsi na kishi daga hannun matar. Dole ya riƙe baikon hatsin a gaban Yahweh ya kuma kawo shi zuwa bagadi.26Firist tilas ya ɗibi tafin hannu na baikon hatsin a matsayin baikon madadi, ya kuma ƙonashi bisa bagadi. Daga nan tilas ya ba matar ruwa mai ɗaci ta sha.27Sa'ad da ya ba ta ruwan ta sha, idan ta ƙazantu saboda ta aikata zunubi gãba da mijinta, to ruwan dake kawo la'ana zai shiga cikinta, ya kuma zama ɗaci. Mararta za ta kumbura kuma cinyarta ta ruɓe. Matar za ta zama la'ananna a cikin mutanenta.28Amma idan matar ba ta ƙazantu ba kuma da tsabtarta, to tilas ta 'yantu. Za ta iya haihuwar 'ya'ya.29Wannan ce shari'ar kishi. Shari'a ce domin matar da ta fita iskanci daga wurin mijinta ta kuma ƙazantu.30Shari'a ce domin mutumin da ka tare da ruhun kishi sa'ad da yake kishin matarsa. Tilas ya kawo matar a gaban Yahweh, kuma firist tilas ya yi mata dukkan abin da shari'ar kishi ta tsara.31Mutumin zai 'yantu daga laifi domin kawo matarsa da ya yi a gaban firist. Tilas ne matar ta ɗauki nauyin kowanne laifi da take da shi."
Wannan na nufin kuturta wata cutar da ke kama fatan mutum kuma zai iya yaduwa zuwa sauran mutane a saukake.
Wannan na nufin ciwon da ke bude kuma na fid da ruwa.
Idan mutum ya taɓa gawa, ana dubansa a matsayin ƙazantacce. An yi maganar mutum da ba karɓaɓɓe bane ga shirin Allah sai ka ce mutumin da ke ƙazantacce ne a jiki.
Anan "ku" na nufin mutanen Isra'ila.
Wannan na nufin cewa sun tura ƙazantattun mutane nesa ga su. Anan iya bayyana ma'anar wannan magana a fili. AT: "Mutanen Isra'ila sun fid da ƙazantattu mutane daga cikin zangon"
"kowane zunubi da mutane ke yi wa juna"
In wani ya yi wa wani laifi, wannan na nufin cewa ya yi wa Yahweh ma laifi kuma Yahweh zai dubi wannan mutum a matasyin mai rashin adalci a gare shi. AT: "sun kuma yi mani laifi"
Anan, "zunubin" mutumin na nufin "laifi." AT: "abin da ake duba a matsayin daidai kuɗin laifin da ya yi"
humushi- Wannan na nufin lallain ne mutumin ya biya ƙarin farashin da ake binsa.
humushi- Wannan kashi ɗaya ne daga ciking kashi biyar.
An saba da cewa mutum mai laifin zai karɓi biyan amma idan mutumin ya mutu to dangin sa na kusa zai karɓa. Anan iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "Amma idan mutum mai lafin ya mutu kuma ba shi da dangi na kusa wanda zai karɓi abin da aka biya"
AT: "idan mutum wanda mai laifin ya yi masa laifi"
Idan mutum ya biya zuwa ga firist domin laifin sa, daidai ne kamar mutumin ya yi biya zuwa ga Yahweh.
Kafarar domin zunubin mutumin ne. Anan Yahweh na duban zunubin mutumin a matsayin mutumin "kansa." AT: "kafara domin zunubin sa"
AT: "abubuwan da mutanen Isra'ila sun keɓe sun kuma kawo shi zuwa ga firist
Waɗannan maganganu biyun a takaice na nufin abu ɗaya an kuma haɗa su don a bayana cewa sadakokin da wani ya bayar na firist ɗin da aka ba wa ne.
Wannan wani abu ne da zai iya faru. Yahweh na gaya wa Musa abin da zai yi in ya faru.
Wannan na nufin cewa ta bar shi da aikat rashin adalci zuwa gare shi. AT: "matar mutumin ta yi rashin adalci"
Wannan na nufin cewa ta zama da rashin adalcin ta kuwa yi masa zunubi ta wurin kwana da wani na miji. Anan iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "yi zunubi ga mai gidan ta ta wurin kwana da wani mutum"
"kuma wani mutum ya kwana da ita." Ana iya rubuta wannan jimlar a matsayin bangaren jilar da ke baya. Wannan na bayana yadda ta yi wa mai gidan ta zunubi. Wannan abu ne mai yiwuwa. Yahweh na gaya wa Musa abin da zai yi in hakan ya faru.
AT: "ta ƙazantar da kanta ... matarsa ta ƙazantar da kanta ... matarsa na ta ƙazantar da kanta
wannan na nufin zina.Anan iya bayana ma'anar wanna magana a fili. AT: "cikin aikin zina" ko "kwana da shi"
Anan kalman nan "ruhu" na nufin halin mutumin da kuma shauƙin sa. An yi maganar "ƙishi" sai ka ce mutum ne ya yi magana da shi. AT: "mai gidan mai yiwuwa ya yi ƙishi ya kuma sa mata ido"
Anan kalman nan "ruhu" na nufin halin mutumin da shauƙinsa. Zance ruhu ya "sauko bisan sa" na nufin cewa ya fara ƙishi. AT: "mutum zai iya jin ƙishi babu wata dalili"
Wannan bangari ɗaya ne da cikin kashi goma.
Ana iya rubuta wannan bisa ga yadda ake awu a wannan zamani. AT: "humushi na garin sha'ir
"hadaya ta gari domin kishi"
"abin nuna" wani abu ne da ke bada tabbaci abu. Ya yi wannan hadaya, a wannan yanayin, don ya duba ko mata tasa ta yi zina ko ba ta yi ba.
"Gaban Yahweh." Firist zai kaita kusa bagadin. AT: "kusa da bagadin, ya kuma tsai da ita a gaban Yahweh"
"a gaban Yahweh"
Ka juya wannan magana daidai yadda ka yi cikin 5:15.
Kalman nan "ɓaude" na nufin "rashin adalci." AT: "idan ba ki yi rashin adalci ga mijin ki ba"
"Ta wurin aikata abu mara tsarki." Wannan magana na nufin "yin zina."
Wannan magana "kuɓuta" daga wani abu na nufin cewa abin ba zai yi wa mutumin lahani ba. AT: "wannan ruwa mai ɗacin ba zai yi miki lahani ba, kodashike zai iya yi"
Anan, an bayana cewa ruwa mai ɗacin zai iya kaow la'ana. Wannan na nufin cewa a sa'ad da macen ta sha ruwan, zai sa ta ta kăsa haifan 'ya'ya in har tana da laifi. AT: "wannan ruwa mai ɗaci zai iya zama la'ana a gare ki"
Wannan magana na nufin tana ƙarƙashin ikon mijin ta. AT: "ƙarƙashin ikon mijin ta"
Kalman nan "ɓaude" na nufin "zama da rashin adalci." AT: "zama da rashin adalci ga mijin ki"
AT: "kin ƙazantar da kanki"
Maganan nan "sauko da la'ana" na nufin cewa la'ana zai sauko a kan ta. AT: "wannan zai iya sa la'ana ya sauko kan ta"
Anan, marubucin na magana game da ɗaukan la'anar da macen za ta yi wadda Yahweh ya ba ta, wanda kuma ya sa saura mutane sun la'anta ta. An yi maganar wannan sai ka macen kanta ta zama la'ana. AT: "Saboda Yahweh ya la'anta ki, sauran mutane za su la'anta ki, Yahweh kuma zai nuna wa mutane cewa lallai an la'anta ki"
AT: "zai nuna wa mutanen cewa lallai la'ana ne"
Ma'ana maiywuwa suna kamar haka 1) cewa mace ba za ta iya ta haifi 'ya'ya ba ko 2) cewa zama da juna biyu zai kai ga karshe, jaririn cikin ta kuwa zai mutu.
Anan kalman nan "cinya" hanya ce mai ladabi in ana maganar mahaifan mace ko gaban mace. AT: "mahaifar ki ba zai zama da amfani ba"
Wannan na nufin cewa ya kamata ya wanke tawada da ke littafin.
AT: "la'anonin da ya rubuta"
Yadda aka shirya abubuwan da suka faru cikin waɗannan ayoyi na iya rikitar da mutum. An rubuta shi a wannan hanya don a nanata yadda ruwan zai kawo la'ana. Mai yiwuwa macen ta sha ruwan, firist na kona hadayan, sai macen kuma ta sha ruwan kuma. Ta kan sha ruwan sau ɗaya kamar yadda yake a fili cikin juyin da aka yi na UDB.
Zai zama da taimako a sake shirya bayani da ke waɗannan ayoyin ta wurin sa aya ta 24, wanda ta yi bayani game da shan ruwan da macen ta yi, bayan aya 26. An juya waɗannan ayoyi a UDB makamancin haka.
Hadaya ta gari cike a tafin hannu na wakilcin dukkan hadaya ta gari. Wannan na nufin cewa dukka hadayan na Yahweh ne.
"hadaya ta gari na kishi." Duba yadda ka juya wannan cikin 5:15.
AT: "in ta ƙazantar da kanta ta wurin yin"
Anan, "zunubi" na nufin yin zina. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "yi zina"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) cewa mace ba za ta iya ta haifi 'ya'ya ba ko 2) cewa zama da juna biyu zai kai ga karshe, jaririn cikin ta kuwa zai mutu. Anan, kalman nan "cinya" hanya ce mai ladabi ta musamman a lokacin da ana nufin mahaifan mace ko kuwa gaban ta. . Dubi yadda ka juya waɗannan cikin 5:20.
AT: "Mutanen ta za su la'anta ta"
AT: "ba ta ƙazantar da ita ba"
Anan, an yi maganar "mara laifi" kamar "zama da tsarki"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) "sa'annan ba za a la'anta ta ba" ko 2) "sa'annan za ta kuɓuta daga zama mai laifi."
"sami juna biyu"
"dokar da ta yi magana kan kishi"
Kalman nan "ɓaude" na nufin "rashin adalci." AT: "wanda ta ke da rashin adalci ga mijin ta"
AT: "ta kuma ƙazantar da kanta"
Wannan magana na nufin halin mijin da kuma shauƙin sa na kishi. Dubi yadda ka juya wannan cikin 5:13. "da ke kishi"
Wannan karin magana ne da ke nufin cewa zargin da ya ke yi mata tasa cewa ba ta yi masa adalci don tana kwana da wasu maza. AT: "na kuma zaton cewa mata tasa ba ta yi masa adalci" ko "na kuma zaton cewa mata tasa ta kwana da wani na miji"
"a gaban Yahweh"
"ba zai zama da laifi yin wani abu da ba daidai ba ta wurin kawo mata tasa gaban firist"
"lallai ne ya jimre"
1Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Ka yi magana da mutanen Isra'ila. Ka ce masu, 'Idan namiji ko mace ya keɓe kansa ga Yahweh tare da alƙawari na musamman na zama Nazari,3ba zai taɓa shan ruwan inabi da abin sha mai ƙarfi ba. Ba zai taɓa shan abin sha mai tsami da aka yi daga ruwan inabi ba ko daga abin sha mai ƙarfi. Ba zai taɓa shan abin da aka matso daga inabi ba ko ya ci sabobbin 'ya'yan inabi ko busassun 'ya'yan inabi ba.4A cikin dukkan kwanakin keɓewarsa gare ni, ba zai ci wani abin da aka yi da inabi ba, tare da dukkan abin da aka yi daga tsabar inabin zuwa fãtunsa.5A cikin dukkan lokacin alƙawarinsa na keɓewa, ba za a yi amfani da aska ba a bisa kansa har sai kwanakin keɓewarsa ga Yahweh sun cika. Tilas a ware shi ga Yahweh. Tilas ya bar gashinsa ya yi tsawo a bisa kansa.6A cikin dukkan lokacin da ya keɓe kansa ga Yahweh, tilas ne ba zai zo kusa da gawa ba.7Tilas ne ba zai mai da kansa marar tsarki ba ko da domin mahaifinsa, mahaifiyarsa, ɗan'uwansa, da 'yar uwarsa ba, idan suka mutu. Wannan kuwa saboda an keɓe shi ga Allah, kamar yadda kowa zai gani ta wurin dogon gashinsa.8A cikin dukkan lokacin keɓewarsa mai tsarki ne shi, ajiyayye domin Yahweh.9Idan wani da gaske farat ɗaya ya mutu a gefensa, ya kuma ɓãta keɓaɓɓen kansa, Daga nan tilas ya aske kansa a ranar tsarkakewarsa - a rana ta bakwai tilas ya aske shi.10A rana ta takwas tilas ya kawo kurciyoyi biyu ko tantabaru 'yan shila biyu ga firist a ƙofar shiga rumfar taruwa.11Firist kuma tilas ya miƙa tsuntsuwa ɗaya a matsayin baikon zunubi, ɗaya kuma a matsayin baikon ƙonawa. Waɗannan za su yi masa kafara saboda ya yi zunubi ta wurin kasancewa kusa da gawa. Tilas ya sake keɓe kansa kuma a wannan rana.12Tilas ya kiyaye kansa ga Yahweh domin kwanakin keɓewarsa. Tilas ya kawo ɗan rago ɗan shekara ɗaya a matsayin baikon laifi. Kwanakin da ya yi kafin ya ƙazantar da kansa tilas ba za a lissafa su ba, domin keɓewarsa ta ƙazantu.13Wannan ce shari'a game da Nazari domin sa'ad da lokacin keɓewarsa ya cika. Tilas a kawo shi ƙofar shiga rumfar taruwa.14Tilas ya gabatar da baikonsa ga Yahweh. Tilas ya miƙa a matsayin baikon ƙonawa ɗan rago ɗan shekara ɗaya kuma marar aibi. Tilas ya miƙa a matsayin baikon zunubi 'yar tunkiya 'yar shekara ɗaya kuma marar aibi. Tilas ya kawo rago a matsayin baikon zumunta wanda yake marar aibi.15Tilas ya kawo kwandon gurasa da aka yi ba tare da gami ba, dunƙule-dunƙule na gari mai laushi da aka gauraya da mai, waina marar gami da aka shafe da mai, tare da baikon hatsinsu da baye-baye na sha.16Tilas ne firist ya gabatar da su a gaban Yahweh. Tilas ya miƙa baikon zunubinsa da baikon ƙonawa.17Tare da kwandon gurasa marar gami, tilas ya miƙa ragon a matsayin hadaya, baikon zumunta ga Yahweh. Firist kuma tilas ya gabatar da baikon hatsi da baikon abin sha.18Nazirin tilas ya aske kansa don a nuna cewa an keɓe shi ga Allah a ƙofar shiga rumfar taruwa. Tilas ya ɗauki gashin dake daga kansa ya kuma sanya a cikin wutar dake ƙarƙashin hadayar baye-bayen zumunta.19Tilas firist ya ɗauki dafaffiyar kafaɗar ragon, curin gurasa ɗaya marar gami daga cikin kwandon, da waina ɗaya marar gami. Tilas ya ɗora su cikin hannuwan Banazaren bayan ya aske kansa nuna keɓewa.20Tilas firist ya wurga su a matsayin baiko a gaban Yahweh, kaso mai tsarki domin firist, tare da ƙirgin da aka wurga da kuma cinyar da aka gabatar domin firist. Bayan haka, Banazaren zai iya shan ruwan inabi.21Wannan ce shari'a domin Nazari wanda ya yi alƙawarin baikonsa ga Yahweh domin keɓewarsa. Kowanne abu kuma da zai iya bayarwa, tilas ya kiyaye ka'idodin alƙawarin da ya ɗauka, ya kiyaye alƙawarin da aka nuna ta wurin shari'a domin Banazare."'22Yahweh ya sake magana da Musa. Ya ce,23"Ka yi magana da Haruna da 'ya'yansa maza. Cewa, 'Tilas ku albarkaci mutanen Isra'ila ta wannan hanya. Tilas ku ce masu,24"Bari Yahweh ya albarkace ku ya kuma kiyaye ku.25Bari Yahweh ya sa fuskarsa ta haskaka a bisanku ya kuma yi maku alheri.26Bari Yahweh ya kalle ku da tagomashi ya kuma ba ku salama."'27Ta wannan hanya ce tilas za su bayar da sunana ga mutanen Isra'ila. Daga nan zan albarkace su.
"ka keɓe kanka ga wani" na nufin "mika kanka" ga wannan mutum. AT: "mika kansa ... ya mika kansa"
Wannan na nufin cewa ba zai ci ko ya sha su ba. AT: "ba zai ci ba faufau"
AT: "ruwan tsami da mutane ke yi daga ruwan inabi"
ruwan sha da aka yi a sa'ad da ruwan inabi da wasu ruwan sun yi tsami don sun jima a ajiye
Ka na iya bayana abin da aka fahim ta anan a fili. AT: "ko ruwan tsami da mutane suka yi daga ruwa mai sa maye"
"busassun inabi"
AT: "ya raba kansa da ni"
AT: "wani abin da mutane suka yi daga inabi"
An ba da waɗannan matsananci biyu don a nana cewa ba zai kyautu a ci inabin ba. AT: "daga wani bangaren inabi"
Wannan karin magana ne. A nan "keɓe" na nufin "mika kai" AT: "wa'adin mika kai"
AT: "kada kowa ya haske masa kai"
Kalman nan "keɓe" ana iya bayana shi cikin aikatau. A nan "keɓewa" na nufin "mika kai." AT: "ranakun da ya keɓe kansa ga Yahweh" ko "ranakun da ya mika kansa ga Yahweh"
AT: "ga Yahweh sun cika"
AT: "Lallai ne ya keɓe kansa ga Yahweh"
A nan "keɓewa" na nufin "mika kai." AT: "mika kai ... mika kai ... mikawa"
An yi magana game da mutumin da ba karɓaɓɓe bane don nufin Allah kamar mutum da ya ƙazantu a jiki.
AT: "ya keɓeɓɓe kansa"
Kalman nan "keɓewa" ana iya bayana shi cikin aikatau. AT: "cewa ya keɓe kansa"
AT: "ya keɓe kansa don Yahweh" ko "keɓe don Yahweh"
A nan "kai" na wakilcin gashin mutumin Naziriyawa wanda ke nuna alamar wa'adin sa. AT: "ƙazantar da dogon gashin sa wanda ke nuna wa kowa cewa ya rabu da Allah" ko "ya ƙazantu"
AT: "a ranar da ya maishe kansa karaɓaɓɓe a gaban Allah"
"rana ta 7"
"rana ta 8"
"lokacin da za a keɓe shi kuma"
Mutumin zai kawo ɗan rago ga firist don a yi hadaya da ita. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "Lallai ne ya kawo ɗan rago bana ɗaya ga firist a yi hadaya da shi don laifi"
AT: "ba lallai ne ya kiɗaya kwanakin da suka wuce kafin ya ƙazantar da kansa ba"
AT: "ya ƙazantar da kansa" ko "ya maishe kansa ƙazamtacce"
A nan "keɓewa" na nufin "mikawa." AT: "na mikawar sa" ko "cewa ya mika kansa"
AT: "Lallai wani ya kawo shi" ko "Lallai ne ya je"
Lallai ne ya kawo hadayarsa gaban firist don a yi wa Yahweh hadaya. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "Lallai ne ya mika hadayarsa ga Yahweh ta wurin kai wa firist ya yi hadaya" ko "Lallai ne ya mika hadayarsa ga Yahweh ta wurin kaiwa firist wanda zai yi hadayarsa"
AT: "gurasa mara yisti wanda ya yi"
AT: "lallausan gari da ya haɗa da mai"
AT: "gurasa mara yisti wanda ya yayyafa masa mai"
burbuɗin gurasa
Kalman nan "su" na nufin sauran hadayun da aka ce wa mutum daga cikin Naziriyawa ya kawo. Yawanci lokaci, ana bukatan hadaya na tsãba da hadaya na sha a maimakon wasu irin hadayun. Ana iya bayana ma'anar wannan a fili. AT: "tare da hadaya ta hatsi da hadaya na sha da Yahweh ke bukata a maimakon sauran hadayun"
"ya" na nufin firist "sa" kuma na nufin mutumin da ya yi wa'adin.
"a matsayin hadaya ta zumunta"
Za ka iya bayana abin da aka fahimta ana a fili. AT: "Lallai ne firist ya mika ... hadaya ta abin sha ga Yahweh"
A nan "keɓewa" na nufin "mikawa." AT: "nuna keɓewarsa" ko "nuna yadda ya mika kansa"
Wannan na nufin cewa ya dafa kafaɗar ragon. AT: "kafadar ragon da ya dafa"
A nan "keɓewa" na nufin "mikawa." AT: "nuna cewa an mika" ko "nuna cewa ya mika kansa ga Yahweh"
Bayan an mika abubuwan ga Naziriyawan, sai firist ya karɓa ya mika su ga Yahweh. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "To, lallain ne firist ya karɓa ya kaɗa su"
"da kuma"
AT: "wanda firist ya kaaɗ"
AT: "wanda ya mika"
A nan "keɓewa" na nufin "mikawa." AT: "mika shi" ko "bayan ya mika kansa ga Yahweh"
Wannan na nufin cewa Naziriyawan za iya bada baiko fiye da abin da aka umuce su su bayar. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "In ya shirya ya yi karin baiko"
"lallai ne ya yi biyayya ga abin da wa'adin da ya ɗauka ya ke bukata"
Waɗannan maganganu biyu a takaice na nufin abu ɗaya an kuma haɗa su don a nanata cewa lallai ne su yi biyayya ga takalifin wa'adin sa.
AT: "alkawarin da shari'ar Naziriyawa ke nunawa"
A nan "kiyaye" na nufin "tsaro."
Wannan karin magana ne da ke nufin samu nufin mai kyau game da wani. Ana iya bayana shi ta wurin fara'a. AT: "fara'a da ku"
A nan kalman nan "dube" na nufin nuna wani iri hali ga mutum. AT: "yi maku tagomashi"
A nan Yahweh na magana game da Isra'ila a matsayin mutanensa ta wurin cewa zai ba su "sunan sa." AT: "lallai ne su sa mutanen Isra'ila su suni cewa su nawa ne"
1A ranar da Musa ya kammala rumfar sujadar, sai ya shafe ta ya kuma keɓe ta ga Yahweh, tare da dukkan kayan adonta. Ya yi haka kuma domin bagadin da dukkan kayayyakinsa. Ya shafesu ya kuma keɓe su ga Yahweh.2A wannan rana, shugabannin Isra'ila, shugabannin iyalan kakanninsu, suka miƙa hadayu. Waɗannan mutane ne ke shugabancin kabilun. Sun shugabanci lissafin mazajen a ƙidaya.3Suka kawo baye-bayensu gaban Yahweh. Suka kawo kekunan noma rufaffu guda shida da shanu sha biyu. Suka kawo kowanne keken noma ɗaya domin shugabanni biyu, kuma kowanne shugaba ya kawo sã ɗaya. Suka gabatar da waɗannan abubuwa a gaban rumfar sujada.4Daga nan Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,5"Ka karɓi baye-bayen daga garesu ka kuma yi amfani da baye-bayen domin aikin rumfar taruwa. Ka bayar da baye-bayen ga Lebiyawa, ga kowannen su bisa ga yadda aikinsa ke buƙatarsu."6Musa ya ɗauki kekunan noman da shanun, ya kuma bayar da su ga Lebiyawa.7Ya bayar da kekunan noma biyu da shanu huɗu ga zuriyar Gashon, saboda abin da aikinsu ke buƙata.8Ya bayar da kekunan noma huɗu da shanu takwas ga zuriyar Merari, cikin kulawar Itama ɗan Haruna firist. Ya yi wannan ne saboda abin da aikinsu ya ke buƙata.9Amma bai ba da ko ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa ba ga zuriyar Kohat, saboda nasu zai kasance aikin dake da dangantaka da abubuwan dake na Yahweh wanda za su ɗauka bisa kafaɗunsu.10Shugabannin suka miƙa kayayyakinsu domin keɓewar bagadi a ranar da Musa ya shafe bagadi. Shugabannin suka miƙa hadayunsu a gaban bagadin.11Yahweh ya cewa Musa, "Kowanne shugaba a ranarsa zai miƙa hadayarsa domin keɓewar bagadi."12A rana ta farko, Nashon ɗan Amminadab, na kabilar Yahuda, ya miƙa tasa hadayar.13Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awo na rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.14Ya bayar da kwanon zinariya guda ɗaya mai nauyin awo goma cike da turaren ƙonawa.15Ya bayar da bijimi ɗaya domin baiko na ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.16Ya bayar da bunsuru ɗaya domin baikon zunubi.17Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar 'yan shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Nashon ɗan Amminadab.18A rana ta biyu, Netanel ɗan Zuyar, shugaban Issaka, ya miƙa hadayarsa.19Ya miƙa a matsayin hadaya tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa ɗaya mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.20Ya kuma bayar da kwanon zinariya guda ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.21Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.22Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.23Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Netanel ɗan Zuyar.24A rana ta ukku, Eliyab ɗan Helon, shugaban zuriyar Zebulun, ya miƙa hadayarsa.25Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130, da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.26Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.27Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.28Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon sujada.29Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar 'yan shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Eliyab ɗan Helon.30A rana ta huɗu, Elizur ɗan Shedeyur, shugaban zuriyar Ruben, ya miƙa hadayarsa.31Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.32Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.33Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, ɗan rago shekara ɗaya.34Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.35Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Elizur ɗan Shedeyur.36A rana ta biyar, Shelumiyel ɗan Zurishaddai, shugaban zuriyar Simiyon, ya miƙa hadayarsa.37Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.38Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.39Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, ɗan rago shekara ɗaya.40Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.41Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar, a matsayi hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Shelumiyel ɗan Zurishaddai.42A rana ta shida, Eliyasaf ɗan Deuyel, shugaban zuriyar Gad, ya miƙa hadayarsa.43Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai a matsayin baikon hatsi.44Ya kuma bayar da kwanon azurfa ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.45Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, ɗan rago shekara ɗaya.46Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.47Ya bayar da shanu biyu, roga biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Eliyasaf ɗan Deuyel.48A rana ta bakwai, Elishama ɗan Ammihud, shugaban zuriyar Ifraim, ya miƙa hadayarsa.49Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai a matsayin baikon hatsi.50Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.51Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.52Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.53Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Elishama ɗan Ammihud.54A rana ta takwas, Gamaliyel ɗan Fedazur, shugaban zuriyar Manasse, ya miƙa hadayarsa.55Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.56Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.57Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.58Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.59Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, da 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Gamaliyel ɗan Fedazur.60A rana ta tara, Abidan ɗan Gidiyoni, shugaban zuriyar Benyamin, ya miƙa hadayarsa.61Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.62Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.63Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.64Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.65Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Abidan ɗan Gidiyoni.66A rana ta goma, Ahiyeza ɗan Ammishaddai, shugaban zuriyar Dan, ya miƙa hadayarsa.67Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai a matsayin baikon hatsi.68Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.69Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, ɗan rago shekara ɗaya.70Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.71Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Ahiyeza ɗan Ammishaddai.72A rana ta sha ɗaya, Fagiyel ɗan Okran, shugaban zuriyar Asha, ya miƙa hadayarsa.73Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai a matsayin baikon hatsi.74Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.75Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.76Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.77Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Fagiyel ɗan Okran.78A rana ta sha biyu, Ahira ɗan Enan, shugaban zuriyar Naftali, ya miƙa hadayarsa.79Hadayarsa ita ce tire ɗaya na azurfa mai nauyin awo 130 da bangajin azurfa mai nauyin awo saba'in, bisa ga matakin awon rumfar sujada. Dukkan waɗannan kaya na cike da gari mai laushi gauraye da mai domin baikon hatsi.80Ya kuma bayar da kwanon zinariya ɗaya mai nauyin awo goma, cike da turaren ƙonawa.81Ya bayar da bijimi ɗaya a matsayin baikon ƙonawa, rago ɗaya, da ɗan rago shekara ɗaya.82Ya bayar da bunsuru ɗaya a matsayin baikon zunubi.83Ya bayar da shanu biyu, rago biyar, bunsuru biyar, 'yan raguna biyar dake shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan ita ce hadayar Ahira ɗan Enan.84Shugabannin Isra'ila suka keɓe dukkan waɗannan a ranar da Musa ya shafe bagadi. Suka keɓe tirirrikan azurfa sha biyu, bangajin azurfa sha biyu, da kwanukan zinariya sha biyu.85Kowanne tire nauyin awo 130 kowanne bangaji kuma nauyin awo saba'in. Dukkan kayan azurfar nauyin su awo 2,400 ne, bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada.86Kowanne kwanukan zinariya sha biyu, cike da turaren ƙonawa, nauyin awo goma bisa ga matakin nauyin awon rumfar sujada. Dukkan kwanukan zinariyar nauyin awo 120 ne.87Suka keɓe dukkan dabbobi domin baye-baye na ƙonawa, bijimai sha biyu, rago sha biyu, 'yan raguna sha biyu 'yan shekara ɗaya. Suka bayar da baikon hatsinsu. Suka bayar da bunsuru sha biyu a matsayin baikon zunubi.88Daga dukkan garken dabbobinsu, suka bayar da bijimai ashirin da huɗu, rago sittin, bunsuru sittin, da 'yan raguna sittin 'yan shekara ɗaya, a matsayin hadaya domin baikon zumunta. Wannan domin keɓewar bagadi ne bayan an shafe shi.89Sa'ad da Musa ya shiga cikin rumfar taruwa domin ya yi magana tare da Yahweh, ya ji muryarsa ya na magana da shi. Yahweh ya yi magana da shi daga bisan marfin kafara dake a kan akwatin alƙawari., daga tsakanin kerubim biyu. Ya yi masa magana.
"Musa ya gama shirya alfarwar"
Waɗannan maganganu biyu na bayana kungiyan mutane ɗaya ne ta hanyoyi biyu dabam daban. AT: "shugabannin Isra'ila wanda sune kan iyalin kakanin su"
Anan, ana duban shugabanin iyalan a matsayin "kai." AT: "shugabanin iyalan kakaninsu"
Sunan nan "kirge" ana iya bayana shi cikin aikatau. AT: "sun taimaki Musa da Haruna a kiɗaya mazajen"
Wannan na nufin cewa sun mika haɗayarsu ga Yahweh sun kuma kawo su zuwa cikin alfarwar. Ana iya haɗa waɗannan maganganun don karin bayani. AT: "Sun kawo hadayar su ga Yahweh sun kuma mika su a gare shi a gaban alfarwar"
karusai 6 rufaffu da takarkarai 12"
"ga kwane mutum bisa ga bukatan aikinsa"
Juya waɗannan sunayen mazajen daidai kamar yadda ka yi cikin 3:17.
"domin shi ne abin da suke bukata su yi aikinsu"
ƙarƙashin shugabancin Itamar ɗan Haruna firist" ko "Itamar ɗan Haruna firist ya duba aikinsu"
Juya wannan sunan na mijin daidai kamar yadda ka yi cikin 3:1.
Kalman nan "ya" na nufin Musa.
"domin abin da suke bukata kenan su yi aikinsu"
Wannan na nufin keken shanu da san noma.
Juya wannan sunan maza daidai kamar yadda ka yi ciking 3:17.
"aikin su zai zama"
Za ka iya bayana ma'anar abin da ke na Yahweh fili. AT: "abubuwan da Yahweh ya ajiya domin alfarwar"
"mika kyauta"
"Kowane rana, lallai ne shugaba ɗaya ya mika hadayar sa"
"rana ta 1"
Waɗannan sunayen mazaje ne. Dubi yadda ka juya waɗannan sunaye cikin 1:7
In ta zama lallai, waɗannan nauyin awu ana iya rubuta shi cikin awu na wannan zamani. AT: "tire na azurfa ɗaya wanda nauyinsa kusan ɗaya da rabi na awu gram" ko "tire ɗaya na azurfa mai nauyi 130"
"tasa ɗaya na azurfa mai nauyi shekel 70." In zai yiwu, waɗannan nauyin awu ana iya rubuta shi cikin awu na wannan zamani. AT: "tasa ɗaya na azurfa wanda nauyinsa kusan takwas daga cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi 770 bisa ga ma'aunin nauyi"
Akwai shekel masu nauyi daban dabam. Wannan ita ce wanda mutane ke amfani da shi a cikin haikali na alfarwa mai tsarki. Idan za ka juya nauyin wannan zuwa ma'aunin nauyin na wannan zamani, to ga hanya da zai kyautu ka juya wannan magana. AT: "auna bisa ga matakin da ake amfani da shi a haikali"
AT: "gari mai laushi da ya gauraye da mai"
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. AT: "kwano ɗaya na zinariya mai nauyi ɗaya cikin goma na kilogram" ko "kwano ɗaya na zinariya mai nauyi gram 110"
"wanda kowanen su mai shekara ɗaya ne"
"Wannan ita ce abin da Nashon ɗan Amminadab ya mika"
Juya wannan sunan na mijin daidai yadda ka yi cikin 1:7
"rana ta 2"
Juya wannan sunan na miji daidai yadda ka yi cikin 1:7
In ta zama dole, to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tire ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da rabi" ko "tire ɗaya na azurfa mai nauyi kilogran ɗaya da gram 430"
"tasa ɗaya na azurfa mai nauyi shekel 70." In zai yiwu, waɗannan nauyin awu ana iya rubuta shi cikin awu na wannan zamani. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa wanda nauyinsa kusan takwas daga cikin goma na kilogram" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 770"
Akwai shekel da nauyin su daban dabam. Wannan shine wanda mutane ke amfani da su cikin haikali na alfarwa mai tsarki. Juya wannan magana daidai kamar yadda ka yi cikin 7:12. AT: "auna bisa ga matakin da ake amfani da shi a haikali"
AT: "gari mai laushi wanda ya gauraye da mai"
IIn ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗanan nauyin cikin 7:12. AT: "kwano ɗaya na zinariya mai nauyi ɗaya cikin goma na kilogram" ko "tasa ɗaya na zinariya mai nauyi gram 110"
"wanda kowanen su na da shekara ɗaya"
"Wannan ita ce abin da Netanel ɗan Zuwar ya mika"
Juya wannan sunan na miji daidai yadda ka yi cikin 1:7
"rana ta 3"
Juya wannan suna na maza daidai kamar yadda ka yi cikin 1:7.
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da rabi" ko "tasa ɗaya na zinariya mai nauyi kilogram ɗaya da gram 110"
"tasa ɗaya na azurfa wanda nauyin ta shekel 70." In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram takwas cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 770"
Akwai shekel da nauyin su daban dabam. Wannan shine wanda mutane ke amfani da shi a haikali na alfarwa mai tsarki. AT: "an anuna bisa ga matakin da ake amfani da shi a haikali"
AT: "gari mai laushi da ya gauraye da mai"
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na zinariya mai nauyi kilogram ɗaya cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 110"
"wanda kowanensu ke shekara ɗaya"
"Wannan ita ce abin da Eliyab ɗan Helon ya mika a matsayin hadaya"
Juya wannan sunan mazan daidai kamar yadda ka yi cikin 1:7
"rana ta 4"
Juya wannan sunan mazan daidai kamar yadda ka yi cikin 1:4.
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Duba yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da rabi" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 430"
"tasa ɗaya na azurfa wanda nauyin ta shekel 70." In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram takwas cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 770"
Akawai shekel da suke da nauyi daban dabam. Wannan shi ne wanda mutane ke amfani da haikali na alfarwa mai tsarki. Juya wannan magana daidai kamar yadda ka yi cikin 7:12. AT: "auna bisa ga matakin auna nauyi da ake amfani shi a haikali"
AT: "gari mai laushi da ya gauraye da mai"
In ta zama lallai, to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na zinariya wanda nauyinsa kilogram ɗaya cikin goma" ko "tasa ɗaya na zinariya mai nauyi gram 110"
"wanda kowanen su na shekara ɗaya"
"Wannan shine abin da Elizur ɗan Shedeyur ya mika a matsayin hadaya"
Juya wannan sunan maza daidai kamar yadda ka yi cikin 1:4.
"rana ta 5"
Juya wannan sunan maza daidai yadda ka juya shi cikin 1:4.
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da rabi" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da gram 430"
"tasa ɗaya na azurfa wanda nauyin ta shekel 70." In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram takwas cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 770"
Akawai shekel da suke da nauyi daban dabam. Wannan shi ne wanda mutane ke amfani da haikali na alfarwa mai tsarki. Juya wannan magana daidai kamar yadda ka yi cikin 7:12. AT: "auna bisa ga matakin auna nauyi da ake amfani shi a haikali"
AT: "gari mai laushi da ya gauraye da mai"
In ta zama lallai, to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na zinariya wanda nauyinsa kilogram ɗaya cikin goma" ko "tasa ɗaya na zinariya mai nauyi gram 110"
"wanda kowannen su na shekara ɗaya"
"Wannan shine Shelumiyel ɗan Zurishaddai ya mika a matsayin hadaya"
Juya wannan sunan daidai yadda ka yi cikin 1:4.
"rana ta 6"
Juya wannan sunan daidai yadda ka yi cikin 1:12.
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da rabi" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da gram 430"
"tasa ɗaya na azurfa wanda nauyin ta shekel 70." In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram takwas cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 770"
Akawai shekel da suke da nauyi daban dabam. Wannan shi ne wanda mutane ke amfani da haikali na alfarwa mai tsarki. Juya wannan magana daidai kamar yadda ka yi cikin 7:12. AT: "auna bisa ga matakin auna nauyi da ake amfani shi a haikali"
AT: "gari mai laushi da ya gauraye da mai"
In ta zama lallai, to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na zinariya wanda nauyinsa kilogram ɗaya cikin goma" ko "tasa ɗaya na zinariya mai nauyi gram 110"
"wanda kowannen su na shekara ɗaya"
"Wannan shine abinda Eliyasaf ɗan Deuyel ya mika a matsayin hadaya"
Juya wannan sunan daidai yadda ka yi cikin 1:12.
"rana ta 7"
Juya wannan sunan daidai yadda ka yi cikin 1:10.
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Duba yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da rabi" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da gram 430"
"tasa ɗaya na azurfa wanda nauyin ta shekel 70." In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram takwas cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 770"
Akawai shekel da suke da nauyi daban dabam. Wannan shi ne wanda mutane ke amfani da haikali na alfarwa mai tsarki. Juya wannan magana daidai kamar yadda ka yi cikin 7:12. AT: "auna bisa ga matakin auna nauyi da ake amfani shi a haikali"
AT: "gari mai laushi da ya gauraye da mai"
In ta zama lallai, to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na zinariya wanda nauyinsa kilogram ɗaya cikin goma" ko "tasa ɗaya na zinariya mai nauyi gram 110"
"wanda kowannen su na shekara ɗaya"
"Wannan shine abinda Elishama ɗan Ammihud ya mika"
Juya wannan sunan daidai yadda ka yi cikin 1:10.
"rana ta 8"
Juya wannan suna daidai kamar yadda ka yi cikin 1:10.
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da rabi" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da gram 430"
"tasa ɗaya na azurfa wanda nauyin ta shekel 70." In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram takwas cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 770"
Akawai shekel da suke da nauyi daban dabam. Wannan shi ne wanda mutane ke amfani da haikali na alfarwa mai tsarki. Juya wannan magana daidai kamar yadda ka yi cikin 7:12. AT: "auna bisa ga matakin auna nauyi da ake amfani shi a haikali"
AT: "gari mai laushi da ya gauraye da mai"
In ta zama lallai, to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na zinariya wanda nauyinsa kilogram ɗaya cikin goma" ko "tasa ɗaya na zinariya mai nauyi gram 110"
"wanda kowannen su na shekara ɗaya"
"Wannan shine abinda Elishama ɗan Ammihud ya mika a matsayin hadaya"
Juya wannan sunan daidai yadda ka yi cikin 1:10.
"rana ta 9"
Juya wannan sunan na miji daidai kamar yadda ka yi cikin 1:10.
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da rabi" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da gram 430"
"tasa ɗaya na azurfa wanda nauyin ta shekel 70." In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Duba yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram takwas cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 770"
Akawai shekel da suke da nauyi daban dabam. Wannan shi ne wanda mutane ke amfani da haikali na alfarwa mai tsarki. Juya wannan magana daidai kamar yadda ka yi cikin 7:12. AT: "auna bisa ga matakin auna nauyi da ake amfani shi a haikali"
AT: "gari mai laushi da ya gauraye da mai"
In ta zama lallai, to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na zinariya wanda nauyinsa kilogram ɗaya cikin goma" ko "tasa ɗaya na zinariya mai nauyi gram 110"
"wanda kowannen su na shekara ɗaya"
"Wannan shine abinda Abidan ɗan Gidiyoni ya mika a matsayin hadaya"
Juya wannan sunan daidai yadda ka yi cikin 1:10.
"rana ta 10"
Juya wannan sunan na miji daidai kamar yadda ka yi cikin 1:12.
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da rabi" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da gram 430"
"tasa ɗaya na azurfa wanda nauyin ta shekel 70." In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram takwas cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 770"
Akawai shekel da suke da nauyi daban dabam. Wannan shi ne wanda mutane ke amfani da haikali na alfarwa mai tsarki. Juya wannan magana daidai kamar yadda ka yi cikin 7:12. AT: "auna bisa ga matakin auna nauyi da ake amfani shi a haikali"
AT: "gari mai laushi da ya gauraye da mai"
In ta zama lallai, to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na zinariya wanda nauyinsa kilogram ɗaya cikin goma" ko "tasa ɗaya na zinariya mai nauyi gram 110"
"wanda kowannen su na shekara ɗaya"
"Wannan shine abinda Abidan ɗan Gidiyoni ya mika a matsayin hadaya"
Juya wannan sunan daidai yadda ka yi cikin 1:12.
"rana ta 11"
Juya wannan suna na mijji daidai kamar yadda ka yi cikin 1:12.
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da rabi" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da gram 430"
"tasa ɗaya na azurfa wanda nauyin ta shekel 70." In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Duba yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram takwas cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 770"
Akawai shekel da suke da nauyi daban dabam. Wannan shi ne wanda mutane ke amfani da haikali na alfarwa mai tsarki. Juya wannan magana daidai kamar yadda ka yi cikin 7:12. AT: "auna bisa ga matakin auna nauyi da ake amfani shi a haikali"
AT: "gari mai laushi da ya gauraye da mai"
In ta zama lallai, to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na zinariya wanda nauyinsa kilogram ɗaya cikin goma" ko "tasa ɗaya na zinariya mai nauyi gram 110"
"wanda kowannen su na shakara ɗaya"
"Wannan shine abin da Fagiyel ɗan Okran ya mika a matsayin hadaya"
Juya wannan suna daidai kamar yadda ka yi cikin 1:12.
"rana ta 12"
Juya wannan suna daidai kamar yadda ka yi cikin 1:12.
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da rabi" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da gram 430"
"tasa ɗaya na azurfa wanda nauyin ta shekel 70." In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram takwas cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 770"
Akawai shekel da suke da nauyi daban dabam. Wannan shi ne wanda mutane ke amfani da haikali na alfarwa mai tsarki. Juya wannan magana daidai kamar yadda ka yi cikin 7:12. AT: "auna bisa ga matakin auna nauyi da ake amfani shi a haikali"
AT: "gari mai laushi da ya gauraye da mai"
In ta zama lallai, to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na zinariya wanda nauyinsa kilogram ɗaya cikin goma" ko "tasa ɗaya na zinariya mai nauyi gram 110"
"wanda kowannen su na shekara ɗaya"
Wannan ita ce abin da Ahira ɗan Enan ya mika a matsayin hadaya"
Juya wannan sunan mazan daidai kamar yadda ka yi cikin 1:12.
Maganan nan "keɓe" na nufin a mika shine don wani manufa ta musamman. A wannan yanayi, an mika wannan baiko ga Yahweh.
A nan kalman nan "rana" na nufin lokaci. Shigabannin Isra'ila sun keɓe waɗannan abubuwa ciki kwanaki 12. AT: "Sa'ad da Musa ya shafe bagadi"
In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da rabi" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram ɗaya da gram 430"
"tasa ɗaya na azurfa wanda nauyin ta shekel 70." In ta zama lallai. to ana iya rubuta wanna bisa ga ma'aunin zamanin nan. Dubi yadda ka juya waɗannan nauyin cikin 7:12. AT: "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi kilogram takwas cikin goma" ko "tasa ɗaya na azurfa mai nauyi gram 770"
Akawai shekel da suke da nauyi daban dabam. Wannan shi ne wanda mutane ke amfani da haikali na alfarwa mai tsarki. Juya wannan magana daidai kamar yadda ka yi cikin 7:12. AT: "auna bisa ga matakin auna nauyi da ake amfani shi a haikali"
"Dukkan kayan azurfa in an haɗa su, nauyin ... Dukkan kwanukan zinariyar in an haɗa su, nauyin"
Wannan na nufin dukkan baikon da aka yi na azurfa, duk da tire da kuma tasa.
Kowane kwanukan zinariya 12 ... nauyin shekel 10." In ya zama lallai, ana iya ruba wannan a matakin awu na wannan zamani. Duba yadda ka juya wannan cikin 7:12. AT: "Kowane kwanukan zinariya 12 ... nauyin ɗaya cikin goma na kilogram ɗaya" ko "Kowane kwanukan zinariya 12 ... nauyin sa gram 110"
huɗu ... sittin "12 ... 24 ... 60."
"wanda suke shekara ɗaya"
AT: "bayan Musa ya shafe ta"
A nan "muryarsa" na nufin Yahweh. AT: "ya ji Yahweh na magana da shi"
Waɗannan maganganu biyu na bayani game da wuri ɗaya ne.
Juya wannan magana daidai yadda ka yi cikin 4:5.
"Yahweh ya yi magana da Musa"
1Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Ka yi magana da Haruna. Ka ce da shi, 'Fitilun nan guda bakwai su bada haske a gaban wurin ɗora fitilar idan ka kunna su."'3Haruna kuwa ya yi haka. Ya kunna fitilun yadda za su ba da haske wajan gaban inda a ke ɗora fitilun, kamar yadda Yahweh ya ummarci Musa.4Haka a ka yi wurin ɗora fitilun yadda Yahweh ya nuna wa Musa. Ya zama bugaggiyar zinariya tun daga ƙasa har sama, da bugaggun koffuna kamar furanni.5Yahweh, ya sake yin magana da Musa. Ya ce,6"Ka ɗebi Lebiyawa daga cikin mutanen Isra'ila ka tsarkake su.7Ga yadda za ka tsarkake su: Ka yayyafa ruwan kafara a kansu. Ka sa su aske jikinsu dukka, su wanke tufafinsu ta haka za su tsarkake kansu.8Ka sa su sami ɗan bijimi da baikonsa na gari wanda a ka gauraya da mai. Su kuma sami wani ɗan bijimin domin baiko na zunubi.9Ka kawo Lebiyawan gaban rumfa ta taruwa ka kuma tattara dukkan mutanen Isra'ila.10Sa'ad da ka kawo Lebiyawan gaban Yahweh, sai dukkan mutanen Isra'ila su ɗora hannuwansu a kan Lebiyawan.11Sai Haruna ya miƙa Lebiyawan a gaban Yahweh, kamar bayarwa ta ɗagawa daga mutanen Isra'ila domin su yi wa Yahweh hidima.12Sai Lebiyawan su ɗora hannuwansu a bisa kawunan bajiman. Sai ka miƙa bijimi ɗaya baiko na zunubi, ɗaya bijimin kuma baiko na ƙonawa gare ni, sai a yi wa Lebiyawan kafara.13Sai ka gabatar da Lebiyawan ga Haruna da 'ya'yansa, ka ɗaga su kamar baiko na ɗagawa a gare ni.14Ta haka za ka keɓe Lebiyawan daga cikin mutanen Isra'ila. Lebiyawan za su zama nawa.15Bayan wannan sai Lebiyawan su shiga su yi hidima a cikin rumfa ta taruwa. Dole ne ka tsarkake su. Dole kuma ka miƙa su kamar baikon na ɗagawa.16Ka yi haka, saboda sun zama nawa ɗungum daga cikin mutanen Isra'ila. Su za su zama kamar kowanne ɗă namiji da aka fara haifuwa, ɗa na fari daga kowacce zuriya ta Isra'ila. Na ɗauki Lebiyawa domin kaina.17Kowanne ɗă na fari na mutanen Isra'ila nawa ne, na mutum dana dabba. A ranar dana ɗauke dukkan rayukan 'ya'yan fari cikin ƙasar Masar, na keɓe su gare ni.18Na ɗauki Lebiyawa daga cikin mutanen Isra'ila a madadin dukkan 'ya'yan fari.19Na bayar da Lebiyawa kyauta ga Haruna da 'ya'yansa. Na ɗauke su daga cikin mutanen Isra'ila domin su yi aikin mutanen Isra'ila a cikin rumfa ta taruwa. Na bayar da su domin su yi kafara saboda mutanen Isra'ila domin kada annoba ta same su sa'ad da suka zo kusa da wuri mai tsarki."20Musa da Haruna da dukkan taron mutanen Isra'ila suka yi haka da Lebiyawa. Suka yi dukkan abin da Yahweh ya ummurci Musa game da Lebiyawa. Mutanen Isra'ila suka yi haka da su.21Lebiyawan su ka tsarkake kansu suka wanke tufafinsu, Haruna ya gabatar da su kamar baiko na ɗagawa ga Yahweh kuma ya yi kafara domin su ya tsaftace su22Bayan haka, sai Lebiyawan suka shiga domin su yi hidima a cikin rumfa ta taruwa a gaban Haruna da 'ya'yansa. Wannan ya zama kamar yadda Yahweh ya ummarci Musa game da Lebiyawa. Haka suka yi da dukkan Lebiyawa.23Yahweh ya sake yin magana da Musa. Ya ce,24"Dukkan wannan saboda Lebiyawan da suka kai shekara ashirin da biyar ne zuwa gaba. Za su haɗu da sauran su yi hidima a cikin rumfa ta taruwa.25Za su dena yin hidima sa'ad da suka kai shekara hamsin. A waɗannan shekarun ba za su ƙara yin hidima ba.26Za su iya taimakon 'yan'uwansu waɗanda suke ci gaba da yin hidima a rumfa ta taruwa, amma su ba za su ƙara yin hidima ba. Sai ka jagoranci Lebiyawa cikin dukkan waɗannan al'amura.
"lallai ya haskaka ta gaba"
"ya haskaka"
AT: "Sun yi fitilun"
An umurce su yi koffuna don su yi kamar furanni. AT: "da bugaggun koffuna da ke kamar furanni"
A nan "su" na nufin Lewiyawa.
Yayyafa ruwan da Musa ke yi alama ce na kafarar su. AT: "Yayyafa masu ruwa wanda ke nuna alama ta kafara"
Ya kamata Lewiyawa su wanke tufafinsu. Za ka iya bayana a fili abin da aka fahimta. AT: "sai ka sa su su wanke tufafinsu"
Sa'ad da ake baikon ɗan bajjimi, a kan yi baikon hatsi.
AT: "gari mai laushi da suka gauraye da mai"
...
A nan Yahweh na nufin kansa bisa ga sunan sa.
"ɗibiya hannuwansu a kan" ana yin hakan so da dama don a mika su don aiki ko hidimar Yahweh. AT: "Lallai ne mutanen Isra'ila su sa wa Lewiyawan hannu, don muka su zuwa gare ni"
Ya kamata Haruna ya mika Lewiyawan ga Yahweh daidai kamar hadaya ne zuwa gare shi. AT: "sai ka ce su hadaya ne na kaɗawa"
Wannan alama ce da ke nuna cewa Lewiyawan tare da dabbobin an mika su. Ta haka mutumin na mika kansa ta wurin dabban ga Yahweh.
Ya kamata Haruna ya mika Lewiyawan ga Yahweh sai ka ce yana daga baikon sama ga Yahweh. AT: "mika su a gare ni, wato kamar ka na daga su sama a matsayin hadaya ta dagawa zuwa gare ni"
Yahweh ya nanata waɗannan abubuwa don ya nanata muhimmancinsu. Lallai ne wannan ya faru kafin Lewiyawa su je hidima a alfarwa ta sujada. Takamammen ma'anar wannan magana ana iya bayana shi a fili. AT: "Amma lallai ne ka far tsarkake su tukuna. Lallai ne ka mika su kamar hadaya ta kaɗawa"
Ya kamata Haruna ya mika Lewiyawan ga Yahweh kamar su hadaya ne na dagawa zuwa gare shi. AT: "Lallai ne ka mika su a gare ni kamar ka na mika hadaya ta daga zuwa gare ni"
Waɗannan maganganu biyun a takaice na nufin abu ɗaya ne an kuma haɗa su don a nanata cewa 'yan fari maza
Wannan na nufin ɗa da aka fara haifarsa. AT: "ɗa na fari daga uwa tasa"
Wannan hanya mai ɗa'a ce da ana nufin sa'ad da an wani ya kashe mutum. AT: "na kashe"
A nan "su" na nufin "ɗan fari daga cikin mutanen Isra'ila"
An yi magana game da zaɓin da Yahweh ya zaɓe Lewiyawa don su taimake Haruna da 'ya'yansa maza sai ka ce su kyauta ce da Yahweh ya ba wa Haruna da 'ya'yansa maza.
A nan "su" na nufin Lewiyawan.
AT: "maimakon ɗauka dukka 'ya'yan fari"
A nan "su" na nufin mutanen Isra'ila.
A nan a kwai jimla uku da suke magana a kan zance ɗaya. An jaddada wannan don a nanata cewa mutanen su yi da Lewiyawan bisa ga umurnin Yahweh. AT: "Musa da Haruna da kuma dukka jama'an Isra'ila sun yi da Lewiyawan dukka abin da Yahweh ya umurce Musa game da Lewiyawan"
AT: "yi hidima"
...
"Abin da suka yi shine"
"Sun yi da Lewiyawan daidai abin da Yahweh ya umurce su." Kalman "su" na nufin mutanen Isra'ila.
"Dukka waɗannan umurnin na Lewiyawa ne"
"shekaru 25"
Kalman nan "sauran" na nufin sauran mutanen da suke aiki cikin alfarwa ta sujada. Duba yadda ka juya wanan cikin 4:1.
"shekara hamsin" ko "sa'ad da suka kai shekaru hamsin"
1Yahweh ya yi magana da Musa a cikin jejin Sinai, a cikin wata na biyu bayan sun fito daga ƙasar Masar. Ya ce,2"Sai mutanen Isra'ila su kiyaye idin Ƙetarewa a lokacin da aka ayyana cikin shekara.3A kan rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, da yamma, dole ne ku kiyaye idin Ƙetarewa a lokacin da aka ayyana shi a shekara. Ku kiyaye shi ku bi dukkan ka'idodi, ku yi biyayya da dukkan farillan da aka ayyana domin sa."4Haka, Musa ya gaya wa mutanen Isra'ila ya wajaba su riƙa kiyaye Idin Ƙetarewa.5Haka suka kiyaye Idin Ƙetarewa a cikin wata na fari a kan rana ta goma sha huɗu ga watan, da yamma, a cikin jejin Sinai. Mutanen Isra'ila suka kiyaye dukkan abin da Yahweh ya ummarci Musa ya yi.6Akwai waɗansu mutanen da suka zama ƙazamtattu ta wurin taɓa gawa. Ba su iya kiyaye Idin Ƙetarewar a wannan ranar ba.7Waɗannan mutane suka ce da Musa, "Mun ƙazamtu ta wurin taɓa gawar wani mutum. Meyasa hana aka mu miƙa hadaya ga Yahweh tare da sauran mutanen Isra'ila a lokacin da a ka ayyana na shekara?"8Musa yace da su, "Ku jira in ji umarnin da Yahweh zai bani saboda ku."9Sai Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,10"Ka yi magana da mutanen Isra'ila. Cewa, 'Idan wani a cikin ku, ko zuriyarku ya ƙazamtu ta wurin taɓa gawa, yana cikin tafiya mai nisa, zai iya kiyaye Idin Ƙetarewa ga Yahweh.'11A cikin wata na biyu a kan rana ta goma sha huɗu da yamma, za su iya cin abincin Idin Ƙetarewa. Za su ci ragon Idin Ƙetarewa da gurasa marar gami da ganyaye masu ɗăci.12Kada su rage shi har zuwa safiya, ko su karya ƙasusuwan. Dole ne su kiyaye dukkan ka'idodin da aka ayyan na Idin Ƙetarewar.13Amma dukkan mutum mai tsarki kuma ba tafiya ya ke yi ba, amma bai yi Idin Ƙetarewar ba, wannan mutum za a datse shi daga cikin mutanensa saboda bai miƙa hadaya ga Yahweh yadda ake bukata a lokacin da aka ayyana a shekara ba. Wannan mutum zai ɗauki zunubinsa.14Idan akwai baƙo a cikin ku yana kiyaye Idin Ƙetarewa domin ya ba Yahweh girma, sai ya kiyaye dukkan abin da aka umarta, da ka'idodinsa, da dukkan dokokinsa. Dokoki ɗaya ne za su shafi wanda aka haifa a ƙasar da kuma baƙo."15A ranar da aka kafa alfarwar, sai girgije ya sauka ya rufe ta, wato rumfar ta alƙawari. Da yamma girgijen yana bisan alfarwar. Ya zama kamar wuta har zuwa safiya.16Haka ya ci gaba. Da dare girgijen ya rufe alfarwar kamar wuta.17Duk lokacin da aka ɗauke girgijen daga bisa rumfar, sai mutanen Isra'ila su ci gaba da tafiyarsu. Dukkan sa'adda girgijen ya tsaya wuri ɗaya, sai mutanen su yi zango.18Idan Yahweh ya bada ummurni, sai mutanen Isra'ila su tafi, idan ya bada ummurni sai su yi zango. Sa'ad da girgijen ya tsaya a bisan alfarwar, sai su tsaya a zangonsu.19Idan girgijen ya tsaya a bisan alfarwar kwanaki da yawa, sai mutanen Isra'ila su yi biyayya da ka'idodin Yahweh ba za su tafi ba.20Wani lokaci girgijen yakan tsaya a bisa alfarwar har 'yan kwanaki. A wannan lokaci, sai su yi biyayya da umarnin Yahweh--sai su yi zango sai in ya bada umarni sai su tafi.21Wani lokacin sai girgijen ya kasance a bisa zangon tun daga yamma har safiya. Idan girgijen ya tashi da safe sai su tafi. Idan kuma ya ci gaba da tsayawa dare da rana, sai sa'ad da girgijen ya tashi za su tafi.22Duk sa'ad da girgijen ya tsaya a bisa alfarwar kwana biyu ko wata ɗaya ko shekara, idan dai girgijen yana tsaye a nan, mutanen za su tsaya a zangonsu ba za su tafi ba. Amma duk lokacin da aka ɗauke girgijen sai su kama tafiyarsu.23Za su yi zango sa'adda Yahweh ya bada umarni, kuma su tafi bisa ga umarninsa. Sun yi biyayya da umarnin da Yahweh ya ba Musa.
"cikin wata na 1." Wannan wata na fari ne na kalandar Yahudawa. Ta na nuna lokacin da Allah ya fitar da mutane Isra'ila daga ƙasar Masar.
"shekara na 2"
A nan "sun" na nufin mutanen Isra'ila. Maganan nan "fita daga" na nufin su bar kasar. AT: "bayan sun bar kasar Masar"
Kalman nan "aiyana" na nufin lokacin da "aka shirya." Wannan na nufin cewa daidai lokacin da suka saba yi a kowane shekara. AT: "bar mutanen ... a daidai lokacin da suke yi a shekaran."
Wannan ita ce lokacin da aka aiyana ciki shekaran don biki idin ƙetarewa. Anan iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "A rana ta goma sha hudu ... kuma yi, domin wannan ita ce lokacin da kuke bikin a kowace shekara"
"rana ta 14"
Waɗannan maganganu biyun a takaice na nufin abu ɗaya ne, an kuma haɗa su don a nanata cewa yakamata su yi biyayya da umurnin.
AT: "Lallai ku yi bikin"
AT: "kiyaye bikin idin ƙetarewa" ko "yi bikin idin ƙetarewa"
"cikin wata na 1, a rana ta sha huɗu ga watan"
Wannan na nufin cewa sun taɓa gawa, wannan kuwa ta sa sun ƙazamtu. Ku na iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "zama ƙazamtattu don sun taɓa gawa"
An yi maganar duk mutumin da Allah na duban sa a matsayin wanda ba karɓaɓɓe bane a gaban Allah ko kuwa wanda ya ƙazamtu sai ka ce mutumin ya zama mara tsarki a jiki.
AT: "yi bikin idin ƙetarewa"
Wannan na nufin cewa sun taɓa gawan mutum. Za a iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "domin sun taɓa gawan mutum"
Mutanen sun yi wannan tambaya don su nuna rashin jin daɗin sun cewa ba a bar su sun yi bikin idin ƙetarewa tare da sauran mutanen ba. Ana iya juya wannan tambaya ba ta hanyar tambaya ba. AT: "ba daidai ba ne ka hana mu mika hadaya ... tare da sauran mutane Isra'ila."
sa ko shirya
An yi maganar duk mutumin da Allah na duban sa a matsayin wanda ba karɓaɓɓe bane a gaban Allah ko kuwa wanda ya ƙazamtu sai ka ce mutumin ya zama mara tsarki a jiki.
Wannan na nufin cewa wani ya taɓa gawa. AT: "domin kun taɓa gawa"
AT: "yi bikin idin ƙetarewa"
AT: "yi bikin idin ƙetarewa"
"a wata na 2 a rana ta 14"
"daidai faɗiwar rana"
"Lallai ne su ci ɗan tunkiyan idin ƙetarewan"
"gurasar da ba a sa yisti ba" ko "da gurasar da babu yisti"
Waɗannan 'yan kananan shuke-shuke da suke da ba ta da daɗi.
"kuma ba za su karya ƙasussuwan ta faufau"
An yi maganar mutumin da Allah ke duban sa a matsayi karɓaɓɓe zuwa a gare shi sai ka mutumin na da tsabta ne cikin jiki.
AT: "yi bikin idin ƙetarewa"
A nan maganan nan "fid da" na nufin a ki sa'annan kuma a kore shi. AT: "lallai ne a kore mutumin nan" ko "lallai ne ku kore mutumin nan"
sa ko shirya
An yi magana game da mutmin zai ɗauki sakamakon zunubinsa sai ka ce zunubi wata kaya ce mai nauyi da lallai ne ya ɗauka. AT: "Lallai ne mutumin ya karɓi hukunci zunubinsa"
A nan "ku" na nufin mutanen Isra'ila.
"lallai ne wannan baƙon ya kiyaye ta ya kuma yi duk abin da Yahweh ya umurta"
Waɗannan maganganu biyun a takaice na nufin abu ɗaya ne, an kuma yi amfani da su don a nanata cewa lallai ne baƙon ya yi biyayya da dukkan ka'idodi game da idin ƙetarewan.
"cikin ƙasar Isra'ila"
AT: "Lewiyawan sun kafa alfarwar"
Wannan wata suna ne ta alfarwar. Duba yadda ka juya wannan magana "alfarwa alkawari na dokoki " cikin 1:50.
Wannan na nufin cewa girgijen ta bayyana da dare. A nan an kwatantan kamani hadarin kamar wuta. AT: "Da daddare, girgijen na kamar wuta ne har zuwa safe"
zai zama da taimako a bayana cewa wannan na nufin girgije na bisan alfarwar. AT: "Girgijen ta kasance a bisan alfarwar"
An kwatanta bayyanuwar girgijen da wuta. AT: "ta na da kamanin wuta da daddare."
AT: "kau da" ko "Yahweh ya ɗauki girgijen"
"girgijen ta tsaya a wuri ɗaya"
Ana iya bayana kalman "umurnin" cikin aikatau. AT: "Sa'ad da Yahweh ya umurta"
"sama bisan alfarwar"
A nan kalman nan "yi" na nufin "shirya." AT: "shirya zangon su"
Wannan na nufin cewa girgijen ta tsaya bisa alfarwar na kwana ɗaya. Ka bayana a fili ma'anar wannan magana. AT: "da yamma har zuwa safe ne kawai" ko "a bisa alfarwar na dare ɗaya ne kawai"
Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. "idan girgijen ya tsaya bisa alfawar"
"har sai bayan girgijen ya tashi za su cigaba da tafiya"
AT: "girgijen ya tashi sama"
Ana iya bayana kalman nan "umurni" cikin aikatau. "abin da Yahweh ya umurta"
AT: "umurnin da Yahweh ya ba wa Musa"
1Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Ka yi kakaki biyu na azurfa. Ka yi su da bugaggiyar azurfa. Ka yi amfani da ƙahonin domin ka kira ƙungiyoyin jama'a su zo su taru kuma domin ka kira ƙungiyoyin jama'a su zakuɗa da zangunansu.3Fristoci su busa kakakin domin su kira dukkan ƙungiyoyin jama'a su taru a gaban rumfa ta taruwa.4Idan firistoci suka busa kakaki ɗaya, sai shugabanni da shugabannin iyalai na Isra; ila, su zo su taru.5Idan ka busa alama mai ƙara, sai zangon gabas su fara tafiyarsu.6Idan ka busa alama mai ƙara ta biyu, sai zanguna na zangon kudu su fara tafiyarsu. Suma sai su busa alama mai ƙara domin su tafi.7Sa'anda jama'a suka taru wuri ɗaya sai ka busa ƙahonin, amma ba da ƙarfi ba.8'Ya'yan Haruna da firistoci ne za su busa kakakin. Wannan za ta zama ka'ida a gare ka dukkan zamanun mutanenka.9Idan kuka tafi yaƙi cikin ƙasarku da maƙiyi wanda yake găba da ku, sai ku busa alama da kakakin. Ni, Yahweh Allahnku, zan tuna daku in cece ku daga maƙiyanku.10Kuma, lokacin bukukuwa, da bukukuwanku na yau da kullum ko na farkon wata, sai ku busa kakaki saboda baye--bayenku na ƙonawa da hadayinku da baye--bayenku na zumunci. Waɗannan abubuwa za su sa in tuna da ku, Ni Allahnku. Ni ne Yahweh Allahnku."11A cikin shekara ta biyu, a cikin wata na biyu, a rana ta ashirin ga watan, sai aka ɗauke girgijen daga bisa rumfar taruwa ta umarnin alƙawari.12Sai mutanen Isra'ila suka ci gaba da tafiyarsu daga jejin Sinai. Sai girgijen ya tsaya a jejin Faran.13Suka yi tafiyarsu ta fari, suna bin umarnin da Yahweh ya ba Musa.14Sai zangon dake ƙarƙashin tutar zuriyar Yahuda suka fara tafiya, suka fara gusawa da sojojinsu. Nashon ɗan Amminadab ya jagoranci sojojin Yahuda.15Netanel ɗan Zuyar ya jagoranci sojojin zuriyar Issaka.16Eliyab ɗan Helon ya jagoranci sojojin zuriyar Zebulun.17Zuriyar Geshon da Merari, waɗanda ke lura da alfarwa, suka ɗauki alfarwar suka tafi.18Na biye su ne sojojin dake ƙarƙashin tutar zangon Ruben suka shirya suka tafi. Elizur ɗan Shedur ya jagoranci sojojin Ruben.19Shenumiyel ɗan Zurishaddai ya jagoranci sojojin zuriyar Simeyon.20Eliyasaf ɗan Dewuyel ya jagoranci sojojin kabilar zuriyar Gad.21Sai Kohatiyawa suka shirya fita. Suka ɗauki kayayyaki masu tsarki na wurin sujada. Waɗansu za su shirya alfarwa kafin Kohatiyawa su zo zango na gaba.22Sojoji na ƙarƙashin tutar zuriyar Ifraim su ne na gaba. Elishama ɗan Amihud ya jagoranci sojojin Ifraim.23Gamaliyel ɗan Fedazur ya jagoranci sojojin kabilar zuriyar Manasse.24Abidan ɗan Gidiyoni ya jagoranci sojojin kabilar zuriyar Banyami.25Sojojin da suka yi zango a ƙarƙashin tutar zuriyar Dan su ne suka tashi daga ƙarshe. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ya jagoranci sojojin Dan.26Fagiyel ɗan Okran ya jagoranci sojojin kabilar zuriyar Asha.27Ahira ɗan Inan ya jagoranci sojojin kabilar zuriyar Naftali.28Wannan shi ne yadda sojojin mutanen Isra'ila suka shirya suka fita tafiyarsu.29Musa ya yi magana da Hobab ɗan Rewuyel mutumin Midiya. Rewuyel ne mahaifin matar Musa. Musa ya yi magana da Hobab ya ce, "Za mu tafi wurin da Yahweh ya bayyana. Yahweh yace, 'Zan baku shi.' Ka biyo mu zamu kyautata maka. Yahweh ya yi alƙawari zai kyautatawa Isra'ila."30Amma Hobab yace da Musa, "Ba zan bi ku ba. Zan tafi ƙasata wurin mutanena."31Sai Musa ya amsa, "Idan ka yarda kada ka rabu da mu. Ka san yadda a ke yin zango a cikin jeji. Sai ka kula da mu.32Idan ka biyo mu, zamu kyautata ma ka kamar yadda Yahweh zai kyautata mana."33Suka yi tafiya ta kwana uku daga tsaunin Yahweh. Akwatin alƙawari na Yahweh ya tafi a gabansu kwana uku domin ya samar masu wurin da za su huta.34Girgijen Yahweh yana bisansu da rana inda suke tafiya.35Dukkan lokacin da akwatin alƙawari ya tashi, Sai Musa yace, "Yahweh, tashi ka watsar da maƙiyanka. Ka sa masu ƙin ka su gudu daga wurinka."36Duk sa'ad da akwatin alƙawari ya tsaya, sai Musa yace,"Yahweh ka dawo wurin Isra'ila masu yawa dubbai."
Wannan na nufin cewa Yahweh ya umurci Musa cewa ya sami wani ya yi kakakin. Bai yi da kansa ba. AT: "Ka gayawa wani ya yi kakaki biyu na azurfa"
Ba Musa ba ne zai busa kakakin ba, amma zai umurci firistocin su busa.
"lokacin da ka na nan." Wannan na nufin cewa ya kamata Musa ya na tare da firistocin a sa'ad da zai busa kakakin.
shugabanni da shugabannin iyalai na Isra'ila Waɗannan maganganu biyun na nufin ƙungiyan mutane ɗaya ne. A nan an yi amfani da magana na biyun don a bayana magana na farin. AT: "shugabanni, wanda su ne kan iyalan Isra'ila"
Yahweh na magana da Musa, amma ya na nufin firitocin ne. Firistocin za su busa kakakin, Musa kuwa ba zai busa ba. AT: "Sa'ad da sun busa ya yi ƙara"
Yahweh na magana da Musa, amma ya na nufin firitocin ne. Firistocin za su busa kakakin, Musa kuwa ba zai busa ba. AT: "Sa'ad da sun busa ya yi ƙara"
"Don a tara jama'an wuri ɗaya"
"2"
"Su" na nufin firistocin. kalman nan "su" kuma na nufin mutanen Isra'ila.
"ku" a nan na nufin mutanen Isra'ila.
Yahweh yana magana da Musa sa'annan ya yi amfani da kalman nan "ku" amma kuwa yana nufin tafiyar mutane Isra'ila zuwa yaƙi. AT: "Sa'ad da mutanen Isra'ila sun tafi yaƙi ... zalunce Isra'ila"
A nan Yahweh kuma na magana da Musa ta wurin yin amfani da kalman nan "ku" amma ya na so Musa ya sami firistocin da za su busa kakakin. AT: "lallai ne ka umurce firistocin su busa kakaki"
AT: "sa'ad da kuke biki"
A nan Yahweh kuma na magana da Musa ta wurin yin amfani da kalman nan "ku" amma ya na so Musa ya sami firistocin da za su busa kakakin. AT: "lallai ne ka umurce firistocin su busa kakaki"
Akwai watanni 12 a kalandar Yahudawa.
Cikin waɗannan maganganu biyu, kalman nan "ku" na nufin mutanen Isra'ila.
"don martaba hadayun"
"zai zama abin da zai tunashe ku game da ni." Kalman nan "tunawa" za a iya bayana shi cikin aikatau wato "tuna." AT: "zai tunashe ku a koyaushe game da ni"
Kalman nan "waɗannan" na nufin kakakin da hadayun.
"A cikin shekara ta 2" Wannan shekara ta biyu ne bayan da Yahweh ya fid da Isra'ilawa daga Masar.
"a cikin wata na 2, a rana ta 20 ga watan." Wannan wata ce na biyu a kalandar Yahudawa.
AT: "girgijen ya tashi"
An kira alfarwar da wannan suna saboda akwatin alkawarin tare da dokokin da Allah ya sa cikin. Ka juya wannan daidai kamar yadda ka yi cikin 1:50.
Wannan zangon na haɗe da kabilu uku da ke ƙarƙashin Yahuda: Yahuda, Issaka da Zabaluna.
Maganan nan "tafi" na nufin sun kwashe zangon sun sun kama hanya.
Ka juya wannan sunan maza daidai kamar yadda ka yi ckin 1:7.
Ka juya wannan sunan maza daidai kamar yadda ka yi ckin 1:7.
Ka juya wannan sunan maza daidai kamar yadda ka yi ckin 1:7.
Ka juya wannan sunan maza daidai kamar yadda ka yi ckin 3:17.
Wannan na nufin sojojin kabilu da ke ƙarƙashin Ra'ubainu, Saminu da Gad.
Ka juya wannan sunan maza daidai kamar yadda ka yi ckin 1:4.
Ka juya wannan sunan maza daidai kamar yadda ka yi ckin 1:4.
Ka juya wannan sunan maza daidai kamar yadda ka yi ckin 1:12.
Juya wannan sunan namijin daidai kamar yadda ka juya shi cikin 3:27.
Wannan na nufin sojojin kabilun da ke ƙarƙashin Ifraimu: Ifraimu, Manassa da Biliyaminu.
Juya wannan sunan namijin daidai kamar yadda ka juya shi cikin 1:10
Juya wannan sunan namijin daidai kamar yadda ka juya shi cikin 1:10.
Juya wannan sunan namijin daidai kamar yadda ka juya shi cikin 1:10.
Wannan na nufin sojojin kabilun da ke ƙarƙashin Dan: Dan, Ashiru da Naftali.
Juya wannan sunan namijin daidai kamar yadda ka juya shi cikin 1:12.
Juya wannan sunan namijin daidai kamar yadda ka juya shi cikin 1:12.
Juya wannan sunan namijin daidai kamar yadda ka juya shi cikin 1:12.
Wannan sunan maza ne.
"wandan Yahweh ya bayana mana"
"zamu kyautata maka"
Maganan nan "kula" na nufin a bi da, da kula da. AT: "Za ka iya bi da mu ka kuma nuna mana yadda za mu yi rayuwa a jeji"
"Su" na nufin mutanen Isra'ila.
Wannan na nufin dutsen Sinai. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "Dutsen Sinai, Dutsen Yahweh"
ƙungiyan Lewiyawa sun ɗauki akwatin alkawarin sun yi gaba da mutanen Isra'ila a sa'ad da suke tafiya. AT: "Mazaje sun ɗauki akwatain alkawari Yahweh a gaban su a yayin da suna tafiya"
"kowane rana" ko "da rana"
A nan an yi magana game da sanduƙin sai ka ce mutum matafiyi. Mutane ne suke ɗaukan sanduƙin. AT: "Duk sa'ad da mutanen da ke ɗaukan sanduƙin sun fara tafiya"
A nan maganan nan "tashi" roƙo ne zuwa ga Yahweh don ya yi wani abu, saboda haka, a wannan yanayi, Musa na roƙo shi ya watsar da abonkan găban su.
A nan Musa ya yi magana game da, Yahweh ya sa abokan găban su su rabu da mutanen Isra'ila sai ka ce suna guduwa ne daga gaban Yahweh kansa. AT: "Ka sa waɗanda suke maƙiyanka su yi nesa daga sanduƙin da kuma mutanen ka"
A nan an yi magana game da sanduƙin sai ka ce mutum matafiyi. Mutane ne suke ɗaukan sanduƙin. AT: "Duk sa'ad da mutanen da ke ɗaukan sanduƙin sun tsaya"
Wannan na nufin mutanen. An iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "da yawan mutanen dubun dubbai"
1Sai mutanen suka yi kuka game da matsalolinsu Yahweh kuwa yana ji. Yahweh ya ji ya yi fushi. Sai wuta ta fito daga wurin Yahweh ta kama a cikinsu har ta ƙone gefunan wasu bayan wani zangon.2Sai mutanen suka yi kira ga Musa, sai Musa ya yi addu'a ga Yahweh, sai wutar ta mutu.3Aka kira wannan wurin da suna Tabera, saboda wutar Yahweh ta yi ƙuna a wurin.4Sai waɗansu baƙi suka fara sauka a zangon zuriyar Isra'ila. Suka so su ci abinci mai kyau. Daga nan mutanen Isra'ila suka fara kuka suka ce, "Wane ne zai ba mu nama mu ci?5Mun tuna da kifin da muka ci a Masar kyauta, da kukumba da kabewa da albasa da kankana da tafarnuwa.6Yanzu har ma bamu da marmari, saboda wannan mannar kaɗai muke iya gani."7Manna dai tana kama da ƙwayar riɗi. Launinta kuma kamar ƙaro.8Mutanen suka zagaya suka ɗebo ta. Suka niƙa ta a dutse, suka daka ta a turmi, su ka dafa ta a tukwane, suka yi waina da ita. Sai ɗanɗanonta ya zama kamar na sabon man zaitun.9Sa'ad da raɓa ta sauko a kan zangon da dare, manna kuma ta faɗo.10Musa ya ji mutanen suna ta kuka cikin iyalansu, kowanne mutum ya fito ƙofar rumfarsa. Sai Yahweh ya yi fushi ƙwarai, Musa kuwa yana ganin koken-koken nasu bai yi dai-dai ba.11Musa yace da Yahweh, "Me yasa ka yiwa mutanenka mummunan abu haka? Me yasa baka yarda da ni ba? Ka sa na ɗauki nawaiyar mutanen nan dukka.12Ni na ɗauki cikin dukkan mutanen nan? Ni na haife su da zaka ce dani, 'Ka ɗauke su a ƙirjinka kamar yadda uba yake ɗaukar jariri?' Ni zan ɗauke su in kai su ƙasar da ka rantse wa kakaninsu cewa za ka ba su?13A ina zan sami naman da zan ba dukkan mutanen nan? Suna ta kuka a gabana suna cewa, 'Ka bamu nama mu ci.'14Ba zan iya da mutanen nan ba ni kaɗai. Sun yi mani yawa.15Tun da haka kake yi da ni, gara ka kashe ni yanzu--Idan na sami tagomashi a idanunka -- kada ka bari in ga takaicina."16Sai Yahweh yace da Musa, "Ka kawo dattawan Isra'ila guda saba'in a wurina. Ka tabbatar su dattawa ne kuma shugabannin jama'a. Ka kawo su rumfa ta taruwa su tsaya nan tare da kai.17Zan sauko in yi magana da su a can. Zan ɗauka daga Ruhun da yake a kanka in sashi a kansu. Za su ɗauki nawayar mutanen tare da kai. Ba za kayi ta fama da su kai kaɗai ba.18Ka ce da mutanen, 'Ku tsarkake kanku, gama gobe za ku ci nama sosai, gama kun yi kuka kuma Yahweh ya ji. Kun ce, "Wane ne zai ba mu nama mu ci? Gama dã abincinmu ne a Masar." Yahweh zai ba ku nama, kuma za ku ci shi.19Ba wai zaku ci nama yini ɗaya ko biyu ko biyar ko goma ko ma ashirin ba,20amma zaku yi wata guda kuna cin nama har sai ya fito maku a ƙofar hancinku. Sai ya ginshe ku, gama kun ƙi Yahweh, wanda ke cikin ku. Kun yi kuka a gabansa. Kun ce, "Meyasa muka baro Masar""'21Sa'an nan Musa yace, "Mutane 600,000 ne ke tare dani, kuma ka ce, 'Zan ba su nama su yi ta ci har wata guda ɗungum.'22Garkunan shanu dana tumaki za a yanka har ya ƙosar da su?"23Sai Yahweh yace da Musa, "Hannuna ya kasa ne? Yanzu zaka gani ko maganata gaskiya ce ko a'a."24Musa ya fita ya faɗawa mutanen maganar Yahweh. Ya tattara dattawan su saba'in ya sa suka kewaye rumfar.25Yahweh ya zo cikin girgije ya yi magana da Musa. Yahweh ya ɗauka daga cikin Ruhun da yake kan Musa ya sa a kan dattawan su saba'in. Sa'ad da Ruhun ya sauko a kansu, sai suka yi anabci, amma a wannan lokacin ne kaɗai ba su ƙara yi ba kuma.26Sai mutane biyu suka rage a zangon, su ne Eldad da Medad. Su ma Ruhun ya sauko a kansu. An rubuta sunayensu, amma basu fita sun je rumfa ta taruwa ba. Duk da haka, sun yi anabci a cikin zangon.27Wani saurayi ya ruga daga cikin zangon ya gaya wa Musa cewa, Ga Eldad da Medad suna yin anabci a cikin zango."28Sai ɗaya daga cikin zaɓaɓɓun mutanensa Yoshuwa mataimakin Musa, ya ce da Musa, "Shugabana Musa, ka hana su."29Musa yace da shi, "Kana jin kishi saboda ni ne? So na ne dukkan mutanen Yahweh su zama annabawa ya kuma sawa dukkan su Ruhunsa!"30Daga nan sai Musa da dattawan Isra'ila suka koma cikin zango.31Daga nan sai iska ta taso daga wurin Yahweh ta kawo makware daga teku. Suka faɗo kusa da zangon, misalin kusan tafiyar yini ɗaya a wannan sashi, haka kuma a ɗaya sashin. Makwaren suka kewaye zangon wajen kamu ɗaya daga bisa suka kere ƙasa.32Mutanen suka yi ta tara makware a wannan yini dukka da wannan daren dukka da kuma washe gari dukka. Kowanne mutum ya kama makware da yawan gaske. Suka raba makwaren cikin zangon dukka.33Sa'anda naman ke tsakankanin haƙoransu, suna tauna shi, Sai Yahweh ya yi fushi da su. Ya sa wani ciwo mai zafi ya auko masu.34Aka kira sunan wannan wurin Kibrot Hattãba, saboda sun rufe mutanen da suka yi zarin cin nama.35Daga Kibrot Hattãba mutanen suka yi tafiya zuwa Hazerot, suka tsaya a can.
"Yahweh ya aiko da wutar da ta ƙona"
AT: "Sun ba wa wannan wuri suna"
Isra'ilawa sun yi wannan tambaya do gunaguni ne don kuma su nuna cewa suna son wani abu dabam da manna su ci. AT: "Da so shine samu da mu samu nama mu ci."
"ba mu so mu ci" ko "ba za mu ci"
Wannan tsabar na kamar yaji ne in ya bushe.
Wannan wani abu ne mai danƙo da launinta ta kamar rawaye ta ke
Maganan nan "gaban Musa" na wakilcin ra'ayinsa ko tunaninsa. AT: " a ra'ayin Musa"
Musa ya yi kuka ga Yahweh ta wurin yin amfani da tambayoyin ganganci.
Musa ya yi amfani da wannan tambayar don ya yi gunaguni game da yadda Allah ya yi da shi. Ana iya sa wannan cikin magana. AT: "Bai kamata ka yi mummunan abud da ni, bawanka ba" ko "Ni, a matsayin bawan ka ban yi wani abin da ba daidai ba da ya cancanci ka yi mani mummunan abu ba."
An yi magana game da kukar Musa da kuma maganarsa game da shugabancinsa ga mutanen da tanadin da yake yi musu sai ka ce yana ɗauke da kaya ne mai nauyi. AT: "Ka sa na ɗauki alhakin dukkan waɗannan mutanen, amma ta yi mani wuya"
Musa ya yi waɗannan tambayoyin don ya sa Allah ya yi tunani ya kuma hakikance cewa ba Musa ba ne ubansu. AT: "Ni ba uban waaɗannan mutane ba ne. Saboda haka bai kyautu ka ce da ni."
Wannan na nufin cewa ya kamata Musa ya ɗauki alhakin mutanen da ba za su iya lura da kansu ba, daidai kamar yadda iyaye ke lura da jariri.
Ana iya juya wannan tambayar ganganci daidai kamar magana. AT: "Kada ka sa tsammani zan ɗauke su ... ba su" ko "ba zan iya ɗaukan su ... ba su."
Musa ya yi amfani da wannan tambayar don ya nuna cewa ba zai yiwu ya ba wa dukkan waɗannan mutanen nama ba. AT: "Ba zan iya samin isasshen nama da zan ba wa dukkan waɗannan mutanen ba."
Musa ya yi magana game da shugabanta da kuma yi wa mutanen tanaɗi kamar ya ɗauke su ne. AT: "Ni kaɗai ba zan iya yi wa dukkan mutanen nan tanaɗi ba"
Wannan karin magana ne. AT: "Wannan alhakin ya fi karfi na"
"Ruhu" a nan na wakilcin ikon da Ruhun Allah ya ba wa Musa don ya iya yin aikin da Allah ya ba shi ya yi. AT: "kadan daga cikin ikon da Ruhun ya ba ka"
All ya yi magana game da alhaki shugabanci da kuma tanaɗa wa mutanen kamar wata kăya ne Musa da shugabannin za su ɗauka"
Allah ya yi magana game da alhakin shugabanci da tanada wa mutanen sai ka ce wata kãya ne Musa da shugabannin za su ɗauka. AT: "Ba za ka lura da su kai kaɗai ba"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa.
Isra'ilawa sun yi wannan tambaya do gunaguni ne don kuma su nuna cewa suna son wani abu dabam da manna su ci. AT: "Da so shine samu da mu samu nama mu ci."
Ma'ana mai yiwuwa na kamar haka 1) Allah ya yi magana game da amai kamar abincin zata fita ta hancinsu. AT: "har sai kun yi ciwo da amai" ko 2) za su ci sosai har kamar za ta fita ta hancin su. AT: "har sai kun ji kamar za ta fito ta hancin ku."
Mutanen sun yi wannan tambayar don su yi da na sanin da kuma gunaguni. AT: "Da mun sani da ba mu baro Masar ba."
Musa ya yi amfani da waɗannan tambayoyin do ya bayana shakkarsa cewa za a iya samun isasshen nama da zai ciyar da dukkan waɗannan mutanen. AT: "Sai dai mu yanka garken shanu da tumaki mu kuma kama dukkan kifayen da ke cikin tekun don mu ciyar da su!"
A takaice waɗannan maganganu biyun na nufin abu ɗaya. Su na nanata yawan dabbobin ne.
Musa ya zuguiguta wannan don ya nuna bangaskiyar sa cewa ba zai yiwu a tanaɗa wa dukkan mutanen Isra'ila abinci ba.
"ƙosar da su"
A nan "hannu" na wakilcin ikon Allah. Allah ya yi amfani da wannan tambayar don ya tsauta wa Musa don ya yi tunanin cewa Allah ba shi da ikon ya tanaɗa wa mutanen isaschen nama. AT: "Shin, kanan tunanin cewa ba ni da ikon da zan yi wannan?" ko "Ka sani da cewa ina da matuƙar ikon yin wannan."
"maganar Yahweh" na wakilcin abin da Yahweh ya faɗa. AT: "abin da Yahweh ya faɗa"
"Ruhu" a nan na wakilcin ikon da Ruhun Allah ya ba wa Musa. AT: "kadan daga cikin ikon da Ruhun ya ba ka"Dubi yadda ka juya magana makamancin haka cikin 11:16
An yi magana game da ba da iko ga dattawan kamar an sanya ruhu ne a bisan su. AT: "ba wa dattawa saba'in" Dubi yadda ka juya magana makamancin haka cikin 11: 16
An yi magana game da samin iko daga Ruhun kamar Ruhun na zaune a bisan su. AT: "A sa'ad da sun sami kon daga Ruhun"
An yi magana game da ikon da Ruhun ya ba su kamar Ruhun ya sauko a kansu. AT: "Ruhun kuwa ya ba su iko"
AT: "Musa ya rubuta sunayensu a tsarin"
"ka gaya musu su bar yin anabci"
Musa ya yi amfani da wannan tambayar don ya tsauta wa Yoshuwa. AT: "Bai kamata ka yi kishi a maimako na ba"
Ana iya bayana abin da Yoshuwa na kishi a kai a fili. AT: "Shin, kana damuwa ko mai yiwuwa za su .ɗauki abin da ke nawa?" ko "Shin, kana damuwa ko mutanen ba za su martaba iko na ba?"
Musa ya yi magana game da Ruhun zai ba wa mutanen iko kamar Allah zai sa Ruhun sa bisan su. AT: "Ruhun Allah zai ba su dukkan ikon"
karamin tsuntsu
"a kowane farni muɗɗin mutum zai yi tafiya a rana ɗaya"
kamu wata ma'auni ne da ke daidai da santimita 46. AT: "wajen santimita 92" ko "wajen mita ɗaya"
AT: "Kowanne mutum ya tara garwa metan na makware"
Wannan ma'auni ne da yawansa daidai ne da lita 220. AT: "lita 2,220"
A takaice waɗannan maganganu biyun na nufin abu ɗaya. Maganganun na nanata cewa Allah ya hukunta a sa'ad da suke cin naman. AT: "A sa'ad da suke cikin cin naman"
AT: "Sun ba wa wurin suna Kibrot Hattãba"
Wannan sunan wurin ne a jejin.
1Sai ya zama Miriyam da Haruna suka yi gunaguni a kan Musa saboda wata mace Bakushiya da ya aura.2Suka ce, "Kai kaɗai ne Yahweh ya yi magana da kai? Mu ma bai yi magana da mu ba ne?" Sai Yahweh ya ji abin da suka ce.3Musa kuwa mutum ne mai tawali'u, fiye da kowa a duniya.4Nan take Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna da Miriyam: "Ku uku ɗin, ku fito, ku zo rumfa ta taruwa." Sai su uku ɗin suka fito suka je.5Sa'an nan Yahweh ya sauko ta cikin umudin girgije. Ya tsaya a ƙofar rumfa ta taruwa ya kira Haruna da Miriyam. Sai suka matso.6Sai Yahweh yace, "Sa'ad da annabina ke tare da ku, zan bayyana kaina a wurinsa ta wurin ruya in yi magana da shi cikin mafarkai.7Bawana Musa ba haka yake ba. Shi mai aminci ne a cikin dukkan gidana.8Na kan yi magana da shi kai tsaye, ba a zaurance ko da ruya ba. Ya kan ga zatina. Me yasa ba ku ji tsoron yin gunaguni a kan bawana Musa ba?"9Fushin Yahweh ya yi ƙuna a kansu, kana ya bar su.10Girgijen ya tashi daga bisa rumfar, nan da nan Miriyam ta zama kuturwa--ta yi fari kamar auduga. Da Haruna ya juya sai ya ga Miriyam ta zama kuturwa.11Sai Haruna yace da Musa, "Ya shugabana, idan ka yarda kada ka riƙe mu a kan wannan abu. Mun yi magana cikin wawanci, kuma mun yi zunubi.12Idan ka yarda kada ka barta ta zama kamar jaririn da naman jikinsa ya lalace sa'ad da yake fitowa daga cikin mahaifar uwarsa."13Sai Musa ya yi kira zuwa ga Yahweh. Ya ce, "Idan ka yarda ka warkar da ita, Ya Allah, idan ka yarda."14Sai Yahweh yace da Musa, "Idan ubanta ya tofa mata yau a fuska, za a ƙasƙantar da ita har kwana bakwai. Ka rufe ta a bayan zango har kwana bakwai. Bayan haka sai ka dawo da ita."15Haka aka rufe Miriyam har kwana bakwai a bayan zango. Mutanen ba su tafi ba sai da ta dawo zangon.16Bayan haka, mutanen suka tafi daga Hazerot suka yi zango a cikin jejin Faran.
Maryamu da Haruna sun yi amfani da waɗannan tambayoyin don su yi gunaguni cewa Musa yana da iko sosai fiye da su. AT: "Yahweh bai yi magana da Musa kawai ba. Ya yi magana da mu ma."
Kalman nan "yanzu" ya ji na jawo hankali zuwa ga zance mai muhimmanci da ke biye.
An yi amfani da kalman nan "Yanzu" don nuna alama na dakatawa daga ainihin kan labarin. Mai ba da labarin ya yi zance game da halin Musa.
An yi magana game da siffar girgijen sai ka ce wata al'amudi ne. AT: "siffar girgije kamar al'amudi" ko "girgije mai tsayi"
"Ba na magana da Musa kamar haka"
Anan "gida na" na wakilcin Isra'ila. Zama da adalcin cikin gidan Allah na wakilcin zama da adalcin cikin shugabanci Isra'ila. AT: "Musa ya yi adalcin cikin shugabancin mutane na" ko "Na dogara ga Musa ya shugabanci mutanen na Isra'ila"
Yahweh ya yi wannan tambaya don ya tsauta wa Maryamu da Haruna. AT: "Ya kamata ku ji tsoron magana gãba da bawana Musa."
Maganan nan "gãba da Musa" ta bayana a fili cewa shi "bawa" ne wanda Yahweh ke magana.
An yi magana game da fushin Yahweh sai ka ce wuta. AT: "Yahweh ya yi fushi da su"
Kuturtar ya juya fatan Maryamu ya zama fari fat. AT: "zama fari fat"
sa zunubi bisan su na nufin cewa suna da laifin saboda zunubinsu. Anan wannan na nufincewa an hukunta su saboda zunubin su.
Kuturtar Maryamu zai sa jikin ta ya ruɓe har sai ta mutu. An yi maganar ruɓewan kamar cinyewa ne. AT: "Na roƙe ka kada ka bari ta zama kamar matacce wanda rabin jikinta ya ruɓe"
Anan "roƙo" an maimaita ta don nanaci ne.
Wannan na bayana wani abin da zai iya faruwa amma bai faru ba. Tufa yau a fuskar wani ba karamin zagi ba ne.
An yi maganar fid da wani daga zangon da kuma hana shi dawowa cikin, sai ka ce kofa ne da aka kulle a bayanta. AT: "An fid da Maryamu daga zango" ko "An kai Maryamu bayan zangon"
AT: "Musa ya kulle Maryamu a bayan zangon" ko "Musa ya tura ta bayana zangon"
Wannan suna wani wurin ne a hamada. Duba yadda ka juya shi cikin 11:13.
1Sa'an nan Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Ka aiki waɗansu mutane su dubo ƙasar Kan'ana, wadda na ba mutanen Isra'ila. Ka aiki mutum ɗaya daga kowacce kabila ta ubanninsu. Kowanne ya zama shugaba ne a cikinsu."3Musa ya aike su daga jejin Faran, domin su yi biyayya da ummarnin Yahweh. Dukkan su shugabanni ne a cikin mutanen Isra'ila.4Ga sunayensu: daga kabilar Ruben, Shammuya ɗan Zakkur;5daga kabilar Simiyon kuma, Shafat ɗan Hori;6daga kabilar Yahuda, kuma Kaleb ɗan Yefunne;7daga kabilar Issakar kuma, Igal ɗan Yosef;8daga kabilar Ifraim kuma, Hosheya ɗan Nun;9daga kabilar Benyamin kuma, Falti ɗan Rafu;10daga kabilar Zebulun kuma, Gaddiyel ɗan Sodi;11daga kabilar Yosef kuma, (wato daga kabilar Manasse), Gaddi ɗan Susi;12daga kabilar Dan kuma, Ammiyel ɗan Gemalli;13daga kabilar Asha kuma, Shetur ɗan Mikayel;14daga kabilar Naftali kuma, Nãbi ɗan Bofsi;15daga kabilar Gad kuma, Gewuyel ɗan Maki.16Waɗannan su ne sunyen mazajen da Musa ya aika su dubo ƙasar. Musa ya kira Hosheya ɗan Nun da suna Yoshuwa.17Musa ya aike su domin su dubo ƙasar Kan'ana. Ya ce da su, "Ku bi ta Negeb ku hau ta ƙasar kan tudu.18Ku dubo ƙasar ku ga yadda ta ke. Ku yi la'akari da irin mutanen da suke zauna a can, ko suna da ƙarfi ko kuwa raunana ne, kuma ko suna da yawa ko 'yan kaɗan ne.19Ku ga yadda ƙasar ta ke inda suke zaune. Ta na da kyau ko ba ta da kyau? Yaya biranen suke? Kamar zango--zango suke, ko kuwa ƙayatattun birane ne?20Ku gano yadda ƙasar ta ke, ko shuka za ta iya yin girma da kyau ko babu, ko akwai itatuwa ko babu. Ku yi ƙarfin hali ku kawo abin misali daga irin amfanin ƙasar." Lokacin kuwa na nunar fari na inabi ne.21Sai mazajen suka je suka duba ƙasar tun daga jejin Zin zuwa Rehob, kusa da Lebo Hamat.22Suka hau ta Negeb suka ɓullo Hebron. Ahiman da Sheshayi da Talmai, waɗanda jinsinsu ya fito daga Anak, suna nan. Ya zama an gina Hebron shekaru bakwai kafin Zowan ta cikin Masar.23Sa'ad da suka kawo kwarin Eshkol, suka yanki reshe da kurshen zaitun. Suka sagalo shi a jikin sanda tsakanin ƙungiyoyinsu biyu. Suka kawo rumman da ɓaure kuma.24Wannan wurin a ka kira da suna kwarin Eshkol, saboda kurshen zaitun da mutanen Isra'ila suka yanko daga can.25Bayan kwana arba'in, suka dawo daga dubo ƙasar.26Suka dawo wurin Musa da Haruna da dukkan taron jama'ar Isra'ila a cikin jejin Faran a Kadesh. Suka kawo masu labari tare da dukkan jama'a, suka nuna masu irin amfanin ƙasar.27Suka ce da Musa, "Mun kai ƙasar daka aike mu. Gaskiya ne tana zubo da madara da zuma. Ga irin amfanin wurin.28Duk da haka, mutanen da suka yi gidajensu a can ƙarfafa ne. Biranen ƙayatattu ne manya ne kuma. Mun kuma ga kabilar Anak a can.29Amelekawa na zaune a Negeb. Hitiyawa da Yebusawa da Amoriyawa na da gidajensu a ƙasar kan tudu. Kan'aniyawa na zama a bakin teku kusa da Kogin Yodan."30Kaleb ya sa mutanen suka yi shiru a gaban Musa yace, '"Bari mu je mu karɓe ƙasar, gama ba shakka za mu iya cin nasara da ita."31Amma mazajen da suka je tare da shi suka ce, "Ba za mu iya kai wa mutanen nan hari ba domin sun fi mu ƙarfi."32Sai suka kai rahoton karya gwiwa ga mutanen Israila game da ƙasar da suka je suka dubo. Suka ce, "Ƙasar da muka je muka dubo cinye mazauna ƙasar su ke yi. Dukkan mazajen da muka gano a can dogaye ne ƙwarai.33Mun gano jarumawa a can, zuriyar Anak, waɗanda dama jarumawa ne. Idan a ka kwatanta mu da su, mu kamar fara mu ke, haka kuma suka gan mu."
Allah ya shirya cewa kasar Kan'ana zai zama na mutanen Isra'ila amma ba su riga sun shiga cikin ta ba. AT: "wanda na shirya zan ba wa" ko "wanda ba da jimawa ba zan ba"
"Lallai ne kowane mutum da ka aika, ya zama shugaba a tsakanin kabilun"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Anan iya bayana dangantakan Yusufu da Manassa a fili. AT: "daga kabilan Manassa ɗan Yusufu"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Juya waɗannan sunayen mazaje kamar yadda ka yi cikin 13:5
Musa ya yi waɗannan tambayoyin don ya bayyana ko wani irin bayani ne yana so mutanen su kawo masa. AT: "Duba ko kasar na da kyau ko mummuna ne, wanne irin birane ne suke a wurin, ko kuwa waɗancan biranen zango ne kawai, ko suna da garu kewaye da su."
Birane masu garu su na da ganuwa masu karfi kewaye da su don ya tsare su daga abokan gãbansu. Zango ba ta da waɗannan ganuwan.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Kalman nan "Zin" a nan suna ne na jejin da harshen Ibrananci. Ba kalmar "zunubi" bane a turance.
AT: "Kan'anawa sun gina Hebron shekaru 7 kafin Masarawa suka gina Zowan"
Waɗannan su ne sunayen zuriya da aka ambata sunayensu bayan kakaninsu.
Wannan sunan na miji ne.
Wannan sunan wuri ne.
"tsakanin mazaje biyu na kungiyansu"
AT: "Sun ba wa wurin suna"
"bayan kwanaki 40"
Anan "magana" na nufin rohoto. AT: "Sun kawo rohotonsu" ko "Sun ba da rohoton abin da suka gani"
"Hakika madara da zuma na a yalwace a wurin." Sun yi magana game da kyaun kasar don dabbobi da shuke-shuke kamar madara da zuma ne daga waɗannan dabbobin da kuma shuke-shuken suna a yalwace a kasar. AT: "hakika kasa mai kyau ne don kiwon dabbobi da kuma amfanin gona" ko "hakika ta na kasa mai kyau ne don gona"
Da shike madara na samuwa daga shanaye da kuma awaki, wannan na wakilcin dabbobi da kuma abin ci daga dabbobin. AT: "abin ci daga dabbobin"
Da shike zuma na samuwa daga fure, wannan na wakilcin amfanin gona da kuma abin ci daga amfanin gonar. AT: "abin ci daga amfnin gona"
A nan "su" na nufin dukka mazajen da suka bincika ƙasar ban da Kaleb da Joshuwa
A nan "su" na nufin dukka mazajen da suka bincika ƙasar duk da Kaleb da Joshuwa.
Mazajen sun yi magana game da ƙasar ko mutanen ƙasar, mugaye ne sai ka ce ƙasar ta cinye mutanen. AT: "ƙasa ne mai hatsari" ko "ƙasa ne wanda mutanen ta za su kashe mu"
Wannan sunan na miji ne.
A nan gaba na wakilcin ra'ayi. AT: "A na mu ra'ayin ... a na su ra'ayin"
Mazajen suna magana game da fara don su nuna yadda sun dubi kansu in an kwatanta su da mutanen ƙasar. AT: "mu na nan kanana kamar fara in an kwatanta mu da su"
1A wannan daren al'ummar dukka ta yi kuka da ƙarfi.2Dukkan mutanen suka ba Musa da Haruna laifi. Dukkan al'ummar suka ce da su, "Da ma mun mutu a ƙasar Masar, ko nan cikin jeji!3Meyasa Yahweh ya kawo mu wannan ƙasar mu mutu ta wurin takobi? Matayenmu da ƙanananmu za su cutu. Ba zai fi kyau a gare mu mu koma Masar ba?"4Suka cewa junansu, "Bari mu zaɓi wani shugaba, mu koma Masar."5Sai Musa da Haruna suka kwanta a gaban taron mutanen Isra'ila da fuskokinsu a ƙasa.6Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne, waɗanda ke cikin waɗanda aka aika dubo ƙasar, suka tsage tufafinsu.7Suka yi magana da al'ummar mutanen Isra'ila. Suka ce, "Ƙasar da muka ratsa muka dubo muka wuce, ƙasa ce mai kyau ƙwarai.8Idan Yahweh ya ji daɗin mu, zai kai mu cikin wannan ƙasa ya ba mu ita. Ƙasar tana zubowa da madara da zuma.9Amma kada ku bijire wa Yahweh, kuma kada ku ji tsoron mutanen ƙasar, gama su gurasa ne a gare mu. Tsaronsu zai rabu da su, saboda Yahweh na tare da mu. Kada ku ji tsoron su."10Sai dukkan taron suka ce a jejjefe su da duwatsu. Amma sai ga darajar Yahweh ta bayyana ga dukkan mutanen Isra'ila a rumfar taruwa.11Yahweh yace da Musa, "Har yaushe waɗannan mutane za su rena ni? Har yaushe za su kasa gaskatawa dani, su rena dukkan alamu da ikon dana yi a cikin su?12Zan sa annoba ta auko masu, ba za su zama gãdona ba kuma, in sa kabilarka ta zama babbar al'ummar da za ta fi su girma."13Musa yace da Yahweh, "Idan ka yi haka Masarawa za su ji labari, saboda ka kuɓutar da waɗannan mutane da ikonka daga wurinsu.14Za su gaya wa mazaunan wannan ƙasar. Sun ji labarinka, Yahweh, kana tare da waɗannan mutane ne saboda ana ganin ka fuska da fuska. Girgijenka yana tsayawa a bisa mutanenka. Kana tafiya a gabansu da umudin girgije da rana da dare kuwa da umudi na wuta.15Yanzu idan ka kashe mutanen nan kamar mutum ɗaya, sa'an nan al'umman da suka ji labarin jaruntakarka zasu ce,16'Saboda Yahweh ya kăsă kai mutanen nan ƙasar da ya rantse zai ba su, sai ya kashe su a cikin jeji.'17Ina roƙon ka, ka yi amfani da ikonka mai girma. Gama ka ce,18'Yahweh mai jinkirin fushi ne kuma mai yalwar jinƙai. Yakan gafarta mugunta da laifofi. Ba zai yafe mugunta ba sa'ad da ya kawo horon zunubin kakanni a kan zuriyarsu, har zuwa zuriya ta uku da ta huɗu.'19Ka yafe, zunubin mutanen nan, ina roƙon ka, saboda alƙawarin jinƙanka mai girma, kamar yadda kake ta gafarta wa mutanen nan tun daga cikin Masar har zuwa yanzu."20Sai Yahweh yace, "Na yafe masu saboda roƙonka,21amma gaskiya, kamar yadda nake a raye, dukkan duniya zata cika da ɗaukakata,22dukkan mutanen nan da suka ga ɗaukakata da alamu na ikon da na yi a cikin Masar da cikin jeji--har yanzu suna jarabta ta sau goma kenan ba su saurari muryata ba.23Babu shakka ba za su ga wannan ƙasar da nayi wa ubanninsu alƙawari ba. Waɗannan da suka rena ni ba ko ɗaya a cikin su da zai gan ta,24sai bawana Kaleb kaɗai, saboda da ruhunsa daban yake. Ya bini da gaske; zan kai shi ƙasar da ya je ya dubo. Zuriyarsa zasu gaje ta.25(To Amelikawa da Kan'aniyawa suna zaune a cikin kwari.) Gobe ka juya ka tafi jejin ka bi ta Teku na Iwa."26Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna. Ya ce,27"Har yaushe zan jure da muguntar mutanen nan da suke ta ganin laifina? Na ji gunagunin mutanen Isra'ila game da ni.28Ka ce da su, 'Yahweh yace, 'kamar yadda nike a raye, 'kamar yadda kuka yi magana ina ji, ga abin da zan yi ma ku:29Dukkan ku da kuka yi gunaguni a kaina zaku mutu a cikin jeji, ku da aka ƙirga cikin lissafi, dukkan ma su shekara ashirin zuwa gaba.30Babu shakka ba zaku shiga ƙasar dana yi alƙawari zan yi maku gida ba. Sai dai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.31Amma ƙanananku da kuka ce abin zai shafe su, su zan kai cikin ƙasar. Za su ji yadda ƙasar da kuka ƙi ta ke!32Ku kuwa jikkunanku za su faɗi su mutu a cikin jeji.33'Ya'yanku za su zama makiyaya a cikin jeji har shekara arba'in. Dole ne za su sha sakamakon aikinku na bijirewa a cikin jeji har sai gawarwakinku sun ƙare.34Kamar yadda kuka yi kwana arba'in kuna dubo ƙasar, Haka zaku yi shekara arba'in kuna ɗaukar alhakin zunubanku-- kowanne kwana ɗaya a matsayin shekara ɗaya, zaku gane abin da zai faru da ku idan na yi găba da ku.35Ni, Yahweh ne na faɗa. Babu shakka haka zan yi wa wannan al'umma mai mugunta da suka haɗa kai gãba dani. Za a datse su gaba ɗaya, a nan za su mutu."36Haka mazajen da Musa ya aika su gewayo ƙasar, waɗanda suka dawo suka kawo rahoton da ya sa dukkan taron jama'a suka yi gunaguni a kan Musa game da ƙasar--37Waɗan nan mazaje da suka kawo rahoto marar daɗi aka hallaka su da annoba daga wurin Yahweh suka mutu.38A cikin mazajen da suka gewaya ƙasar, Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne ne kaɗai suka rage da rai.39Sa'ad da Musa ya bada wannan rahota ga mutanen Isra'ila dukka, sai suka yi baƙinciki ƙwarai.40Suka fita tun da sassafe suka hau bisa kan tsauni suka ce, "Dubã, ga mu nan, kuma za mu tafi wurin da Yahweh ya yi alƙawari, gama mun yi zunubi."41Amma Musa yace, "Meyasa kuke wulakanta ummarnin Yahweh? Ba za ku yi nasara ba.42Kada ku tafi, saboda Yahweh ba ya tare da ku, domin ya kare ku, don kada abokan gãbarku su yi nasara a kanku ba.43Su Amelekawa da Kan'aniyawa suna can, kun zo ku mutu da kaifin takobi saboda kun dena bin Yahweh. Saboda haka ba zai kasance tare da ku ba."44Amma sai suka yi taurin kai suka tafi ƙasar kan tudu; amma kuma, ko Musa ko akwatin alƙawarin Yahweh ba wanda ya bar zangon.45Sai Amelekawa suka sauko, Kan'aniyawa ma suka sauko daga tuddai. Suka kai hari a kan Isra'ilawa suka kuma ci nasara a kansu har zuwa Horma.
Mutanen sun yi wannan tambayar don su yi gunguni ne don kuma su zargi Yahweh cewa ba yi musu abu mai kyau ba. AT: "Bai kamata Yahweh ya kawo mu wannan ƙasar don kawai mu mutu ta wurin takobi ba."
A nan, "takobi" na wakilcin kisa tawurin takobi ko kuwa wurin yaƙi. AT: "mutu sa'ad da mutanen sun kai mana hari da takobi" ko "mutu cikin yaƙi"
Mutanen sun yi amfani da wannan tambay don su karfafa mutane su yarda cewa zai fi musu su koma Masar. Ana iya juya wannan cikin magana. AT: "zai fi mana mu koma Masar da mu yi ƙoƙarin cin Kan'ana da yaƙi."
Wannan na nufin mutanen Isra'ila.
"kwanta ƙasa fuskokinsu na taɓa ƙasa." Musa da Haruna sun yi wannan don su nuna cewa sun kaskantar da kansu a gaban Allah. Sun ji tsoron ko mai yiwuwa Allah zai hukunta mutanen don sun yi masa tawaye. AT: "kwanta fuskokinsu ƙasa cikin kaskanci ga Allah" ko "kwanta fuskokinsu ƙasa don su yi addu'a ga Allah"
Waɗannan sunayen maza ne.
AT: "waɗanda ke cikin waɗanda Musa ya aika"
Yage tufafin alamace da cewa mutum na cikin damuwa kuma yana makoki.
Sun yi magana game kyau ƙasar don dabbobi da shuke-shuke kamar madara da zuma da ke samuwa tawurin waɗannan dabbobin da fure. Dubi yadda ka juya wannan cikin 13:27. AT: "na da kyau don kiwon dabbobi da kuma shuki" ko "ƙasa ce mai ni'ima ƙwarai da gaske"
Yeshuwa da Kaleb sun cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Yeshuwa da Kaleb sun yi magana game da hallaka abokan gãbansu kamar za su cinye su.
AT: "Yawe zai cire abin da ke tsaron su"
Wannan na nufin duk wanda ko juwa duk abin da ke tsaron su. AT: "Duk wanda zai tsare su"
Yawe ya yi amfani da waɗannan tambayoyi don ya nuna cewa ya yi fushi ya kuma ƙãsa hakuri da mutanen. AT: "Tun da jimawa mutanen na sun rena nu. Sun kasa dogara a gare ni tun da jimawa, sun yi wasi da dukka alamun ... su."
"ba za su zama mutane na kuma ba." Mai yiwuwa wannan na nufin cewa shi zai hallaka su, kuma wasu juyi sun juya shi a hakan.
A nan "ka" na nufin Musa
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) Musa ya yi magana game da Allah ya bayyana kansa ga mutanensa kamar Allah ya barsu su ga fuskars. AT: "sun gan ka" ko 2) Musa ya yi magana game da dagantakarsa da Allah kamar cewa Musa ya ga fuskar Allah a sa'ad da ya yi magana da shi. AT: "ya yi mgana da ni"
An yi magana game da kisan da aka yi musu kamar kisan mutum ɗaya ne. AT: "dukkansu a lokaci ɗaya"
"hakika ba zai yafe wa mutane masu laifi ba." tsarkake mutane daga zunubansu wata salon magana ne na rashin yi musu hukunci. Allah ba zai yafe zunuban mutane masu laifi ba. AT: "Zai hukunta masu laifi a kullayomi"
An yi magana game da hukunci ga mutanen kamar hukunci wani abu ne da za a iya kawowa a sanya a bisa mutane. AT: "sa'ad da ya hukunta laifin zuriyar mutanen don zunuban mutanen"
AT: "ɗaukaka ta zata cikai dukka duniya"
"sun cigaba da jaraba ni"
A nan 10 na wakilcin sau da yawa. AT: "sau da yawa"
A nan "kassa kunne" na nufin biyayya. Muryar Allah kuma na wakilcin abin da ya faɗa. AT: "ba su yi biyayya ga abin da na faɗa ba"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa.
A nan "ruhu" na wakilcin halinsa. Kaleb yana shirye ya yi biyayya ga Allah. Ana iya bayana halinsa a fili. AT: "domin yana da hali dabam" ko "domin yana shirye ya yi biyayya ga Allah" (Duba: and )
Yahweh ya yi wannan tambaya domin ya yi fushi ne da mutanen. AT: "Na yi haukuri da wannan mugayen jama'a na sawon lokaci."
AT: "Na ji gunagunin mutanen Isra'ila"
...
Jikunansu za su faɗi su mutu na wakilcin mututwarsu. AT: "za ku mutu"
AT: "Ku da Musa ya kiɗaya ku cikin lissafi"
"daga mai shekara ashirin zuwa fiye"
jikunansu za su faɗi su mutu na wakilcin mutuwarsu. AT: "za ku mutu"
Wasu juyi sun zaɓa su juya shi haka " 'Ya'yanku za su yi yawo a jeji." Dalili kuwa ita ce a zamanin dã, makiyaya su kan yi yawo zuwa wurare daban-dabam domin dabbobi da garkensu su sami abinci.
"Lallai ne su sha wahala saboda sakamakon aikinku" ko "Lallai su sha wahala saboda aikinku"
ƙarshen gawakinsu na wakilcin mutuwar na ƙarshe daga cikinsu. AT: "har sai na ƙarshe daga cikinku ya mutu" ko "har sai dukkanku kun mutu"
"sha wahala saboda zunubanku"
Maiyiwuwa wannan na nufin ba za su sake rayuwa ba. AT: "za su kai ga ƙarshensu" ko "za a hallaka su"
An sãke sarafa zancen da ke cikin 14:36 domin a iya fahimtar ma'anarsa a saukake.
"ta wurin anoba suka mutu a gabansa." Saboda ance sun mutu a gabansa, wannan na nufin cewa ya sa sun mutu. AT: "mutu a gaban Yahweh ta wurin annoba da ya sa"
Kalman nan "Duba" na ƙara nanata abin da ke a gaba ne. "haƙika"
Musa ya yi wannan tambaya don ya tsauta wa mutanen Isra'ila. AT: "Kada ku karya umurnin Yahweh kuma."
An yi magana game da yin musu taikmako daidai kamar zama tare da su. AT: "Yahweh ba zai taimake ku ba"
AT: "kãre abokan gãbanku ga yin nasara da ku" ko " ya ba ku nasara bisan abokan gãbanku"
A nan, "takobi" na nufin yaƙi. AT: "za ku mutu a yaƙi" ko "za su karkashe ku sa'ad da ku ke yaƙi da su"
An yi magana game da yi wa Yahweh biyayya kamar binsa, an kuma yi magana game da yin masa rashin biyayya kamar an juya masa baya. AT: "kun bar yi wa Yahweh biyayya" ko "kun shirya cewa ba za ku yi wa Yahweh biyayya ba"
An yi magana game da yi musu taimako kamar zama tare da su. AT: "ba zai taimake ku ba"
kodashike Allah bai amince ba, amma suka yi taurin ka har suka tafi cikin ƙasar kan tuɗu"
Yawanci ƙasar Isra'ila na saman tuɗu. Lokacin da Isra'ilawa sun ƙetare kogin Urdun don su kai wa Kan'anawa hari, akwai tuɗɗai da za su hau domin su shiga cikin Kan'ana.
1Sai Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Kayi magana da mutanen Isra'ila ka ce dasu, 'Sa'ad da kuka shiga ƙasar da zaku zauna, wadda Yahweh zai ba ku,3sai ku shirya baiko da wuta domin Yahweh, ko baiko na ƙonawa ko hadaya domin a cika alƙawarin baiko na yardar rai, ko baiko na idodinku, domin ku kawowa Yahweh baiko na ƙamshi mai daɗi daga garkenku ko daga dangwalinku.4Dole ku kawo wa Yahweh baiko na ƙonawa da baiko na gari da hadaya ta sha ta gari mai kyau wanda aka gauraya da mai kwalba bakwai.5Kuma za ku haɗa baiko na ƙonawar ko hadayar da ruwan inabi saboda sha domin kowanne ɗan rago.6Idan rago ne ake miƙawa, sai kuma a shirya baiko na gari awo uku wanda aka gauraya da mai kwalba biyar.7Domin baiko na sha kuwa sai a bada ruwan inabi kwalba biyar. Zai bada ƙanshi mai daɗi ga Yahweh.8Idan kuka shiya bijimi domin baiko na ƙonawa ko hadaya domin ku cika alƙawari, ko baiko na zumunci ga Yahweh,9sai ku miƙa bijimin tare da baiko na hatsi, gari mai kyau awo uku wanda aka gauraya da mai kwalba biyu.10Dole kuma ku ba da baiko na ruwan inabi kwalba biyu, baikon da aka yi da wuta, da zai bada ƙanshi mai daɗi ga Yahweh.11Haka za ayi wa kowanne bijimi da kowanne rago da kowanne ɗan rago da 'yan awaki.12Kowacce hadaya za ku shirya ku miƙa haka za ku yi ta kamar yadda aka bayyana a nan.13Dukkan 'yan ƙasa da aka haifa a Isra'ila haka za su yi waɗannan abubuwa, sa'adda wani ya kawo baikon da za ayi da wuta, domin ya kawo ƙanshin da zai gamshi Yahweh.14Idan baƙo na zaune wurinku, ko duk wanda zai zauna a cikin ku a dukkan zamanin mutanenku, dole ne ya yi baikon da za ayi da wuta domin ya bada ƙanshi mai daɗi ga Yahweh. Dole ne shi ma ya yi kamar yadda kuke yi.15Dokar da ta shafi taron jama'arku ita ce za ta shafi baƙon da yake zaune a wurinku, wannan zaunanniyar doka ce gare ku dukkan zamanin jama'arku. Kamar yadda kuke haka ma wanda ya zo wurin ku zai zama. Dole ne ya yi kamar yadda kuke yi a gaban Yahweh.16Doka da ka'idar da ta shafe ku ita ce kuma za ta shafi baƙon da yake tare da ku.'"17Yahweh ya sake yin magana da Musa. Ya ce,18"Ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce da su, 'Idan kuka zo ƙasar da zan kai ku,19idan kuka ci abincin da aka yi a ƙasar, sai ku yi baiko ku miƙa shi gare ni.20Cikin abin da za ku fara ɓarzawa sai ku yi dunƙule da shi ku ɗaga shi kamar baiko na ɗagawa a masussuka. Ga yadda za ku ɗaga shi.21Daga abin da kuka ɓarza da fari sai ku yi bayarwa ta ɗagawa a dukkan zamanin mutanenku.22Wani lokaci za ku yi zunubi ba tare da saninku ba, idan ba ku yi biyayya da dukkan umarnin dana gaya wa Musa ba--23dukkan abin dana umarce ku ta wurin Musa tun daga ranar dana fara baku umarni har zuwa zamanin mutanenku dukka.24A lamarin zunubin da aka yi ba tare da niyya ba kuma jama'a ba su sani ba, sai dukkan jama'a kowa ya yi baiko na ƙonawa da bijimi domin ya bada shessheƙi na ƙanshi mai daɗi ga Yahweh. Tare da wannan sai a yi baiko na hatsi dana sha, kamar yadda aka umarta a ka'idodi, da baiko na ɗan akuya ɗaya domin baiko na zunubi.25Sai firist ya yi kafara domin dukkan taron jama'ar Isra'ila. Za a gafarta masu saboda zunubin kuskure ne. Sun kawo hadayarsu, baikon da aka yi da wuta zuwa gare ni. Sun kawo baiko na zunubi gare ni gama kuskure ne.26Sa'an nan za a gafartawa dukkan taron jama'ar Isra'ila, da dukkan baƙin da suke zaune tare da su, saboda dukkan taron jama'ar sun yi zunubin ba tare da sanin su ba,27Idan wani mutum ya yi zunubi cikin rashin sani, sai ya miƙa baiko na ɗan akuya bana ɗaya saboda zunubinsa.28Sai firist ya yi kafara a gaban Yahweh saboda mutumin da ya yi zunubi ba tare da saninsa ba. Idan aka yi kafara za a gafarta wa wannan mutum.29Sai ku kasance da doka iri ɗaya ga duk wanda ya yi wani abu ba tare da saninsa ba. Doka ɗaya da ta shafi ɗan ƙasa da aka haifa a Isar'ila ita ce kuma za ta shafi baƙin dake zaune a cikin su.30Amma idan mutum ya yi ba dai--dai ba cikin sanin sa, ko ɗan ƙasa ne ko baƙo, ya yi mani zunubi. Wannan mutum za a datse shi daga cikin mutanensa.31Saboda ya rena maganata ya karya dokokina, wannan mutum za a datse shi sarai. Zunubinsa zai zauna a kansa.32Sa'ad da mutanen Isra'ila ke a cikin jeji, sai suka tarar da wani mutum na tattara itace ranar Asabaci.33Waɗanda suka tarar da shi suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukkan taron jama'ar Isra'ila.34Sai suka sa shi a cikin kurkuku saboda ba a yanke abin da za a yi masa ba.35Sa'an nan Yahweh yace da Musa, "Sai a kashe wannan mutum. A kai shi bayan zango, dukkan jama'a su jejjefe shi da duwatsu.36Haka dukkan jama'ar suka kawo shi bayan zango suka jejjefe shi da duwatsu har ya mutu kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.37Yahweh ya sake yin magana da Musa. Ya ce,38"Kayi magana da 'ya'yan Isra'ila ka umarce su da su yi tutoci su maƙala a kafaɗun rigunansu, su maƙala su a kowacce kafaɗa da shuɗin zare. Za su yi haka a dukkan zamanin mutanensu.39Idan kuka dube su za su zama abin tunawa da dukkan dokokina na musamman a gare ku. Ku ɗauke su a wurinku domin kada ku dubi zuciyarku da idanunku ku yi karuwanci da su.40Ku yi wannan domin ku tuna ku yi biyayya da dukkan dokokina, kuma domin ku zama da tsarki, keɓaɓɓu domina Allahnku.41Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito da ku daga ƙasar Masar, ya zama Allahnku. Ni ne Yahweh Allahnku."
Littafin Kiɗaya 15:1-32 ta yi magana game da abin da Allah ya gaya wa Musa ya faɗa wa mutanen Isra'ila.
"don ba da ƙanshi daga cikin garken ko babbobin, mai daɗi ga Yahweh." Jin daɗi ga Ubangiji saboda ƙanshi na wakilcin farincikinsa da mutumin da ya ƙona hadayar. AT: "don a faranta wa Yahweh rai ta wurin ƙona hadaya daga cikin garken ko dabbobin"
Wannan na nufin baiko da aka yi magana a kai cikin 15:4.
AT: "kusan lita 2" ko "lita biyu"
kusan lita 3.7. AT: "kusan lita 1" ko kuwa "lita ɗaya"
Humushi wata ma'auni ne da ke daidai da lita 22. AT: "lita 4" ko "lita huɗu da rabi"
AT: "lita ɗaya"
"Zai ba da ƙanshi wanda zai faranta wa Yawe rai." Jin daɗin da Ubangiji zai ji saboda ƙanshin na wakilcin farin cikin sa da mutumin da ya ƙona hadayar. AT: "Za ku faranta wa Yawe rai ta wurin miƙa shi"
Za a iya juya wannan zuwa ma'aunin wannan zamani. AT: "lita shida da rabi"
AT: "da kuka ƙona a kan bagadi"
"Zai ba da ƙanshi wanda zai faranta wa Yawe rai." An yi magana game da jin daɗin da Ubangiji zai ji saboda mutumin da ya yi masa sujada da zuciya ɗaya ya kuma miƙa hadaya kamar Allah ya ji daɗin ƙanshi hadayar. AT: "ku faranta wa Yawe rai ta wurin miƙa shi"
AT: "lallai ne ku yi shi"
AT: "lallai ne ku yi shi kamar yadda na bayana"
AT: "da suka ƙona a kan bagadi"
"ba da ƙanshi wanda zai faranta wa Yawe rai." An yi magana game da jin daɗin da Ubangiji zai ji saboda mutumin da ya yi masa sujada da zuciya ɗaya ya kuma miƙa hadaya kamar Allah ya ji daɗin ƙanshi hadayar. AT: "ku faranta wa Yawe rai ta wurin miƙa shi"
AT: "lallai ne ya ƙona hadaya a kan bagadin"
"ba da ƙanshi wanda zai faranta wa Yawe rai." An yi magana game da jin daɗin da Ubangiji zai ji saboda mutumin da ya yi masa sujada da zuciya ɗaya ya kuma miƙa hadaya kamar Allah ya ji daɗin ƙanshi hadayar. AT: "ku faranta wa Yawe rai ta wurin miƙa shi"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) Ku da waɗanda suke zama tare da ku, ku ɗaya ne a gaban Yawe" ko 2) "Dokar ya shafe ku da masu tafiya da ku"
"Lallai ne ya yi kamar yadda ku ke yi a gaban Yawe" Domin an ce lallai ne su yi kamar yadda Isra'ilawa suke yi a gaban Yawe, wannan na nufin cewa lallai ne su yi biyayya ga dukkan umurnin Yawe. AT: "lallai ne ya yi daidai kamar yadda kuke yi, ya kuma yi biyayya ga dukka umurnin Yawe"
AT: "abincin da ƙasar ta ba da amfanin" ko "abincin da kuka samu a ƙasar"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) hatsi na fari da za su tara a lokacin girbi ko 2) gari da ya su yi daga hatsin su na fari.
Da shike an kira shi dunƙule, wannan na nufin cewa da farko za su dafa garin.
Wannan karin magana "daga shi sama" na nufin miƙa shi a matsayin kyauta. AT: "miƙa shi a matsayi kyauta"
An yi magana game da baikon kamar daga masussuka domin wannan ita ce wurin da ake casan hatsin.
Allah ya cigaba da gaya wa Musa abin da lallai ye ya gaya wa mutanen.
Kalman nan "ku" na nufin mutanen Isra'ila.
"ba da ƙanshi wanda zai faranta wa Yawe rai." An yi magana game da jin daɗin da Ubangiji zai ji saboda mutumin da ya yi masa sujada da zuciya ɗaya ya kuma miƙa hadaya kamar Allah ya ji daɗin ƙanshi hadayar. AT: "a faranta wa Yawe rai ta wurin ƙona shi"
AT: "lallai ne ku yi hadayar hatsi da hadaya sha"
AT: "kamar yadda ka'idar ta ummurta" ko "kamar yadda na ummurta lokacin da yi ka'idar"
AT: "Zan yafe musu"
AT: "da suka yi da wuta" ko "da suka ƙona a kan bagadi"
AT: "Zan yafe wa dukkan jama'ar Isra'ila"
"'yar akiya bana 1"
AT: "Zan yafe wa mutumin sa'ad da firist ya yi kafara"
Maganan nan "kore shi" na da ma'ana uku masu yiwuwa. 1) lallai ne mutanensa su kore shi" ko kuwa 2) "ba zan maishe shi a matsayin ɗaya daga cikin mutanen Isra'ila" ko 3) "lallai ne mutanensa su kashe shi"
An yi magana game da biyayya ga doka kamar an karya ta. AT: "ya yi rashin biyayya ga ummurni na" ko "bai yi biyayya ga abin da na ummurta ba"
A nan "zunubi" na wakilcin 1) hukunci domin zunubi ko 2) laifin wannan zunubi. Zunubi na kansa, wata karin magana ce. 1) a hukunta shi ko 2) zama mai laifi. AT: "zan hukunta shi saboda da zunubinsa" ko 2) "zan maishe shi mai laifin"
AT: "Yawe bai faɗa abin da za su yi da shi ba"
AT: "lallai ne ku kashe mutumin" ko "Lallai ne mutumin ya mutu"
Isra'ila wata suna ne kuma na Yakub. Mutanen Isra'ila zuriyarsa ne. AT: "mutanen Isra'ila"
...
"dubi" a nan na nufin tunani game da. zuciya na wakilcin abin da mutum ke so, idanu kuma na wakilcin abin da mutum ya gani kuma yana so. AT: "don kada ku yi tunani game da duk abin da kuke so"
An yi magana game da zama da rashi aminci ga Allah ta wurin yin duk abin suke so sai ka ce su mataye da ke wa maigidansu rashin aminci ta wurin dangantaka da sauran maza. Ana iya bayana a fili cewa wannan abin kunya ne. AT: "abin kunya ta wurin yi mini rashin aminci" ko "yi waɗannan abubuwa maimakon yin mini biyayya"
Allaha ya cigaba da gaya wa Musa abin da zai gaya wa mutanen Isra'ila. Kalman nan "ku" na nufin mutanen.
An sake faɗin wannan magana don nanaci.
1Ana nan sai Korah ɗan Izhar ɗan Kohat ɗan Lawi, tare da Datan da Abiram 'ya'yan Eliyab da On ɗan Felet, zuriyar Ruben, suka taru da waɗansu mutane.2Suka tayar wa Musa, tare da waɗansu daga cikin mutanen Isra'ila, su ɗari biyu da hamsin shugabannin jama'a sanannu sosai a cikin jama'a.3Suka tattaro kansu domin su fuskanci Musa da Haruna. Suka ce da su, "Fankamarku ta yi yawa! Dukkan mutanen keɓaɓɓu ne, kowanne ɗayan su, kuma Yahweh na tare da su. Meyasa kuke ɗaukaka kanku fiye da sauran mutanen Yahweh?"4Sa'ad da Musa ya ji haka, sai ya kwanta da fuskarsa ƙasa.5Ya yi magana da Korah da dukkan waɗanda ke tare da shi, "Gobe da safe Yahweh zai nuna wanda ke nasa, da wanda ya keɓe domin kansa. Zai kawo wannan mutum kusa da shi. Zai kawo wanda ya zaɓa kusa da shi.6Korah, kai da ƙungiyarka ga abin da za ku yi.7Gobe ku ɗauki turare ku sa wuta a gaban Yahweh. Wanda Yahweh ya zaɓa, zai zama keɓaɓɓe na Yahweh. Fankamarku ta yi yawa, ku 'ya'yan Lebi."8Musa ya ƙara cewa da Korah, "Ka saurara, kai zuriyar Lebi:9ƙaramin abu ne a wurin ka da Allah na Isra'ila ya keɓe ka daga cikin mutanen Isra'ila, ya kawo ka kusa da shi, domin ka yi aiki cikin alfarwar Yahweh, kuma ka tsaya a gaban jama'a ka yi masu hidima?10Ya kawo ku kusa da dukkan 'ya'uwanka, zuriyar Lebi, tare da kai, kuma kana nema ka zama firist!11Wannan ne yasa kai da ƙungiyarka kuka taru ku yiwa Yahweh tayarwa. Meyasa kake gunaguni a kan Haruna, wanda ya yi biyayya da Yahweh?"12Sai Musa ya kira Datan da Abiram, 'ya'yan Eliyab, amma suka ce, "Ba za mu hawo ba.13Ƙaramin abu kayi daka fito da mu daga ƙasa mai zubo da madara da zuma, ka kashe mu a cikin jeji? Yanzu kana so ka maida kanka mai mulki a kan mu!14Bugu da ƙari, baka kai mu ƙasar dake zubowa da madara da zuma ba, ko ka bamu gonaki da lambuna su zama gadonmu. Yanzu kana so ka makantar da mu da alƙawuran wofi? Ba zamu zo wurin ka ba."15Musa ya yi fushi ƙwarai ya ce da Yahweh, "Kada ka karɓi baikonsu. Ban ɗauki ko jaki ɗaya daga wurin su ba, kuma ban ji wa ko ɗaya a cikin su ba.16Sa'an nan Musa yace da Korah, "Gobe kai da mutanenka za ku je gaban Yahweh--kai da su, da Haruna.17Kowannen ku ya ɗauki tasa ya sa turare a ciki. Kuma dole kowanne mutum ya kawo tasarsa gaban Yahweh, tasoshi ɗari biyu da hamsin. Kai da Haruna kuma kowa ya kawo tasarsa,"18Sai kowanne mutum ya ɗauki tasarsa, yasa wuta a ciki, yasa turare a cikin ta, suka tsaitsaya a ƙofar rumfa ta taruwa tare da Musa da Haruna.19Sai Korah kuma ya tattara dukkan mutanen da suke tayarwa Musa da Haruna a ƙofar rumfa ta taruwa, sai ɗaukakar Yahweh ta bayyana ga dukkan jama'a.20Sa'an nan Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna:21"Ku ware kanku daga cikin wannan taron domin in hallaka su yanzun nan."22Musa da Haruna suka kwanta da fuskokinsu a ƙasa suka ce, "Ya Allah, Allah na ruhohin dukkan mutane, idan mutum ɗaya ya yi zunubi, ka yi fushi da dukkan mutane?"23Yahweh ya amsa wa Musa. Ya ce,24"Ka faɗawa taron jama'ar. Ka ce, 'Ku gudu daga rumfar Kora da Datan da Abiram."'25Sai Musa ya tashi ya je wurin Datan da Abiram; dattawan Isra'ila suka bi shi.26Ya yi magana da taron ya ce, "Sai ku gudu daga rumfunan waɗannan mugayen mutane kada ku taɓa kome nasu."Idan ba haka ba zunubinsu zai cinye ku dukka."27Haka jama'ar dake cikin rumfunan su Korah da Datan da Abiram suka rabu da su. Datan da Abiram suka fito suka tsaya a ƙofar rumfunansu, tare da matansu da 'ya'yansu da ƙananansu.28Sa'an nan Musa yace, "Ta wurin wannan za ku sani Yahweh ne ya aiko ni in yi dukkan waɗannan ayyuka, gama ba domin kaina nake yin su ba.29Idan mutanen nan suka yi mutuwa irin ta kowanne mutum, kamar yadda abu yakan sami kowanne mutum, ba Yahweh ne ya aiko ni ba.30Amma idan Yahweh ya halitto wani sabon abu, idan ƙasa ta buɗe bakinta ta haɗiye su, tare da dukkan abin da suke da shi, suka tafi cikin lahira da rai, sa'an nan za ku gane waɗannan mutane sun rena Yahweh."31Da dai Musa ya gama faɗin wannan magana, ƙasa ta buɗe a ƙarƙashin waɗannan mutane.32Ƙasa ta buɗe bakinta ta haɗiye su, da iyalinsu da dukkan jama'ar dake na Korah, tare da dukkan abin da suka mallaka.33Haka su da dukkan abin da suka mallaka suka tafi lahira da ransu. Ƙasa ta rufe a kan su, suka lalace daga wurin taron jama'a.34Dukkan mutanen Isra'ila dake kewaye da su suka gudu daga biranensu. Suka yi kururuwa, watakila mu ma ƙasa za ta haɗiye mu!"35Sa'an nan wuta ta walƙato daga wurin Yahweh ta haɗiye mutane 250 da suka miƙa turare.36Yahweh ya ƙara yin magana da Musa ya ce,37Ka yi magana da Eliyeza ɗan Haruna firist bari ya ɗauke tasoshin daga cikin wuta, gama tasoshin keɓaɓɓu ne a gare ni. Sa'an nan ya barbaza garwashin daga nesa.38Ɗauke tasoshin waɗanda suka rasa rayukansu saboda zunubinsu. A bubbuge su su zama marfin bagadinsu. Waɗancan mutanen sun miƙa su a gabana, don haka sun zama keɓaɓɓu a gare ni. Za su zama alamar kasancewata ga mutanen Isra'ila."39Sai Eliyeza firist ya ɗauki tasoshi na tagulla da mutanen da suka ƙone suka yi amfani da su, aka bubbuga su, suka zama marfin bagadin,40domin su zama abin tunawa ga mutanen Isra'ila, domin ya zama ba wani baƙo wanda ba a cikin kabilar Haruna yake ba da zai zo ya ƙona turure a gaban Yahweh, domin kada su zama kamar Korah da ƙungiyarsa--kamar yadda Yahweh ya bada umarni ta wurin Musa.41Amma da safiya ta yi sai dukkan taron jama'ar suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna. Suka ce, "Kun kashe mutanen Yahweh."42Sai ya zama, sa'ad da mutanen suka taru gãba da Musa da Haruna, da suka duba wajen rumfa ta taruwa, duba sai gashi girgije ya rufe ta. Darajar Yahweh ta bayyana,43sai Musa da Haruna suka zo gaban rumfar ta taruwa.44Sa'an nan Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,45"Ka gudu daga gaban wannan taron domin in hallaka su yanzu--yanzu." Sai Musa da Haruna suka kwanta da fuskokinsu a ƙasa.46Musa yace da Haruna, "Ka ɗauki tasa, ka sa wuta a ciki ba a kan bagadin ba, ka sa turare a cikin ta, ka kai ta wurin taron jama'ar, da sauri ka yi kafara saboda su, saboda fushi na zuwa daga wurin Yahweh. Annobar ta fara."47Sai Haruna ya yi kamar yadda Musa ya ummurce shi. Ya ruga cikin tsakiyar taron jama'ar. Annobar ta fara bazuwa a cikin mutanen, sai ya sa turaren a ciki ya yi kafara saboda mutanen.48Haruna ya tsaya a tsakanin matattu da masu rai; ta haka annobar ta tsaya.49Waɗanda annobar ta kashe sun kai 14,700, ban da waɗanda suka mutu cikin lamarin Korah.50Haruna ya dawo wurin Musa a ƙofar rumfa ta taruwa, sai annobar ta ƙare.
Juya wannan sunan mazan daidai kamar yadda ka yi cikin 3:17.
An yi magana game da yin tawaye ko zargi ga wanda ke mulki kamar suna tsaye da shirin faɗa. AT: "tayar wa Musa"
"250"
sanannun mutane cikin jama'a- "sanannen mutane na jama'a" ko "muhimman mazaje cikin jama'an"
Wannan na wakilcin yin fiye da yakamata. AT: "Kã yi fiye da yadda ya kamata" ko "Kã sammaci cewa kana da iko fiye da yadda ya kamata"
Mazajen su yi wannan tambaya don su tsauta wa Musa da Haruna. AT: "Ba daidai ne ka ɗauke kanka fiye da sauran jama'an Yahweh."
An yi magana game da ɗaukan wani da muhimmanci sai ka ce an daga shi sama. AT: "duba kanka da muhimmanci fiye da sauran"
Wannan na nuna cewa Musa ya kaskantar da kansa a gaban Allah. Ya ji tsoron cewa Allah zai hukunta mutanen don sun tayar wa Allah da kuma shugabannen da ya zaɓa.
AT: "wanda Yahweh ya keɓe don kansa"
Musa ya cigaba da magana da Kora da mutanen da ke tare da Kora.
...
Wannan karin magana nen. AT: "a gaban Yahweh"
AT: "Yahweh zai keɓe mutumin don kansa"
Wannan na wakilcin yin fiye da yadda ya kamata. AT: "Ka yi fiye da yadda ya kamata" ko "Kã sammaci cewa kana da iko fiye da yadda ya kamata"
Musa ya yi amfani da wannan tambayar don ya tsauta wa Kora da mazaje da ke tare da shi. Ana iya juya shi cikin magana. AT: "Kana yi kamar ƙaramin abu ne gare ka ... yi musu hidima."
"bai yi maka yawa ba" ko "ba shi da muhimmanci a gare ka"
An yi magana game da son zama firist sai ka ce suna nemansa. AT: "kai ma kana so ka zama firist" ko "kuma kana so ka zama firist"
Musa ya yi amfani da wannan tambaya don ya nuna cewa duk sa'ad da suke gunaguni game da abin da Haruna ke yi, suna gunaguni ne game da Yahweh saboda Haruna yana yin abin da Yahweh ya ce masa ya yi ne. AT: "hakika ba ga Haruna kuke gunaguni ba, amma ga Yahweh, wanda Haruna ke yi wa biyayya."
Datan da Abiram sun yi amfani da wannan tambaya don su tsauta wa Musa. Ana iya juya shi cikin magana. AT: "Kana yi kamar ƙaramin abu ne ka yi da ka fito da mu ... don mu mutu cikin jeji."
"bai isa ba" ko "ba shi da muhimmanci"
Sun yi magana game da ƙasar da ke da kyau don dabbobi da shuke-shuke sai ka ce madara da zuma daga waɗannan dabbobi da shuke-shuken suna zubowa daga ƙasar. Duba yadda ka juya wannan cikin 14:6. AT: "wanda ke da kyau kwarai don kiwon dabbobi da kuma shuki" ko "ƙasa ce mai ni'ima ƙwarai da gaske"
Sun yi magana game da abin da Allah zai ba su ya zama nasu har abada sai ka ce gãdo.
Mutanen nan su yi amfani da wannan tambaya don su zargi Musa. Ana iya juya shi cikin magana. AT: "Yanzu kana so ka makatar da mu da alkawaren wofi."
An yi magana game da yuadaran mutane kamar a makatan su. AT: "yaudare mu"
Sun yi magana game da alkawaren da ba a cikawa sai ka ce bokati ne da ba kome a ciki. AT: "da alkawaren da ba ka cikawa" ko "ta wurin yin alkawarin abubuwan da ba ka yi"
Jaki ɗaya a nan na wakilcin kowane abu da mutum zai iya karɓa daga wurin wani. AT: "Ban karɓi kome daga wurin su ba, ba ma jaki ɗaya ba"
...
AT: "zan kuma hallaka su"
Wannan na nuna cewa Musa da Haruna na kaskantar da kansu a gaban Allah.
A nan "ruhohin" na wakilcin rayuwa. AT: "Allahn da ya bada rai ga dukkan 'yan'adam"
Musa da Haruna sun yi wannan tambaya don su yi roƙo ga Allah saboda mutanen. Ana iya juya wannan cikin magana. AT: "ina roƙo kada ka yi fushi da dukkan jama'an saboda zunuban mutum ɗaya"
An yi magana game da hallakawa saboda zunubansu sai ka ce zunuban za su hallaka su. AT: "za ku hallaka saboda da zunubansu"
AT: "dukka zunubansu za su hallaka ku" ko "Yahweh zai hallaka ku saboda zunubansu"
A nan, "wannan" na nufin abin da Musa zai faɗa a gaba.
Musa yana magana sai ka ce duniya na da rai kuma buɗewar ƙasa da waɗannan mutanen za su faɗi ciki kamar babban baki ne da zai cinye su. AT: "sun kuma faɗa cikin ta an kuma binne su ƙarƙashin ƙasa"
Musa ya yi magana game da ƙasa sai ka ce ta na da rai, ramin da mutanen sun faɗi cikin kuma sai ka ce ƙasa na da baki. AT: "Ƙasar ta buɗe kamar babban baki, sai suka faɗi cikin ta, an kuma binne su ciki" ko "Sai ga wata babbar rami a ƙasa, nan suka faɗi ciki an kuma binne su cikinta"
Magana makamancin haka ta auku cikin 16:28. Dubi yadda ka juya shi a wurin.
"Su" na nufin "Dukka Isra'il."
Mutanen sun yi magana game da ƙasa sai ka ce ta na da rai. AT: "Idan ƙasar ta buɗe kuma, mu ma za mu faɗi ciki a kuma binne mu"
An yi magana game da hallaka da wuta sai ka ce wuta ta cinye su. AT: "wuta ta haskaka daga wurin Yahweh ta kuma hallaka mazaje 250"
Wannan na nufin wutar da ta ƙone mazaje 250.
Rasa rayukansu na wakilcin mutuwa. AT: "waɗanda suka mutu"
A nan, "su" na nufin farantin ƙona turare. AT: "Bari Eliyazar ya yi su"
A nan "su" da "Su" na nufin farantin ƙona turare.
AT: "wanda mutanen da wuta ta ƙone su sun yi amfani da shi"
Ana iya bayana yadda suka zama kamar su a fili. AT: "mutu kamar Kora da ƙungiyarsa sun mutu"
An yi amfani da wannan magana a nan don nuna alamar abu ma muhimmanci da ta faru a labarin. Idan harshen ku na da hanyar yin wannan, to za ku iya yin amfani da shi a nan.
"taru don gunaguni ga Musa da Haruna"
"ba zato ba tsammani." A nan "ga shi" na nuna cewa mutanen sun yi mamakin abin da sun gani.
AT: "don in hallaka su" ko "kuma zan hallaka su"
Wannan na nuna cewa Musa da Haruna suna kaskantar da kansu a gaban Allah.
Fushi da ke zuwa daga wurin Allah na nufin Allah na nuna fushinsa. AT: "Yahweh na nuna mana fushinsa" ko "Yahweh ya yi fushi kwarai kuma yana yi bisa ga fuhinsa"
Sanya turaren cikin farantin ƙona turare a nan na wakilcin ƙonawa. AT: "ya ƙona turaren"
AT: "annobar ta bar yaduwa"
1Yahweh ya yi magana da Musa. Ya ce,2"Faɗa wa mutanen Isra'ila, su ɗauki sanduna daga gare su, kowanne ɗaya domin kabilar kakanni, sanduna goma sha biyu. Rubuta sunan kowanne mutum a kan sandarsa.3Ka rubuta sunan Haruna a kan sandan Lebi. A kan kowacce sanda domin shugaban kabilar kowanne kakanninsa.4Ka ajiye sandunan a cikin alfarwar taro a gaban ka'idodi alƙawari, wurin da nakan sadu da kai.5Zai zamana sandan mutumin dana zaɓa za ta yi toho. Zan sa ƙorafe-ƙorafe daga mutanen Isra'ila ya tsaya, waɗanda suke magana a kanka."6Sai Musa ya yi magana da mutanen Isra'ila. Dukkan shugabannin kabilu suka ba shi sandunan, sanda ɗaya daga kowanne shugaba, da aka zaɓa daga dukkan kabilun kakanin, sanduna goma sha biyu dukka. Sandan Haruna na cikinsu.7Sai Musa ya ajiye sandunan a gaban Yahweh cikin alfarwar ka'idodin alƙawari.8Kashegari Musa ya tafi cikin alfarwar ka'dodin alƙawari, sai ga shi, sandar Haruna ta kabilar Lebiyawa ta yi toho. Ta tuko tayi toho ta bada 'ya'yan almon nunannu!9Musa kuwa ya fito da dukkan sandunan a gaban Yahweh zuwa ga dukkan mutanen Isra'ila, sai kowanne mutum ya ɗauki sandansa.10Yahweh yace da Musa, "Sa sandan Haruna a gaban ka'idodin alƙawari. Ka ajiye ta alama ce a kan mutane waɗanda ke tawaye saboda ka kawo ƙarshen gunaguni a kaina, ko kuwa za su mutu.11Musa kuwa ya yi kamar yadda Yahweh ya umarce shi.12Mutanen Isra'ila suka yi magana da Musa suka ce, "Za mu mutu a nan. Dukkan mu zamu lalace! Duk wanda ya zo nan, kowa ya kusanci alfarwar Yahweh, zai mutu.13Mu dukka za mu lalace?"
"12"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa.
Sunan nan Lewi a nan na nufin kabilan Lewi.
A nan, "sa" na nufin "kowane shugaba."
Magannan nan "ka'idodin alkawari" na nufin akwatin da ke ɗauke da fallen da aka rubuta ka'idodin alkawarin a kai. AT: "akwatin alkawarin" ko "akwatin da ke ɗauke da ka'idodin alkawarin"
"fure zai fara tohuwa a kan sandan mutumin da na zaɓa"
AT: "sa mutanen Isra'ila su daina gunaguni a kanka"
AT: "wadda Musa ya zaɓa daga kowane kabilun kakanin"
Magannan nan "ka'idodin alkawari" na nufin akwatin da ke ɗauke da fallen da aka rubuta ka'idodin alkawarin a kai. AT: "alfawar akwatin alkawarin" ko "alfarwar da ka'idodin alkawarin na ciki"
Kalman nan "ga shi" a nan na nuna cewa wani abu mai muhimmanci ya faru. Mai yiwuwa kuna da kalma makamanci haka a harshenku.
Magannan nan "ka'idodin alkawari" na nufin akwatin da ke ɗauke da fallen da aka rubuta ka'idodin alkawarin a kai. AT: "akwatin alkawarin" ko "akwatin da ke ɗauke da ka'idodin alkawarin"
AT: "don ka hana su gunguni a kaina"
Wannan shine abin da zai faru idan mutanen sun cigaba da gunaguni. Allah yana so ya kawar da wannan. AT: "don kada su mutu"
A takaice waɗannan maganganu biyun na nufin abu ɗaya, za a kuma iya haɗa su don a nanaci.
1Yahweh yace da Haruna, "Kai, da 'ya'yanka, da kabilar kakanninka za ku ɗauki hakkin dukkan zunubai da za ayi game da alfarwar sujada. Amma kai da 'ya'yanka ne kaɗai za ku ɗauki hakkin dukkan zunuban da ya shafi kowanne firist.2Kuma sauran 'yan'uwan kabilar Lebi, kakanninka, ka kawo su tare da kai saboda su kasance tare da kai don su taimake ka da 'ya'yanka aiki a gaban alfarwa ta ka'idodin alƙawari.3Su yi maka dukkan ayyukan alfarwa. Amma ba za su zo su kusanci kowanne abu dake a wuri mai tsarki, ko wani abu da ya shafi bagaɗi ba, ko su da kai dukka ku mutu.4Su haɗu da kai, don su lura da alfarwar taruwa, domin dukkan aikace-aikace na alfarwar. Kada wani baƙo ya zo kusa da ku.5Ku ɗauki nauyin ayyukan wuri mai tsarki da kuma bagaɗi saboda kada fushina ya zo a kan mutanen Isra'ila kuma.6Duba, ni da kaina na zaɓi 'yan 'uwan Lebiyawa daga cikin zuriyar Isra'ila. Kyauta suke a gare ku, an bani su don su yi aikin lura da alfarwar taro.7Amma da kai da 'ya'yanka za ku yi aikin firist da duk abin da ya shafi bagaɗi da dukkan aiki na bayan labule. Kune da kanku za ku yi waɗannan aikace-aikace. Ina baku aikin firist a matsayin kyauta. Duk wani baƙo wanda ya matso zai mutu."8Sai Yahweh ya cewa Haruna, "Duba, na baka aikin, kula da baikon ɗagawa a gare ni, da dukkan baye -baye masu tsarki da mutanen Isra'ila suka bani. Na bada dukkan baye-bayen a gare ka da 'ya'yanka maza har abada.9Wannan zai zama rabonka daga abubuwa masu tsarkin gaske da za a ajiye daga wuta. Daga kowanne baiko nasu--kowacce bayarwar hatsi, da kowacce bayarwa don zunubi da bayarwar laifi--za su ajiye su gare ka da 'ya'yanka.10Waɗannan baye-baye suna da tsarki sosai, kowanne namiji ya ci shi, domin suna da tsarki a gare ka.11Waɗannan su ne baye-bayen da za su zama naka: sun zama da tsarki daga dukkan bayarwar ɗagawa daga mutanen Isra'ila. Na bada su a gare ka da 'ya'yanka maza da 'ya'yanka mata, a matsayin naka har abada. Duk wanda yake da tsarki a iyalinka zai iya cin kowanne daga waɗannan baye-bayen.12Dukkan mai mai kyau, dukkan sabon ruwan inabi da hatsi da nunar fari masu kyau da mutane suka bada gare ni--dukkan waɗannan abubuwa na bada su a gare ka.13Nunan fari na dukkan amfanin gonarsu, wanda suke kawo wa gare ni, za su zama naka. Duk wanda yake da tsarki a iyalinka zai iya cin waɗannan abubuwa.14Iyakar abin da aka keɓe a Isra'ila zai zama naka.15Dukkan abin da aka haifa, dukkan nunar fari wadda jama'a suka bayar ga Yahweh, mutum ko dabba, zai zama naka. Duk da haka, mutane dole su fanshi kowanne haihuwar fari na mutum, su kuma fanshi ɗan fari na dabba namiji da ba shi da tsarki.16Waɗanda mutane za su fansa dole sai sun kai wata ɗaya da haihuwa. Sa'an nan mutane zasu iya fansar su, gama kuɗinsu shekel biyar ne bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi na shekel, wanda ya ke dai dai da awo ashirin na gerah.17Amma haihuwar fari ta saniya, ko ta tunkiya ko ta akuya--ba za ka fanshi waɗannan dabbobi ba; keɓaɓɓu ne a gare ni. Sai ka yayyafa jininsu a kan bagaɗi, ka ƙona kitsensu a matsayin baiko na ƙonawa, abin ƙanshi mai gamsarwa ga Yahweh.18Namansu zai zama naka. Kamar ƙirjin da aka ɗaga da cinyar dama, namansu zai zama naka.19Dukkan baye--baye masu tsarki da mutanen Isra'ila suka bayar ga Yahweh, na bada su gare ka da 'ya'yanka maza da 'ya'yanka mata tare da kai, yadda za ku ci gaba da samun rabo ke nan. Wannan alƙawarin gishiri mara ƙarewa ne, alƙawarin yana nan har abada, a gaban Yahweh domin ka da zuriyarka.20Yahweh yace da Haruna, "Ba za ka sami gãdo a cikin ƙasar mutane ba, ko ka sami rabon kaya a cikin mutane. Ni ne rabonka da gãdonka a cikin mutanen Isra'ila.21Duba, ga zuriyar Lebi, na ba su dukkan zakar Isra'ila a matsayin gãdonsu saboda hidimar da suke yi a cikin rumfa ta taruwa.22Daga yanzu mutanen Isra'ila za su zo kusa da rumfa ta taruwa, ko su ɗauki alhakin wannan zunubi, su mutu.23Lebiyawa ne za su yi aikin da ya shafi rumfa ta taruwa. Za su ɗauki alhakin kowane zunubi dangane da shi. Wannan zai zama doka ta din-din-din a dukkan zamanan mutanenka. A cikin mutanen Isra'ila ba za su sami gãdo ba.24Gama zakkar mutanen Isra'ila, wadda za su miƙa a matsayin gudummuwarsu gare ni-- waɗannan ne na bayar ga Lebiyawa a matsayin gãdonsu. Wannan shi yasa na ce da su, 'Baza su sami gãdo ba a cikin mutanen Isra'ila.'"25Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,26"Dole ka yi magana da Lebiyawa ka ce da su, 'Sa'ad da suka karɓi kashi goma daga mutanen Isra'ila wanda na basu gãdo, sai ku bada gudummuwa daga cikin ta ga Yahweh, kashi goma na zakkar.27dole ku ɗauke ta kamar kashi goma na hatsinsu ne daga masussuka ko kuma kamar amfani daga wurin matsewar inabinku.28Haka kuma dole ku miƙa gudummuwa ga Yahweh daga dukkan zakkar da kuke karɓa daga wurin mutanen Isra'ila. Daga ciki dole za ku bayar da gudummuwa ga Haruna firist.29Daga dukkan kyaututtukan da kuke karɓa, dole ku bada kowacce gudummuwa ga Yahweh. Dole ku yi wannan daga dukkan abu mafi kyau mafi tsarki da aka ba ku.'30Saboda haka dole ka ce da su, 'Sa'ad da kuka bada mafi kyau daga ciki, sai ya zama na Lebiyawa kamar amfanin da ya fito daga masussuka da wurin matsewar inabi.31Za ku iya cin sauran kyaututtukanku a kowanne wuri, ku da iyalinku, gama ladanku ke nan saboda aikin da kuke yi a rumfa ta taruwa.32Ba kuwa za ta zama maku sanadin laifi ba ta wurin cinta da shanta, in dai har kuka bada ga Yahweh mafi kyau daga cikin abin da ku ka karɓa. Amma ba za ku ɓata tsarkakakken baye-bayen na mutanen Isra'ila ba, ko ku mutu.'"
AT: "dukkan zunuban da wani ya yi game da alfarwa ta sujada"
AT: "dukkan zunuban da wani daga cikin firist ya aikata"
"wani firist"
Yahweh ya cigaba da magana da Haruna.
"Su" na nufin 'yan kabilan Lewi; kalman nan "kai" na nufin Haruna.
A nan "su" na nufin 'yan kabilan Lewi wanda suka yi "kusa da wani abu da ke cikin alfarwar;" kalman nan "kai" na nufin Haruna da sauran Lewiyawan da ke hidima a bangare da aka yadda masu.
A nan "ku" na nufin Haruna sa sauran Lewiyawan.
Ma'ana mai yiwuwa 1) wannan na wakilcin cewa Allah ya yi matuƙar fushi da mutanensa. AT: "don kada in yi fushi da mutanen Isra'ila kuma: ko 2) wannan na wakilcin cewa Allah ya hukunta su saboda fushinsa. AT: "don kada in hukunta mutanen Isra'ila kuma"
Yahweh ya cigaba da magana da Haruna.
An yi magana game da zaɓen da Yahweh ya yi wa Lewiyawa don ya taimake Haruna sai ka ce kyauta ce da Yahweh ya ba wa Haruna. AT: "Su kamar kyauta ce a gare ka"
A nan "ba" wa Allah na wakilcin keɓewa don hidima ga Allah. AT: "wadda na keɓe domin kaina" ko "na kuma keɓe su domin kaina"
A nan "kai" da "ka" na nufin Haruna.
...
Kasancewa cikin labulen na wakilcin kasancewa cikin ɗakin da ke bayan labulen. AT: "kowane abu da ke ɗakin da ke bayan labublen"
AT: "Du wani baƙo da ya matso lallai ne ya mutu" ko "Kowane baƙon da ya matso lallai ne ka kai shi ga mutuwa"
Ana iya bayana abin da bai kamata su yi matso kusa da shi ba a fili. AT: "wanda ya matso kusa da abubuwa ma su tsarki"
A nan "mika a gare ni" na nufin ba da wani abu ga Allah. AT: "baye-bayen da mutanen su mika a gare ni"
Allah yana magana sai ka ce ya riga ya yi wannan domin shiri ne da ya riga ya yi. AT: "Na mika waɗannan baye-bayen a gare ka"
Rabo wani bangaren abu ne da wani ya samu. AT: "a matsayin anin da za ka cigaba da karɓawa"
AT: "wanda ba ka ƙona shi gabaɗaya a kan bagadin ba"
"waɗannan bangaren suna da tsarki ƙwarai da gaskiya"
Allah ya cigaba da magana Haruna.
An yi magana game da zama karɓaɓɓe ga Allah sai ka ce su na da tsarki. AT: "karɓaɓɓe a gare ni"
Allah ya cigaba da magana da Haruna.
Wannan na nufin mai, da ruwan inabi, da hatsi na farko da suka girbe.
An yi magana game da zama karɓaɓɓe ga Allah sai ka ce su na da tsarki. AT: "Duk wanda ke karɓaɓɓe a gare ni daga cikin iyalinka"
Allah ya cigaba da magana da Haruna.
Waɗannan maganganu biyun a takaice suna nufin abu ɗaya. AT: "Kowane ɗan fari"
Maimaƙon yin hadaya da ɗan farinsu, mutanen suna biyan firist domin 'ya'yan su maza.
AT: "Lallai ne mutanen su fanshi su a sa'ad da sun kai wata ɗaya"
Mai yiwuwa wannan na nufin 'yan farin na mutane da lallai ne a fanshe su ba kuwa 'yan fari na dabbobi mara tsarki.
In mai yiwuwa ne a yi amfani da ma'aunin wannan zamanin, to ga hanyoyi biyu da za a iya yin wannan. AT: "azurfa biyar... kowanen su nauyinsa daida da gram goma" ko "gram hamsin na azurfa, kamar yadda ake amfani da ma'aunin nauyin na haikali"
Shekel ma'aunin nauyi ne. Abin da aka auna nauyinsa ana iya bayana a fili. AT: "shekel biyar na azurfa"
Akwai shekel da nauyin su daban-dabam ne. Wannan ita ce wanda mutanen ke amfani da shi a haikali ta alfarwar mai tsarki. Nauyin sa gerahs ashirin, wanda ke kusan gram goma sha ɗaya.
Allah ya cigaba da magana da Musa.
Ana iya bayana a fili cewa lallai ne ya yanka dabbobin da farko. AT: "Lallai ne ka kashe su ka kuma yayyafa jininsu"
AT: "da ka yi da wuta" ko "da ka ƙona da wuta a kan bagadin"
Gamsuwar Ubangiji da ƙanshin na wakilcin gamsuwarsa da mutumin da ya ƙona hadayar"
AT: "ƙirjin da cinyan dama da ka ɗaga a matsayin kyauta zuwa gare ni"
Allah ya cigaba da magana da Musa.
Allah ya yi magana sai ka ce ya riga ya yi wannan domin shiri ne da ya riga ya yi. AT: "Na ba ka"
Rabo na bangare wani abu da wani ya karɓa. AT: "rabon da za ka cigaba da samuwa"
Maganganu biyun nan na nufin abu ɗaya. Duk suna nanata cewa alƙawarin zai dawwama har abada. AT: "yarda ne na har abada"
"alƙawari da aki da gishiri." Gishiri na wakilcin dawwamamme ana kuma amfani da shi don baye-baye da kuma alƙawari na abinci. AT: "alƙawari da ta dawwama" ko "alƙawarin da ta dawwama"
Allah yana magana game da ƙasar da zai zama na sauran mutanen sai ka ce za su gãda ƙasar. AT: "ƙasar mutanen ba zai zama naka ba" ko "Ba za ka sami wani ƙasar da zai zama na Isra'ilawan ba"
Allah yana magana game da martaban da Haruna da zuriyarsa za su samu ta waurin bauta masa a matsayin firist sai ka ce Allah wani abu ne da za su gãda. AT: "Maimakon haka, ni ne abin da za ku sami" ko "Maimakon haka, zan bar ku ku bauta mani ni kuwa zan tanaɗa maku ta wurin wannan bauta"
Allah ya cigaba da magana da Musa.
Kalman nan "duba" a nan na kara nanata abin da ya bi baya ne. AT: "hakika, na ba wa"
Allah ya yi magana game da abin da Haruna da zuriyarsa za su samu sai ka ce za su gãda, AT: "a matsayin bangaren da na ba wa Isra'ila"
Allah ya cigaba da magana da Musa.
Allah ya yi magana game da abin da Haruna da zuriyarsa za su samu sai ka ce za su gãda. Lewiyawan ba za su sami wani ƙasar ba. AT: "hakika ba za su sami wani ƙasar da sauran mutanen Isra'ila sun samu ba"
Allah ya yi magana game da abin da Haruna da zuriyarsa za su samu sai ka ce za su gãda. AT: "a matsayin nasu bangaren daga cikin abin da na ba wa Isra'ila"
Mutanen Isra'ila za su mika wa Yahweh ƙashi goma na hatsin su da dabbobi, Yahweh kuwa zai bada wannan ga Lewiyawa.
Allah ya yi magana game da abin da Haruna da zuriyarsa za su samu sai ka ce za su gãda. AT: "a matsayin naku bangaren daga cikin abin da na ba wa Isra'ila"
AT: "Lallai ne ku ba da gudumawar ku"
Allah ya cigaba da gayawa Musa abin da lallai ne ya gaya wa Lewiyawan.
A nan "sa" na nufin Yahweh. Gudumawar Yahweh ne a nufin cewa za su mika ta ga Yahweh tukuna. AT: "lallai ne ka ba wa Haruna gudumawar da Yahweh ke bin ka"
AT: "wanda mutanen Isra'ila sun ba ka"
Allah ya cigaba da magana da Musa.
"mafi kyau daga cikin abin da ka samu daga wurin mutanen Isra'ila"
"kyauta" su ne baye=bayen da Isra'ilawa su ba wa Allah da kuma wadda Lewiyawa sin samu daga wurin su.
Ba za ku zama masu laifi ba a sa'ad da kuka ci kuka kuma sha"
1Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna.2Ya ce, "Wannan ita ce ka'ida, da doka wadda nake umartar ku: Ka faɗawa mutanen Isra'ila dole su kawo maka jar karsana marar lahani ko wadda ba ta da wani aibi, wadda ba a taɓa aza mata karkiya ba.3Sai ka ba Eliyeza firist karsanar. Dole ya kawo ta a wajen zango, kuma dole wani zai yanka ta a gabansa.4Dole Eliyeza, firist, ya ɗibi jininta da yatsansa ya yayyafa sau bakwai a gaban rumfa ta taruwa.5Dole sai wani firist ya ƙone karsanar a idonsa. Dole zai ƙone fatarta da namanta da jinin tare da ƙashinta.6Dole firist ya ɗauki itacen al'ul da abin tsaftacewa da mulufi ya jefa su dukka a cikin tsakiyar wutar da take ƙone karsanar.7Sa'an nan dole ya wanke tufafinsa ya yi wanka a cikin ruwa. Sa'an nan zai zo ya shiga zangon, a wurin zai zama da ƙazamta har zuwa maraice.8Shi kuwa wanda ya ƙone karsanar zai wanke tufafinsa a cikin ruwa, ya yi wanka a cikin ruwa. Zai zama da ƙazamta har zuwa maraice.9Mutumin dake da tsarki shi zai tara tokar karsanar, ya sa ta wajen sansani a wuri mai tsabta. Za a adana tokar saboda jama'a mutanen Isra'ila. Za su riƙa zubawa a ruwa don tsarkakewar zunubi, tun da yake tokar daga bayarwar zunubi ce.10Shi kuwa wanda ya tara tokar karsanar sai ya wanke tufafinsa. Zai zama ƙazantacce har maraice. Wannan doka ce ta har abada domin mutanen Isra'ila da baƙin dake zama tare da su."11Duk wanda ya taɓa jikin gawar mutum zai ƙazantu har kwana bakwai.12Wannan mutum zai tsarkake kansa a rana ta uku da rana ta bakwai. Sa'an nan zai tsarkaka. Amma in a rana ta uku bai tsarkake kansa ba, ba zai zama da tsarki ba a rana ta bakwai.13Duk wanda ya taɓa jikin gawar mutum wanda ya mutu, bai tsarkake kansa ba--wannan mutum zai kazantar da alfarwar Yahweh. Wannan mutum za a yanke shi daga cikin Isra'ila domin ba a yayyafa masa ruwan tsarkakewa ba. Zai kasance ƙazantacce; ƙazancewarsa za ta kasance a kansa.14Wannan ita ce doka a kan wanda ya rasu a cikin alfarwa. Duk wanda ya shiga alfarwar da wanda ke cikin alfarwar za su ƙazantu har kwana bakwai.15Kowanne buɗaɗɗen akwati da ba a rufe ba, zai ƙazantu.16Hakanan ma duk wanda ke wajen alfarwar ya taɓa jikin mamacin wanda aka kashe da takobi, ko kowacce gawa, ko ƙashin mutum, ko kabari--wannan mutumin zai ƙazantu har kwana bakwai.17A yi wannan domin mutumin da ya ƙazantu: A ɗibi toka daga cikin bayarwar ƙonawa a haɗa su a cikin tulu tare da sabon ruwa.18Duk wanda ke da tsarki zai ɗauki abin tsaftacewar ya tsoma a ruwan, ya yayyafa wa alfarwar da dukkan kayayyakin dake cikin alfarwar, da mutanen dake a wurin, da wanda ya taɓa ƙashin ko wanda aka kashe ko wanda ya mutu, ko kabari.19A kan rana ta uku da ta bakwai kuma wanda yake da tsarki zai yayyafa wa mutum marar tsarkin ruwa. A rana ta bakwai mutum mara tsarki zai tsarkake kansa. Zai wanke tufafinsa, ya yi wanka a ruwa. Da maraice kuwa zai tsarkaka.20Amma duk wanda ya kasance da rashin tsarki, wanda ya ƙi ya tsarkake kansa--wannan mutum za a datse shi daga jama'a, domin ya ƙazantar da wuri mai tsarki na Yahweh. Kuma ba a yayyafa masa ruwan da ake yayyafa wa marasa tsarki ba.21Wannan zai zama doka a gare su a kan abubuwa kamar haka. Wanda ya yayyafa ruwan don tsarkakewa, zai wanke tufafinsa, wanda kuma ya taɓa ruwan don tsarkakewa zai zama marar tasrki har maraice.22Duk abin da mutumin da ba shi da tsarki ya taɓa, zai ƙazantu. Duk wanda kuma ya taɓa abu marar tsarki, zai ƙazantu har maraice."
Waɗannan kalamomin na da ma'ana kusan iri ɗaya. AT: "ka'ida ta doka" ko "ka'ida"
"ka" a nan na nufin Musa.
Waɗannan kalmomin a takaice na nufin abu ɗaya na kuma nanata cewa kada a sami wannan dabba da wata lahani.
"a iddonsa" ko "don ya gan shi"
"firist" na nufin Eliyaza.
"jan ulu"
A nan "ya" na nufin Eliyazar firist.
An yi magana game da rashin karɓuwa a gaban Allah kamar ƙazamtuwa.
An yi magana game da zama karɓaɓɓe ga Allah don a cancanta a yin aiki mai tsarki kamar zama da tsarki.
AT: "Lallai ne ka adana wannan tokar"
An yi magana game da zama karɓaɓɓe ga Allah kamar zama da tsarki.
An yi magana game da rashin karɓuwa ga Allah ko kuwa rashin cancanta don yin aiki mai tsarki kamar zama da rashin tsarki.
Ra'ayin game da "tsarki" na wakilcin zamar karɓaɓɓe ga Allah.
Ra'ayin game da "rashin tsarki," "ƙazamta" "rashin tsabta" na nufin cewa Allah bai amince ba.
"gawan kowane mutum"
Mutumin zai roƙi wani wanda ke da tsarki ya tsarkake shi ta wurin yayyafa masa ruwan da ke garwaye da toka. An yi magana game da roƙon wani ya tsarkake shi kamar shi zai tsarkake kansa ne. AT: "roƙi wani ya tarkake shi"
AT: "zai zama da tsarki a rana ta bakwai in har ya tsarkake kansa a rana ta uku"
A nan maganan nan "fid da" na nufin a ki sa'annan kuma a kore shi. Dubi yadda ka juya wannan cikin 9:13. AT: "lallai ne a kore mutumin nan" ko "lallai ne ku kore mutumin nan"
AT: "babu wanda ya yayyafa masa ruwan tsarkakewa"
"ruwan da ake yayyafa wa abubuwan da ba su da tsarki don su zama da tsarki" ko "ruwan don tsarkake abubuwa"
Waɗannan maganganu biyun a takaice na nufin abu ɗaya an haɗa su don a nanaci.
Ra'ayin game da "tsarki" na wakilcin zamar karɓaɓɓe ga Allah ko cancanci a yi amfani da shi.
AT: "Akwatin da ke a buɗe zai kasance da tsarki in har suna da murfi"
AT: "wani wanda wani ya kashe da takobi"
Ra'ayin game da "rashin tsarki," na nufin cewa Allah bai amince ba ko bai cancanci a yi amfani da shi ba.
Ra'ayin game da "tsarki" na wakilcin zamar karɓaɓɓe ga Allah ko cancanci a yi amfani da shi.
Ra'ayin game da "tsarki" na wakilcin zama karɓaɓɓe ga Allah.
Ra'ayin game da "rashin tsarki," na nufin cewa Allah bai amince ba.
A nan maganan nan "fid da" na nufin a ki sa'annan kuma a kore shi. Dubi yadda ka juya wannan cikin 9:13. AT: "lallai ne a kore mutumin nan" ko "lallai ne ku kore mutumin nan"
"ruwan da ake yayyafa wa abubuwan da ba su da tsarki don su zama da tsarki" ko "ruwan don tsarkake abubuwa." Duba yadda ka juya wannan cikin 19:11
1Sai mutanen Isra'ila da dukkan taron jama'a suka zo jejin Zin a wata na fari, suka sauka a Kadesh. A nan ne Miriyam ta rasu, a nan kuma aka bizne ta.2Babu ruwa domin jama'a, sai suka taru suka tayar wa Musa da Haruna.3Mutane kuwa suka yi wa Musa gunaguni. Suka ce, "Zai fi kyau idan da mun mutu yadda 'yan'uwanmu Israilawa suka mutu a gaban Yahweh!4Donme ka fito da taron jama'ar Yahweh a cikin wannan jeji mu mutu a nan, mu da dabobbinmu?5Donme kuma ka sa muka fito daga Masar ka kawo mu a wannan mugun wuri? A nan babu hatsi, ko ɓaure ko inabi ko rumman ko ruwan da za a sha."6Sai Musa da Haruna suka tafi daga gaban taron. Suka shiga alfarwar taro, suka faɗi rub da ciki. A wurin ɗaukakar Yahweh ta bayyana a gare su.7Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,8"ɗauki sandarka ka tara jama'a, kai da Haruna ɗan'uwanka. Yi magana da dutse a gaban idanunsu, ya bada ruwan dake cikinsa. Za ka sa ruwa ya ɓuɓɓugo daga dutsen domin su, ka bada ruwan ga jama'ar da garkunansu su sha."9Musa ya ɗauki sandar daga gaban Yahweh, kamar yadda Yahweh ya umarce shi ya yi.10Sai Musa da Haruna suka tara dukkan jama'ar, a gaban dutsen. Musa yace da su, "Ku saurara yanzu, ku 'yan tawaye. Za mu fito da ruwa daga cikin dutsen nan domin ku?11Musa kuwa ya ɗaga hannu, ya bugi dutsen sau biyu da sandarsa, sai ruwa mai yawa ya yi ta kwararowa. Jama'a kuwa suka sha, dabobbi ma suka sha.12Sai Yahweh yace da Musa da Haruna, "Tun da yake baku gaskata ni ba, baku kuwa ɗaukaka ni akan ni mai tsarki bane a idon mutanen Isra'ila, to, baza ku kai wannan taron a cikin ƙasar dana ba su ba."13Wannan wuri ne aka kira shi ruwan Meriba domin mutanen Isra'ila suka yi wa Yahweh gunaguni a wurin, inda shi kuma ya nuna masu shi kansa mai tsarki ne.14Musa ya aika da manzanni daga Kadesh zuwa ga sarkin Idom: Yan'uwanka Israila sun faɗi wannan: "Ka san dukkan wahalun da suka same mu.15Ka san yadda kakanninmu suka tafi can Masar, suka zauna a Masar da daɗewa. Masarawa suka wahalshe mu, mu da kakanninmu.16Sa'ad da muka yi kira ga Yahweh, ya ji muryarmu, ya aiko da mala'ikansa, ya fishe mu daga Masar. Duba, muna nan a Kadesh, birni dake kan iyakar ƙasarka.17Ina roƙonka ka yardar mana mu ratsa ƙasarka. Za mu bi ta cikinta mu wuce gona, ko gonar inabi, ba za mu sha ruwa daga cikin rijiyarka ba. Za mu bi ta gwadaben sarki. Ba za mu kauce dama ko hagu ba, har mu wuce ƙasarka."18Amma sarkin Idom ya amsa masa, "Ba za ku ratsa ta nan ba. Idan kuwa kuka yi, zan fita tare da takobi, za mu ci ku da yaƙi."19Sai mutanen Isra'ila suka ce da shi, "Za mu bi gwadabe ne kawai. Idan kuwa mu da dabobbinmu mun sha ruwanku, za mu biya. Mu dai, a yardar mana mu wuce a ƙafafunmu, ba tare da yin wani abu ba kuma."20Amma sarkin Idom ya sake amsa masu da cewa, "Ba mu yarda ba. "Sai sarkin Idom ya fito gãba da Isra'ila da runduna mai yawa.21Sarkin Idom ya ƙi ya bar Isra'ila su ratsa a kan iyakarsu. Domin wannan, Isra'ila suka juya daga ƙasar Idom.22Sai mutane suka kama tafiya daga Kadesh. Mutanen Isra'ila da dukkan jama'a suka zo Tsaunin Hor.23Yahweh ya yi magana da Musa da Haruna a Tsaunin Hor, a iyakar Idom. Ya ce,24"Dole ne Haruna ya tarar da mutanensa, don ba zai shiga ƙasar dana ba mutanen Isra'ila ba. Wannan domin ku biyun kun yi mani tawaye a kan maganata a kan ruwan Meriba.25Ka ɗauki Haruna da Eliyeza ɗansa, ka zo da su bisa Tsaunin Hor.26Ka ɗauki rigar firistanci ta Haruna, ka sawa ɗansa Eliyeza. Haruna zai mutu, za a tara shi ga mutanensa a can.27Musa kuwa ya yi yadda Yahweh ya umarta. Suka hau bisa Tsaunin Hor a idon dukkan jama'a.28Musa ya ɗauki rigar Haruna ta firist ya sawa Eliyeza ɗansa. Haruna kuwa ya rasu a bisa tsaunin. Sa'an nan Musa da Eliyeza suka sauko ƙasa.29Sa'ad da dukkan jama'a suka ga Haruna ya rasu, sai dukkan jama'a suka yi kuka da makoki domin Haruna har kwana talatin.
Kalman nan "Zin" a nan sunan jejin ne a yahudanci. Ba kalman zunubi ba ne a turanci.
Wata na fari bisa ga kalandar Yahudawa. Na nuna alamar sa'ad da Allah ya cece Isra'ilawa daga ƙasar Masar. Wata na fari ƙarshen watan uku da kuma farkon watan huɗu bisa ga kalandar bature.
AT: "an kuma binne ta"
A nan, "su" na nufin jama'an.
"zo kamar taron jama'a"
Wannan na wakilcin zama a gaban alfarwar Yahweh.
Mutanen Isra'ila sun cigaba da yi wa Musa da Haruna gunaguni.
Mutanen sun yi amfani da wannan tambayar don su yi gunaguni ga Musa da Haruna. AT: "Da ma ba ka kawo jama'ar Yahweh zuwa cikin wannan jeji don mu mutu a nan ba, mu da dabbobin mu."
Mutanen sun yi amfani da wannan tambayar don su yi gunaguni ga Musa da Haruna. AT: "Da ma baka sa muka bar ƙasar Masar zuwa wannan mummunan wuri ba."
Wannan na nuna cewa Musa da Haruna sun kasƙantar da kansu a gaban Yahweh.
A nan "a gabansu" na wakilcin mutanen sun ga abin da Musa ya yi. AT: "a sa'ad da suke ganin ka"
Wannan na wakilcin alfarwar Yahweh. AT: "daga alfarwar Yahweh"
Musa ya yi wannan tambaya ciki fushi ne don ya tsauta wa mutanen don gunagunin sa suke yi. Ana iya juya wannan cikin magana. AT: "Ku yi gunaguni cewa babu ruwa. To, za mu sa ruwa ta fito daga wannan dutse." ko "Ba za ku yi murna ba ko mun sa ruwa ta fito daga wannan dutse. Duk da haka zan yi hakan."
A nan "mu" na nufin Musa da Haruna mai yiwuwa har da Yahweh amma ban da Mutanen.
Ana iya bayana a fili, yadda Musa bai dogara ga Allah ba bai kuma daraja shi ba, a fili. AT: "Domin ba ka dogara a gare ni ba, ba ka kuma daraja ni ba a matsayin mai tsarki a gaban Isra'ila ba, amma ka buga dutsen a maimaƙon ka yi magana da ita kamar yadda na faɗa maka"
A nan "a gaban" na nufin cewa mutanen suna ganin abin da Musa yana yi. AT: "sa'ad da mutanen Isra'ila suna ganin ka"
AT: "Mutanen sun kira wannan wuri"
Musa ya yi amfani da wannan magana don ya nanata cewa Isra'ilawa da Edomawa 'yan'uwa ne saboda kakaninsu, Yakub da Isuwa 'yan'uwa ne.
"Sa'ad da mun yi addu'a ga Yahweh muna roƙonsa ya taimake mu"
A nan "murya" na wakilcin kukansu, ko kuwa abin da suka faɗa masa. AT: "ya ji kukanmu" ko "ya ji abin da muka roƙa"
A nan "Duba" alama ce na sabuwan kan magana. suna magana ne game da abin da ya faru da su a baya. Yanzu kam, suna magana ne game da yanayinsu na yanzu a sa'ad da suke shirin roƙon sarkin ya yi wani abu.
Masu kai saƙon sun cigaba da magana da sarkin Edom.
A nan "kauce" na nufin barin hanya. AT: "Ba za mu bar hanyar zuwa wata hanya ba"
Wannan ita ce hanyar da ta haɗa Dimashƙu ta bangaren arewa ta mashigar ruwa na Akaba ta bangaren kuɗu.
A nan "ka" na nufin Musa wanda ke wakilcin mutanen Isra'ila. AT: "Mutanen ka ba za ratsa ... in kai musu hari"
A nan "takobi" na wakilcin rundunan sojojin sarkin. AT: "Zan tura rundunan sojoji na" UDB
Wannan na nufin masu kai saƙo na Isra'ila.
Wannan karin maganan na nufin cewa za su yi tafiya da kafafunsu. Ba za su zo a karusai don su kai wa mutanen Edom hari ba.
AT: "sarkin Edom ya tura rundunar soja son su kai wa Isra'ila hari"
A nan "su" na nufin Edomawa.
Maganan nan "dukkan jama'an" na nanata cewa kowane mutum wanda ke cikin "Mutanen Isra'ila" na nan, babu wanda aka bari a baya.
Wannan na nufin cewa lokaci ya yi da Haruna zai mutu, ruhunsa kuma ya tafi wurin da kakaninsa suke.
A nan "magana ta" na wakilcin abin da Yahweh ya faɗa. AT: "ƙi yi abin da na faɗa"
Allah ya cigaba da magana da Musa.
Waɗannan maganganu biyu a takaice na nufin abu ɗaya. Su na nufin cewa lokaci ya yi da Haruna zai mutu ruhunsa kuma ya tafi wurin da kakaninsa suke.
"kwanaki 30"
1Sa'ad da sarkin Kan'ana na Arad wanda ke zaune a Negeb, ya ji Isra'ila na zuwa ta hanyar Atarim, sai ya yi faɗa da Isra'ila ya ɗauki waɗansu a matsayin kamammun yaƙi.2Isra'ila suka yi wa'adi ga Yahweh cewa, "Idan zaka ba mu nasara a kan waɗannan mutane, sai mun hallakar da su da biranensu."3Yahweh ya saurari muryar Isra'ila, ya kuma ba su nasara a kan Kan'aniyawa. Suka hallaka su da biranensu. Shiyasa ake kiran wurin Horma.4Suka yi tafiya daga Tsaunin Hor ta hanya zuwa Tekun Iwa a kewayen ƙasar Idom. Sai mutane suka kusan fitar da zuciya a hanya.5Mutane suka yi gunaguni da Allah da Musa: "Meyasa kuka fitar da mu daga Masar don mu mutu a cikin jeji? Babu abinci, babu ruwa kuma bamu son irin wannan abinci mai gundura."6Sai Yahweh ya aika da macizai masu zafin dafi a cikin mutane. Suka kuwa sassari mutane, har mutane da yawa suka mutu.7Mutane suka zo wurin Musa suka ce, "Mun yi zunubi gama mun yi wa Yahweh gunaguni, mun kuma yi maka. Ka roƙi Yahweh domin ya ɗauke macizan daga gare mu." Musa kuwa ya yi addu'a saboda mutanen.8Yahweh ya cewa Musa, "Ka yi maciji ka sa shi a sanda, zai zamana duk wanda macijin ya sare shi idan ya dubi macijin tagulla zai tsira."9Musa kuwa ya yi maciji na tagulla ya sarƙafa shi a bisa dirka. Idan kuwa maciji ya sari mutum, in dai ya dubi macijin tagulla sai ya tsira.10Sai mutanen Isra'ila suka kama hanya suka yi zango a Obot.11Sun yi tafiya daga Obot, suka yi zango a Iye Abarim a cikin jeji suna fuskantar Mowab wajen gabas.12Daga can suka tashi suka sauka a Kwarin Zered.13Daga can kuma suka tashi suka sauka hayin Kogin Arnon, wanda ke cikin jeji wanda ya nausa zuwa iyakar Amoriyawa. Kogin Arnon shi ne kan iyakar Mowab, tsakanin Mowab da Amoriyawa.14Saboda haka aka faɗa a littafin Yaƙoƙi na Yahweh,"--"Waheb ta cikin yankin Sufa da kwaruruka na kogin Arnon,15da gangaren kwaruruka wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab."16Daga can suka ci gaba da tafiya zuwa Biyer, rijiya wadda Yahweh yace da Musa, "Ka tattara mutane wuri ɗaya domi na, zan kuwa ba su ruwa."17Sai Isra'ila suka raira waka: "Ƙorama ki, ɓuɓɓugo yadda ya kamata! Rera waƙa a game da ita,18a game da rijiyar da shugabanninmu suka gina, rijiyar da mutanenmu masu daraja suka gina, da sandan sarauta da kuma sandunansu." Daga cikin jeji suka tafi har zuwa Mattana.19Daga Mattana suka tafi Nahaliyel, daga can kuma suka tafi Bamot,20daga Bamot kuma suka tafi kwarin dake a ƙasar Mowab wajen ƙwanƙolin Dutsen Fisga wanda ke duban hamada.21Sai Israila suka aiki manzanni zuwa wurin Sihon sarkin Amoriyawa suna cewa,22"Ka yarda mana mu ratsa ta ƙasarka. Ba za mu ratsa ta cikin gonaki ko cikin gonakin inabi ba, ba kuwa za mu sha ruwan rijiyarka ba, gwadaben sarki za mu bi sosai har mu fita daga iyakarka."23Amma sarkin Sihon bai yarda wa Isra'ila su ratsa ta kan iyakarsa ba. Maimakon haka, sai ya tattara dukkan sojojinsa don su kaiwa Isra'ila hari a cikin jeji. Ya zo Yahaz, wurin da ya yi yaƙi da Isra'ila.24Sojojin Isra'ila suka faɗa su da karkashewa da kaifin takobi suka karɓe ƙasar daga Arnon zuwa kogin Yabbok, har ma zuwa ƙasar mutanen Ammonawa. To sai aka ƙayata iyakar mutanen Amonawa.25Isra'ila kuwa su ka ci dukkan biranen Amoriyawa da dukkan waɗanda su ke zama da su, ya haɗa da Heshbon da dukkan kauyukanta.26Heshbon ita ce birnin Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi yaƙi da sarkin Mowab a dã. Sihon ya ƙwace dukkan ƙasarsa daga yakinsa zuwa Kogin Arnon.27Don haka shi ya sa waɗanda suka yi magana suke misali cewa, "Ku zo Heshbon. Bari birnin Sihon a sake gina shi, ya kuma tabbata.28Wuta daga Heshbon, hasken wuta daga birnin Sihon ya lanƙwame Ar ta Mowab, da mazaunan tuddan wuraren Arnon.29Kaitonki, Mowab! Kin lalace, mutanen Kemosh. Ya sa 'ya'yansa maza na gudu, an kama 'ya'yansa mata sun zama 'yan kurkukun Sihon sarkin Amoriyawa.30Amma yanzu an ci nasarar Sihon. Heshbon ta lalata dukkan hanya zuwa Dibon. Mun ci nasararsu a dukkan hanya zuwa Nofa, wadda ta kai kusa da Medeba."31Sai Isra'ila suka fara zama a ƙasar Amoriyawa.32Musa ya aika mutane su leko asirin Yazar. Suka tafi suka ci ƙauyukanta, suka kori Amoriyawa daga cikinta waɗanda ke a can.33Sa'an nan suka juya suka tafi su haura ta hanyar Bashan. Og sarkin Bashan ya fita gãba da su, shi da dukkan sojojinsa su yi yaƙi da su a Edirai.34Sai Yahweh yace da Musa, "Kada ka ji tsoronsa, gama na baka nasara a kansa, da dukkan sojojinsa da ƙasarsa. Ka yi masa yadda ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, waɗanda suka zauna a Heshbon."35Haka fa suka kashe shi da 'ya'yansa maza da dukkan sojojinsa, har babu wani a mutanensa da ya rage a raye. Sai suka mallaki ƙasarsa.
A nan "ya yi yaƙi" na nufin cewa rundunan sojojins sun yi yaƙi. AT: "rundunan sojojinsa sun yi yaƙi da Isra'ila"
Wannan na nufin mutanen Isra'ila. AT: "Mutanen Isra'ila sun yi wa'adi" ko "Isra'ilawan sun yi wa'adi"
A nan "kasa kunne" na nufin cewa Yahweh ya yi abin da suka roƙa. AT: "yi abin da Isra'ila suka roƙa"
A nan "murya na nufin roƙo. AT: "abin da Isra'ila suka roƙa"
"Mutanen Isra'ila sun hallaka rundunan sojojin Kan'aniyawa da biranensu gabaɗaya"
AT: "Sun kira wannan wuri Horma"
Mutanen nan sun yi amfani da wannan tambaya don su tsauta wa Musa. AT: "Da ma ba ka fid da mu daga Masar don mu mutu cikin jeji ba!"
"mun faɗi mugayen abubuwa game da Yahweh game da kai kuma"
Kalman nan "mu" a nan na nufin mutanen amma ban da Yahweh da Musa.
Da shike ba mai yiwuwa ba ne Musa ya hallici maciji, wannan na nufin cewa ya sifanta maciki. Ana iya bayana abin da ke nufin a fili. AT: "Ka yi sifan maciji"
"maciji da aka yi da tagulla"
A nan "ya" na nufin " duk mutumin" da maciji ya sare shi.
A nan "fuskatar" na nufin "na wancan bangare daga" ko "gaba da." AT: "da ke gaba da Mowab"
Wannan na nufin cewa al'umma biyun na zama bagare dabandabam na kogin da ke alaman iyaka tsakanin su. Mutanen Mowab suna zama a kudanci kogin, sa'an nan Amoriyawa suna zama a Arewacin kogin.
Waɗannan sunayen wurare ne.
"ƙasar garin Ar da kuma iyakar yankin Mowab"
Ana iya bayana wannan cikin jimloli biyu. AT: "zuwa Biyer. A kwai wata rijiya a wurin" (UDB)
AT: "inda Yahweh ya ce wa Musa ya tattara mutanen a wuri ɗaya don ya ba su ruwa"
A nan "rijiya" na wakilcin ruwan da ke cikin rijiya. Isra'ilawan sun yi magana da ruwa sai ka ce mutum ne wanda zai iya jinsu, kuma suna roƙo ta ta cika rijiyar. AT: "Ruwa ya cika rijiyara"
Waɗannan maganganu biyun, a takaice suna nufin abu ɗaya, na kuma nanata cewa shine zai zama shigaba sa'ad da ake tonon rijiyar.
Waɗanda ke da iko ne ke ɗaukan sandan sarauta, kowa na iya ɗaukan sanda. Duk ba kayan aiki tono bane. Waɗannan abubuwa biyu na nanata cewa ba zama musu da damuwa su yi amfani da abun da suke da shi ba. AT: "amfani da sandan sarauta da kuma sandunansu"
Waɗannan sunayen wurare ne.
Wannan shine sunan tsauni.
Wannan karin magana ne. Wata hanya ce na cewa tsaunin ta yi tsawo. An kuma yi magana game da tsaunin sai ka ce mutum da ya dubi ƙasa don ya ga hamadan da ke ƙasa da shi. AT: "ya yi tsawo fiye da hamadan"
A nan "Isra'ila" na nufin mutanen Isra'ila, musamman shugabannin su. AT: "Sai Isra'ilawan"
"Ba za mu shiga cikin gonaki ko gonakin inabin ku ba"
Wannan ita ce hanyar da ta haɗa Dimashƙu ta bangaren arewa ta mashigar ruwa na Akaba ta bangaren kuɗu.20:17.
"wuce iyakar ƙasar su." A nan "su" na nufin Amoriyawan.
Wannan sunan wuri ne.
A nan "ya" na nufin Sojojin Sarkin Sihon, "Isra'ila" kuma na nufin mutanen Isra'ila. AT: "sojojinsa sun yi yaƙi da Isra'ilawa"
A nan "Isra'ila" na nufin mutanen Isra'ila. AT: "Isra'ilawa sun faɗa wa"
"da wuri mai kaifi na takobin." "kaifin takobin" na nufin mutuwa da kuma hallaka gabaɗaya. AT: " da cin gabaɗayan su da yaƙi " (UDB)
"ci ƙasar Amoriyawa da yaƙi." A nan kalman nan "su" na nufin Amoriyawan.
"Amoniyawan ... Amoriyawan" ko "mutanen Ammon ... da mutanen Amor." Waɗannan sunayen sun yi kama, amma suna nufin ƙungiyan mutane biyu ne.
"matuƙar tsaro" (UDB). Isra'ilawan ba su kai wa Amonawan hari ba.
A nan "ta" na nufin dangantakan da ke tsakanina birnin Heshbon da waɗannan kauyukan da ke kusa. AT: "Heshbon da kauyukan da ta ke mulki"
A nan "sa" na nufin sarkin Mowab.
Waɗannan sunaye biyun na nufin birni ɗaya.
AT: "Bari wani ya sãke gina, ya kuma sa birnin Sihon ta tabbata"
Waɗannan kalmomi biyun sun yi kama kuma suna nanata cewa za a sake gina birnin gabakiɗaya. AT: "sake ginawa gabakiɗaya"
Waɗannan maganganu biyun a takaice na nufin abu ɗaya, na kuma nanata cewa za a fara hallaka Heshbon. Wutan na nufin sojojin masu hallakawa. AT: "Sarkin Sihon ya shugabanci sojojin masu ƙarfi daga birnin Heshbon."
An yi magana game da Sihon sai ka ce wata dabba ce da ta cinye birnin Ar. AT: "hallaka birnin Ar da ke cikin ƙasar Mowab"
Waɗannan maganganu biyun na nufin ƙungiyan mutane ɗaya.
"Kemosh" sunan wani gunƙi ne wanda Mowabawa ke bauta wa. AT: "mutanen da ke bauta wa Kemosh"
"Ya" da "sa" na nufin Kemosh.
A nan "mu" na nufin Isra'ilawa wanda sun yi nasara kan Sihon.
AT: "mun lalace Heshbon"
Waɗannan wurare ne ƙarkashin mulkin Sihon. Wannan na nufin cewa Isra'ilawa sun hallaka al'umman Sihon gabaɗayan.
...
"kai musu hari"
Isra'ilawan sun hallaka gabaɗayan Sihon. AT: "Hallaka shi kamar yadda ka hallaka Sihon sarkin Amoriyawa"
"Sojojin Isra'ila sun kashe Og"
AT: "dukka mutanensa sun mutu"
"sun mulki ƙasarsa"
1Mutanen Isra'ila suka kama tafiya har suka yi zango a filayen Mowab kusa da Yeriko, a ɗaya gefen a Kogin Yodan daga birnin.2Balak ɗan Ziffor ya ga dukkan abin da Isra'ila suka yi wa Amoriyawa.3Mowab sun firgita kwarai saboda mutanen, domin suna da yawa. Mowab sun ji tsoron mutanen Isra'ila kwarai.4Sarkin Mowab ya cewa dattawan Midiyanawa, "Wannan taro zai cinye dukkan abin da ke kewaye da mu, kamar yadda sã ya kan cinye ciyawar saura" Yanzu Balak ɗan Zippor wanda ke sarkin Mowab a wancan lokacin.5Ya aika da manzanni zuwa wurin Balaam dan Beyor, a Fetor wadda ke kusa da Kogin Yuferatis, a cikin ƙasar al'ummar mutanensa. Ya kira shi ya ce, "Duba, mutane sun zo nan daga Masar. Sun rufe fuskar duniya, ga shi suna zaune kusa da ni.6Ina roƙonka ka zo, ka la'anta mutanen nan domi na, gama suna da ƙarfi sosai fiye da ni. Ko ya yiwu in ci su, in kore su daga ƙasar. Na sani duk wanda ka sawa albarka zai albarkatu, wanda kuwa ka la'anta zai zama la'ananne."7Sai dattawan Mowab da dattawan Midiyanawa suka tafi, suka ɗauki ladar duba tsibbu. Suka tafi wurin Balaam suka faɗa masa saƙon Balak.8Balaam yace da su, "Ku kwana a nan. Ni kuwa zan baku abin da Yahweh ya faɗa mani." Shugabannin Mowab suka tsaya suka kwana tare da Balaam.9Allah kuwa ya zo wurin Balaam yace,10"Su wane ne mutanen dake tare da kai? Balaam ya amsa wa Allah, Balak ɗan Zippor, sarkin Mowab, ya aiko su gare ni. Ya ce,11'Duba, mutanen da suka zo daga Masar suka cika fuskar ƙasata. Yanzu zo ka la'anta su domi na. Watakila zan iya faɗa da su, har in kore su.'"12Allah ya amsa wa Balaam, "Ba za ka tafi tare da mutanen ba, ba kuwa za ka la'anta mutanen Isra'ila ba domin masu albarka ne."13Balaam ya tashi da safe ya yi magana da shugabannin Balak, "Ku koma ƙasarku gama Yahweh ya hana ni in tafi tare da ku."14Shugabannin Mowab suka koma wurin Balak. Suka ce, "Balaam ya ƙi ya taho tare da mu."15Sai Balak ya sake aiken shugabannin, kuma masu yawa masu daraja fiye dana fari.16Suka zo wurin Balaam suka ce da shi, "Balak ɗan Zippor ya faɗi wannan, 'Idan ka yarda kada ka bar wani ya hana ka zuwa gare ni,17gama zan biya ka sosai, za a ɗaukaka ka ƙwarai, kome kuwa ka faɗa mani in yi, zan yi. Ka zo ka la'anta wannan jama'a domi na.'"18Balaam ya amsa, yacewa mutanen Balak, "Ko da a ce Balak zai bani fadarsa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Yahweh, Allahna ba, ba zan ƙara wani abu ko in rage ba sai dai abin da ya faɗa mani.19Amma yanzu, ina rokonku ku kwana a nan, har in san abin da Yahweh zai sake faɗa mani."20Allah ya zo wurin Balaam da dare, ya ce masa, "Tun da mutanen nan sun zo kiran ka ne, sai ka tashi, ka tafi tare da su, amma abin dana umarce ka kaɗai za ka yi."21Balaam ya tashi da safe, ya yi wa jakarsa shimfiɗa, ya tafi tare da shugabannin Mowab.22Amma saboda ya tafi, fushin Allah ya yi zafi. Mala'ikan Yahweh ya tsaya a hanya kamar wani ya tarye Balaam, wanda ya ke bisa jakarsa. Barorin Balaam biyu na tare da shi.23Jakar kuwa ta ga mala'ikan Yahweh na tsaye kan hanya da takobi zare a hannunsa. Sai jakar ta kauce daga hanya ta shiga saura. Balaam ya bugi jakar don ta juyo a kan hanyar.24Sai mala'ikan Yahweh ya tsaya a inda hanyar ta yi matsatsi a tsakanin bangayen gonakin inabi, bango a gefen damarsa da bango gefen hagunsa.25Jakar ta ga mala'ikan Yahweh kuma. Sai ta matsa a jikin bango, ta goge ƙafar Balaam ga bangon. Balaam ya sake bugunta.26Mala'ikan Yahweh kuma ya sha kanta ya tsaya a ƙuntataccen wuri inda ba wurin juyawa zuwa dama ko hagu.27Jakar ta ga mala'ikan Yahweh, sai ta kwanta a ƙafafun Balaam. Sai Balaam ya husata ya bugi jakar da sandarsa.28Sa'an nan Yahweh ya buɗe bakin jakar har ta yi magana. Ta ce da Balaam, "Me nayi maka da ka buge ni har sau uku?"29Balaam ya amsa wa jakar, "Domin kin shashantar da ni. Dama a ce ina da takobi a hannuna, da na kashe ki."30Jakar ta ce wa Balaam, "Ba ni ce jakarka ba wadda kake ta hawa dukkan lokacin rayuwarka har zuwa wannan ranar ba? Na taɓa yi maka haka? Balaam ya ce, "A'a."31Sa'an nan Yahweh ya buɗe idanun Balaam, ya ga mala'ikan Yahweh na tsaye a hanya da takobi zare a hanunsa. Balaam ya sunkuyar da kansa, ya faɗi rubda ciki.32Mala'ikan Yahweh yace da shi, "Meyasa ka bugi jakarka har sau uku? Duba, na fito ne kamar wani abokin gãba don ayyukanka a wuri na mugunta ne.33Jakar ta gan ni, ta kauce mani har sau uku. Da a ce bata kauce mani ba, lallai da na kashe ka, in bar ta da rai."34Balaam ya cewa mala'ikan Yahweh, "Na yi zunubi. Ban san ka tsaya gãba da ni a hanya ba. To yanzu, idan ka ga mugun abu ne, sai in koma."35Amma mala'ikan Yahweh ya cewa Balaam, "Tafi tare da mutanen. Amma abin da na faɗa maka shi kaɗai zaka faɗa." Sai Balaam ya tafi tare da shugabannin Balak.36Sa'ad da Balak ya ji Balaam ya zo, ya fita ya tarye shi a birnin Mowab a Arnon, wadda ke kan iyaka.37Balak yace wa Balaam, "Ashe, ban aika a kirawo ka ba? Meyasa baka zo wurina ba? Ko ban isa in ɗaukaka ka ba ne?"38Sai Balaam ya amsa wa Balak yace, "Ga shi, na zo gare ka. Ina da wani ikon yin wata magana ne? Zan iya faɗin maganar da Allah ya sa a bakina ne kawai."39Balaam ya tafi tare da Balak, suka je Kiriyat Huzot.40Sai Balak ya yi hadaya da sã da tunkiya ya aika wa Balaam da shugabannin da ke tare da shi.41Washegari, Balak ya ɗauki Balaam ya kai shi kan tudu wurin Ba'al. Daga wurin Balaam ya ga wasu daga mutanen Isra'ilawa a zangonsu.
Isra'ilawan sun yi zango a gabanci Kogin Urdun. Yeriko na yammacin kogin.
Dã Balak sarkin Mowab ne.
Ziffor shine mahaifin Balak.
Waɗanna maganganu biyu na nufin abu ɗaya, kuma na nanata yadda Mowab sun firgita.
A nan "Mowab" na nufin mutanen Mowab. AT: "Dukkan Mowabawan sun firgita"
"domin suna da yawa"
Mowabawan da Madayanawa ƙungiyan mutane biyu ne, amma Madayanawa suna zama a ƙasar Mowab a wancan lokaci.
An yi magana game da yadda Isra'ilawa za su hallaka abokan gãbansu sai ka ce su sã ne wanda ke cin ciyawa a gona.
Wannan ya fara bayani game da Balak.
"Balak ya aika da masu kai saƙo"
Wannan shine sunan mahaifin Bal'amu.
Wannan sunan birni ne.
"na ƙasar Bal'amu da mutanensa"
"Balak ya kira Bal'amu." Balak bai yi magana da Bal'amu ido da ido ba amma ta wurin mai kai saƙon da ya aika.
Wannan na nanata yawan sun ne. AT: "Yawan sun ya fi a kirga"
"kore su a guje"
AT: "Na san ka na da iko ka albarkaci ko kuwa ka la'anta mutanen"
Ana iya bayana wannan suna "duba" cikin kalma da ke nuna aiki. AT: "biya kuɗi don Bal'amu ya la'anta Isra'ila"
Za ka iya cewa "sun je wurin Bal'amu"
AT: "faɗa masa saƙo daga Balak"
Wannan sunan namiji ne. Duba yadda ka juya wannan cikin 22:2.
An yi magana game da rohoton Bal'amu sai ka ce wani abu ne wanda zai ɗauka ya kai wa masu kai saƙon. AT: "zan faɗa maka"
"Allah ya bayyana ga Bal'amu"
Yahweh ya yi amfani da tambaya don ya gabatar da sabuwan kan magana. Ana iya juya wannan tambayar gangancin zuwa magana. AT: "Gaya mini game da mutanen na da suka zo wurin ka."
Waɗannan sunayen maza ne. Dubi yadda ka juya waɗannan cikin 22:2.
Bal'amu ya sake faɗin saƙon da Balak ya aika masa. Dubi yadda ka juya waɗannan maganganu cikin 22:5.
"kore su a guje"
AT: "domin na sa musu albarka"
Wannan sunan nan mutum na miji. Duba yadda ka juya wannan cikin 22:2.
Mai yiwuwa za ku so ka ce "Sun tafi wurin Bala'am"
Wannan sunan mutun na miji ne. Duba yadda ka juya wannan cikin 22:2.
Wannan suna na nufin Isra'ilawa a matsayin ƙungiya. AT: "wannan ƙungiyar mutane"
Wannan sunan namiji ne. Duba yadda ka juya wannan cikin 22:2.
Bal'amu bayani a kan abin da ba zai taba faruwa ba. Ya na nanata cewa babu wani abin da zai iya sa shi ya yi rashi biyayya ga Yahweh.
Wannan na nufin cewa Bal'amu ba zai iya yi wa Yahweh rashin biyayya ba ko da a wata hanya ne.
shimfiɗa wata wurin zama ne da ake sa bayan dabba don hawa a yi tafiya da shi.
AT: "Allah ya yi fushi ƙwarai da gaske"
"kamar abokin gãban Bal'amu" ko kuwa "don ya hana Bal'amu"
An cire takobi daga gidan ta saboda a yi amfani da shi. AT: "da takobinsa a shirye don kai hari"
Jakar ta yi hakan don ta guje wa mala'ikan Yahweh.
Wasu lokuta a kan dubi dabbobi a matsayin "ta" ko "ita." AT: "juya bayar ta"
Wannan shirin guje wa mala'ikan Yahweh da ke kan hanyar.
Wasu lokuta a kan dubi dabbobi a matsayin "ta" ko "ita."
"tura ƙafar Bal'amu ga bangon" ko "yi wa Bal'amu rauni a bangon"
Dubi yadda kun juya magana makamanci haka cikin 22:21. AT: "Bal'amu ya husata ƙwarai da gaske"
Buɗe bakin na nufin ba da zarafin iya yin magana. AT: "Sa'an nan Yahweh ya sa jakar ta iya yi magana kamar ɗan adam ke yi"
"Jakar ta ce wa Bal'amu"
An yi amfani da wannan tambayar gangancin don a tabbatar wa Bal'amu cewa shari'ar da ya yi wa jakar ba daidai ba ne. Ana iya juya wannan cikin magana. AT: "Ni ne jakar da kake da hawa dukkan rayuwar ka, har wa yau."
An yi amfani da wannan tambayar gangancin don a tabbatar wa Bal'amu cewa shari'ar da ya yi wa jakar ba daidai ba ne. Ana iya juya wannan cikin magana. AT: "Ban taɓa yi maka wannan hali ba"
A "buɗe wa wani ido" na nufin cewa ya iya gani. AT: "Sa'an nan Yahweh ya ba wa Bal'amu iyawa don ya ga mala'ikan Yahweh"
An cire takobi daga gidan ta saboda a yi amfani da shi. Dubi yadda ka juya wannan cikin 22:21 AT: "da takobinsa a shirye don kai hari"
Wannan na nuna cewa Bal'amu ya kaskantar da kansa a gaban mala'ikan.
An yi amfani da tambayar ganganci don a zargi Bal'amu da yi abin da ba daidai ba. Ana iya juya wannan cikin magana. AT: "Bai kamata ka bugi jakar ka sau uku ba."
"kamar abokin gãban ka" ko "gãba da kai"
Wannan magana na nuna abin dama zai faru, amma bai faru ba domin abin da jakar ta yi ya cece Bal'amu.
"To idan ba ka so in cigaba da tafiya" (UDB)
"shugabanin da Balak ya aika." Dubi yadda ka juya "Balak" cikin 22:2.
Wannan sunan kogi ne. Dubi yadda kun juya wannan cikin 21:12.
An yi amfani da wannan tambayar gangancin do a sauta wa Bal'amu don ya yi jinkiri zuwa. Ana iya juya wannan cikin magana. AT: "Hakika na aiki mazaje su kira ka."
An yi amfani da wannan tambayar gangancin do a sauta wa Bal'amu don ya yi jinkiri zuwa. Ana iya juya wannan cikin magana. AT: "Ai da ka zo wuri na"
An yi amfani da wannan tambayar gangancin do a sauta wa Bal'amu don ya yi jinkiri zuwa. Ana iya juya wannan cikin magana. AT: "Ka sani cewa lallai zan iya biyan kuɗi don ka zo wuri na."
Bal'amu ya yi amfani da wannan tambayan gangancin do ya gaya wa Balak cewa ba zai iya yin dukka abin da Balak ya ce masa ya yi ba. AT: "Amma ba ni da iko in ce wani abu da ina so"
A nan "kalmoni" na nufin saƙo daga Allah. An yi magana game saƙon sai ka ce wani abu ne da Allah ya sa cikin bakinsa. AT: "saƙon da Allah na so in faɗa"
Wannan sunan gari ne.
"wasu nama daga cikin hadayun"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) wannan na nufin wuri ɗaya ne da Bamot cikin 21:19. Kalman nan Bamot na nufin "wuri mai tuɗu", ko 2) wannan wani wuri ne kuma inda mutane da yin hadaya ga Ba'al.
1Balaam ya cewa Balak, "Ka gina mani bagadai guda bakwai a nan, ka shirya bijimai bakwai da raguna bakwai."2Balak ya yi yadda Balaam ya bukace shi ya yi. Sai Balak da Balaam suka miƙa bijimi da rago a kan dukkan bagadan.3Balaam yace da Balak, "Tsaya kusa da bayarwar ƙonawa, ni kuwa zan tafi can. Watakila Yahweh zai sadu da ni. Duk abin da ya bayyana mani zan faɗa maka." Ya kuwa tafi wani fako a kan tudu wurin da ba itatuwa.4A lokacin da yake a kan tudu, Allah ya sadu da shi, Balaam yace da shi, "Na riga na shirya bagadai bakwai, na kuwa miƙa bijimai guda da rago guda a kan kowanne bagadi."5Yahweh ya sa magana a bakin Balaam yace, "Koma wurin Balak, ka yi magana da shi."6Sai ya koma wurin Balak, wanda ke tsaye kusa da hadayar ƙonawarsa, da dukkan shugabannin Mowab tare da shi.7Balaam kuwa ya fara maganarsa ta annabci ya ce, "Balak ya kawo ni daga Aram, sarkin Mowab daga duwatsun gabas. 'Zo, la'anta Yakubu domi na,' ya ce, 'Zo, ka tsine wa Isra'ila.'8Ƙaƙa zan iya la'anta waɗanda Allah bai la'antar ba? Ƙaƙa zan iya tsine wa waɗanda Yahweh bai tsine wa ba?9Gama daga kan duwatsu na gan shi, daga bisa kan tuddai na hange shi. Duba, akwai mutane waɗanda ke zama su kaɗai, ba su ɗauki kansu a bakin kome ba a cikin jama'a.10Wa zai iya ƙidaya ƙurar Yakubu ko ya iya yin lissafin ɗaya bisa hudu na Isra'ila? Ka sa in mutu mutuwar adalin mutum, ka sa in mutu cikin salama kamar irin mutuwarsa."11Balak ya cewa Balaam, "Me kenan ka yi mani? Na kawo ka ka la'anta abokan gãbana amma ga shi sai albarka kake sa masu."12Balaam ya amsa ya ce, "Ba zan yi hankali da abin da zan ce abin da Yahweh ya sa a bakina ba?13Balak yace da shi, "Idan ka yarda zo tare da ni zuwa wani wuri inda za ka gan su. Za ka gansu a kurkusa, ba dukkansu ba. A can sai ka la'anta su domi na."14Ya kuwa ɗauki Balaam a cikin filin Zofim, a bisa Dutsen Fisga, ya gina bagadai bakwai. Ya miƙa bijimi da rago a kan kowanne bagadi.15Sai Balaam yace da Balak, "Tsaya nan kusa da hadayarka ta ƙonawa, ni kuwa in tafi in sadu da Yahweh a can.16Yahweh kuwa ya sadu da Balaam, ya sa masa magana a bakinsa. Ya ce, "Koma wurin Balak ka faɗa masa maganata."17Balaam ya koma wurinsa, ga shi a tsaye kusa da bayarwarsa ta ƙonawa, shugabannin Mowab na tare da shi. Balak yace da shi, "Me Yahweh ya ce?"18Balaam ya fara annabcinsa. Ya ce, "Tashi, Balak, ka ji. Ka saurare ni, ya ɗan Ziffor.19Allah ba mutum ba ne, da zai yi ƙarya, ko kuwa mutum ne, da zai canza tunaninsa. Ya yi wani alƙawarin da bai cika shi ba? Ko ya ce zai yi wani abu kuma bai yi shi ba?20Duba, an umarce ni in sa albarka. Allah ya bada albarka, ba zan iya janye ta ba.21Ya ga babu mugunta a Yakubu ko wahala a Isra'ila. Yahweh Allahnsu na tare da su, suna sowa domin sarkinsu na cikinsu.22Allah ne ya fishe su daga Masar da ƙarfi kamar kutunkun ɓauna.23Babu wata maitar da zata cuci Yakubu, ba sihirin da zai cuci Isra'ila. Maimakon haka dole ace da, Yakubu da Isra'ila, 'Duba abin da Allah ya yi!'24Duba, mutane sun tashi kamar ƙaƙƙarfan zaki, yadda zai fito ya hallakar. Ba ya kwantawa har sai ya cinye ganimarsa, ya lashe jinin abin da ya kashe."25Sai Balak ya cewa Balaam, "Kada ka la'anta su ko ka albarka ce su dukka."26Amma Balaam ya amsa ya ce da Balak, "Ban faɗa maka ba, zan faɗi dukkan abin da Yahweh ya ce da ni shi zan ce?"27Balak ya amsa wa Balaam, "Ka zo yanzu, zan ɗauke ka zuwa wani wuri. Watakila Allah zai yarda ka la'anta su a can domi na."28Balak kuwa ya kai Balaam a ƙwanƙolin Dutsen Feyor, wanda ke fuskantar hamada.29Balaam yace da Balak, "Gina mani bagadai bakwai a nan ka shirya bijimai bakwai da raguna bakwai."30Balak ya yi yadda Balaam ya ce ya yi; ya miƙa hadayar bijimi da rago a kan kowanne bagadi.
Wannan sarkin Mowab ne. Duba yadda ka juya wannan cikin 22:2.
"kashe bijimai bakwai da raguna bakwai a matsayin hadaya"
"Tsaya a nan da baikon ka na ƙonawa, ni kuma zan tafi nesa"
An riga an bayana cewa ya mika waɗannan dabbobin a matsayin baikon ƙonawa. AT: "Na kashe bijimi da rago, na kuma ƙona su a matsayin hadaya"
A nan an yi magana game da cewa Yahweh ya ba wa Bal'amu saƙo sai ka ce Yahweh ya sa ta cikin bakinsa ne. AT: "Yahweh ya gaya wa Bal'amu abin da yana so ya faɗa wa Balak"
Waɗannan maganganu biyun na nufin abu ɗaya.
Waɗannan maganganu biyun suna nufin abu ɗaya. Su na nanata cewa Balak yana so Bal'amu ya la'anta mutanen Isra'ila.
Waɗannan tambayoyin ganganci na nanata cewa Bal'amu ya ƙi ya yi wa Allah rashin biyayya. Ana iya juya wannan kamar magana. AT: "Amma ba zan iya la'anta waɗanda Allah bai la'anta ba. Ba zan iya yaƙi da waɗanda Yahweh ba ya yaƙi da su ba!"
Waɗannan maganganu biyun suna nufin abu ɗaya. Bal'amu ya dubi Isra'ila daga bisa tuɗu.
A nan "shi" na nufin mutanen Isra'ila.
"Akwai ƙungiyan mutane"
AT: "dun dubi kansu a matsayi al'umma ta musamman"
Ana iya Juya wannan tambayar ganganci cikin magana. AT: "Akwai mutanen Isra'ilawa fiye da yadda za a ƙidaya. Babu wanda zai iya ƙidaya ɗaya bisa huɗu na Isra'ila saboda suna da matuƙar yawa."
An fahimci cewa wannan mutuwa ce cikin salama. AT: "mutuwar mutum mai adalci cikin salama"
Waɗannan suna duban mutanen Isra'ila a matsayin mutum ɗaya.
Wannan shine sarkin Mowab. Dubi yadda ka juya wannan cikin 22:2.
Balak ya yi amfani da wannan tambayar don ya sauta wa Bal'amu. Ana iya juya wannan tambayar gangancin cikin magana. AT: "Ban sammani za ka yi mini wannan abu ba!"
Wannan na nanata abin mamaki da ya biyo baya.
Bal'amu ya yi amfani da wannan tambayar ganganci don ya kare kansa don abin da ya yi. Ana iya juya wannan cikin magana. AT: "Lallai ne in yi hankali don in faɗa abin da Yahweh ya ce mini in faɗa kawai."
An yi magana game da saƙon sai ka ce wani abu ne da Allah ya sa a cikin bakinsa. Dubi yadda ka juya magana makamanci haka cikin 22:38. AT: "faɗa abin da Yahweh yana so in faɗa kawai"
"A can za ka la'anta mini Isra'ilawan"
Masu juyi zai su iya ƙara magana a ƙasa wanda ke cewa: "Kalman nan "Zofim" na nufin "yi tsaro" ko kuwa "megewaye"
Wannan sunan tsauni ne. Duba yadda ka juya wannan cikin 21:19.
Dubi yadda ka juya magana makamancin haka cikin 22:38.
"Sai Yahweh ya ce"
Waɗannan maganganu biyun suna nufin abu ɗaya an kuma sake faɗa don a nanata yaddaa yake da muhimmanci Balak ya saurara.
Wannan na nufin Balak. Duba yadda ka juya wannan cikin 22:2.
Duk waɗannan tambayoyin suna nufin abu ɗaya, suna kuma nanata cewa Allah na yin duk abin da ya ce zai yi. AT: "Bai taba yin wani alƙawarin abu da ba cika ba. A kullayomi ya kan yi daidai abin da ya ce zai yi."
AT: "Allah ya umurce ni in Albarkaci Isra'ilawan"
Waɗannan maganganu biyun suna nufin abu ɗaya. Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) Allah ya ba wa Isra'ila abubuwa masu kyau ko 2) babu zunubi a Isra'ila wanda ya sa shi ya hukunta su.
"sun yi sowa da farin ciki saboda Yahweh shine sarkin su"
Wannan na nufin cewa ƙarfin Yahweh kamar ɓauna ne.
faɗin mummunan abu kan Isra'ila- Waɗannan maganganu biyun suna nufin abu ɗaya, cewa babu wata la'anar da wani ya sa wa al'umman Isra'ila, babu wanda zai kama su. A nan "Yakub" na nufin Isra'ila.
AT: "lallai ne mutane su ce"
Wannan na nufin cewa Allah ya yi musu abu mai kyau. AT: "Dubi abubuwa masu kyau da Allah ya yi musu!"
Wannan aya wata karin magana ne da ke maganar cewa Isra'ila ta ci nasara bisa abokan gãban ta sai ka zaki ne da ya kashe naman jeji.
Wannan shine sarkin Mowab. Dubi yadda ka juya wannan cikin 22:2.
Bal'amu ya yi amfani da wannan tambayar gangacin don ya tunashe Balak cewa Bal'amu ya ƙi ya yi wa Allah rashin biyayya tun ma kamin ya zo wurin Balak. AT: "Na gaya maka dã cewa lallai ne in faɗi dukk abin da Yahweh ya ce mini in faɗa."
An fahimci cewa wannan hamadar na daidai in da Isra'ila ta kafa zangon ta. AT: "wanda ke fuskantar hamadar daida inda Isra'ila ta ke"
1Da Balaam ya ga Yahweh ya ji daɗin da aka sawa Isra'ila albarka, bai tafi ba, kamar waɗancan lokutan, don ya yi aiki da tsafi. Maimakon haka, sai ya duba wajen jeji.2Ya tada idanunsa, ya ga Isra'ila sun yi zango, kowa a cikin kabilarsu, Ruhun Allah ya sauko masa.3Ya karɓi wannan annabci, ya ce, "Balaam ɗan Beyor ne ke magana, mutumin da idanuwansa a buɗe suke.4Ya faɗa, an ji maganar Allah. Ya ga wahayi daga wurin Maɗaukaki. A gaban wanda ke durƙushe tare da idanuwansa a buɗe.5Yaya kyan alfarwarka, Yakubu, a wurin da ka zauna, Isra'ila!6Kamar kwarurruka suka bazo, kamar gonaki a gefen kogi, kamar itatuwan aloyes da Yahweh ya dasa, kamar itatuwan al'ul a gefen ruwaye.7Ruwa na malalowa daga bokatansu, iri ya jiƙu sosai. Sarkinsu zai fi Agag girma, za a ɗaukaka mulkinsu.8Allah ne ya fisshe su daga Masar da iko kamar kutunkun ɓauna. Zai cinye al'ummai waɗanda suka yi faɗa gãba da shi. Zai kakkarya ƙasusuwansu gutsu gutsu. Zai harbe su da kibiyoyinsa.9Zai laɓe a ƙasa kamar zaki, kamar zakanya. Ba bu wanda zai dame shi? Bari duk wanda ya albarka ce shi ya yi albarka; duk wanda ya la'anta shi ya zama la'ananne."10Balak ya husata da Balaam, ya tafa hannunsa a cikin fushi. Balak yace da Balaam, "Na kirawo ka ka la'anta maƙiyana, amma ga shi har sau uku kana sa masu albarka.11Yanzu sai ka tafi gidanka. Na ce zan ɗaukaka ka, amma ga shi Yahweh ya hana ka samun wani lada."12Sai Balaam ya amsa wa Balak, "Na faɗa wa manzanninka waɗanda ka aiko gare ni.13Idan Balak ya ba ni fadarsa cike da azurfa da zinariya, ba zan iya in zarce maganar Yahweh ba, da wani mugun abu ko mai kyau ne, kai kowanne irin abu ne zan so in yi. Zan faɗi abin da Yahweh ya faɗa mani shi zan ce.' Ban faɗa masu haka ba?14Saboda haka yanzu, ga shi, zan koma ga mutanena. Amma da farko bari in gargaɗe ka abin da waɗannan mutane za su yiwa mutanenka a ranaku masu zuwa."15Balaam ya fara wannan annabci. Ya ce, "Balaam ɗan Beyor ya faɗa, mutumin da idanunsa ke buɗe.16Wannan shi ne annabcin wanda yake jin magana daga Allah, wanda ke da ilimi daga wurin Maɗaukaki, wanda ke da wahayi daga Mai Iko Dukka, A gaban wanda yake durƙurshe tare da idannunsa a buɗe.17Na gan shi, amma baya nan yanzu. Ina hangensa, amma baya kusa. Tauraro zai fito daga cikin Yakubu, kendir zai fito daga cikin Isra'ila. Za ya ragargaje shugabannin Mowab ya hallaka dukkan zuriyar Shitu.18Sai Idom ta zama mallakar Isra'ila, Seyir kuma za ta zama mallakarsu, abokan gãbar Isra'ila, waɗanda Isra'ila zasu ci da ƙarfi.19Daga cikin Yakubu sarki zai zo wanda zai yi mulki, zai hallaka waɗanda suka ragu a birninsu."20Sai Balaam ya dubi Amalek ya fara annabcinsa. Ya ce, "Amalek mafi girma ne cikin al'ummai, amma ƙarshensa zai kasance hallaka."21Sai Balaam ya duba zuwa wajen Kan'aniyawa, ya fara annabcinsa. Ya ce, "Wurin da kuke zama mai ƙarko ne, gidajenku kuma na cikin duwatsu.22Duk da haka ku Kan'aniyawa za a lalatar da ku da wuta idan Asiriyawa suka ɗauke ku bayi."23Sai Balaam ya fara annabcinsa na ƙarshe. Ya ce, "Kaito! Wa zai rayu sa'ad da Allah ya yi wannan24Jiragen ruwa kuwa za su zo daga gaɓar tekun Kittim; za su faɗawa Asiriya, zasu ci Eber, amma kuma, ƙarshensu hallaka ce."25Sai Balaam ya tashi ya tafi. Ya koma gidansa, Balak ma yayi tafiyarsa.
"kamar yadda ya yi a dã"
A nan "ya ta da idanunsa" na nufin cewa ya dubi sama. AT: "Ya dubi sama"
Wannan na nufin cewa Ruhun Allah ya shugabanci shi ya yi annabci.
AT: "Allah ya ba shi wannan annabci"
Beyor mahaifin Bal'amu ne. Duba yadda ka juya wannan cikin 22:5.
Wannan na nufin cewa yana gani kuma ya fahimta a fili.
Bal'amu ya cigaba da annabci ƙarƙashin ikon mulkin Ruhun Allah.
A nan Bal'amu na nufin kansa a mastayin "sa"
Wannan halin ƙaskanci.
A nan "idanu a buɗe" na nufin cewa Bal'amu ya sami iyawa na sanin abin da Allah yana so ya faɗa.
Duk waɗannan maganganu suna nufin abu ɗaya. Su na nanata cewa zangon ya yi wa Bal'amu kyau.
Bal'amu ya cigaba da annabci tawurin shugabanci Ruhu Allah.
Bal'amu yana magana game da Isra'ilawa sai ka ce yawansu zai rufe gabadayan kwari.
Bal'amu yana magana game da Isra'ilawa sai ka ce gonaki da ke ba da amfani mai yawa.
Aloyes itatuwa ne da ke da anshi mai daɗi, wadda ke girma a busasshiyar ƙasa. Bal'amu ya yi magana game da Isra'ilawa sai ka ce za su cigaba cikin arxiki da lafiya, su kuma zama da kyau kamar itatuwa. AT: "aloyes wanda Yahweh ya shuka"
Itacen al'ul su ne itace mafi girma a Isra'ila. Bal'amu ya yi magana da Isra'ilawa sai ka ce sun yi girma kamar babbar itacen al'ul da ke samun ruwa sosai.
Tawurin ikon Ruhu Allah, Bal'amu ya cigaba da annabci.
ruwa- Ruwa a yalwace na nufin albarkar Allah bisa amfani gonaki a ƙasar. AT: "Allah zai albarkaci Isra'ila da ruwa a yalwace don amfanin gona"
ruwa- Ruwa a yalwace na nufin albarkar Allah bisa mutanen sa don su sami amfani gonaki a yalwace.. AT: "za su sami ruwa a yalwace don gonakin su su yi girm a kuma sami amfani mai kyau"
Waɗannan maganganu biyun na da ma'ana kusan iri ɗaya, su na kuma nanata yalwar albarka Allah bisan su in an kwatanta shi da sauran al'ummai.
A nan "girma" na nufin mafi daraja da iko. Wannan na nufin cewa sarkin mai zuwa na Isra'ila zai fi Agag daraja da iko. Agag sarkin Amalakawa ne.
AT: "sauran mutane za su daraja mulkinsu"
Tawurin ikon Ruhun Allah, Bal'amu ya cigaba da annabci.
"Allah ya fisshe Isra'ilawan"
Wannan na nufin cewa Isra'ilawan sun da ƙarfi sosai.
Bal'amu yana magana ne game da Isra'ilawa sai ka ce naman jeji ne da zai cinye abokan gãbansu. Wannan na nufin cewa za su hallak abokin gãbansu.
Ta wurin ikon Ruhun Allah, Bal'amu ya gama annabcinsa.
A nan Bal'amu ya kwatanta Isra'ilawa da zaki na miji da ta mace. Wannan na nufin cewa su abin ban tsoro ne kuma a kullayomi suna shirye su kai hari.
Bal'amu ya yi wannan tambayar don ya gargaɗi dukka mutanen kada su sa Isra'ila su husata. AT: "Babu wanda ya isa ya dame shi!"
AT: "Bari Allah ya albarkaci waɗanda sun albarkaci Isra'ilawan; bari ya la'anta waɗanda sun la'anta Isra'ilawan"
AT: "Balak ya husata ƙwarai da gaske"
Wannan alama ce na jin matuƙar takaici da fushi.
Bal'amu na bayana wani abu da ba zai taba yiwuwa ba. Wannan maganan na nufin cewa babu wani abin da zai sa Bal'amu ya yi wa Allah Rashin biyayya.
Bal'amu ya yi amfani da tambaya don ya tunashe Balak game da abin da ya faɗa tun da wuri. AT: "Na faɗa musu wannan."
"Isra'ilawan"
Beyor shine mahaifin Bal'amu. Duba yadda ka juya wannan cikin 22:5.
Wannan na nufin cewa yana gani kuma ya fahimta da kyau. Duba yadda ka juya wannan cikin 24:2.
Ana iya bayana kalman nan "ilimi" cikin aikatau. AT: "wanda ya san abubuwan da Allah maɗaukaki ya bayyana masa"
Wannan alama ce ta mika kai ga Allah.
Bal'amu ya cigaba da annabcinsa na fakor guda hudu.
Waɗannan maganganu biyun suna nufin abu ɗaya.Bal'amu ya zami wahayin abin da zai faru nan gaba. Kalman nan "shi" na nufin shugaban Isra'ila a nan gaba.
A nan "tauraru" na nufin sarkin Isra'ila da zai yi mulki.
A nan "Yakub" na nufin zuriyar Yakub. AT: "daga cikin zuriyar Yakub"
Wannan na nufin abu ɗaya da bangare na farko na jimlar. A nan "sandar sarauta" na nufin sarki mai matuƙar iko.
A nan "Isra'ila" na nufin Isra'ilawan nan gaba. AT: "daga cikin Isra'ilawa a nan gaba"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) zai ƙarye kan shugabannin Mowab ko 2) zai hallak shugabannin Mowab.
Wannan ma na nufin Mowabawa, wanda su zuriyar Shitu ne.
Bal'amu ya cigaba da annabcinsa na fakor guda hudu.
AT: "Isra'ilawa za su mallaki Edom"
A nan "Seyir" na nufin mutanen da ke zama a tuɗun Seyir. AT: "Isra'ila za ta yi nasara bisa mutanen Seyir"
Yakub kakan Isra'ila ne. "Yakub" na nufin dukka mutanen.
Wannan na nufin Ar inda Balak ya sadu da Bal'amu.
A nan "Amalek" na nufin mutanen ƙasar Amalek. Wahayin ta cigaba da cewa Bal'amu ya juya zuwa ƙasar Amalek, sa'an nan ya yi su annabcinsa game da Amalekawan.
An yi amfani da mufuradi "sa" domin an yi magana game da Amalekawan a matsayin mutum ɗaya.
Wannan sunan mutanen da ke daga zuriyar Ken.
"An tsare wurin da kuke zama ƙwarai da gaske"
Wannan na nufin cewa su na zama a wurin da aka tsare sosai. AT: "inda kuke na tsare kamar gida tsutsun da ke can kan dutse"
Ken ɗaya daga cikin ainihin biranen da Keniyawa suke zama ne. AT: "Duk da haka Assuriyawa za su hallak Keniyawa, su kuma ɗauke su a matsayin bayi"
Ba wanda zai rayu a sa'ad da Allah ya yi wannan!-
Wannan sunan wani birni ne da ke tsibirin da ke Takun Meditaraniya.
AT: "Allah zai hallaka su kuma"
1Isra'ila ta zauna a Shittim, maza suka fara yin karuwancinsu da matan Mowab,2domin Mowabawa sun gayyaci mutane zuwa wajen hadayar allolinsu. Saboda haka mutane suka ci suka durƙusa wa allolin Mowabawa.3Mutanen Isra'ila suka shiga bautawa gumakun Ba'al na Feyor, Yahweh ya yi fushi da Isra'ila.4Yahweh yace da Musa, "Kashe dukkan shugabannin mutanen, ka rataye su a gabana a nuna su a fili, don in huce daga fushi da nake yi da Isra'ila."5Musa kuwa ya cewa shugabanin Isra'ila, "Kowannen ku dole ya kashe mutanensa waɗanda suka shiga bautar gumakun Ba'al Feyor."6Sai ɗaya daga cikin mutanen Isra'ila ya zo, ya kawo mace Bamidiyaniya cikin iyalinsa. Wannan ya faru ne a idannun Musa da dukkan jama'ar mutanen Isra'ila, a sa'ad da suke kuka a ƙofar alfarwar taro.7Finehas ɗan Eliyeza ɗan Haruna firist, ya gani, sai ya tashi daga cikin jama'a, ya ɗauki mãshi a hannunsa.8Ya bi Ba'isra'ilen cikin alfarwa, ya soke dukkansu biyu, Ba'isra'ilen da macen. Da haka aka tsaida annobar da Allah ya aiko wa mutanen Isra'ila.9Waɗanda suka mutu saboda annobar sun kai jimilar mutane dubu ashirin da hudu.10Yahweh ya faɗa wa Musa ya ce,11"Finehas ɗan Eliyeza ɗan Haruna firist, ya kawar da fushina daga mutanen Isra'ila gama yayi kishi irin nawa a cikinsu. Saboda haka ba zan hallakar da mutanen Isra'ila da fushina ba.12Saboda haka ne, 'Yahweh ya faɗa, "Duba, ina ba Finehas alƙawarin salamata.13Dominsa da zuriyarsa zasu bi shi, alƙawarin da ba zai taɓa ƙarewa ba daga firistoci gama yana da kishi domin, Allahnsa. Ya kuwa yi kafara domin mutanen Isra'ila.'"'14Yanzu sunan Ba'isra'ilen da aka kashe tare da Bamidiyar, Zimri ɗan Salu, shugaban zuriyar iyalin Simiyonawa.15Sunan Bamidiyar wanda aka kashe, ita ce Kozbi 'ɗiyar Zur, wanda yake shi ne shugaban wata kabila na iyalin Midiyan.16Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,17"Ku fãɗa wa Midiyanawa abokan gãbarku, ku hallaka su,18gama sun yi maku kamar abokan gãbanku da makircinsu. Sun kai ku cikin mugun abu a kan Feyor da na Kozbi 'yar'uwarsu, ɗiyar shugaban Midiyan, wadda aka kashe a ranar da aka yi annoba a Feyor."
Wannan sunan wure ne a Mowab.
Wannan halin sujada ne.
Feyor sunan wani tsauni ne. Duba yadda ka juya wannan cikin 23:28.
Dubi Yadda ka juya magana makamancin wannan cikin 21:19. AT: "Yahweh ya yi fushi ƙwarai da gaske"
Na nufin cewa wannan na nufin shugabanin da ke laifin bautar gumaka. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "dukka shugabannin mutanen wanda suke da lafin bautar gumaka"
Wannan na nufin cewa shugabannin Isra'ila za su kashe waɗannan mutanen, a kuma bar gawakin su a fili inda mutane za su gani.
"ga shugabannin Isra'ila wanda ba su da laifin bautar gumaka"
Feyor sunan wani tsauni ne. Duba yadda ka juya wannan cikin 23:28.
wannan na nufin cewa ya kawo ta zuwa cikin zangon don ya kwana da ita. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "kawo mace Bamadayaniya zuwa zangon Isra'ila don ya kwana da ita"
A nan "a gaban" na nufin cewa sun ji game da ita, ko kuwa sun tarar da ita.
Wannan sunan ɗan Haruna ne. Duba Yadda ka juya shi cikin 3:1.
"Finehas ya bi"
An yi magana game da fushin Allah sai ka ce wani abu ne da za a iya tura shi gafe don a tsayar da shi. AT: "sa ni kada in yi fushi kuma da mutanen Isra'ila"
An yi magana gamd da Allah sai ka ce wani dabba ne da ke fushi har da zai iya cinye mutenen Isra'ila. AT: "ban hallak mutanen Isra'ila cikin mummunar fushina ba"
Wannan ya cigaba da magana game da magana Yahweh daga ayar da ke a baya. Wannan an ambaci abin da wani ya faɗa ne cikin abin da an faɗa. AT: "Saboda haka, gaya wa Finehas cewa zan ba shi ... mutanen Isra'ila."
Wannan ya koma zuwa ga ainihin zance game da Zimri da Kozbi.
AT: "wanda Finehas ya kashe"
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan sunan ta mace ce.
Ana iya juya sunan nan "makirci" cikin aikatau. AT: "ta wurin yauɗaran ku"
"Sun sa ku kun yi wannan mugun abu"
Waɗannan maganganu biyun suna nufin cewa waɗannan abubuwa sun faru ne a kan tuɗun Feyor.
Feyor sunan wani tsauni ne. Duba yadda ka juya wannan cikin 23:28.
AT: "wanda Finehas ya kashe"
1Ya zamana bayan annobar sai Yahweh ya yi magana da Musa da Eliyeza ɗan Haruna firist. Ya ce,2"Ku ƙidaya dukkan taron mutanen Isra'ila, daga mai shekaru ashirin zuwa gaba, bisa ga zuriyar kakanninsu, da dukkan waɗanda za su iya zuwa yaƙi domin Isra'ila."3Musa da Eliyeza firist suka yi masu magana a filayen Mowab daura da Yodan a Yeriko, suka ce,4"A ƙidaya mutane daga mai shekaru ashirin zuwa gaba kamar yadda Yahweh ya umarci Musa da mutanen Isra'ila, waɗanda suka fito daga ƙasar Masar."5Ruben shi ne ɗan fari na Isra'ila. Daga ɗansa Hanok kabilar Hanokiyawa ta zo. Daga Fallu kabilar Falluniyawa ta zo.6Daga Hesruna har zuwa kabilar Hezaroniyawa. Daga Karmi har zuwa kabilar Karmiyawa.7Waɗannan su ne kabilun Ruben, waɗannan yawansu ya kai jimilar mutane 43,730.8Eliyab shi ne ɗan Fallu.9'Ya'yan Eliyab su ne Nemuwel da Datan da Abiram. Waɗannan su ne Datan da Abiram waɗanda suka bi Korah a lokacin da suka yi wa Musa da Haruna ƙalubale, suka kuma yi tawaye ga Yahweh.10Ƙasa kuwa ta buɗe bakinta ta haɗiye su tare da Kora da dukkan mabiyansa suka mutu. A wancan lokaci, wuta kuma ta cinye mutane 250, waɗanda suka zama abin faɗakarwa.11Amma iyalin Kora ba su mutu ba.12Kabilar zuriyar Simiyon su ne waɗannan: Ta wurin Nemuwel, aka sami kabilar Nemuwelawa, ta wurin Yamin, kabilar Yaminawa, ta wurin Yakin, kabilar Yakinawa,13ta wurin Zera, kabilar Zerawa, ta wurin Shawul, kabilar Shawulawa.14Waɗannan su ne kabilun zuriyar Simiyon, waɗanda aka ƙidaya jimilar mutane 22,200.15Kabilar zuriyar Gad su ne waɗannan: Ta wurin Zifon, aka sami kabilar Zifonawa, ta wurin Haggi, kabilar Haggiyawa, ta wurin Shuni, kabilar Shuniyawa16ta wurin Ozni, kabilar Oziniyawa, ta wurin Eri, kabilar Eritiyawa,17ta wurin Arod kabilar Arodiyawa, ta wurin Areli, aka sami kabilar Areliyawa.18Waɗannan su ne kabilar zuriyar Gad sun kai jimilar mutane 40,500.19'Ya'yan Yahuda su ne Er da Onan, amma waɗannan mutane sun rasu a ƙasar Kan'ana.20Sauran kabilar zuriyar Yahuda su ne: ta wurin Shela, kabilar Shelatawa, ta wurin Feresa, kabilar Feresawa, da ta wurin Zera, kabilar Zerawa.21Zuriyar Ferez su ne: Ta wurin Hezron, kabilar Hezronawa, ta wurin Hamul, kabilar Hamulawa.22Waɗannan su ne zuriyar kabilar Yahuda sun kai jimilar mutane 76,500.23Kabilar zuriyar Issaka su ne: Ta wurin Tola, kabilar Tolawa, ta wurin Fuwa, kabilar Fuwayawa,24ta wurin Yashub, kabilar Yashubawa, ta wurin Shimron, kabilar Shimronawa.25Waɗannan su ne kabilun Issaka, waɗanda sun kai jimilar mutane 64,300.26Zuriyar kabilar Zebulun su ne waɗannan: Ta wurin Sered, kabilar Seredawa, ta wurin Elon, kabilar Elonawa, ta wurin Yaleyel, kabilar Yaleyawa.27Waɗannan su ne kabilun Zebulun, sun kai jimilar mutane 60,500.28Zuriyar kabilar Yosef su ne Manasse da Ifraim.29Zuriyar Manasse su ne waɗannan: ta wurin Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Giliyad), ta wurin Giliyad, kabilar Gilidiyawa.30Zuriyar Giliyad su ne waɗannan: Ta wurin Leza, kabilar Lezawa, ta wurin Helek, kabilar Helekawa,31ta wurin Asriyel, kabilar Asrilawa,32ta wurin Shekem, kabilar Shekemawa, ta wurin Shemida, kabilar Shemidawa, ta wurin Hefer, kabilar Heferawa.33Zelofehad ɗan Hefer ba shi da 'ya'ya maza, amma sai 'ya'ya mata kaɗai. Sunayen 'ya'yansa mata su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka daTirza.34Waɗannan su ne kabilar Manasse, sun kai jimilar mutane 52,700.35Zuriyar kabilar Ifraim su ne waɗannan: Ta wurin Shutela, kabilar Shutelawa, ta wurin Beker, kabilar Bekerawa, ta wurin Tahat, kabilar Tahatawa.36Zuriyar Shutela su ne, ta wurin Eran, kabilar Eraniyawa.37Waɗannan su ne zuriyar kabilar Ifraim, sun kai jimilar mutane 32,500. Waɗannan su ne zuriyar Yosef an lissafta kowanne bisa ga kabilunsu.38Zuriyar kabilar Benyamin su ne waɗannan: Ta wurin Bela, kabilar Belayawa, ta wurin Ashbel, kabilar Ashbelawa, ta wurin Ahiram, kabilar Ahiramawa,39ta wurin Shefufam, kabilar Shefufamawa, ta wurin Hufam, kabilar Hufamawa.40'Ya'yan Bela maza su ne Ard da Na'aman. Daga Ard aka sami kabilar Ardawa, daga Na'aman aka sami kabilar Na'amawa.41Waɗannan su ne zuriyar Benyamin. Yawan mutane 45,600 ne.42Zuriyar kabilar Dan su ne, ta wurin Shuham, aka sami kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne zuriyar kabilun Dan.43Dukkan kabilun Shuhamawa sun kai yawan mutane 64,400.44Zuriyar kabilar Asha su ne waɗannan: Ta wurin Imna, kabilar Imnawa, ta wurin Ishbi, kabilar Ishabawa, ta wurin Beriya, kabilar Beriyawa.45Zuriyar Beriya su ne waɗannan: Ta wurin Hebar, kabilar Hebarawa, ta wurin Malkiyel, kabilar Malkiyawa.46Sunan 'yar Asha Sera.47Waɗannan su ne zuriyar kabilun Asha, sun kai jimilar mutane 53,400.48Zuriyar kabilar Naftali su ne waɗannan: Ta wurin Yazeyel, kabilar Yazelawa, ta wurin Guni, kabilar Guniyawa,49ta wurin Yezer, kabilar Yezerawa, ta wurin Shilem, kabilar Shilemawa.50Waɗannan su ne zuriyar kabilun Naftali sun kai jimilar mutane 45,400.51Wannan shi ne cikakken lissafin maza a cikin mutanen Isra'ila: 601,730.52Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,53"Dole a raba ƙasar ga waɗannan mutane gãdo bisa ga yawan sunayensu.54Za ka ba babbar kabila babban rabon gãdo, ka ba karamar kabila karamin rabon gãdo. Kowacce kabila za a ba ta gãdo bisa ga yawan mutanenta da aka lissafta.55Amma za a rarraba ƙasar ta wurin kuri'a. Za su gaji ƙasar yadda aka raba a tsakanin kabilun kakanninsu.56Za a rarraba gãdo tsakanin manya da ƙananan kabilai ta hanyar kuri'a."57Kabilar Lebiyawa da aka ƙidaya bisa kabila kabila, su ne waɗannan: Ta wurin Gershon, kabilar Gershawa, ta wurin Kohat, kabilar Kohatiyawa, ta wurin Merari, kabilar Merariyawa.58Kabilar Lebi su ne waɗannan: kabilar Lebiyawa da kabilar Hebroniyawa da kabilar Maliyawa da kabilar Mushiyawa da kabilar Koriyawa. Kohat shi ne kakan Amram.59Sunan matar Amram ita ce Yokabed, zuriyar Lebi, wanda ya haifi Lebiyawa a Masar. Ta haifa wa Amram 'ya'yansu, su ne Haruna da Musa da Miriyam 'yar uwarsu.60Haruna ya haifi Nadab da Abihu, Eliyeza da Itamar.61Nadab da Abihu sun rasu saboda sun miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Yahweh.62Mazan da aka ƙidaya daga cikinsu sun kai dubu ashirin da uku, dukkansu maza daga wata ɗaya zuwa sama. Amma ba a ƙidaya su ba cikin zuriyar Isra'ila domin ba a ba su gãdo a cikin mutanen Isra'ila ba.63Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eliyeza firist suka ƙidaya. Suka ƙidaya mutanen Isra'ila a kwarin Mowab Yodan a Yeriko.64Gama a cikin waɗannan babu mutum wanda Musa da Haruna firist ba su ƙidaya ba a zuriyar Isra'ila da aka ƙidaya a jeji Sinai.65Gama Yahweh ya ce da dukkan waɗannan mutane lalle za su mutu a jeji. Ba wani mutumin da ya ragu daga cikinsu, sai dai Kalibu ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
Maza ne kawai ya kamata su kiɗaya ban da mata. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "kiɗaya dukka mazaje da ke cikin jama'an"
"shekaru 20 da fiye"
"yi magana da shugabannin Isra'ila"
Fili wata ƙasa ce mai faɗi kuma babu tuɗu
"shekaru 20 da fiye"
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
A nan "Isra'ila" na nufin mutumin da ake kuma kiran sa Yakub.
Kalman nan "sa" na nufin Ra'ubainu.
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Juya wannan sunayen mazajen daidai kamar yadda ka yi cikin 16:1.
A nan an yi magana game da ƙasa sai ka ce mutum ne da ya buɗe bakinsa yana cin wani abu. AT: "Yahweh ya sa ƙasa ta buɗe baki, sa'an nan mutanen sun faɗa cikin ramin"
A nan an yi magana game da wuta sai ka ce wata babbar dabba da ta ke ƙoƙarin cinye wani abu. AT: "Yahweh ya sa wuta ta kashe mazaje 250"
"dukka iyalin Kora
"ƙarshe"
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Kalman nan "waɗannan" na nufin dukka mazaje daga 'ya'yan Yusuf, Ifraimu da Manase. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "Waɗannan su ne zuriyar Yusuf, daga 'ya'yansa maza biyu, Manase da Ifraimu,"
AT: "sun kiɗaya su daidai da kabilunsu"
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
Shugabannen Isra'ila suna kiɗaya mazaje masu shekaru 20 zuwa fiye bisa ga kabilunsu da kuma iyalinsu.
"jimila"
"dubu ɗari shida da ɗari bakwai da talatin"
AT: "Lallai ne ka raba ƙasar"
Wannan na nufin dukkan mazajen da aka kiɗaya daga cikin kabiluns, daga 26:5.
"bisa ga yawan mutane da ke a kowane kabila"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa.
Cikin wannan bangaren, kalman nan "gãdo" na nufin gãdon ƙasar. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "ba su kãrin ƙasa a matsayin gãdo"
AT: "wanda shugabannin Isra'ila sun kiɗaya"
AT: "lallai ne ka raba ƙasar"
"ta wurin jefa ƙuri'a"
AT: "za ka raba ta"
AT: "ka rarraba musu ƙasar"
Wannan shine tsarin sunayen kabilan Lewiyawa. Musa ya kiɗaya Lewiyawan a daban da sauran kabilun domin ba su karɓi wani ƙasa ba.
AT: "cewa shugabannin sun kiaɗya kabila da kabila"
Juya waɗannan sunayen mazaje daidai kamar yadda ka yi cikin 3:17.
"Ita da Amram sun sami 'ya'ya"
Juya waɗannan sunayen daidai kamar yadda ka yi cikin 3:1.
An yi amfani da kalman nan "wuta" a nana don ana nufin "ƙona turare". Dubi yadda ka juya magana makamanci haka cikin 3:3. AT: "sun ƙona turare hadaya ga Yahweh a hanyar da bai amince da shi ba"
AT: "wanda shugabannin sun ƙidaya"
23,000
"wata ɗaya har fiye"
AT: "amma shugabannin ba su ƙidaya su ba"
A nan "gãdo" na nufin ƙasar gãdo. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "saboda Yahweh ya ce ba za su karɓi wata ƙasa a matsayin gãdon su ba"
"babu mazaje"
AT: "sa'ad da suka ƙidaya zuriyar Isra'ila"
Kalman nan "su" na nufin dukka mutanen da aka ƙidaya a cikin jejin Sinai. AT: "sauran da suke da rai an"
Yefunne shine mahaifin Kalibu. Duba yadda ka juya wannan cikin 13:5.
Nun shine mahaifin Yoshuwa. Duba yadda ka juya wannan cikin 11:28.
1Sai Musa ya zo wurin 'ya'ya mata na Zelofehad ɗan Hefer ɗan Giliyad ɗan Makir ɗan Manasse, kabilar Manasse ɗan Yosef. Waɗannan su ne sunayen 'ya'yansa mata: Mala, Nowa, Hogla, Milka da kuma Tirza.2Suka tsaya a gaban Musa da Eliyeza firist, da shugabanni, da dukkan jama'a a ƙofar shiga rumfar taro. Suka ce,3"Mahaifinmu ya rasu a cikin jeji. Ba ya cikin waɗanda suka tayar wa Yahweh a ƙungiyar Kora. Ya mutu saboda alhakin zunubinsa, ga shi ba shi da 'ya'ya maza.4Donme za a cire sunan mahaifinmu daga cikin kabilar iyalinsa saboda ba shi da ɗa? Ka ba mu gãdo tare da 'yan'uwan mahaifinmu"5Musa ya kai maganarsu a gaban Yahweh.6Yahweh ya yi magana da Musa, ya ce,7"Ya'ya mata na Zelofehad suna magana dai dai. Ka ba su ƙasa a matsayin gãdo a cikin 'yan'uwansu, za ka tabbatar sun sami gãdon mahaifinsu.8Ka yi magana da mutanen Isra'ila, ka ce, 'Idan mutum ya rasu, ba shi da ɗa, sai ka sa gãdon mahaifinsa ya koma kan 'yarsa.9Idan ba shi da 'ya, sai ka bada gãdon ga 'yan'uwansa.10Idan kuma ba shi da 'yan'uwa maza, sai ka bada gãdonsa ga 'yan'uwan mahaifinsa maza.11Idan kuwa ba shi da 'yan'uwa maza, sai ka bada gãdonsa ga 'yan'uwansa na kusa a kabilarsa, zai ɗauke ta don kansa. Wannan ita ce doka da aka tabbatar da ka'ida saboda mutanen Isra'ila, kamar yadda Yahweh ya umarce ni.'"12Yahweh yace da Musa, "Tafi bisa duwatsun Abarim, ka dubi ƙasa wadda na ba mutanen Isra'ila.13Bayan daka ganta, kai ma, za a tara ka ga mutanenka, kamar Haruna ɗan'uwanka.14Wannan zai kasance domin ku biyun kun yi tawaye akan umarnina cikin jejin Zin. A can, lokacin da ruwa ke kwararowa daga dutse, a cikin fushi baku girmama ni kamar mai tsarki a gaban idannun dukkan jama'a ba." Waɗannan su ne ruwayen Meriba dana Kadesh a jejin Zin.15Sai Musa ya yi magana da Yahweh, ya ce,16"Bari kai, Yahweh, Allah na ruhohin dukkan 'yan adam, ya naɗa mutum bisa kan jama'a,17mutum wanda zai tafi, ya dawo a gabansu, ya shugabance su ya fita, ya dawo, saboda jama'arka ba kamar tumakin da ba makiyayi suke ba."18Yahweh yace da Musa, "Ka ɗauki Yoshuwa ɗan Nun, mutum wanda Ruhuna yake raye a cikinsa, ka sa hannunka a kansa.19Sa shi a gaban Eliyeza firist da gaban dukkan jama'a, ka umarce shi a gaban idanunsu ya shugabance su.20Ka danka masa ikonka a kansa, don dukkan jama'ar mutanen Isa'ila su yi masa biyayya.21Zai wuce gaban Eliyeza firist ya nemi nufina domin sa, ta wurin yanke shawarar Urim. Zai zama bisa ga umarninsa da mutane za su tafi waje su kuma komo ciki, shi da dukkan mutanen Isra'ila tare da shi, da kuma dukkan jama'a."22Sai Musa ya yi kamar yadda Yahweh ya umarce shi. Ya ɗauki Yoshuwa ya sa shi a gaban Ele'yazar firist da dukkan jama'a.23Ya ɗibiya hannuwansa a kansa, ya umarce shi ya yi shugabanci, kamar yadda Yahweh ya umarce shi ya yi.
"Sai 'ya'yan Zelofehad ɗan Hefer ɗan Gileyad ɗan Makir ɗan Manassa, daga kabilar Manassa ɗan Yusuf ya zo wurin Musa." Wannan magana na gaya mana cewa wannan shine labarin asalin Zelofahad.
Juya waɗannan sunayen daidai kamar yadda ka yi cikin 26:33.
Juya waɗannan sunayen daidai kamar yadda ka yi cikin 26:28.
"'ya'yan Zelofahad mata sun tsaya"
Mutanen da ke ƙungiyar Kora sun taru a wuri ɗaya, sa'an nan suka tayar wa Yahweh. Yahweh ya sa suka mutu saboda zunubinsu. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "waɗanda suka mutu saboda suna tare da mabiyan Kora da suka yi wa Yahweh tawaye"
"saboda zunubinsa"
A wancan loƙacin, 'ya'ya maza ne kawai ke samun gãdon ƙasa. 'Ya'ya matan sun yi amfani da wannan tambayar don ba da ra'ayin cewa za su gãji gãdon, su kuma sami cigaba da kabilan iyalin. AT: "Kada ka cire sunan mahaifin mu daga kabilan don ba shi da ɗa."
Wannan na nufin cewa suna so su gãji ƙasar da ke kusa da inda dangin mahaifinsun sun gãda. Ana iya bayana ma'anar wannan a fili. AT: "Ka ba mu ƙasa a inda dangin mahaifin mu suke zama"
Wannan na nufin cewa za su gãji ƙasar a inda 'yan'uwan mahaifinsu suka gãda. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "inda 'yan'uwan mahaifinsu suke zama"
Wannan ya cigaba da ba da bayani game da shari'ar Allah a kan wa zai karɓi ƙasar idan mutum ba shi da ɗa.
AT: "dokar da ke cewa lallai ne dukka mutanen Isra'ila su yi biyayya"
A nan "ni" na nufin Musa.
Wannan tsauni ne da ke Mowah.
A nan Yahweh ya yi magana game da ƙasar da ya ce zai ba wa Isra'ila sai ka ce ya riga ya ba su. Ya yi magana ta wannan hanya don ya nuna cewa ya yi shirin ba su. AT: "za zan ba wa mutanen Isra'ila"
Wannan na nufin cewa Musa zai mutu, ruhunsa kuma zai tafin in da kakaninsa suke. AT: "lallai ne ka mutu"
Za a iya bayana a fili zance da aka fahimta a nan cewa Haruna ya mutu. AT: "kamar yadda yayan ka Haruna ya mutu"
Wannan na nufin Musa da Haruna.
Juya wannan magana daida kamar yadda ka yi cikin 13:21.
Wannan na nufin lokacin da Yahweh ya yi abin al'ajibi ta wurin sa ruwa ya fito daga dutse. Allah ya cewa Musa ya yi magana da dutsen. Maimaƙon haka, Musa ha buga dutsen saboda yana fushi da mutanen.
"ba ka maishe ni a matsayin mai tsarki ba"
An rubuta shi hakan don a nanata abin da suka gani.
Juya wannan daidai kamar yadda ka juya wannan cikin 20:12.
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) A nan "ruhohi" na nufin dukkan mutanen. AT: "Allahn dukkan 'yan'adam" ko kuwa 2) "ruhohi" na nufin cewa Allah ya ba da rai da nufashi ga dukka mutane. AT: "Allahn da ya ba da nufashi ga dukkan mutane" ko kuwa "Allahn da ya ba da rai ga dukkan 'yan'adam"
"bisa kan" mutanen na nufin samin ikon shugabancinsu. AT: "mutum da shugabanci jama'ar"
Wannan na nufin mutumin da ya shugabanci dukkan mutanen da kuma sojojin zuwa yaƙi.
Wannan na nufin cewa idan babu shugaba, mutanen za su yi yawan banza, za su kuma zama kamar wanda ba su da taimako.
Ruhun Yahweh na cikin Yoshuwa na nufin cewa Yoshuwa na biyayya ga Yahweh, yana kuma bin umurninsa.
Wannan alama ce da ke nuna cewa wani ya mika kai don aikin Allah. AT: "sa hannunka a kansa don ka zaɓe shi"
A nan "a gabansu" na nufin mutanen. An rubuta shi hakan don a nanata abin da suka gani. AT: "a gaban dukkan su ka umuric Koshuwa ya shugabanci mutanen Isra'ila"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa game da Yoshuwa.
A nan Yahweh ya yi magana game da ikon da Musa zai ba wa Joshuwa sai ka ce tufa ne da zai sa masa. AT: "ka ba shi kaɗan daga cikin ikon ka" ko "ya shirya abin da ya kamata mutanen su yi"
Wannan dutse ne mai tsarki da Babban Firis ke sanya kirginsa. Ya yi amfani da shi don ya gano nufin Allah.
Wannan na nufin cewa Joshuwa zai sami ikon bada umurni game da tafiyar jama'ar Isra'ila. "Fita" da "shiga" umurni biyu ne da an yi amfani da shi don a nanata cewa shi zai bada umurni game da yaddaza su yi tafiya. AT: "Zai ba da umurni game da tafiyar jama'ar"
Duk waɗannan maganganu suna nufin abu ɗaya ne, an kuma yi amfani da su don nanaci. AT: "shi da gabaɗayan al'umma Isra'ila"
"ya ce masa ya tsaya a gaban"
"Ya" na nufin Musa, "sa" kuma na nufin Yoshuwa.
Sa wa mutum hannu wata hanya ce na keɓewa don aiki Allah ta musamman.
Za a iya bayana abin da aka fahimta game da shugabantar mutanen a fili. AT: "shugabanci mutanen" ko kuwa "zama shugaban Isra'ilawan"
A nan "shi" na nufin Musa.
1Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,2"Ka umarci mutanen Isra'ila, ka ce da su, 'Za ku miƙa hadaya gare ni a ayyanannun lokatai, ta abincin baye-baye na ta wurin wuta mai daɗin ƙanshi domi na.'3Ka kuma ce da su, 'Wannan bayarwa da za a yi da wuta, za ku bayar ga Yahweh--ɗan tunkiya shekara ɗaya wanda babu lahani a gare shi, guda biyu kowacce rana, matsayin bayarwar ƙonawa.4Dan tunkiya ɗaya za ku bayar da safe, ɗaya kuma da maraice.5Za ku bayar da mudun lallausan garin filawa matsayin bayarwar hatsi, kwaɓaɓɓe da man zaitun mafi kyau har rubu'in moɗa.6Wannan zata zama ta bayarwar ƙonawa da za ku riƙa yi yadda an umarta a Tsaunin Sinai baiko mai daɗin ƙanshi, da aka yi da wuta ga Yahweh.7Bayarwar sha zata zama ɗaya bisa huɗu na moɗa don ɗaya ɗan rago. Za a kwarara a wuri mai tsarki baiko na sha mai ƙarfi ga Yahweh.8Ɗaya ɗan ragon kuma za a miƙa da maraice tare da baiko na gari kamar baiko na safe. Dole ne kuma a miƙa wani na sha tare da shi, baikon ƙonawa da wuta, mai daɗin ƙamshi ga Yahweh.9A ranar Asabaci kuwa za a miƙa 'ya'yan raguna biyu kowanne bana ɗaya marasa lahani, da mudu biyu na lallausan gari a matsayin baiko, kwaɓaɓɓe da mai, da baiko na sha tare da shi.10Wannan shi ne baikon ƙonawa domin kowacce Asabaci, a kan kowanne baiko na ƙonawa da baiko na sha tare da shi.11A farkon kowanne wata, za a miƙa baikon ƙonawa ga Yahweh. Za a miƙa 'yan bijimai biyu, da rago ɗaya da kuma 'yan raguna bakwai bana ɗaya ɗaya, marasa lahani.12Za a kuma miƙa kwaɓaɓɓen gari kashi uku bisa ɗaya na garwa da man zaitun don kowanne bijimi, da gari kashi biyu bisa goma na garwa don rago ɗaya.13Za a kuma miƙa humushin lallausan gari za a haɗa shi da mai kamar baikon hatsi don kowanne rago. Wannan zai zama baikon ƙonawa, domin ya bayar da ƙamshi mai daɗi, baiko da aka yi da wuta ga Yahweh.14Baiko na sha na mutane dole ya zama rabin moɗa na ruwan inabi don bijimi, da ɗaya bisa uku na moɗa don rago da ɗaya bisa huɗu na moɗa don ɗan rago. Wannan shi ne baiko na ƙonawa a kowanne wata a dukkan watannin shekara.15Dole kuma a miƙa bunsuru ɗaya a matsayin baiko na zunubi ga Yahweh. Wannan zai zama ƙarin baiko na ƙonawa da baiko na sha da za a riƙa yi da su.16A cikin wata na farko, a rana ta goma sha huɗu ga watan, idin Ƙetarewa ga Yahweh.17A kan rana ta goma sha biyar ga wannan watan kuwa za a yi idi. Gama kwanaki bakwai na cin abinci mara gami ne.18A rana ta fari, za ku yi tsarkakakken taron girmama Yahweh. Ba za ku yi aikin da kuka saba yi a ranar ba.19Duk da haka, dole ku miƙa baiko da aka yi da wuta, a baiko na ƙonawa ga Yahweh. Dole ku miƙa 'yan bijimai biyu da rago ɗaya, da 'yan tumaki bakwai bana ɗaya ɗaya marasa lahani.20Tare da bijimi, za ku miƙa lallausan gari kashi uku na garwa wanda aka kwaɓa da mai tare da rago, kashi biyu bisa uku.21Tare da kowanne 'yan raguna bakwai, za ku miƙa lallausan gari haɗe da mai,22da ɗan akuya ɗaya a matsayin baikon zunubin ƙafara domin kanku.23Dole ku miƙa waɗannan a kan bayarwar ƙonawa da kuke miƙawa kowacce safiya.24Kamar yadda aka nuna a nan, za ku miƙa waɗannan hadayu kullum, saboda ranaku bakwai na Idin Ƙetarewa, za ku yi baikon abincin da aka yi da wuta mai daɗin kamshi ga Yahweh. Za a miƙa a kan bayarwar ƙonawa da kuke yi da baiko na sha.25A rana ta bakwai za ku yi tsattsarkan taro na girmama Yahweh, ba za ku yi aikin da kuka saba yi ba a ranar.26Haka nan a ranar nunar fari, da kuke miƙa baikon sabon hatsi ga Yahweh a Bikin Makonni, za ku yi tsattsarkan taro na girmama Yahweh, ba za ku yi aikin da kun saba yi ba a ranar.27Dole ne ku miƙa baikon ƙonawa mai dadin ƙamshi ga Yahweh. Dole ne ku miƙa 'yan bijimai biyu da rago ɗaya da 'yan tumakai maza guda bakwai bana ɗaya ɗaya.28Kuma ku miƙa baikon gari tare da su: gari haɗe da mai, gari kashi uku bisa uku da aka haɗa da mai domin kowanne bijimi da kashi biyu don rago ɗaya.29Ku miƙa kashi goma na garwa da aka haɗa da mai don kowanne 'yan raguna bakwai,30da ɗan akuya na ƙafara domin kanku.31Idan kuka miƙa waɗannan dabobbin marasa lahani, tare da baye bayenku na sha, wannan zai zama a kan baye-bayen ƙonawa, da hatsi da kuke bayarwa tare su.'"
"daidai lokacin da aka shirya"
AT: "baye-baye na abin ci da za ku ƙona a kan bagadi za tanada"
"ƙanshi da nake jin daɗi"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abin da lallai ne yakamata su yi.
AT: "baikon ƙonawa" ko "baikon da ka ƙona da wuta a kan bagadin"
AT: "wanda ka gauraye da"
kashi goma "ɗaya cikin goma" na nufin kashi ɗaya cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin ma'auni na wannan zamani. AT: "lita 2" ko kuwa "ɗaya cikin goma na gãri
na huɗu a kashin man zaitun - "Ɗaya cikin huɗu" na nufin bangare ɗaya cikin kashi huɗu. Ana iya juya wanna cikin ma'auni na wannan zamani. AT"lita guda" ko kuwa "ɗaya daga cikin kashi huɗu na man zaitun
"man da aka matse" ko "tsantsan man zaitun." Wannan na nufin mai da aka matse daga zaitun.
AT: "wanda Yahweh ya umurta a Dutsen Sinai"
AT: "da ka ƙona a kan bagadi"
na huɗu a kashin man zaitun - "Ɗaya cikin huɗu" na nufin bangare ɗaya cikin kashi huɗu. Ana iya juya wanna cikin ma'auni na wannan zamani. AT"lita guda" ko kuwa "ɗaya daga cikin kashi huɗu na man zaitun
Wannan jimlar na bayani game da baikon sha da ke bin bayan ɗan rago. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "Lallai ne ya zama hadayar sha kuma lallai ne ka zuba shi a wuri mai tsarki zuwa ga Yahweh"
AT: "kamar wanda ka miƙa"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abin da lallai ne yakamata su yi.
"uku cikin goma" na nufin kashi uku cikin kashi goma. Ana iya rubata wannan cikin ma'aunin wannan zamanin. AT: "lita shida" ko "uku cikin goma na gãri
AT: "wanda ka gauraye da mai"
Yawancin hadayar su na tafiya tare da hadayar sha wadda ake bukata. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "hadayar sha da ke biye da shi"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abin da lallai ne yakamata su yi.
"uku cikin goma" na nufin kashi uku cikin kashi goma. Ana iya rubata wannan cikin ma'aunin wannan zamanin. AT: "lita shida" ko "uku cikin goma na gãri
Za a iya ƙara kalmomin nan "na gãri." "Biyu cikin goma" na nufin kashi biyu daga cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin awu na wannan zamani. AT: "lita hudu da rabi" ko kuwa "kashi biyu cikin goma na gãri
"ɗaya cikin goma" na nufin kashi ɗaya cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin ma'auni na wannan zamani. AT: "lita 2" ko kuwa "ɗaya cikin goma na gãri
AT: "wanda ka gauraye da mai"
AT: "da ka ƙona a kan bagadi"
"rabi" na nufin bangare ɗaya bisa biyu. Ana iya juya wannan cikin ma'aunin wannan zamanin. AT: "lita biyu" ko "rabin moɗa
"ɗaya bisa uku na moɗa." "na uku" na nufin bangare ɗaya bisa uku. Ana iya rubuta wannan cikin ma'aunin wannan zamani. AT: "lita 1.2" ko "Ɗaya da kashi ɗaya cikin biyar" ko "rabin moɗa"
ɗaya bisa huɗu na moɗa- "ɗaya bisa huɗu" na nufin kashi ɗaya bisa kashi huɗu. Ana iya rubuta wannan cikin ma'aunin wannan zamani. AT: "lita ɗaya" ko kuwa "ɗaya bisa huɗu na moɗa
AT: "lallai ne ka miƙa bunsuru ɗaya ga Yawe a Matsayin hadaya ta zunubi"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa game da abin da lallai ne mutanen su yi.
"wata na 1, a rana ta 14 ga watan ... rana ta 15 ga watan." Wannan na nufin bisa ga kalandar Yahudawa.
"lallai ne ku yi bikin idin ketarewa na Yawe"
AT: "lallai ne ku yi biki"
AT: "lallai ne ku ci gurasa mar yisti"
"rana ta 1"
"lallai ne ku taru a wuri ɗaya don ku yi sujada ku kuma girmama Yawe." Kalman nan "taro mai tsarki na nufin mutanen sun taru a wuri ɗaya don su yi wa Yawe sujada. Sujada ga Yawe abu ne mai tsarki.
Yawe ya cigaba da magana da Musa game da abin da lallai mutanen su yi.
AT: " lallai ne ku ƙona hadaya a kan bagadi"
"uku cikin goma" na nufin kashi uku cikin kashi goma. Ana iya rubata wannan cikin ma'aunin wannan zamanin. AT: "lita shida" ko "uku cikin goma na gãri
AT: "wanda kun gauraye da mai"
Za a iya ƙara kalmomin nan "na gãri." "Biyu cikin goma" na nufin kashi biyu daga cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin awu na wannan zamani. AT: "lita hudu da rabi" ko kuwa "kashi biyu cikin goma na gãri
kashi goma "ɗaya cikin goma" na nufin kashi ɗaya cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin ma'auni na wannan zamani. AT: "lita 2" ko kuwa "ɗaya cikin goma na gãri
AT: "wadda Yawe ke bukata a kowace safe"
AT: "Kamar yadda Ni, Yawe na bayana a nan"
AT: "lallai ne ku ƙona hadayar abincin a kan bagadin"
"kamar ƙanshi mai daɗin don Yaweh"
AT: "lallai ne ku miƙa shi"
taru a wuri ɗaya don yin sujada da girmama Yawe." Maganan nan "taro mai tsarki" na nufin mutane sun taru a wuri ɗaya don su yi wa Yawe sujada. Sujada ga Yawe abu ne mai tsarki.
Yawe ya cigaba da magana da Musa game da abin da lallai ne mutanen su yi.
"a ranar nunar fari, wannan rana ce."Wannan na nufin ranar bikin cikin makonin sa'ad da suka miƙa hadayar hatsi ga Yawe.
taru a wuri ɗaya don yin sujada da girmama Yawe." Maganan nan "taro mai tsarki" na nufin mutane sun taru a wuri ɗaya don su yi wa Yawe sujada. Sujada ga Yawe abu ne mai tsarki.
AT: "wadda kuka gauraye da mai"
"uku cikin goma" na nufin kashi uku cikin kashi goma. Ana iya rubata wannan cikin ma'aunin wannan zamanin. AT: "lita shida" ko "uku cikin goma na gãri
Za a iya ƙara kalmomin nan "na gãri." "Biyu cikin goma" na nufin kashi biyu daga cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin awu na wannan zamani. AT: "lita hudu da rabi" ko kuwa "kashi biyu cikin goma na gãri
Yawe ya cigaba da magana da Musa game da abin da lallai ne mutanen su yi.
kashi goma "ɗaya cikin goma" na nufin kashi ɗaya cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin ma'auni na wannan zamani. AT: "lita 2" ko kuwa "ɗaya cikin goma na gãri
AT: "humushin garu gauraye da mai"
Wannan na nufin hadayar sha da ake bukata a kowace hadayar dabbobi. AT: "hadayar sha dake miƙawa tare da su" ko "hadayar sha da ke biye da su"
1A cikin wata na bakwai, a rana ta farko ta watan, za ku yi taro mai tsarki na girmama Yahweh. Tilas ba za ku yi wani aikin da aka saba a koda yaushe ba a wannan rana. Dole ne ta zama ranar da za ku busa ƙahonni.2Za ku miƙa ƙonannen baiko domin abin daɗi da ƙamshi ga Yahweh. Dole ku miƙa ɗan bijimi, rago ɗaya, da 'yan raguna bakwai masu shekara ɗaya, mara aibi.3Dole ne ku miƙa su tare da baikonsu na hatsi, gari mai laushi cuɗaɗɗe da mai, uku cikin goma na efa domin bijimi, biyu cikin goma domin ragon,4ɗaya cikin goma kuma domin kowanne cikin raguna bakwai.5Dole ne ku miƙa bunsuru ɗaya domin baiko na zunubi don a yi maku kafara.6A miƙa waɗannan baye-baye a cikin wata na bakwai a bisa kan sauran dukkan baye-bayen da za ku bayar a ranar farko ta kowanne wata: ƙonannen baiko na musamman da kuma baiko na hatsi a haɗa da shi. Waɗannan dole za a miƙa su zama ƙãri bisa ga ƙonannen baikon da aka sãba, baiko hatsin, da kuma baye-bayensa na sha. Sa'ad da kuka miƙa waɗannan baye-bayen, za ku yi biyayya da abin da aka umurtar don ya bãda ƙamshi mai daɗi, baiko na wurin wuta ga Yahweh.7A rana ta goma ga watan bakwai za ku yi taro mai tsarki don girmama Yahweh. Dole ku ƙasƙantar da kanku ba za ku yi wani aiki ba.8Dole ku miƙa baiko na ƙonawa mai bãda ƙamshi mai daɗi ga Yahweh. Dole ku miƙa ɗan bijimi ɗaya, da ɗan rago ɗaya, da kuma 'yan raguna 'yan shekara ɗaya guda bakwai.9Dole ku miƙa tare da su baiko na hatsi, gãri mai laushi gauraye da mai,10uku cikin goma na efa domin bijimi, biyu cikin uku domin tunkiya guda ɗaya, da kuma kashi goma na efa domin dukkan raguna bakwai ɗin.11Dole ku miƙa ɗan akuya ɗaya don baikon na zunubi. Wannan zai zama ƙãri bisa baikon zunubi na kaffara, da baye-bayensu na sha.12A rana ta sha biyar ga watan bakwai za ku yi taro mai tsarki don girmama Yahweh. Ba za ku taɓa yin wani aiki yadda kuka sãba a kodayaushe a wannan rana ba, kuma za ku yi buki gare shi kwana bakwai.13Dole ku miƙa baiko na ƙonawa, hadaya da aka miƙa ta wurin wuta domin abin ƙamshi da daɗi ga Yahweh. Dole ku miƙa 'yan bijimi guda sha uku, tumaki guda biyu, da kuma tumakai guda sha huɗu 'yan shekara ɗaya. Kowanen su ya zama mara aibi.14Dole ne ku miƙa tare da su baiko na hatsi, niƙaƙƙen gari harɗe da mai, kashi uku na efa don kowanne rago na raguna sha ukun, kashi biyu domin kowanne rago na raguna biyun,15da kashi ɗaya na efa domin dukkan tumaki guda sha huɗun.16Dole ku miƙa baiko na zunubi namijin akuya ɗaya ƙãri bisa ƙonannun baiko na kodayaushe, baikon hatsin, tare da shi kuma da baikon abin sha.17A rana ta biyu na taruwa, dole ne ku miƙa 'yan raguna guda sha biyu, tumaki biyu, da awakai maza goma sha huɗu 'yan shekara ɗaya, kowanne mara aibi.18Dole ku miƙa su tare da baikon hatsi da baye-baye na shã domin ragunan, domin tumakin, domin kuma awakan, kuna miƙa baye-baye masu yawa kamar yadda aka umarce ku.19Dole ne ku miƙa baiko na zunubi ɗan rago ɗaya ƙãri bisa baiko na ƙonawa a kodayaushe yaushe, da kuma baye-bayensu na shã.20A rana ta uku na taruwan, dole ne ku miƙa raguna shaɗaya, tumaki biyu, da bunsurai sha huɗu 'yan shekara ɗaya, kowanne mara aibi.21Dole ne ku miƙa su tare da baiko na hatsi da baye-baye na abin shã domin ragunan, domin su tumakin, da kuma don su awakan, kuna miƙa baye-baye masu yawa kamar yadda aka umarce ku.22Dole ne ku miƙa namijin tunkiya ɗaya baiko na zunubi ƙãri bisa baiko na ƙonawa na kodayaushe, baikon hatsinta, da kuma baye-bayensu.23A rana ta huɗu ta taruwa, dole ne ku miƙa raguna guda goma, tumaki guda biyu, da mazajen awakai 'yan shekara ɗaya guda shahuɗu, kowannensu marasa aibi.24Dole ne ku yi tare da su baiko na hatsi da baye-baye na shã domin ragunan, domin tumakin, da kuma domin awakan, kuna miƙa baye-baye masu yawa kamar yadda aka umarce ku.25Dole ne ku miƙa bunsuru ɗaya baiko na zunubi ƙãri bisa baiko na ƙonawa na kodayaushe, baiko na hatsinsa, da baye-bayensu na shã.26A rana ta biyar ta taruwa, dole ne ku miƙa raguna guda tãra, tumaki biyu, da bunsurai 'yan shekara ɗaya guda sha huɗu, marasa aibi.27Dole ne ku miƙa su tare da baiko na hatsi da kuma baye-baye na shã domin ragunan, domin tumakin, domin kuma awakan, ana miƙa baye-baye masu yawa kamar yadda aka umurta.28Dole ne ku miƙa namijin tunkiya ɗaya na baikon domin zunubi ƙari bisa ƙonannen baiko na kodayaushe, baikon hatsin, da baye-baye na shãnsu.29A rana ta shida ta taruwar, dole ne ku miƙa raguna takwas, tumaki biyu, da mazajen awakai guda sha huɗu 'yan shekara ɗaya, marasa aibi.30dole ne ku miƙa su tare da baiko na hatsi da kuma baye-baye na shã domin ragunan, domin tumakan, domin kuma awakan, kuna miƙa baye-baye masu yawa kamar yadda aka umurce ku.31dole ne ku miƙa bunsuru guda ɗaya baiko na zunubi, baikon hatsi, da baye-bayensu na shã.32A rana ta bakwai na taruwa, dole ne ku miƙa raguna guda bakwai, tumakai biyu, da kuma bunsurai guda sha huɗu 'yan shekara ɗaya, marasa aibi.33Dole ne ku miƙa tare da su baiko na hatsi da baye-baye na shã domin ragunan, domin tumakan, domin kuma awakan, kuna miƙa baye-baye masu yawa kamar yadda aka umurce ku.34Dole ne ku miƙa namijin akuya domin baiko na zunubi don ƙari bisa ga baiko na ƙonawa kamar na kodayaushe, domin baiko na hatsin, da kuma baye-bayensu na shã.35A rana ta takwas zaku sake yin wani taron mai tsarki. Kar ku kuskura ku yi wani aiki kamar yadda kuka saba a wannan rana.36Dole ne ku miƙa hadaya na ƙonawa, baiko da aka yi da wuta domin a miƙa abin ƙamshi mai daɗi ga Yahweh. Za ku miƙa ɗan bijimi guda ɗaya, akuya ɗaya, da kuma 'yan raguna guda bakwai masu shekara ɗaya, kowanne mara aibi.37Dole ne ku miƙa baikon hatsinsu da kuma baikon abin sha domin bijimi, domin ɗan akuya, kuma domin 'yan raguna, kuna miƙa baye-baye kamar yadda aka umurta.38Dole ne ku miƙa bunsuru guda ɗaya baiko na zunubi ƙari bisa ƙonannen baikon da aka sãba kodayaushe, baikon hatsinsu, da kuma baye-bayensu na shã.39Waɗannan su ne dole ku miƙa ga Yahweh a tsayayyun bukukuwanku. Waɗannan za su zama ƙãri ne bisa alƙawaranku da kuma baye-bayenku na yardan rai. Dole ne ku miƙa waɗannan a matsayin baye-bayenku na ƙonawa, baye-baye na hatsi, baye-baye na shã, da baye-baye na zumunci."40Sai Musa ya gaya wa mutanen Isra'ila dukkan abin da Yahweh ya umurce shi ya faɗa.
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abin da lallai ne mutanen su yi.
"wata na bakwai, a rana ta fari a watan." Wannan na nufin wata na bakwai bisa ga kalandar Yahudawa.
"taru a wuri ɗaya don su yi wa Yahweh sujada su kuma girmama Yahweh." Maganan nan "taro mai tsarki" na nufin cewa mutanen sun taru don su yi wa Yahweh sujada. Sujada ga Yahweh abu ne mai tsarki.
A nan kalman nan "ku" na nufin mutanen Isra'ila wanda suke wakilcin firist. Firist ya busa ƙaho don a fara sujada ko kuwa don a tara jama'ar a wuri ɗaya. AT: "zai zama ranar da firist ya busa ƙahoni"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abin da lallai ne mutanen su yi.
Wannan na nufin baikon hatsi da ake buƙata a haɗa da kowane dabbar a sa'ad da ake hadaya. AT: "baikon hatsi da aka mika da su" ko kuwa "baikon hatsin da ya biyo baya"
AT: "wanda ka gauraye da mai"
"Humushi uku cikin goma na gãri" na nufin uku cikin goma. Za a iya rubuta wannan cikin awu na wannan zamani. AT: "lita shida" ko kuwa "uku cikin goma na gãri
Za a iya ƙara kalmomin nan "na gãri." "Biyu cikin goma" na nufin kashi biyu daga cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin awu na wannan zamani. AT: "lita hudu da rabi" ko kuwa "kashi biyu cikin goma na gãri
kashi goma "ɗaya cikin goma" na nufin kashi ɗaya cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin ma'auni na wannan zamani. AT: "lita 2" ko kuwa "ɗaya cikin goma na gãri
AT: "yi kafara"
"wata na 7 ... rana ta 1 a kowace wata" Kalman nan "wata" na nufin bisa ga kalandar Yahudawa.
"ta kowanne wata -- baikon ƙonawa ta musamman ... da shi." Wannan shine baiko da ake yi a rana ta fari a kowane wata.
Wannan na nufin baikon da ya kyautu firist su miƙa kowane rana. Za a miƙa baikon hatsi da baiko na sha tare da baikon ƙonawa. AT: "baikon ƙonawan da baikon hatsi da baikon sha da an sãba mikawa tare da shi"
AT: "za ku yi biyayya ga umurnin Yahweh" ko kuwa "za ku yi biyayya ga abin da Yahweh ya umurta"
AT: "baikon da ka ƙona a kan bagadin ga Yahweh"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Musa abin da lallai ne mutanen su yi.
"ranar ta 10 a wata na 7" Kalman nan "wata" na nufin bisa ga kalandar Yahudawa.
"taru a wuri ɗaya don su yi sujada su kuma girmama Yahweh." Manganan nan "taron jama'a mas tsarki" na nufin cewa mutanen sun taru a wuri ɗaya don su yi sujada ga Yahweh. Sujada ga Yahweh abu ne mai tsarki.
AT: "wanda ka gauraye da mai"
"uku cikin goma" na nufin kashi uku cikin kashi goma. Ana iya rubata wannan cikin ma'aunin wannan zamanin. AT: "lita shida" ko "uku cikin goma na gãri
Za a iya ƙara kalmomin nan "na gãri." "Biyu cikin goma" na nufin kashi biyu daga cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin awu na wannan zamani. AT: "lita hudu da rabi" ko kuwa "kashi biyu cikin goma na gãri
kashi goma "ɗaya cikin goma" na nufin kashi ɗaya cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin ma'auni na wannan zamani. AT: "lita 2" ko kuwa "ɗaya cikin goma na gãri
AT: "yi kafara"
Za a miƙa baikon hatsi da baikon ƙonawa. Za a miƙa baikon sha tare da baikon zunubi da na ƙonawa. AT: "tare da baikon hatsi da baikon sha za su bi baya"
Yahweh ya cigaba da gayawa Musa abin da lallai ne mutanen su yi.
"rana ta 15 ga watan 7." Kalman nan "wata" na nufin waɗannan daga cikin kalandar Yahudawa.
"taru a wuri ɗaya don su yi sujada su kuma girmama Yahweh." Maganan nan "taro mai tsarki" na nufin cewa mutanen sun taru a wuri ɗaya don su yi sujada ga Yahweh. Abu ne mai tsarki a yi wa Yahweh sujada.
Wannan karin magana. A nan kalman "yi" na nufin kiyaye ko kuwa a yi murna. Kalman "sa" na nufin Yahweh. AT: "lallai ne ku kiyaye bukin domin Yahweh" ko kuwa "lallai ne ku yi bukin domin Yahweh"
AT: "lallai ne a ƙona shi a kan bagadin"
"'yan bijimi 13, rago 2, ɗan rago guɗa sha huɗu"
AT: "wanda ka gauraye da mai"
"uku cikin goma" na nufin kashi uku cikin kashi goma. Ana iya rubata wannan cikin ma'aunin wannan zamanin. AT: "lita shida" ko "uku cikin goma na gãri
"bijimi 13 ... 'yan rago 14"
Za a iya ƙara kalmomin nan "na gãri." "Biyu cikin goma" na nufin kashi biyu daga cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin awu na wannan zamani. AT: "lita hudu da rabi" ko kuwa "kashi biyu cikin goma na gãri
kashi goma "ɗaya cikin goma" na nufin kashi ɗaya cikin kashi goma. Za a iya rubuta wannan cikin ma'auni na wannan zamani. AT: "lita 2" ko kuwa "ɗaya cikin goma na gãri
Baikon hatsi da baikon sha tare da baikon ƙonawa da aka sãba miƙawa.
"rana ta 2 na bukin." Kalman nan "taro" na nufin buki cikin makonai.
"bijimi 12, raguna 2 da 'yan raguna 14"
AT: "kamar yadda Yawe ya umurta"
Ya kamata a miƙa hadayar hatsin tare da hadayar ƙonawa. Ya kamata a miƙa hadaya sha tare da hadaya ta zunubi da hadayar ƙonawa. AT: "tare da hadayar hatsi da hadayu na sha za su biyo"
"rana ta 3 na biki." A nan kalman nan "taro" na nufin Bikin Makon.
"bijim 11, raguna 2 da 'yan raguna 14"
AT: "kamar yadda Yawe ya umurta"
Ya kamata a miƙa hadayar hatsin tare da hadayar ƙonawa. Ya kamata a miƙa hadaya sha tare da hadaya ta zunubi da hadayar ƙonawa. AT: "tare da hadayar hatsi da hadayu na sha za su biyo"
Yawe ya cigaba da magana da Musa game da abin da lallai ne mutanen su yi a lokaicn bikin ciki wata na bakwai.
"rana ta na biki." A nan kalman nan "taro" na nufin Bikin Makon.
"'yan rago maza 14"
AT: kamar yadda Yawe ya umurta-
Ya kamata a miƙa hadayar hatsin tare da hadayar ƙonawa. Ya kamata a miƙa hadaya sha tare da hadaya ta zunubi da hadayar ƙonawa. AT: "tare da hadayar hatsi da hadayu na sha za su biyo"
"rana ta 5 na biki." A nan kalman nan "taro" na nufin Bikin Makon.
"'yan rago maza 14"
AT: kamar yadda Yawe ya umurta-
Ya kamata a miƙa hadayar hatsin tare da hadayar ƙonawa. Ya kamata a miƙa hadaya sha tare da hadaya ta zunubi da hadayar ƙonawa. AT: "tare da hadayar hatsi da hadayu na sha za su biyo"
"rana ta 6 na biki." A nan kalman nan "taro" na nufin Bikin Makon.
"'yan rago maza 14"
AT: kamar yadda Yawe ya umurta-
Ya kamata a miƙa hadayar hatsin tare da hadayar ƙonawa. Ya kamata a miƙa hadaya sha tare da hadaya ta zunubi da hadayar ƙonawa. AT: "tare da hadayar hatsi da hadayu na sha za su biyo"
"rana ta 7 na biki." A nan kalman nan "taro" na nufin Bikin Makon.
"'yan rago maza 14"
AT: kamar yadda Yawe ya umurta-
Ya kamata a miƙa hadayar hatsin tare da hadayar ƙonawa. Ya kamata a miƙa hadaya sha tare da hadaya ta zunubi da hadayar ƙonawa. AT: "tare da hadayar hatsi da hadayu na sha za su biyo"
Yawe ya gaya wa Musa abin da lallai ne mutanen su yi bayan kwana bakwai na bikin a wata na bakwai.
"ta takwas" lamba ne.
"taru a wuri ɗaya kuma don a yi wa Yawe." Wannan na wani taro ne daidai kamar buki na fari.
AT: "lallai ne ku ƙona shi a kan bagadi"
Za a miƙa waɗannan hadayu tare da bijimi da rago da kuma 'yan rago. AT: "hadayun hatsi da kuma hadayun sha"
AT: kamar yadda Yawe ya umurta- (Duba
Ya kamata a miƙa hadayar hatsin tare da hadayar ƙonawa. Ya kamata a miƙa hadaya sha tare da hadaya ta zunubi da hadayar ƙonawa. AT: "tare da hadayar hatsi da hadayu na sha za su biyo"
"Waɗannan shine baiko da lallai ne ka miƙa"
"bukukuwan da aka shirya." Waɗannan sune bukukuwan da suke aukuwa kowace lokacin da aka shirya shi. Kalman nan "shirya" na nufin "kafa" ko kuwa "shirya tun da wuri."
1Musa ya yi magana da shugabannin ƙabilun mutanen Isra'ila. Ya ce, "Ga abin da Yahweh ya umarta.2Idan wani ya yi wa'adi ga Yahweh, ko ya yi rantsuwa don ya riƙe kansa ga alƙawari, kada ya karya maganarsa. Dole ya cika alƙawarinsa ya aikata duk abin da ya fito daga bakinsa.3Idan 'yar matashiya mace mai zama cikin gidan mahaifinta ta yi wa'adi ga Yahweh ta ɗaure kanta ga alƙawari,4idan mahaifinta ya ji wa'adin da kuma alƙawarin da ta daukar wa kanta, kuma idan bai ce komai ba domin ya hana ta ba, to dukka wa'adodinta za su tsaya. Kowanne alƙawarin da ta ɗaukar wa kanta zai tsaya.5Amma idan mahaifinta ya ji game da wa'adinta da alƙawarinta, idan kuma bai ce da ita komai ba, to dukkan wa'adodinta da alƙawaranta da ta ɗaukar wa kanta za su tsaya.6Amma, idan mahaifinta ya ji dukkan wa'adodin da ta yi da kuma alƙawura masu tsarki da ta ɗaukar wa kanta, idan kuma ya sọke abin da ta yi a wannan ranar, to ba za su tsaya ba. Yahweh zai gafarta mata domin mahaifinta ya sọke abin da ta yi.7Idan ta auri mutum yayin da ta ke ƙarƙashin waɗannan wa'adodin, ko kuma idan ta furta alƙawarai cikin garaje da ta ɗaukar wa kanta nawaya, wannan nawayar tilas ta tsaya.8Amma idan mijinta ya hana ta a ranar da ya ji game da zancen, sa'an nan ya hana alƙawarin da ta ɗauka, maganar gangancin da ta yi ta fita daga leɓunanta da ta ɗaure kanta. Yahweh zai sãke ta.9Amma game da gwauruwa ko sakakkiyar mace, dukkan abin da ta ɗaure kanta da shi zai tsaya a kanta.10Idan mace ta ɗauki alƙawari a cikin gidan mijinta ko ta yi wa kanta hani ta wurin yin rantsuwa,11sai kuma maigidanta ya ji game da wannan, amma bai ce mata komai ba, to sai dukkan abin da ta alƙawarta su tsaya.12Amma idan maigidanta ya hana su a wannan ranar da ya ji game da su, to duk abin da ya fito daga leɓunanta game da wa'adodinta ko alƙawaranta baza su tsaya ba. Mijinta ya hana su. Yahweh zai sãke ta.13Kowanne wa'adi ko rantsuwar da mace ta yi da suka ɗaure ta har ta hana wa kanta wani abu maigidanta na iya tabbatarwa ko ya hana.14Amma idan bai ce mata komai a ranar ba, to ya tabbatar da dukkan wa'adodi da zaunannun alƙawarai wadanda ta ɗauka. Ta haka ya tabbatas da su domin bai ce da ita komi ba a ranar da ya ji game da su.15Idan mijinta yayi ƙoƙarin hana alƙawarin da matarsa ta ɗauka da daɗewa bayan ya ji shi, don haka zai ɗauki laifinta."16Waɗannan su ne farillan da Yahweh ya umarci Musa da ya sanar - da farillai game da abin dake tsakanin mutum da matarsa da kuma tsakanin mahaifi da ɗiyarsa a matashiyarta sa'ad da take tare da iyalin mahaifinta.
Waɗannan maganganu biyun na da ma'ana kusan iri ɗaya an kuma haɗa su don a nanata zance wa'adi ko alkawari.
A nan Musa yana magana game da alƙawarin da mutum ya yi na yi wani abu kamar alƙawarinsa wani abu ne da mutumin ya ɗaure kansa da shi. AT: "mika kai don cika alƙawari" ko "alƙawarin yin wani abu"
Waɗannan maganganu biyun na da ma'ana kusan iri ɗaya an kuma haɗa su don a nanata cewa lallai ne ya cika alƙawari. A nan "magana" nufin abin da ya furta da bakinsa.
Wannan magana "maganarsa" na nufin rantsuwa da wa'adin mutum. A nan Musa yana magana game da rashin cika waɗannan kamar wani abu ne da mutum zai iya karye. AT: "lallai ne ya cika alƙawarinsa"
A nan, kalman nan "baki" na nufin abin da mutumin ya faɗa. AT: "yi abin da ya ce zai yi"
A nan, Musa yana magana game da alƙawarin da mace ta yi kamar alƙawarinta wani abu ne da ta ɗaure kanta da shi. AT: "mika kanta ga cika alƙawari" ko "alƙawari yin wani abu"
Waɗannan maganganu biyun na da ma'ana kusan iri ɗaya. Su na kuma nanata abinda nan da ta alƙawarta za ta yi. AT: "wa'adin"
A nan, Musa yana magana game da alƙawarin da mace ta yi kamar alƙawarinta wani abu ne da ya ɗaure ta. AT: "wanda ta mika kanta ga cikawa"
"don ya warware abin da ta faɗa"
Waɗannan maganganu biyun a takaice na nufin abu ɗaya su na kuma nanata cewa lallai ne ta cika wa'adinta.
Wannan na nufin cewa wa'adodinta zai tsaya kuma tana bukata ta cika su. AT: "zai zama lallai ta cika"
Waɗannan maganganu suna da ma'ana kusan iri ɗaya. Suna kuma nanata abinda ta alƙawarta za ta yi. AT: "wa'adinta"
An yi magana game da wa'adodin da macen ta mika kanta don cikawa kamar tufafi ne da ta sanya a kanta. AT: "da ta mika kanta ga" ko "da ta yi"
Wannan na nufin cewa wa'adodinta zai tsaya kuma tana bukata ta cika su. Duba yadda ka juya wannan magana cikin 30:3. AT: "zai zama lallai ta cika"
A nan Musa ya yi magana game da yadda mace ta mika kanta ga cika alƙawari kamar alƙawarin wani abu ne da ta ɗaure kanta da shi. AT: "alƙawaren da ta mika kanta ga cikawa"
A nan an yi magana game da mahaifinta ya sọke alƙawarin macen kamar ya warware "ta" AT: "idan ya sọke alƙawarinta" ko "idan ya warware alƙawarinta"
Wannan na nufin cewa wa'adodinta ba za su tsaya ba kuma ba ta bukata ta cika su. AT: "ba zai zama lallai ta cika ba"
Wannan na nufin cewa Yahweh zai gafarceta don ba ta cika wa'adodin ta ba. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "Yahweh Zai gafarce ta don ba ta cika wa'adodinta ba"
Wannan karin magana ne. Zama "ƙarƙashin" wa'adodinta na nufin cewa ta mika kanta gare su kuma har yanzu wa'adodin na tsaye. AT: "a sa'ad da ta mika kanta ga waɗannan wa'adodin"
wani abu da aka yi cikin rashin tunani
AT: "abubuwan da ta ta sa kanta lallai za ta yi"
"wa'adin da ta yi ... wato maganar da ta yi cikin gareje." Waɗannan maganganu biyun na nufin abu ɗaya ne. Magana na biyun na bayana wa'adin da macen ta yi.
Maganan nan "maganar da ta yi cikin garaje" na nufin alkawaren da macen ta yi cikin garaje. AT: "abubuwan da ta furta cikin garaje" ko "alƙawarin ta na garaje"
A nan Musa ya yi magana game da yadda macen ta mika kanta ga cika alƙawarin kamar alƙawarinta wani abu ne da ta ɗaure kanta da shi. AT: "wanda ta mika kanta ga cikawa"
A nan Musa ya yi magana game da gafarar Yahweh ga macen don ba ta cika wa'adin ta ba sai ka ce yana kwance ta ne daga wani abinda ya ɗaure ta. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "Yahweh zai gafarce ta" ko "Yahweh zai gafarce ta don ba ta cika wa'adin ta ba"
Musa ya cigaba da gaya wa shugabannin kabilun abin da Yahweh ya umurta.
AT: "macen da mijin ta ya sake ta"
A nan Musa yana magana game da Yadda macen ta mika kanta ga cika alƙawari kamar alƙawarin wani abu ne da ta ɗaure kanta. AT: "wanda ta mika kanta ga cikatawa"
Wannan karin magana ne. Ya na nufin cewa wa'adodinta zai tsaya kuma lallai ne ta cika su. Dubi yadda ka juya wannan magana ciki 30:3. AT: "zai zama lallai ta cikata"
Wannan na nufin matan aure. Ka na iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "idan matan aure ta yi wa'adi"
Wannan karin magana ne. Ya na nufin cewa wa'adodinta zai tsaya kuma lallai ne ta cika su. Dubi yadda ka juya wannan magana ciki 30:3. AT: "zai zama lallai ta cikata wa'adodinta ... lallai ne ta cika"
A takaice waɗannan maganganu biyun na nufin abu ɗaya, an kuwa nanata ta ne kuma ana iya haɗa su. AT: "sa'an nan dukka wa'adodinta da alƙawaren da ta yi lallai ne su tsaya"
A nan abin da mace ta faɗa ana duban sa a matsayin abin da ya fito daga bakin ta. AT: "sa'an nan duk abin da ta faɗa"
Wannan karin magana ne da ke nufin cewa wa'adin ta ba zai tabbata ba kuma ba ta bukata ta cika su. dubi yadda ka juya wannan magana cikin 30:6. AT: "ba zai zama lallai ta cika ba"
A nan Musa yana maganar cewa Yahweh zai yafe wa macen don ba ta cika wa'adin ta ba kamar yana kwance ta ne daga wani abu da ya ɗaura ta. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "Yahweh zai yafe mata" ko "Yahweh zai yafe mata don ba ta cika wa'adin ta ba"
AT: "maigidanta na iya tabbatar da ko kuwa ya hana kowane wa'adi ko rantsuwar da ta yi suka ɗaure ta har ta hana wa kanta wani abu"
A nan Musa yana magana game da alkawarin da mace ta mika kanta ga shi kamar wani abu ne da ya ɗaure ta a jiki. AT: "wanda ta mika kanta"
Musa bayana alkawarin da mace ta yi kamar wani abu ne da ya ɗaure ta a jiki. AT: "takalifi" ko "alkawaren"
Kana iya bayana abin da aka fahimtan a nan a fili. AT: "domin bai ce mata kome game da su ba"
Wannan na nufin cewa shi zai ɗauki laifin zunubin ta a maimaƙo ta idan ba ta cika wa'adin ta ba. Ana iya bayana ma'anar wannan magana a fili. AT: "idan ba ta cika wa'adinta ba, ba za ta ɗauki laifin zunubin ta ba, shi kuwa zai zama mai laifi a maimaƙon ta"
1Yahweh ya yi magana da Musa ya kuma ce,2"Ka ɗauki fansa a bisa Midiniyawa kan abin da suka yi wa Isra'ilawa. Bayan ka yi wannan, za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka."3Sai Musa ya yi magana da mutanen. Ya ce, "Ku shirya wasu daga cikin mazajenku don yaƙi gãba da Midiyan, ku kuma yi ramako na Yahweh a bisanta.4Kowacce kabila cikin dukkan Isra'ila dole ta aika da sojoji dubu zuwa yaƙi."5Saboda haka cikin dubban mazajen Isra'ila, aka aika da dubu ɗaya daga kowacce kabila, mazaje dubu sha biyu shiryayyu don yaƙi.6Sai Musa ya aika da su zuwa yaƙi, daga kowacce kabila dubu ɗaya, tare da Finehas ɗan Eliyeza firist, da kuma wasu kayayyaki daga cikin wuri mai tsarki da kuma su ƙahonni dake a hannunsa don busawa ta alamar yaƙi.7Suka yi yaƙi da Midiya, kamar yadda Yahweh ya bada umarni ga Musa. Suka karkashe kowanne mutum.8Suka kashe sarakunan Midiyan tare da sauran matattunsu: Ebi, da Rekem, da Zur, da Hur, da kuma Reba, sarakuna guda biyar na Midiyan. Suka kuma kashe Bala'am ɗan Beyor, da takobi.9Rundunar Isra'ila suka kwashe bayi matayen Midiyan, da yaransu, da dukkan shanunsu, da garkunansu, da dukkan dukiyarsu. Suka kwashe su ganima.10Suka ƙone dukkan biranensu inda suke zama da dukkan sansaninsu.11Suka kwashe dukkan ganimar da kuma 'yan sarƙoƙi, da mutane da dabbobi.12Suka dawo da 'yan sarƙoƙin, da ganimar, da abubuwan da aka ƙwace wurin Musa, ga Eliyeza firist, zuwa kuma ga jama'ar Isra'ila. Suka kawo su zuwa cikin sansani cikin kwarurukan Mowab, wanda ke bakin Yodan kurkusa da Yeriko.13Musa, da Eliyeza firist, da dukkan shugabannin jama'a suka fito domin su tarye su a wajen sansani.14Amma Musa ya yi haushi da shugabannin rundunar, kwamandojin na dubbai da kuma na ɗari ɗari, waɗanda suka dawo daga yaƙi.15Musa yace masu, "Kun bar dukkan matayen su rayu ko?16Duba, waɗannan mataye sun jawo wa mutanen Isra'ila, ta wurin shawarar Bala'am, su aikata zunubi ga Yahweh ga zancen Feyor, yayinda annoba ta bazu cikin mutanen Yahweh.17Yanzu fa, sai ku kashe kowanne namiji cikin dukkan ƙananan, ku kuma kashe kowacce macen da ta taɓa kwana da namiji.18Amma ku ɗaukar wa kanku dukkan 'yan matan da ba su taɓa kwana da namiji ba.19Dole ku yi sansani can a wajen sansani na Isra'ila har na kwana bakwai. Dukkan ku da kuka kashe wani da kuma ko kuka taɓa duk wani matacce -dole ku tsarkake kanku a rana ta uku a rana ta bakwai kuma- ku da bayinku.20Dole ku tsarkake kowacce tufa da kowanne abin da aka yi da fatar dabba da gashin akuya, da kuma kowanne abin da aka yi da itace."21Sai Eliyeza yace da sojoji waɗanda suka tafi yaƙi, "Wannan shi ne umarnin shari'a da Yahweh ya bayar ga Musa:22Zinariyar, da azurfa, da jangaci, da tama, da kuza, da dalma,23da kuma kowanne abin da ya jimre ma wuta, sai ka saka shi ta wurin wuta, za shi kuma yi tsabta. Dole daga nan ka tsarkake waɗannan abubuwa da ruwan tsarkakewa. Duk abin da ba za shi shiga ta wuta ba sai ka tsarkake da ruwa.24Dole ku wanke tufafinku a rana ta bakwai, daga nan zaku zama da tsabta. Daga nan kuna iya shigowa cikin sansanin Isra'ila."25Sai Yahweh ya yi magana da Musa ya kuma ce,26"Ka ƙirga dukkan abin ganimar da aka kawo, da mutane da dabbobi. Kai, da Eliyeza firist, da kuma shugabanni na gidajen ubanni na mutane27za a raba ganimar gida biyu. Ka raba a tsakanin sojojin da suka tafi yaƙi da kuma dukkan sauran mutanen.28Sa'an nan za ka sa a karɓi haraji domina daga wurin sojojin da suka tafi yaƙi. Wannan harajin dole ya zama ɗaya daga cikin kowanne ɗari biyar, ko na mutane, ko na dabbobi, ko na jakuna, ko na awakai, ko tumakai.29Ka ɗauki wannan haraji daga rabinsu ka kuma bada su ga Eliyeza firist abin baikon da za a miƙa gare ni.30Haka kuma daga rabin mutanen Isra'ila, sai ka karɓi ɗaya daga cikin kowanne hamsin - daga wurin mutane, ko shanu, ko jakai, ko awakai, da kuma tumaki. Ka miƙa su ga Lebiyawa ma su lura da mazamnina.31Sai Musa da Eliyeza firist suka yi kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.32To yanzu dai ganimar da ta rage daga cikin abin da sojojin suka ɗauka su ne tumaki 675,000,33shanu dubu saba'in da biyu,34jakuna dubu sittin da ɗaya,35da kuma 'yan mata dubu talatin da biyu waɗanda ba su taɓa kwana da wani namiji ba.36Rabin da aka ajiye domin sojoji tumaki 337,000 ne.37Tumaki waɗanda suke na Yahweh kuma 675 ne.38Shanu dubu talatin da shida ne waɗanda harajin Yahweh saba'in da biyu ne.39Jakunan 30,500 ne, waɗanda daga ciki na Yahweh sittin da ɗaya ne.40Mutum dubu sittin ne daga ciki kuwa na harajin Yahweh talatin da biyu ne.41Sai Musa ya ɗauki harajin da za a miƙa ta baiko ga Yahweh. Ya bayar ga Eliyeza firist, kamar yadda Yahweh ya umarci Musa.42Game da rabi na mutanen Isra'ila waɗanda Musa ya karɓa daga sojojin da suka tafi yaƙi -43rabi na mutane kuwa, tumaki 337,500 ne,44shanu dubu sittin ne,45jakai 30,500 ne,46mata kuma dubu sha shida.47Daga cikin rabi na mutanen Isra'ila, Musa ya ɗauki ɗaya daga kowanne hamsin, da na mutane da kuma dabbobi. Ya bayar da su ga Lebiyawa waɗanda ke lura da mazaunin Yahweh, kamar yadda Yahweh ya umarce shi ya yi.48Sai shugabannin runduna, da na dubu dubu da kuma na bisa ɗari ɗari, suka zo wurin Musa.49Suka ce masa, "Bayinka sun lisafta sojojin dake a ƙarƙashinsu, kuma babu mutum ɗaya da ya ɓace.50Mun kawo baiko na Yahweh, abin da kowanne mutum ya samu, kayayyakin ado na zinariya, ƙarafu na ƙafa da na hannu, zoben hannu, da zoben kunne, da kayan ado na wuya, domin a yi kafara domin mu kanmu a gaban Yahweh."51Sai Musa da Eliyeza firist suka karɓa daga garesu zinariyar da dukkan kayayyaki na aikin gwaninta.52Dukkan baiko na zinariya da suka miƙa ga Yahweh - baye-baye daga shugabanni na dubbai daga kuma shugabanni na ɗari ɗari - an auna shekel 16,750.53Kowanne soja ya ɗauki ganima, kowanne mutum domin kansa.54Musa da Eliyeza firist suka karɓi zinariyar daga shugabanni na dubbai da na ɗari ɗari. Suka kai zuwa cikin alfarwa ta taruwa domin tunawa ta mutanen Isra'ila ga Yahweh.
Yawe yana yi wa Midiniyawa humunci domin sun sa Isra'ilawa ba su yi shakkan yiwa wa gumaka sujada ba.
Waɗannan maganganu biyun a takaice suna nufin abu ɗaya. Wannan wa hanya ce mai ladabi da ake amfani da shi don nanata cewa lokaci ya yi da Musa zai mutu, ruhunsa kuma zai tafin in da kakaninsa suke.
"Ba wa wasu mazaje maƙamai"
"je ku yi yaƙi da Midiyawa, ku kuma hukunta su saboda abin da suka aikata"
"1,000 ... 12,000"
"mazaje da yawa na Isra'ila"
AT: "kowace kabila sun aika da mazaje 1,000 don yaƙi"
Dukka kabilu 12 sun aika da mazaje, duk da kabilan Lewi. Duk sun aika da mazaje 1,000 don yaƙi.
Waɗannan sunayen sarakunan Midiyanawa.
Beyor shine mahaifin Bal'amu. Duba yadda kuka juya wannan cikin 22:5.
"Sun kwashe mallakar Midiyanawa a matsayin mallakar su"
"Sojojin Isra'ila sun ƙona dukka biranen da Midiyanawa suke zama da dukka zangon Midiyanawa"
"Sojojin Isra'ila sun kwashe"
Wannan na nufin kayaki da suka kwashe sa'ad da suka karkashe mazajen Madayanawa
babban shimfiɗaɗɗe fili
Waɗannan shugabannin sojojin su ne ke shugabantar mazaje fiye da 1,000, amma kasa da mazaje 10,000.
An fahimci kalman nan "na sojoji". AT: "na sojoji dubbai ... na sojoji ɗari ɗari"
Waɗannan shugabannin sojojin su ne ke shugabantar mazaje fiye da 100, amma kasa da mazaje 1,000.
Dokar da bayana wanda za a bar su su rayu. Sojojin su karyata dokar ta wurin barin dukka matayen da 'ya'ya su rayu. Wannan tsautawa shugabannin sojojin aka yi.
Wannan na nufin kassa kunne a kuma fahimci abin da mai magana ke faɗa wa masu sauraro.
yi jima'i da namiji
Musa ya na magana da shugabannin sojojin Isra'ila game da rashin tsarki a gaban Allah.
Wannan na nufin budurwa.
Musa na nufin duk wanda ya yi yaƙi ba shugabannin kawai ba.
Lallai ne su zama tsarkakku a ruhaniya kafin su shiga zangon.
AT: "kowane abin da wani ya yi da fatan dabba da gashin awaki ko itace"
Ele'azara ya koyawa sojojin yadda za a zama tsarkakakku a gaban Yawe bayan a dawo daga yaƙi.
ƙarafunan da ake amfani da su a wancan lokacin
"da ba za ta ƙone ba"
"sata cikin wuta"
Wannan na nufin ruwan da aka gauraye da toƙa daga hadayar zunubi. (Duba: 19:17.
Waɗannan su ne al'adun zama tsarkakke a gaban Yaweh.
AT: "Kirga dukkan mallakar da sojojin da sun kwashe"
Wannan na nufin abubuwan da aka kwashe daga wurin mutanen da Isra'ila suka kashe ko kuwa kama a yaƙi.
"shugabannin kowace kabila"
Yawe ya cigaba da magana da Musa.
"ni" na nufin Yaweh.
AT: "Karɓi dukka harajin daga ganimar da sojojin suka kwashe, sai ku bani"
"kowace 500"
"rabi daga cikin sojojin"
AT: "wanda zai ba miƙa mini"
Yawe ya cigaba da magana da Musa.
"Da kuma rabi daga cikin ganimar da mutanen Isra'ila suka kwashe"
"kowace 50"
waɗanda suke lura da alfarwa da kuma hadayar Yawe
An yi amfani da wannan kalman nan don nuna alamar canci daga kan koyasuwar. A nan Musa ya fara bada sarin sunayen ganimar da aka kwashe da kuma yawan abin da aka ba wa sojojin, ba wa mutanen, da kuma Yaweh.
shanu dubu biyu, jakai dubu sittin da ɗaya, da mataye dubu talatin da biyu- "shanu 72, jakai 61,000, da kuma mataye 32,000"
Wannan na nufin budurwai.
Musa yana ba da jeri sunayen ganimar da aka ba wa sojojin da kuma harajin da aka ba wa Yawe.
AT: "Tumaki na sojojin"
36,000
72
Musa yana ba da jeri sunayen ganimar da aka ba wa sojojin da kuma harajin da aka ba wa Yawe.
61
16,000
32
AT: "zama hadayar ga Yaweh"
Musa yana ba da jeri sunayen ganimar da aka ba wa sojojin da kuma harajin da aka ba wa Yawe.
shanu 36,000
"mataye 16,000." An bayana da farko cewa an karkashe dukka maza da mataye ma'aurata
Musa yana ba da jeri sunayen ganimar da aka ba wa sojojin da kuma harajin da aka ba wa Yawe.
Harajin mutanen ya fi haraji sojojin
Waɗannan shugabannin sojojin su ne ke shugabantar mazaje fiye da 1,000, amma kasa da mazaje 10,000. Duba yadda ka juya wannan cikin 31:13.
An fahimci kalman nan "na sojojin" AT: "bisa sojoji dubbai ... bisa sojoji ɗari ɗari"
Waɗannan shugabannin sojojin su ne ke shugabantar mazaje fiye da 100, amma kasa da mazaje 1,000.Dubi yadda ka juya magana makamancin haka cikin 31:13
Shugabanini sun dubi kansu a matsayin "bayin ku." Wannan hanya ce mai ladabi na magana da wani wanda ke da ikon.
AT: "tabbatar cewa kowane mutum na nan"
Shugabannin sojojin sun cigaba ada magana da Musa.
Waɗannan kayakin ado ne irir da mutanen su ka sanya.
"don yin godiya ga Allah domin ya cece ran mu"
"dukka kayakin zinary" ko "kayan ado na zinariya"
"Nauyin dukka zinariyan da shugabannin sojojin da suka ba wa Yawe"
"dubu goma sha biyar da ɗari bakwai da hamsin"
Shekel ɗaya daidai ne da giram 11
Zinariya za ta tunashe mutanen da cewa Yaweh ya ba su nasara. Zai kuma tunashe Yaweh da cewa mutanen sun ɗauki wa Yawe fansa bisa Madayanawa.
1A wannan lokacin zuriyar Ruben da ta Gad suna da garkunan shanu masu yawan gaske. Da suka lura cewa ƙasar Yaza da Giliyad, ƙasa ce mai kyaun gaske domin kiwon shanu.2Saboda haka zuriyar Gad da ta Ruben suka zo suka yiwa Musa magana, ga Eliyeza firist, ga kuma shugabannin jama'a. Suka ce,3"Ga lissafin wuraren da muka yi bincike: Atarot, Dibon, Yaza, Nimra, da Heshbon, Eliyele, Sebam, Nebo, da kuma Beyon.4Waɗannan su ne ƙasashen da Yahweh ya yaƙa a gaban shugabannin Isra'ila, kuma suna da kyau domin kiwon shanu. Mu, bayinka muna da shanu masu yawa."5Suka ce, "Idan mun sami tagomashi a wurinka, bari a bamu wannan ƙasa, mu bayinka, abin mallaka. Kada a ƙetare Yodan da mu."6Sai Musa ya amsa wa zuriyar Gad da ta Ruben, "To 'yan'uwanku sun tafi yaƙi, ku kuma kwa zauna a nan?7Don me kuke karya zuciyar mutanen Isra'ila daga shiga cikin ƙasar alƙawarin da Yahweh ya ba su?8Haka ubanninku suka yi sa'ad da na aike su daga Kadesh Barniya su yi duban ƙasa.9Suka tafi zuwa kwarin Eshkol. Suka ga ƙasar amma suka karya zukatan mutanen Isra'ila har da ba su yarda su shiga ƙasar da Yahweh ya basu ba.10Fushin Yahweh ya yi ƙuna a wannan rana. Ya kuma yi rantsuwa ya ce,11'Hakika babu wani daga cikin mazajen da suka fito daga cikin Masar, daga mai shekara ashirin da fiye da haka, da zai ga ƙasa wadda na yiwa Ibrahim, da Yakubu, da Ishaku alƙawari, domin basu bi ni da dukkan yadda ya kamata ba, sai dai12Kaleb ɗan Yefunne Bakeniziye, da kuma Yoshuwa ɗan Nun. Kaleb da Yoshuwa kaɗai suka bi ni yadda ya kamata.'13Fushin Yahweh kuma ya yi ƙuna a bisa Isra'ila. Ya sa suka yi watangaririya a cikin jeji na tsawon shekaru arba'in har sai da wannan tsãra ta waɗanda suka aikata wannan mugunta a fuskarsa suka hallaka.14Duba, kun tashi a cikin mazaunin ubanninku, haka kuma kuke mazaje masu zunubi, domin ku daɗa fushin Allah mai ƙuna gãba da Isra'ila.15Idan kuka juya daga binsa, shi kuma zai ƙara barinsu a cikin jeji, ku kuma da kun gama hallaka dukkan mutanen nan."16Sai suka zo wurin Musa suka kuma ce, "Ka barmu mu gina ganuwa ta shimge a nan domin dabbobinmu da kuma birane domin iyalanmu.17Duk da haka, mu da kanmu za mu shirya mu ɗauki makamai mu tafi tare da rundunar Isra'ila har sai mun tafi da su zuwa wurarensu. Amma iyalanmu za su zauna a birane masu ganuwa saboda sauran mutanen dake zama cikin ƙasar.18Ba zamu dawo ba har sai dukkan mutanen Isra'ila kowa ya karɓi gãdonsa.19Ba zamu ci gãdon ƙasan tare da su a ƙetaren Yodan ba, domin gãdonmu na a nan yamma da Yodan."20Sai Musa ya amsa masu, "Idan kuka yi abin da kuka faɗa, idan kuka ɗauki makamai don ku wuce gaban Yahweh don yaƙi,21don haka kowanne mutum daga cikin mayaƙanku za shi ƙetare Yodan a gaban Yahweh, har sai ya kori maƙiyansa daga gabansa,22ƙasar kuma a ci mulkinta a gabansa. Sa'an nan daga baya ku komo. Za ku zama marasa laifi a gaban Yahweh da kuma wurin Isra'ila. Wannan ƙasa za ta zama abin mallaka a gaban Yahweh.23Amma idan ba ku yi haka ba, duba, da ko za ku yi wa Yahweh zunubi. Ku kuma san da cewa lallai za a bayyana zunubinku a fili.24Ku gina birane domin iyalanku, shimgayen kuwa domin dabbobinku; sai ku yi abin da kuka faɗi."25Sai zuriyar Gad da na Ruben suka yi magana da Musa suka kuma ce, "Bayinka za su yi kamar yadda kai, shugabanmu, ka umarta.26Da ƙanananmu, da matayenmu, da garkunan tumakinmu, da dukkan shanunmu za su zauna can cikin biranen Giliyad.27Amma, mu, bayinka, za mu ƙetare a gaban Yahweh zuwa ga yaƙi, kowanne mutum a shirye domin yaƙi, yadda kai, ubangidanmu, ka faɗi."28Don haka sai Musa ya yi umarni game da su zuwa ga Eliyeza firist, zuwa ga Yoshuwa ɗan Nun, da kuma zuwa ga shugabanni na ubannin kabilun mutanen Isra'ila.29Musa yace masu, "Idan zuriyar Gad da na Ruben suka ƙetare Yodan tare da ku, kowanne mutum da ya yi shirin yaƙi a gaban Yahweh, idan kuwa aka sarayyar da ƙasar a gabanku, to, sai ku ba su ƙasar Giliyad abin mallaka.30Amma idan har basu ƙetare da ku da shirin yaƙi ba, don haka za su sami ta su mallakar tare da ku a cikin ƙasar Kan'ana."31Sai zuriyar Gad da ta Ruben suka amsa suka ce, "Kamar yadda Yahweh ya faɗa mana, mu bayinka, wannan ita za mu yi.32Za mu ƙetare da shirin yaƙi a gaban Yahweh zuwa cikin ƙasar Kan'ana, amma namu gãdon mallakar za su zauna da mu a wannan sashe na Yodan."33Don haka ga zuriyar Gad da na Ruben, da kuma ga rabin kabilar Manasse ɗan Yosef, Musa ya ba su masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da na Og, sarkin Bashan. Ya ba su ƙasar, ya kuma raba masu dukkan biranenta da iyakokinta, da biranen dake kewaye da su.34Sai zuriyar Gad suka sãke gina Dibon, Atarot, Arowa,35da Atrot Shofan, Yaza, Yogbeha,36Bet Nimra, da Bet Haran birane masu ganuwa da shimgaye domin tumaki.37Zuriyar Ruben kuma suka gina Heshbon, da Eleyale, da Kiriyatayim,38da Nebo, da Ba'al Meyon - daga baya aka canza sunayensu, da kuma Sibma. Suka bada wasu sunaye ga biranen da suka sãke ginawa.39Zuriyar Makir ɗan Manasse ya tashi ya tafi Giliyad, ya kuma ɗauke ta daga Amoriyawa waɗanda ke cikinta.40Sai Musa ya bãda Gilyad ga Makir ɗan Manasse, mutanen sa kuma suka zauna nan.41Yayir ɗan Manasse ya tashi ya tafi ya ci garuruwanta, ya kuma kira su da suna Habbot Yayir.42Noba ya tafi ya kuma cinye Kenat da kauyukanta, ya kuma kirata da suna Noba, bisa ga sunansa.
An yi amfani da waɗannan kalmomin don nuna alama ce na canji daga salon labarin. A nan Musa ya bada bayani game da kabilun Ra'ubainu da Gad.
Waɗannan sunayen birane ne.
Mutanen daga Ra'ubainu da Gad sun cigaba da yi wa Musa, Eliyazara da sauran shugabannin.
An yi magana game damar da Yahweh ya ba wa Isra'ila bisa mutanen da ke zama a ƙasar kamar Yahweh ne ya yi yaƙi da mutanen kamin Isra'ilawan. AT: "ƙasar da Yahweh ya ba mu daman yi nasara ga mutanen da ke zama ciki" (Duba:|Metaphor)
Mutanen Kabilun Ra'ubainu da Gad sun dubi kansu ta wannan hanya don su nuna bangirma ga mai iko dukka.
Maganan nan "gabanka" na nufin tunani ko ra'ayi. AT: "idan mun sami tagomashi a gare ka" ko "idan ka yi farinciki da mu" (Duba:|Metonymy)
AT: "bamu wannan ƙasa" (Duba:|Active or Passive)
Suna son ƙasar da ke Gabacin kogin Urdun a maimaƙo su haye zuwa ta yammacin su mallaki ƙasar da ke a wurin. AT: "Kada ka sa mu ƙetare kogin Urdun don mu mallaki ƙasar da ke gefen" (Duba:|Assumed Knowledge and Implicit Information)
Musa ya yi wannan tambayar don ya tsautawa mutane daga kabilar Gad da Ra'ubainu. AT: "Ba daidai ba ne ku zauna a wannan ƙasar sa'an nan 'yan'uwanku su tafi yaƙi."
Musa ya yi wannan tambayar do ya gyara kuskuren mutanen kabilun Gad da Ra'ubainu. AT: "Kada ku karya zuciyar ... ƙasar da Yahweh ya ba su." ko "Halin da kuna nunawa zai karya zuciyar ... ƙasar da Yahweh ya ba su."
A nan, "zuciya" na wakilcin mutanen kuma na nufin inda shauƙin su take. AT: "karya gwiwan mutanen Isra'ila daga tafiya" ko "sa mutanen Isra'ila su ƙi tafiya"
Musa ya cigaba da magana da mtuanen Ra'ubainu da Gad.
Wannan sunan wuri ne. Duba yadda ka juya wannan cikin 13:23.
Wannan na nufin cewa sun ga abinda ke cikin ƙasar. AT: "Sun ga karfafan mutanen da biranen da ke cikin ƙasar"
A nan, "zuciya" na wakilcin mutanen kuma na nufin inda shauƙin su take. Dubi yadda ka juya wannan cikin 32:6. AT: "karya gwiwan mutanen Isra'ila"
AT: Yahweh ya husata kwarai da gaske"
"ba wani daga cikin mtuanen." Wannan na nufin maza da mata.
"shekara 20 da fiye"
An yi magana game da duƙufa ga Yahweh da kuma yin masa biyayya kamar suna bin Yahweh. AT: "yi mini matuƙar biyayya" ko "duƙufa gare ni da dukkan ransu"
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan sunan rukunen mutane ne.
"Yahweh ya yi fushi da Isra'ila"
"shekaru 40"
AT: "ya hallaka dukka tsãran ... gaban" ko "dukkan tsãra ... gabansa sun mutu"
Zama a gaban wani na nufin zama inda mutumin zai iya ganin ka. AT: "waɗanda su yi mugunta a gaban Yahweh"
An yi magana game da mutanen Ra'ubainu da Gad sun yi kamar kakaninsu sai ka ce suna tsaye a daidai wurin da kakaninsu suke. AT: "kun fari yi kamar kakaninku."
An yi magana game da yadda mutanen sun sa Yahweh ya yi fushi sosai kamar fishin sa wuta ne, mutanen kuma na kãra abin da zai sa wuta ya kãra ci, a wuta. AT: "sa Yahweh ya kãra yin fushi da Isra'ila"
"gabadayan mutanen" ko dukka wannan tsãra mutanen"
"za mu shirya da makami" ko "za mu shirya do yin yaƙi"
...
Shugabannin Gad da Ra'ubainu sun cigaba da magana.
An yi magana game da ƙasar da mutanen za su karɓa ta zama nasu har matuka kamar gãdo ne za su karɓa. AT: "karɓi nasa rabon ƙasar"
...
Wannan na nufin cewa Yahweh zai je yaƙin tare da su, zai kuma ba su dama yi nasara ga abokan gãbansu su kuma karɓi ƙasarsu. AT: "a gaban Yahweh"
"har sai Yahweh ya kor abokan gãbansu daga gabansa." Kalmonin nan "ya" da "sa" su na nufin Yahweh. An yi magana game da ba da dama da Yahweh ya ba wa Isra'ila su yi nasara da abokan gãbansu kamar Yahweh ne yana yi masu yaƙi. AT: "har sai Yahweh ya ba wa sojojin ku daman yi nasara da abokan gãba har sai ya kori su daga gabansa"
A nan, kalman nan "ƙasa" na nufin mutanen da ke zama a wurin. AT: "kuma a gabansa Isra'ilawa sun ci mutanen da ke cikin ƙasar"
Wannan na nufin cewa za su komo zuwa gabacin Urdun. AT: "za ku komo wannan ƙasar, a gabacin Urdun"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) Za ku cika alkawarinku ga Yahweh da Isra'ila" ko 2) "Ba bu wani laifin ko wnai abin da Yahweh ko mutanen za su sa muku."
Musa ya yi magana game da zunubi sai ka ce mutum ne wanda zai hukunta mai laifi. Wannan na nufin cewa mutanen ba za su gujewa hukuncin da ta cancanci zunubansu ba. AT: "ku tabbata cewa Yahweh zai hukunta ku don zunubanku"
Mutanen Gad da Ra'ubainu sun dubi kansu a matsayin "bawan ka." Wannan hanya ce mai ladabi ta magana game da wani mai matuƙar iko.
Za ka iya bayana shi a fili cewa za su ƙetare zuwa Urdun. AT: "za mu ƙetare zuwa kogin Urdun
"kowane mutum da ya yi shiri don yaƙi"
"kowane mutum da ya shirya da makaminsa"
A nan kalman nan "ƙasa" na nufin mutanen da ke zama a wurin. AT: "idan Yahweh ya mallaki mazaunan ƙasar a gaban ku" ko "ida sun taimake ku mallakan mutanen da ke cikin ƙasar"
"ta haka zuriyar Gad da Ra'ubainu za su karɓi ƙasar Kan'ana tare da ku"
Za a iya bayana a fili cewa za su ƙetare Urdun. AT: "A shirye domin yaƙi zamu ƙetare Urdun."
An yi magana game da ƙasar da mutanen za su karɓa a matsayi mallakarsu kamar gãdo ne da za su karɓa. AT: "bangaren ƙasar da za mu mallaki"
Wannan karin maganan na nufin mallaki. AT: "zai zama namu"
Waɗannan sunayen sarakuna ne da ke mulkin a mulkoki daban-dabam. AT: "mulkin Sihon ... da mulkin Og"
Waɗannan sunayen birane ne.
Waɗannan sunayen birane ne.
AT: "daga baya mutane sun canza sunayen biranen"
Wannan sunan maza ne. Duba yadda ka juya wannan suna cikin 26:28.
Wannan sunan maza ne.
Wannan sunayen birane ne.
1Waɗannan su ne zangon mutanen Isra'ila bayan da suka bar ƙasar Masar da runduna bayan runduna a ƙarƙashin shugabancin Musa da Haruna.2Musa ya rubuta duk inda suka baro da inda suke kaiwa, yadda Yahweh ya umarta. Ga yadda zangon suka kasance, tashi bayan tashi.3Suka yi tafiya daga Ramesis cikin wata na farko, da suka taso a rana ta sha biyar ga wata na farko. Da safe bayan Bikin Ƙetarewa, sai mutanen Isra'ila suka fito a fili, dukkan Masarawa na gani.4Wannan ya faru ne sa'ad da Masarawa ke binne dukkan 'ya'yan farinsu matattu, waɗanda Yahweh ya kashe a cikinsu, gama ya kawo hukunci a bisa allolinsu.5Sai mutanen Isra'ila suka tashi daga Ramesis suka kuma yi zango a Sukkot.6Suka tashi daga Sukkot suka yi zango a Etam, a gacin jejin.7Suka tashi daga Etam suka juya baya zuwa Fi Hahirot, wadda take kallon Ba'al Zefon, inda suka yi zango fuska da fuskar Migdol.8Sai suka shirya tashi domi tafiya daga gaban Fi Hahirot suka kuma wuce ta tsakiyar teku zuwa cikin jeji. Sun yi tafiyar kwana uku zuwa cikin jejin Etam suka kuma yi zango a Mara.9Suka shirya tafiya daga Mara suka kuma isa Elim. A Elim inda akwai maɓulɓulan ruwa da kuma itatuwan dabino. A nan ne suka kafa zango.10Sai suka tashi daga Elim suka kafa zango a bakin Tekun Iwa.11Sai suka tashi daga bakin Tekun Iwa suka yi zango a cikin jejin Sin.12Suka tashi daga jejin Sin suka yi zango a Dofka.13Suka tashi daga Dofka suka kuma yi zango a Alush.14Suka tashi daga Alush suka yi zango a Refidim, inda ba a sami ruwan da mutane zasu sha ba.15Suka tashi daga Rafidim suka yi zango a cikin jejin Sinai.16Suka tashi daga jejin Sinai suka kuma yi zango a Kibrot Hattaba.17Suka tashi daga Kibrot Hattaba suka yi zango a Hazerot.18Suka tashi daga Hazerot suka kuma yi zango a Ritma.19Suka tashi daga Ritma suka kuma yi zango a Rimmon Ferez.20Su ka tashi daga Rimmon Ferez suka kuma yi zango a Libna.21Suka tashi daga Libna suka kuma yi zango a Rissa.22Suka tashi daga Rissa suka kuma yi zango a Kehelata.23Suka tashi daga Kehelata suka kuma yi zango a Tsaunin Shefa.24Suka tashi daga Tsaunin Shafa suka yi zango a Harada.25Suka tashi daga Harada suka kuma yi zango a Makhelot.26Suka tashi daga Makhelot suka yi zango a Tahat.27Suka tashi daga Tahat suka kuma yi zango a Tera.28Suka tashi daga Tera suka kuma yi zango a Mitka.29Suka tashi daga Mitka suka kuma yi zango a Hashmona.30Suka tashi daga Hashmona suka kuma yi zango a Moserot.31Suka tashi daga Moserot suka kuma yi zango a Bene Ya'akan.32Suka tashi daga Bene Ya'akan suka kuma yi zango a Hor Haggidgad.33Suka tashi daga Hor Haggidgad suka kuma yi zango a Yotbata.34Suka tashi daga Yotbata suka kuma yi zango a Abrona.35Suka tashi daga Abrona suka kuma yi zango a Ezion Geba.36Suka tashi daga Ezion Geba suka kuma yi zango a cikin jejin Zin a Kadesh.37Suka tashi daga Kadesh suka kuma yi zango a Tsaunin Hor, a bakin iyakar ƙasar Idom.38Sai Haruna firist ya haura bisa Tsaunin Hor ga umarnin Yahweh ya kuma mutu can a cikin shekara ta arba'in bayan da mutanen Isra'ila suka fito daga ƙasar Masar, a cikin wata na biyar, a rana ta farko ga watan.39Haruna na da shekaru 123 lokacin da ya mutu a Tsaunin Hor.40Sarkin Arad, Bakan'ane, wanda ke zama cikin kudancin jeji a ƙasar Kan'ana, ya ji game da isowar mutanen Isra'ila.41Suka tashi daga Tsaunin Hor suka kuma yi zango a Zalmona.42Suka tashi daga Zalmona suka kuma yi zango a Funon.43Suka tashi daga Funon suka kuma yi zango a Obot.44Suka tashi daga Obot suka kuma yi zango a Iye Abarim, a bakin iyakar Mowab.45Suka tashi daga Iye Abarim suka kuma yi zango a Dibon Gad.46Suka tashi daga Dibon Gad suka kuma yi zango a Almon Diblatayim.47Suka tashi daga Almon Diblatayim suka kuma yi zango a cikin duwatsu na Abarim, fuska da Nebo.48Suka tashi daga duwatsun na Abarim suka kuma yi zango a cikin kwarrurukan Mowab a bakin Yordnn a Yeriko.49Suka yi zango a bakin Yodan, daga Bet Yeshimot zuwa Abel Shittim cikin filayen Mowab.50Yahweh ya yi magana da Musa a cikin filayen Mowab a bakin Yodan a Yeriko ya kuma ce,51"Ka yi magana da 'ya'yan Isra'ila ka kuma ce masu, 'Yayin da kuka ƙetare Yodan zuwa cikin ƙasar Kan'ana,52dole ne ku kori dukkan mazauna ƙasar daga gareku. Dole ku hallakar da dukkan sassaƙaƙƙun siffofinsu. Dole ku hallakar da siffofinsu na zubi ku kuma farfasa dukkan tuddan wurarensu.53Dole ku mallaki ƙasar ku kuma zauna cikinta, domi na baku ƙasar abin mallaka.54Dole ne ku yi gãdon ƙasar yanki-yanki, bisa ga kowacce kabila. Dole ne ku bada yanki mai girma zuwa kabilar da tafi kowacce kabila, ga kabila mafi ƙanƙata kuwa ƙaramin yankin ƙasar. Duk sa'ad da yankin ya fãɗa ga kowacce kabila, wannan ƙasa zata zama tata. Za ku gãji ƙasar bisa ga kabilar ubanninku.55Amma idan baku kori mazaunan ƙasar a gaban ku ba, sa'an nan mutanen da kuka bari su tsaya, za su zama maku kamar wani abu cikin idanunku da kuma ƙaya a kwiɓinku. Za su wahalshe da rayukanku cikin ƙasar da kuka zauna.56Sa'an nan zai zama kuma duk abin da na yi niyyar yi wa waɗannan mutanen, zan yi maku shi."'
"bisa ga rundunar sojojinsu." Wannan na nufin cewa kowace kabila sun shirya mazaje ɗauke da makami don su tsare su. Dubi yadda ka juya "ruduna ɗauke da makami" cikin 1:1.
AT: "kamar yadda Yaweh ya umurta"
"daga wuni wuri zuwa wani"
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
A nan "farko" lamba ne. Wannan na nufin wata na fari bisa ga kalandar Yahudawa. Rana ta sha biyar ta kusa da farkon wata huɗu bisa ga kalandar Romawa.
"Masarawan suna gani a sa'ad da Isra'ilawa suka bar"
Wannan na nufin 'ya'yan fari maza. AT: "'ya'yansu maza na fari"
An yi magana cewa Yawe ya nuna cewa ya fi dukkan allolin da Masarawa ke bauta wa sai ka cewa Yawe ya hukunta waɗannan allolin. AT: "ya nuna cewa ya fi allolinsu"
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
"tafi daga"
"a iyakar jeji"
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
Wannan na nufin lokacin da Yawe ya raba Jan Teku domin Isra'ila wa su tsere daga sojojin Masarawa.
"maɓulɓulan ruwa 12... itatuwan dabino 70"
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
AT: "inda mutanen ba su samu ruwan sha ba"
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
AT: "shekara ta 40 bayan"
Wannan watan biyar ne bisa ga kalandar Yahudawa. Rana ta farin ya yi kusa ta wata bakwai bisa ga kaladar turawa.
Bakan'ani sarkin Arad"
Wannan shine sun wani birni a Kan'ana.
"ya ji cewa mutanen Isra'ila suna zuwa"
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
Musa ya bada tsarin sunaye wuraren da Isra'ila sun je bayan sun fita daga ƙasar Masar.
babbar ƙasar mai faɗi
"sassaƙaƙƙun duwatsun su"
Yawe ya cigaba da magana da Musa game da abin da lallai ne mutanen su.
An yi magana game da Isra'ilawa sun ɗauki ƙasar ta zama tasu sai ka ce su gãji ƙasar.
"Kowane kabila za su karɓi ƙasar bisa ga yadda kuri'ar ta faɗi"
Yawe ya cigaba da magana da Musa game da abin da lallai ne mutanen su.
Daidai kamar yadda wani abu ƙarami a idon mutum ko kuwa ƙaramin ƙaya da ya shiga cikin fatan mutum zai iya sa mutum ya ji ƙaiƙayi sosai, haka kuma in an bar ƙaɗan daga cikin Kan'aniyawan za su kawo wa Isra'ilawa damuwa.
1Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,2"Ka umarci mutanen Isra'ila ka kuma ce ma su, 'Sa'ad da kuka shiga cikin ƙasar Kan'ana, ƙasar da zata zama taku, ƙasar Kan'ana da iyakokinta,3iyakarku daga yamma zata kai har cikin jejin Zin kusa da iyakar Idom. Gabashin ƙarshe na yamma za shi zama kan layin da ya kai ƙarshe a yammancin ƙarshe na Tekun Gishiri.4Iyakarku zata juya zuwa yamma daga dutsen Akrabbim ta wuce ta jejin Zin. Daga nan, zata tashi zuwa gabas da Kadesh Baniya har ta kai Harza Adda zuwa ga Azmon.5Daga nan, iyakar zata juya daga Azmon zuwa wajen rafin Masar ta kuma bi zuwa teku.6Iyaka ta Kudu za ta zama kan iyakar Babban Teku. Wannan zai zama iyaka gareku ta yammanci.7Iyakarku ta Arewa zata tashi daga kan layin da zaku sa alama daga Babban Teku zuwa Tsaunin Hor,8daga Tsaunin Hor zuwa Lebo Hamat, daga nan zuwa Zedad.9Daga nan iyakar zata ci gaba zuwa Zifuron ta tsaya a Hazar Enan. Wannan zata zama iyakarku ta arewa.10Zaku saka alama mai nuna iyakarku ta gabas daga Hazar Enan kudu da Shefam.11Daga nan iyaka ta gabas za ta kai daga Shefam zuwa Ribla, gabas da Ain. Iyakar za ta gangaro ta wajen gabas gefen Teku na Kinneret.12Iyakar kuma za ta gangaro zuwa ga Kogin Yodan zuwa ga Tekun Gishiri ta kuma gangaro zuwa iyaka ta gabashin Tekun Gishiri. Wannan za ta zama ƙasarku, da dukkan iyakokinta dake zagaye da ita.13Sai Musa ya umarci mutanen Isra'ila ya ce, "Wannan ce ƙasar da zaku yi gãdonta ta wurin rabo, wanda Yahweh ya umarta a bayar ga sauran kabilu tãre da kuma rabin kabilar.14Kabila ta zuriyar Ruben, bisa ga rabon gãdo ga ubannin kabilunsu, da kuma kabila ta zuriyar Gad, bisa ga rabon gãdo ga ubannin kabilunsu, da kuma rabin kabilar Manasse dukkansu suka karɓi tasu ƙasar.15Kabilun biyu da kuma rabin kabilar suka karɓi tasu gãdon na ƙasar a ƙetaren Yodan a sashen Gabashin Yeriko, wajen fitar rana."16Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,17"Ga sunayen mazajen da zasu raba maku ƙasar domin gãdonku: Eliyeza firist da kuma Yoshuwa ɗan Nun.18Za ku zaɓi shugaba daga kowanne kabila don ya raba ƙasar domin zuriyarsu.19Ga sunayen mazajen: Daga kabilar Yahuda, Kaleb ɗan Yefunne.20Daga kabilar zuriyar Simiyon, Shemuwel ɗan Ammihud.21Daga kabilar Benyamin, Elidad ɗan Kislon.22Daga kabila ta zuriyar Dan aka sami shugaba, Bukki ɗan Yogli.23Daga cikin zuriyar Yosef, daga kabila ta zuriyar Manasse shugaba, Hanniyel ɗan Efod.24Daga kabila ta zuriyar Ifraim aka sami shugaba, Kemuwel ɗan Shiftan.25Daga kabila ta zuriyar Zebulun aka sami shugaba, Elizafan ɗan Farnak.26Daga kabila ta zuriyar Issaka aka sami shugaba, Faltiyel ɗan Azzan.27Daga kabila ta zuriyar Asha aka sami shugaba, Ahihu ɗan Shelomi.28Daga kabila ta zuriyar Naftali aka sami shugaba, Fedahel ɗan Ammihud."29Yahweh ya umarci waɗannan mutanen su raba ƙasar Kan'ana su kuma raba wa kowanne kabila na Isra'ila gãdonsu.
Juya wannan maganan daidai kamar yadda ka yi cikin 33:11.
Yahweh ya cigba da gaya wa Musa inda iyakar ƙasar dai zai ba wa Isra'ila yake.
Yahweh ya cigba da gaya wa Musa inda iyakar ƙasar dai zai ba wa Isra'ila yake.
Yahweh ya cigba da gaya wa Musa inda iyakar ƙasar dai zai ba wa Isra'ila yake.
Juya wannan daidai kamar yadda ka yi cikin 20:22.
Yahweh ya cigba da gaya wa Musa inda iyakar ƙasar dai zai ba wa Isra'ila yake.
Wannan na nufin sauran kabilun Isa'ila wanda za su zauna a yammanci Kogin Urdun da ke ƙasar Kan'ana. Kabilun Ra'ubainu da Gad da rabin kabilan Manassa sun riga sun karɓi ƙasar da ke gabacin Kogin Urdun.
"bisa ga yadda Yahweh ya ba da kayakin ga kakanin su"
Kabilan Ra'ubainu da Gad da kuma rabin kabilan Manassa"
A nan "ku" na nufin mutanen Isra'ila. Waɗannan mazaje za su jefa kuri'a don su raba ƙasar. Sa'an nan za su raba kasar ga kabilun.
Wannan shine tsarin sunayen mazajen da za su taimaka cikin raba ƙasar tsakanin kabilun.
Wannan ya cigaba da bada tsarin sunayen mazajen da za su taimaka cikin raba ƙasar tsakanin kabilun.
Wannan ya cigaba da bada tsarin sunayen mazajen da za su taimaka cikin raba ƙasar tsakanin kabilun.
Wannan ya kammala tsarin sunayen mazajen da za su taimaka cikin raba ƙasar tsakanin kabilun.
1Yahweh ya yi magana da Musa a kwarin Mowab kusa da Yodan a Yeriko ya kuma ce,2"Ka umarci jama'ar Isra'ila su baiwa Lebiyawa kaɗan daga gãdonsu na ƙasar. Zasu basu birane su zauna ciki da kuma wuraren kiwo zagaye da waɗannan birane.3Su Lebiyawan zasu sami waɗannan biranen su zauna a ciki. Wuraren kiwon za su zama domin garkunansu na shanu, da na tumaki, da na dukkan dabbobinsu.4Wuraren kiwon zagaye da birnin da zaku baiwa Lebiyawan zai tashi daga bangon birnin kãmu dubu ɗaya a kowanne sashi.5Dole ka auna kãmu dubu biyu daga wajen birnin a sashen gabas, kãmu dubu biyu zuwa sashen kudu, kãmu dubu biyu zuwa sashen yamma, kãmu dubu biyu kuma zuwa ga sashen arewa. Wannan za shi zama wuraren kiwo domin biranensu. Biranen zasu kasance a tsakiya.6Birane shida da zaku ba Lebiyawa zasu zama biranen mafaka. Zaku ku yi tanadin waɗannan wurare domin duk wanda ya kashe wani na iya guduwa can. Haka kuma za ku yi tanadin wasu birane arba'in da takwas.7Biranen da zaku bai wa Lebiyawa gaba ɗaya zai zama arba'in da takwas. Dole ku basu tare da wuraren kiwonsu.8Manyan kabilu na jama'ar Isra'ila, kabilar da take da yawan ƙasa, zata tanada birane fiye da kowa. 'Yar ƙaramar kabila kuwa zata tanadi birane kaɗan. Kowacce kabila zata tanada wa Lebiyawa dai-dai bisa ga gãdon da ta karɓa.9Sai Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,10"Ka yi magana da 'ya'yan Isra'ila ka ce masu, 'Idan kuka ƙetare Yodan zuwa ƙasar Kan'ana,11sa'an nan zaku zaɓi birane su zama biranen mafaka dominku, wurin da idan mutum ya kashe wani ba da gangan ba, yana iya guduwa can.12Waɗannan biranen zasu zama mafakarku daga mai ramako, domin kada a kashe mai kisa ba tare da ya gurfana gaban shari'a a gaban jama'ar ba.13Za ku zaɓi birane shida a matsayin birnin mafaka.14Dole ku shirya birane uku a ƙetaren Yodan, uku kuma a cikin ƙasar Kan'ana. Za su zama birane na mafaka.15Domin jama'ar Isra'ila, domin baƙi, domin kowanne mai zama tare da ku, waɗannan birane shida zasu zama maku mafaka ga duk wanda ya kashe wani ba da gangan ba yana iya gudu can.16Amma idan mutumin mai kisan ya bugi wani da ƙarfe, idan kuma mutumin ya mutu, to mutumin tabbas mai kisan kai ne. Lallai dole a kashe shi.17Idan wani mutum ya bugi wani da dutse cikin hannunsa dake iya kashe wani, idan kuma mutumin ya mutu, to tabbas wannan mutumin mai kisan kai ne. Lallai dole a kashe shi.18Idan mutum mai kisa ya bugi wani mutum da makami na sanda dake iya kashe wani mutumin, idan kuma mutumin ya mutu, to tabbas wannan mutumin mai kisan kai ne. Lallai dole a kashe shi.19Mai ramakon jini zai kashe mai kisan. Idan ya same shi, mai ramakon jini sai ya kashe shi.20Idan ya bugi wani da ƙiyayya ko ya wurga masa wani abu, yayin da yake ɓuya domin ya yi masa kwanto, har mutumin ya mutu,21ko idan ya buge shi ƙasa da ƙiyayya da hannunsa har mutumin ya mutu, to mai kisan da ya buge shi dole za a kashe shi. Shi mai kisan kai ne. Mai ramakon jini na iya kashe mai kisan kan idan ya gãmu da shi.22Amma idan mutumin mai kisan ya bugi wani nan da nan ba tare da ya shirya ƙiyayya ko ya wurga wani abin da ya buge shi ba tare da ya yi niyar yin hakan ba23ko ya wurga dutsen dake iya kashe shi ba tare da ya gan shi ba, don haka mai kisan bai zama maƙiyin sa ba; ba ƙoƙarin cutar da mutumin ya yi ba. Amma ga abin da za a yi idan mutumin ya mutu har wa yau.24Idan haka ne, jama'ar zasu yi shari'a tsakanin mai kisan da mai ramakon jinin da waɗannan sharuɗa.25Jama'ar zasu kuɓutar da mai kisan daga ikon mai ramakon jinin. Su jama'ar zasu komo da mai kisan kan zuwa birnin ramakon wanda asali ya guje daga gare shi. Za ya zauna a wurin har sai bayan mutuwar babban firist, wanda aka shafe da mai mai-tsarki.26Amma idan mai kisan ya fita daga iyakar birnin mafakan da ya gudu zuwa gare ta,27idan kuma mai ramakon jini ya gamu da shi a wajen iyakar birninsa na mafaka, idan kuma ya kashe mutumin mai kisan, mai ramakon jini ba zai zama mai laifi game da kisan kai ba.28Dalili kuwa shi ne mutumin mai kisan kai da bai fito daga cikin birnin mafaka ba har sai babban firist ya mutu. Bayan mutuwar babban firist, mai kisan kan na iya komawa ƙasarsa inda gãdonsa yake.29Waɗannan dokokin zasu zama maku farillai dominku cikin dukkan tsararrakin mutanenku a dukkan inda kuka zauna.30Duk wanda ya kashe wani, za a kashe mai kisan, kamar yadda aka yi shaida daga shaidu. Amma shaidar mutum ɗaya baza ta iya sa a kashe mutum ba.31Haka kuma, ba zaku karbi ɗiyya domin ran mai kisa wanda aka iske shi da laifin kisa ba. Dole a kashe shi.32Ba zaku karbi ɗiyya domin wanda ya gudu zuwa birnin mafaka ba. Da haka ba zaku yardar ma sa ya zauna bisa gãdonsa ba har sai babban firist ya mutu.33Kada ku ƙazantar da wannan ƙasar da kuke zama a cikinta ta yin haka, gama jinin da aka zubar ta hanyar kisa na ƙazantar da ƙasa. Babu kafarar da za a iya yi domin ƙasar yayin da aka zubar da jini bisanta, sai dai da jinin shi wanda ya zubas da jinin.34Don haka baza ku ƙazantar da ƙasar da kuke zama cikinta ba domni ina zama cikinta. Ni, Yahweh, ina zaune cikin mutanen Isra'ila."'
babbar fili da babu tuɗu
Yahweh bai ba wa Lewiyawan ƙasar su ba, don su zauna a biranen sauran kabilun.
ƙasa ne inda dabbobi su ka ci ciyawa
"kãmu 1,000." In ta kama lallai to sai a yi amfani da ma'aunin wuri mai nisa na wannan zamani. Ga yadda za a yi hakan. AT: "mita 457"
Yahweh ya cigaba da gayawa Musa abin da lallai ne mutanen za su yi.
"kãmu 2,000." Kãmu ɗaya santimita 46 ne.
Wannan na nufin mutanen da sun kashe wani amma ba tabbatar ko sun kashe mutumin da sanin su ko kuwa ba da son ran su ba.
"42 ... 48"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa game da abin da lallai mutanen su yi.
"cikin kuskure"
Wannan na nufin dangi na kusa da ke so ya yi ramako ta wurin kashe mutumin da ake zarga.
AT: "don kada wani ya kashe mutumin da ake zarga kamin jama'ar su yanka hukunci a dakalin shari'a"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa game da abin da lallai mutanen su yi.
Yahweh ya cigaba da magana da Musa game da abin da lallai mutanen su yi.
AT: "Ya kama dole a kashe shi"
A nan kalman nan "jini" na nufin mai kisan. AT: "Mutumin da ya rama kisan" ko kuwa "Dangi da ke nema ya yi ramako"
AT: "lallai ne dangi ya kashe mutumin da ake zargin sa" ko kuwa "lallai ne wanda ake zarga ya mutu"
"ba domin ya shirya shi saboda ƙiyayya tun da wuri ba"
An yi magana game da mutumin da ke ƙoƙarin yi wa wani lahani sai ka ce mutum ne da ya ɓoye don ya kai wa wani hari. AT: "ba tare da ya yi ƙoƙarin yi wa mutumin lahani ba"
A nan kalman nan "jini" na nufin mai kisan. A juya wannan daidai kamar yadda aka yi cikin 35:19. AT: "Mutumin da ya rama kisan" ko kuwa "Dangi da ke nema ya yi ramako"
Wannan na nufin cewa idan jama'ar sun tabbata cewa mutuwan ya faru cikin hatsari ne to lallai ne su cece mutumin da ake zarga daga dangin da suke so su kashe sh. In kuwa sun tabbatar da cewa mutuwar ya faru ne ba cikin hatsari ba, to sai dangi su kashe mutumin.
AT: "wanda ka shafe shi da mai mai-tsarki"
A nan kalman nan "jini" na nufin mai kisan. A juya wannan daidai kamar yadda aka yi cikin 35:19. AT: "Mutumin da ya rama kisan" ko kuwa "Dangi da ke nema ya yi ramako"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa game da abin da lallai ne mutanen su yi.
"da dukka zuriyar ku wanda zu yi rayuwa kamin ku"
AT: "lallai ne wani ya kashe mutumin da ya yi kisa"
AT: "bisa ga shaidan daga shaidu" ko "kamar yadda shaidu sun shaida game da kisan"
Shaidar mutum ɗaya bai isa har da za kashe wanda ya yi kisa. AT: "Amma shaidar mutum ɗaya bai isa har da za ka kashe mutum"
AT: "Lallai ne ka kashe shi"
Wannan na nufin cewa mutumin ya bar birnin fansa ya kuma koma gida. AT: "Kada ka ... yarda ya zauna a birnin kubuta har ya koma gida zuwa inda kayakinsa suke"
"ta ɗaukan fansa"
An yi magana game da sa ƙasar ta zama a rashin gamsuwa ga Yahweh sai ka ce and ƙazantar da ƙasar. AT: "Kada ku sa ƙasar da kuke zama ƙazantacce a gare ni, domin jini wanda aka kashe ta kan sa ƙasar ta zama ƙazamtacce a gare ni"
Wannan na nufin cewa ta wurin rashin biyayya ga shari'a da ke game da mutumin da ya kashe wani.
Wannan na nufin lokacin da mutum ya kashe wani da gangan. AT: "Sa'ad da wani ya zub da jini a ƙasar, za a yi wa ƙasar kafara ta wurin kashe wanda ya kashe wani"
1Sa'an nan shugabanni na gidajen kakannin iyalai na zuriyar Giliyad ɗan Makir (wanda shi ne ɗan Manasse), waɗanda suke daga zuriyar Yusufu, suka iso suka yi magana da Musa da a gaban shugabanni waɗanda ke kan gaba daga gidajen kakanni na mutanen Isra'ila.2Suka ce, "Yahweh ya umarce ka, ubangidanmu, ka bada rabon ƙasa bisa ga ƙuri'a ga mutanen Isra'ila. Yahweh ya umarce ka da ka bada rabon Zelofehad ɗan'uwanmu ga 'ya'yansa mata.3Amma idan 'ya'yansa mata suka yi aure zuwa wata ƙabilar mutanen Isra'ila, sai gãdonsu na ƙasa a cire daga gãdon dake na ubanninmu. Za a ƙara bisa gãdon dake na ƙabilar da dã suka shiga. Don haka, za a cire daga namu gãdon.4Don haka, idan shekarar Yubili na mutanen Isra'ila ta zo, sai a harɗa gãdonsu da gãdon kabilar da suka yi aure. Ta haka, za a cire gãdonsu daga gãdon kabilar kakanninmu."5Sai Musa ya ba da umarni ga mutanen Isra'ila, bisa ga maganar Yahweh. Ya ce, "Abin da kabilar zuriyar Yosef suka ce dai-dai ne.6Wannan ne abin da Yahweh ya faɗa game da 'ya'ya mata na Zelofehad. Ya ce, 'Bari su auri duk wanda ya yi masu dai-dai, amma dole ne su yi aure daga cikin zuriyar iyalin mahaifinsu.'7Kada a canza gãdon wata kabilar mutanen Isra'ila zuwa ga wata kabilar. Duk mutumin Isra'ila dole ya ci gaba da zama da nasa gãdo na kabilar ubanninsa.8Kowacce ɗiya ta mutanen Isra'ila wadda take da gãdo cikin kabilarta za ta auri wani daga zuriyar mahaifinta. Wannan zai zama haka domin dukkan mutanen Isra'ila su ajiye abin gãdonsu daga ubanninsu.9Babu gãdon da za a ɗauka daga kabila ɗaya zuwa wata kabilar. Kowacce kabila ta mutanen Isra'ila za ta riƙe nata abin gãdon.10Sai 'ya'ya ɗiyan Zelofehad suka aikata kamar yadda Yahweh ya umarce Musa.11Mahal, Tirza, Hogla, Milka, da Nowa, 'ya'ya mata na Zelofehad, suka auri zuriyar Manasse.12Suka yi aure cikin dangin iyalin Manasse ɗan Yosef. Ta haka, gãdonsu ta kasance tare da kabilar da mahaifinsu ya fito.13Waɗannan su ne umarnai da shari'un da Yahweh ya bai wa mutanen Isra'ila ta bakin Musa a cikin kwarurukan Mowab a bakin Yodan a Yeriko.
Wannan sunan maza ne. Juya wannan suna daidai kamar yadda ka yi cikin 26:28.
Wannan sunan maza ne. Juya wannan suna daidai kamar yadda ka yi cikin 26:33.
AT: "ba zai zama na kakaninmu ba"
AT: "zai zama na"
AT: "ba zai zama a cikin gãdon"
Wannan na nufin bikin da ake yi sau ɗaya a shekara hamsin. A wannan biki, dukka ƙasar da wani ya sayar ko ya yi musaya, to lallai ne ya mayar wa maishi.
AT: "nasu rabon zai zama"
AT: "za su karɓi rabon ƙasar kabilan"
"bisa ga abin da Yahweh ya faɗa"
AT: "Bar su su auti wanda suke so"
AT: "amma za su auri wani daga kabilan kakaninsu ne kawai"
Kalman nan "raba" na wakilcin ƙasar da kowane kabula ta ƙarba a matsayin gãdo. AT: "Ba wani rabon ƙasar"
"wanda take da gãdon ƙasar kabilar ta"
An yi magana game mallakan kowane iyali kamar gãdo ne da suka karɓa.
An yi magana game da mai da gãdo daga wani kabila zuwa wani kamar kayan ya fito daga hannun wani zuwa hannun wani. AT: "Ba wanda zai canza rabon da yake da shi na ƙasar daga wani kabila zuwa wani"
Waɗannan sunayen mata ne. Juya wanan sunayen daidai kamar yadda ka yi cikin 26:33.
An yi magana game da ƙasar da kowane diyar Zelofehad ta mallaka kamar gãdo ne da suka karɓa. AT: "ƙasar da suka karɓa a matsayin gãdon"
babban shimfiɗaɗɗe fili
1Waɗannan ne maganganun da Musa ya gaya wa dukkan Isra'ila a ƙetaren Yodan a cikin jeji, a sararin kwarin Kogin Yodan daura da Suf, tsakanin Faran, da Tofel, da Laban, da Hazerot, da kuma Di Zahab.2Tafiyar kwana sha ɗaya ce daga Horeb ta hanyar Dutsen Seyir zuwa Kadesh Barniya.3Ya kasance a shekara ta arba'in, a wata na sha ɗaya, a kan ranar farko na watan, Musa ya yi magana da mutanen Isra'ila, yana gaya masu dukkan abin da Yahweh ya umarce shi game da su.4Wannan kuwa bayan da Yahweh ya kai hari ga Sihon sarkin Amoriyawa ne, wanda ke zama a Heshbon, da Og sarkin Bashan, wanda ke zama a Ashtarot a Edrayi.5A ƙetaren Yodan, ƙasar Mowab, Musa ya fara sanar da waɗannan umarnai, cewa,6"Yahweh Allahnmu ya yi magana da mu a Horeb, cewa, 'Dogon zaman da kuka yi a wannan ƙasar tudu ya isa.7Ku juya ku kama tafiyarku, ku kuma tafi ƙasar tudu ta Amoriyawa da dukkan wurare kusa da sararin kwarin Kogin Yodan, a cikin ƙasar tudu, a cikin ƙasar kwari, a cikin Negeb, da bakin teku - ƙasar Kan'aniyawa, da cikin Lebanon har ya zuwa babban kogi, wato Yufiretis.8Duba, na sanya ƙasar a gaban ku; ku tafi ciki ku kuma mallaki ƙasar da Yahweh ya rantse wa ubanninku - ga Ibrahim, ga Ishaku, ga kuma Yakubu - ya basu da kuma zuriyarsu a bayansu.'9Na yi magana da ku a wancan lokacin, cewa, 'Bazan iya ɗaukarku da kaina ni kaɗai ba.10Yahweh Allahnku ya riɓanɓanya ku, kuma, duba, a yau kun riɓanɓanyu kamar taurarin sama.11Bari Yahweh, Allahn ubanninku, ya maida ku fiye da yadda kuke sau dubu, ya kuma albarkace ku, kamar yadda ya yi maku alƙawari!12Amma ta yaya ni da kaina ni kaɗai zan ɗauki nawayoyinku, karkiyoyinku, da saɓananku?13Ku ɗauki mutane masu hikima, mutane masu fahimta, da mutane masu kyakkyawar shaida daga kowacce kabila, zan kuma sanya su shugabanni a bisan ku.'14Kuka amsa mani kuka ce, ' Abin da ka faɗa ya yi mana kyau mu yi.'15Sai na ɗauki shugabanni daga cikin kabilunku, mutane masu hikima, mutane kuma masu kyakkyawar shaida, na kuma mai da su shugabanni a bisan ku, hafsoshin dubbai, hafsoshin ɗaruruwa, hafsoshin hamsin-hamsin, hafsoshin goma-goma, da ofisoshi, kabila bayan kabila.16Na umarci alƙalanku a wancan lokaci, cewa, 'Ku saurari saɓanai tsakanin 'yan'uwanku, ku kuma yi hukuncin adalci tsakanin mutum da ɗan'uwansa, da bãre wanda ya ke tare da shi.17Ba zaku nuna sonkai ga kowa ba a cikin saɓani; zaku saurari ƙarami da babba bai ɗaya. Ba zaku ji tsoron fuskar mutum ba, domin hukuncin na Allah ne. Saɓanin da yafi ƙarfinku, zaku kawo a gare ni, zan kuma saurare shi.'18Na umarce ku a wancan lokaci dukkan abubuwan da zaku yi.19Muka yi tafiyarmu daga Horeb muka kuma tafi ta cikin dukkan babban jeji da ban razana da kuka gani, a kan hanyarmu ta zuwa ƙasar tudu ta Amoriyawa, kamar yadda Yahweh Allahnmu ya umarce mu; kuma muka zo Kadesh Barniya.20Na ce maku, 'Kun zo ƙasar tudu ta Amoriyawa, wadda Yahweh Allahnmu ya ke bamu.21Duba, Yahweh Allahnku ya sanya ƙasar a gaban ku; ku tafi, ku mallaketa, kamar yadda Yahweh, Allah na ubanninku, ya faɗi maku; kada ku ji tsoro, ko ku karaya.'22Kowannenku ya zo gare ni ya kuma ce, 'Bari mu aika da mutane gaba da mu, saboda suyi binciken ƙasar domin mu, su kuma kawo mana magana game da hanyar da zamu bi mu kai hari, game kuma da biranen da zamu je.'23Shawarar ta gamshe ni sosai; na ɗauki mutanenku sha biyu, mutum ɗaya domin kowacce kabila.24Suka juya suka tafi zuwa cikin ƙasar tudu, suka isa kwarin Eshkol, suka kuma yawace shi.25Suka ɗauko daga cikin amfanin ƙasar a cikin hannuwansu, suka kuma kawo mana. Suka kuma kawo mana magana suka kuma ce, 'Ƙasa ce mai kyau da Yahweh Allahnmu ya ke bamu.'26Duk da haka kuka ƙi kai hari, amma kuka yi tawaye gãba da dokar Yahweh Allahnku.27Kuka yi gunaguni a rumfunanku kuka kuma ce, "Saboda Yahweh ya ƙi mu ne ya fito da mu daga ƙasar Masar, ya bayar da mu cikin hannun Amoriyawa su hallaka mu.28Ina zamu iya zuwa yanzu? 'Yan'uwanmu sun sa zuciyarmu ta narke, cewa, 'Waɗannan mutane masu girma ne da tsayi fiye da mu; biranensu kuma manya ne kuma da garu har cikin sammai; bugu da ƙari, munga 'ya'ya maza na Anakim a wurin."'29Daganan nace maku, 'Kada ku firgita, ko ku ji tsoronsu.30Yahweh Allahnku, wanda ya ke tafiya a gaban ku, zai yi yaƙi domin ku, kamar dukkan abin da ya yi domin ku a Masar, a gaban idanunku,31da kuma a cikin jeji, inda kuka ga yadda Yahweh Allahnku ya ɗauke ku, kamar yadda mutum ke ɗaukar ɗansa, dukkan inda kuka tafi har sai da kuka zo wannan wuri.'32Amma duk da wannan magana baku gaskata da Yahweh Allahnku ba,33wanda ya tafi a gaban ku a bisa hanya don ya sami wuri domin kuyi sansani, cikin wuta da dare cikin kuma girgije da rana.34Yahweh ya ji ƙarar maganganunku ya kuma yi fushi; ya yi rantsuwa ya ce,35'Tabbas babu ko ɗaya daga cikin waɗannan mutane na wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba kakanninku,36sai Kaleb ɗan Yefunne; zai gan ta. A gare shi zan bayar da ƙasar da ya taka akai, ga 'ya'yansa kuma, saboda ya bi Yahweh ɗungum.'37Sa'an nan Yahweh ya fusata da ni saboda ku, cewa, 'Kai ma baza ka je cikin wurin ba;38Yoshuwa ɗan Nun, wanda ke tsayawa a gaban ka, shi zai je cikin wurin; ka ƙarfafa shi, domin zai bida Isra'ila su gãje ta.39Haka kuma, ƙananan yaranku, waɗanda kuka ce zasu hallaka, waɗanda a yau basu da sanin nagarta ko mugunta - zasu je cikin wurin. A gare su zan bayar da ita, kuma zasu mallake ta.40Amma game da ku, ku juya ku kama tafiyarku zuwa cikin jeji ta gefen hanyar zuwa Tekun Iwa.'41Daganan kuka amsa kuka ce mani, 'Mun yi zunubi gãba da Yahweh; zamu tafi mu yi yaƙi, kuma zamu bi dukkan abin da Yahweh Allahnmu ya umarce mu mu yi.' kowanne mutum a cikin ku ya sanya makaman yaƙinsa, kuma kuka shirya ku kai hari ga ƙasar tudu.42Yahweh ya ce mani, 'Ka ce masu, "Kada ku kai hari kuma kada ku yi yaƙi, gama bazan kasance tare da ku ba, kuma zaku sha kaye daga maƙiyanku.'43Na yi magana da ku ta wannan hanya, amma baku saurara ba. Kuka yi tawaye gãba da dokar Yahweh; kuka kangare kuma kuka kai hari ga ƙasar tudu.44Amma Amoriyawa, waɗanda ke zaune a ƙasar tudu, suka fito gãba da ku kuma suka kore ku kamar zuma, suka kuma mãke ku ƙasa a Seyir, har nesa zuwa Horma.45Kuka dawo kuma kuka yi kuka a gaban Yahweh; amma Yahweh bai saurari muryarku ba, ko kuma ya kula da ku ba.46Sai kuka dakata a Kadesh na kwanaki da yawa, dukkan kwanakin da kuka dakata a can.
Wannan na nufin ƙasan dake hayin Rafin Urdun zuwa gabas na Isra'ila. Musa na gabas na Urdun a loƙacin da ya yi magana da yan Isra'ilan. AT: "gabas na Urdun"
Waɗannan ne sunayyen wurare. (Dubi:|How to Translate Names)
"Ana ɗaukar kwana goma sha ɗaya a tafiya daga Horeb ... zuwa Kadesh Barniya"
Wannan wurin duwatsu ne a kudun Mataccen Tekun. Ana kiran wurin "Edom."
(Dubi:|Numbers)
Ana iya fasara lamba da ke bayyana abu. AT: "Sun yi zama a jeji har shekaru arba'in, watanni sha ɗaya, da kwana ɗaya a loƙacin da Musa ya yi maganan"
Wannan ne watar goma sha ɗaya na kalandan Yahudawa. Rana ta farko na nan kusa da tsakiyar watan farko a kalandar yammanci.
(Dubi:
Wannan ne sunan Allah da ya bayyana wa mutanensa a cikin Tsohon Alkawari. Dubi kalman fasara game da Yahweh akan yadda za a fasara wannan.
"Yahweh ya sa yan Isra'ila cin nasara"
Waɗannan sunayyen Sarakuna ne.
Waɗannan sunayyen gari ne.
Wannan na nufin ƙasan dake hayin Rafin Urdun zuwa gabas na Isra'ila. Musa na gabas na Urdun a loƙacin da ya yi wannan magana. AT: "gabas na Rafin Urdun." Fasara wannan kamar yadda yake a cikin 1:1.
Kalmar "mana" na nufin Musa da sauran mutanen Isra'ila.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "Ba lalai ne ku sake zama a wannan dutsen ba"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da Yahweh ya faɗa masu.
Kalmar "juya" ƙarin magana ne na yin abu. AT: "Fara kuma a tafiyarku"
Yahweh na bayyana wurare a garin da ya yi alkawari za ba wa Isra'ila.
Wannan wuri ne a cikin duwatsu kusa da wurin da Amoriyawa sun yi zama.
filin ƙasa da na nan shimfiɗaɗɗe
"Ba da hankali da abin da zan gaya maku"
"Yanzu ina ba ku wannan ƙasan"
Yahweh na magana kamar shi wani mutum ne. AT: "cewa Ni, Yahweh, na rantse"
Kalmar "Ubanne" ƙarin magana ne wa dukkan kakkanninku. AT: "kakkanninku"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da Yahweh ya faɗa masu.
A nan "Na" na nufin Musa. Jimlar "a wancan loƙacin" na nufin loƙacin da yan Isra'ila su na Horeb, da ke ɗaya da Dutsen Sina. AT: "A loƙacin da mu na Horeb, Na yi maku magana"
A nan "ɗuakarku" na nufin "bi da ku" ko "mulki da ku." AT: "Ya yi mani yawa sosai in bi da ku da kai na"
Wannan ƙarin magana ne da na nufin Allah ya kara lambar Isra'ilan. AT: "babban taron mutane da yawa"
Jimlar "dubu" ƙarin magana ne na "yawa sosai." AT: "so dayawa"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Musa ya yi amfani da tambaya domin ya nanata cewa ba zai iya warware dukkan damuwarsu da kansa ba. AT: "Ba zan iya ɗaukar nawayyanku ba, da dawainiyarku, da kuma husumarku da kai na ba."
Musa ya yi magana kaman damuwowi da ƙaran mutanen da ya kamata ya kula da su, abubuwa ne masu nauyi da ya yi ta ɗaukawa. AT: "kula da damuwanku, ƙaranku"
gardamanku" ko "saɓaninku"
"mutane daga kowane kabila wanda mutanen Isra'ila na girmamawa"
Musa ya cigaba da yi wa mutanen Isra'ila magana.
"kuma mutanen da mutanenku ke girmamawa." Dubi yadda an fasara wannan a cikin 1:12.
"na taron dubu ɗaya ... na taron ɗari ...na taron hamsin ... da kuma taron goma"
Waɗannan lakami ne wa shugabane dabam dabam a gwamnatin Isra'ila.
"daga kowacee kabilunku"
"yi hukunci na gaskiya game da gardama da Isra'ila ke da shi da junansu"
Musa ya cigaba da magana da masu shari'a, don haka umurnin jam'i ne.
" kada ku nuna son zuci"
Waɗannan matsananci biyun "ƙarami" da "babba" na wakilcin dukka mutane. AT: "za ku yi wa dukka mutane daidai"
Kalmar "fuska" ƙarin magana ne na dukkan mutum. "Ba za ku" umurni ne. "Kada ku ji tsoron wani"
Wannan na nufin loƙacin da su ke Horeb, a Dutsen Sina.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da yan Isra'ilawa suka yi a zamanin da ta wuce.
"babban jeji mai muni da kuka haye"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da yan Isra'ilawa suka yi a zamanin da ta wuce.
Musa na magana da Isra'ilawa kamar ya na magana da mutum ɗaya, don haka wannan ya zama ɗaya. .
"na ba ku wannan ƙasa yanzu." Dubi yadda an juya wannan a cikin 1:7.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da yan Isra'ilawa suka yi a zamanin da ta wuce.
"Sun bar wurin suka tafi"
Wannan ƙwari ne a cikin jihar Hebron, wanda yake kudun Urushalima.
"nemi wuraren da za su kai hari"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da yan Isra'ilawa suka yi a zamanin da ta wuce.
"Mazaje goma sha biyun suka ɗauki"
"ɗauki wasu amfanin ƙasar"
Mai maganan na magana kamar "labari" abu ne na jiki da ana iya gani, wadda wani na iya kawowa. AT: "gaya mana"
AT: "cewa ƙasa da Yahweh Allahnmu zai ba mu na da kyau"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da yan Isra'ilawa suka yi a zamanin da ta wuce.
Allah ya umurci yan Isra'ila da cewa su kai hari su kuma hallakar da Amoriyawa, amma yan Isra'ila sun ji tsoro suka ki yin fada da su.
A nan "cikin hannun" na nufin ba wa Amoriyawa iko akan su. AT: "cikin ikon Amoriyawan"
A nan wannan tambaya ya nanata yadda sun ji tsoro. Ana iya juya wannan tambaya zuwa jimla. AT: "Ba mu da inda za mu je."
Wannan na nufin cewa sun ji tsoro. AT: "sa mu tsoro sosai"
Wannan zuguiguita ne da na nanata fargaban da mutanen sun yi saboda garin babba ne, na da kuma ƙarfi sosai.
"na da ganuwa musa tsawo kamar"
Waɗannan zuriyar mutanen Anak ne wanda su na nan da girma da kuma ban tsoro.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da yan Isra'ilawa suka yi a zamanin da ta wuce.
"Na gaya wa kakanenku"
Anan "a idanunku" na nufin abin da sun gani. AT: "wanda ku da kanku kun gani"
Musa na magana da yan Isra'ilan kaman su mutum ɗaya ne, don haka duk misalen "ku" jam'i ne.
A nan an ƙwatanta kula da Yahweh ke yi wa mutanensa da na Uba. AT: "Yahweh Allahnku ya kula da ku, kamar yadda Uba yake kula da ɗansa"
"har kun zo wannan ƙasa da Allah ya yi alkawari zai ba ku"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da yan Isra'ilawa suka yi a zamanin da ta wuce.
Musa ya tuna masu game da yadda Yahweh ya sha gaban Isra'ilawa a dukkan tafiyarsu a zamanin da ta wuce.
"shirya laimarku"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin Yahweh ya faɗa masu.
"ji abin da kuke faɗa"
Allah ya yi alwashin hana waɗanda sun yi masa tawaye ga shiga ƙasar da ya yi alkawari zai ba su.
"zai shiga"
"sai dai Kaleb"
Wannan ne sunan mahaifin Kaleb.
Yahweh ya yi magana kamar shi wani ne dabam. AT: "ya yi mani biyayya gaba ɗaya"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da yan Isra'ilawa suka yi a zamanin da ta wuce.
Wannan na nufin loƙacin da Musa ya yi rashin biyayya da abin da Yahweh ya faɗa mashi ya yi don Musa na fushi da mutanen Isar'ila.
Wannan ne sunan mahaifin Joshua.
Ana iya sa a bayyane dalilin da Joshua ya tsaya a gaban Musa. AT: "wanda tsaya a gabanku kamar bawarku" ko "wanda ya taimake ku"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da yan Isra'ilawa suka yi a zamanin da ta wuce.
Ba su rigaya sun san abin da ke da kyua ko mugunta ba.
"juya ku koma kan hayar da kun bi"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da yan Isra'ilawa suka yi a zamanin da ta wuce.
"mun yi wa Yahweh tawaye ta wurin yin masa rashin biyayya"
"za mu yi biyayya"
"Duwatsun" na matsayin mutanen da sun yi zama a wurin. AT: "kai hari wa mutanen da sun yi zama a cikin duwatsun"
AT: "abokan gabanku za su ci nasara da ku domin ba zan kasance tare da ku ba"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"Duwatsun" na matsayin mutanen da sun yi zama a wurin. AT: "kai hari wa mutanen da sun yi zama a cikin duwatsun"
"Zuma" ƙaramin, kwaro ne dake yawo a babban taro na kuma harbin mutanen da sun yi masu barazana. Wannan na nufin cewa Amoriyawan dayawa suka kai hari wa sojojin Isra'ilan da har sun bar yaƙin.
Wannan sunan ƙaramin wuri ne.
Wannan sunan gari ne.
"ƙashe sojojinku dayawa"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da yan Isra'ilawa suka yi a zamanin da ta wuce.
"koma Kadesh"
1Daga nan muka juya muka ɗauki tafiyarmu ta hanyar cikin jeji ta wajen Tekun Iwa, kamar yadda Yahweh ya yi magana da ni; muka tafi kewaye da Dutsen Seyir na kwanaki da yawa.2Yahweh ya yi magana da ni, cewa,3'Tafiyarku kewaye da wannan dutse ya isa; ku juya arewa.4Ka umarci mutanen, cewa, "Zaku bi ta cikin kan iyakar 'yan'uwanku, zuriyar Isuwa, waɗanda ke zaune a Seyir; zasu ji tsoronku. Saboda haka ku kiyaye5kada ku yi yaƙi da su, domin ba zan baku ko ɗaya daga cikin ƙasarsu ba, a'a, bama wadda ta isa tafin ƙafarku ya taka ba; gama na bayar da Dutsen Seyir ga Isuwa a matsayin mallaka.6Za ku sayi abinci daga gare su da kuɗi, domin ku ci; zaku kuma sayi ruwa daga gare su da kuɗi, domin ku sha.7Gama Yahweh ya albarkace ku a cikin dukkan aikin hannunku; ya san tafiyarku cikin wannan babban jeji. Cikin waɗannan shekaru arba'in Yahweh Allahnku yana tare daku, kuma baku rasa komai ba."'8Sai muka ratsa ta wurin 'yan'uwanmu, zuriyar Isuwa da ke zaune a Seyir, nesa da hanyar Araba, daga Elat daga kuma Eziyon Gebar. Daganan muka juya muka kuma ratsa ta jejin Mowab.9Yahweh ya ce mani, 'Kada ku matsawa Mowab, kada kuma ku yi faɗa da su a yaƙi. Domin ba zan bayar da ƙasarsa ba a gare ku domin mallakar ku, saboda na bayar da Ar ga zuriyar Lutu, domin mallakar su,'10(Emiyawa suka yi zama a wurin a dã, mutane manya, masu yawa, masu tsayi kuma kamar Anakimawa;11su kuma waɗannan ana ɗaukar su 'yan Refayim, kamar Anakimawa; amma Mowabawa suna kiransu Emiyawa.12Horitawa su kuma sun yi zama a Seyir a dã, amma zuriyar Isuwa suka gaje su. Suka hallakar da su a gabansu suka kuma zauna a wurin su, kamar yadda Isra'ila ya yi da ƙasar mallakarsa wadda Yahweh ya basu.)13Yanzu ku tashi ku tafi tsallaken kwarin Zered.' Sai muka tafi tsallaken rafin Zered.14Yanzu daga kwanakin da muka zo daga Kadesh Barniya har muka ketare rafin Zered, shekaru talatin da takwas ne. A wannan lokacin ne dukkan tsarar mazajen da suka isa yaƙi aka kawar da su daga mutanen, kamar yadda Yahweh ya rantse masu.15Haka nan kuma, hannun Yahweh ya yi gãba da wannan tsara domin a lalatar da su daga mutanen har sai da suka ƙare.16Sai ya kasance, sa'ad da dukkan mazajen da suka isa yaƙi suka mutu suka kuma ƙare daga cikin mutanen,17sai Yahweh ya yi magana da ni, cewa,18'A yau ne zaku ƙetare Ar, kan iyakar Mowab.19Sa'ad da kuka zo kusa daura da mutanen Ammon, kada ku matsa masu ko ku yi yaƙi da su; gama ba zan baku ko ɗaya daga cikin ƙasar mutanen Ammon ba a matsayin mallaka; saboda na bayar da ita ga zuriyar Lutu a matsayin mallaka."'20(Wannan ita ma an ɗauke ta ƙasar Refayim. Refayim ne suka yi zama a wurin a dã - amma Ammoniyawa suna kiransu Zamzumiyawa -21mutane manya, masu yawa, masu tsayi kuma kamar Anakimawa. Amma Yahweh ya hallakar da su a gaban Ammoniyawa, suka kuma gaje su suka zauna a wurin su.22Wannan kuma Yahweh ya yi domin mutanen Isuwa, waɗanda ke zaune a Seyir, da ya hallakar da Horinawa a gabansu, zuriyar Isuwa kuma suka gaje su suka zauna a wurin su har ya zuwa yau.23Amma game da Abibiyawa waɗanda ke zaune a ƙauyuka har nesa zuwa Gaza, Kaftorimawa, waɗanda suka zo daga Kafto, suka hallakar da su suka zauna a wurin su.)24Yanzu ku tashi, ku kama tafiyarku, ku kuma ratsa ta kwarin Arnon; duba, Na bayar cikin hannunku Sihon Ba'amoriye, sarkin Heshbon, da ƙasarsa. Ku fara mallakarta, ku kuma yi faɗa da shi a yaƙi.25A yau zan fara sanya tsoronku da fargabanku a bisa mutanen da ke dukkan ƙarƙashin sama; zasu ji labari game da ku zasu kuma yi rawar jiki su kuma kasance cikin ƙunci sabili da ku.'26Na aika da manzanni daga jejin Kedemot ga Sihon, sarkin Heshbon, da maganar salama, cewa,27Bari in ratsa ta cikin ƙasarka; zan bi ta kan titi; bazan juya ko zuwa hannun dama ba ko zuwa na hagu.28Za ka sayar mani da abinci domin kuɗi, saboda in ci; ka bani ruwa domin kuɗi, saboda in sha; ka dai bar ni kawai in ratsa ta ciki bisa sawaye na;29kamar zuriyar Isuwa da ke zaune a Seyir, da Mowabawa da ke zaune a Ar; har sai na ketare Yodan zuwa cikin ƙasar da Yahweh Allahnmu ya ke bamu.'30Amma Sihon, sarkin Heshbon, ba zai barmu mu ratsa ta wurinsa ba; domin Yahweh Allahnku ya taurare tunaninsa ya kuma sa zuciyarsa ta kafe, domin ya kayar da shi ta wurin ƙarfinku, wanda yanzu ya yi shi a yau.31Yahweh ya ce mani, 'Duba, Na fara miƙa Sihon da ƙasarsa a gaban ku; ku fara mallakar ta, domin ya zama kun gaji ƙasarsa.'32Daganan Sihon ya fito gãba da mu, shi da dukkan mutanensa, su yi faɗa a Yahaz.33Yahweh Allahnmu ya bayar da shi a gare mu muka kuma kayar da shi da 'ya'yansa maza da dukkan mutanensa.34Muka ɗauki dukkan biranensa a wancan lokaci muka kuma hallakar da kowanne birni ɗungum - maza da mata da ƙanana; bamu bar mai tsira ba.35Garken dabbobi ne kawai muka ɗauka a matsayin ganima domin mu, tare da ganimar biranen da muka ɗauka.36Daga Arowa, wadda ke gefen kwarin Arnon, daga kuma birnin da ke cikin kwarin, dukkan hanya har Giliyad, babu birnin da ya fi ƙarfin mu. Yahweh Allahnmu ya bayar da su cikin hannuwanmu.37Ƙasar zuriyar Ammon ce kawai baku je ba, har ma dukkan gefen kogin Yabbok, da biranen ƙasar tudu - kowanne wurin da Yahweh Allahnmu ya hana mu zuwa.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da yan Isra'ilawa suka yi a zamanin da ta wuce.
"Sai muka kewaya muka tafi"
AT: 1) Yan Isra'ilan suka yi tafiya a ta dutse da a ke kira Seir na tsawon loƙaci ko 2) Yan Isra'ila sun yi yawo a wata yanki da ake kira Dutsen Seir na tsawon loƙaci.
Wannan wuri ne mai duwatsu a kudun Mataccen Teku. Ana kiran wurin "Edom." Dubi yadda kun juya wannan a cikin 1:1
Wasu harshuna na fasara wannan kaman "dare dayawa."
Yahweh ya cigaba da magana da Musa.
"na danginku, zuriyar Esau"
Yahweh ya na tuna wa Isra'ila cewa ya ba da wannan yankin wa zuriyar Esau.
Musa ya cigaba da umurce yan Isra'ila game da yadda za su yi wa zuriyar Esau.
Yahweh ya na ba su izini ko doka, umurni, ya kuma gaya masu kada su yi sata. "Na yarda maku ku saya abinci daga wurin su" ko "idan ku na son abinci, ku saya daga wurinsu"
"daga zuriyar Esau"
Za ku iya cirewa idan ba a bukatan waɗannan kalmomin.
Musa ya yi magana da yan Isra'ila kamar su mutum ɗaya ne, don haka misalan "ku" jam'i ne.
"aikin hannunku" na nufin dukka aikin da sun yi. AT: "dukka aikinku"
Wannan ƙarin magana ne na "ya san abin da ya faru da ku a loƙacin da ku na tafiya."
Wannan bayani ne na "kun samu komai da ku na bukata."
Musa ya cigaba da magana wa mutanen Isra'ila.
"ta danginmu"
Waɗannan sunayyen gari ne.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "mun yi ta tafiya"
Wannan ne karshen wata sashin maganar Musa dake tuna wa yan Isra'ila game da yadda Yahweh ya bi da su a cikin jeji.
Kalmar "Moab" ƙarin magana ne na mutanen Moab. AT: "Kada ku dame mutanen Moab"
Wannan ne sunan wata birni a cikin Moab.
Mutanen Isra'ila sun hada zuriya da mutanen Moab. Moab ɗan Lot ne. Lot kuma ɗan ƙanwan Ibrahim.
Marubucin ya faru ba da tushen bayani game da mutanen ƙasan. Waɗannan kalmomi ba sua cikin maganan Musa wa yan Isra'ila.
Waɗannan kalmomin sun ba da tushen bayani game da mutanen Emim, wanda sun zauna a ƙasan kafin Moabites. Harshenku na iya samin wata takamaiman hanya na sa alama a tushen bayanin.
Waɗannan ne sunayyen ƙungiyan mutanen da ana ɗaukansu ƙatte.
Waɗannan ne zuriyar mutanen Anak wanda suke da girma da kuma ban tsoro. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 1:26.
Wannan ya cigaba da tushen bayani game da bambancin mutanen da sun yi zama a ƙasan. .
Wannan ne sunan ƙungiyan mutane.
"ƙashe dukkansu don kada a bar wani ya rayu a sakaninsu" ko "cire su daga gabansu ta wurin ƙashe su dukka"
Musa ya cigaba da tuna wa yan Isra'ila game da abin da ya faru da su a cikin jeji.
"Sai Yahweh ya ce, "Ku tashi yanzu ... Zered.' Sai." AT: "Sai Yahweh ya ce mana mu tashi ... Zered. Sai
fara yin wani abu
Ƙoraman na gudu zuwa cikin mataccen Teku daga kudu ya kuma yi iyaka sakanin Edom da Moab.
Kalmar "yanzu" ya sa alama canji daga labarin zuwa tushen bayani game da yadda mutanen Isra'ila suka yi tafiya da kuma game da fushin Allah akan wannan zamanin. Idan harshenku na da wata hanyar nuna cewa abin da ke biye tushin bayani ne, ku yi amfani da shi anan.
Wannan wata hanya ne na ladabi na ce "sun mutu."
A nan "hannun Yahweh" na nufin ikon Yahweh. AT: "Yahweh ya yi amfani da ikonsa akan" ko "Yahweh ya hukunta"
Musa ya cigaba da tuna wa yan Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
Musa ya yi magana da yan Isra'la kaman su mutum ɗaya ne, don haka duk misalin "ku" da kuma umurnin "kada ku dame" ɗaya ne.
Wannan sunan gari ne a cikin Moab. Dubi yadda kun fasara "Ar" a cikin 2:9.
Mutanen Isra'ila sun hada dagi da zuriyar Ammon. Ammon ne ɗan Lot. Lot kuma ɗan ɗan'uwar Ibrahim ne.
Waɗannan ayoyin sun fara ba da tushen bayani game da irin mutanen da sun yi zama a ƙasan. Idan harshenku na da wata hanyar nuna cewa abin da ke biye ne tushen bayani, ku yi amfani da shi a nan.
AT: "Mutane na kuma gani cewa"
Wannan ne sunan taron mutane. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 2:10.
Wannan kuma wani sunan taron mutanen Rephaim.
Wannan ne sunan taron mutane. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 1:26.
"bar Ammoniyawan su ci nasara da su" ko "bar Ammoniyawan su kashe su dukka"
"Ammoniyawan suka ɗauki dukka abubuwan da Rephaim suka mallaka, sai suka zauna a wurin da Rephaim suka yi zama"
Wannan kuma wani sunan taron mutane ne. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 2:12.
"ɗauki dukka abubuwan da Horites suka mallaka, sai suka zauna a wurin da Horites suka yi zama"
Marubucin ya gama kwatanta yanda Allah ya sa Esau ya ci nasara da ƙasar da Esau na zama yanzu.
Waɗannan sunayyen taron mutane ne.
Wannan sunan wuri ne. zai iya zama wani suna na Crete da ke cikin tsibirin Tekun Mediterran
"hallakar da Avvim"
"zuana inda Avvim suka yi zama"
Marubucin ya gama ba da tushen bayani, ya na kuma faɗa abin da Musa ya gaya wa yan Isra'ila.
Yahweh na gaya wa Musa abin da mutanen za su yi. "Yanzu ku tashi" ko "Yanzu ku tafi."
"cigaba da tafiyarku"
Wannan ne sunan kwarin rafin Arnon. Ya yi iyaka a sakanin Moab da yan Amonites.
Maganar "a hannunku" na nufin "cikin iko ko ƙarfinku." AT: "Na riga na ba ku ikon cin nasara"
Musa ya yi magana da yan Isra'ilan kamar su mutum ɗaya ne, kuma umurnin "fara mulki" da "faɗa" ɗaya ne.
Wannan sunan Sarki ne. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 1:3.
Wannan sunan gari ne. Dbi yadda kun fasara wannan a cikin 1:3.
"yi fada da shi da sojojinsa"
Kalmomin "tsoro" da "razana" a takaice na nufin abu ɗaya ne, ya na kuma nanata cewa tsoron na da tsanani. AT: "sa mugun tsoro"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "mutanen a kowane ƙasa"
Wannan kuma na nanata cewa mutanen za su "razana a cikin azaba."
Musa ya cigaba da magana wa mutanen Isra'ila.
Anan "Na" na nufin Musa.
Wannan ne sunan wurin da ke kusa da kwarin Arnon.
Waɗannan ne sunayyen mutum da kuma wani wuri. Dub yadda kun fasarasu a cikin 1:3.
A nan maganan "kalmomin salama" na nufin "da kyautan salama na" ko "da sako daga wuri na da rokon salama."
Wannan jimla ya nanata cewa za su yi tafiya a hanya ɗaya a kowane loƙaci. AT: "Ba zan canza wuri ba" ko "Zan tsaya kullum a kan hanyan"
Wannan ya cigaba da sakon Musa wa Sarki Sihon.
Musa ya gaya wa Sihon cewa yan Isra'ilan ba za su yi sata daga Amoriyawan ba, ya kuma roka cewa Sihon da mutanensa su sayar da abinci da ruwa wa yan Isra'ilan; ba umurni ne yake bayerwa ba. AT: "Na zata zan biya wa abinci don in ci da kuma biya wa ruwa don in iya sha"
Musa na maganan mutanen Isra'ila kamar su ne Musa da kansa. AT: "sayar ma ni da mutane na ... mu iya ci ... ba mu .... mu iya sha"
"bar mu mu wuce ta cikin ƙasarku"
Wannan sunan wuri ne. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 2:9.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
Waɗannan sunayyen mutum da kuma wuri ne. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 1:3.
Musa ya yi magana da yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Dukka waɗannan jimlan su na nufin abu ɗaya kuma na nanata cewa Yahweh "ya sa shi ya yi taurin kai."
"ba wa Sihon da kasarsa maku"
"ɗauki shugabancin ƙasarsa, domin ku gaje shi"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin ya faru zamanin da ta wuce.
Wannan ne sunan mutum. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 1:3.
Wannan ne sunan wata birni a cikin Moab.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin ya faru zamanin da ta wuce.
"Mun ƙwace dukka biranen sarki Sihon"
"ƙashe dukka mutane da suka yi zama a cikin birnin"
Wannan ne wata sunan birni a arewancin bankin rafin Arnon.
"Arnon" sunan wata rafi ne. Fasara kaman a cikin 2:24.
An yi amfani da wannan magana domin a nanata cin nasaransu a yaki. AT: "mun iya cin nasara da mutanen kowane birni ko da birnin na da ganuwa mai tsawo a kewaye da ita"
Musa ya yi magana da yan Isra'ilan kaman su mutum ɗaya ne.
Wannan ne sunan rafin da ya yi iyaka sakanin ƙasan Sihon da ƙasan yan Amoniyawa.
1Daga nan muka juya muka tafi hanyar Bashan. Og, sarkin Bashan, yazo kuma ya kawo mana hari, shi da dukkan mutanensa, ya yi faɗa a Edrai.2Yahweh ya ce mani, "Kada ka ji tsoronsa; gama na baka nasara a kansa kuma na sanya dukkan mutanensa da ƙasarsa a ƙarƙashin mulkinka. Zaka yi masa yadda kayi wa Sihon, sarkin Amoriyawa, wanda ya zauna a Heshbon.'3Sai Yahweh Allahnmu ya bamu nasara a bisa Og sarkin Bashan, dukkan mutanensa kuma aka sanya su ƙarƙashin mulkinmu. Muka fyaɗe su har ba ko ɗaya daga cikin mutanensa da ya rage.4Muka ɗauki dukkan biranensa a wancan lokaci. Babu ko ɗaya daga cikin biranen nan sittin da bamu karɓe ba daga gare su - dukkan lardin Argob, masarautar Og a Bashan.5Dukkan waɗannan birane tsararru ne da dogayen ganuwoyi, ƙofofi, da ƙarafuna; waɗannan kuwa baya ga ƙauyuka marasa ganuwa masu yawan gaske.6Muka hallakar da su ɗungum, kamar yadda muka yi da Sihon sarkin Heshbon, muka hallakar da kowanne birni ɗungum - maza da mata da ƙanana.7Amma dukkan garken dabbobin da ganimar biranen, muka ɗauka a matsayin ganima domin mu.8A wannan lokacin muka ɗauke ƙasar daga hannun sarakunan Amoriyawa biyu, waɗanda ke ƙetaren Yodan, daga kwarin Arnon zuwa dutsen Hamon9(Sidoniyawa na kiran dutsen Hamon Siriyon, Amoriyawa kuma na kiran sa Senir)10da dukkan biranen sarari, dukkan Giliyad, da dukkan Bashan, har ya zuwa Saleka da Edrai, biranen masarautar Og a Bashan."11(Game da ragowar Refayim, Og sarkin Bashan ne kaɗai ya rage. Duba! gadonsa gadon ƙarfe ne. Ba yana a Rabba ba, inda zuriyar Ammon suka zauna? tsawonsa kamu tara ne fãɗinsa kuma kamu huɗu, bisa ga yadda mutane ke gwaji.)12Wannan ƙasa muka ɗauka mallaka a wannan lokaci - daga Arowa, wato ta gefen kwarin Arnon, da rabin ƙasar tudu ta Giliyad, da biranenta - Na bayar ga Rubenawa ga kuma Gadanawa.13Sauran Giliyad da dukkan Bashan, masarautar Og, Na bayar ga rabin kabilar Manasse. (Dukkan lardin Argob, da dukkan Bashan. Wannan gundumar ce ake kira ƙasar Refayim.14Yayir, wata zuriyar Manasse, suka ɗauki dukkan lardin Argob zuwa kan iyakar Geshurawa da Ma'akatawa. Ya kira lardin, wato Bashan, da sunansa, Habbot Yayir, har ya zuwa yau.)15Na bayar da Giliyad ga Makir.16Ga Rubenawa ga kuma Gadawa na bayar da gunduma daga Giliyad zuwa kwarin Arnon - tsakiyar kwarin shi ne kan iyakar gundumar - zuwa kuma kogin Yabbok, wanda ke kan iyaka tare da zuriyar Ammon.17Wasu kan iyakokinta kuma su ne sararin kwarin Kogin Yodan, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) zuwa gangarowar Dutsen Fisga maso gabas.18Na dokace ku a wancan lokaci, cewa, 'Yahweh Allahnku ya baku wannan ƙasa ku mallake ta; ku, dukkan ku mazajen yaƙi, zaku ƙetare shirye da makamai a gaban 'yan'uwanku, mutanen Isra'ila.19Amma matayenku, da ƙanananku, da garken dabbobinku (nasan kuna da garken dabbobi masu yawa), zasu tsaya a biranen da na baku,20har sai Yahweh ya bayar da hutawa ga 'yan'uwanku, kamar yadda ya yi a gare ku, har su ma sai sun mallaki ƙasar da Yahweh Allahnku ke bayarwa a gare su a ƙetaren Yodan; daganan za ku dawo, kowanne mutum a cikinku, ga kaddararku da na bayar a gare ku.'21Na dokaci Yoshuwa a wancan lokacin, cewa, 'Idanunka sun ga dukkan abin da Yahweh Allahnka ya yi ga waɗannan sarakuna biyu; Yahweh zai yi irin haka ga dukkan masarautun da za ku je a ƙetare.22Ba za ku ji tsoronsu ba, gama Yahweh Allahnku shi ne zai yi yaƙi dominku.'23Na yi roƙo da naciya ga Yahweh a wancan lokaci, cewa,24'Ya Ubangiji Yahweh, ka fãra nuna wa bawanka girmanka da ƙarfin hannunka; gama wanne allah ne a sama ko a duniya da zai yi irin ayyukan da ka aiwatar, kuma dai-dai irin manyan ayyukan?25Ka barni in ƙetare, na roƙe ka, in kuma kalli ƙasar mai kyau da ke ƙetaren Yodan, wannan ƙasar tudu mai kyau, da kuma Lebanon.'26Amma Yahweh ya yi fushi da ni saboda ku; bai saurare ni ba. Yahweh ya ce mani, 'Bari wannan ya ishe ka - kada ka ƙara yi mani magana game da wannan al'amari:27ka hau zuwa ƙwalƙolin Fisga ka kuma ɗaga idanunka zuwa yamma, zuwa arewa, zuwa kudu, da zuwa gabas; ka duba da idanunka, domin ba zaka je ƙetaren Yodan ba.28A maimakon haka, ka umarci Yoshuwa ya ƙarfafa ka kuma ƙarfafashi, gama zai shiga gaban waɗannan mutane ya ƙetare, zai kuma sa su gãji ƙasar da za ka gani.'29Sai muka tsaya a kwari daura da Bet Feyo.
Musa ya cigaba da tuna wa mutuanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ya wuce.
Waɗannan ne sunayyen Sarakuna. Dubi yadda kun fasara waɗannan a cikin 1:3.
Waɗannan ne sunayyen birane. Dubi yadda kun fasara waɗannan a cikin 1:3.
Yahweh na magana da Musa kaman Musa ne yan Isra'ilan, don haka urmunin "kada ko ji tsoro"
Anan kalmomin "shi" da "sa" na nufin Og.
Yahweh na maganan abin da zai yi kamar ya riga ya yi.
Kalmar "sa" ƙarin magana ne na "mutanensa." AT: "Za ku hallaka Og da mutanensa kamar yadda kun yi a Sihon"
AT: "kuma Yahweh ya sa dukka mutanen Og a karkashin ikonmu"
Wannan ƙarin magana ne da ana nanata cewa yan Isra'ila ba su bar kowa ya rayu ba. AT: "dukka mutanensa sun muttu"
Wannan magana ne da an nanata cewa sun ƙarbi dukka birane sittin. AT: "mun ƙarbi kowane biranen"
Wannan sunan yankin sakanin Bashan.
Musa ya cigaba da tuna wa mutuanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ya wuce.
"Waɗannan ne dukku birnin da ake karewa da"
"da kari" ko "ba tare da"
Wannan ne sunan sarki. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 1:3.
Wannan sunan gari ne. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 1:3.
"kashe dukka mutanen da sun zauna a kowane gari"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Anan "daga hannun" na nufin "daga ikon." AT: "daga ikon sarakuna biyu" ko "daga sarakuna biyun"
"mutanen Amoriyawa ... asar Bashan ... garin Edrei ... Sarkin Og" Fasara waɗannan kamar yadda kun yi a cikin 1:3.
Wannan na nufin ƙasar hayen Rafin Urdun, zuwa yammancin Isra'ila. Musa na yammancin Rafin Urduna loƙacin da ya faɗa wannan. AT: "yammancin Rafin Urdun."Fasara wannan kamar yadda yake a cikin 1:1.
Fasara waɗannan kalmomin kamar yadda kun yi a cikin 2:24.
Waɗannan dukka sunayyen dutsen da na iyakan arewan Bashan.
Wannan tudu ne, shimfiɗeɗɗen ƙasa a sakanin rafin Arnon da dutsen Gilead.
Wannan wata sunan garin ne kusa da Edrei.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Wannan ne tushen bayani game da Sarki Og.
Fasara wannan kaman yadda kun yi a cikin 2:10.
"Ba da hankali ga muhimmin abin da zan gaya maku."
Marubucin ya yi amfani da tambaya don ya tuna wa mutanen Isra'ila cewa za su iya zuwa Rabbah su gan yadda Og ya yi girma. AT: 1) "a Rabbah ne, ... zauna." ko 2) " Rabbah ne, ... zauna."
kãmu mita arba'in da shida ne.
"bisa kubit da awancin mutanen na amfani"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
Fasara wannan a kamar yadda yake a cikin 2:36.
Fasara wannan a kamar yadda yake a cikin 2:24.
Fasara wannan a kamar yadda yake a cikin 3:3.
Marubucin ya fara ba da tushen bayani game da ƙasar da mutanen sun karba. Idan harshenku na da wata hanyar nuna cewa abin da ke biye shi ne tushen bayani, ku yi amfani da shi anan.
Fasara wannan a kamar yadda yake a cikin2:10.
Wannan ya cigaba da tushen bayani game da ƙasr da mutanen Isra'ila suka karba. (Dubi: 3:12)
Wannan sunan mutum ne.
Waɗannan taron mutane ne da suka yi zama a yamman Bashan.
Masu fasara na iya yin bayani da cewa: "Sunan 'Havvot Jair" na nufin 'kauyukan Jair" ko "madawamin Jair."
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
A nan "Na" na nufin Musa.
Macir ne ɗan Manasseh. Ya mutu kafin Musa ya bada wannan ƙasan. Sunan ƙarin magana ne na zuriyar mutumin. AT: "ga zuriyar Macir"
Wannan ne sunan kwarin Rafin Arnon. Ya yi iyaka a sakanin Moab da Amorites. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 2:24.
Wannan ne sunan rafin da ya yi iyaka a sakanin ƙasara Sihon da ƙasar Ammoniyawa. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 2:36.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"Iyaka Reubenite ta yamma da ƙasar Gadite na"
"Tekun Chinneret." Wannan wuri ɗaya ne da "Tekun Galilli" ko tabkin Gennesaret."
Wannan ne wata sunan dutse a gefen kudun dutsen Abarim.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Musa ya tuna wa kabilan Reuben, kabilan Gad, da kuma rabin kabilan Manasseh cewa ɗole ne su taimake sauran Isra'ilan cin nasara a ƙasar da Allah ya yi masu alkawari.
"za ku ɗauki takobinku ku kuma haye Rafin Urdun"
"yan'uwanku Isra'ila"
Musa ya cigaba da magana da kabilun Reuben da Gad da kuma rabin kabilan Manasseh.
Marubucin ya yi magana kaman hutawa abin da ana iya gani kuma ana iya ba da shi kaman kyauta. Kalmar "hutu" ƙarin magana na rayuwar salama wanda babu yaki. AT: "Yahweh ya bar yan'uwanku sun huta" ko "Yahweh ya bar yan'uwanku sun daina yin faɗan yake-yake sun kuma yi zaman salama"
Wannan na nufin ƙasar a hayen Rafin Urdun, zuwa yammancin Isra'ila. Musa na yammancin Rafin Urduna loƙacin da ya faɗa wannan. AT: "yammancin Rafin Urdun."Fasara wannan kamar yadda yake a cikin 1:1.
Musa na nanata cewa ɗole ne sauran kabilun su mallaki ƙasarsu kafin Yahweh ya yarda wa waɗannan kabilu guda ukun su mallaki ƙasar su. "shi ne kadai za ku kuma."
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
A nan "idannu" na nufin Joshua. AT: "Kun gani"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
A nan "Na" na nufin Musa. Wannan na nufin cewa ya roki Allah da gaskiya da kuma ladabi.
A nan "bawanka" wata hanya mai kyau ne na magana da wani mai babban iko. AT: "don ya nuna ma ni, bawanka,"
A nan kalmar "hannu" na nufin shugabanci ko iko. AT: "ikonka"
Musa ya yi amfani da tambaya domin ya nanata cewa Yahweh ne Allah kadai ke da ikon yin ayukan da ya yi. AT: "gama babu wani allah ... aikata."
Waɗannan biyun na nufin "ko ina."
"yammancin Rafin Urdun." Musa na yammancin Rafin Urdun a Moab a loƙacin da ya yi waɗannan maganganun da Yahweh.
Musa ya cigaba da gaya wa mutane game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
Wannan na nufin loƙacin da Musa ya yi rashin biyayya da abin da Yahweh ya ce masa ya yi domin Musa na fushi da mutanen Isra'ila. Fasara wannan kamar yadda yake a cikin 1:37.
Fasara wannan kamar yadda yake a cikin 3:17.
Kalmomin "ɗaga idannunku" ƙarin magana ne da na nufin duba. AT: "Duba"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa.
Wannan ne sunan wata gari a cikin Moab kusa da Dutsen Pisgah.
1Yanzu, Isra'ila, ku saurari shari'o'i da dokoki da nake gab da koya maku, ku aikata su; saboda ku rayu ku kuma shiga ku kuma mallaki ƙasar da Yahweh, Allah na ubanninku, ya ke baku.2Ba zaku ƙara bisa ga maganganun dana umarce ku ba, ko kuma ku rage su, saboda ku kiyaye dokokin Yahweh Allahnku wanda na ke gab da umartar ku.3Idanunku sun ga abin da Yahweh ya yi saboda Ba'al Feyo; domin dukkan mutanen da suka bi Ba'al na Feyo; Yahweh Allahnku ya lalatar da su a tsakaninku.4Amma ku da kuka manne wa Yahweh Allahnku kuna raye a yau, kowannen ku.5Duba, na koya maku shari'u da dokoki, kamar yadda Yahweh Allahna ya umarce ni, cewa kuyi haka a tsakiyar ƙasa inda kuke tafiya ciki domin ku mallake ta.6Saboda haka ku kiyaye su ku kuma aikata su; domin wannan shi ne hikimarku da fahimtarku a idanun mutanen da zasu ji dukkan waɗannan farillai su kuma ce, 'Tabbas wannan babbar al'umma mutane ne masu hikima da fahimta.'7Gama wacce al'umma ce da suke da allah da ke kusa da su sosai, kamar yadda Yahweh Allahnmu ya ke a duk sa'ad da muka yi kira a gare shi?8Wacce babbar al'umma ce da ke nan da take da shari'u da dokoki masu adalci sosai kamar dukkan shari'a da nake shiryawa a gaban ku a yau?9Kawai dai ku lura ku kuma jagoranci kanku a hankali, domin kada ku manta da abin da idanunku suka gani, saboda kada su bar zukatanku domin dukkan kwanakin rayuwarku. A maimakon haka, ku sanar da su ga 'ya'yanku da 'ya'yan 'ya'yanku.10A ranar da kuka tsaya a gaban Yahweh Allahnku a Horeb, sa'ad da Yahweh ya ce mani, 'Ka tattara mani mutanen, zan kuma sa su su ji maganganuna, domin su koyi jin tsorona dukkan kwanakin da suke raye a duniya, domin kuma su koyawa 'ya'yansu.'11Kuka zo kusa kuka tsaya a gindin dutsen. Dutsen na ƙonewa da wuta har tsakiyar sama, tare da duhu, girgije, da duhu mai kauri.12Yahweh ya yi magana daku daga cikin tsakiyar wuta; kuka ji muryar tare da maganganunta, amma baku ga wata siffa ba; murya kaɗai kuka ji.13Ya furta maku alƙawarinsa da ya umarceku ku aikata, Dokoki goma. Ya rubuta su a allunan duwatsu biyu.14Yahweh ya dokace ni a wannan lokaci da in koya maku farillai da shari'u, saboda ku aikata su a cikin ƙasar da kuke ƙetarawa ku ɗauki mallaka.15Saboda haka ku yi hankali da kanku - domin baku ga wata siffa ba a ranar da Yahweh ya yi magana daku a Horeb daga tsakiyar wuta -16domin kada ku lalata kanku ta wurin yin sassaƙaƙƙen siffa bisa ga siffar wani abu, a cikin kamannin namiji ko mace,17a cikin kamannin kowacce irin dabba a duniya, kamannin kowanne irin tsuntsu mai fukafukai da ke shawagi a sammai,18kamannin kowanne irin abu da ke rarrafe a bisa ƙasa, ko kamannin kowanne irin kifi da ke cikin ruwa a ƙarƙashin duniya.19Ba zaku ɗaga idanunku zuwa sammai ba ku dubi rana, wata, ko taurari ba - dukkan rundunar sammai - kuma ku janye zuwa yi masu sujada ku kuma girmama su - waɗannan abubuwa waɗanda Yahweh Allahnku ya bada kaso ga dukkan mutanen ƙarƙashin sararin sama baki ɗaya.20Amma Yahweh ya ɗauko ku ya kawo ku kuma daga tanderun ƙarfe, daga Masar, ku zama a gare shi mutanen gãdonsa, kamar yadda kuke a yau.21Yahweh yaji haushina saboda ku; ya yi rantsuwa cewa bazan ƙetare Yodan ba, da cewa kada in tafi cikin wannan ƙasa mai kyau, ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke bayarwa a gare ku a matsayin gãdo.22A maimako, tilas in mutu a wannan ƙasa; tilas ba zan tafi ƙetaren Yodan ba; amma ku zaku ƙetare ku kuma mallaki ƙasar mai kyau.23Ku lura da kanku, domin kada ku manta da alƙawarin Yahweh Allahnku, wanda ya yi tare daku, ku kuma yi wa kanku sassaƙaƙƙen siffa a cikin siffar wani abu wanda Yahweh Allahnku ya hanaku ku yi.24Gama Yahweh Allahnku wuta ne mai lanƙwamewa, Allah ne mai kishi.25Sa'ad da kuka haifi 'ya'ya da 'ya'yan 'ya'ya, sa'ad da kuma kuka kasance a ƙasar na dogon lokaci, idan kuma kuka lalata kanku kuka kuma yi wa kanku sassaƙaƙƙen siffa bisa ga siffar kowanne abu, kuka kuma aikata abin da ke na mugunta a idanun Yahweh Allahnku, domin ku tunzura shi zuwa fushi -26na kira sama da duniya suyi shaida gãba da ku a yau cewa ba da daɗewa ba zaku lalace daga ƙasar da kuke ƙetare Yodan domin ku mallaka; ba zaku tsawonta kwanakinku ba a cikin ta, amma ɗungum zaku rushe.27Yahweh zai warwatsa ku cikin mutane, kuma zaku zama 'yan kaɗan a cikin al'ummai, inda Yahweh zai aika da ku.28A can zaku yi bautar wasu alloli, ayyukan hannuwan mutane, katako da dutse, waɗanda basu gani, ji, ci, ko sunsunawa.29Amma daga can zaku biɗi Yahweh Allahnku, kuma zaku same shi, sa'ad da kuka neme shi da dukkan zuciyarku da dukkan ranku.30Sa'ad da kuke cikin ƙunci, sa'ad da kuma dukkan waɗannan abubuwa suka zo kanku, cikin waɗannan kwanakin ƙarshe zaku dawo ga Yahweh Allahnku kuma ku saurari muryarsa.31Gama Yahweh Allahnku Allah ne cike da jinƙai; ba zai gaza maku ba ko ya rusa ku, ko kuwa ya manta da alƙawarin ubanninku wanda ya rantse masu.32Ku yi tambaya yanzu game da kwanakin da suka wuce, waɗanda suke kafin lokacinku, tun ranar da Allah ya halitta mutum a duniya, ku yi tambaya daga ƙarshen sama zuwa ɗaya ƙarshen sama, ko an taɓa yin wani abu babba kamar wannan, ko an taɓa jin wani abu kamar wannan?33Ko an taɓa yin wasu mutane da suka ji muryar Allah na magana daga cikin wuta, kamar yadda kuka ji, kuka kuma rayu?34Ko kuwa Allah ya taɓa ɗaukar wani mataki yaje ya ɗaukarwa kansa al'umma daga cikin wata al'ummar, ta wurin gwaje-gwaje, ta wurin alamu, da ta wurin al'ajibai, da ta wurin yaƙi, da ta wurin hannu mai ƙarfi, da ta wurin miƙaƙƙen damtse, da ta wurin babbar razana, kamar dukkan abin da Yahweh Allahnku ya yi domin ku a Masar a gaban idanunku?35A gare ku aka nuna waɗannan abubuwa, saboda ku sani cewa Yahweh shi ne Allah, kuma da cewa babu wani baya gare shi.36Daga sama ya sa kuka ji muryarsa, saboda ya umarce ku; a duniya ya sa kuka ga babbar wutarsa; kuka ji maganganunsa daga cikin tsakiyar wutar.37Saboda yana ƙaunar ubanninku, ya zaɓi zuriyarsu bayansu, ya kuma fito daku daga Masar tare da bayyanuwarsa, tare da babban ikonsa;38domin ya kore daga gabanku al'ummai da suka fi ku girma da ƙarfi, saboda ya kawo ku ciki, saboda ya baku ƙasarsu a matsayin gãdo, kamar a yau.39Saboda haka ku sani a yau, ku kuma ajiye shi a zukatanku, cewa Yahweh shi ne Allah a sama can da duniya a ƙarƙashi; babu wani kuma.40Zaku kiyaye farillansa da dokokinsa waɗanda ya dokace ku a yau, domin lafiya ta tafi tare da ku da 'ya'yanku a bayanku, saboda kuma ku tsawonta kwanakinku a cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku har abada."41Daganan Musa ya zaɓi birane uku daga sashen gabas da Yodan,42saboda wani yana iya gudu zuwa ɗaya daga cikinsu idan ya kashe wani taliki cikin kuskure, wanda ba maƙiyinsa bane a dã. Ta wurin tserewa zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane, zai iya tsira.43Su ne: Bezar a jeji, ƙasar sarari, domin Rubenawa; Ramot a Giliyad, domin Gadawa; da Golan a Bashan, domin Manasawa.44Wannan ita ce shari'ar da Musa yasa a gaban mutanen Isra'ila;45waɗannan ne dokokin alƙawari, shari'u, da sauran dokoki daya faɗi ga mutanen Isra'ila sa'ad da suka fito daga Masar,46sa'ad da suke a gabas da Yodan, a kwari daura da Bet Feyo, a ƙasar Sihon, sarkin Amoriyawa, wanda ya zauna a Heshbon, wanda Musa da mutanen Isra'ila suka kayar sa'ad da suka fito daga Masar.47Suka ɗauki ƙasarsa a matsayin mallaka, da ƙasar Og sarkin Bashan - waɗannan, sarakuna biyu na Amoriyawa, waɗanda ke ƙetaren Yodan zuwa gabas.48Wannan gunduma ta tafi daga Arowa, a gaɓas Kwarin Arnon, zuwa Dutsen Sihiyona (ko Dutsen Hamon),49ya kuma haɗa da dukkan sararin kwarin Kogin Yodan, maso gabas a ƙetaren Yodan, zuwa Tekun Araba, zuwa gangaren Dutsen Fisga.
Musa na gaya wa mutanen Isra'ila abin da Allah na so su yi.
"kum yi biyayya da su"
Yahweh ba ya son mutanensa su yi sabon dokoki, ko su ƙyale wanda ya riga ya basu.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
A nan "idannu" na nufin mutanen Isra'ila. AT: "Kun gani"
AT: "saboda zunuban da kuka yi a Baal Peor"
Fasara wannan kamar yadda kun yi a cikin 3:28.
Musa na magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya.
Marubucin na magana kamar gaskanta da Yahweh da kuma yin biyayya da shi na nan kamar manne wa mutum.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"sa hankali"
"domin ku yi biyayya da su a lokacin da kun yi zama a kasan"
Wadannan jimlolin a takaice na nufin abu daya kuma na nanata cewa ya kamata su yi biyayya da su. AT: "yi masu biyayya da kyau"
Ana iya fasara jam'in "hikima" da "fahimta" kamar jimla, kuma "idanu" na nufin yadda mutane na yin shariya ko kimanta darajan abu. AT: "wannan ne abin da zai nuna wa mutanen cewa ku na da hikima kuma kun fahimci abin da na da amfani" Dubu: and
Kalmar "al'umma" karin magana ne na mutanen wancan al'umma. AT: "mutanen wannan babbar al'umman na da hikima da fahimta"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Gama babu wani babban ƙasa ... shi. Babu wani babban ƙasa ... yau."
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Musa ya yi magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne, don haka duk misalen "ku" da "kanku" da kuma umurnen "ba da hankali," "lura," da "sa sananne" ɗaya ne.
Ba da hankali ku kuma tabatar cewa kun tuna da waɗannan abubuwan kullum"
Waddanan jimlolin na nufin abu daya ne kuma na nanata cewa dole ne mutanen Isra'ila su tuna abin da sun gani.
A nan "idannu" karin magana ne na mutum. AT: "kun gani"
"kowa mutanen tare ka kuma kawo mani su"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da tarihunsu.
Wannan karin magana ne. "Zuciyar" na nufin "sakiyar" ko "cikin sashin," da "sama" na nufin sarari. AT: "da wutan da ya tafi sama"
A nan "bakin duhu" ya kwatanta girgije. AT: "da duhu, girgije"
Wata ma'ana mai yiwuwa ne "girgijen nauyi"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"Yahweh ya ce"
A nan "ku" na nufin 'yan Isra'ila wanda suke Dutsen Horeb.
"bayan kun haye zuwa Rafin Urdun kun kuma karbi kasan"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
AT:1) "don haka ku yi hankali da yadda ku na aikata" ko 2) "Kare zuciyarku sosai."
"kada ku yi abin da ba daidai ba"
"jan jiki a kasa"
Musa ya yi magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne, don duk misalen "daga", "gani," da "nise" ɗaya ne.
AT: Kada ... kuma kada ku bar wani ya sa ku ku so ku yin bauta" ko "Kada ... kuma kada ku yarda kanku ya bautata"
"komai da ku na iya gani a sarari." Wannan wata hanya ne na kiran rana, wata, da kuma tauraro.
Wannan ƙarin magana ne. Musa ya yi maganar tauraro kamar sun zama ƙaramin abu ne kamar abinci da Yahweh ke rabawa na kuma ba wa taron mutane. AT: "wanda Yahweh Allahnku ya sa a can don ya taimake dukkan taron mutane"
Musa ya yi maganan Egypt da aikin wuya da 'yan Isra'ilan sun yi a wurin kamar tanda ne da ake zafafa kuma 'yan Isra'ilan ne karfen. AT: "fitar da ku daga ƙasar da mutane sun sa ku yin aiki mai wuya"
Wannan ƙarin magana ne da ana iya fasara kamar "mutanen da sun zama nashi kadai."
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'la.
Wannan na nufin lokacin da Musa ya yi rashin biyayya da abin da Yahweh ya gaya ma shi ya yi domin Musa ya yi fushi da mutanen Isra'ila. Ana iya sa a bayyane cikakken ma'anar wannan magana. Fasara wannan kamar yadda kun yi a cikin 1:37.
Musa na magana da 'yan Isra'ila kamar su mutum daya ne.
"ba da hankali sosai"
Musa na magana da yan Isra'ila kaman sun mutum ɗaya ne, don haka duk misalan "ku" ɗaya ne.
Musa ya kwatanta yadda Yahweh na yi a loƙacin da ya na fushi da yadda wuta ke hallakar da abubuwa. AT: "Yahweh Allahnku zai hukunta ku sosai ya kuma hallakar da ku kaman yadda wuta na yi domin ba ya so ku bauta wa wasu alloli"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Kalmomi "ku" da "na ku" daya ne.
zaman mahaifin, ko zama kakan
"idan kun yi abin da ba daidai ba."Kalmomi irin wannan sun bayyane a cikin 4:15.
Wannan karin magana ne. AT: "kun kuma sa Yahweh Allahnku fushi ta wurin yin abin da ya ce mugu ne"
AT: 1) Musa na kiran dukkan waddanda na zama a sama da kasa su zama shaidun abubuwan da ya faɗa ko 2) Musa na magana da sama da kasa kamar su mutane ne, ya na kuma gaya masu su zama shaidun abin da zai fada.
tsawon lokaci karin magana ne na tsawon rai. AT: "ba za ku iya rayu a tsawon lokaci ba"
Kamar yadda ya ke a 4:27, ba kowane Isra'ila ne za a kashe ba. A nan "hallaka gabadaya" karin magana ne kuma na nanata cewa Isra'ilawa dayawa za su mutu. AT: "amma Yahweh zai hallakar da yawancinku"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Musa ya na magana kaman mutanen iri ne da Yahweh zai baza a fili. AT: "Yahweh zai aike ku zuwa wurare dabam dabamya kuma tilasa maku ku zauna a wurin"
"zai aike ku" ko "zai sa makiyan ku su ɗauke ku"
A nan "hannuwan mutane" na nufin mutanen da kansu, da "ayukan ... itace da dutse" wa gumakai da sun halitta. AT: " gumakan itace da dutse da mutane sun yi"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila. Ya yi magana kamar su mutum ɗaya ne, don hakaon duk misalan "ku" da umurnin "roka yanzu" ɗaya ne.
"Amma idan ku na wancan sauran ƙasashen"
"idan kun yi kokarin neman shi sosai" ko "idan kun yi kokarin sanin shi"
Karin maganan "da dukkan ... zuciya" na nufin "gabaɗaya" da "da dukka ... rai" na nufin "da dukka ... rai." AT: "da dukkan ranku" ko "da dukkan karfinku"
"ya faru a da"
"bayan haka" ko "sai"
A nan "ji" na nufin ji da biyayya, kuma "muryarsa" na nufin Yahweh da abin da ya ce. AT: "yi biyayya da abin da ya ce"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kamar su mutum ɗaya ne. Don duk misalan "ku" da umurnin "roka yanzu" ɗaya ne.
A nan an tuna wa mutanen Isra'ila game da yadda Yahweh ya yi magana da su a hanyar ban mamaki a zamanin da ta wuce. AT: "Babu mutane kamar ku da sun ji Allah na magana daga tsakiyar wuta har sun rayu."
Kalmar "murya" ƙarin magana ne na Allah, wanda na magana. AT: "ji muryan Allah sa'adda ya yi magana"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
A nan "babban hannu" da "mikakiyar hannu" ƙarin magana ne na ikon Yahweh. AT: "da kuma nuna babban ikonsa"
A nan "idannu" na nufin dukkan mutum. AT: "a gaban ku"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kamar su mutum ɗaya ne.
AT: "Yahweh ya nuna maka waɗannan abubwa"
"ya tabatar cewa ka ji ... ya tabatar cewa gani"
Musa na magana kaman mutanen da ya yake magana da su, su ne mutanen da ya riga ya yi magana da su a Dutsen Sina a shekaru dayawa da ta wuce. Mutanen Dutsen Sina ne ubannen mutanen da yake waɗannan kalmomin. AT: "sa ubannenku ... ubannenku su ji"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kamar su mutum ɗaya ne.
Wannan na nufin Ibrahim, Ishaku, Yakubu, da 'ya'yan Yakubu.
"da babban ikon da ke zuwa daga kasancewarsa" ko "da babban ikonsa"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kamar su mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "tuna da shi"
Jimloli biyun nan "a sama" da "a kasa" na nuna tsanani kuma na nufin " ko ina." AT: "akan komai"
Tsawon kwanaki ƙarin magana ne na tsawon rai. AT: "iya zama da tsawon loƙaci." Fasara waɗannan kalmomi kamar yadda kun yi a cikin 4:25.
Maganar Musa da ya fara a cikin 1:5 ya kare, marubucin ya kuma cigaba da bayanin da ya kare a 1:5.
Waɗannan sunayyen birane ne.
Wannan na nufin dokokin da Musa zai ba da a cikin cikin ayoyin da ke biye.
Wannan ne suna wata gari a cikin Moab kusa da Dutsen Pisgah. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 3:28.
"Sarki Sihon ... mutanen Amoriyawa ... garin Heshbon. " Fasara waɗannan kamar yadda kun yi a cikin 1:3.
ƙasar sarki Sihon
Fasara wannan kamar yadda kun yi a cikin 1:3
Wannan na nufin ƙasar hayen Rafin Urdun, zuwa yammancin Isra'ila. Musa na yammancin Rafin Urduna loƙacin da ya faɗa wannan. AT:"daga gefen Rafin Urdun zuwa gabas ... gabas daga gefen Rafin Urdun"
Wannan ne sunan birni. Fasara wannan kamar yadda kun yi a cikin 2:36.
Wannan sunan wuri ne. Fasara wannan kamar yadda kun yi a cikin 2:24.
Waɗannan sunayyen duwatsu ne. Fasara wannan kamar yadda kun yi a cikin 3:8.
Fasara wannan kamar yadda kun yi a cikin 3:17.
1Musa ya yi kira ga dukkan Isra'ila ya ce masu, "Ku saurara, Isra'ila, ga farillai da dokoki da zan faɗa cikin kunnuwanku a yau, domin ku koye su ku kuma kiyaye su.2Yahweh Allahnmu ya yi alƙawari tare da mu a Horeb.3Yahweh bai yi wannan alƙawari tare da kakanninmu ba, amma tare da mu, dukkan mu da muke a raye a nan a yau.4Yahweh ya yi magana daku fuska da fuska a dutse daga tsakiyar wuta5(na tsaya tsakanin Yahweh daku a wancan lokaci, in bayyana maku maganarsa; domin kuna jin tsoro saboda wutar, kuma baku hau zuwa tsaunin ba). Yahweh ya ce,6'Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito daku daga ƙasar Masar, daga gidan bauta.7Ba za ku yi wasu alloli ba a gabana.8Ba za kuyi wa kanku sassaƙaƙƙen siffa ba ko kamannin wani irin abu da ke sama can, ko da ke a duniya a ƙasa, ko da ke a cikin ruwa a ƙarƙashi.9Ba zaku russuna masu ba ko ku bauta masu, domin Ni, Yahweh Allahnku, ni Allah ne mai kishi. Ina hukunta muguntar kakanni ta wurin sauko da hukunci bisa 'ya'yan, har zuwa tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suka ƙi ni,10da nuna alƙawarin aminci ga dubbai, ga waɗanda ke ƙaunata da kiyaye dokokina.11Ba zaku ɗauki sunan Yahweh Allahnku ba a banza, gama Yahweh ba zai riƙe shi marar laifi ba shi wanda ya ɗauki sunansa a banza.12Ka lura da ranar Asabaci ka kiyaye ta da tsarki, kamar yadda Yahweh Allahnka ya dokace ka.13Gama cikin kwana shida zaka yi aikin ƙarfi kayi kuma dukkan ayyuka;14amma rana ta bakwai Asabaci ce ga Yahweh Allahnka. A cikin ta ba za ka yi wani aiki ba - ban da kai, ko ɗanka, ko ɗiyarka, ko bawanka, ko baiwarka, ko san ka, ko jakinka, ko wani daga cikin garken dabbobinka, ko wani baƙo daga cikin ƙofofinka. Wannan kuwa haka ne domin bawanka da baiwarka su huta kamar yadda za ka huta.15Za ka tuna da cewa kaima bawa ne a ƙasar Masar, kuma Yahweh Allahnka ya fito da kai daga can da hannu mai ƙarfi da miƙaƙƙen damtse. Saboda haka Yahweh Allahnka ya dokace ka da ka kiyaye ranar Asabaci.16Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kamar yadda Yahweh Allahnka ya dokace ka kayi, domin ka zauna na dogon lokaci a cikin ƙasar da Yahweh Allahnka ya ke baka, domin kuma ya kasance lafiya tare da kai.17Ba za kayi kisa ba.18Ba zaka aikata zina ba.19Ba zaka yi sata ba.20Ba zaka bada shaidar zur ba gãba da maƙwabcinka.21Ba zaka yi ƙyashin matar maƙwabcinka ba, ba zaka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka ba, ko gonarsa, ko bawansa, ko baiwarsa, ko sansa, ko jakinsa, ko wani abu da ke na maƙwabcinka.'22Waɗannan maganganu Yahweh ya faɗi da babbar murya ga dukkan taronku a bisa dutse daga tsakiyar wuta, daga gizagizai, daga kuma duhu mai kauri; baiyi ƙarin wasu maganganu ba. Ya rubuta su bisa allunan dutse ya kuma bani su.23Sai ya kasance, da kuka ji muryar daga tsakiyar duhu, yayin da dutsen ke ƙonewa, sai kuka zo kusa da ni - dukkan dattawanku da shugabannin kabilunku.24Kuka ce, 'Duba, Yahweh Allahnmu ya nuna mana ɗaukakarsa da girmansa, kuma mun ji muryarsa daga tsakiyar wuta; mun gani a yau cewa sa'ad da Yahweh ya yi magana da mutane, za su iya rayuwa.25Amma me yasa zamu mutu? gama wannan babbar wuta zata cinye mu; idan muka ƙara jin muryar Yahweh Allahnmu, zamu mutu.26Gama banda mu wane ne a cikin nama da jini, ya taɓa jin muryar Allah mai rai daga tsakiyar wuta ya kuma rayu, kamar yadda muka yi?27Game da kai, ka tafi ka saurari dukkan abin da Yahweh Allahnmu ya ce; ka maimaita mana dukkan abin da Yahweh Allahnmu ya ce maka; zamu saurara kuma mu yi biyayya.'28Yahweh yaji maganganunku sa'ad da kuka yi zance da ni. Ya ce mani, 'Na ji maganganun waɗannan mutane, abin da suka ce maka. Abin da suka ce mai kyau ne.29Oh, ace ma akwai irin wannan zuciyar a cikinsu, cewa zasu girmama ni kuma koyaushe zasu kiyaye dokokina, domin ya tafi lafiya tare da su tare kuma da 'ya'yansu har abada!30Ka je kace masu, "Ku koma rumfunanku."31Amma game da kai, ka tsaya nan gefe na, zan kuma gaya maka dukkan dokokin, farillai, da shari'u da zaka koya masu, saboda su kiyaye su a cikin ƙasar da zan ba su su mallaka.'32Saboda haka, zaku kiyaye, abin da Yahweh Allahnku ya dokace ku; ba zaku kauce ba zuwa hannun dama ko hagu.33Zaku yi tafiya cikin dukkan hanyoyi da Yahweh Allahnku ya dokace ku, domin ku rayu, domin kuma ya tafi lafiya tare da ku, ku kuma tsawonta kwanakinku a cikin ƙasar da zaku mallaka.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Musa ya so kowa a Isra'ila ya ji shi, ya kuma yi biyayya da kalmominsa, amma mai yiwuwa muryarsa bai da ƙarfi sosai da kowa ya ji shi.
A nan "kunnuwa" na nufin dukkan mutum. Wannan magana na nanata cewa mutanen sun san abin da Musa ya faɗa masu, don haka ba za su iya yin zunubi sai su ce ba su san cewa su na yin zunubi ba. AT: "da zan yi maku magana yau"
At: 1) Yahweh bai yi alkawri da waɗanda suke Horeb kadai ba; alkawarin na kuma tare da 'yan Isra'ila a zamanin da ta wuce ko 2) Yahweh bai yi wannan alkawari da kakaninsu masu nisa ba, kamar, Ibrahim, Yakubu, da Ishaku ba; a maimakon haka, wannan alkawarin ya fara da Isra'ila a Horeb.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Yi amfani da ƙarin maganan harshenku a mutane biyu wanda suke kusa da juna, su na kuma kallon juna a loƙacin da suke magana.
"Akan Dutse"
Musa na nufin abin da ya faru a shekaru arba'in da ta wuce.
A nan "gidan bauta" na nufin Masar inda mutanen Isra'ila sun yi bauta. AT: "daga inda kun yi bauta"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da Yahweh ya umurce su. Jimlolon "za ku" da 'ba za ku" umurni ne. Ya na magana da 'yan Isra'ila kamar su mutum ɗaya ne.
"Kada ka bauta wa wasu alloli sai de ni"
AT: "da ke cikin ƙasa a ƙarƙashin kafanka, ko da ke cikin ruwa a ƙarƙashin ƙasa"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"Ba za bauta wa abin da an yi ko kuma aikata yadda sun umurta ba"
"Taba"
Ni ... ina so ka bauta ma ni kadai"
Wasu juyin su na karanta "ga zamani dubu-dubu na waɗanda sun ƙaunace ne." Kalmar "dubu-dubu" ƙarin magana ne na lambar mai yawa. AT: "ga dubu-dubun mutane, ga waɗanda ke kauna na"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"Ba za ka yi amfani da sunan Yahweh"
Fasara wannan kamar yadda yake a cikin 5:9.
"sakaci" ko "da rashin daraja" ko "da nufi mara kyau"
AT: "Yahweh zai gan shi da laifi" ko "Yahweh zai hukunta shi"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"mika shi wa Allah"
"yi dukka ayukanka na kullum"
"A ranan nan kada ka yi"
A nan "kofofi" na nufin birin da kansa. AT: "a cikin al'ummanka" ko "cikin birninka" ko "zama da kai"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana ne. AT:"Dole ne ku tuna"
A nan "hannu mai ƙarfi" da "miƙaƙƙiya hannu" ƙarin magana ne na ikon Yahweh. Fasara wannan kamar yadda yake a cikin 4:34. AT: "ta nuna babban ikonsa"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Fasara wannan kamar yadda yake a cikin 5:9.
"Ba za ku kwana da kowa ba sadai abokin aurenku"
"Ba za ku faɗa karya game da wani ba"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Fasara wannan kamar yadda yake a cikin 5:9.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da Yahweh ya ce.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
Kalmar "murya" ƙarin magana ne na ƙarar muryar ko na mutumin da ke magana. AT: "ji ƙarar muryar" ko "ji Yahweh na magana"
Musa ya cigaba da tuna wa 'yan Isra'ilawa game da abin da sun gaya ma shi.
Sun ji tsoro cewa za su mutu idan Yahweh ya yi magana da su. AT: "Mu na tsoro cewa za mu mutu."
AT: "Babu wasu mutane in ban da mu ... yi."
Wannan ƙarin magana ne na "dukka mutane" ko "dukka rayayyu."
A nan "ni" na nufin Musa.
Idan harshenku na da ƙarin magana da na bayyana babban sha'awan wani abu, za ku iy so ku yi amfani da shi anan. AT: "Zan yi murna idan akwai"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa.
"za ka koya wa mutanen Isra'ila"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Musa ya na ba da umurni wa mutanen Isra'ila.
Wannan na kwatanta mutum mai rashin biyayya ga Allah da mutum mai bijire daga hanya mai kyau. AT: "ba za ku yi ma sa rashin biyayya ba" ko "za ku yi duk abin da ya ce"
Tsawon kwanaki magana ne na tsawon rai. Fasara wannan kaman yadda yake a 4:39. AT: "ku iyarayuwar tsawon loƙaci"
1Yanzu waɗannan ne dokoki, da farillai, da kuma shari'un da Yahweh Allahnku ya dokace ni in koya maku, domin ku kiyaye su a cikin ƙasar da kuke tafiya ƙetaren Yodan ku mallaka;2saboda ku iya girmama Yahweh Allahnku, saboda ku kiyaye dukkan farillansa da dokokinsa waɗanda nake dokatarku a yau - ku, da 'ya'yanku, da 'ya'yan 'ya'yanku, dukkan kwanakin rayuwarku, saboda kwanakinku su yi tsawo.3Saboda haka ku saurare su, Isra'ila, ku kuma kiyaye su, saboda ya tafi lafiya tare daku, saboda ku yi babbar ruɓanɓanya, a cikin ƙasar da ke malalowa da madara da zuma, kamar yadda Yahweh, Allah na ubanninku, ya yi maku alƙawari zai yi.4Ku saurara, Isra'ila:5Yahweh Allahnmu ɗaya ne. Zaku ƙaunaci Yahweh Allahnku tare da dukkan zuciyarku, tare da dukkan ranku, tare kuma da dukkan ƙarfinku.6Maganganun da nake umartarku a yau za su kasance a zukatanku;7da ƙwazo kuma zaku koyar da su ga 'ya'yanku; zaku yi magana game da su sa'ad da kuke zaune cikin gida, sa'ad da kuke tafiya akan hanya, sa'ad da kuke kwance, da sa'ad da kuka tashi.8Za ku ɗaura su a matsayin alama a bisa hannunku, zasu kuma zama kamar 'yan goshi a tsakanin idanunku.9Zaku rubuta su a ginshiƙan gidajenku da ƙofofinku.10Sa'ad da Yahweh Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya yi rantsuwa ga ubanninku, ga Ibrahim, ga Ishaku, ga kuma Yakubu, cewa zai baku, da birane manya-manya kyawawa da baku gina ba,11da gidaje cike da dukkan abubuwa iri-iri masu kyau da baku yi ba, tankunan ruwa da baku gina ba, garkunan inabi da itatuwan zaitun da baku dasa ba, zaku ci ku ƙoshi -12daganan ku lura saboda kada ku manta da Yahweh, wanda ya fito da ku daga ƙasar Masar, daga gidan ƙunci.13Zaku girmama Yahweh Allahnku; shi ne zaku yi wa sujada, kuma zaku yi rantsuwa da sunansa.14Ba zaku bi waɗansu alloli ba, allolin mutanen da suke kewaye daku kakaf -15domin Yahweh Allahnku da ke tsakiyarku Allah ne mai kishi - idan kuka yi, fushin Yahweh Allahnku zai kunnu gãba daku kuma zai hallakar daku daga fuskar duniya.16Ba zaku gwada Yahweh Allahnku ba kamar yadda kuka gwada shi a Massa.17Zaku yi ƙwazo ku kiyaye dokokin Yahweh Allahnku, dokokinsa natsastsu, da farillansa, waɗanda ya dokace ku.18Zaku yi abin da ke dai-dai mai kyau kuma a idanun Yahweh, saboda ya kasance lafiya a gare ku, ku kuma iya zuwa ku mallaki ƙasa mai kyau da Yahweh ya rantse wa ubanninku,19ya kori dukkan maƙiyanku daga gare ku, kamar yadda Yahweh ya faɗa.20Sa'ad da ɗanku ya tambaye ku a lokaci mai zuwa, cewa, 'Waɗanne ne dokokin alƙawari da farillai da sauran dokoki da Yahweh Allahnmu ya umarce ku?21daganan zaku cewa ɗanku, 'Mu bayin Fir'auna ne a Masar; Yahweh ya fito da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi,22ya kuma aiwatar da alamu, da al'ajibai, manya masu tsanani, a bisa Masar, a bisa Fir'auna, a kuma bisa dukkan gidansa, a gaban idanunmu;23ya kuma fito da mu daga wurin, saboda ya kawo mu ciki, ya ba mu ƙasar da ya rantse wa ubanninmu.24Yahweh ya dokace mu da a koyaushe mu kiyaye waɗannan farillai, mu ji tsoron Yahweh Allahnmu domin kyaunmu, domin ya iya kiyaye mu a raye, kamar yadda muke a yau.25Idan muka kiyaye dukkan waɗannan dokoki a gaban Yahweh Allahnmu, kamar yadda ya dokace mu, wannan ne zai zama adalcinmu.'
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila da ya fara a cikin 5:1. Farawa daga aya 2, ya yi magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"yi biyayya ... yi biyayya"
"tafiya zuwa ɗayan gefen Rafin Urdun"
Tsawon kwanaki magana ne na tsawon rai. AT: "Ana iya fasara wannan zuwa "tsawanta kwanakinku" a cikin 4:25. AT: "in iya tsawanta kwanakinku" ko "in iya sa ku yi zama na tsawon loƙaci"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
A nan "saurara" na nufin biyayya, kuma "su" na nufin dokokin Yahweh. AT: "Sauraru dokoki Yahweh, matsyai, da umurnin"
"yi biyayya da su"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "ƙasar da madara mai yawa da zuma ke zuba" ko "ƙasar da na da kyau wa tumaki da noma"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Irsa'ilawan mutum ɗaya ne.
"Allahnmu Yahweh ne Allah ɗaya kadai"
Waɗannan jimlolon a haɗe na nanata cewa ya kamata mutum ya ƙaunace Allah gabaɗaya ya kuma yi mika kai.
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Irsa'ilawan mutum ɗaya ne.
Musa na faɗa dokokin Allah wa mutanen Isra'ila.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "ɗole ne ku tuna kullum"
"Na umurce ka ka koyar da ƙwazo ... Na umarce ku ku yi magana." Ya kamata mai karantawa ya fahimci waɗannan kaman dokoki.
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
Wannan magana ne na "rubuta waɗannan kalmomin a takarda, sa takardar a yar jaka, ka kuma ɗaura." Wannan ƙarin magana na iya zama "yi biyayya da waɗannan kalmomin don ya zama kaman su na nan a wurin." AT: "ɗaura waɗannan kalmomin"
"kamar wani abu don ya sa ka tuna da dokoki na"
Wannan ƙarin magana ne na "rubuta waɗannan kalmomin a takarda, sa takardar a yar jaka, ka kuma ɗaura yar jakan a kanka." Wannan ƙarin maganar na iya zama "yi biyayya da waɗannan kalmomin don ya zama kaman su na nan a wurin." AT: "kalmomi na za su zama kamar alama a goshi"
Adon da mutum na sa a gaban goshi
Wannan doka ne.
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
Dukka waɗannan biranen za su zama na mutanen Isra'ila a loƙacin da sun ci nasara da mutanen Kenan.
A nan "gidan bawantaka" na nufin Egypt, wurin da mutanen Isra'ila sun yi bauta. AT: "daga wurin da kuka yi bauta"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
"Yahweh Allahnku ne kuma babu wanin da za ku daraja; shi ne kadai za ku yi wa sujada, kuma ta sunansa ne kadai za ka rantse." Harshenku na iya samin wata hanyar nanata cewa Yahweh na faɗa wa 'yan Isra'ilan cewa kada su yi sujada ko bauta wani allah.
Rantsewa da sunan Yahweh na nufin sa Yahweh ya zama tushe ko ikon da aka yi rantsuwan. Maganar "sunansa" na nufin Yahweh da kansa. AT: "za ka rantse ka kuma roke Yahweh ya tabbatar da shi" ko "idan ka yi rantsuwa, za ka faɗa sunansa"
"wanda su na zama a cikinku"
Musa ya kwatanta fushin Allah da wanin da ke motsa wuta don ya hallakar da abubuwa. AT: "Hura wuta ƙarin magana ne na jin fushi. AT: "Yahweh Allahnku zai hura fushinsa" ko "Yahweh Allahku zai yi fushi sosai"
"hallakar da ku don kar komai ya rage maku"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
A nan "gwada" na nufin tsokane Yahweh da kuma tilasa shi ya tabbatar da kansa.
Wannan sunan wuri ne a jeji. Mai fasaran na iya kara bayani da ke cewa: "sunan 'Massa' na nufin "jarabtan."
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin maganan doka ne da kuma albarka. Idan Isra'ilawan sun yi biyayya da Yahweh, za su karbi albarku daga Yahweh. AT: "Yi abin da Yahweh ya ce shi ne daidai da kuma kyau"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
Wannan tambaya ƙarin magana ne. AT: "Menene alkawarin ya bayar ... umurni na nufi ma ka" ko "Don me za ka yi biyayya da dokokin alkawarin ... umurce ka"
Wannan na nufin 'ya'yan manyan mutanen Isra'ila wanda Musa ya ke faɗan kalmomin Yahweh.
A nan "ƙarfin hannu" na nufin ikon Yahweh. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 4:34. AT: "da ƙarfin ikonsa"
A nan "gidansa" na nufin mutanen Yahweh. AT: "da kuma dukka mutanensa"
A nan kalmar "idannu" na nufin dukkan mutum. AT: "inda za mu iya ganinsu"
AT: "iya kawo mu cikin Kanan"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne. Ya gaya masu abin da za su gaya wa 'ya'yansu game da dokokin Yahweh.
"a hallarar Yahweh" ko "inda Yahweh zai iya ganin mu"
biyayya"
AT: "zai ɗauke mu da adalci"
1Lokacin da Yahweh Allahnku ya kawo ku zuwa ƙasar da kuke shiga domin ku mallake ta, za ya kori al'ummai masu yawa - su Hittiyawa, da Girgashawa da Amoriyawa da Kan'aniyawa, da Feriziyawa, da Hibiyawa da kuma Yebusawa - al'ummai guda bakwai masu girma da ƙarfi fiye da ku.2Yahweh Allahnku ne ya miƙa su cikin hannunku lokacin da kuka ci su da yaƙi, haka nan kuma dole ne ku hallaka su dukka. Ba zaku ɗauki alƙawari da su ba, kada kuma ku nuna masu jinƙai.3Kada kuma ku shirya aurayya da su. Ba zaku miƙa 'ya'yanku mata aure ga 'ya'yansu maza ba, kuma ba zaku ɗauko 'ya'yansu mata domin 'ya'yanku maza ba.4Gama zasu juyar da hankalin 'ya'yanku maza daga bina, domin su yi sujada ga wasu alloli. Da haka fushin Yahweh za shi yi ƙuna gãba daku, kuma za ya hallaka ku da sauri.5Ga yadda zaku yi da su: Zaku rushe har ƙasa bagadansu, ku farfashe umudansu, ku datse Asherim da mazamninta, ku kuma ƙone sassaƙaƙƙun siffofinsu.6Gama ku al'umma ce da aka keɓe ga Yahweh Allahnku. Ya zaɓe ku ku zama mutane domin ya mallaka, gaba da dukkan sauran mutanen da ke fuskar duniya.7Yahweh bai ɗora ƙaunarsa bisanku ko ya zaɓe ku domin kun fi sauran mutane yawa bane - gama kun zama ƙalilan cikin dukkan mutane -8amma domin ya ƙaunace ku, kuma yana kiyaye alƙawarinsa da ya yi wa ubanninku. Wannan shi ne dalilin da yasa Yahweh ya fito daku da hannu mai girma ya kuma fanshe ku daga gidan bauta, daga hannun Fir'auna, sarkin Masar.9Saboda haka ku san cewa Yahweh Allahnku - shi ne Allah, Allah mai aminci, mai cika alƙawari da kuma aminci ga dubban tsararraki da waɗanda suke ƙaunarsa suna kuma kiyaye dokokinsa,10amma yana saka wa waɗanda suka ƙi shi a fuskarsu, domin ya hallaka su; ba za ya tausaya wa duk wanda ya ƙi shi ba; zai yi masa sakamako yana ji yana gani.11Don haka zaku kiyaye dokoki, da farillai, da kuma umarnai dana dokace ku yau, domin ku aikata su.12Idan kuka saurari waɗannan umarnai, kuka kiyaye ku kuma aikata su, za shi zama kuma Yahweh Allahnku za ya kiyaye ku da alƙawari da kuma amincin da ya rantse wa ubanninku.13Za ya ƙaunace ku, ya albarkace ku, ya kuma riɓanɓanya ku; za ya kuma albarkaci 'ya'yan jikinku da kuma na ƙasarku, hatsinku, da sabuwar inabinku, da kuma mai da ke naku, da ƙaruwar garkunanku da 'ya'yan garkunanku, a cikin ƙasan da ya rantse wa ubanninku zai baku.14Zaku yi albarka fiye da dukkan sauran mutane; ba za a samu bakararre ko bakararriya cikinku ba ko a cikin garkunanku.15Yahweh zai ɗauke dukkan ciwo daga gare ku; babu ko ɗaya daga cikin mugayen cututtuka na Masarawa da kuka sani da zai sa a bisanku, amma zai sa su bisa dukkan waɗanda suka ƙi ku.16Zaku hallaka dukkan mutanen da Yahweh Allahnku za ya bada su cikin hannunku, kuma idanunku ba zasu tausaya masu ba. Kada ku yi sujada ga allolinsu, gama wannan tarko ne a gare ku.17Idan kun ce cikin zuciyarku, 'Waɗannan al'ummai sun sha ƙarfinmu da yawa; yaya zan ci ƙarfinsu in kore su?' -18kada ka ji tsoronsu; ka tuna da abin da Yahweh ya yi ma Fir'auna da dukkan Masarawa;19anobai masu girma da idanuwanka suka gani, alamu, da al'ajibai, hannu mai ƙarfi, da kuma miƙaƙƙiyar hannu wadda Yahweh Allahnku ya fito daku. Yahweh zai yi haka kuma ga dukkan mutanen da kuke tsoron su.20Bayan wannan kuma, Yahweh Allahnku zai aika zirnaƙo a cikinsu, har sai duk waɗanda suka rage da waɗanda suka ɓoye kansu daga gare ku sun hallaka daga fuskarku.21Ba zaku razana ta dalilinsu ba, gama Yahweh Allahnku na cikinku, Allah mai girma mai ban razana.22Yahweh Allahnku zaya kori waɗannan al'ummai daga gabanku kaɗan-kaɗan. Ba zaku iya hallaka su dukka a lokaci ɗaya ba, don kada namomin jeji su yi yawa kewaye daku.23Amma Yahweh Allahnku zaya baku nasara bisansu sa'ad da kuka gamu da su a dagar yaƙi; za ya rikitar da su matuƙa har sai sun lalace sarai.24Za ya sanya sarakunansu a ƙalƙashin ikonku, kuma zaku sa sunansu ya hallaka daga doron ƙasa. Babu wanda zaya iya tsayayya daku, har sai kun hallaka su sarai.25Zaku ƙona sassaƙaƙƙun siffofin allolinsu - kada ku yi ƙyashin azurfa ko zinariyar da ta dalaye su ku kuma ɗauke ta domin amfaninku, don in kun yi haka, zai zama tarko gare ku - gama abin kyama ne ga Yahweh Allahnku.26Ba zaku kawo kowanne ƙazamtaccen abu cikin gidanku ba har da zaku yi masa sujada. Amma zaku yi matuƙar ƙyama ku kuma tsane su, gama keɓaɓɓe ne domin hallakarwa.
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
Musa na maganan nasara kamar abu ne da mutum na iya ba wani. AT: "sa ku ci nasara da su"
A nan "su" na nufin al'ummai bakwai daga 7:1.
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
"Idan kun bar 'ya'yanku sun aure mutane daga wasu al'ummai, mutane daga al'umman za su"
Musa ya kwatanta fushin Allah da wani da ke motsa wuta. Wannan na nanata ikon Yahweh a hallakar da abin da na sa shi fushi. AT: "Yahweh zai hura fushinsa a kanku" ko "Sai Yahweh zai fushi da ku sosai"
Kalmar "ku" na nufin dukka 'yan Isra'ila.
Musa na magana da dukka 'yan Isra'ila anan, don haka waɗannan kalmomin jam'i ne.
Musa ya gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
An yi maganar zaben mutanen Isra'ila da Yahweh ya yi don su zama na shi na musamman kaman Yahweh ya ƙebe su daga dukkan al'umman.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "da na zama a duniya"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "bai kaunace fiye da yadda ya kaunace saura ba"
A nan "ƙarfin hannu" na nufin ikon Yahweh. AT: "da babban ikonsa." Waɗannan kalmomin sun bayyana a cikin 4:34.
Musa na maganar ceton mutanen Isra'ila daga bauta da Yahweh ya yi kaman Yahweh ya biya kuɗi wa wani mai bawa. AT: "cece ku daga zama bayi"
A nan "gidan bauta" na nufin Ma'sar, wuirn da mutanen Isra'ila suka yi bauta. AT: "daga wurin da kuka yi bauta." Fasara waɗannan kalmomin kamar yadda suke a 6:10.
A nan "hannu" na nufin "ikon." AT: "ikon Fir'auna"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana na nufin "rama da sauri kuma a bayyane don su san cewa Allah ya hukunta su."
Yehweh zai hukunta kowane mutum da ya tsane shi sasai"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh. Ya yi magana kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne a aya 12 ya kuma faɗa su kamar taro a aya 13.
"ya kuma kara lumbar mutanenka"
Wannan ƙarin magana ne na "'ya'yanku."
Wannan ƙarin magana ne na "hatsinku."
"shanunku don su yi yawa"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
AT: "Zan albarkace ku fiye da yadda na albarkace kowane mutane"
Musa ya yi amfani da wannan don ya nanata cewa za su iya samin 'ya'ya. AT: "Dukkan ku za ku iya samin 'ya'ya kuma shanukan ku za su iya ba da 'ya'ya"
"ku tabbatar cewa ba ku yi rashin lafiya ba" ko "bar da cikakken lafiya"
Musa ya yi magana kaman cuta abu ne mai ƙarfi da Yahweh zai sa saman kan mutane. AT: "ba zai sa ku rashin lafiya da kowane mugun cututtuka ... amma zai sa maƙiyanku rashin lafiya da su"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
"Na umurce ku ku hallakar da dukkan taron mutane"
Wannan doka ne. Masu ya yi magana kaman abin da idon ya gani idon ne da kansa. AT: "kada ku yarda abin da kun gani ya sa ku ku ji tausayinsu" ko "kada ku ji tausayinsu domin kun gan abin da ku na yi masu na yi masu zafi"
"kada ku bauta"
Idan mutanen na bautan wasu alloli, za su zama kamar dabba da tarkon mafarauci ya kama, kuma ba za su iya tsira ba.
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
Kada mutanen su ji tsoro ko da sun gan cewa al'umman sun fi su ƙarfi. AT: "Ko da kun ce a zuciyarku"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "tunani"
Musa ya yi amfani da tambaya domin ya nuna cewa mutanen na iya jin tsoron sauran al'umman. AT: "ba zan iya cin nasaransu ba"
Wannan ƙarin magana ne. AT" ɗole ne ku tuna"
A nan "idannu" na nufin abin da mutanen sun gani. AT: "da kun gani"
A nan "ƙarfin hannu" da "shimfiɗaɗɗen hannu" ƙarin magana ne na ikon Yahweh. AT: "da ƙarfin hannu." Fasara wannan kamar yadda yake a cikin 4:34.
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
"Da kuma"
AT: 1) Allah zai aiko da ainahin ƙwaro masu yawo da ke harbin mutane ya kuma sa zafi, ko 2) Allah zai sa mutanen su ji tsoro su kuma so su gudu.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "mutu don kar ku gan su kuma"
"Taba"
"Allah mai girma da ɗaukaka" ko "Allah mai girma da ya sa mutanen jin tsoro"
"a hankali"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "sa ku ci nasara"
"nasara akan sojoji daga sauran al'umman"
"zai sa su don kada su iya tuna da kyau"
AT: "sai kun hallakar da su"
'Yan Isra'ilan za su hallaka dukka mutanen waɗancan al'umman gabaɗaya, kuma bubu wanda zai tuna da su nan gaba.
tsaya a kan ku" ko "kare kansu a kanku"
Musa ya cigaba da gaya wa mutanen Isra'ila maganar Yahweh. A aya ta 25, ya yi magana da kungiyan kamar kungiya, don haka "ku" jami ne, amma a aya 26, ya yi magana kamar Isra'ilawan mutum ɗaya ne.
Wannan umurni ne.
"allolin waɗansu al'umman"
Waɗannan kalmomin sun kara umurci a kunen allolin.
Ko ɗaukan zinariya ko azurfa a kan allolin na iya sa mutanesu fara bautan su. Ta yin haka, za su zama kaman dabba da tarko ya kama. AT: "zai zama maku kaman tarko"
Waɗannan kalmomin sun faɗa dalilin da Yahweh na son mutane su kone allolin. "yi wannan domin Yahweh Allahnku a tsane shi sosai"
Kalmomin "ƙi" da "ƙyama" a takaice na nufin abu ɗaya kuma na nuna tsananin tsanan. AT: "Za ku tsana gabaɗaya"
An yi maganar yadda Yahweh ya la'anta wani abu da alkawarin hallakar da shi kamar Yahweh na ƙebe abun daga kowane abu. AT: "Gam Yahweh ya ƙebe shi don hallaka"
1Dole ku kiyaye dukkan dokokin da nake baku yau, domin ku rayu ku kuma riɓaɓɓanya, ku kuma fita ku mallaki ƙasar da Yahweh ya rantse ga ubanninku.2Zaku tuna da dukkan hanyoyin da Yahweh Allahnku ya bi daku waɗannan shekaru arba'in cikin jeji, domin ya ɗauke girman kai daga gare ku, domin ya gwada ku ya kuma san mene ne ke cikin zuciyarku, ko zaku kiyaye dokokinsa ko a'a.3Ya ɗauke girman kanku, ya sa kun ji yunwa, ya kuma ciyar daku da manna, wadda ba ku taɓa sani ba wadda kuma ubanninku ba u sani ba. Ya yi haka ne domin ya koya maku da cewa bada gurasa kaɗai mutane ke rayuwa ba; sai dai, ta kowacce abin da ke fitowa daga bakin Yahweh mutane ke rayuwa.4Tufafinku basu koɗe su kuma faɗi daga jikinku ba, kuma sawayenku basu kumbura cikin shekarun nan arba'in ba.5Zaku yi tunani cikin zuciyarku, ta yaya, kamar yadda mutum ke horon ɗansa, haka Yahweh Allahnku ya ke horonku.6Zaku kiyaye dokokin Yahweh Allahnku, domin ku yi tafiya cikin tafarkunsa ku kuma girmama shi.7Gama Yahweh Allahnku yana kawo ku zuwa cikin ƙasa mai kyau, ƙasa mai rafuffuka, da ɓulɓulai da zurfafa da masu gangarowa daga tuddai, suna gudu zuwa cikin kwarurrukai da tuddai;8ƙasa mai alkama da bali, na inabi, itacen ɓaure, dana rumana; ƙasar da akwai man zaitun da kuma zuma.9́Ƙasa ce inda zaku ci gurasa babu rashi, kuma inda zaku tafi ba da rashin komai ba; ƙasa wadda duwatsunta tama ce, kuma daga cikin tsaunukanta kana iya haƙa jan ƙarfe.10Zaku ci ku kuma ƙoshi, ku kuma albarkaci Yahweh Allahnku domin ƙasa mai kyau da ya baku.11Ku kula kada ku manta da Yahweh Allahnku, kuma kada kuyi banza da dokokinsa, farillansa, da umurnansa da nake dokace ku yau,12in ba haka ba, lokacin da kuka ci kuka kuma ƙoshi, kuka kuma gina gidaje kuka kuma zauna cikinsu, zuciyarku za ta yi kumburi.13Ku kula sa'ad da garkunanku na shanu dana tumaki suka ƙaru kuma lokacin da azurfanku da zinariyarku suka ƙaru, da dukkan mallakarku suka yawaita,14sai zuciyarku ta kumbura har ku manta da Yahweh Allahnku, wanda ya fito daku daga ƙasar Masar, daga gidan bauta.15Kada ku manta da shi wanda ya bishe ku ta cikin jeji babba da mai ban-razana, tare da macizai masu masifa da kunamai da ƙasa mai ƙishi inda babu ruwa, wanda ya fito maku da ruwa daga dutse fa.16Ya ciyas da ku cikin jeji da manna abin da ubanninku basu taɓa sanin ta ba, domin ya ɗauke fahariya daga gare ku ya kuma gwada ku, domin ya yi maku alheri a ƙarshe,17amma zaku ce a zuciyarku, 'Ai ƙarfina ne da ikon hannuna ne suka bani wannan dukkan dukiyar.'18Amma zaku tuna da Yahweh Allahnku, domin shi ne ke baku iko don ku wadata; domin ya kafa alƙawarinsa da ya yi wa ubanninku, kamar yadda ya ke a yau.19Haka za shi zama, idan zaku manta da Yahweh Allahnku ku kuma bi wasu alloli, kuyi masu sujada, ku kuma girmamasu, nayi shaida gãba daku yau da cewa zaku hallaka.20Kamar al'ummai da Yahweh ke sasu hallaka a gaban ku, haka kuma zaku hallaka, domin kun ƙi ku saurari muryar Yahweh Allahnku.
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "Dole ku tuna"
"ya nuna muka yadda ku ke da kasawa da kuma yadda ka ke da zunubi"
"ya bayyana" ko "ya nuna"
Zuciya alama ne na halin mutum. AT: "wane irin mutani ne ku" ko "yadda za ku yi"
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne. Ya cigaba da tuna masu game da abin da za su "tuna"
"Yahweh ya nuna muka yadda ku ke da kasawa da kuma yadda ka ke da zunubi." Dubi yadda an fasara "Ya iya kaskantar da ku"a cikin 8:1.
"ya baku manna ku ci"
A nan "gurasa" na wakilcin dukka abinci. AT: "abinci ba shi ne kadai abin da mutane ke bukata don su iya rayuwa ba"
A nan "bakin Yahweh" ƙarin magana ne na kalmomin da Yahweh na faɗa. AT: "ɗole ne mutane su yi biyayya da umurnin Yahweh don su rayu" ko "ɗole ne mutane su yi abin da Yahweh ya faɗa masu su iy don su rayu"
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Wannan ne abu na karshe da za su "tuna" (8:1).
Wannan ya cigaba da tsarin dokoki da ya fara a cikin 8:1.
A nan "zuciya" na wakilcin tunani da fahimtar mutum. AT: "za ku gane"
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"ƙasa da" ko "ƙasa da ke da"
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
AT: "ƙasar da babu akwai abinci dayawa maku"
AT: "inda za ku samu duk abin da ku na so"
Duwatsun na cike da tama. Bakin ƙarfe, ƙarfe ne mai amfani a wukake da garma.
"ma'adinin jangaci." Jangaci ƙarfe ne mai laushi da ake amfani a yin kayan amfani a gida.
"Za ku samu abinci ɗayawa har ku ci ku kushi"
"za ku yabe" ko "za ku goɗe wa"
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ia kaman su mutum ɗaya ne.
"kada ku daina yin biyayya da umurninsa" ko "cigaba da biyayya da umurninsa"
"loƙacin da ka na da abincin ci ɗayawa"
A nan "zuciya" na wakilcin cikin mutum. An yi maganar zama da girman kai da rashin biyayya da Yahweh kaman zuciyar mutumin na dage a sama. AT: "za ku zama da girman kai kuma ba za ku yi biyayya da Yahweh ba"
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"garken shanukan ka da tumakai da kuma akuyoyi"
"karu a lumba" ko "zama dayawa"
AT: "ku na da abubuwa ɗayawa" ko "ku na da dukiya ɗayawa"
A nan "zuciya" na wakilcin cikin mutum. An yi maganar zama da girman kai da rashin biyayya da Yahweh kaman zuciyar mutumin na dage a sama. AT: "kun zama da girman kai kuma ba ku biyayya da Yahweh"
Musa ya cigaba da tuna wa 'yan Isra'ila akan da bin da sun sani game da Yahweh.
Wannan ƙarin magana ne na loƙacin da su na bauta a cikin Ma'sar. AT: "daga wurin da kun yi bauta"
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Musa ya cigaba da tuna wa 'yan Isra'ila abin da sun sani game da Yahweh.
"Yahweh, wanda ya ratsadda ... Yahweh, wanda ya kawo ... Yahweh Ya shiyad
"macizai masu dafi"
Wannan jimla ya kwatanta ƙasa da kishi kaman mutumin da na kishi a loƙacin da ya na bukatan ruwa. AT: "bushashen ƙasa"
"ya taimake ka" ko "saboda zai yi maka kyau"
Wannan ne abu na uku da mutanen na iya yi a loƙacin da zuciyarsu "sun dagu" kuma sun "manta Yahweh"
A nan "hannu" na nufin ƙarfi da iyawan mutum. AT: "Na samu wannan arzikin domin ina da ƙarfi da iko sosai" ko "na samu waɗannan abubuwan ta ƙarfi na da iyawana"
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ilan kaman sun mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana umurni ne. AT: "Amma ku tuna"
AT: 1) "a haka ya kafa" ko 2) "a haka ya na da amincin kafa."
"don ya iya"
"cika" ko "ajiye"
"kaman yadda ya na yi yanzu" ko "kamar yadda ya na kafa alkawarinsa yanzu"
Tafiya ƙarin magana ne na yin biyayya. AT: "bauta wasu alloli"
"na gaya maku" ko "Na gaya maku a gaban shaidu"
"hakika za ku mutu"
"a gabanku"
A nan "muryan Yahweh" na nufin abin da Yahweh ya ce wa mutanensa su yi. AT: "ba za ku yi biyayya da dokokoin Yahweh"
1Ku saurara, Isra'ila; kuna gab da ƙetare Yodan yau, ku shiga ciki ku kaɓantar da al'ummai waɗanda suka fi ku girma da kuma ƙarfi, da kuma birane ƙarfafa da ganuwa na tsaro da ke kaiwa har sama,2mutane masu girma da tsawo, 'ya'yan Anakim, waɗanda kuka sani, kuma waɗanda kuka ji mutane ke cewa game da su, 'Waye zai iya tsayayya da 'ya'yan Anak?'3Saboda haka yau ku sani cewa Yahweh Allahnku shi ne wanda ya ke tafiya a gabanku kamar wuta mai cinyewa; zaya hallakar da su, kuma zaya ci ƙarfinsu a gabanku; da haka zaku kore su ku kuma sasu hallaka da sauri, kamar yadda Yahweh ya gaya maku.4Kada ku faɗi a zuciyarku, bayan da Yahweh Allahnku ya ture su waje a gabanku, 'Saboda adalcina ne Yahweh ya kawo ni ciki domin in mallaki wannan ƙasa; gama sabili da muguntar waɗannan al'ummai ne yasa Yahweh ya ke korarsu a gabanku.5Ba saboda adalcinku ko dai-daituwa ta zuciyarku ne yasa zaku shiga ku mallaki ƙasarsu ba, amma saboda muguntar waɗannan al'ummai ne yasa Allahnku ke koran su waje daga gabanku, kuma domin ya cika maganarsa da ya rantse wa ubanninku, ga Ibarahim, da Ishaku, da kuma Yakubu.6Don haka ku san cewa, Yahweh Allahnku ba yana baku wannan ƙasa mai kyau domin ku mallake ta don adalcin ku bane, gama ku mutane ne masu taurin zuciya.7Ku tuna kada kuma ku manta yadda kuka tozarta Yahweh Allahnku ga fushi a cikin jeji; daga ranar da kuka baro ƙasar Masar har kuka iso wannan ƙasa, kun yi ta tayarwa gãba da Yahweh.8Haka ma a Horeb kuka tozarta Yahweh ga fushi, har Yahweh ya yi fushin da har zai iya hallaka ku.9Da na tafi kan dutsen domin in karɓo allunan dutse, alluna na alƙawarin da Yahweh ya yi da ku, na zauna a dutsen har kwanaki arba'in da dare arba'in; ban ci gurasa ba ban kuma sha ruwa ba.10Yahweh ya ba ni allunan dutse guda biyu da ya yi rubutu da yatsansa; a cikinsu kuma aka rubuta dukkan maganganun da Yahweh ya shaida maku a kan dutse daga cikin tsakiyar wuta a ranan taro.11Haka ya zama a ƙarshen waɗannan yini arba'in da dare arba'in da Yahweh ya bani allunan duwatsu guda biyu, alluna na alƙawari.12Yahweh ya ce da ni, 'Tashi, sauka ƙasa da sauri daga nan, gama mutanen ka, waɗanda ka fito da su daga Masar, sun ƙazamtar da kansu. Sun yi hamzari daga juyawa daga tafarkin dana dokace su. Sun yi ma kansu sassaƙaƙƙen siffa.'13Gaba da wannan, Yahweh ya yi mani magana ya ce, 'Na ga waɗannan mutanen; mutane ne masu taurin zuciya.14Ka bar ni, don in hallaka su in shafe sunansu daga ƙarƙashin sama, sai kuma in maishe ka al'umma mafi ƙarfi da girma fiye da su.'15Sai na juya na kuma sauko daga dutsen, dutsen kuma na ci da wuta. Allunan alƙawari guda biyu a cikin hannuwana.16Sai na duba, ai kuwa, kun rigaya kun saɓa wa Yahweh Allahnku. Kun yi wa kanku siffar gumaka. Kun juya da sauri daga tafarkin da Yahweh ya dokace ku.17Sai na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana. Na karya su a idanunku.18Sai na sake kwantawa da fuska a ƙasa a gaban Yahweh yini arba'in da dare arba'in; ban ci ko burodi ko in sha ruwa ba, saboda zunubinku da kuka yi, na aikata abin da ke na mugunta a gaban Yahweh, domin ku tozarta shi ga fushi.19Gama na ji tsoron fushi da rashin jin daɗi mai zafi irin wadda Yahweh ya yi gãba daku da ya isa har ya hallaka ku. Amma Yahweh ya saurare ni a wannan lokaci kuma.20Yahweh ya yi matuƙar fushi da Haruna har da zai hallaka shi; Na yi ma Haruna addu'a shi ma a wannan sa'a.21Na ɗauki zunubinku, siffar ɗan maraƙin da kuka yi, na ƙone shi, na tattake shi, na kuma niƙa su gaba ɗaya, har ya zama kamar ƙura. Na zubas da ƙurar cikin rafin da ke gangarowa daga dutsen.22A Tabera, a Massa, da kuma Kibrot Hatta'aba, kuka cakuni Yahweh ya fusata.23Lokacin da Yahweh ya aike ku daga Kadesh Barniya ya kuma ce, 'Ku haura ku mallaki ƙasar dana rigaya na baku,' sai kuka yi tawaye da dokokin Yahweh Allahnku, baku kuma gaskanta da shi ba koku saurari muryarsa ba.24Kun daɗe kuna tayaswa gãba da Yahweh tun daga ranar dana sanku.25Sai na faɗi da fuskata ƙasa a gaban Yahweh a waɗannan yini arba'in da dare arba'in, domin ya ce zai hallaka ku.26Na yi addu'a ga Yahweh na kuma ce, 'Ya Ubangiji Yahweh, kada ka hallakar da mutanenka ko abin gãdon ka daka fanshe su ta wurin girmanka, waɗanda ka fitar daga Masar da hannu mai iko.27Ka tuna da bayinka Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu; kada ka kula da taurin kan waɗannan mutane, ba kuma ga muguntarsu ba, ko ga zunubinsu ba,28domin kada ƙasar daka fito da mu su ce, "Domin Yahweh bai iya ya kai su zuwa cikin ƙasar da ya yi alƙawari garesu ba, kuma domin ya ƙisu, sai ya fito da su zuwa jeji domin ya kashe su a nan."29Duk da haka su mutanenka ne da kuma abin gãdonka, wanda ka fito da su da girman ƙarfinka da kuma ta wurin bayyana aikakkiyar ikonka.'
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Kalmar "Isra'ila" aƙrin magana ne na mutanen Isra'ila. AT: "Saurara, mutanen Isra'ila"
"ƙarba ƙasan daga"
Wannan magana ne da na nanata ban tsoron da mutanen suke domin biranen babba ne da kuma ƙarfi. Dubi yadda kun fasara wannan a ckin 1:26. AT: "na da garurruka masu tsawo"
Zuriyar mutanen Anak wanda su na nan manya da ban tsoro. Dubi yadda kun fasara irin kalmomin nan a cikin 1:26.
Wannan na nufin cewa 'ya'yan Anak su na da ƙarfi kuma mutane na tsoronsu. AT: "Babu wanin da zai iya kare kana akan 'ya'yan Anak."
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"yanzu"
Yahweh na da iko kuma na iya hallakar da sojojin wasu al'umman.
"sa su raunana don ku iya yin mulki da su"
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
A nan "a cikin zuciyarku" na nufin "a cikin tunaninku." AT: "Kada ku yi tunani"
"ya kore sauran mutanen waje"
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana ne. "saboda ku na tunan kullum, kun kuma so abubuwan da sun dace"
"A nan "maganan" na nufin alkawarin Allah. AT: "don ya ciki alkawarinsa"
Ibrahim, Ishaku, da yakubu ne "kakanin" da Musa ke maganan.
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Musa ya sake nanata umurnin don ya nuna amfanin tunawa. AT: "Ku yi hankali da tunawa" (Dubi: [[rc://*/ta;vol2/translate/figs-doublet]])
A nan "ku" na nufin 'yan Isra'ila da su na nan da Musa da kuma 'yan Isra'ilan zamanin da ta wuce.
Wannan na nufin kwarin Rafin Urdun.
Musa na tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
A nan jimla ta biyu ya bayyan cewa "allunan dutse" su ne wanda Allah ya rubuta dokoki goman.
AT: "Yahweh ya rubuto akansu maganan da ya faɗa mauka"
Ya yi kaman Yahweh mutum ne da na tsaye a tsakiyar wuta na kuma magana da murya mai ƙarfi.
Ana iya bayyana "taron" da "taru tare." AT: "a ranar da ku Isra'ilawa kun zo kun hadu tare a wuri ɗaya"
Jimla na biyu ya bayyana cea "alluna biyu na dutsen" su ne wanda Allah ya rubuta dokoki goman.
"mutanenka ... na yin abin da ba daidai ba." Kalmomi irin wannan sun bayyana a cikin 4:15.
Musa na magana kaman yin biyayya da umurnin Allah yin tafiya ne a hanya mai tsawo. AT: "Sun riga sun yi rashin biyayya da dokoki na"
"sa sunansu ya bata gabaɗaya" ko "kashe su dukka don kar wani ya tuna da su." Dubi yadda kun fasara irin wannan jimla a cikin 7:23.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
Kalmar "gani" a nan na nuna cewa Musa ya yi mamakin abin da ya gani.
'Yan Isra'ila na zamani ta farko sun roki Aaron ya yi masu siffan ƙarfe don su bauta masa. Ana iya sa a bayyane cikakken wannan bayani.
Musa ya yi magana kaman yin biyayya da umurnin Allah tafiya ne a kan hanya. AT: "Kun yi saurin rashin biyayya da abin da Yahweh ya umurce ku" Kalmomi irin wannan sun bayyana a cikin 9:11.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
A nan "idanunku" ƙarin magana ne na mutanen Isr'ila. AT: "na jefa shi a gabanku" ko "na jefa shi a inda za ku iya gani"
"faɗi da fuska na a ƙasa." Wannan hanya ce na nuna cewa Yahweh mai girma ne kuma Musa ba haka ba ne.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
Kalmomin "zafin fushin" ƙarin magana ne na abin da Yahweh zai yi domin ya yi fushi. AT: "Yahweh ya yi fushi da ku-bai ji dadinku ba-ya yi fushin da ya kai na hallaka k, sai na ji tsoron abin da zai yi maku"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
Mai yiwuwa Musa ya umurci wasu mutane su yi ainahin aikin. AT: "na ji mutane na kai ... kone ... buga ... nika ... jefa"
sifan maraƙin. AT: "gumkin da ku ka yi zunubi ta wurin yin"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
Waɗannan sunayyen wurare ne da mutanen Isra'ila sun bi a loƙacin da su ke jeji.
Su na shimfiɗaɗɗen ƙasa ne, kuma ƙasan da Yahweh ya gaya masu su karba na tudu, sai sun je kan tudu don su samu.
Kalman "umurni" ƙarin magana ne na Yahweh da kansa. AT: "yi tawaye da Yahweh; ba ku yi biyayya da umurnin ba"
A nan "muryarsa" na nufin abin da Allah ya ce. AT: yi biyayya da bin da ya ce"
"daga ranar da na fara jagoranku." Wasu juyin na karanta "daga ranar da ya san ku," ranar da Yahweh ya fara saninku.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
"kwanta da fuska na a ƙasa." Fasara wannan kamar yadda yake a cikin 9:17.
Musa na magana kaman Yahweh ya cece Isra'ilawan ta wurin biyan kuɗi don ya yantacce su daga bauta. AT: "ka yantacce"
Kalmar "girma" ƙarin magana ne na babban ikon Yahweh. AT: "ta wurin babban ikonka"
A nan "babban hannu" na nufin ikon Yahweh. AT: "da babba ikonka." Kalmomi irin wannan sun bayyana a cikin 4:34.
Musa ya cigaba da yin addu'a wa Yahweh don kar ya hallakar da mutanen Isra'ilan.
wannan ƙarin magana ne.
Kalmomin "ƙasar" ƙarin magana ne na mutanen Ma'sar. AT: "don mutanen Ma'sar"
"iya ce"
Waɗannan jimlan a takaice na nufin abu ɗaya ne kuma na nanata girman ikon Yahweh da ya yi amfani a ceton mutanensa.
1A wannan lokaci Yahweh ya ce da ni, 'Kayi sassakan alluna guda biyu kamar na farko, sai ka hauro wurina kan dutsen, kayi akwatin alƙawari na itace.2Zan yi rubutu a cikin allunan maganganun da suke cikin alluna na farkon daka farfasa, zaka kuma sanya su cikin akwatin.'3Sai na yi akwatin alƙawari daga itacen maje, sai na sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farkon, sai kuma na haura zuwa saman dutse, riƙe da allunan biyu a hannuna.4ya yi rubutu a bisa allunan, kamar rubutu na farko, Dokoki Goma wanda Yahweh ya yi maku magana a kan dutse daga cikin tsakiyar wuta a ranar taruwa; sai Yahweh ya miƙa mani su.5Sai na juyo na sauko daga dutsen, na kuma sanya allunan cikin akwatin alƙawarin dana yi; a nan suke, kamar yadda Yahweh ya umarce ni."6(Jama'ar Isra'la suka yi tafiya daga Birot Bene Ya'akan zuwa Mosera. A nan ne Haruna ya rasu, a nan kuma aka binne shi; Eleyaza, ɗansa, ya yi hidima na firist a matsayinsa.7Daga can suka yi tafiya zuwa Gudgoda, daga Gudgoda kuma zuwa Yotbata, ƙasa mai rafuffuka na ruwa.8A wannan lokaci sai Yahweh ya zaɓi ƙabilar Lebi don su ɗauki akwatin alƙawari na Yahweh, domin su tsaya a gaban Yahweh su yi masa hidima, su kuma albarkaci mutane a cikin sunansa, kamar yau.9Don haka Lebi ba shi da rabo ko gãdon ƙasa tare da 'yan'uwansa; Yahweh ne gãdonsa, kamar yadda Yahweh Allahnka ya yi masa magana.)10"Na zauna a kan dutsen kamar yadda nayi da farko, yini arba'in dare arba'in. Yahweh ya saurare ni wannan lokaci kuma; Yahweh ba shi da niyyar hallaka ku.11Yahweh ya ce mani, 'Ka tashi, ka sha gaban mutanen domin ka shugabance su a kan hanyarsu; za su shiga ciki su kuma mallaki ƙasar dana rantse wa ubanninsu in ba su.'12Yanzu, Isra'ila, mene ne Yahweh Allahnka ke buƙata daga gare ka, sai dai ka ji tsoron Yahweh Allahnka, kayi tafiya cikin dukkan tafarkunsa, ka ƙaunace shi, ka kuma yi sujada ga Yahweh Allahnka da dukkan zuciyarka da kuma dukkan ranka,13don ka kiyaye dokokin Yahweh, da farillansa, waɗanda nake umartan ka yau domin lafiyarka?14Duba, sama da kuma sama ta sammai na Yahweh Allahnka ne, duniyan, da dukkan abin da ke cikinta.15Yahweh ne kawai ya ji daɗin ubanninku da har ya ƙaunace su, ya kuma zaɓe ku, zuriyarsu, a bayansu, fiye da kowanne sauran mutane, kamar yadda ya ke yi yau.16Don haka kuyi wa loɓan zuciyarku kachiya, kuma kada ku ƙara taurin kai kuma.17Gama Yahweh Allahnku, shi ne Allahn alloli da kuma Ubangijin iyayengiji, Allah Alƙadiru, mai girma mai bantsoro, wanda baya nuna sonkai baya kuma karɓan toshi.18Yana aikata adalci domin marayu da gwamraye, kuma yana nuna ƙauna ga wanda ke baƙo ta yadda ya ke ba shi abinci da tufafi.19Saboda haka ka ƙaunaci wanda ya ke baƙo; gama ku da kanku dã baƙi ne a ƙasar Masar.20Zaka ji tsoron Yahweh Allahnku; shi ne zaka yi masa sujada. Gare shi dole zaka manne, kuma da sunansa zaka yi rantsuwa.21Shi ne yabonka, kuma shi ne Allahnka, wanda ya aikata domin ka waɗannan al'amura masu girma da kuma ban-tsoro, waɗanda idanunku suka gani.22Ubanninku suka tafi cikin Masar su mutum saba'in ne; yanzu Yahweh Allahnka ya maishe ka dayawa kamar taurarin sammai.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
"bayan na gama addu'a"
"farko" na nufin farkon allunen da Musa ya karya.
A nan "akan dutsen" na nufin Dutsen Sina.
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
A nan "farko" na nufin farkon allulen dutse. AT: "kamar farkon allunen ditse"
"hau Dutsen Sina"
Na nan kaman Yahweh mutum ne da na tsaye a tsakiyar wuta, na kuma magana da murya mai ƙarfi. Fasara wannan kamar yadda kun yi a cikin 9:9.
Ana ia bayyana "taro" da "taru tare." AT: "a ranar da ku Isra'ilawa kun zo kun hadu tare a wuri ɗaya"
Musa ya cigaba da tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
A nan "Na" na nufin Musa.
"sako daga dutsen Sina"
"cikin akwati" (UDB)
Murubucin ya ba da ƙaramin labarin inda Isra'ila suka yi tafiya.
Wannan ya ba da tushen bayani game da inda mutanen Isra'ilan suka yi tafiya. Ya kuma shafi mutuwar Haruna a Moserah.
Waɗannan sunayyen wurare dabam dabam ne da mutanen Isra'ila suka bi a loƙacin da su na jejin.
Mai fasara na iya kara bayani. "Sunan "Beerot Bene Jaakan" na nufin "su rijiyan mutanen Jaakan."
AT: "wurin ne aka binne shi" ko "Isra'ilawan suka binne shi a wurin"
Wannan sunan ɗan Haruna.
Murabucin ya ba da tushen bayani game da kabilab Lawi.
Wannan ƙarin magana ne. "don su mika hadayan da Yahweh ke bukata"
"da ikon Yahweh" ko "kamar wakilin Yahweh"
"kaman yadda suna yi yau"
Kabilan lawi ba su ƙarbi rabon alkawarin ƙasan a loƙacin da suka isa wurin ba. Ana iya sa a bayyane cikakken ma'anar wannan magana.
Yahweh na maganan dangantaka da Haruna da zuriyarsa za su yi da shi kaman Yahweh wani abu ne da za su gada. AT: "Yahweh ne abin da za su samu" ko "Yahweh zai bar su su bauta masa kuma zai tanada masu ta wurin wannan aiki"
Musa na magana da Isra'ilan kaman su mutum ɗaya ne.
"faɗa wa kabilan Lawi"
Musa ya dawo tuna wa mutanen Isra'ila game da abin da ya faru a zamanin da ta wuce.
"farko" adadin lamba ɗaya. Anan ya na nufin farkon loƙacin da Musa ya je kan Dutsen Sina don ya karba dutsen allune daga Yahweh. "kaman yadda na ni a farko"
Musa na magana da 'yan Isra'ilan kaman mutum ɗaya ne.
"ƙarba ƙasan" ko "ɗau mallakar aƙsan"
Wannan na nufin Ibrahim, Ishaku, da yakubu.
"da zan ba ku, zuriyarsu"
Musa na magana da 'yan Isra'ila kaman su mutumɗaya ne.
A nan "Isra'ila na nufin mutanen Isra'ila. AT: "Yanzu, mutanen Isra'ila"
Musa ya yi amfani da tambaya don ya koyar da mutanen Isra'ila. AT: "wannan ne abin da Yahweh Alahnku na bukatanku ku yi: ku ji tsoro ... don mafaninku."
Musa na magana kaman yin biyayy da Yahweh tafiya ne a kan hanya. AT: "yi biyayya da dukka dokokinsa"
Ƙarin maganan "da dukka zuciyarku" na nufin "gabaɗaya" da "da dukka ranku". Waɗannan jimla na da ma'ana iri ɗaya. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 4:29. AT: "da dukka ranku" ko "da dukka ƙarfinku."
Musa ya cigaba da magana da 'yan Isra'ilan kaman su mutum ɗaya ne.
Kalmar "gani" na nanata cewa abin da ana faɗa na da muhimminci. "Ba da hankali" ko "Duba" ko "saurara"
Waɗannan ƙalmomin na nuna iyaka biyu, kuma na nufin cewa dukka abubuwa a ko ina na Yahweh ne.
Wannan na nufin wurere masu tudu a cikin samai. Kowane abu a cikin samai na Allah ne.
A nan kalmar "ka" na nufin dukka Isra'ila.
"Saboda wannan"
Kalmar "loɓa" na nufin naduwan fata a gaban na miji da ake cirewa a loƙacin kaciya. Anan Musa na nufin kaciya na ruhaniya. Wannan na nufin cewa ɗole ne mutanen su cire zunubi daga rayuwarsu.
"Allah maɗaukaki" ko "Allah kadai na gaskiya"
"Ubangiji maɗaukaki" ko "babban Ubangiji"
"wanda na sa mutane tsoro"
Musa ya cigaba da magana da nutanen Isra'ila.
"yahweh na tabbatar cewa mutanen sun yi wa marayu adalci"
Waɗannan 'ya'ya ne da iyayyensu dukka sun mutu kuma ba su da dangi da za su lura da su.
Gwauruwa mace ce ta gaskiya da mijinta ya mutu kuma ba ta da 'ya'ya da za su lura da ita a sufanta.
"Saboda wannan"
Musa na magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
"shi ne wanda ɗole za ku bauta"
An yi maganan samin zumunci mai kyau da Yahweh da kuma dogara da shi gabaɗaya kaman mutumin na mane wa Yahweh. AT: "Dole ne ku dogara da shi" ko "Shi wanda za ku dogara da shi"
Rantse da sunan Yahweh na nufin sa Yahweh ya zama tushen ko ikon da akeyin rantsuwan. A nan "suna" na wakilcin Yahweh da kansa. Dubi yadda akun fasara irin wannan magana a cikin 6:13. AT: "za ku rantse ku kuma roke Yahweh ya tabbatar da shi" ko "indan kun rantse za ku kira sunan shi"
A nan "idannu" na nufin dukkan mutum. AT: "wanda ku da kanku kun gani"
AT: 1) "shi ne wanda ɗole za ku ɗaukaka" ko 2) "don kun bauta ma sa ne wasu mutane za su ɗaukaka shi"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"yi kudu zuwa Ma'sar" ko "je Ma'sar"
Wannan na nanata yawan Isra'ilawa da su ke tare da Musa. AT: "fiye da za ka iya lissafta"
1Saboda haka zaka kaunaci Yahweh Allahnka ka kuma kiyaye umarnansa, da farillansa, da shari'unsa, da dokokinsa koyaushe.2Ku yi la'akari da cewa ba da 'ya'yan ku nake magana ba, waɗanda basu sani ko suka ga hukuncin Yahweh Allahnku, da girmansa, hannunsa mai iko, ko miƙaƙƙiyar zira'assa,3da alamomi da kuma ayyukan da ya yi cikin Masar ga Fir'auna, sarkin Masar, ga kuma dukkan ƙasarsa.4Ba su kuma ga abin da ya yi wa rundunar Masarawa ba, ko ya yi wa karusansu, yadda ya sa ruwayen Jan Teku suka haɗiye su yayin da suke bin bayansu, da kuma yadda Yahweh ya hallakar da su har wa yau,5ko abin da ya yi maku cikin jeji har kuka zo wannan wuri.6Ba su ga abin da Yahweh ya yi wa Datan da Abiram, 'ya'yan Eliyab ɗan Ruben ba, yadda ƙasa ta buɗe bakinta ta haɗiye su dukka, da danginsu, da rumfarsu, da kowanne abu mai rai da ya biyo su, a tsakiyar dukkan Isra'ila.7Amma idanunku sun ga dukkan manyan ayyukan Yahweh da ya aiwatar.8Don haka ku kiyaye dukkan dokokin da nake baku yau, domin ku yi ƙarfi, ku kuma shiga ku mallaki ƙasa inda kuke shigowa don ku mallake ta,9don kuma kwanakinku ya daɗe cikin ƙasar da Yahweh ya rantse wa ubanninku domin ya basu da kuma zuriyarsu, ƙasa mai zubowa da madara da zuma.10Gama ƙasar, inda kuke shiga don ku mallake ta, ba kamar ƙasar Masar ba ne, inda kuka fito, wurin da kuka yi shukin irinku kuka kuma yi ban-ruwa da kafafunku, kamar lambun baƙulai;11amma ƙasar, da zaku shiga don ku mallake ta, ƙasa ce mai tuddai da kwaruruka, suna kuma shanye ruwan sama na sammai,12ƙasa wacce Yahweh Allahnku ke kula da ita; idanun Yahweh Allahnku na bisan ta koyaushe, daga farkon shekara har zuwa ƙarshen shekara.13Zai faru haka, idan kuka saurara da aniya ga dokokina da nake dokace ku yau, cewa ku ƙaunaci Yahweh Allahnku ku kuma bauta masa da dukkan zuciyarku da kuma dukkan ranku,14sa'an nan zan bada ruwan sama na ƙasarku a kan lokaci, ruwa na farko dana ƙarshe, domin ku tara hatsinku, da sabuwar inabinku, da kuma manku.15Zan bada ciyawa cikin filayenku domin garkunanku, kuma zaku ci ku kuma ƙoshi.16Ku lura da kanku don kada a ruɗar da zuciyarku, har da zaku kauce ku yi sujada ga wasu alloli ku kuma russuna masu;17har fushin Yahweh shi yi ƙuna gãba daku; kuma har kada ya kulle sammai da baza a yi ruwan sama ba, kuma ƙasa ta ƙi bada amfaninta, da kuma har ku hallaka da gaggawa daga cikin ƙasa mai kyau da Yahweh ya ke baku.18Saboda haka ku ajiye waɗannan maganganuna a cikin zuciyarku da ranku, ku ɗaura su kamar alama a hannunku, kuma bari su zama kamar layu a tsakiyar idanunku.19Zaku koyar da su ga 'ya'yanku ku kuma yi zancensu lokacin da kuka zauna a gidanku, sa'ad da kuke tafiya kan hanya, da lokacin da kuke kwance, da kuma sa'ad da kuka tashi.20Zaku rubuta su kan kofofin gidanku da kuma bisa kofofin biranenku,21don kwanakinku dana 'ya'yanku shi riɓaɓɓanya cikin ƙasar da Yahweh ya rantse wa ubanninku ya ba su har iyakar tsawon yadda sammai ke bisa duniya.22Domin idan kuka yi himma ga kiyaye dukkan waɗannan dokokin da nake dokatan ku, don ku aikata su, kuna ƙaunar Yahweh Allahnku, kuna tafiya cikin dukkan tafarkunsa, ku kuma manne masa,23sa'annan Yahweh zai kori dukkan waɗannan al'ummai a gabanku, kuma zaku washe al'umman da suka fi ku yawa da kuma ƙarfi.24Duk inda tafin sawunku zasu taka zasu zama naku; daga jeji zuwa Lebanon, daga kogin, Kogin Yufiretis, zuwa gabashin teku zasu zama iyakarku.25Babu mutumin da za ya iya tsayayya da ku. Yahweh Allahnku zai sa tsoronku da kuma razanarku bisa dukkan ƙasan da kuka taka, kamar yadda ya gaya maku.26Duba, na sa a gabanku yau albarka da kuma la'ana:27albarkan, idan kuka yi biyayya da dokokin Yahweh Allahnku dana dokace ku yau,28la'anar kuma, idan baku yi biyayya da dokokin Yahweh Allahnku ba, amma kuka juya daga hanyar dana dokace ku yau, don ku bi wasu allolin da baku sani ba.29Zai zama kuma, sa'ad da Yahweh Allahnku ya kawo ku zuwa ƙasar da kuke shiga domin ku mallake ta, zaku aza albarka bisa Dutsen Gerizim, la'ana kuma a bisa Dutsen Ebal.30Ba a ƙetaren Yodan suke ba, ta faɗuwar rana kan hanya, cikin ƙasar Kan'aniyawa waɗanda suke zama cikin Araba, gaba da Gilgal, daura da itatuwa na More?31Gama zaku ƙetare Yodan domin ku shiga ciki ku mallaki ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku, kuma za ku mallaketa ku kuma zauna cikinta.32Za ku kiyaye dukkan farillai da umarnan dana shirya a gabanku yau.
Musa ya cigaba da magana da magana da mutanen Isra'ila.
"yi biyayya kullum"
"wanda ba su ji"
A nan "girman hannu" da "shifiɗaɗɗen hannu" ƙarin magana ne na ikon Yahweh. Kalmomi irin wannan sun bayyana a cikin 4:34. AT: "ko babban ikonsa"
"a Ma'sar"
A nan "ƙasa" na wakilcin mutanen. AT: "ga dukka mutanensa"
Musa ya cigaba da magana da manyan Isra'ilawan da sun sufa har sun iya ganin abin da Allah ya yi a cikin Ma'sar.
"ko 'ya'yanku sun gan abin da Yahweh ya yi"
"sojojin Ma'sar
A nan "ku" na nufin Isra'ilawan da su ke raye a shekaru arba'in.
Wannan na nufin wurin kwarin Rafin Urdun inda Musa na magana da su kafin su haye cikin kanan.
Musa ya cigaba da magana da manyan Isra'ilawan da sun sufa har sun iya ganin abin da Allah ya yi a cikin Ma'sar.
Musa na nufin abin da ya faru a baya loƙacin da Datan da Abiram su yi wa Musa da Haruna tawaye. Ana iya sa cikakken ma'anar wannan magana a bayyane.
Waɗannan sunayyen maza ne.
"zuriyar Ra'ubainu"
An na maganan Yahweh ya sa ƙasan ta rabu don mutane su fada a ciki kaman ƙasan na da baki da iya haɗiye mutane.
wannan na nufin bayinsu da dabobinsu.
Wannan na nufin dukka mutanen Isra'ila sun gan abin da ya faru da iyalin Datan da Abiram da kuma mallakarsu.
A nan "idanu" na wakilcin dukkan mutum. AT: "Amma kun gani"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"ƙarba ƙasan"
An yi amfani da jimlar "je" saboda mutanen Isra'ila za su haye Rafin Urdun kafin su shiga Kanan.
Tsawon kwanaki ƙarin magana ne tsawon rai. AT: "iya rayuwa na tsawon lokaci" Fasara waɗannan kalmomi kamar yadda suke a cikin 4:25.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "ƙasa da da madara da zuma mai yawa na gudu" ko "ƙasa da na da kyau ma shanu da gona" Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 6:3.
AT: 1) "kafafu" ƙarin magana ne da na wakilcin aikintafiya da ɗaukan ruwa zuwa fili ko 2) za du yi amfani da kafafunsu su juya ƙarfen da ke ba da ruwa a gonakin.
"lambun ganye"
An yi maganar ƙasaan na karban da janye ruwan sama daya kaman ƙasan na shan ruwan. AT: "ruwan daga sarari na ba shi ruwa dayawa"
A nan "idannu" na wakilcin hankali da lura. AT: "Yahweh Allahnku na duba shi kullum"
A nan an yi amfani da "farko" da ƙarshe" don a nuna dukka shekaru. AT: "cigaba a har zuwa shekara"
Wannan na nufin abin da Yahweh ya yi alkawari zai faruidan 'yan Isra'ilan sun yi biyayya da umurninsa.
A nan "na" na nufin Musa.
Ƙarin maganan "da dukkan zuciyarku: na nufin "gabaɗaya" da "da ... rai" na nufin "da dukka ran ku." Waɗannan jimlolin na da irin ma'ana gudu. Dubi yadda kun Fasara wannan a cikin 4:29. AT: "da dukkan ranku" ko "da dukkan ƙarfinku"
"Za sa ruwan sama a ƙasanku a loƙacin da ya dace"
A nan "Zan" na nufin Yahweh. Ana iya bayyan wannan a mutum na uku. AT: "Yahweh zai ba da" ko "Zai ba da"
Wannan na nufin ruwan sama a farkon loƙacin shuki da kuma ruwan sama don girman amfanin gona don girbi. AT: "ruwan saman kaka da ruwan saman bazara" ko "ruwan sama a loƙacinta"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"yi hankali" ko "ku kula"
A nan "zuciya" na wakilcin sha'awa da tunanin mutum. AT: "don kada sha'awarku ta rude ku" ko "don kada ku rude kanku"
An yi maganan kin Yahweh da bautan wasu alloli kaman mutumin zai juya ya tafi wata hanya dabam daga Yahweh. AT: "kun fara bauta wasu alloli"
An yi maganan fushin Allah kaman wuta ne da na farawa. AT: "don kada Yahweh ya yi fushi da ku"
An yi maganan Allah ya ki ba da ruwan sama kaman ya na rufe sarari. AT: "don kada ya hana ruwan sama daga zuba daga sama don kada amfanin gona ta yi girma a ƙasan"
An yi magana game da mutum da ke tunani da duba kullum abin da Musa ya umurci kaman zuciya da rai gongoni ne kuma kalmomin Musa ne abin da ke cikin gongonin. AT: "Ku yi hankali ku tuna waɗannan kalmomin da ina gaya maku"
A nan "kalmomi" na wakilcin dokokin da Musa ke faɗa.
A nan "zuciya" da "rai" na wakilcin hankali da tunanin mutum.
"ɗaura waɗannan kalmomin." Wannan ƙarin magana ne da ke wakilcin mutum da ke rubuta kalmomin takarda, saka takardan a ƙaramin jaka, da kuma ɗaura ƙaramin jakan. Wannan ƙarin maganan na iya nufin ɗole ne mutanen nan su yi hankali da biyayya da dokokin Musa. Dubi yadda kun fasara irin wannan jimla a cikin 6:8.
"kaman wani abu don ya sa ku tuna dokokina"
"Bari kalmomi na su zama kaman alama a sakanin idannunku." Wannan ƙarin magana ne da ke wakilcin mutum da ke rubuta kalmomin takarda, saka takardan a ƙaramin jaka, da kuma ɗaura ƙaramin jakan. Wannan ƙarin maganan na iya nufin ɗole ne mutumin nan ya yi hankali da biyayya da dokokin Musa. Dubi yadda kun fasara irin wannan jimla a cikin 6:8.
adon da mutum na sa a gaban goshi
Yin amfani da wurare dabam dabam "a gidanku" da "a hanya," da akasin "loƙacin da kun kwanta" da "tashi," na wakilcin ko ina, ko wane loƙaci. Mutanen Isra'ila za su tatuana dokokin Allah su kuma koya wa 'ya'yansu ko wane loƙaci da kuma ko ina.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Fasara waɗannan kalmomin kamar yadda kun yi a 6:8.
A nan "kwanaki" na wakilcin tsawon lokaci. AT: "Yahweh ya sa ku da 'ya'yanku ku yi rayuwa na tsawon loƙaci"
Wannan na nufin Ibrahim, Ishaku da Yakubu.
Wannan ya kwatanta tsawan loƙacin da mutanen za su iya zama a ƙasan da tsawon loƙacin da sama zai kasance bisa duniya. Wannan hanya ne na ce "har abada." AT: "ba su kaman dukiya har abada" ko "bar su u yi rayuwa a wurin har abada"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"Idan kun iya kiyaye kowane abin da na umarceku ku"
An yi maganan yadda Yahweh na so mutum ya yi rayuwa kaman hanyoyin Yahweh ne. An yi maganan mutumin da ke yin biyayya da Yahweh kaman ya na tafiya a hanyoyin Yahweh.
An yi maganan sa da zumunci da Yahweh da kuma dogara da shi kaman mutumin na manne wa Yahweh. AT: "dogara da shi" ko "sa da zumunci mai kyau da shi" Dubi kalmomi irin wannan da an fasara a 10:20.
A nan "al'umman" na wakilcin taron mutanen da suke zama a Kanan. AT: "dukka waɗannan taron mutane a gabanku, kuma zu ku karba ƙasan daga taron mutanen"
Ko da shike sojojin Isra'ila ƙanana ne da kuma rauni fiye da mutanen da suke zama a Kanan, Yahweh zai sa taron mutanen Isra'ila su ci nasara da su.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
A nan "tafin ƙafarku" na wakilcin dukkan mutum. AT: "Duk inda kun je"
"daga Kogin Yufiretis"
Jimlar "tsaya a gaban" ƙarin magana ne. AT: "Babu wanda zai iya hana ku" ko "Babu wanda zai iya hamayya da ku"
An yi maganan yadda Yahweh na sa mutanen jin tsoro kaman tsoro da babban tsoro abu ne zai sa akan mutanen. AT: "Yahweh Allahnku zai sa mutanen a duk inda kun je su ji tsoronku"
Kalmomin "tsoro" da "babban tsoro" na nufin abu ɗaya kuma na nanata tsananin tsoron. AT: "mumunan tsoronku"
A nan "ƙasan" ƙarin magana ne na dukka mutanen ƙasan. AT: "a kan dukka mutane a ko wane wurin da kun tafi"
A nan Musa ya bayyana zažužžuka biyu da mutanen Isra'ila za su zaba. Za su iya zaba su yi biyayya su kuma ƙarba albarkan Allah ko za su iya zaba yi rashin biyayya su kuma karbi hukuncin Allah.
"ba da hankali"
An yi maganan yarda mutanen su zaba ko su na so Allah ya albarkace su ko ya la'anta su kaman albarka da la'anta abu ne da Musa ke shiryawa a gabansu.
AT: "Allah zai albarkaceku"
AT: "Allah zai la'antaku"
An yi maganan dokokin Yahweh da Musa ke gaya wa mutanen kaman su hanyan Allah ne. An yi maganan rashin biyayya da umurnin Allah kaman mutane za su juya wa Yahweh a wani gefe daga don su bi wasu alloli. AT: "amma ku daina yin biyayya da abin da na umurce ku yau, don bauta wa wasu alloli"
Wannan na nufin allolin da wasu taron mutane ke bauta wa. Isra'ilawa sun san Yahweh saboda ya bayyana masu kanshi kuma sun gan ikonsa.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
An yi maganar albarka da la'ana kaman abubuwa ne da wani zai shirya a kan dutse. AT: "Dole ne wasunku su tsaya a kan dutsen Gerazim su shela abin da zai sa Yahweh ya albarkace ku, kuma sauran su tsaya a kan Dutsen Ebal su kuma yi shelar abin da zai sa Yahweh la'antaku"
Waɗannan sunayyen duwatsu ayammancin Tekun Urdun.
Isra'ilawan su na gabashin Tekun Urdun. Musa ya yi amfani da tambaya domin ya tuna wa mutanen inda waɗannan duwatsun suke. AT: "Kaman yadda kun sani, su na gaban Urdun ... Moreh."
"a yammancin Tekun Urdun"
"a yammancin"
"kusa da gilgal"Wannan zai iya zama ba wuri ɗaya kaman birin Jericho ab. Musa na iya nufin wurin da ke kusa da shekem.
Waɗannan tsarkakkun itace ne da ke kusa da Gigal.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Wdannan ne dokokin da Musa zai bayar a 12-26.
Wannan ba ya nufin cewa waɗannan sabbi ne. Musa ya na sake duba dokoki da farllai da ya bayar a shakaru arba'in da ta wuce.
Ana maganar dokoki da farillan Allah da Musa na gaya wa mutane kaman anu ne da Musa na shiryawa a gabn mutanen. AT: "Ina ba ku"
1Waɗannan su ne farillai da dokoki da zaku kiyaye cikin ƙasar da Yahweh, Allahn ubanninku, ke baku domin ku mallaka, dukkan kwanakin da zaku rayu a duniya.2Tabbas zaku lallata dukkan wuraren da al'umman da zaku kora suka bauta wa allolinsu, a bisa duwatsu masu tsawo, a bisa tsaunuka, da kuma ƙarƙashin kowanne koren itace.3Dole ku rurrushe bagadansu, ku ragargaje ginshiƙansu na dutse, ku ƙone dogayen sandunansu na Ashera. Dole ku sassare sassaƙaƙƙun siffofin allolinsu ku hallaka sunayensu daga wurin nan.4Ba zaku yi sujada ga Yahweh Allahnku haka ba.5Amma wurin da Yahweh Allahnku zai zaɓa daga cikin dukkan kabilunku ya sa sunansa, wannan zai zama wurin da zai zauna kuma wurin ne zaku tafi.6A can ne zaku kawo baye-bayenku na ƙonawa, hadayunku, zakkarku, da baye-bayenku da kuka bayar da hannunku, baye-bayenku na wa'adodi, da baye-bayenku na yaddar rai, da 'ya'yan fari na garkunanku na shanu dana tumaki.7A can ne zaku ci a gaban Yahweh Allahnku ku yi murna akan kowanne abin da kuka sa hannunku a gare shi, ku da iyalanku, wurin da Yahweh Allahnku ya albarkace ku.8Ba zaku yi dukkan abubuwan da muke yi anan ba yau; yanzu kowanne yana yin abin da yaga ya dace a gare shi;9gama baku zo wurin hutawa ba tukuna, ga abin gãdo da Yahweh Allahnku ya ke baku.10Amma idan kuka haye Yodan kuka kuma zauna cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ke baku ita gãdo, kuma zai baku hutu daga dukkan maƙiyanku da ke kewaye da ku, domin ku zauna lafiya.11Daga nan zuwa wurin da Yahweh Allahnku ya zaɓa yasa sunansa ya zauna a wurin -- a can ne zaku kawo kowanne abin da na umarce ku: baye-bayenku na ƙonawa, da hadayunku, da zakkarku, da baye-bayen da kuka bayar da hannunku, da dukkan baye-bayen da kuka zaɓa domin wa'adodi da zaku yi wa'adi ga Yahweh.12Zaku yi murna a gaban Yahweh Allahnku -- ku, da 'ya'yanku maza, da 'ya'yanku mata, da bayinku maza, da bayinku mata, da Lebiyawan da ke zama tare da ku, saboda ba shi da rabo ko gãdo a cikin ku.13Ku kula da kanku kada ku miƙa baye-bayenku na ƙonawa a kowanne wurin da kuka gani;14amma a wurin da Yahweh zai zaɓa a cikin ɗaya daga cikin kabilunku zaku miƙa baye-bayenku na ƙonawa, kuma a can ne zaku yi kowanne abin da na dokace ku.15Duk da haka, zaku iya yanka dabbobi ku kuma ci a ko'ina cikin biranenku, kamar yadda kuke so, kuna karɓan albarkar Yahweh Allahnku domin dukkan abin da ya baku; mutane marasa tsarki da masu tsarki dukkansu za su iya ci, dabbobi kamar gada da barewa.16Amma ba zaku ci jinin ba; zaku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.17Ba zaku ci waɗannan a garuruwanku ba daga zakkar hatsinku, sabon inabinku, man ku, ko 'ya'yan farin shanunku, ko tumakinku; ba zaku ci kowanne nama da kuka yi hadaya tare da kowanne wa'adodinku da kuka yi, ko kuma baye-bayenku na yaddar rai, ko baikon da kuka bayar da hannunku.18Maimakon haka, sai ku ci su a gaban Yahweh Allahnku a wurin da Yahweh Allahnku ya zaɓa -- ku, da 'ya'yanku maza, da 'ya'yanku mata, da barorinku maza, da barorinku mata, da Balebi wanda ke zaune a garuruwanku; zaku yi murna a gaban Yahweh Allahnku game da kowanne abin da ya sa a hannunku.19Ku lura da kanku domin kada ku manta da Lebiyawa muddin kuna zaune a ƙasarku.20Sa'ad da Yahweh Allahnku ya fãɗaɗa iyakokinku, kamar yadda ya alƙawarta maku, sa'annan kuka ce, 'Zan ci nama,' saboda ƙãwar cin nama, zaku iya cin nama, yadda ranku ya ke so.21Idan wurin da Yahweh Allahnku ya zaɓa ya sa sunansa ya yi maku nisa sosai, daganan sai ku yanka wasu daga garken shanunku da tumaki da Yahweh ya baku, kamar yadda na umarce ku; zaku iya ci a garuruwanku, kamar yadda ranku ya ke so.22Kamar gada da barewa zaku ci, sai ku ci su, mutane marasa tsarki da masu tsarki za su iya ci su ma.23Sai dai ku tabbata baku ci jinin ba, gama jinin shi ne ran; ba zaku ci rai da nama ba.24Kada ku ci shi, zaku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.25Ba zaku ci shi ba, domin kome ya tafi lafiya tare da ku, tare da 'ya'yanku a bayan ku, idan kuka yi abin da ke dai dai a gaban Yahweh.26Amma abubuwan da ke na Yahweh da kuke da su da baye-bayen wa'adodinku -- zaku ɗauki waɗannan zuwa wurin da Yahweh ya zaɓa.27A can ne zaku miƙa baye-bayenku na ƙonawa, naman da jinin, akan bagadin Yahweh Allahnku; za a zubar da jinin hadayunku akan bagadin Yahweh Allahnku, kuma zaku ci naman.28Ku lura kuma ku saurara ga dukkan kalmomin da na dokace ku da su, don ku sami zaman lafiya tare da 'ya'yanku a bayanku har abada, yayin da kuke yin abin da ke mai kyau da yin dai-dai a gaban idanun Yahweh Allahnku.29Sa'ad da Yahweh Allahnku ya datse al'umman daga gabanku, sa'ad da kuka je kuka kore su, kuka mallake su, kuka zauna cikin ƙasarsu,30ku yi hankali da kanku kada ku faɗa cikin tarkon bin su, bayan da an hallaka su a gabanku -- kada ku faɗa cikin tarkon binciko allolinsu, cikin tambayar, 'Ta yaya waɗannan al'ummai suka yi wa allolinsu sujada? Zan yi kamar yadda suka yi.'31Kada ku yi wa Yahweh Allahnku sujada ta irin wannan hanya, gama kowanne abin ƙyama ga Yahweh, abubuwan da ya ƙi -- sun yi waɗannan abubuwa tare da allolinsu; har sun ƙona 'ya'yansu maza da mata cikin wuta domin allolinsu.32Iyakar abin dana dokace ku, ku aikata shi, kada ku ƙara masa ko ku rage daga gare shi.
Musa na kan magana da mutanen Isra'ila.
"dole ku yi biyayya"
A nan "kwanakin" na wakilcin tsawon loƙaci. Kuma, "yi a duniya" ƙarin magana ne da na nufin bisa yawan loƙacin da mutum zai yi. AT: "bisa ga yawan zamanku"
"dole ne ku hallaka"
A nan "al'umman" na wakilcin taron mutanen da su na zama a Kanan. AT: "taron mutanen da kun karba ƙasansu"
Musa na kan magana da mutanen Isra'ila.
"dole ne ku sage bagadin waɗannan al'umman" ko "dole ku hallaka bagadin waɗannan al'umman"
"guguntulesu" ko "farfasa"
A nan "sunayyensu" na wakilcin "tunaninsu." AT: "hallakar da su gabaɗaya don kar wani ya tuna da su" ko "hallakar da duk abin da na wakilcin waɗannan allolin"
Wannan na nufin wuraren da al'umman ke bauta wa allolinsu.
"Kada ku bauta Yahweh Allahnku kaman yadda waɗancan al'umman suke bautan allolinsu"
A nan "sunansa" na nufin Allah da kansa. Yahweh zai zaɓa wuri ɗaya da zai zauna kuma mutanen za su zo su bauta masa a wurin.
Za su je inda Allah zai zaɓa.
A nan "hannu" na wakilcin dukka mutum. AT: "hadayun da ku ka mika"
"hadayunku na cika alwashi, hadayunku na yardan rai." Waɗannan irin hadayu ne.
Allah na son mutane su ba shi kowane ɗan farin dabbobinsu.
Wannan na nufin wurin yin sujada da Yahweh zai zaba wa 'ya'yan Isra'ila.
A nan "sa hannunku" na wakilcin dukkan mutum da kuma aikin da ya yi. AT: "yi murya akna dukka aikin da kun yi"
"Ba za ku yi kaman yadda muna yi anan yau." Wannan na nufin cewa za su yi sujada a cikin ƙasan alkawari dabam da yadda su na yin sujada a wannan loƙacin.
A nan "idanu" na wakilcin tunani da ra'ayi. AT: "kowa na yin abin da ya na gani daidai"
Ana iya bayyana ƙarin maganan "hutawan". AT: "a ƙasan da za ku huta"
An yi maganan ƙasan da Allah zai ba mutanen Isra'ilan kaman dukiya ne da Uba ya bar wa 'ya'yansa gado. AT: "ga ƙasan da Yahweh Allahnku zai ba ku kaman dukiya"
Wannan na nufin ƙasar Kanan.
An yi maganan Allah na ba da ƙasan Kanan wa mutanen Isra'ila kaman shi Uba ne da ke ba da gado wa 'ya'yansa.
"sa'ad da ya ba ku salama daga dukka maƙiyanku"
A nan "suna" na wakilcin Allah da kansa. AT: "sai zuwa wurin da Yahweh Allahnku zai zauna"
A nan "hanna" na wakilcin dukkan mutum. AT: "hadayun da kuka mika"
"dukka hadayunku na son kai don ku cika wa'adi"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"yi murna a hallarar Yahweh"
A nan "kofofin" shaida ne wa birin da kanta. AT: "Lawiyawa wanda su na zaune a birninku" ko "Lawiyawan masu zama a cikinku"
An yi maganan ko da shike Yahweh ba zai ba da wani ƙasa wa Lawiyawan ba kaman Uba ba zai basu gado ba.
A nan "shi" na nufin Lawi. Lawi na wakilcin dukka zuriyansa. AT: "ba su da rabo"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"Ku yi hankali"
"duk wurin da ya yi maku" ko "duk inda kuke so"
Za a yi hadayan a alfarwa. Yahweh da kansa zai zaba in da za a yi alfarwan.
Mutanen na niya kashe dabbobi kaman hadaya a wurin da Yahweh zai zaba. Za su iya kashe dabbobi don abinci a duk inda su na so. Ana iya sa a bayyane cikakken wannan magana.
A nan "kofofi" na wakilcin dukka birnin. AT: "cikin birninku" ko "a gidajenku"
An yi maganan mutumin da ke karɓabbe a ayukan Allah kaman mutumin na da tsabta.
An yi maganan mutumin da ba karɓabbe a ayukan Allah ba kaman mutumin na da kazanta.
Waɗannan dabbobin daji da tsawo da siririn kafafu da sun iya gudu. AT: "barewan da maririn"
Jinin na wakilcin rai kuma Allah bai yarda mutanen su ci jinin tare da nama. Ana iya sa a bayyane cikakken wannan magana.
Musa ya kwanta wa mutanen Isra'ila dukka
A nan "kofofi" na wakilcin dukka garin. AT: "cikin garin ku" ko "a gidajenku"
A nan "hannu" na wakilcin dukkan mutum. AT: "ko na wannan hadaya wanda kun kawo wa Yahweh"
Yahweh ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"za ku ci hadayunki"
"a hallarar Yahweh"
A nan "kofofin" shaida ne wa birin da kanta. AT: "Lawiyawa wanda su na zaune a birninku" ko "Lawiyawan masu zama a cikinku"
A nan "sa hannunku" na wakilcin dukkan mutumin da aikin da ya yi. AT: "yi murna akan dukka aikin da kun yi"
"yi hankali"
AT: "don ku kula da"
faɗaɗa ƙasanku" ko "ba ku ƙasa dayawa"
Wannan magana cikin magana ne. AT: "sai kun ce kuna so ku ci nama"
A nan "rai" na nufin dukkan mutu. AT: "kaman yadda ku na so" ko "kaman yadda kun rako"
Yahweh ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
A nan "suna" na nufin Allah da kansa. Yahweh zai zaɓa wurin da zauna kuma mutanen za su zo su bauta masa. AT: "zaba ya zauna"
A nan "kofofi" na wakilcin dukka garin. AT: "cikin birni" ko "a cikin mutanenku"
A nan "rai" na wakilcin dukkan mutum. AT: "kaman yadda ku na so"
AT: "kaman yadda ku na cin barewan da maririn"
Waɗannan dabbobin daji da tsawo da siririn kafafu da sun iya gudu. AT: "barewan da maririn"
An yi maganan mutumin da ba karɓabbe a ayukan Allah kaman mutumin na da kazanta.
An yi maganan mutumin da ke karɓabbe a ayukan Allah kaman mutumin na da tsabta.
An yi maganar yadda jini na rike rai anan kaman jinin rai ne da kansa. At: "jinin na rike rai" ko "jinin na sa dabbobi da mutane su rayu"
Kalman "rai" na wakilcin jinin da na rike rai. AT: "Ba za ku ci abin da na rike rai da naman ba" ko "ba za ku ci jinin, wanda ke rike rai, tare da naman ba"
A nan "idannu" na wakilcin tunani da ra'ayi. AT: "abin da ke daidai bisa ga Yahweh" ko "abin da Yahweh faɗa daidai ne"
"hadayu don ka ciki alkawarinka" ko "hadayun alkawari"
AT: "Firist zai zuba jinin hadayan"
Dokan Allah ya daidaita sashen dabba da ke na hadayan konawa, da kuma wane sashi ne na firist da sashin masu bayarwa da za su ci. AT: "za ku ci naman"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
A nan "kalmomin" na wakilcin abin da Musa na faɗan. AT: "Saurara a hankali ka kuma yi biyayya da koman da ina umartan ka"
A nan "'ya'yan" na nufin dukka zuriyarsu. AT: "domin kai da zuriyarka su cigiba"
Kalmomin "kyau" da "daidai" na da ma'ana iri ɗaya kuma na nanata amfanin halin da ta dace. At: "sa'ada da ka yi abin da ke daidai"
A nan "idannu" na wakilcin tunani da zantattuka. AT: "bisa ga Yahweh"
An yi maganan Yahweh da ya hallakar da taron mutane a cikin Kannan kaman ya na yanka su ne, kaman yadda mutum ke yanka kaya ko rashen itace.
A nan "alumman" na wakilcin mutanen da su na zama a kannan.
"sa'ad kun kwashe komai da wurin su"
"yi hankali"
An yi maganan mutumin da ke koyi da kuma bautan wasu alloli kaman an kama su a cikin tarkon mai farauta. AT: "cewa kada ku yi kamansu ... cewa ku gwauda sanin game da allolinsu, tambaya"
An yi maganan Yan Isra'ila da bautan alloli kaman yadda mutanen Kannan su na yi kaman 'yan Isra'ilan sun na bin bayan taron sauran mutanen.
AT: "bayan Yahweh ya hallakar da su a gabanku"
Wannan magana ne a cikin magana. AT: "zuwa tambaya game da yadda wayancan mutanen su ke bautan allolinsu don ku iya yin haka"
Kada su ƙirƙira dokoki ko su bar dokokin da Allah ya ba suba.
1Idan wani annabi ya tashi daga cikinku ko mai mafarkin mafarkai, kuma idan ya baku wata alama ko mu'ujiza,2kuma idan alamar ko mu'ujizar ta faru, wanda ya yi maku magana ya ce, 'Bari mu bi waɗansu allolin, da baku sani ba, kuma bari muyi masu sujada,'3kada ku saurari maganganun annabin nan, ko mai mafarkin mafarkan; gama Yahweh Allahnku yana gwada kune ya sani ko kuna ƙaunar Yahweh Allahnku da dukkan zuciyarku tare da dukkan ranku.4Zaku bi Yahweh Allahnku, ku girmama shi, ku kiyaye dokokinsa, kuyi biyayya da muryarsa za kuyi masa sujada kuma ku manne masa.5Wannan annabin ko wannan mai mafarkin mafarkai za a kashe shi, saboda ya yi maganar tayarwa gãba da Yahweh Allahnku, wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, da wanda ya fãnshe ku daga gidan bauta. Wannan annabi yana so ya karkatarda ku daga hanyar da Yahweh Allahnku ya dokace ku ku yi tafiya a kanta. Don haka sai ku kawar da mugunta daga cikinku.6Idan ɗan'uwanka, ɗan mahaifiyarka, ko ɗanka, ko ɗiyarka, ko matar da ke ƙirjinka, ko abokinka wanda ke ƙaunar ranka, a asirce ya lallasheka ya ce, 'Bari muje mu bauta wa wasu allolin da baku sani ba, ko ku ko kakanninku --7kowanne allolin mutanen da ke kewaye daku, ko kusa daku, ko nesa can daku, daga wannan iyakar duniya zuwa ƙarshen waccan iyakar duniya,'8Kada ku yarda da shi ko ku saurare shi, kada ku bari idonku ya ji tausayinsa, kada ku barshi koku ɓoye shi.9Maimakon haka, ku tabbata kun kashe shi; hannunku ne zai zama na farko wajen kisan sa, daga nan sai hannun dukkan jama'a.10Zaku jejjefe shi da duwatsu har ya mutu, saboda ya yi ƙoƙarin janye ku daga Yahweh Allahnku, wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, daga gidan bauta.11Dukkan Isra'ila zasu ji kuma suji tsoro, kuma ba zasu ci gaba da yin irin wannan mugun abu a cikin ku ba.12Idan kuka ji wani ya ce wani abu game da ɗaya daga cikin biranenku, da Yahweh Allahnku ya baku ku zauna ciki:13Waɗansu mugaye sun fita daga cikinku har sun janye mazaunan birnin suka ce, 'Bari muje muyi sujada ga allolin da baku sani ba.'14Daganan sai ku yi nazarin shaidar, ku bincika, ku tabbatar da kyau. Idan kun gãne cewa gaskiya ne kun haƙiƙance cewa abin ƙyama irin wannan ya faru a cikinku, daganan sai ku ɗauki mataki.15Ku tabbatar kun kai wa mazaunan birnin hari da kaifin takobi, ku hallaka shi da dukkan mutanen da ke zaune ciki, tare da dabbobinsa, da kaifin takobi gaba ɗaya.16Zaku tattara dukkan ganimar daga gare shi zuwa cikin tsakiyar tituna zaku ƙone birnin, da dukkan ganimar -- domin Yahweh Allahnku. Birnin zai zama tsibin kufai har abada; ba za a ƙara gina shi ba.17Ba ɗaya daga cikin abubuwan da aka keɓe domin hallakarwa da zai liƙe cikin hannunku. Dole haka ya faru, domin Yahweh ya juya daga zafin fushinsa, ya nuna maku jinkai, ya ji tausayinku, yasa ku riɓanɓanya, kamar yadda ya rantse wa kakanninku.18Zai yi wannan saboda kuna sauraron muryar Yahweh Allahnku, kuna kiyaye dukkan dokokin dana dokace ku da su yau, kuna yin abin da ke dai-dai a gaban Yahweh Allahnku.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"idan wani ya bayyana a cikinku" ko "idan wani a cikinku ya ce shi ne"
Wannan wani ne da na karban sako daga Allah ta wurin mafarkai.
Waɗannan kalmomin na da ma'ana kusan iri ɗaya kuma na nufin abubuwan al'ajibi dabam dabam.
"ta yiwu" ko "faru"
AT: "kuma ya gaya maku ku bauta wasu allolin da ba ku sani ba"
An yi maganan bauta wasu alloli kaman su na bin ko bin wasu wasu alloli. AT: "Bari mu bi wasu alloli"
Jimlar "alloli, wanda baku sani ba" na nufin allolin da wasu taron mutane na bauta wa. Isra'ilawan sun san Yahweh saboda ya bayyana masu kansa kuma sun gan ikonsa.
A nan "magana" na wakilcin abin da ya ce. AT: "kada ku saurara abin da annabin ya ce ko abin da mai mafarkin ya faɗa"
Karin maganan "da dukka zuciyarku" na nufin "gabaɗaya" da "da ... rai" na nufin "da dukka ranku." Waɗannan jimlolin na da ma'ana mai makamanci. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 4:29. AT: "da dukka ranku" ko "da dukka ƙarfinku"
An yi maganan yin biyayya da bauta wa Yahweh kaman mutanen su na tafiya ko bin Yahweh. AT: "Za ku yi biyayya da Yahweh"
Anan "murya" na wakilcin abin da ya ya faɗa. AT: "yi biyayya da abin da ya faɗa"
An yi maganan sa da zumunci da Yahweh da kuma dogara da shi kaman mutumin na manne wa Yahweh. AT: "dogara da shi"
AT: "ɗole ku kashe"
Ana iya bayyana "tawaye." AT: "ya yi kokarin sa ku ku yi tawaye"
An i magana ceton da Yahweh ya yi wa mutanen Isra'la daga zama bayi a Ma'asar kaman Yahweh ya biya kuɗi don ya fanshe mutanensa daga bauta. AT: "wanda ya cece ku daga wurin da kun yi bauta"
A nan "gidan bauta" na wakilcin Ma'sar inda mutanen Yahweh sun yi bauta. AT: "Ma'sar inda kuka yi bauta"
An yi maganan yadda Allah na son mutum ya yi yayuwa ko yi kaman hanya ne da Allah na son mutanensa su yi tafiya. An yi maganan mutumin da na sa wani ya daina yin biyayya da Allah kaman mutumin na sa ya sa ɗayan mutumin ya daina tafiya a kan hanyar Allah. AT: "sa ka ka ki biyayya da abin da Yahweh Allahnku ya umurce ku"
A nan "mugunta" na nufin mugun mutum ko mugun hali. AT: "Don haka, ɗole ne ku cire daga cikin mutanen Isra'ila mutumin da na yin wannan mugun abu" ko "Don haka, ɗole ne ku kashe wannan mugun mutum"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Ƙirji, ƙirjin mutum ne. Wannan ƙarin magana ne cewa ya rike kusa da ƙirjinsa, da ke nufin cewa ya na kaunanta kwarai. AT: "matar da ka ke ƙauna" ko "matar da ka ke runguma ta ƙauna"
A nan "rai" na wakilcin ran mutumin. Wannan na nufin mutumin ya damu da abokinsa kaman yadda ya na ƙaunan ransa. AT: "ƙaunataccen abokinka" ko "abokin da ka ke ƙauna sosai kaman yadda ka na ƙaunan kanka"
AT: "gwada rarrashe ka a ɓoye don ku je ku bauta ... wani ƙarshen duniya."
"da su na a kewaye da ku"
A nan matsananci biyu na duniya na nufin "ko ina a duniya." AT: "gabaɗaya a dukka duniya"
"kada ku yarda da abin da ya ke so"
A nan "idanunku" na nufin dukkan mutum. AT: "Ko kuma ku dube shi da tausayi" ko "Ko kuma ku nuna mashi yafewa"
"ko ku nuna msa yafewa ko kuma ɓoye anin da ya i daga sauran"
Wannan na nufin cewa zai jefa dutse na farko akan mutum mai laifin. Kalmar "hannu" na wakilcin dukkan mutum. AT: "ɗole ne ka zama na farkon da za ka buga shi don ka kashe shi"
A nan "hannu" na wakilcin dukka mutum. AT: "sauran mutanen za su hadu da kai"
"juyaku daga Yahweh." An yi maganan mutum mai kokarin sa wani dabam ya daina yin biyayya da Yahweh kaman mutumin na kokarin sa wani ya juya ya bar Yahweh. AT: "ya yi kokarin hanaka rashin biyayya da Yahweh"
A nan "gidan bauta" na wakilcin Ma'sar inda mutanen Yahweh sun yi bauta. AT: "daga wurin da kuka yi bauta"
Ana nufin cewa indan mutanen sun ji game da mutumin da an kashe, za su ji tsoron aikata kaman yadda ya yi.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Jimlar "daga cikinku" na nufin cewa waɗannan mugayen mutanen 'yan Isra'ila ne wanda sun yi zama a garin.
AT: "sun rinjaye waɗanda sun zauna a garin don su je su bauta wasu allolin da basu sani ba"
An yi maganan mutum mai sa wani dabam ya daina yin biyayya kaman mutumin ya sa ɗayan mutumin ya juya ya kuma bar Yahweh.
Dukka waɗannan jimlolin a takaice na nufin abu ɗaya. Musa ya nanata cewa ɗole su bincike abin da ya faru a garin.
AT: "cewa mutanen garin sun yi mumunan abu"
A nan "kaifi" na wakilcin dukkan takobi. AT: "da takobinka"
"dukka gannima." Wannan na nufin mallaka da dukiya da rudunar sojoji suka karba bayan cin nasara.
"tarin har abada"
AT: "kada wani ya sake gina birnin"
An yi maganan yadda Yahweh na la'anta wani abu da yin alkawarin hallaka ta kaman Yahweh na shirya abin daga sauran abubuwa. AT: "Kada ku ajiye waɗannan abubuwan da Allah ya umurce ku ya hallaka"
Wannan wata hanya ne na ce mutum ya ajiye wani abu. AT: "ɗole ku ajiye"
An yi maganan rashin fushin Yahweh kuma kaman fushinsa abu ne kuma Yahweh ya juya daga ita. AT: "Yahweh zai daina yin fushi"
A nan "ubanne" na nufin kakani.
A nan "murya" na wakilcin abin da Yahweh ya ce. AT: "kuna biyayya da abin da Yahweh ya ce"
A nan "idanu" na wakilcin tunani da ra'ayi. AT: "da ke daidai bisa ga Yahweh Allanka" ko "abin da Yahweh Allahnka ya gan ya dace"
1Ku mutanen Yahweh Allahnku ne. Kada ku tsãge kanku, ko ku aske kowanne sashi na fuskarku domin matacce.2Gama ku al'umma ce keɓaɓɓiya ga Yahweh Allahnku, Yahweh kuma ya zaɓe ku ku zama mutane abin mallaka, fiye da dukkan al'umman da ke a fuskar duniya.3Ba zaku ci kowanne abin da ke haram ba.4Waɗannan su ne dabbobin da zaku iya ci: saniya, da tunkiya, da akuya,5da mariri, da barewa, da mazo, da bunsurun daji, da makwarwa, da gada, da ragon dutse.6Zaku iya cin kowacce dabbar da ke da rababben kofato, wato, wadda kofatonta sun rabu kashi biyu, kuma tana tuƙa.7Duk da haka, ba zaku ci waɗansu dabbobin da suke tuƙa kuma suke da rababben kofato ba misali: raƙumi, da zomo, da reman dutse; saboda suna tuƙa amma ba su da rababben kofato, marasa tsarki ne a gare ku.8Alade ma ba shi da tsarki a gare ku saboda yana da rababben kofato amma ba ya yin tuƙa; haram ne a gare ku. Kada kuci naman alade, kada kuma ku taɓa mushensu.9Daga irin waɗannan da suke cikin ruwa zaku iya ci: duk abin da ke da ƙege da ɓanɓaroki;10amma duk abin da ba shi da ƙege da ɓanɓaroki kada ku ci su; marasa tsarki ne a gare ku.11Zaku iya cin dukkan tsarkakakkun tsuntsaye.12Amma waɗannan tsuntsayen da ba zaku ci ba: Mikiya, da Ungulu, da ƙwaƙwa,13da jar shirwa da baƙar shirwa, da kowanne irin shaho.14Kada ku ci kowanne irin hankaka,15da jimina, da ƙururu, da harbiyar ruwa, kowanne irin shaho,16ƙaramar mujiya da babbar mujiya, da farar mujiya,17da zalben ruwa, da ungulu, da agwagwar daji.18Ba zaku ci zalɓe ba, da kowanne irin jinjimi, bunburwa da jemage.19Dukkan abin da ke da fiffike da masu rarrafe marasa tsarki ne a gare ku; ba zaku ci su ba.20Zaku iya cin dukkan tsarkakakkun abubuwan da suke shawagi.21Kada ku ci kowanne abin da ya mutu da kansa; za ku iya ba baƙon da ke cikin garuruwanku, domin ya ci; ko ku sayar da shi ga baƙo. Gama ku al'umma ce keɓaɓɓiya ga Yahweh Allahnku. Ba zaku dafa ɗan akuya cikin madarar uwarsa ba.22Dole ku tabbata kun fitar da zakkar dukkan amfanin irin da kuka shuka, wanda ke tsirowa a gona kowacce shekara.23Dole ku ci a gaban Yahweh Allahnku, a wurin da zai zaɓa a matsayin wuri mai tsarki, zakkar hatsin ku, da sabon inabi, dana manku, da 'ya'yan farin shanunku dana dabbobinku; domin kullum ku koyi girmama Yahweh Allahnku.24Idan tafiyar ta yi maku nisa kwarai da baza ku iya kai ta ba, saboda wurin da Yahweh Allahnku ya zaɓa a matsayin wurin sa mai tsarki ya yi maku nisa, daganan, idan Yahweh ya albarkace ku,25sai ku sayar da zakkar ku mai da ita kuɗi, sai ku ƙulle kuɗin cikin hannunku, ku tafi wurin da Yahweh Allahnku zai zaɓa.26A can ne zaku kashe kuɗin akan duk abin da kuke marmari: domin sã, ko domin tunkiya, ko domin ruwan inabi, ko domin abin sha mai ƙarfi, ko domin duk abin da kuke so; zaku ci a can a gaban Yahweh Allahnku, kuma ku yi murna, kuda iyalin gidanku.27Balebi wanda ya ke cikin garuruwanku -- kada ku yashe shi, gama ba shi da rabo ko gãdo tare da ku.28A ƙarshen kowacce shekara uku za ku kawo dukkan zakkar amfaninku cikin wannan shekarar, zaku ajiye ta cikin ƙofofinku;29Balebi kuma, saboda ba shi da rabo ba shi da gãdo tare daku, da baƙo, da maraya, da gwamruwa waɗanda ke cikin ƙofofinku, za su zo su ci su ƙoshi. Ku yi haka domin Yahweh Allahnku ya albarkace ku cikin dukkan aikin da hannuwanku ke yi.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Duk aukuwa na "ku" na nufin mutanen Isra'ila. An sa Musa a cikin mutanen. AT: "Mu ne mutanen ... mu alumma ne ... ya zaɓe mu"
Waɗannan ne hanyoyin da mutanen masu zama a Kanan na nuna cewa suna makokin mutanen da sun mutu. Musa ya na gaya wa mutanen Isra'ila cewa kada su yi kamansu. Ana iya sa cikakken ma'anan a bayyane .
ko ku aske gaban kanku"
Fasara waɗannan kalmomin kaman yadda kun yi a cikin 7:6.
An yi maganan yadda Yahweh ya zaɓa mutanen Isra'ila kaman Yahweh ya keɓe su daga dukka sauran alummai. AT: "Yahweh Allahnku ya keɓe ku daga sauran al'ummai"
A takaice wannan na nufin abu ɗaya ne da jimla na farko/ Su na nufin mutanen Isra'ila na Yahweh ne.
"mutanen mallakar dukiyarsa" ko "mutanensa"
"daga dukka mutanen cikin duniya"
Bai kamata mutanen Isra'ila su ci koman da Allah ya ce bai dace don ci ba.
Waɗannan dukka irin mariri ne. Idan harshenku ba shi da kalma wa kowane dabba, za ku iya fasara ta kaman "dukka irin mariri."
Wannan dabban jeji ne da dogon tsiririn kafafu da na iya guduwa da sauri. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 12:15.
irin mariri
Duk waɗannan irin gada ne. Idan harsheku babu kalma wa kowane dabba , ana iya fasara ta kaman "dukka irin gada."
irin gada
"da na da kofato masu tsagu" (UDB). Wannan kofato ne da ya tsagu zuwa biyu a maimakon zama ɗaya gabaɗaya.
Wannan na nufin cewa dabban na fiyar da abincinsa daga cikinsa ya kuma tuka.
Wannan ƙaramin dabba ne da dogon kunnuwa da na zama a cikin ramuka a ƙasa.
Wannan ƙaramin dabba ne da na zama a cikin wurin duwatsu.
An yi maganan wani abu da Allah ya ce basu dace wa mutanensa su ci ba kaman su na da datti.
An yi maganan wani abu da Yahweh ya ce basu dace wa mutanensa su ci ba kaman dabbobin su na da datti.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"Za ku iya cin waɗannan irin dabbobin da na zama a cikin ruwa"
tsiririn, shimfiɗaɗɗen gefen da kifi na amfani a yin motsi a ruwan
ƙaramin warka da ya rufejikin kifi
An yi maganan dabbobin da Allah ya ce basu dace wa mutanensa su ci ba kaman dabbobin su na da datti.
An yi maganan dabbobin da Allah ya ce sun dace wa mutanensa su ci kaman dabbobin su na da tsabta.
Waɗannan dukka irin tsutsaye ne da su na a farke da dare, su na kuma cin kananan dabbobi da mushe.
Waɗannan dukka irin tsutsaye ne da su na a farke da dare, su na kuma cin kananan dabbobi da mushe.
Waɗannan irin tsutsaye ne da na cin kananan dabbobi da kadangare.
dabba da fuka-fuki da kuma jiki mai ban tsoro da na farke da dare na kuma cin kwaro da dabbobi masu gurgurawa.
Wannan na nufin duka kwaro masi tafiya a sama a taro dayawa.
An yi maganan dabbobin da Allah ya ce basu dace wa mutanensa su ci ba kaman dabbobin su na da datti.
AT: "kada ku ci su"
An yi maganan dabbobin da Allah ya ce sun dace wa mutanensa su ci kaman dabbobin su na da tsabta.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Wannan na nufin dabban da ya mutu.
An yi maganan zabin mutanen Isra'ila da Yahweh ya yi don su zama nasa kaman Yahweh ya keɓe su daga kowane al'ummai. AT: "Gama Yahweh Allahnku ya keɓe ku daga wasu al'ummai"
Wannan na nufin za su ba da rabin komai daidai daga amfaninsu.
"kowane shekara"
"a hallarar Yahweh"
A nan "ta" na nufin zakkan amfanin gona da dabbobi.
"za ku sayad da hadayanku don kuɗi"
"sa kuɗin a cikin jakan sai ku tafi da shi"
"a duk abin da kuke"
"a hallarar Yahweh"
A nan "kofa" na wakilcin birnin ko garin gaba ɗaya. AT: "Kowane Lawi da ya na zama a cikin biranenku"
AT: "ku tabbatar cewa kun ba da zakanku wa Lawi"
Kabilar Lawi basu karba rabon ƙasa kaman gadonsu. Raban gadonsu ɗaukaka ne na bautan Yahweh kaman firisticinsa.
An yi maganan yadda Allah bai ba da ƙasa wa Lawi kaman ba ya basu gado.
So ɗaya a shekara, 'yan Isra'ila za su ajiye zakkansu a cikin garinsu don a yi amfani da shi don tanada wa Lawiyawa, marayu, gwauraye da kuma baƙi.
A nan "kofofi" na wakilcin gari ko birni gabaɗaya. AT: "cikin garinku"
An yi maganan yadda Allah bai ba wa Lawiyawa ƙasa ba kaman ba zai ba su gado ba.
Waɗannan 'ya'ya ne da iyayensu dukka sun mutu kuma ba su da dangin da za su kula da su.
Wannan mace ne da mijinta ya mutu kuma ba ta da 'ya'yan da za su kula da ita a tsufancinta.
A nan "hannu" na wakilcin dukkan mutum. Wannan na nufin aikin da wani na yi. AT: "a dukkan aikin da ku na yi"
1A ƙarshen kowacce shekara bakwai, dole ku yafe basussuwa.2Ga yadda za a yi yafiyar: Kowanne mai bin bashi zai yafe abin da ya rantawa maƙwabcinsa; ba zai neme shi daga wurin maƙwabcinsa ba ko ɗan'uwansa saboda an yi shelar yafe basussuwa ta Yahweh.3Zaka iya nema daga wurin baƙo; amma duk abin da ke naka ya ke tare da ɗan'uwanka ba za ka nemi a biya ka ba.4Har yanzu, ba za a sami matalauci a cikinku ba (gama lallai Yahweh zai albarkace ku a cikin ƙasar da ya ke baku ita a matsayin gãdo ku mallaka),5muddin kuka saurari muryar Yahweh Allahnku, kuka kiyaye dukkan waɗannan dokoki da nake umartarku da su yau.6Gama Yahweh Allahnku zai albarkace ku, kamar yadda ya alƙawarta maku; zaku ba al'ummai da yawa rance, amma ba zaku ranta ba; zaku yi mulkin al'ummai da yawa, amma ba zasu yi mulkin ku ba.7Idan akwai wani mutum matalauci a cikinku, ɗaya daga cikin 'yan'uwanku, a tsakanin kowacce ƙofofinku cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku, kada ku taurare zuciyarku koku rufe hannunku daga ɗan'uwanku matalauci;8amma lallai sai ku buɗe hannunku gare shi kuma ku ranta masa issashe domin biyan bukatarsa.9Ku lura kada ku kasance da mugun tunani a cikin zuciyarku, kuna cewa, 'Ai shekara ta bakwai, shekarar yafewa, ta kusa,' domin kada ku zama da maƙo game da ɗan'uwanku ku kuma ƙi bashi kome; zai iya yin kuka ga Yahweh game daku, kuma ya zama zunubi a gare ku.10Lallai dole ku bashi, zuciyarku kuma ba zata da mu ba idan kuka bashi, saboda wannan Yahweh Allahnku zai albarkace ku cikin dukkan aikinku da kuma dukkan abin da kuka sanya cikin hannunku ku yi.11Gama ba za a rasa matalauta a cikin ƙasar ba; saboda haka na dokace ku cewa, 'Dole ku zama da hannu sake ga ɗan'uwanku, ga mabuƙatanku, da kuma matalauci a cikin ƙasarku.'12Idan aka sayar maku da ɗan'uwanku, Ba'ibrane ko mace ko namiji sai ya bauta maku shekara shida, daga nan a cikin shekara ta bakwai dole ku 'yantar da shi daga gare ku.13Idan kuka 'yantar da shi daga gare ku, ba zaku barshi ya tafi hannun wofi ba.14Dole ku bashi kyauta a yalwace daga cikin tumakinku, da masussukar hatsinku, da wurin matsewar inabinku. Kamar yadda Yahweh Allahnku ya albarkace ku, dole ku ba shi.15Dole ku tuna cewa dã ku bayi ne a cikin ƙasar Masar, kuma Yahweh Allahnku ya fãnshe ku; don haka nake umartarku yau ku yi haka.16Idan kuma ya ce maku, 'Ba zan tafi daga gare ku ba,' saboda yana ƙaunarku da gidanku, kuma yana jin daɗin zama tare da ku,17daganan sai ku ɗauki bisilla ku huda kunnensa har dogaran ƙofa, zai zama bawanku har iyakar rayuwa. Haka kuma zaku yi da mace baiwa.18Kada ya zama da damuwa a gare ku idan kuka 'yantar shi daga gare ku, saboda ya yi maku bauta shekaru shida darajar bautarsa ta ninka biyu da ta mutumin da aka yi hayarsa. Yahweh Allahnku zai albarkace ku cikin dukkan abin da kuke yi.19Dukkan 'ya'yan farin a cikin garkunan shanunku dana tumaki dole ku keɓe su ga Yahweh Allahnku. Kada ku yi aiki da 'ya'yan farin shanunku, koku yi sausayar ɗan farin tumakinku.20Dole ku ci ɗan farin a gaban Yahweh Allahnku kowacce shekara a wurin da Yahweh ya zaɓa, ku da iyalinku.21Idan tana da wani cikas -- misali, gurguntaka, ko makanta ko tana da wani cikas ta kowanne iri -- kada ku miƙa ta hadaya ga Yahweh Allahnku.22Zaku ci ta a garuruwanku; mutane marasa tsarki da masu tsarki su ma dole su ci, kamar mariri ko barewa.23Sai dai kada ku ci jinin; dole ku zubar da jinin a ƙasa kamar ruwa.
Musa ya cigaba magana da mutanen Isra'ila.
"yafe koman da mutane na binku"
"haka ne yadda za ku warware basusukan"
mutum da ke ba da kuɗi wa wasu mutane
Kalmomin "makwabci" da "ɗan'uwa" na da ma'ana iri ɗaya kuma na nanata kusancin dangantaka da suke da shi da yan'uwansu Isra'ilawan. AT: "ɗan Isra'ila ɗan'uwansa"
AT: "saboda Yahweh ya so cewa ku warware basusuka"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "kada ku sake bukatansa kuma" ko "kada ku so biya"
AT: "babu matalautan mutane" ko "babu wani mai talauci"
Wannan na nufin ƙasar Ƙanan.
An yi maganan ƙasan da Yahweh ke ba wa mutanensa kaman gado ne da Yahweh ke ba su.
A nan "muryar Yahweh" na nufin abin da Yahweh da kansa ya ce. At: "muddin kun yi biyayya da abin da Yahweh Allahnku ya ce"
An fahimci kalman "kuɗi." AT: "za ku ba da rancen kuɗi... ba za ku bukaci rancen kuɗi ba
A nan "al'ummai" na wakilcin mutane. AT: "wa mutanen al'ummai da yawa ... akan mutanen al'ummai da yawa"
A nan "mallaki" na nufin kasance da arziki. A takaice wannan na nufin abu ɗaya da jimla da ta wuce.
AT: "Idan akwai matalaucin mutum"
"wani ɗan Isra'ilanku"
A nan "ƙofofi" na wakilcin garin ko birnin gabaɗaya. AT: "a cikin kowane garinku"
An yi maganan zama da tauri kaman mutumin ya taurara zuciyarsu. AT: "kada ku zama da tauri"
An yi maganan mutumin da ya ƙi ya tanada wa matalauci kaman ya na rufe hannusa don matalaucin ya iya samin wani abu daga wurin sa. AT: "ko ku ƙi taimakawa ɗan Isra'ilanku da ke da talauci"
An yi maganan mutum da na taimakon matalauci kaman ya na buɗe hannunsa ma shi. AT: "amma dole ne ku taimake shi"
A nan "zuciya" na wakilcin hankalin mutum. AT: "kada ku yi mugun tunani"
Ana nufin cewa saboda shekaran yafewa ya gabato, mutum mai wannan tunanin zai ji nauyin taimakon matalaucin tun da yake ba lallai ne matalaucin zai biya shi ba.
"shekarar warware bashi"
An ya maganan abin da zai faru nan ba da daddewa ba kaman ya yi kusa. AT: "zai faru nan ba da daddewa ba"
"don kada ki zama da tauri ku kuma ƙi ba da wani abu wa ɗan'uwanku ɗan Isra'ila"
"yi ihu wa Yahweh don taimako"
"Yahweh zai ɗauki abin da kuka yi zunubi ne"
A nan "zuciya" na wakilcin dukkan mutum. AT: "kada ku yi baƙin ciki" ko "ku yi murna"
A nan "sa hannunku" na wakilcin dukkan mutumin da kuma aikin da ya yi. AT: "a duk abin da kuke yi"
AT: "Gama ba za a taba rasa matalauci a ƙasar ba"
AT:
Wannan na da magana a cikin magana. AT: "Na umurce ku ku buɗe hannunku ... a cikin ƙasarku"
An yi maganan mutumin da ke da niyar taimakon wani dabam kaman hannunsa na buɗe. AT: "taimake ɗan Isra'ila ɗan'uwanku, waɗanda ke da bukata, da kuma waɗanda ke da talauci"
Kalmomin "mabukaci" da "matalauci" a takaice na nufin abu ɗaya kuma ya na nanata cewa waɗannan mutane ne da ba su iya taimaka wa kansu. AT: "taimake yan'uwanku Isra'ilawan da ba za su iya taimakon kansu"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
A nan "ɗan'uwa" na nufin ɗan Isra'ila, mace ko na miji. AT: "Idan ɗan Isra'la" ko "Idan ɗan Ba'ibrane"
Idan mutum bai iya biyan bashinsa ba, wani loƙaci su na sayar da kansu ga bauta don su biya abin da ake bin su. AT: "sayad da kansu maku"
Hannu- An yi maganan mutumin da ba shi da dukiya da zai tanada wa kansa ko iyalinsa kaman hannunsa wofi ne. AT: "kada ku bar shi ya tafi ba tare da abin da zai tanada wa kansa da kuma iyalinsa"
"ba shi da hannu sake"
A nan "ku" ya ƙunsa kakaninsu da sun yi bauta a shekaru dayawa. AT: "ku tuna cewa mutanenku sun taba yin bauta"
An yi maganan ceton mutanen Isra'ila da Yahweh ya yi a Ma'sar kaman Yahweh ya biya kuɗi ne don ya fanshe mutanensa daga bauta.
Wannan magana ne cikin magana. AT: "idan ya faɗa maku cewa ba zan tafi daga gareku ba"
A nan "gida" na wakilcin iyalin wani.
sai za ku sa kansa kusa da ƙofan katako a gidanku, sai ku sa tsinin basillan a kunensa zuwa cikin katakon"
kaifin ƙarfe da ana amfani a sa rami
"sai karshen ransa" ko "sai ya mutu"
Wannan na nufin cewa kada su yi fuhsi sa'ad da sun yantar da wani. AT: "Ku yi farinciki sa'ad da kun yantar da shi"
Wannan na nufin mai shi ya biya rabin kuɗi wa wannan bawan don ya yi aiki ba kaman yadda zai yi wa mutum da ya ɗauka ɗan ƙodago don ya yi aiki ba.
Wannan mutum ne da na aiki don kuɗi.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
yanka ulu ko gashi
"a hallarar Yahweh"
"kowace shekara"
nakassase
A nan "kofofi" na wakilcin gari ko birni gabaɗaya. AT: "cikin garinku"
An yi maganan mutum da ba karɓaɓɓe a aikin Allah ba kaman mutumin na da kazanta.
An yi maganan mutum da ke karɓaɓɓe a aikin Allah kaman mutumin na da tsabta.
Waɗannan dabbobin jeji ne da tsawon tsiririn kafafu da na iya guduwa da sauri. Dubi yadda kun fasara waɗannan a 12:15.
"kada ku cinye jininsa." Yahweh bai bar Isra'ilawa su cinye jini ba saboda jinin na wakilcin rai. (Dubi: 12:23)
1Ku kiyaye watan Abib, kuma ku kiyaye Bukin Ƙetarewa ga Yahweh Allahnku, gama a watan Abib ne Yahweh Allahnku ya fito daku daga Masar da daddare.2Zaku miƙa hadayar Ƙetarewa ga Yahweh Allahnku tare da wasu garkunan tumakinku dana shanu a wurin da Yahweh zai zaɓa a matsayin wurinsa mai tsarki.3Ba zaku ci abinci mai gami tare da ita ba; kwana bakwai zaku ci abinci mara gami tare da hadayar, abincin wahala ne; gama kun fito daga ƙasar Masar da gaggawa. Kuyi haka dukkan kwanakinku domin ku tuna da ranar da kuka fito daga ƙasar Masar.4Kada a ga gami a cikinku a dukkan iyakokinku a lokacin kwanaki bakwai; kada kowanne naman da kuka miƙa hadaya da yamma a rana ta fari ya kwana har safiya.5Kada ku miƙa hadayar Ƙetarewa a kowanne garin da Yahweh ya ke baku.6Maimakon haka, ku miƙa ta a wurin da Yahweh Allahnku zai zaɓa a matsayin wurinsa mai tsarki. A can zaku miƙa hadayar Ƙetarewa da yamma da faɗuwar rana, a dai-dai lokacin da shekarar da kuka fito daga Masar.7Dole ku gasa shi kuma ku ci shi a wurin da Yahweh Allahnku zai zaɓa; da safe zaku juya ku koma zuwa rumfunanku.8Kwana shida zaku yi kuna cin abinci mara gami; a rana ta bakwai sai kuyi muhimmin taro domin Yahweh Allahnku; a wannan ranar kada kuyi aiki.9Zaku ƙirga mako bakwai domin kanku; daga lokacin da kuka fara sa lauje ga hatsinku da ke tsaye dole ku fara ƙirga makonni bakwai.10Dole ku kiyaye Bikin Makonni domin Yahweh Allahnku tare da bada gudunmuwa ta yaddar rai daga hannunku da zaku bayar, gwargwadon yadda Yahweh Allahnku ya albarkace ku.11Zaku yi murna a gaban Yahweh Allahnku - ku, da 'ya'yanku maza, da 'ya'yanku mata, da barorinku maza, da barorinku mata, da Balebiyen da ke zaune a ƙofofin garinku, da baƙo, da marayu, da gwamruwa waɗanda ke tare da ku, a wurin da Yahweh Allahnku zai zaɓa domin wurinsa mai tsarki.12Ku tuna dã ku bayi ne a Masar; dole ku kiyaye kuma ku aikata waɗannan farillai.13Dole ku kiyaye Bikin Bukkoki kwanaki bakwai bayan da kun gama tattara amfaninku daga masussukanku da wurin matsewar ruwan inabinku.14Zaku yi murna a lokaci bikin -- ku, da 'ya'yanku maza, da 'ya'yanku mata, da barorinku mata, da Balebiye, da baƙo, da maraya da gwamruwa waɗanda ke a garuruwanku.15Kwana bakwai zaku kiyaye biki ga Yahweh Allahnku a wurin da Yahweh zai zaɓa, saboda Yahweh Allahnku zai albarkace ku a cikin dukkan aikin hannuwanku, kuma dole ku zama da cikakkiyar murna.16Sau uku a shekara dole dukkan mazajenku su hallara a gaban Yahweh Allahnku a wurin da zai zaɓa: a lokacin Bikin Abinci Marar Gami, da lokacin Bikin Makonni, da kuma lokacin Bikin Bukkoki. Kada wani ya hallara gaban Yahweh hannu- wofi;17maimakon haka, kowanne mutum zai bayar gwargawdon abin da zai iya, domin ku san albarkar da Yahweh Allahnku ya bayar gare ku.18Dole ku naɗa alƙalai da shugabannai a dukkan ƙofofin garuruwanku da Yahweh Allahnku ya ke baku; za a ɗauko su daga kowacce kabilarku, dole su shari'anta jama'a da shari'a ta adalci.19Kada ku ɗauke adalci da ƙarfi; kada ku nuna son kai koku karɓi cin hanci, gama cin hanci yana makantar da idanun mai hikima ya karkatar da maganganun adali.20Dole kubi adalci, bayan adalci kaɗai, domin ku rayu ku iya gãdon ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku.21Kada ku sanya wa kanku Asherah, kowanne irin itace, kusa da bagadin Yahweh Allahnku da zaku yi domin kanku.22Kada kuma ku gina wa kanku al'amudin dutse, wanda Yahweh Allahnku ya ke ƙi.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Wannan ne watan farko na kalandan Hebrew. Ya nuna loƙacin da Allah ya fitar da mutanen Isra'ila daga Masar. A loƙacin karshen Maci da farkon watan hudu a kalanda na yamma.
An na nufin "kiyaye Idin ƙetarewa" cewa za su yi bikin su kuma ci abincin idin ƙetarewa. AT: "yi bikin idin ƙetarewa" ko "ci abincin ƙetarewa"
Anan "ƙetarewa" na wakilcin dabban da ake yin hadaya da shi don bikin ƙetarewa. AT: "Gama don ƙetarewan, za ku miƙa hadaya"
A nan "shi" na nufin dabban da za su yi hadaya su kuma ci.
Wannan ne sunan gurasa mara yisti. AT: "wannan gurasan zai tuna maku yadda kun sha wahala sa'ad da ku ke Masar"
Mutanen sun bar Masar da sauri har ba su da loƙacin sosai da za su yi gurasa da yisti a ciki. AT: "fita daga ƙasar Masar a cikin wannan sauri ba ku sami loƙacin yin gurasa da yisti a ciki ba"
"yi wannan a duk rayuwanku"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "tuna"
AT: "Kada ku sami yisti a cikinku"
"cikin dukka ƙasanku"
A nan "ketarewa" na wakilcin dabban da za a yi hadayarsa. AT: "Gama idin ketarewan ba za ku yi hadayar dabban ba"
A nan "kofofi" na wakilcin garin da birane. AT: "a kowane garin"
"a faɗuwar rana"
"Dole ku dafa shi"
"taro ta musamman"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Wannan jimalar "sa laujen akan tsayeyen hatsin" wata hanya ce na ce farkon loƙacin girbi. AT: "daga loƙacin da kun fara girba hatsin"
ƙarfe mai lankwasa da ake amfani don yanka shiyawa, hatsi da ruwan inabi.
A nan "hannu" na wakilcin dukan mutum. AT: "kuma za ku ba da hadayan yardar rai"
"bisa ga girbin da Yahweh Allanku ya ba ku" Wannan na nufin cewa mutanen za su sa bayaswarsa akan nawa su ke girba a wannan shekara.
Wannan ba ya nufin takamaiman mutum. AT: "'ya'yanku mata da maza, da barorinku maza da mata, kowane Lawi"
A nan "kofofi" na wakilcin gari da birane. AT: "cikin garinku"
Wannan na nufin irin waɗannan mutane a takaice. AT: "dukka baƙi, marayu, da kuma gwauraye"
Waɗannan yara ne da iyayensu sun mutu kuma ba su da dangi da za su kula a su.
Wannan na nufin macen da mijin ta ya mutu kuma ba ta da yaran da za su lura da ita a tsufancinta .
Wannan ƙarin magana ne. AT: "ku tuna"
Wasu sunayyen wannan idin su ne "Idin alfarwa," "Idin bukoki," da kuma "Idin tattarawa." A loƙacin wannan girbin, manuma za su shirya bukoki na dan loƙaci a filin. Wannan idin ya faru a bayan girbi na karshen shekara.
A nan kalman "ƙofofi" na wakilcin birane ko garuruka. AT: "a biranenku"
"Idin Bukkoki"
A nan "hannaye" na wakilcin dukkan mutum. AT: "dukka aikin da ku na yi"
An na barin mata, amma Yahweh bai ce su zo ba. Mazaje na iya wakilance dukan iyalensu.
"ɗole su zo su tsaya a gaban Yahweh"
Hannu; a maimakon, kowane mutum- "ba za su zo gaban Yahweh ba tare da hadaya ba; a maimakon haka, kowane mutum." AT: "ɗole kowane mutum da ya zo gaban Yahweh ya kawo hadaya. Kowane mutum"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"Dole ku naɗa aƙalai" ko "Ɗole ku zabi alƙalai"
A nan "kofofi" na wakilcin gari ko birni. AT: "a cikin dukka garin"
AT: "za ku zaɓe su "
"hukunta mutanen da gaskiya"
Musa ya yi maganan adalci kaman kaman abu ne da mutum mai ƙarfi na iya jawowa daga mutum mara ƙarfi. AT: "Kada ku da rashin gaskiya sa'ad da ku na shari'a" Harshenku na iya samin kalma ɗaya da na nufin "yi amfani da ƙarfi ka karbi." AT: "Ɗole ne ku yi gaskiya a yanke shawara"
A nan "ku" na nufin waɗanda za a naɗa su masu shair'a da yan jami'a.
An yi maganan karban cin hanci kaman cin hanci yake bata mutanen. AT: "domin ko mutum mai hikima da ke karban cin hanci za makanta, kuma mutum mai adalci da ya karbi cin hanci zai faɗa karya"
An yi maganan mutum mai hikima da ke karban cin hanci don ya yi magana akan abin da ba daidai ba kaman ya makanta.
AT: "mutum mai hikima" ko "mutane masu hikima"
AT: "ya kuma sa mutum mai adalci ya yi karya"
An yi maganan adalci kaman mutum ne nai tafiya. An yi maganan mutum mai yin abu da gaskiya da adalci kaman ya na bin kusa da bayan adalci. AT: "yi abin da ke gaskiya"
An yi maganan karban ƙasan da Allah yake ba wa mutanen kaman mutanen sun gaji ƙasan daga Allah.
A nan "ku" na nufin dukka mutanen Isra'ila.
Jimlar "wanda Yahweh Allahnku ya ƙi" na ba da bayani game da al'amudi masu tsarki. AT: "kowane al'amudi masu tsarki domin Yahweh Allahnku ya ƙi su"
Wannan na nufin gumakan al'amudi da ana amfani a bautan alloli.
1Kada ku miƙa wa Yahweh Allahnku hadaya ta sã ko tunkiya da ke da kowanne lahani ko duk abin da bashi da kyau, gama wannan zai zama abin ƙyama ga Yahweh Allahnku.2Idan aka sami wani, a tsakanin kowaɗanne ƙofofin garinku da Yahweh Allahnku ya ke baku, kowanne mutum ko mace, wanda ya aikata abin da ke mugu a gaban Yahweh Allahnku yana karya alƙawarinsa,3duk wanda yaje ya yi sujada ga waɗansu alloli ya kuma russuna masu, ko rana, ko wata, ko kowacce rundunar sama - ba abin dana umarce ku ba -4idan aka faɗa maku game da wannan, ko kuka ji labarinsa, daganan dole kuyi bincike a hankali. Idan gaskiya ne kuma an tabbatar da anyi irin wannan abin ƙyamar a Isra'ila, wannan shi ne abin da zaku yi.5Dole ku kawo wannan mutum ko macen, wanda ya aikata wannan mugun abu, ga ƙofofin garuruwanku, wannan mutumin ko macen, dole ku jejjefe shi da duwatsu har ya mutu.6Bisa ga shaidu biyu ko shaidu uku, za a kashe shi; amma ba za a kashe mutum bisa ga shaidar mutum ɗaya ba.7Hannun shaidun zasu fara jifansa ga mutuwa, daganan sauran dukkan jama'a; ta haka zaku kawar da mugunta daga cikinku.8Idan wani abu ya taso da ya zama da wahala a gare ku ku shari'anta - watakila zancen kisankai ko haɗarin mutuwa, ta zancen 'yancin wani da ta wani, ko tambaya akan wani irin lahani da aka yi, ko dai wani al'amari, al'amura masu wahalarwa a cikin ƙofofin garinku -- daga nan dole ku tafi wurin da Yahweh Allahnku zai zaɓa a matsayin wurinsa mai tsarki.9Dole ku je wurin firist, zuriyar Lebi, da kuma wurin alƙali da zai yi hidima a lokacin; zaku nemi shawararsu, zasu baku mafita.10Dole ku bi shari'ar da aka baku a wurin da Yahweh zai zaɓa a matsayin wurinsa mai tsarki. Dole ku lura ku yi dukkan abin da suka jagorance ku ga yi.11Kubi shari'ar da suka koya maku, ku kuma yi bisa ga shawarwarin da suka baku. Kada ku kauce daga abin da suka faɗa maku, zuwa hananun dama ko zuwa hannun hagu.12Duk wanda ya yi isgilanci, ta wurin ƙin sauraron firist wanda ke tsaye ya bauta wa Yahweh Allahnku, ko ta ƙin sauraron alƙali - wannan mutum zai mutu; dole ku kawar da mugunta daga Isra'ila.13Dukkan mutane dole suji kuma suji tsoro, ba zasu ƙara yi isgilanci ba.14Sa'ad da kuka zo ƙasar da Yahweh Allahnku ya ba ku, kuma idan kuka mallake ta kuka fara zama cikinta, sa'an nan kuka ce, 'Zan sanya sarki a bisa kaina, kamar dukkan al'umman da suke kewaye da ni,'15daga nan dole ku tabbatar kun naɗa wa kanku sarki wanda Yahweh Allahnku zai zaɓa. Dole ku naɗa wa kanku sarki wanda ke daga cikin 'yan'uwanku. kada ku sanya baƙo, wanda ba ɗan'uwanku ba, a bisa kanku.16Amma kada ya ƙara wa kansa dawakai, kada ya sa mutane su koma Masar don su ƙaro masa dawakai, gama Yahweh ya ce maku, 'Kada ku ƙara komawa can.'17Kada ya ɗauki mata da yawa domin kansa, domin kada zuciyarsa ta karkace. Kada ya tattara wa kansa tulin kuɗin azurfa da zinariya.18Sa'ada da ya zauna kan gadon sarautar mulkinsa, dole ya rubutawa kansa a cikin naɗaɗɗen kwafin littafi shari' an nan, daga shari'a da ke gaban firist, waɗanda suke Lebiyawa.19Naɗaɗɗen littafin zai kasance tare da shi, kuma dole ya karanta shi cikin dukkan kwanakin ransa, domin ya koyi girmama Yahweh Allahnsa, domin ya kiyaye dukkan kalmomin shari'ar da waɗannan farillai, ya kiyaye su.20Dole ya yi haka domin kada zuciyarsa ta kumbura bisa kan 'yan'uwansa, domin kada ya kauce daga bin dokokin, zuwa dama ko hagu; domin ya sami dalilin daɗewa cikin mulkinsa, shi da 'ya'yansa, a cikin Isra'ila.
Musa ya na magana da mutanen Isra'ila.
"da ke da lahani" ko "wanda akwai damuwa." Wannan dabban zai bayyana da lafiya ba tare da wani rauni ba.
"wannan zai zama abin ƙyama ce ga Yahweh"
AT: "Idan kun samu wani" ko "idan akwai wani"
A nan "kofofin garin" na wakilcin gari da birane. AT: "zama a ɗaya daga cikin biranenku"
A nan, "a gaban Yahweh" na nufin abin da ya na gani ko tunani game da wani abu. AT: "wani abin da Yahweh Allahnku ke tunani mugu ce"
"rashin biyayya da alkawarinsa"
"ɗaya daga cikin tauraro""
"wanda ban umurce kowa ya yi ba"
AT: "Idan wani ya gaya maku game da wannan ayukan rashin biyayya"
Ana iya bayyana "bincike" da fi'ili. AT: "dole ne ku bincika cikakken abin da ya faru"
AT: "wani ya yi irin wannan abin tsoro a Isra'ila"
A nan "bakin" na wakilcin shaidar mashaida. AT: "idan mutane biyu sun yi magana akan sa, ɗole ne ku kashe shi"
A nan "bakin" na wakilcin shaidar mashaida. AT: "amma idan mutum ɗaya kadai ya yi magana akan sa, kada ku kashe shi"
A nan "hannu" na wakilcin dukka taron shaidu. AT: "Ɗole ne shaidun da kansu su zama na farkon da za su jefa duwatsu. Sai dukka mutanen za su kashe mutumin ta wurin jifansa da duwatsu"
AT: "ɗole ku cire daga cikin Isra'ilawan wannan mutum wanda ke aikata wannan muguntan" ko "dole ku kashe wannan mugun mutum"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
" idan akwai al'amari" ko "idan akwai halin da ake ciki"
"Dama"iko ne na biye da dokan mutum na yin wani abu ko mallakar wani abu.
A nan "kofofin birane" na wakilcin birane ko garin. AT: "cikin garinku"
AT: "za ku ce masu su ba ku shawara"
AT: "za su yanke shawara akan maganan"
An yi maganan mutum mai biyayya da abin da firistoci da mai shari'a sun yanke shawaran kaman mutumin na bin bayan dokoan. AT: "Dole ku yi biyayya da abin da mai shari'a da firistoci sun yanke akan al'amarin"
An yi maganan mutumin da ba ya yin abin da mai shari'a da firistoci sun ce kaman ya na juyawa daga hanyan da ba daidai ba. AT: "Kada ku yi rashin biyayya da abin da sun gaya maku" AT: "Yi kaman yadda sun ce"
"kuma ba ya yin biyayya da firist ... ko ba ya yin biyayya da alƙalin"
AT: "dole ku cire daga cikin Isra'ilawa, mutumin da ya yi wannan muguntan" ko "ɗole ku kashe wannan mutumin"
An na nufin cewa loƙacin da mutanen sun ji game da mutumin da an kashe don girman kai, za su ji tsoro kuma ba za su yi girman kai ba.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Ana iya fasar kalman "zo" kaman "je" ko "shigo."
AT: "sai kun yanke shawara cewa ku na son sarki kaman yadda mutanen al'umman da ke kewaye ku da na da sarakuna"
Musa ya sa mutanen magana kaman su mutum ɗaya ne. Zai yi kyau ku fasara wannan da jam'i da kuma wakilan suna. AT: "Za mu kafa wa kanmu ... kewaye da mu"
An yi maganan ba wani ikon mulki kaman sarki a Isra'ila kaman mutanen su na shirya mutumin bisa kansu.
"dukka al'ummai da ke kewaye"
dukka al'umman, Anan "al'ummai" na nufin mutanen da su na zama a al'umman.
"ɗaya daga cikin yan'uwanka Isra'ilawa"
Dukka waɗannan jimlolin na nufin abu ɗaya. Su na nufin mutumin da ɗan Isra'ila ba. Yahweh na nanata cewa kada mutanen Isra'ila su bar baƙo ya yi masu mulki. AT: "baƙo a kanka" ko "wanda ba ɗan Isra'ila ba a kanka"
Wannan na da magana a cikin magana. AT: "gama Yahweh ya faɗa cewa kada ku koma Masar kuma"
A nan "zuciya" na nufin dukkan mutum. An yi maganan sarkin Isra'ila da ya auri mataye daga waje ya kuma fara bauta wa allolinsu kaman zuciyarsa za su juya daga Yahweh. AT: "don kada su sa shi ya juya wa Yahweh ya kuma fara bauta wa allolin karya"
A nan "kursiyin" na wakilcin ƙarfi da ikon mutum a matsayin sarki. Zauna a kursiyi na nufin zama sarki. AT: "Sa'ad da ya zama sarki"
AT: 1) "dole ya rubuta a cikin gungura juyin wannan umurni wa kansa" ko 2) "dole ya nadda wani ya rubuta a cikin gungura juyin wannan umurnin masa"
"daga juyin umurni da firistocin Lawiyawa sun kiyaye"
Waɗannan jimloli biyun a takaice na nufin abu ɗaya kuma na nanata cewa ɗole ne sarkin ya yi biyayya dukka umurnin Allah.
A nan "zuciya" na nufin dukkan mutum. An yi maganan sarki mai girman kai kaman an daga zuciyarsa. AT: "don kada ya zama da girman kai" ko "don kada ya yi tunani cewa ya fi yan'uwansa Isra'ilawa"
An yi maganan sarki mai rashin biyayya da dokokin Allah kaman mutumin zai juye a hanyan da ta dace. AT: "don kada ya yi rashin biyayya da dokokin" An iya bayyan wannan a cikin sifar aiki. AT: "don ya yi biyayya da dukka dokokin"
Tsawowin kwanaki ƙarin magana ne na tsawon rai. Dubi yadda kun fasara irin wannan magana "tsawanta rananku" a cikin 4:25. AT: "iya zama da tsawon loƙaci"
1Firistoci, da suke Lebiyawa, da dukkan kabilar Lebi, ba za su sami rabo ko gãdo tare da Isra'ila ba; dole su ci baye-bayen Yahweh da aka yi da wuta a matsayin gãdonsu.2Ba zasu sami gãdo tare da 'yan'uwansu ba; Yahweh shi ne gãdon su, kamar yadda ya faɗa masu.3Wannan shi ne rabon da aka ba firistoci, aka basu daga mutanen da suka miƙa hadaya, ko ta sã ne ko tunkiya ce: kafaɗar, kumatu biyu, da kuma kayan ciki.4Sai nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabi, da manku, da gashin tumakinku da kuka fara sausaya, dole ku ba shi.5Gama Yahweh Allahnku ya zaɓe shi da ga cikin kabilunku su tsaya su yi hidima a cikin sunan Yahweh, shi da 'ya'yansa har abada.6Idan Balebiye ya fito daga kowanne garinku na dukkan Isra'ila daga inda ya ke zama, kuma ya yi marmari da dukkan ransa ya zo wurin da Yahweh ya zaɓa,7daganan dole ya yi hidima a cikin sunan Yahweh Allahnsa kamar yadda dukkan 'yan'uwansa Lebiyawa suke yi, waɗanda ke tsayawa a can a gaban Yahweh.8Dole su sami rabo iri ɗaya su ci, banda abin da ke zuwa daga abin da iyalinsa suka sayar na gãdo.9Sa'ad da kuka zo cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku, kada kuyi kwaikwayon ayyukan banƙyama na waɗannan al'ummai.10Kada a sami wani a cikinku da zai miƙa ɗansa ko 'yarsa hadaya cikin wuta, duk wanda ke amfani da maita ko mai faɗin gaibu, ko mai sihiri, ko ya shiga maita,11duk mabiya, ko mai sha'ani da ruhohi ko mai surkulle, mai magana da ruhohin matattu.12Gama duk mai yin waɗannan abubuwa abin ƙyama ne ga Yahweh; saboda waɗannan abubuwan ban ƙyama ne Yahweh Allahnku ya ke korarsu daga gaban ku.13Sai ku zama marasa aibu a gaban Yahweh Allahnku.14Gama waɗannan al'ummai da zaku kora suna sauraran masu aikata maita da masu duba; amma ku, Yahweh Allahnku bai yaddar maku ku yi haka ba.15Yahweh Allahnku zai tayar maku da wani annabi daga cikinku, ɗaya daga cikin 'yan'uwanku, kama ta. Dole ku saurare shi.16Wannan shi ne abin da kuka roƙa a wurin Yahweh Allahnku a Horeb a ranar taron, cewa, 'Kada ka barmu mu ƙara jin muryar Yahweh Allahnmu, ko mu ƙara ganin wannan babbar wuta, don zamu mutu.'17Yahweh ya ce mani, 'Abin da suka ce yana da kyau.18Zan tayar masu da wani annabi daga cikin 'yan'uwansu, kamar ka. Zan sa maganganuna cikin bakinsa, zai faɗa masu dukkan abin da na dokace shi.19Zai kasance kuwa duk wanda bai saurari maganganuna da zai faɗa a cikin sunana ba, Zan nemi haƙƙinta a gareshi.20Amma annabin da ya faɗi maganar isgilanci cikin sunana, maganar da ban umarce shi ba ya faɗa, ko wanda ya yi magana cikin sunan waɗansu alloli, wannan annabin dole ya mutu.'21Wannan shi ne abin da zaku ce a cikin zuciyarku: 'Ta yaya zamu san saƙon da Yahweh bai faɗi ba?'22Zaku gane saƙon da Yahweh ya faɗa idan annabi ya yi magana a cikin sunan Yahweh. Idan wannan abin bai zo ba, ko bai faru ba, daganan wannan shi ne abin da Yahweh bai faɗa ba kuma annabin ya faɗe shi ne cikin isgilanci, kada ku ji tsoronsa.
Musa ya cigaba da faɗa wa mutanen Isra'ila game da abin da Yahweh na so su yi.
An yi maganan yadda Lawiyawa ba za su karbi ƙasa daga Yahweh kaman ba za su karbi gado ba. AT: "ba zai mallaki ko wani ƙasar mutanen ba" ko "ba zai ƙabi ko wani ƙasar da Isra'ilawan sun mallaka ba"
"ba sashi"
"a cikin wasu kabilun Isra'ila" ko "a cikin sauran Isra'ilawa"
Musa ya yi maganan babban ɗaukaka da Haruna da zuriyarsa za su samu ta wurin yin hidima wa Yahweh a matsayin firist kaman Yahweh wani abu ne da za su gada. Dubi yadda kun fasara jimla irin wannan a cikin 10:8. AT: "a maimakon haka, za su sami Yahweh" ko "a maimakon haka, Yahweh zai bar su su yi masa hidima kuma zai tanada masu ta wurin hidimarsu"
"neman firist" ko "rabon firist"
"Wannan ne cikin da kuma su hanji.
"dole ku ba wa firist"
A nan "shi" na wakilcin dukka Lawiyawa.
A nan "sunan Yahweh" na matsayin Yahweh da kansa da ikonsa. AT: "ya zama bawansa na musamman" ko "ya yi hidima kaman wakilin Yahweh"
A nan "shi" na wakilcin dukka Lawiyawa. AT: "Lawiyawan da zuriyarsu har abada"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "so sosai"
A nan "suna" na wakilcin Yahweh da ikonsa. AT: "sai dole ya yi wa Yahweh Allahnsa hidima a kaman firist"
"wanda ke hidima a cikin haikali a gaban Yahweh"
Wannan ne abin da firist zai gada daga wurin ma haifinsa.
Ana iya fasara anan "zo" kamar "tafi" ko "shiga."
Allah ya tsane ayukan addini na mutanen a al'ummai da ke kewaye. Ya na ɗaukansu da muni. AT: "A nan "alummai" na wakilcin mutanen. AT: "kada ku yi mumunan abubuwan da mutanen sauran al'umman ke yi"
AT: "Kada a sami wani a cikinku"
"yi hadayan 'ya'yansa da wuta a kan bagadi"
Waɗannan mutane dabam ne wanda su na yin sihiri. Allah ya haramta kowane irin sihiri. Ana iya bayyana ta musamman idan ba ku da kalma wa dukka irin waɗannan mutanen. AT: "duk wanda ya yi amfani da sihiri don ya san abin da zai faru nan gaba, yin kirari, ko yin magana wa ruhohin matattun mutane"
amfani ya sihiri shi ne faɗin abin da zai faru nan gaba
A nan "su" na nufin mutanen da su na zama a Kanan.
A nan "al'ummai" na matsayin taron mutane da sun yi zama a cikin Kanan. AT: "Gama waɗannan taron mutane"
"fittar da"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
An yi maganan yadda Yahweh ya naɗa wani ya zama annabi kaman Yahweh zai daga mutumin sama.
"ɗaya daga yan Isra'ilawa"
A nan "kuka" na nufin Isra'ilawan a Dutsen Horeb kusan shakaru arba'in a baya.
"a ranar da kun hadu tare a Horeb"
Wannan magana ne a cikin magana. AT: "ranar taron da kun faɗa cewa ba ku son ku ji muryar Yahweh Allahnku, ko gan babbar wutarsa kuma ba, don kun ji tsoron cewa za ku mutu"
A nan "murya" na wakilcin maganar Yahweh. AT: "Kada mu ji Yahweh Allahnmu ya yi magana kuma"
An yi maganan yadda Yahweh ya naɗa wani ya zama annabi kaman Yahweh zai daga mutumin sama.
daga ɗan Isra'ilawa
An yi maganan yadda Yahweh na faɗa wa annabin abin da zai ce kaman Yahweh zai sa maganan a bakin annabin.
"faɗa wa mutanen Isra'ila"
A nan "magana" na wakilcin abin da Yahweh ya ce. A nan "sunana" na wakilcin Yahweh da ikonsa. AT: "bai saurar shi sa'ad da ya na faɗan sako na"
"Zan rike shi da alhakin" ko "Zan hukunta shi." A nan "shi" na nufin mutum da ba ya sauraran annabin.
Yahweh ya cigaba da magana.
A nan "magana" na wakilcin sako. AT: "wanda ya gwado faɗan sako" ko "wanda ke da izgilin faɗan sako"
A nan "sunana" na nufin Yahweh da kansa da kuma ikonsa. AT: "wa ni" ko "da iko na"
A nan "magana" na wakilcin sako. AT: "sakon da ban umurta ba"
A nan "suna" na wakilcin allolin da kansu ko ikonsu. Wannan na nufin cewa annabin na faɗa cewa allolin ƙarya sun ce mashi ya faɗa wata sako.
A nan "zuciya" na wakilcin tunanin mutum. AT: "Kun tambayi kanku" ko "Ɗole ku ce wa kanku"
"Ta ya yaza mu san ko sakon da annabin ke faɗa daga Yahweh ne?" A nan "mu" na nufin mutanen Isra'ila.
Yahweh ya cigaba da magana.
A nan "sunan Yahweh" na nufin Yahweh da kansa da kuma ikonsa. AT: "annabi ya ce ya na magana masa" ko "annabi ya ce ya na magana da iko na"
"annabin ya yi wannan magana ba tare da iko na ba"
1Sa'ad da Yahweh Allahnku ya datse al'ummai, waɗannan waɗanda Yahweh Allahnku zai baku ƙasarsu, sa'ad da kuka zo bayansu kuka zauna a cikin garuruwansu da gidajensu,2sai ku zaɓi birane uku domin kanku a tsakiyar ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke ba ku ku mallaka.3Sai ku gina hanyoyi ku kuma raba iyakokin ƙasarku kashi uku, ƙasar da Yahweh Allahnku ke saku gãda, domin duk wanda ya kashe wani mutum sai ya gudu zuwa can.4Wannan itace doka domin wanda ya kashe wani da wanda ya gudu can don ya tsira - duk wanda ya kashe maƙwabcinsa ba don ya yi niyya ba, kuma bai ƙi shi ba a dã.5Misali, idan mutum ya tafi cikin jeji tare da maƙwabcinsa domin su saro itace, sai ruwan gatarin ya kwaɓe daga ƙotar ya sari maƙwabcinsa ya kashe shi - daganan wannan mutumin dole ya gudu zuwa ɗaya daga biranen domin ya tsirar da ransa.6Idan ba haka ba mai bin haƙƙin jini zai iya bin shi wanda ya ɗauki ran, cikin zafin fushinsa ya cim masa, idan nisan ya yi yawa sosai, ya cim masa ya kashe shi, koda shike mutumin nan bai cancanci mutuwa ba, tunda shike bai ƙi shi ba a dã.7Don haka na dokace ku ku keɓe wa kanku birane uku.8Idan Yahweh Allahnku ya fãɗaɗa iyakokinku, kamar yadda ya alƙawarta wa kakanninku zai yi, ya baku dukkan ƙasar da ya alƙawarta ya ba kakanninku;9idan kuka kiyaye dukkan waɗannan dokoki kuka aikata su, waɗanda nake dokatarku da su yau - dokokin ku ƙaunaci Yahweh Allahnku kullum kuyi tafiya cikin hanyoyinsa, daganan sai ku ƙara birane uku domin kanku, akan waɗannan ukun kuma.10Kuyi haka domin kada a zubar da jinin mara laifi a cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku domin gãdo, domin kada alhakin jini ya kasance a kanku.11Amma idan wani yana ƙin maƙwabcinsa, ya yi kwanto yana jiransa, ya tasar masa, ya yi masa rauni har ya mutu, idan ya gudu zuwa cikin ɗaya daga cikin biranen nan -12daganan dattawan garinsu dole su aika a kawo shi daga can, daganan su miƙa shi a hannun ɗan'uwan mai bin hakƙin jini domin a kashe shi.13Kada idannunku su tausaya masa; maimakon haka dole ku kawar da alhakin zubar da jini daga Isra'ila, domin ku sami zaman lafiya.14Kada ku kawar da iyakar maƙwabcinka da kakanninku suka kafa tuntuni, a cikin gãdon da zaku gãda, a cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku ku mallaka.15Shaidar mutum ɗaya ba zata isa a tabbatar da cewa mutum ya yi kowanne irin laifi ba, ko kowanne zunubi, a kan kowanne zunubin da ya yi; sai an ji a bakin shaidu biyu ko uku, kafin a tabbatar da kowanne abu.16Alal misali idan mashaidi marar adalci ya tashi gãba da kowanne mutum ya shaida sharri game da laifinsa.17Daganan sai dukkansu mutanen, waɗanda rashin jituwar ta faru tsakaninsu, dole su tsaya gaban Yahweh, a gaban firistoci da alƙalai masu yin hidima akwanakin nan.18Dole alƙalan suyi bincike sosai; su duba, idan mai shaidar mai shaidar zur ne, ya yi shaidar ƙarya game da ɗan'uwansa,19daganan sai ku yi masa, kamar yadda ya so ayi wa ɗan'uwansa; kuma zaku kawar da mugunta daga cikinku tawurin yin haka.20Daganan sauran da suka ragu zasu ji su ji tsoro, kuma daganan ba zasu ƙara aikata irin wannan mugunta a cikinku ba.21Kada idannunku su tausaya; rai maimakon rai, ido mai makon ido, haƙori mai makon haƙori, hannu mai makon hannu, ƙafa mai makon ƙafa.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
An yi maganan yadda Yahweh zai hallaka mutanen da su ke zama a Kanaan kaman yana yanka su, kaman yadda wani ke yanka gutun tufafi ko yanka reshe daga itace.
Wannan na wakilcin taron mutanen da su na zama a Kanaan.
"al'umman da su ke zama a ƙasar da Yahweh Allahnku zai ba ku"
"ɗauki ƙasan daga waaɗannan al'umman" ko "mallaki ƙasan bayan waɗannan al'umman sun tafi
Za ku gina hanya don ya zama da sauki wa mutane su yi tafiya zuwa waɗannan garuruka.
Ana nufin cewa ɗole ne ɗaya daga cikin garurruwan da sun zaɓa ya kasance a kowane sashin ƙasan.
An yi maganar yadda Yahweh ke ba wa mutanen Isra'ila ƙasan kaman mutanen su na gadan ƙasan.
"Waɗannan ne umarnin" ko "Waɗannan ne kwatanin"
An fahimci kalmar." AT: "wa mutumin da ya kashe wani mutum"
"kuma wanda ya yi gudun hijira zuwa ɗaya daga cikin waɗannan garuruwa" ko "kuma wanda ya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan garuruwan"
"don ya ceci ransa." AT: "don kada iyalin mutumin da ya mutu su kashe shi don su ɗauki fansa"
A nan "makwabci" na nufin ko wane mutum. AT: "ko wane mutum da ya kashe wani mutum ta hasari"
"amma bai tsane makwabcinsa kaman ya kashe shi." Wannan na nufin ba shi da dalilin kashe makwabcinsa da saninsa.
Marubucin ya bayyana wata yanayin da mutum ya kashe wani ba da ganganci ba"
Gefen ƙarfen digan ya fita daga makaman.
Wannan na nufin cewa kan gatarin ya buga, ya kuma kashe makwabcinsa.
"zuwa ɗaya daga cikin waɗannan biranen don ya tsire ransa." Ana nufin cewa iyalin mutumin da ya mutu na iya ɗaukan fansa. Mutumin da ya kashe shi na iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan garuruwa, kuma mutanen wurin za su ƙare shi.
Musa na kan magana da mutanen Isra'ila.
A nan "jini" na wakilcin mutumin da an kashe. Kuma " bin hakin jini" dangi na kusa na mutum da an kashe. Wannan dangin na da alhakin hukunta mai kisan.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "wanda ya kashe wani mutum"
An yi maganar wani da fushi sosai kaman fushi abu ne da zai iya yi zafi. AT: "yin fushi"
"Kuma mai bin hakin jini ya buga ya kuma kashe wanda ya kashe ɗayan mutumin"
"ko da yake mutumin bai cancanci ya mutu ba tun da ya kashe mutumin ba da gangan ba kuma ba makiyansa ba ne, kuma bai so ya yi wa mutumin rauni ba"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"ba ku ƙasa dayawa don ku mallaka"
"kamar yadda ya yi wa kakaninku alkawari cewa zai yi"
"idan kun yi biyayya da wadannan umurnin"
An yi maganan yadda Allah ya na son mutum ya yi rayuwa ko ya nuna hali kaman hanyar Yahweh ne. An yi maganan mutum da na biyayya da Yahweh kaman ya na tafiya a hanyar Yahweh. AT: "yi masa biyayya kullum"
AT: "sa'an nan za ku kara zaḅa garuruwa uku don tsiran mutum idan ya kashe wani ba da saninsa ba"
"akan sauran garuruka uku da kun riga kun kafa"
AT: "Yi wannan don kada mutanen iyalin su kashe mutum mara alhaki"
A nan "jini" na wakilcin ran mutum. Zub da jini na nufin kashe mutum. AT: "babu wani da yake kashe mutum mara laifi"
"a ƙasan"
An yi maganan ƙasan da Yahweh ke ba wa mutanen Isra'ila kaman gado ne.
An yi maganan kasancer mutanen Isra'ila da alhakin mutum da ke mutuwa domin ba su gina garin da zai tsira daga "mai bin hakin jini" kaman alhakin mutuwarsa na kansu.
A nan "jini" na wakilcin rai kuma "alhakin jini" na nufin alhakin da wani ya ke da shi don kashe mutum mara laifi.
Wannan na nufin idan ɗan iyali ya kashe mutum mara laifi, dukka mutanen Isra'ila za su zama da alhakin barin wannan ya faru.
Anan "makwabci" a takaice na nufin kowane mutum.
AT: "ɓoye ya jira don ya kashe shi" ko "nshirya kashe shi"
AT: "faɗă masa"
"kuma cutar da shi don ya mutu" ko "kuma kashe shi"
"aike wani ya same shi ya dawo da shi daga garin da ya tsira"
AT: "ba da shi"
A nan "hannun" na wakilcin ikon wani. AT: "ga hukumar dangin mai alhakin" ko "ga dangi mai alhakin"
Wannan dangin mutumin da an kashe. Wannan dangin na da hakin hukunta mai kisan.
"mai kisan na iya mutuwa" ko "dangin mai hakin na iya kashe mai kisan"
A nan "idanunku" na wakilcin dukka mutum. AT: "Kada ku yafe masa" ko "Kada ku ji tausayinsa"
A nan "jinin laifi" na wakilcin laifin kisan mutum mai mara laifi. At: "ku kashe mai kisan don mutanen Isra'ila ba za su zama da laifin mutuwan mutum mai mara laifi"
A nan "Isra'ila na nufin mutanen Isra'iala.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
AT: "Kada ku kwace ƙasa daga makwabcinku ta wurin matsar da alamun a iyakan ƙasarsa"
"wanda kakaninkuj sun kafa"
Musa na nufin cewa sa'ada da mutanen sun yi zama a ƙasan na tsawon loƙaci, kada su matsar da iyakan da kakaninsu su yi a loƙacin da sun karba ƙasan.
An yi magana yadda Yahweh yake ba wa mutanen Isra'ila ƙasan kaman su na gadan ƙasan. AT: "a săan da Yahweh Allahnku ke ba ku ku mallaka"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isral'ilan
"Shada ɗaya" ko "Shaida ɗaya kadai"
A nan "tashi" na nufin tashiwa a kotu da kuma yin magana wa alƙali akan wani. AT: "yi magana game da wani mugun abu da mutum ya yi"
"duk loƙacin da mutum ya yi mumunan abu"
A nan "baki" na wakilcin abin da shaidun sun ce. Ana nufin cewa ɗole ne a sami shaidu biyu ko uku. AT: "a shaidan mutane biyu ko uku" ko "bisa abin da mutane biyu ko uku sun ce ya faru"
AT: "za ku tabbatar da cewa mutumin na da laifi"
"Sa'ad da" ko "Idan"
"shaida da ya yi niyar cutar da wani dabam"
A nan "taso" na nufin tashiwa a kotu da kuma yin magana wa alƙali akan wani. AT: "gaya wa alƙalin cewa mutumin ya yi laifi don ya sa mutumin a damuwa" ko "gayawa alƙalin cewa mutumin ya yi laifi, don alƙalin ya hukunta shi"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"waɗanda ba su yarda da juna ba"
Wannan na nufin cewa dole mutane biyun su je haikali, inda Yahweh yake. A kwai firistoci da Alƙalai wanda da suke da ikon yanke shawara wa Yahweh.
Jimlar "tsaya a gaban" ƙarin magana ne. Ya na nufin tafiya zuwa wurin wani mai iko, ya kuma yanke shawara game da maganan.
dole alƙalin ya aiki da kyau don ya ƙudura abin da zai faru"
"sai ku hukunta mai shaidan karya kamar yadda ya so ku hukunta ɗayan mutumin"
AT: "ta wurin hukunta mai shaidan karyan, za ku hana mugayen ayuka a cikin al'ummanku"
"Sa'ad da kun hukunta shaida mara gaskiya, sauran mutanen"
AT: "su ji game da hukuncin su kuma ji tsoron hukunci"
"kada ka sake yin wani mugun abu kamar haka"
A nan "idanu" na nufin dukka mutum. AT: "Kada ku ji tausayinsa" ko "Kada ku yafe masa"
An rage jimlolin domin an fahimci ma'anan. Na nufin ɗole mutanen su hukunta mutum yadda ya cutar da wani mutum.
1Sa'ad da kuka tafi yaƙi gãba da maƙiyanku, idan kunga dawakai, karusai, da mutanen da suka fi ku yawa, kada ku ji tsoronsu; Gama Yahweh Allahnku yana tare daku, shi wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar.2Sa'ad da kuke gab da shiga cikin yaƙi, sai firist ya kusato ya yi magana da mutane.3Dole ya ce masu, 'Ku saurara, Isra'ila, zaku tafi yaƙi gãba da maƙiyanku. Kada ku bari zukatanku su karaya. Kada kuji tsoro ko ku firgita. Kada kuji tsoronsu.4Gama Yahweh Allahnku shi ne mai tafiya tare daku ya yi yaƙi domin ku gãba da maƙiyanku ya cece ku kuma.'5Dole shugabanni suyi magana da mutane su ce, 'Ko akwai wani mutum wanda ya gina sabon gida da bai buɗe shi ba? Bari ya koma gidansa, domin kada ya mutu cikin yaƙi sa'an nan wani mutum dabam ya yi bikin buɗewarsa.6Ko akwai wani daya dasa gonar inabi da bai ci amfaninta ba? Bari ya koma gida, domin kada ya mutu a cikin yaƙi wani mutum dabam yaci amfaninta.7Wanne mutum ne ya ke tashin mace amma bai aure ta ba tukuna? Bari ya koma gida domin kada ya mutu a cikin yaƙi sa'an nan wani mutum dabam ya aure ta.'8Shugabannin zasu ci gaba da yiwa mutane magana su ce, 'Ko a kwai wani mutum a nan da ya ke jin tsoro ko mai karyayyar zuciya? Bari ya koma gidansa, domin kada zuciyar 'yan'uwansa su narke kamar yadda zuciyarsa ta narke.'9Sa'ad da shugabanni suka gama yin magana da mutane, dole su naɗa hafsoshi a kansu.10Sa'ad da kuka kusanci wani birni don ku kai masa hari, ku ba mutanen birnin kyautar salama.11Idan suka karɓi kyautar ku har suka buɗe maku ƙofofinsu, dukkan mutanen da kuka sãmu a cikinsa dole suyi maku aikin gandu kuma su bauta maku.12Amma idan ya ƙi yin salama daku, maimakon haka sai ya yi yaƙi daku, daganan sai ku kewaye shi da yaƙi,13idan kuma Yahweh Allahnku ya baku nasara ya sa su ƙarƙashin sarrafawar ku, dole ku kashe kowanne mutum a cikin garin.14Amma mata da ƙanana, da dabbobi, da kowanne abin da ke cikin birnin, da dukkan ganimarsu, zaku ɗauka a matsayin ganima domin kanku. Zaku ci ganimar maƙiyanku, wadda Yahweh Allahnku ya baku.15Haka zaku aikata ga dukkan biranen da ke nesa daku sosai, biranen da ba biranen waɗannan al'ummai ba.16A cikin biranen al'umman nan da Yahweh Allahnku ya ke baku a matsayin gãdo, kada ku bar kowanne abin da ke numfashi da rai.17Maimakon haka zaku hallakar da su ƙarƙaf: Su Hittiyawa, da Amoriyawa, da Kan'aniyawa, da Feriziyawa, da Hibiyawa, da Yebusiyawa, kamar yadda Yahweh Allahnku ya dokace ku.18Ku yi haka domin kada su koya maku ku aikata kowanne abin banƙyamarsu kamar yadda suka yi tare da allolinsu. Idan kuka yi, zaku yi zunubi ga Yahweh Allahnku.19Sa'ad da kuka daɗe da kewaye birni, yayin da kuke yaƙi da shi domin ku ci shi, kada ku hallaka itatuwansa da gatari ta wurin saransu. Gama zaku iya ci daga gare su, don haka kada ku sare su ƙasa. Gama itacen gona mutum ne da zaku kewaye shi da yaƙi?20Itatuwan kaɗai da kuka sani ba itatuwan da ake ci ba, zaku iya hallakarwa ku sare su ƙasa; zaku gina kagara da su gãba da birnin da ke yaƙi daku, har sai ya faɗi.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"Sa'ad kun fita je ku yi yaƙi akan makiyanku"
Mutane sun ɗauke soja masu dawakai da karusai dayawa masu ƙarfi. Ana iya sa a bayyane wannan magana.
Yahweh ya kawo mutane daga Masar zuwa Kanaan. An saba amfani da kalmar "kawo" wa masu tafiye-tafiye daga Masar zuwa Kanaan. AT: "Yahweh wanda ya bi da ku daga ƙasar Masar"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"yi magana da sojojin Isra'ila"
Dukk waɗannan bayyane hudun na nufin abu ɗaya kuma na nanata cewa kada su ji tsoro. Idan harshenku ba ta da hanyoyi hudu na bayyana wannan magana, za ku iya amfani wanda kuke da shi.
A nan "zuciya" na wakilcin ƙarfin halin mutum. Karayan zuciya ƙarin magana ne da na nufin "Kada ku ji tsoro."
An yi maganan yadda Yahweh na cin nasara da makiyan mutanen Isra'ila kaman Yahweh jarumi ne wanda zai yi fada tare da mutanen Isra'ila.
"ba ku nasara"
Musa ya cigaba da kwatanta yanayin da ke sa mutum barin soja.
Ɗaya daga cikin aikin jami'an shi ne su zaɓi wanda zai iya barin sojan. Ana iya sa a bayyane cikakken wannan bayani.
"Idan wani soja ya gina sabon gida kuma bai buɗe ta ba, ya koma gidansa"
ɗan jami'in na kwatanta yanayin da ke iya faru wa soja. AT: "don, idan ya mutu a yaƙi, wani mutum ba zai buɗe gidansa a maimakonsa ba"
Musa ya cigaba da kwatanta yanayin da ke sa mutum barin soja.
"Idan wani soja anan na da gonar inabi, amma bai girbe amfaninsa ba, ya koma gidansa"
ɗan jami'in na kwatanta yanayin da ke iya faru wa soja. AT: "don, idan ya mutu, wani mutum ba zai girba amfaninsa a maimakon shi ba"
"Idan wani soja anan ya yi alkwarin aure, amma bai riga ya aure ta ba, ya koma gidansa"
ɗan jami'in na kwatanta yanayin da ke iya faru wa soja. AT: "don, idan ya mutu a yaƙi, wani mutum zai aure ta a maimakon shi"
Musa ya cigaba da kwatanta yanayin da ke sa mutum barin soja.
"Idan wani wani soja na jin tsoro kuma ba jarumin ba, ya koma gidansa"
Waɗannan kalmomin a takaice na nufin abu ɗaya. AT: "jin tsoron fada a yaƙi"
AT: "kada wani ɗan Isra'ila ya ji tsoro kaman shi"
A nan "zuciya" na wakilcin ƙarfin hali.
"dole shugabaninnin su naɗa mutane su zama jarumai, su kuma shugabanci mutanen Isra'ila"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Anan "garin" na wakilcin mutanen. AT: "Sa ad da kun je kai hari wa mutanen garin"
"ba mutanen garin loƙacin sallamar"
A nan "ƙofofi" na nufin garuruwa. Jimlar "buɗe muku ƙofofinsu" na wakilcin mutanen da sun sallamar sun kuma bar Isra'ilan su shiga. AT: "bar ku ku shiga garin ku da salama"
AT: "dukka mutanen a garin"
"dole su zama bayinku"
A nan "idan" na nufin garuruwan da na wakilcin mutanen. AT: "Amma idan mutanen garin ba su sallamar ba" ko "Amma idan mutanen garin ba su karbi salamar ku ba"
"yaran"
"da kuma dukka abubuwa masu daraja"
Waɗannan ne abubua masu daraja da mutanen da sun ci yaƙi ke ɗaukawa daga mutanen da suka kai masu hari.
A nan "garuruwa" na wakilcin mutanen. AT: "dukka mutanen da su na garurukan"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Irs'ila.
An yi maganan garuruka a kanaan da Yahweh zai ba wa mutanensa kaman garuruwan gadon mutanen ne.
"Kada ku bar wani abu mai rai ya rayu." AT: "ku kashe kowane abu mai rai"
"ku hallaka taron waɗannan mutanen gabaɗaya"
"Hallaka waɗannan al'umman don su"
"yi ayukan banƙyama kaman yadda mutanen waɗannan al'umman sun yi da allolinsu"
"Idan kun yi kaman waɗannan mutanen, za ku yi wa Yahweh Allahnku zunubi"
Musa ya cigaba da magana da mutanen isra'ila.
"yi yaƙi"
"ta wurin yanka itatuwan da gatari"
An yi wannan tambaya don a tuna wa mutanen game da abin ya kamata da sun sani. AT: "Gama itatuwa masu 'ya'ya ba mutane ba ne, su ba makiyanku ba ne."
"kun san cewa itatuwa ne ke ba da amfane don ci"
Waɗannan kayayyakin aiki da abubuwan da aka kafa kaman kuranga da hasumiya, da a na bukata a kewaye gari da yaƙi.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "sai mutanen garin sun rasa"
A nan "ta" na nufin garin wanda ke wakilcin mutanen garin.
1Idan aka iske an kashe wani a cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku ku mallaka, a kwance cikin gona, kuma ba a san wanda ya kai masa hari ba;2daganan sai dattawanku da alƙalanku su fita, dole su auna zuwa garuruwan da ke kewaye da shi wanda aka kashe.3Daganan dattawan garin da ke kusa da gawar mataccen dole su ɗauki karsana daga garke, wadda ba a taɓa aiki da ita ba, kuma ba a taɓa sa mata karkiya ba.4Daganan dole su jagoranci karsanar zuwa kwari inda ruwa ke gudu, kwarin da ba a noma ko shuka ba, kuma a can cikin kwarin zasu karya wuyar karsanar.5Sai firistoci, zuriyar Lebi, dole su zo gaba, domin Yahweh Allahnku ya zaɓe su su hidimta masa su kuma sa albarka a cikin sunan Yahweh su kuma dai-dai ta kowacce matsalar jayayya da cin mutunci ta wurin maganarsu.6Dukkan dattawan birni da ya fi kusa da mutumin da aka kashe dole su wanke hannuwansu a kan karsanar wadda aka karya wuyanta a cikin kwari;7kuma dole su amsa ga matsalar su ce, 'Hannayenmu ba su zubar da wannan jinin ba, idanunmu kuma ba su ga wanda ya zubar da shi ba.8Yahweh, ka gafarta, wa mutanenka Isra'ila, waɗanda ka fansa, kuma kada ka ɗora alhakin jinin mara laifin nan a tsakiyar mutanenka Isra'ila.' Daganan za a yafe masu zubar da jinin.9Ta haka zaku kawar da alhakin jinin mara laifi daga cikinku, sa'ad da kuka yi abin da ke dai-dai a idanun Yahweh.10Sa'ad da kuka fita yaƙi gãba da maƙiyanku Yahweh Allahnku kuwa ya baku nasara yasa su ƙarƙashin sarrafawarku, kuka kuwa ɗauke su a matsayin bayi,11idan a cikin bayinka akwai kyakkyawar mace, wadda ka yi sha'awarta kuma kana so ka ɗauke ta domin ta zama matarka,12daganan sai ka kawo ta gidanka; za ta aske kanta ta kuma yanke farshenta.13Daganan zata tuɓe tufafinta da take sawa sa'ad da aka ɗauko ta bauta zata kasance cikin gidanka tana makokin mahaifinta da mahaifiyarta wata guda cif. Bayan haka zaka iya kwana tare da ita ka zama mijinta, ita kuma ta zama matarka.14Idan ka ji baka jin daɗinta, daganan sai ka barta ta tafi wurin da ta ga dama. Amma kada ka yarda ka sayar da ita domin kuɗi, kada kuma ka wahalsheta kamar baiwa, saboda ka ƙasƙantar da ita.15Idan mutum yana da mata biyu sai ya nuna yana son ɗayar kuma ya ƙi ɗayar, kuma dukkansu sun haifa masa 'ya'ya - dukka da wadda ya ke ƙauna da wadda ya ke ƙi - idan ɗan farin na wadda ya ke ƙi ce,16daganan a ranar da zai sa 'ya'yansa su gãji abin da ya mallaka, kada yasa ɗan matar da ya ke ƙauna ya zama ɗan fari gaban ɗan matar da ya ke ƙi, wanda shi ne ainihin ɗan farin.17Maimakon haka, dole ya amince da wanda ya ke ɗan farin, wato ɗan matar da ya ke ƙi, ta wurin bashi kaso biyu na dukkan abin da ya mallaka; gama wannan ɗan shi ne farkon ƙarfinsa; haƙin ɗan fari nasa ne.18Idan mutum yana da gagararren ɗa kuma mai tayaswa wanda ba ya biyayya da maganar mahaifinsa ko maganar mahaifiyarsa, kuma wanda, koda shike sun kwaɓe shi, ba ya sauraron su;19daganan sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su cafke shi su kawo shi waje wurin dattawansu na birni kuma zuwa ƙofar birninsa.20Dole su ce da dattawan birnisa, 'Wannan ɗanmu ne gagararre ne kuma ɗan tayarwa; baya biyayya da maganar mu; shi mai zarin ci ne kuma mashayi.'21Daganan dukkan mutanen birni dole su jejjefeshi da duwatsu har ya mutu; ta haka zaku kawar da mugunta daga cikinku. Dukkan Isra'ila zasu ji suji tsoro.22Idan mutum ya aikata zunubin da ya isa mutuwa kuma aka kashe shi, kuma aka rataye shi a bisa itace,23daganan kada abar jikinsa ya kwana dukkan dare a kan itace, amma, dole ku tabbatar kun bizne shi a ranar; gama duk wanda aka rataye shi la'ananne ne ga Allah. Ku yi biyayya da dokar nan domin kada ku ƙazantar da ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku a matsayin gãdo.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
AT: "Idan wani ya sami mutum da wani dabam ya kashe"
mataccen mutumin na kwance a filin.
AT: "kuma babu wanda ya san wanda ya kai mai hari"
"za su auna nisan zuwa garururwan"
AT: "shi wanda wani ya kashe" ko "mataccen jikin"
"bai sa karkiya ba"
Wannan aƙrin magana ne na ruwan da ke motsi. AT: "rafi"
AT: "kwarin da babu wanin da ya nome ƙasan ko shuka iri"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"dole ya zo kwarin"
"domin firistocin ne wanda Yahweh Allahnku ya zaɓe su su yi masa aiki"
Musa ya yi magana da Isra'ilawa kaman ya na magana da mutum ɗaya ne.
"don su sa wa mutanen Isra'ila albarka"
A nan "a cikin sunan" na nufin Yahweh ko ikonsa. AT: "kaman wanin da yake ce da kuma aikata abin da Yahweh da kansa zai faɗa ya kuma aikata"
"saurara abin da firistocin za su ce"
A nan "maganarsu" na nufin abin da firistoci sun faɗa. AT: "saboda duk abin da firistocin sun ce, shi zai zama shawaran"
"duk loƙacin da mutane su na cikin kotun shariya don ba su yarda da junansu ba ko kuma wani ya yi wani rauni"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
AT: "karsanar wanda firistoci sun karya wuyanta"
"kuma ɗole su shaida wa Yahweh game da wannan"
A nan "hannu" ƙarin magana ne na dukkan mutum kuma "zub da wannan jinin" ƙarin magana ne na kashe mutum mai mara laifi. AT: "Ba mu kashe wannan mutum mai mara laifi ba"
A nan "idannu" na nufin dukkan mutum. AT: "kuma ba mu gan wanin da ya kashe wannan mutum ba"
Musa ya cigaba da gaya wa shugabanin abin da za su ce sa'ad da sun wanke hannunsu akan karsanar. Yi masu magana kaman ya na magana da mutum ɗaya.
An yi magana yadda Yahweh ya ceci mutanen Isra'ila daga bauta a Masar kaman Yahweh ya biya kuɗi don ya fanshe mutanen daga bauta.
AT: "kuma kada yi mutanenka Isra'ila kaman su na da lahakin kashen mutum mai mara laifi"
AT: "Sa'an nan Yahweh zai gafarta wa mutanen Isra'ila don mutuwar mutum mai mara laifi"
"ba za ku sake zama da alhakin kashen mutum mai mara laifi ba"
Kalmomin "a idanun Yahweh" ƙarin magana ne na "abin da Yahweh na tunani daidai ne."
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman ya na magana da mutum ɗaya.
"ku da kuke sojoji ku fita" (UDB)
Yi amfani da jimlar da ta dace wa "ka na so ka kuana da ita."
"so ka aure ta"
"za ta aske gashin kanta"
"yanke farcenta"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman ya na magana da mutum ɗaya.
Za ta yi wannan bayan mutumin ya kawo ta gidansa kuma a loƙacin da ta aske gashinta, da kuma ƙumbanta na hannu da kafa kaman yadda an ambata a cikin 21:10. AT: "za ta cire tufafin mutanenta ta kuma sa tufafin Isra'ila"
AT: "sa'ad da ya ɗauke ta"
"wata gabaɗaya"
Za ku iya sa a bayyane cewa mutumin na ƙwana da matan. AT: "Amma idan ka ƙwana da ita sai ka gan cewa ba ka son ta a matsayin matarka kuma ba"
"sake tata tafi duk inda take so ta tafi"
"domin ka kunyatar da ita ta wurin ƙwana da ita da kuma korinta"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
AT: 1) "kuma mutumin na kuanar ɗaya daga cikin matanshi, ya na kuma ƙin ɗayan matan" ko 2) "kuma mutumin na ƙaunar mata ɗaya fiye da yadda ya na ƙaunar ɗayan matan"
"kuma dukka matan su na da 'ya'ya da shi"
AT: "idan ɗan farin na matar da mutumin ke ƙi"
"sa'ad da mutumin"
"mutumin zai ba wa 'ya'yansa gadon mallakarsa"
"Ba zai yi wa ɗan matarso kaman shi ne ɗa na fari ba, a maimakon ɗan matar da an ƙi ta"
"da yawa sau biyu"
AT: "wannan ɗan ne mai nuna cewa mutumin zai iya zama mahaifin 'ya'ya"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
A nan "murya" ƙarin magana ne na abin da mutum ya ce. AT: "wanda ba zai yi biyayya da abin da mahaifinsa ko mahaifiyarsa sun ce"
"sun hukunta don mumunan ayukansa" su na horad da kuma umurta shi"
"dole a tilasa shi ya fita"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"Dan mu"
A nan "murya" ƙarin magana ne na abin da mutum ya ce ko ƙarin magana da dukkan mutum. AT: "ba zai yi abin da mun ce masa ya yi ba" ko "ba zai yi biyayya da mu ba"
mutum mai ci da sha dayawa
mutum mai shan barasa ɗayawa kuma na yawan buguwa
"jajjefe masa duwatsu har sai ya mutu"
AT: "dole mu cire daga cikin Isra'ilawa mutum mai aikata wannan mugun abu" ko "dole ku kashe wannan mugun mutum"
Kalmar "Isra'ila ƙarin magana ne na mutanen Isra'ila. AT: "Dukka mutanen Isra'ila"
AT: "za su ji game da abin da ya faru da ɗan, su kuma ji tsoron cewa mutanen za su hukunta su"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"idan mutum ya yi abu mai muni sosai da ya kai na hukunta shi ta kashe shi"
AT: "ku kashe shi"
AT: 1) "kuma bayan ya mutu, sai ku rataye shi a kan itace" ko 2) "kuma za ku kashe shi ta rataye shi akan itace"
binnne a ranar da kun kashe shi"
At: 1) "domin Allah ya la'anta duk wanda mutane sun rataye a kan itace" ko 2) "mutane na rataye waɗanda Allah ya la'anta a kan itace."
ta wurin barin wani abin da Allah ya la'anta a rayae a kan itace
1Kada ku kalli sã ko tunkiyar ɗan'uwanku Ba-isra'ile yana ɓacewa ku ƙyale su; dole ku tabbatar kun dawo da su ga maishi.2Idan ɗan'uwanku mutumin Isra'ila ba ya kusa daku, ko idan baku sanshi ba, daganan dole ku kawo dabbar wurinku a gidanku, za ta kasance tare daku har lokacin da ya zo neman ta, daganan dole ku mayar masa da ita.3Dole kuyi irin haka da jakinsa, dole kuyi haka ga rigarsa; dole kuyi haka da kowanne abin da ya ɓace na ɗan'uwanku Ba-isra'ile, duk abin da ya ɓata kuka tsinta; lallai ba zaku ɓoye kanku ba.4Ba zaku ga jaki ko san ɗan'uwanku Ba-isra'ile ya faɗi a hanya ku ƙyale su ba; dole ku tabbatar kun taimake shi tawurin sake ɗaga shi sama.5Kada mace ta sanya abin da ya shafi suturar maza, kuma kada namiji ya sanya suturar mata; gama duk wanda ya yi waɗannan abubuwa abin ƙyama ne ga Yahweh Allahnku.6Idan kuna tafiya a kan hanya sai kuka ga sheƙar tsuntsu, a kan kowanne itace, ko a ƙasa, da 'ya'yansa ko ƙwayaye a ciki, uwar kuma na kwance a kan 'ya'yan ko a kan ƙwayayen, kada ku kama uwar duk da 'ya'yan.7Ku tabbatar uwar ta tafi, amma zaku iya kwashe 'ya'yan domin kanku. Ku yi biyayya da dokar nan domin ku sami zaman lafiya ta haka kuma zaku tsawaita kwanakinku.8Sa'ad da kuka gina sabon gida, daganan dole ku ja rawani a rufin domin kada ku jawo wa gidanku alhakin jini idan wani ya faɗi daga can.9Kada ku shuka iri biyu a gonar inabinku, domin kada wuri mai tsarki ya karɓe dukkan amfaninku, irin da kuka shuka da kuma amfanin gonar inabinku.10Kada ku haɗa sa da jaki suyi huɗa tare.11Kada ku sanya rigar da aka saƙa da ulu garwaye da lilin.12Dole kuyi wa kanku geza a kusurwoyi huɗu na suturar da kuke suturta kanku.13Idan mutum ya ɗauki mace, ya kwana da ita, daga nan ya ƙi ta,14kuma yana zarginta da yin abubuwan kunya ya sanya mummunar shaida akan ta, ya ce, 'Na ɗauki wannan mace, amma sa'ad da na yi kusa da ita, Na iske babu shaidar budurci a cikinta.'15Daganan sai mahaifinta da mahaifiyar yarinyar su kawo shaidar budurcinta gaban dattawa a ƙofar birni.16Mahaifin yarinyar zai cewa dattawan, 'Na bada 'yata aure ga wannan mutum, amma ya ƙi ta.17Duba, ya zarge ta da abubuwan kunya har ya ce, 'Ban sami ɗiyarka da shaidar budurci ba.' Amma ga shaidar budurcin 'yata.' Daganan zasu shimfiɗa ƙyalle a gaban dattawan birni.18Sai dattawan garin su kama wannan mutumin su hukunta shi;19kuma zasu yi masa tarar awo ɗari na azurfa, su bada su ga mahaifin yarinyar, saboda mutumin ya bada mummunar shaida ga budurwa a Isra'ila. Dole ta zama matarsa; ba shi da iko ya sallame ta dukkan kwanakin ransa.20Amma idan wannan gaskiya ne, cewa ba a ga shaidar budurci a cikin yarinyar ba,21daganan dole su kawo yarinyar a ƙofar gidan mahaifinta, daganan mutanen garin dole su jejjefeta da duwatsu har ta mutu, saboda ta aikata abin kunya a cikin Isra'ila, ta aikata karuwanci a cikin gidan mahaifinta; ta haka za ku kawar da mugunta a cikinku.22Idan aka iske mutum yana kwana da matar wani, dukkansu biyu dole su mutu, wato mutumin da ke kwana da matar da matar kanta; ta haka zaku kawar da mugunta daga cikinku.23Idan akwai yarinyar da ke budurwa, da wani ke tashinta, sai wani mutum ya iske ta cikin gari ya kwana da ita,24ku ɗauki dukkansu biyun zuwa ƙofar birni, a jejjefe su su mutu. Dole ku jejjefe yarinyar da duwatsu, saboda bata yi kururuwa ba, koda shike tana cikin gari. Dole ku jejjefe mutumin, saboda ya ɓata matar maƙwabcinsa; kuma dole ku kawar da mugunta daga cikinku.25Amma idan mutumin ya iske yarinyar a cikin gona, idan ya ɗauke ta da ƙarfi ya kwana da ita, daga nan mutumin kaɗai daya kwana da ita za a kashe.26Amma ga yarinyar ba za ayi mata kome ba; domin bata yi zunubin da ya cancanci mutuwa ba. Gama wannan matsalar na dai-dai da mutumin da ya fãɗa wa maƙwabcinsa ya kashe shi.27Gama ya same ta a cikin gona; ita wadda ake tashinta ta yi kururuwa, amma ba wanda zai cece ta.28Idan mutum ya iske yarinya wadda take budurwa amma ba a tashinta, idan ya kama ta da ƙarfi ya kwana da ita, idan aka gane su,29shi mutumin da ya kwana da ita dole ya biya shekel hamsin na azurfa ga mahaifin yarinyar, kuma dole ta zama matarsa, saboda ya ƙasƙantar da ita. Ba zai sallame ta ba dukkan kwanakin ransa.30Kada mutum ya ɗauki matar mahaifinsa a matsayin matarsa; kada kuma ya ɗauke 'yancin auren mahaifinsa.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"ƙwace daga mai shi"
AT: "yi kaman ba ku gan su ba" ko "tafi ba tare da yin wani abu ba"
"Idan ɗan Isra'ila na zama da nisa da kai"
"ko idan ba ku san mai dabban ba"
"kuma dole ku ajiye dabban da ku sai mai shi ya zo neman ta"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"Haka nan ɗole ku mai da masa jajinsa"
"Haka nan ɗole ku mai da masa suturansa"
AT: "kada ku yi kaman ba ku gan cewa ya batar da wani abu ba" ko "kada ku tafi ba tare da yin wani abu ba"
"dole ku taimake ɗan'uwanku ɗan Isra'ila ta da dabban tsaye"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"tufafin maza"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
gidan da tsuntsaye ke yi wa kansu daga itace, ciyawa, shuka da kuma taɓo
"da 'ya'yan tsuntsaye ko ƙwai a cikin shekan"
kuma uwar tsuntsun ta na zaune akan 'ya'yan tsuntsayen"
Tsawon kwanaki ƙarin magana ne na tsawon rai. AT: "yin rayuwa na tsawon loƙaci." Fasara waɗannan kalmomin kamar yadda suke a cikin 4:25.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
ƙaramin shinge a kewaye da gefen jinka don kada mutane su faɗi daga jinkan
Jini alama ce na mutuwa. AT: "don kar ya zama laifin gidanku idan wani ya mutu"
"idan wani ya fadi daga jinkan don ba ku yi rawani ba"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Kalmomin "wurin mai tsarki" ƙarin magana ne wa firistocin da suke aiki a cikin wuri mai tsarkin. AT: "don kada firitocin cikin tsarkaken wurin Yahweh su ɗauke dukka girbin" ko "don kada ko kazantar da dukka girbin, kuma kada firistocin su bar ku ku yi amfani da shi"
"kuma amfanin da ke girma a gonan inabi"
gashi da ta nade, da laushi, da na girma a tumakai
zare da ake yi daga shuka
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
"tundu" (UDB). Waɗannan zare ne da ana hadawa a kuma rataye daga karshen kowane gefen mayafi.
doguwar riga da mutum ke sa akan wasu tufafinsa
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"sai kuma ya yi zargin da cewa ta kusanci wani kafin ta yi aure"
AT: "ya sa sauran mutane su yi tunani cewa ita mugun mutum ne"
Wannan wata hanya ne da ta dace na ce "yin jima'i da wani." AT: "amma da na kusance ta"
AT: "ba ta iya nuna mani cewa ita budura ce ba"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
AT: "dole su ɗauke wani abin da ya shaida cewa ita budurwa ce"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
AT: "ya yi zargin cewa ta ƙwana da wani kafin ya aure ta"
AT: "yarinyar ku ba ta iya ba da shaidar cewa ita budurwa ce ba"
AT: "Amma wannan ya shaida cewa wannan yarinyar mu budurwa ce"
Ana iya sa a bayyane wannan cikakken bayanin. AT: "Sai mahaifiyarta da mahaifinta za su nuna tufafin da tabon jinin wa dattawan don shaida cewa ita budurwa ce"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"kuma dole su sa shi ya biya a matsayin hukunci"
"kuma ba da ƙuɗin wa mahaifin yarinyan"
AT: "ya sa mutane yin tunanin cewa budurwan Isra'ila bacecen mutum ne"
"kada ku bar shi ya sake ta"
AT: "wa dukkan rayuwarsa"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"Amma idan gaskiya ne" ko "Amma idan abin da mutumin ya ce gaskiya ne"
AT: "cewa mutumin bai samu shaidan cewa yarinyar budurwa ce ba"
AT: "ani abin da ya nuna cewa yarinyan budurwa ce"
"dole dattawan za su fitar da yarinyan"
"jajjefe ta da duwatsu sai ta mutu"
"domin ta yi abin kunya a Isra'ila"
"yi kamar karuwa sa'ad da ta ke zama a gidan mahaifin ta"
AT: "dole ku cire daga Isra'ila, mutumin da ke yin wannan mugun abu" ko "dole ku kashe wannan mugum mutum"
Musa na magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
AT: "Idan wani ya same mutum"
"a haka za ku cire" (dubi UDB)
Musa na magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne.
"wanda aka yi alkawarin auren ta da wani mutmu"
Ana ba da waɗannan umurnin wa taron Isra'ila don haka, jam'i ne.
"sai dole ku kawo macen da mutumin da ya kwana da ita"
"domin ba ta yi kira don taimako ba"
Isra'ila a wannan loƙacin su na ɗaukan mutum da macen da suke tashin juna, mata da miji. Ana iya sa a bayyane wannan cikakken bayanin. AT: "domin ya kwana da 'yar Isra'ila"
AT: "dole ku cire daga cikin Isra'ila, mutum mai yin wannan mugun abu" ko "dole ku kashe wannan mugun mutum"
Wannan na nufin yarinyar da mahaifinta sun yarda ta aure wani mutum, amma yarinyar ba ta riga ta aure shi ba.
"sai za ku kashe mutumin da ya kwana da ita kadai"
"kada ku hukunta ta ta wurin kashen ta don abin da ta yi ba"
"Domin wannan yanayin na nan ne kaman yanayin da wani ya kai hari wa wani mutum ya kuma kashe shi"
"Domin mutumin ya same yarinyar ta na aiki a filin"
"wanda mahaifinta ba su yi wa wani mutum alkawarin cewa za ta aure shi ba"
AT: "kuma idan wani yi san abin da ya faru"
Skekel na ɗaukan gram sha ɗaya. AT: "azurfa hamsin" ko "gram na azurfa ɗari biyar da hamsin"
AT: "Kada ya ta sakin ta a muddin ransa"
AT: "kada ya aure matar mahaifinsa, ko ba ita ce mahaifiyarsa ba"
1Ba mutumin da aka yi wa rauni ta wurin dandaƙa ko yanke gabansa da zai shiga taron jama'ar Yahweh.2Shegen ɗa ba zai shiga taron jama'ar Yahweh ba; har tsara ta goma ta zuriyarsa, ba mutum a cikinsu da zai kasance a taron jama'ar Yahweh.3Ba'ammone ko Bamowabe ba zai zama cikakken mutum a taron jama'ar Yahweh ba; har tsara ta goma ta zuriyarsu, ba wani a cikinsu da zai shiga taron jama'ar Yahweh ba.4Saboda basu zo sun tarye ku da abinci da ruwa ba sa'ad da kuke kan hanyarku lokacin da kuka fito daga Masar, kuma suka yi hayar Bala'am ɗan Beyor daga Fetor cikin Aram Naharayim, ya la'anta ku.5Amma Yahweh Allahnku bai saurari Bala'am ba; sai Yahweh Allahnku ya juyar da la'anar ta zama albarka dominku, saboda Yahweh Allahnku yana ƙaunarku.6Kada ku taɓa nemar musu zaman lafiya ko wadata, lokacin dukkan kwanakinku.7Kada kuji ƙyamar Ba'idome, gama shi ɗan uwanku ne; kada ku ƙi Bamasare, domin kunyi baƙunci a cikin ƙasarsa.8Zuriyarsu tsara ta uku da aka haifa masu zasu iya shiga taron jama'ar Yahweh.9Sa'ad da kuka fita domin ku kafa sansani gãba da maƙiyanku, daganan dole ku kiyaye kanku daga kowanne mugun abu.10Idan a cikinku akwai wani mutum daya ƙazantu saboda abin da ya faru da shi da dare, daganan dole ya fita daga cikin sansanin; kada ya komo cikin sansanin.11Sa'ad da yamma ta yi, dole ya yi wanka cikin ruwa; sa'ad da rana ta faɗi, sai ya dawo cikin sansani.12Dole ku kasance da wani wuri kuma a bayan sansani in da zaku je;13kuma sai ku kasance da wani abu cikin kayanku da zaku yi gini da shi; sa'ad da kuka tsuguna domin kuyi bayan gari, dole kuyi gini da shi daganan sai ku mayar da ƙasar ku rufe bayan garin da kuka yi.14Gama Yahweh Allahnku yakan yi yawo cikin sansaninku ya baku nasara ya kuma bada maƙiyanku cikin hannunku. Domin haka dole sansaninku ya kasance da tsarki, domin kada ya ga abu mara tsarki a cikinku ya juya daga gare ku.15Kada ku bada bawan da ya tsere daga ubangijinsa.16Ku bar shi ya zauna tare daku, a cikin kowanne garin da ya zaɓa. Kada ku tsananta masa.17Kada a sami ko ɗaya daga cikin 'yan'matan Isra'ila, ko 'ya'yansu maza a cikin ƙungiyar karuwanci na addini.18Kada ku kawo kuɗin da aka samu ta wurin karuwanci ko kuɗin da aka samu tawurin yin luɗu a cikin haikalin Yahweh Allahnku domin cika kowanne wa'adi; gama dukkan wannan abin ƙyama ne ga Yahweh Allahnku.19Kada ku bada bashi da ruwa ga danginku Ba-isra'ile - ribar kuɗi, ribar abinci, kona kowanne irin abu da akan bada shi da ruwa.20Ga wanda ya ke baƙo zaku iya bashi rance da ruwa, domin Yahweh Allahnku yasa maku albarka a kan dukkan abin da kuka sa hannunku ga yi, a cikin ƙasar da zaku shiga ku mallake ta.21Sa'ad da kuka yi wa'adi ga Yahweh Allahnku, kada kuyi jinkirin cikawa, gama Yahweh Allahnku lallai zai neme shi gare ku; zai zama zunubi a gare ku idan baku cika shi ba.22Amma idan kuka nisanci yin wa'adi, ba zai zama zunubi gare ku ba.23Duk abin da ya fita daga cikin leɓunanku dole ku kula ku aikata; bisa ga yadda kuka alƙawarta ga Yahweh Allahnku, duk abin da kuka alƙawarta da yaddar ranku da bakinku.24Sa'ad da kuka shiga cikin gonar inabin maƙwabcinku, zaku iya cin inabin 'ya'yan inabin yadda kuke so har ku ƙoshi, amma kada ku sa ko ɗaya a cikin kwandonku.25Sa'ad da kuka shiga cikin hatsin maƙwabcinku daya nuna, zaku iya tsinke kawunan hatsin da hannunku, amma kada ku sa lauje ku yanki hatsin maƙwabcinku da ya nuna.
"mutumin da an yanka ko murkushe wasu gabobin jikinsa na siri"
AT: "na iya zama cikakken ɗan Isra'ila"
AT: 1) ɗan da kak haifa wa iyayen da sun yi zina ko lalata ko 2) ɗan da an haifa wa karuwa.
AT: "ko bayan tsara ta goma na zuriyar ɗan shegen"
"ko ɗayan waɗannan zuriyan"
AT: "ba za su zama cikakken ;yan Isra'ila ba"
AT: "ko bayan tsara goma na zuriyarsa"
AT: "ba su marabce ku ta wurin kawo maku abinci da ruwa ba"
Musa ya yi magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne.
AT: "ba da hankali ba"
"sa shi ya albarkace ku ba kuma la'anta ku ba"
AT: 1) "Kada ku yi yarjejeniya da Ammoniyawa da Moabites" ko 2) "Kada ku yi komai da zai sa abubuwa su yi kyau wa waɗannan mutane biyunhar su ci gaba" (UDB).
AT: "tun da ku al'umma ce"
Musa ya cigabada magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"Kada ku ƙi Ba'edome"
"domin shi danginku ne"
Kada ku ƙi Bamasare"
Ana iya sa cikakken wannan bayanin a bayyane. AT: "Idan Ba'edome ko Bamasare ya zo zama a cikin jama'an Isra'ila, jikokinsa za su iya zama cikakken mutanen wannan garin"
A nan Musa ya yi magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne.
"yi faɗa da makiyanku"
"kiyaye kanku daga mugayen abubuwa"
Wannan wata hanar ladabi ne na faɗa cewa ya yi watsin maniyyi. AT: "duk mutum da ke da kazanta don ya yi watsin maniyyi a loƙacin da yake barci"
Musay na magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"kuma ku sami kayan aikin da za ku iya amfani a tonon"
Wannan wata hanya ne n ce najasa. AT: "sa'ad da kun tsuguna yin najasa"
"ku tona rami da kayan aikin"
"ruffe tukar tumbinku"
"don kada Yahweh ya gan abin ƙyama a cikinku"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne.
AT: "bawan daga wata ƙasa da ya tsere daga ubangijinsa sai ya zo Isra'ila" (Dubi: )
"Ku bar bawan ya zauna a cikin mutanenku"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne.
Yahweh ya ba da cikakken tsarin irin karuwanci na maza da mata don ya haramta karuwanci don kowane dalili.
AT: 1) haramta a bayyane mata da maza a yin jima'i kamar hidimar haikali ko 2) ya yi amfani da ƙarin magana don ya haramta mata da maza a yin jima'i don kuɗi.
"Macen da ta na samu kuɗi a kuruwanci ba za ta kawo wannan kuɗin ... cikin gidan ba"
mutum da ya na barin mutane su kwana da shi don kuɗi
"cikin haikalin"
"don a cikan alwashi"
ladan aikin karuwa na mace da karuwa na miji.
Musa na magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"Idan kun ba da rancen wani abu wa ɗan Isra'ila ɗan'uwanku, kada ku sa shi ya biya fiye da abin da ya ranta"
ba wana ranci da kuma tilasa mutumin ya biya fiye da abin da aka ara masa
"kada ku karbi riba idan kun ba da rancen kuɗi, abinci ko wani abu wa wani"
AT: "dukka abin da ku na yi"
Musa na magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"kada ku ɗauki tsawon loƙaci a cika wa'adinku"
"domin Yahweh Allahnku zai ba ku laifi ya kuma hukunta ku idan ba ku cika wa'adinku ba"
AT: "Amma, idan ba ku yi wa'adi ba, ba za ku yi zunubi ba domin ba ku da wa'adin da za ku cika"
AT: "Maganan da kun ce"
"duk abin da ku ka yi wa'adi wa Yahweh Allahnku cewa za ku yi"
"duk abin da mutane sun ji kun alkawarta ku yi don kun so ku yi"
"don mutane su ji kun ce"
Musa na magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum ɗaya ne.
"sai za ku iya jin dadnin cin inabin sai kun koshi"
AT: "amma kada ku sa wani inabin a cikin jakanku ku tafi da shi"
"Sa'ad da ka yi tafiya a cikin filin maƙwabcinku inda akwai hatsin da ke girma"
"sai za ku iya cin kwayan hatsin da hannunku"
"amma kada ku yanka hatsin maƙwabincku da ya nuna ku tafi da shi"
kaifi ne da manoma ke amfani da shi a girba alkama
1Idan namiji ya ɗauki mata ya aure ta, idan bata sami tagomashi a idanunsa ba saboda ya sami wani abin aibatarwa da ita, sai dole ya rubuta mata takardar saki, yasa a hannunta, ya sallame ta daga gidansa.2Sa'ad da ta fita daga gidansa, zata iya ta tafi ta zama matar wani.3Idan mijinta na biyun ya ƙi ta ya kuma rubuta mata takardar saki, yasa mata a hannunta, ya kuma sallame ta daga gidansa; ko kuma mijinta na biyun ya rasu, wato mutumin daya ɗauke ta ta zama matarsa -4sai mijinta na dã, wannan na farko wanda ya fara sallamar ta, ba zai koma ya ɗauke ta ta zama matarsa kuma ba, bayan ta rigaya ta ƙazamtu; domin wannan zai zama abin ƙyama ga Yahweh. Ba zaku sa ƙasar ta zama da laifi ba, ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku abin gado.5Lokacin da namiji ya ɗauki sabuwar mata, ba zai tafi yaƙi da sauran mayaƙa ba, ba za a kuma umarce shi ya tafi ya yi aikin ƙarfi da yaji ba; yana da 'yanci ya zauna a gida har shekara guda ya faranta wa matarsa da ya aura rai.6Kada wani ya karɓi jinginar dutsen niƙa ko ɗan dutsen niƙa, domin wannan zai zama karɓar ran mutum ne jingina.7Idan an kama wani ya saci ɗan'uwansa daga cikin mutanen Isra'ila, ya mai da shi kamar bawa ya saida shi, wannan ɓarawon dole ya mutu; haka zaku kawar da mugunta daga tsakaninku.8Ku kula game da annobar kuturta, domin ku aikata dai-dai a kowace ka'ida da aka baku, wanda firistoci, da lebiyawa, suka koya maku; kamar yadda na umarce su, haka zaku yi.9Ku tuna da abin da Yahweh Allahnku ya yi wa Maryamu sa'ad da kuke fitowa daga Masar.10Sa'ad da ka ranta wa makwabcinka wani irin abu, ba zaka shiga cikin gidansa ka ɗauko jinginar ba.11Zaka tsaya a waje, sa'an nan mutumin nan daka ba shi rance zai fito waje ya baka jinginar.12Idan mutumin matalauci ne, kada jinginarsa ta kwana a hannunka.13Hakika dole zaka mayar masa da jinginarsa kafin faɗuwar rana, domin ya yi barci cikin mayafinsa yasa maka albarka; zai zama adalci dominka a gaban Yahweh Allahnka14Ba zaka zalumci bawanka ɗan ƙwadago matalauci fakiri ba, ko shi ɗan'uwanka Ba'isra'ile, ko daga baƙi waɗanda ke cikin ƙasarku cikin ƙofofin biranenku;15Dole kowacce rana ka bashi albashinsa; kada rana ta faɗi baka cika wa'adin nan ba, domin matalauci ne zuciyarsa tana kan hakinsa. Kayi wannan domin kada ya yi kuka gãba da kai ga Yahweh, kuma domin kada ya zama zunubin daka aikata.16Ba za a kashe iyaye saboda 'ya'yansu ba, haka ma 'ya'ya ba za a kashe su saboda iyayensu ba. Maimakon haka, dole ne kowa ya mutu domin nasa zunubin.17Ba zaka fizgi adalci daya cancanta karfi da yaji daga baƙo ba, ko maraya, ko ka ɗauki mayafin gwauruwa don jingina.18Maimakon haka, zaku tuna ku bayi ne dã a Masar, kuma Yahweh Allahnku ya kuɓutar daku daga can. Saboda haka ina umartar ku kuyi biyayya da wannan doka.19Sa'ad da kuka girbe amfaninku daga gonakinku, idan kuka manta da dami guda a gonar, kada ku koma domin ku ɗauko shi; dole zai zama domin baƙo, domin marayu, domin gwauruwa, saboda Yahweh Allahnku ya albarkace ku a cikin dukkan aikin hannuwanku.20Sa'ad da kuka kakkaɓe itacen zaitunku, kada ku koma ku rore rassansu, zai zama domin baƙo, da marayu da, kuma gwauruwa.21Sa'ad da kuka tattara 'ya'yan inabin garkarku, ba zaku yi kalarta kuma ba. Abin da aka bari baya zai zama na baƙo, na marayu, dana gwauruwa.22Dole ne ku tuna dã ku bayi ne a cikin ƙasar Masar. Saboda haka ina umartarku kuyi biyayya da wannan doka.
Musa ya cigaba da magana da mutanin Isra'ila.
Wannan maganar "ɗauki mata" da "aure ta" na nufin abu ɗaya. AT: "Sa'dda namiji ya auri mace"
A nan "a idanunsa" na nufin dukkan mutumin. AT: "idan ya yanke shawarar cewa ba ya son ta kuma"
"saboda wasu dalilai, ya yanke shawarar cewa ba ya so ya rike ta"
"dole ya ba matarsa takardar cewa ba su tare kuma"
"zata iya tafiya ta aure wani mutum"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila game da macen da ta sami saki ta kuma aure wani mutum.
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
"Idan mijin na biyun ya yanke shawarar cewa ya ƙi matan"
Wannan takarda ce na faɗa cewa babu aure a sakanin mutumin da matan. Fasara wannan kamar a 24:1.
"ba wa matan"
"mutumi na biyu da ya aure matan"
A na iya sa wannnan maganar a bayyane. AT: "bayan ta rigaya ta ƙazamtu ta wurin saki da kuma sake aure da wani mutum"
An yi maganar ƙasar kamar na iya yin zunubi. AT: "Kada ku baza laifi a aƙsar"
Musa na kan magana da mutanen Isra'ila.
"Lokacin da namiji ya yi sabuwar mata"
AT: "kada wani ya tilasa shi ya yi nisa da gidansa, ya kuma yi kowane irin aiki ba"
"zai sami 'yanci ya zauna a gida "
Karfen niƙa da ake niƙa gari a sakanin duwatsu biyu.
saman dutsen niƙa
Kalamar "rai" magana ne na abin da mutum ke bukata ya bar kansa da rai. AT: "domin za a ɗauka daga mutumin, abin da mutumin ke bukata don yin abinci wa iyalinsa"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana ne na "Idan mutum ya sace." AT: "Idan kun sami mutum na sata"
yin amfani da ƙarfi don a ɗauki mutum mara laifi daga gidansa a kuma ɗaure shi
"wani ɗan'uwansa ɗan Isra'ila
"sai wasu Isra'ilawan su ƙashe ɓarawon, a matsayin hukuncin don abin da ya yi"
AT: "kuma dole ku kawar da mugunta daga cikin Isra'ilawa, mutumin da ya yi wannan muguntan" ko "dole ku ƙashe wannan mugun mutum"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
"Ku yi hankali idan kun sha wahala daga kuturta" ko "ku yi hankali idan ku na da kuturta"
AT: "dukka ka'idodin da na baku kuma da firistoci, wanda suke Lebiyawa, ke koya maku"
Musa na magana da Isra'ilawa kamar taro ne, don haka, duk misalan kalmar "ku" jam'i ne.
"dole ku tabatar cewa kun yi abin da na umarce su"
Kalmar "su" na nufin firistoci,su Lebiyawa.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "Tuna"
"a loƙacin da ku ke barin Masar"
Musa ya yi magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne, don haka, kalmomin "ku" jam'i ne.
Sa'ad da ka ranta wa makwabcinka wani abu"
"ɗauko jinginarsa"
Wannan magana ne na "abin da ya yi alkawarin cewa zai ba ku idan be biya rancen ba"
"Ku jira a wajen a gidansa"
Musa ya yi magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne, don haka, kalmomin "ku" jam'i ne.
"kada ka ajiye rigansa ya ƙwana"
Wannan magana ne na "abin da ya yi alkawari cewa zai ba ka idan bai biya racen ba" Fasara kamar yadda kun yi a 24:10.
"mayar masa da abin da ya ba ka, don ya nuna cewa zai biya rancen"
Ana iya sa wannan maganan a bayyane. AT: "domin ya sami mayafinsa don ya rufe kansa, zai kuma goɗe maka"
Mayafi ko tufafin da ke sa mutum yi ji dumi da dare. Mai yiwuwa wannan ne "jingina" da Musa na magana akai a cikin 24:10
"Yaweh Allahnku zai amince da yadda kun yi da wannan magana"
Musa ya yi magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne, don haka, kalmomin "ku" jam'i ne.
"Kada ka yi wa bawanka ɗan ƙwadago mugunta"
mutumin da a na biyansa kullum don aikinsa
Waɗannan kalmomin na da ma'ana iri ɗaya kuma na nanata cewa wannan ne mutumin da ba zai iya taimakon kansa ba.
A nan "ƙofofin biranen" na nufin garuruka ko birane. AT: "a ɗaya daga cikin biranenku"
"Dole ka ba mutumin ƙudin ladan aikin da ya samu ko wane rana"
Wannan ƙarin magana ne. Isra'ilawa na ganin farwar sabon ranan a loaƙcin da rana ta faɗi. AT: "ka biya mutumin a ranar da ya yi aikin"
AT: "domin matalauci ne kuma ya sa zuciyarsa a kan hakinsa don ya saya abincinsa don gaba"
"kada ya kira Yaweh, ya ce mashi ya hukunta ka"
AT: "Kada ku ƙashe iyayen saboda wani mumunan abu da wani 'yaran sun yi"
AT: "Kada ku ƙashe'ya'yan saboda wani mumunan abu daiyayensu sun yi"
AT: "ku ƙashe mutum saboda mumunan abin da ya yi da kansa"
Musa ya yi magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne, don haka, kalmomin "ku" jam'i ne.
Musa ya yi maganar adalci kamar wani abu ne da mutum mai ƙarfi na iya amfani ya kwace daga mutuma mai mara ărfi. AT: "Kada ku yi wa baƙo ko maraya rashin adalci"
Wannan na nufin 'ya'yan da iyayensu sun mutu duka kuma basu da dangin da za su kula da su.
Mai ba da rance na karban wani abu daga mai karban rancen domin a tabatar cewa za ta biya shi. Ba a yarda masa ya karbi mayafinta, saboda ta na bukatan shi don ta ji dumi. AT: "kuma kada ka karbi mayafin gomruwa a jingina, saboda tana bukatarsa don ta ji dumi"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "Tuna"
Musa ya yi magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne, don haka, kalmomin "ku" jam'i ne.
"Sa'ad da kuka yanke amfaninku a gonakinku"
amfanin da mai girbin ya ɗaura
AT: "dole ku bar dami domin baƙo, ko maraya, ko gwauruwa ya iya ɗauka"
A nan "hannuwa" na nufin dukkan mutum. AT: "a dukkan aikin da kuke yi"
AT: "Sa'ad da kuka kakkaɓe itacen inabinku, sa inabin su zuba a ƙasa don ka iya ɗaukansu"
"kada ku ɗauka dukka zaitun daga itacen"
AT: "amfanin da suke itacen inabin za su zama na baƙi, da marayu, da kuma gwauraye don su ɗauka su tafi da su"
Musa ya yi magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne, don haka, kalmomin "ku" jam'i ne.
"'ya'yan da ba ku ɗauka ba zai zama na bao, marayu, kuma gwauruwan za ta dauka"
Wannan na nufin taron mutuane. AT: "wa baƙo, wa marayu, ko na gwauruwa"
Wannan arin magana ne. AT: "Tuna"
1Idan akwai jayayya tsakanin mutane sai suka tafi kotu, sai al'ƙalai suka shari'anta su, zasu kuɓutar da mai adalci su hukunta mugun.2Idan mai laifi ya cancanci dukã, sai al'ƙali yasa shi ya kwanta ayi masa bulala a gabansa iya ƙididdigar bugun, daya dace da laifinsa.3Al'ƙali zai iya yi masa bulala arba'in, amma ba zai zarce wannan lambar ba; gama idan ya zarce lambar nan ya bulale shi da abin da yafi haka yawa, to za a ƙasƙantar da ɗan'uwanku Ba'isra'ile a kan idanunku.4Ba zaku sa wa san da ke casar hatsi takunkumi ba.5Idan 'yan'uwa maza suna zaune tare sai ɗayan ya rasu, kuma bashi da ɗa, ba za a aurar da matar marigayin ba ga wani a waje wanda baya cikin iyalin. Maimakon haka, dole ɗan'uwan miji marigayi ya kwana da ita ya ɗauke ta ta zama matarsa, ya yi mata abin da ya kamaci ɗan'uwan miji ya yi mata.6Wannan ya zama haka domin ɗan farin da zata haifa zai ci gaba da sunan ɗan'uwa marigayi, domin kada sunansa ya ɓace a Isra'ila.7Amma idan mutumin baya so ya ɗauki matar ɗan'uwansa, sai matar ɗan'uwan ta tafi ƙofa wurin dattawa ta ce, 'Ɗan'uwan mijina yaƙi ya wanzar da sunan ɗan'uwansa a Isra'ila; ba zai yi abin da ya kamaci ɗan'uwan miji ya yi mani ba.'8Dole sai dattawan birnin su kira shi suyi masa magana. Amma idan yaƙi ya ce, 'bana so in ɗauke ta.'9Dole matar ɗan'uwansa ta je wajensa a gaban dattawa, ta cire takalminsa daga ƙafarsa, ta tofa masa miyau a fuskarsa. Zata amsa masa ta ce, 'Wannan shi ne abin da ake yi wa wanda yaƙi gina gidan ɗan'uwansa.'10Za a kira sunansa a Isra'ila, 'Gidan wandan aka saluɓe takalminsa.'11Idan mutane suka yi faɗa da junansu, sai matar ɗaya daga cikinsu ta zo ta kuɓutar da mijinta daga hannun wanda ya mare shi, idan ta miƙa hannuta ta kama gabansa,12sai dole a yanke hannunta; kada idonku ya ji tausayi.13Ba zaku riƙe ma'aunan nauyi iri biyu a jakarku ba, da babba da ƙarami.14Ba zaku ajiye a cikin gidanku ma'aunai iri biyu ba, da babba da ƙarami.15Sai ku kasance da ma'aunin nauyi da ya ke dai dai; mudu na adalci zaku kasance da shi, domin kwanakinku suyi tsawo a cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ke baku.16Domin duk masu yin irin abubuwan nan, duk waɗanda ke aikata rashin gaskiya, abin ƙyama ne ga Yahweh Allahnku.17Ku tuna da abin da Amalek suka yi maku a hanya sa'ad da kuka fito daga Masar,18yadda suka gamu daku a hanya suka fãɗa wa na bayanku, dukkan marasa ƙarfi na bayanku, sa'ad da kuka some kuka gaji; bai girmama Allah ba.19Saboda haka, sa'ad da Yahweh Allahnku zai baku hutawa daga dukkan maƙiyanku da kewaye, a cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ya ke baku ku mallaka abin gado, ba zaku manta cewa dole ku shafe tunawa da Amalek daga ƙarƙashin sama ba.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
AT: "Idan al'ƙalin ya umarce su su duke mutum mai laifin"
AT: "kuma zai gan su su na dukanshi"
"lumbar ƙididdigar da ya umarta saboda mugun ayukan da ya yi"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"Al'ƙalin na iya cewa su yi wa mai lafin bulala so arba'in"
"amma Al'ƙalin ba zai umurce su su bulale shi fiye da arba'in ba"
"saboda idan Al'ƙalin ya umurce su su bulale shi fiye da arba'in"
AT: "Sai Al'ƙalin zai ƙasƙantar da ɗan'uwanku Ba'isra'ile a gaban dukka mutanen Isra'ila"
A nan, "a gabanku" na nufin abin da za su gani. AT: "ƙasƙantar, kuma za ku gani." Kalmomi irin wannan sun bayyana a 1:7
"Kada ku sa wani abu akan bakin sa"
sa'ad da yake ware hatsi daga ɓuntu ta wurin tafiya akai ko jan itace mai nauyi
Musa na kan magana da mutanen Isra'ila.
AT: 1) "Idan 'yan'uwa su na zama akan dukiya ɗaya" ko 2) "Idan 'ya'uwa su na zama kusa da juna."
AT: "sai kada iyalin marigayin su bar gwauruwan ta aure wani dabam"
"kuma ya yi abin da ɗan'uwan marigayi ya kamata ya yi"
Kalmar "suna" magana ne na zuriyar mutumin. AT: "zai cigaba da zuriyar marigayin"
Kalmar "suna" magana ne na zuriyar mutumin. AT: "domin kada zuriyarsa ya ɓace daga Isra'ila"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
AT: "dole ta je ƙofan garin, wurin da dattawan ke hukunci"
A nan "suna" na nufin tuni na wani ta wurin zuriyarsa. AT: "ya ƙi ya ba ɗan'uwansa ɗa"
"ba zai yi abin da ya kamaci ɗan'uwan miji ya kamata ya yi, ya kuma aure ni"
"ban so in ɗauke ta ba"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
"dole ta je kusa da shi, da dattawan a wurin su na gani"
A nan "gida" magana ne na iyali. AT: "wanda bai ba ɗan'uwansa ɗa, ya kuma cigaba da zuriyar ɗan'uwansa ba"
"Mutane a Isra'ila za su san iyalinsa kamar"
A nan cire takalmar, ya nuna cewa ɗan'uwan ba zai ƙarbi wani dukiyan marigayi ɗan'uwansa ba. AT: "Gidan shi wanda takalmarsa, gwauruwar ɗan'uwansa ta saluɓe a kafansa" ko "Iyalin da kowa ke kushe" ko "Iyalin da ya kunyata"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawa kamar su mutum ɗaya ne.
A nan "hannu" na nufin ƙarfi ko iko. AT: "sai wanda ya mare shi ba zai mare shi kuma ba" ko "daga mutumin da ya buga shi"
A nan "ido" na nufin dukkan mutum. AT: "kada ku ji tausayinta" ko "kada ku nuna mata yafewa"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawa kamar su mutum ɗaya ne.
AT: "Kada ku yaudare mutane da amfani da nauyin da ta fi abin da kun faɗa, sa'ad da kun saya abubuwa da kuma amfani da ƙaramin nauyi a loƙacin da ku na sayar da abubuwa"
Nauyi duwatsu ne da ana amfani a daidaita abu
AT: "Kada ku yaudare mutane ta wurin amfani da babban ma'aunai fiye da kun ce yake a loƙacin da kun saya abubuwa da kuma amfani da ƙaramin ma'aunai da ta fi ƙarami fiye da kun ce a loƙacin da ku na sayar da abubuwa"
Ma'auni kwando ne ko wani abu na auna yadda abu yake
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila game da amfani da nauyi da kuma ma'aunai a loƙacin saya da sayarwa. Ya na magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
"daidai da adalci"
Fasara waɗannan kalmomin kamar yadda yake a 25:13.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "za ku iya rayuwa na tsawon loƙaci"
"domin duk wanda yi yaudare mutane ta wurin amfani da nauyi da ma'aunai dabam dabam"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawa kamar su mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana ne, "Amalek" magana ne na mutanen Amalekiyawa. AT: "Ku tuna da abin da Amalekiyawan sun yi maku"
"yadda suka gamu da ku a hanya"
"suka fãɗa wa mutanenku da suke bayanku"
"dukka mutanen da basu da ƙarfi a baya"
Waɗannan na da ma'ana irin ɗaya kuma na nnuna yadda mutanen sun gaji. AT: "gaji"
AT: "bai ji tsoron hukuncin Allah ba" ko "bai yi wa Allah biyayya ba"
"dole ku ƙashe dukka Amalakiyawan domin kar wani ya tuna da su kuma"
1Sa'ad da kuka zo ƙasar da Yahweh Allahnku ke ba ku abin gãdo, kuma lokacin da kuka mallaƙeta kuka zauna cikinta,2sai dole ku ɗauki nunan farinku na dukkan girbin ƙasar wanda kuka kawo cikin gida daga ƙasar da Yahweh Allahnku ke baku. Dole kusa shi a kwando ku je inda Yahweh Allahnku zai zaɓa a matsayin haikalinsa.3Dole za ku je wajen firist wanda shi ne mai hidima a kwanakin nan kuce masa, 'Ina shaida yau ga Yahweh Allahnka cewa nazo ƙasar da Yahweh ya rantse wa kakanninmu zai bamu.'4Dole firist zai karɓi kwandon daga hannunsa ya ajiye shi a gaban bagadin Yahweh Allahnku.5Dole ku faɗi haka a gaban Yahweh Allahnku, 'Kakana mayawacin Ba'aramiye ne. Ya gangara zuwa cikin Masar ya zauna a can, kuma mutanensa kima ne. A can ya yi girma, ya ƙasaita, kuma ya zama al'umma mai jama'a.6Masarawa suka wulaƙanta mu ainun suka tsananta mana. Suka bautar da mu.7Muka yi kuka ga Yahweh, Allah na ubanninmu, ya kuma ji muryarmu, ya dubi azabarmu da wahalarmu, da zalumtarmu da aka yita yi.8Yahweh ya fitar da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi, da damtsensa miƙaƙƙe, da babbar razanarwa, da alamu da kuma al'ajibai;9ya kuma kawo mu nan wajen ya kuma bamu wannan ƙasar, ƙasa wacce take zuba da madara da zuma.10Duba yanzu, na kawo maka nunan fari na girbin ƙasar da kai, Yahweh, ka bani.' Dole ka ajiye shi a gaban Yahweh Allahnka kayi sujada a gabansa;11kuma dole kayi farinciki cikin dukkan abubuwa nagari da Yahweh Allahnka ya yi dominka, da kuma gidanka - da kai. da kuma Lebiyawa, da baƙon da ke tsakiyarku.12Bayan kun gama bada dukkan zakkarku ta girbi a shekara ta uku, wato, shekara ta zakka, dole ne kuba Lebiyawa, da baƙo, da maraya, da kuma gwauruwa, domin su ci a ƙofofin biranenku su kuma ƙoshi.13Dole ku ce a gaban Yahweh Allahnku, 'Na kawo waɗannan daga cikin gidana abubuwan da suke na Yahweh, na kuma ba Lebiyawa, da baƙo da maraya, da kuma gwauruwa, bisa ga dukkan umarnai waɗanda ka bani. Ban kuskure ko kaɗan ba daga umarnanka, ban kuma manta da su ba.14Ban ci ko kaɗan daga cikinsu a cikin baƙin cikina ba, ban kuma aje su a wani wuri marar tsarki ba, ko in miƙa su don girmama matacce. Na saurari muryar Yahweh Allahna; Nayi biyayya da dukkan abin da ka umarce ni in yi.15Ka duba daga wuri mai tsarki inda kake zaune, daga sama, ka albarkaci mutanenka Isra'ila, da ƙasar daka bamu, kamar yadda ka rantse wa ubanninmu, ƙasa wadda take zuba da madara da zuma.'16Yau, Yahweh Allahnku yana umartarku kuyi biyayya da ka'idodinsa da dokokinsa; saboda haka za ku kiyaye su zaku yi biyayya da su da dukkan zuciyarku da kuma dukkan ranku.17Kun furta yau cewa Yahweh shi ne Allahnku, zaku kuma yi tafiya a tafarkunsa ku kuma kiyaye ka'idodinsa, da umarnansa da dokokinsa, cewa kuma zaku kasa kunne da muryarsa.18Yau Yahweh ya furta cewa ku mutane ne waɗanda mallakarsa ce, kamar yadda ya alƙawarta maku, cewa zaku yi biyayya da dukkan umarnansa,19zai fifita ku sama da dukkan sauran al'umman da ya yi, zaku kuma sami yabo, da suna, da daraja. Zaku zama mutanen da aka keɓe su ga Yahweh Allahnku, kamar yadda ya faɗi."
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum daya ne.
"wasu nunan fari na girbin" ko "wasu amfanin fari na dukkan girbin."
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum daya ne.
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila kaman su mutum daya ne.
Wannan ne farkon maganan da dan Isra'ila zai yi sa'ad da ya na kawo kwaundonsa.
Wannan na nufin Yakub, wanda shi ne kakan dukka Isra'ilawa. Ya yi zama na shekaru dayawa a Aram-Nairam, yankin da ke Siria.
"ya kuma yi sauran rayuwansa a wurin"
Kalmar "ya" magana ne na "zuriyar Yakub."
Waddannan kalmomin a takaice na nufin abu ɗaya. Su na nanata cewa Isra'ila ya zama babba da kuma al'umma mai ƙarfi.
Wannan ya cigaba da abin da ya kamata Ba-Isra'ilan zai ce sa'ad da ya kawo nunan farinsa wa Yahweh.
Waɗannan jimloli biyun a takaice na nufin abu ɗaya. Su na nanata cewa Masarawan sun yi tsanani.
A nan "mu" na nufin mutanen Isra'ila da sun yi zama a Masar. Mai maganan ya hada da kansa kamar ɗaya daga cikin mutanen ko ya yi zama a Masar ko bai yi ba.
A nan "murya" na nufin dukkan mutum da kukansa ku addu'o'i. AT: "ya ji muryarmu" ko "ya ji addu'o'inmu"
"wai Masarawan su na azabantar da mu, mu na yin ayuka masu wahalla, da kuma wai Masarawan su na zalumtarmu"
Wannan ya cigaba da abin da ya kamata Ba-Isra'ilan zai ce sa'ad da ya kawo nunan farinsa wa Yahweh.
A nan "mu" na nufin na nufin mutanen Isra'ila da sun yi zama a Masar. Mai maganan ya hada kansa da kaman ɗaya daga mutanen ko ya na zama a Masar ko babu.
A nan " babban hannu" da "da damtsensa miƙaƙƙe" magana ne na ƙarfin Yahweh. AT: "ta wurin nuna ikonsa." 4:34.
"da ayuka da ke tsorata mutanen da sun gan su"
Wannan ƙarin magana ne. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 6:3. AT: "ƙasar da madara ɗayawa ke zuba" ko "ƙasar da ke da ƙyau ma dabbobi da noma"
Musa ya cigaba da faɗa wa Isra'ilawa abin da ya kamata ya ce sa'ad da zai kawo nunan farinsa wa Yahweh. Ya yi masu magana kaman su mutum ɗaya ne.
"'ya'yan nunan fari" ko "amfanin nunan fari"
"Dole ku shirya kwaundon a kasa."
" dole ka yi murna da godiya domin dukkan ƙyauwawan abubuwan da Yahweh Allahnka ya maka"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne.
Kowane shekaru uku, mutanen Israli su na ba da zakkansu wa tallakawa.
Waɗannan 'ya'ya ne da iyayensu sun mutu kuma ba su da ɗangin da za su kulla da su.
Wannan na nufin macen da mijinta ya mutu kuma ba ta da yaran da za su kulla da ita yanzun da ta tsufa.
A nan "ƙofofi" na nufin birane garuruka. AT: "don waɗanda suke cikin biranenku su iya samu abinci ɗayawa su ci"
Waɗannan kalmomi wani maganan ne da ya kamata Isra'ilawan su ce.
Wannan na nufin cewa ya yi biyayya da umarnen Allah.
Wannan ya cigaba da abin da ya kamata Ba-Isra'ilan zai ce sa'ad da ya kawo nunan farinsa wa Yahweh.
"Ban ci ko kaɗan daga zakkan a loƙacin baƙin cikina ba"
A nan "tsarki" na nufin mutumin ba shi da tsarki bisa ga doka. Allah ba ya barin mutum mai mara tsarki ya taba zakkan da zai ba Allah. AT: "a loƙacin da ba ni da tsarki bisa ga doka" ko " a loƙacin da dokan ya ce ba zan iya taba ba"
A nan "muryar Yahweh" magana ne na abin da Yahweh ya faɗa. Su na da ma'ana iri ɗaya. Su na nanata cewa mutumin ya yi biyayya da dukkan umarnen Allah.
AT: "daga sama, tsarkakan wurin zamanka"
Wannan ƙarin magana ne, Dubi yadda kun fasara wannan a 6:3. AT: "ƙasar da madara ɗayawa da zuma ke zuba" ko "ƙasar da na da ƙyau ma dabbobi da noma"
Musa na magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
Ƙarin maganar "da dukkan ... zuciya" na nufin "gaba ɗaya." Su na da ma'ana iri ɗaya. AT: "da dukkan ranku" ko "da dukkan ƙarfinku." Fasara wannan a kamar yadda kun yi a 4:29.
Kalmomin "tafiya," kiyaye," da "saurara" na da ma'ana iri ɗaya. A nan "murya" na nufin abin da Allah ya ce. AT: "cewa za ku yi biyayya da koman da Yahweh ya umarta gabaɗaya"
Musa na magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
"mutanen da sun zama nasa"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "zai sa ku zama da daraja fiye da" ko "zai ɗaukaka ku fiye da"
AT: 1) "zai sa ku ku fi duk wani al'umma da ya kafa, kuma zai sa ku ku yaɓe shi ku kuma girmama shi" (UDB) ko 2 "zai sa mutane su yaɓe ku fiye da yadda suke yaɓon kowane al'umman da ya yi; mutane za su ce wai kun fi sauran al'umman, kuma za su girmamaku."
An yi maganar zaɓen mutanen Isra'ila da Yahweh ya yi don su zama na shi a hanya mai ƙyau kaman Yahweh ya keɓe su daga dukka sauran al'umma. AT: "Yahweh Allahnku zai keɓe ku daga sauran al'ummai"
1Musa da dattawan Isra'ila suka umarci mutanen suka ce, "Ku kiyaye dukkan umarnan dana umarce ku yau.2A ranar da zaku tsallake Yodan zuwa ƙasar da Yahweh Allahnku ke baku, sai dole ku kafa manyan duwatsu ku shafe su da farar ƙasa.3Dole ne ku rubuta a kansu dukkan maganganun dokokin nan sa'ad da kuka rigaya kuka ƙetare; domin ku tafi cikin ƙasar da Yahweh Allahnku ke baku, ƙasa mai zubar da madara da zuma, kamar yadda Yahweh, Allahn kakanninku ya yi maku alƙawari.4Sa'ad da kuka ƙetare Yodan, ku kafa waɗannan duwatsu da nake umartanku yau, a kan Dutsen Ibal, ku shafe su da farar ƙasa.5A can zaku gina bagadi ga Yahweh Allahnku, bagadi na duwatsu; amma ba zaku yi amfani da alatu na ƙarfe ku sassaƙa duwatsun ba.6Dole ku gina wa Yahweh Allahnku bagadin da ba a sassaƙa duwatsun ba. Dole ku miƙa baye-baye na ƙonawa a kansa ga Yahweh Allahnku,7zaku miƙa hadayar baye-baye na zumunci ku kuma ci a can; zaku yi farinciki a gaban Yahweh Allahnku.8Zaku rubuta dukkan waɗannan maganganu na wannan dokoki a kan duwatsu su fita a fili sosai."9Musa da firistoci, da Lebiyawa, suka yi magana da dukkan Isra'ilawa suka ce,10"Kuyi shuru ku saurara, ya Isra'ila: Yau kun zama mutanen Yahweh Allahnku. Saboda haka dole kuyi biyayya da muryar Yahweh Allahnku ku kuma yi biyayya da umarnansa da dokokinsa waɗanda nake umartan ku yau."11Musa ya umarci mutanen a ranan nan ya ce,12"Waɗannan kabilu dole su tsaya a kan Dutsen Gerizim su albarkaci mutane bayan kun ƙetare Yodan: Simiyon, da Lebi, da Yahuda, da Isakar, da Yosef, da kuma Benyamin.13Waɗannan su ne kabilun da dole su tsaya a kan Dutsen Ibal su furta la'anu: Ruben, da Gad, da Ashar, da Zebulun, da Dan da kuma Naftali.14Lebiyawa zasu amsa su cewa dukkan mutanen Isra'ila da murya mai ƙafi:15Bari mutumin ya zama la'ananne wanda ya siffanta ko ya yi zubin ƙarfe, abin ƙyama ga Yahweh, aikin hannun gwanin masassaƙi, wanda ya kafa shi a asirce.' Dole ne dukkan mutane su amsa su ce, 'Amin.'16'Bari mutumin ya zama la'ananne wanda bai girmama mahaifinsa da mahaifiyarsa ba.' Daganan dole ne dukkan mutane su ce, 'Amin.'17'Bari mutumin ya zama la'ananne wanda ya cire shaidar iyakar makwabcinsa.' Daganan dole ne dukkan mutane su ce, 'Amin.'18Bari mutumin ya zama la'ananne wanda yasa makaho ya saki hanya.' Sai dole mutanen su ce,; Amin.'19Bari mutumin ya zama la'ananne wandan karfi da yaji ya ƙwace adalci daga baƙo, maraya, ko gwauruwa.' Daganan dole ne dukkan mutane su ce. 'Amin.'20'Bari mutumin nan ya zama la'ananne wanda ya kwana da matar mahaifinsa, domin ya karɓe hakkin mahaifinsa.' Daganan sai dukkan mutane su ce, 'Amin.'21'Bari mutumin nan ya zama la'ananne wanda ya kwana da kowacce irin dabba.' Daganan dole ne dukkan mutane su ce, 'Amin.'22'Bari mutumin nan ya zama la'ananne wanda ya kwana da 'yar'uwarsa, ɗiyar mahaifinsa, ko ɗiyar mahaifiyarsa.' Daganan dukkan mutane dole su ce, 'Amin.'23'Bari mutumin nan da zai kwana da surukarsa ya zama la'ananne.' Daganan dukkan mutane dole su ce, 'Amin.'24Bari mutumin nan ya zama la'ananne wanda ya kashe makwabcinsa a ɓoye.' Sai dole dukkan mutane su ce, 'Amin.'25'Bari mutumin nan ya zama la'ananne wanda zai karɓi toshiya domin ya kashe da mutum marar laifi.' Sai dole dukkan mutane su ce, 'Amin.'26'Bari mutumin nan ya zama la'ananne wanda ba zai yi biyayya da shariɗun nan ba.' Sai dole dukkan mutane su ce, 'Amin.'
Musa na magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
Musa na magana da Isra'ilawan kaman taro ne.
A nan "Na" na nufin Musa. Dattawan su na tare da Masu, amma shi ne kadai ke magana.
Farar ƙasan hadi ne na tsami, kasa da kuma ruwan da ake baza a wani abu. Ya na bushewa, ya kuma yi arfi, sa wuri laushi don mutum ya iya rubutu. AT: "baza farar kasa akansu" ko "yi su don ku iya rubutu a kansu"
Wannan karin magana ne. Dubi yadda an fasara wannan a cikin 6:3. AT: "ƙasa ne mai zuba da madara dayawa da zuma" ko "ƙasa mai kyau ma dabbobi da noma"
Musa na magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
Musa na magana da Isra'ilawan kaman taro ne.
"baza farar kasa akansu" ko "yi su don ku iya rubutu a kansu" Fasara wannan kaman yadda yake a cikin 27:1.
Wannan dutse ne ke kusa da Shekem. Dubi yadda kun fasara a 11:29.
Wannan na nufin kurfi da zai sa duwatsun laushi, don su zama daidai. AT: "ba za ku shirya duwatsun bagadin da alatun karfe ba"
Musa na magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
duwatsun da babu wanda ya ya sassaƙa da alatu na ƙarfe
Wannan na nufin duwatsun da an kafa a Dutsen Ibal an kuma rufe da farar ƙasa. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 27: 1 da 27:4
Musa na magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
A nan "muryar Yahweh"na nufin abin da ya faɗa. AT: "yi biyayya da abin da Yahweh Allahnku ya faɗa"
Musa ya na umartawa. Lebiyawan su na wurin tare da Musa, amma shi kadai ne na magana.
A nan "kabilu" na nufin mutane daga kabilan Simiyon, da Lebi, da Yahuda, da Issakar, da Yosef, da kuma Benyamin. AT: "Mutane daga wannan kabilun"
Ƙaramin dutse da ke arewancin Dutsen Ibal. Fasara kamar yadda yake a 11:29.
Wannan ya hada kabilan Efraim da Manasse, wanda su ne zuriyar Yusuf.
Fasara wannan kamar yadda yake a 11:29.
"faɗa a murya mai ƙarfi yadda Yahweh zai la'anta Isra'ila"
Wannan ne maganan da Lawiyawan za su faɗa wa duka mutanen Isra'ila. AT: "Bari Yahweh ya la'anta mutumin"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "wani abin da mutum ya yi"
mutumin da ya iya yin abubuwa da ƙyau
Musa ya cigaba da gayawa Lebiyawan da mutanen abin da ya kamata su faɗa.
AT: "Bari Yahweh ya la'anta mutumin"
AT: "wanda ya ƙwace gonan makwabcinsa ta wurin cire shaidar iyakan sa"
Musa ya cigaba da gayawa Lebiyawan da mutanen abin da ya kamata su faɗa.
AT: "Dubi yadda kun fasara wannan a 27:16. AT: "Bari Yahweh ya la'anta mutumin"
Musa ya yi maganan adalci kamar abu ne da mutum mai ƙarfi na iya ja da ƙarfi daga mutum mai mara ƙarfi. Harshenku na iya samin kalma ɗaya da ke nufin "yi amfani da ƙarfi a ƙwace." Kalmomi irin waɗannan sun bayyana a 24:17. AT: "yi wa ɓako ... gwauruwa rashin adalci"
Waɗannan 'ya'ya ne da iyayensu sun mutu kuma ba su da dagin da za su kulla da su.
Wannan na nufin matar da mijinta ya mutu kuma ba ta 'ya'yan da za su kulla da ita a tsofanta.
Musa ya cigaba da gayawa Lebiyawan da mutanen abin da ya kamata su faɗa.
AT: "Dubi yadda kun fasara wannan a 27:16. AT: "Bari Yahweh ya la'anta mutumin"
Wannan ba ya nufin mahaifiyar mutumin, amma wata matar mahaifinsa.
Idan mutum ya aure mata, shi ne kadai ke da izinin kwana da ita. AT: "ya karɓe hakin mahaifinsa"
AT: "wanda ya kwana da kowacce irin dabba kamar yadda mutum na kwana da mace"
Musa ya cigaba da gayawa Lebiyawan da mutanen abin da ya kamata su faɗa.
AT: "Dubi yadda kun fasara wannan a 27:16. AT: "Bari Yahweh ya la'anta mutumin"
Wannan na nufin na miji ba zai iya kwana da 'ya'uwarsa ba, ko ta na da mahaifiya ko mahaifi dabam.
Musa ya cigaba da gayawa Lebiyawan da mutanen abin da ya kamata su faɗa.
AT: "Dubi yadda kun fasara wannan a 27:16. AT: "Bari Yahweh ya la'anta mutumin"
Musa ya cigaba da gayawa Lebiyawan da mutanen abin da ya kamata su faɗa.
AT: "Dubi yadda kun fasara wannan a 27:16. AT: "Bari Yahweh ya la'anta mutumin"
1Idan kuka saurari muryar Yahweh Allahnku da kirki domin ku kiyaye dukkan dokokin nan da nake umartan ku yau, Yahweh Allahnku zai fifita ku fiye da dukkan sauran al'umman duniya.2Dukkan waɗannan albarku zasu zo bisanku har ma suyi amabaliya, idan kuka saurari muryar Yahweh Allahnku.3Zaku zama da albarka cikin birni, kuma zaku zama da albarka a jeji.4'Ya'yanku zasu zama da albarka, ƙasarku zata zama da albarka wajen bada amfani, da'ya'yan dabbobinku, shanunku zasu yi yabanya, haka ma 'ya'yan tumakinku.5Kwandunanku zasu zama da albarka, haka ma wurin kwaɓar wainarku.6Zaku shiga da albarka, ku fita da albarka.7Yahweh zai sa maƙiyanku da suka tashi gãba daku a buge su a gaban ku; zasu tasar maku ta gefe guda amma zasu gudu daga gaban ku ta hanyoyi bakwai.8Yahweh zai umarta albarka ta zo bisanku a cikin rumbunanku, kuma da cikin dukkan abin da kuka sa hannunku; zai albarkace ku a cikin ƙasar da ya ke ba ku.9Yahweh zai kafa ku a matsayin mutanen daya keɓe domin kansa, kamar yadda ya rantse maku, idan kuka kiyaye umarnan Yahweh Allahnku, kuma kuka yi tafiya a hanyoyinsa.10Dukkan al'umman duniya zasu ga ana kiranku da sunan Yahweh, zasu kuwa ji tsoronku.11Yahweh zai azurta ku ainun, da 'ya'yan jikinku, da 'ya'yan shanunku, da amfanin ƙasa, a ƙasar da ya rantse wa ubanninku zai baku.12Yahweh zai buɗe maku rumbunsa na sammai ya baku ruwa domin ƙasarku a dai-dai lokaci, ya kuma albarkaci dukkan aikin hannuwanku; zaku ranta wa al'ummai da yawa, amma ku ba zaku karɓi rance ba.13Yahweh zai saku zama kai, ba wutsiya ba; zaku kasance kullum a bisa, ba a ƙasa ba, idan kun kasa kunne ga umarnan Yahweh Allahnku da nake umartanku yau., domin ku lura ku yi su,14kuma idan baku juya daga waɗannan maganganu da nake umartanku a yau, ga hannun dama ko hagu ba, har da zaku bi waɗansu alloli ku bauta masu.15Amma idan baku saurari muryar Yahweh Allahnku, kuka kiyaye dukkan umarnansa da ka'idodinsa da nake umartan ku yau ba, to dukkan waɗannan la'anu zasu afka maku su mamayeku.16La'anannu zaku zama cikin birni, la'anannu zaku zama a jeji.17La'ana za ta bi kwandonku da kuma makwabar wainarku.18'Ya'yanku zasu zama la'anannu, amfanin gonakinku zasu zama la'anannu, da 'yan maruƙanku da 'ya'yan garken tumakinku.19La'anannu ne ku sa'ad da kuka shiga, la'anannu ne ku sa'ad da kuka fita.20Yahweh zai aiko maku la'ana, ruɗewa, da kwaɓa a dukkan abin da kuka ɗibiya hannunku, har sai kun lalace har sai kun hallaka nan da nan sabili da miyagun ayyukanku ta yadda kuka yashe ni.21Yahweh zai sa annoba ta manne maku har sai ya hallaka ku daga ƙasar da kuke tafiya zuwa cikin ta ku mallaka.22Yahweh zai buge ku da annobai masu yaɗuwa, zazzaɓi, da marurai, da fãri, da zafin rana, da iska mai ƙuna, da kuturta. Waɗannan zasu runtume ku har sai kun hallaka.23Samaniyar da ke kanku zata zama tagulla, ƙasar kuma da ke ƙarƙashinku zata zama ƙarfe.24Yahweh zai maida ruwan saman ƙasarku gari da ƙura; daga sammai zasu sabko kanku, har sai kun hallaka.25Yahweh zai sa a buge ku a gaban maƙiyanku; za ku fita ta hanya guda gãba da su zaku guje daga gabansu ta hanyoyi bakwai. Za a yi ta kora ku gaba da baya cikin dukkan mulkokin duniya.26Gawawakinku za su zama abinci ga dukkan tsuntsayen sama da dabbobin duniya; ba wanda zai tsorata su su gudu.27Yahweh zai far maku da maruran Masar da gyambuna, da ƙusumbi, da ƙaiƙayi wanda ba za a iya warkar daku daga su ba.28Yahweh zai buge ku da ciwon hauka, da makamta, da rikicewar hankali.29Zaku yita lalubawa da tsakar rana kamar yadda makaho ya ke yi a duhu, ba zaku azurta ba a ayyukanku; kullum za ayi ta zalumtarku ana maku ƙwace, ba kuma wanda zai cece ku.30Zaku yi tashin matã, amma wani namiji zai ƙwace ta ya yi mata fyaɗe. Zaku gina gida amma ba zaku zauna a ciki ba; zaku noma garkar inabi amma ba zaku ji daɗin 'ya'yansa ba.31Za a yanka san nomanku a kan idanunku; amma ba zaku ci namansa ba; za a karɓe jakinku ƙiri ƙiri ƙarfi da yaji ba za a kuma mayar maku ba. Za a bada tumakinku ga magabtanku, ba ko ɗaya da zaku samu ya taimaka maku.32Za a bada 'ya'yanku maza da mata ga wasu mutane; idanunku zasu neme su dukkan rana, amma za su gaji da sa zuciya. Hannuwanku zasu yi rauni.33Girbin ƙasarku da dukkan wahalarku - wata al'ummar da baku santa ba zata cinye su; kullum za a zalumce ku a murƙushe ku,34haka zaku haukace tawurin abin da ya zama dole ku ga ya faru.35Yahweh zai bugi gyiwowinku da ƙafafunku da marurai wanda ba za a iya warkar daku daga su ba, daga tafin kafafunku har ƙolƙolin kanku.36Yahweh zai ɗauke ku da sarkin da zaku naɗa bisa kanku zuwa wata al'umma da baku santa ba, koku ko kakanninku; a can zaku yi sujada ga allolin itace da duwatsu.37Zaku zama ban tsoro, da karin magana, da gatse, cikin dukkan mutane inda Yahweh zai kora ku.38Zaku kai hatsi da yawa gona, amma zaku sami amfanin hatsin kaɗan, gama fãri zasu cinye su.39Zaku dasa garkunan inabi ku kuma noma su, amma ko kaɗan ba zaku sha ruwansu ba, ba ma zaku girbi 'ya'yansu ba, gama tsutsotsi zasu cinye su.40Zaku kasance da itatuwan zaitun a dukkan yankinku, amma ba zaku shafa ko ɗan man a jikinku ba, gama itatuwan zaitunku zasu zubar da 'ya'yansu.41Zaku haifi 'ya'ya maza da mata, amma ba zasu zama naku ba, gama zasu tafi bautar talala.42Dukkan itatuwanku da amfanin ƙasarku - fãri za su mamayesu.43Baƙon da ke tsakiyarku zai yi ta ƙaruwa fiye daku gaba gaba; amma ku zaku yi ta komawa baya baya.44Zai ranta maku, amma ku ba za ku ranta masa ba; shi zai zama kai, ku kuwa zaku zama wutsiya.45Dukkan waɗannan la'anu zasu afko kanku su bi ku su chafke ku har sai sun hallaka ku. Wannan zai faru domin ba ku saurari muryar Yahweh Allahnku ba, da zaku kiyaye umarnansa da farillansa daya umarce ku.46Waɗannan la'anu suna kanku a matsayin alamu da al'ajibai, da kuma kan zuriyarku har abada.47Saboda baku yi sujada ga Yahweh Allahnku tare da murna da farin cikin zuciya lokacin yalwarku ba,48domin wannan fa, zaku bauta wa maƙiyan da Yahweh zai aiko gãba da ku; zaku bauta masu da yunwa, cikin ƙishirwa, cikin tsiraici, da cikin talauci. Zai ɗibiya maku karkiyar ƙarfe a wuyanku har sai ya hallaka ku.49Yahweh zai aiko da wata al'umma gãba daku daga nesa, daga ƙarshen duniya, kamar yadda gaggafa takan fyauce abincinta, al'ummar da baku fahimci harshenta ba;50al'umma da fuskarta abin ban razana ne waɗanda bata ganin kwarjinin tsoffi ko ta nuna alfarma ga matashi.51Zasu cinye 'yan maruƙanku da amfanin ƙasarku har sai sun hallaka ku. Ba zasu bar maku hatsi ba, ko sabon ruwan inabi, ko mai, ko 'yan maruƙanku na shanu ko na tumaki, har sai sun saku ku lalace.52Zasu yi maku kwanto a dukkan ƙofofin biranenku, har sai tsararrun ganuwowinku masu tsayi sun faɗi a koina a ƙasarku, garu waɗanda kuka dogara a gare su. Zasu kafa maku dãga a dukkan ƙofofin biranenku a dukkan iyakar ƙasar da Yahweh Allahnku ya baku.53Zaku ci 'ya'yan da kuka haifa, naman 'ya'yanku maza da na 'ya'ya mata, waɗanda Yahweh Allahnku ya baku, a cikin kwanto da wahalai waɗanda maƙiyanku zasu ɗibiya maku.54Mutum mai taushin zuciya kuma mai kula da ke tare daku-zai ji kyashin ɗan'uwansa da matarsa da ya ke ƙauna, da dukkan yaransa da suka rage.55Ba zai ba ko ɗayansu naman 'ya'yan jikinsa da zai ci ba, domin ba abin da zai rage ya ci don kansa a cikin kwanto da wahalai da maƙiya suka ɗibiya maku a dukkan ƙofofin biranenku.56Mace mai taushin zuciya mai kula da ke a cikinku, wanda ba za ta kuskura ta aje tafin sawunta a ƙasa saboda taushin zuciya da kyakkyawan hali - zata ji kyashin mijinta da take ƙauna, da ɗanta, da ɗiyarta,57da sabon jaririnta da ya fito ta tsakanin ƙafafunta, da 'ya'ya waɗanda zata haifa. Zata cinye su a ɓoye domin babu abinci, a cikin kwanto da wahalai waɗanda maƙiyanku zasu ɗibiya maku a ƙofofin biranenku.58Idan ba ku kiyaye dukkan maganganun dokokin da aka rubuta cikin wannan littafi ba, domin ku girmama wannan suna mai ɗaukaka da banrazana, Yahweh Allahnku,59sai Yahweh ya tsananta annobarku, dana zuriyarku; za a yi maku manyan annobai, masu tsawon lokaci, cututuka masu azabtarwa, na dogon lokaci.60Zai sake maido da dukkan cututukan Masar bisa kanku waɗanda kuka ji tsoronsu; zasu manne maku.61Kuma kowacce cuta da annoba da ba a rubuta a wannan littafin shari'a ba, su kuma Yahweh zai kawo bisa kanku har sai kun hallaka.62'Yan kaɗan zaku ragu, koda shike dã kuna kamar taurarin sammai a yawa, saboda baku saurari muryar Yahweh Allahnku ba.63Kamar yadda dã Yahweh ya yi farinciki da yi maku kirki, ya riɓaɓɓanya ku, haka ma zai yi farinciki da saku ku lalace da kuma hallakar daku. Za a tumbuƙe ku daga ƙasar da kuke tafiya ku mallaka.64Yahweh zai warwatsar daku cikin dukkan al'ummai daga wannan bangon duniya zuwa wancan bangon duniya; a can za ku yi sujada ga allolin da baku taɓa sani ba, ko ku, ko kakanninku, allolin itace da dutse.65Ba zaku sami sakewa wurin waɗannan al'umman ba, kuma babu hutawa ga tafin ƙafafunku; maimakon haka, Yahweh zai baku a can zuciya mai fargaba, idanu marasa gani, da rai mai makoki.66Ranku zai kasance cikin shakka a gabanku; zaku zauna cikin tsoro kowanne dare da rana baku da tabbas ko kaɗan a dukkan rayyuwarku.67Da safe zaku ce, 'Ina ma maraice ne!' da maraice zaku ce, 'Ina ma safiya ce!' saboda da tsoro a zukatanku da abubuwan da dole idanunku su gani.68Yahweh zai dawo daku cikin Masar a jiragen ruwa, ta hanyar dana riga na faɗa maku, 'Ba zaku ƙara ganin Masar ba.' A can zaku miƙa kanku domin saye ga maƙiyanku bayi maza da mata, amma ba wanda zai saye ku."
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
A nan "muryar Yahweh Allahnku" na nufin abin da ya ce. AT: "ga abin da Yahweh Allahnku na ce"
"ku kuma yi biyayya"
Musa ya yi maganan kasancewa da daraja ko girma kamar na da tudu, akan dutse. AT: "daraja ku sosai" ko "girmama ku fiye da"
Musa ya kwatanta albarkun kaman mutum da zai kai masu hari ko ya bi ya kama su. AT: "Yahweh zai albarkace ku kamar haka, a hanyoyin da za su ba ku mamaki, kuma zai zama kaman ba za ku iya gudun albarkansa ba"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
AT: "Yahweh zai albarkace ku"
Wannan na nufin cewa Yahweh zai albarkace su a ko ina.
Wannan ƙarin magana na "Ya'yanku, amfaninku, da dukka dabbobinku" na nufin dukka abubuwan da Isra'ilawan sun daraja.
Wannan wata hanya ne na faɗa cewa Yahweh zai sa dabbobin Isra'ilawan su yi yawa su kuma yi ƙarfi. AT: "dukka dabbobinku tare da shanunkan da tumakan garkin"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
AT: "Yahweh zai albarkace ku"
Isra'ilawan su na amfani da kwandu a ɗaukan hatsi. "abin ƙwabar waina" tasa ne da ake amfani a kwaɓan hatsi a yi gurasa. AT: "duk abincin da kun noma da duk abincin da kuke ci"
Wannan na nufin duk ayukan da suke yi a duk inda sun je.
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
AT: "sa ku ci nasara da sojojin da su na harin ku"
" amma za su gudu daga gaban ku ta hanyoyi bakwai"
Wannan ƙarin magana ne. Anahin lambar na iya zama fiye ko kasa da bakwai. AT: "a hanyoyi dayawa"
Musa ya kwatanta albarkun Isra'ilawan kaman Yahweh na umarta mutum ya kai masu hari ba da zato ba. AT: "Sa'ad da Yahweh ya albarkace ku, za ku yi mamaki da yawan hatsin da kuke da shi a rumbunanku"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "a koman da ku ke yi"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
An yi maganar yadda Yahweh ya zaɓe mutanen Isra'ila don su zama nasa a hanyanr da ta dace kamar Yahweh ya sa su a wuri dabam da wurin da dukka al'ummai suke. AT: "Yahweh zai sa ku zama tsarkakun mutane da sun zama na shi"
A nan "kira da sunan Yahweh" na nufin na shi. AT: "Yahweh ya kira ku na shi"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana ne. Kalmomi irin waɗannan sun bayyana a 28:3. AT: "da 'ya'ya, dabbobi da amfanin gona."
Musa na maganan hadarin da ruwa ke zuwa kamar gini ne da ake ajiyar ruwan. AT: "hadari"
"a loƙacin da amfanin na bukatar sa"
Kalmar "hannu" magana ne na dukkan mutum. AT: "dukka aikin da ku ke yi"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
Wannan maganan ya nuna al'umman Isra'ila kaman dabba kuma na nufin cewa Isra'ilawan za su zama shugabane akan wasu al'ummai, ba kuwa bayi ba. Isra'ilan za su fi da iko, kuɗi da daraja.
Isra'ilawan za su yi shugabanci akan wasu amma ba za su samu wasun da za su shugabance su ba.
Musa na magana da dukka Isra'ilawan.
An yi maganar rashin biyayya wa Yahweh da kuma bautan wasu alloli kamar mutum ya juya ya kuma kwace daga kalmomin Yahweh. AT: "idan ba ku yi rashin biyayya da abin da ina umartanku yau ta wurin bautan wasu alloli ba"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
Musa a nan ya fara nuna la'anun da mutanen za su samu idan sun yi rashin biyayya.
A nan "muryar Yahweh" na nufin abin da Yahweh ya ce. AT: "abin da Yahweh Allahnku na faɗa"
Musa ya kwatanta la'anu kaman mutum da zai kai masu hari ko ya bi ya kama su. AT: "Yahweh zai la'anta ku kamar haka, a hanyoyin da za su ba ku mamaki, kuma zai zama kaman ba za ku iya gudun la'anansa ba"
Fasara kamar yadda ya ke a 28:1.
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
Waɗannan jimlolin sun bayyana a sura da suka wuce. Dubi yadda kun fasara yawancin waɗannan kalmomin a 28:3 da 28:5.
AT: "Yahweh zai la'antaku"
Wannan na nufin cewa Yahweh zai albarkacesu a koina. Fasara wannan kamar yadda yake a 28:3.
Isra'ilawan su na amfani da kwandu a ɗaukan hatsi. "abin ƙwabar waina" tasa ne da ake amfani a kwaɓan hatsi a yi gurasa. AT: "duk abincin da kun noma da duk abincin da kuke ci"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
Waɗannan jimlolin sun bayyana a sura da suka wuce. Dubi yadda kun fasara yawancin waɗannan kalmomin a 28:3 da 28:5.
AT: "Yahweh zai la'antaku"
Wannan ƙarin magana ne na "'ya'yanku, amfanin gonanku" Fasara kamar yadda yake a 28:3.
Wannan hanyoyi ne na faɗa cewa Yahweh zai sa dabbobin Isra'ila yawa da kuma ƙarfi. AT: "'ya'yan maruƙanku da 'ya'yan garken tumakinku"
Wannan na nufin dukka ayuka a kininan da sun tafi. Fasara kamar yadda yake a 28:5.
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
"masifa, tsoro, da takaici"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "a koman da ku na yi"
AT: "sai makiyanku sun hallaka ku"
A nan "ni" na nufin Yahweh.
"kasance akanku"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
"cututuka masu yaɗuwa da zazzaɓi za su sa ku rauni." Waɗannan dukka na nufin cututuka da ke sa mutane rauni su kuma mutu.
"da rashin ruwan sama"
abin da ke girma a amfanin gona, da na kuma sa su su ruba
Musa ya yi maganar mumunan abubuwan da za su faru da Isra'ilawan kamar su mutani ne ko dabbobi ne da za su bi Isra'ilawan. AT: "Za su ba ku azaba"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
Musa ya yi maganar yadda sammai za ta zama kamar tagulla domin ba za a yi ruwan sama ba. AT: "sammai ... ba za ta ba da ruwa ba"
Musa ya yi maganar yadda duniyar ta zama kamar ƙarfe domin babu amfanin gonan da za ta yi girma. AT: "babu abin da zai yi girma daga ƙasa"
"a maimakon ruwan sama, Yahweh zai aiko da hadarin ƙasa"
AT: "har sai ya hallaka ku"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
AT: "Yahweh zai sa maƙiyanku su buga ku"
Fasara kamar yadda yake a 28:7.
Wannan na nufin cewa Isra'ilawan za su ji tsoro da gigitawa su kuma gudu daga maƙiyansu. Dubi irin wannan kalmomin a 28:7. AT: "za ku guje a hanyoyi bakwai"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "a yawan hanyoyi dabam dabam"
AT: "Mutanen wasu al'umman za su kore ku daga wannan al'umma zuwa wacan"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
"cutar fata wanda na la'anta Masarawan"
Waɗannan cututuka dabam dabam ne na fata.
AT: "wanda babu wanda zai iya warkad da ku"
"Za ku zama kamar makafen da suke lalubawa a duhu ko da rana." Isra'ilawan za su sami mawuyancin loƙaci ko a loƙacin da kowa na jin dadi rayuwa.
"kullum mutane masu ƙarfi za su ta zalumtarku su kuma yi maku ƙwace"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
AT: "Zan ku gani sa'ad da wani na yanka sanku"
AT: "wani zai kwace jakinku kuma ba zai mayar ba"
AT: "Za ba da tumakinku ga maƙiyanku" ko "Zan bar maƙiyanku su kwace tumakinku"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
AT: "Zan ba da 'ya'yanku maza da mata ga wasu mutane" ko "Maƙiyan ku za su kwace 'ya'yanku maza da mata"
A nan "idanunku" na nufin dukkan mutumin. AT: "za ku gaji sa'ad da ku na gadinsu ku na kuma jiran ganinsu"
A nan "ƙarfi a hannunku" na nufin ƙarfi. AT: "Za ku rasa ƙarfin yin wani abu game da ita"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
A nan "al'umma" na nufin mutane daga wani al'umma. AT: "mutane daga al'umma"
Kalmomin "tsananta" da "murƙushe" na nufin abu ɗaya. AT: "za su tsananta ma ku kullum su kuma murƙushe ku" ko "za su cigaba da tsananta ku"
"abin da kun gani zai sa ku ku haukace"
AT: "wanda ba bu wanin da zai iya warkad da"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
A nan kalmomin "karin magana" da "gatse" na nufin abu ɗaya. AT: "na ban tsoro. Mutanen wuraren da Yahweh zai aike ku za su shirya karin magana da gatse game da ku" ko "na ban tsoro. Yahweh zai aike ku wa mutanen da za su yi maku dariya su kuma yi maku ba'a"
kalma ko jimla da mutane su na amfani a kunyata wasu
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
"amma za ku girba abinci kadan"
Musa ya cigaba da bayyana la'anun Allahn idan mutanen sun yi masa rashin biyayya.
Mutane za su shafa man zaitun a jikinsu don su sa jikinsu ya lafiya. AT: "itacen zaitunku za su zub da 'ya'yansu kafin su nuna"
AT: "itacen zaitunku za su zub da 'ya'yansu kafin su nuna"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum daya ne.
Wannan ba ya nufin wani baƙo amma na nufin baƙi gabadaya. AT: "Baƙin da ... Za su ... masu"
Wannan ƙarin maganan na nufin baƙin za su sami iko, kuɗi da daraja fiye da Isra'ilawan.
Wannan na nufin baƙin za su sami ƙarfi da iko fiye da Isra'ilawan. Dubi yadda kun fasara irin wannan a cikin 28:13.
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum daya ne.
Musa ya kwatanta la'anun kamar mutum zai kai masu hari ba da saninsu ba ko kuma ya bi ya kama su. Dubi yadda kun fasara irin wannan a 28:1. AT: "Yahweh zai la'anta ku kamar haka a hanyoyin da zai ba ku mamaki, kuma zai zama kamar ya na bin ku kuma ba za ku tsira daga la'anarsa ba"
A nan kalmomin "muryar Yahweh" magana ne na abin da Yahweh ya faɗa. AT: "ga abin da Yahweh Allahnku ya faɗa"
Kalmomin "umarne" da "ƙa'idodi" na nufin "dukka abin da Yahweh ya umarce ku ku yi."
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum daya ne.
A nan "murna" da "farin cikin zuciya" na nufin abu daya. Su na nanata cewa ya kamata mutanen su yi murna a yabon Yahweh.
Wannan magana ne na yadda Yahweh ya bar makiyan sun yi wa Isra'ilawan ba dadi su kuma mayar da bayi.
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kamar su mutum daya ne.
Wannan jimloli biyun na nufin abu daya kuma na nanata cewa makiyan za su zo daga al'umma da ke da nisa sosai daga Isra'ila.
Wannan karin magana ne. AT: "daga wuraren da ba ku san komai game da su ba"
Wannan na nufin makiyan za su zo da sauri kuma Isra'ilawan ba za su iya tsayar da su ba.
Kalmar "al'umma" magana ne na mutanen al'umman. AT: "al'ummar da mutanensa na da ban razana, wanda ba ta girmama tsoffi ta kuma nuna alfarma"
AT: "sai sun hallaka ku" ko "sai sun bar ku ba tare da komai ba"
Musa ya cigaba da bayyana sojojin da za su kai hari wa Isra'ilawan idan ba su yi biyayya da Yahweh ba.
A nan "ƙofofin birane" na wakilcin birni. AT: "biranenku"
A nan "naman 'ya'yanku maza da na 'ya'ya mata" ya bayyana "'ya'yan da kuka haifa." Mutanen za su ji yunwa sosai bayan sojojin makiyan sun kewaye birninsu da har za su ci 'ya'yansu.
Wannan na maganar 'ya'yan kamar 'ya'yan itace ne da da jikunar iyayensu sun sarrafa. AT: "'ya'yanku"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum daya ne.
"mai taushin zuciya kuma mai kula da ke tare da ku-har zai." Musa na cewa ba waddanda ana zata za su ci 'ya'yansu kadai ba, amma har na karshen, mutum zai zata zai ci 'ya'yansa kuwa zai ci.
A nan "ƙofofin birane" na wakilcin biranen da kansu. AT: "dukkan biranenku"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kaman su mutum daya ne.
"Mace mai taushin zuciya mai kula da ke cikinku-har ita." Musa na fada cewa ba waddannan ne kadai za su ci 'ya'yansu ba, amma har da matayen masu haifuwa masu daraja da tawali'u, wanda wani ba zai taba zata cewa za su ci 'ya'yansu ba, za su ci 'ya'yansu.
Musa na zuguiguita. Ya na nanata cewa wannan mace mai darajan ta na da dukiya kuma ta na zama a irin wannan wadatta da har ba za ta bar kanta ta yi datti ba.
AT: "domin ta na da taushin zuciya da kyakkyawan hali"
A nan "ƙofofin biranen" na wakilcin biranen da kansu. AT: "a biranenku"
Musa ya yi maganar mutanen Isra'ilawa kamar su mutum ɗaya ne.
AT: "da na rubuta"
A nan "suna" na nufin Yahweh da kanshi. AT: "Yahweh Allahnku mai girma da ɗaukaka"
"Yahweh zai aiko da mummunan annobai a kanku da zuriyarku" ko "Yahweh zai tabatar cewa ku da zuriyarku kun sha wahala daga mummunan annobai"
Musa ya yi maganar mutanen Isra'ilawa kamar su mutum ɗaya ne.
Wannan karin mgana ne. AT: "Zai tabatar cewa kun sake shan wahala daga cututukar Masar"
Wannan karin magana ne. AT: "cututukan ba za su daina ba, kuma babu wanda zai iya warkad da ku daga su"
AT: "har cututuka da annobai da ban rubuta ba"
AT: "har sai ya hallaka ku"
Musa na magana da Isra'ilawan kamar taro.
Wannan na nufin akwai Isra'ilawa dayawa a zamanin da ta wuce.
A nan "muryar Yahweh" na nufin abin da Yahweh ya fada. AT: "ga abin da Yahweh ya fada"
"Yahweh ya taɓa farinciki da yi maku kirki, ya kuma sa ku ku yi yawa"
"zai ji dadin sa ku ku mutu"
Musa ya yi amfani da wannan domin ya yi magana da mutanen kamar su 'ya'yan itace ne da Yahweh zai tuge daga jeji. AT: "Zai cire ku daga kasar da za ku shiga ku mallaka"
Waddannan na nufin ko ina a duniya. AT: "ko ina a duniya" ko "duk duniya"
Musa ya yi maganar mutanen Isra'ilawa kamar su mutum ɗaya ne.
A nan, jimlar "tafin ƙafafunku" na nufin dukkan mutumin. AT: "za ku cigaba da yawo domin ba ku da gidan da za ku iya hutawa"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "Yahweh zai sa ku ku ji tsoro, ba bege, da bakin ciki"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "Ba za ku san ko za ku rayu ko ku mutu ba"
Musa ya yi maganar mutanen Isra'ilawa kamar su mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "saboda tsoron da ku ke ji"
A nan "idanu" na nufin dukkan mutum. AT: "abubuwan ban tsoro da zan tilista ku ku gani"
A nan "Na" na nufin Yahweh.
1Waɗannan su ne maganganun da Yahweh ya umarta wa Musa ya faɗi wa 'ya'yan Isra'ila a ƙasar Mowab, maganganu da aka ƙara a kan alƙawarin da ya yi da su a Horeb.2Musa ya kira dukkan Isra'ila ya ce masu, "Kun dai ga dukkan abin da Yahweh ya yi a kan idanunku a ƙasar Masar ga Fir'auna, da dukkan barorinsa da dukkan ƙasarsa -3manyan wahalai da idanunku suka gani, da alamu, da waɗannan dukkan al'ajibai.4Har wa yau Yahweh bai baku zuciya ta sani ba, idanu domin a gani, ko kunnuwa domin ji.5Na bisheku a jeji shekaru arba'in, rigunanku basu tsufa a jikinku ba, takalmanku ma basu tsufa a ƙafafunku ba.6Baku ci waina ba, baku sha ruwan inabi ba, ko barasa mai sa maye, domin ku sani nine Yahweh Allahnku.7Sa'ad da kuka zo wannan wurin, Sihon, sarkin Hesbon, da Og sarkin Bashan, suka fito suyi yaƙi gãba daku, muka buga su.8Muka karɓe ƙasarsu muka ba Rubenawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manasa.9Saboda haka, ku kiyaye waɗannan maganganun alƙawari ku aikata su, domin ku azurta cikin dukkan abubuwan da zaku yi.10Kuna tsaye yau, dukkanku, a gaban Yahweh Allahnku, da sarkinku, da kabilunku, da dattawanku, da shugabanninku-da dukkan mazajen Isra'ila,11da 'yan ƙanananku, da matanku, da baƙi waɗanda suke zaune a tsakiyarku cikin zangonku, da shi wanda ke saro maku itace da mai ɗibar maku ruwa.12Kuna nan domin ku ƙulla alƙawari da Yahweh Allahnku da rantsuwa da Yahweh Allahnku ya ke yi da ku yau,13domin ya maishe ku yau mutane na kansa, domin kuma ya zama Allahnku, kamar yadda ya yi maku magana, kamar kuma yadda ya rantse wa kakanninku, ga Ibrahim, ga Ishaku, ga kuma Yakubu.14Domin bada ku kaɗai nake yin wannan alƙawari da rantsuwa ba -15da kowannenku da ke tsaye tare da mu yau a gaban Yahweh Allahnmu - amma da kuma waɗanda basa nan tare da mu a yau.16Kun sani mun zauna a ƙasar Masar, da yadda muka biyo ta tsakiyar al'ummai waɗanda kuka wuce.17Kun ga allolinsu masu banƙyama da aka yi su da itace da dutse, azurfa da zinariya, da ke tsakiyar su.18Ku tabbata ba wani a cikinku, wani mutum, mata, iyali, ko kabila da zuciyarsa take juyawa daga Yahweh Allahnmu, ya tafi ya yi sujada ga allolin waɗancan al'umman. Ku tabbata ba wani tushe a cikinku mai ba da ɗaci da dafi.19Lokacin da mutumin nan yaji maganganun la'anan nan, zai albarkaci kansa ya ce a zuciyarsa, "Zan sami salama koda shike zan yi tafiya cikin taurin zuciyata.' Wannan zai haddasa hallaka mai adalci tare da mugu.20Yahweh ba zai gafarta masa ba, fushin Yahweh da kishinsa zai auka wa mutumin nan, kuma dukkan la'anan da aka rubuta a littafin nan zasu bi ta kansa, Yahweh zai shafe sunansa daga ƙarƙashin sama.21Yahweh zai ware shi domin bala'i daga dukkan kabilun Isra'ila, domin kiyaye dukkan la'ana na alƙawari da aka rubuta cikin wannan littafin dokoki.22Tsara mai zuwa, yaranku da zasu tashi a bayanku da baƙon da zai zo daga ƙasa mai nisa, zasu yi magana sa'ad da suka ga annobai a kan ƙasannan da cututukan da Yahweh yasa mata ciwo -23sa'ad da suka ga dukkan ƙasar ta zama wuta da ƙibiritu, inda ba shuki ko ya bada 'ya'ya, inda ba tsiro, kamar sa'ad da aka kaɓar da Soduma da Gomarata, Adma da Zeboyim, waɗanda Yahweh ya hallakar cikin fushinsa da hasalarsa. -24zasu ce tare da dukkan wasu al'ummai, 'Meyasa Yahweh ya yi wa ƙasar nan haka? Mene ne ma'anar zafin hasalar nan?'25Sa'annan mutane zasu ce, 'Domin sun watsar da alƙawarin Yahweh, Allahn kakanninsu, da ya yi da su lokacin daya fitar da su daga ƙasar Masar,26kuma domin sun tafi sun bauta wa wasu alloli suka russuna masu, allolin da basu sani ba ba kuma shi ya basu ba.27Saboda haka fushin Yahweh ya yi ƙuna akan wannan ƙasa, har ya kawo a kanta dukkan la'anar da aka rubuta a littafin nan.28Yahweh ya tumbuƙe su daga ƙasarsu cikin fushi, da hasala, da fushi mai ƙuna, ya kuma jefar da su cikin wata ƙasa, har wa yau.'29Sanin abubuwan asiri na Yahweh Allahnmu ne kaɗai; amma abubuwan da aka bayyana su namu ne har abada mu da kuma zuriyarmu, domin mu aikata dukkan maganganun waɗannan dokoki.
Wannan na nufin maganganun da Musa zai yi.
Wannan na kudun Urdun inda Isra'ilawa suke zama kafin su shi aƙsar Kanan. "sa'ad da su na cikin ƙasar Mowab"
An ba da waɗannan karin umarnen don a sa alkawerin Yahweh ya yiwu da kau wa mutanen sa'ad da za su zauna a sabon ƙasarsu. Waɗannan dokokin ba na sabon alkawari ba ne, amma kari ne a ainahin alkawarin.
A nan "idanu" na nanata cewa Yahweh ya so su tuna cewa sun gani. AT: "kun gan duk abin da Yahweh ya yi don ku gani ku kuma tuna da abin da ya yi"
A nan "idanu" na nanata cewa Yahweh ya so su tuna cewa sun gani. AT: "kun gani wa kanku cewa mutanen sun sha wahala sosai"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
Kalmomi "alamu" da "al'ajibai" na nufin annoban da Yahweh ya aika wa Masarawa. AT: "da dukkan abubuwan da Yahweh ya yi"
Mutanen su na da zuciya, idanu, da kunnuwa. Wannan maganar ya faɗa cewa Yahweh bai sa su su gane abin da sun gani da kuma ji game da shi ba, da kuma yadda za su yi masa biyayya.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "sa ku ku gane"
Yahweh na magana da mutanen Isra'ila.
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
Barasa mai sa maye da mai yiwuwa a na yi daga 'ya'yan tsami.
Fasara waɗannan sunayen kamar yadda yake a 1:3.
A nan "mu" na nufin Musa da mutanen Isra'ila.
Waɗannan jimloli biyun na nufin abu ɗaya kuma na nanata cewa ya kamata mutanen su yi biyayya da dokokin Yahweh. AT: "yi biyayya da dukka kalmomin wannan alkawarin"
Musa ya cigaba da magana da mutanen Isra'ila.
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
Akwai baƙi dayawa a cikin Isra'ilawan. AT: "baƙin da suke cikinku a zangonku, daga waɗanda suke saro itatuwarku zuwa waɗanda diba maku ruwa"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
"ku yarda da alkawarin ku kuma rantse cewa za ku yi biyayya da dukka abin da Yahweh Allahnku ya umarta"
"taron mutanen da sun zama na shi shi kadai"
A nan "Ina" na nufin yahweh. "Yahweh na yin"
A nan "mu" na nufin Musa da mutanen Isra'ila.
"zuriyarmu na nan gaba, wanda ba su nan"
"mu bayi ne da"
A nan "zuciya" na nufin dukkan mutumin, kuma "juyawa" na nufin daina yin biyayya. AT: "wanda sun daina yin biyayya da Yahweh Allahnmu"
Musa ya yi maganar wanin da ke bauta wa Allah a ɓoye kamar shi saiwa ne, da kuma mumunan ayukan da yake yi a bautar wannan allahn, da kuma yanda yake karfafa wasu su yi, kamar shuka mai ɗaci da ya zama guba wa mutane. AT: "duk wanda ya bauta wa gumakai ya kuma sa wasu sun yi wa Yahweh rashin biyayya"
Mutumin da an bayana a aya 18.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "taya kansa murna" ko "karfafa kansa"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "ko da shike na ƙi yin biyayya ga Yahweh"
A nan kalmomin "jiƙaƙƙen" da "busasshen" magana ne na mutane masu adalci da mugayen mutane. AT: "Wannan zai sa Yahweh ya hallaka mutane masu adalci da mugayen mutanen dukka a ƙasar"
Domin ƙasar na yawan bushewa kuma mutanen su na bukatar ruwa don amfanin gonarsu su ya girma, waɗannan kalmomin magana ne na "rayayyu ... matattu" ko "kyau ... mugu." AT: "jiƙaƙƙen abubuwa ... busasshen abubuwa" ko "kyauwawan mutane ... mugayen mutane"
Kamar yadda wuta na iya ci da tsanani, haka ne fushi da kishin Allah ke ƙaruwa da tsanani. AT: "Kishin fushin Yahweh zai ƙaru kamar wuta"
A nan kalmar "kishi" ya bayyana "fushin Yahweh." AT: "Fushin kishin Yahweh"
AT: "Da na rubuta"
Musa ya kwatanta la'anuna kamar mutum da zai kai masu hari ba da saninsu ba. AT: "Yahweh zai la'anta shi da la'anun da ke a rubuce a wannan lattafin, a hanyoyin da zai ba shi mamaki gabadaya." Kalmomin irin waɗannan sun bayyana a 28:15.
Wannan na nufin cewa Allah zai hallaka mutumin da iyalinsa gabadaya. Nan gaba mutane ba za su tuna da shi ba. Irin wannan jimla ya bayyana a 7:23.
Kalmomin "yaranku ... bayanku" na maganar "tsara mai zuwa".
"yanda Yahweh ya la'anta ƙasar Kanan da annobai da cuta"
Mutane na sa sulfur da gishiri a ƙasan don ya hana abubuwa girma. "sa'ad da sun gan cewa Yahweh ya kuna ƙasar da sulfur da gishiri"
AT: "inda babu wanin da zai yi shuki kuma amfanin gonan ba su ba da 'ya'ya"
AT: "kamar loƙacin da Yahweh ya hallaka Soduma da Gomrata gabadaya"
"zuriyarku da mutanen dukka sauran al'umman za su ce"
Marubucin na bayyana abu ɗaya a kalmomi biyu. AT: "Me ne wannan zafin fushi ke nufi?"
Wannan amsa ne na "Don me ne Yahweh ya yi wa ƙasar nan wannan?" (29:22). "Yahweh ya yi wa ƙasar nan wannan abu saboda Isra'ilawan ba su bi alkaware da dokokin alkawarinsa ba"
"yi wa wasu alloli biyayya da kuma bauta masu"
Musa ya kwatanta Yahweh na fushi da wanin da ke kuna wuta. Wannan ya nanata ikon Allah a hallka duk abin da ya sa shi fushi. AT: "Yahweh ya yi fushi da wannan ƙasan"
A nan "ƙasar" magana ne da ke wakilcin mutanen. AT: "mutanen wannan ƙasar, don ya kawo a kansu"
AT: "da na rubuta"
An kwatanta Isra'ila da mumunan iri da Yahweh ya tumbuƙe ya kuma jefar da shi daga lambun. AT: "Yahweh ya cire su daga ƙasar su ... ya kuma tilasta su su tafi"
Kalmomin "fushi," "hasala," da "fushi mai ƙuna" na nufin abu ɗaya kuma na nanata tsananin fushin Yahweh. AT: "a cikin fushi mai tsanani" ko "saboda ya yi fushi mai tsanani."
"Wasu abubuwan da Yahweh Allahnku bai bayyana ba, kuma shi kadai ne ya san su"
AT: "da ya bayyana"
Kalmar "kalmomi" magana ne na "umarne." AT: "za ku iya yin dukka abubuwan da wannan dokan ya umarce mu mu yi"
1Sa'ad da dukkan waɗannan abubuwa suka zo kanku, albarku da la'ana dana sa a gabanku, kuma sa'ad da kuka tuna da su yayin da kuna cikin dukkan al'ummai inda Yahweh Allahnku ya kora ku,2sa'ad da kuma kuka koma ga Yahweh Allahnku kuka yi biyayya da muryarsa, kuna yin dukkan abin da na umarce ku yau - ku da 'ya'yanku, - da dukkan zuciyarku da kuma dukkan ranku,3sa'an nan Yahweh Allahnku zai komo daku daga bautar talala ya yi juyayinku; zai juya ya tattaroku daga cikin dukkan al'ummai da Yahweh Allahnku ya warwatsa ku.4Idan korarrun mutanenku suna cikin manisantan wuraren ƙasa da sammai, daga can Yahweh Allahnku zai tattara ku, kuma daga can zai kawo ku.5Yahweh Allahnku zai kawo ku cikin ƙasar da kakanninku suka mallaka, kuma zaku sake mallakarta; zai yi maku alheri ya riɓaɓɓanya ku fiye da yadda ya yi da kakanninku.6Yahweh Allahnku zai yi wa zuciyarku kaciya da ta zuriyarku, domin ku ƙaunaci Yahweh Allahnku da dukkan zuciyarku da dukkan ranku, domin ku rayu.7Yahweh Allahnku zai sa dukkan waɗannan la'ana a kan maƙiyanku da kan waɗanda suke ƙin ku, waɗanda suka tsananta maku.8Zaku juyo kuyi biyayya da muryar Yahweh, kuma zaku aikata dukkan umarnansa da nake umartar ku yau.9Yahweh Allahnku zai yalwata dukkan aikin hannunku, da 'ya'yan jikinku, da 'yan maruƙanku, da amfanin gonakinku, domin wadata; gama Yahweh zai sake yin farin ciki a kanku ya azurta ku, kamar yadda ya yi farinciki da ubanninku.10Zai yi wannan idan kuka yi biyayya da muryar Yahweh Allahnku, kuka kiyaye umarnansa da sharuɗansa da ke rubuce cikin littafin dokokin nan, idan kuka juyo ga Yahweh Allahnku da dukkan zuciyarku da dukkan ranku.11Domin wannan umarni da nake umartan ku yau baifi ƙarfin ku ba, kuma bai yi nisa har da ba zaku kama ba.12Ba a sama ya ke ba, har da zaku ce, 'Wa zai je can sama domin mu ya sauko mana da ita yasa mu iya jinta, domin mu yi ta?'13Kuma ba a ƙarshen ruwaye ya ke ba, da zaku ce, 'Wa zai haye ruwaye domin mu ya kawo mana ita yasa mu mu jita, domin mu aikata ta?'14Amma maganar tana kurkusa da kai, a bakinka da kuma zuciyarka, domin ka aikata ta.15Duba, yau nasa a gabanku rai da nagarta, mutuwa da mugunta.16Idan kun yi biyayya da dokokin Yahweh Allahnku, waɗanda nake umartanku yau ku ƙaunaci Yahweh Allahnku, ku yi tafiya a tafarkunsa, ku kuma kiyaye umarnansa, da ka'idodinsa da kuma farillansa, zaku rayu ku riɓaɓɓanya, kuma Yahweh Allahnku zai albarkace ku cikin ƙasar da kuke shigarta domin ku mallaka.17Amma idan zuciyarku ta juya, baku saurara ba a maimako kuka janye kuka russuna wa waɗansu alloli kuka yi masu sujada,18to yau ina maku shela cewa ba shakka zaku lalace; ba zaku yi tsawon kwanaki ba cikin ƙasar da kuke ƙetare Yodan domin ku shiga cikinta ku mallaka.19Na kira sama da ƙasa suyi shaida gãba daku yau, cewa na ajiye a gabanku rai da mutuwa, albarku da la'ana; saboda haka ku zaɓi rai domin ku rayu, daku da zuriyarku.20Kuyi wannan don ku ƙaunaci Yahweh Allahnku, kuyi biyayya da muryarsa, ku kuma manne masa. Gama shi ne ranku da tsawon kwanakinku; kuyi haka domin ku zauna cikin ƙasar da Yahweh ya rantse wa kakanninku, ga Ibrahim, ga Ishaku, ga Yakubu kuma, zai ba su."
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
A nan "waɗannan abubuwan" na nufin albarku da la'anannu da an bayana a sura 28-29. Jimlar "sun zo kanku" ƙarin magana ne da ke nufin faru. AT: "Sa'ad da dukkan waɗannan abubuwan sun faru da ku"
Wannan na maganar albarku da la'anu da Musa ya gaya wa mutanen kamar abubuwa ne da ya shirya a gabansu. AT: "da yanzu na rigaya na faɗa maku"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "tuna da su"
"sa'ad da ku na zama a cikin sauran al'imman"
"ya tilasta ku ku tafi"
A nan "murya" na nufin abin da Yahweh ya faɗa. AT: "yi biyayya da abin da ya faɗa"
Karin maganar "da dukkan ... zuciya" na nufin "gabadaya" da "da dukkan ... rai" na nufin "da dukkan kasancewarku." AT: "da dukkan kasancewarku" ko "da dukkan ƙarfinku." Fasara wanan kamar yadda yake a 4:29.
"sake ku daga bauta." AT: "sake ku daga wanda sun kama ku"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
"har ko korarrun mutanenku da suke manisantan wuraren"
"karƙashin sasari" ko "a duniya"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
Wannan ba cire fata ba ne. Na nufin Allah zai cire zunubansu ya kuma sa su su ƙaunace shi su kuma yi masa biyayya.
Karin maganar "da dukkan ... zuciya" na nufin "gabadaya" da "da dukkan ... rai" na nufin "da dukkan kasancewarku." AT: "da dukkan kasancewarku" ko "da dukkan ƙarfinku." Fasara wanan kamar yadda yake a 4:29.
A nan "murya" na nufin abin da Yahweh na faɗa. AT: "yi biyayya da abin da Yahweh ya faɗa"
Musa ya yi maganar la'anu kamar kaya ne ko rufi da wani na iya sa akan mutum. AT: "zai sa makiyanku su sha wahala daga wannan la'anun"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
A nan "hannu" na nufin dukkan mutum. AT: "a dukkan aikin da ku ke yi"
Waɗannan jimloli uku ne na "a 'ya'ya ... maraƙi ... a amfanin gona." Kalmomi irin waɗannan sun bayyana na 28:3.
AT: "da na rubuta"
Karin maganar "da dukkan ... zuciya" na nufin "gabadaya" da "da dukkan ... rai" na nufin "da dukkan kasancewarku." AT: "da dukkan kasancewarku" ko "da dukkan ƙarfinku." Fasara wanan kamar yadda yake a 4:29.
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
Musa ya yi maganar iya fahimtar abin da doko ke bukata mutum ya yi kamar mutumin ne zai iya kai wani abu. AT: "kuma ya yi maku wuya ku fahimci abin da Yahweh ke bukuta ku yi"
A nan Musa ya yi amfani da tambaya don ya nanata cewa mutanen Isra'ila sun yi tunani cewa dokokin Yahweh na da wuya. AT: "Dole wani ya yi tafiya zuwa sama, ya koya dokokin Allah sai ya dawo ya gaya mana abin da suke don mu iya yin biyayya da su."
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
Wannan tambaya ya cigaba da maganar cewa mutanen Isra'ila su na tunani cewa umarnen Yahweh na da wuyan sani. AT: "Dole wani ya yi tafiya zuwa hayin tekun, ya yi koyi game da dokokin sai ya dawo ya faɗa mana game da su."
Wannan na nufin cewa mutanen sun rigaya sun san dokokin Allah kuma za su iya gaya wa wasu.
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
Sa wani abu a inda wani zai iya gani magana ne na gaya wa wani game da wani abu. AT: "Na gaya maku game da"
AT: "abin da ke da kyau, kuma abin da ke mugu kuma zai sa ku ku mutu"
"kuma sami zuriya dayawa"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
A nan "zuciya" na nufin dukkan mutumin. AT: "idan kun daina yin biyayya ga Allah ... kuma mutanen da suke zama a cikin ƙasar sun ruɗe ku ku durkusa ku bauta wasu alloli"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar taro.
Tsawon kwanaki magana ne na tsawon rai. AT: "iya yin rayuwa na tsawon loƙaci." Fasara waɗannan kalmomin kamar yadda suke a 4:25.
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
AT: 1) Musa na kira ga duk waɗanda suke zama a sama da ƙasa su zama shaidar abin da ya faɗa, ko 2) Musa na magana da sama da ƙasa kamar su mutane ne, kuma na kiransu su zama shaidu ga abin da ya faɗa
"su yarda su ce kun yi mumunan abubuwa"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar taro.
A nan "murya" na nufin abin da Yahweh ya ce. AT: "yi biyayya da abin da ya ce"
"kuma su dogara da shi"
"Ranku" da "tsawon kwanakinku" magana ne na wanda zai iya ba da rai da tsawon kwanaki. AT: "Yahweh ne kadai zai iya sa ku ku yi rayuwan tsawon loƙaci"
AT: "rantse cewa zai ba wa kakanninku"
1Musa ya tafi ya faɗa wa Isra'ila waɗannan maganganu.2Ya ce masu, "Yanzu ina da shekaru ɗari da ashirin bana iya shiga in fita; Yahweh ya ce mani, 'Ba zaka ƙetare wannan Yodan ba.'3Yahweh Allahnku, zai sha gabanku; Zai hallaka waɗannan al'ummai a gaban ku, zaku ƙwace mallakarsu. Yoshuwa, zai jagorance ku, kamar yadda Yahweh ya faɗi.4Yahweh zai yi masu kamar yadda ya yi wa Sihon da kuma Og, sarakunan Amoriyawa, da kuma ƙasarsu, waɗanda ya hallakar.5Yahweh zai baku nasara a kansu sa'ad da zaku kara da su a yaƙi, zaku yi masu dukkan yadda na umarce ku.6Ku ƙarfafa kuyi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro, kada kuma ku firgita domin su; gama Yahweh Allahnku, shi ne wanda ya ke tafiya tare daku; ba zai kunyatar daku ba ko ya yashe ku."7Musa ya kira Yoshuwa a gaban dukkan Isra'ila ya ce masa, "Ka ƙarfafa kayi karfin hali, gama zaka tafi da mutanen nan cikin ƙasar da Yahweh ya rantse wa kakanninsu zai basu; zaka sasu su gaje ta.8Yahweh, shi ne wanda ya sha gabanku; zai kasance tare daku; ba zai kunyatar daku ba ba zai yashe ku ba; kada ku ji tsoro, kada ku karaya."9Musa ya rubuta wannan doka yaba firistoci, 'ya'yan Lebi, waɗanda suke ɗaukar akwatin alƙawari na Yahweh; ya kuma ba dukkan dattawan Isra'ila.10Musa ya umarce su ya ce, "A ƙarshen kowacce shekara bakwai, lokacin da aka ƙayyade domin kashe basussuka, lokacin Idin Rumfuna,11lokacin da dukkan Isra'ila ke zuwa su bayyana a gaban Yahweh Allahnku a wurin da zai zaɓa domin haikalinsa, zaku karanta wannan doka a gaban dukkan Isra'ila a kunnuwansu.12A tara mutane, da maza, da mata, da 'yan ƙanana, da baƙon da ya ke a cikin ƙofar birninku, domin su ji su koya, domin kuma su girmama Yahweh Allahnku su kiyaye dukkan maganganun wannan dokoki.13Kuyi wannan domin 'ya'yansu da ba su sani ba, su ji su koya su girmama Yahweh Allahnku, dukkan kwanakin da zaku kasance a ƙasar nan da kuke ƙetare Yodan domin ku mallaketa."14Yahweh ya cewa Musa, "Duba rana tana zuwa, da dole ka mutu; ka kira Yoshuwa ku nuna kanku a rumfar taruwa, domin in ba shi umarni." Sai Musa da Yoshuwa suka tafi suka nuna kansu a rumfar taruwa.15Sai Yahweh ya bayyana a umudin girgije; umudin girgijen ya tsaya a bakin ƙofar rumfa.16Yahweh ya cewa Musa, "Duba, zaka yi barci tare da ubanninka; waɗannan mutane zasu tashi suyi kamar karuwai su bi waɗansu baƙin alloli waɗanda ke a tsakaninsu a cikin ƙasar da zasu. Zasu yasheni su karya alƙawarin da nayi da su.17Sa'annan, a ranar nan, fushina zai yi ƙuna a kansu zan kuwa yashe su. Zan ɓoye fuskata za a kuma hallaka su. Masifu da wahalai zasu auka masu zasu ce a ranan nan, 'Ba waɗannan masifu sun zo kanmu domin Allahnmu ba shi tare da mu ba?'18Hakika zan ɓoye fuskata daga gare su a ranar nan, saboda dukkan muguntar da zasu aikata, domin sun juya ga waɗansu alloli.19Saboda haka yanzu fa, ka rubuta wannan waƙa domin kanku ka koya wa mutanen Isra'ila. Ka sa a bakinsu, domin wannan waƙa ta zama shaida gãba da mutanen Isra'ila.20Gama bayan na kawo su cikin wannan ƙasar dana rantse zan ba kakaninsu ƙasa mai zuba da madara da zuma, bayan sun ci sun ƙoshi sun yi ƙiba, zasu juya ga wasu alloli su kuma bauta masu su rena ni su karya alƙawarina.21Sa'ad da mugayen abubuwa da wahalai suka zo kan mutanen nan wannan waƙa za ta faɗa a gabansu ita ce shaida (gama ba za a manta ta ba a bakunan tsararrakinsu). Gama na san shirye-shiryen da suke ƙuƙƙullawa yau, tun ma kafin in kawo su ƙasar dana alƙawarta masu."22Sai Musa ya rubuta wannan waƙa a ranan nan ya kuma koya wa mutanen isra'ila.23Yahweh ya ba Yoshuwa ɗan Nun umarni ya ce, "Ka ƙarfafa kayi ƙarfin hali; gama zaka kawo mutanen Isra'ila cikin ƙasar dana rantse masu, zan kuma kasance tare da kai."24Da Musa ya gama rubuta waɗannan maganganun shari'a a cikin littafi,25sai ya umarci Lebiyawa masu ɗaukar akwatin alƙawari na Yahweh, ya ce,26"Ku ɗauki wannan littafin sharia ku aje shi a gefen akwatin alƙawari na Yahweh Allahnku, domin ya kasance a can ya zama maku shaida gãba da ku.27Gama na san tayarwarku da taurin kanku; duba, da raina ma ina tare daku yau, kuna tawaye gãba da Yahweh; ballantana bayan na mutu?28Ku tattaro mani dattawan kabilunku, da shugabanninku, domin in faɗi maganganun nan a kunnuwansu in kira sama da ƙasa suyi shaida gãba da su.29Gama na sani bayan rasuwata zaku ƙazamtar da kanku zaku kauce ku bar tafarkin dana umarce ku; Masifa zata auka maku cikin kwanaki masu zuwa. Wannan zai faru domin zaku yi abin mugunta a idon Yahweh, har da zaku cakune shi ya yi fushi ta wurin aikin hannuwanku."30Musa ya maimaita maganganun wannan waƙa a kunnuwan dukkan taron Isra'ila har sai da suka ƙare.
An yi amfani da "fita" da "shiga" tare don a nuna cewa Musa ba zai iya yin abin da mai lafiya zai iya yi ba. AT: "Ba zan iya je duk inda za ku je ba, ba zan iya zama shugaban ku kuma ba"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
"za ku karba ƙasarsu"
"Yoshuwa zai bi da ku a hayin tekun, kamar yadda Yahweh ya yi alkawari"
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan.
A nan "Sihon" da "Og" na nufin Sarakuna biyu na Amoriyawan da sojojinsu. Fasara waɗannan sunayen a 1:3. "ya yi wa Sihon da kuma Og, sarakunan Amoriyawa, da kuma sojojinsu"
"Ku ƙarfafa ku yi ƙarfin hali"
"kada ku ji tsoronsu ko kadan"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
AT: "zai cika maku alkawarinsa kullum kuma zai kasance tare da ku kullum"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
Wannan na nufin dukka mutanen Isra'ila su na nan. AT: "a gaban dukka Isra'ilawa"
"Ka ƙarfafa ka yi karfin hali." Fasara kamar yadda yake a 31:4.
"za ku taimake su karban ƙasar"
"ya ba wa Lewiyawan. wanda su ne firistocin"
"don warware basussuka"
Wasu sunayen wannan idin su ne "Idin alfarwar," "Idin bukkoki," da "Idin tattarawa." A loƙacin girbi, manoma za su yi rumfuna a gonan. Wannan idin ya faru a bayan girbi na karshen shekara. Fasara wannan kamar yadda yake a 16:13.
-Musa ya yi magana da Isra'ilawa kamar su mutum ɗaya ne.
"don su iya ji"
Musa ya cigaba da magana da firistoci da dattawan.
A nan "ƙofofin" na wakilcin biranen da kansu. Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne. AT: "bakinku da suke zama a cikin biranenku"
"yi biyayya da dukka umarne a cikin wannan dokar"
"Saurare abin da zan gaya maku. Rana"
Wannan majimaran mai hayaki kamar abin da ke tsaye.
"Saurare abin da zan gaya maku. Za"
Wannan wata hanya ne na ce "za ka mutu." AT: "za ka mutu ka same kakaninka wanda sun mutu kafin kai"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa.
Yahweh ya kwatanta fushinsa da wani mai ƙuna wuta. Wannan ya nanata ikon Allah a hallaka duk abin da ya sa shi fushi. AT: "zan hura fushina a kansu" ko "Zan yi fushi da su"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "Ba zan taimake su ba"
AT: "Zan cinye su" ko "Zan bar maƙiyansu su cinye su"
Wannan magana ne na "hallaka gabadaya."
Wannan ya kwatanta masifu da wahalolin kamar su mutum ne. AT: "Za su gan masifu da wahaloli dayawa"
Wannan ya kwatanta masifu da wahalolin kamar su mutum ne. AT: "Waɗannan masifun su na hallaka ni ... tsakiyar."
"Allah ba ya sake kiyaye mu" ko "Allah ya bar mu mu kadai"
Yahweh ya cigaba da magana da Musa game Isra'ilawan.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "Sa su su haddace shi su kuma yi wakan"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "ƙasar da madara da zuma mai yawa suke zuba" ko "ƙasar da ke da kyau wa tumaki da noma" Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 6:3.
A nan an kwatanta muguye da wahaloli kamar su mutane ne kuma su na iya neman mutum. AT: "Sa'ad da mutanen nan sun ji mugunta da wahaloli"
Wannan ya yi maganar wakan kamar ya zama shaidar mutum a kotu da ke gaba da Isra'ilawa.
AT: "zuriyarsu ba za su manta su kiyaye shi a bakunarsu ba"
AT: "zuriyarsu za su tuna su rike shi a bakunarsu"
Karin maganar "manta daga bakin" na nufin daina yin maganan. AT: "zuriyarsu ba za su daina yi wa juna magana game da shi ba"
An yi maganar abin da mutane ke shirya yi kamar abin da ana iya gani. AT: "abin da sun yi shirin yi"
"ƙasar dana alƙawarta cewa zan basu"
"Ka ƙarfafa ka yi ƙarfin hali." Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 31:4.
Musa ya yi da Lawiyawan kamar su mutum ɗaya ne.
Musa ya cigaba da magana da Lawiyawa game da dukka mutanen Isra'ila.
Musa ya yi magana da Lawiyawan kaman su mutum ɗaya.
Fasara wannan kamar yadda kun fasara "taurin kai" a cikin 9:6.
Wannan tamabaya ya bayana yadda mutanen ke da tawaye. AT: "za ku zama masu tawaye sosai bayan na mutu."
A nan "a kunnuwansu" na nufin mutanen da kansu. AT: "domin in faɗi masu maganganun wannan wakan"
AT: 1) Musa na kira ga dukka waɗanda suke sama da kasa su zama shaidar abin da ya faɗa ko 2) Musa na magana da sama da kasa kamar su mutani ne, kuma ya na kiran su su zama shaida da abin da zan faɗa. Irin wannan maganan ya bayyana a 30:19.
A nan "hannunku" na nufin mutanen da kansu. AT: "saboda abin da kun yi"
A nan "kunnuwa" na nufin dukkan mutum. AT: "Musa ya maimaita wa dukkan mutanen Isra'ila "
AT: 1) yi waă" ko 2) "yi magana."
AT: "kalmomin wakokin da Yahweh ya koya masa"
1Ku saurara, ku sammai, bari in yi magana. Bari duniya ta saurari maganganun bakina.2Bari koyarwata ta zubo kamar ruwan sama, bari maganata ta zubo kamar raɓa, kamar yayyafi a kan ɗanyar ciyawa, kamar ɗiɗɗigar ruwa akan shuke-shuke.3Domin zan yi shelar sunan Yahweh, kuma in faɗi girman Allanmu.4Dutse ne, aikinsa cikakke ne; gama duk hanyoyinsa na adalci ne. Shi Allah mai aminci ne, marar zunubi. Mai adalci ne nagari kuma.5Sun aikata mugunta gãba da shi. Ba 'ya'yansa ba ne. Abin ƙasƙancinsu ne. Su kam kangararru ne karkatacciyar tsara.6Haka zaku rama wa Yahweh, ku wawayen mutane marasa tunani? Shi ba mahaifinku bane, wanda ya hallice ku? Shi ya yi ku ya kuma kafa ku.7Ku tuna da kwanakai da lokatan dã, ku tuna da shekaru na zamanai da yawa da suka wuce. Ku tambayi mahaifinku zai nuna maku, dattawanku zasu kuma gaya maku.8Lokacin da Maɗaukaki yaba al'ummai gadonsu - sa'ad da ya raba 'yan adam, ya rabawa al'ummai wurin zamansu, kamar yadda ya san yawan allolinsu.9Gama rabon Yahweh mutanensa ne; Yakubu shi ne rabon gadonsa.10Ya same shi a cikin hamada, a cikin ƙasa marar amfani, wurin kuka a jeji; ya kare shi ya lura da shi, ya tsare shi kamar kwayar idonsa.11Kamar yadda gaggafa take tsare sheƙarta tana shawagi bisa 'ya'yanta, haka Yahweh ya buɗe fuka- fukansa ya ɗauke su, ya tafi da su a kan kafaɗarsa.12Yahweh kaɗai ya bishe su; babu baƙon allah tare da su.13Ya sa shi ya hau manyan tuddai na ƙasar, ya ciyar da shi da 'ya'yan itatuwan saura; ya yi kiwonsu da zuma daga dutse, da mai daga dutsen daya tsage..14Ya sha man shanu daga garke kuma ya sha madara daga garken tumaki, daga ƙibar 'yan tumaki, ragunan Bashan da awakai, da lallausar garin alkama - kuka sha ruwan inabi mai kumfa da aka yi da ruwan 'ya'yan itacen inabi.15Amma Yeshurun ya yi ƙiba ya yi hauri - ka yi ƙiba, ka ma zarce da ƙiba, ka ci isasshe - sai ya yashe da Allahn da ya yi shi, yaƙi Dutsen cetonsa.16Suka sa Yahweh ya ji kyashi ta wurin baƙin allolinsu; da abubuwan ƙyamarsu suka sa shi fushi.17Suka yi wa al'jannu hadaya, waɗanda ba Allah ba - allolin da basu sani ba, sabobbin alloli, gumakun da ubanninku basu ji tsoro ba.18Kuka yashe da Dutsen, daya zama maku mahaifi, kuka manta da Allahn daya haife ku.19Yahweh ya ga haka ya kuma ƙi su, sabili da 'ya'yansa maza da 'ya'yansa mata sun tsokane shi.20"Zan ɓoye fuskata daga gare su," ya ce, "zan ga yadda ƙarshensu zai zama; gama kangararrun tsara ne, 'ya'ya marasa aminci.21Suka sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba suka sa ni fushi da abubuwan wofinsu. Zan sa suji kyashi da waɗanda ba mutane ba; tawurin wautar al'umma zan sasu yi fushi.22Gama fushina ya kunna wuta yana kuma ci zuwa zurfafan Lahira; yana hallaka duniya da girbinta; yana kunna wuta a harsashin duwatsu.23Zan tara masihu a kan su; zan harba dukkan kibiyoyina a kansu;24Yunwa za ta ƙarasa su zasu hallaka da ƙuna mai zafi da hallakarwa mai ɗaci; zan aika a bisansu haƙoran namun jeji, da dafin abubuwan da ke rarrafe cikin ƙura.25A waje takobi zai kawo rashi, a ɗakunan kwana razana zata yi haka. Zata hallaka matashi da budurwa, da jariri mai shan mama, da mutum mai furfura.26Na ce zan warwatsa su da nisa, in sa tunawa da su ya shuɗe daga 'yan adam.27Da ba domin ina tsoron tsokanar maƙiyi ba, cewa maƙiya zasu zaci kuskure, kuma zasu ce, 'Hannunmu ya sami ɗaukaka,' dana aikata dukkan waɗannan abubuwa.28Gama Isra'ila al'umma ce marar hikima, babu fahimta a cikinsu.29Ai ya, da suna da hikima, da sun fahimci wannan, da zasu yi la'akari da ƙaddararsu mai zuwa!30Ta ya ya ɗaya zai kori dubu, biyu su sa dubu goma su tsere, sai ko Dutsensu ya sayar da su, Yahweh kuma ya sadakar da su?31Gama dutsen maƙiyanmu ba kamar Dutsenmu ba, kamar dai yadda maƙiyanmu suke cewa.32Gama kuringar inabinsu ta zo ne daga kuringar Saduma, daga kuma jejin Gomarata; inabinsu inabin dafi ne; nonan masu ɗaci ne.33Ruwan inabinsu dafin macizai ne, da mugun dafin kumurci.34Wannan shiri ban aje shi a ɓoye ba, a kunle cikin kayayyakina masu daraja ba?35Ni ke bada sakamako, da ramako, a lokacin da kafafunsu suka zarme; gama ranar masifa domin su tayi kusa, abubuwan da zasu zo ta kansu zasu hanzarta su faru."36Gama Yahweh zai yi wa mutanensa adalci, kuma zai ji tausayin bayinsa. Zai ga cewa ƙarfinsu ya ƙare, kuma ba wanda ya rage, ko bawa ko baratattun mutane.37Sa'annan zai ce, "Ina allolinsu suke, duwatsu waɗanda suka dogara a gare su? -38allolin da suka ci kitsen hadayunsu suka sha ruwan inabin baye-bayensu na sha. Bari su tashi su taimaka maku; bari su zamar maku kariya.39Duba yanzu da Ni, har Ni, Allah nake, kuma babu wani allah banda ni; Nakan kashe, in kuma rayar; na kan sa rauni, in warkar, kuma ba wani da zai iya cetonku daga ƙarfina.40Gama na kan tada hannuna zuwa sama in ce, "kamar yadda na dawwama har abada, zan aikata.41Sa'ad da na wasa takobina mai walƙiya, kuma sa'ad da hannuna ya fara kawo adalci, zan yi sakayya akan maƙiyana, in kuma sãka wa duk waɗanda suka ƙi ni.42Zan sa kibiyoyina su bugu da jini, takobina zai ci tsoka tare da jinin kasassu da kamammu, tun daga kan shugabannin maƙiyan.'"43Ku yi farinciki, ya ku al'ummai, da mutanen Allah, gama zai yi sakayyar jinin bayinsa; zai bada sakamako a kan maƙiyansa, kuma zai yi kafara domin ƙasarsa, kuma domin mutanensa.44Musa ya zo ya maimaita dukkan maganganun waƙar nan a kunnuwan mutane, shi, da Yoshuwa ɗan Nun.45Sai Musa ya gama maimaita dukkan waɗannan maganganun ga dukkan Isra'ila.46Ya ce masu, "Ku sa zuciyarku akan maganganun da nayi maku kashedi yau, domin ku umarci 'ya'yanku su kiyaye su, dukkan maganganun shari'ar nan.47Gama wannan ba wani abu ne kurum dominku ba, sabili da ranku ne, kuma tawurin wannan abu zaku tsawaita kwanakin ku a ƙasar da kuke tafiya ku haye Yodan ku mallaka."48A ranar nan Yahweh ya yi magana da Musa ya ce,49"Ka hau cikin waɗannan duwatsen Abarim, ƙolƙolin Dutsen Nebo, wanda ke ƙasar Mowab, hannun riga da Yariko. Zaka duba ƙasar Kan'ana, wanda nake ba mutanen Isra'ila abin mallakarsu.50Zaka mutu akan dutsen da zaka hau, za a tattara ka zuwa ga mutanenka, kamar yadda Haruna ɗan'uwanka Ba'isra'ile ya rasu akan Dutsen Hor aka tattara shi zuwa ga mutanensa.51Wannan zai faru domin ka yi rashin aminci a gare ni a tsakiyar mutanen Isra'ila a bakin ruwayen Meriba a Kadesh, a jejin Zin; domin baka ɗaukakani ba kuma baka girmama ni cikin mutanen Isra'ila ba.52Gama zaka hangi ƙasar a gabanka, amma ba zaka je can ba, cikin ƙasar da nake ba mutanen Isra'ila."
Musa ya yi waka wa mutanen Isra'ila.
Yahweh ya yi magana da sammai da duniya kamar su na wurin kuma su na ji. AT: 1) Yahweh na magana da mazaunan duniyako 2) Yahweh na magana da sammai da duniya kamar su matani ne.
Wannan na nufin cewa Yahweh na son mutanen su ƙarbi koyarwarsa mai taimako da sauri.
Yi amfani da kalman a harshenku a yadda raɓa ke bayyana.
ruwa da ke kumfa a ganye da ciyawa da safiya
"sabon shuke-shuke"
"ruwa mai ƙarfi"
Musa ya yi waka wa mutanen Isra'ila.
Wannan ƙarin magana ne. "faɗa yadda Yahweh n da kyau"
"tabatar mutane sun san cewa Allahnmu mai girma ne"
Wannan suna ne da Musa ya ba Yahweh, wanda, kamar dutse, na da ƙarfi da kuma iya kare mutaninsa.
"duk abin da yake yi"
"na yin komai a hanyar adalci"
A takaice waɗannan kalmomin na nufin abu ɗaya kuma na bayyana cewa Yahweh na da adalci kuma na yin abin da ke daidai.
Musa ya yi waka wa mutanen Isra'ila. Musa ya cigaba da amfani da ƙarin magana domin ya nanata abin da yake faɗi.
"yi hamayya da shi ta wurin yin abin da ba daidai ba." Kalmomi irin waɗannan sun bayyana a 4:15.
Kalmomin "kangararru" da "karkatacciyar" a takaice na nufin abu ɗaya. Musa ya yi amfani da su domin ya nanata muguncin tsarar. AT: "cikakkiyar mugun tsara"
Musa ya yi amfani da tambaya don ya kwaɓe mutanin. AT: "Ku ba wa Yahweh yaɓon da ya kamata ... mutane."
Kalmomin "wawaye" da "marasa tunani" a takaice na nufin abu ɗaya kuma na nanata yadda mutanin sun yi wawanci a rashin biyayya ga Yahweh. AT: "ku wawayen mutane"
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su ɗaya ne.
Musa ya yi amfani da tambaya dan ya sauta mutanen. AT: "Yahweh mahaifinku ne kuma wanda ya halliceku."
Musa ya yi waka wa mutanen Isra'ila.
Musa ya yi magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "Tuna"
"kwanakai da lokatan da suka wuce." Musa na nufin loƙacin da kakanin mutanen Isra'ila suke da rai.
Wannan maimeci ne na abin da Musa ya ce a maganar da ta wuce. Musa na son mutanen Isra'ila su yi hankali da tarihinsu na al'umma.
"zai bayyana maku" ko "zai sa ku fahimta"
Wannan ƙarin magana ne. "sa al'umman a wuraren da za su zauna." Kalmomi irin wannan "ya ba ku a matsayin gado," sun bayyana a 4:21.
Allah ya sa ko wane mutum, tare da allolinsu, zuwa wurin su. A haka, ya rage albarkacin allolin mutanen.
Musa ya yi waka wa mutanen Isra'ila. Sa'ad da ya na magana da Isra'ilawan, ya yi maganar su kamar su wasu dabam ne kuma kamar su mutum ɗaya ne.
A takaice waɗannan jimloli biyun na nufin abu ɗaya kuma za a iya hada. AT: "Zuriyar Yakubu gadon Yahweh ne"
"Ya same Yakubu ... kare shi ya kuma lura da shi ... tsare shi" Za ku so ku fasara wannan kamar Musa na magana game da Isra'ilawan kaman mutane dayawa." Ya sami kakaninmu ... ya kare su ya kuma lura da su ... tsare su" (Dubi UDB)
A nan "raraka" na nufin karar da iska na yi sa'ad da yake buga ƙasar da babu komai.
Wannan ƙarin magana ne. kwayar idanu na nufin sashin duhu a cikin kwayar ido dake sa mutum gani. Wannan sashin jikin mutum ne mai muhimminci da daraja. Wannan na nufin cewa mutanen Isra'ila su na da muhimminci ga Allah da abin da yake kiyayewa. AT: "ya kare shi kaman wani abu mai daraja da amfani"
Musa ya yi waka wa mutanen Isra'ila.
Wannan na nufin lura da kuma kiyaye Isra'ilawan sa'ad da su na cikin jejin.
wajen gefen fuka-fukin tsuntsu
Musa ya kuma sake yin maganar Isra'ilawan kaman "Yakubu"
Musa ya yi waka wa mutanen Isra'ila.
Wannan ƙarin magana ne. Kalmar "shi" na nufin mutanen Isra'ila. AT: "Yahweh ya sa sun hau manyan tuddan ƙasar" ko "Yahweh ya taimake su ƙarban ƙasar da kuma zama a ƙasan"
Musa ya cigab da maganar Isra'ilawan kamar "Yakubu"
"ya kawo shi ƙasa mai amfanin gona dayawa da zai iya ci"
Ƙasar na da ƙudan zuman jeji, wanda ke ba da zuma, da amya a cikin ramukan dutsen. Akwai kuma itatuwan zaitun dayawa, wanda ke ba da mai, na kuma girma a duwatsu da tuddai.
Wannan na nan kamar mahaifiya ta na ba wa jariri nono. "bar shi ya tsotsa zuma"
Musa ya yi waka wa mutanen Isra'ila. Ya yi magana da Isra'ilawan kaman su mutum ɗaya ne.
Musa ya cigaba da magana da Isra'ilawan kamar "Yakubu"
Mutanen Isra'ilawa na da garken dabbobi masu lafiya.
Musa ya yin wakokinsa wa mutanen Isra'ila.
Musa ya yi maganar Isra'ilawan kamar su dabbobi ne wanda an ciyar da su sosai, wanda Yeshurun ne sunar mai shi. Za ku iya kara bayana cewa "Sunar "Yeshurun' na nufin 'na gari." Idan harshen ba zai iya maganar Isra'ilawan kamar Yeshurun ba, za ku iya yin maganar Isra'ilawan kamar mutane dayawa. kamar da UDB ke yi.
Yeshurun, dabban da an ciyar sosai, wanda ke shuri a maimakon zama da tawali'u, magana ne na Isra'ialwa wanda sun yi tawaye ko da shike Allah ya lura da su.
Musa ya sauta wa mutanen Isra'ilawa ta wurin magana a waka ga Yeshurun. "ka yi ƙiba, ka kara ƙiba, ka kuma zama da ƙiba fiye da yadda za ka iya zama"
Wannan na nufin Yahweh na da ƙarfi kamar dutse kuma na iya kare mutanensa.
Wannan suna ne mai kyau da Musa ya ba Yahweh, wanda kamar dutse, na da ƙarfi kuma na iya kare mutanensa. Fasara kamar yadda yake a 32:3.
Isra'ilawan sun sa Yahweh jin kishi.
Musa ya yin wakokinsa wa mutanen Isra'ila.
"Mutanen Isra'ila sun yi haday"
Wannan na nufin cewa Isra'ilawan sun san game da waɗannan allolin.
Musa na magana da Isra'ilawan kamar mutane dayawa.
Musa na magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne.
A nan an kira Yahweh dutsen saboda ya na da ƙarfi da kuma kariya. AT: "Kun bar kariyar Yahweh"
Wannan suna ne da Musa ya ba Yahweh, wanda, kamar yadda dutse na da ƙarfi kuma ya iya kare mutanensa. Fasara kamar yadda yake a 32:3.
Wannan ya kwatanta Yahweh da mahiafi da kuma mahaifiya. Wannan na nufin Allah ya sa su rayu su kuma zama al'umma. AT: "wanda da ya zama mahaifinku ... wanda ya ba ku rai"
Musa na magana da Isra'ilawan kamar mutane dayawa.
Wannan na nufin mutanen Isra'ilawa wanda Yahweh ya ba su rai, ya kuma sa sun zama al'umma.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "zan juya daga gare su" ko "Zan daina taimake su"
"Zan ga abin da zai faru da su"
Musa na magana da Isra'ilawan kamar mutane dayawa. Ya cigaba da yin maganar Yahweh.
A nan "ni" na nufin Yahweh.
"abin da allolin karya ne"
AT: "allolin wofi"
"mutanen da ba su cikin taron mutane ɗaya"
Fasara "wawa" kamar yadda yake a 32:5.
Musa na magana da Isra'ilawan kamar mutane dayawa. Ya cigaba da yin maganar Yahweh.
Yahweh ya kwatanta fushinsa da wuta. Wannan ya nanata ikonsa na hallaka abin da ke na shi fushi.
AT: "Na kuna wuta saboda ina fushi, kuma na ci ... na hallaka ... na sa " ko "a loƙacin da na ke fushi, Ina hallaka maƙiya na kamar wuta, kuma ina bata komai a duniya da kuma a cikin ... Ina hallaka ... Ina shirya"
"har zuwa duniyar mutuwa"
Musa na magana da Isra'ilawan kamar mutane dayawa. Ya cigaba da yin maganar Yahweh.
Yahweh na maganar mumunan abubuwa da za su faru da Isra'ilawan kamar su wasu abubuwa ne kman datti da zai iya tara akan Isra'ilawan. AT: "Zain tabatar cewa mumunan abubuwa dayawa sun faru da su"
A nan Yahweh ya kwatanta mumunan abubuwan da zai tabatar ya faru da Isra'ilawan da wanin da ke harba kibiyoyi daga baka. AT: "Zan yi duk abin da zan iya don in ƙashe su"
AT: "Za su rasa ƙarfi su kuma mutu domin su na jin yunwa"
AT: "ƙuna mai zafi" su ne 1) Isra'ilawan za su sha wahala da zazzabi ko 2) wurin zai zama da zafi sosai a loƙacin damina da rani. AT: "Za su ... yunwa, da zufa mai zafi kuma ambali'a zai cinye su" ko "Za su ... yunwa, kuma za su mutu daga zafi da kuma ambali'a"
Haƙoran da dafin magana ne na dabbobin da sun yi amfani da waɗannan abubuwan su kashe-kashen. AT: "Zan tura dabbobin jeji su ciza su, da kuma abubuwan da ke rarrafe a ƙura su cize su, su kuma sa masu dafi"
Musa na magana da Isra'ilawan kamar mutane dayawa. Ya cigaba da yin maganar Yahweh.
A nan "takobi" na wakilcin sojojin makiyan. AT: "Sa'ad da Isra'ilawan su na waje, maƙiyan za su ƙashe su"
Yaweh ya yi maganar jin tsoro kamar mutum ne da ya zo ya ƙashe waɗanda suke wani gida. AT: "za ku mutu saboda ku na jin tsoro"
An hada waɗannan magana don a bayana yadda mutane daga shekaru dabam dabam za su mutu.
AT: "Na ce. 'Zan ... ɗan adam"
"Zan sa dukka mutane su manta da su"
Musa na magana da Isra'ilawan kamar mutane dayawa. Ya cigaba da yin maganar Yahweh.
"Na ji tsoron tsonakar maƙiyin"
AT: "wai maƙiyin zai tsokane ni" ko "wai maƙiyin zai sa in ji fushi"
Yahweh na maganar maƙiyan kamar su mutum ɗaya ne. AT: "maƙiyi na" ko "makiya na"
"rasa fahimta"
A nan "hannu" na wakilcin ƙarfi da ikon mutum. Ɗaukaka ƙarin magana ne na cin nasara da maƙiya. AT: "Mun yi nasara domin mun fi ƙarfi"
Musa ya yi wakoki wa mutanen Isra'ila.Ya cigaba da yin maganar Yahweh.
Musa ya bayyana wani abin da ya so da gaskiya ne, amma ya san cewa ba su da hikima kuma basu fahimci cewa rashin biyayyarsu zai sa Yahweh ya sauko da wannan hukuncin a kansu ba.
AT: "me ne zai faru da su"
Musa ya yi wakoki wa mutanen Isra'ila.Ya cigaba da yin maganar Yahweh ya kuma gaya masu game da abin da ya kamata sun fahimta inda su na da hikima.
Musa ya yi amfani da tambaya domin ya kwaɓe mutanen don rashin hikimar fahimitar dalilin da maƙiyarsu na cin nasara a kansu.
AT: "Ta ya ya sojan maƙiya ɗaya zai kori mutane dubu, kuma sojan maƙiya biyu su sa mutane dubu goma guguwa"
Kalmar "Dutse" na nufin Yahweh wanda ke da ƙarfi da kuma ikon kare mutanensa. AT: "sai dai Yahweh, Dutsensu, ya mikasu"
"Dutsen" suna ne da Musa ya ba wa Yahweh, wanda, kamar dutse, na da ƙarfi da kuma ikon kare mutanensa. Fasara "Dutse"kamar yadda yake a 32:3.
Gumakan maƙiyan da allolin karyan ba su da iko kamar Yahweh.
"ba haka kadai maka ce ba, amma maƙiyanmu sun ce haka ma"
Musa ya yi wakoki wa mutanen Isra'ila.Ya cigaba da yin maganar Yahweh.
Musa ya kwatanta maƙiyan da su ke bautar allolin karya da mugayen mutanen da sun yi zama a Saduma da Gomarata kuma da inabin da suke ba da 'ya'ya masu dafi. Wannan na nufin maƙiyansu mugaye ne kuma za su sa Isra'ilawan su mutu Idan Isra'ilawan sun fara yi kaman mutanen da suke zama a kewaye da su.
Inabin magana ne na taron mutane. "na nan kamar inabinsu rashen inabi ne da ya yi girma a gonakin Saduma da Gomarata" ko AT: "su na yin mugunta kamar yadda mutanen da sun yi zama a Saduma da Gomarata sun yi"
"nonan amfaninsu"
Musa ya yi wakoki wa mutanen Isra'ila.Ya cigaba da yin maganar Yahweh.
Musa ya cigaba da kwatanta maƙiyan mutanen Isra'ila da 'ya'yan inabi da ke ba da 'ya'ya masu dafi da ruwan inabi. Wannan na nufin maƙiyansu mugaye ne.
"macizai"
Wannan tambaya na nanata cewa shirin Yahweh wa mutanen Isra'ila na ajiye a ɓoye kamar abubuwa masu daraja. AT: "Na san abin da na shirya zan yi wa mutanen Isra'ilawa ba wa maƙiyansu ba, kuma na rufe waɗannan shirin kamar yadda wani zai rufe dukiyarsa masu daraja."
Musa ya yi wakoki wa mutanen Isra'ila. Wannan ne karshen maganar Yahweh da ya fara a 32:19.
Kalmomin "sakamako" da "ramako" a takaice na nufin abu ɗaya. AT: "Zan sami sakamako in kuma hukunta maƙiyan Isra'ila"
hukunta ko ba mutum lada don abin da ya yi
Mumunan abu ya faru da su. AT: "ba su da taimako"
"loƙaci na don in hallaka su"
Yahweh ya yi maganar mumunun abubuwan da za su faru da maƙiyansa kaman mumunan abubuwan mutani ne da suke guduwa don su hukunta su. AT: "kuma zan hukunta su da sauri"
Musa ya yi wakoki wa mutanen Isra'ila.
AT: "Gama Yahweh zai yi wa mutanensa abin adalci"
"zai ji cewa ya na son ya taimake bayinsa"
Musa ya yi wakoki wa mutanen Isra'ila.
Yahweh ya tsautawa mutanen Isra'ila don neman kariya daga wasu alloli. AT: "Gani, allolin da Isra'ilawa sun yi tunani cewa zasu kare su ba su zo su taimake su ba. "
A nan yahweh ya tsokane mutanen Isra'ila don mika hadayu wa wasu alloli. AT: "Alloli da Isra'ilawan sun mika nama da ruwan inabi, ba su zo sun taimake su ba."
Yahweh ya faɗa wannan domin ya tsokane Isra'ilawan. Ya san waɗannan allolin ba za su iya taimake su ba. AT: "Waɗannan allolin ba su iya tashi su taimaka ko kare ku ba"
Musa ya yi wakoki wa mutanen Isra'ila.
"Ni, Ni kai na" ko Ni kadai." Yahweh ya maimaita "Ni" don ya nanata cewa shi ne kadai Allah.
"Na daga hannu na zuwa sama na rantse" ko "Na yi rantsuwa." Daga hannu alama ne na yin rantsuwa.
"kamar tabacin yadda na dawwama har abada" ko "Na rantse da rai na wadda babu iyaka." Wannan maganan ya tabatar wa mutanin cewa abin da Allah ya faɗa a 32:41-32:42 zai faru.
Musa ya yi wa mutanen Isra'ila waka.
Wannan na nufin Allah na kan shiri domin ya hukunta maƙiyansa. AT: "Sa'ad da na wasa takabina mai walƙiya" ko "Sa'ad da na yi shirin hukunta maƙiya na"
A nan "hannu" na wakilcin dukkan jiki. AT: "sa'ad da na yi shirin hukunta mugayen"
Musa ya yi wa mutanen Isra'ila waka.
Yahweh ya yi maganar kibiyoyi kamar mutani ne da zai iya ba su barasa ya kuma sa su bugu, da kuma takobi kamar mutum ne da ke jin yunwa sosai da har zai iya cin dabba kafin janye jinin. Wannan magana ne na soja da ke amfani da kibiyoyi da takobi don ya ƙashe maƙiya dayawa. Wannan kuma magana ne na Yadda Yahweh ke ƙashe maƙiyansa. (Dubi: and and
AT: "daga tsawon gashin kan maiƙiyan."
Wannan ne karshen wakar Musa.
Masu na magana da mutanen dukka alumman kaman su na nan su na ji.
A nan "jinin bayinsa" na wakilcin rayukan bayinsa marasa laifi da na ƙashe. AT: "gama zai ɗauki fansa a kan makiyansa, wanda sun ƙashe bayinsa"
AT: 1) "yi magana ... yin magana" 2) "yi waka ... yin waka."
A nan "kunnuwa" na wakilcin mutanen da kansu kuma na nanata cewa Musa ya so ya tabatar sun ji wakon da kyau. AT: "wa mutanen don su tabatar sun ji"
"Musa ya ce wa mutanen Isra'ila"
Wannan ƙarin magana ne. "ku ba da hankalinku" ko "Yi tunani akai"
AT: 1) "Na shaida maku," ga abin da Yahweh ya ce zai yi wa Isra'ilawa idan sun yi rashin biyayya, ko 2) "Na urmarce ku," ga abin da Yahweh na umartan su su yi.
"'ya'yanku da zuriyarku"
"wannan umarni shi ne"
AT: "abu mani muhimminci"
"domin za ku rayu indan kun yi biyayya da shi"
Tsawon kwanaki magana ne na tsawon rai. AT: "iya rayuwa na tsawan loƙaci." Fasara waɗannan kalmomi kamar yadda suke a 4:25.
Wannan sunar iyakan dutsen da ke Moab.
" Abarim, kuma ya hau samar Dutsen Nebo"
Wannan wuri ne mai tudu sosai a duwatsun Abarim.
"a ɗayar gefen rafi daga Yariko"
Yahweh ya gama magana da Musa.
Wannan wata hanya ne na faɗa cewa ruhun Musa zai sami ruhuyin daginsa a ƙasar matattu. AT: "sadu da kakaninka wanda sun mutu kafin kai" (Dubi: )
Wannan ne sunar dutsen da ke iyakan Edom.
Wannan sunar wuri ne a jejin da Musa ya yi wa Allah rashin biyayya.
Wannan sunar jejin da ke kudun iyakar Juda.
1Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya albarkaci mutanen Isra'ila da ita kafin rasuwarsa. Ya ce:2Yahweh ya taho daga Sinai, kuma ya taso daga Seyir a bisansu. Ya haskaka daga Dutsen Faran, yazo da dubun dubbai goma na tsarkaka. A cikin hannun damarsa akwai tarwatsun walƙiya.3Hakika, yana ƙaunar mutane; dukkan tsarkakansa suna cikin hannunka, suna kuma russunawa a ƙafafunka; suna karɓar maganganunka.4Musa ya umarta mana ka'idodi, abin gãdo domin taro na Yakubu.5A sa'annan akwai sarki a Yeshurun, lokacin da shugabannin mutane suka taru, dukkan kabilar Isra'ila suka taru.6Bari Ruben ya rayu kada ya mutu, amma bari mutanensa su zama ƙalilan.7Wannan ce albarkar Yahuda, Musa ya ce: Ku saurara, Yahweh, ga muryar Yahuda, a sake dawo da shi ga mutanensa. Kuyi yaƙi dominsa; ku zama taimako gãba da maƙiyansa.8Game da Lebi, Musa ya ce: Da Tumim ka da Yurim ka na aminanka ne, waɗanda ka gwada su a Massa, waɗanda kayi jayayya da su a ruwayen Meriba.9Mutumin da ya ce game da mahaifinsa da mahaifiyarsa, "Ni ban gansu ba." Bai kuma shaidi 'yan'uwansa maza ba, hallau bai yi la'akari da 'ya'yansa na cikinsa ba. Gama ya tsare maganganunka ya kuma kiyaye alƙawarinka.10Yana koya wa Yakubu dokokinka da Isra'ila shari'arka. Zai sa turare a gabanka da dukkan baye- baye na ƙonawa akan bagadinka.11Kasa albarka, Yahweh, bisa mallakarsa, ka karɓi aikin hannunsa. Ka rushe kwankwasan waɗanda suka tashi gãba da shi, da mutanen da suka ƙi shi, domin kada su sake tashi kuma.12Game da Benyamin, Musa ya ce: Shi wanda Yahweh ya ke ƙauna yana zaune lafiya a gefensa; Yahweh ya kãre shi dukkan rana, yana zaune tsakiyar hannuwan Yahweh.13Game da Yosef, Musa ya ce: Bari Yahweh ya albarkaci ƙasarsa da abubuwa masu daraja na sama, tare da raɓa, kuma tare da zurfafa da ke kwance a ƙasa.14Bari ƙasarsa ta zama da albarkar abubuwa masu daraja na girbi dana rana, da abubuwa masu daraja na watanni,15tare da kyawawan abubuwa daga duwatsun dã, da kuma abubuwa masu daraja daga dawwamammun tuddai.16Bari a albarkaci ƙasarsa da abubuwa masu daraja na duniya duk da cikarta, tare kuma da fatan alheri ga wanda ya zauna cikin saura. Bari albarka ta sauka a kan Yosef, da a kan shi wanda ya zama sarki bisa 'yan'uwansa maza.17Ɗan fari na bijimi, mai daraja ne shi, ƙahonninsa kamar ƙahonnin bijimin jeji ne. Da su zai tunkuɗe mutane, dukkansu, har ƙarshen duniya. Waɗannan su ne dubbai goma na Ifraimu; waɗannan su ne dubbai na Manasa.18Game da Zebaluna, Musa ya ce: Kayi farinciki, Zebaluna, cikin fitarka, kai kuma, Isakar, a cikin rumfunarka.19Zasu kira mutane zuwa duwatsu. A can zasu miƙa hadayu na adalci. Domin zasu sha wadatar tekuna, daga kuma yãshin da ke a bakin teku.20Game da Gad, Musa ya ce: Mai albarka ne wanda ya faɗaɗa Gad. Zai zauna a can kamar zakanya, zai kuma farke hannu ko ƙoƙon kai.21Ya samar wa kansa sashe mafi kyau, domin akwai rabon ƙasa da aka keɓe domin shugaba. Yazo da shugabannin mutane. Ya aiwata adalcin Yahweh da dokokinsa da Isra'ila.22Game da Dan, Musa ya ce: Dan ɗan zaki ne da ya yi tsalle waje daga Bashan.23Game da Naftali, Musa ya ce: Naftali, ya ƙoshi da tagomashi, cike ya ke da alheran Yahweh, ya mallaki ƙasar daga yamma da kudu.24Game da Ashiru, Musa ya ce: Mai albarka ne Ashiru fiye da sauran 'ya'ya maza; bari ya zama karɓaɓɓe ga 'ya'uwansa maza, bari ya tsoma ƙafarsa cikin man zaitun.25Bari ƙurfan birninka su zama na baƙin ƙarfe da tagulla; dukkan kwanakin ranka, haka ma tsaron lafiyarka.26Babu ko ɗaya kamar Allah, Yeshurun - mai gaskiyan nan, mai hawa cikin sammai ya kawo maka taimako, kuma cikin darajarsa bisa gajimarai.27Allah madawwami mafaka ne, a ƙarƙashi kuma dawwamammun hannuwa. Yakan kori maƙiya daga gaban ka, sai kuma ya ce, "Hallaka!"28Isra'ila ta zauna lafiya. Maɓulɓular Yakubu tana tsare cikin ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi; labudda, bari sammansa su zubo raɓa a kansa.29Albarkunka da yawa, Isra'ila! Wane ne kamarka, mutane da Yahweh ya ceta, garkuwar taimakonka, da takobin ɗaukakarka? Magabtanku zasu zo gare ku da rawar jiki, zaku tattake masujadarsu.
Musa ya fara albarkace kabilun Isra'ila. Masu ya fadi albarkan kamar waka.
Musa ya kwatanta Yahweh da tashiwar rana. AT: "Sa'ad da Yahweh ya taho daga Sinai, ya yi masu kamar rana ne da ya fita daga Sayir sai ya kuma haskaka daga Dutsen Faran"
"bisa mutanen Isra'ila"
AT: 1) "a hannun damansa inda harshen wuta" ko 2) "Ya ba su dokar wuta" ko 3) "ya zo daga kudu, kasan gangaran dutsen shi."
Musa ya cigaba da albarkace kabilan Isra'ila, wanda ya fara yi a 33:1; Masu ya fadi albarkan kamar waka.
Waɗannan Aya na da wuyan fahimta.
"mutanen Isra'ila"
Wannan "sa" da "ka" na nufin Yahweh. AT: "dukkan tsarkakan Yahweh suna hannunsa ... ƙafaffunsa ... maganganunsa"
Hannun magana ne na iko da kariya. AT: "ka kiyaye dukkan tsarkakan mutanen sa"
"dukiya"
Musa ya cigaba da albarkace kabilan Isra'ila, wanda ya fara yi a 33:1; Masu ya fadi albarkan kamar waka.
Aya biyar na da wuyan fahimta.
"Yahweh ya zama sarki" (UDB)
Wannan wani suna ne na Isra'ila. Fasara shi yadda yake a 32:15.
Wannan ya fara albarkun Musa ga ko wane kabilun Isra'ila.
AT: 1) "kuma bari mutanensa su zama ƙalilan" ko 2) "ko da shike mutanensa ƙalilan ne."
Musa ya cigaba da albarkace kabilan Isra'ila, wanda ya fara yi a 33:1; albarkun guntun waka ne.
A nan " muryar Yahuda" na nufin kuka da addu'o'in mutanen Yahuda. AT: "a loƙacin da mutanen Yahuda sun yi maku addu'a"
AT: "taimake shi ya yake"
Musa ya cigaba da albarkace kabilan Isra'ila, wanda ya fara yi a 33:1; albarkun guntun waka ne.
Waɗannan ne tsarkakan duwatsun da babban firist ke ɗauka akan tassa a na kuma amfani don ya yi tabatar da nufin Allah. A nan "ka" na nufin Yahweh.
"tsarkakanka" ko "wanda ya na so ya faranta maka rai." Wannan na nufin kabilan Lewi.
Fasara shi yadda yake a 6:16. Masu juyi na iya kara bayani da cewa: "Sunar 'Massa' na nufin 'gwaji."'
Fasara shi yadda yake a 6:16. Masu juyi na iya kara bayani da cewa: "Sunar 'Meriba' na nufin 'gardama' ko 'faɗa'"
Musa ya cigaba da albarkace kabilan Isra'ila, wanda ya fara yi a 33:1; albarkun guntun waka ne. Ya cigaba da kwatanta kabilan Lawi, wanda ya fara yi a 33:8.
A nan "magana" na nufin umarnen Yahweh. AT: "gama sun yi biyayya da umarnenka"
Waɗannan kalmomin na nufin kula da kuma kare. Su magana ne na "yin biyayya," amma a nan, a fasara su kalma-kalma domin su na nufin a zahiri loƙacin da Lawiyawa sun ƙashe mutanen da suke tawaye da Yahweh.
Musa ya cigaba da albarkace kabilan Isra'ila, albarkun guntun waka ne. Ya cigaba da kwatanta kabilan Lawi, wanda ya fara yi a 33:8.
Musa na magana da Yahweh, don haka duka waɗannan kalmomin jam'i ne.
Musa ya cigaba da albarkace kabilun Isra'ila; albarkun wakoki kadan ne. Ya cigaba da kwatanta kabilar Lewi, wanda ya fara yi a 33:8.
"ka ji daɗi da" ko "ka ji daɗin karban"
A nan "hannu" na nufin dukkan mutumin. AT: "dukka aikin da yake yi"
A na ɗaukar kwankwaso kamar tushen ƙarfi. AT: "Ɗauki ƙarfin " ko "hallaka sifan"
AT: "tashi don yin fada ... sa wani a damuwa sosai"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "yi fada da"
Musa ya cigaba da albarkace kabilun Isra'ila; albarkun wakoki kadan ne.
A nan Musa na nufin mutanen kabilan Benjamin. AT: "Waɗanda Yahweh ke ƙauna na raye"
AT: "na rayuwa a inda babu wanda zai yi lahani"
AT: 1) Yahweh na kiyaye mutanen Benjamin da ikonsa ko 2) Yahweh na zama a tudun yankin kabilar Benjamin. A duka juyin, na nufin Yahweh na lura da su.
Musa ya cigaba da albarkace kabilun Isra'ila; albarkun wakoki kadan ne.
Wannan na nufin kabilan Ifraim da kuma kabilan Manassa. Dukka kabilun daga zuriyar Yusuf ne.
AT: "Bari Yahweh ya albarkaci ƙasarsu"
"da raɓa masu daraja daga sama" ko "da ruwan sama masu daraja daga sama"
ruwan da ye yin kumfa a ganyayyaki da ciyawa da safe. Fasara kamar yadda yake a 32:1.
Wannan na nufin ruwan da ke ƙarƙashin ƙasa.
Musa ya cigaba da albarkace kabilun Isra'ila; albarkun wakoki ne kadan. Ya cigaba da kwatanta kabilan Yusuf, wanda ya fara yi a cikin 33:13.
AT: "Bari Yahweh ya albarkace ƙasarsa." Fasara kamar yadda yake a 33:13.
"da amfanin gona mafi ƙyau da rana ke sa ta yi girma"
"da amfanin gona da ke girma a wata wata"
Mai yiwuwa Musa na nufin abinci ne. AT: "amfani mafi ƙyau ... amfani mafi daraja"
"duwatsun da suke da dadewa"
"tuddan da za su rayu har abada"
Musa ya cigaba da albarkace kabilun Isra'ila; albarkun wakoki ne kadan. Ya cigaba da kwatanta kabilan Yusuf, wanda ya fara yi a cikin 33:13.
AT: "Bari Yahweh ya albarkace ƙasarsa." Fasara kamar yadda yake a 33:13.
AT: "yawan abin da yake sarrafawa"
AT: "Yahweh, wanda ya yi magana da Musa daga jeji da wuta ke ci"
Wannan magana ne na mutum da ke sa hannunsa a kan ɗa, ya na kuma rokan Allah ya albarkaci ɗan. Mutumin anan Yahweh ne. AT: "Bari Yahweh ya albarkace Yusuf kamar yadda mahaifi ke albarkace ɗansa"
A nan "kan" da "saman kan" na nufin dukkan mutumin kuma su na nufin zuriyar Yusuf. AT: "sauko a kan zuriyar Yusuf"
Wata ma'ana mai yiwuwa shi ne "goshi."
Musa ya cigaba da albarkace kabilun Isra'ila; albarkun wakoki ne kadan. Ya cigaba da kwatanta kabilan Yusuf, wanda ya fara yi a cikin 33:13.
Bijimin magana ne na abu babba da kuma ƙarfi. Kalmar "ɗan fari" magana ne na girma. AT: "Mutane za su girmama zuriyar Yusuf, wanda su na nan dayawa da kuma ƙarfi"
Ƙahon magana ne na ƙarfi. AT: "ya na da ƙarfi kamar"
Tunkuɗewa da ƙaho magana ne na ƙarfi. AT: "Ya na da ƙarfi sosai da har zai tunkuɗ"
Wannan na nufin kabilan Ifraimu za su fi kabilan Manassa ƙarfi. AT: "mutanen Ifraimu, dubbai goma ... mutanen Manassa, dubbai"
Musa ya cigaba da albarkace kabilun Isra'ila; albarkun wakoki kadan ne. Ya yi magana da kabilun Zebaluna da Issakar kaman su mutum ɗaya ne.
Mutanen Zebaluna su na kusa da Tekun Mediterranean. Su na yin tafiya a ruwa su kuma yi kasuwanci da sauran mutane. Mutanen Issakar sun fi son zamar lafiya da kuma noma da kiwon tumaki.
"A wurin ne za su miƙa"
"karbabben hadayu" ko "hadayun da sun dace"
AT: 1) za su yi kasuwanci da mutanen tsalakin teku 2) sun fara amfani da kasa a yin tukwance.
Kalmar Yahudanci "sha" a nan na nufin yadda yaro ke shan nonon mahaifiyarsa. A
Musa ya cigaba da albarkace kabilun Isra'ila; albarkun wakoki kadan ne.
AT: 1) "Bari Yahweh ya albarkaci Gad ya kuma ba shi ƙasa dayawa da zai zauna" ko 2) "Mutane su ce wai Yahweh na da kyau saboda ya ba wa Gad ƙasa dayawa ya zauna"
Wannan na nufin mutanen Gad su na da ƙarfi , za su ci nasara da makiyansu a yaki.
Musa ya cigaba da albarkace mutanen Isra'ila; albarkun wakoki kadan ne. Ya cigaba da kwatanta kabilan Gad kamar mutum ɗaya, wanda ya fara yi a 33:20.
Wannan na nufin babban ƙasa da shugaba ke ɗauka.
"Sun hadu da dukka shugabannin Isra'ilawa"
"Sun yi biyayya da dukkan abubuwan da Yahweh ya umarce Isra'ilawan"
Musa ya cigaba da albarkace kabilan Isra'ila, albarkun wakoki ne kadan.
Mutanen Dan su na da ƙarfi kaman ɗan zaki, kuma su na kai hari wa makiyansu da sun zauna a Bashan.
Musa ya cigaba da albarkace kabilun Isra'ila; albarkun wakoki ne kadan. Ya yi magana akan zuriyar Naftali kaman su mutum ɗaya.
An yi maganar yadda Yahweh ya ji daɗin Naftali kaman "tagomashi" abinci ne da Naftali ya ci da har ya daina jin yunwa. AT: "wanda yake da dukka kyauwawan abubuwan da yake so, saboda Yahweh ya ji daɗinsa"
An yi maganar Albarku kaman su abinci ne da Naftali ya ci har ya koshi. AT: "wanda Yahweh ya albarkace domin ya kasance da dukka abin da yake bukata"
Musa ya yi magana kaman kabilan naftali ɗaya ne.
Wannan na nufin ƙasa ta Tafkin Galili. A na iya sa cikakken wannan bayanin a bayyane.
Musa ya cigaba da albarkace kabilun Isra'ilawa; albarkun wakokin kadan ne.
A na amfani da man zaitun don cin abinci da kuma don fata, da ƙafa, da kuma hannuwa. Ƙafan na da datti, don haka, sa ƙafan a man zaitun batta man mai daraja ne. AT: "na da man zaitun dayawa da har na iya ɓattawa"
Musa ya yi magana da kabilan Ashiru kamar su mutum ɗaya ne.
Birane na da babban ƙurfi a kofofinsu domin karewa daga makiya. AT: "Bari ka tsira daga harin makiyanku"
Wannan wani suna ne na mutanen Isra'ila. Na nufin "na gari." Fasara kamar yadda yake a 32:15.
Wannan kammanin Yahweh ne da na hawa cikin sammai kamar sarki a kan karusarsa da yake tafiya fagen daga. AT: "hawa cikin sammai ... bisa gajimarai kaman sarki a kan karusarsa"
"don ya taimakeku." Musa na magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne.
"Mafaka," na nufin tsara ko wurin da babu damuwa. AT: "Allah madawwami zai kiyaye mutanensa"
Kalmomin "dawwamammun hannuwa" magana ne na alkawarin Yahweh na kiyaye mutanensa har abada. AT: "zai taimaka ya kuma lura da mutanensa har abada"
Musa na maganar loƙacin nan gaba kamar zamanin da ta wuce domin ya nanata cewa abin da ya na faɗa zai faru. AT: "zai kori ... zai ce"
Musa na magana da Isra'ilawan kamar su mutum ɗaya ne, don haka kalmar "ka" da umarnin "hallaka" ɗaya ne.
Idan wannan maganan ba zai yiwu a harshenku ba, za ku iya sa a yadda ya kamata. AT: "zai gaya maku ku hallakar da su!"
AT: 1) Musa ya yi maganar loƙacin nan gaba kamar zamanin da ta wuce domin ya nanata cewa abin da yake faɗawa zai faru, "Isra'ila ta zauna ... Maɓulɓular Yakubu tana tsare" ko 2) Musa na albarkace Isra'ila, "bari Isra'ila ta zauna ... kuma bari Maɓulɓular Yakubu tana tsare."
AT: 1) gidan Yakubu ko 2) zuriyar Yakubu.
An yi maganar yawan raɓan kamar ana ruwan samma. AT: 1) "bari raɓa dayawa ya rufe ƙasan kaman ruwan samma" ko 2) Masu ya na faɗa abin da zai faru nan gaba, "raɓa dayawa zai rufe ƙasan kamar ruwan samma."
ruwan da ke kumfa a ganyayyaki da ciyawa da safe. Fasara kamar yadda yake a 32:1.
Musa na magana da Isra'ilawa kamar su mutum ɗaya.
AT: "Babu wani kabila kamarka, mutane da Yahweh ya ceta ...ɗaukaka."
Wannan na maganar yadda Yahweh ya kare Isra'ila daga makiyansu da kuma sa su su kai hari ga makiyansa.
Kalmar "garkuwa" magana ne na Karewa da tsarewa da Yahweh na yi wa Isra'ilawa. AT: "wanda na kare ku da kuma taimake ku"
Kalmar "takobi" magana ne na ikon yin ƙisa da takobi domin cin nasara a yaki. AT: "wanda ya na barin ku ku ci nasara a yaki, ku kuma samu ɗaukaka"
AT: 1) "Isra'ilawan za su hallaka wuraren da mutanen na bautan allolin karya" ko 2) "Isra'ilawan za su yi tafiya a bayan makiyansu sa'ad da sun yi nasara da su.
1Musa ya haura daga filin Mowab zuwa Dutsen Nebo, zuwa ƙwolƙwolin Fizga, wacce take hannun riga da Yariko. A nan Yahweh ya nuna masa dukkan ƙasar Giliyad har ya zuwa Dan,2da dukkan Naftali, da ƙasar Ifraimu da ta Manasa, da dukkan ƙasar Yahuda, har ya zuwa tekun kudu,3da Nageb, da filin Kwarin Yariko, Birnin Itatuwan Dabino, har ya zuwa Zowar.4Yahweh ya ce masa, "Wannan ita ce ƙasar dana rantse wa Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu, cewa, "Ni zan bada ita ga zuriyarku.' Na yardar maka ka ganta da idanunka, amma ba zaka je can ba."5Sai Musa bawan Yahweh, ya rasu a nan ƙasar Mowab, kamar yadda maganar Yahweh ta alƙawarta.6Yahweh ya bizne shi a cikin kwari cikin ƙasar Mowab mai hannun riga da Bet Feyor, amma ba wanda yasan inda kabarinsa ya ke har wa yau.7Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa'ad da ya rasu, idanunsa basu dushe ba ƙarfinsa kuma bai ragu ba.8Mutanen Isra'ila suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab har kwana arba'in, sai kwanakin makoki domin Musa suka ƙare.9Yoshuwa ɗan Nun yana cike da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Mutanen Isra'ila suka saurare shi kuma suka yi abin da Yahweh ya umarci Musa.10Ba wani annabi da ya taɓa tashi a Isra'ila kamar Musa, wanda Yahweh ya san shi fuska da fuska.11Ba a taɓa yin wani annabi kamarsa ba a cikin dukkan alamu da mu'ujizai waɗanda Yahweh ya aike shi ya yi a ƙasar Masar, wurin Fir'auna, da dukkan barorinsa, da dukkan ƙasarsa.12Ba a taɓa yin wani annabi kamarsa ba a dukkan manyan, ayyukan ban tsoro da Musa ya yi a idanun dukkan Isra'ila.
Wannan ne tudun Dutsen Fizga wanda yake arewancin sashin dutsen Abarim. Fasara kaman yadda ya ke a 32:48.
Fasara kaman yadda ya ke a 3:17.
Wannan wani suna ne na Yariko.
Wannan gari ne a Mowab. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 3:28.
"gani wa kanka"
Wannan na nufin loƙacin da an rubuta wannan ko an gyara, ba zuwa wannan loƙacin a ƙarni ashirin da ɗaya ba.
Wannan na nufin idanunsa da jikinsa su na da ƙarfi da kuma lafiya.
Fasara kamar yadda yake a 1:37.
Marubucin na magana kaman Yoshuwa abu ne kuma ruhun abu ne da a na iya sa a cikin bukiti. AT: "Yahweh ya sa Yoshuwa ... ya zama da hikima"
AT: "Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa don ya keɓe Yoshuwa don Yoshuwan ya bauta masa."
Wannan ƙarin magana ne. Na nufin Yahweh da Musa su na abokantaka sosai.
"wanda ya yi dukkan manyan"
1Ya zamana fa bayan mutuwar Musa bawan Yahweh, sai Yahweh ya yi magana da Yoshuwa ɗan Nun, babban mataimakin Musa, ya ce,2"Bawana Musa, ya rasu. Yanzu fa, ka tashi, ka haye wannan kogin Yodan, da kai da dukkan mutanen nan, zuwa cikin wannan ƙasa da zan ba su - ga mutanen Isra'ila.3Na rigaya na ba ku dukkan inda sawun ƙafafunku za su taka. Na baku ita, kamar yadda na yi wa Musa alƙawari.4Daga jejin Lebanon, har zuwa babban kogin Yufaratas, dukkan ƙasar Hatiyawa, da Babban Teku, inda rana take faɗuwa, za ta zama ƙasarku.5Ba wanda zai iya tsayayya da kai dukkan kwanakin ranka. Zan kasance tare da kai kamar yadda na kasance da Musa. Bazan yasheka ba ko in bar ka.6Ka dage ka yi ƙarfin hali. Za ka sa mutanen nan su gaji ƙasar da na alƙawarta wa kakanninsu zan ba su.7Ka dage ka yi ƙarfin hali sosai. Ka yi hankali ka yi biyayya da dukkan dokokin da bawana Musa ya umarce ka. Kada ka kauce masu zuwa dama ko hagu, domin ka yi nasara duk inda ka tafi.8Kullum za ka riƙa yin magana a kan wannan littafin shari'a. Za ka riƙa binbini a kansa dare da rana domin ka yi biyayya da dukkan abin da aka rubuta a ciki. Sa'annan za ka zama da albarka da nasara.9Ba ni ne na urmace ka ba? Ka ƙarfafa ka yi ƙarfin hali! Kada ka ji tsoro. Kada ka karaya. Yahweh Allahnka ya na nan tare da kai duk inda ka tafi."10Sai Yoshuwa ya umarci shugabannin jama'a,11"Ku tafi cikin sansanin ku dokaci mutanen, 'Ku shirya wa kanku guzuri. Cikin kwana uku za ku haye wannan Yodan ku mallaki wannan ƙasa da Yahweh Allahnku ya ke ba ku gãdo."'12Ga Rubainawa, da Gadawa da rabin kabilar Manasse, Yoshuwa ya ce,13"Ku tuna da maganar da Musa bawan Yahweh, ya umarce ku sa'ad da ya ce, 'Yahweh Allahnku ya na ba ku hutawa, ya na kuma ba ku wannan ƙasa.'14Matanku, da 'yan ƙanananku, da dabbobin ku za ku barsu a ƙasar da Musa ya ba ku, can ƙetaren Yodan. Amma jarumawanku za su tafi da 'yan 'uwanku su taimaka masu15har sai Yahweh ya ba 'yan 'uwanku hutawa kamar yadda ya baku. Haka su ma za su mallaki ƙasar da Yahweh Allahnku ke ba su. Sa'annan za ku dawo zuwa taku ƙasar ku gaje ta, ƙasar da Musa bawan Yahweh ya baku can ketaren Yodan inda rana take fitowa."16Sa'annan su ka amsa wa Yoshuwa, su ka ce, "Za mu yi dukkan abin da ka umarce mu, kuma duk in da ka aike mu za mu je.17Za mu yi maka biyayya kamar yadda muka yi wa Musa biyayya. Allahnka Yahweh dai ya kasance tare da kai, kamar yadda ya kasance da Musa.18Duk wanda ya yi tawaye gãba da umarninka ya kuma yi rashin biyayya da maganarka za a kashe shi. Ka dage ka yi ƙarfin hali."
Wannan shi ne sunar da Allah ya bayyana wa mutanensa a tsohon Alkawari. Duba translationWord page game da Yahweh akan yadda za ku juya shi.
Mahaifin Yoshuwa
Yă "haye" na nufin "yă ƙetere zuwa ɗayan gefen kogin." AT: "yi tafiya da wannan gefen zuwa ɗayan gefen kogin"
Kalmar nan "kai" anan na nufin Yoshuwa.
Ana maganar yadda Allah zai ba wa Isra'ilawa ƙasar a nan gaba ne kamar ya rigaya ya basu ne da daɗewa. AT: "Zan ba ku go wame wuri"
Kalmar nan "ku" na nufin Yoshuwa da al'ummar Isra'ila.
Wannan na nufin wuraren da Yoshuwa da Isra'ilawa za su je bayan sun ƙetere Kogin Urdu. AT: "duk wurin da kuka je a wannan ƙasar "
Yahweh ya cigaba da wa Musa Magana.
Kalmar nan "ku" na nufin kabilun Isra'ila ba Yoshuwa kadai ba.
A aya 5 kalamun nan "kai" da kuma "ka" na nufin Yoshuwa.
Kalmun nan "yashe" da "bar" na nufin abu ɗaya ne a takaice. Yahweh ya haɗa su ne domin yă nanata cewa ba zai yi su ba. AT: "Hakika zan kasance tare da ku a kodayaushe"
Yahweh ya ba wa Yoshuwa jerin dokokin.
Yahweh yana ƙarfafa Yoshuwa ya shawo kan fargabansa da ƙarfin hali.
AT: "Ka bi shi daidai" ko kuma "ka bi su daidai"
"cimma manufanka" ko kuma "ka kai ga manufanka"
Yahweh ya cigaba da yi wa Yoshuwa magana.
Wannan na nufin cewa Yoshuwa yă riƙa maganar littafin shari'a a kodayaushe. Kalmar nan "kodayaushe" na kara nanaci.
Kalamun nan biyu na nufin abu ɗaya ne a takaice kuma sun nanata babbar nasara.
Wato Yahweh yana umurtan Yoshuwa kenan. AT: "Na umarce ke!"
Yahweh yana umurtan Ysohuwa.
AT: "Ga zaga dukka sansanin ka umarce mutanen su shirya kayayyakinsu. A kwana uku za su je su haye Urdun su shiga su mallaki ƙasar da Yahweh Allahn yake basu su mallaka.
"mutanen Isra'ila"
Anan Yoshuwa yana kirga ranar da yake magana a matsayin rana ta fari. AT: "Bayan kwana biyu daga yau" ko kuma "Bayan gobe"
"haye" na nufin su ƙetere zuwa ɗayan gefen kogin. AT: "yi tafiya zuwa ɗaya gefen Kogin Urdun"
Kabilun Rubaina, Gad da rabin kabilar Manasse za su zaɓa su zauna a gabashin Kogin Urdu.
Wato zuriyar Rubaina kenan.
Wato zuriyar Gad.
Yoshuwa ya cigaba da wa Rubainawa da Gadawa, da rabin kabilan Manasse.
"karnen ku"
Wato gefen gabashin Kogin Urdu. Nan gaba yawancin Isra'ilawan za su bar yammacin Urdun, don haka ake ce da gefen gabas din "ƙeteren Urdu". Amma dai a wannan lokacin sun nan a gefen gabas. AT: "yammacin Kogin Urdu"
Wannan na nufin Nasarar Isra'ilawa da abokan gãbansu da ke zaune a Kan'ana da za su ci mamaye.
Wato za su yi rayuwarsu a ƙasar su kuma zauna lafiya.
Wato gefen gabashin Kogin Urdu.
Waɗannan Isra'ilawan musamman Rubainawa ne, da Gadawa, da rabin kabilar Manase suke amasa Yoshuwa.
Waɗannan jimla biyun a takaice na nufin abu ɗaya ne kuma suna nanata ne da cewa za a hukunta duk wani halin rashin biyayya.
AT: "Za mu kashe shi"
Da Isra'ilawa da Allah dukka suna duban cewa waɗannan hallayen ne masu muhimmanci ga Yashuwa yă bi a matsayinsa na zama Shugaba.
1Sai Yoshuwa ɗan Nun a asirce ya aiki mutum biyu daga Shittim magewaya. Ya ce; "Ku je, ku dubo ƙasar, musamman Yeriko." Su ka yi tafiyarsu su ka isa gidan wata karuwa mai suna Rahab, a nan ne su ka sauka.2Aka cewa sarkin Yeriko, "Duba, mutanen Isra'ila sun zo nan domin su leƙi ƙasar."3Sai sarkin Yeriko ya aika wa Rahab cewa, "Ki fito da mutanen da su ka zo wurinki waɗanda su ka shiga gidanki, gama sun zo ne domin leƙen dukkan ƙasar."4Amma matar ta rigaya ta ɗauki mutanen nan biyu ta ɓoye su. Sai ta amsa masu, "I, mutanen sun zo wurina amma ban san daga inda su ka fito ba.5Sun bar nan da sauran duhu, lokacin da ake kulle ƙofar birni. Ban san inda su ka tafi ba. Mai yiwuwa ku cim masu idan kun bi su da sauri."6Gama ta rigaya ta kai su bisa rufin ɗakinta ta rufe su da ƙeƙasheshen rama waɗanda ta shinfiɗa a bisa rufin.7Sai mutanen su ka bi su a kan hanya da ta kai su kwarin Yodan. Nan da nan aka rufe ƙofar bayan da masu bin su su ka fita.8Kafin mutanen su kwanta da dare, sai ta zo wurinsu a rufin kan ɗaki.9Ta ce, "Na sani Yahweh ya rigaya ya ba ku ƙasar kuma tsoronku ya faɗo kanmu. Dukkan waɗanda ke zaune a ƙasar za su narke a gabanku.10Mun ji yadda Yahweh ya sa ruwan Jan teku ya ƙafe dominku sa'ad da kuka fito daga Masar. Mun ji kuma abin da ku ka yi wa sarakunan nan biyu na Amoriyawa a hayin Yodan - Su Sihon da - Og waɗanda ku ka hallaka dukka.11Da dai mu ka ji haka, zukatanmu su ka narke har babu karfin hali da ya rage a cikin ko ɗayanmu. Domin Yahweh Allahnku, shi ne Allah na sama da na duniya a ƙasa.12Yanzu dai, ku rantse mani da Yahweh cewa, kamar yadda na yi maku alheri, kuma ku yi wa gidan ubana alheri. Ku bani tabbatacciyar alama13cewa za ku tsirar da ran mahaifina, da mahaifiyata, da 'yan 'uwana maza, da mata da dukkan iyalansu, za ku kuma cece mu daga mutuwa."14Mutanen su ka ce ma ta, "Ran mu a bakin na ki, har ma ga mutuwa! Idan baki tona al'amarin nan ba, idan Yahweh ya ba mu ƙasar za mu nuna maki jinkai da aminci."15Sai ta zura su ƙasa ta taga da igiya. Gidan da take zaune an gina shi cikin ganuwar birnin.16Ta ce masu, "Ku hau cikin duwatsu ku ɓoye, ka da masu bin ku su same ku. ku ɓoye a can har kwana uku bayan masu bin ku sun dawo. Sa'annan ku yi tafiyarku."17Mutanen su ka ce ma ta, "Za mu zama kuɓutattu da ga rantsuwar da mu ka rantse ma ki, idan ba ki riƙe amanar ba.18Lokacin da za mu zo ƙasar, dole ki ɗaura wannan jar igiya a tagar da ki ka zura mu, za ki kawo cikin gidan ki mahaifinki da mahaifiyarki, da 'yan'uwanki da dukkan gidan mahaifinki.19Duk wanda ya fita daga ƙofar gidanki zuwa titi, jininsu na bisa kansu, mu kuwa mun kuɓuta. Amma idan muka sa hannu a kan wanda ke cikin gida tare da ke, alhakin jininsa na kan mu.20Amma idan ki ka furta al'amarin nan, za mu kuɓuta daga rantsuwar da ki ka sa mu ka rantse maki,"21Rahab ta amsa, "Bisa ga maganar da ku ka faɗa bari ya zama haka." Sai ta sallame su, su ka tafi. Sai ta ɗaura jar igiyar a tagar.22Su ka tafi su ka haye cikin tsaunuka su ka kuma zauna can kwana uku har sai da masu bin sawun su su ka koma. masu bin sawunsu su ka yi ta neman su a kan hanya ba su sami komai ba.23Mutanen biyu su ka ƙetare su ka komo wurin Yoshuwa, ɗan Nun, su ka labarta masa dukkan abubuwan da su ka faru da su.24Su ka ce ma Yoshuwa, "Gaskiya Yahweh ya ba mu wannan ƙasar. Dukkan mazaunan ƙasar su na ta narkewa sabili da mu."
Wannan shi ne mahaifin Yoshuwa.
Wannan shi ne sunan wurin da ke gabashin Kogin Urdun. Yanan nufin "bishiyoyin Ƙirya"
Waɗannan mutanen na za su ziyarce ƙasar su samo labarin yadda Isra'ilawa za su ci mamayen ƙasar.
Wata ƙaruwa mai suna Rahab ta kare masu leƙo asirin gari, Isra'ilawa biyu daga lahani.
Hakan ya faru ne kamun masinja sarki ya yi mata magana.
Wato Rahab kenan, ƙaruwan.
...
Wannan na bayyana asalin yadda ta yi ta boye mutanen a 2:4
Wannan rufin shimfiɗaɗɗe ne kuma da ƙarfi, son haka mutane na iya tafiya a bisansa.
Wani dasa ne da ake shukawa domin zarensa, ana kuma yin kaya da su.
Mutanen sun bi su ne domin abinda Rahab ta faɗa masu a 2:4.
Wuraren da kogin ko wurin ruwan ba zurfi da mutane ke iya bi su haye ɗayan gefen da kafa
Wato kafin su yi barcin ɗare kenan.
Kalmar nan "ku" na nufin dukkan mutanen Isra'ila. (Duba:
ana iya nuna tsoro daban daban. AT: "Muna tsoronku"
Wannan na ƙwatanta matsoratan ne kamar wani kankara ne da ke narkewa har ya kare. Wannan na iya nufin 1) za su zama raunana a gaban Isra'ilawa ko kuma 2) za su warwatsu. AT: "za su tsorata ƙwarai har ma ba za su yi tsayayya da ku ba"
Rahab da cigaba da magana da 'yan leƙa asirin ƙasa na Isra'ilawa.
...
Waɗannan sunayen sarakan Amoriyawa ne.
Waɗannan jimla biyun sun nufin abi ɗaya ne, an haɗa su ne anan domin nanaci. Jimlar nan "zukatanmu sun narke" na ƙwatanta matsoratan mutanen Yerico ne da kankara da ke narkewa har yă kare.
Rahab da cigaba da magana da 'yan leƙa asirin ƙasa na Isra'ilawa.
Waɗannan maganganun nă neman tabbacci ne daga wurin 'yan leƙan asirin ƙasar.
Kalmar nan "ku" na nufin 'yan leƙan asirin ƙasa biyun ne.
Wannan wani hanya ne na ce "kada ku kashe mu"
'Yan leƙan asirin ƙasar daga Isra'ila sun ɗauki alkawarin da Rahab ta roƙa a 2:12.
Wannan karin maganar wani hanya ne na ɗaukan rantsuwa da kuma roƙon Allah yă la'anta su idan basu cika alkawarinsu ba. AT: "Idan ba mu yi abinda muka alkawari ba, bari Yahweh yă sa mu mu mutu"
'Yan leƙan asirin ƙasa daga Isra'ila sun cigaba da magana da Rahab.
Wannan karin maganar wani hanya ne na ɗaukan rantsuwa da kuma roƙon Allah yă la'anta su idan basu cika alkawarinsu ba. AT: "Idan ba mu yi abinda muka alkawari ba, bari Yahweh yă sa mu mu mutu"
'Yan leƙan asirin ƙasa daga Isra'ila sun bayyana ka'aida da suka fada a 2:15.
'Yan leƙan asirin ƙasa daga Isra'ila sun cigaba da magana da Rahab.
Jimlar na cigaba da bayyana ka'ida, yana ba da misali wana hali da ake iya shiga cikinta.
Anan "jini" na nufin mutuuwar mutumin. Ana maganar mutum ya ɗauki hakkin mutuwarsa ne kamar jini ne da ke zama a kan sa. AT: "mutuwarsu zai zama don kuskuransu"
"ba za mu zama da laifi ba"
Anan "hannu a kan" wani hanya ne na sa wani ya ji rauni. AT: "idan mun ji wa wani rauni"
'Yan leƙan asirin ƙasa biyun daga Isra'ila sun cigaba da magana da Rahab game da alkawarin da sun yi mata.
'Yan leƙan asirin ƙasa sun bukaci Rahab ta cigaba da yin shiru game da ziyararsu, ko ba za su zama da wani hakin alkawarin kare iyalin ta ba.
"ki" na nufin Rahab.
Rahab ta amince da ka'aidodin alkawarin kare iyalinta.
'Yan leƙan asirin ƙasa biyun daga Isra'ila sun bar ƙasar Yarico.
"masu bin sawun su suka koma zuwa garin, zuwa Yarico"
Wannan na nufin cewa mutanen ba su sami 'yan leƙa asirin ƙasar ba.
Wato suka komo sansanin Isra'ilawa
Wannan furuci iri ɗaya ne da ke nufin komowa zuwa wurin da Isra'ilawan suka kafa sansani.
"ƙetere" na nufin cewa sun tafi ɗayan gefen Kogin. AT: "suka yi tafiya daga wannan gefen kogin zuwa ɗayan gefen Urdun"
Wannan sunan namiji ne; mahaifin Yoshuwa.
...
Kalmar nan "mu" na nufin Isra'ila.
Mutanen ƙasar ga Isra'ila suna kamar wani abu ne da ke narkewa saboda kasancewar zafi.
1Yoshuwa ya tashi da sassafe, sai su ka yi ƙaura daga Shittim. Su ka iso Yodan, shi da dukkan mutanen Isra'ila, su ka sauka a nan kafin su haye.2Bayan kwana uku, sai shugabanni su ka ratsa ta tsakiyar zangon;3su ka umarci mutane, "Lokacin da ku ka ga akwatin alƙawari na Yahweh Allahnku, da firistoci daga kabilar Lebiyawa ɗauke da shi, sai dole ku bar nan wajen ku bi shi.4Dole ku sa ratar ƙafa dubu biyu tsakanin ku da akwatin. Kada ku je kusa da shi, domin ku iya hango inda za ku bi, da shike ba ku taɓa bin wannan hanyar ba,"5Yoshuwa ya cewa jama'a; "Ku tsarkake kanku gobe, domin Yahweh zai yi abin al'ajibi a tsakanin ku."6Sa'annan Yoshuwa ya cewa Firistoci, "Ku ɗauki akwatin alƙawari ku wuce gaban jama'a." Sai su ka ɗauki akwatin alƙawarin su ka wuce gaban jama'a da shi.7Yahweh ya cewa Yoshuwa, "A ranar yau zan maishe ka babban mutum a idanun Isra'ilawa dukka. Za su sani, kamar yadda na kasance da Musa, zan kasance da kai.8Za ka umarci Firistoci su ɗauki akwatin alƙawari, 'Lokacin da ku ka isa bakin ruwayen Yodan, dole ku tsaya cik a cikin Kogin Yodan."'9Yoshuwa ya cewa mutanen Isra'ila, "Ku zo nan ku saurari maganar Yahweh Allahnku.10Ta wurin wannan za ku sani Allah mai rai na tare da ku zai kori Kan'aniyawa, Hatiyawa da Hibiyawa da Farizziyawa da Girgashiyawa da Amoriyawa da Yebusawa daga gaban ku.11Duba! Akwatin alƙawari na Ubangijin dukkan duniya ya shiga gaban ku zuwa cikin Yodan.12Yanzu ku zaɓi mutum goma sha biyu daga ƙabilar Isra'ila, mutum guda daga kowannen su.13Sa'ad da tafin sawun firistoci masu ɗauke da akawatin Yahweh, Ubangijin dukkan duniya, ya taɓa ruwayen Yodan, ruwayen za su datse, har ma ruwayen da suke kwararowa daga bisan kogin za su daina kwararowa su tsaya a tari guda."14A lokacin da jama'a su ka tashi domin su ƙetare Yodan, firistoci ɗauke da akwatin alƙawari su ka wuce gaban jama'a.15Da zarar mutane masu ɗauke da akwatin su ka iso Yodan, da ƙafafunsu su ka taɓa gacin ruwan (Yodan dai yakan yi ambaliya dukkan lokacin girbi),16sai ruwayen da suke gangarowa daga tudun rafin su ka taru wuri guda. Ruwan ya dena gangarowa daga nesa. Ya kuma dena gagarowa daga Adam, birnin da ke kusa da Zaretan, har ya zuwa tekun Negeb, Tekun Gishiri. Jama'a su ka ƙetare kurkusa da Yeriko.17Firistocin da ke ɗauke da akwatin alƙawari na Yahweh su ka tsaya a kan busasshiyar ƙasa a tsakiyar Yodan har sai da jama'ar Isra'ila su ka ƙetare a kan busasshiyar ƙasa.
...
Wani wuri ne a ƙasar Mowaba, yammacin Kogin Urdu wurin da Isra'ila suka kafa sansani kamun shigar su Ƙasar Alkawari, Kan'ana.
Waɗannan ne mutanen da ke riƙe da matsayin ba da umarni da iƙo.
Wato al'ummar Isra'ila kenan.
"ƙafa 2000." Kalmar nan "ƙafa" ma'auni ne na nisa daga gwiwar hannu zuwa ƙarshen yatsu.
Wannan na nufin shiri ta musamman na zama da tsabta a gaban Yahweh.
Yahweh zai yi mu'ajizai domin dukakkanku ku gani ku kuma ɗanɗana.
Wannan na nufin lewiyawa su ɗauka akwatin domin masar da shi da wani mazauni zuwa wani mazauni.
Yahweh yana gaya wa Yoshuwa abinda firistocci za su yi.
Anan "idanu" na nufin mutane za su gani su fahimta. AT: "mutane za su gani abinda nake yi su gane cewa na mayar da kai babban mutum"
Yoshuwa zai matso kusa da bakin Kogin Urdun kenan.
Yoshuwa yana fadi wa Isra'ila abinda Yahwen zai yi.
Yahweh zai tilasta sauran mutane da ke zama a ƙasar su tafi ku a kashe su.
"ya shiga gaban" na nufin ya ƙetere akin kogin. AT: "zai tafi daga wannan hayin zuwa ɗayan hayin"
Yoshuwa ya cigaba da gaya wa Isra'ila game da al'ajibin da Yahweh zai yi.
Kamar yadda kakkanin Isra'ila sun ɗandana ƙetere Jan Teku, waɗannan mutanen za su ɗandana ƙetere kogin Urdu a busasshen kasa.
wato tafin ƙafa kenan.
Wannan na nufin gefen da ruwan Kogin Urdun ke gudãna zuwa Isra'ila.
Ruwan zai tsaya a wuri ɗaya. Ba zai guɗãna kewaye da firistoccin ba.
Kalmar nan "aƙwati" na nufin aƙwatin da ke ɗauke da allunan duwatsu.
Wannan na nufin farfajiyar ruwa kamar yadda bakin ruwa yake guda zuwa busasshen kasa.
Wannan na ba da bayanin abinda ya faru a baya ne kuma yana nanata yanayin girman abinda Yahweh ke yi.
Al'ajibin ƙetere Kogin Urdun ya cigaba.
...
Wannan jimlar na nufin a je ɗayan hayen bakin kogin. AT: suka yi tafiya daga wannan hayen zuwa wancan haye"
1Sa'ad da dukkan mutane su ka ƙetare Yodan, Yahweh ya cewa Yoshuwa,2"Ku zaɓa wa kan ku mutum goma sha biyu, daga kowanne kabila mutum ɗaya.3Ka ba su wannan umarni: 'Ku ɗauki duwatsu goma sha biyu daga tsakiyar Yodan inda firitoci ke tsaye a kan busasshiyar ƙasa, ku kawo su ku ajiye su inda za ku kwana daren yau."'4Sai Yoshuwa ya kira mutanen nan goma sha biyu waɗanda ya zaɓo daga kabilar Isra'ila, guda ɗaya daga kowacce kabila.5Yoshuwa ya ce masu, "Ku wuce gaban akwatin Yahweh Allahnku zuwa cikin tsakiyar Yodan. Kowannen ku zai ɗauki dutse a kafaɗarsa, bisa ga yawan kabilun mutanen Israila.6Wannan zai zamar ma ku alama a tsakanin ku sa'ad da 'ya'yanku za su tambaya a kwanaki masu zuwa, 'Menene ake nufi da waɗannan duwatsu?'7Sa'annan za ku ce, 'An yanke ruwayen Yodan a gaban akwatin alƙawari na Yahweh. Lokacin da ya ƙetare Yodan, ruwan Yodan ya yanke. Saboda haka waɗannan duwatsu za su zama abin tunawa ga jama'ar Isra'ila har abada."'8Jama'ar Isra'ila su ka yi dai-dai abin da Yoshuwa ya umarce su, su ka ɗauki duwatsu goma sha biyu daga tsakiyar Yodan, kamar yadda Yahweh ya cewa Yoshuwa. Suka shirya duwatsun yadda lambar kabilar Isra'ila ta ke. Su ka ɗebo duwatsu, su ka kawo masaukinsu su ka shirya su a nan.9Sa'annan Yoshuwa ya jera wasu duwatsu a tsakiyar Kogin Yodan, a inda sawun firistoci da su ka ɗauki akwatin alƙawari su ka tsaya. Wannan alamar tana nan har yau.10Firitoci da ke ɗauke da akwatin alƙawari su ka tsaya a tsakiyar Yodan cik har sai duk abubuwan da Yahweh ya umarci Yoshuwa ya faɗa wa mutane sun cika sarai, bisa ga duk abin da Musa ya umarci Yoshuwa.11Sa'ad da dukkan jama'a su ka gama ƙetarewa, akwatin Yahweh da firistoci su ka ƙetare a gaban jama'a.12Kabilar Ruben, da kabilar Gad, da rabin kabilar Manasse su ka wuce a gaban Isra'ilawa shirye 'yan yaƙi, kamar yadda Musa ya ce masu.13Kimanin maza dubu arba'in shiryayyu mayaƙa su ka wuce a gaban Yahweh, domin yaƙi wajen filayen Yeriko.14A ranan nan Yahweh ya ɗaukaka Yoshuwa a idanun dukkan Isra'ilawa. Su ka girmama shi - dai dai da yadda su ka ga ƙwarjinin Musa - dukkan kwanakinsa.15Sai Yahweh ya yi magana da Yoshuwa,16"Ka umarci firistoci masu ɗauke da akwatin alƙawari su hauro daga cikin Yodan."17Sai, Yoshuwa ya umarci firistoci, "Ku fito daga cikin Yodan."18Da firistoci da ke ɗauke da akwatin alƙawari na Yahweh su ka fito daga tsakiyar Yodan, su ka sa tafin ƙafarsu a busasshiyar ƙasa, sai ruwayen Yodan su ka koma magudanarsu su ka cike ta da ambaliya, kamar yadda ta ke kwanaki hudu da su ka wuce.19Jama'a su ka fito daga Yodan a rana ta goma ga watan ɗaya. Su ka zauna a Gilgal, gabashin Yeriko.20Duwatsu sha biyu da su ka ɗauko daga Yodan, Yoshuwa ya shiryasu a Gilgal.21Ya cewa jama'ar Isra'ila, "Sa'ad da zuriyarku za su tambayi ubanninku a zamanai masu zuwa, 'Waɗannan duwatsun fa?'22Ku gayawa 'ya'yanku, 'Nan ne Isra'ila ya ƙetare Yodan kan busasshiyar ƙasa.'23Yahweh Allahnku ya janye ruwan Yodan domin ku, har sai da su ka ƙetare, kamar yadda Yahweh Allahnku ya yi wa Jan Teku, wadda ya busar da ita domin mu sai da muka haye,24domin mutanen duniya dukka su sa ni hannun Yahweh mai karfi ne, ku kuma ku girmama Yahweh Allahnku har abada."
Kodashike Yahweh na magana da Yoshuwa ne, duk wuraren da an yi amfani da ku ko ka yana haɗe ne da Isra'ila.
Kalamun nan "suka ƙetere" na nufin tafiya zuwa ɗayan hayen bakin kogin. AT: "suke haye"
Kogin Urdun
Ana iya sanar da wannan ba lallai ta wurin saka su kamar ambaci ba. AT: "Ka basu wannan umarnin, su ɗauki duwatsu gomashabiyu daga tsakiyar Urdun inda firistocin ke tsaye a kan busasshiyar ƙasa, ku kawo su ku ajiye su a inda za ku kwana daren yau."
Yoshuwa yana fada wa mutane goma sha biyun abin yi.
Kowannen mutane goma sha biyun zai ɗauki wani babbar dutse daga tsakar Kogin Urdun, yă ɗauke su zuwa ɗayan gefe ku gina abin tunawa.
Yoshuwa yana gaya wa Isra'ila abinda tarin duwatsu goma sha biyun ke nufi.
AT: "Yahweh ya yanke ruwayen Urdun a gaban akwatin alƙawari"
"Kogin Urdun"
Allah ya hana Kogin Urdun gudana har wurin da firistocin suka ɗauki firistocin.
Ruwan da ke gudana zuwa Kogin Urdun ya tsaya a gaban akwatin domin dukkan kowa har da akwatin su wuce a busasshen tsakiyar kasa.
Yoshuwa da Isra'ila sun cigaba da yin yadda Yahweh ya umurta.
Wannan na nufin mutane goma sha biyun da suka ɗauki duwatsu daga tsakiyar Kogin Urdun.
Waɗannan wasu karin duwatsu ne, ba duwatsun da mutane goma sha biyun suka ɗauka daga tsakar kogin ba.
Wannan na nufin cewa alamar na wurin har ranar da marubucin ya wallafa wannan littafin.
Wato Kogin Urdun.
Wato al'umman Isra'ila.
Wannan na nufin a je ɗayan gefene bakin kogin. AT: "suka yi tafiya daga wannan gefen zuwa ɗayan gefen"
... Kowa ya ga firistocin ɗauke da akwatin.
Waɗannan ne 'yan yaƙin kabilu 3 da ke cika abinda ya wajaba su yi na zuwa jagorantan Isra'ilawan zuwa yaƙi domin zama a Gabashin Kogin Urdun.
Kalmar nan "su" na nufin al'umman Isra'ila.
Wannan na nufin ba daraja kawai ba amma sun miƙa kai ga umarninsa sun kuma bi da shi kamar shugaban 'yan yakinsu sun bi shi.
Yahweh yana gaya wa Yoshuwa cewa yă cewa wa firistocin su fita daga Kogin Urdun.
Marubucin yanan nunwa a fili cewa barin Kogin Urdun bai bambanta da barin Jan Teku ba ga tsararrakin baya.
Kogin Urdun na na cika da ambaliya kamun da kuma bayan da Isra'ila suka ƙetere a busasshen ƙasa.
"kwanaki 4"
Wannan na nufin lokacin da Isra'ila suka ƙetere Kogin Urdun a busasshen kasa.
Wannan na nufin watan ɗaya a kalandar Yahudawa. Rana ta gomas ya kusa da ƙarshen watan Uku a kalandar yammaci.
Kowane kabila za su ɗauka dutsa ɗaya daga Kogin Urdun domin Yoshuwa yă iya gina abinda tunanwa da wannan ƙeterewar.
Yoshuwa ya cigaba da tuna wa mutanen dalilin tattara duwatsun.
Ya rage wa Isra'ila ne su koya wa 'ya'yansu kame da al'ajiban Allah domin su girmama Yahweh har abanda.
Wannan na nufin cewa iƙon Yahweh mai ƙarfi ne. AT: "Yahweh na da ƙarfi"
1Nan da nan da dukkan sarakunan Amoriyawa na yamma da Yodan, da dukkan sarakunan Kan'aniyawa, waɗanda su ke gefen Babbar Teku, su ka ji yadda Yahweh ya sa ruwayen Yodan su ka ƙafe har sai da jama'ar Isra'ila suka haye zuwa ɗaya gacin, sai zukatansu suka narke, ba su da sauran wani ƙarfin hali kuma saboda mutanen Isra'ila.2A lokacin sai Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Ka yi wuƙar dutse ka sake yi wa dukkan mazajen isra'ila kaciya."3Sai Yoshuwa ya yi wuƙar dutse ya yi wa dukkan mazajen Isra'ila kaciya a Gibiyat Hãralot.4Wannan shi ne dalilin da Yoshuwa ya yi masu kaciya: dukkan mazajen da su ka fito daga Masar, tare da dukkan mayaƙa, sun mutu a cikin jeji a kan hanya, bayan sun baro Masar,5Ko da shike dukkan mazajen da su ka baro Masar suna da kaciya, amma, duk yara maza da aka haifa cikin jeji a kan hanyar fitowar su daga Masar ba su da kaciya.6Gama mutanen Isra'ila su ka yi tafiya shekara arba'in a jeji, har sai da dukkan mazajen da su ka fito Masar mayaƙa su ka mutu, domin ba su yi biyayya da muryar Yahweh ba. Yahweh ya rantse masu ba za su shiga ƙasar da ya rantse wa kakanninsu zai ba mu, ƙasa wadda take zubo da madara da zuma.7'Ya'yansu ne waɗanda Yahweh ya tăda a madadinsu, su ne Yoshuwa ya yi wa kaciya, domin ba a yi masu kaciya a hanya ba.8Sa'ad da aka yi wa dukkan su kaciya, su ka zauna cikin sansani har sai da su ka warke.9Sai Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Wannan rana ta yau na cire ƙunyar Masar daga gare ku." Saboda haka, ake kiran sunan wurin Gilgal har wa yau.10Jama'ar Isra'ila su ka yi sansani a Gilgal. Su ka kiyaye Idin Ketarewa a rana ta goma sha hudu ga wata, da yammaci, a filayen Yeriko.11Su ka ci daga waɗansu amfanin ƙasar a rana ta fari bayan Idin Ketarewa: waina marar yisti da gasasshen hatsi.12Manna ta dena saukowa bayan ranar da su ka ci daga amfanin ƙasar. Babu manna kuma domin jama'ar Isra'ila, amma su ka ci daga cikin amfanin ƙasar Kan'ana a shekaran nan.13Sa'ad da Yoshuwa ya kusa da Yariko, sai ya tada idanunsa ya duba, sai, ga wani mutum tsaye a gabansa; da takobi a zare a hannunsa. Yoshuwa ya tafi wurin sa ya ce, "Kana wajenmu ne ko kana wajen abokan găbarmu?"14Sai ya ce, "Ko ɗaya. Ni ne sarkin yaƙin rundunar Yahweh. Yanzu na zo." Sai Yoshuwa ya russuna da fuskarsa ƙasa ya yi masa sujada ya ce, "Menene ubangijina zai faɗa wa bawansa?"15Sai sarkin yaƙin rundunar Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Ka cire takalmanka daga ƙafafunka, domin inda ka ke tsaye wuri mai tsarki ne." Haka kuwa Yoshuwa ya yi.
Waɗannan jimla biyun a takaice na nufin abu ɗaya ne, suna kuma nanata tsananin tsoronsu ne.
Anan "zukata" na nufin ƙarfin halinsu. Suna da matuƙar tsoro har ƙarfin halinsu ya narke kamar kitse a wuta. AT: "sun rasa ƙarfin halin su"
Wato sun rasa ƙarfin hali su na yin fada. AT: "ba su da wani son yin wafa kuma"
Akwai sama da maza 600,000 a lokacin, don haka muna iya gane da cewa yayin da Yoshuwa yana shugabacin wannan aiki, akwai sauran mutane da dama da suka taimaka masa. Idan har wannan zai kawo rikicewa ga masu karatu a harshenku, kuna iya bayana wannan a fili. AT: "Yoshuwa da Isra'ilawan sun yi wa kansu wuƙar dutse suka yi wa dukkan mazajen kaciya"
Wannan sunan wuri ne da ke kadamar bikin sake miƙe kai ne Isra'ilawa ga Yahweh. Yanan nufin "tudun loɓar."
An bayana dalilin da yana zamato lallai ayi was Isra'ilawa kaciya.
maza da sun isa su zama 'yan yaƙi
Anan "Murya" na nufin abubuwan da Yahweh ya faɗa. AT: "yi biyayya da abubuwan da Yahweh ya umurcesu"
Allah na maganar yadda ƙasar ke da kyau ga dabbobi da shuke-shuke ne kamar madara da zuma da ake samowa daga dabbobin da shuke-shuken suna gudana ne a gonar gabaɗaya. AT: "ƙasar da ke mafi inganci ayi kiwon dabbobi da yin noma"
Anan maganar ƙunyar su ne kamar wani babbar dutse ne da ya tare masu hanya. AT: "Wannan rana ta yau na cire maku ƙunyar Masar daga gare ku" ko kuma "An kunyatar da ku a lokacin da kuke barori a Masar. Amma dai, yau na sa kada ku cigaba da kunyata"
Wato kusa da ƙarshen watan uku kenan a kalandar Yammaci. AT: "rana ta goma sah huɗu ga watan fari"
Ana maganar tada idanun Yoshuwa ne kamar ya ainihin tada idanunsa ne da hannayensa. AT: "ya dubi sama ya ga cewa wani mutum na tsaye"
Wannan "sa, ga" na jan hankalinmu ne mu sa hankalinmu ga wata sabuwar sanarwa. Mai yiwuwa harshenku na da wata hanya ta musamman na yin haka.
Anan mai takobin shi ne mutumin da yake tsaye a gaban Yoshuwa.
"Kalmar nan "ya" nannufin mutumin da yoshuwa ya gani.
Wannan ne farkon amsar da mutumin ke yi ga tambayar da Yoshuwa Yoshuwa ya yi, "Kana wajenmu ne ko kana wajen abokan găbarmu?" Ana iya bayyana wannan gajeren amsa. AT: "Bana tare da kai ko da abokan găbarku"
Wannan yin sujada ne.
Wannan alama ce ta girmamawa.
1Aka rufe dukkan ƙofofin shiga Yeriko saboda mayaƙan Isra'ila. Ba wanda ya fita ko ya shigo.2Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Duba, na bada Yeriko da sarkinta, da horarrun sojojinta a hannunka.3Dole ku zagaya birnin, dukkan mazaje mayaƙa za su zaga birnin sau ɗaya. Dole za ku yi haka har kwana shida.4Dole firistoci bakwai su ɗauki ƙahonni bakwai na raguna a gaban akwati. A rana ta bakwai, dole ku zagaya brinin sau bakwai, firistoci kuma dole su busa ƙahonni da babbar busa.5Daga nan dole su yi doguwar busa da ƙahon rago, kuma sa'ad da ku ka ji busar ƙahon dukkan mutane dole su yi ihu da babbar murya, garun birnin zai faɗi ya rushe. Dole sojojin su kai hari, kowannensu ya miƙe ya tafi gaba."6Sa'annan Yoshuwa ɗan Nun ya kira firistoci ya ce masu, "Ku ɗauki akwatin alƙawari, kuma firistoci bakwai su ɗauki ƙahonnin raguna bakwai a gaban akwatin Yahweh."7Ya cewa jama'a, "Ku tafi ku zagaya birnin, masu makamai kuma za su je gaban akwatin Yahweh."8Kamar yadda Yoshuwa ya cewa mutane, firistoci bakwai su ka ɗauki ƙahonni bakwai na raguna a gaban Yahweh. Da su ka cigaba da tafiya sai su ka busa ƙaho da babbar murya. Akwatin alƙawari na Yahweh na biye da su.9Masu makamai su ka tafi gaban firistoci, su ka yi babbar busa, wasu masu makamai kuma su ka bi bayan akwatin, firistoci kuma su ka yi ta busa ƙahonni.10Amma Yoshuwa ya dokaci mutane, cewa, "Kada ku yi ihu. Kada wata ƙara ta fito daga bakinku sai randa na ce ku yi ihu. Lokacin ne za ku yi ihu."11Sai ya sa aka zagaya birnin da akwatin Yahweh sau ɗaya a ranar. Sa'annan suka komo sansaninsu, su ka kwanta daren nan.12Sai Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma su ka ɗauki akwatin Yahweh.13Firistoci bakwai, masu ɗauke da ƙahonnin raguna bakwai a gaban akwatin Yahweh su ka yi ta busa ƙahonni su na tafiya gaba gaɗi. Sojoji masu makamai suna tafiya a gabansu. Amma sa'ad da 'yan tsaron baya su ka biyo akwatin Yahweh, sai aka dinga busa ƙahonni.14Su ka zaga birnin sau daya a rana ta biyu su ka komo sansaninsu. Haka suka dinga yi har kwana shida.15A rana ta bakwai su ka tashi da sassafe kafin gari ya waye, su ka zãga birnin kamar yadda su ka saba yi, wannan karon sau bakwai.16A wannan ranar ce su ka zagaya birnin sau bakwai, firistoci su ka busa ƙahonni, sai Yoshuwa ya umarci mutane, "Ku yi ihu! Gama Yahweh ya ba ku birnin.17Za a keɓe wa Yahweh birnin da dukkan abin da ke cikinta domin hallakarwa. Rahab karuwan nan ce kaɗai za ta rayu - ita da dukkan waɗanda ke tare da ita a gidanta - domin ta ɓoye waɗanda mu ka aika.18Amma ku kam, ku yi lura game da abubuwan da aka ƙeɓe domin hallakarwa, domin kada bayan kun waresu saboda hallakarwa, ku koma ku ɗauka. Idan ku ka yi haka, za ku maida sansanin Isra'ila abin da za a hallakar kuma za ku jawo ma ta masifa.19Dukkan azurfa, zinariya da abubuwan tagulla da ƙarfe a keɓe su ga Yahweh. Dole a kai su cikin ma'ajin Yahweh."20Da su ka yi babbar busa ƙahonni, sai mutane su ka yi gawurtaccen ihu ganuwar ta faɗi ƙasa, sa'annan kowanne mutum ya shiga ciki kai tsaye su ka ci birnin.21Su ka lalatar da dukkan abin da ke birnin da kaifin takobi - maza da mata, yaro da tsoho, shanu, tumaki, da jakai.22Sa'annan Yoshuwa ya cewa mutanen biyu da su ka leƙo asirin ƙasar, "Ku shiga gidan karuwar nan. Ku fitar da ita waje da dukkan waɗanda suke tare da ita, kamar yadda ku ka rantse ma ta."23Sai samarin nan biyu magewaya su ka shiga ciki su ka fitar da Rahab. Su ka fitar da mahaifinta, mahaifiyarta, 'yan'uwanta maza da dukkan 'yan'uwanta da su ke tare da ita. Su ka kai su wani wuri dabam da sansanin Isra'ila.24Su ka ƙona garin da dukkan abin da ke cikinsa. Sai dai azurfa, zinariya da kwanonin tagulla da na ƙarfe ne su ka ajiye a ma'ajin gidan Yahweh.25Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwa, gidan ubanta, da dukkan waɗanda ke tare da ita da rai. Tana zaune a Isra'ila har wayau domin ta ɓoye masu leƙen asirin ƙasa waɗanda Yoshuwa ya aika su leƙo Yeriko.26Sai Yoshuwa ya umarce su a lokacin da rantsuwa, ya kuma ce, "La'anannen mutum ne a idon Yahweh wanda ya sake gina wannan birni, Yeriko. A bakin ran ɗan farinsa, zai sa harsashen, a kuma bakin ran ɗan autansa, zai kafa ƙofofinta."27Haka Yahweh ya kasance tare da Yoshuwa, sunansa ya shahara ko'ina a faɗin ƙasar.
Anan marubucin na gaya mana dalilin da ya sa aka rufa ƙofofin Yarico ne.
Yahweh yana gaya wa Yoshuwa cewa zai aikata wannan da tabbaci ne ta wurin cewa ya rigaya ya yi.
Allah ya cigaba da gaya wa Yoshuwa abinda mutanen za su yi.
"Dole za ku yi haka sau ɗaya kullum har kwanaki shiɗa"
Firistocin bakwai ɗin za su yi tafiya ne a gaban sauran firsitocin da ke ɗauke da akwatin suna tafiya suna kewaye garin.
Allah ya cigaba da gaya wa Yoshuwa abinda mutanen za su yi.
Kalmar nan "su" na nufin firistoci bakwain. "Ƙahon ragon" da "busa" na nufin busar rago da firistocin ke hurawa a 6:3.
"garun da ke kewaye birnin dukka"
Wannan ne Mahaifin Yoshuwa.
"Ku ɗaga akwatin alƙawar"
Wannan na iya nufin 1) "cikin biyayya da Yahweh" 2) "a gaban akwatin Yahweh"
"sai su ka busa ƙahon da ƙara ƙwarai" ko kuma "firistocin su ka busa cikin busar ƙahon ragon"
Ana iya sanar a fili cewa akwai mutane masu ɗaukar akwatin. AT: "Firistocin da ke ɗauke da akwatin alƙawarin Yahweh su ka biyo su a baya"
Ƙarar da ke fito daga bakin mutum na nufin mutumin na magana ko ihu. AT: "Kada ku yi ihu ko magana"
Yoshuwa ya dokaci mutanen kamun su fara tafiya suna kewaye birnin. AT: "Yoshuwa ya dokoci mutanen"
"Firistoci 7 ... ƙahohin raguna 7"
Wannan na nufin sun busa ƙahonninsu har su ka yi ƙara sosai, sau da dama. AT: "suka riƙa yin ƙara da ƙarfi ƙwarai" ko kuma "suka busa ƙahonninsu na raguna ba tsayawa"
washe gari
Isra'ila sunka yi tafiya suna kewaye Yarico sau ɗaya kullum.
"kwana 6"
Wato mutanen Isra'ila kenan.
su ka busa ƙahonnin da ƙarfi ƙwarai" ko kuma "su ka busa ƙahonnin su na raguna"
Yoshuwah yana cewa ba shakka Yahweh zai ba su birnin ne ta wurin cewa Yahweh ya rigaya ya ba su.
Kalmar nan "ku" na nufin al'ummar Isra'ila gabakiɗaya.
Yahweh ya cigaba da yi wa mutanen Isra'ila magana.
AT: "Ku tabbatar kun keɓe wa Yahweh birnin da dukkan abinda ke cikinta domin hallakarwa" ko kuma "Ku tabbatar kun keɓe wa Yahweh birnin da dukkan abinda ke cikinta ta wurin hallakr da shi"
AT: "Ku yi lura, kada ku ɗauki abubuwa"
Ana maganar aikatan abinda ke sa mugayen abubuwa su faru da gari ne kamar jawo masa masifa kenan. AT: "za ku sa mugayen abubuwa su faru da shi"
matattaran abubuwa da aka keɓe domin ya wa Yahweh sujada
"mutanen Isra'ila su ka yi ihu"
"su ka busa ƙahonni da ƙarfi ƙwarai" ko kuma "su ka busa ƙahonnin raguna"
Kodahike yawancin mutanen Isra'ila sun yi amfani da takobi, wannan na nufin domin kai tarzomar hari a lokacin yaƙi gabaɗaya. AT: "da kaifin takobansu" ko kuma "a cikin yaƙi"
Kalmar nan "su" na nufin 'yan yaƙin Isra'ilawa. Ba wai yana nufin matasa biyun da su ka ciro Rahab da iyalinta daga birnin kawai ba.
Kalmar nan "ta" na nufin Rahab kuma yana haɗe da ita da zuriyarta. AT: "Zuriyar ta na zaune a Isra'ila"
"yanzu" ko "har wayau." Rahab da zuriyarta na zaune a Isra'ila har lokacin da ainihin mai rubutawa labarin na wallafa ta.
Zaman la'anne a idon Allah ne nufin Yahweh ya la'anta wannan mutum. AT: "Bari Yahweh yă la'anta mutumin da ya sake gina"
Sakamakon mutumin da ya sa wata sabuwar harshahe a Yarico shi ne ɗansa na farko zai mutu. An faɗi wannan ne kamar tsada da mutum zai biya kenan. AT: "idan ya har ya sa harshashen, zai rasa ɗansa na fari" ko kuma "idan ya sa harshashen, ɗansa na fari zai mutu"
Sakamakon mutumin da ya kafa wata sabuwar kofa a Yarico shi ne ɗan autarsa zai mutu. An faɗi wannan ne kamar tsada da mutum zai biya kenan. AT: "Idan har ya kafa ƙofofinta, zai rasa ɗan autarsa" ko kuma "Idan ya kafa ƙofofinta, ɗan'autarsa zai mutu"
Wannan na nufin sunan Yosuhwa, ba na Yahweh ba. Ana maganar zama sananne ne a tsakananin mutanen a ko'ina a ƙasar kamar sunarsa ne yă shahara. AT: "Yoshuwa ya zama sanannae a ko'ina a ƙasar" ko kuma "Mutanen ko'ina a ƙasar sun ji labarin Yoshuwa"
1Amma jama'ar Isra'ila su ka yi rashin aminci game da abubuwan da aka ƙeɓe domin hallakarwa. Akan ɗan Karmi, ɗan Zabdi ɗan Zera, daga kabilar Yahuda ya ɗauka daga cikin abubuwan da aka ƙeɓe domin hallakarwa, sai fushin Yahweh ya yi ƙuna a kan 'ya'yan Isra'ila.2Yoshuwa ya aiki mutane daga Yeriko zuwa Ai da take kusa da Bet Aben gabas da Betel. Ya ce masu, "Ku tafi ku leƙo ƙasar." Sai mutanen su ka tafi su ka leƙo Ai.3Da su ka dawo wurin Yoshuwa, su ka ce masa, "Kada ka aika mutane dukka zuwa Ai. Ka aika misalin dubu biyu ko uku kawai, su je su kai ma ta hari. Kada ka bari dukkan mutane su wahala a yaƙi, domin ba su da yawa."4Saboda haka mutum dubu uku ne kaɗai cikin mayaƙa su ka tafi.5Mutanen Ai su ka kashe misalin mutane talatin da shida su ka fafare su daga ƙofar birnin har zuwa mafasar duwatsu, su ka karkashe su sa'ad da su ke gangarowa daga kan tudu. Zukatan mutanen su ka tsorata ƙarfin halinsu kuma ya rabu da su.6Sai Yoshuwa ya yayyage tufafinsa. Da shi da shugabanin Isra'ila su ka zuba ƙura a kansu su ka faɗi rub da ciki a ƙasa a gaban akwatin Yahweh har yamma.7Sa'annan Yoshuwa ya ce, "Ya Ubangiji Yahweh, me ya sa ma ka haye da mutanennan daga Yodan? Don ka bashe mu a cikin hannun Amoriyawa su hallakar da mu? Ai da mun gwammace mu yi zamanmu a wancan hayin Yodan!8Ubangiji, me zan ce, bayan Isra'ila ta juya ta guje ma abokan gabanta?9Gama Kan'aniyawa da dukkan mazaunan ƙasar za su ji. Za su kewaye mu su sa mutanen duniya su manta da sunanmu. To me za ka yi domin sunanka mai girma?"10Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Tashi! Me ya sa ka kwanta fuskarka ƙasa?11Isra'ila ta yi zunubi. Sun karya dokata da na umurce su. Sun sãci waɗansu abubuwan da aka keɓe. Sun sata sun kuma ɓoye zunubinsu ta wurin aje abubuwan da su ka ɗauka cikin kayansu.12Saboda haka ne, mutanen Isra'ila ba za su iya tsayawa a gaban maƙiyansu ba. Sun juya wa maƙiyansu baya domin su kan su an ƙebe su domin hallakarwa. Ba zan kasance tare da ku kuma ba sai ko kun hallaka waɗannan abubuwa da ya kamata an hallakar da su, amma suna nan tare da ku.13Tashi! Ka tsarkake jama'ar a gareni ka ce masu, 'Ku tsarkake kanku domin gobe. Domin Yahweh, Allah na Isra'ila ya ce, "Akwai abubuwan da aka keɓe saboda hallakarwa waɗanda su ke a tsakaninku, Isra'ila. Ba za ku iya tsayawa gaban maƙiyanku ba, sai kun fitar da dukkan abubuwan da aka keɓe domin hallakarwa daga tsakaninku."14Da safe, dole ku taru bisa ga kabilarku. Kabilar da Yahweh ya zaɓa za ta matso iyali - iyali. Iyalin da Yahweh ya zaɓa dole su matso gida - gida. Gidan da Yahweh ya ware dole a gabatar da su mutum - mutum.15Zai zamana duk wanda aka zaɓa, da yake da waɗannan keɓaɓɓun abubuwan hallakarwa, za a ƙone shi, da duk abin da yake da shi, domin ya karya dokar Yahweh, kuma ya yi abin ban kunya a Isra'ila."'16Saboda haka, Yoshuwa ya tashi da sassafe, ya gabatar da Isra'ilawa, kabila - kabila, sai aka zaɓi kabilar Yahuda.17Yoshuwa ya gabatar da kabilar Yahuda, sai aka zaɓi iyalin Zera. Ya gabatar da iyalin Zera mutum - mutum, sai aka zaɓi gidan Zabdi.18Ya gabatar da gidan Zabdi, mutum - mutum, sai aka zaɓi Akan, ɗan Karmi, ɗan Zera daga kabilar Yahuda, shi ne aka zaɓa.19Sai Yoshuwa ya cewa Akan, "Ɗana, ka faɗi gaskiya a gaban Yahweh Allah na Isra'ila, ka ba da shaidarka gareshi. Idan ka yarda, ka gaya ma ni abin da ka yi. Ka da ka ɓoye ma ni."20Akan ya amsa wa Yoshuwa, "Gaskiya na yi wa Yahweh zunubi, Allah na Isra'ila. Ga abin da na yi:21Sa'ad da na ga wata kyakkyawar alkyabba daga Babila, a cikin ganima, da shekel dari biyu na azurfa, da curin zinariya mai nawin shekel hamsin, sai na yi sha'awarsu na ɗauka. Sunanan a binne a ƙasa a tsakiyar rumfata, azurfar kuwa ta na ƙarƙashinsu.22Yoshuwa ya aiki manzanni, da su ka sheƙa da gudu zuwa rumfar, sai kuwa gasu. Da suka duba, su ka tarar da abubuwan bizne cikin rumfarsa, da azurfar a ƙarƙashi.23Sai su ka kwaso su daga tsakiyar rumfar su ka kawo wa Yoshuwa da dukkan mutanen Isra'ila. Su ka zuba su gaban Yahweh.24Sai Yoshuwa, tare da dukkan Isra'ila, su ka ɗauki Akan ɗan Zera, da azurfar, da alkyabbar, da curin zinariyar, da 'ya'yansa maza da mata, da shanunsa, da jakunansa da tumakinsa, da rumfarsa da dukkan mallakarsa, su ka kawo su Kwarin Akor.25Sa'annan Yoshuwa ya ce, "Don me ka wahalshe mu? Yahweh zai wahalsheka yau." Dukkan Isra'ila su ka jejjefe shi da duwatsu. Su ka jejjefi sauran da duwatsu su ka ƙone su da wuta.26Su ka tula duwatsu a kansa mai tudu da su ke nan har yau. Yahweh ya juya daga fushinsa mai zafi. Saboda haka aka kira sunan wurin Kwarin Akor har zuwa yau.
"abubuwan da Allah ya ce zaa keɓe masa ta wurin hallakar da su"
Waănnan sunayen mazaje ne.
"fushi" da "ƙuna" na nufin tsanani ba wai akwai wuta ba. AT: "Fushin Yahwh yana ƙuna kamar wuta" ko kuma "Yahweh ya yi fushi ƙwarai"
Wannan na nufin 'yan yaƙin Isra'ila.
Kalmar nan "su" na nufin mutanen Ai.
Waɗannan mutanen na cikin mayaƙan. AT: "mutum dubu uku cikin mayaƙan suka haura"
mutum shida-"mutum 3000 ... mutum 36"
Waɗannan jimla biyun suna da ma'annan kusan ɗaya ne, kuma an haɗa su ne domina a nanata cewa ,utam sun tsorota ƙwarai.
Ana maganar tsoron mutanen ne kamar zukatansu ne ke tsoro. AT: "Mutanen sun tsorata ƙwarai"
"mutane" na nufin mayaƙan Isra'ilawa.
"ba su da ƙwarin gwiwa kuma"
Sun yi waɗannan abubuwan duk ne domin sun nunan bakin cikinsu da wuya da suke sha.
Yoshuwa na tambaya ne ko dalililn da Allah ya kawo su ƙeteren Urdun kenan. AT: "Ko ka yi haka ne domin ka bashe mu a cikin hannun Amoriyawa su hallakar da mu?
Hannun Amoriyawa na nufin nuna nuna iƙonsu akan Isra'ilawa. Bashe Isra'ilawa a cikin hannunsu su hallakar da su na nufin barin Amoriyawa su su nuna iƙo a bisa Isra'ilawa su kuma hallakar da su. AT: "Don ka bar Amoriyawa su hallakar da mu?
Kalamun nan "Ai idan" na nuna cewa wannan marmari ne cewa da abun ma bai faru ba. AT: "Na gwammace da mun yi wani abu daban"
Yoshuwa ya nuna wa Allah bakin cikinsa.
Yoshuwa ya faɗi haka ne domin ya nuna yawan bacin ransa har ma bai san abin da zai faɗa ba. AT: "Ban san menene zan ce ba. Isra'ila ta juya baya ga maƙiyanta"
Yin haka na nuna guje wa maƙiyansu. AT: "Isra'ila ta tsere wa maƙiyansu"
Sa mutane su manta da sunan Isra'ilawa na nufin sa su su manta da Isra'ila. A wannan hali, za su yi haka ne ta wurin ƙashe Isra'ilawan. AT: "Za su kewaye mu su ƙashe mu, har mutanen duniya za su manta da mu"
Jimlar nan "sunanka mai girma" anan na nufin halin Allah da iƙonsa. AT: "To yanzu me za ka yi domin mutane su san cewa kai mai girma ne"
Yoshuwa yana amfani ne da wannan tambayan domin yă faɗa wa Allah cewa idan Isra'ilawa sun hallaka, to sauran al'umma za su ɗauke da cewa Allah ba mai girma bane. AT: "Sa'annan ba abinda za ka yi domin girman sunanka." Ko kuma "Sai mutane ba za su kasa ganin girmanka."
Yahweh ya faɗa wa Yoshuwa dalilin da ya sa Isra'ila sun la'antu.
Allah yayi amfani ne da wannan tambayan ya tsauta wa Yoshuwa domin kwanta fuskarsa ƙasa da yayi. AT: "Ka daina kwanciye da fuskar ka cikin datti!"
Waɗannan abubuwa ne da "ƙebe domin hallaka" daga 6:17. AT: "la'anannun abubuwa" ko kuma "abubuwan nan da Allah ya la'anta"
Ɓoye zunubansu na nufin ƙi su sa wasu wasu su san cewa sun yi zunubi. AT: "Sun sata waɗancan abubuwan can, sa'annan sun yi ƙokarin ƙi mutane su san cewa sun yi zuniubi"
Tsaye a gaban maƙiayansu na nufin yin nasara da maƙiyansu. AT: "ba za su iya faɗa da abokan gabansu su yi nasara ba" ko kuma "ba za su iya yin nasara da maƙiyansu ba"
Yin haka na nufin gujewa maƙiyansu. AT: "Sun guje wa maƙiyansu"
Kasancewa da Isra'ila na nufin taimaka wa Isra'ila. AT: "Ba zan taimake ku kuma ba"
Yahweh ya cigaba da yi wa Yoshuwa magana, yana gaya mishi abinda zai gaya wa mutanen.
Wannan na nufin mutanen Isra'ila.
Tsayawa a gaban maƙiyaya na nufin cin nasara da su a yaƙi. AT: "Ba za ku iya yin yaƙi da maƙiyayanku har ga nasara ba" ko kuma "Ba za ku iya yin nasara da maƙiyayanku ba"
Yahweh ya cigaba da gaya wa Yoshuwa abinda zai gaya wa mutanen.
Akwai kabilu goma sha biyu da suka kumshi mutanen Isra'ila. Jimlar nan "bisa ga kabilarku" na nufin "kowace kabila". AT: "dole kowace kabilarku su taru su gabatar da kansu ga Yahweh" (Duba: figs2_idiom)
Shugabannin Isra'ila za su jefa kuri'a, ta yin haka ne, za su san ko wanne kabila ne Yahweh ya zaɓa. AT: "Kabilar da Yahweh ya zaɓa ta wurin kuri'a" ko kuma "Kabilar da Yahweh ya zaɓa idan mun jefa kuri'a"
Kabilar ta kumshi iyalai AT: "Daga kabilar da Yahweh ya zaɓa, kowace iyali za ta matso kusa"
Iyalin sun kumshi gida-gida da dama. AT: "Daga iyalin da Yahweh ya zaɓa, kowanne gida za su matso kusa"
AT: "Daga iyalin da Yahweh ya ware, kowanne mutum zai matso kusa"
AT: "shi wanda Yahweh ya zaɓa"
Karya doka na nufin yin rashin biyayya da shi. AT: Ya yi rashin biyayya da dokar Yahweh"
Yoshuwa ya bi umurnin Yahwah na kawo Isra'ila gaban Yahweh.
Jimlar nan "kabila kabila" na nufin kowace kabila. AT: ya kawo kowace kabilar Isra'ila kusa"
AT: "Yahweh ya zaɓi kabilar Yahweh"
Jimlar nan "mutum-mutum" karin magana ne da ke nufin kowanne mutum. Mutanennen a wannan sha'annin yanayin su ne shugabannin gidaje. AT: "Ya gabatar da kowane mutum daga iyalin Zera" ko kuma "Daga iyalin Zera,ya gabatar da kowane mutum da ke shugabancin gidansa"
Iyalin na auke ne da sunan wani mutum mai suna Zera.
Waɗannan sunayen mazaje ne. Ku juya su yadda kuka yi a 7:1.
AT: "ka shaida masa"
Ɓoye zance na nufin kasa sa wani yă sani. AT: "Kada ka sa in kasa sanin sanin abinda ka yi"
Wannan na sama da kilo biyu.
Wannan na sama da giram 500.
AT: "Na ɓoye su a ƙasa"
"mutanen da Yoshuwa ya aika suka duba"
Ku mori kalmar harshenku dake nufin an zuba abubuwa kadan cikin mai yawa da ke wani babbar buhu.
Wannan na nufin "kwarin Matsala," amma ya fi a juya zuwa Akor yadda ake kira.
Yoshuwa yana amfani ne da wannan tambayan domin ya tsauta wa Akan. AT: "Ai ka wahalshe mu"
Wannan iya nufin 1) Isra'ilawan suka ƙona gidan Akan har ga mutuwa suka rufa su da suwatsu ko kuma 2) Isra'ilawan sun jejjefi gidan Akan auwa ga mutuwa sai sun ƙona gawakinsu ko kuma 3) Akan da mallakarsa dukka an jejjefe su an kuma ƙona kurmus.
Juyawa daga fushi na nufin daina yin fushi. AT: "Yahweh ya daina yin fushi"
Ana ce da shi kwarin Akor har zuwa lokacin da aka wallafa wannan littafin. AT: "har yau" ko kuma "har yanzu"
1Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Ka da ka ji tsoro; ka da ka karaya. Ka ɗauki dukkan mayaƙa. Ku haura zuwa Ai. Duba, na rigaya na ba ka sarkin Ai, da mutanensa, birninsa da kuma ƙasarsa a hunnunka.2Za ka yi wa Ai da sarkinta kamar yadda ka yi wa Yeriko da sarkinta, amma za ku washe ganima da dabbobi domin kan ku. Ku yi kwanto a bayan birnin."3Saboda haka Yoshuwa ya tashi ya ɗauki dukkan mazaje mayaƙa zuwa Ai. Sa'annan Yoshuwa ya zaɓi mazaje dubu talatin - ƙarfafa, jarumawa -- ya aike su da dare.4Ya umarce su, "Ku duba, za ku yi wa birnin kwanto, a bayansa. ka da ku yi nisa da birnin sosai, amma dukkan ku ku kasance a shirye.5Ni da dukkan mutanen da ke tare da ni za mu kusanci birnin, sa'ad da da za su fito su yi karo da mu, za mu guje da ga garesu kamar dă.6Za su fito su fafare mu har sai mun rinjayesu daga birnin. Za su ce, 'Suna guje ma na karmar dă.' Haka za mu gudu da ga garesu.'7Sa'annan za ku fito da ga maɓuyarku, ku ci birnin. Yahweh Allahnku zai ba da shi a hannunku.8Sa'ad da ku ka ci birnin, za ku cinna masa wuta. Za ku yi wannan lokacin da ku ka yi biyayya da umarnin da aka bayar cikin maganar Yahweh. Duba, na umarce ku."9Yoshuwa ya aike su, su ka tafi wurin kwanto, su ka yi faƙo tsakanin Betal da Ai, wato yamma da Ai ke nan. Yoshuwa kuwa ya kwana cikin jama'a a daren nan.10Yoshuwa ya tashi da sassafe ya shirya sojojinsa, shi da shugabannin Isra'ila su ka kai wa mutanen Ai hari.11Dukkan mayaƙa maza da ke tare da shi su ka tafi tare da shi su ka kusanci birnin. Su ka matsa kusa arewa da Ai. Akwai kwari tsakaninsu da Ai.12Ya ɗauki mayaƙa kusan dubu biyar ya sa su ka yi kwanto yamma da birnin tsakanin Betel da Ai.13Ya sanya dukkan sojojin ko'ina, muhimman rundunar ya sa su arewa da birnin, 'yan tsaron baya kuwa a yammancin birnin. Yoshuwa ya kwana a kwari a darennan.14Ananan da sarkin Ai ya ga haka, sai shi da mayaƙansa suka tashi da sassafe su ka gaggauta su ka kai wa Isra'ila hari ta gefen da ya fuskanci kwarin kogin Yodan. Bai sani ba cewa 'yan kwanto suna jiran su auka wa birnin ta baya.15Yoshuwa da dukkan Isra'ila suka yi kamar an rinjayesu su ka gudu cikin jeji.16Aka kira dukkan mutane da ke cikin birnin su ka fafare su, su ka sheƙa da gudu su na bin Yoshuwa, aka kuwa rinjaye su nesa da birnin.17Ba a bar ko mutum ɗaya a cikin Ai da kuma Betel da bai fito ya fafari mutanen Isra'ila ba. Su ka bar birnin da ƙofofin sa a buɗe sa'ad da suke fafarar Israi'ila.18Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Ka miƙa mashin da ke hannun ka wajen Ai, domin zan ba da Ai cikin hannunka."Yoshuwa ya miƙa mashin da ke hannunsa wajen birnin.19Sai sojojin da su ka yi kwanto a saura su ka fito da ga inda suke sa'ad da ya mika hannunsa. Su ka yi gudu su ka shiga birinin su ka cinye shi. Nan da nan su ka cinna wa birnin wuta.20Mutanen Ai su ka waiga baya. Su ka ga hayaƙi da ga birnin ya turmuƙe ya tashi sama, ba su iya kuɓucewa nan ko can ba. Gama sojojin Isra'ila da su ka gudu jeji su ka juyo su ka fuskanci masu fafarar su.21Sa'ad da Yoshuwa da dukkan Isra'ila su ka ga mutanen da su ka ɓoye sun kone birnin, da kuma hayaƙin da ke tashi, su ka juyo su ka karkashe mutanen Ai.22Sauran sojojin Isra'ila, waɗanda su ka shiga birnin, su ka fito su kai masu hari. Ta haka aka cafke mutanen Ai gaba da baya a tsakiyar rundunar Isra'ila, wasu a wannan gefe wasu a can. Isra'ila su ka buga mayaƙan Ai; ba wanda ya tsira ko ya kuɓuce.23Su ka tsare sarkin Ai, wanda suka kama da rai, su ka kawo shi wurin Yoshuwa.24Ana nan da Isra'ila ta gama karkashe mazaunan Ai a fili kusa da jejin da su ka fafare su, sa'ad da dukkansu, har ga na ƙarshe su ka mutu da kaifin takobi, dukkan Isra'ila su ka koma Ai. Su ka faɗa masu da kaifin takobi.25Dukkan waɗanda aka kashe maza da mata, dubu goma sha biyu ne, dukkan mutanen Ai.26Yoshuwa bai janye hannunsa ba da ya mika ta sa'ad da ya ke rike da mashi, har sai da ya gama hallakar da dukkan mutanen Ai.27Isra'ila su ka ɗauki dabbobi kawai da ganimar da ke cikin birnin don kan su, kamar yadda Yahweh ya umarci Yoshuwa.28Yoshuwa ya ƙone Ai ya maishe ta kango har abada. Yasasshen wurin ne har yau.29Ya rataye sarkin Ai akan bishiya har sai maraice. Da rana ta kusan faɗuwa, Yoshuwa ya umarta a saukar da gangar jikin sarki da ga itace a jeffa shi a kofar birnin. A nan ne su ka tula tarin duwatsu akansa. Tsibin ya na nan har yau.30Sai Yoshuwa ya ginawa Yahweh bagadi, Allah na Isra'ila, a kan Dutsen Ebal,31dai - dai yadda Musa bawan Yahweh ya umarci mutanen Isra'ila, kamar yadda aka rubuta a littafin shari'a ta Musa: "Bagadi da ga duwatsun da ba a sassaƙa ba, wanda ba mutumin da ya ɗibiya guduma a kai." Ya mika hadayun ƙonawa ga Yahweh akan bagadin, su ka kuma miƙa hadayun salama.32A nan a gaban mutanen Isra'ila ya rubuta shari'ar Musa bisa duwatsun.33Dukkan Isra'ila, da shugabanninsu, da hakimai, da mahukuntansu, su ka tsaya a gefe biyu na akwatin alƙawari a gaban firistoci da Lebiyawa da ke ɗaukar akwatin alƙawari na Yahweh - baƙi da haifaffun wurin - rabinsu su ka tsaya a gaban Dutsen Gerizin, rabin kuma su ka tsaya a gaban Dutsen Ebal. Su ka albarkaci mutanen Isra'ila, kamar yadda Musa bawan Yahweh ya umarce su tun da farko.34Bayan haka, Yoshuwa ya karanta dukkan zantattukan shari'a, da albarkun da la'anun, kamar yadda aka rubuta a littafin shari'a.35Babu kalma ko ɗaya da ga dukkan abin da Musa ya umarta da Yoshuwa bai karanta a gaban taron Isra'ila ba, har ma da mata, da ƙananan yara. da baƙin da su ke zaune tare da su.
Waɗannan jimla biyun a takaice na nufin abu ɗaya ne. Yahweh ya haɗa su ne domin yă nanata cewa babu dalilin jin tsoro.
Ba da su ga Isra'ila na nufin ba wa Isra'ila nasara da mulki a kansu. AT: "Na ba ku nasara a kan sarkin Ai da mutanensa, na kuma ba ku mulki a bisa birninsa da ƙasarsa"
Allah na maganar abinda ya alƙawarta kamar ya rigaya ya aikata ne, domin ba shakka zai yi haka. AT: "Ba shakka za ba" ko kuma "Ina ba da"
Kalmar nan "ta" na nufin birnin Ai. Akam kiran biranane kamar mata. AT: "sarkinsu"
"sojojin Isra'ila"
"mazaje 30,000"
Yoshuwa ya cigaba da bayanin shirin yaƙi ga mayaƙan.
Anan "hannu" alama ce na mulki da iƙo da mutanen ka da shi a bisa makiyansu.
Yoshuwa ya gama bayanin shirin yaƙin ga mayaƙan.
Wannan jimlar nan nufin cewa Yoshuwa yana aikana mazaje dubu talatin da ya zaɓa su su je su yi wa Ai kwanto a wurin da za su yi kwanto.
"wurin da za su ɓuya har sai lokacin kai hari"
"mutum 5 000." Mai yiwuwa suna daga "mazaje dubu talatin"
Isra'ilawan sun yi shirin yaƙi da mutanen Ai.
Wannan na nufin babbar rundunar mazajen yaƙin, waɗanda basu rundunar kwanto.
waɗanda "ke kwanto a yammacin birnin" (Duba: 8:10)
"suka yi kamar mutanenAi sun rinjaye su." Kalmar nan "yi kamar" na nufn abinda mutanen Ai za su ga su kuma yi tunani. AT: "suka bar mutanen Ai su yi tunani kamar sun yi nasara da Isra'ilawa"
AT: bar mutanen Ai su ɗauki cewa sun rigaya sun yi nasara da Isra'ilawa"
Kalmar nan "su" na nufin mayaƙan Ai ne.
Kalmar nan "su" anan na nufin mayaƙan Isra'ila.
AT: "Shugabannin birnin su ka kira dukkan mutane da ke cikin birnin"
Marubucin yana magana ne na duka game da dukkan mutane, amma dai yana maganar dukkan mutanen da za su iya faɗa ne., AT: "dukkan mutane da ke garin da za su iya bin mayaƙan Isra'ila"
sa a buɗe ƙofofin birnin"
Ba da Ai a cikin hannun Isra'ila na nufin ba wa isra'ila nasara da mulƙi akan Ai. AT: "Zan ba ku nasara a kan Ai" ko kuma "Zan sa ku kama Ai"
Murubucin yana amfani ne da waɗannan jimla biyun, da ke da ma'anan kusan ɗaya domin yă nanta cewa Isra'ilawan sun yi biyayya da umarnin Allah su karkashe kowa da kowa a Ai.
Faɗuwa na nufin mutuwa, sa'annan kaifin takobi na nufin yaƙi ko sojojin Isra'ila. AT: "suka mutu a yaƙi" ko kuma "suka mutu da sojojin Isra'ila suka kai masu hari"
"12, 000"
Wannan shi ne wurin da mutane suka taɓa zama, amma babu masu zama a wurin kuma.
"har yanzu" ko kuma "ko yanzu"
a sutsen Kan'anan
AT: "Yoshuwa ya karana sukkan abinda Musa ya umarta" ko kuma "Yoshuwa ya karanta dukka dokokin Musa"
Wannan na nufin al'umman Isra'ila.
1Sai dukkan sarakunan dake zaune a ƙetaren Yodan a ƙasar duwatsu, da kuma kwarin gaɓar Babbar Teku wajen Lebanon - Hitiyawa, Amoriyawa Kan'aniyawa, Feriziyawa Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa -2waɗannan su ka tattaru ƙarƙashin tuta guda, domin su yaƙi Yoshuwa da Isra'ila.3Da mazaunan Gibiyon su ka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,4su ka yi masu hila. Suka tafi kamar jakadu. Su ka ɗauki koɗaɗɗun buhuna su ka ɗibiya su kan jakunansu. Su ka kuma ɗauki tsofaffin salkunan ruwan inabi da su ka ƙoɗe, yagaggu, sun kuma sha ɗinki.5Su ka sa tsoffofin takalman da suka sha gyara a ƙafafunsu, su ka sa ka tsofoffin riguna da su ka koɗe. Guzurin wainarsu kuma duk sun bushe sun yi fumfuna.6Su ka tafi wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal, su ka ce masa da shi da mutanen Isra'ila, "Mun taho da ga ƙasa mai nisa, saboda haka sai ku yi alƙawari da mu."7mutanen Isra'ila su ka cewa Hiviyawa, "Watakila ku na zaune kusa da mu. Ƙaƙa za mu yi alƙawari da ku?"8Su ka cewa Yoshuwa, "Mu bayinka ne," Yoshuwa ya ce masu, "Ku su wanene? Daga ina ku ka fito?"9Su ka ce masa, "Barorinka sun zo daga ƙasa mai nisa, sabili da sunan Yahweh Allahnka. Mun ji rahoto a kan sa da kuma dukkan abubuwan da ya yi a Masar -10da dukkan abubuwan nan da ya yi wa sarakunan nan biyu na Amoriyawa da ke hayin Yodan - Sihon sarkin Hesbon da kuma Og sarkin Bashan da ke Astarot.11Dattawanmu da dukkan mazaunan ƙasarmu su ka ce mana, 'Ku ɗauki guzuri a hannuwanku saboda tafiyarku. Ku je ku same su ku ce masu, "Mu bayinku ne. Ku yi yarjejeniya da mu."12Waɗannan gurasunmu ne, da ɗumi mu ka ɗauko su daga gida ranar da mu ka fito tafiya gunku. Amma yanzu, ku duba, sun bushe sun kuma yi funfuna.13Wannan salkunan ruwan inabi sabbi ne da muka cika su, amma ku duba, yanzu suna ɗiga. Rigunanmu da takalmanmu sun koɗe saboda nisan tafiya."'14Sai Isra'ilawa su ka karɓi waɗansu guzurinsu, amma ba su biɗi shawara ba da ga Yahweh domin ya bishe su.15Yoshuwa ya dai - daita da su ya kuma yi alƙawari da su, a barsu su rayu. Shugabannin mutanen kuma su ka yi masu alƙawari.16Bayan kwana uku da Isra'ilawa su ka yi alƙawari da su, sai su ka ji ai makwabtansu ne kuma su na zaune kurkusa.17Sai mutanen Israa'ila su ka tashi su ka isa biranensu a kan rana ta uku. Biranensu kenan Gibiya, Kefira, Birot, da Kiriyet - Yarim.18Mutanen Isra'ila ba su kai masu hari ba saboda shugabanninsu sun rantse masu a gaban Yahweh, Allah na Isra'ila. Isra'ilawa dukka su ka yi ta gunaguni găba da shugabanninsu.19Amma dukkan shugabanni su ka cewa mutane dukka, "Mun rigaya mun rantse masu da Yahweh Allah na Isra'ila, yanzu fa ba za mu cuce su ba.20Ga abin da za mu yi masu: Domin mu guji duk wani fushi da zai afko mana sabili da rantsuwa da mu ka yi masu, za mu bar su su rayu.21Shugabanni su ka cewa mutanensu, "Mu bar su su rayu." Sabili da haka, Gibiyaniyawa su ka zama masu sarar itace da masu jan ruwa domin dukkan Israa'ilawa, kamar yadda shugabanni su ka umarta game da su.22Yoshuwa ya kira su ya ce, "Me ya sa ku ka ruɗemu ku ka ce, 'Muna nesa da ku', alhali kuwa ku na nan cikinmu?23Yanzu fa, sabili da wannan, la'anannu ne ku waɗansunku za su zama bayi ko yaushe, masu saro itace da masu jan ruwa domin gidan Allahnmu."24Su ka amsa wa Yoshuwa su ka ce, "Sabili da an faɗa wa bayinka cewa, Yahweh Allahnku ya umarci bawansa Musa ya ba ku dukkan ƙasar, ya kuma karkashe dukkan mazaunan ƙasar a gabanku - shi ne mu ka ji tsoronku saboda ranmu. Shi ya sa mu ka yi wannan abu.25Yanzu dai, ku duba, muna ƙalƙashin ikonku. Duk iyakar abin da ku ka ga ya dace kuma dai -dai ne ku yi da mu, sai ku aiwatar."26Sai Yoshuwa ya yi masu haka: ya fitar da su da ga ƙarƙashin mallakar mutanen Isra'ila. Isra'ilawa kuwa ba su kashe su ba.27A ranar Yoshuwa ya maida Gibiyanawa masu sarar itace da masu jawo ruwa domin mutanen Isra'ila, da na bagadin Yahweh, har wa yau, duk inda Yahweh ya zaɓa.
gajertaccen sunar da ake kiran Kogin Urdu
Anan "tuta" na nufin mai umurtansu. Kasancewa a karkashinsa na nufin biyayya da umarninsa. AT: "biyayya da umarnin shugaba guda"
wani makirci ne da kaɗa niyyar zambar Yoshuwa da Isra'ilawa.
...
Wannan na nufin al'ummar Isra'ila.
Wannan wata suna ce na Gibiyaniyawa.
Yoshuwa yana nanata ne da cewa ya wajaba mutanen Isra'ila su bi umurnin Yahweh fiye da da dukkan kome. AT: "Idan kuna zaune kusa da mu, ba za mu iya yin alƙawari da ku ba."
Wannan wata gajertaccen suna ce da ake kiran Kogin Urdu.
Wannan shi ne sunan sarkin Amoriyawa da aka yi nasara da shi.
Wannan shi ne sunan birnin sarautar ƙasar Mowaba.
Wannan shi ne sunnan sarkin Bashan da aka yi nasara da shi.
Wannan shi ne sunan wani birni da aka sani da yi wa wata allahiya mai wannan sunan.
Jimlar na nufin "ta tafi da shi." Annan kalmar nan "hannu" na nufin kayar arziki daga Gibiyaniyawa.
Kalmar nan "su" na nufin mutanen Isra'ila.
Waɗannan jimla biyun dai na fadin abubuwan da suka faru ne. Yoshuwa, shugaban al'ummar Isra'ila ya alaƙwarta cewa ba zai Gibiyaniyanawa. Shugabannin al'ummar Isra'ila, haka ma, ya yi wannan alƙawari.
Anan wannan na nufin jama'ar Isra'ila.
...
Wannan yana ɗaya daga cikin biranen Gibiyaniyawa.
Wannan sunan wani wuri ne.
Wannan sunan wani wuri ne.
Anan wannan jimlar na nufin al'ummar Isra'ila.
...
Anan wannan jimlar na nufin wurin kasancewar Yahweh, Akwatin Alƙawari.
Kalmar nan "kyau" da kuma "dai-dai" a takaice na nufin abu ɗaya.
Kalmar nan "su" anan na nufin Gibiyaniyawa.
Jimlar nan "wa yau" na nufin lokacin da marubucin na da rai.
1Yanzu da Adonizedek, sarkin Yerusalem, ya ji yadda Yoshuwa ya kama Ai kuma har ya hallakar da ita baki ɗaya (kamar yadda ya yi da Yeriko da kuma sarkinta) ya kuma ji yadda mutanen Gibeyon suka ƙulla alkawarin zaman lafiya da Isra'ila har ma suna acikinsu.2Mutanen Yerusalem sun tsorata ƙwarai gama Gibeyon babban birnin ainin, kamar ɗaya daga cikin manyan sarakunan biranen. Har ma ta fi Ai ga shi kuma dukkan mayaƙan mazaje ne ƙarfafa.3Saboda haka Adonizedek, sarkin Yerusalem, ya aika da saƙo ga Hoham, sarkin Hebron, ga Piram, sarkinYarmut, da Yafiya sarkin Lakish, da kuma Debir sarkin Eglon:4"Ku zo nan wurina ku taimake ni. Bari mu je mu yaƙi Gibeyon gama sun ƙulla alkawarin salama tare da Joshuwa da kuma mutanen Isra'ila."5Sarakunan nan biyar na Amoriyawa, sarkin Yerusalem da sarkin Hebron da sarkin Yarmut da sarkin Lakish, da sarkin Eglon sun zo, dukkansu kuma da abokan gãbarsu. Sun kafawa Gibeyon sansani domin su yaƙe ta.6Mutanen Gibeyon sun aika da saƙo ga Yoshuwa da kuma sojojin Gilgal. Sun ce, "Zo da sauri! Kada ka janye hanuwanka daga bayinka. Zo wurinmu da sauri ka ce-ce mu. Taimaka mana, domin dukkan sarakunan Amoriyawa da suke zaune a ƙasar tuddai sun tattaru a kanmu."7Joshuwa ya tafi daga Gilgal, shi da dukkan mutanen yaƙinsa, tare da dukkan jarumawa.8Yahweh kuma ya ce da Yoshuwa, "Kada ka ji tsoronsu. Na riga na ba da su a hannunka. Babu wani daga cikinsu da zai hana ka yaƙe su."9Yoshuwa ya tafi nan da nan ya auka masu, bayan ya yi tattaki dukkan dare daga Gilgal.10Yahweh kuwa ya rikita abokan gãbar Isra'ila, Isra'ilawa kuwa su ka kashe su da yawa a Gibeyon su ka bi su ta hanyar haurawa zuwa Ber-horon, a nan masu ka yi ta karkashe su a hanyar Azeka da Makkeda.11A sa'ad da suke gudu daga Isra'ilawa, a gangarar hawan Bet-horon, Yahweh ya jefe su da manyan duwatsu daga sama a kansu dukka hanyar zuwa Azeka, sun kuma mutu. Waɗanda suka mutu ta ƙanƙarar duwatsu sun fi yawan mutanen Isra'ila su ka kashe da takobi.12Sai Yoshuwa ya yi magana da Yahweh a ranar da Yahweh ya ba mutanen Israila nasara a kan Amoriyawa. Wannan shi ne abin da Yoshuwa ya ce da Yahweh a gaban Isra'ila, "Rana, ki tsaya a Gibeyon, wata kuma, a kwarin Ayalon."13Rana ta tsaya cik, wata kuma ya tsaya ba ya motsi har al'ummar ta ɗauki fansa a kan abokan gãbarsu. Wannan ba shi ne ke rubuce a Littafin Yashar ba? Rana ta tsaya a tsakar sararin sama; ba ta faɗi ba dukkan yini.14Ba a taba yin yini kamar wannan ba ko kuma makamancinsa ba, da Yahweh ya saurari muryar mutum. Domin Yahweh ya yi yaƙi a madadin Isra'ila.15Yoshuwa tare da dukkan Isra'ila sun koma zango a Gilgal.16Yanzu waɗannan sarakuna biyar kuma suka gudu suka ɓuya a cikin kogon Makkeda.17Sai aka faɗawa Yoshuwa, "An same su-sarakuna biyar suna ɓoye a kogon Makkeda."18Yoshuwa ya ce, "Murgina manyan duwatsu a kan bakin kógon a kuma sa sojoji a wurin don su tsaresu.19Amma kada ku tsaya. Sai ku runtumi abokan ǧabanku ku kuma faɗa masu daga baya. Kada ku bar su su shiga biranensu, gama Yahweh Allahnku ya rigaya ya ba da su a hannunku."20Yoshuwa da 'ya'yan Isra'ila sun gama karkashe su kisa mai yawa ƙwarai, har sai da aka kusan halaka su dukka; sai sauran kaɗan ne ba a kashe ba; sauran da su ka ragu suka shige birane masu garu.21Sa'annan dukkan sojojin sun koma da salama wurin Joshuwa a sansani a Makkeda. Ba kuma mutumin da ya faɗi wata kalmar ǧaba da ɗaya daga cikin mutanen Isra'ila.22Sai Yoshuwa ya ce, "Ku buɗe bakin kógon kuma daga cikin kogon ku ba ni waɗannan sarakuna biyar."23Sun aikata kamar yadda ya ce. Sun kawo masa waɗannan sarakuna biyar daga kógon--sarkin Yerusalem, sarkin Hebron, sarkin Yarmut, sarkin Lakish, da kuma sarkin Eglon.24Da su ka kawo sarakunan a wurin Yoshuwa, ya ƙirawo kowanne mutum da ke Isra'ila. Ya cewa shugabanin mayaƙa waɗanda su ka tafi tare da shi, "Ku sa ƙafafunwanku a wuyansu."Su kuwa sun zo sun taka wuyansu da ƙafafuwansu.25Sai ya ce da su, "Kada ku ji tsoro ko kuwa ku razana. Ku yi ƙarfin hali. Wannan shi ne abin da Yahweh zai yi da dukkan abokan gãbarku waɗanda za ku yi yaƙi da su.26Sai Yoshuwa ya kai masu hari har ya kashe sarakunan. Ya kuma rataye su a kan itatuwa biyar. An rataye su a kan itatuwa har yamma.27Amma sa'ad da rana take faɗuwa, Yoshuwa ya ba da umarni, sai aka saukar da gawawwakinsu daga bisa itatuwan sai aka jefa su cikin kõgon da su ka ɓoye kansu. Sai su ka sa manyan duwatsu aka rufe baƙin kõgon. Waɗannan duwatsun suna nan har wannan rana.28Ta wannan hanya, Yoshuwa ya kama Makkeda a ranar, ya kuma kashe kome a wurin da takobi, har ma da sarkin. Ya hallakar da su da dukkan wani abu mai rai a wurin. Bai ƙyale kowa da rai ba. Ya yi wa sarkin Makkeda kamar yadda ya yi wa sarkin Yeriko.29Yoshuwa tare da dukkan Isra'ilawa sun zarce daga Makkeda zuwa Libna.30Yahweh kuma ya ba su ita ta hannun Isra'ila -- tare da sarkinsu. Yoshuwa kuwa ya kashe kowanne abu da ke rayuwa a cikinta da takobi. Bai bar wani abu da zai rayu ba a cikinta. Ya yi wa sarkin kamar yadda ya yi wa sarkin Yeriko.31Sai Joshuwa tare da dukkan Isra'ila su ka zarce daga Libna zuwa Lakish. Ya kewaye ta kuma ya auka mata da yaƙi.32Yahweh ya ba da Lakish a hannun Isra'ila. Yoshuwa ya cinye ta a rana ta biyu. Ya kashe kowanne abu mai rayuwa da takobi wanda ke cikinta, kamar yadda ya yi da Libna.33Sai Horam, sarkin Gezer, ya zo ya kawo wa Lakish taimako. Yoshuwa kuwa ya fãɗa masa shi da sojojinsa har babu wani abu mai rai da ya rage.34Sai Yoshuwa tare da dukkan Isra'ila su ka zarce zuwa Lakish ta Eglon.35Sun kewaye ta sun auka mata da yaƙi, a wannan rana su ka cinyeta da yaƙi. Sun buge ta da takobi sun kuma hallaka kowanne mutum da ke cikinta, kamar yadda Yoshuwa ya yi a Lakish.36Sai Yoshuwa tare da dukkan Isra'ila su ka haura daga Eglon zuwa Hebron.37Sun auka mata da yaƙi. Sun cinyeta suka kuma bugi kowanne mutum da ke cikinta da takobi, har ma da sarkin da kuma dukkan ƙauyukan da ke kewaye da ita, sun karkashe komai da ke rayuwa a cikinta, ba su ƙyale wani abu da zai rayu ba, kamar yadda Yoshuwa ya yi wa Eglon. Ya hallaka komai da kowanne abu mai raI a cikinta.38Sai Yoshuwa ya juya, tare da dukkan sojojin Isra'ila da ke tare da shi, sun kuma wuce zuwa Debir sun kuma auka mata da yaƙi.39Ya kame ta tare da sarkinta, da dukkan ƙauyukan da ke kewaye da ita. Sun buge su da takobi har sun kashe dukkan abun da ke rayuwa a cikinta. Yoshuwa bai bar masu rayuwa ba, kamar yadda ya yi a Hebron da sarkinta, da kuma kamar yadda ya yi a Libna da sarkinta.40Yoshuwa ya ci nasara da dukkan ƙasar, da tuddan ƙasar, da Negeb, da filayen kwarurruka, da kuma gangare. Da dukkan sarakunansu babu wanda ya tsira. Ya karkashe su babu wani abu mai rai, kamar yadda Yahweh, Allah na Isra'ila, ya ummarta.41Yoshuwa kuwa ya kai masu hari da takobi tun daga Kadesh Barneya har zuwa Gaza, da dukkan ƙasar Goshen zuwa Gibeyon.42Yoshuwa kuma ya cinye dukkan waɗannan sarakuna da kuma ƙasashensu a lokaci ɗaya domin Yahweh Allah na Isra'ila, ya yi yaƙin don Isra'ila.43Sa'annan Yoshuwa, da dukkan Isra'ila tare da shi, sun koma zuwa zango a Gilgal.
Marubucin yana amfani ne da wannan kalmar domin ya dan kauce daga ainihin labarin da yake bayar wa. Anan, marubucin ya yi magana ne game da wani sabon mutum mai suna Adonizedek a labarin.
Wannan sunan wani mutum ne, sarki mai muhimmanci. *
Waɗannan sunayen birane ne.
Waɗannan sunayen sarakuna ne.
"Ku yi tafiya zuwa wurin da nake." Yerushalima yana sama da sauran biranen Kan'anan a tadawa.
"sarakunan ... 5"
Waɗannan sunayen birane ne.
Wannan na nufin cewa sun kafa sansanin su kewaye da biranen su. Wannan wata hanya ce na ƙarya wa waɗanda ke cikin garin gwiwa. Ya hana mutanen birnin fita su gudu, ya kuma hana sauran mutane kawo wa mazaunan garin abinci da ruwa.
Kalmar nan "Su" na nufin Gibiyoniyawa.
... AT: "Muna roƙo, ka zo ka yi amfani da ƙarfinka ka kare mu."
Kalmar nan "hannuwa" na nufin mutane, ƙarfin Israra'ila. AT: "ƙarfinka"
Anan "hannu" na nufin ƙarfin mutanen Isra'ila da kuma iya nasara da maƙiyansu. Kalmar nan "su" na nufin kai hari ga mayakan.
Kalmar nan "su" na nufin mayaka masu kawo hari.
Ana kiran dukkan mayaƙan Isra'ila ne anan da sunan shugabansu, Yoshuwa.
Anan "Isra'ila" na nufin mayaƙan Isra'ila gaba ɗaya.
Waɗannan sunayen birane ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
...
Yoshuwa yana addu'a cewa Yahweh tsayar da tafiyar lokaci a wannan rana.
Yoshuwa ya umurce rana da wata kamar mutane ne su.
Wannan sunan wani wuri ne.
Wannan na nufin mutanen Isra'ila.
Marubucin yana amfani ne da wannan tambayan domin yă yi wa masu karatu bayani yă kuma tunashe su cewa abinda ya faru yana nan a rubuce. AT: "Wannan shi ne rubuttacen Littafin Yashar."
Wannan sunan wani birni ne.
'Yan ba da sako sun zo sun faɗa wa Yoshuwa. AT: "Wani ya faɗa wa Yoshuwa"
Jimlar nan "hannunku" annan na nufin "iƙon ku."
Ku juya wannan sunan kamar yadda kuka yi a 10:9.
Anan "kalma ɗaya" na nufin maganar maƙiyan Isra'ila. AT: "Ba kuma mutumin da ya yi gunaguni ko tawaye ǧaba"
Anan "baki" karin magana ne da ke nufin "ƙofar shiga." AT: "Ku buɗe ƙofar shiga kogon"
Waɗannan sunayen wurare ne.
kowane soja da ke Isra'ila
"har marubucin ya rubuta wannan labarin"
Wannan sunan wani birni ne. Duba yadda kuka juya wannan a 10:9.
Jimla na biyun yana taƙaita jimla na farin ne domin a nanata cewa Yoshuwa bai bar ko mutum ko dabba da rai ba.
Wannan sunan wani birni ne.
Anan "hannu" na nufin "iƙon." AT: "ba wa Isra'ilawa iƙon"
Waɗannan sunayen birani ne.
Wannan jimlar nan nufin "ba da iƙo ga al'ummar Isra'ila." AT: "Yahweh ya ba da Lakish a karkashin al'ummar Isra'ila"
Wannan sunan wani mutum ne, sarki mai muhimminci.
Waɗannan sunayen birane ne.
Waɗannan sunayen birane ne.
Waɗannan jimlar biyun na da ma'ana ɗaya. Dukkansu na nuna cikar hallakar Eglon.
Wannan sunan wani birni ne. )
AT: "Sun auka mata suka kashe sun kuma hallaka"
Waɗannan jimla biyun a takaice na faɗin abu ɗaya ne kuma an haɗa su ne domin a nanata. A haɗe suna jadada tsananin hallakar Hebron ne.
Waɗannan sunayen birane ne.
Takobi anan na nufin mayakan Isra'ila yana kuma bayana yadda suka yayyanke su suka kuma hallaka su. AT: "Suk kakkashe su sun hallakar da su"
Jimla biyun na da ma'anan ɗaya ne, yana kuma nanata cikar hallakar da mutanen Isra'ila suka yi bisa ga umurnin Yahweh.
Takobi anan na nufin mayakan Isra'ila yana kuma bayana yadda suka yayyanke su suka kuma hallaka su. AT: "Yoshuwa ya kashe ya kuma hallakar da su"
Wannan na nufin sarakuna da kasashe da aka lisafta da farko a 10:28.
Anan Yoshuwa na nufin dukkan mayakan Isra'ila. AT: "Yoshuwa da sojojin sun kama"
Ba a kwanan ɗaya ake nufi ba. Yana nufin lokacin yaƙin sojoji, kuma yana yiwuwa ma ya ɗauki kwanaki ko makonni.
1Sa'ad da Yabin, sarkin Hazor, yaji wannan, ya aika da saƙo ga Yobab, sarkin Madon, zuwa ga sarkin Shimron, da sarkin Akshaf.2Ya kuma aika da saƙon ga sarakuna waɗanda suke arewacin ƙasar tuddai, da ke cikin kudancin Kinneret, da ke cikin filayen kwari da kuma tuddai da ke cikin Dor a yamma.3Ya kuma aika da saƙon zuwa ga Kanaaniya gabas da yamma da Amoriyawa da Hatiyawa da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa da suke cikin ƙasar tuddai, da kuma Hiwiyawa da ke Tsaunin Harmon a ƙasar Mizfa.4Dukkan mayaƙansu su ka fito wurinsu, babbar rundunar sojoji mai yawa kamar yashin teku. Su na da yawan dawakai da karusai ƙwarai da gaske.5Dukkan waɗannan sarakuna kuwa su ka shirya lokacin da za su haɗu, sun yi sansani a bakin ruwayen Merom don su yi yaƙi da Isra'ila.6Yahweh ya cewa Yoshuwa, "Kada ka ji tsoron kasancewarsu, domin gobe war haka zan ba da su ga dukkan Isra'ila kamar matattun mutane. Za ku daddatse agaran dawakansu, za ku kuma ƙone karusansu"7Yoshuwa da dukkan mayaƙansa za su ma-mayesu. Nan da nan suka zo ruwayen Meron, suka karkashe abokan ǧabarsu.8Yahweh kuma ya ba da abokan gãbar a hannun Isra'ila, sun kuma hallaka su da takobi su ka runtume su har zuwa Sidon, Misrefot Ma'im, har zuwa gabashin ƙwarin Mizfa. Sun karkashe su har babu wani mai tsira da ya rage a cikinsu.9Yoshuwa kuwa ya yi masu kamar yadda Yahweh ya faɗa masa. Ya daddatse agaran dawakansu ya kuma ƙone ƙarusansu.10A wannan lokaci Yoshuwa ya juya da baya ya ci Hazor. Ya kashe sarkinta da takobi. (Hazor ita ce cibiyar dukkan waɗannan mulkokin.)11Sun kashe dukkan abin da ke raye a wannan wurin da takobi, ya kuma hallakar da su kakaf, saboda haka babu wanda aka rage da rai a wurin. Ya kuma ƙone Hazor.12Yoshuwa kuwa ya ci dukkan biranen sarakunan. Ya kuma ci dukkan sarakunansu da takobi. Ya hallakar da su kakaf kamar yadda Musa bawan Yahweh ya ummarta.13Isra'ila ba su ƙone ko ɗaya daga cikin biranen da aka gina bisa tuddai ba, sai dai Hazor, ita kaɗai Yoshuwa ya ƙone.14Sojojin Isra'ila kuwa su ka kwashe dukkan ganima daga waɗannan birane tare da shanu domin kansu. Sun kashe kowanne mutum da takobi har sai da dukkansu su ka mutu. Ba su bar wata hallita da ke da rai ba.15Kamar yadda Yahweh ya ummarci bawansa Musa, ta hanyar da Musa ya ummarci Yoshuwa, haka nan Yoshuwa ya yi da ita. Bai bar kome ba da bai aikata ba cikin dukkan abin da Yahweh ya ummarci Musa ya yi.16Yoshuwa ya ɗauke dukkan ƙasar, da ƙasar tuddai, da dukkan Negeb, da dukkan ƙasar Goshen, da filayen kwari, da Yodan Kogin kwari, da ƙasar tuddai ta Isra'ila, da filayen gangare.17Daga Tsaunin Halak kusa da Idom, da wanda ya tafi zuwa arewa har zuwa wajen Ba'al Gad a kwari kusa da Lebanon a ƙarƙashin Tsaunin Hermon, ya kama dukkan sarakunansu ya kuma kashe su.18Yoshuwa ya ɗauki dogon lokaci yana yaƙi da dukkan sarakunan.19Ba bu wani birni da ya yi zaman salama da sojojin Isra'ila sai dai Hiwiyawa da su ke zaune a Gibiyon. Isra'ila kuwa ta ci dukkan sauran biranen da yaƙi.20Domin Yahweh ne ya taurare zukatansu har da za su tasar ma Isra'ila da yaƙi, don a hallaka su a kuma shafe su ba tare da tausayi ba, kamar yadda aka ummarci Musa.21A wannan lokaci kuwa Yoshuwa ya tafi ya kuma hallaka Anakawa. Ya kuma yi wannan a ƙasar tuddai, da Hebron, da Debir, da Anab, da kuma dukkan ƙasar tuddai ta Yahuda, da dukkan ƙasar tuddai ta Isra'ila. Yoshuwa ya hallaka su sarai duk da biranensu.22Babu wani gwarzon da ya ragu a ƙasar Isra'ila sai ko Gaza, da Gat, da kuma Ashdod.23Ta haka Yoshuwa ya ci dukkan ƙasar, kamar yadda Yahweh ya faɗawa Musa. Yoshuwa kuwa ya ba da ita gãdo ga Israila bisa ga kabilar kowa, Sai ƙasar ta shaƙata daga yaƙe -yaƙe.
Waɗannan sunayen sarakuna ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Dukkan sarakunan Kan'aniyawa sun kai wa Yoshuwa da al'ummar Isra'ila hari.
Wannan ƙari na nanata yawan sojoji da waɗannan sarakunan suka harhada. AT: "wata irin babbar rundunar sojoji da sun bayyana da yawansu wane hatsi ko yashin teku"
Wannan sunan wani wuri ne.
Ana maganar yadda Yahweh zai bar Isra'ila su yi nasara da sojoji maƙiyansu ne kamar Yahweh ya kashe sojojin sa'annan ya ba da su ga Isra'ila. AT: "Zan bar Isra'ila ta kashe dukkansu a yaƙi"
"naƙassas da dawakansu ta wurin yanke kafofinsu." Wannan wani al'ada ne da ake yanke jijiyar bayan kafafun domin a hana dawakan iya tafiya.
Wannan sunan wani wuri ne.
Kalmar nan "hannu" na nufin iƙo. Ana maganar yadda Yahweh ya bar mayaƙan Isra'ila su yi nasara da maƙiyan su ne kamar Yahweh ya sa su ne a hannan Isra'ila. AT: "Yahweh ya ba wa Isra'ila dama su yi nasara da maƙiya"
Anan kalmar nan "takobi" na nufin dukkan makamai da ake amfani da su kai wa abokan gaban su hari. AT: " sun kai masu hari da kayan yakinsu ... sun kai masu hari"
Wannan sunan wani wuri ne.
Wannan wani aal'ada ne da ake yanke jijiyar bayan kafafun domin a hana dawakan iya gudu. Ku juya wannan kalmar yadda kuka yi a 11:6.
"Yoshuwa ya kashe sarkin Hazor da takobinsa"
Ana maganar Hazor wannan birni mai muhimmanci a matsayin zama cibiyar mulkoki. AT: "Hazor ya zama birni mafi muhimminci a dukkan mulkoki"
Waɗannan jimla suna da ma'ana ɗaya suna kuma nanata hallakar wa kurmus.
Kalmar nan "ya" anan na nufin Yoshuwa ne, kuma karin magana ne da ke nufin mayaƙan da ya shugabanta. Anan maganar hallakar da abu mai rai kakaf a ne kamar an sadakar da dukkan masu rai ga hallaka. AT: "mayaƙan sun hallakar da su kakaf"
"kashe su"
"biranen da aka gina a kananan tuddai"
Wannan jimlar na nufin mayaƙan Isra'ila.
Waɗannan jimla biyun na da ma'ana ɗaya ne kuma suna nanata hallaka kakaf.
Wannan jimlar na nufin cewa Yoshuwa ya yi kome da Yahweh ya umurta. AT: "Yoshuwa ya yi kome da Yahweh ya umurta"
Waɗannan sunayen wurare ne.
AT: "Yahweh ne ya sa su su yi taurin kai"
Wato zuriyar Anak kenan.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Ana maganar yadda Yahweh ke ba wa Isra'ila ƙasar ne kamar ya ba su gãdo ne a matsayin mallaƙar su na harabada. AT: "Yoshuwa ya wa Isra'ila ƙasar ne a matasyin mallaƙar su ne na har'abada"
Wato mutanen su daina faɗe-faɗe da yaƙe-yaƙe. AT: "mutanen ba su yi yaƙe-yaƙe a ƙasar kuma ba"
1Yanzu waɗannan su ne sarakunan ƙasar, wadda mutanen Isra'ila su ka cinye da yaƙi. Isra'ilawa sun mallaki ƙasar a gabashin Yodan inda rana ta ke fitowa daga Kwarin Kogin Arnon zuwa Tsaunin Harmon, da dukkan Arabah wajen gabas.2Sihon, sarkin Amoriyawa, wanda yake zaune a Heshbon. Ya yi mulki daga Arower, wadda ta ke iyakar kwarin Arnon Gorge daga tsakiyar kwarin, har rabin Giliyad zuwa ga Kogin Yabbok iyakar Amoniyawa.3Sihon kuma ya yi mulki a kan Arabah zuwa Tekun Kinneret, da zuwa gabashin Tekun Arabah (Tekun Gishiri) a wajen gabas, da dukkan hanyar Ber Yeshimot da wajen kudu, zuwa gangaren gindin Tsaunin Fisga.4Og, sarkin Bashan, ɗaya daga cikin sauran Refayim, wanda ya zauna a Ashtarot da Edirai.5Ya yi mulki a Tsaunin Hermon, Salika, da dukkan Bashan, har zuwa iyakar mutanen Geshur da kuma Ma'akatiyawa, da rabin Giliyad, zuwa kan iyakar Sihon, sarkin Heshbon.6Musa bawan Yahweh, da mutanen Isra'ila sun yi nasara da su, kuma Musa bawan Yahweh ya ba su ƙasar gãdo ga Rubenawa, da Gadawa, da kuma rabin kabilar Manassa.7Waɗannan su ne sarakunan ƙasar waɗanda Yoshuwa da mutanen Isra'ila suka ci a yammacin Yodan, daga Ba'al Gad a ƙwari kusa da Lebanon zuwa Tsaunin Halak kusa da Idom. Yoshuwa ya ba da ƙasar ga kabilun Isra'ila don su ǧada.8Ya ba da tuddan ƙasar, da kwaruruka, da Arabah, da gefan tuddai, da jejin da kuma Negeb - ƙasar Hitiyawa, Amoriyawa, Kan'aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa, da kuma Yebusiyawa.9Sarakunan sun haɗa da sarkin Yeriko da sarkin Ai da ke kusa da Betel,10da sarkin Yerusalem da sarkin Enayim,11da sarkin Yarmut da sarkin Lakish,12da sarkin Eglon da sarkin Gezer,13da sarkin Debir da sarkin Geder,14da sarkin Horma da sarkin Arad,15da sarkin Libna da sarkin Adullam,16da sarkin Makkeda da sarkin Betel,17da sarkin Taffuwa da sarkin Hefer,18da sarkin Afek da sarkin Lasharon,19da sarkin Madon da sarkin Hazor,20da sarkin Shimron Meron da sarkin Akshaf,21da sarkin Ta'anak da sarkin Megiddo,22da sarkin Kedesh da sarkin Yokniyam a Karmel,23da sarkin Dor a Nafat Dor da sarkin Goyim a Gilgal,24da kuma sarkin Tirza. Yawan sarakunan kuwa talatin da ɗaya ne dukkansu.
Wannan kalmar na juya labarin daga labarin da ake bayarwa. Anan, marubucin na ba da tarihi ne.
Wannan na nufin jerin sarakunan da ya cigaba daga aya 24.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Ku juya waɗannan kalamun yadda kuka juya su a 9:9.
Wannan wani wuri ne. Juya wannan yadda kuka juya shi a 11:1.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Ku juya waɗannan kalamun yadda kuka juya su a 9:9.
Waɗannan sunayen rundunar mutane ne.
Waɗannan zuriyar Ruben ne.
Waɗannan zuriyar Ga ne.
Ana ce da su rabin kabila ne domin sauran rabin kabilar sun karɓi nasu gadon a ƙasar Kan'anan.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen wurare ne. Ku juya "Yarmut," "Lakish", da "Eglon" yadda kuka yi a 10:3.
Waɗannan sunayen biranene.
Waɗannan sunayen biranene.
Waɗannan sunayen biranene.
ɗaya ne dukka - "31 ne dukka"
1Yanzu Yoshuwa ya tsufa ƙwarai sai Yahweh ya ce da shi, "Ka tsufa ƙwarai, amma har yanzu akwai sauran ƙasar da yawa da ba a mallaka ba.2Wannan ita ce ƙasar da ta rage: a dukkan sashin Filistiyawa, da dukkan waɗanda ke Geshuriyawa,3(daga Shihor, wanda ke gabas da Masar da wajen arewanci iyakar Ekron, wanda ake ɗauka ta Kan'aniyawa ce, da sarakuna biyar na Filistiyawa, da su ke Gaza, Ashdod, Ashkelon, Gat da Ekron - da ƙasar Aviyawa).4A kudu (da ƙasar Aviyawa); akwai sauran ƙasashen Kan'aniyawa, da Ara wanda ta ke ta Sidoniyawa, zuwa Afek har kuma iyakar Amoriyawa;5da ƙasar Gebaliyawa, dukkan Lebanon wajen fitowar rana, zuwa Ba'al Gad ƙasar Tsaunin Hermon zuwa Lebo Hamat.6Kuma da dukkan mazaunan ƙasar tuddai daga Lebanon har zuwa can Misrefot Mayim, da dukkan mutanen Sidon. Zan kore su a gaban sojojin Isra'ila. Ka tabbatar ka raba ƙasar ga Isra'ila a matsayin gãdonsu, kamar yadda na ummarce ka.7Raba wannan ƙasar a matsayin gãdo ga kabilu tara, da kuma ga rabin kabilar Manasse.8Tare da sauran rabin kabilar Manasse, da Rubenawa da kuma mutanen Gad sun karɓi nasu gãdon wanda Musa ya ba su a wajen gabas da Yodan,9daga Arowa wadda take a gefen kwarin Kogin Arnon (ya hada da birnin da ke tsakiyar kwarin), da dukkan ƙasar tudu ta Medeba har zuwa Dibon;10dukkan biranen Sihon da sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon, zuwa ga iyakar Amoniyawa;11Giliyad, da kuma yankin Geshuriyawa da Makatiyawa da dukkan na Tsaunin Harmon da dukkan Bashan zuwa Saleka;12da dukkan mulkin Og a Bashan, wanda ya yi sarauta a Ashtarot da Edirai - waɗannan su ne ragowar mutanen Refayim - Musa ya buge su ya kuma kore su.13Amma duk da haka mutanen Israila ba su kori Geshuriyawa ko Makatiyawa ba. Maimakon haka, Geshuriyawa da Makatiyawa sun zauna a cikin Isra'ila har wa yau.14Ga kabilar Lebi ne kaɗai Musa bai ba da ta gado ba. Hadayu na Yahweh, Allah na Isra'ila, wanda aka yi da wuta, ǧadonsu, kamar yadda Allah ya faɗawa Musa.15Musa ya riga ya ba kabilar Ruben nasu ǧadon bisa ga iyali-iyali.16Nasu yankin ƙasar daga Arowa, a gefen ƙwarin Kogin Arnon, da kuma birnin da yake tsakiyar kwarin, da dukkan tuddai kusa da Medeba.17Ruben kuma ya sami Heshbon da dukkan biranenta da suke kan tudu, Dibon, da Bamot Ba-al, da Bet Ba'al Miyon,18da Yahaz, da Kedemot, da Mefa'at,19da Kiriyatayim, da Sibma, da Zeret Shahar da ta ke bisa tudun da yake cikin kwarin.20Ruben kuma ya karɓi Bet Feyor, da gangaren Fisga, da Bet Yeshimot,21da dukkan biranen kan tudu, da dukkan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya sarauci Heshbon, wanda Musa ya ci shi da yaƙi tare da shugabanin Midiyawa, Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba, sarakunan Sihon, wanda ya zauna a ƙasar.22Mutanen Isra'ila kuma su ka kashe shi da takobi, Balaam ɗan Beyor, matsubbaci, daga cikin sauran waɗanda da su kashe.23A iyakar kabilar Ruben akwai Kogin Yodan, wannan shi ne iyakarsu. Wannan shi ne ǧadon kabilar Ruben, da aka ba kowanensu na iyalinsu, tare da biranensu da ƙauyukansu.24Wannan shi ne abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalinsu:25Yankin ƙasarsu shi ne Yaza, da dukkan biranen Giliyad da rabin ƙasar Ammoniyawa, zuwa Arowa, wadda ke gabas da Rabbah,26daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, daga Mahanayim zuwa iyakar Debir.27A kwarin, Musa ya ba su Bet Haram, Bet Nimrah, Sukkot da Zafon da sauran ragowar mulkin Sihon sarkin Heshbon, tare da Yodan ne iyaka, zuwa iyakar Tekun Kinneret a gabashin hayin Yodan.28Wannan shi ne gãdon kabilar Gad bisa ga iyalinsu, tare da biranensu da ƙauyukansu.29Musa ya ba da gãdo ga rabin kabilar Manasse. An ba da ita ga rabin kabilar mutanen Manasse, bisa ga iyalinsu.30Yankin ƙasarsu daga Mahanayim, da dukkan Bashan da dukkan sarautar Og sarkin Bashan da dukkan garuruwan Yayir da waɗanda su ke a Bashan, birane sittin ne;31rabin Giliyad, da Ashtarot da Edirai (biranen masarautar Og a Bashan). Waɗannan ne aka ba da su ga iyalin Makir ɗan Manasse - rabin mutanen Makir, an ba kowanne iyali.32Wannan shi ne gãdon da Musa ya ba su a kan filayen Mowab, a hayin gabashin Yodan na Yeriko.33Musa bai ba kabilar Lebi gãdo ba. Yahweh, Allah na Isra'ila, shi ne gãdonsu, kamar yadda ya faɗa masu.
Kuna iya karin bayani cewa wannan ita ce ƙasar da Isra'ila tana buƙata ta kama. AT: "Wannan itace ƙasar da ya rage wa Isra'ila ta kama"
Wannan sunan wani wuri ne.
AT: "Wanda Kan'ananiyawa suna ɗauka nasu ce"
Wannan sunan wata kabila ce.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Wannan sunan wata kabila ce da ke zama a Geba.
Wannan sunan wani wuri ne
Ana maganar ƙasar da Isra'ila za ta mallaka ne kamar gãdo ne da zasu karba a matsayin mallakar su ta har abada.
Waɗannan sunayen wurare ne.
wuri ne da kogin ke kasa da ƙasa a gefe-gefen
...
Waɗannan sunayen wurare ne.
"ƙasar da Geshuriyawa da Makatiyawa ke zama"
Waɗannan sunayen kabilu ne.
Anan "Musa" na nufin mayaƙan Isra'ila da Musa ya shugabanta. AT: "Musa da Isra'ilawan suka kai wa hari"
Waɗannan sunayen kabilu ne.
"Geshur" da "Ma'aka" sunayen kakkanin "Geshuriyawa" ko kuma sunayen birane ne suka zauna. AT: "mutanen da ke zama a cikin Isra'ila"
Wannan na nufin lokacin da marubucin ya wallafa wannan litafi.
Ana maganar ƙasar da Musa ya sanya wa kabilun Isra'ila ne kmamar wata gãdo ne da suka karɓa a matsayin mallaka na har abada.
Marubucin yana maganar babbar girma da Lewiyawan za su samu ta wurin bauta wa Yahweh as matasyin firistoci ne kamar hadayun wani abu ne da za asu gãda. AT: "Haduyun Yahweh ... su ne abinda za su samu a tanaɗinsu"
"Haduyun da mutanen za su kawo wa Yahweh"
AT: "da firistoci suka ƙona da wuta"
Waɗannan sunayen wurare be.
Ku juya waɗannan kalamun yadda kuka juya su a 13:8.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
"yadda ya ci nasara da shugabannin Midiyawa"
Kogin Urdu ne iyakar yammacin ƙasar da kabilar Ra'ubain suka samu.
Ana maganar ƙasar da Musa ya sanya wa kabilar Ra'ubainu ne kamar wani gãdo ne da kabilar Ra'ubainu suka samu a matasyin mallakar su na har'abada.
AT: "da Musa ya sanya wa kowanne iyalinsu"
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Ana maganar ƙasar da Musa ya sanya wa kabilar Gad ne kamar wani gãdo ne da kabilar Gad suka samu a masyin mallakar su na har abada.
Ana maganar ƙasar da Musa ya ba wa rabin kabilar Manassa ne kamar wani gãdo ne da ya ba su a matasyin mallakar su na har abada.
Rabin kabilar ne kawai sun samo wannan ƙasar domin sauran rabin su samo wuri a ɗayan gefen Kogin Urdun.
AT: "Musa ya ba da ita"
Waɗannan sunayen wurare ne.
AT: Waɗannan ne Musa ya sa su"
Ana maganar ƙasar da Musa ya ba kabilun isra'la a gabashin Urdun kamar wani gãdo ne da Musa ya ba su a matasyin mallakar su na har abada. AT: "Wannan shi ne ƙasar da Musa ya ba su gãdo"
Marubucin yana maganar babbar girma da Lewiyawa za su samu ta wurin bauta wa Yahweh a matsayin firistoci kamar Yahweh wani abu ne da za su gãda. AT: "Yahweh, Allah na Isra'ila, shi ne na su"
1Waɗannan su ne yankunan ƙasar da mutanen Isra'ila suka karɓa matsayin gãdo a ƙasar Kan'ana, wanda Eliyeza firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma iyalin shugabainin kabilun kakaninsu na mutanen Isra'ila.2Gãdonsu ya sa mu ne ta hanyar jefa kuri'a don kabilun nan tara da rabi, kamar yadda Yahweh ya ummarta ta hannun Musa.3Domin Musa ya riga ya ba da gãdon ga kabilu biyu da rabi can hayin Yodan, amma ga Lebiyawa bai ba su gãdo ba.4Kabila Yosef kuma kabilu biyu ne, Manasse da Ifaim. Lebiyawa kuwa ba a ba su wani yanki na ƙasar gãdo ba, sai dai an ba su birane da za su zauna, tare da filayen da za su yi kiwon garkensu da kuma kayan da su ke bukata.5Mutanen Isra'ila kuwa su ka yi kamar yadda Yahweh ya ummarci Musa, sun rarraba ƙasar.6Sai kabilar Yahuda suka je wurin Yoshuwa a Gilgal. Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze, ya ce masa, "Ka san abin da Yahweh ya ce da Musa mutumin Allah a kanka da ni a Kadesh Barneya.7Ina da shekaru arba'in sa'ad da Musa bawan Yahweh ya aike ni daga Kadesh Barneya in leƙo asirin ƙasar. Na kuma kawo masa ainihin rahoton yadda ya ke a zuciyata.8Amma 'yan'uwana da mu ka tafi tare sun karyar da zukatan mutanen da tsoro. Amma ni da na bi Yahweh Allahna.9Musa kuwa ya rantse a wannan rana, cewa, 'Hakika a ƙasar nan wanda ƙafafunka su ka ta ka za ta zama gãdonka da kai da 'ya'yanka har abada, domin ka bi Yahweh Allahnka sosai.'10Yanzu, duba! Yahweh ya kiyaye ni da rai waɗannan shekaru arba'in da biyar, kamar yadda ya faɗa-daga lokacin da Yahweh ya faɗi wannan magana ga Musa, sa'ad da Isra'ila suke tafiya a jeji. Yanzu, duba! ina mai shekaru tamanin da biyar da haihuwa.11Har wannan rana ina nan kamar ranar da Musa ya aike ni waje. ƙarfina yanzu yana nan kamar ƙarfin dă domin yaƙi da kuma zuwa da kowowa.12Saboda haka yanzu ka ba ni ƙasar tuddai, wadda Yahweh ya yi mani alkawari a waccan rana. Gama ka ji a wannan rana yadda gwarzaye suke a can da manyan birane masu garu. Watakila Yahweh zai kasance tare da ni, ni kuma in kore su, kamar yadda Yahweh ya faɗa."13Sai Yoshuwa ya sa masa albarka ya kuma ba da Hebron a matsayin gãdo ga Kalibu ɗan Yefunne.14Saboda haka Hebron ta zama gãdon Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze har zuwa wannan rana, domin ya bi Yahweh, Allah na Israila sosai.15Yanzu sunan Hebron kamar da Kiriyat Arba ne. (Arba kuwa ya zama babbban mutum ne cikin gwarzayen.) Ƙasar kuwa ta huta daga yaƙi.
Ana maganar ƙasar da mutanen Isra'ila suka samu ne kamar gãdo ne da suka samu a matsayin mallakarsu ta har abada.
AT: "da Ele'azara firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma kakkaninsu shugabannin iyalin kabilun cikin mutanen Isra'ila suka basu"
...
AT: "Eliyezara, da Yoshuwa, da shuganannin kabilun sun jefa kuri'a domin sanin gaskiyar gãdon"
Anan "kalmar nan "hannu" na maganar Musa ne da kansa kuma yana nufin cewa Yahweh ya yi amfani ne da Musa a natasyin wakili domin yă isar da umurni. AT: "ta wurin Musa"
rabin kabilar na bayan Urdu, amma bai ba wa Lewiyawan gãdo ba- Ana maganar ƙasar da Musa ya ba wa kabilun ne kamar gãdo ne da suka samu a matasyin mallakar na har abada.
AT: "Kuma Musa bai ba wa Lewiyawa wani yankin ƙasar a su gãda ba"
"bangare"
AT: "amma ya ba su wasu birane ne da za su zauna"
filayen da ke da ciyawa domin garken su ci
abubuwan da su ke buƙata domin su yi wa iyalensu tanadi
Wannan sunan wani mutum ne.
Wannan sunan wani kabila ne.
Anan kalmar nan "zuciya" na nufin tunani. Jimlar nan karin magana ne da ke nufin rohoton da aka bayar cikin gaskiya. AT: "Na kawo masa rohoto mai gaskiya"
Ana maganar sa mutanen sun tsorata ne ƙwarai kamar ana sa zukatansu mutanen ne su narke. AT: "sun sa mutanen sun tsorata ƙwarai"
"Zan kasance da aminci ga Yahweh"
Wato ƙasar da Caleb da zuriyarsa za su samu.
Anan "ƙafafu" na nufin Kalibu. AT: "ƙasar nan wanda ka taka"
Wannan na nufin "ku saurara." Wannan kalmar na ƙara nanata abinda nassi ke faɗi.
"sa'anda mutanen Isra'ila ke tafiya a jeji"
"Ina nan da ƙarfi kamar yadda nake dă"
Wannan wani karin magana ne da ke nufin rayuwa na yau da kullum. AT: "domin abubuwa da nake yi kullim"
Wannan na iya nufin 1) manyar tuddai da dama ko kananan tuddai ko kuma 2) wani tudu.
Wannan sunan wani kabila ne.
Ana maganar Kalibu ne kamar wani gãdo ne da Kalibu ya samu a matasyin mallaka na har'abada.
Wannan na nufin lokacin da marubucin ya wallafa wannan littafin.
...
Wanna sunar wani wuri ne.
Duba yadda kuka juya wannan a 11:23. AT: "Sai mutanen suka daina yaƙe-yaƙe a ƙasar"
1Rabon ƙasar da aka yi wa kabilar mutanen Yahuda, an ba su ne bisa ga iyalansu, ya kai kudu iyaka da Idom, zuwa jejin Zin wanda ta ke can kudu nesa.2Iyakarsu wajen kudu ta mike tun daga ƙarshen Tekun Gishiri, daga sashen gaɓar da ta fuskanci kudu.3Iyakarsu ta tafi har kudancin tuddan Akrabbim ta kuma zarce zuwa Zin, ta kuma tafi har zuwa kudancin Kadesh Barneya, ta wajen Hezron, har kuma zuwa Addar, ta kuwa karkata zuwa Karka.4Ta wuce zuwa Azmon, ta bi ta rafin Masar, kuma ta zo ƙarshe a teku. Wannan ita ce iyakarsu a kudu.5Iyakarsu wajen gabas ta kama daga Tekun Gishiri, har zuwa bakin Yodan. Iyakar arewa kuma ta miƙe daga teku zuwa bakin Yodan.6Ta tafi zuwa Bet Hogla ta kuma wuce zuwa arewa da Bet Arabah. Sai ta haura zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.7Iyakar da ta tafi Debir zuwa Kwarin Achor, da kuma arewacin, sa'an nan ta juya zuwa Gilgal, wadda ta ke daura da tuddun Adummim, wanda ke kudu da gefen kwari. Sai ta zarce zuwa ruwan En Shemesh ta kuma tafi En Rogel.8Sai iyakar ta bi ta Kwarin Ben Hinnom a wajen kudancin birnin Yebusawa (wato Yerusalem). Sa'an nan ta bi ta sashen tuddun da ke shimfiɗe daura da kwarin Hinnom, wajen yamma, a arewacin ƙarshen Kwarin Refayim.9Sa'an nan iyakar ta faɗaɗa daga bisan tuddai zuwa maɓuɓɓugar ruwan Neftowa, har zuwa can biranen Tsaunin Efron. Sai iyakar ta karkata zuwa Ba'ala (wato Kiriyat Yeyarim).10Sa'an nan iyakar ta kewaye yammacin Ba'ala zuwa Tsaunin Seyir, daga nan kuma ta zarce gefen Tsaunin Yeyarim a arewa (wato Kesalon), sai ta gangara zuwa Bet Shemesh, ta kuma ƙetare har can zuwa Timna.11Iyakar kuwa ta bi ta gefen arewacin tuddun Ekron, sa'an nan ta karkata kewayin Shikkeron ta kuma wuce zuwa Tsaunin Ba'ala, daga wurin ta tafi zuwa Yabneyel. Iyakar ta ƙare a teku.12Yammacin iyakar Babbar Tekun da kuma gaɓarta. Wannan iyakar na kewaye da kabilar Yahuda, bisa ga iyalin kowa.13Don kiyaye ummarnin Yahweh ga Yoshuwa, Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne rabonsa na ƙasar a tsakiyar kabilar Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron (Arba shi ne uban Anak).14Kaleb kuwa ya kori mazan 'ya'yansa uku daga wurin Anak: Sheshai, Ahiman da Talmai, zuriyar Anak.15Ya tafi daga wurin ta wurin rashin amincewar mazaunan Debir (Debir da dã ake Kiriyat Sefer).16Kaleb yace, "Duk mutumin da ya kai hari ga Kiriyat Sefer har kuma ya kama ta, zan ba shi 'yata Aksa a matsayin mata."17Da Otniyel ɗan Kenaz, ɗan'uwan Kaleb, ya ci ta, Kalibu kuwa ya ba shi Aksa 'yarsa matsayin matarsa.18Bayan wannan, Aksa ta zo ga Otniyel ta kuma iza shi ya roƙi babanta fili. Da ta sauka daga kan jakinta, Kaleb ya ce mata, "Me kike bukata?"19Aksa ta amsa, "Ka yi mani alheri na musamman, da yake ka ba ni ƙasa a Negeb: ka kuma ba ni maɓuɓɓugar ruwa."Kaleb kuwa ya ba ta maɓuɓɓugar tuddu da kuma maɓuɓɓugar kwari.20Wannan shi ne gãdon kabilar Yahuda, da aka ba iyalinsu21Biranen na kabilar Yahuda da ke can kudu sosai, suna wajen iyakar Idom, su ne Kabzeyel, Eder, Yagur,22Kina, Dimona, Adada,23Kedesh, Hazor, Yitnan,24Zif, Telem, Beyalot.25Hazor Hadatta, Kiriyot Hezron (wato an san shi da Hazor),26Amam, Shema, Molada,27Hazar Gadda, Heshmon, Bet Felet,28Hazar Shuwal, Biyasheba, Biziyotiya.29Ba'ala, Iyim, Ezem,30Eltolad, Kesil, Horma,31Ziklag, Madmanna, Sansanna,32Labayot, Shilhim, Ayin, Rimmon. Wadannan su ne birane ashirin da tara dukkansu, har da ƙauyukansu.33A kwarin ƙasar tuddu ta yamma, akwai su Eshtawol, Zora, Ashna,34Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,35Yamut, Adullam, Soko, Azeka36Shayarim, Aditayim, Gedera, (wato Gederotayim). Waɗannan su ne birane goma sha huɗu yawansu duk da ƙauyukansu.37Zenan, Hadasha, Migdalgad,38Diliyan, Mizfa, Yokteyel,39Lakish, Bozkat, Eglon.40Kabbon, Lahmas; Kitlish,41Gederot, Bet Dagon, Na'ama, Makkeda. Waɗannan su ne birane goma sha shida yawansu duk da ƙauyukansu.42Libna, Eter, Ashan,43Yifta, Ashna, Nezib,44Kaila, Akzib, Maresha. Waɗannan su ne birane tara, duk da ƙauyukansu.45Ekron, tare da kewayan garuruwa da ƙauyuka;46daga Ekron zuwa Babbar Teku, dukkan mazaune waɗanda su ke kusa da Ashdod, da dukkan ƙauyukanta.47Ashdod, da kewayan garuruwa da ƙauyukanta; Gaza, da kewayan garuruwa da ƙauyukanta; zuwa rafin Masar, da kuma zuwa Babbar Teku tare da gaɓarta.48A tuddun ƙasar, Shamir, Yattir, Soko,49Danna, Kiriyat Sanna (wato Debir),50Anab, Eshtimo, Anim,51Goshen, Holon, da Gilo. Waɗannan su ne birane goma sha daya, tare da ƙauyukansu.52Arab, Duma, Eshan,53Yanim, Bet Taffuwa, Afeka,54Humta, Kiriyat Arba (wato Hebron), da Ziyor. Waɗannan su ne birane tara, tare da ƙauyukansu.55Mawon, Karmel, Zif, Yutta,56Yezriyel, Yokdiyam, Zanowa,57Kayin, Gibiya, da kuma Timna, Waɗannan su ne birane goma, tare da ƙauyukansu.58Halhul, Bet Zur, Gedor,59Ma'arat, Bet Anot, da kuma Eltekon. Waɗannan su ne birane shida, tare da ƙauyukansu.60Kiriyat Ba'al (wato Kiriyat Yeyarim), da kuma Rabba. Waɗannan su ne birane biyu, tare da ƙauyukansu.61A cikin jeji kuwa, akwai su Bet Arabah, Middin, Sekaka,62Nibshan, da Birnin Gishiri, da En Gedi. Waɗannan su ne birane shida, tare da ƙauyukansu.63Amma domin Yebusiyawa, mazaunan Yerusalem, kabilar Yahuda ba su iya korar su ba, don haka Yebusiyawa su ka yi zamansu tare da kabilar Yahuda har zuwa wannan ranar.
Wannan ne sunan yankin Jejin.
"daga sashin takun da ke fuskantar kudu a karshen Tekun Gishiri." Jimla biyun na maganar wuri ɗaya ne. Jimla na biyun na kara bayani ne game da wurin da iyankan gefen kudun ta fara.
wani karamin shashin tekun da ya miƙe zuwa ƙasa
"da ta juya zuwa ta kudu"
"Iyakar ƙasar kabilar Yahuda"
Waɗannan sunayen wurare ne.
wata karamin rafi a kudancin gefen ƙasar, kusa da Masar
Ana maganar daidai wurin da kogin ke ba da ruwa zuwa tekun ne kamar shi ne bakin rafin.
...
Waɗannan sunayen wurare ne.
Wata ilawannan wani babbar dutse ne da wani ya sa a matasyin alamar ƙasar suka ba sa sunar wani mai suna Bohan.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wasu mutane ne, maza.
Waɗannan sunayen na nufin dangogin mutane ne, 'yan zuriyar sheshai, da Ahiman, da Talmai. Kalamun nan "'ya'ya" da "zuriya" a wannan halin na nufin abu ɗaya. AT: "dangogi uku, da Sheshai, Ahiman, da Talmai, zuriyar Anak ne"
"Ya tafi wurin domin ya yi yaƙi ta wurin rashin"
Wannan suna wani wuri ne.
Wannan sunan wata mace ce.
Waɗannan sunayen wasu mutane ne, maza.
Wannan karin maganar na nufin Aksa ta za matar Otiniyel. AT: "Da Aksa ta zama matar Otiniyel"
AT: "ta ce masa 'Ka ce wa babana ya ba ni fili"
Kalmar nan "tuddu" da "kwari" na iya nufin tsawon ƙasar maɓuɓɓugar.
Ana maganar ƙasar da kabilar Yahuza sun samu ne kamar gãdo ne da suka samu a matsayin mallakar su ne na har abada. AT: "Wannan shi ne ƙasar da kabilar Yahuza suka samu a matsayin gãdo"
AT: "da Yoshuwa ya ba wa iyalinsu"
Marubucin ya ba da jerin sunayen biranen kudanci da Yahuda suka mallaka. Jerin ya cigaba har 15:29.
Jerin sunayen biranen ya cigaba.
Jerin sunayen biranen ya cigaba.
Marubucin ya ba da jerin sunayen biranen da Yahuda sun mallaka.
Marubucin ya ba da jerin sunayen biranen da Yahuda sun mallaka.
Marubucin ya cigaba da ba da jerin sunayen biranen da Yahuza sun mallaka.
Marubucin ya cigaba da ba da jerin sunayen biranen da Yahuza sun mallaka.
Marubucin ya cigaba da ba da jerin sunayen biranen da Yahuza sun mallaka.
"kauyuka"
wani karamin rafin a karshen kuduncin ƙasr kusa da Masar
Marubucin ya cigaba da ba da jerin sunayen biranen da Yahuza sun mallaka.
Marubucin ya cigaba da ba da jerin sunayen biranen da Yahuza sun mallaka.
Marubucin ya cigaba da ba da jerin sunayen biranen da Yahuza sun mallaka.
Marubucin ya cigaba da ba da jerin sunayen biranen da Yahuza sun mallaka.
Marubucin ya cigaba da ba da jerin sunayen biranen da Yahuza sun mallaka.
Wannan na nufin lokacin da marubucin ya wallafa wannan littafin.
1Ƙasar da aka ba kabilar Yosef ta kama tun daga Yodan har zuwa Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, zuwa daji, ta haura daga Yeriko zuwa ƙasar tuddun Betel.2Sai ta tafi zuwa Betel ta Luz ta kuma zarce zuwa Atarot, karkarar Arkiyawa.3Sai ta gangara yammacin karkarar Yafletiyawa, har can ƙarƙashin karkarar Bet Horon, ta kuma tafi har Gezer; ta ƙare a teku.4Ta wannan hanyar ce kabilun Yosef, da Manasse da kuma Ifraim su ka sami na su gãdon.5Karkarar kabilar Ifraim wadda aka ba iyalinsu ta kama kamar haka: iyakar gãdonsu a wajen gabas ta tafi zuwa Atarot Addar har can kwarin Bet Horon,6daga can ta cigaba har teku. Daga Mikmetat a arewa ta juya zuwa gabashin Ta'anat Shilo, ta kuma wuce gaba wajen gabas da Yanowa.7Sai ta tafi can har Yanowa zuwa Atarot ta kuma tafi Na'ara, ta kuma kai Yeriko, ƙarshen Yodan.8Daga Taffuwa iyakarta ta tafi yammacin rafin Kana ta kuma ƙare a teku. Wannan shi ne gãdon kabilar Ifraim, wadda aka ba iyalinsu,9tare da biranen da aka zaɓa don kabilar Ifraim a cikin gãdon kabilar Manasse - dukkan biranen, tare da ƙauyukansu.10Su ba su ƙore Kan'aniyawa waɗanda su ke zama a Gezer ba, saboda haka Kan'aniyawan da ke zama cikin Ifraim su na nan har wannan rana, amma waɗannan mutanen an sa su yin aikin dole.
"Kabilar" na kumshi da da kabilar Yosef biyu, Manassa da Ifraimu. Tun da rashin kabilar manassa suna zama a gabashin Urdune, wannan jimlar na nufin kabilar Ifraimu da sauran raguwar Manassa. AT: "kabilar Ifraimu da sauran kabilar Manassa"
Waɗannan sunayen wurare ne.
Wannan sunar wata kabila ce.
Wannan sunar wata kabila ce.
Waɗannan sunayen wurare ne.
"kabilun Manassa da kanilar Ifraimu, 'ya'yan Yosef"
Ana maganar ƙasar da kabilan Manassa da Ifraimu suka samu ne kamar wani gãdo ne da suka samu a matasyin mallakar su na har abada. AT: "sami wannan ƙasar a matsayin gãdon su"
AT: "Karkakar ... da Yoshuwa ya ba iyalinsu"
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Ana maganar ƙasar da Ifraimu suka mallaka ne a matsayin mallakar da suka samu har abada. AT: "Wannan shi ne ƙasar da lkabilar Ifraimu suka samu a mastayin gãdon su"
AT: "Da Yoshuwa ya ba wa iyalinsu"
AT: "biranen da Yoshuwa ya zaɓa"
Ana maganar ƙasar da kabilar Manasssa suka mallaka ne kamar wani gãdo ne da suka sama a matsayin mallakar su na har abada. AT: "a cikin ƙasar da kabilar Manassa suka samu a matsayin gãdon"
Wannan na nufin lokacin da marubucin ya wallafa wanna littafi.
AT: "Isra'ilawan sun sa waɗannan mutanen su yi aiki a matsayin bayi"
1Wannan it ce ƙasar da aka ba kabilar Manasse (wanda ya ke shi ne ɗan farin Yosef) - wato, Makir wanda ya ke ɗan farin Manasse shi ma kuma uban Giliyad. Zuriyar Makir an ba su ƙasar Giliyad da Bashan, domin Makir mutum ne jarumi a gun yaƙi.2Ƙasar an ba da ita ga sauran kabilar Manassa, an ba da ita ga iyalinsu -- Abiyeza, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer, da Shemida. Waɗannan su ne zuriyar maza na Manasse ɗan Yosef, bisa ga iyalinsu.3Yanzu Zelofehad ɗan Hefer ɗan Giliyad ɗan Makir ɗan Manasse ba shi da 'ya'ya maza, amma sai 'ya'ya mata kaɗai. Sunayen 'ya'yansa mata su ne Mala, Noah, Hogla, Milka, da Tirza.4Sun zo wurin Eliyeza firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabanin, sun kuma ce, "Yahweh ya umarci Musa da ya ba mu gãdo tare da 'yanuwanmu maza." Saboda, bin umarnin Yahweh, ya ba waɗannan matan gãdo a cikin 'yan'uwansu maza na mahaifinsu.5Yanki goma na ƙasar da aka ba Manasse a Giliyad da Bashan, wanda ya na ɗaya gefen Yodan,6domin 'ya'ya mata na Manasse sun karɓi gãdonsu tare da 'ya'yansa maza. Ƙasar Giliyed an ba sauran kabilar Manasse.7Yankin ƙasar Manasse ya kai daga Ashar zuwa Mikmetat, wadda ta ke gabas da Shekem. Sai kuma iyakarta ta tafi kudu zuwa waɗanda su ke zama kusa da ruwan Taffuwa.8(Ƙasar Taffuwa ta ƙarƙashin Manasse, amma garin Taffuwa ya na kan iyakar Manassa ƙarƙashin kabilar Ifraim.)9Iyakar kuma ta gangara zuwa rafin Kana. Waɗannan biranen kudu da rafin da ke cikin garuruwan Manasse su na ƙarƙashin Ifraim. Iyakar Manasse kuwa tana arewacin rafin, ta kuma ƙarashe a teku.10Ƙasar da ke kudu ta na ƙarƙashin Ifraim, kuma ƙasar da ke arewa ta Manasse ce; kuma teku ce ƙarshen iyakarta. A arewacin gefenta kuwa Ashar za a tarar, a kuma gabashinta, Issaka.11A cikin Issaka kuma da Ashar, Manasse ya sa mi Bet Shan da ƙauyukanta, Ibleyam da ƙauyukanta, mazaunan Dor da ƙauyukanta, mazaunan Endor da ƙauyukanta, mazaunanTa'anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta, (da kuma sulusin birin Nafet).12Duk da haka kabilar Manasse ba su iya mallakar waɗannan biranen ba, domin Kan'aniyawa sun ci gaba da zama a wannan ƙasar.13Lokacin da mutanen Isra'ila su ka yi ƙarfi, sai su ka tilasta wa Kan'aniyawa su yi aikin dole, amma ba su kore su gaba ki ɗaya ba.14Sai zuriyar Yosef su ka ce da Yoshuwa, "Me ya sa ka ba mu ƙasa ɗaya kaɗai da kuma kashin gãdo ɗaya, da ya ke mu mutane masu yawa ne, duk da albarkar da Yahweh ya yi mana?"15Yoshuwa yace da su, "Idan ku babbar jama'a masu yawa ce, ku tafi can da kanku a jeji ku gyarawa kanku ƙasa acikin ƙasar Ferizziyawa da kuma Refayawa. Ku yi haka, a tuddan ƙasar Ifraim da ya ke ta yi ma ku kaɗan ainun.16Sai zuriyar Yosef su ka ce, "Ƙasar tuddai ba za ta ishe mu ba. Amma dukkan Kan'aniyawa da su ke zaune a kwarin su na da karusai na ƙarafa, dukkan waɗanda zaune a Bet Shan da ƙauyukanta, da kuma waɗanda ke zaune a kwarin Yezriyel."17Yoshuwa kuwa ya cewa gidan Yosef - wato Ifraim da Manasse, "Ku mutane ne masu girma da yawa, kuma ku na da iko da ƙarfi. Kada ku tsaya a kashin ƙasa ɗaya kaɗai da aka ba ku.18Ƙasar tuddai ma za ta zama taku. Ko da yake daji ne, ku gyara ta ku kuma mallake ta har iyakokinta masu nisa. Sai ku kore Kan'aniyawa daga cikinta, ko da ya ke su na da karusai na ƙarfe, kuma su na da ƙarfi ainun."
"ɗan fara; shi kuma"
Waɗannan sunayen mutane ne, maza.
AT: "Yoshuwa ya ba da ƙasar Giliyad da Bashan ga zuriyar Makir"
AT: "Yoshuwa ya ba da ƙasar ... ba da ita ga iyalinsu"
Waɗannan sunayen mutane ne, maza.
Waɗannan sunayen mutane ne, mata.
Ana maganar gonar ne kamar wani gãdo ne da mutane ke iya samunta a nmatasyin mallakar su na har abada. AT: "ya ba mu gãdon wat gonar"
Wannan na iya nufin 1) Yoshuwa ya ba waɗannan matan gãdo" ko kuma 2) Eliyaza ya ba wa waɗannan matan gãdo."
AT: "Yoshuwa ya ba da yanki goma na ƙasar"
"rabi goma"
Ana maganar ƙasar ne a matsayin gãdo ne da za su samu har abada. AT: "sun samu ƙasar a matsayin gãdonsu"
AT: "Yoshuwa ya ba da ƙasar Giliyad"
"ta gefen kudu"
Waɗannan sunayen wurare ne.
"Iyakar ƙasar Manassa"
wani karamin rafi
sunan wani rafi
Wannan na iya nufin 1) iyakar ƙasar Manassa a ƙasar da ke gefen arewa ta taɓa ƙasar da ke na kabilar Ashar ko kuma 2) da mutum zai iya tafiya ta arewa har yă kai Ashar. AT: "Ashar yana gefen arewa" ko kuma :Mutum na iya tafiya ta arewa har yă kai Ashar"
AT: "zuwa gabas, muutum na iya kai issaka"
Waɗannan sunayen wurare ne.
Wannan na nufin kabbilar Ifraimu da Manassa.
Mutanen kabilar Ifraimu da Manassa sun yi wannan tambayan ne domin su nanate cewa ya kamata Yoshuwa yă kara masu ƙasar. AT: "Ai da ka kara mana ƙasar ta zama fiya da ɗaya ... Yahweh ya albarkace mu."
Waɗannan jimla biyun a takaice na nufin abu ɗaya ne. A jimla na biyun, ana maganar ƙasar ne kamar wani gãdo ne da mutanen suka samu har abada. AT: "AT: "ƙasa ɗaya a matsayin gãdon mu"
sashi
"mutane da yawa"
"Da shike ku mutane ne masu yawa"
Wannan sunar wata kabila ce.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Anan kalmar nan "gida" na nufin zuriya. AT: "zuriyar Yosef"
"ku share gandun jejin da itatuwan" ko kuma "za ku yanke bishiyoyin"
1Sai dukkan taron jama'ar Isra'ila su ka taru a Shilo. A wurin su ka kafa rumfar taruwa sun ci nasara akan ƙasar dake gabansu.2Har yanzu akwai kabilu bakwai cikin mutanen Isra'ila waɗanda ba a ba su na su gãdon ba tukuna.3Yoshuwa ya ce da mutanen Isra'ila, "Har yaushe za ku ƙi tafiya cikin ƙasa wadda Yahweh, Allah na kakanninku ya ba ku?4Ku sanya wa kanku mutum uku daga kowacce kabila, kuma zan aike su waje. Za su fita su duba ƙasar tudu da gangare. Za su rubuta bayanin ta bisa ga gădon kowannensu, sa'an nan za su komo wuri na.5Za su raba ta kashi bakwai. Yahuda za su kasance cikin na su yanki wajen kudu, sai gidan Yosef kuma za su ci gaba da zama a yankin arewa.6Za ku kasa ƙasar kashi bakwai sa'annan ku kawo taswirar ƙasar wurina. Zan jefa ma ku ƙuri'u a nan gaban Yahweh Allahn mu.7Gama Lebiyawa ba su da gădo a cikin ku, gama aikin Lebiyanci na Yahweh shi ne rabon su. Gad, da Ruben da rabin ƙabilar Manasse sun karɓi gadon su a ƙetaren Yodan. Wannan shi ne gãdon da Musa bawan Yahweh ya ba su."8Sai mutanen su ka tashi su ka tafi. Yoshuwa ya umarci waɗan da su ka tafi domin su rubuta tsarin taswirar ƙasar, ya ce, "Ku tafi ku kai ku komo cikin ƙasar ku rubuta adadinta sa'annan ku komo wurina. Zan jefa ƙuri'u a nan domin ku a gaban Yahweh a Shilo."9Mutanen kuwa su ka tashi suka tafi cikin ƙasar tudu da gangare su ka rubuta bayanin yadda ƙasar take kashi bakwai bisa ga biranenta, sun tsara biranen da sashin sa. Daga nan suka dawo wurin Yoshuwa cikin sansani a Shilo.10Sai Yoshuwa ya jefa masu ƙuri'u a Shilo gaban Yahweh. A can ne Yoshuwa ya rabawa mutanen Isra'ila ƙasar, kowannesu aka bashi nasa rabon ƙasar.11Ƙasar da aka ba kabilar Benyamin kowanne an ba su bisa ga iyalinsu. Yankin ƙasarsu tana tsakanin zuriyar Yahuda da zuriyar Yosef.12Ta ɓangaren arewa, iyakarsu ta fara daga Yodan. Iyakar ta hau wajen sashin arewacin Yeriko, daga nan ta hau zuwa wajen tudun ƙasar yamma. Can ta kai jejin Bet Aben.13Daga can iyakar ta wuce zuwa kudu sashen Luz (wato Betel ke nan). Iyakar kuwa ta gangara zuwa Atarot Addar, tabi ta tsaunin da ke kwance a kudancin Bet Horon.14Sai iyakar tabi ta wani sashi dabam: ta ɓangaren yamma ya juya wajen kudu, ta nufi wajen hayin dutse daga Bet Horon. Wannan iyakar ta ƙarasa a Kiriyet Baal (wato Kiriyet Yeyarim), birni wanda mallakar kabilar Yahuda ne. Wannan ta haɗa iyakar yammaci.15Iyaka ta wajen kudu ta fara daga wajen Kiriyat Yeyarim. Iyakar ta tafi daga nan zuwa Efron, zuwa maɓulɓular ruwayen Neftowa.16Sai iyakar ta gangaro ƙasa zuwa iyakar dutsen dake akasi da Kwarin Ben Hinom, wanda ke arewacin ƙarshen Kwarin Refayim. Daga nan ya gangara zuwa Kwarin Hinnom, kudancin gangaren Yebusiyawa ya nausa ƙasa zuwa En Rogel.17Ta juya wajen arewa, ta nufi wajen En Shemesh, daga nan kuma ta fita zuwa Gelilot, wanda ke akasi da mahayin Adumim. Daga nan sai ya gangara zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.18Ya wuce zuwa arewa inda suke kafaɗa da Bet Arabah ta gangara zuwa Arabah.19Iyakar ta wuce arewa kafaɗa da Bet Hogla. Iyakar ta ƙarasa arewa wajen gaɓar Tekun Gishiri, ta ɓangaren kudu ta ƙare a Yodan. Iyaka ta kudu kenan.20Yodan kuwa ta kafa iyakarta ta ɓangaren gabas. Wannan shi ne gadon Kabilar Benyamin, an kuma ba kowannensu bi sa ga zuriyar su, iyaka bayan iyaka, a ko'ina.21Biranen kabilar Benyamin bisa ga iyalansu su ne; Yeriko, Bet Hogla, da Emek Keziz,22Bet Arabah, Zemarayim, Betel,23Abbim, Fara, Ofra,24Kefar Ammoni, Ofni da Geba. Birane goma sha biyu ne haɗe da ƙauyukansu.25Akwai kuma biranen Gibiyon, Ramah,26Birot, Mizfa, Kefira, Mozah,27Rekem, Irfil, Tarala,28Zela, Hayelef, Yebus, (wato Yerusalem ke nan) Gibiya da Kiriyat. Akwai birane goma sha hudu, duk da ƙauyukan su. Wannan shi ne gãdon Benyamin domin zuriyarsu.
Suka ci nasara kan mutanen da ke zama a ƙasar kamun sun kafa rumfar taruwar. AT: "bayan da sun ci nasara da ƙasar"
AT: waɗanda Yoshuwa bai riga ya basu ƙasar gãdonsu ba"
Yoshuwa ya yi wannan tambayan ne tomin yă ƙarfafa Isra'ilawa to mallaki ƙasar. AT: " Ka jima, ka ƙi ka ... ya ba su".
Kalmar nan "tudu da gangare" na nufin kowanne gefe. AT: "ƙasar a kowanne gefe" ko kuma "ƙasar dukka"
Wannan na nufin cewa za su yi bayanin sashin ƙasar da kowannensu na son ya gãda.
Yoshuwa ya cigaba da maganarsa ne ga 'ya'yansu Isra'ila.
"Za su raba ƙasar"
"Kabilar Yahuza za su kasance"
Anan Kalmar nana "gida" na nufin zuriya. Jimlar na nufin Ifraimu da Manassa. AT: "kabilun Ifraimu da Manassa"
Yoshuwa ya cigaba da maganarsa ne ga 'ya'yansu Isra'ila.
...
Yoshuwa na maganar babbar girman da Lewiyawa za su samu ne ta wurin bauta wa Yahweh a matsyin firist kamar wani abu ne da suka gãda. AT: "gama firsitancin Yahweh ne abinda suke da shi"
...
AT: "sun karɓi ƙasar su ta gãdo"
Yoshuwa yana maganar da mutane ashirin da ɗaya da za su je su dubi ƙasar.
Wannan na nufin su shiga cikin ƙasar dukka. Duba yadda kuka juya ta a 18:3. AT: "a kowane gefen ƙasar" ko kuma "dukka ƙasar"
AT: "Yoshuwa ya ba kowane kabila shashin ƙasar"
AT: "Kowanne iyalin Benyamin sun sami ƙasar da aka bayar"
"tsakanin ƙasar zuriyar Yahuda da ƙasar Yosef"
Wannan na nufin kabilun Ifraimu da Manasse.
Wannan sunan wani wuri ne.
...
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Wata ila wannan wani babbar dutse ne da wani ya sa alamar ƙasa, sa'annan aka ba ta sunar mutumin, Bohn, Duba yadda kuka juya shi a 15:5)
Wannan na nufin ƙasar da ke a gangare ko da kunya-kunya. AT: "gangarar Bet-Araba"
Wannan na nufin ƙasar da ke a gangare ko da kunya-kunya.
Wannan sunan wani wuri ne.
AT: "Wannan shi ne ƙasar da kabilar Benyamin suka gãda"
AT: "Yoshuwa ya ba wa kowanne iyalinsu"
Marubucin ya ba da jerin biranen da ke cikin ƙasar da kabilar Benyamin sun gãda.
"ƙauyukan da ke keway da su"
Marubucin ya ba da jerin biranen da ke cikin ƙasar da kabilar Benyamin sun gãda.
AT: "Wannan shi ne ƙasa da birane da kabilar Benyamin sun gãda"
1Kaɗa ƙuri'u na biyu ta faɗa kan Simiyon aka ba su bisa ga zuriyarsu. Gãdonsu ya na tsakiyar gãdon kabilar Yahuda.2Su ka samu domin gãdonsu Biyasheba, Sheba, Modala,3Hazar Shuwal, Balal, Ezem,4Eltolad, Betul, da Hormah.5Simiyon kuma ya na da Ziklag, Bet Markabot, Hazar Susa,6Bet Lebayot, da Sharuhen, Waɗannan birane goma sha uku sun haɗa da ƙauyukansu.7Har yanzu Simiyon ya na da Ayin, Rimmon, Etar da Ashan. Birane huɗu kenan duk da ƙauyukansu.8Waɗannan tare da ƙauyaukan dake tare da biranen har zuwa Ba'alat Biya (ɗaya suke da Ramah cikin Negeb). Wannan shi ne gãdon ƙabilar Simiyon, wanda aka ba iyalinsu.9Daga cikin gãdon ƙabilar Simiyon aka sami wani sashin rabon kabilar Yahuda. Saboda rabon ƙasar da aka ba Yahuda ya yi masu yawa, ƙabilar Simiyon sun karɓi gădonsu daga cikin tsakiyar nasu rabo.10Kaɗa ƙuri'u na uku ya faɗa akan kabilar Zebulun, aka kuma ba da ita ga zuriyarsu. Iyakar gãdonsu ta fara daga Sarid.11Iyakar su ta hau wajen yammaci ta nufi Marala, ta kai Dabbeshet; ta malala zuwa rafin dake akasi da Yokneyam.12Daga Sarid iyakar ta karkato zuwa gabashi ta tafi zuwa iyakar Kislot Tabor. Daga nan ta fita zuwa Daberat ta hau zuwa Yafiya.13Daga can ta ratsa zuwa gabas har Gat Hefa, zuwa Et Kazin; ta sake fita zuwa Rimmon ta juya zuwa wajen Neya.14Iyakar ta karkato zuwa wajen arewa zuwa Hannaton ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.15Wannan yankin ya hada da biranen Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem. Akwai birane goma sha biyu duk da ƙauyukansu.16Wannan shi ne gãdon ƙabilar Zebulun, wanda aka ba zuriyarsu - da birane duk da ƙauyukansu.17Kaɗa kuri'u na hudu ya faɗa kan Issaka, an ba su bisa ga zuriyarsu.18Iyakarsu ta haɗa da Yezriyel, Kesulot, Shunem,19Hafarayim, Shiyon da Anaharat.20Ya haɗa da Rabbit, Kishon, Ebez,21Remet, En Gannim, En Hadda da Bet Fazzez.22Iyakarsu takai Tabor, Shahazuma, da Bet Shemesh, ta ƙarasa a Yodan. Birane goma sha shida, duk da ƙauyukansu.23Wannan shi ne gãdon kabilar Issaka, wanda aka ba su bisa ga zuriyarsu - birane da ƙauyukansu.24Kaɗa Kuri'u na biyar ya faɗa kan kabilar Asha, aka kuma ba zuriyarsu.25Iyakarsu ta hada da Helkat, Hali, Beten, Akshaf,26Allammelek, Amad da Mishall. Daga yamma iyakar ta kai zuwa Karmel da Shiho Libnat.27Daga nan ta karkata zuwa gabas zuwa Bet Dagon sa'an nan ta tafi har Zebulun, zuwa Kwarin Ifta El, arewaci zuwa Bet Emek da Neyiyel. Taci gaba zuwa Kabul wajen arewa.28Daga nan tayi wajen Abdon, Rehob, Hammon da Kana har zuwa Babban Sidon.29Iyakar tayi kwana zuwa Ramah, zuwa birnin Taya mai ganuwa. Sai iyakar ta karkata zuwa Hosa ta ƙarasa a teku a yankin Akzib,30Umma, Afek, da Rehob. Akwai birane ashirin da biyu duk da ƙauyukansu.31Wannan shi ne gãdon kabilar Asha, an basu bisa ga zuriyarsu - birane da ƙauyukansu.32Kaɗa Kuri'u na shida ya faɗa kan Naftali, aka kuma ba zuriyarsu.33Iyakar ta fara daga oak a Za'ananim, zuwa Adami Nekeb da Yabneyel, zuwa Lakkum; ta ƙarasa a Yodan.34Iyakar ta karkata zuwa yammaci har Aznot Tabor ta nausa zuwa Hukkok; ta taɓa Zebulun daga kudanci ta kai Asha daga yamma da Yahuda daga gabas har Kogin Yodan.35Birane masu ganuwa sune Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,36Adama, Ramah, Hazor,37Kedesh, Edirai da En Hazor.38Har yanzu akwai Yiron, Migdal El, Horem, Bet Anat da Bet Shemesh. Akwai birane goma sha tara, duk da ƙauyukansu.39Wannan shi ne gãdon kabilar Naftali wanda aka ba zuriyarsu biranensu duk da ƙauyukansu.40Kãɗa kuri'u na bakwai suka faɗa kan kabilar Dan an basu bisa ga zuriyarsu.41Iyakar rabon su ya haɗa da Zora, Estawol, Ir Shemesh,42Sha'alabbin, Aijalon da Itla.43Ta haɗa da Elon, Timna, Ekron,44Elteke, Gibbeton, Ba'alat,45Yehud, Bene Berak, Gat Rimmon.46Me Yarkon da Rakkon tare da iyaka a ƙetare daga Yoppa.47Lokacin da iyakar kabilar Dan ta ɓace masu, sai su ka kaiwa Leshem hari su ka yi yaƙi da su, suka ci su, su ka kashe kowanensu da kaifin takobi, suka kwashe mallakar su, suka zauna cikin ta. Suka sake ma Leshem suna zuwa Dan sunan kakansu.48Wannan shi ne gãdon kabilar Dan, an ba zuriyarsu - biranensu, da ƙauyukansu.49Bayan da suka gama rarraba ƙasar a matsayin gãdonsu, mutanen Isra'ila suka ɗauka daga cikin gãdonsu suka ba Yoshuwa ɗan Nun.50Bisa ga umarnin Yahweh suka bashi birnin daya roƙa, an bashi Timnat Sera cikin ƙasar duwatsu ta Ifraim. Ya gina birni ya zauna ciki.51Waɗannan sune gãdon da Eliyeza firist, Yoshuwa ɗan Nun, da shugabannin kabilu na mutanen Isra'ila suka raba bisa ga ƙuri'a a Shiloh, a gaban Yahweh a ƙofar shiga rumfar taruwa. Da haka suka gama rarraba ƙasar.
"Da aka kaɗa kuri'a na biyu, sai kuri'an ta nuna kabilar Simiyon"
lamba ta biyu a jeri ko lisafi
AT: "Yoshuwa ya ba da ƙasar ga kowane zuriyansu"
AT: "Ƙasar da suka gãdoa yana tsakiyar ƙasar da kabilar Yahuda suka gãda"
Marubucin ya ba da jerin sunayen biranen da ke ƙasar da Simiyon suka gãda.
AT: "Sun gãda birane kamar haka"
Marubucin ya cigaba da ba da jerin sunayen biranen da ke ƙasar da kabilar Simiyon ta gãda.
Ku juya wannan kamar yadda kuka yi a 15:29.
AT: "Wannan shine ƙasa da biranen da kabilar Simiyon ta gãda"
AT: "da Yoshuwa ya ba wa zuriyarsu"
AT: "rabon ƙasar da Yoshuwa ya ba wa kabilar Yahuda"
"tsakiyar rabon ƙasar Yahuda"
Juya wannan jimlar yadda kuka yi a 19:1.
jerin lamba ta ukku
Waɗannan sunayen wurare ne.
"da ke ƙeteren"
Waɗannan sunayen biranenne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Wannan ba "Baitalahmi" ɗaya ne da wanda ke kudancin Urushalima a Yahuda ba.
AT: "Wannan shi ne ƙasa da biranen da kabilar Zebulun sun gãda"
AT: "da Yoshuwa ya ba iyalinsu"
Juya wannan jimlar yadda kuka yi a 19:1.
jerin lamba ta ukku
Waɗannan sunayen birane ne.
Waɗannan sunayen biranene ne.
AT: "Wannan shi ne ƙasa da birane da kabilar Issaka suka gãda"
AT: Yoshuwa ya ba zuriyarsu"
Juya wannan jimlar yadda kuka yi a 19:1.
jerin lamba ta biyar
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
AT: "Wannan shine ƙasa da birane da kabilar Asha sun gãda
AT: "Yoshuwa ya ba wa zuriyarsu"
Ku juya wannan jimlar yadda kuka yi a 19:1.
jerin lamba ta shida
AT: "Yoshuwa ya ba zuriyarsu"
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen birane ne.
Wannan ba a wura ɗaya yake da "Hammat" ba, amma yana yammacin tudun Tekun Galili ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
AT: "Wannan shine ƙasa da birane da kabilar Naftali suka gãda"
AT: "Yoshuwa ya ba wa zuriyarsu"
Ku juya wannan jimlar yadda kuka yi a 19:1.
jerin lamba ta bakwai
AT: "Iyakar ƙasar da kabilar Dan suka gãda"
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen birane ne.
"yana akasi da Yoppa" ko kuma "a gefen Yoppa"
Wannan sunan wani birni ne.
AT: "Wannan shine ƙasa da birane da kabilar Dan suka gãda"
AT: "Yoshuwa ya ba zuriyarsu"
AT: "ba wa Yoshuwa da Nun wani birni daga cikin ƙasarsu su gãda"
Wannan sunan wani birni ne.
AT: "Waɗannan ne sunayen ƙasa da birane ... aka ba da su gãdo"
1Sai Yahweh yace da Yoshuwa.2"Kayi magana da mutanen Isra'ila, kace, 'Ka keɓe biranen mafaka wanda nayi magana da kai ta hannun Musa.3Kayi haka domin duk wanda ya kashe wani bada gangan ba zai iya zuwa can. Waɗannan birane za su zama wurin mafaka domin duk wanda ya nemi ɗaukar fansar jinin mutumin da aka kashe.4Zai ruga zuwa ɗaya daga cikin waɗannan biranen zai tsaya a ƙofar shiga birnin, zai bayyyana damuwarsa ga dattawan garin. Daga nan za su ɗauke shi zuwa cikin birni su bashi wuri domin ya zauna a cikinsu.5Idan wani daga cikin su ya zo domin ya yi ƙoƙarin ɗaukar fansar jinin wanda aka kashe, mutanen garin ba za su bada wanda ya yi kisan ga hukuma ba. Ba za su yi haka ba domin ba da gan - gan ne ya kashe maƙwabcinsa ba, kuma bashi da wata ƙiyayya game dashi a baya.6Dole ya zauna cikin birnin har lokacin da zai tsaya gaban jama'a domin hukunci, har lokacin mutuwar babban Firist mai aiki a kwanakin nan, daga nan sai shi wanda ya yi kisan bisa ga kuskure ya koma garinsu gidansa kuma, daga in da ya gudu."'7Sai Isra'ilawa suka zaɓi Kedesh cikin Galili, cikin ƙasar duwatsu ta Naftali, Shekem cikin ƙasar duwatsu ta Ifraim da Kiriyet Arba (wato Hebron ke nan) cikin ƙasar duwatsu ta Yahuda.8Ƙetaren Yodan gabashin Yeriko, suka zaɓi Beza, cikin jeji bisa tudu daga kabilar Ruben; Ramot Giliyad, daga kabilar Gad; da Golan cikin Bashan, daga kabilar Manasse.9Waɗannan sune biranen da aka zaɓa domin dukkan mutanen Isra'ila da kuma baƙin dake zaune cikinsu, domin duk wanda ya kashe wani bada gan - gan ba zai iya rugawa don tsirar da ransa. Wannan mutum ba zai mutu ta hanun wanda yake son ɗaukar fansar jinin da aka zubar ba, har sai shi wanda ake zargin ya tsaya gaban taron jama'a.
Anan "hannun Musa" na nufin litattafen da Musa ya rubuta. AT: "ta wurin abubuwa da Musa ya rubuta"
Wannan na faruwa ne idan sausayi ya sami mutum har ya kashe wani ba tare da niyyar yin haka ba.
Anan, jinin mutum na nufin mutuwarsa. AT: "ɗaukar fansar mutuwar mutum"
Wato mutumin da ya kashe wani ba da niyyar yin haka ba.
"tabbatar wa dattawan garin da cewa bai kashe mutumin da gangan ba"
Kalmar nan "su" na nufin dattawan, sa'annan "shi" na nufin mutum da ya kashe wani ba da gangan ba.
Wannan na nufin garin gabaɗaya, ba dattawan kadai ba.
Duba yadda kuka juya wannan a 20:1. AT: "ɗaukar fansar mutuwar mutumin"
Waaɗannan jimlar na nufin abu ɗaya ne.
Wannan jimlar na ba da bayani ne na tsayawas domin neman adalci a a gaban 'yan uwansa mazaunan gari.
Akwai sunaye da yawa a wannan sashin.
Wannan wata gajeruwar suna ce na Kogin Urdu.
Anan "ta hannun" na nufin zai zama mutumin da ya kashe ɗan gudun hijiran.
Duba yadda kuka juya wannan a 20:1. AT: "ɗaukar fansar mutuwar mutumin"
1Daga nan sai shugabanni na zuriyar Lebiyawa suka zo wurin Eliyeza firist, da Yoshuwa ɗan Nun da shugabanni na iyalan kakanninsu a tsakanin mutanen Isra'ila.2Sai suka yi magana da su a Shilo cikin ƙasar Kan'ana suka ce, "Yahweh ya umarta ta hannun Musa a ba mu birane mu zauna ciki, tare da makiyayarsu domin dabbobinmu."3Bisa ga umarnin Yahweh, mutanen Isra'ila suka ɗiba daga cikin gãdonsu na birane da makiyayarsu suka ba Lebiyawa.4Kaɗa kuri'u domin zuriyar Kohatawa ya bada wannan sakamako: Firistoci - zuriyar Haruna waɗanda su ke daga Lebiyawa - sun karɓi birane goma sha uku daga kabilar Yahuda, daga kabilar Simiyon da kuma daga kabilar Benyamin.5Sauran zuriyar Kohatawa bisa ga kuri'u sun karɓi birane goma daga zuriyar kabilar Ifraim, Dan da rabin kabilar Manasse.6Mutanen zuriyar Gashon an basu, ta wurin kaɗa kuri'u birane goma sha uku daga zuriyar Issaka, Asha, Naftali da rabin kabilar Manasse cikin Bashan.7Mutanen da su ke daga zuriyar Merari sun karɓi birane goma sha biyu daga kabilar Ruben, Gad da Zebulun.8Don haka mutanen Isra'ila sun bada waɗannan birane, ga Lebiyawa ta wurin jefa kuri'u (duk da makiyayarsu) kamar yadda Yahweh ya umarta ta hannun Musa.9Daga kabilun Yahuda da Simiyon aka bada waɗannan birane da aka lisafta sunayensu a nan.10Waɗannan birane an bayar da su ga zuriyar Haruna, waɗanda su ke daga zuriyar Kohatawa waɗanda daga kabilar Lebi su ke. Waɗanda kaɗa ƙuri'un farko kansu ya faɗa.11Isra'ilawa sun basu Kiriyat Arba (Arba shi ne uban Anak), wato Hebron ke nan, cikin ƙasar duwatsu ta Yahuda, tare da makiyayar da ke kewaye da ita.12Amma gonakin da ke birane da ƙauyukansu an riga an ba Kaleb ɗan Yefunne, a matsayin mallakarsa.13Ga zuriyar Haruna firist sun bashi Hebron da makiyayarta, wanda shi ne birnin mafaka ga wanda ya kashe wani cikin kuskure da Libna duk da makiyayarta.14Yattir da makiyayarta da Eshtemowa da makiyayarta.15Suka kuma ba da Holon da makiyayarta, Debir da makiyayaarta,16Ayin da makiyayarta, Jutta da makiyayarta da Bet Shemesh da makiyayarta. Akwai birane tara da aka bayar daga cikin kabilun nan biyu.17Daga kabilar Benyamin an bada Gibiyon duk da makiyayarta, Geba da makiyayarta,18Anatot duk da makiyayarta, da Almon da kewayenta birane huɗu ke nan.19Biranen da aka ba firistoci zuriyar Haruna, dukkan su birane goma sha uku ne, haɗe da makiyayarsu.20Sauran Kohatawa - su Lebiyawan nan waɗanda su ke daga iyalin Kohat - sun sami nasu biranen daga kabilar Ifraim, ta wurin jefa kuri'u.21An basu Shekem duk da makiyayarsu cikin ƙasar duwatsu ta Ifraim - birnin mafaka domin wanda ya yi kisan kai cikin kuskure - Geza da makiyayarsu.22Kibzayim da makiyayarsu, da Bet Horon da makiyayarsu - birane huɗu ne dukka.23Daga kabilar Dan, zuriyar Kohat an ba su Eltike da makiyayarsu, Gibbeton da makiyayarsu.24Aijalon da makiyayarsu da Gat Rimmon da makiyayarsu - duka birane huɗu ne.25Daga rabin kabilar Manasse, zuriyar Kohat an basu Ta'anak tare da makiyayarsu da Gar Rimmon tare da makiyayarsu - birane biyu.26Akwai birane goma dukka domin sauran zuriyar Kohatawa, duk da makiyayarsu.27Daga rabin kabilar Manasse, zuwa zuriyar Gashon waɗannan sauran zuriyar Lebi ne, an bada Golan cikin Bashan tare da makiyayarsu - birnin mafaka domin wanda ya yi kisan kai bisa ga kuskure, tare da Be Eshtera da makiyayarsu - birane biyu ne duka.28Ga zuriyar Gashon an basu Kishon daga kabilar Issaka, tare da makiyayarsu, Daberat tare da makiyayarsu,29Yarmut tare da makiyayarsu, da En Gannim tare da makiyayarsu.- birane hudu.30Daga kabilar Asha, sun bada Mishal tare da makiyayarsu, Abdon tare da makiyayarsu,31Helkat tare da makiyayarsu da Rehob tare da makiyayarsu - birane huɗu ne dukka.32Daga kabilar Naftali, sun ba zuriyar Gashon Kedesh cikin Galili tare da makiyayarsu - birnin mafaka domin wanda ya yi kisan kai cikin kuskure; Hammot Dor tare da makiyayarsu, da Kartan tare da makiyayarsu - birane uku ne duka.33Akwai birane goma sha uku duka, daga zuriyar Gashon, tare da makiyayarsu.34Ga sauran Lebiyawa - na zuriyar Merari - an ba su daga cikin kabilar Zebulun: Yokniyam tare da makiyayarsu, Karta tare da makyyayarsu,35Dimna tare da makiyayarsu, da Nahalal tare da makiyayarsu - dukka birane huɗu ke nan.36Ga zuriyar Merari an ba su daga kabilar Ruben: Bezer tare da makiyayarsu, Yahaz tare da makiyayayarsu,37Kedemot tare da makiyayarsu, da Mefa'at tare da makiyayarsu - birane huɗu.38Daga cikin kabilar Gad an ba su Ramot cikin Giliyad tare da makiyayarsu - birnin mafaka domin wanda ya yi kisan kai cikin kuskure - da Mahanayim tare da makiyayarsu.39Zuriyar Merari an ba su Heshbon tare da makiyayarsu, da Yazer tare da makiyayarsu. Waɗannan birane huɗu ne dukka.40Dukkan waɗannan birane ne na zuriyar Merari, waɗanda su ke daga kabilar Lebi - dukka birane goma sha biyun an ba su ne bisa ga kaɗa ƙuri'u.41Biranen Lebiyawa da aka ɗauka daga cikin tsakiyar mallakar Isra'ila sun kai birane arba'in da takwas, ya haɗa da wuraren kiwonsu.42Waɗannan birane kowanne ya haɗa da makiyayarsu da ke kewaye da su. Haka ya ke ga dukkan waɗannan birane.43Haka nan Yahweh ya ba da wannan dukkan ƙasa da ya rantse wa kakanninsu, Isra'ilawa su ka mallaketa, su ka zauna cikinta.44Yahweh ya ba su hutawa ta kowanne gefe, kamar yadda ya rantse wa kakanninsu. Babu wani daga cikin maƙiyansu da zai yi nasara da su. Yahweh ya ba da dukkan abokan gabarsu cikin hannunsu.45Babu wani cikin dukkan alƙawura masu kyau da Yahweh ya furta a kan gidan Isra'ila da ya kasa cika. Dukkan su sun tabbata.
Waɗannan sunayen mutane ne.
"Sai Lewiyawan suka ce masu"
Jimlar nan "ta hannun Musa" na nufin Yahweh ya yi amfani da Musa ne ya idar da umarninsa. AT: "Yahweh ya gaya wa Musa yă umurce ku"
Wannan na nufin biranen da aka jera a ayoyin da ke gaba.
Wannan wata hanya ce na zaɓin shugaba, ana yin haka ne da tunanin cewa Allah zai nuna ta wurin sakamakon kuri'ar. Duba yadda kuka juya shi a 19:1.
Waɗannan firistocin zuriyar Lewi ne 'ya'yan Kohat. Waɗansunsu ma zuriyar Haruna ne, jikan Kohat.
yawan birane
Rabin kabilar domin sauransu sun sami gãdonsu kamun sun ƙetere Kogin Urdun.
Goshon na ɗaya daga cikin 'yan'yan Lewi.
Wannan wata hanya ce na zaɓin shugaba, ana yin haka ne da tunanin cewa Allah zai nuna ta wurin sakamakon kuri'ar. Duba yadda kuka juya shi a 19:1.
Merari yama ɗaya daga cikin 'ya'yan Lewi.
Wannan jimlar "ta hannun Musa" anan na nufin Yahweh ya yi amfani da Musa ya iddar da umurninsa. AT: "Yahweh ya ce wa Musa yă umurce"
Waɗannan firistocin zuriyar Lewi ne 'ya'yan Kohat. Waɗansunsu ma zuriyar Haruna ne, jikan Kohat. Duba yadda kuka juya shi a 21:4.
Wannan wata hanya ce na zaɓin shugaba, ana yin haka ne da tunanin cewa Allah zai nuna ta wurin sakamakon kuri'ar. Duba yadda kuka juya shi a 19:1.
Wannan takaitaccen bayani ne game da mutumin da ya kafa birnin Kiriyet Arba.
Wannan sunan wani mutum ne.
...
Sashi da ke cike da ciyawa ko shuke-shuke da ke da kyau na kiwon dabbobi.
Gonar da ke a fili, da aka yi shuƙi wa mazaunan biranen.
Kananan al'ummomi, sun dan kãsa da birni kadan.
Waɗannan sukka sunayen birane ne.
Yawan biranen da kabilun da ke ayan.
AT: "Kabilar Benyamin sun ba wa Gebiyon"
Waɗannan sunayen birane ne.
"birane 13"
Waɗannan firistocin zuriyar Lewi ne 'ya'yan Kohat. Waɗansunsu ma zuriyar Haruna ne, jikan Kohat.
...
Wannan wata hanya ce na zaɓin shugaba, ana yin haka ne da tunanin cewa Allah zai nuna ta wurin sakamakon kuri'ar. Duba yadda kuka juya shi a 19:1.
sunayen birane
AT: "Kabilar Dan sun ba wa zuriyar Elkete"
Waɗannan firistocin zuriyar Lewi ne 'ya'yan Kohat. Waɗansunsu ma zuriyar Haruna ne, jikan Kohat. 21:20.
Waɗannan sunayen birane ne.
Wanan na nufin yawan birane.
AT: "Rabin kabilar Manasse sun ba wa zuriyar Kohat Taanak"
Waɗannan sunayen birane ne.
yawan biranen da aka lisafta
Waɗannan firistocin zuriyar Lewi ne 'ya'yan Kohat. Waɗansunsu ma zuriyar Haruna ne, jikan Kohat. Duba yadda kuka juya wannan a 21:4.
AT: "Rabin kabilar Manasse, sauran zuriyar Lewi, sun karɓa daga rabin kabilar Manasse Golan"
sunayen birane
...
yawan birane
AT: "Zuriyar Gashon sun sami Kishon"
sunayen birane
AT: "Sun samo daga kabilar Asha Misha"
Wanna na nufin yawan biranen da aka lisafta.
AT: "Zuriyar Gashon sun samo daga kabilar Naptali Kedesh"
Wannan sunan wani mutum ne.
Waɗannan sunayen birane ne.
"birane 13 ne dukka"
AT: "Sauran Lewiyawa - zuriyar Merari - sun samo daga kabilar zebulun Yokneyam"
sunan wani mutum ne.
sunayen birane ne
...
AT: "Zuriyar Merari sun samo daga kabilar Ruben Bezer"
Wannan na nufin kimamun yawan biranen
sunayen birane
AT: "Sun samo daga kabilar Gad Ramot"
Wannan sunan wani birni ne.
AT: "Zuriyar Merari su ma sun samo Heshbon"
Waɗannan sunayen birane.
"dukka birane 12 ne" (Duba:
AT: "sun samo waɗannan birane goma sha biyu ne ta wurin kaɗa kuri'a"
Wannan wata hanya ce na zaɓin shugaba, ana yin haka ne da tunanin cewa Allah zai nuna ta wurin sakamakon kuri'ar. Duba yadda kuka juya shi a 19:1.
AT: "Lewiyar sun samo biranen su ne daga tsakiyar ƙasar"
birane takwas - "birane 48"
"ya yi alƙawari"
AT: "Sun yi nasara da dukkan maƙiyansu"
Anan "a cikin hannunsu" na nufin "a cikin ikonsu." AT: "ya ba su iƙo su yi nasara"
AT: "Kowanne alƙawarin da Yahweh ha yi wa Isra'ila ta cika"
1A wan can lokaci Yoshuwa ya kira Rubenawa da Gadawa da rabin kabilar Manasse.2ya ce masu, "Kun yi dukkan abin da Musa bawan Yahweh ya umarce ku. Kunyi biyayya da muryata a kan dukkan abinda na umarce ku.3Baku yãshe da 'yan uwanku a yawan kwanakin nan ba, har ya zuwa wannan rana, kun kuma kiyaye umarnan Yahweh Allahn ku.4Yanzu Yahweh Allahnku ya ba da hutu ga "yan'uwanku, kamar yadda ya alƙawarta masu. Don haka ku juya ku tafi rumfunanku cikin ƙasar mallakarku, wadda Musa bawan Yahweh ya baku a ƙetaren Yodan.5Don haka sai ku kula sosai ku kiyaye dokoki da umarnai waɗanda Musa bawan Yahweh ya umarce ku, ku ƙaunaci Yahweh Allahnku. Kuyi tafiya cikin hanyoyinsa, ku kiyaye dokokinsa, ku manne masa kuyi masa sujada da dukkan zuciyarku da ranku."6Sai Yoshuwa ya albarkace su ya sallame su sai su ka koma rumfunansu.7Yanzu ga rabin kabilar Manasse Musa ya rigaya ya ba su gãdonsu cikin Bashan, amma ga ɗaya rabin Yoshuwa ya bada gãdo daga cikin na 'yan'uwansu a yammacin Yodan. Yoshuwa ya sallamesu zuwa rumfunansu; ya sa masu albarka, ya ce da su,8"Ku koma rumfunanku da kuɗi masu yawa, da dabbobi masu yawa, da azurfa da zinariya, da tagulla da ƙarfe, da tufafi masu yawan gaske. Ku raba ganimar abokan gabanku tare da 'yan'uwanku."9Sai zuriyar Ruben da zuriyar Gad, da rabin kabilar Manasse su ka koma gida, suka bar mutanen Isra'ila a Shilo, wadda ke cikin ƙasar Kan'ana. Sun tafi zuwa yankin ƙasar Giliyad, zuwa ƙasar su, wadda su da kansu su ka mallaka, cikin biyayya ga umarnin Yahweh, ta hannun Musa.10Sa'ad da suka zo Yodan wadda ke cikin ƙasar Kan'ana, sai Rubenawa da Gadawa da rabin kabilar Manasse su ka gina bagadi kusa da Yodan, babban bagadi shahararre kuma.11Da mutanen Isra'ila suka ji labarin nan cewa, "Duba! mutanen Ruben da Gad da rabin kabilar Manasse sun gina bagadi a gaban ƙasar Kan'ana a Gelilot, a yankin da ke kusa da Yodan, a yankin da ke mallakar mutanen Isra'ila."12Da mutanen suka ji haka, sai dukkan mutanen Isra'ila suka taru a Shilo domin su je su yi yaƙi gãba da su.13Sai mutanen Isra'ila suka aiki 'yan saƙo ga su Rubenawa da Gadawa da rabin kabilar Manasse, cikin ƙasar Giliyad. Sun kuma aiki Finehas ɗan Eliyeza, Firist.14Tare da shi kuma akwai shugabanni goma, ɗaya daga cikin kowacce kabilar Isra'ila, kuma kowannensu shugabane daga cikin zuriyar mutanen Isra'ila.15Suka zo wurin mutanen Ruben da Gad da rabin kabilar Manasse, cikin ƙasar Giliyad, suka yi magana da su:16"Dukkan taron jama'ar Yahweh sun faɗi haka, "Wanne irin rashin aminci ne wannan ku ka aikata gãba da Allah na Isra'ila, a wannan rana kun juya daga bin Yahweh kun ginawa kanku bagadi don ku tayarwa Yahweh?17Zunubinmu a Feyor bai ishe mu ba? Har yanzu bamu tsarkake kanmu daga gare shi ba. Saboda wannan zunubi annobai su ka abko wa jama'ar Yahweh.18Ko ya zama dole ne ku juya ga bin Yahweh a wannnan rana? Idan kuma ku ka yi wa Yahweh tayarwa yau, gobe zai yi fushi da dukkan taron jama'ar Isra'ila.19Idan ƙasar da ku ka mallaka ta ƙazantu, sai ku ƙetaro ƙasa inda mazaunin Yahweh ya ke zaune domin ku samar wa kanku mallaka daga cikin mu. Ku dai kada ku tayarwa Yahweh, ko ku tayar mana ta wurin gina wa kanku bagadi banda bagadin Yahweh Allahnmu.20Ko Akan ɗan Zera, bai yi laifin karya imani akan zancen waɗannan abubuwa da su ke keɓaɓɓu domin Allah ba? ko hasala ba ta afko wa mutanen Isra'ila ba? Wannan mutum bai mutu shi kaɗai domin laifinsa ba."21Daga nan sai kabilar Ruben Gad da rabin kabilar Mannasse suka amsa wa shugabannin zuriyar Isra'ila:22"Maigirman nan, Allah, Yahweh! Maigirman nan, Allah, Yahweh! - Ya sani, bari Isra'ila kanta kuma ta sani! Idan cikin tayaswa ne ko cikin saɓawa imani gãba da Yahweh, kada ka yi mana ceto yau23domin mun gina bagadi muka juya ga bin Yahweh. Idan mun gina wannan bagadi domin mu miƙa hadayun ƙonawa, hadayun gari, ko hadayun salama a kansa to bari Yahweh yasa mu biya.24A'a! Munyi shi cikin tsoro da nufin cewa a lokaci mai zuwa 'ya'yanku za su iya cewa da 'ya'yanmu, 'Ina ruwanku da Yahweh, Allah na Isra'ila?25Gama Yahweh ya sa Yodan ta zama iyaka tsakanin mu da ku. Ku mutanen Ruben da mutanen Gad, baku da abinda zaku yi da Yahweh.'Da haka 'ya'yan ku zasu iya sa 'ya'yan mu su dena yin sujada ga Yahweh.26Don haka sai mu ka ce, 'Bari yanzu mu gina bagadi, ba don ƙonannun hadayu ba ba kuma domin wasu hadayu ba,27amma domin zama shaida tsakanin mu da ku, da kuma don zuriya masu tasowa bayan mu, da kuma zamu bauta wa Yahweh a gaban sa, da ƙonannun hadayu da kuma hadayun mu tare da hadayun mu na salama, domin kada 'ya'yanku su ce da 'ya'yanmu a lokaci mai zuwa, "Baku da rabo cikin Yahweh."'28Sai mu ka ce, 'Idan zasu faɗi mana haka ko su faɗi wa zuriyarmu a lokaci mai zuwa, za mu ce, "Duba! wannan shi ne kwatancin bagadin Yahweh, wanda kakanninmu suka yi, ba domin ƙonannun hadayu ba, ba kuma don hadayu ba, amma domin shaida tsakanin mu da ku".29Bari tayaswa ga Yahweh ta yi nesa da mu, har yau mu juya daga bin sa ta wurin gina bagadi domin ƙonanniyar hadaya, domin hadaya ta gari, ko domin hadayar yanka, banda bagadin Yahweh Allahn mu wanda ke gaban mazamninsa."'30Sa'ad da Fenihas firist da shugabannin jama'a, wato shugabannin zuriyar Isra'ila waɗanda suke tare dashi, su ka ji kalmomin mutanen Ruben, Gad, da Manasse suka ce, wannan ya zama abu mai kyau a garesu.31Sai Fenihas ɗan Eliyeza firist ya ce da mutanen Ruben, Gad, da Manasse, "Yau mun sani cewa Yahweh yana tsakiyar mu, saboda baku aikata wannan saɓo gãba da shi ba. Yanzu kun ceci mutanen Isra'ila daga hannun Yahweh."32Daga nan sai Fenihas ɗan Eliyeza firist da shugabannin su ka juya su ka bar Rubenawa da Gadawa, suka bar ƙasar Giliyad, su ka koma ƙasar Kan'ana, zuwa ga mutanen Isra'ila, su ka dawo masu da magana.33Rahoton su ya gamshi mutanen Isra'ila. Mutanen Isra'ila suka albarkaci Allah ba su ƙara maganar yaƙi da Rubenawa da Gadawa ba kan zancen hallaka ƙasar da su ke zaune a ciki.34Sai mutanen Ruben da Gadawa suka ba bagadi suna, "Shaida" gama suka ce, "Shaida ce tsakanin mu cewa Yahweh shi ne Allah."
Mutanen kabilar Ruben
mutanen kabilar Gad
Anan "muryata" na nufin abubuwan da Yoshuwa ya ce. AT: "yi biyayya da komai da na faɗa"
AT: "Kuna tare da 'yan'uwanku"
Ana maganar biyayya da Yahweh ne kamar tafiya ne a cikin hanyar sa ko titinsa. AT: "Ku yi biyayya da komai da ya faɗa"
Kalamun nan "zuciya" da "ranku" anan na nufin mutum ne gabaɗaya. AT: "da dukkan tunaniku da yadda kuke ji" ko kuma "gabaɗayanku"
Wannan wata gajeruwar sunan ce na Kogin Urdu.
ƙarfi, mayan ƙarfe
Sojojin da sun ci nasara za su kwashe duk abubuwa masu amfani daga mutanen da suka ci su da yaƙi.
Jimlar nan "ta hannun Musa" anan na nufin cewa Yahweh ya yi amfani ne da Musa yă iddar da umarnin sa. AT: "umurnin da Yahweh ya ba wa Musa yă ba ku"
Wannan wata gajeruwar suna ce ta Kogin Urdu.
Kabilun da ke zama a ƙeteren Kogin Urdu za su shigo Kan'ana wurin da suka gina bagadin. Ana maganar wannan wurin ne kamar "gaban" ko kuma "ƙofar shiga" Kan'ana wurin da sauran kabilun ke zama. AT: "a ƙofar shiga ƙasar Kan'anan" )
sunan wani gari
...
sunan wani mutum
Ana maganar dukkan mutane Isra'ila ne gabaɗaya kamar mutum ɗaya ne su. AT: "Dukkan sauran Isra'ilawann suna tambaya" (UDB"
Wannan tambayan na nanataca tsananin zunubansu na da yaka. AT: "Mun rigaya mun yi zunubi ƙwarai a Fowa"
Wannan sunana wani wuri ne. Juya shi yadda kuka yi a 13:20.
AT: "muna kan fama da wancan zunubin har yanzu"
Ana amfani ne da wannan tambayan domin a tsauta wa mutanen saboda zunubansu. AT: "Kada ku juya daga bin Yahweh a yau!"
sunayen mutane, maza.
Ana amfani ne da wannan tambayan domin a tunashe mutane da zunubansu na da. AT: "Ai Akan ɗan Zera ya yi zunubi ta wurin ɗaukan abubuwan da aka keɓe ga Allah. Kuma don haka Allah ya hukunta dukkan mutane Isra'ila"
Kabilun ukun nan na maganar ne da sun nace da cewa ba haka bane. Ba su gina wani bagaɗi domin su yi wa wani Allah sujada bane.
Kabilun Ruben, da Gad da rabin kabilar Manasse sun ba da amsar su.
Wannan zargi ne da kabilu ukun na tunanin cewa 'ya'yan wasu kabilu za su iya keɓe lokaci nan gaba.
Kabilu ukun nan na amfani ne da wannan tambayan gangancin domin su nanata yanayin da suke kokarin kauce wa. AT: "Babu abinda ya haɗa ku da Yahweh, Allah na Isra'ila!"
Kabiilun Rubnen, da Gad, da sauran Manasse sun cigaba da ba da amsa.
Wannan cigaba ne na zargin da 'ya'yan sauran kabilun na iya yi nan gaba.
Wannan wata gajeruwar suna ce na Kogin Urdu.
Kabilu ukun sun gina domin su kauce wa irin wannan yanayin da zai iya ya auku nan gaba.
Kabilun Ruben, da Gad, da sauran kabilun Manasse sun su ma sun ba da amsar su yanzu.
Ana maganar bagadin ne kamar wani mashaidi ne da ke iya ba da shaida akan yancin kabilu ukun.
Wannan shi ne yanayin da kabilu ukun ba su su yă kuskura yă faru.
"ba ko da gãdo"
Yanzu kabilun Ruben, da na Gad, da sauran kabilun sun kammala ba da amsar su.
Kabilu ukun na bayyana amsar su ga zargin da ke iya tasowa ko kin tasowa nan gaba.
Ana maganar zaton tayawa ne kamar wani babbar abu ne da ke iya nesa da su. AT: "Ba za mu kuskura mu tayas ba"
Ana maganar daina bin Yahweh ne kamar juya wa ne daga gare sa. AT: "daina bin sa"
Anan "kalmomin" na nufin sakon da aka haɗa su daga kalmomin. AT: "suka ji tsakonnin"
Anan "a idanun su" means "a nasu ra'ayi."
"sun karya alkawarin da kun yi masa"
Anan "hannu" na nufin hukuncinsa. Anan maganar kare mutane ne kamar ceton su ne daga hannunsa. AT: "kun hana Yahweh hukunta mu"
Anan "gamshi mutanen" na nufin ya "samu karɓa." AT: "Mutanen sun karɓa rohoton shugabannin."
"hallaka kome a ƙasar"
Wannan na nufin Rubenawa da Gadawa.
Ana maganar bagadi ne kamar wani mashaidi ne da ke iya yi wa kabilu ukun shaida.
1Bayan kwanaki masu yawa, bayan da Yahweh ya bada hutu ga Isra'ila daga abokan gãbansu da ke kewaye da su, Yoshuwa kuma ya tsufa ƙwarai.2Sai Yoshuwa ya kira dukkan Isra'ila, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, da manyansu - ya ce masu, "Ni na tsufa sosai.3Kunga dukkan abin da Yahweh Allahn ku ya yi da dukkan ƙasashen nan domin ku, domin Yahweh Allahn ku shi ne ya yi yaƙi domin ku.4Duba! Na sanya sauran al'umman da su ka rage a cisu su zama abin gãdo ga kabilun ku tare da dukkan ƙasashen dana rigaya na hallakar daga Yodan zuwa Babban Teku daga yamma.5Yahweh Allahnku zai kore su. Zai tuttura su daga gaban ku. Zai ƙwace ƙasar su, za ku mallaki ƙasar su, kamar yadda Yahweh ya alƙawarta ma ku.6Sai ku yi ƙarfafa sosai, ku kuma kiyaye dukkan abin da aka rubuta cikin shari'ar Musa kada ku kauce daga gare ta dama ko hagu,7domin kada ku yi cuɗanya da waɗannan al'ummai da su ka rage a cikin ku kada ma ku ambaci sunayen allolin su, ko ku rantse da su, ko ku yi masu sujada, ko ku russuna masu.8Maimakon haka; dole ku manne wa Yahweh Allahn ku kamar yadda ku ka yi zuwa wannan rana.9Gama Yahweh ya kori al'ummai da manya, masu ƙarfi daga gaban ku. Amma ku, ba mutumin da ya iya tsayawa a gaban ku har wa yau.10Kowanne mutum ɗaya daga cikinku za ya runtumi dubu, domin Yahweh Allahnku, shi ne ya ke yaƙi domin ku, kamar yadda ya alƙawarta maku.11Ku kula da kyau, domin ku ƙaunaci Yahweh Allahnku.12Amma idan ku ka juya ku ka manne wa waɗannan sauran al'ummai waɗanda su ka rage a tsakiyar ku, ko idan ku ka yi auratayya da su, ko in ku ka yi huɗɗa tare da su su kuma tare da ku,13ku sani tabbas cewa Yahweh Allahnku ba zai ƙara korar waɗannan al'ummai daga gaban ku ba, maimakon haka, za su zama azargiya da tarko gareku, bulala a bayanku, ƙayayuwa cikin idanunku, har sai kun hallaka daga ƙasan nan mai kyau wadda Yahweh Allahnku ya baku.14Gashi yanzu ina kan tafiya hanya ta dukkan duniya, kuma kun sani da dukkan zukatanku da rayukanku, babu wata kalma data kasa zama gaskiya cikin dukkan abubuwa masu kyau da Yahweh Allahnku ya alƙawarta game da ku, dukkan waɗannan abubuwa sun tabbata game da ku, babu wani abu daya ka sa cika.15Ya zama kuwa kamar yadda kowacce maganar Yahweh Allahnku ya alƙawarta ma ku ta cika, Yahweh zai kawo ma ku dukkan miyagun abubuwa har sai ya hallakar da ku daga ƙasa mai kyau wadda Yahweh Allahnku ya baku.16Zai yi haka idan har kuka karya alƙawarin Yahweh Allahnku, wadda ya umarce ku ku kiyaye. Idan ku ka je ku ka yi sujada ga waɗansu alloli ku ka russuna masu, sa'annan fushin Yahweh zai yi ƙuna a kan ku, da sauri zaku hallaka daga ƙasa mai kyau wadda ya baku."
ya yi shekaru da yawa
Wannan wata gajeruwar suna ce ta Kogin Urdu.
Wannan na nufin gefen da rana ke faɗuna.
Ana maganar karya dokokin Musa ne kamar kaucewa zuwa dama ko hagu daga hanya.
Wannan na iya nufin 1) samun dangartaka da su ko kuma 2) aurayya da su.
faɗi
Wannan na nufin allolin sauran al'ummai.
"ku riƙe Yahweh tam." Ana maganar gaskantawa da Yahweh ne kamar suna riƙe ne da Yahweh tam. AT: "cigaba da gaskanta da Yahweh"
"har wannan lokacin"
Wata tasaye maku da yaƙi. Kalmar nan "ku" na nufin al'umman Isra'ila gabaɗaya.
"1,000"
Ana maganar amincewa da al'addun waɗannan al'umma ne kamar manne wa ne masu tam. AT: "amincewa da al'addun mutanen al'umman da sun tsira daga yaƙin"
Kalamun nan "arzagiya" da "tarko" a takaice na nufin abu ɗaya ne. Dukkansu na maganar sauran al'ummai ne kamar suna da abinda ke da illa har ya jawo wa Isra'ila matsala.
Waɗannan jimla na maganar matsloli ne da waɗannan al'ummai za su jawo wa Isra'ila ne kamar bulalu ne masu zafi da ƙayuyuwa.
Yoshuwa na maganar mutuwarsa kenan. AT: "Za mutu"
Anan "kalamun nan "zukata" da rayuka" na nufin abu ɗaya ne. Dukkansu na nanata cewa kowane mutum ya sani ƙawara.
Waɗannan kalamun na nanata cewa alkawaran Yahweh dukka sun cika. AT: "kowanne magana ta cika"
Wannan na nufin hukuncin da ke barazana a ayoyin da ke baya.
Waɗannan jimla biyun a takaice na nufin abu ɗaya ne. Na biyun na bayyana yadda mutane ke "rusuna wa wasu alloli ne."
"ƙuna" wata karin magana ce da ke nufin farin fushin Yahweh, kamar muta ne ke "ƙuna" ko ta fara "ƙunawa" ko kuma na da saukin fara ƙunawa kamar busashen ciyawa. AT: "Yahweh zai fara fushi da ku"
1Sai Yoshuwa ya tara dukkan kabilun Isra'ila a shekem, ya kira dattawan Isra'ila, da shugabanninsu, da alƙalansu, da magabatansu, suka bayyana kan su gaban Allah.2Sai Yoshuwa ya cewa dukkan jama'a, "Wannan shi ne abinda Yahweh Allah na Isra'ila, ya ce, 'Kakanninku da daɗewa su ka zauna a ƙetaren kogin Yuferatis - Tera, mahaifin Ibrahim da mahaifin Naho - sun kuma yi sujada ga waɗansu alloli.3Amma na ɗauki mahaifinku zuwa ƙetaren Yuferitis na bishe shi cikin ƙasar Kan'ana na bashi zuriya masu yawa ta wurin ɗan sa Ishaku.4Ga Ishaku na bashi Yakubu da Isuwa. Na ba Isuwa ƙasar tudu ta Seyir domin ya mallaketa, amma Yakubu da 'ya'yansa suka gangara zuwa Masar.5Na aika masu Musa da Haruna, Na azabtar da Masarawa da annobai. Bayan haka, sai na fito da ku daga ciki,6Na fito da kakanninku daga Masar. Ku ka zo teku. Masarawa su ka bi su da karusai da mahayan dawakai har zuwa jan teku.7Sa'ad da kakannin ku su ka yi kira ga Yahweh, ya sa duhu tsakanin ku da Masarawa. Ya jawo teku a kan su ta rufe su. Kun ga abin da na yi cikin Masar. Da ga nan ku ka zauna kwanaki da yawa cikin jeji.8Na kawo ku cikin ƙasar Amoriyawa, waɗanda su ke zaune a ƙetaren Yodan. Sun yi yaƙi da ku, na kuma bashe su cikin hannun ku. Ku ka mallaki ƙasar su, kuma na hallakar da su a gabanku.9Sai Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab, ya ta shi ya kai hari a Isra'ila. Ya aika a kira Balaam ɗan Beyor, ya la'antaku.10Amma ban saurari Balaam ba. Babu shakka, sai ya albarkaceku. Da haka na cece ku daga hannunsa.11Kuka haye Yodan ku ka zo Yeriko. Shugabannin Yeriko su ka yi yaƙi da ku, tare da Amoriyawa da Ferizziyawa da Kan'aniyawa, da Hittiyawa da Girgashiyawa da Hibiyawa da Yebusiyawa na ba ku nasara a kansu na sa su ƙarƙashin mulkinku.12Na ku ma aike da zirnaƙo gabanku, ya kore su daga gabanku da sarakuna biyu na Amoriyawa daga gabanku, wannan bai faru ta wurin takobinku ko bakanku ba.13Na ba ku ƙasa wadda ba ku yi aikin kome ba da biranen da ba ku gina ba, yanzu ku na zaune a cikinsu. Ku na cin 'ya'yan kuringar inabi da na zaitun wanda ba ku ne ku ka dasa su ba.'14Yanzu fa sai ku ji tsoron Yahweh ku bauta masa da dukkan sahihanci da gaskiya; sai ku ƙi allolin da kakannin ku suka yi wa sujada a ƙetaren Yodan da cikin Masar, ku yi wa Yahweh sujada.15Idan a gare ku ba daidai bane a yi wa Yahweh sujada, ku zaɓa da kan ku yau wanda zaku bautawa, ko dai alloli waɗanda kakanninku su ka yi wa sujada na ƙetaren Yufiretes ko kuwa allolin Amoriyawa, waɗanda ku ke zaune cikin ƙasarsu. Amma ni da gidana, Yahweh za mu yi wa sujada."16Daga nan mutanen suka amsa suka ce, "Ba zamu taɓa yashe da Yahweh sa'annan mu bautawa wa su alloli ba,17gama Yahweh Allahnmu wanda ya fitar da mu da kakanninmu da ga ƙasar Masar, da ga gidan bauta, wanda ya aikata manyan al'ajibai a idanun mu, ya ku ma tsare mu cikin dukkan hanyar da mu ka bi, da ku ma cikin dukkan al'umman da mu ka ratsa ta tsakiyarsu.18Yahweh kuma ya kori dukkan mutane daga gabanmu, har da Amoriyawa da su ke zaune cikin ƙasar. Don haka mu ma zamu yi wa Yahweh sujada, gama shi ne Allahnmu."19Amma Yoshuwa ya cewa mutane, "Ba zaku bautawa Yahweh ba, gama shi Allah ne mai kishi; ba zai gafarta laifofinku ko zunubanku ba.20Idan ku ka yashe da Yahweh ku ka yi sujada ga baƙin alloli, daga nan zai juya ya azabtar da ku. Daga nan zai hallaka ku, bayan da ya riga ya kyautata ma ku."21Amma mutanen suka cewa Yoshuwa, "Sam, za mu yi sujada ga Yahweh."22Daga nan sai Yoshuwa ya ce ma mutanen, "Ku shaidu ne bisa kanku kun zaɓi Yahweh, ku yi masa sujada." Su ka ce, "Mu shaidune"23Yanzu ku kawar da baƙin allolin da ke tare da ku, ku juyo da zuciyarku ga Yahweh, Allah na Isra'ila."24Sai mutanen suka cewa Yoshuwa, "Za mu yi sujada ga Yahweh Allahnmu. Za mu saurari muryarsa."25Yoshuwa ya yi wa'adi tare ta mutanen a wannan rana. Ya shimfiɗa masu dokoki da farillai a Shekem.26Yoshuwa ya rubuta waɗannan maganganu cikin littafin shari'ar Allah. Ya ɗauki babban dutse ya kafa shi ƙarƙashin itacen oak da ke kusa da wuri mai tsarki na Yahweh.27Yoshuwa ya cewa dukkan mutanen, "Duba, wannan dutse zai zama shaida a kanmu. Gama ya ji dukkan maganganun da Yahweh ya ce da mu. Don ha ka zai zama shaida a kanku, Idan har ku yi musun Allahnku."28Sai Yoshuwa ya sallami mutanen, kowanne ya tafi wurin gãdonsa.29Bayan waɗannan abubuwa Yoshuwa ɗan Nun, bawan Yahweh, ya rasu, yana da shekaru 110.30Aka bizne shi cikin iyakar, gãdonsa a Timnat Sera, wadda ke cikin ƙasar tuddai ta Ifraim, arewacin Tsaunin Gaash.31Isra'ila su ka yi sujada ga Yahweh dukkan kwanakin Yoshuwa, da dukkan kwanakin dattawan da su ka kasance bayan Yoshuwa, waɗanda su ka san dukkan abin da Yahweh ya yi domin Isra'ila.32Ƙasusuwan Yosef, da mutanen Isra'ila suka ɗauko daga Masar - aka bizne su a Shekem, ciki yankin ƙasar da Yakubu ya sayo daga 'ya'yan Hamor, mahaifin Shekem. Ya saye ta a bakin azurfa ɗari, ta zama gãdon zuriyar Yosef.33Eliyeza ɗan Haruna shi ma ya mutu. Su ka bizne shi a Gibiya, a birnin Fenihas ɗansa, wanda aka bashi. Tana cikin ƙasar duwatsu ta Ifraim.
Ana maganar kiran kabilun ne kamar an tattara su ne dukka a wani kwando. AT: "Yoashuwa ya kira dukkan kabilun Isra'ila ne da cewa su same shi"
"suka zo suka tsaya a gaban" ko kuma "sun zo gaban"
"shekaru da dama da suka wuce"
Yoshuwa ya fara ambata abinda Yahweh ya faɗa a dama. Wanna ambacin ya cigaba ne har karshen aya 13.
Waɗannan sunayen mutane ne, maza.
Yoshuwa ya cigaba da ambata abinda Yahweh ya faɗa ne game da yadda ya bi da mutanen sa.
sunar wani wure
Masar na ƙasa da kasar Kan'anan ne a tadawa. AT: "suka tafe"
Yoshuwa ya cigaba ne da ambata abinda Yahweh ya faɗa game da yadda ya bida da mutanensa.
Anan dukkanu na nufin dukkan Isra'ilawan ne, na da da na yanzu. Kalmar nan "ku" na nufin dukkan mutanen Isra'ila.
Yoshuwa ya cigaba ne da ambata abinda Yahweh ya faɗa game da yadda ya bida da mutanensa.
Anan dukkanu na nufin dukkan Isra'ilawan ne, na da da na yanzu. Kalmar nan "ku" na nufin dukkan mutanen Isra'ila.
Wannan na nufin Jan Teku.
wurin da ba mazaune, a hamada
Yoshuwa ya cigaba ne da ambata abinda Yahweh ya faɗa game da yadda ya bida da mutanensa.
Kalmar nan "ku" na nufin al'ummar Isra'ila gabaɗaya.
Wannan wata gajeruwar suna ce da ake ce da Kogin Urdu.
Anan "hannu" na nufi iƙo. AT: "ya sa ku ci nasara a kansu"
Yoshuwa ya cigaba ne da ambata abinda Yahweh ya faɗa game da yadda ya bida da mutanensa.
sunayen mutane ne, maza
Kalmar nan "ku" na nufin al'ummar Isra'ila gabaɗaya. Duba:
Anan "hannu" na nufin iƙo. AT: "ya sa kun yi nasara da shi"
Yoshuwa ya cigaba ne da ambata abinda Yahweh ya faɗa game da yadda ya bida da mutanensa.
Kalmar nan "ku" na nufin al'ummar Isra'ila gabaɗaya.
Wanna wata gajeruwar suna ce na Kogin Urdu.
Wani karamin kwari mai shawagi da ke da mazauni. Anan "ana maganar zinarƙo da yawa ne kamar ɗaya.
Yoshuwa ya gama ambata abinda Yahweh ya faɗa ne game da yadda ya bi da mutanensa.
AT: "Idan ba ku son"
Wannan na nufin iyalinsa da ke zama a gidansa. AT: "iyali na"
...
Anan "gida" wata karin magana ce da ke nufin wurin bauta. AT: "wurin da muka yi bauta"
"al'umman da muka bi"
Wannan na nufin Isra'ilawa.
Allah yana son mutane su ya wa shi kadai ne sujada.
Ana maganr fushin Yahweh ne kamar wani wuta ne da zau hallakar da su. AT: "Za hallakar da ku kamar wuta"
Wanna na nufin Isra'ilawa.
Ana maganar kudura bin Yahweh ne kamar juya zukata ne a gareshi. Anan zuciya na nufin mutum gabaɗaya. A wannan halin, zuciya" na nufin dukkan Isra'ila ne a matsayin mutum ɗaya. AT: "ku juyo kanku ga Yahweh" ko kuma "ku kuduraku yi biyayya da Yahweh"
Wannan na nufin Isra'lawan.
Ana "saurara" na nufin yin biyayya. AT: "Za mu yi biyayya da duk abinda ya ce mu yi"
Ana maganar kafa dokoki ne kamar an saka su ne a wani wuri kamar siffar tuni. AT: "Ya kafa dokoki da farillai" ko kuma "Ya ba su dokoki da farilai su kiyaye"
Wannan na nan kamar cigabar rubuce-rubucen Musa ne.
"ya saka shi"
Wannan na nufin Isra'ila ne.
Ana maganar dutsen da Yoshuwa ya kafa ne kamar wani mutum ne da ya ji abinda aka faɗa kuma zai iya ba da shaidar abinda aka faɗa.
...
"shekaru ɗari ɗaya da goma"
names of places
Wannan wata karin magana ne da ke nufin rayuwan Yoshuwa gabaɗaya.
"zun fi Yoshuwa jimawa"
Zai iya zama da amfani an canza jerin jimlar. AT: "Mutanen Isra'ila sun kawo ƙasusuwan Yosef daga Masar suka bizne shi a Shekem"
"azurfa 100"
sunan wani mutum ne.
sunan wani wuri ne
1Bayan mutuwar Yoshuwa, mutanen Isra'ila suka tambayi Yahweh cewa, "Wane ne zai fara kai wa kan'aniyawa hari domin mu, don yin faɗa da su?"2Sai Yahweh yace "Yahuda zai kai hari, Duba, na ba su iko a kan ƙasar."3Mutanen Yahuda suka ce da mutanen Simiyon, 'yan'uwansu, "Ku zo tare da mu a yankin da aka ɗebo mana don mu je tare mu yi yaƙi da Ka'aniyawa. Mu ma za mu je tare da ku a yankin da aka ɗiba maku". Sai kabilar Simiyon ta tafi tare da su.4Mutanen Yahuda suka kai hari kuma Yahweh ya ba su nasara a kan Ka'aniyawa, da Feriziyawa. Suka kashe masu mutum dubu goma a Bezek.5Suka sami Adoni-Bezek a Bazek, sai suka yi yaƙi da shi suka kuma cinye Kan'aniyawa da Feriziyawa a yaƙi.6Amma Adoni-Bezek ya gudu, sai suka fafare shi suka kamo shi suka yanke yatsunsa da tafin ƙafafunsa.7Adoni-Bezek yace "Sarakuna saba'in da aka yanke masu yatsunsu da tafin ƙafafunsu suna neman abincinsu a ƙarƙashin teburina. "Kamar yadda na yi haka nima Allah ya yi mani." Sai suka kawo shi Yerusalem, ya kuma mutu a can.8Mutanen Yahuda sun yaƙi birnin Yerusalem suka kuma ɗauke ta. Sun kai hari da kaifin takobi kuma suka banka wa garin wuta.9Bayan haka mutanen Yahuda suka je suyi faɗa da Ka'aniyawa da ke zaune a bisan tsibirin ƙasar, a cikin Negeb, da cikin tsibirin duwatsun yammacin.10Yahuda ya haura gãba da Ka'aniyawa da ke zaune a Hebiron (sunan Hebiron a dã shi ne Kiriyat Arba), suka kuma buge Sheshai, da Ahiman, da Talmaye.11Daga can sai mutanen Yahuda suka nausa gãba da mazaunan Debir (sunan Debir a dã shi ne Kiriyat Sefa).12Kalibu ya ce, "Duk wanda ya kai wa Kiriyat Sefa hari ya kuma ɗauke ta, Zan ba shi Aksa, ɗiyata, ta zama matarsa."13Otniyel ɗan Kenaz (ƙanin Kaleb) ya yi nasara a kan Debir, sai Kaleb ya ba shi Aksa, ɗiyarsa, ta zama matarsa.14Da sauri Aksa ta zo wurin Otniyel, sai ta iza shi ya sa mahaifinta ya bata fili. Da ta ke saukowa a kan jaki, Kaleb ya tambaye ta, "Mene ne zan yi maki?"15Ta ce da shi, "Ba ni albarka. Tun da ka ba ni ƙasar Negeb, ka kuma ba ni maɓulɓullan ruwa." Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓullan tudu da na fadama.16Zuriyar surukin Musa Bakenine sun hauro daga Birnin Dabino tare da mutanen Yahuda, zuwa ga tsibirin Yahuda, wanda ke cikin Negeb, su zauna tare da mutanen Yahuda kusa da Arad.17Mutanen Yahuda suka tafi tare da mutanen Simiyon 'yan'uwansu sai suka tunkari Kan'aniyawan da ke zaune a Zefat suka hallakar da su kakaf. Sunan birnin Hormah.18Mutanen Yahuda suka kuma kame Gaza da ƙasashen da ke kewaye da ita, Ashkelon da ƙasar da ke maƙwabtaka da ita, da kuma Ekron tare da ƙasar da ke kewaye da ita.19Yahweh na tare da mutanen Yahuda suka kuma ɗauki mallakar ƙasar kan tudu, amma ba su iya korar mazaunan ƙasar kan tudun ba don su masu karusan ƙarfe ne.20Hebron kuwa Kaleb aka baiwa (kamar yarda Musa yace), ya kuma kori 'ya'yan Anak uku daga wurin.21Amma mutanen Benyamin ba su kori Yebusiyawan da ke zaune a Yerusalem ba. Sai Yebusiyawan suka zauna tare da mutanen Benyamin a Yerusalem har ranar nan.22Gidan Yosef suka yi shirin kai wa Betel hari, kuma Yahweh na tare da su.23Suka aiki maza su leƙo asirin Betel (Birnin da dã ake kira Luz).24Masu leken asirin suka ga wani mutum na fitowa daga birnin, sai suka ce da shi, "In ka yarda, nuna mana yadda za a shiga cikin birnin nan, kuma za mu yi maka alheri."25Ya nuna masu hanyar zuwa cikin birnin, sai suka kai wa birnin hari da kaifin takobi, amma suka bar mutumin da dukkan iyalinsa suka kuɓuta.26Sai mutumin ya je ƙasar Hitiyawa ya gina wani birnin da ya kira shi Luz, shi ne kuwa sunansa har wa yau.27Mutanen Manasse ba su kori mutanen da ke zama a biranen Bet Shan da ƙauyukansu ba, ko Ta'anak da ƙauyukansu, ko waɗanda suka zauna a Dor da ƙauyukansu, ko waɗanda suka zauna a Ibilim da ƙauyukansu, ko waɗanda suka zauna a Megiddo da ƙauyukansu ba, domin Ka'aniyawan sun bugi ƙirjinsu don zama a cikin ƙasar.28Da Isra'ila ta yi ƙarfi, suka tilasta wa Ka'aniyawa su yi masu bauta ta aiki mai tsanani, amma ba su taɓa korar su kakaf ba.29Ifraim bai kori Ka'aniyawan da suka zauna a Gezer ba, don haka Ka'aniyawa suka ci gaba da zama a Gezer a cikin su.30Zebulun bai tumɓuke mutanen da ke zama a Kitiron, ko mutanen da ke zama a Nahalol ba, saboda haka Ka'aniyawan suka ci gaba da zama a cikinsu, amma Zebulun ya tilasta wa Ka'aniyawan su bauta masu tare da aiki mai tsanani.31Asha bai tumɓuke mutanen da ke zama a Akko, ko mutanen da ke zama a Sidon, ko waɗanda ke zama a Alab, Akzib, Helba, Afek, ko Rehob ba.32Don haka kabilar Asha ta zauna cikin Ka'aniyawan (waɗanda ke zaune a ƙasar), saboda ba su kore su ba.33Kabilar Naftali ba su kori waɗanda ke zaune a Bet Shemesha, ko waɗanda ke zaune a Bet Anat ba. Don haka kabilar Naftali ta zauna cikin Ka'aniyawa (mutanen da tun asali ke zaune a ƙasar). Duk da haka, aka nawaita wa mazaunan Bet Shemesha da Bet Anata aikin bauta ga Naftali34Amoriyawa suka tilasta wa kabilar Dan su zauna a ƙasar kan tudu, ba su kuma ba su damar saukowa kwari ba.35Don haka Amoriyawa suka zauna a Tsaunin Heres, a Aijalon, da Sha'albim, amma ƙarfin mayaƙan gidan Yosef ya mamaye su, ya kuma sa aka tilasta masu su bauta masu da aiki mai tsanani.36Iyakar Amoriyawa ta kama daga tudun Akrabbim a Sela zuwa cikin ƙasar kan tudu.
Littafin Alƙalai ya ci gaba labarin Joshua na, da kuma farkon wani sabon sashin labarin.
Wannan sunan da Allah ya bayyana wa mutanen sa ne Tsohon Alƙawari. Duba waje translationWord domin sani game da yadda za a juya wannan.
Kalmar "mu" na nufi mutanen Isra'ila ne.
"Yahuda" na wakilce mazajen kabilar Yahuda. Yahweh na umurtar waɗannan mazajen su za farko a kai harin. AT: "Lalle ne mazajen Yahuda su kai hari a farko"
"Duba" ko "haƙika" ko "Wannan na jadada abin da zai biyo baya"
Wannan na nufin ƙasa da Kan'aniyawa su ke zama. AT: "ƙasar Kan'aniyawa"
"'yan'uwansu Isra'ilawa"
'Yan kabilar Yahuda and Simiyon na tare da sauran mutanen Isra'ila a kwarin Kogin Yodan. Ƙasar da aka bayar wa Yahuda na tudai ne ba a kwari ba. AT: "ku taho tare da mu" ko "mu tafi tare"
AT: "da Yahweh ɗebo mana ... da Yahweh ya ɗebo muku"
"Mu ma sai mu je da ku" ko "Haka kuma, mu ma za mu tafi tare da ku"
Wannan na nufi mazajen Simiyon ma sun kai har tare da mazajen Yahuda.
"Su ka kashe kusa da 10, 000" ko "Suka kashe da yawa"
"sojojin Kan'aniyawa da Feriziyawa" ko "abokan gãba"
Wannan wani yanki ne a tudan Kan'aniyawa.
Wannan mutumin shi ne shugaban sojojin Kan'aniyawa da Feriziyawa.
"Shi" a nan na nufi Adoni-Bezek ne da sojojinsa. AT: "su ka yaƙe shi da sojojinshi"
"kore shi"
"Sarakuna 70"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Waɗanda na faɗa wa mazaje na su yanke yatsun da ƙafafun" ko "wanda yatsun da kafafun aka yanke"
"su ci raguwar abinci da ƙarƙashin teburina" yadda Adoni-Bezek ya tilasta waɗannan sarakuna su ci kankara abinici na nuna yadda ya walãkanta waɗannan sarakuna.
A nan "birni" na nufi mutanen. AT: "mutanen su ke zama a Yerusalem aka kuma ci su da yaki"
"da bakin takobi." "takobi" a nan na nufi takobi da sauran kayan yaƙi da sojojin su ka yi amfani da shi a yaƙi. AT: "da takobinsu" ko "da kaya yaƙin su"
"a kuduncin hamadan Yahuda"
jerin tudai
Wannan bayanin karin haske ne. Mai yiwuwa wasu mutanen da suka fara karanta wannan littafi sun san da Kiriyat Arba amma ba su san cewa wuri ɗaya ne ake kira Hebiron ba.
Waɗannan sunayen uku na shugabanen Hebiron ne. Kowani shugaba na wakilce sojojinsa. AT: "Sheshai, Ahiman, da Talmaya, da sojojinsu"
Watakila marubucin na rubuta wannan domin masu karatun sun san birnin da sunan Dibir. Amma a sa'ad Isra'ila su ka kai hari, ana kiran birnin Kiriyata Sefa. AT: "Wanda ake kira Kiriyat Sefa"
AT: "Duk wanda ya kai wa mutanen Kiriyat Sefa hari ya kuma ci birnin ya ɗauke ta "
Wannan sunar 'yar Kaleb ce.
Waɗannan sunayen maza ne.
"Aksa ta takurawa Otniyel"
Wannan na nuna cewa Kaleb ya ba ta filin da tambayeshi a aya 14. Yanzu a aya 15, tana roƙon inda ruwa yake bubbugowa daga kasa a haɗe da filin.
"Ka yi mini alfarma" ko "Ka yi mini wannan"
Kaleb ya ba da Aksa wa Otniyel a aure, don haka ta kasance da Otniyel a birnin da ya karba a Negeb. Gamsashen bayani game da ma'anar wannan maganar shine. AT: "Tunda shike ka ba da ni a aure a cikin Negeb"
"na mahaifin matar Musa"
suruki, wanda ke ɗaya daga cikin mutanen Ken, suka hauro"
"bar Birnin Dabino ... su ka kuma je cikin jeji"
Wannan wani suna ne na birnin Yeriko.
Wannan sunan wani birni ne a Kan'ana.
A nan '''yan'uwan" na ma'anar 'yan iyali da suke wani kabilar Isra'ila daban.
Wannan sunan wani birni ne a Kan'ana.
Bayan da Isra'ilawa su ka ci Zefat da yaƙi, sun canja sunar zuwa "Hormah." Ma'anar sunar "Hormah" ita ce "hallakar gaba ɗaya."
Ma'anar kalmar "na tare da" shi ne, Yahweh ya taimake mutanen Yahuda.
babban sarari fili, inda ba ko itace
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Musa ya ba Kaleb Hebron"
Ana amfani da sunayan shugabanen kabilar a nufin dukka mutanen. AT: "'ya'yan Anak uku da mutanensu"
Wannan sunan na miji ne. Zuriyar Anak sanannu maso tsawo ne.
"har yanzu." Wannan na nufi har lokacin da aka rubuta littafin Alƙalai.
A nan "gida" na wakilce zuriya. Ifraim da Manassa 'ya'yan Yosef ne, kuma "gidan Yosef" na iya nufin zuriyar Ifraim ne da Manassa. AT: "Zuriyar Ifraimu da Manassa" ko "Mazajen kabilun Ifraim da Manassa"
A nan "Betel" na wakilce mutanen da suke zama a Betel.
samun bayani a asirinci
Wannan bayayin karin haske ne. Watakila wasu mutane masu karatun wannan littafi sun taba jin sunnan Luz, amma ba su san cewa wuri ɗaya ne ake kira Betel ba.
masu samun bayani a asirinci
A nan "birni" na wakilce mutanen. AT: "su ka kai hari wa mutanen birnin"
"da bakin takobin." "takobi" a nan na nufin takobi ne da sauran kayan yaƙi da sojoji su ka yi amfani da shi a yaƙi. AT: "da kayan yaƙinsu"
Wannan karin magana ne. AT: "kuɓutar"
Wannan sabon gari na a ƙasar Hitiyawa da aka ba da sunan Luz, kusa da Betel, in da mutumin ya bari.
"wannan har yanzu sunan kenan." A nan "har wa yau" na nufin lokacin da aka rubuta littafin Alƙalai.
Waɗannan sunayen birane ne.
"Bugin ƙirji" na nufi ɗaukar kudiri mai ƙarfi a akan abu. AT: "domin Kan'aniyawan sun yanke shawara mai ƙarfi ba za su bar ƙasar ba"
AT: "Da mutanen Isra'ila su ka yi ƙarfi"
"su ka tilasta Kan'aniyawa wajen yin musu aiki mai wahala"
A nan "Ifraim" na wakilce mazaje ko sojojin kabilar Ifraim.
Wannan sunan wani birni ne ta yankin Ifraim.
A nan "Zebulun" na wakilce mazaje ko sojojin kabilar Zebulun
"Waɗannan sunayen birane ne a Kan'ana.
A nan "Zebulun" na wakilce mutanen kabilar Zebulun.
"aiki mai wahala"
A nan "Asha" na nufi mazaje ko sojoin kabilar Asha.
Waɗannan sunayen birane ne a ƙasar Kan'ana.
Waɗannan sunayen birane ne.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "mutanen Naftali su ka tilastawa mutanen Bet Shemesh da Bet Anat wajen yi musu aiki a matsayin bayi"
"hana su saukowa ƙasa"
babban sararin ƙasa ba ko itace
Wannan sunan babban tudu ne inda aka gina birnin Aijalon.
Waɗannan sunayen birane ne.
"domin ƙarfin mayaƙansu, kabilar nan daga Yosef sun iya mamyesu"
A nan "gida" na wakilce zuriya. Manassa da Ifraim 'ya'yan Yosef ne kuma "gidan Yosef" na iya nufin zuriyar Manassa da Ifraim ne. AT: "zuriyar Manassa da Ifiaim" ko "mutanen kabilar Manassa da Ifraim"
Wannan hanya ne kudu maso yammacin Teku Mutuwa. Ana iya kiran wurin "Hanyar Kunama."
Wannan sunan birni ne.
1Mala'ikan Yahweh ya taso daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, "Na fitar da ku daga Masar, na kuma kawo ku ƙasar da na yi rantsuwa zan ba kakaninku. Na ce 'ba zan taɓa karya alƙawarina da ku ba.2Ba za ku yi yarjejeniya da mazaunan garin nan ba. Wajibi ne ku rurrushe bagadansu.' Amma ba ku saurari muryata ba. Me kenan ku ka yi?3Yanzu sai na ce, 'ba zan kori Kan'aniyawa daga gare ku ba, amma za su zama ƙaya a gare ku, kuma allolinsu za su zama tarko a gare ku."'4A lokacin da mala'ikan Yahweh ya furta waɗannan kalmomin ga mutanen Isra'ila, sai suka yi kuka mai ƙarfi.5Suka kira wurin Bokim. A wurin suka miƙa hadayu ga Yahweh.6Sa'ad da Yoshuwa ya aike mutanen a hanyarsu, kowanne ɗaya daga mutanen Isra'ila kuwa kowa ya nufi wurin da aka sa shi don mallakar ƙasar.7Mutanen kuwa sun bauta wa Yahweh a zamanin Yoshuwa da kuma ta dattawan da suka bi bayansa, waɗanda suka ga dukkan abubuwa masu girma da Yahweh ya yi wa Isra'ila.8Yoshuwa ɗan Nun, bawan Yahweh, ya rasu yana da shekaru 110.9Aka kuwa binne shi a tsibirin ƙasar da aka ba shi ya mallaka a Timnat Heres, a tudun ƙasar Ifiraim, arewa da Tsaunin Ga'ash.10Dukkan wannan tsarar kuwa sun kasance tare da kakaninsu. bayansu sai wata tsara da ba ta san Yahweh ko abin da ya yi wa Isra'ila ba ta taso biye da su.11Mutanen Isra'ila kuwa sun yi mugun abu a fuskar Yahweh suka kuma bautawa Ba'aloli.12Sun kauce daga Yahweh, Allahn kakaninsu, wanda ya fitar da su daga ƙasar Masar. Sun bi waɗansu alloli, wato allolin mutanen da ke kewaye da su, kuma sun rusuna ƙasa gare su. Suka sa Yahweh ya fusata domin13sun kauce daga Yahweh sun kuma yi wa Ba'al da Ashtoret sujada.14Fushin Yahweh ya taso wa Isra'ila, sai ya sa 'yan fashi suka ƙwace mallakarsu daga gare su. Ya maishe su barorin da ke ƙarƙashin ƙarfin maƙiyansu da ke kewaye da su, saboda haka ba su iya kare kansu daga maƙiyansu ba.15Duk inda Isra'ila su ka je faɗa, hanuwan Yahweh na gãba da su don a yi nasara da su, kamar dai yadda ya rantse masu kuma sun shiga ƙunci mai tsanani.16Sa'an nan Yahweh ya taso da Alƙalai, waɗanda su ka ceto su daga hanuwan masu satar mallakarsu.17Duk da haka ba su saurari alƙalansu ba. Suka zama marasa aminci ga Yahweh, suka kuma maida kansu kamar karuwai ga waɗansu alloli suka kuma yi masu sujada. Suka juya baya daga hanyar da kakaninsu suka yi rayuwarsu - waɗanda suka yi biyayya da umurnin Yahweh - amma su da kansu ba su yi haka ba.18A lokacin da Yahweh ya naɗa masu alƙalai, Yahweh ya taimaki alƙalan ya kuma ƙuɓutar da su daga hanuwan maƙiyansu a dukkan kwanakin alƙalan. Yahweh ya yi masu tagomashi yayin da suke nishi saboda waɗanda ke zalunta da kuma ƙuntata masu.19Amma sa'ad da alƙalan su ka mutu, sai suka juya baya suna yin miyagun abubuwan da suka fi waɗanda ma ubaninsu suka yi. Suka biɗi waɗansu alloli don su bauta masu su kuma yi masu sujada. Suka ƙi barin miyagun ayukansu ko taurin kansu.20Fushin Yahweh kuwa ya taso ma Isra'ila; ya ce "Saboda wannan al'umma ta karya sharuɗan alkawarina wanda na kafa domin ubaninsu-saboda ba su saurari muryata ba -21Daga yanzu ba zan korar masu ko ɗaya daga cikin al'umman da Yoshuwa ya rage kafin mutuwarsa ba.22Zan yi haka domin in gwada Isra'ila, ko za su yi biyayya da hanyar Yahweh da tafiya cikinta ko ba za su yi ba. Kamar yadda ubaninsu suka yi biyayya."23Shi ya sa Yahweh ya bar al'ummomin nan bai kuma kore su da sauri ya ba da su ga hannun Yoshuwa ba.
Ma'ana mai yiwuwa 1) "mala'ika da ke wakilce Yahweh" ko 2) "manzo da ke yi wa Yahweh hidima" ko 3) "mai yiwuwa Yahweh ne da kansa, amma ya yi kamar da mala'ika sa'ad da ya ke magana da mutumin". Ɗaya a cikin waɗannan ke ba da ma'anar "Ni" da mala'ikan ya yi amfani da shi kamar shine Yahweh da kansa.
"ya bar Gilgal zuwa Bokim"
Wannan ne saunar da 'ya'yan Isra'ila suka sa wa wurin a Alƙalai 2:5 bayan mala'ikan ya tsauta wa mutanen. Ma'anar "Bokim" shi ne "kuka."
An fahimci cewa mala'ikar Yahweh na magana ne da mutanen Isra'ila. AT: "sai ya ce wa mutanen Isra'ila"
"na jagorance ku daga Masar"
"ubanninsu"
Wannan karin magana ne. AT: "kasa aikata abin da na ce zan yi muku"
"murya" na wakilce abin da Yahweh ya faɗa ne a nan. AT: "ba ku yi biyyaya da umurni na ba"
An yi wannan tambaya domin a sa mutanen Isra'ila su san cewa sun yi rashin biyyaya kuma za su sha hukuncin yin haka. AT: "Kun aikata mummunar abu."
Mala'ikan Yahweh ya ci gaba da magana da mutanen Isra'ila.
AT: "Yanzu dai ina faɗa muku cewa ba zan ... tarko a gare ku."
Ana maganar yadda Kan'aniyawa za su zama matsala ga Isra'ilawa kamar za su zama ƙaya ne a cikin Isra'ilawa. AT: "sa muku matsala"
Ana maganar yadda Isra'ilawa na bautar allolin Kan'aniyawa kamar allolin karyan tarko ne da mai farauta ke kaman dabbobi da shi.
"kuka da hawaye kwarai"
A nan mai ba da labarin na ba da takaitaciyar bayani game da tsaran Isra'ila bayan Yoshuwa suka yi zunubi wajen bautar allolin ƙarya, saboda haka Yahweh ya hukunta su. Amma zai turo da alkalai domin ceton su. Wannan takaitacen labarin ya tsaya a Alƙalai 2:23.
Aukuwar Alƙalai 1:1-2:5 ya faru ne bayan Yoshuwa ya rasu. Wannan na ba da labarin abun da ya faru a karshen lattifin Yoshuwa ne.
Wannan bayani na iya zama a fili. AT: "zuwa wurin da Yahweh ya ba su"
Ma'anar wannan shi ne lokacin da ruwar wani. AT: "a lokacin ruwar"
Wannan na nufin mutanen da suka taimaka a shugabancin Isra'ilawa, a sashin zaman adalci na jama'a da kuma al'amuran addini kamar doƙar Musa.
Ma'anar wannan shi ne wadda suka yi rayuwa fiye da wani. AT: "suka rayu fiye da shi"
Wannan suna na miji ne.
"shekaru ɗari da goma"
AT: "da Allah ya ba shi"
Wannan sunan wani ƙasa ne.
Wannan sunar wani tsauni ne.
Ma'anar wannan magana "sun kasance tare da kakaninsu" shi ne da mutanen wacan tsaran su ka mutu ruhun su na tafiya wuri ɗaya ne da na kakaninsu wanda su ka mutu kafin su. Wata hanyar cewa sun mutu ne.
A nan ma'anar "ba ta san" shi ne basu dandana ikon Yahweh ba kamar tsaran baya.
"A fuskar Yahweh" a nan na nufin tunanin Yahweh game da abu. AT: "Abun da Yahweh ya ce mugunta ne"
Ana amfani da sunan "Ba'al" wa wani allahn ƙarya, amma ana amfani da kalmar wa dukka allolin da ake bauta musu tare da Ba'al.
Ana maganar yadda Isra'ilawa sun daina yi wa Yahweh biyyaya kamar suna tare ne sai suka tafi.
Ana maganar yadda Isra'ilawa su ka fara bauta wa allolin ƙarya, kamar Isra'ilawan na tafiya ne da kafafun su, su na kuma bin allolin ƙarya.
Wannan sujada ne da kuma ba wani girma.
"Su ka sa Yahweh ya yi fushi"
Wannan wata allah ce da ake bauta wa a hanyoyi dabam dabam.
Ana bayana fushin Yahweh kamar wutar da ke ci. AT: "Yahweh ya yi fushi da mutanen Isra'ila ƙwarai"
"ya sa 'yan fashi su ka sace mallakar su"
"hanu" a nan na wakilce ikon Yahweh. AT: "Yahweh ya taimakawa maƙiyansa wajen ci nasara a gare su"
"suna cikin wahala mai tsanani"
Ana maganar yadda ya zaɓe Alƙalai kamar ya na ta da mutanen ne.
"ba su yi wa alƙalansu biyyaya"
Ana maganar yadda mutanen su ka musunce Yahweh su na kuma bautar wasu alloli kamar mutanen karuwai ne. AT: "musunce shi ta wurin bautar allolin ƙarya"
An yi maganar yadda mutanen ba su aikata yadda kakaninsu su ka yi kamar mutanen sun juya baya ne su ka bi wani hanya daban da kakaninsu.
An yi maganar yadda Yahweh ya zaɓa musu alƙalai kamar ya na ta da mutanen ne.
Kalmar "su" na nufi Isra'ilawa.
"mudin alƙalin na a raye"
tagomashi ko nuna jinka ga wani
Yadda mutum ke yi da murya a sa'ad da yana wahala shine ake amfani da shi a bayana raɗaɗin wahalar da Isra'ilawa ke ciki. AT: "Ya yin da suke wahala"
"Su ka ƙi daina aikata mugunta da taurin kai." AT: "Su ka ci gaba da aikata mugunta da kuma taurin kai"
An bayana fushin Yawweh kamar kamar wutar da ke ci.
A nan "al'umma" a nan na wakilce mutane ne. AT: "Waɗannan mutanen sun karya" ko "Isra'ilawa sun karya"
"Murya" na wakilce abun da Yahweh ya ce. AT: "ba su yi biyyaya da abun da na umurce su su yi ba" ko "ba su yi mini biyyaya ba"
Ana maganar yadda Yahweh na so mutanen su yi rayuwa kamar wani hanya ne da ake iya bi. Ana maganar biyyaya ga Yahweh kamar tafiya ne a kan hanyar sa.
"baya bar Yoshuwa ya ci su da yaƙi ba"
1Yanzu kuwa Yahweh ya bar waɗannan ƙasashen domin ya gwada Isra'ila ne, wato duk wanda bai taɓa sanin yaƙe-yaƙen da Isra'ila ta yi da Kan'ana ba2(Ya yi wannan ne domin ya koyar da al'amarin yaƙi ga sabon zamanin Isra'ilawan da ba su san shi ba.)3Waɗannan su ne alu'mman: sarakuna biyar wato Filistiyawa da dukkan Kan'aniyawa da Sidoniyawa, da Hibitiyawa da ke zaune a duwatsun Lebanon, daga Tsaunin Ba'al Hermon zuwa Hamat Fass.4Waɗannan al'umman aka rage da manufar kasancewar hanyar da Yaahweh zai gwada Isra'ila, ko tabbas za su yi biyayya da dokokin da ya ba kakaninsu ta wurin Musa.5Mutanen Isra'ila kuwa sun yi zama a cikin Kan'aniyawa da Hitiyawa da Amoriyawa da Feriziyawa da Hibiyawa da Yebusiyawa.6Suka ɗauki 'yammatansu su zama matayensu, haka kuma nasu 'yammatan suka bayar ga samarinsu, suka kuma bauta wa allolinsu.7Mutanen Isra'ila sun yi mugun abu a fuskar Yahweh kuma sun mance da Yahweh Allahnsu. Suka bauta wa gumakan Ba'al da Ashira.8Ta haka, fushin Yahweh mai zafi ya sauko wa Isra'ila, sai ya sayar da su ga hannun Kushan Rishata'imi sarkin Aram Naharayim. Mutanen Isra'ila kuwa sun bautawa Kushan Rishatayim shekaru takwas.9Sa'ad da mutanen Isra'ila suka yi kira ga Yahweh, sai Yahweh ya tayar da wani wanda zai taimaka wa mutanen Isra'ila, wanda kuma zai kuɓutar da su: Otniyel ɗan Kenaz (ƙanin Kaleb).10Ruhun Yahweh ya ƙarfafa shi, ya yi alƙalancin Isra'ila, ya kuma je yaƙi. Yahweh ya ba shi nasara a kan Kushan Rishatayim sarkin Aram. Hanuwan Otniyel ya ragargaza Kushan Rishatayim.11Ƙasar ta kasance da salama shekaru arba'in. Sai Otniyel ɗan Kenaz ya mutu.12Bayan haka, Isra'ilawa kuma sun yi mugun abu a fuskar Yahweh, sai Yahweh ya ba Eglon sarkin Mowab ƙarfin da zai mallaki Isra'ilawa.13Eglon ya haɗu da Amoniyawa da Amelikawa sai suka yi nasara da Isra'ila, suka kuma ɗauki mallakar Birnin Dabino.14Mutanen Isra'ila sun bauta wa Eglon sarkin Mowab shekaru goma sha takwas.15Sa'ad da mutanen Isra'ila suka yi kira ga Yahweh, sai Yahweh ya tayar da wani mai taimako wanda zai taimake su, Ehud ɗan Gera, na kabilar Benyamin, bahago ne shi. Mutanen Isra'ila sun aike shi, da kyautukkansu, zuwa ga Eglon sarkin Mowab.16Ehud ya ƙera wa kansa takobi mai ƙaifi biyu, kamu guda a tsawo; ya yi ɗammara da ta a ƙarƙashin tufafinsa ta wajen cinyarsa ta dama.17Ya ba da kyautar ga sarki Eglon na Mowab. (Eglon kuwa mai ƙiba ne.)18Bayan Ehud ya gama miƙa kyautar, sai ya bar wurin tare da waɗanda suka ɗauke ta suka kai ciki.19Ehud da kansa kuwa, ko da yake, lokacin da ya iso wurin da ake yin siffofi kusa da Gilgal, sai ya juyo ya koma baya, sai ya ce, "Ina da saƙo a asirce domin ka, sarkina." Eglon yace, "Shiru" Sai dukkan waɗanda ke yi masa hidima suka bar ɗakin.20Ehud ya je wurin sa. Sarkin yana zaune da kansa, shi kaɗai a inuwar bene. Ehud yace, "Ina da saƙo daga Allah domin ka." Sarkin ya miƙe tsaye daga kujerarsa.21Ehud ya shigar da hannun hagunsa ya ɗauki takobin daga cinyarsa ta dama, sai ya cake jikin sarkin.22Ƙotar takobin kuma ta shige cikin jikinsa biye da wuƙar. Tsinin takobin ya fita ta bayansa kuma rufe da ƙitse, domin Ehud bai zaro takobin daga tumbinsa ba.23Sai Ehud ya fita daga shirayin ya kukkulle ƙofofin babban benen a bayansa.24Bayan Ehud ya tafi, barorin sarki suka zo; suka ga ƙofofin ɓenen a kulle, sai suka yi zaton, "Tabbas ya na hutawa a inuwar benen ne."25Suka yi ta ƙaruwa da kulawa har sai da suka ji lallai suna sakaci da aikinsu ne yayin da sarki fa bai buɗe ƙofofin babban benen ba. Sai suka ɗauki makullin suka buɗe, sai ga ubangijinsu a kwance, a ƙasa, matacce.26Yayin da barorin ke jira, suka rasa mema za su yi, Ehud kuwa ya tsere har ya wuce wurin da ake sassaƙa sifofin gumaka, sai ya tsere zuwa Se'ira.27Sa'ad da ya iso, sai ya busa kakaki a ƙasar tudu ta Ifraim. Sa'an nan mutanen Isra'ila suka je ƙasa tare da shi daga tuddai, kuma yana yi masu jagora.28Ya ce masu, "Ku biyo ni, gama Yahweh na gab da yin nasara da maƙiyanku, Mowabawa. "Suka bi shi suka kuma kama mashigin Yodan ƙetare zuwa Mowabawa, ba su kuma bar wani ya ƙetare kogin ba.29A lokacin nan ne suka kashe kusan dubu goma na mazajen Mowab, kuma dukkan su masu ƙarfi ne gwarzaye. Babu ko ɗayan da ya tsere.30Wato, a ranar nan ne Isra'ila ta mamaye Mowab da ƙarfinta, kuma ƙasar ta sami hutawa shekaru tamanin31Bayan Ehud, alƙali na biye shi ne Shamgar ɗan Anat wanda ya kashe maza 600 na Filistiyawa da tsabgar dabbobi. Ya kuma kuɓutar da Isra'ila daga hatsari.
A nan "yanzu" fara wani sabon sashi na labarin.
AT: "duk da wanda bai yi yaƙi a cikin kowane yaƙe-yaƙen a Kan'ana"
Waɗannan sarakuna biyar suna wakiltar kansu da mutanensu. AT: "sarakuna biyar da mutanensu"
Wannan shi ne sunan yanki a arewacin iyakar Kan'ana
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Yahweh ya aka rage wadannan al'umman a cikin Kan'ana"
"da dokokin da Yahweh ya ba"
"A fuskar Yahweh" a nan na nufin tunanin Yahweh game da abu. AT: "abun da Yahweh ya ce mugunta ne"
Wannan karin magana ne. A nan "mance" na nufin "Isra'ilawa suka daina yi wa Yahweh biyayya"
AT: "Yahweh ya yi fushi kwarai"
A nan "hanu" na wakilce iko ko sarrafawa. Wato, Kushan Rishatayim na wakilce kansa da sojojinsa.
Wannan sunan al'umma ne.
An ambaci Yahweh wanda ya naɗa wani zai yi masa aiki na musamman kamar dai wanda ya ɗaga shi.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan kalmar tana nufin cewa Yahweh ya taimake Otniyel da halaye don zama babban shugaba.
A nan "alƙalancin" yana nufin ya jagoranci mutanen Isra'ila.
A nan "ƙasar" na nufin mutanen da suke zama a wurin. AT: "mutane sun zauna lafiya"
"shekaru 40"
AT: "Yahweh ya sa Eglon sarkin Mowab ya yi ƙarfi"
Wannan wani suna ne na Yeriko.
"shekaru 18"
A nan wannan yana nufin yin ihu ga wani nisa. Hakanan yana iya nufin neman wani don taimako, musamman Allah.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"ya ɗaure shi a cinyarsa ta dama a ƙarƙashin tufafinsa"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Da ya iso wani wuri kusa da Gilgal inda mutane ke yin siffofi"
Wannan wani daki ne a saman gini, wajen hutu daga zafin rana.
Tashiwa ya tsaya alama ce Allah zai daraja maganar sa.
"wuri mai ci na takobin ya fita a bayansa"
wani ɗan daki da ke kafin babban daki
Wannan magana ne ciki da'a, ana nufin bayi ne ko fitsari
Su ka jira har su ka fara damuwa ko wani abu ya faru ne, kuma aikinsu ne su buɗe kofar dakin sarkin su.
"ɗauki makullin su ka kuma buɗe kofofin"
Wannan na faɗin abu da ya faru kafin barorin su bude kofar ɓene su ka kuma ga sarkin a mace. AT: "A sa'ad da barorin suna kan jira a wajen bene ... Ehud kuwa ya tsere"
Wannan sunan wani birni ne.
Ana iya bayana wannan a fili. AT: "Sa'ad da ya iso Se'ira"
Ehud na magana da mutanen Isra'ila a Ifraim.
An yi maganar yadda Yahweh na taimakon Isra'ilawa wajen nasara da maƙiyan kamar shi Yahweh jaromin yaƙi ne da zai yi fada ya kuma yi nasara da maƙiyansu.
"samu ikon bisa mashigin ƙetare"
gyafen kogi da ba zurfi kuma na da saukin ƙetare wa zuwa wani gyafen
"hana kowa ƙetare wa"
"mazaje 10,000"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "sojojin Isra'ila suka yi nasara da Mowabawa."
A nan "ƙasar" na wakilce mutane ne. AT: "Isra'ilawa su ka zauna cikin salama"
"shekaru 80"
Allah ya kan zaɓi alƙalai su shugabanci Isra'ilawa a lokacin da suka shiga matsala bayan da su na cikin ƙasar Alkawari, kafin su ka samu sarakuna. Alƙalan ne a yawanci lokaci su ke ceton Isra'ilawa daga maƙiyansu.
Wadannan sunayen mazaje ne.
"jagora"
Kalmar "hatsari" na nufin maƙiyan da su ke koƙarin cutar da mutanen Isra'ila. AT: "Ya kuma kuɓutar da mutane Isra'ila daga miƙiyan su"
1Bayan da Ehud ya mutu, mutanen Isra'ila suka sake yin mugun abu a fuskar Yahweh.2Yahweh ya sayar da su ga hanun Yabin sarkin Kan'ana wanda ya yi mulki a Hazor. Babban shugaban rundunar sojojinsa shi ne Sisera, yana zaune a Haroshet Haggoyim.3Mutanen Isra'ila sun yi kira ga Yahweh domin taimako, saboda Sisera na da karusan ƙarfe guda ɗari tara ya kuma ƙuntata wa mutanen Isra'ila shekaru ashirin.4Debora kuwa, annabiya (matar Laffidot), tana jagoranci a matsayin mai sharia a Isra'ila a lokacin.5Ta kan zauna a ƙarƙashin itacen dabino na Debora tsaƙanin Ramah da Betel a tuddun ƙasar Ifraim, kuma mutanen Isra'ila na zuwa wurinta domin sassanta jayayya a tsakaninsu6Ta aika saƙo ga Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali. Ta ce masa, "Yahweh, Allahn Isra'ila, ya umarce ka, 'Jeka Tsaunin Tabor, tare da kai ka ɗauki maza dubu goma daga Naftali da Zabulun.7Zan ciro Sisera, shugaban rundunar sojojin Yabin, ya haɗu da kai a Kogin Kishon, tare da karusansa da sojojinsa, kuma Zan ba ka nasara a kansa."8Barak yace ma ta, "Idan za ki tafi tare da ni zan je, amma idan ba za ki tafi tare da ni ba, ba za ni ba."9Ta ce, "Zan tafi tare da kai tabbas. Ko da yake, hanyar da ka ke tafiya ba za ta kai ka ga martaba ba, domin Yahweh zai sayar da Sisera ga hannun mace." Sai Debora ta tashi tsaye ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh.10Barak ya yi kira ga mazan Zebulun da Naftali su zo tare a Kedesh. Maza dubu goma suka bi shi, kuma Debora ta tafi tare da shi.11Haber kuwa (Bakeniye) ya raba kansa daga Keniyawa - su zuriyar Hobab ne (surukin Musa) - ya kuma kafa rumfarsa a gefen itacen al'ul a Za'ananim kusa da Kedesh12Sa'ad da suka faɗa wa Sisera cewa Barak ɗan Abinowam ya hauro Tsaunin Tabor,13Sisera ya kira dukkan karussansa, karussan ƙarfe ɗari tara, da dukkan sojojin da ke tare da shi, daga Haroshet Haggoyim zuwa Kogin Kishon.14Debora ta ce da Barak, "Jeka! Domin wannan ranar ce Yahweh ya ba ka nasara a kan Sisera. Ashe ba Yahweh ne ke jagorantakar ka ba?" Sai Barak ya je gangare daga Tsaunin Tabor tare da maza dubu goma biye da shi.15Yahweh ya sa sojojin Sisera su ruɗe, dukkan karusansa, da dukkan sojojinsa. Mazajen Barak suka faɗa masu har Sisera ya sauko daga karusa ya gudu da ƙafa.16Amma Barak ya runtumi karusan da sojojin zuwa Haroshet Haggoyim, sai aka kashe dukkan sojojin Sisera da kaifin takobi, kuma babu mutumin da ya tsira.17Amma Sisera ya ruga a guje da kafa zuwa rumfar Ya'el, matar Heber Bakenine, gama akwai salama tsakanin Yabin sarkin Hazor, da gidan Heber Bakenine.18Ya'el ta fito ta sadu da Sisera sai ta ce masa, juyo, ubangijina; juyo gare ni kar ka ji tsoro." Sai ya juyo gare ta ya zo wurinta cikin rumfarta, sai ta rufe shi da bargo.19Ya ce mata, "In kin yarda ki ba ni ruwa kaɗan in sha, don ina jin ƙishi." Ta buɗe jakar fata ta madara ta ba shi ya sha, sai ta sake rufe shi.20Ya ce mata, "Tsaya a ƙofar rumfar. Idan wani ya zo ya tambaye ki, 'akwai wani a nan ne?', ki ce 'A a'."21Sai Ya'el (matar Heber) ta ɗauki turken rumfar da guduma a hannunta ta je gunsa a asirce, gama ya na cikin zurfin barci, sai ta kafa turken rumfar ta ɗora guduma har ta soke gefen kansa zuwa ƙasa, har ya mutu.22Yayin da Barak ke fakon Sisera, Ya'el ta je ta tarye shi ta ce masa, "Zo, Zan nuna maka mutumin da ka ke nema." Sai ya je tare da ita, sai ga Sisera kwance matacce, tare da turken rumfar a gefen kansa.23Don haka a ranar nan Allah ya yi nasara da Yabin, sarkin Kan'ana, a idon mutanen Isra'ila.24Ƙarfin mutanen Isra'ila ya ƙaru sosai gãba da Yabin sarkin Kan'ana, har suka hallakar da shi.
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 2:11.
A nan "hanu" na nufin iko da Yabin ke da shi a bisa Isra'ila. An yi maganar yadda Yahweh ya ba Yabin iko bisa sun kamar Yahweh ya sayad da su ne wa Yabin. AT: "Yahweh ya yaddar na Yabin sarkin Ka' anan ikon cin nasara a kan su"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Waɗannan sunayen birane ne
"karusan ƙarfe guda 900"
"shekaru 20"
Ana amfani da wannan kalmar wajen dakatar da wani sashin asalin labari. A nan marubucin na ba da bayanin karin haske game da Debora.
Wannan sunar mace ce.
Wannan sunan na miji ne
Allah ya kan zaɓi alƙalai su shugabanci Isra'ilawa a lokacin da suka shiga matsala bayan da su na cikin ƙasar Alkawari, kafin su ka samu sarakuna. Alƙalan ne a yawanci lokaci su ke ceton Isra'ilawa daga maƙiyansu.
A sa wa wannan Itacen sunar Debora.
Marubucin Littafin Alƙalai na kiran mutane, birni, tudu, da teku da sunayen su.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan sunan tsauni ne.
"maza 10,000"
A nan "Zan" na nufin Allah ne.
A nan "Sisera" na wakilce kansa da sojojinsa. AT: "ciro Sisera da sojojinsa"
sa mutane su tsira daga wani wuri
Wannan sunan teku ne.
Barak na tattaunawa da Debora.
Ana maganar zaɓin da Barak ya yi kamar yana zaɓen wani hanya ne na tafiya. "Martaba" kuma kamar masaukin da ake tafiya zuwa gareshi. AT: "ba wanda zai martaba ka domin abin da ka aikata"
A nan "hanu" na nufi ba ta ikon kashe shi. AT: "gama Yahweh zai sa mace da yi nasara da Sisera"
"maza 10,000"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 1:16
"mahaifin matar Musa"
Wannan sunan birni ne.
A nan ba wani takamame da ake nufi da "su". AT: "Sa'ad da wani ta faɗa wa Sisera"
a nan "karussansa" na wakilce sojojin da su ke tuƙin karussansa.
Domin Debora na da tabbacin nasara, tana magana kamar Barak ya riga ya yi nasara a yaƙin. AT: "Yahweh zai ba ka nasara"
Debora na wanar tambaya domin ta tunashe Barak cewa Yahweh na tare da su a yaƙin. AT: "Ka tuna, Yahweh ne ke jagorance ka."
"tare da 10,000"
"Yahweh ya hana sojojin Sisera tunani da kyau" ko "Yahweh ya sa sojojin Sisera su firgita"
A nan "Barak" na wakilce kansa da sojojinsa. AT: "Barak da sojojinsa"
A nan "takobi" na nufin takobi da sauran kayan yaƙi da sojojin su ka yi amfani da shi a yaƙi. Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Barak da sojojinsa sun kashe dukka sojojin Sisera da takobin su"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan sunar ta mace ne.
A nan "gida" na wakilce iyalinsa. AT: "Iyalin Heber Bakanine"
Ma'anar wannan shi ne canja tunani domin a huta daga tafiya. AT: "taho nan"
"Sisera ya cewa Ya'el"
Wani itace ne ko karfe mai tsinin baki kamar kusa, da ake bugawa ƙasa domin ya riƙe rumfa.
Kamar yadda mutum na wahala kafin ya fita daga rami mai zurfi, haka ma mutumin da ke barci mai zurfi baya tashiwa a sauki ba.
"ya huda rami"
"Barak na bi a guje" ko "Barak na bi a baya"
Ana maganar yadda Allah ya sa Isra'ilawa su ka yi nasara da Yabin kamar Allah ne da kansa ya yi nasara da Yabin sai mutanen Isra'ila na kallo.
"ƙarfin sojoji"
A nan "shi" na nufin Yabin ne da sojojinsa. AT: "su ka hallakar da Yabin da sojojinsa"
1A ranar nan ne Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa:2"Sa'ad da shugabanin suka ɗauki jagorancin Isra'ila, sa'ad da mutane cikin murna suka miƙa kai domin yaƙi - mu yabi Yahweh!3Ku saurara, ku sarakuna! Mai da hankali, ku shugabanni! Ni, Zan raira waƙa ga Yahweh, Allahn Isra'ila.4Yahweh, sa'ad da ka fito daga Se'ir, a sa'ad da ka tako daga Idom, ƙasa ta girgiza, kuma sammai sun yi makyarkyata; har giza-gizai sun zubo ruwa ƙasa.5Duwatsu na rawa a gaban Yahweh; har Tsaunin Sinai na rawa a gaban Yahweh, Allahn Isra'ila.6A kwanakin Shamgar (ɗan Anat), a kwanakin Ya'el, an ƙyale manyan hanyoyi, kuma waɗanda ke tafiya na yin amfani da ƙananan hanyoyin ne kurum.7Akwai jarumawa ƙaɗan ne a Isra'ila, har sai lokacin da ni Debora, na ɗauki matsayin shugabanci a Isra'ila - uwa ta ɗauki shugabancin a Isra'ila!8Sa'ad da suka zaɓi sababbin alloli, an yi faɗa a ƙofofin biranen amma duk da haka babu garkuwoyin yaƙi ko mãsu da aka gani a cikin mutum dubu arba'in a Isra'ila.9Zuciyata ta tafi ga shugabanin rundunar sojojin Isra'ila, tare da mutanen da a cikin murna suka miƙa kansu - mu yabi Yahweh domin su!10Yi tunani a kan wannan - ku masu hawan fararen jakuna kuna zaune a shinfiɗun ɗaurawa, da ku masu tafiya a hanyar.11Ji muryoyin waɗanda ke waƙa a cikin lambu. A wurin suke sake faɗin adalcin ayyukan Yahweh, da aikin adalcin jarumansa a Isra'ila. Sai mutanen suka sauko ƙasa zuwa ƙofofin birnin12Tashi, tashi, Debora! Tashi, tashi, ki raira waƙa! Tashi tsaye, Barak, ka kama 'yan kurkukunka, kai ɗan Abinowam.13Sai waɗanda suka tsira suka zo gun masu martaba; mutanen Yahweh suka zo gare ni tare da jarumawa.14Suka iso daga Ifraim, waɗanda asalinsu na Amalek ne; mutanen Benyamin sun bi ka. Daga Makir shugabanin yaƙi suka iso, daga Zebulun kuma waɗanda ke ɗauke da sandar hafsan.15Sarakunan da ke Issaka na tare da Debora; kuma Issaka na tare da Barak yana biye da shi da sauri har cikin kwari a bisa ga umurninsa. Cikin zuriyar Ruben ana ta nazari a zuci.16Me ya sa kuka zauna a tsaƙanin wuraren jin ɗumi, kuna sauraron makiyaya na wasa da sandunansu domin garkensu? Zuriyar Ruben dai suna ta nazari a zuci.17Giliyad ya tsaya a ƙeteren Yodan; kuma Dan, me ya sa yake ta zirgazirga a jiragen ruwa? Asha ya kasance a bakin teku ya kuma zauna kusa da babbar matsayar jiragen teku,18Zebulun kabila ce waɗanda suka sadaukar da rayukansu har ga mutuwa, har da Naftali ma, a filin yaƙi.19Sarakunan suka iso, suka yi faɗa; sarakunan Kan'ana suka yi faɗa a Ta'anak cikin ruwayen Megiddo, Amma ba su ɗauki azurfa a matsayin ganima ba.20Daga sammai, taurari suka yi faɗa, daga hanyoyinsu a ƙeteren sammai suka yi faɗa gãba da Sisera.21Kogin Kishon ya share su daga nan, wannan tsohon kogin, Kogin Kishon. Taka ya raina, ka yi ƙarfin hali!22Sai ƙarar kofaton dawakan - sukuwa, sukuwar jarumawansa.23'La'anta Meroz!' inji mala'ikan Yahweh. 'Tabbas la'anta mazaunanta! - saboda ba su zo sun taimake Yahweh ba - su taimaki Yahweh a yaƙi gãba da manyan jarumawa.'24An albarkaci Ya'el fiye da dukkan mata, Ya'el (matar Heber Bakenine), ita mai albarka ce fiye da dukkan matan da ke zama a rumfuna.25Mutumin ya biɗi ruwa, sai ta ba shi madara; ta kawo masa nono a akushin da ya cancanci a ba 'ya'yan sarki.26Ta sa hannunta a turken rumfa, da guduma a hannun damarta; da gudumar ta buge Sisera, ta ragargaza kansa. ta farfasa masa ƙwaƙwalwa sa'ad da ta soke shi ta gefen kansa.27Ya kasa tashi tsakanin tafinta, ya kwanta warwas a wurin. Tsakanin tafin kafafunta ya faɖi laƙwas. A wurin da ya ɓungire ne aka kashe shi ƙarfi da yaji.28Ta taga ta duba - mahaifiyar Sisera ta duba ta taga ta yi kira cikin baƙinciki, 'Me ya sa aka ɗauki tsawon lokaci karusansa basu iso ba? Me ya sa karar kofaton dawakan da ke jan karusansa suka yi jinkiri?'29Gimbiyoyinta masu hikima suka ba ta amsa, ita kuma ta ba kanta amsa irin tasu.30Ko basu samo ganima sun raba ba ne? - Mace, mata biyu domin kowanne mutum; ganimar kyawawan tufafi domin Sisera, tufafi masu tsada, kashi biyu na tufafi masu tsada domin wuyan waɗanda suka kwaso ganima?31Don haka bari dukkan maƙiyanka su lalace, Yahweh! Amma abokanka su zama kamar rana sa'ad da ta tashi a cikin ƙarfinta." Sai ƙasar ta sami salama shekaru arba'in.
Cikakiyar ma'anar wannan maganar na a fili kamar haka. AT: "A ranar nan da Isra'ilawa su ka yi nasara da sojojin Yabin"
"da mutanen su ka yarda su yi yaƙi"
Waƙar Debora da Barak sun ci gaba da yin amfani da waƙa
Wannan shi ne tsaunin a kan iyakar tsakanin Isra'ila da Idom
AT: "Duwatsu suka girgiza saboda tsoro"
A nan "fuskar" na nufi kasancewar Yahweh. AT: "A kasancewar Yahweh"
"a lokacin ruwar"
AT: "Ni, Debora, na fara shugabanci - Na kula da Isra'ilawa kamar yadda uwa take kula da 'ya'yanta"
AT: "Mutanen Isra'ila suna bauta wa sababbin alloli"
"mutum 40,000 a Isra'ila"
Kalmar "zuciya" na wakilce motsin zuciyar mutum. AT: "Ina jinjinawa shugabanin rundunar sojojin Isra'ila"
A nan "muryoyin" na wakilce mutane suna waƙa.
A nan "kofofin" na wakilce dukan birnin. AT: "An koma garuruwansu"
Kalmar "ni" na nufin Debora.
AT: "daga Ifraim, ƙasar inda zuriyar Amalekawa suka taba zama a can"
A nan "ka" na nufin mutane Ifraim. AT: "bi su"
AT: "shugabannin sojoji daga Zebulun"
A nan "da" na nufin Debora. AT: "Sarakunan da Issaka suna tare da ni"
A nan "Issaka" na nufin kabilar Issaka. AT: "kabilar Issaka yana tare da Barak"
A nan "zuciya" na wakilce tunani. AT: "akwai tattaunawa da yawa game abin da ya kamata su yi"
Wannan za a iya fassara ta a matsayin wata sanarwa. AT: "Kamata ya yi ku taimaka mana mu yi yaƙi, maimakon kasancewa a gida"
A nan "Giliyad" na wakilce mazajen Giliyad. AT: Mazajen Giliyad suka tsaya"
A nan "Dan" na wakilce mazajen Dan. AT: Mazajen Dan, meyasa suka ya"
AT: Mazajen Asha suka kasance"
A nan "sarkin" na wakilce kansa da sojojinsa. AT: "sarakunan da sojojinsu suka iso"
Waɗannan sunayen wurare ne.
abubuwan da aka tilasta da ƙarfi, yawanci a yaƙi ko ɓarayi
A nan "Sisera" na wakilce kansa da sojojinsa. AT: "Sisera da sojojinsa"
Dashike ruwa mai ƙarfi ta sauko, ta kuma sa ambaliya a rafin sai karusan suka maƙale a taɓo, sojojin dayawa kuwa suka nutse. AT: "Aka yi ambaliya a rafin Kishon da ya share sojoji Sisera"
A nan "rai" na nufin mutum ne gaba ɗaya. "a" na nufin Debora ne. AT: "Na ce da kai na taka da kuma karfin hali"
AT: "Sai na ji ƙarar dawakai suna gudu. Dawakan Sisera masu karfi suna guduwa"
gudu da sauri
"Meroz" na wakilce mutanen da suke zama a nan. AT: "La'anta mutanen Meroz"
Wannan sunar wani birni ne.
mutanen da suken zama a wannan wurin
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 4:17.
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 4:1.
"Man shanu" a nan madara ne. Wannan ne madara mafi kyau da mutanen Yael suka fi so. AT: "kawo masa madara"
Ma'anar wannan jimala ita ce cewa akushin mai kyaun gaske ne domin 'ya'yan sarki a ke ba su abubuwa mafi kyau.
"Yael ta kama turken rumfar da hannun hagun"
Ana iya bayana wannan wannan a cikakiyar jimla. AT: "ta kuma riƙe guduma a hannun damarta"
ba ko karfin motsi
AT: "ta kashe shi" ko "ya mutu"
Wannan tsari ne a taga da aka yi da katako.
Duk waɗannan tambayoyin na da ma'ana ɗaya. Ana iya haɗa waɗannan maganganu. AT: "Me ya sa Sisera ya ɗauki lokaci kafin ya iso gida"
Duk waɗannan na nufin Sisera ne. AT: "ɗauki Sisera ... Me ya sa ya"
"Gimbiya" 'yar sarki ce, amma sunar na iya nufin mashawaciyar iyalin sarki. AT: "mata masu hikima"
"ta kuma faɗa wa kanta abu ɗaya da su"
Matan sun yi amfani da tamtaya domin su jadada bangaskiyar su a kan cewa lalle haka ya faru. AT: "Suka samu ganima mai yawa har ya ɗauke su sawon lokaci suna rabawa."
Matan sun yi amfani da tamtaya domin su jadada bangaskiyar su a kan cewa lalle haka ya faru. AT: "Lalle ne a ba mace ko mata biyu ga kowani mutum ... ga waɗanda su ka kwaso ganima."
Mahaifiyar Sisera ta ba da gaskiya cewa sojojin Sisera sun kama mata dayawa. AT: "Kowani soja da mace ɗaya ko biyu"
"tufafi ma su tsada"
"Wuya" a nan na wakiltar sojojin Sisera. AT: "domin sojojin da su ka kwaso ganima su sa ka"
"bari waɗanda su ke ƙaunar Yahweh"
Mutanen Isra'ila na so su zama kamar rana da ta tashi, domin ba wani al'umman da sojojinta na da ikon hana rana tashiwa.
A nan "ƙasar" na wakilce mutanen Isra'ila. AT: "Mutane Israi'la ya zauna lafiya"
"na shekaru 40"
1Mutanen Isra'ila sun kuma yin abin da ke mugu a fuskar Yahweh, sai ya bada su ga hannun Midiyan na tsawon shekaru bakwai.2Ikon Midiyan ya ƙuntata wa Isra'ila. Saboda Midiyan, mutanen Isra'ila sun yi wa kansu mafaka a ramummuka a tuddai da kogonni da wuraren ɓoyewa.3Sai ya zamana a duk lokacin da Isra'ila suka shuka amfanin gona, sai Midiyanawa da Amelikawa da mutanen gabas su kai wa Isra'ila hari4Sukan sa mayaƙansu a ƙasar su lalatar da hatsi, har zuwa Gaza. Ba za su bar ko abinci a Isra'ila ba, ko tumaki, ko shanu, ko jakuna ba.5Sa'ad da suka iso da dabbobbinsu da rumfuna, sukan shigo kamar cincirundon fãri, kuma ya kan zama da wuya a ƙidaya mutanen ko raƙumansu, Sun farmaƙe ƙasar ne don su hallaka ta.6Midiyan sun rage ƙarfin Isra'ilawa ƙwarai har ya kai ga mutanen Isra'ila yin kira ga Yahweh.7Sa'ad da mutanen Isra'ila suka yi kira ga Yahweh saboda Midiyan,8Yahweh ya aiko annabi ga mutanen Isra'ila. Anabin ya ce masu, "Wannan ne abin da Yahweh, Allahn Isra'ila ya faɗi: 'Na kawo ku daga Masar; Na fitar da ku daga gidan bauta.9Na kuɓutar da ku daga hannun Masarawa, daga kuma hannun dukkan waɗanda ke muzguna maku. Na kore su daga gare ku, na kuma ba ku ƙasarsu.10Na ce da ku, "Ni ne Yahweh Ahllahnku; Na Umurce ku kada ku bauta wa allolin Amoriyawa, waɗanda a cikin ƙasarsu ku ke." Amma ba ku yi biyayya da muryata ba,"'11Yanzu kuwa Malai'kan Yahweh ya zo ya zauna a ƙarƙashin itacen rimi a Ofra, wanda yake na Yowash (Ba'abiyezare), sa'ad da Gidiyon, ɗan Yowash, ke bugun alkama a masussuka, a wurin matsar ruwan inabi - don ya ɓoye shi daga Midiyanawa.12Mala'ikan Yahweh ya bayyana gare shi ya ce masa, "Yahweh na tare da kai, kai jarumi mai ƙarfi!"13Gidiyon yace masa, "Kash, ubangijina, idan Yahweh na tare da mu, me yasa dukkan waɗannan abubuwan suke faruwa da mu? Ina dukkan ayyukan al'ajibansa da ubaninmu suka labarta mana, sa'ad da suka ce, 'Ba Yahweh ba ne ya kawo mu daga can Masar ba? Amma yanzu Yahweh ya yashe mu ya bayar da mu ga hannun Midiyanawa."14Yahweh ya dube shi ya ce, "Jeka cikin ƙarfin da ka ke da shi. Ka kuɓutar da Isra'ila daga hannun Midiyan. Ko ban aike ka ba ne?"15Gidiyon yace masa, "In ka yarda Ubangiji, ta yaya zan kuɓutar da Isra'ila? Duba, iyalina su ne mafi rashin ƙarfi a Manasse, kuma ni ne mafi ƙarancin muhimmanci a gidan mahaifina."16Yahweh yace masa, "Zan kasance tare da kai, kuma za ka yi nasara da dukkan sojojin Midiyanawa kai kaɗai kuwa."17Gidiyon yace masa, "Idan kana farinciki da ni, ka ba ni allamar cewa kai ne ka ke magana da ni.18In ka yarda, kar ka bar nan, sai na zo gare ka na kawo kyautata na ajiye a gabanka." Yahweh ya ce, "Zan jira sai ka dawo."19Gidiyon kuwa ya je ya shirya ɗan'akuya ya kuma auna gari misalin mudu guda, ya yi gurasa mara yisti. Ya sa nama a kwando, ya kuma sa romon a tukunya ya kawo su gare shi a ƙarƙashin itacen rimi, sai ya miƙa su.20Mala'ikan Allah ya ce masa, "Ɗauki naman da gurasa mara yisti ka sa su a wannan dutsen, ka kuma zuba romon a bisan su." Haka kuwa Gidiyon ya yi.21Sai mala'ikan Yahweh ya miƙo kan sandar da ke hannunsa. Da ita ya taɓa naman da gurasa mara yisti; Wuta kuwa ta fito daga dutsen ta cinye naman da gurasar mara yisti. Sai mala'ikan Yahweh ya tafi Gidiyon kuma bai kara ganin shi ba.22Gidiyon ya fahimci cewa wannan mala'ikan Yahweh ne. Gidiyon yace, Ah! Ubangiji Yahweh! Gama na ga mala'ikan Yahweh fuska da fuska!"23Yahweh yace ma sa, Salama a gareka! Kada ka ji tsoro, ba za ka mutu ba."24Sai Gidiyon ya gina bagadi a wurin domin Yahweh. Ya kira shi, "Yahweh salama ne." Har yau yana nan a Ofra ta iyalin Abiyeza.25A daren nan Yahweh yace masa, "Ka ɗauki bijimin mahaifinka, da bijimi na biyu mai shekara bakwai, kuma ka rurushe bagadin mahaifinka, ka sare Ashera da ke kusa da shi.26Ka gina wa Yahweh Allahnka bagadi a kan wannan wurin fakewa, ka gina shi da kyau. Ka miƙa bijimi na biyu a matsayin hadaya ta ƙonawa, kana amfani da itacen Ashera da ka sare."27Sai Gidiyon ya ɗauki goma daga cikin barorinsa ya yi dai dai yadda Yahweh ya faɗa masa. Amma saboda tsananin tsoron iyalin gidan mahaifinsa da mutanen gari bai yi shi da rana ba sai da dare.28Da sassafe lokacin da mutanen gari suka tashi, an kakkarya bagadin Ba'al, Ashera da ke kusa da shi kuma an datse shi, bajimi na biyu kuma an miƙa shi hadaya a kan bagadin da aka gina.29Mutanen gari suka ce da junansu, "wa ya yi wannan abu?" Da suka yi magana da waɗansu suka nemi amsoshi, suka ce, "Gidiyon ɗan Yowash ne ya yi wannan abu."30Daga nan sai mutanen gari suka ce da Yowash, Ka fiito da ɗanka domin a kashe shi, saboda ya rushe bagadin Ba'al, ya kuma datse Ashera da ke gefensa."31Yowash yace da dukkan mutanen da ke jayayya da shi, "Za ku yi hamayya domin Ba'al ne? Za ku cece shi ne? Duk wanda ya yi hamayya dominsa, bari a kashe shi da safe, Idan Ba'al allah ne, bari ya kare kansa sa'ad da wani ya rushe bagadinsa."32Saboda haka a ranan nan suka kira Gidiyon "Yerub Ba'al," domin ya ce, "Bari Ba'al ya kare kansa," domin Gidiyon ya rushe bagadin Ba'al.33Yanzu dukkan Midiyanawa da Amelikawa da mutanen gabas suka taru wuri ɗaya. Suka ƙetare kogin Yodan suka kuma kafa sansaninsu a kwarin Yezriyel34Amma Ruhun Yahweh ya sauko wa Gidiyon. Gidiyon ya busa ƙaho, yana kiran zuriyar Abiyeza, ko za su bi shi.35Ya aiki 'yan saƙo ga dukkan Manasse, kuma suma an kirawo su su bi shi. Ya kuma aiko da 'yan saƙo ga Asha da Zebulun da Naftali, suka kuma fito su tarbe shi.36Gidiyon yace da Allah, "Idan ka yi niyar ka more ni don ka ceci Isra'ila, kamar yadda ka faɗa -37Duba, Zan shimfiɗa ƙyallen ulu a masussuka. Idan da safe akwai raɓa a kan kyallen ulu kaɗai, amma ƙasa ta kasance a bushe, to zan sani cewa zaka more ni ka ceci Isra'ila kamar yadda ka ce."38Ga abin da ya faru - washegari Gidiyon ya tashi da sassafe, ya matse kyallen ulun wuri ɗaya, har ruwan raɓar daga kyallen ulun ya cika ƙwarya.39Sai Gidiyon yace da Allah, "Kada ka yi fushi da ni, Zan yi magana sau ɗaya kuma. In ka yarda ka bari in ƙara gwaji ɗaya kuma da ƙyallen ulun. Wannan karon, ka sa ƙyallen ulun ya bushe amma bari dukkan ƙasa ta kasance da raɓa.40Allah ya yi abin da ya roƙa a cikin daren nan. ƙyallen ulun ya bushe amma ƙasa ta kasance da raɓa kewaye da shi.
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 2:11.
A nan "Midiyan" na wakilce mutane Midiyan. Wato "hannun" na wakilce sarrafawa. AT: "da sarrafawa da Midiyawa"
wurare a cikin tsaunukan dutse wanda zai ba da mafaka
"Sojojin za su kafa rumfuna"
AT: "Duk lokacin da Midiyawa suka kawo dabbobinsu da rumfuna zuwa ƙasar Isra'ila"
Ana kwatanta Midiyawa da yawa kamar fara ta birgewa saboda sun zo da ɗimbin mutane. Wato dabbobinsu ke kwance duk ciyayi.
Wannan karin magana ne. AT: "ya yi addu'a ga Yahweh neman taimako"
A nan "Midiyan" na wakilce mutane Midiyan. AT: "saboda Midiyawa"
AT: "wurin da kake kasance bayi"
Kalmar "hannu" na wakilce iko ko sarrafawa
A nan "muryata" tana wakilce abin da Yahweh ya umarta. AT: "biyayya umarni na"
Ana amfani da wannan kalmar wajen dakatar da wani sashin asalin labarin. Mai ba da labari ya fara ba da ɓangaren labarin.
Wannan sunan gari ne.
Wannan shi ne mutane kungiyar mai suna bayan kakansu Abiyeza.
"ya tafi da shi"
Kalmomin "ya ba mu cikin" yana nufin cewa Yahweh ya ƙyale Isra'ilawa su ci su da Midiyawa.
"Yahweh da dube Gidiyon"
AT: "Ni, Yahweh, zan aike ka"
A nan "gida" na wakilce iyali. AT: "a iyalin mahaifina"
Wannan karin magane ne. "Kasance tare da kai" na nufin Yahweh zai taimaka kuma ya albarkace Gidiyon.
AT: "a sauƙaƙe kamar kuna fada da mutum ɗaya ne"
"sanya shi a gabanka"
"ya kawo su gare mala'ikan Allah
"ya ɓace"
Kalmar "Ah" a nan na nufin cewa Gidiyon ya firgita kwarai.
Wannan na nufin zuwa lokacin da aka rubuta Littafin Alƙalai.
"da ke kusa da bagadin Ba'al"
"sanya duwatsu a cikin tsari"
Wannan na nufin umarnin Yahweh ne a cikin Alƙalai 6:25-26.
"tashi daga gado"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "mu kashe shi azaba"
AT: "Bai kamata ku kare Ba'al ba."
Wannan kuma sunan Gidiyon ne. Yana nufin "bari Ba'al ya kare kansa"
AT: "suka hallara a matsayin sojoji"
Wannan karin magana ne. AT: "ya yi amfani da Gidiyon"
AT: "ko za su bi shi zuwa yaƙi"
Duk waɗannan suna wakilce mutanen kowace kabila ne. AT: "ga kabilan Asha, Zebulun, da Naftali"
AT: "wannan zai zama alama daga gare ku, sa'an nan zan sani cewa za ku"
"Gidiyon ya tashi daga gado"
1Sai Yerub Ba'al (wato Gidiyon) ya tashi da sassafe, da dukkan mutanen da ke tare da shi, sai suka yi sansani a gefen rafin Harod. Zangon Midiyan kuwa na ɓangaren arewa da su a kwari kusa da tuddun Moreh.2Yahweh yace da Gidiyon, "Ana da sojoji fiye da yadda nake so domin in ba ka nasara kan Midiyanawa, don kar Isra'ila ta yi taƙama a kaina, cewa, 'Ikonmu ne ya cece mu.' Yanzu kuwa, ka shaida a cikin kunuwan mutanen ka ce,3'Duk wanda ya ke jin tsoro, duk wanda ke rawar jiki, bari ya koma ya tashi daga Tsaunin Giliyad."' Sai mutane dubu ashirin da biyu suka tafi, dubu goma kuma suka rage.4Sai Yahweh yace da Gidiyon, "Mutanen sun yi yawa har yanzu, Kai su wurin ruwa, Ni kuma zan rage yawansu domin ka a wurin. Idan nace maka, 'Wannan zai tafi da kai,' zai tafi da kai; amma idan na ce, 'Wannan ba zai tafi da kai ba,' ba zai tafi ba."5Sai Gidiyon ya kawo mutanen wurin ruwan, Yahweh kuma ya ce masa, "Ware duk wanda ya lashi ruwan, kamar yadda kare ke lasa, daga waɗanda suka durƙusa ƙasa suka sha."6Mutum ɗari uku suka lasa.7Yahweh yace da Gidiyon, "Da mutum ɗari ukun da suka lashi ruwa, zan 'yantar da kai in ba ka nasara a kan Midiyanawa. Sai kowanne mutum ya koma wurinsa."8Saboda haka waɗanda aka zaɓa suka ɗauki kayayyakin aiki da kakakinsu. Gidiyon ya komar da mazan Isra'ila, kowanne zuwa rumfarsa, amma ya keɓe mutum ɗari uku. Midiyanawan kuwa sun yi zango a ƙasa da shi a cikin kwari.9A wannan daren Yahweh ya ce masa, "Tashi! ka kai wa sansanin hari, domin zan ba ka nasara a kansa.10Amma idan kana tsoron gangarawa kai kaɗai, ka tafi tare da Fura, baranka,11sai ka ji abin da suke faɗi, ƙarfin halinka kuma ya ƙarfafa har ka kai hari a sansanin." Sai Gidiyon ya tafi da Fura baransa, zuwa ƙofar sansanin.12Midiyanawa, da Amelikawa da dukkan mutanen gabas suka yi shiri a kwarin, yawansu kamar cincirindon fãra. Raƙumansu sun fi ƙarfin a ƙirga; sun fi yashin teku yawa.13Sa'ad da Gidiyon ya iso wurin, wani mutum ya na gaya wa abokinsa mafarkin da ya yi. Mutumin yace, "Duba! Na yi mafarki, sai na ga dunƙulen gurasar bali mai fuskar waina ta na gangarawa zuwa sansanin Midiyanawa. Ta iso rumfar, ta kuma buge ta da ƙarfi har sai da ta faɗi ta juyad da rumfar, ta kuma kwantar da ita ƙasa.14Sai ɗaya mutumin ya ce, "Wannan ba komai ba ne ban da takobin Gidiyon (ɗan Yowash), Ba'isra'ile. Allah ya ba shi nasara a kan Midiyan da dukkan sojojinsu."15Sa'ad da Gidiyon ya ji yadda aka sake faɗin mafarkin da fasararsa, ya russuna ƙasa ya yi sujada. Ya koma sansanin Isra'ila ya ce, "Ku tashi tsaye! Yahweh ya ba ku nasara a kan sojojin Midiyan."16Ya raba mutun ɗari uku kashi uku, sai ya ba dukkansu kakaki da gorunan da ba kome a ciki, sai cocila.17Ya ce masu, "Dube ni ku yi abin da na yi. Duba! Sa'ad da na iso gab da iyakar sansanin, dole ku yi abin da na yi.18Sa'ad da na busa kakaki, Ni da duk waɗanda ke tare da ni, sai ku busa naku kakakin har a dukkan gefen sansanin gaba ɗaya kuma ku yi ihu, 'Domin Yahweh da kuma domin Gidiyon!'"19Sai Gidiyon da mazaje ɗari uku waɗanda ke tare da shi suka iso gabashin sansanin, misalin ƙarfe goma na dare. Dai-dai lokacin da Midiyanawan na canjin masu gadi, suka busa kakaki suka kuma farfasa gorunan da ke hanuwansu20Rundunoni ukun suka busa kakaki suka kuma farfasa gorunan. Suka riƙe tociloli a hannayen hagunsu da kuma kakaki a hannayen damarsu don su busa su. suka yi ihu, "Takobin Yahweh da na Gidiyon."21Kowanne mutum ya tsaya a wurinsa a kewaye da sansanin sai dukkan sojojin Midiyanawa suka tsere suka yi ihu suka ruga a guje.22Sa'ad da suka busa kakaki ɗari ukun, Yahweh ya sa kowanne sojan Midiyanawa ya ɗauki takobi gãba da ɗan'uwansa da kuma gãba da dukkan sojojin. Sojojin suka tsere ta Bet Shitta har zuwa Zerera, harma ga iyakar Abel Mehola, kusa da Tabbat.23Aka kira mazajen Isra'ila daga Naftali da Asha, da dukkan Manasa, suka kuma fafari Midiyan.24Gidiyon ya aiki masu ba da saƙo a ko'ina a duk tuddun ƙasar Ifraim, cewa, "A gangara gãba da Midiyan a mamaye Kogin Yodan, har faɗin Bet Bara, a tsayar da su." Saboda haka dukkan mutanen Ifraim suka taru suka kuma mamaye ruwayen, har zuwa Bet Bara da Kogin Yodan.25Suka cafko 'ya'yan sarakuna biyu na Midiyan wato Oreb da Ze'eb. Suka kashe Oreb a dutsen Oreb, suka kuma kashe Ze'eb a wurin matsar ruwan Inabi ta Ze'eb. Suka bi bayan Midiyanawa, suka kuma taho da kawunan Oreb da Ze'eb ga Gidiyon, wanda ke a keteren Yodan.
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 6:32
Waɗannan sunayen wurare ne.
AT: "a gare ni in ba ka damar zama nasara bisa Midiyawa"
A nan "kunnuwa" na nufin mutum gaba ɗaya. AT: "ka yi shela ga mutane"
Waɗannan jumla suna nufin abu ɗaya ne.
AT: "10,000 mutane ko mazaje suka rage"
A nan "kamba " na wakilce sojojin. Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "A can, zan nuna maka yadda ake rage adadin maza"
a sha ruwa ta hanyar lasar tare da harshe
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "don haka ne waɗanda Yahweh ya zaɓa"
AT: "Ku yi yaki da Midiyawa a cikin sansaninsu, domin zan taimake ku nasara a kansu"
Wannan sunan mutum ne.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "abin da kuka ji zai karfafa ku"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "raƙumansu suna da yawa da ba za a iya ƙididdige su ba"
AT: "Allah zai taimaka wa Isra'ilawa su ci Midiyawa"
"mazaje 300"
AT: "Mu yi yaƙi domin Yahweh da kuma domin Gidiyon"
A nan "takobi" yanan nufin yaƙinsu. AT: "Mu yi yaƙi domin Yahweh da kuma domin Gidiyon"
AT: "Yahweh ya sa kowane Midiyawa ya yi yaƙi da 'yan'uwansa sojojin"
Waɗannan sunayen garuruwa da birane ne.
Wannan sunan gari ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
1Mutanen Ifraim suka ce da Gidiyon, "Mene ne wannan da ka yi mana? Ba ka kira mu ba sa'ad da ka tafi wurin faɗa da Midiyan." Daga nan sai suka yi gardama mai zafi da shi.2Sai ya ce da su, "Me na yi idan a ka kwatanta da ku?" Kalar inabin Ifraim, ba ta fi cikakken girbin inabin Abiyeza ba?3Allah ya ba ku nasara a kan 'ya'yan sarakunan Midiyan -- Oreb da Ze'eb! Wacce riba na ci idan an kwatanta da ku?" Sai fushinsu ya huce sa'ad da ya faɗi masu haka.4Gidiyon ya zo ya haye Yodan, shi da mutane ɗari uku da ke tare da shi. Sun gaji, amma duk da haka ba su fasa bi ba.5Ya ce da mutanen Sukkot, "Idan kun yarda ku ba mutanen da suka biyo ni dunƙulen gurasa, gama sun gaji, domin ina bin sawunsu Zeba da Zalmunna sarakunan Midiyan."6Sai shugabannin suka ce, "Hannuwan Ziba da Zalmunna suna hannunka ne a yanzu? Me zai sa mu ba sojojin ka gurasa?"7Gidiyon yace, "Idan Yahweh ya ba mu nasara a kan Zeba da Zalmunna, zan yayyaga maku fata da ƙayayuwan sahara da tsabgogi."8Ya wuce zuwa Feniyel ya yi magana ga mutanen can ma, mutanen Feniyel masu ka ba shi amsa dai-dai da ta mutanen Sukkot.9Shi kuma ya yi magana da mutanen Feniyel ya ce, "Idan na dawo cikin salama, zan rushe wannan hasumiyar."10Zeba da Zalmunna kuwa suna Karkor tare da sojansu, wajan mutum dubu goma sha biyar, dukkan waɗanda suka rage a sojojin mutanen Gabas, gama mutane 120,000 waɗanda a ka koyar a yaƙi da takobi sun faɗi.11Gidiyon ya yi gaba kan hanyar da mazauna rumfa, ya wuce Nabo da Yogbeha. Ya ci nasara a kan sojojin abokan gãba, da yake ba su yi zaton za a kawo masu hari ba.12Zeba da Zalmunna suka gudu, Gidiyon kuma ya bi su, ya kamo sarakunan Midiyan su biyu - Zeba da Zalmunna - ya sa sojojinsu cikin ruɗami.13Gidiyon ɗan Yowash ya dawo daga yaƙi, ya bi ta Heres.14Ya gamu da wani saurayi daga mutanen Sukkot, ya nemi shawara daga wurinsa. Shi kuma ya baiyana masa game da shugabannin Sukkot da dattawansu mutum saba'in da bakwai.15Gidiyon ya zo ya sami mutanen Sukkot, ya ce "Da su ga Zeba da Zalmunna, da ku ka yi mani ba'a a kansu cewa, ka riga ka kama Zeba da Zalmunna ne?" Ba mu sani wai sai mun ba sojojinka gurasa ba.16Gidiyon ya ɗauki dattawan ya hori mutanen Sukkot da ƙayayuwa.17Ya rushe hasumiyar Feniyel ya kashe mutanen wannan birnin.18Sa'an nan Gidiyon yace da Zeba da Zalmuna, "Wadanne irin mazaje ku ka kashe a Tabor"? Suka amsa, "Kamar yadda ka ke haka su ke, kowannensu kamar ɗan sarki ya ke."19Gidiyon yace, 'Yan'uwana ne, 'ya'yan mamata ne. Muddin Yahweh na raye, da ba ku kashe su ba, ni ma da ba zan kashe ku ba."20Ya ce da Yeter (ɗansa na fari), "Tashi ka karkashe su!" Amma matashin bai zaro takobinsa ba, yana jin tsoro, saboda shi yaro ne.21Sai Zeba da Zalmunna suka ce, "Tashi ka kashe mu kai da kan ka! gama yadda mutum yake, haka ƙarfinsa yake." Gidiyon ya tashi ya kashe Zeba da Zalmunna, kuma ya ɗauke kayan adon da ke a wuyan raƙumansu.22Mutanen Isra'ila suka ce da Gidiyon, "Ka yi mulkin mu da kai - da 'ya'yanka da jikokinka,- saboda ka cece mu daga hannun Midiyan."23Gidiyon yace da su, "Ni ba zan mulke ku ba, ɗana kuma ba zai mulke ku ba. Yahweh ne zai yi mulkinku.24Gidiyon yace da su, "Zan roƙe ku: abu ɗaya, kowannenku ya ba ni ɗankunne daga abin da ya samu ganima." (Midiyanawa su na da 'yankunne na zinariya saboda su "ya'yan Isma'ila ne.)25Suka amsa suka ce, "Da farinciki za mu baka su". Suka yi shimfiɗa, kowannen su ya buɗe ganimarsa suka yi ta jefa 'yan kunnen a kan ta daga cikin ganima.26'Yankunnen da ya buƙata, nauyinsu shekel 1,700 na zinariya ne. Wannan ganimar ƙari ee a kan kayan adon sarakunan Midiyan wato tufafinsu na shunaiya. Da kuma sarƙoƙin da ake sawa a wuyan raƙumansu.27Gidiyon ya yi falmara da 'yankunnen da yakarɓa yasa a cikin birnisa, a Ofra, dukkan Isra'ila suka yi karuwanci ta wurin yi masa sujada a can. Wannan ya zama tarko ga Gidiyon da waɗanda ke cikin gidansa.28Mutanen Isra'ila suka mallake Midiyanawa, kuma basu ƙara tada kansu ba. Ƙasar ta zauna cikin salama shakara arba'in a cikin kwanakin Gidiyon.29Yerub Ba'al ɗan Yowash ye je ya zauna a cikin gidansa.30Gidiyon yana da 'ya'ya saba'in a zuriyarsa, da yake yana da mata da yawa.31Ƙwarƙwararsa wadda ke a Shekem ma ta haifa masa ɗa, Gidiyon kuma ya ba shi suna Abimelek.32Gidiyon ɗan Yowash ya mutu cikin shekarun tsufa masu kyau, aka bizne shi cikin kabarin Yowash ubansa, na kabilar Abiyeza.33Bayan mutuwar Gidiyon mutanen Isra'ila suka koma karuwanci ta wurin bautawa Ba'aloli, sun maida Ba'al Berit allahnsu.34Mutanen Isra'ila ba su tuna su girmama Yahweh Allahnsu ba, wanda ya kuɓutar da su daga hannun abokan gãbarsu ta kowanne gefe.35Ba su kiyaye alƙawuransu ga gidan Yerub Ba'al ba (wato Gidiyon), sakamakon dukkan abin kirki da ya yi a Isra'ila.
Wannan za a iya fassara ta a matsayin wata sanarwa. AT: "Ba ku yi mana adalci ba"
"sai suka yi muhawara da shi"
Gidiyon ya amsa wa mutanen Ifraim
AT: "Na yi kaɗan kaɗan aka kwatanta da abin da kuka yi"
"ya ragu"
"mazaje 300"
AT: "sun ci gaba da bin maƙiyansu"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
A nan "hannuwa" suna nufin dukkan jiki.
AT: "Babu dalilin da zai sa mu ba sojojinsu ka gurasa"
A nan Gidiyon na wakilce kansa da sojojinsa. AT: "Suka bar a can" ko "Gidiyon da ɗari uku mazajensa suka bar a can"
Wannan sunan wurin ne.
AT: "Bayan na fatattaki sojojin Midiyawa gaba ɗaya"
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 6:11
Wannan sunan birni ne.
"mutum 15,000"
"mutane dubu ɗari da ashirin"
AT: "Gidiyon da sojojinsa ya ci nasara"
Waɗannan sunayen garuruwa ne.
Wannan shi ne matsanancin tsoro ko damuwa
AT: "ya yi masa tambayoyi game da shugabannin"
AT: "Gidiyon da sojojinsa ya suka ɗauki dattawan ya hori mutanen Sukkot da ƙayayuwa"
"Su ma kamar kai ne"
Wannan magana kalmar rantsuwa ce ta addini da aka yi amfani da ita don jaddada cewa abin da zai kusan faɗi gaskiya ne. AT: "Na yi maku alƙawarin cewa"
Wannan karin magana ne. AT: "Wannan aikin yana buƙatar mutum ya yi shi"
AT: "kai da zuriyarka bayan ka mutu"
"Gidiyon yace da mazajen Isra'ila"
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 5:19
A nan marubucin na ba da bayayin karin haske game da Midiyawa.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "sarakunan Midiyawa sun sa waɗannan kayan"
AT: "Isra'ilawa sun yi zunubi bisa Yahweh ta hanyar bauta wa da falmaran a wurin"
AT: "Wannan ya zama jaraba ga Gidiyon da iyalinsa"
AT: "Mutanen Isra'ila sun zauna lafiya"
"a lokacin rayuwar Gidiyon"
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 6:32.
Wannan karin magana ne. AT: "lokacin da ya tsufa"
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 6:11.
Wannan sunan wani allahn ƙarya ne.
"wanda ya kewaye su"
AT: "iyalin Yerub Ba'al"
1Abimelek ɗan Yarub Ba'al, ya tafi wajan 'yan'uwan mamarsa a Shekem, ya ce da su da dukkan dangin mamarsa,2"Idan ka yarda ka fadi wannan domin dukkan shugabannin Shekem su ji, 'Wanne ya fi a gare ku, dukkan 'ya'ya saba'in na Yerub Ba'al su yi mulki a kanku ko kuwa guda ɗaya ya mulke ku?' Ku tuna ni ƙashinku ne da jikinku."3Dangin mamarsa suka yiwa shugabannin Shekem magana a kansa, suka amince, gama suka ce, "Shi ɗan'uwanmu ne"4Suka ba shi azurfa guda saba'in daga gidan Ba'al Berit, Abimelek kuma ya yi anfani da ita ya gaiyato mutane marasa ɗa'a da rashin hankali suka yi tafiya tare da shi.5Abimelek ya tafi gidan ubansa a Ofra ya yi makokin 'yan'uwansa su saba'in, 'ya'yan Yerub Ba'al a bisa wani dutse. Yotam ƙaraminsu kaɗai ya rage cikin 'ya'yan Yerub Ba'al, gama ya ɓoye kansa.6Dukkan shugabannin Shekem da Bet Millo suka zo suka taru suka maida Abimelek ya zama sarki daura da rimi, kusa da ginshiƙi wanda ke cikin Shekem.7Sa'ad da Yotam ya ji haka, ya tafi ya tsaya a kan Tsaunin Gerizim. Ya tada murya ya ce da su, "Ku saurare ni, ku shugabannin Shekem, ko Allah ya ji ku.8Itatuwa suka je domin su naɗa sarki. Gama sun ce da itacen zaitun ka zama sarkinmu,'9Amma itacen zaitun yace da su, 'In dena ba da maina da ake anfani da shi ana girmama alloli da mutane, in kuma dawo wurin sauran itatuwa?'10Itatuwan suka ce da itacen ɓaure, 'Kazo ka yi mulkin mu,'11Amma itacen ɓaure yace da su, 'Zan bar zaƙina da 'ya'yana masu kyau, domin in dawo in dogara ga sauran itatuwa?'12Itatuwa suka ce da inabi, 'Kazo ka yi mulkin mu,'13Inabi ya cewa, 'Zan bar ba da sabon ruwan anab ɗina mai ƙarfafa alloli da mutane, in dawo in dogara ga sauran itatuwa?'14Sai dukkan itatuwa suka ce da ƙaya, 'Ki zo ki yi mulkin mu.'15Sai ƙaya ta ce da itatuwa, 'Idan gaskiya ne kuna so ku naɗa ni sarauniya a bisanku, sai kowannenku ya zo ya sami wuri a ƙarƙashin inuwata. Idan ba haka ba, bari wuta ta fito daga cikin ƙaya ta ƙone rimi na Lebanon.16To yanzu, idan dai gaskiya ne kun yi aminci, da kuka sa Abimelek ya zama sarkinku, idan kun yi abin da ya wajaba ga Yerub Ba'al da gidansa, kuma kun yi masa horon da ya kamata -17- da tunanin ubana ya yi faɗa dominba, ya sa ransa cikin hatsari ya kuɓutar da ku daga hannun Midiyan -18amma yau kun tashi gãba da gidan ubana, kun kashe 'ya'yansa saba'in a bisa dutse ɗaya. Sa'an nan kun maida Abimelek ɗan baiwarsa ya zama sarkin shugabanin Shekem, da yake shi ɗan'uwanku ne.19Idan dai kun yi gaskiya da girmamawa ga gidan Yerub Ba'al, to ku yi farinciki da Abimelek shi ma ya yi farinciki da ku.20Amma idan ba haka ba ne, bari wuta ta fito daga cikin Abimelek ta cinye mutanen Shekem da na Bet Millo. Bari wuta ta fito daga mutanen Shekem da Bet Millo ta cinye Abimelek.21Yotam ya gudu ya tafi ya gudu ya tafi Biya. Ya zauna a can da ya ke nesa ta ke da Abimelek, ɗan'uwansa.22Abimelek ya yi mulkin Isra'ila shekaru uku.23Sai Yahweh ya aiko da mugun ruhu tsakanin Abimelek da shugabannin Shekem. Shugabannin Shekem suka juyawa Abimelek baya.24Yahweh ya yi haka ne domin a rama muguntar da aka yi a kan 'ya'yan Yerub Ba'al su saba'in, aka kuma lissafta muguntar a kan Abimelek ɗan'uwansu. Haka kuma aka lissafta muguntar kisan a kan shugabannin Shekem saboda sun taya Abimelek ya kashe 'yan'uwansa maza.25Shugabannin Shekem suka sa mazaje su yi masa kwanton ɓauna, suka yiwa dukkan masu wucewa fashi a kan hanyar. Aka kaiwa Abimelek rahoton wannan abu.26Ga'al ɗan Ebed yazo shi da 'yan'uwansa suka je Shekem. Shugabannin Shekem kuwa sun amince da shi.27Suka je cikin gona suka kakkaryo kuringar anab domin su bi ta kai. Suka yi buki a gidan allahnsu, suka ci suka sha, suka la'anci Abimelek.28Ga'al ɗan Ebed ya ce, "Wane ne Abimelek, kuma wane ne Shekem da za mu bauta masa? Shi ba ɗan Yerub Ba'al ba ne? Zebul ba jami'in sa ba ne? Ya bautawa mutanen Hamor, uban Shekem! Me zai sa mu bautawa Abimelek?29Dama mutanen nan ƙarƙashi na suke! In fitar da Abimelek. In ce da Abimelek, 'Ka kira dukkan sojanka dukka.'"30Sa'ad da Zebul, jami'in birni, ya ji maganar Ga'al da Ebed, ya ji haushi sosai.31Ya aika da 'yan saƙo zuwa ga Abimelek domin ya ruɗe shi, cewa, "Duba, ga Ga'al ɗan Ebed da 'yan'uwansa suna zuwa Shekem, suna kuma zuga birnin gãba da kai.32Ka tashi idan dare ya yi, kai da sojojin da ke tare da kai ku yi masu kwanton ɓauna a cikin daji.33Da safiya ta yi, sa'ad da rana ta fito, ka shiga ka kaiwa birnin hari. Idan shi da mutanensa suka taso maka, ka yi masu abin da ka ga dama."34Abimelek ya tashi daddare, suka kasu huɗu suka yiwa Shekem kwanton ɓauna.35Ga'al ɗan Ebed ya tashi ya tsaya a ƙofar birni. Abimelek da mazajen da ke tare da shi suka fito daga inda suke a ɓoye.36Da Ga'al ya ga mazajen, ya ce da Zebul, "Duba ga mutane na gangarowa daga kan duwatsu!" Zebul ya ce da shi, "Kana ganin inuwoyi a kan duwatsu ne kamar mutane."37Ga'al ya ƙara cewa, "Duba mutane suna gangarowa daga tsakiyar ƙasa, wani kashi kuma na zuwa ta hanyar rimi na masu duba."38Sai Zebul ya ce da shi, "Ina maganarka ta fankama yanzu, 'Kai da ka ce wane ne Abimelek da zamu bauta masa?' Waɗannan ba su ne mazajen da ka rena ba? Ka fita yanzu ka yi faɗa da su."39Ga'al ya jagoranci mazajen Shekem, suka yi faɗa da Abimelek.40Abimelek ya kore shi, Ga'al ya gudu daga gabansa. Da yawa suka faɗi da raunuka kafin mashgin ƙofar birni.41Abimelek ya tsaya a Aruma, Zebul ya kori Ga'al da 'yan'uwansa daga cikin Shekem.42Washegari mutanen Shekem suka fita cikin jeji, a ka kaiwa Abimelek rahoton haka.43Ya ɗauki mazajensa ya raba su uku, su ka yi kwanton ɓauna a jeji. Ya ga mazajen suna fitowa daga cikin birni, ya kai masu hari ya kashe su.44Abimelek da ƙungiyoyin da ke tare da shi suka kai hari suka toshe ƙofar birni. Sauran kungiyoyi biyu suka kaiwa waɗanda ke cikin jeji suka kashe su.45Abimelek ya yi faɗa da birnin dukkan yini, ya ci birnin ya kashe mutanen da ke cikinsa. Ya rushe ganuwar birnin ya barbaɗa mata gishiri.46Sa'ad da shugabannin hasumiyar Shekem suka ji, suka shiga babbar maɓoya ta gidan El-Berit.47Aka kaiwa Abimelek labari cewa dukan shugabannin sun taru a hasumiyar Shekem.48Abimelek tare da mazajen da ke tare shi suka hau Tsaunin Zalmon. Abimelek ya ɗauki gatari ya datso rassa. Ya ɗora a kafaɗarsa ya ummurci mazajen da ke tare da shi. "Abin da ku ka ga na yi, ku yi sauri kowa ya yi."49Haka kowannen su ya saro rassa suka bi Abimelek. Suka tara su jikin hasumiyar birni, suka sa wuta, dukkan mutanen da ke hasumiyar Shekem suka mutu, kusan su dubu maza da mata.50Sai Abimelek ya tafi Tebez, ya ya kafa sansani a Tebez ya mallake ta.51Amma akwai wata hasumiya mai karfi a birnin, dukan mazaje da mata suka shiga cikin ta suka kulle kansu. Sa'an nan sai suka hau can kan hasumiyar.52Abimelek yazo wurin hasumiyar da faɗa, ya zo kusa kofar domin ya ƙone ta.53Amma wata mace ta sako nuƙunyar dutsen niƙa a kan Abimelek ta fasa masa kwanya.54Nan da nan ya kira saurayin da ke ɗaukar masa kayan yaƙi ya ce masa, "Ka zaro takobinka ka kashe ni, domin kada a ce, 'mace ce ta kashe shi.'" Sai saurayin ya soke shi, ya mutu.55Sa'ad da mazajen Isra'ila suka ga Abimelek ya mutu, sai suka koma gida.56Yahweh ya ɗauki fansa a kan Abimelek saboda muguntar da ya yi ta kashe 'yan'uwansa su saba'in.57Yahweh ya mai da muguntar mutanen Shekem ta koma kan su, da la'anar Yotam ɗan Yerub Ba'al.
A nan "ƙashinku ne da jikinku" na wakilce kasancewa dangi ne. AT: "Ni memba ne a cikin iyalinku"
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 8:33
"tashin hankali da wawaye"
Wannan sunan wurin ne.
Yotam ya fara ba da wani misali inda itatuwa ke wakilce ƙungiyoyin mutane daban-daban.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Lokacin da Yotam ya ji cewa Abimelek ya kashe saba'in 'yan'uwansa"
A cikin wannan misali Yotam ya bayyana itatuwa yin abubuwan da cewa mutane suka yi.
Don "motsa daga gefe zuwa gefe" na nufin don matsar da baya da kuma fitar a cikin iska. A nan itaciyar ta yi amfani da wannan kalmar don nuna "sarauta bisa."
Wannan shi ne wani daji tare da da yawa kaifi tsininnuka a kan rassanta.
AT: "a zauna lafiya"
AT: "Idan kun yi abin da yake dai-dai kuma Yerub Ba'al ya cancanci ku kashe duk 'ya'yansa maza.
A nan "gida" na wakilce iyali. AT: "iyalin mahaifina"
A nan "shi" na nufin Gidiyon.
AT: "Amma idan ba ku yi wa Yerub Ba'al da iyalinsa dai-dai ba"
Yotam yana magana la'ana. Ya yi magana game da mutanen Shekem da Bet Millo suna lalata Abimelek.
Wannan sunan birni ne.
Wannan nufin Allah ya aiko da baƙin ruhu ya sa matsala a tsakanin Abimelek da shugabannin Shekem.
"sun aiki mutane su ɓuya a kan tuddai da jira don kai farmaki Abimelek"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
AT: "sun dogara shi"
"murƙushe"
AT: "Kada mu bauta wa Abimelek"
Wannan sunan mutum ne.
"Ina so na mulki da mutanen Shekem"
AT: "ya yi fushi sosai"
AT: "sun rinjayi mutanen birnin su tayar maka"
"don ɓoye da kai farmaki da ba zato ba tsammani"
"dukan mazajen da suke yaƙi da Abimelek"
"rabuwa zuwa kungiyoyi huɗu"
Zebul yana ƙoƙarin rikitar da Ga'al kuma ya hana shi shirya yaƙi. AT: "Wancan ba mutane ba, sune inuwoyi ce kawai a kan tuddai"
"Ba ku da girman kai yanzu"
Wannan karin magana ne. AT: "mutane da yawa sun mutu sakamakon raunuka"
Wannan sunan birni ne.
A nan "ya" na nufin Abimelek wanda yake wakilta kansa da dukkan sojojinsa. AT: "suka farmaki"
A nan Abimelek na wakilce kansa da sojojinsa.
Yaɗa gishiri yana hana wani abu tsiro a can.
Wannan shi ne allahn ƙarya wanda ya ke "Ba'al-Berit" a cikin Alƙalai 8:33.
Wannan yana nufin tunzura rassan tare a cikin babban tsibin.
Wannan sunan birni ne.
"suka kafa sansani a wajen birnin Tebez"
Wannan yana nufin cewa saurayin ya sa takobi dama ta hanyar a cikin jikin Abimelek.
Wannan karin magana ne. AT: "Yahweh ya hukunta mutanen Shekem saboda muguntar da suka aikata"
1Bayan Abimelek, Tola ɗan Fuwa ɗan Dodo, mutumin Issaka wanda ya zauna a Shamir, a ƙasar duwatsu ta Ifraim, ya taso domin ya ceci Isra'ila.2Ya alƙalanci Isra'ila shekara ashirin da uku. Ya mutu aka binne shi a Shamir.3Ya'ir Bagiliyade ya bi bayansa, ya yi alƙalancin Isra'ila shekara ashirin da biyu.4Yana da 'ya'ya talatin, masu hawan jakuna talatin, suna da birane talatin, waɗanda a ke kira Habbot Ya'ir har zuwa yau, suna cikin ƙasar Giliyad.5Ya'ir ya mutu a ka binne shi a cikin Kamon.6Mutanen Isra'ila suka ƙara a kan muguntar da suka yi a idanun Yahweh, suka bautawa Ba'al, da Ashtoret allolin Aram, da allolin Sidon, da allolin Mowab da allolin mutanen Amon da allolin Filistiyawa. Suka watsar da Yahweh suka dena bauta masa.7Yahweh ya yi fushi da mutanen Isra'ila, ya sayar da su a hannun Filistiyawa da Amoniyawa.8Suka ragargaza Isra'ila suka gallaza masu azaba a wannan shekara, shekara goma sha takwas suna gallazawa mutanen Isra'ila waɗanda suke a ƙetaren Yodan a ƙasar Amoriyawa wadda ke cikin ƙasar Giliyad.9Sai Amoniyawa suka ƙetare Yodan garin su yi faɗa da Yahuda, da Benyamin da gidan Ifraim, domin a wulaƙanta Isra'ila.10Sa'an nan mutanen Isra'ila suka yi kira ga Yahweh, suka ce, "Mun yi maka zunubi da yake mun watsar da kai mun bautawa Ba'al."11Yahweh yace da mutanen Isra'ila, "Ban ceto ku daga Masarawa da Amoriyawa da Amoniyawa da Filistiyawa12da kuma Sidoniyawa ba?" Amelikawa da Ma'oniyawa waɗanda suke gallaza maku; kuka kira ni na, ceto ku daga ikonsu.13Duk da haka kuka watsar da ni kuka bautawa waɗansu alloli. Saboda haka ba zan ƙara wani lokaci na ceton ku ba.14Ku tafi wurin allolin da ku ke bautawa. Sai su kuɓutar da ku idan kuna da damuwa."15Mutanen Isra'ila suka ce da Yahweh, "Mun yi zunubi. Ka yi mana abin da ya yi maka kyau. Sai dai idan ka yarda ka cece mu yau."16Suka rabu da baƙin allolin da ke tare da su, suka yi sujada ga Yahweh. Daga nan ne Yahweh bai ƙara riƙe damuwarsu ba.17Sa'an nan Amoniyawa suka taru suka kafa sansani a Giliyad. Isra'ilawa kuma suka taru suka kafa sansaninsu a Mizfa.18Shugabannin Giliyad suka ce da junansu, "Wane ne zai fara yin faɗa da Amoniyawa? Shi ne zai zama shugaba a kan dukkan mazauna Giliyad."
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"ya zama shugaba ya ceci Isra'ila"
A nan "alƙalanci" na nufin shi ne ya shugabanci mutanen Isra'ila.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Ya'ir Bagiliyade ya kasance shugaba bayan Tola"
Wannan yanki ne wanda aka sanya wa suna bayan mutum.
Wannan yana nufin zuwa lokacin da aka rubuta Littafin Alƙalai.
Wannan sunan wurin ne.
AT: "Sun ci gaba da yi abin da Yahweh ya ce mugunta ne"
A nan bayana fushin Yahweh kamar wutar da ke ci. AT: "Yahweh ya yi fushi da mutanen Isra'ila kwarai"
AT: "Yahweh yarda wa Filistiyawa da Amoniyawa kayar da Isra'ilawa"
"Yahuda" da "Benyamin" na nufin mutanen wadanda kabilan. AT: "mutanen daga kabilar Yahuda ... mutanen daga kabilar Benyamin"
A nan "gida" na nufin mutanen daga kabilar Ifraim. AT: "mutanen daga kabilar Ifraim"
AT: "don haka Isra'ilawa kuwa suka wahala sosai"
Wannan yana nufin cewa mutanen Isra'ila sun yi ta roƙon Yahweh don neman tamaiko.
Waɗannan sune mutanen daga zuriyar ko iyalin Ma'on.
AT: "Zan ba ci gaba da ceton ku kuma da sake"
AT: "Yahweh kuwa bai so mutanen Isra'ila su ƙara shan wahala ba"
"Wanene zai jagoranci sojojinmu don su yi yaƙi da Amoniyawa?"
1Sai ga Yafta mutumi Giliyad babban mayaƙi ne, amma ɗan karuwane. Giliyad ne ubansa.2Matar Giliyad ta haifa masa waɗansu 'ya'ya, sa'ad da suka yi girma sai suka kori Yafta daga gidan, suka ce masa, "Ba zaka gaji kome a iyalinmu ba. Kai ɗan wata mata ne."3Sai Yafta ya gudu daga wurin 'yan'uwansa, ya tafi ya zauna a ƙasar Tob. Mutane marar sa ɗa'a suka haɗu da Yafta, suka tafi tare da shi.4Bayan waɗansu kwanaki, mutanen Amon suka yi yaƙi da Isra'ila.5Sa'ad da mutanen Amon suka yi yaƙi da Isra'ila, sai shugabannin Giliyad suka je suka dawo da Yafta daga ƙasar Tob.6Suka ce da Yafta, "Zo ka zama shugabanmu domin mu yi faɗa da mutanen Amon."7Yafta yace da shugabannin Giliyad, "Kun ƙi ni kun kore ni daga gidan ubana. Me ya sa kuka zo wurina yanzu da kuka sami damuwa?"8Shugabannin Giliyad, suka ce da Yafta, "Shi yasa muka zo wurin ka yanzu, ka zo muje ka yi faɗa da mutanen Amon, za ka zama shugaba a kan dukan mazauna a Giliyad."9Yafta yace da Shugannin Giliyad, "Idan ku ka kawo ni gida domin in yi faɗa da mutanen Amon, idan Yahweh ya ba mu nasara a kan su, zan zama shugabanku."10Shugabannin Giliyad suka ce da Yafta, "Yahweh ya zama shaida tsakanin mu da kai idan ba mu yi yadda muka ce ba."11Sai Yafta ya tafi tare da shugabannin Giliyad, mutanen suka sa ya zama jagora da shugaban sojojinsu. Sa'ad da yake a gaban Yahweh a Mizfa, Yafta ya maimaita dukkan alƙawuran da ya yi.12Daga nan Yafta ya aika jakadu wurin sarkin mutanen Amom, cewa, "Wacce matsala ce tsakaninmu da ku? Me ya sa kuka zo ku ƙwace kasarmu?13Sarkin mutanen Amon ya amsa wa jakadun Yafta, "Saboda lokacin da Isra'ila suka fito daga Masar, sun ƙwace ƙasarmu daga Arnon zuwa Yabbok har zuwa Yodan. Yanzu ku maido mana da ƙasarmu cikin salama."14Yafta ya sake aikawa da jakadu wurin sarkin mutanen Amon,15ya ce, "Ga abin da Yafta ke cewa: Isra'ila ba su ɗauki ƙasar Mowab da ƙasar mutanen Amon ba,16amma Isra'ila sun fito daga Masar suka bi ta jeji zuwa Tekun Iwa zuwa Kadesh."17Sa'ad da Isra'ila suka aika jakadu zuwa sarkin Idom, cewa, 'Idan ka yarda ka bari mu wuce ta ƙasarka', amma sarkin Idom bai saurare su ba. Suka kuma aika da jakadu wurin sarkin Mowab, amma ya ƙi, sai Isra'ila suka tsaya a Kadesh.18Sai suka bi ta jeji su kewaye ƙasar Idom da ƙasar Mowab, sai suka bi ta gabas da ƙasar Mowab, suka raɓi ƙasar Arnon suka sauka. Amma ba su je yankin Mowab ba, da ya ke Arnon iyakar Mowab ce.19Isra'ila suka aika da jakadu wurin Sihon, sarkin Amoriyawa, wanda yake mulki a Heshbon; Isra'ila suka ce masa, 'Idan ka yarda ka bari mu bi ta ƙasarka mu je wurin da ke namu.'20Amma Sihon bai amince da Isra'ila su bi ta yankinsa ba. Sai Sihon ya tattara sojojinsa ya zakuɗa zuwa Jahaz, can ya yi faɗa da Isra'ila.21Yahweh, Allah na Isra'ila, ya ba da Sihon da mutanensa a hannun Isra'ila suka yi nasara a kan su. Isra'ila suka mallaki ƙasar Amoriyawa waɗanda ke zaune a wannan, ƙasar.22Suka mallake komi da komi na ƙasar Amoriyawa tun daga Arnon har zuwa Yabbok, daga jeji kuma har zuwa Yodan.23Haka kuma Yahweh, Allah na Isra'ila ya kori Amoriyawa a gaban mutanen Isra'ila, ko yanzu kuma za ku mallake ƙasarsu?24Ba zaku mallaki ƙasar da Kemosh, allahnku yake ba ku ba? Domin haka duk ƙasar da Yahweh Allahnmu ya ba mu za mu mamaye ta.25Yanzu ka fi Balak ɗan Ziffo, sarkin Mowab ne? Ya taɓa yin jayayya da Isra'ila ne? Ya taɓa yin yaƙi da su ne?26Sa'ad da Isra'ila suka zauna a Hesbon da ƙauyukanta shekara dari uku, da Arowa da ƙauyukanta, da kan iyakokin Arnon - meyasa ba ka mallake su a wancan lokaci ba?27Ni ban yi maka laifi ba, kai ne ka yi mani laifi da ka kawo mani hari. Yahweh mai shari'a, yau zaya hukunta tsakanin mutanen Isra'ila da mutanen Amon."28Amma sarkin mutanen Amon ya yi ƙi gargaɗin da Yafta ya aika masa.29Sai Ruhun Yahweh ya sauko kan Yafta, ya ratsa ta Giliyad da Manasse, ya kuma ratsa ta Giliyad ɗin Mizfa, daga Giliyad ɗin Mizfa ya bi ta mutanen Amon.30Yafta ya yi alƙawari da Yahweh ya ce, "Idan ka ba ni nasara a kan mutanen Amon, idan na dawo cikin salama,31duk abin da ya fito daga ƙofofin gidana ya tarbe ni zai zama na Yahweh, zan miƙa shi hadaya."32To sai Yafta ya bi ta wurin mutanen Amon ya yi faɗa da su, Yahweh kuma ya ba shi nasara.33Yakai masu hari ya yi babban kisa tun daga Arowa har zuwa Minnit - birane ashirin - da zuwa Abel Keramim. Ta haka mutanen Amon suka zauna a ƙarƙashin mutanen Isra'ila.34Yafta ya koma gidansa a Mizfa, sai ga ɗiyarsa ta fito tarbarsa da kayan kiɗi da rawa. Ita kaɗai ce ɗiyarsa, banda ita ba shi da wani ɗa ko ɗiya.35Da dai ya gan ta ya yage tufafinsa ya ce, "Haba ɗiyata! Kin sa ni nukura, kin sa mani jin zafi a raina! Gama nayi alƙawari ga Yahweh, ba zan iya janye alƙawarina ba.36Ta ce masa "Babana, Ka yi wa Yahweh alƙawari, ka yi mani ko mene ne ka yi wa Yahweh alƙawari gama Yahweh ya ɗaukar maka fansa a kan abokan gabarka, Amoniyawa.37"Ta cewa babanta, "Bari wannan alƙawari ya zauna a kaina, ka bani wata biyu da zan je kan duwatsu in yi kukan budurcina ni da ƙawayena."38Ya ce da ita. "Jeki." Ya bata wata biyu. Ta tafi, ta bar shi ta tafi ita da Ƙawayenta suka yi kukan budurci a cikin tuddai.39Bayan watanni biyun ta dawo wurin babanta, wanda da ita bisa ga alƙawari na wa'adi. Ita kuwa ba ta san namiji ba, wannan ya zama al'ada a cikin Isra'ila40'yan'matan Isra'ila kowacce shekara sukan ɗauki kwanaki huɗu, suna maimaita labarin ɗiyar Yafta Bagiliyade.
"Lokacin da 'ya'yan matar Giliyad suka zama manya"
Wannan sunan yanki ne.
"suka bi shi" ko "sun tafi ko'ina tare"
"wani lokacin daga baya"
"domin mu iya yaƙi mutanen Amon"
A nan "gida" na nufin mutanen da suke zaune a gidan. AT: "iyalin ni"
Waɗannan kalmomin biyu nufin abu aya ne. AT: "shugaban"
Yana nufin alƙawuran da Yafta ya yi wa shugabannin Giliyad.
Yefta yana tambayar sarki dalilin da ya sa ya yi fushi da Isra'ila.
Kalmar "ku" na nufin Sarkin Amon wanda ke wakiltar kansa da sojojinsa. AT: " Me yasa kai ku da sojojinsa kuka zo mu ɗauki kasarmu?
Waɗannan sunayen kogin ne.
AT: "sun bar ƙasar Masar"
AT: "A lokacin da shugaban Isra'ila suka aika jakadu"
Wannan karin magana ne na nufin "a ki". AT: "ki amincewa da buƙatarsu"
Waɗannan sunayen birane ne.
A nan kalmar "ya" na wakilce Sihon da sojojinsa. AT: "can sukan yi faɗa da Isra'ila"
A nan "hannun" tana nufin iko don kayar a yaƙi. AT: "Yahweh ya ba da ikon Isra'ila a kan Sihon da duka mutanensa"
A nan, Yefta yana tsauta wa sarkin Amoniyawa. AT: "Sai dai ku mallaki ƙasar da Kemosh, allahnku, yake ba ku."
Wannan shi ne sunan da allahn ƙarya.
A nan, Yefta yana tsauta wa sarkin Amoniyawa. Wannan za a iya fassara ta a matsayin wata sanarwa. AT: "Ba ka fi Balak, ɗan Ziffo, wanda shi ne sarkin Mowab."
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan sunan birni ne.
Wannan karin magana ne. AT: "ni bi da ku ba dai-dai ba ... kai bi da ni ba dai-dai ba"
Wannan karin magana ne. AT: "Ruhun Yahweh ya dauki iko da Yefta"
AT: "ya tattara mazaje don sojojinsa, ya haye Giliyad da Manasse ... daga Mizfa ta Giliyad"
Waɗannan sunayen birane ne.
Wannan shi ne an yi da ke nuna baƙin ciki mai girma.
Yefta ya faɗi wannan maganar a cikin hanyoyi biyu don ya nanata cewa ya yi baƙin ciki kwarai.
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "Yahweh ya ɗauki fansa a kan maƙiyanku, Amoniyawa"
1Kira ya zo ga mazajen Ifraim, suka bi ta Zafon suka ce da Yafta, "Meyasa ka wuce ka yi faɗa da mutanen Amon baka ce mu zo mu tafi tare da kai ba? Za mu ƙone gidanka a kan ka."2Yafta ya ce da su, "Ni da mutanena muna da babbar matsala da mutanen Amon. Sa'ad da na kira ku baku cece ni daga wurinsu ba."3Sa'ad da naga ba ku cece ni ba, sai na sa raina da ƙarfina na wuce gãba da su, kuma Yahweh ya ba ni nasara. Meyasa kuka zo ku yi faɗa da ni yau?4Yafta ya tattaro dukan mazajen Giliyad ya yi faɗa da Ifraim. Mazajen Giliyad suka kai hari ga mazajen Ifraim saboda sun ce, "Ku Giliyadawa masu gudu ne na cikin Ifraim - da Ifraim da cikin Manasse."5Giliyadawa suka kama magangarun Yodan masu kaiwa Ifraim. Idan wani wanda ya tsira na Ifraim ya zo yace, "Bari in haye kogin", sai mazajen Giliyad su ce da shi, "Kai Ba'ifrane ne?" Idan ya ce, "A'a,"6sai su ce da shi ka ce, "Shibbolet," idan ya ce, "Sibbolet" (gama ba zai iya fadin kalmar dai-dai ba), Giliyadawa sai su kama shi su kashe shi a magangarun Yodan. Mutanen Ifraim dubu arba'in da biyu aka kashe a wannan lokacin.7Yafta ya yi alƙalanci a Isra'ila shekara shida. Sa'an nan Yafta ya mutu aka bizne shi a cikin ɗaya daga biranen Giliyad.8Bayan shi Ibzan na Betlehem ya yi alƙalancin Isra'ila.9Yana da 'ya'ya talatin. Ya aurar da 'ya'ya mata talatin, kuma ya kawo wa 'ya'yansa 'yan'mata talatin, daga waje. Ya yi alƙalancin Isra'ila shekara bakwai.10Ibzan ya mutu aka bizne shi a Betlehem.11Bayan shi Ilon mutumin Zebulun ya yi alƙalanci a Isra'ila, ya yi alƙalancin Isra'ila shekara goma.12Ilon mutumin Zebulun ya mutu aka bizne shi a Aijalon cikin ƙasar Zebulun.13Bayan shi, Abdon ɗan Hillel Ba-firatone ya yi alƙalancin Isra'ila.14Yana da 'ya'ya arba'in da jikoki talatin. Suna hawan jakai saba'in, ya yi alƙalancin Isra'ila shekara takwas.15Abdon dan Hillel Ba-firatone ya mutu aka bizne shi a Firaton cikin ƙasar Ifraim a ƙasar duwatsu ta Amelikawa.
AT: "Mazajen Ifraim da aka kira tare sojojinsu"
Wannan sunan birni ne.
Wannan shi ne karin magana ne; tana nufin ƙone gidan da mutanen da ke ciki.
A nan, Yefta yayi amfani da "ni" don nuna kansa da kuma dukkan mutanen Giliyad.
AT: " Yahweh ya ba mu nasara bisa su"
Ana iya bayyana ma'anar wannan zagi. AT: "Ku Giliyadawa, ku baƙi ne a nan"
"kaiwa da ƙasar Ifraim"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Giliyadawa suka kashe mutanen Ifraim dubu arba'in da biyu a wannan lokacin"
Wannan sunan mutumin Betlehem ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Firaton shi ne sunan wurin. Ana kiran wani daga wannan wurin a Ba-firatone.
Waɗannan maza mallakar jakai saba'in.
1Mutanen Isra'ila suka sake yin aikin mugunta a fuskar Yahweh, kuma ya bayar da su a hannun Filistiyawa shekara arba'in.2Akwai wani mutumin Zorah, na iyalin Danawa, sunansa Manowa. Matarsa ba ta iya ɗaukar juna biyu saboda haka bata haihu ba.3Mala'ikan Yahweh ya baiyana ga matar ya ce da ita, "Duba, baki iya kin ɗauki juna biyu ba, kuma baki haihu ba, amma za ki sami juna biyu, za ki haifi ɗa.4Duba, kada ki sha ruwan inabi, kada ki ci abu marar tsarki.5Duba za ki sami juna biyu, za ki haifi ɗa. Ba za a yi anfani da reza a kansa ba, gama yaron zai zama Naziri ga Yahweh tun daga cikin ciki. Shi zaya fara kuɓutar da Isra'ilawa daga hannun Filistiyawa."6Matar ta je ta gaya wa mijinta, "Wani mutumin Yahweh, ya zo wurina, kamanninsa kamar na mala'ikan Yahweh, da ban razana ƙwarai. Ban tambaye shi daga inda ya fito ba, kuma bai faɗa mani sunansa ba.7Ya ce da ni, "Duba! Za ki yi juna biyu za ki haifi ɗa. Kada ki sha ruwan inabi ko wani abin sha mai ƙarfi, kada ki ci abin da shari'a ta ce ba shi da tsarki, gama yaron zai zama Naziri ga Yahweh tun daga cikin ciki har ranar mutuwarsa."8Sai Manowa ya yi addu'a ga Yahweh, ya ce, "Ya Yahweh, idan ka yarda ka sake aiko da wannan mutum domin ya koya mana yadda za mu yi da yaron da za a haifa ba da daɗewa ba."9Yahweh ya saurari muryar Manowa, kuma sai mala'ikan Yahweh ya zo wurin matar lokacin da ta ke zaune a fili. Amma mijinta Manowa ba ya tare da ita.10Sai matar ta yi gudu da sauri ta gaya wa mijinta, "Duba! Mutumin ya baiyana gare ni, wanda ya zo wuri na waccan ranar!"11Manowa ya tashi ya bi matarsa. Sa'ad da ya zo wurin mutumin, ya ce, "Kai ne mutumin da ya yi magana da matata?" Mutumin yace, "Ni ne."12Sai Manowa yace, bari maganganunka su zama gaskiya. Mene ne zai zama ka'idodi game da yaron, kuma mene ne zai zama aikinsa?"13Mala'ikan Yahweh ya ce da Manowa, "Dole ta yi hankali ta yi dukan abin da na faɗa mata.14Kada ta ci kowanne abu da ya fito daga kuringa, kada ta sha ruwan inabi ko abin sha mai ƙarfi; kada ka bari ta ci kowanne abinci da shari'a ta ce ba shi da tsarki. Ta yi biyaiya da dukan abin da na ummurce ta ta yi."15Manowa yace da mala'ikan Yahweh, "Idan ka yarda ka ɗan jira, ka ba mu lokaci mu shirya maka 'yar burguma."16Sai mala'ikan Yahweh yace da Manowa, "Ko na tsaya ba zan ci abincinku ba. Idan kun shirya hadaya ta ƙonawa, ku miƙa ta ga Yahweh." (Manowa bai san cewa shi mala'ikan Yahweh ne ba.)17Manowa yace da mala'ikan Yahweh, "Mene ne sunanka, domin mu darajanta ka, idan kalmominka suka zama gaskiya?"18Mala'ikan Yahweh ya ce masa, "Meyasa ka ke tambayar sunana? Shi ne abin mamaki!"19Sai Manowa ya ɗauki 'yar akuya da baiko na hatsi ya miƙa su a dutsen Yahweh. Ya yi wani abin mamaki Manowa da matasa suna kallo.20Sa'ad da harshen wuta ya tashi sama daga bagadin, mala'ikan Yahweh ya tafi sama cikin harshen wuta na bagadin. Da ganin haka Manowa da matarsa suka faɗi da fuskokinsu a ƙasa.21Mala'ikan Yahweh bai ƙara baiyana ga Manowa ba ko matarsa. Sa'an nan ne Manowa ya sani mala'ikan Yahweh ne.22Manowa yace da matarsa, "Ba shakka za mu mutu da ya ke mun ga Yahweh!"23Matarsa ta ce da shi, "Da Yahweh ya so ya kashe mu, da bai karɓi baiko na ƙonawa da hatsin da muka ba shi ba. "Da bai nuna mana dukkan waɗannan abubuwan ba, ko ya bari mu ji waɗannan abubuwa a wannan lokaci."24Daga baya, matar ta haifi ɗa, aka kira sunansa Samsin. Yaron ya yi girma, Yahweh ya albarkace shi.25Ruhun Yahweh ya fara ƙarfafa shi a cikin Mahane Dan, tsakanin Zora da Eshtawol.
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 2:11
A nan "hannun" na nufin iko don samun nasara a yaƙi . AT: "Yahweh yarda Filistiyawa kayar da Isra'ilawa"
Wannan sunan gari a cikin Isra'ila.
mutanen daga kabilar Dan
Wannan sunan mutum ne.
Wani abu da Yahweh yace bai dace a ci ba.
A nan kalmar "kai" na nufin ya gashi. Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Babu wanda ya kamata taba yanka masa gashi"
AT: " A Naziri ne wanda ke keɓewa ga Allah"
Wannan yana nuna cewa Allah ne ya aiko mutumin. Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "Wani mutum ne Allah ya aiko"
A nan "mummunan" yana nufin "tsoratarwa". AT: "Na ji tsoronsa domin yana kama da mala'ikan Allah"
AT: "duk rayuwarsa"
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "ya zo wurin matar Manowa"
Wannan yana nufin mala'ikan Allah a Alƙalai 13:3.
"abin da kuka faɗa"
A nan, mala'ikan yana maganar duk wani abinci da yake girma akan itacen inabi kamar "yana zuwa" daga itacen inabi. AT: "duk abin da yake girma akan itacen inabi"
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "dafa ɗan akuya a gare don ku ci"
Mala'ika ya tambaye wannan tambayar a matsayin tsauta. AT: "Bai kamata ku tambaye ni menene sunaba ba"
AT: "Shi ne fiye da mai ban mamaki a gare ku ka fahimci"
"Mala'iki yayi abin mamaki"
Wannan alama ce ta girmamawa. Amma kuma ya nuna tsoron da suke yi wa Yahweh.
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "Allah zai sa mu mutu saboda mun gan shi"
Matar Manowa ta faɗi dai-dai wannan abu sau biyu don ƙarfafawa.
"ya zama ya girma" ko "lokacin da ya balaga"
AT: Ruhun Yahweh kuwa ya fara yin amfani da Samsin"
Wannan sansani ne na ɗan lokaci kabilar Dan suka zaune a ciki.
Wannan sunan gari ne.
1Samsin ya je Timna, a can ya ga wata mata, ɗiyar Filistiyawa.2Sa'ad da ya dawo ya ce da babansa da mamarsa, "Na ga wata mata a Timna, ɗaya daga cikin 'ya'yan Filistiyawa. Sai ku ɗauko mani ita ta zama mata ta."3Babansa da mamarsa suka ce da shi, "Ba wata mata a cikin 'ya'yan danginka, ko cikin dukkan mutanen mu?" Za ka ɗauko mata daga Filistiyawa marasa kaciya?" Samsin yace da babansa, "A ɗauko ta domi na, idan na dube ta, ta gamshe ni."4Amma babansa da mamarsa ba su sani ba wannan daga wurin Yahweh ne, domin ya yi shirin ƙulla husuma da Filistiyawa (gama a wannan lokaci Filistiyawa ne ke mulki a Isra'ila).5Samsin ya gangara zuwa Timna tare da babansa da mamarsa, suka zo gonakin Timnah. Sai ga wani ɗan zaki ya taso masa ya na ruri.6Ruhun Yahweh ya zo kansa ya yayyaga ɗan zakin kamar ɗan akuya, kuma ba komi a hannunsa. Amma bai gaya wa babansa ko mamarsa abin da ya yi ba.7Ya je ya yi magana da matar, sa'ad da ya dube ta ta gamshi Samson.8Bayan 'yan kwanaki da ya dawo ya aure ta, ya juya ya dubi gawar zakin. Sai ga kututun zuma a cikin abin da ya rage na gawar zakin.9Ya yagi zuman ya tafi, yana tafiya ya na ci. Ya zo wurin babansa da mamarsa ya ba su su ma suka ci. Amma bai gaya masu ya samo zuman daga abin da ya rage na jikin gawar zakin ba ne.10Baban Samsin ya je wurin da matar ta ke, Samson ya yi buki a wurin gama wannan ita ce al'adar samarin.11Da dai danginta suka gan shi suka kawo masa abokai talatin su zauna tare da shi.12Samsin ya ce masu, "Bari in gaya maku wani karin magana. Idan wani a cikin ku ya gaya ma ni ma'anarsa cikin kwanakin nan bakwai na biki, zan ba da rigunan lilin guda talatin da suturu guda talatin.13Amma idan ba ku iya ba ni amsa ba, za ku ba ni rigunan lilin talatin da suturu guda talatin. Suka ce da shi, "Ka faɗa mana karin maganarka mu ji."14Ya ce da su, "A cikin maciyi, akwai abin da za a ci; a cikin mai ƙarfi akwai abu mai zaƙi." Amma baƙinsa ba su iya gano amsar cikin kwana uku ba.15A kan rana ta huɗu suka ce da matar Samsin, "Ki zolayi mijinki domin ya gaya mana amsar karin maganar, ko kuma mu ƙone gidan mahaifinki. Kin gaiyato mu nan ne domin ki mai da mu marasa anfani?"16Matar Samsin ta fara yin kuka a gabansa ta ce, "Dukkan abin da ka ke yi ƙi na! Ka ke yi ba ka ƙauna ta. Ka gaya wa waɗansu mutanena karin magana, amma ba ka gaya mani amsar ba." Samsin yace da ita, "Duba nan, abin da ban gaya wa babana ko mamata ba, sai in gaya maki?"17Dukkan kwanakin nan bakwai na buki ita tana ta kuka. Ta matsa masa ƙwarai, a rana ta bakwai ya gaya mata amsar. Ita kuma ta gayawa dangin mutanenta amsar.18A rana ta bakwai kafin rana ta faɗi, mazajen garin suka ce da shi, "Me ya fi zuma zaƙi? Me ya fi zaki ƙarfi? Samsin yace da su, "Da ba domin kun yi huɗa da karsanata ba, da ba ku gano amsar karin maganata ba."19Sai Ruhun Yahweh ya zo kan Samsin da iko. Samsin ya je Ashkelon ya kashe mazajen su guda talatin. Ya kwashe ganimarsu, ya bada tufafinsu ga waɗanda suka baiyana masa karin zaurancensa. Ya tafi gidan ubansa cikin fushi mai zafi.20Aka bada matar Samsin ga babban abokinsa.
Wannan sunan birni a cikin Kwarin Sorek.
Wannan karin magana ne. Samsin yana neman iyayensa suyi magana da iyayen matar game da aure. AT: "Yi shiri domin ni ya aure ta"
Suna yin wannan tambayar don bayar da shawarar cewa Samsin zai iya samun mace tsakanin mutanensu. Wannan za a iya fassara ta a matsayin wata sanarwa. AT: "Tabbas akwai mata daga cikin mutanen mu da zaku iya aura"
AT: "Yanzu shiri domin ta ya zama matata"
Kalmomin "ya zo" na nufin cewa Ruhun Yahweh ya rinjayi Samsin. Anan, Ruhun ya sa Samsin karfi sosai. AT: "Ruhun Yahweh ya sa Samsin karfi sosai"
"tsage shi kashi biyu"
AT: "ba shi da makami"
Wannan na nuna yana zaton tana da kyau sosai.
Wannan ya nuna cewa ya bar hanyar ya yin wani abu ne.
AT: "ya sami wani taro na ƙudan zuma"
AT: "Mahaifin Samsin ya tafi inda matar ta zama"
Wannan wasa ne wanda dole ne 'yan wasa su nemo ansar tambayar mai wuya.
nemo ma'anar da wasa
Samsin ya gaya wa karin magana.
"Wani abun ci ya fito daga wani abu da ke cin abinci"
"Wani abu mai daɗi ya fito wani abu mai ƙarfi"
Wannan na nufin yaudarar wani ya aikata abin da ba sa son yi.
Wannan kalmar "ƙone" na nufin ƙona wani abu gaba ɗaya.
Matar Samsin ta fadi dai-dai wannan abu sau biyu don ƙarfafawa. AT: "Ba kwa ƙaunar da ni ko kaɗan"
Samsin ya tsawata ta ga tambayar shi ya gayi amsar. Wannan za a iya fassara ta a matsayin wata sanarwa. AT: "Ban ma gaya wa mahaifina ko mahaifiyata ba. Ba zan gaya muku ba."
Ma'anar yiwu: 1) "a kwana bakwai ɗin bikinsu" ko 2) "sauran kwanakin bakwai na bikinsu."
AT: "ta ci gaba da roƙonsa ya gaya mata"
Wannan na nufin dangin matar Samsin. AT: "samari" ko "dangin ta"
AT: "idan baku yi amfani da matata ba"
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 14:6.
abubuwan da aka tilasta da ƙarfi, yawanci a yaƙi ko ɓarayi
"mai matukar sosai"
1Bayan waɗansu kwanaki, a lokacin girbin alkama, sai Samsin ya ɗauki 'yar akuya ya tafi domin ya ziyarci matarsa. Ya ce a ransa, "Zan shiga ɗakin matata." Amma mahaifinta bai bar shi ya shiga ba.2Sai mahaifinta yace, "Tabbas na zaci ka ƙi jininta, sai na bayar da ita ga abokinka. Ai ƙanwarta ta fi ta kyau, ko kuwa? Sai ka ɗauke ta a maimakonta."3Samsin yace masu, "Wannan karon ba ni da hakkin Filistiyawa duk zafin da zan sa masu game da wannan al'amari."4Samsin ya tafi ya kamo diloli ɗari uku ya ɗaura su biyu-biyu, bindi da bindi. Sai ya ɗauko gaushen wuta ya ɗaɗɗaura a tsakiyar kowanne ɗaurin bindi biyu.5Da ya kunnawa gaushen wuta, sai ya tura dilolin cikin hatsin Filistiyawa, suka cinnawa hatsin wuta duk da zangarniyar da ke cikin gonakin, duk da Inabinsu garka-garka da lambunan zaitun.6Filistiyawa kuwa suka yi tambaya, "Wane ne ya yi wannan?" Aka gaya masu, "Samsin ne, surukin Batimne ya yi haka, domin Batimnen ya ɗauki matar Samsin ya ba abokinsa." Sai Filistiyawan suka tafi suka ƙone ta tare da mahaifinta.7Samsin yace masu, "Idan haka ku ka yi, zan ɗauki ramuwata a kanku, bayan haka ya faru, zan dakata."8Sai ya datsa su gunduwa-gunduwa, kwankwaso da cinya, da babbar gunduwa. Sai ya gangara ya tafi ya zauna cikin kogon dutsen Itam.9Sai Filistiyawa suka fito da shirin yaƙi cikin Yahuda suka kuma jera sojojinsu a Lehi.10Mutanen Yahuda suka ce, "Mene ne ya sa ku ka fito ku kawo mana hari?" Suka ce, "Mun kawo hari ne domin mu kama Samsin, kuma mu yi masa yadda ya yi mana."11Sai mutanen Yahuda su dubu uku suka tafi suka gangara kogon dutsen Itam, suka kuma cewa Samsin, "Ba ka san cewa Filistiyawa ne ke mulkinmu ba? Mene ne ka yi mana haka?" Samsin yace masu, "Sun yi mani, saboda haka nima na yi masu."12Suka cewa Samsin, "Mun gangaro ne domin mu ɗaure ka kuma mu miƙa ka cikin hannun Filistiyawa." Samsin yace masu, "Ku rantse mani cewa ku da kanku ba za ku kashe ni ba."13Suka ce masa, "A a, zamu ɗaure ka ne kawai da igiyoyi kuma mu miƙa ka gare su. Mun yi alƙawari ba za mu kashe ka ba." Daga nan suka ɗaure shi da sabbin igiyoyi biyu suka fito da shi daga dutsen.14Da ya zo Lehi, Filistiyawa suka fito da Ihu yayin da suke zuwa su gamu da shi. Sai Ruhun Yahweh ya sauko kansa da iko. Sai igiyoyin da ke bisa hannuwansa suka zama kamar ƙonannar ciyawa, suka kuma zube daga hannuwansa.15Sai Samsin ya samo sabon ƙashin muƙamuƙin jaki, ya ɗauko ya kuma kashe mutane dubu da shi.16Samsin yace, "Da ƙashin muƙamuƙin jaki, tari bisa tari, da ƙashin muƙamuƙin jaki na kashe mutane dubu."17Da Samsin ya gama magana, sai ya jefar da ƙashin muƙamuƙin jakin, sai ya kira wurin da suna Ramat Lehi.18Samsin ya ji ƙishi sosai sai ya yi kira ga Yahweh ya ce, "Ka bayar da nasara mai girma ga bawanka. Amma yanzu zan mutu da ƙishi ne kuma in faɗa cikin hannuwan waɗancan marasa kaciyar?"19Sai Allah ya tsaga cikin sararin da ke Lehi sai ruwa ya ɓulɓulo. Da ya sha, sai karfinsa ya dawo kuma ya farfaɗo. Saboda haka ya kira sunan wannan wuri En Hakkori, kuma yana nan a Lehi har yau.20Samsin ya yi alƙalancin Isra'ilawa a zamanin Filistiyawa har shekaru ashirin.
Wannan na nufin tunani . AT: "ya yi tunani a ransa"
Wannan na nuna cewa ya ba ta ta auri da abokin Samsin.
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "Ka ɗauke ta ta zama martaka a madadin"
Samsin ya tunanin cewa ba zai zama mai laifi ba idan ya farmaki Filistiyawa domin sun zalunce shi.
Wannan ya nuna cewa shi ne mijin 'yar mutumin.
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 14:15.
"ya cewa da Filistiyawa"
Wannan bayanin cikakken ne na yadda Samsin ya kashe Filistiyawa. AT: "Ya yanyanka jikinsu guntu-guntu"
Wannan shi ne buɗewa a cikin tudun ko a gefen tsauni
Wannan sunan yankin dutse ne kusa da Yerusalem.
"suka shirya kansu don yaƙi"
Wannan sunan gari a cikin Yahuda.
AT: "kashe shi kamar yadda ya kashe da yawa daga mutanenmu"
Mazajen Yahuda sun yi waɗannan tambayoyin don su tsauta wa Samsin. AT: "Kun san cewa Filistiyawa suna mulkinmu amma kuna nunawa kamar ba su bane. Abin da kuka yi ya cutar da mu sosai."
Samsin yana nufin yadda Filistiyawa suka kashe matarsa da yadda ya kashe su domin ɗaukar fansa. AT: "Sun kashe matata, don haka na kashe su"
A nan "hannun" na nufin iko ko sarrafawa. AT: "sarrafawan na Filistiyawa"
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 14:6.
Wannan kalmonin ya bayyana yadda mutane da yawa Samsin kuka kashe.
Wannan sunan wurin ne. Sunan na nufin "Tudun Muƙamuƙin"
Kalmomin "fada cikin hannuwa" yana nufin a kama shi.
Waɗannan jumla biyu suna ma'ana dai-dai ne. AT: "ya sake karfi" ko "ya farfado"
Wannan sunan marmaro ne na ruwa. Sunan yana nufin "maɓuɓɓugar ga wanda yayi addu'a"
Wannan yana nufin lokacin da Filistiyawa sarrafawa da Isra'ila.
1Samsin ya tafi Gaza sai ya ga karuwa a can, sai kuwa ya kwana da ita.2Aka faɗa wa Gazawa, "Samsin ya shigo nan fa." Gazawa suka kewaye wurin a asirce, suka yi masa kwanto tsawon dare a ƙofar birnin. Suka yi tsit dukkan tsawon daren. Sun riga sun ce, "Mu jira har sai wayewar gari, sa'an nan kuma mu kashe shi."3Samsin ya yi kwance bisa gado har tsakiyar dare. Da dare ya yi tsaka sai Samsin ya tashi ya tafi ya kama ƙofar birnin da ginshiƙanta biyu. Ya tumɓuko su daga ƙasa, duk da ƙarafunan da komai, ya ɗorasu bisa kafaɗunsa, ya tafi da su bisa tudu, a gaban Hebron.4Bayan wannan, Samsin ya zo ya ƙaunaci wata mata da ke zaune a Kwarin Sorek. Sunanta Delila.5Masu mulkin Filistiyawa suka zo wurinta, suka ce da ita, "Ki yaudari Samsin domin ki gane inda babban ƙarfinsa yake, da kuma ta yaya zamu sha ƙarfinsa, domin mu ɗaure shi mu kuma yi masa wulaƙanci. Ki yi mana wannan, mu kuma kowanne zai ba ki azurfa 1,100 ."6Daga nan Delila ta ce da Samsin, "Ina roƙonka, ka gaya mani yadda aka yi ka ke da ƙarfi haka, kuma ta yaya za a iya ɗaure ka, domin a mulke ka?"7Samsin yace mata, "Idan aka ɗaure ni da ɗanyen ƙiri guda bakwai, daga nan zan zama marar ƙarfi kuma in zama kamar kowanne mutum."8Sai masu mulkin Filistiyawa suka kawo wa Delila igiyoyin ƙiri guda bakwai ɗanyu, ita kuwa ta ɗaure Samsin da su.9Ta riga ta ɓoye mutane a asirce, suna jira cikin ƙuryar ɗakinta. Sai ta ce da shi, "Filistiyawa suna kanka, Samsin!" Amma ya tsisttsinke igiyoyin kamar zare a mazari idan ya taɓa wuta. Ta haka ba a gane asirin ƙarfinsa ba.10Daga nan Delila ta ce da Samsin, "Yadda ka ruɗe ni kenan kuma ka yi mani ƙarya. Ina roƙon ka, ka faɗa mani yadda za a sha ƙarfinka."11Sai ya ce mata, "Idan aka ɗaure ni da sabbin igiyoyin da ba a taɓa aiki da su ba, daganan zan zama marar ƙarfi kuma in zama kamar kowanne mutum."12Sai Delila ta ɗauki sabbin igiyoyi ta ɗaure shi da su, sai ta ce da shi, "Filistiyawa suna kanka, Samsin!" Mutanen kuwa 'yankwanto suna cikin ƙuryar ɗakin. Samsin kuwa ya tsisttsinke igiyoyin kamar zare.13Delila ta ce da Samsin, "Har yanzu ruɗi na ka ke yi kuma kana faɗa mani ƙarairayi. Ka gaya mani yadda za a sha ƙarfinka." Samsin yace mata, "Idan ki ka saƙa tukkun kaina guda bakwai bisa masaƙa kamar yadda ake saƙa sutura, sa'an nan ki sa allura ki kafe gashin bisa gungumen masaƙar, zan zama kamar kowanne mutum."14Yayin da ya yi barci, sai Delila ta yi wa tukkun kansa bakwai saƙa kamar an saƙa sutura bisa masaƙa ta kuma sa allura ta kafe shi bisa masaƙa, sai ta ce da shi, "Filistiyawa suna kanka, Samsin!" Ya farka daga barci kuma ya yage gashin duk da allurar daga jikin masaƙar.15Sai ta ce masa, "Ta yaya za ka ce, 'Ina son ki,' amma baka iya faɗa mani asirinka ba? sau uku kenan kana yi mani ba a kuma ba ka gaya mani yadda aka yi ka ke da babban ƙarfi haka ba."16Kowacce rana ta dinga gasa masa tsanani ta wurin maganganu, ta tsananta masa ƙwarai da gaske har ya gwammace ya mutu.17Sai Samsin ya faɗa mata dukkan komai ya ce mata, "Ba a taɓa sa reza aka yanke gashin kaina ba, Gama ni Naziri ne domin Allah tun daga mahaifar uwata. Idan aka aske kaina, to ƙarfina zai rabu da ni, daganan zan zama marar ƙarfi kuma in zama kamar kowanne mutum."18Da Delila ta ga cewa ya faɗa mata gaskiya game da komai, sai ta aika aka kira masu mulkin Filistiyawa, ta na cewa, "Ku sake dawowa, gama ya faɗa mani komai." Sai masu mulkin Filistiyawa suka tafi wurinta, suna ɗauke da azurfa a hannuwansu.19Sai ta sa barci ya kwashe shi a bisa cinyarta. Ta kira wani mutum yazo ya aske tukkaye bakwai da ke a kansa, daga nan ta dinga jujjuya shi, domin ƙarfinsa ya riga ya rabu da shi.20Ta ce, "Filistiyawa suna kanka, Samsin!" ya farka daga barcinsa ya ce, "Zan tashi kamar lokutan baya in kuma girgije kaina kuɓutacce." Amma ba ya sani cewa Yahweh ya riga ya rabu da shi ba.21Filistiyawa suka kama shi suka ƙwaƙule masa idanu. Suka kawo shi har Gaza suka kuma ɗaure shi da sarƙoƙin tagulla. Shi ne ke aikin juya dutsen niƙa a kurkuku.22Amma gashin kansa ya soma sake tuƙowa bayan askin da aka yi masa.23Masu mulkin Filistiyawa suka taru domin su miƙa babbar hadaya ga Dagon allahnsu, su kuma yi farinciki. Suka ce, "Allahnmu ya yi nasara da Samsin, maƙiyinmu, ya kuma sa shi cikin hannuwanmu."24Da mutanen suka gan shi, sai suka yi yabo ga allahnsu, domin suka ce, "Allahnmu ya yi nasara da maƙiyinmu kuma ya miƙa shi gare mu - mai lalatar da ƙasarmu, wanda ya kashe masu yawa daga cikinmu."25Yayin da suke cikin shagali, sai suka ce, "A kira mana Samsin, domin ya zo ya sa mu dariya." Aka kira Samsin daga cikin kurkuku ya zo ya yi ta ba su dariya. Suka sa ya tsaya a tsakanin ginshiƙan ginin.26Samsin yace da saurayin da ya riƙe hannunsa, "Ka bar ni in taɓa ginshiƙan da ke riƙe da ginin, domin in jingina da su."27Yanzu fa gidan na cike da mutane maza da mata. Dukkan masu mulkin Filistiyawa suna wurin. A bisa rufin ginin akwai mutum dubu uku maza da mata, waɗanda ke kallo yayin da Samsin ke yi masu wasa.28Samsin ya yi kira ga Yahweh ya ce, "Ubangiji Yahweh, ka tuna da ni! Ina roƙon ka ka ƙarfafa ni sau ɗaya kacal, ya Allah, domin in ɗauki fansa bugu ɗaya tak akan Filistiyawa saboda idanuna biyu da suka ƙwaƙule."29Samsin ya riƙe ginshiƙan nan biyu da ke ɗauke da ginin, sai ya jingina kansa da su, hannunsa na dama na riƙe da ɗaya, kuma hannunsa na hagu na riƙe da ɗayan.30Samsin yace, "Bari in mutu tare da Filistiyawa!" Ya miƙe iya ƙarfinsa ginin kuwa ya rugurguje bisa masu mulkin da dukkan mutanen da ke ciki. Saboda haka matattun da ya kashe a mutuwarsa sun fi waɗanda ya kashe a lokacin rayuwarsa.31Daga nan 'yan'uwansa da dukkan gidan mahaifinsa suka gangaro. Suka ɗauko shi, suka dawo da shi suka kuma binne shi tsakanin Zora da Eshtawol a maƙabartar Manowa, mahaifinsa. Samsin ya yi alƙalacin Isra'ila shekaru ashirin.
Waɗannan su ne mutanen Gaza.
Mai yiwuwa ma'anar su ne: 1) "ba su yi hayaniya ba a dukan dare" ko "Ba su yi ƙoƙarin kai masa hari dukan dare ba."
Waɗannan su ne tallafawa na ƙofar birnin.
Wannan sunan birni ne.
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 14:15.
Wannan karin magana ne; yana nufin inda babban ƙarfinsa ya fito. AT: "abin da ke ba shi karfi sosai"
"ta yaya zamu iya rinjaya masa"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: " ɗaure ku don sarrafa ku"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "waɗanda bai ba bushe ba"
A nan amfani da wannan kalmar wajen dakatar da wani sashin asalin labari. A nan marubucin na ba da bayayin karin haske game da mazajen Filistiyawa waɗanda suke jira su kama Samsin.
Kalmomin "a kansu" na nufin cewa suna shirye su kama masa". AT: "Filistiyawa suna nan don su kama ku"
Delila ta yi amfani da waɗannan jumlolin don jaddada yadda take fushi da Samsin. AT: "Kun yaudare ni sosai"
Wannan na nuna cewa sun kasance suna ɓoye kuma suna jiran lokacin da ya dace don kai hari.
"sa'an nan ki kafe masana'anta gashin bisa gungumen masaƙar"
Za a iya rubuta wannan tambaya a matsayin wata sanarwa. AT: "Lokacin da kuka ce 'ina son ku', larya kuke yi domin ba ku raba asirin ku"
AT: "ta yi iya kokarin ta don lallashe shi ... ta ci gaba da kokarin matsa masa lamba"
Wannan bayanin ya jaddada irin baƙin cikin da Samsin ya ji. AT: "ya kasance mai baƙin ciki sosai"
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "ya fada mata asalin karfin sa" ko "ya fada mata gaskiya"
Duba yadda zaka fassara a wannan a Alƙalai 13:5.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "idan wani ya aske kaina"
AT: "Ba zan ƙara yin ƙarfi ba"
"ta sa shi barci"
Wannan na nuna cewa ya kwana da kansa a bisa cinyarta. AT: "da kansa a bisa cinyarta"
AT: "karfinsa ya tafi" ko "bai kasance mai ƙarfi ba"
An yi tsammanin cewa idan Yahweh ya bar Samsin, ba zai ƙara zama mai ƙarfi ba.
"ya ja dutsen niƙa a cikin da'irar"
Wannan sunan allahn ƙarya na Filistiyawa.
Wannan yana nufin Samsin.
"ginshiƙan da suka rike ginin, don in jingina da su"
"mutanen da suke kallo"
"ya yi addu'a ga Yahweh"
Wannnan yana nufin don Yahweh ya tuna da shi da kuma halin da yake ciki.
AT: "ya yi amfani da ƙarfinsa don tura gunshiƙan a ƙasa"
"a wurin da aka binne mahaifinsa Manowa"
Wannan maganar kuma tana ciki Alƙalai 15:20. An maimaita shi anan don tunatar da masu karatu cewa Samsin ya yi mulkin Isra'ila na shekara ashirin kafin ya mutu.
1Akwai wani mutum a ƙasar tudu ta Ifraim, sunansa Mika.2Sai ya ce da mahaifiyarsa, "Azurfarki 1,100 da aka ɗauke maki, wanda kuma ki ka furta la'ana akai, wanda kuma na ji - duba nan! azurfar na wurina. Ni ne na sace." Mahaifiyarsa ta ce, "Yahweh ya albarkace ka, ɗana!"3Sai ya maido wa mahaifiyarsa azurfa 1,100 sai mahaifiyarsa ta ce, "Na keɓe wannan azurfa ga Yahweh, domin ɗana ya sassaƙa kuma ya sarrafa siffofi na ƙarfe. Saboda haka yanzu, na maido maka azurfar."4Da ya maido wa mahaifiyarsa kuɗin, sai mahaifiyarsa ta ɗauki azurfa ɗari biyu ta ba maƙeri wanda shi kuma ya sassaƙa ya kuma sarrafa siffofi na karfe da su, sai aka ajiye su a gidan Mika.5Mutumin nan Mika ya na da gidan gumaka sai ya yi falmarar haikali da kuma allolin gida, sai ya ɗauki hayar ɗaya daga cikin 'ya'yansa maza ya zama firist.6A waɗannan kwanaki ba sarki a Isra'ila, kowa na yin abin da ya yi dai-dai a idanunsa.7Akwai wani saurayi daga Betlehem ta cikin Yahuda, daga iyalin Yahuda, shi kuwa Balebi ne. Ya na zaune anan domin ya aiwatar da ayyukansa.8Mutumin ya bar Betlehem ta Yahuda ne domin ya fita ya je ya sami wani wurin zama. Yayin da ya ke tafiya, sai ya zo gidan Mika da ke ƙasar tuddun Ifraim.9Sai Mika yace masa, "Daga ina ka fito?" Mutumin yace masa, "Ni Balebi ne na Betlehem ta cikin Yahuda, kuma na fito tafiya ne domin neman wurin zama."10Mika yace da shi, "Ka zauna da ni, sai ka zama uba da firist a gare ni. Zan ba ka azurfa goma a shekara, da kayan sawa, da abinci." Sai Balebin ya shiga cikin gidansa.11Balebin ya dangana da zama da mutumin, kuma saurayin ya zame wa Mika kamar ɗaya daga cikin 'ya'yansa maza.12Mika ya keɓe Balebin saboda ayyukan ibada, sai saurayin ya zama firist ɗinsa, kuma yana cikin gidan Mika.13Sai Mika yace, "Yanzu na sani cewa Yahweh zai yi mani abin alheri, domin Balebin nan ya zama firist ɗina."
Wannan wata hanya ce da za a gabatar da sabon mutum zuwa layin labari.
Wannan sunan mutum ne. Amma ba ɗaya bane mutumin da ya rubuta Littafin Mika.
Wannan yana nufin sadaukar da wani abu ga wani takamaiman manufa. AT: "saduakar"
"Zan ba ku ita"
Wannan na nufin gidan ne don bautar gumaka.
Idani suna wakiltar gani, da gani suna wakiltar tunani ko hukunci. AT: "kowane mutum ya yi yadda ya ga dama"
"Ya rayu kuma yayi aiki a wurin"
AT: "inda zan iya rayuwa da sami aiki"
Wannan yana nuna cewa dangantakar da ke tsakanin Balebi da Mika ta zama kamar mahaifin da ɗa.
AT: "shi zauna a gidan Mika"
1A waɗannan kwanaki babu sarki a Isra'ila. Kabilar zuriyar Dan suna neman wajen da za su yi wa kansu wurin zama, domin har zuwa wannan lokaci ba su karɓi wani gãdo daga cikin kabilun Isra'ila ba.2Mutanen Dan suka aika da mutum biyar daga dukkan cikin kabilarsu, mutanen da suka ƙware wajen yaƙi daga Zora zuwa Eshtawol, domin su kewaye ƙasar da ƙafa, kuma su duba ta. Suka ce masu, "Ku je ku duba ƙasar." Suka zo ƙasar tudu ta Ifraim, suka zo gidan Mika, suka kwana anan.3Da su na kusa da gidan Mika, sai suka gane karin harshen saurayin nan Balebiye. Sai suka tsaya suka tambaye shi, "Wa ya kawo ka nan? Me kake yi a nan wurin? Meyasa ka ke nan?"4Ya ce masu, "Ga abin da Mika ya yi mani: Ya ɗauki hayata in zama firist ɗin sa."5Suka ce da shi, "Muna roƙon ka ka nemi shawara daga Allah, domin mu sani ko tafiyar nan da muke yi za ta yi nasara."6Sai firist ɗin ya ce masu, "Ku tafi cikin salama. Yahweh za ya bi da ku hanyar da zaku bi."7Sai mutanen nan biyar suka tafi har suka isa Layish, sai suka iske mutanen na zaune lafiya, hakanan kuma Sidoniyawa suke zaune, babu abin da ya dame su a tsare suke. Babu wanda ya taɓa yin nasara da su ko kuma ya taɓa tsananta masu a ƙasar ko kaɗan. Suna zaune nesa da Sidoniyawa kuma ba su da wata hurɗa da kowa.8Suka dawo wurin kabilarsu a Zora da Eshtawol. 'Yan'uwansu suka tambaye su, "Mene ne rahotonku?"9Suka ce, "Ku zo! Mu kai masu hari! Mun ga ƙasar kuma mai nagarta ce. Ba za kuyi wani abu ba? Kada ku yi jinkirin kai hari kuma ku ci ƙasar.10Idan ku ka je, za ku iske mutane waɗanda ke tunanin a tsare suke, kuma ƙasar na da fãɗi! Allah ya bayar da ita a gare ku - wurin da babu rashin komai a ƙasar."11Mutane ɗari shida daga kabilar Dan, shirye da kayan yaƙi, suka fito daga Zora da Eshtawol.12Suka tafi su ka yi sansani a Kiriyat Yerayim, cikin Yahuda. Wannan ya sa mutane ke kiran wurin Mahane Dan har wa yau; yana yamma da Kiriyat Yerayim.13Suka tafi daga wurin zuwa ƙasar tudu ta Ifraim sai suka zo gidan Mika.14Sai mutanen nan biyar da suka je gewayar ƙasar Layish suka ce da 'yan'uwansu, "Kun kuwa san cewa a cikin gidajen nan akwai falmarar haikali, da allolin gida, sassaƙaƙƙiyar siffa, da siffar ƙarfe da aka sarrafa? Yanzu ku yi shawarar abin da za ku yi."15Sai suka juya daga nan suka shiga gidan saurayin nan Balebi, a gidan Mika, sai suka gaishe shi.16Daga nan Danawan nan ɗari shida, shirye da kayan yaƙi, suka tsaitsaya a ƙofar gidan.17Mutanen nan biyar da suka je gewayar ƙasar suka shiga suka ɗauko sassaƙaƙƙiyar siffar, da falmarar haikalin, da allolin gida, da sarrafaffiyar siffar ƙarfen, lokacin da firist ɗin ke tsaye bakin ƙofar gidan tare da mutanen nan ɗari shidda da ke shirye da kayan yaƙi.18Da waɗannan suka shiga cikin gidan Mika suka ɗauko sassaƙaƙƙiyar siffar nan, da falmarar haikali, da allolin gida, da sarrafaffiyar siffar ƙarfen nan, sai firist ɗin ya ce masu, "Me ku ke yi?"19Suka ce da shi, "Yi shiru! Ka sa hannunka a bakinka ka taho tare da mu, sai ka zama Uba da firist a gare mu. Wanne ne ya fi maka ka zama firist na gidan mutum ɗaya, ko kuwa ka zama firist na kabila da kuma ɗaya daga cikin zuriyar Isra'ila?"20Firist ɗin ya yi murna a zuciyarsa. Ya ɗauki falmarar haikalin, da allolin gidan, da sassaƙaƙƙiyar siffar, sai ya tafi tare da mutanen.21Sai suka juya suka yi tafiyarsu. Suka sa ƙananan yaran a gabansu, da kuma shanun da dukkan mallakarsu.22Da suka yi 'yar tazara daga gidan Mika, sai aka kira mutanen da ke maƙwaftaka da gidan Mika suka tattaru, suka tafi suka tarar da Danawan.23Suka yi kururuwa ga Danawan, suka juya suka ce wa Mika, "Me ya sa ku ka tattaro kanku?"24Ya ce, "Kun sãce allolin da na yi, kun ɗauke mani firist, kuma kun tafi. Me kuma ya rage mani? ya ya za ku yi mani tambaya, "Me ke damun ka?"25Mutanen Dan suka ce da shi, "Kada ka bari mu ji ka ce wani abu, ko kuwa wasu mutane masu fushi da ke nan wurin ransu ya ɓaci sosai su kai maka hari, kai da iyalinka kuma a kashe ku."26Sai mutanen Dan suka yi tafiyarsu. Da Mika ya ga cewa sun sha ƙarfinsa, sai ya juya ya koma gidansa.27Mutanen Dan suka ɗauke abin da Mika ya sassaƙa, duk da firist ɗinsa, sai suka zo Layish, wurin mutanen da babu abin da ya dame su kuma cikin tsaro suka kashe su da takobi suka ƙone birnin.28Babu wanda yazo ya cece su domin sun yi nisa da Sidon, kuma ba su da wata hurɗa da wani. A kwari ne da ke kusa da Bet Rehob. Danawan suka sake gina birnin suka zauna a ciki.29Suka sa wa birnin suna Dan, bisa ga sunan Dan kakansu, wanda ya ke ɗaya daga cikin 'ya'yan Isra'ila. Amma dã sunan birnin Layish ne.30Mutanen Dan suka kafa wa kansu sassaƙaƙƙiyar siffar nan. Yonatan ɗan Gashom, ɗan Musa, shi da 'ya'yansa maza suka zama firistocin kabilar Danawa har zuwa ranar tafiya ƙasar bauta.31Haka nan suka yi sujada ga sassaƙaƙƙiyar siffar Mika wanda ya sarrafa dukkan tsawon kwanakin da gidan Allah ya ke a Shilo.
Wannan magana tana gabatar da farawar wani abin aukuwa a cikin almara.
Wannan shi ne bayanin asalin game da Isra'ila da mutanen kabilar Dan.
Wannan kalmar "a kafa" tana nufin tafiya. AT: "su leƙo asirin ƙasar ta wajen tafiya ta hanyar da shi"
Sun gane da saurayin ta wajen da sauti muryansa.
Wannan sunan birni ne.
"Babu wanda ya ci su da yaƙi da babu wanda ya yi zalunta su ta kowane hanya"
"Ba su da kasuwanci tare da bare."
Za a iya rubuta wannan tambaya a matsayin wata sanarwa. AT: "Ya kamata kayi wani abu yanzu!"
AT: "Hanzarta!" "Kai farmaki!"
AT: "ƙasar tana da komai"
Wannan sunan gari ne.
Da 'yan leken asirin biyar sun faɗi waɗannan ga danginsu don ƙarfafa su don satar waɗannan abubuwan.
Kalmar "shi" na nufin Balebi.
Za a iya rubuta wannan tambaya a matsayin wata sanarwa. AT: "Zai fi kyau ku zama firist na kabila cikin Isra'ila fiye da zama firist a gidan mutum ɗaya."
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "ya tara mazajen da suke zaune a gidaje kusa"
Za a iya fassara wannan tambaya a matsayin wata sanarwa. AT: "Ba lallai ne ku kira mutanenku don su gudun bayan da mu ba."
AT: "Babu abin da na rage" ko "Kun ɗauki duk abin da yake da muhimmanci a gare ni."
Wannan yana nufin Danawa. Sun fi karfin Mika da mutanensa.
A nan "takobi" na wakilce takobi da sauran kayan yaƙi da sojojin su ka yi amfani da shi a yaƙi.
Wannan sunan gari ne.
Wannan sunan saurayi Balebi ne wanda yake firist a gidan Mika.
1A waɗannan kwanaki, sa'ad da babu sarki a Isra'ila, akwai wani mutum, Balebi, ya yi zama na ɗan wani lokaci a wani ƙauye a ƙasar tudu ta Ifraim. Sai ya ɗauko wa kansa mace, kuyanga daga Betlehem cikin Yahuda.2Amma kuyangar tasa ta yi masa rashin aminci; sai ta bar shi ta koma gidan mahaifinta a Betlehem cikin Yahuda. Ta zauna a can watanni huɗu.3Sai mijinta ya tashi ya tafi wurinta domin ya lallashe ta ta dawo. Baransa kuwa na tare da shi, da jakai guda biyu. Sai ta kawo shi cikin gidan mahaifinta. Da mahaifin yarinyar ya gan shi, sai ya yi murna.4Sai surukinsa, mahaifin yarinyar, ya lallashe shi ya zauna kwana uku. Suka ci su ka sha suka kwana a can.5A rana ta huɗu suka tashi suka yi asubanci suka shirya domin su tafi, amma mahaifin yarinyar ya ce da surukinsa, "Ka ci ɗan abinci domin ka sami ƙarfi, daga nan sai ka tafi."6Sai su biyun suka zauna domin su ci su kuma sha tare. Daga nan mahaifin yariyar ya ce, "Ina roƙon ka ka yarda ka sãke kwana domin ka wartsake."7Da Balebin ya tashi zai tafi, sai mahaifin yarinyar ya roƙe shi da ya tsaya, sai ya canza shirinsa ya sake kwana.8A rana ta biyar ya tashi ya yi asubanci domin ya tafi, amma mahaifin yarinyar ya ce, "Ka ƙarfafa kanka, ka jira sai rana tayi." Sai suka zauna su ka ci abinci su biyu.9Da Balebin da kuyangarsa da baransa suka tashi za su tafi, sai surukinsa, mahaifin yarinyar ya ce da shi, "Duba, yanzu yamma ta ƙarato. Ina roƙonka ka tsaya ka sãke kwana, ka kuma wartsake. Kana iya yin asubanci gobe ka tashi ka koma gida."10Amma Balebin ba ya so ya sake kwana. Sai ya tashi ya tafi. Ya yi tafiya ya fuskanci Yebus (wato Yerusalem). Yana da jakai biyu shiryayyu domin hawa - kuma kuyangarsa na tare da shi.11Da suka iso gaf da Yebus, rana ta kusa faɗuwa, sai baran ya ce wa maigidansa, "Ka zo, mu juya mu shiga birnin Yebusawa mu kwana a ciki."12Sai ubangidansa yace masa, "Ba za mu juya mu shiga birnin bãre waɗanda ba na mutanen Isra'ila ba ne. Mu ci gaba da tafiya mu kai Gibiya."13Balebin ya ce wa bãransa, "Zo, mu tafi ɗaya daga cikin wuraren nan, mu kwana a can ko dai Gibiya ko kuma Ramah."14Sai suka ci gaba da tafiya, rana kuwa ta faɗi da suka yi gaf da Gibiya, cikin yankin Benyamin.15Sai suka juya suka shiga domin su kwana a Gibiya. Sai suka je suka zauna a dandalin birnin, amma babu wanda ya kira su domin su kwana a gidansa.16Amma sai ga wani mutum tsoho yana dawowa daga aikin gonarsa a yammacin nan. Shi kuwa mutumin ƙasar tudu ta Ifraim ne, amma ya na zama a Gibiya na ɗan wani lokaci. Amma mutanen da ke zama a wannan wuri Benyaminawa ne.17Ya ɗaga idanunsa sai ya ga matafiyin a dandalin birni. Tsohon ya ce, "Ina za ku? Daga ina ku ka fito?"18Balebinn yace masa, "Mun fito ne daga Betlehem cikin Yahuda za mu wani ƙauyen ƙasar tudu ta Ifraim, wato inda na fito. Na je Betlehem cikin Yahuda, kuma za ni gidan Yahweh, amma babu wanda zai karɓe ni cikin gidansa.19Muna da harawa da abinci domin jakkanmu, akwai gurasa da ruwan inabi domina da wannan mace baiwarka a nan, da kuma wannan saurayin tare da barorinka. Ba mu rasa komai ba."20Sai tsohon nan ya gaishe su, "Salama a gare ku! Zan biya dukkan buƙatunku. Kada dai ku kwana a dandali kawai."21Sai mutumin ya kawo Balebinn cikin gidansa ya kuma ba da abinci ga jakunansa. Suka wanke sawayensu suka ci suka sha.22Lokacin da suke cikin annashuwa, sai waɗansu mutanen birnin, 'yan'iskan gari, suka zo suka kewaye gidan, suna bubbuga ƙofar. Suka yi wa tsohon nan magana, wato mai gidan, suna cewa, "Ka fito da mutumin nan da ya shigo cikin gidanka, domin mu yi luɗu da shi."23Mutumin nan, mai gidan, ya fita ya same su ya ce masu, "A 'a, 'yan'uwana, ina roƙon ku kada ku yi wannan irin mugun abu! Tun da wannan mutum baƙon gidana ne, kada ku yi wannan irin mugun abu!24Duba, ɗiyata budurwa da kuma kuyangarsa ga su nan. Bari in fito da su yanzu. Ku yi masu fyaɗe ku kuma yi yadda kuka ga dama da su. Amma kada ku yi wannan irin mugun abu ga mutumin nan!"25Amma mutanen nan ba su saurare shi ba, sai mutumin nan ya fizgi kuyangarsa ya kuma fitar masu da ita. Suka fizge ta, suka yi mata fyaɗe, suka wulaƙanta ta dukkan tsawon dare, da asuba ta yi suka bar ta ta tafi.26Da asuba matar ta dawo sai ta faɗi a bakin ƙofar gidan mutumin inda maigidanta ya ke, sai ta yi kwance a nan har gari ya waye sarai.27Maigidanta ya tashi da safe ya buɗe ƙofofin gidan ya fita domin ya kama hanyar tafiyarsa. Sai ya lura da kuyangarsa a kwance a bakin ƙofa, da hannuwanta bisa dankarin ƙofar.28Balebin ya ce mata, "Tashi. Mu tafi." Amma ba ta amsa ba. Sai ya ɗora ta bisa jaki, mutumin kuwa ya kama hanya zuwa gidansa.29Sa'ad da Balebin nan ya iso gidansa, sai ya ɗauko wuƙa, ya kuma kama kunyangar tasa, ya daddatsa ta, ya yi mata gunduwa-gunduwa, ya kasa ta kashi goma sha biyu, sai ya aika da kashi-kashin nan ko'ina cikin dukkan ƙasar Isra'ila.30Dukkan waɗanda suka ga wannan abu suka ce, "Wannan irin abu bai taɓa faruwa ba ko aka taɓa ganinsa ba tun daga ranar da mutanen Isra'ila suka fito daga ƙasar Masar har ya zuwa wannan rana. Ku yi tunani akai! Ku bamu shawara! Ku gaya mana abin da za'a yi!"
Wannan magana tana gabatar da farawar wani abin aukuwa a cikin layin labari.
yanki mai nisa; nesa da inda yawancin mutane ke zama.
Wannan yana nufin cewa ta fara yin barci tare da wasu mazajen.
"ya tafi tare da baransa da jakai biyu"
Balebi ya shirya
"Ina roƙon ka tsaya na wani dare"
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "Ku ci abinci don ku sami ƙarfi don tafiya ko kuma jira har sai da rana don tafi"
"ranar ta kusa karewa" ko "kusan yamma ta yi"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Ya sa sirddadai a kan jakansa biyu"
Wannan ya nuna cewa ya bar hanyar ya yin wani abu ne.
Duba yada zaka fassara a wannan a Alƙalai 19:11.
Duba yada zaka fassara a wannan a Alƙalai 19:11. AT: "tsaya"
wannan kuma ana kiranta wurin kasuwa
Wannan jumla na nufin wani mutum ya gayyace su ya kwana a gidansu.
Waɗannan su na zuriyar Benyamin.
AT: "Ya sama ido"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "muna da abinci da ruwan inabi"
Za a iya rubuta wannan azaman sanarwa tabbatacce. AT: "muna da duk abin da muke buƙata"
Wannan na nuna cewa tsohon mutum ya gayyaci Balebi da bayinsa su kwana a gidansa.
Kalmomin nan "farantawa zukatansu rai" na nufin samun lokacin mai kyau tare da wani. AT: "suna jin daɗin kansu"
AT: "tsohon mutum nan ya fizgi kuyangarsa"
Mata ba ta amsa ba saboda ta mutu.
Wannan na nufin ya aika da daban-daban guntu-guntu zuwa da wuraren daban-daban goma sha biyu na Isra'ila.
1Daga nan dukkan mutanen Isra'ila suka fito a matsayin mutum guda, daga Dan har zuwa Biyasheba, duk da ƙasar Giliyad ma, suka tattaru tare a gaban Yahweh a Mizfa.2Shugabannin dukkan mutanen, da kuma dukkan kabilun Isra'ila, suka ɗauki wurarensu a cikin taron mutanen Allah - Mutane 400,000 a ƙasa, waɗanda ke a shirye domin su tafi su yi yaƙi da takobi.3Mutanen Benyamin suka ji cewa mutanen Isra'ila sun haye zuwa Mizfa. Mutanen Isra'ila suka ce, "Gaya mana yadda wannan mugun abu ya faru."4Balebin mai gidan matar wadda aka kashe, ya amsa, "Na zo Gibiya ne wadda ke yankin Benyamin, ni da kuyangata, domin mu kwana.5A cikin dare, shugabannin Gibiya suka kawo mani hari, suka kewaye gidan suna nema su kashe ni. Suka fizge kuyangata su a yi mata fyaɗe, sai kuwa ta mutu.6Na ɗauki kuyangata na datsa ta kashi-kashi, na kuma aika cikin kowanne lardin gãdon Isra'ila, saboda sun aikata wannan irin mugunta da hasala a cikin Isra'ila.7Yanzu, dukkan ku Isra'ilawa, sai ku ba da shawara ku kuma ɗauki mataki a nan."8Dukkan mutanen suka tashi tsaye a matsayin mutum guda, suka ce, "Babu wani cikinmu da za ya koma rumfarsa, babu kuma wani cikinmu da zaya koma gidansa!9Amma dole yanzu ga abin da zamu yi wa Gibiya: Za mu kai mata hari bisa ga yadda ƙuri'a za ta bi da mu.10Za mu ɗauki mutane goma cikin ɗari daga cikin dukkan kabilun Isra'ila, da kuma mutane ɗari cikin dubu, mutane dubu cikin dubu goma, su samo kayan masarufi domin waɗannan mutanen, domin idan suka zo Gibiya ta Benyamin, su ba su horo domin muguntar da suka aikata a Isra'ila."11Sai dukkan sojojin Isra'ila suka taru a matsayin mutum guda, domin yin tsayayya da birnin.12Sai kabilun Isra'ila suka aika da mutane cikin dukkan kabilar Benyamin, suna cewa, "Wacce irin mugunta ce haka aka aikata a cikinku?13Saboda haka, ku ba mu waɗannan miyagun mutanen na Gibiya, domin mu kashe su, ta haka za mu cire wannan mugunta da ke cikin Isra'ila ɗungun." Amma Benyaminawa suka ƙi sauraron muryar 'yan'uwansu, mutanen Isra'ila.14Sai mutanen Benyamin suka fito daga cikin biranensu suka tattaru a Gibiya domin su yi shirin yin yaƙi da mutanen Isra'ila.15Mutanen Benyamin suka tattaro mutane daga cikin biranensu a wannan rana sojoji dubu ashirin da shida horarru wajen faɗa da takobi. Bugu da ƙari, akwai mutane ɗari bakwai zaɓaɓɓu daga cikin mazauna a Gibiya.16Daga cikin waɗannan sojoji dukka akwai mutane ɗari bakwai zaɓaɓɓu waɗanda su bahagwai ne. Kowannen su za ya iya wurga dutse ga gashin kai ba tare da yin kuskure ba.17Mutanen Isra'ila, ba tare da lissafin mutanen Benyamin ba, su mutum dubu ɗari huɗu ne, waɗanda kuma horarru ne wajen faɗa da takobi. Dukka waɗannan mutanen yaƙi ne.18Mutanen Isra'ila suka tashi, suka hau zuwa Betel, suka tambayi shawara daga wurin Allah. Suka yi tambaya,"Wane ne za ya fara kai wa mutanen Benyamin hari domin mu?" Yahweh yace, "Yahuda ne za ya fara kai hari."19Mutanen Isra'ila suka tashi da sassafe suka matsa da sansaninsu kusa da Gibiya.20Mutanen Isra'ila suka tafi yin yaƙi da Benyamin. Suka tashi suka yi jeren yaƙi da Gibiya.21Mutanen Benyamin suka fito daga cikin Gibiya, suka kashe mutum dubu ashirin da biyu na sojojin Isra'ila a wannan rana.22Amma mutanen Isra'ila suka ƙarfafa kansu suka sãke kafa layin yaƙi dai-dai wurin da suka jera a rana ta farko.23Sai mutanen Isra'ila suka haye suka yi kuka a gaban Yahweh har zuwa yamma, suka kuma nemi bishewa daga wurin Yahweh. Suka ce, "Mu kuma sãke tafiya mu yi yaƙi da 'yan'uwanmu, mutanen Benyamin?" Yahweh yace, "Ku kai masu hari!"24Sai mutanen Isra'ila suka kai hari ga sojojin Benyamin a rana ta biyu.25A rana ta biyu, Benyamin ya fito daga Gibiya suka kuma kashe mutum dubu sha takwas daga cikin mutanen Isra'ila. Dukkan su horarru ne wajen faɗa da takobi.26Daga nan dukkan sojojin Isra'ila da dukkan mutanen Isra'ila suka tashi su ka haye zuwa Betel suka yi kuka, a nan suka zauna a gaban Yahweh suka yi azumi a wannan rana har zuwa yamma suka miƙa baye-baye na ƙonawa da baye-baye na salama a gaban Yahweh.27Mutanen Isra'ila su ka tambayi Yahweh - domin akwatin alƙawari na Allah na nan a waɗannan kwanaki,28a sa'annan Fenihas, ɗan Eliyeza ɗan Haruna, yana hidima a gaban akwatin a waɗannan kwanaki - "Mu sake tafiya mu yaƙi mutanen Benyamin, 'yan'uwanmu, ko mu tsaya?" Yahweh yace, "Ku kai hari, gama gobe zan taimake ku ku yi nasara da su."29Sai Isra'ila suka sa mutane suka kewaye Gibiya gaba ɗaya a asirce.30Mutanen Isra'ila suka yi yaƙi da mutanen Benyamin a rana ta uku, suka kafa layin yaƙi da Gibiya kamar yadda suka yi a dã.31Mutanen Benyamin suka fita suka yi yaƙi da mutanen, har suka fita suka yi nisa da birnin. Suka fara kashe wasu daga cikin mutanen. Wajen mutane talatin na Isra'ila suka mutu cikin gonaki da bisa hanyoyi. Ɗaya daga cikin hanyoyin ta hawa zuwa Betel ce, ɗayar kuma ta tafi zuwa Gibiya.32Sai mutanen Benyamin suka ce, "An kãshe su gashi nan suna guduwa daga gare mu, kamar yadda ya faru da farko." Amma sojojin Isra'ila suka ce, "Mu gudu baya domin mu janye su daga cikin birnin zuwa bisa hanyoyi."33Dukkan mutanen Isra'ila kuwa suka fito daga wurarensu suka jera kansu layi-layi domin yaƙi a Ba'al Tama. Sai sojojin Isra'ila waɗanda ke ɓoye a asirtattun wurare suka fito da gudu daga wurarensu daga Ma'are Gibiya.34Sai ga shi an fito wa Gibiya da yaƙi mutane dubu goma daga cikin dukkan Isra'ila, yaƙi kuwa ya yi zafi, amma mutanen Benyamin ba su san bala'i na gaf da su ba.35Sai Yahweh ya kayar da Benyamin a gaban Isra'ila. A wannan rana, sojojin Isra'ila suka kashe mutum 25,100 na Benyamin. Dukkan waɗanda suka mutu horarru ne wajen faɗa da takobi.36Sai sojojin Benyamin suka ga cewa an kayar da su. Mutanen Isra'ila kuwa sun ba Benyamin sarari, sabo da suna la'akari da mutanen da ke ɓoye a kewaye da Gibiya.37Sai mutanen da ke a ɓoye suka tashi da sauri suka auka cikin Gibiya, da takubbansu kuwa suka kashe duk wanda ke zaune a cikin birnin.38Alamar da aka shirya tsakanin sojojin Isra'ila da mutanen da ke ɓoye a asirtattun wurare shi ne za su ga girgijen hayaƙi ya turniƙe yana fitowa daga birnin.39Idan aka aika da alamar sojojin Isra'ila za su juya daga yaƙin. To Benyamin ya fara kai hari har sun kashe mutane wajen talatin na Isra'ila, sai suka ce, "babu shakka an kayar da su a gabanmu, kamar a yaƙin farko."40Amma da tuƙuƙin hayaƙi ya fara tashi sama daga cikin birnin, mutanen Benyamin kuwa suka juya suka ga hayaƙi na tashi daga cikin dukkan birnin har zuwa sararin sama.41Sai kuwa mutanen Isra'ila suka juyo kansu. Mutanen Benyamin suka tsorata, domin sun ga bala'in da ya afko masu.42Sai suka gudu daga wurin mutanen Isra'ila, suna tserewa hanyar zuwa jeji. Amma yaƙin ya ci ƙarfinsu. Sojojin Isra'ila suka fito daga birane suka kuwa karkashe su a inda suke tsaye.43Suka kewaye mutanen Benyamin, su a kora su, suka tattake su a Noha, har ya zuwa gabashin Gibiya.44Daga kabilar Benyamin, mutane dubu goma sha takwas suka mutu, dukkan su mutane ne ƙwararru a yaƙi.45Suka juya suka sheƙa da gudu zuwa jeji zuwa dutsen Rimon. Isra'ilawa suka ƙara kashe mutane dubu biyar a kan hanyoyi. Suka ci gaba da bin su, suna binsu ƙut da ƙut har zuwa Gidom, suka kuma ƙara kashe dubu biyu a can.46Dukkan sojojin Benyamin da suka fãɗi a wannan rana mutane dubu ashirin da biyar ne - horarrun mutane wajen faɗa da takobi, dukkan su ƙwararru ne a wajen yaƙi.47Amma mutane ɗari shida suka juya suka gudu zuwa jeji, zuwa dutsen Rimon. Suka yi wata huɗu suna zama a dutsen Rimon.48Sojojin Isra'ila suka juya su ka fãɗa wa mutanen Benyamin suka hare su suka kashe birnin gaba ɗaya, da shanu dukka, da dukkan abin da suka iske. Suka kuma ƙone duk wani gari da suka iske a hanyarsu.
Wannan bayanin na nufin gungun mutane waɗanda suke yin komai da tare. AT: "kamar sai su mutum guda ɗaya"
"don ikon zuwa yaƙi"
Ana amfani da wannan kalmar wajen dakatar da wani sahin asalin almara. A nan marubucin na ba da bayayin karin haske game da abin da mutanen Benyamin suka sani.
"na dare"
Waɗannan kalmomin suna nufin abu ɗaya ne. An yi amfani dasu tare a nan don ƙarfafawa.
Waɗannan jumlolin suna ma'anar dai-dai ne, ana amfani dasu sau biyu don ƙarfafawa. AT: "Dukkan mu zamu tsaya anan"
abinci da sauran abubuwan da mutane ke buƙata
"suka taru don su farmaki birnin"
A nan "murya" na nufin saƙon da suka faɗa.
Wannan yana nuna yadda ya kamata waɗannan mazajen zai iya jefa dutse.
"ban da"
"tambaya Allah abin da ya kamata su yi"
Ma'anar wannan magana a cikin juyin Ibraniyanci ba a sarari. Yana iya cewa sojojin suna tsaya daga Gibiya a shirye don yaƙi.
Anan "karfafa" na nufin sun goya baya juna.
AT: "sun shirya don yaƙi gobe"
"ga Yahweh"
Wannan bayanin asalin ne don taimaka wa mai karatu ya fahimci yadda mutane suka nemi Yahweh don amsawa.
"kasance a Betel a wancan lokaci"
"shirye don kai hari na mamaki"
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "suka yi yaƙi da mutanen Isra'ila"
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "Mazajen Benyamin suka fara kashe wasu daga cikin mazajen Isra'ila"
"kamar yadda yake a da" ko "kamar dai yadda a farkon lokatun biyu"
Wannan sunan birni ne.
Wannan sunan wurin ne.
AT: "da sannu za a shafe su gaba ɗaya"
Daga wannan jumla zuwa ƙarshen aya ta 41 bayani ne na asali don bayyana wa mai karatu yadda maharan suka ci mutanen Benyamin.
Wannan na nuna cewa sun gangan ja da baya. AT: "suka yarda mutanen Benyamin don matsawa gaba"
Wannan aya ta ci gaba da bayanin asalin don bayyana wa mai karatu yadda maharan suka ci mutanen Benyamin.
"sojojin Israila za su juya daga yaƙin"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "mu ci su"
AT: "ya faru da su"
AT: "Amma sun kasa tserewa daga yaƙin"
Wannan sunan wurin ne.
AT: "sun hallakar da mutanen Benyamin gaba ɗaya"
"Sauran mutanen Benyamin suka juya da suka sheƙa"
Wannan sunan wurin ne.
Waɗannan su ne mutanen Benyamin waɗanda suka zauna a birnin.
1Daga nan mutanen Isra'ila suka ɗauki alƙawari a Mizfa, "Babu wani cikin mu da zai bada ɗiyarsa aure ga Benyamine."2Sai mutanen suka haye zuwa Betel suka zauna can a gaban Allah har yamma, da muryoyi masu ƙarfi suka yi kuka mai zafi.3Suka yi kira, "Meyasa, Yahweh, Allah na Isra'ila, wannan irin abu ya faru da Isra'ila, cewa a yau ɗaya daga cikin kabilunmu ya ɓace?"4Washegari mutanen suka tashi da sassafe suka gina bagadi suka miƙa baiko na ƙonawa da na salama.5Mutanen Isra'ila suka ce, "Daga cikin kabilun Isra'ila dukka wane ne bai fito taron Yahweh ba?" Gama sun riga sun ɗauki alƙawari mai muhimmanci game da duk wanda bai zo wurin Yahweh ba a Mizfa. Suka ce, "Babu shakka za a kashe shi."6Sai mutanen Isra'ila suka ji tausayin ɗan'uwansu Benyamin. Suka ce, "A yau an datse kabila ɗaya daga cikin Isra'ila.7Wane ne za ya bada matayen aure ga waɗanda suka rage, tun da mun riga mun yi alƙawari ga Yahweh cewa babu wanda za ya bar wani daga cikin su ya auri 'ya'yanmu mata?"8Suka ce, "Wace ce cikin kabilun Isra'ila ba ta zo wurin Yahweh ba a Mizfa?" Sai aka iske cewa babu wanda yazo taron daga Yabish Giliyad.9Domin da aka sa mutane suka tsaya jeri-jeri, duba, babu ko ɗaya daga cikin mazaunan Yabish Giliyad da ya kasance.10Sai taron suka aika da jarumawansu mutum dubu sha biyu da umarnin cewa su je Yabish Giliyad su kai masu hari, su kuma kashe su, har ma da mata da 'ya'ya.11"Haka za ku yi: dole ne ku kashe kowanne namiji da kowace mace da ta san namiji."12Mutanen suka samo daga cikin mazauna Yabish Giliyad 'yanmata ɗari huɗu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, suka kawo su sansani a Shilo, cikin Kan'ana.13Taron ga baki ɗaya suka aika da saƙo ga mutanen Benyamin da ke a dutsen Rimon su na cewa muna neman ku da salama.14Mutanen Benyamin suka dawo a wannan lokacin kuma suka basu matan Yabish Giliyad, amma kuma matan basu isa kowannen su ya samu ba.15Mutanen suka yi juyayin abin da ya faru da Benyamin, saboda Yahweh ya sa rarrabuwa a tsakanin kabilun Isra'ila.16Sai shugabannin taron suka ce, "Yaya za mu shirya wa mutanen Benyamin da suka rage matan aure, tun da an kashe matayen Benyamin?"17Sai suka ce, "Dole ne a sami gãdo domin waɗanda suka tsira a Benyamin, domin ka da kabila ɗaya ta lalace a Isra'ila.18Ba za mu iya ba su matan aure daga cikin 'ya'yanmu mata ba, gama mutanen Isra'ila sun yi alƙawari, 'La'ananne ne wanda ya ba da mace ga Benyamin.'"19Sai suka ce, "Kun san akwai bikin idin Yahweh kowacce shekara a Shilo (wadda ke arewa da Betel, gabas da hanyar da ke tafiya daga Betel zuwa Shekem, a kudacin Lebona)."20Sai suka yi wa mutanen Benyamin umarni, suka ce, "Ku je ku ɓoye a asirce ku yi kwanto cikin garkar inabi.21Ku lura da lokacin da 'yanmata daga Shilo za su fito rawa, sai ku hanzarto daga garkar inabin kowanen ku ya kama wa kansa mata daga cikin 'yanmatan Shilo, daga nan ku koma ƙasar Benyamin.22Idan ubanninsu ko 'yan'uwasu maza suka zo domin su yi mana tawaye, za mu ce masu, 'Ku yi mana tagomashi, ku bar su su zauna saboda ba mu samarwa dukkansu matan aure ba a lokacin yaƙin. Ba ku da laifi, tun da ba ku bayar da 'ya'yanku mata ba a gare su.'"23Mutanen Benyamin suka yi yadda aka ce. Suka ɗauki iya matan auren da suke bukata daga cikin 'yan'matan da ke rawa sai su da ke raka kwashe su suka tafi da su su zama matansu. Suka koma wurin gãdonsu. Suka sake gina garuruwansu suka zauna a ciki.24Daga nan mutanen Isra'ila suka bar wurin suka koma gida, kowanensu ya koma cikin kabilarsa da zuriyarsa, kowanensu kuma ga gãdonsa.25A cikin waɗannan kwanaki babu sarki a Isra'ila. Kowa yana yin abin da ya ga ya yi dai-dai a idanunsa.
Wannan bayanin asalin ya gaya wa mai karatu game da alƙawarin da Isra'ilawa suka yi a Mizfa kafin yaƙin tare da Benyaminawa.
Za a iya fassara wannan tambaya a matsayin wata sanarwa. AT: "Ah Yahweh, muna bakin ciki cewa ɗaya daga kabilan Isra'ila sun lalace gaba ɗaya"
Wannan bayanin asalin ya gaya wa mai karatu game da alƙawarin da Isra'ilawa suka yi a Mizfa kafin yaƙin tare da Benyaminawa.
AT: "sauran mutanen Benyaminawa"
Isra'ilawa sun so su samar da mata don mazajen Benyamin da suka tsira, amma alƙawarin da suka yi a Mizfa ya hana yin hakan.
Wannan sunan birni ne.
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "babu wani daga cikin mazaunan Yabish Giliyad da yake a Mizfa"
Wannan hanya ce ta ladabi da ake faɗi game da jima'i.
AT: "sun so daina fada da su"
Akwai mazajen ɗari shida daga kabilar Benyamin, amma mata ɗari huɗu kawai daga birnin Yabish Giliyad.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "mun kashe dukkan matan Benyamin"
A nan "Benyamin" na nufin zuriyar maza na Benyamin. AT: "ya ba da mace ga mazajen Benyamin"
Wannan sunan birni ne.
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "kowannenku ya kama dayan 'yan matan Shilo, ku koma da ita tare da shi zuwa kasar Benyamin don ku zama ita matarku"
AT: "ku yi mana alheri"
Wannan na nufin mazajen Shilo ne. Saboda ba su ba da 'ya'ya mata ga mazajen Benyamin yarda ba, ba su karya alƙawarin da suka yi a Mizfa.
Idani suna wakiltar gani, da gani suna wakiltar tunani ko hukunci. AT: "kowane mutum ya yi yadda ya ga dama"
1Ya kasance a kwanakin da alƙalai ke mulki, sai a ka yi yunwa a cikin ƙasar, sai kuma wani mutumin Betlehem ta Yahuda ya tafi ƙasar Mowab tare da matarsa da 'ya'yansa maza guda biyu.2Sunan mutumin Elimelek, sunan matarsa kuma Na'omi. Sunayen 'ya'yansa biyu kuwa su ne Mahlon da Kiliyon, su Ifratawa ta Betlehem ta Yahuda ne, sai suka je ƙasar Mowab suka zauna a can.3Ana nan sai Elimelek mijin Na'omi ya mutu a ka bar ta da 'ya'yanta maza biyu.4Waɗannan 'ya'ya maza suka yi aure da 'yan matan Mowabawa guda biyu, sunayensu kuwa shi ne Orfa da Rut sun zauna a can har kusan shekaru goma.5A na nan sai Mahlon da Kiliyon suka mutu, aka bar Na'omi ba miji ba 'ya'yanta guda biyu.6Daga nan sai Na'omi ta yanke shawara ta bar Mowab tare da matan 'ya'yanta zuwa Yahuda saboda ta ji cewa Yahweh ya taimaki mutanensa da ke cikin buƙata ya kuma basu abinci.7Saboda haka sai ta bar wurin da take tare da surukanta biyu, suka kama hanya don su koma ƙasar Yahuda.8Sai Na'omi ta ce da surukanta biyu "Kowaccenku ta koma gidan iyayenta. Dama Yahweh ya yi mu ku jinkai, kamar yadda ku ka nuna jinkai gare ni da kuma mamatan.9Dama Ubangiji ya ba ku hutu a gidan mazanku da za ku aura. "Sai ta sunbace su sai suka tada murya suka yi kuka.10Sai suka ce da ita "A'a za mu koma wurin mutanenki tare da ke".11Amma Na'omi ta ce, "ku koma, 'ya'yana! Don me za ku tafi tare da ni? Har yanzu ina da sauran 'ya'ya maza a cikina dominku, da za su aure ku?12Haba 'ya'yana ku koma, don na tsufa sosai har da zan yi aure, Ko da ma ace ina begen yin aure yanzu, in haifi 'ya'ya maza,13Za ku jira har su yi girma? Za ku yi ta jira ba za ku yi aure yanzu ba? A'a 'ya'yana! Hakika ina cike da baƙin ciki sosai, fiye da na ku bakin cikin, Don Yahweh ya juya mani baya."14Sai surukanta su ka sake ɗaga murya su ka ɓarke da kuka. Sai Orfa ta sumbaci surukarta suka yi ban kwana, amma Rut ta manne mata.15Na'omi ta ce, kin ga 'yar'uwarki ta koma wurin mutanenta da kuma allolinta. Ki koma tare da 'yar'uwarki."16Amma Rut ta ce, "Kar ki sa in rabu da ke, don inda za ki can za ni; inda kika zauna nan zan zauna, mutanenki za su zama mutanena, kuma Allahnki zai zama Allahna.17Inda ki ka mutu can zan mutu, a binne ni a can. Yahweh ya hukunta ni fiye da haka, idan har wani abu in ba mutuwa ba ya raba mu."18Sa'adda Na'omi ta ga Rut ta ƙudurta ta bi ta, sai ta dena gardama da ita.19Sai su biyun su ka yi tafiya har garin Betlehem. Bayan sun zo sai duk garin ya cika da murna saboda su, Sai mataye suka ce "Na'omi ce wannan?"20Amma ta ce da su "Kada ku kira ni Na'omi. Ku kira ni mai baƙinciki, don Mai Iko Dukka ya azabtar da ni.21Na fita a wadace, amma Yahweh ya sake dawo da ni gida hannu wofi. To don me ku ke kira na Na'omi, da ya ke Yahweh ya yashe ni, Mai iko dukka ya wahalshe ni?"22To Na'omi da surukarta Rut 'Yar Mowabawa su ka komo daga ƙasar Mowab. Suka zo Betlehem a farkon kakar bali.
"haka dă ta ke" ko kuma "haka ta faru". wannan wata hanya ce na gabatar da farkon labarin tarihi.
"a lokacin da alkalai su ka yi mulkin kasan isra'ila''
wannan na nufin kasan israila. AT: "a kasan israila" (Dubi: fig _explicit)
"wani mutum." wannnan wata hanya ne na gabatar da mutum a labari
su ne mutanen kabilun Ifraimu wanda suka zauna a kasan baitalami na yankin yahudiya
"Naomi na tare da 'ya'yanta maza biyu''
''matan aure.'' wannan karin magana ne na auren mata. Basu dauki matan da suna da aurensu ba,
'ya'yan Naomi sun aure mata da ga kabilan Mowab. mutanen Mowab suna bautawa wasu alloli.
''sunan wata mace ... sunan daya kuma''
shekaru goma bayan elimelek da Naomi su ka zo kasan Mowab, 'ya'yansu su Malon da Kiliyon suka rasu.
Naomi ta zama gwauruwa.
''a lokacin da Naomi ta ke zama a kasar Moab ta ji'' wannan na nuna labari ce daga israila. AT: '' ta ji da kasan israila tun da ta ke can kasan Mowab''
wannan shi ne sunan da Allah ya bayyanăwa mutanen sa a zamanin da.
Allah ya ga bukatan su ya tanada ma su abinci
matan da sun aure 'ya'yan Naomi
...
''gidan iyayyen kowace ''
''ya nuna ku na biyayya''
''alheri'' na hade da ayyukan kauna, alheri da aminci.
''zuwa ga mazajenku, da suka mutu''. Naomi ta na maganan 'ya'yanta maza biyu da suka mutu.
''ya ba ku'' ko ''ya yarda ma ku''
''kwanciyar hankali'' anan na nufin har da kwanciyar hankali a aure.
da mazajen da za su sake aure ba na wasu ba. wannan na nufin gidan mazajen su da kuma kariyan da za su samu daga kunyan zama ba aure.
daga murya wata karin magana ne da ke nufin magana da karfi. 'ya'yan suka yi kuka da karfi ko kuma kuka mai zafi
da Orfa da Rut su ka ce ''mu'' anan suna nufin su biyu ne ba tare da Naomi ba.
anan ''ke'' na nufin Naomi ne
wannan tambayan ganganci ne AT: ''ba shi da ma'ana ku tafi tare da ni.'' ko kuma ''kada ku tafi tare da ni.''
Naomi ta yi tambayan nan ne don ta nuna cewa ba za ta iya haifan wasu yayan da za su aura ba. AT: 'hakika ba zai yiwu in sake haifan yayan da za su zama mazajen ku ba.''
ana iya bayana a fili bukatan miji. AT: ''na wuce shekarun aure har in sake haifuwan yaya.''
''haifi yaya'' ko ''haifi 'ya'ya maza''
wannan tambayoyin ganganci ne. AT: ''ba za ku jira sai sun yi girma ku aure su ba. ba za ku zabi maza ku aura ba?''
AT: ''ina bakin ciki sosai yadda ba ku da mazan aure''
wannan kalma ''Hannu'' yana nufin ikon Allah ko kuwa tasiri AT:''Allah ya sa abubuwa masu muni sun faru da ni''
wannan na ma'ana sun yi kuka da karfi ko kuma sun yi kuka mai zafi.
''saurare ni sosai, domin maganan da zan fada gaskiya ne kuma ya na da muhimmanci, yar'uwarki.''
''Rut ta rike ta sossai.'' AT: ''Ruth ta ki ta rabu da ita'' ko ''Rut ta ki rabuwa da ita''
'''matan dan'uwan mijin ki'' ko ''Ofra''
kafin Ofra da Rut su aure 'ya'yan Naomi, suna da allolin su na Mowab da suke bautawa. a lokacin auren su, su ka fara bautawa Allan Naomi.
''wurin zaman ki''
Rut ta nufin mutanen Naomi, israilawa. AT: ''zan dubi mutanen kasar ki kamar nawa.'' ko ''zan dubi dangin ki kawar nawa''
wanan na nufin marmarin da Rut ta ke yi ta kasance da Naomi duk inda za ta zauna har tsawon kwanakin ran ta.
Rut na rokon Allah ya azabta ta idan bata aikata inda ta ce ba kamar karin maganan nan ''Allah ya haramta, idan''
''Naomi ta daina jayyaya da Rut''
''gari'''anan na nufin mutanen da suke zama can. AT: ''duka mutanen garin''
tun da yake shekaru masu yawa sun wuce tun da Naomi ta zauna a kasar baitalami, kuma yanzu bata da miji da yaya, mai yiwuwa ne matan garin basu iya ganewa ko Naomi ce da kanta. a fasara wanan kamar tambayya na gaskiya ba na ganganci ba.
sunan Naomi na ma'anan '' mai ni'ima na.'' tun da Naomi ta rasa mijin ta da yayanta, ba ta ji kaman wannan sunan ya dace da ita.
wannan shine fassaran ma'anan sunan. ana kuma yawan fassarar a yadda ya ke kara wato ''Mara.''
da Naomi ta bar baitalami, mijin ta da yayanta biyu suna raye, kuma tan farin ciki. Naomi na bama Allah laifin mutwan danta da mijinta, tana cewa ya sa ta ta dawo baitalami babu su, gashi yanzu tana haushi da bakin ciki.
''an yi min hukuncin mai laifi''
''bala'i ta sauko min''
AT: '' a laokacin da manoma suka fara girbin sha'ir''
1Mijin Na'omi Elimelek ya na da ɗan'uwa mai suna Bo'aza, shi mawadaci ne, sananne.2Sai Rut 'yar Mowabawa ta ce da Na'omi, "Yanzu ki bar ni in je in yi kalar abin da ya ragu a gonakin hatsi. Zan bi duk wanda na sami tagomashi a wurinsa". Sai Na'omi ta ce da ita, '"Yata, ki je."3Sai Rut ta tafi ta yi kalar abin da ya ragu a gonaki bayan sun yi girbi, Sai ta je yankin gonar Bo'aza, wanda ɗan'uwa ne ga Elimelek.4Sai Bo'aza ya zo daga Betlehem ya ce da masu girbin, "Yahweh ya kasance tare da ku" Suka amsa masa, "Yahweh ya albarkace ka."5Sai Bo'aza ya ce wa barorinsa da ke kula da masu girbin, "Wannan yarinyar ɗiyar wanene?"6Baran da ke kula da masu girbin ya amsa, "Yar Mowabawa ce da ta zo tare da Na'omi daga ƙasar Mowab.7Ta ce da ni, "Ina roƙon ka bar ni in yi kalar abin da ya rage a gonar bayan masu girbin sun girbe hatsin. Sai ta zo nan tun da safe har yanzu, sai dai ɗan shaƙatawa da ta yi a gida"8Daga nan sai Bo'aza ya ce da Rut, 'Yata ki na ji na? Kada ki bar gonata ki je wata gona don ki yi kala, amma ki tsaya nan ki yi aiki tare da barorina mata da ke aiki.9Ki zuba idonki kawai a inda masu girbin ke girbi ki na bin bayan sauran matan. Ashe ban umarci mazan da kada su taɓa ki ba? Duk lokacin da ki ka ji ƙishi sai ki je wurin tulunan ruwa ki sha ruwan da mazan su ka ɗebo."10Daga nan sai ta sunkuyar da kanta har ƙasa a gaban Bo'aza. Ta ce, 'Ta yaya na sami tagomashi a gabanka, har da zaka kula da ni, ni da nake baƙuwa?"11Bo'aza ya amsa ya ce da ita, an labarta mini duk abin da ki ka yi tun lokacin da mijinki ya mutu, kin bar babanki, da kuma ƙasarki, ki ka biyo surukarki, ki ka zo wirin mutanen da ba ki sani ba.12Yahweh ya ba ki lada kan abin da ki ka yi, dama ki sami cikkaken lada daga Yahweh, Allah na Isra'ila, wanda ki ka sami mafaka a gare shi."13Sai ta ce, "Bari in sami tagomashi a gareka, shugabana, don ka ta'azzantar da ni, ka yi mani maganar kirki, ko da ya ke ni ba ɗaya daga cikin barorinka mata ba ce."14A lokacin cin abinci sai Bo'aza ya ce da Rut "Zo nan ki ci wani abinci, ki kuma sa gutsuranki a cikin kunu." Sai ta zauna a gefen masu girbin, sai ya ba ta wani gasasshen hatsi. Ta ci har sai da ta ƙoshi ta bar sauransa.15Da ta tashi za ta yi kala sai Bo'aza ya ce da ma'aikatansa, "Ku barta ta yi kala har ma daga cikin dammunan, kada ku hana ta.16kuma ku dinga zarar ma ta zangarkun hatsin daga dammuna, ku bar ma ta ta tara ka da ku tsauta ma ta."17To sai ta yi ta kala a gonar har yamma. Daganan ta sussuke zangarkun hatsin ta sami kusan garwa biyu na bali.18Sai ta ɗauka ta tafi gari. Sai surukarta ta ga abin da ta samo. Rut kuma ta zo mata da soyayyen hatsin da ta ci ta rage sai ta bata.19Surukarta ta ce da ita, "Ina ki ka je kala yau? Ina ki ka je aiki yau? Dama mutumin da ya taimake ki ya sami albarka". Sai Rut ta faɗawa surukarta labarin mutumin da ya ke da gonar da kuma inda ta yi aiki. Ta ce "Sunan mutumin da na yi aiki a gonarsa Bo'aza"20Na'omi ta ce da surukarta Yahweh ya albarkace shi, wanda bai dena nuna amincinsa ga rayayyu da matattu ba." Na'omi ta ce wannan mutumin danginmune na kusa mai kuma fansarmu."21Rut mutumiyar Mowab ta ce, "Hakika, ya ce mani, "Ki dinga bin bayan ma'aikatana har sai sun gama girbin dukkan amfanin".22Sai Na'omi ta ce da Rut surukarta, '"Yata ya fi kyau da kike tafiya tare da ma'aikatansa 'yanmata, don ka da ki je wata gonar ki cutu."23To sai ta tsaya kusa da ma'aikatan Bo'aza 'yanmata don ta dinga kala har ya zuwa karshen kakar bali, don haka sai ta zauna tare da surukarta.
wannan maganan na gabatar da farkon bayani kamin labari ta ci gaba. idan yaren ku tana da wata hanyar gabatar da sabon bayani ayi amfani da shi anan
''shaharraren, mai arziki.'' wannan na nufin Bo'aza mutum ne sannanne mai arziki, mutumin kirki.
...
wannan wata hanya ce na cewa matan daga kasar ko kabilar Mowab
''tara kwayoyin hatsi da suka rage bayan an yi girbi'' ko kuma '' tsince kwayoyin hatsi da masu girbi suka bari a baya''
''kunnuwan hats''i su ke dauke da yayan hatsi.
wannan maganan ''samun yarda'' karin maganan ce wande ke ma'anan sami amincewa a idon wani. Rut tana maganan samun amincewa kamar samun izini ne. haka kuma idanu na wakiltan gani, gani kuma na wakiltan tunani da AT:
Rut tana lura da Naomi kamar uwa ce a wurin ta.
Rut ba ta san cewa gonan da ta je taran kwayan hatsi na dangin Naomi Boaz bane.
...
ba a fada ko ina ne wanna gonakin suke ba, da nesan su da ga Baitalami
''ya baku abbubuwa masu kyau'' ko kuwa ''ya baku farin ciki''
wannan na iya ma'ana 1)Boaz na tambaya wanene mijin Rut ko 2)Boaz na tambaya akan iyayen Rut ko masu kula da ita
''ke cajin'' ko kuwa ''ke manajan''
''Bukkan'' ko ''tsari''.wannan tsari ne ko kuwa bukka da ake gina wa a gona don inuwa
ana iya sauya wannan kamar umarni.AT:''saurare ni diya ta'' ko kuma ''ki lura da abun nan da nike gaya miki, diya ta''
wannan kyakyawar hanya ce na magana da iya mace. Rut ba iyar cikin boaz ba ce.
AT: ''duba fillin nan kawai'' ko kuwa ''sa hankali a fillin nan''
AT: ''na ba da umarni zuwa ga mazajen nan ...ke.'' (Dubi:
...
wannan na iyan nufin 1) mazan nan ba za su yi ma Rut rauni ba ko kuwa 2) mazajen nan baza su hana ta kala a gonnan shi ba
debo ruwa anan na nufin debo ruwa daga rijiya ko kuwa daga wata tafkin ruwa.
wannan ayyukan na nuna daraja ko kuwa girmamawa. ta yi haka ne domin ta nuna ma Boaz godiyar ta domin abbubuwan da yayi mata. wannan hali ne kuma na nuna tawali'u'.
Rut tana tambaya na gaskiya ne
Rut ta yi alkawari na biyayya da Allan Israila a boye, amma a idanun jama'a kuwa ita yar 'Mowab' ce.
AT: ''mutane sun kawo mini rahoto'' ko kuwa ''mutane sun gaya mini''
Boaz na maganan zuwan Rut da Naomi kasa da adinin da ba ta sani ba.
...
wannan bangaskiya ne, ta zaba zama da Naomi a Baitalami ta kuma dogara ga Allan Naomi.
AT: ''Bari Yahweh ya mayar maki fiye da inda ki ka ba da''
AT:'''wanda ki ka kuwa sanya lafiyar ki''
''yarda'' annan karin magana ce mai nufin amince wa ko kuwa ya ji dadin ta .''idanu kuwa karin magana ce mai nufin gani, gani kuma na nufin kimanatawa .AT: ''Don Allah ka karbe ni''
wannan na iya nufin 1) Rut ba daya da ga cikin bayin Boaza ba ne ko kuwa 2) Rut bata yi tunani ce wa auren ts da dan Naomi zai ba ta gata a Baitalami ba.
wannan na nufin abincin rana
...
wannan wata irin miya ce da ake tsoma gurasa a ciki.
AT: ''sa'ad da Rut ta tashi ta tara hatsi, sai Boaza ya gaya ma bayin sa''
...
...
''ku cire daga dauren ku bar mata'' ko kuwa ''ku bar wasu kunnuwan hatsin don ta samu ta tattara''
''kar ku kunyata ta'' ko kuwa ''kar ku kaskanta ta''
...
wannan na nufin sashin hatsi da ake cin (Dubi:
AT: ''wajen lita ashirirn da biyu na hatsi''
wannan na nuna Rut ta tafi da hatsin gida
''Naomi ta ga''
Naomi ta yi tambayan nan a hanya dabam dabam don ta nuna yadda ta ke marmarin sanin me ya faru da ranar Rut.
Naomi na rokon Allah ya saka wa Boaza domin alheri da ya ke nuna ma ta da Rut.
''wanda bai daina nuna alheri ba'' wannan na iya ma'anan 1) Boaza bai manta da takalifin sa a kan dangantakar sa da Naomi ba'' ko kuwa 2)Naomi na nufin Yahweh, wanda ke aiki ta bawan sa Boaza ko kuwa 3)Yahweh na ci gaba da nuna alherin sa ga masu rai da matattu.
''ga mutanen da suke da rai''. ''Naomi da Rut su ne "masu rai''.
mijin Naomi da 'ya'yan ta biyu sune ''matattu'' AT: ''mutanen da suka mutu''
...
...
''har ya ce ma ni'' wannan na nuna maganan da ya bi bayan wannan kalmomin ne ma fi muhimminci a cikin magangannun Boaza zuwa Rut.
Boaza na nufin bayin shi zasu tsare ta
''ki yi aiki da''
wannan na iya ma'anar 1) masu aikin gonakin zasu iya lalata Rut ko kuwa 2) in ta je wani gonan, mai gonan na iya hanata tsince har zuwa karshen lokacin girbi.
Rut ta yi ta aiki da ma'aikatan Boaza kawace rana, domin ta samu kariya.
Rut ta kan je gidan Naomi ta kwana.
1Surukarta, Naomi ta ce ma ta, '"Yata "Ba sai in samar miki wurin da za ki huta ba, don komai ya zamar miki dai-dai?2To yanzu shi Bo'aza da ki ke aiki tare da ma'aikantansa mata ba danginmu ba ne? Kin ga zai je shikar bali yau a masussuka.3Don haka, sai ki yi wanka ki yi kwalliya, ki sa tufafinki mafi kyau, ki tafi masussukar. Amma kada ki yarda ya gan ki har sai ya gama ci da sha.4Amma bayan ya kwanta, sai ki kula da inda ya kwanta don in an jima ki je wurinsa, ki yaye mayafinsa, ki kwanta a ƙafafunsa. Daga nan zai faɗa miki abin da za ki yi"5Rut ta ce wa Na'omi, "Zan yi duk abin da ki ka ce."6To sai ta tashi ta tafi masussukar, ta kuma bi umarnin surukarta.7Bayan Bo'aza ya ci ya sha zuciyarsa na annashuwa, sai ya je don ya kwanta a ƙarshen tarin hatsinsa. Daga nan sai ta lallaɓa ta yaye ƙafafunsa, ta kwanta.8Can wajen tsakar dare bayan mutumin ya farka, sai ya juya kawai sai ya ji mace kwance a ƙafafunsa!9Ya ce, "Ke wacece?". Ta ce, "Ni ce Rut baiwarka. Gama kai danginmune na kusa, sai ka bude mayafinka ka rufe ni."10Bo'aza ya ce '"Yata, Yahweh ya sa miki albarka. Yanzu a ƙarshe kin nuna kirki fiye da na farko, saboda ba ki je wurin matasa, ko matalauta, ko mawadata ba.11Yanzu, 'yata, ka da ki ji tsoro! Zan yi miki duk abin da ki ka ce, don duk mutanen garin nan sun san ke mace ce da ta can-canta.12Gaskiya ne ni dangi ne, amma akwai ɗan'uwan da ya fi kusa da ku fiye da ni.13Yanzu sai ki tsaya nan, da safe kuma in zai cika hakin ɗan'uwa a kanki to ya yi dai-dai, sai ya cika, Amma idan ba zai cika hakin ɗan'uwa ba to ni zan cika hakin ɗan'uwa a kanki, na rantse da Yahweh. Ki kwanta har sai da safe."14To sai ta kwanta a ƙafafunsa har sai da gari ya waye. Amma ta tashi tun kamin a fara gane mutane da sassafe. Don Bo'aza ya ce, "Don ka da a san cewa mace ta zo massusukar"15Bo'aza ya ce, "Kawo gyalenki ki shimfiɗa." Bayan ta yi haka, sai ya auna ma ta bali tiya shida a ciki ya dora ma ta. Daga nan sai ya tafi gari.16Bayan Rut ta dawo wurin surukarta sai ta ce, "Yaya ki ka yi ɗiyata?." Rut ta faɗa ma ta duk abin da mutumin ya yi ma ta.17Ta ce, "Wannan tiya shida ta bali shi ne ya ba ni, don ya ce, "Kada ki koma wurin surukarki ba tare da komai ba".18Sai Na'omi ta ce, "Yata ki zauna a nan, har sai kin san yadda al'amarin zai zama, don mutumin ba zai huta ba har sai ya gama wannan al'amarin yau."
Naomi ce uwar mijin Rut mai rasuwa.
Rut ta zama diya a wurin Naomi ta sanadin auren dan ta da kuma yadda ta ke kula da Naomi bayan da suka dawo Baitalami
Naomi tana amfani da wannan tambayan ne don ta gaya ma Rut abin da take shirya mata. AT: ''dole in nema maki wurin hutu...maki. ''dole in nema maki miji wanda zai kula da ke ... maki
wannan na iya ma'anan 1)nema mata gidan zama ko kuwa 2) nema mata mijin da zai kula da ita. ya na yiwuwa Naomi na nufin wannan biyu ne.
AT: ''ma'aikatan da ki kai ta aiki da su a gonaki'' (Dubi:
ya na iya yiwuwa Naomi ta na wannan tambayan ne don ta tuna ma Rut wani abun da ta taba gaya mata. AT: ''shi dangin mu"
wannan kalman na nuna ce wa wannan magannan na da muhimmanci sosai
wannan na ma'anan wata hanya ne da ake sheka hatsi don a cire yayi dabam.
wannan na iya nufin shafa man kamshi a jiki, kamar yadda mata su ke pesa turare a yanzu.
wannan na nufin fita da ga gari zuwa wurin massusuka.
wannan na ma'anan cire mayafin ko kuwa bargon da ka rufe kafan sa.
''kwanta a gefen kafansa''
...
''idan ya tashi, zai''
AT: ''ya gamsu'' ko kuwa ''ya na yanayi mai kyau'' (Dubi:
''ta yi tsegumi'' ko kuwa ''ta shiga a hankali yadda ba wanda zai ji shigowan ta''
''ta cire bargonsa daga kafansa''
''kwanta a gefen kafansa''
...
''a cikin tsakiyar dare''
ba a bayyana ko mene ya firgita Boaza anan ba, watakila sanyin data hura kafansa ne.
Ya duba ya ga ko mene ta firgita shi.
macen kuwa Rut ce, amma Boaza bai iya gane ta a cikin duhu ba.
Rut tayi magana da Boaza da tawali'u
wannan karin magana ne na aldan aure. AT: ''Aure ni''
dangi na kusa mai daukan takalafin iyali
''alheri ma fi girma yanzu fiye da na dã''
wannan na nufin rokon da Rut tayi wa Boaza ya aureta. auren dangin Naomi ya nuna Rut zata dinga biya ma Naomi bukatunta ta kuma nuna ma ta alheri sosai.
wannan na nufin yadda Rut da zauna da uwar Mijinta ta fita tsince don ta tanada masu da abinci.
''ba ki nema aure da'' Rut tana iya yin watsi da Naomi da fita nema ma kanta mijin aure ko da ba dangin Naomi ba ne.
wannan wajibi ne ma dangin ya taimaki gwauruwan dan uwan sa
Boaza na nufin yadda dangin mijin Rut ya kamata su aure ta don sunnan mijin ta ya cigaba.
''har ga tsawon da yahweh na da rai'' wannan alwashi ne da Ibraniyawa suke amfani da sosai.
Rut ta kwanta a gefen kafan Boaza. amma ba su yi jima'i ba.
ana iya fadi wannan kamar dare. AT: ''tun da sauran duhu''
wannan tufafi ne da ake sa a kafada
ko da yake ba a fadi ainahin yawwan hatsin ba. an kimanta shi da ya na da yawa amma bai kai inda ya fi karfin Rut daukawa ba. wasu suna cewa ya kai kusan kilo talatin.
hatsin ya yi yawa sosai Rut ta bukaci a taya ta azawa a kă.
...
AT: ''Mai ya faru, 'iya ta?'' ko kuwa ''Ya Boaza ya karbe ki?''
''duk abubuwan da Boaza yayi''
''kar ki koma hannu wofi'''ko kuwa ''kar ki koma ba komai'' ko kuwa ''ki tabbata kin rike abu''
wannan na nufin yanke shawaran wanda zai sayi dukiyan Naomi ya aure Rut.
1To sai Bo'aza ya tashi ya tafi ƙofar gari ya zauna a can. Ba da jimawa ba, sai ga wani daga cikin dangin Na'omi na kusa wanda Bo'aza ya yi maganarsa ya zo zai wuce. Bo'aza yace da shi. "Abokina, zo nan ka zauna." Sai mutumin ya zo ya zauna.2Sai Bo'aza ya kira dattawan garin guda goma ya ce, "Ku zauna nan." Sai suka zauna.3Bo'aza yace da ɗan'uwan na kusa, "Na'omi, da ta dawo daga ƙasar Mowab, za ta sayar da wata gonar ɗa'uwanmu Elimelek.4Na yi tunanin in sanar da kai in kuma yi maka magana, 'ka saye ta a gaban waɗanda ke zaune tare da mu a nan, da a gaban dattawan mutanena, In har kana so ka fanshe ta. Amma in ba ka so ka fansa sai ka faɗa mani don in sani, don ba wanda ya dace ya fanshe ta daga kai sai ni a bayanka. "Sai mutumin ya ce zan fanshe ta."5Sai Bo'aza yace "A ranar da ka sayi gonar daga hannun Na'omi, dole ne kuma ka haɗa da Rut 'yar Mowabawa, matar marigayin, don a tada sunan marigayin akan gãdonsa."6Sai wannan ɗan'uwan na kusa ya ce ba zan iya fansar ta don kaina ba, ba tare da ɓata nawa gãdon ba. Ka ɗauki tawa damar ta fansar don kanka, don ba zan iya fansar ta ba."7To wannan ita ce al'adar Isra'ila a waɗancan kwanakin akan al'amuran fansa da kuma canjin kayayyaki. Don a tabbatar da komai, sai mutum ya cire takalminsa ƙafa ɗaya ya ba maƙwabcinsa, haka ake yin yarjejeniyar da ta dace a Isra'ila.8To sai ɗan'uwan mafi kusa ya ce da Bo'aza, "Ka saye ta don kanka," sai ya tuɓe takalminsa.9Daga nan sai Bo'aza yace da dattawan da dukkan jama'ar, "Ku ne shaidu cewa yau na saye dukkan mallakar Elimelek, da duk abin da ke na Kiliyon da Mahlon daga hannun Na'omi.10Bugu da ƙari game da Rut ɗiyar Mowab, matar Mahlon; ita ma na mallake ta ta zama matata, don in tãda sunan marigayin a kan gãdonsa, don in kafa ma sa zuriya, don kada a yanke sunansa daga cikin 'yan'uwansa da kuma gidansa. Yau ku ne shaidu."11Dukkan mutanen da ke ƙofar da dattawan su ka ce, "Mu shaidune. Dãma Yahweh ya sa matar da ta zo gidanka ta zama kamar Rahila da Lai'atu, su biyu da su ka kafa gidan Isra'ila; kuma dãma ka azurta a Ifarata ka kuma yi suna a Betlehem12Dãma gidanka ya zama kamar na Ferez wanda Tamar ta haifawa Yahuda, Ta wurin zuriyar da Yahweh zai ba ka tare da wannan matashiyar mata."13Sai Bo'aza ya ɗauki Rut, daga nan ta zama matarsa. Sai ya kwana da ita, sai Yahweh ya sa ta yi ciki, sai ta haifi ɗa namiji.14Sai mataye su ka ce da Na'omi, "Albarka ta tabbata ga Yahweh, wanda bai bar ki yau ba ɗan'uwa na kusa ba, wannan yaron. Dãma ya zama sanannen mutum a Isra'ila.15Dãma ya zama mai dawo maki da rayuwa ya kuma inganta kwanakinki na tsufa, saboda wannan surukar ta ki, wadda ta ƙaunace ki, wadda ta fi 'ya'ya bakwai maza a gare ki, ce ta haife shi."16Na'omi ta ɗauki ɗan, ta rungume shi a kafaɗarta, ta kuma kula da shi.17Mataye maƙwabta su ka ba shi suna cewa, "An haifawa Na'omi ɗa," Sai suka raɗa masa suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, wanda ya haifi Dauda.18To waɗanan su ne zuriyar Ferez: Ferez ya haifi Hezron,19Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,20Aminadab ya haifi Nahshon, Nahshon ya haifi Salmon,21Salmon ya haifi Bo'aza, Bo'aza ya haifi Obed,22Obed ya haifi Yesse, Yesse ya haifi Dauda.
''kofan gannuwa'' ko kuwa ''kofan Baitalami''. Wannan ne babban hanyar shigar garin baitalami. Akwai zauren da akan yi zama a tattauna alamura da ke shafi al'umma.
wannan shine dangi ma fi kusa da Elimelek wanda ke rayyaye.
''shugabannin gari''
...
anyi haka ne domin sayar da fillin ta zama na biye da doka.
wannan na ma'anar sayar wanann fillin don kada ta fita da ga hannun wannan iyalin.
Boaza ne dangin mai bin bayan da ya kamata ya fanshe wannan filin.
Boaza na amfani da wannan maganar ne ya nuna wa dan dangin sa alhakin da yana kansa har idan ya sayi wannan filli.
kalmar ''hannu'' anan na nufin Naomi ne, wanda ke da fillin. AT: ''daga Naomi''
''tilas ne kuma ka aure Rut''
''Rut ... gwauruwar ɗan Elimelek''
''domin ta sami ɗan da zai gaji dukiyan da zai sa sunnan mijin ta marigayi ya cigaba.
zai kamata ya ba da daga cikin dukiyansa zuwa ga 'ya'yan da Rut zata haifa.
Ka fanshe shi domin kan ka'' ko kuwa ''ka fanshe shi da kan ka a maimako na''
marubucin wannan littafi na bayanin al'adar musaya a zamanin Rut.
'''a lokacin dă.'' Wannan na nufin al'adun lokacin da wannan labari ta faru ya canza a lokacin da aka rubuta littafin.
...
Wannan na nufin wanda yake wannan sharadi da shi. A wannan hali da ake ciki dangin Boaza ya ba da takalmansa ne.
wannan na nufin duka mutanen da suka kasance lokacin wannan gamuwa ne, ba duka mutanen da ke a garin ba.
Wannan na nufin duk filli da dũkiyar marigayi miji da 'ya'yan Naomi.
AT: ''domin in ba ta ɗă wanda zai gaji dukiyar marigayin''
ana maganan mantawa da mutum anan kamar an yanke sunan mutum daga sunayen wanda suka yi rayuwa a dă. AT: '' domin kada zuriyar 'yan'uwansa da kuma mutanen garinsu duka su manta da shi''
a kofar garin ake zauna a yi shawarwari masu muhimminci, kamar shawarwarin waye ke mallaka filli.
''mutanen da suke gamuwa a kofar ganuwar''
Wannan na da ma'ana biyu. Wato idan Rut ta aure Boaza , za ta zo gidansa. Gida anan kuma na iya nufin zata zama daya daga iyalin Boaza idan ta aure shi.
wadanan sune matan Yakubu, da aka canza sunnan sa zuwa Isra'ila.
''suka haifi 'ya'ya a yawa wanda suka zama al'umman Isra'ila
Efrata shi ne sunnan kabilan da Boaza ke ciki a garin Baitalami.
Allah ya albarkace Yahuda ta wurin ɗan sa Feresa. Mutanen nan suna rokon Allah ya albarkaci Boaza kamar yadda ya albarkace wadannan mutanen ta wurin 'ya'yan da Rut za ta haifa.
Tamar wata gwauruwa ce ita ma. Yahuda ya sami ɗa ta wurinta, wanda ya sa sunnan gidan ta cigaba.
Yahweh zai ba ma Boaza 'ya'ya ta wurin Rut.
''Boaza ya aure Rut'' ko kuwa ''Boaza ya dauki Rut ta zama matarsa''
AT: ''Ya yi ma'amala da ita''
AT:'' wanda ya yi miki tanadi da dangi na kusa''
wannan na nufin suna da halin jikan Naomi.
AT: ''wanda zai kawo miki farinciki kuma'' ko kuwa ''wanda zai saki ji kamar yarinya karama''
''shi zai kula da ke indan kin tsufa''
''bakwai'' shine lambar cikawa a kasar Ibraniyawa. 'ya'yan Naomi duka biyu sun mutu babu 'ya'ya, amma Rut ta haifa ma Naomi jika ta wurin Boaza. AT: ''fiye da kowani ɗa''
...
...
''wannan ɗan na kamar ɗan cikin Naomi ne''. ko da yake jika ne a wurin ta ba ɗan cikin ta ba.
''mahaifin sarki Dauda'' ko da ya ke ba a ambace ''sarki'' annan ba, amma wannan ya nuna ce wa masu sauraro sun gane cewa ana nufin Dauda wato sarki Dauda.
''zuriyar da suka biye da wadanan'' da shike an ambaci sunan Feresa a matsayin ɖan Yahuda, marubucin ya cigaba da ambata sunyen zuriyar Feresa.
1Akwai wani mutumin Ramatayim ta Zufiyawa, ta ƙasar tudu na Ifraim; Sunansa Elkana ɗan Yeroham ɗan Elihu ɗan Tohu ɗan Zuf, Ifraimiye.2Yana da mata biyu; Sunan ta farkon Hannatu, sunan ta biyun kuma Fenina. Fenina na da 'ya'ya, amma Hannatu ba ta da ko ɗaya.3Wannan mutum yakan fita daga birninsa shekara bayan shekara domin ya yi sujada ya kuma yi hadaya ga Yahweh mai runduna a Shilo. 'Ya'yan Eli maza guda biyu, Hofni da Finehas, firistocin Yahweh, suna wurin.4Idan ranar ta zo wadda Elkana ke yin hadaya ko wace shekara, koyaushe yakan ba Fenina matarsa kason nama mai yawa, da dukkan 'ya'yan ta maza da mata.5Amma ga Hannatu a koyaushe yakan ba ta kaso ruɓi biyu, gama yana ƙaunarta, koda ya ke Yahweh ya rufe mahaifarta.6Kishiyarta kuma na tsokanar ta ƙwarai da gaske domin ta tunzura ta, saboda Yahweh ya rufe mahaifarta.7Domin haka shekara bayan shekara, idan ta tafi gidan Yahweh tare da iyalinta, kishiyarta a koyaushe tana tsokanar ta. Saboda haka takan yi kuka ta ƙi cin komai.8Elkana mijinta a koyaushe sai ya ce mata, "Hannatu, me yasa ki ke kuka? Me yasa ba za ki ci komai ba? Me yasa zuciyarki ta ɓaci? Ban fi 'ya'ya maza goma ba a gareki?"9A ɗaya daga cikin irin wannan tattaruwar, sai Hannatu ta tashi bayan da suka gama ci da sha a Shilo. Yanzu dai Eli firist yana zaune a bisa mazauninsa a ƙofar hanyar zuwa shiga Haikalin Yahweh.10Tana cikin ɓacin rai mai zurfi; ta yi addu'a ga Yahweh ta kuma yi kuka mai ɗaci.11Sai ta yi wa'adi ta ce, "Yahweh mai runduna, idan za ka dubi azabar baiwarka ka kuma tuna da ni, ba za ka kuma manta da baiwarka ba, amma za ka ba baiwarka ɗa namiji, daga nan zan ba da shi ga Yahweh dukkan kwanakin ransa, ba bu kuma wata aska da za ta taɓa kansa ko kaɗan."12Yayin da ta ci gaba da addu'a a gaban Yahweh, Sai Eli ya lura da bakinta.13Hannatu ta yi magana a zuciyarta. Leɓunanta na motsawa, amma ba a jin muryarta. Sai Eli ya yi tunanin ta bugu ne.14Eli ya ce mata, "Har yaushe za ki zama cikin buguwa? ki kawar da ruwan inabinki."15Hannatu ta amsa, "A a, shugabana, ni mace ce mai ruhu cike da baƙinciki. Ban sha ruwan inabi ba ko abin sha mai ƙarfi, amma ina kwarara rai na ne a gaban Yahweh.16Kada ka ɗauki baiwar ka a matsayin mace marar kunya; Ina magana ne daga cikin yalwar damuwata da tsokanata."17Daga nan Eli ya amsa ya ce, "Tafi cikin salama; bari Allah na Isra'ila ya ba ki abin nan da ki ka roƙe shi."18Ta ce, "Bari baiwarka ta sami tagomashi a gaban ka." Daga nan matar ta yi tafiyarta ta kuma ci abinci; fuskarta kuma ba ta sake nuna baƙinciki ba.19Suka tashi da sassafe suka kuma yi sujada a gaban Yahweh, daga nan kuma suka sake komawa gidansu a Rama. Elkana ya kwana da Hannatu matarsa, Yahweh kuma ya tuna da ita.20Da lokacin ya zo, Hannatu ta ɗauki ciki ta haifi ɗa namiji. Ta kira sunansa Sama'ila, tana cewa, "Saboda na roƙo shi daga Yahweh."21Sa'an nan kuma, Elkana da dukkan gidansa suka tafi domin su miƙa wa Yahweh hadaya ta shekara - shekara ya kuma biya wa'adinsa.22Amma Hannatu ba ta tafi ba; ta riga ta faɗa wa mijinta, "Ba zan tafi ba sai an yaye yaron; daga nan zan kawo shi, domin ya kasance gaban Yahweh ya kuma zauna wurin har abada."23Elkana mijinta ya ce da ita, "Ki yi abin da ya yi dai-dai a gare ki. Ki jira sai kin yaye shi; Yahweh ya tabbatar da maganarsa, kaɗai." Sai matar ta jira ta kuma yi renon ɗanta har sai da ta yaye shi.24Da ta yaye shi, sai ta ɗauke shi tare da ita, tare da sã ɗan shekara uku, da gari mudu ɗaya, da kwalbar ruwan inabi ɗaya, ta kawo shi kuma gidan Yahweh a Shilo. To har yanzu dai yaron ƙarami ne.25Suka yanka sãn, suka kuma kawo yaron wurin Eli.26Ta ce, "Ya, shugabana! muddin ka na raye, shugabana, ni ce matar nan da ta tsaya kusa da kai tana addu'a ga Yahweh.27Domin wannan yaron na yi addu'a kuma Yahweh ya ba ni abin da na roƙa daga gare shi.28Na bayar da shi ga Yahweh, dukkan tsawon ransa an ba da shi rance ga Yahweh." Daga nan ya yi sujada ga Yahweh a wurin.
Wannan shine sunan wani karamin kauye mai yiwuwa yana da nisan kilomita takwas arewa maso yamma da Yerusalem.
Wannan sunan ƙungiyar mutane ne waɗanda suka fito daga Zuf.
Waɗannan sunayen maza.
Wannan sunan mace.
"Wannan mutum" yana nufin Elkana.
Wannan sunan Allah ne wanda ya bayyana wa mutanensa a Tsohon Alkawari. Duba translationWord shafi game da Yahweh game da yadda za a fassara wannan.
Waɗannan sunayen maza.
Wannan sunan mace ne. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 1: 1.
"sanya ta bakarariya" ko "hana ta daukar ciki"
Sauran matar tana yawan yin baƙin ciki da kunya Hannatu.
Wannan ita ce Fenina, matar Elkana kuma. Kishiya ita ce wanda ya yi gasa da wani mutum. A wannan yanayin Fenina tana gasa da Hannatu don neman Elkana ya ƙaunace ta mafi kyau.
Waɗannan tambayoyin na magana za a iya fassara su azaman maganganu, idan ya cancanta. AT: "Hannatu, ba za ku yi kuka ba. Ya kamata ku ci, kuma zuciyarku ta yi murna domin na fi ku a kan 'ya'ya maza goma!" ko "Ba ku da ɗan dalilin bakin ciki. Ina fifita ku kuma wannan ya isa."
Elkana yana wannan jimlar don jaddada muhimmancin Hannatu a gare shi. AT: "yadda kowane ɗa zai iya zama"
Hannatu ta fara addu'a ga Yahweh, Eli kuwa yana kallo.
Bayanai bayyananne anan ana iya bayyana su a sarari. Ko alfarwar Hannatu tana kusa da alfarwa ta alfarwa ko kuma ta yi tafiya daga alfarwa zuwa alfarwa don yin addu'a. AT: "Hannatu ta tashi ta tafi gidan Yahweh don yin addu'a bayan"
"Yanzu" ana amfani dashi anan don alamar hutu a layin babban labari. Anan marubucin ya faɗi game da sabon mutum a cikin labarin. Wannan mutumin firist ne Eli.
"Haikalin" haƙiƙa tanti ne, amma a wurin ne mutane suke yin sujada, don haka ya fi kyau a fassara shi "haikalin" a nan
Hannatu ta damu ƙwarai ko kuma ta yi baƙin ciki domin ba ta da yara kuma Fenina, matar mijinta ta yi mata ba'a a kai a kai.
Addu’ar Hannatu ga Yahweh ta ci gaba.
Wannan yana nufin ko dai 1) Hannatu ta kasa yin ciki. AT: "yadda nake wahala saboda ba zan iya daukar ciki ba" ko 2) yadda Fenina take wulakanta ta koyaushe. AT: "yadda waccan matar ke wahalar da ni"
Wannan roƙo ne na musamman ga Allah don ya ɗauki mataki a madadin Hannatu. Allah ya san abin da ke faruwa da Hannatu; bai manta ba.
Wannan jumlar ta faɗi kusan abu ɗaya kamar "kira ni a zuciya."
Eli babban firist ne, saboda haka yana cikin alfarwa ta Allah da kuma lura da shi.
"Ni mace ce mai bakin ciki sosai"
Wannan karin magana ne da ke nufin "gaya wa Yahweh abubuwan da ke cikin zuciyata."
Hannatu ta yi magana game da kanta a cikin mutum na biyu don nuna tawali'u. Ana iya bayyana shi a farkon mutum. AT: "Kada ku ɗauke ni bawanku, in zama" ko kuma "Kada ku ɗauke ni"
Wannan wata hanya ce ta cewa tana da "ruhun baƙin ciki," kamar yadda yake a cikin 1:15. AT: "Ina magana ne saboda bakin ciki, kuma kishiya ta tsokane ni sosai"
Eli babban firist ne wanda yake zaune a mazauni.
Hannatu ta yi magana game da kanta a cikin mutum na biyu don girmama Eli, babban firist. Ana iya bayyana wannan a farkon mutum. AT: "Bari ni, bawanka ya nemo" ko "Bari in nemo"
Anan "sami" magana ce da ke nufin a yarda da shi ko kuma ya yarda da ita. Anan idanu sunaye ne na gani, kuma gani yana wakiltar hukunci ko yanke shawarar ƙimar wani abu. AT: "sun kimanta ni kuma sun yarda"
Allah ya san abin da ke faruwa da Hannatu; bai manta da ita ba. Dubi yadda kuka fassara irin waɗannan kalmomin a cikin 1 Sama'ila 1:11.
"Hannatu tayi ciki"
Kalmar "gida" na nufin mutanen da suka rayu a gidan. AT: "danginsa"
ya daina shan madara sai ya fara cin abinci mai tauri kawai
Hannatu ta yi wa Allah alkawari cewa za ta bar Sama'ila ya zauna tare da Eli firist tare da shi a cikin haikalin (1 Sama'ila 1:11).
Wannan wakiltar kusan lita 22 na kayan busasshe.
Anan karin maganar "Kamar yadda kuke rayuwa" yana nuna cewa Hannatu tana da gaskiya da gaskiya. AT: "Shugabana, abin da zan gaya muku gaskiya ne"
Kalmar suna "koke" na nuni zuwa ga bukatar mutum don aiwatar da wani abu. Ana iya fassara shi da kalmar aikatau. Kalmomin "ba da takaddama" na nufin a yi abin da mutum ya nema. AT: "ya amince da yin abin da na roƙe shi da gaske ya yi"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Ina ba shi rance ga Yahweh"
Abubuwan da ke yiwuwa ma'anar: 1) "ya" yana nufin Elkana ko 2) "ya" magana ne wanda yake nufin Elkana da danginsa. AT: "Elkana da danginsa"
1Hannatu ta yi addu'a ta ce, "Zuciyata ta ɗaukaka Yahweh. Ƙahona ya ɗaukaka cikin Yahweh. Bakina ya yi kuri mai yawa akan maƙiyana, saboda na yi farinciki cikin cetonka.2Babu wani mai tsarki kamar Yahweh, Gama babu wani baya gare ka; babu wani dutse kamar Allahnmu.3Kada a ƙara kuri cikin matuƙar girman kai; kada wata gadara ta fito daga bakinku. Gama Yahweh Allah ne masani; shi ne ke gwada ayyuka.4Bakan mutane masu ƙarfi ya karye, amma waɗanda suka yi tuntuɓe suka sanya ƙarfi kamar ɗamara.5Waɗanda suke a cike sun bayar da kansu haya domin gurasa; waɗanda suke jin yunwa sun daina jin yunwa. Bakarariya mata haifi bakwai, amma mace mai 'ya'ya da yawa ta yi yaushi.6Yahweh na kashewa kuma ya rayar. Yana korawa ƙasa zuwa lahira yana kuma ɗagawa sama.7Yahweh yana maida wasu mutane talakawa wasu kuma masu arziki. Yana ƙasƙantarwa yana kuma ɗaukakawa sama.8Yana ɗaga talaka daga turɓaya. Yana ɗaukaka mabuƙaci daga tarin toka ya sa ya zauna tare da sarakuna ya kuma sa ya gaji wurin zama mai daraja. Gama ginshiƙan duniya na Yahweh ne ya kuma ɗora duniyar a bisan su.9Yana bida sawayen amintattun mutanensa, amma za a rufe bakin mai mugunta cikin duhu, gama babu mai yin nasara ta ƙarfi.10Waɗanda ke tsayayya da Yahweh zasu karye gutsu-gutsu; zaya yi cida daga sama a kansu. Yahweh za ya hukunta ƙarshen duniya; zaya bada ƙarfi ga sarkinsa ya kuma ɗaukaka ƙahon shafaffensa."11Daga nan Elkana ya tafi Rama, zuwa gidansa. Yaron ya bauta wa Yahweh a gaban Eli firist.12Yanzu dai 'ya'yan Eli mutane ne marasa cancanta. Ba su san Yahweh ba.13Al'adar firistoci da mutanen shi ne idan kowanne mutum ya miƙa hadaya, bawan firist za ya zo da cokali mai yatsu uku a hannunsa, yayin da naman ke tafasa.14Za ya caka cokalin a cikin kaskon, ko garwar, ko tanderun, ko tukunyar. Duk abin da cokalin ya tsamo sama firist za ya ɗaukar wa kansa. Haka suka riƙa yi a Shilo ga dukkan Isra'ilawa da suka zo wurin.15Mafi ɓaci, kafin su ƙona kitsen, bawan firist za ya zo, ya kuma cewa mutumin da ke yin hadayar, "Bayar da naman gashi domin firist; domin ba za ya karɓi dafaffen nama ba daga gare ka, sai ɗanye kaɗai."16Idan mutumin ya ce masa, "Dole ne su ƙona kitsen da farko, daga nan sai ka ɗauki iya yadda kake so." Daga nan sai ya ce, "A a, yanzu zaka ba ni; idan ba haka ba, zan ɗauka da ƙarfi da yaji."17Zunubin waɗannan yara maza ya yi girma sosai a gaban Yahweh, gama sun wulaƙanta baikon Yahweh.18Amma Sama'ila ya bauta wa Yahweh a matsayin yaro yana sanye da falmarar linin.19Mahaifiyarsa takan yi masa ƙaramar riga ta kuma kai masa daga shekara zuwa shekara, idan ta zo tare da mijinta domin miƙa hadaya ta shekara-shekara.20Eli za ya albarkaci Elkana da matarsa ya ce, "Bari Yahweh ya ba ka ƙarin 'ya'ya ta wurin wannan matar saboda roƙon da ta yi ga Yahweh." Daga nan sai su koma nasu gidan.21Yahweh ya sake taimakon Hannatu, ta kuma sake ɗaukar ciki. Ta haifi 'ya'ya maza uku mata biyu. Yayin da ake haka, yaron kuwa Sama'ila ya yi girma gaban Yahweh.22Yanzu dai Eli ya tsufa; ya ji kuma dukkan abin da 'ya'yansa maza ke yi ga dukkan Isra'ila, da yadda suke kwana da dukkan matayen da ke bauta a ƙofar shiga rumfar taruwa.23ya ce masu, "Me yasa kuke yin irin abubuwan nan? gama na ji ayyukan muguntarku daga dukkan mutanen nan."24A'a, 'ya'ya na; Ba rahoto bane mai kyau da na ji. Ku na sa mutanen Yahweh rashin biyayya.25Idan mutum ɗaya ya yi zunubai gãba da wani, Allah za ya hukunta shi; amma idan mutum ya yi zunubai gãba da Yahweh, wane ne za ya yi magana a madadinsa?" Amma ba zasu saurari muryar mahaifinsu ba, saboda Yahweh ya shirya kashe su.26Yaron kuwa Sama'ila ya girma, ya ƙaru a tagomashi tare da Yahweh tare kuma da mutane.27Yanzu dai wani mutumin Allah ya zo wurin Eli ya ce ma shi, "Yahweh ya ce, 'Ban bayyana kai na ba ga gidan kakanka, sa'ad da suke a Masar cikin ƙangin gidan Fir'auna?28Na zaɓe shi daga cikin dukkan kabilun Isra'ila ya zama firist ɗi na, ya hau zuwa bagadi na, ya kuma ƙona turare, ya sanya falmara a gabana. Na bayar ga gidan kakanka dukkan baye-bayen mutanen Isra'ila da aka yi tare da wuta.29Me yasa, daga nan, ka yi ba'a ga hadayu na da baye-bayen da na buƙata a wurin da nake zama? Me yasa ka girmama 'ya'yanka fiye da ni ta wurin mai da kanka mai ƙiba tare da kowanne baikon mutane na Isra'ila?'30Gama Yahweh, Allah na Isra'ila, ya ce, 'Na yi alƙawarin cewa gidanka, da gidan kakanka, zasu yi tafiya a gabana har abada.' Amma yanzu Yahweh ya ce, 'Ya yi nesa da ni in yi haka, gama zan girmama waɗanda ke girmama ni, amma waɗanda suka rena ni zasu sha ƙasƙanci.31Duba, kwanaki na zuwa da zan datse ƙarfinka da ƙarfin gidan mahaifinka, yadda ba za a sake samun tsohon mutum ba a cikin gidanka.32Za ka ga ƙunci a cikin wurin da nake zama. Koda ya ke abu mai kyau za a ba Isra'ila, ba za a sake samun tsohon mutum ba a gidanka.33Kowanne daga cikinku da ban datse ba daga bagadina, Zan kawo faɗawa ga idanunku, Zan kawo baƙinciki ga rayukanku. Dukkan mazajen da aka haifa a iyalinku zasu mutu.34Wannan zai zamar maka alama da zata zo bisa 'ya'yanka maza biyu, bisa Hofni da Finehas: Dukkan su zasu mutu a rana ɗaya.35Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai yi abin da ke cikin zuciyata da cikin raina. Zan gina masa tabbataccen gida; kuma za ya yi tafiya a gaban shafaffen sarkina har abada.36Duk wanda aka bari daga cikin gidanka zaya zo ya rusuna masa, yana roƙon ɓallin azurfa da gutsuren gurasa, kuma za ya ce, "Ina roƙon ka ka naɗa ni ɗaya daga cikin guraben firistoci domin in samu in ci gutsuren gurasa.""'
Hannatu ta sake rera waƙa ga Yahweh.
"Ina da babban farin ciki"
Ƙahon alama ce ta ƙarfi. AT: "Yanzu ina da ƙarfi"
Hannatu ta ci gaba da rera waƙa ga Yahweh.
Wannan wata hanya ce ta faɗi cewa Allah mai ƙarfi ne kuma mai aminci.
Hannatu ta ci gaba da rera waƙa ga Yahweh. Tana magana kamar wasu mutane suna saurarenta.
"babu kalmomin girman kai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "yana auna ayyukan mutane" ko "ya fahimci dalilin da yasa mutane suke aiki kamar yadda suke yi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh yana karya bakkunan masu ƙarfi" ko "Yahweh na iya sanya ko da mafi ƙarfi daga mutane rauni"
Wannan jimlar yana nufin ba zasu sake yin tuntuɓe ba, amma ƙarfin su zai kasance tare da su sosai kamar ɗamara. AT: "zai sa waɗanda suka yi tuntuɓe su yi ƙarfi"
"ta haifi yara bakwai"
"ya zama mai rauni da bakin ciki da kadaici"
Yahweh yana da iko akan komai.
Hannatu ta ci gaba da rera waƙa ga Yahweh.
Waɗannan maganganu ne na ƙaramar matsayi a cikin al'umma.
mutanen da ba su da abubuwan da suke buƙata
Anan "ƙafa" magana ne ta hanyar yadda mutum yake tafiya, wanda hakan kuma ishara ce ta yadda mutum ya yanke shawarar yadda zai gudanar da rayuwarsa. AT: "ka kiyaye mutanensa masu aminci daga yanke shawara na wauta" ko "bawa mutanensa amintattu damar yanke shawara mai kyau"
Wannan hanyar ladabi ta cewa Yahweh zai kashe miyagu ana iya bayyana ta cikin aiki. AT: "Yahweh zai sa mugaye su yi shuru cikin duhu" ko "Yahweh zai sa mugaye cikin duhu da duniyar matattu"
"saboda yana da ƙarfi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai karya waɗanda suka yi adawa da shi"
Wannan karin magana ne da ke nufin ko'ina. AT: "duk duniya"
ƙahon alama ce ta ƙarfi. Duba yadda kuka fassara irin waɗannan kalmomin a cikin 1 Sama'ila 2: 1. AT: "zai sanya shugaban da ya zaɓa ya fi abokan gaba ƙarfi"
Idan mutane zasu bada hadaya, zasu fara kona kitse na dabbar sannan su dafa naman su cinye.
"bai saurari Yahweh ba" ko "bai yi biyayya ga Yahweh ba"
Al'ada wani aiki ne da mutane suke yi a kai a kai.
Waɗannan kwantena ne waɗanda za'a dafa abinci dasu. Idan yarenku bashi da kalmomi daban don waɗannan abubuwa ana iya bayyana shi gaba ɗaya. AT: "a cikin duk abin da mutane ke dafa naman a ciki"
Lokacin da mutane zasu bada hadaya, zasu fara kona kitsen dabbar sannan su dafa naman, su baiwa firist, su ci sauran.
"Har ma sun yi abin da ya fi wannan. Kafin"
Mutumin da ya yi ƙonewa za a iya bayyana shi a bayyane. AT: "mutumin da yake ba da hadaya ya kai wa firistocin kuma firistocin sun ƙone"
"Bani ɗan nama don in bashi wa firist ɗin ya soya shi"
Samarin ba su ji daɗin umarnin Yahweh a kan hadayar ba, ba su kula da su ba.
Hannatu ta roƙi Yahweh don a ba ta jariri kuma ta yi masa alkawari cewa za ta ba da yaron don yin hidima a cikin haikalin.
Wannan yana nufin inda Yahweh zai iya ganinsa kuma Sama'ila ya iya koyo game da Yahweh
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Abin takaici ne yadda kuke yin waɗannan abubuwan!"
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "tabbas babu wanda zai iya magana saboda shi."
Anan “muryar” uba tana wakiltar uba. AT: "mahaifinsu" ko "abin da mahaifinsu ya ce"
Wannan jimlar galibi tana nufin annabin Yahweh. AT: "mutumin da ya ji kuma ya faɗi kalmomi daga wurin Allah"
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Ya kamata ku sani cewa na bayyana kaina ... gida."
Kalmar "gida" magana ne ga mutanen da suka rayu a gidan. AT: "dangin kakanka"
Wannan yana nufin yin hadaya ga Yahweh.
Kalmomin “sanya falmara” kalmoni ne ta aikin firistocin da ke sa falmaran. AT: "su yi abin da na umarci firistoci su yi"
Wannan tambayar tsawatarwa ce. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Bai kamata ku raina sadaukarwata ba ... a inda nake zaune."
Mafi kyawun hadayar za a ƙone ta a matsayin hadaya ga Yahweh, amma firistocin suna ci.
Wannan karin magana ne wanda ke nufin "rayu cikin biyayya gareni."
"Lallai ba zan bari iyalanka su yi min hidima ba har abada"
Kalmomin "ɗauka da daraja" kalma ce ta izgili don "raina ƙwarai." Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan ɗaukaka waɗanda suka raina ni da sauƙi" ko "Zan raina waɗanda suka raina ni ƙwarai"
"Ku saurari abin da zan ce da kyau" ko "Abin da zan faɗa yana da mahimmanci"
Kalmomin "yanke ... ƙarfi" wataƙila kalmomi ne don mutuwar ƙaƙƙarfan ƙarfi, samari; kalmomin "gidan mahaifinka" sunaye ne na "danginku." AT: "Zan kashe ku da dukkan ƙarfi, samari daga zuriyar ku a cikin danginku"
"zama kowane dattijo" ko "kasance duk wani mazan da ya tsufa"
"zai sa ka rasa gani" ko kuma "ya sa ka makance"
Wannan karin magana ne. AT: "Zan sa mutum ya zama firist"
"abin da nake so ya yi da kuma abin da na ce masa ya yi"
Anan "gida" wani karin magana ne da ake amfani da shi don "zuriya." AT: "Zan tabbatar da cewa koyaushe yana da zuriyar da ke aiki a matsayin babban firist"
Anan ana amfani da "gutsuren gurasa" don "abinci." AT: "don haka zan sami abin da zan ci"
1Yaron nan Sama'ila ya bauta wa Yahweh a gaban Eli. Maganar Yahweh ta yi ƙaranci a waɗannan kwanaki; babu yawan wahayin anabci.2A wannan lokaci, sa'ad da Eli, wanda idanunsa sun fara yin dishi-dishi yadda ba ya iya gani sosai, yana kwance a bisa nasa gadon.3Fitilar Allah bata riga ta mutu ba, kuma Sama'ila yana kwance domin ya yi barci a haikalin Yahweh, inda akwatin Yahweh ya ke.4Yahweh ya yi kira ga Sama'ila, wanda ya ce, "Ga ni nan."5Sama'ila ya ruga wurin Eli ya kuma ce, "Ga ni nan, gama ka kira ni." Eli ya ce, "Ban kira ka ba, ka sake kwantawa." Sai Sama'ila ya koma ya sake kwantawa.6Yahweh ya sake kira, "Samai'la." Sama'ila ya sake tashi ya tafi wurin Eli ya kuma ce, "Gani nan, gama ka kira ni." Eli ya amsa, "Ban kira ka ba, ɗana, ka sake kwantawa."7Yanzu dai Sama'ila bai taɓa samun wata gamuwa da Yahweh ba, ko wani saƙo daga Yahweh ya taɓa bayyana a gare shi ba.8Yahweh ya sake kiran Sama'ila karo na uku. Sama'ila ya sake ta shi ya tafi wurin Eli ya ce, "Ga ni nan, gama ka kira ni." Daga nan Eli ya fahimci cewa Yahweh ya kira yaron.9Daga nan Eli ya cewa Sama'ila, "Ka je ka sake kwantawa kuma, idan ya sake kiran ka, dole ka ce, 'Yi magana, Yahweh, gama bawanka yana saurare."' Daga nan Sama'ila ya tafi kuma ya sake kwantawa a na sa wurin kuma.10Yahweh ya zo ya tsaya; ya yi kira kamar sauran lokuttan, "Sama'ila, Sama'ila." Daga nan Sama'ila ya ce, "Yi magana, gama bawanka yana sauraro."11Yahweh ya cewa Sama'ila, duba, Ina gaf da yin wani abu a Isra'ila wanda kunnuwan dukkan wanda za ya ji za su karkaɗa.12A wannan rana zan aiwatar ga Eli dukkan abin da na ce game da gidansa, daga farko har ƙarshe.13Na gaya masa ina gaf da hukunta gidansa karo ɗaya tak domin zunubin da ya riga ya sani, saboda 'ya'yansa sun kawo la'ana a kansu bai kuma hana su ba.14Saboda wannan na yi rantsuwa game da gidan Eli cewa zunuban gidansa ba za a iya yi masu kaffara ba da hadaya ko baiko."15Sama'ila ya kwanta har gari ya waye; daga nan ya buɗe ƙofofin gidan Yahweh. Amma Sama'ila ya ji tsoron gaya wa Eli game da wahayin.16Daga nan Eli ya kira Sama'ila ya ce, "Sama'ila, ɗana." Sama'ila ya ce, "Ga ni nan."17ya ce, "Wacce magana ce ya faɗi maka? Ina roƙon ka kada ka ɓoye mani. Bari Allah ya yi maka haka, fiye da haka ma, idan ka ɓoye wani abu daga gare ni a dukkan maganganun da ya faɗi maka."18Sama'ila ya faɗi masa dukkan abu; bai ɓoye masa komai ba. Eli ya ce, "Yahweh ne. Bari ya yi abin da ya yi kyau a gare shi."19Sama'ila ya yi girma, kuma Yahweh na tare dashi kuma bai bar ko ɗaya daga cikin maganganun anabcinsa ba su kãsa zama gaskiya.20Dukkan Isra'ila daga Dan zuwa Biyasheba suka sani cewa an naɗa Sama'ila annabin Yahweh.21Yahweh ya sake bayyana a Shilo, gama ya bayyana kansa ga Sama'ila a Shilo ta wurin maganarsa.
"Yahweh baya yawan magana da mutane"
Wannan alkukin ne na fitilun fitila guda bakwai a cikin tsattsarkan wuri na alfarwa da take ci kowace rana da dare har zuwa wofi.
"Haikalin" haƙiƙa a rumfar ne, amma a wurin ne mutane suke yin sujada, don haka ya fi kyau a fassara kalmar a matsayin "haikalin" a nan. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Samuila 1: 9.
Eli ba shi ne mahaifin Sama’ila na gaske ba. Eli yayi magana kamar wanda shi ne mahaifin Sama’ila don ya nuna wa Sama’ila cewa bai yi fushi ba amma Sama’ila yana bukatar ya saurare shi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kuma Yahweh bai taɓa bayyana masa wani saƙo ba" ko "kuma Yahweh bai taɓa bayyana masa wani saƙo ba"
Eli ya gaya wa Sama'ila ya yi magana da Yahweh kamar Sama'ila wani mutum ne don Sama'ila ya girmama Yahweh. AT: "Ni ne"
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) Yahweh ya bayyana a zahiri kuma ya tsaya a gaban Sama'ila ko 2) Yahweh ya bayyana gaban Sama'ila ga Sama'ila.
Sama'ila yayi magana da Yahweh kamar Sama'ila wani mutum ne don ya girmama Yahweh. AT: "Ni ne"
Anan "kunnuwa ... za su tsuji" wani karin magana ne da ke nufin kowa zai gigice da abin da ya ji. AT: "wannan zai girgiza duk wanda ya ji shi"
Wannan magana ne ga cikakke. AT: "kwata-kwata komai"
"ya aikata abin da Yahweh ya ce zai hukunta waɗanda suka aikata su"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "babu wata sadaukarwa ko hadaya da kowa zai iya bayarwa wanda zai kankare zunuban gidansa"
"Gidan" a zahiri rumfar ne, amma zai fi kyau a fassara "gida" a nan.
"sakon da Yahweh ya bayar"
Wannan karin magana ne don jaddada yadda Eli yake da hankali. AT: "Allah ya yi muku azaba kamar yadda ya ce zai hukunta ni, har ma da ƙari"
Anan ana maganar sakonnin da basu zama gaskiya ba kamar sun fadi kasa. Ana iya bayyana hakan da kyau. AT: "ya sanya duk abubuwan da ya annabta sun faru"
"Dukkan mutanen Isra'ila"
Wannan magana ne ga "a kowane yanki na ƙasar." AT: "daga wannan ƙarshen ƙasar zuwa wancan" ko "daga Dan a cikin arewa sosai zuwa Biyasheba a kudu" sosai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya sanya"
1Maganar Sama'ila ta zo ga dukkan Isra'ila. Yanzu dai Isra'ila sun fita yaƙi gãba da Filistiyawa. Suka kafa sansani a Ebeneza, Filistiyawa kuma sukakafa sansani a Afek.2Filistiyawa suka jera domin yaƙi gãba da Isra'ila. Da aka baza yaƙin, Filistiyawa sukakayar da Isra'ila, wanda sukakashe wajen mutum dubu huɗu a filin yaƙin.3Da mutanen suka zo cikin sansanin, dattawan Isra'ila suka ce, "Me yasa Yahweh yakayar damu yau a gaban Filistiyawa? Bari mu kawo akwatin alƙawarin Yahweh a nan daga Shilo, domin yakasance a nan tare da mu, domin ya ajiye mu a tsare daga hannun maƙiyanmu."4Sai mutanen suka aiki mazaje zuwa Shilo; daga nan suka ɗauko akwatin alƙawarin Yahweh mai runduna, wanda ke zaune a bisa kerubim. 'Ya'yan Eli maza biyu, Hofni da Finehas, suna nan tare da akwatin alƙawarin Allah.5Da akwatin alƙawarin Yahweh ya iso cikin sansani, dukkan mutanen Isra'ila suka yi babbar kururuwa, har ƙasa ta amsa.6Da Filistiyawa suka ji ƙarar kururuwar, suka ce, "Me wannan ƙarar kururuwar a cikin sansani Ibraniyawa ke nufi?" Sai suka tantance cewa akwatin Yahweh ya zo cikin sansanin.7Filistiyawa suka tsorata; suka ce, "Wani allah ya shigo cikin sansanin." Suka ce, "Kaitonmu! Babu wani abu kamar haka da ya faru a dã!8Kaitonmu! Wane ne zai cece mu daga ƙarfin waɗannan alloli masu iko? Waɗannan allolin ne sukakaiwa Masarawa hari da allobai iri-iri a cikin jeji.9Ku yi ƙarfin hali, ku kuma zama mazaje, ku Filistiyawa, ko kuwa ku zama bayi ga Ibraniyawa, kamar yadda suke bayi a gare ku. Ku zama mazaje, ku kuma yi faɗa."10Filistiyawa suka yi faɗa, aka kumakayar da Isra'ila. Kowanne mutum ya tsere zuwa gidansa, kisan da aka yi babba ne ƙwarai; gama sojojin ƙasa dubu talatin ne daga Isra'ila suka faɗi.11Aka ɗauke akwatin Allah, 'ya'yan Eli maza biyu kuma, Hofni da Finehas, suka mutu.12Wani mutumin Benyamin ya gudu daga fagen yaƙin ya kuma zo Shilo a ranar nan, ya iso da tufafinsa a yage da kuma ƙasa bisakansa.13Da ya iso, Eli na zaune bisa mazauninsa a bakin hanya yanakallo saboda zuciyarsa na fargaba tare da damuwa domin akwatin Allah. Da mutumin ya shiga cikin birnin ya faɗi labarin, dukkan birnin aka yi kuka.14Da Eli ya ji ƙarar kukan, ya ce, "Mene ne ma'anar wannan yamitsin?" Mutumin ya zo da sauri ya kuma faɗa wa Eli.15Yanzu dai Eli shekarunsa tasa'in da takwas; idanunsa ba su fuskanta dai-dai, kuma baya gani.16Mutumin ya cewa Eli, "Ni ne na zo daga fagen yaƙin. Na gudo daga yaƙin yau." Eli ya ce, "Ya abin ya tafi, ɗa na?"17Mutumin da yakawo labarin ya amsa kuma ya ce, "Isra'ila sun gudu daga Filistiyawa. Haka kuma, babbar kayarwa takasance a tsakanin mutanen. Haka kuma, 'ya'yan ka maza biyu, Hofni da Finehas, sun mutu, akwatin Allah kuma an ɗauke."18Da ya faɗi akwatin Allah, Eli ya fãɗi ta baya daga bisa kujerarsa ta gefen ƙofa. Wuyansa yakarye, ya kuma mutu, saboda ya tsufa kuma yana da nauyi. ya yi alƙalancin Isra'ila shekaru arba'in.19Yanzu dai surukarsa, matar Finehas, tana da ciki kuma ta yi gaf da haihuwa. Da ta ji labarin an cafke akwatin Allah da surukinta da mijinta kuma sun mutu, ta durƙusa kuma ta haihu, amma zafin naƙudarta ya mamaye ta.20Wajen lokacin mutuwarta matan da ke yi mata unguwar zoma suka ce mata, "Kada ki ji tsoro, gama kin haifi ɗa namiji." Amma ba ta amsa ba ko ta ɗauki abin da suka ce a zuciya.21Ta raɗa masa suna Ikabod, cewa, "Ɗaukaka ta tafi da ga Isra'ila!" domin an cafke akwatin Allah, saboda kuma surukinta da mijinta.22Ta ce, "Ɗaukaka ta tafi daga Isra'ila, saboda an cafke akwatin Allah."
Waɗannan su ne sunayen wuraren. (Duba: Translate_names)
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Filistiyawa sun ci Isra'ilawa kuma sun kashe"
Anan lambar ta dubu hudu lambar zagaye ce. Zai yiwu a sami fewan kaɗan fiye da hakan ko kuma 'yan ƙasa da hakan. Kalmar ''wajen '' tana nuna cewa ba shine ainihin lambar ba. AT: "kimanin maza 4,000"
sojojin da suka kasance suna yaƙi
Da gaske dattawan ba su san dalilin da ya sa Yahweh ya ci su ba, amma sun yi kuskuren tunanin sun san yadda za su tabbatar da hakan ba ta sake faruwa ba, ta hanyar kawo akwatin don ya kasance tare da su.
Kuna iya bayyanawa a sarari cewa kerubobin sune waɗanda suke kan murfin akwatin alkawari. Marubutan Littafi Mai Tsarki sau da yawa suna magana game da akwatin alkawari kamar dai matashin sawun Yahweh ne wanda ya dogara da ƙafafunsa yayin da yake zaune a kan kursiyinsa a sama. AT: "wanda ke zaune a kan kursiyinsa sama da kerubim a kan akwatin alkawari"
"Lokacin da mutane suka ɗauki akwatin alkawarin Yahweh cikin zango" Wasu yaruka na iya buƙatar ƙara bayanan da aka fahimta don yin ma'anar a sarari. AT: "Mutanen, tare da Hophni da Finehas, suka ɗauki akwatin alkawarin Yahweh suka ɗauke shi zuwa zangon. Lokacin da mutanen suka ɗauki akwatin a cikin zangon"
"sun fada wa kansu ... Sun ce wa juna" ko "sun ce wa juna ... Sun ce da juna." Sashe na biyu a fili yana nuni ga abin da Filistiyawa suka faɗa wa juna. Yankin farko yana iya nufin abin da suke tsammani, kodayake yana iya nufin abin da suka faɗa wa juna. Idan za ta yiwu, kauce wa bayyana wa aka yi magana da shi.
Filistiyawa suna bauta wa alloli da yawa, don haka wataƙila sun yi imani cewa ɗayan allolin, ko kuma wanda ba sa bauta wa, ya zo sansanin. Wata ma'ana mai yiwuwa ita ce suna magana da sunan Allah na Isra'ila mai dacewa: "Yahweh ya zo." Saboda 1 Sama'ila 4: 8 yayi magana akan "alloli," wasu fassarar sun karanta, "Alloli sun zo," ma'ana, "Alloli ne suka zo."
Wannan tambaya yana nuna tsananin tsoro. Ana iya rubuta shi azaman bayani. AT: "Babu wanda zai iya kare mu daga waɗannan manyan alloli."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Hakanan, "Isra'ila" tana nufin sojojin Isra'ila. AT: "sun fatattaki sojojin Isra'ila"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Filistiyawan kuma sun ɗauki akwatin alkawarin Allah"
Wannan hanya ce ta nuna baƙin ciki mai yawa a cikin al'adun Isra'ilawa.
Wannan karin magana ne wanda ke nufin ya kasance mai matukar tsoro ko kuma damuwa matuka game da wani abu.
"Mutumin Benyamin"
Wannan bayani ne na gaba ɗaya game da abin da ya faru. Sauran kalmomin mutumin suna ba da cikakken bayani.
"Yanzu zan fada muku wani abu mafi muni ... yanzu zan fada muku wani abu mafi muni" ko "Ba wai kawai an samu ... mutane ba, amma 'ya'yanku maza biyu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Filistiyawan sun ɗauki akwatin alkawarin Allah"
"Lokacin da mutumin Benyamin ya ambata"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Wuyansa ya karye saboda ya faɗi" ko "Ya karye wuyansa lokacin da ya faɗi"
surukar Eli
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Filistiyawa sun kama akwatin alkawarin Allah"
"ku kula da abin da suka faɗa" ko "ƙyale kanta ta ji daɗi"
Sunan ainihin magana ce da ke nufin "babu ɗaukaka." Sunan mutum wani lokaci yakan bayyana bayani game da mutum, wuri, ko abin da yake nufi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "don Filistiyawan sun kama akwatin alkawarin Allah"
1Yanzu dai Filistiyawa sun cafke akwatin Allah, su ka kumakawo shi daga Ebeneza zuwa Asdod.2Filistiyawa suka ɗauki akwatin Allah, sukakawo shi cikin gidan Dagon, suka jera shi a gefen Dagon.3Da mutanen Asdod suka tashi da sassafe washegari, duba, Dagon ya faɗi ƙasa da fuskarsa ƙasa gaban Yahweh. Sai suka ɗauki Dagon suka kuma sake jera shi a wurinsa.4Amma da suka tashi da sassafe washegari, duba, Dagon ya faɗi ƙasa da fuskarsa ƙasa a gaban akwatin Yahweh. Kan Dagon da hannuwansa suna kwance datsastsu a hanyar ƙofa. Gangar jikin Dagon kawai ya rage.5Wannan ne yasa, har yau ma, firistocin Dagon da ko wane ne ya zo cikin gidan Dagon ba ya taka hanyar ƙofar Dagon a Asdod.6Hannun Yahweh kuwa ya yi nauyi a bisa mutanen Asdod. Ya lalatar da su ya azabce su da marurai. Asdod duk da kewayenta.7Da mutanen Asdod suka lura da abin da ke faruwa, suka ce, "Akwatin Allahn Isra'ila dole ba za ya zauna ta re da mu ba, saboda hannunsa ya yi tsanani gãba da mu da gãba da allahnmu Dagon."8Sai suka aika suka kuma tattaro tare dukkan shugabannin Filistiyawa; suka ce masu, "Me za mu yi da akwatin Allah na Isra'ila?" Suka amsa, "Bari akawo akwatin Allah na Isra'ila zuwa Gat." Sai suka ɗauki akwatin Allah na Isra'ila zuwa can.9Amma bayan da sukakawo shi wurin, hannun Yahweh ya yi gãba da birnin, ya sanya babbar ruɗewa. Ya azabtar da mutanen birnin, ƙarami da babba dukka; marurai kuma suka faso akansu.10Sai suka aika da akwatin Allah zuwa Ekron. Amma nan da nan da akwatin Allah ya zo cikin Ekron, Ekroniyawa suka koka, cewa, "Sun kawo mana akwatin Allah na Isra"ila domin yakashe mu da mutanenmu."11Sai suka aika aka tattaro tare dukkan shugabannin Filistiyawa; suka ce masu, "Ku aika da akwatin Allah na Isra'ila, bari kuma ya koma na sa wurin, domin kada yakashe mu da mutanenmu." Domin akwai razana mai mutuwa cikin dukkan birnin; hannun Allah yana da nauyi sosai a wurin.12Mutanen da ba su mutu ba an azabce su da marurai, kukan birnin kuma ya hau zuwa sammai.
Wannan kalmar ita ce farkon sabon sashin labarin. Idan yarenku yana da kalma ko jumla wanda yayi haka, kuna iya amfani da shi anan.
Wannan yana nufin haikalin Dagon, allahn Filistiyawa.
Ya kamata mai karatu ya fahimci cewa Yahweh ne ya sa mutum-mutumin ya faɗi a fuskarsa cikin dare. (|Assumed Knowledge|da Implicit Information)
Kamar dai Yahweh soja ne wanda ya ci nasara a kan maƙiyinsa ya datse kansa da hannayen magabcin.
Marubucin yana gab da bayar da wasu bayanan daban daban da babban labarin.
Wannan karin magana ne. "Yahweh yayi hukunci mai tsanani"
Mai yiwuwa ma'anoni sune 1) kumburi mai raɗaɗi ƙarƙashin fata ko 2) basur.
Sunan garin suna ne nuna mutanen da ke zaune a garin. AT: "duka mutanen Ashdod da mutanen da ke cikin ƙasar da ke kewaye da Ashdod"
Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 3: 3. Wannan dai-dai yake da "akwatin alkawarin Allah" a cikin 1 Sama'ila 4: 3.
Wannan karin magana ne. AT: "An hukunta Yahweh"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan magana ne wanda ke nufin shekaru. AT: "maza na kowane zamani" ko 2) wannan magana ne wanda ke nuni da ajin zamantakewar. AT: "daga mafi talauci da rauni zuwa ga mawadata da mafiya ƙarfi"
Dalilin da ya sa suka yi kuka za a iya bayyana a sarari. AT: "ya yi ihu cikin tsoro"
"Mutane a duk faɗin garin suna tsoron kada su mutu"
Hannu yana nuna don Allah yana azabtar da mutane. AT: "Yahweh yana azabtar da mutanen wurin sosai"
Wannan yana nuna cewa maza da yawa sun mutu.
Kalmar "birni" yana nuna mutanen garin. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) kalmomin "haura zuwa sammai" karin magana ne ta "ta kasance mai girma ƙwarai." AT: "mutanen birni sun yi ihu da ƙarfi" ko 2) kalmomin "sammai" magana ne ta gumakan mutane. AT: "mutanen birni sun yi kuka ga gumakansu"
1Yanzu dai akwatin Yahweh na cikin ƙasar Filistiyawa har watanni bakwai.2Daga nan Mutanen Filistiyawa suka kira firistoci da masu sihiri; suka ce masu, "Me zamu yi da akwatin Yahweh? ku gaya mana yadda zamu aika da shi zuwa ƙasarsa."3Firistoci da masu sihiri suka ce, "Idan kuka aika da akwatin Allah na Isra'ila, kada ku aika da shi ba tare da kyauta ba; ta ko ƙaƙa ku aika masa da baiko na laifi. Daga nan zaku warke, daga nan kuma zaku ga ne dalilin da yasa hannunsa bai ɗauke ba daga bisanku har yanzu.4Daga nan suka ce, "Mene ne za ya zama baiko na laifin da zamu maida masa?" Suka maida amsa, "Marurai na zinariya biyar da ɓerayen zinariya biyar, biyar lissafin yawa ne wanda ya yi dai-dai da lissafin yawan shugabannin Filistiyawa. Domin annoba iri ɗaya ce ta azabce ku da shugabanninku.5Dole ku yi marurai na kwaikwayo, da ɓerayen kwaikwayo da suka addabi ƙasar, ku kuma bada ɗaukaka ga Allah na Isra'ila. Wataƙila zai ɗauke hannun sa daga gare ku, daga allolinku, daga kuma ƙasarku.6Me yasa zaku taurare zukatanku, kamar yadda Masarawa da Fir'auna suka taurare zukatansu? Ta haka Allah na Isra'ila ya tsananta masu da zafi; Ashe Masarawan basu fitar da mutanen ba, suka kuma tafi?7To yanzu, ku shirya amalanke da shanu biyu masu shayarwa waɗanda ba a taɓa ɗaurawakarkiya ba. Ku ɗaura shanun ga amalanken, amma ku ɗauki 'yan maruƙansu daga gare su, ku kai gida.8Daga nan ku ɗauki akwatin Yahweh ku sa cikin amalanken. Ku sanya siffofin zinariyar da zaku maida masa a matsayin baiko na laifi cikin wani akwatin a gefensa. Daga nan ku aika da shi kuma bari ya tafi hanyarsa.9Daga nan ku kalla; Idan ya yi tafiyarsa bisa hanya zuwa cikin ƙasarsa zuwa Bet Shemesh, to Yahweh ne ya zartar da wannan babban bala'i. Amma idan ba haka ba, daga nan za mu sani cewa ba hannunsa ba ne ya azabtar damu ba; maimakon haka, zamu sani cewa ya faru da mu ne hakakawai."10Mutanen suka yi yadda aka gaya masu; suka ɗauki shanu biyu masu shayarwa; suka ɗaura su ga amalanken, suka tsare 'yan maruƙansu a gida.11Suka sanya akwatin Yahweh a cikin amalanken, tare da akwatin da ke ɗauke da ɓerayen zinariyar da sarrafaffun maruransu.12Shanun suka tafi a miƙe a hanyar Bet Shemesh. Suka tafi bisa babbar hanya, suna tafiya suna kuka, ba su kumakauce daga hanya ba ko zuwa dama ko zuwa hagu. Shugabannin Filistiyawa suka bi bayansu har zuwakan iyakar Bet Shemesh.13Yanzu dai mutanen Bet Shemesh suna girbin alkamarsu a kwari. Da suka ɗaga idanunsu suka ga akwatin, suka yi farinciki.14Amalanken ya iso cikin gonar Yoshuwa daga Bet Shemesh ya kuma tsaya a wurin. Wani babban dutse na wurin, suka tsinke itacen amalanken, suka miƙa shanun a matsayin baikon ƙonawa ga Yahweh.15Lebiyawa suka sauke akwatin Yahweh da akwatin da ke tare da shi, inda siffofin zinariyar suke, suka ɗora su bisa babban dutsen. Mutanen Bet Shemesh suka miƙa baye-baye na ƙonawa suka kuma yi hadayu a wannan rana ga Yahweh.16Da shugabannin Filistiyawa biyar suka ga haka, suka koma Ekron a ranar.17Waɗannan ne maruran zinariya da Filistiyawa suka maido domin baiko na laifi ga Yahweh: ɗaya domin Asdod, ɗaya domin Gaza, ɗaya domin Askelon, ɗaya domin Gat, ɗaya domin Ekron.18Ɓerayen zinariyar ma lissafinsu ya yi dai-dai da lissafin dukkan biranen Filistiyawa da sukakasance na shugabannin biyar, dukkansu tsararrun birane ne da ƙauyukansu. Babban dutsen, gefen da aka ajiye akwatin Yahweh, ya zama shaida har yau a cikin filin Yoshuwa Betshemiye.19Yahweh yakai hari ga wasu daga cikin mutanen Bet Shemesh saboda sun duba cikin akwatin Yahweh. Yakashe mutum 50,070. Mutanen suka yi makoki, saboda Yahweh ya ba mutanen babban naushi.20Mutanen Bet Shemesh suka ce, "Wane ne zaya iya tsayawa gaban Yahweh, wannan Allah mai tsarki? daga gare mu wurin wa akwatin zaya tafi?"21Suka aika manzanni zuwa ga mutanen Kiriyat Yerim, cewa, "Filistiyawa sun maido da akwatin Yahweh; ku zo ku ɗauka ku kuma koma da shi tare da ku."
Waɗannan firistocin arna ne da masu duba waɗanda suke bautar Dagon.
Filistiyawa suna so su san yadda za su kawar da jirgin ba tare da ƙarin fushin Yahweh ba.
Kalmomin "ta kowace hanya" hanya ce mai ƙarfi ta faɗar wani abu. AT: "dole ne ku aika da hadaya don laifi"
"ba za ku ƙara rashin lafiya ba"
Anan "hannu" wani magana ne wanda ake amfani dashi don wakiltar ikon Allah don azaba ko horo. AT: "me yasa bai sauƙaƙa wahalar ku ba"
linzamin kwamfuta sama da daya
Samfurin wani abu ne wanda yake kamar da ainihin abu
Anan "hannu" wani magana ne wanda ake amfani dashi don wakiltar ikon Allah don azaba ko horo. AT: "ku daina azabtar da ku, gumakanku da ƙasarku"
Firistoci da matsafa suna amfani da tambaya don ƙarfafa Filistiyawa su yi tunani sosai game da abin da zai faru idan suka ƙi yin biyayya ga Allah. Ana iya fassara wannan azaman faɗakarwa. AT: "Kada ku taurare kamar Masarawa da Fir'auna!"
Wannan wata tambaya ce ta magana da aka yi amfani da ita don tunatar da Filistiyawa yadda Masarawa a ƙarshe suka kori Isra'ilawa daga Masar don Allah ya daina wahalar da Masarawa. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "ku tuna cewa Masarawa sun kori Isra'ilawa daga Masar."
"shanu biyu da ke da 'yan maruƙan da har yanzu suna shan madara"
A ka'ida shanu biyun za su koma gidansu ga 'ya'yan maruran.
Yana da wuya a ce shanun sun zaɓi su yi yawo zuwa Bet Shemesh lokacin da 'yan maruƙansu suka dawo yankin Filistiyawa.
Shanu masu shayarwa koyaushe za su koma cikin ’yan maruƙansu, amma waɗannan shanun sun tafi Bet Sshemesh.
Ragewa shine sautin da shanun ke yi da muryoyin su.
"ba su kauce daga babbar hanya ba." Ana iya bayyana hakan da kyau. AT: "sun tsaya a kan babbar hanya" ko "sun ci gaba kai tsaye"
Marubucin yana gabatar da sabon sashi na labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin alama ga farkon sabon ɓangaren labarin, kuna iya amfani da shi anan.
Waɗannan Isra'ilawa ne.
Wannan karin magana ne. AT: "an duba"
Mutanen sun yi amfani da wannan dutsen a matsayin bagade lokacin da suke ba da shanun hadaya.
Wannan hakika ya faru ne kafin su yanka keken a itacen wuta don amfani da shanun ga Yahweh.
"akwatin mai dauke da sifofin zinare na beraye da kumburi"
"sarakunan Filistiyawa biyar"
Waɗannan garuruwa ne da ke da katangu masu tsayi kewaye da su don kare mutane daga ciki daga abokan gaba.
Ana maganar dutse kamar mutum ne zai iya gani. AT: "Babban dutse ... yana nan har yanzu, kuma mutane suna tuna abin da ya faru a kansa"
Wannan shi ake kira wani mutum daga Bet Shemesh. AT: "daga Bet Shemesh"
Akwatin yana da tsarki sosai don haka ba wanda aka yarda ya kalli cikinsa. Firistoci ne kawai aka ba su izinin ganin akwatin.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan tambaya ce ta zance da ke nuna tsoron mutane ga Yahweh. AT: "Babu wanda zai iya tsayayya da Yahweh saboda yana da tsarki sosai!" ko 2) wannan tambaya ce da ake neman bayani. Kalmar "ka tsaya a gaban Yahweh" na iya nufin firistocin da suke bauta wa Yahweh. An nuna cewa mutane suna neman firist wanda Yahweh zai ba shi izinin kula da akwatin. AT: "Shin akwai firist a cikinmu wanda ke bautar wannan Allah mai tsarki, Yahweh, kuma zai iya ɗaukar wannan akwati?"
Wannan tambaya ce don neman bayani. An nuna cewa mutane suna son Yahweh da akwatin su tafi wani wuri don haka ba zai sake azabtar da su ba. AT: "A ina za mu aika da akwatin don kada Yahweh ya sake azabtar da mu?"
Wannan wani gari ne a cikin Isra'ila.
1Mutanen Kiriyat Yerim suka zo, suka ɗauki akwatin Yahweh, suka kumakawo shi cikin gidan Abinadab a bisa tudu. Suka keɓe ɗansa Eliyeza ya ajiye akwatin Yahweh.2Daga ranar da akwatin ya zauna a Kiriyat Yerim, lokaci mai tsawo ya wuce, shekaru ashirin. Dukkan mutanen Isra'ila suka yi makoki kuma suka yi marmarin komawa ga Yahweh.3Sama'ila ya cewa gidan Isra'ila gaba ɗaya, "Idan kun dawo ga Yahweh da dukkan zuciyarku, ku cire bãƙin alloli da kuma Ashtoret daga cikinku, ku juyo da zukatanku ga Yahweh, ku kuma yi masa sujada shi kaɗai, daga nan zai kuɓutar daku daga hannun Filistiyawa."4Daga nan mutanen Isra'ila suka fitar da Ba'aloli da Ashtoret, suka kuma yi sujada ga Yahweh kaɗai.5Daga nan Sama'ila ya ce, "Ku kawo a tattare dukkan Isra'ila zuwa Mizfa, zan kuma yi addu'a ga Yahweh domin ku."6Suka tattaru a Mizfa, suka jawo ruwa suka zuba kuma a gaban Yahweh. Suka yi azumi a ranar suka ce, "Mun yi zunubi ga Yahweh." A can ne Sama'ila ya sasanta saɓanai domin mutanen Isra'ila ya kuma shugabanci mutanen.7Yanzu da Filistiyawa suka ji mutanen Isra'ila sun taru a Mizfa, sai shugabannin Filistiyawa sukakai hari ga Isra'ila. Da mutanen Isra'ila suka ji haka, suka ji tsoron Filistiyawa.8Daga nan mutanen Isra'ila suka cewa Sama'ila, "Kadaka daina kira ga Yahweh Allahnmu domin mu, domin ya cece mu daga hannun Filistiyawa."9Sama'ila ya ɗauki ɗan rago mai shan nono ya miƙa shi gaba ɗaya a matsayin baikon ƙonawa ga Yahweh. Daga nan Sama'ila ya yi kuka ga Yahweh domin Isra'ila, Yahweh kuma ya amsa masa.10Yayin da Sama'ila ke miƙa baikon ƙonawar, Filistiyawa suka matso domin su kawo hari ga Isra'ila. Amma Yahweh ya yi kwarankwatsi da babbar ƙara a wannan rana ga Filistiyawa ya kuma watsa su cikin ruɗewa, kuma suka shakaye a gaban Isra'ila.11Mutanen Isra'ila suka tafi daga Mizfa, suka kuma runtumi Filistiyawa suka kumakarkashe su har ya zuwa ƙarƙashin Bet Ka.12Daga nan Sama'ila ya ɗauki dutse yakafa tsakanin Mizfa da Shen. Ya raɗa masa suna Ebeneza, cewa, "Har ya zuwa haka Yahweh ya taimake mu."13Saboda haka Filistiyawa suka shakaye ba su kuma iya shigakan iyakar Isra'ila ba. Hannun Yahweh ya yi gãba da Filistiyawa dukkan kwanakin Sama'ila.14Garuruwan da Filistiyawa sukakarɓe daga Isra'ila aka maidawa Isra'ila, daga Ekron zuwa Gat; Isra'ila suka maido da lardinsu daga Filistiyawa. Daga nan aka sami salama tsakanin Isra'ila da Amoriyawa.15Sama'ila ya yi alƙalancin Isra'ila dukkan kwanakin ransa.16Kowacce shekara yakan tafi ya zagaye zuwa Betel, da Gilgal, da Mizfa. Yana ɗaukar mataki akan saɓanai domin Isra'ila a dukkan waɗannan wurare.17Daga nan sai ya koma Rama, saboda gidansa na wurin; haka kuma a anan yana ɗaukar mataki akan saɓanai domin Isra'ila. Ya kuma gina bagadi a wurin ga Yahweh.
Waɗannan sunayen maza.
Kalmar "gida" ishara ce ga mutanen da ke zaune a gidan da zuriyarsu. AT: "dukkan zuriyar Isra'ila" ko "duk mutanen Isra'ila ne"
Anan "da dukkan zuciyar ku" wani karin magana ne wanda yake nufin keɓewa ga abu gaba ɗaya. AT: "ku himmatu gabadaya don bauta da yi wa Yahweh biyayya kawai"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) mutane sun hana wa kansu ruwa a matsayin wani ɓangare na azumi ko 2) sun sami ruwa daga rafi ko rijiya suka zuba a ƙasa a matsayin alama ta waje ta nadamar zunubinsu.
Ana iya bayyana a sarari cewa sojoji ne ba sarakunan da kansu suka kai wa Isra'ila hari ba. AT: "sarakunan Filistiya sun jagoranci sojojinsu kuma sun kai wa Isra'ila hari"
“Hannu” magana ne ta ƙarfin mutum. AT: "Ka cece mu daga sojojin Filistiyawa" ko "ka hana sojojin Filistiyawa cutar da mu"
"ya yi ihu don taimako"
"Yahweh yayi yadda Sama'ila ya umarce shi yayi"
Kalmar "rikicewa" a nan ana amfani da ita azaman hanya ce ta yau da kullun da ake cewa Filistiyawa sun kasa yin tunani sosai. AT: "ya sa sun kasa yin tunani mai kyau"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. Mai yiwuwa su ne 1) "Yahweh ya fatattake su a gaban Isra'ila" ko 2) "Isra'ila ta fatattake su"
Isra'ilawa da sauran mutanen ƙasar za su saka babban dutse inda muhimman abubuwa suka faru don tunatar da taimakon Allah.
Waɗannan su ne sunayen wuraren.
Marubucin ya gama faɗi yadda aka ci Filistiyawa. Idan yarenku yana da hanyar yin alamar ƙarshen bayanin, kuna iya amfani da shi anan.
Filistiyawa ba su shiga yankin Isra'ila don su yi yaƙi da su ba.
Kalmar "hannu" magana ne ta iko. AT: "Yahweh yayi amfani da ikonsa kan Filistiyawa"
Sabani rigima ne ko rashin jituwa tsakanin mutane biyu ko sama da haka.
1Da Sama'ila ya tsufa, sai ya naɗa 'ya'yansa alƙalai bisa Isra'ila.2Sunan ɗan farinsa Yowel, sunan kuma ɗansa na biyu Abiya.3Su alƙalai ne a Biyasheba. 'Ya'yansa ba su yi tafiya bisa hanyoyinsa ba, amma suka bi bayan ƙazamar riba. Sukakarɓi cin hanci suka danne adalci.4Daga nan dukkan dattawan Isra'ila suka tattaru tare suka kuma zo wurin Sama'ila a Rama.5Suka ce masa, "Duba, ka tsufa, kuma 'ya'yanka ba su yi tafiya cikin hanyoyinka ba. Ka naɗa mana sarki ya yi hukunci akan mu kamar sauran al'ummai."6Amma Sama'ila bai ji daɗi ba da suka ce, "Ka bamu sarki ya yi hukuncinmu." Sai Sama'ila ya yi addu'a ga Yahweh.7Yahweh ya cewa Sama'ila, "Ka yi biyayya da muryar mutanen a cikin dukkan abin da suka ce maka; gama bakai suka ƙi ba, amma ni suka ƙi da zama sarki a bisansu.8Suna aikatawa yanzu dai-dai yadda suka yi tun daga ranar dana fito da su daga Masar, suka yashe ni, da bautar wasu alloli, haka kumakaima suke yi maka.9Yanzu ka saurare su; ammaka gargaɗe su da aniya bari kuma su san yadda sarkin zai yi mulki akansu."10Sai Sama'ila ya faɗi dukkan maganganun Yahweh ga mutanen da ke tambaya domin sarki.11Ya ce, "Wannan zai zama al'adar sarkin da zai yi mulki a bisanku. Zai ɗauki 'ya'yanku maza ya naɗa su gakarusansa ya kuma sa su zama mutanen dawakansa, su kuma yi gudu a gaban karusansa.12Zai naɗa wakansa ofisoshin bataliyar sojoji dubbai, da ofisoshin bataliyar sojoji hamsin. Zai sa wasu su yi noman gonarsa, wasu suyi girbin amfaninsa, wasu kuma suyi masa makaman yaƙi dakayan karusansa.13Zai kuma ɗauki 'ya'yanku mata su zama masu yi masa turare, da girke-girke, da gashe-gashe.14Zai ɗauki gonakinku mafi kyau, da garkunan inabinku, da kuma fadamunku na itatuwan zaitun, ya bayar dasu ga bayinsa.15Zai ɗauki kashi goma daga cikin hatsinku da garkarku ya kuma ba ofisoshinsa da bayinsa.16Zai ɗauki bayinku maza da bayinku mata da mafi nagarta na matasanku maza da jakanku; zai sanya su duka su yi masa aiki.17Zai ɗauki kashi goma daga cikin garken dabbobinku, kuma za ku zama bayinsa.18Daga nan a wannan rana za ku koka game da sarkinku wanda kuka zaɓarwakanku; amma Yahweh ba zai amsa maku ba a ranar."19Amma mutanen suka ƙi sauraron Sama'ila; suka ce, "A a! dole sarki yakasance a bisanmu20saboda mu zamakamar dukkan sauran al'ummai, saboda kuma sarkinmu ya hukunta mu ya kuma fita a gabanmu ya kuma yi faɗan yaƙe-yaƙenmu."21Da Sama'ila ya ji dukkan maganganun mutanen sai ya maimaita su a kunnuwan Yahweh.22Yahweh ya cewa Sama'ila, "Ka yi biyayya da muryarsu ka kuma sa wani ya zama sarki domin su." Sai Sama'ila ya cewa mutanen Isra'ila, "Kowanne mutum dole ya tafi nasa birnin."
Marubucin ya yi maganar kuɗi da mutane za su ba ’ya’yan Sama’ila kamar mutum ne ko dabba da ke guje wa’ ya’yan Sama’ila, kuma ya yi maganar ’ya’yan Sama’ila kamar suna bin mutumin ko dabba a zahiri. AT: "sun yi aiki tuƙuru don neman kuɗi ta hanyar rashin gaskiya"
"hukunci a cikin ni'imar daga waɗanda suka aikata mugunta"
Ana magana akan yadda mutum yake rayuwa kamar yana tafiya akan hanya. AT: "kada ku aikata abubuwan da kuke yi" ko "kada ku yi abin da ya dace kamar yadda kuke yi"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Ku nada mana sarki kamar sarakunan dukkan al'ummu don ya yi hukunci a kanmu" ko 2) "Ku nada mana sarki wanda zai yi mana hukunci yadda sarakunan al'ummai suke hukunta su"
Sama'ila bai ji daɗin cewa mutane ba kawai suna so ya cire removea sonsan nasa lalatattu kuma ya nada alƙalai masu gaskiya ba, amma suna son sarki ya mulke su kamar yadda sauran ƙasashe suke.
Anan “muryar”magana ne ta nufin ko sha'awar mutane. AT: "Yi abin da mutane suka ce"
Yahweh ya sani cewa mutanen ba kawai suna ƙi da lalatattun alƙalai ba, amma sun ƙi Yahweh a matsayin sarkinsu.
Wannan yana nufin Yahweh ne ya 'yantar da Isra'ilawa daga bautar ƙasar Masar shekaru da yawa da suka gabata.
"Yanzu ka yi abinda suka ce ka yi"
"zama ƙwarai da gaske kamar yadda ka yi musu gargaɗi"
Cikakken sunan "aiki" ana iya fassara shi azaman aiki. AT: "Ta haka ne sarkin da zai yi sarautarku zai yi aiki" ko "Wannan shi ne abin da sarkin da zai yi sarautarku zai yi"
"a ba su damar korar karusai a yaƙi"
Za su hau dawakai zuwa yaƙi.
Sama'ila ya ci gaba da faɗin abubuwan da sarkin zai ƙwace.
"don yin mai mai ƙanshi mai kyau don sanyawa a jikinsa"
Za su raba ruwan inabin da suka kawo a gonakin inabinsu kashi goma daidai, sa'an nan su ba fādawan da barorinsa ɗayan.
Waɗannan su ne shugabannin sojojin sarki.
Sama'ila ya ci gaba da faɗin abubuwan da sarkin zai ƙwace.
"zaka ji kamar kai bayinsa ne"
Zai yiwu ma'anonin su ne 1) mutane su roƙi Yahweh ya cece su daga sarki ko 2) mutane za su roƙi sarki ya daina wulakanta su.
Anan "kunnuwan Yahweh" na nufin Yahweh. Sama'ila ya yi addu'a ga Yahweh ya maimaita dukan abin da mutane suka ce. AT: "ya maimaita su ga Yahweh"
A nan ma'anar sunan "muryar su" tana nufin nufin mutane. AT: "Ku yi biyayya ga mutane"
"sanya wani sarki a kansu." Yi amfani da kalmar gama gari a cikin yarenku don sanya wani sarki.
1Akwai wani mutum a Benyamin, sanannen mutum. Sunansa Kish ɗan Abiyel ɗan Zeror ɗan Bekorat ɗan Afiya, ɗan wani Benyamine.2Yana da wani ɗa mai suna Saul, kyakkyawan saurayi. Babu wani taliki a cikin mutanen Isra'ila wanda ya ke mai asali ne fiye da shi. Dagakafaɗarsa zuwa sama yafi kowanne mutanen tsayi.3Yanzu dai jakan Kish, mahaifin Saul, sun ɓace. Sai Kish ya cewa ɗansa Saul, "Ka ɗauki ɗaya daga cikin bayin tare dakai; ka ta shi ka tafi neman jakan."4Sai Saul ya ratsa ta cikin ƙasar tudu ta Ifraim ya kuma tafi ta cikin ƙasar Shalisha, amma ba su same su ba. Daga nan suka ratsa ta cikin ƙasar Sha'alim, amma ba su a wurin. Sai ya ratsa ta cikin ƙasar Benyaminawa, amma ba su same su ba.5Da suka zo ƙasar Zuf, sai Saul ya cewa bawansa da ke tare da shi, "Zo, bari mu koma, ko mahaifina na iya daina damuwa domin jakan ya fara damuwa game da mu."6Amma bawan ya ce masa, "Saurara, akwai mutumin Allah a cikin wannan birnin. Mutum ne da aka riƙe da daraja; duk abin da ya ce yana zama gaskiya. Mu tafi can; watakila zai iya gaya mana wacce hanya zamu bi a tafiyarmu."7Daga nan Saul ya cewa bawansa, "Amma idan muka je, me za mu kawo wa mutumin? Domin gurasar da ke jakarmu ta ƙare, ba bu kuma wata kyauta da za mu kawo wa mutumin Allahn. Me muke da shi?"8Bawan ya amsa wa Saul ya kuma ce, "Nan, akwai tare da ni kwatar shekel na azurfa da zan ba mutumin Allahn, ya gaya mana hanyar da za mu je."9(A dã a Isra'ila, idan mutum ya tafi neman sanin nufin Allah, zai ce, "Zo, bari mu tafi wurin mai gani." Gama annabi a yau mai gani ake kiran sa a dã.)10Daga nan Saul ya cewa bawansa, "Faɗar ta yi dai-dai. Zo, bari mu tafi." Sai suka tafi birnin inda mutumin Allah ya ke.11Yayin da suka tafi zuwa tudun birnin, sai suka sami 'yan mata na fitowa jan ruwa; Saul da bawansa suka ce masu, "Mai ganin na nan?"12Suka amsa, suka kuma ce, "Yana nan; kalli, yana ɗan gaba da ku. Yi sauri, gama yana zuwa birnin yau, saboda mutanen suna hadaya a yau a wuri mai bisa.13Da zarar kun shiga birnin zaku same shi, kafin ya hau zuwa wuri mai bisa domin cin abinci. Mutanen ba zasu ci ba sai ya zo, saboda zai albarkaci hadayar; bayan haka waɗanda aka gayyata zasu ci. yanzu ku haura, gama zaku same shi nan da nan."14Sai suka tafi zuwa birnin. Yayin da suke shiga birnin, suka ga Sama'ila na zuwa ta wurinsu, domin ya tafi zuwa wuri mai bisa.15Yanzu dai ana gobe Saul zai zo, Yahweh ya bayyanawa Sama'ila:16"Gobe war haka zan aiko maka wani mutum daga ƙasar Benyamin, zaka kuma naɗa shi ya zama shugaba bisa mutane na Isra'ila. za ya ceci mutanena daga hannun Filistiyawa. Domin na dubi mutanena tare da tausayi saboda kiran su domin taimako ya zo gare ni."17Da Sama'ila ya ga Saul, Yahweh ya ce masa, "Shi ne mutumin da na gaya maka game da shi! shi ne wanda zai yi mulki bisa mutanena."18Daga nan Saul ya zo kusa da Sama'ila a ƙofa kuma ya ce, "Ka gaya mani ina ne gidan mai gani?"19Sama'ila ya amsa wa Saul ya ce, "Ni ne mai gani. Ka hau a gabana zuwa wuri mai bisa, domin yau zaka ci tare da ni. Da safe zan bar kaka tafi, kuma zan gaya maka kowanne abu da ke cikin ranka.20Game da jakanka da suka ɓace kwana uku da suka wuce, kadaka damu game da su, domin an same su. Daga nan akan wane ne dukkan marmarin Isra'ila yakasance? Ba akanka ba ne da kuma dukkan gidan mahaifinka?"21Saul ya amsa ya ce, "Ni ba Benyamine ba ne, daga mafi ƙanƙanta nakabilun Isra'ila? Ba zuriyarmu ce mafi ƙanƙanta ba a cikin dukkan zuriyar Benyamin? To me yasakake magana da ni irin haka.22Sai Sama'ila ya ɗauki Saul da baransa, yakawo su cikin harabar, ya zaunar da su a wuri mafi girma na waɗanda aka gayyata, waɗanda kimanin mutum talatin ne.23Sama'ila ya cewa mai girkin, "Kakawo kason da na baka, wanda na ce maka, 'Ka ajiye shi a gefe."'24Sai mai girkin ya ɗauko cinyar da abin da ke bisanta ya kuma sanya a gaban Saul. Daga nan Sama'ila ya ce, "Kalli abin da aka ajiye an sanya a gabanka. Ka ci, saboda an ajiye maka har zuwa zaɓaɓɓen lokaci, daga lokacin da na ce, 'Na gayyaci mutanen."' Sai Saul ya ci tare da Sama'ila a ranar.25Da suka sauko daga wuri mai bisa zuwa cikin birnin, Sama'ila ya yi magana da Saul a bisa saman rufi.26Daga nan da gari ya waye, Sama'ila ya yi kira ga Saul a bisa saman rufi ya kuma ce, "Ta shi, domin in aika dakai kan hanyarka." Sai Saul ya tashi, da shi da Sama'ila kuma dukka suka fita bisa titi.27Suna cikin tafiya zuwa waje da birnin, Sama'ila ya cewa Saul, "Ka cewa baran ya tafi gaba da mu" - sai ya tafi gaba - "amma dole ka tsaya a nan na ɗan lokaci, domin in shelar da saƙon Allah a gare ka."
Idan yarenku yana da hanyar fadawa mai karatu cewa marubucin yana bada bayanai ne a cikin wadannan ayoyin, kuna iya amfani da shi anan.
Zai yiwu ma'anonin su 1) ya kasance attajiri ko 2) ya kasance mai martaba ko 3) ya kasance mutum ne mai ƙarfi da jarumtaka.
Waɗannan su ne sunayen mutanen iyalin Saul.
Mutumin Benyamin ɗan kabilar Benyamin ne.
Sauran dogayen mutanen Isra'ila ba su ma zo kafaɗunsa ba.
Marubucin ya ƙare bayanan bayanan da suka fara a 1 Sama'ila 9: 1 kuma ya fara sabon ɓangaren labarin.
Duk waɗannan yankuna ne a cikin Isra'ila.
Kalmomin "su" da "duk" suna nufin jakuna ne.
Wannan yanki ne a cikin Isra'ila a arewacin Yerusalem.
Wannan jimlar galibi tana nufin annabin Yahweh. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 2:27. AT: "mutumin da ya ji kuma ya faɗi kalmomi daga wurin Allah"
"wacce hanya ya kamata mu bi domin gano jakuna"
Yin kyauta alama ce ta girmamawa ga mutumin Allah.
"1/4 na shekel." Shekel wani nau'in kuɗi ne da ake amfani da shi a Tsohon Alkawari.
"Mai gani shine tsohon suna don abin da muke kira annabi a yau"
Waɗannan wataƙila bikin ne ko hadayu na farko, ba hadaya na zunubi ba, wanda dole ne a gudanar a alfarwa.
Wannan wuri ne da mutane suka keɓe domin su miƙa hadayu da sadakoki ga Yahweh. Marubucin ya yi rubutu kamar a bayan bango da ke kewayen birnin.
Marubucin ya daina ba da labarin kuma ya ba da bayanan baya don mai karatu ya fahimci abin da zai biyo baya.
Ana amfani da kalmar yarima a nan maimakon sarki. Wannan shi ne mutumin da Allah ya zaɓa ya zama Sarkin Isra'ila.
Anan kalmar "hannu" isar metonym don sarrafawa. AT: "daga ikon Filistiyawa" ko "don haka Filistiyawa ba za su ƙara mallakar su ba"
"Mutanena suna wahala kuma ina so in taimaka musu"
"Yahweh ya gaya wa Sama'ila"
Waɗannan tambayoyin nuna tabbaci ne ƙwarai cewa Saul shi ne wanda Yahweh yake so ya zama sarki wanda Isra'ilawa suke nema. Ana iya fassara tambayoyin azaman maganganu. AT: "Ya kamata ku sani cewa a kanku ne aka saita dukkan buƙatun Isra'ila. An ɗora su a kanku da dangin mahaifinku."
Saul yana nuna mamaki saboda Benyamin shi ne karamar kabila a Isra'ila, kuma sauran Isra'ilawa sun ɗauki ƙabilar ba ta da muhimmanci. Hakanan, mutanen Benyamin sun ɗauki dangin Saul wanda ya kasance mabikai. Wadannan tambayoyin ana iya fassara su azaman maganganu. AT: "Ni daga kabilar Biliyaminu nake, mafi kankanta a cikin dukkan kabilu. Kuma dangi na ba su da wata muhimmanci a cikin kabilarmu. Ban fahimci dalilin da ya sa kuke cewa mutanen Isra'ila suna so ni da iyalina mu yi ba wani abu mai muhimmanci."
Wannan shi ne mazaunin girmamawa.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) sauran abincin da Saul zai ci tare da naman ko 2) wasu ɓangarorin bijimin.
A cikin asalin yare ba a bayyana wanda ke magana ba. Zai yiwu mai dafa abincin yana magana da Saul. AT: "Sa'an nan mai dafa abincin ya ce"
Abin da Saul yake yi a kan rufin za a iya bayyana a sarari. AT: "yayin da Saul yake barci a kan rufin, Sama'ila ya kira shi ya ce"
Zai yiwu Sama'ila ya faɗi waɗannan kalmomin duka. AT: "a gabanmu, kuma idan ya ci gaba, dole ne ku zauna"
"domin in gaya muku saƙon Allah gare ku"
1Sai Sama'ila ya ɗauki kwalbar mai, ya zuba akan Saul, ya kuma sumbace shi. Ya ce, "Ba Yahweh ya shafe ka baka zama shugaba bisa gãdonsa?2Idan ka bar ni yau, zaka sami mutum biyu kusa dakabarin Rahila, cikin lardin Benyamin a Zelza. Zasu ce maka, 'Jakan dakake nema an same su. Yanzu mahaifinka ya daina kula wa da jakan yana damuwa game dakai, cewa, "Me zanyi game da ɗa na?"'3Daga nan zaka tafi daga wurin, zaka kuma zo rimin Tabor. Mutane uku masu tafiya wurin Allah a Betel zasu gamu dakai a wurin, ɗaya na ɗauke da 'yan awaki uku, wani kuma na ɗauke da dunƙulen gurasa uku, wani kuma na ɗauke da salkar inabi.4Zasu gaishe ka su baka dunƙulen gurasa biyu, wanda zakakarɓa daga hannuwansu.5Bayan wannan, zaka zo tudun Allah, inda sansanin Filistiyawa ya ke. Idan ka isa birnin, zaka iske ƙungiyar annabawa na saukowa daga wuri mai bisa tare da algaita, da tambari, dakakaki, da sarewa, a gabansu; za su riƙayin anabci.6Ruhun Yahweh zai abko maka, zaka kuma yi anabci tare da su, zaka kuma sauya zuwa wani mutum daban.7Yanzu, idan waɗannan alamu suka zo maka, ka aiwatar da duk abin da hannunka ya sami damar yi, gama Allah na tare dakai.8Ka gangara gaba da ni zuwa Gilgal. Daga nan zan gangaro zuwa gare ka in miƙa baye-baye na ƙonawa in kuma yi hadayar baye-baye na salama. Ka jira kwana bakwai har sai na zo gare ka in kuma nuna maka abin da dole ka yi."9Da Saul ya juya bayansa domin ya bar Sama'ila, Allah ya ba shi wata zuciyar. Daga nan dukkan waɗannan alamu suka faru a ranar.10Da suka iso tudun, wata ƙungiyar annabawa ta gamu da shi, Ruhun Allah kuma ya abko bisansa har ya yi anabci tare da su.11Da dukkan waɗanda suka san shi a dã suka ga yana anabci tare da annabawan, mutanen suka ce da junansu, "Mene ne ya faru da ɗan Kish? Saul shi ma ɗaya daga cikin annabawan ne yanzu?"12Wani mutum da ya fito daga wuri ɗaya da shi ya amsa, "To wane ne mahaifinsa?" Saboda wannan, ya zama abin faɗi, "Saul shi ma ɗaya ne daga cikin annabawan?"13Da ya gama anabcin, ya zo wuri mai bisan.14Daga nan kawun Saul ya ce masa da kuma bawansa, "Ina kuka je?" Ya mai da amsa, "Neman jakan. Da muka ga ba mu iya samo su ba, muka je wurin Sama'ila."15Kawun Saul ya ce, "Ina roƙon kaka gaya mani abin da Sama'ila ya ce maka."16Saul ya amsa wakawunsa, "Ya gaya mana a sarari cewa an samo jakan." Amma bai gaya masa game da al'amarin masarautar ba, wanda Sama'ila ya yi magana akai.17Yanzu Sama'ila ya kira mutanen tare a gaban Yahweh a Mizfa.18Ya cewa mutanen Isra'ila, "Wannan ne abin da Yahweh, Allah na Isra'ila ya faɗa: 'Nakawo Isra'ila daga ƙasar Masar kuma na ƙwato ku daga hannun Masarawa, daga kuma hannun dukkan masarautun da suka tsananta maku.'19Amma yau kun watsar da Allahnku, wanda ya cece ku daga dukkan bala'o'inku da ƙuncinku; kuma kun ce da shi, 'Naɗa sarki a bisanmu.' Yanzu ku gabatar dakanku a gaban Yahweh takabilunku da zuriyarku."20Sai Sama'ila yakawo dukkan kabilun Isra'ila kusa, kumakabilar Benyamin aka zaɓa.21Daga nan yakawo kabilar Benyamin kusa ta zuriyarsu; kuma zuriyar Matirawa aka zaɓa; kuma Saul ɗan Kish aka zaɓa. Amma da suka tafi neman sa, ba a iya samun sa ba.22Daga nan mutanen suka so su roƙi Allah ƙarin tambayoyi, "Akwai kuma wani mutumin da zai zo?" Yahweh ya amsa, "Ya ɓoye kansa cikin kayayyaki."23Daga nan suka ruga suka tsamo Saul daga wurin. Da ya tsaya cikin mutanen, yafi kowanne daga cikin mutanen tsayi, dagakafaɗarsa zuwa sama.24Daga nan Sama'ila ya cewa mutanen, "Kun ga mutumin da Yahweh ya zaɓa?" Babu wani kamar sa daga cikin dukkan mutanen!" Dukkan mutanen suka yi sowa, "Ran sarki ya daɗe!"25Daga nan Sama'ila ya gaya wa mutanen al'adu da dokokin sarautar, ya rubuta su cikin littafi, ya kuma ajiye su gaban Yahweh. Daga nan Sama'ila ya sallami dukkan mutanen, kowanne mutum zuwa nasa gidan.26Saul shi ma ya tafi gidansa a Gibiya, tare da shi kuma wasu ƙarfafan mutane, waɗanda Allah ya taɓa zukatansu.27Amma wasu mutane marasa amfani suka ce, "Ta yaya wannan mutum zai cece mu?" Waɗannan mutane suka rena Saul, ba su kumaka wo masa wata kyauta ba. Amma Saul ya yi shiru.
A al'adun Isra'ilawa, idan annabi ya zuba mai a kan wani, mutumin ya sami albarka daga Yahweh.
Sama'ila ya san amsar tambayarsa. Yana tuna wa Saul cewa Yahweh ya zaɓe shi ya zama sarkin Isra'ila. AT: "Lallai Yahweh ya shafe ku don ku mallaki gadonsa."
Wannan sunan wani wuri ne.
Mahaifin Saul yanzu ya damu da Saul kuma yana so ya nemo shi.
Wannan sunan wani wuri ne.
Hannun yana nufin wani mutum. "karɓa daga gare su" ko "karɓa"
Kalmar "zai abko" na nufin cewa Ruhun Yahweh zai rinjayi Saul. A wannan yanayin yana nufin yana nufin zai sa Saul ya yi annabci kuma ya yi kamar wani mutum dabam.
Anan Sama'ila yayi magana game da hannun Saul kamar mutum ne mai ƙoƙarin neman abubuwa. AT: "ku aikata duk abin da kuke ganin ya dace a yi"
Allah ya ba Saul damar yin tunani dabam da yadda yake tunani a dā.
Sama'ila yayi magana kamar Ruhun Yahweh mutum ne da ke gudu zuwa wurin Saul kuma ya mallaki shi sosai. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 10: 6. AT: "Ruhun Yahweh ya mallake shi sosai"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) mutane suna neman bayani ko 2) wannan tambaya yana nufin Saul ba shi da mahimmanci. AT: "Kish ba wani muhimmin mutum bane, don haka ba zai zama gaskiya cewa ɗansa ya zama annabi ba!"
Wannan mutumin yana amfani da tambaya don tunatar da mutane cewa kasancewa annabi ba shi da wata alaƙa da wane ne iyayen mutum. Ana iya fassara tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Babu damuwa ko su waye iyayen waɗannan annabawan. Abin da ya ke mahimmanci shi ne, abin mamaki, Saul yana magana da saƙo daga Allah."
Wannan ya zama misali a tsakanin Isra'ilawa. Da alama mutane sun faɗi hakan ne don nuna mamakin lokacin da mutum ba zato ya yi abin da ba a taɓa yi ba. Ana iya bayyana ma'anar tambayar a bayyane. AT: "Kuma shi yasa, lokacin da mutane ba za su gaskanta wani rahoto ba, suna tunanin abin da ya faru da Saul sai su ce," Shin Saul da gaske yana ɗaya daga cikin annabawa?
"Sai ɗan'uwan mahaifin Saul ya cewa Saul"
"Saul bai fada wa kawunsa cewa Allah ya nada shi ya zama sarkin Isra'ila ba"
Sunan "Isra'ila" yana nfin mutanen Isra'ila. "Na fito da mutanen Isra'ila daga Masar"
Kalmar "hannu" na nufin ta iko. AT: "ikon Masarawa ... ikon dukkan mulkoki"
"Ka ba mu sarki da zai mallake mu"
"ku taru wuri ɗaya ta kabilu da dangi ku zo ku tsaya a gaban Yahweh"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. Zai fi kyau kada a faɗi yadda mutane suka san waɗanda Yahweh ya zaɓa. AT: "Yahweh ya zaɓi ƙabilar Benyamin ... Yahweh ya zaɓi dangin Matirawa ... Yahweh ya zaɓi Saul ɗan Kish"
Sauran dogayen mutanen Isra'ila ba su ma zo kafaɗunsa ba. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 9: 1.
AT: "al'adu da dokokin da sarki zai buƙaci ya bi"
Allah taɓa zuciyar mutum magana ce ta magana wacce ke nufin Allah ya sanya wani abu a cikin tunaninsu ko kuma ya motsa su suyi wani abu. AT: "wanda yake so ya tafi tare da Saul saboda Allah ya canza tunaninsu"
Wannan tambaya don wacce ake amfani da ita don bayyana sarƙar.AT: "Wannan mutumin ba shi da ikon da zai cece mu!"
1Daga nan Nahash Ba'ammoniye ya tafi yakafa sansani ga Yabesh Giliyad. Dukkan mutanen Yabesh suka cewa Nahash, "Ka yi alƙawari da mu, kuma za mu bauta maka."2Nahash Ba'ammoniye ya maida amsa, "Bisa wannan matsayin zan yi alƙawari da ku, cewa zan ƙwaƙule dukkan idanunku na dama, ta wannan hanya kuma in kawo kunya bisa dukkan Isra'ila."3Daga nan dattawan Yabesh Giliyad suka mai da masa amsa, "Ka rabu da mu na kwana bakwai, saboda mu aika da saƙonni ga dukkan lardin Isra'ila. Daga nan, idan ba bu wani da zai cece mu, za mu sadauƙar a gare ka."4Manzannin suka zo Gibiya, inda Saul ke zama, suka kuma gayawa mutanen abin da ya faru. Dukkan mutanen suka yi kuka da ƙarfi.5Yanzu dai Saul na biye da shanu daga saura. Saul ya ce, "Me ke damun mutanen da suke kuka?" Suka gaya wa Saul abin da mutanen Yabesh suka ce.6Da Saul ya ji haka, Ruhun Allah ya afko masa, ya kuma fusata sosai.7Ya ɗauki shanun huɗa biyu, ya datse su gunduwa-gunduwa, ya kuma aika da su cikin dukkan lardin Isra'ila tare da manzanni. ya ce, "Duk wanda bai fito bayan Saul da bayan Sama'ila ba, haka za a yi wa shanun huɗarsa." Daga nan razanar Yahweh ta faɗo bisa mutanen, suka kuma fito tare a matsayin mutum ɗaya.8Da ya tattara su a Berek, mutanen Isra'ila dubu ɗari uku ne, mutanen Yahuda kuma dubu talatin.9Suka ce wa manzannin da suka zo, "Za ku cewa mutanen Yabesh Giliyad, "Gobe, lokacin da rana takai tsaka, za a ceto ku." Sai manzannin suka tafi suka gaya wa mutanen Yabesh, suka kuma yi farinciki.10Daga nan mutanen Yabesh suka cewa Nahash, "Gobe za mu sadaukar a gare ka, sai kumaka yi da mu duk abin da ya yi kyau a gare ka."11washegari Saul yasa mutanen ƙungiya uku. Suka zo tsakiyar sansanin a lokacin wayewar gari, suka kumakai hari suka kumakayar da Ammoniyawa har zafin rana. Waɗanda suka tsira su ka watse, har babu mutum biyun su da aka bari tare.12Daga nan mutanen suka ce wa Sama'ila, "Wane ne wanda ya ce, 'Saul zai yi mulki a bisanmu?' akawo mutanen, domin mu kashe su."13Amma Saul ya ce, "Babu wanda za akashe dole a wannan ranar, saboda a wannan ranar Yahweh ya ceto Isra'ila."14Daga nan Sama'ila ya cewa mutanen, "Ku zo, bari mu tafi Gilgal mu sabunta sarautar a can."15Saboda haka dukkan mutanen suka tafi Gilgal suka kuma maida Saul sarki a gaban Yahweh a Gilgal. A can suka yi hadayar baye-baye don salama a gaban Yahweh, da Saul da dukkan mutanen Isra'ila suka yi farinciki babba.
Wannan wani mutum ne daga Ammon, zuriyar Lot, ɗan yayan Ibrahim.
Wannan sunan wani wuri ne.
"Na yanke" ko "na fisge"
"kawo kunya akan" ko "kawo mummunan suna ga"
"Kwanaki 7"
Wannan sunan wani wuri ne.
Kalmomin “garaje” yana nufin Ruhun Yahweh ya rinjayi Saul. A wannan yanayin ya sa Saul ya sa mutane su girmama shi da girmamawa kamar sarkinsu kuma su haɗa kai da rundunarsa. Duba yadda kuka fassara makamancin magana a cikin 1 Sama'ila 10:5.
Saul ya kirawo Isra'ilawa duka don su zo su yi yaƙi da Nahash da Ammonawa.
Yahweh ya sa mutane su girmama Saul da ƙarfi a matsayin sarkinsu. Sakamakon ya nuna cewa mutanen sun haɗa kai tare da Saul a Bezek.
Wannan sunan wani gari ne kusa da Jabesh Gileyad.
"mutanen Isra'ila sun kasance 300,000, kuma mutanen Yahuda sun kasance 30,000"
"Su" suna nufin Sama'ila da Saul.
"kafin lokacin mafi zafi na rana" ko "kafin tsakar rana"
Wannan ya kasance kafin wayewar gari lokacin da yawancin mutanen da ke sansanin har yanzu suna barci.
"sanya Saul sarki yayin da Yahweh ke kallo"
Wani ɓangare na hidimar Sama'ila ga Yahweh shine bayar da hadayu duk da cewa bai fito daga zuriyar Haruna ko Lebi ba.
1Sama'ila ya cewa dukkan Isra'ila, "Na saurari dukkan abin da kuka faɗi mani, na kuma naɗa sarki a bisanku.2Yanzu, ga sarkin nan na tafiya a gabanku; kuma na tsufa da furfura; kuma, 'ya'yana maza na tare da ku. Nayi tafiya a gabanku daga ƙuruciyata har wa yau.3Ga ni nan; ku yi shaida gãba da ni a gaban Yahweh da gaban shafaffensa. Saniyar wa na ɗauka? Jakin wa na ɗauka? Wane ne na yi wa damfara? Wane ne na tsanantawa? Daga hannun wa nakarɓi cin hanci don ya makantar da idanuna da shi? Ku shaida gãba da ni, kuma zan maido maku da shi."4Suka ce, "Baka cuce mu ba, baka tsananta mana, ko ka saci wani abu daga hannun wani mutum ba."5ya ce masu, "Yahweh ne shaida gãba da ku, kuma shafaffensa shaida ne a yau, cewa ba ku sami komai ba a cikin hannuna." Suka mai da amsa, "Yahweh ne shaida."6Sama'ila ya ce da mutanen, "Yahweh ne ya naɗa Musa da Haruna, wanda kuma ya fito da ubanninku daga ƙasar Masar.7Yanzu daga nan, ku miƙakanku, domin in yi roƙo tare da ku a gaban Yahweh game da dukkan ayyukan adalci na Yahweh, wanda ya yi domin ku da ubanninku.8Da Yakubu ya zo Masar, kumakakanninku suka yi kuka ga Yahweh, daga nan Yahweh ya aika da Musa da Haruna, waɗanda suka bi dakakanninku fita daga Masar suka kuma zauna a wannan wuri.9Amma suka manta da Yahweh Allahnsu; ya sayar da su cikin hannun Sisera, shugaban sojojin Hãzo, cikin hannun Filistiyawa, kuma cikin hannun sarkin mutanen Mowab; dukkan waɗannan suka yi faɗa gãba dakakanninku.10Suka yi kuka ga Yahweh suka kuma ce, 'Mun yi zunubi, saboda mun yashe da Yahweh kuma mun bauta wa Ba'aloli da Ashtatori. Amma yanzu ka cece mu daga hannun maƙiyanmu, kuma za mu bauta maka.'11Sai Yahweh ya aika da Yerub Ba'al, Bedan, Yefta, da Sama'ila, ya kuma ba ku nasara akan maƙiyanku dukka a kewaye da ku, yadda kuka zauna cikin tsaro.12Da kuka ga Nahash sarkin mutanen Ammon yakawo maku hari, kuka ce mani, "A a! maimako, dole wani sarki ya yi mulki akanmu' - ko da ya ke Yahweh Allahnku, shi ne sarkinku.13Yanzu ga sarkin daku ka zaɓa, wanda kuka yi roƙo domin sa wanda kuma Yahweh ya naɗa sarki a bisanku.14Idan ku na tsoron Yahweh, ku bauta masa, ku yi biyayya da muryarsa, kuma ba wai ku kangare ga dokokin Yahweh ba, daga nan ku dukka da sarkin da ke mulki a bisanku za ku zama masu bin Yahweh Allahnku.15Idan ba ku yi biyayya da muryar Yahweh ba, amma kukakangare ga dokokin Yahweh, daga nan hannun Yahweh zai yi gãba da ku, kamar yadda ya yi gãba dakakanninku.16Ko yanzu ma ku miƙakanku kuma ku ga wannan babban abu wanda Yahweh zai yi a gaban idanunku.17Ba kamar alkama ba ce yau? Zan yi kira ga Yahweh, domin ya aiko da aradu da ruwan sama. Daga nan za ku sani ku kuma gani cewa muguntarku babba ce, wadda kuka aikata a idanun Yahweh, cikin roƙar wakanku sarki."18Sai Sama'ila ya yi kira ga Yahweh; a wannan rana kuma Yahweh ya aiko da aradu da ruwan sama. Daga nan dukkan mutanen suka ji tsoron Yahweh da Sama'ila ƙwarai.19Daga nan dukkan mutanen suka ce da Sama'ila, "Ka yi addu'a domin bayinka ga Yahweh Allahnka, domin kada mu mutu. Gama mun ƙara wakanmu dukkan zunubanmu wannan muguntar cikin roƙo domin sarki domin kanmu."20Sama'ila ya maida amsa, "Kada ku ji tsoro. Kun yi dukkan wannan mugunta, ammakada ku juya ga Yahweh, amma ku bauta wa Yahweh da dukkan zuciyarku.21Kada ku juya zuwa holoƙan abubuwa waɗanda ba za su iya bada riba ko cetonku ba, saboda ba su da amfani.22Domin albarkacin sunansa mai girma, Yahweh ba zai watsar da mutanensa ba, saboda ya gamshi Yahweh ya maida ku mutane domin kansa.23Game da ni, ya yi ne sa da ni in yi zunubi gãba da Yahweh ta wurin tsaida yin addu'a domin ku. Maimako, zan koyar da ku hanya da ke mai kyau kuma dai-dai.24Kawai dai ku ji tsoron Yahweh kuma ku bauta masa cikin gaskiya da dukkan zuciyarku. Kuyi la'akari da manyan abubuwan da ya yi domin ku.25Amma idan kuka nace ga aikata mugunta, ku dukka da sarkinku zaku lalace."
Waɗannan maganganun suna nuna cewa mutane za su iya ganin irin rayuwar da Saul da Sama'ila suke yi. AT: "an ga rayuwar sarki ... An ga rayuwata"
Ta wannan bayanin, Sama'ila yana ƙalubalantar mutane su yi magana idan ya yi wa wani laifi. AT: "Ina tsaye a gabanku yanzu. Ina roƙonku da ku yi magana a gaban Yahweh da zaɓaɓɓen sarkinsa idan na yi muku wani laifi"
Sama’ila yayi amfani da tambayoyin magana don tunatar da mutane cewa bai taɓa satar dabbobinsu ba. AT: "Ban taɓa satar dabba mai daraja daga kowa ba." (Duba: fig_rquestion)
Sama'ila ya sake yin amfani da wata tambaya don ya ce ya kasance mai gaskiya. AT: "Ban taɓa yaudara ko cin hanci ga wani mutum ba."
"Idan na yi ɗaya daga cikin waɗannan mugayen abubuwa, yi magana yanzu, zan kuma biya bashin da ke kaina. Zan gyara kowane irin laifi."
Wannan jimlar na nufin abin da mutum ya mallaka ko kuma abin da ya yi don samun tagomashi daga wasu. Wannan hanyar ladabi ce ta cewa bai sata ba, kuma bai bayar ko karɓar rashawa ba.
Sama’ila yana kiran hankalinsu ga tarihin yadda Yahweh ya yi hulɗa da Isra’ila, wanda ya cika da nagarta da manufa.
"A cikin Sisera ... Filistiyawa ... sarkin Mowab"
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan sunan wani wuri ne.
Wannan magana ce don Allah ya bashe su ga magabtansu don su zama bayinsu.
"Su" suna nufin al'ummar Isra'ila.
Hidima anan yana nufin yin sujada ga gumakan karya. AT: "sun yi bautar gumakan ƙarya da alloli"
Wannan ana fassara shi a wasu lokuta Yerubba'al. Wannan suna ne na girmamawa na ibada da ƙarfi don yaƙi da allahn ƙarya.
Sama’ila yana ba da labarin abin da Allah ya yi ne bayan da mutane suka faɗi zunubansu da neman taimako.
Waɗannan sunayen wasu alƙalai ne da Allah ya ɗaukaka su. Sama'ila ya saka kansa cikin wannan jerin.
Wannan bayanin ya nuna maƙiyan Isra'ilawa game da Sama'ila lokacin da ya gaya musu game da dogara ga Allah domin Allah ya cece su a dã.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna karfafa cewa wannan shi ne sarki waɗanda mutane suke so.
Ana amfani da waɗannan kalmomin makamantan don jaddada muhimmancin wannan.
Kalmar "hannu" a nan tana wakiltar iko da ikon Yahweh. AT: "Yahweh zai hore ku, kamar yadda ya hukunta kakanninku"
Kalmar nan “idanu” a nan tana wakiltar mutanen Isra’ila. AT: "a bayyane inda duk al'ummar Isra'ila zasu iya gani"
Sama'ila ya san lokacin girbi ne. Yana amfani da tambaya don jaddada cewa yawanci ba ya ruwa a wannan lokacin don haka mutane zasu san cewa ruwan saman da zai lalata girbinsu hukunci ne daga Yahweh. AT: "Lokacin girbi ne kuma ba kasafai ake yin ruwan sama ba a wannan lokacin"
Sama’ila yana roƙon Yahweh ya hukunta Isra’ila saboda neman sarki ta hanyar aiko da ruwan sama a lokacin girbin wanda zai lalata hatsi.
Babban hukuncin zunubi shi ne mutuwa. Al’ummar Isra’ilawa sun ga yadda Ubangiji ya hallaka al’ummar da ta zalunce su. Sun damu da cewa sun zama "sadaukarwa don hallaka" kamar waɗancan al'ummomin.
Mutanen sun aikata mugunta kuma suna tsoron kada Allah ya hallaka su. AT: "Kada ku ji tsoron cewa Allah zai yi fushi ya hallaka ku saboda wannan zunubin"
"bi bautar gumakan ƙarya"
Anan “suna” yana nufin sunan Yahweh. AT: "Don mutane su ci gaba da girmamawa da girmama Yahweh"
Mutanen sun cika da tsoro saboda ruwan sama da tsawar da Yahweh ya aiko sa'ad da Sama'ila ya yi addu'a. Wasu mutane na iya gaskanta Sama'ila zai yi amfani da addu'arsa don ya cutar da su.
1Saul na da shekaru talatin sa'ad da ya fara mulki; sa'ad da ya yi mulki shekaru arba'in a bisa Isra'ila,2ya zaɓi mutane dubu uku na Isra'ila. Dubu biyu suna tare da shi a Mikmash da kuma ƙasar tudu ta Betel, dubu ɗaya kuma suna tare da Yonatan a Gibiya ta Benyamin. Sauran sojojin ya aika da su gida, kowanne mutum zuwa rumfarsa.3Yonatan yakayar da sansanin Filistiyawa da ke Geba Filistiyawa kuma suka ji haka. Daga nan Saul ya busa ƙaho cikin dukkan ƙasar, cewa, "Bari Ibraniyawa su ji."4Dukkan Isra'ila kuwa suka ji cewa Saul yakayar da sansanin Filistiyawa, da cewa kuma Isra'ila ta zama ɗoyi mai ruɓa ga Filistiyawa. Daga nan aka yi wa sojojin sammace tare su haɗu da Saul a Gilgal.5Filistiyawa suka tattaru tare suyi faɗa gãba da Isra'ila: karusai dubu uku, mutane dubu shida suyi tuƙin karusan, rundunai kuma yawan su kamar rairayin da ke bakin teku. Suka zo sukakafa sansani a Mikmash, gabas da Bet Aben.6Da mutanen Isra'ila suka ga cewa suna cikin matsala - domin mutanen sun ƙuntata, mutanen suka ɓoɓɓoye a kogonni, da ƙarƙashin zangarniyoyi, da duwatsu, da rijiyoyi, da ramuka.7Wasu Ibraniyawan suka tafi ƙetaren Yodan zuwa ƙasar Gad da Giliyad. Amma Saul yana Gilgal tukuna, dukkan mutanen kuma suka bi shi suna rawar jiki.8Ya jira kwana bakwai, lokacin da Sama'ila ya tsaida. Amma Sama'ila bai zo Gilgal ba, mutanen kuma suna warwatsewa daga Saul.9Saul ya ce, "Kawo mani baikon ƙonawar da baye-bayen salamar." Daga nan ya miƙa baikon ƙonawar.10Nan da nan yana gama miƙa baikon ƙonawar Sama'ila ya iso. Saul ya fita domin ya same shi ya kuma gaishe shi.11Daga nan Sama'ila ya ce, "Mene ne ka yi?" Saul ya maida amsa, "Da naga cewa mutanen na bari na, kuma cewa baka zo ba cikin lokacin da aka tsaida, kuma cewa Filistiyawa sun riga sun taru a Mikmash,12Na ce, 'Yanzu Filistiyawa zasu gangaro gãba da ni a Gilgal, kuma ban biɗi tagomashin Yahweh ba.' Sai na tilasta wakaina in miƙa baikon ƙonawar."13Daga nan Sama'ila ya cewa Saul, "Ka yi wawanci. Baka kiyaye dokar Yahweh Allahnka ba wadda ya baka. Domin daga nan da Yahweh ya tabbatar da mulkin ka bisa Isra'ila har abada.14Amma yanzu mulkin ka ba zai ci gaba ba. Yahweh ya samo wani mutum bisa ga zuciyarsa, kuma Yahweh ya naɗa shi ya zama shugaba bisa mutanensa, saboda baka yi biyayya da abin da ya dokace ka ba."15Daga nan Sama'ila ya tashi ya tafi ya haye daga Gilgal zuwa Gibiya ta Benyamin. Daga nan Saul ya lissafa mutanen da ke tare da shi, kimanin mutane ɗari shida.16Saul, da ɗansa Yonatan, da mutanen da ke tare da su, suka tsaya a Geba ta Benyamin. Amma Filistiyawan suka yi sansani a Mikmash.17Mahaya suka zo daga sansanin Filistiyawa cikin ƙungiyoyi uku. Ƙungiya ɗaya ta juya wajen Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.18Wata ƙungiyar ta juya wajen Bet Horon, wata ƙungiyar kuma ta juya wajen kan iyakar da ke fuskantar kwarin Zeboyim wajen jeji.19Babu wani maƙeri da aka iya samu cikin dukkan ƙasar Isra'ila, saboda Filistiyawan sun ce, "Idan ba haka ba Ibraniyawa zasu yi takubba da mãsu domin kansu."20Amma dukkan mutanen Isra'ila sukan je wurin Filistiyawa, kowanne domin ya wãsakayan aikin gonarsa, da addarsa, da gatarinsa, da laujensa.21Farashin kuwakashi biyu cikin uku ne na shekel akan kowanne washin bakin kayan aiki, da adduna, dakashi ɗaya cikin uku na shekel domin washin gatura, domin kuma miƙar da silkuna.22Saboda haka a ranar yaƙi, babu takubba ko mãsu da aka samu a hannuwan ko ɗaya daga cikin sojojin da ke tare da Saul da Yonatan; Saul ne kaɗai da ɗansa Yonatan suke da su.23Sai sansanin Filistiyawa suka fita zuwa hanyar Mikmash.
Sama'ila ya sabunta mulkin Saul a Gilgal kuma Sama'ila ya tunatar da jama'a su bi Yahweh.
Nassin wannan aya a cikin tsofaffin kofe kamar an yanke shi, don haka fasalin zamani yana da fassarori daban-daban. Dukkanin ƙoƙari ne don wakiltar mafi yuwuwar ma'anar asalin rubutu.
"2,000 maza suna tare da shi a Mikmash"
Gibeah wani birni ne. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Samuila 10:26.
"sansanin soja na Filistiyawa" ko "sansanin sojojin Filistiyawa"
Wannan shine sunan garin da sansanin sojojin Filistiya suka kafa.
Ana magana game da Filistiyawa da suke ƙin Isra’ilawa kamar Isra’ilawa sun zama wari mai daɗi wanda ya ɓata wa Filistiyawa rai. AT: "Filistiyawa sun ƙi Isra'ilawa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Saul ya kira sojoji tare don su tafi tare a Gilgal"
Wannan karin magana ne wanda ke nufin gungun sojoji da yawa wanda ya yi wuya a kirga su.
Wannan sunan wani wuri ne.
Filistiyawa suka tattaru don su yi yaƙi da Isra'ilawa.
"mutane sun damu matuka"
Mutanen suka tsorata ƙwarai.
"bisa ga lokacin da Sama'ila ya ce musu zai zo"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutanen sun fara barin Saul"
Layin Haruna ne kawai aka ba da izinin yin hadaya ta ƙonawa ga Allah.
Sama'ila bashi da tambaya da gaske, amma yana tsawata wa Saul. Saul ya nemi ya kāre ayyukansa duk da cewa ba su da kyau.
Saul ya jira Sama'ila ya zo ya miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah. Bai kamata ya yi hadayar da kansa ba.
"kafa dokar ka" ko "sanya dokar ka" ko "sanya dokar ka"
Wannan magana ne waɗanda za'a iya bayyana su a cikin kyakkyawar siga. AT: "mulkinka zai ƙare ba da daɗewa ba"
Anan “zuciya” tana wakiltar muradin Yahweh ko kuma nufinsa. Kalmomin "mutum bayan zuciyarsa" magana ce da ke nufin mutum ya aikata abin da Yahweh yake so. AT: "mutumin da yake irin mutanen da yake so" ko "mutumin da zai yi masa biyayya"
Wannan karin magana ne don "Sama'ila ya tafi ya hau."
Maharan galibi mutane ne sojoji waɗanda ke kai hari kan ƙauyukan abokan gaba don abincinsu da sauran kayayyakinsu.
Waɗannan su ne sunayen wuraren.
Labarin ya canza zuwa bayanan da suka gabata game da maƙera a Isra'ila.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba wanda ya sami maƙeri"
Kalmomin "wuraren nitsuwa" suna nufin batun kayan aikin ƙarfe da ake amfani da shi don haƙa ƙasa don dasa shuki.
Labarin ya ci gaba.
Wannan yayi bayani dalla-dalla dalilin da yasa sojojin Saul suka tsorata. Ba su da makaman da za su yi yaƙi.
1Wata rana, Yonatan ɗan Saul ya cewa saurayin da ke ɗauke da makamansa, "Zo, mu tafi zuwa sansanin Filistiyawa da ke ɗaya ɓarayin." Amma bai gaya wa mahaifinsa ba.2Saul na zama a waje da Gibiya a ƙarƙashin itacen manta'uwa da ke cikin Migron. Wajen mutane ɗari shida na tare da shi,3har da Ahija ɗan Ahitub (ɗan'uwan Ikabod) ɗan Fenihas ɗan Eli, firist ɗin Yahweh a Shilo, wanda ya sanya falmara. Mutane ba su san cewa Yonatan ya tafi ba.4A kowanne gefen hanyar inda Yonatan ya so ya bi domin yakai ga sansanin Filistiyawan, akwai dutse mai tsini a gefe ɗaya da kuma wani dutsen mai tsini a ɗayan gefen. Ɗaya dutse mai tsinin a na kiran sa Bozez ɗaya kuma dutsen mai tsini a na kiran sa Sene.5Ɗaya dutsen mai tsini yana tsaye a arewa a gaban Mikmash, ɗayan kuma a kudu a gaban Geba.6Yonatan ya ce da saurayin da ke ɗauke da makamansa, "Zo, mu ƙetara sansanin waɗannan marasakaciyar. Zai yiwu cewa, Yahweh ya yi aiki a madadin mu, domin babu abin da zai tsaida Yahweh daga yin ceto ta wurin masu yawa ko mutane kaɗan."7Mai ɗaukar makamansa ya maida amsa, "Ka yi duk abin da ke cikin zuciyarka. Ka yi gaba, duba, ina tare dakai, in yi biyayya ga dukkan dokokinka."8Daga nan Yonatan ya ce, "Za mu ƙetara zuwa ga mutanen, za mu kuma nunakanmu gare su.9Idan suka ce mana, 'Ku dakata nan har sai mun hauro gare ku'- daga nan za mu tsaya a wurinmu ba kuma za mu ƙetara zuwa gare su ba.10Amma idan suka maida amsa, 'Ku ƙetaro zuwa gare mu,' daga nan za mu ƙetara; saboda Yahweh ya bayar da su cikin hannunmu. Wannan ne zai zama alama a gare mu."11Sai dukkan su suka bayyanakansu ga sansanin Filistiyawa. Filistiyawan suka ce, "Duba, Ibraniyawa na fitowa daga ramukan da suka ɓoye kansu."12Daga nan mutanen sansanin suka yi kira ga Yonatan da mai ɗaukar makamansa, suka ce kuma, "Ku zo gare mu, za mu kuma nuna maku wani abu." Yonatan ya ce da mai ɗaukar makamansa, "Bi yo bayana, saboda Yahweh ya bayar da su cikin hannun Isra'ila."13Yonatan ya hau bisa hannuwansa da ƙafafunsa, mai ɗaukar makamansa kuma ya bi bayansa. Filistiyawa suka sha kisa a gaban Yonatan, kuma mai ɗaukar makamansa yakarkashe wasu bayansa.14Wannan hari na farko da Yonatan da mai ɗaukar makamansa sukakai, yakashe mutane ashirin a cikin yankin fili kimanin rabin Eka.15akayi fargaba a sansanin, da cikin filayen, da kuma cikin mutane. Har sansanin da mahayansu suka yi fargaba. Ƙasa ta girgiza, aka kuma yi babbar fargaba.16Daga nan matsaran Saul a Gibiya ta Benyamin suka duba; taron sojojin Filistiyawa na bajewa, kuma suna tafiya nan da can.17Daga nan Saul ya ce da mutanen da ke tare da shi, "Ku lissafa ku gani wane ne ya ɓace a cikinmu." Da suka yi lissafi, Yonatan da mai ɗaukar makamansa sun ɓace.18Saul ya cewa Ahija, "Kawo akwatin Allah a nan," domin a lokacin yana tare da mutanen Isra'ila.19Yayin da Saul ke magana da firist, yamutsin a cikin sansanin Filistiyawa yana ci gaba kuma yana ƙaruwa. Daga nan Saul ya cewa firist, "Janye hannunka."20Saul da dukkan mutanen da ke tare da shi suka jera kuma suka shiga cikin yaƙin. Kowacce takobin Bafaliste tayi gãba da mutumin garinta, aka kuma yi babbar rikicewa.21Yanzu waɗannan Ibraniyawa waɗanda dã suke tare da Filistiyawa, waɗanda kuma suka tafi tare da su cikin sansani, su ma kuma suka haɗe tare da Isra'ilawan da ke tare da Saul da Yonatan.22Da mutanen Isra'ila waɗanda suka ɓoye kansu cikin tuddai kusa da Ifraim suka ji cewa Filistiyawa na tserewa, su ma suka bi bayansu cikin yaƙi.23Haka Yahweh ya ceto Isra'ila a wannan rana, Yaƙi kuma ya wuce har gaban Bet Aben.24A wannan rana mutanen Isra'ila sukakasance cikin ƙunci saboda Saul ya sanya mutanen ƙarƙashin rantsuwa ya kuma ce, "La'ananne ne mutumin da yaci wani abin ci har sai da yamma kuma nayi ramuwa akan maƙiyana." Don haka babu wani cikin mayaƙan da ya ɗanɗana abinci.25Daga nan dukkan mutanen suka shi ga cikin jeji kuma akwai zuma a bisa ƙasar.26Da mutanen suka shiga cikin jejin, zuman ya malalo, amma babu wanda ya sanya hannunsa ga bakinsa domin mutanen sun ji tsoron rantsuwar.27Amma Yonatan bai ji cewa mahaifinsa ya ɗaure mutanen tare da rantsuwa ba. Ya miƙa tsinin sandar da ke hannunsa ya luma cikin saƙar zuman. Ya ɗaga hannunsa zuwa bakinsa, idanunsa kuma suka wartsake.28Daga nan ɗaya daga cikin mutanen, ya amsa, "Mahaifinka ya yi wa mutane umarni mai tsanani tare da rantsuwa, ta wurin cewa, 'La'ananne ne mutumin da yaci abinci a wannan ranar,' ko da ya ke mutanen sun yi yaushi saboda yunwa.29Daga nan Yonatan ya ce, "Mahaifina ya aiwatar da matsala a ƙasar. Kalli yadda idanuna suka wartsake saboda na ɗanɗanakaɗan daga cikin zuman nan.30Yaya kuma in da mutanen yau sun ci a sake daga cikin ganima daga maƙiyansu da suka samo? Saboda yanzu kisan bai yi yawa ba a cikin Filistiyawa."31Sukakaiwa Filistiyawa hari a wannan rana daga Mikmash zuwa Aiyalon. Mutanen suka gaji sosai.32Mutanen suka afka da haɗama bisa ganimar suka kuma ɗauki tumaki, da shanu da maruƙa, suka kuma yanka su a ƙasa. Mutanen suka cinye su tare da jinin.33Daga nan suka gayawa Saul, "Duba, mutanen suna zunubi gãba da Yahweh ta wurin ci tare da jinin." Saul ya ce, "Kun aikata rashin aminci. Yanzu, a gangaro da wani babban dutse nan a gare ni."34Saul ya ce, "Fita cikin mutanen, ku kuma gaya masu, 'Bari kowanne mutum yakawo sansa da tunkiyarsa, ya yanka su a nan, ya kuma ci. Kada kuyi zunubi gãba da Yahweh ta wurin ci tare da jinin."' Sai kowanne mutum yakawo sansa tare da shi a wannan dare ya kuma yanka a wurin.35Saul ya gina bagadi ga Yahweh, shi ne kuma bagadi na farko da ya gina ga Yahweh.36Daga nan Saul ya ce, "Bari mu runtumi Filistiyawa da dare mu kuma warwatsa su har wayewar gari; kada mu bar ko ɗayan su da rai." Suka amsa, "Kayi duk abin da ya yi kyau a gare ka." Amma firist ɗin ya ce, "Bari mu kusanci Allah a nan."37Saul ya tambayi Allah, "In runtumi Filistiyawa? Zaka bayar da su cikin hannun Isra'ila?" Amma Allah bai amsa masa ba a wannan ranar.38Daga nan Saul ya ce, "Ku zo nan, dukkan ku shugabannin mutane; ku koya ku kuma duba yadda wannan zunubin ya faru a yau.39Domin, da wanzuwar Yahweh, wanda ke ceton Isra'ila, ko ma idan yana cikin Yonatan ne ɗana, tabbas zai mutu." Amma ba ko ɗaya daga cikin jama'ar daga cikin dukkan mutanen ya amsa masa.40Daga nan ya ce da dukkan Isra'ila, "Dole ku tsaya gefe ɗaya ni da Yonatan ɗana kuma mu tsaya gefe ɗaya." Mutanen suka ce da Saul, "Ka yi abin da ya yi kyau a gare ka."41Saul ya ce, Yahweh, Allah na Isra'ila! Idan ni ne na yi wannan zunubin ko kuma ɗana ne Yonatan ya yi shi, daga nan, Yahweh, Allah na Isra'ila, ka bada Urim. Amma idan wannan zunubi mutanenka Isra'ila ne suka aikata shi"Ka bada Tummim." Sai Yonatan da Saul aka ɗauka ta ƙuri'a, amma mayaƙan sukakaucewa Zaɓen.42Daga nan Saul ya ce, "akaɗa ƙuri'u tsakani na da Yonatan ɗa na." Daga nan aka ɗauki Yonatan ta ƙuri'a.43Daga nan Saul ya ce wa Yonatan, "Gaya mani abin daka yi." Yonatan ya gaya masa, "Na ɗanɗana zumakaɗan dakarshen sandar da ke hannuna. Ga ni nan; zan mutu."44Saul ya ce, "Allah ya yi haka kuma fiye ma a gare ni, idan baka mutu ba, Yonatan."45Daga nan mutanen suka cewa Saul, "Yonatan ya mutu kuwa, wanda ya aiwatar da wannan babbar nasara ga Isra'ila? Ya yi nesa da shi! da wanzuwar Yahweh, ba bu ko gashi ɗaya bisakansa da zai faɗi ƙasa, gama ya yi aiki tare da Allah a yau." Haka mutanen suka kuɓutar da Yonatan yadda bai mutu ba.46Daga nan Saul ya tsaida runtumar Filistiyawa, kuma Filistiyawan suka tafi na su wurin.47Da Saul ya fara mulki bisa Isra'ila, ya yi yaƙi gãba da maƙiyansa ta kowanne gefe. Ya yi yaƙi gãba da Mowab, Ammoniyawa, Idom, da sarakunan Zoba, da Filistiyawa. Duk inda ya juya, yana azabta horo akansu.48Ya yi aiki da ƙarfin hali mai girma yakayar da Amalekawa. Ya kuɓutar da Isra'ila daga hannuwan waɗanda suka washe su.49'Ya'yan Saul maza su ne Yonatan, Ishbi, da Malkishuwa. Sunayen 'ya'yansa mata biyu kuwa su ne Merab, ta fari, da Mikal, ƙaramar.50Sunan matar Saul shi ne Ahinowam; ita ce ɗiyar Ahimãz. Sunan shugaban sojojinsa kuwa Abna ɗan Nã, kawun Saul.51Kish ne mahaifin Saul; Nã kuma, mahaifin Abna, shi ne ɗan Abiyel.52An yi yaƙi mai tsanani gãba da Filistiyawa dukkan kwanakin Saul. Idan Saul ya ga wani ƙaƙƙarfan mutum, ko mutum mai ƙwazo, sai ya jawo shi a gare shi.
Yonatan ya fara kai wa sojojin Filistiyawa hari na biyu.
wani saurayi wanda ke da alhakin kula da makaman yakin maigidansa
itaciya wacce itacen ta ke da fata mai kauri, zagaye, ja kuma tana da tsaba manya da yawa da za ta ci
"Migron" sunan wani wuri ne a arewacin Yerusalem.
"Ahitub" da "Ichabod" sunaye ne na maza.
"Dutsen dutse" ne mai tsayi tare da daddafe mai tsayi. Dutsen sananne ne sosai kuma an ba shi suna "Bozez."
Wannan sunan ɗayan dutsen.
kalma mai wulakanci da aka yi amfani da ita ga maza waɗanda ba Yahudawa ba
"yi aiki don tallafawa" ko "taimake mu"
Wannan mummunan sau biyu ana iya bayyana ta cikin tsari mai kyau. AT: "Yahweh na iya yin ceto"
Wadannan tsauraran matakan sun hada da komai a tsakanin. AT: "ta kowane adadi na mutane"
"ba zai haye zuwa wancan gefen kwarin da Filistiyawa suke ba"
Anan "hannu" yana nufin ikon kayar dasu. AT: "zai ba mu damar cin nasara a kansu"
"Wannan zai tabbatar da cewa Ubangiji zai kasance tare da mu"
"ya kyale sojojin Filistiya su gansu"
Filistiyawa sun nufa cewa Ibraniyawa sun ɓuya a cikin rami a ƙasa kamar dabbobi.
Wannan karin magana ne da ke nufin "za mu koya muku darasi."
Anan "hannu" yana nufin iko don cin Filistiyawa. AT: "zai ba Israila damar cin galaba akansu"
Yayi wannan saboda yana da matukar tsayi. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "Don haka Yonatan ya hau sama, yana amfani da hannayensa da ƙafafunsa saboda yana da tsayi sosai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yonatan ya kashe Filistiyawa"
"Mai ɗaukar makaman Yonatan ya bi shi ya kuma kashe sojojin Filistiyawa"
AT: "Sojojin Filistiyawan a sansanin da filin, da duk mutanen da ke tare da su, sun firgita" ko "Sojojin Filistiyawan da ke sansanin da cikin filin, da duk mutanen da ke tare da su, suka tsorata ƙwarai"
Yana iya zama da taimako a faɗi dalilin. AT: "Allah ya sa ƙasa ta girgiza"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna jaddada cewa sojoji suna gudu zuwa kowane bangare.
Wasu juyi sigogi suna da "falmaran" a nan maimakon "akwatin Allah."
babban hayaniya da rudani
Wannan karin magane ne ta ma'anar "Dakatar da abin da kuke yi." Saul ba ya son Ahijah ya ci gaba da yin amfani da jirgin don neman taimakon Allah. AT: "Kada ku kawo kirji mai tsarki a wannan lokacin"
sauran rundunar Isra'ilawa da suka ragu tare da Saul
Ana magana da takuba kamar dai mutane masu rai. AT: "Sojojin Filistiyawa suna saran juna da takubba"
Wannan baya nufin kwanton-bauna. Waɗannan sojoji suna ɓuya saboda tsoron Filistiyawa. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Sojojin Isra'ila da suka tsorata kuma suka ɓuya a kan tsaunuka"
Sojojin sun fahimci cewa ba a yarda da shakatawa ba yayin rantsuwar Saul.
Filistiyawa suka gudu zuwa cikin daji, sojojin Isra'ila kuma suka bi su zuwa can.
Wannan karin magana ne don jaddada yawan zumar da ke cikin daji. AT: "an sami zuma mai yawa ko'ina"
Anan sanya “hannu a bakinsa” magana ne wanda ke nufin cin abinci. AT: "babu wanda ya ci wani"
Yonatan ya fahimci rantsuwar mahaifinsa.
Anan ana maganar wajibcin yin biyayya ga rantsuwa kamar ana daure mutane da igiyoyi. AT: "ya yi umarni cewa mutane su yi biyayya ga rantsuwarsa"
Anan "hannu zuwa bakinsa" wani magana ne wanda ke nufin cin abinci. AT: "Ya ɗan ci zuma"
Wannan karin magana yana nufin cewa an ƙarfafa shi. AT: "ya dawo da ƙarfinsa"
Wannan magana ne wanda yake wakiltar al'ummar Isra'ila. AT: "ga Isra'ila"
Yonatan ya yi amfani da wannan tambayar don ya nuna cewa ya kamata a bar mutane su ci. Wannan na iya zama sanarwa. AT: "Nasararmu za ta fi kyau idan da mutane sun ci abinci da yardar kaina a yau daga ganimar da suka kwashe daga abokan gaba."
Saboda sojoji ba su iya cin abinci yayin yaƙin, yayin da ranar ta ci gaba, sai suka yi rauni. Saboda wannan, ba su iya kashe yawancin Filistiyawa.
Kalaman Yonatan sun sa sojojin yin zunubi ga Allah a cikin babbar yunwa.
wani wuri a cikin Zebulun a Isra'ila
Yunwa ta kama su sosai ba su zubar da jinin ba tukuna kafin su ci. Wannan karya doka ne da aka ba Musa saboda al'ummar Isra'ila. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "sun ci su ba tare da sun zubar da jini ba kamar yadda doka ta tanada"
Saul yana zargin dukkan rundunarsa da aikata rashin aminci duk da cewa wannan magana ce ta kowa saboda ba kowane soja ne ya aikata rashin gaskiya ba.
Saul ya gaya wa mutanen su kawo dabbobinsu a babban dutse su yanka su ci.
Babu tabbacin idan Saul ya gina wannan bagaden tare da babban dutsen da mutane suka kawo masa a cikin 1 Samuila 14:33.
Saul yana so ya ci gaba da yaƙi da Filistiyawa.
An bayyana wannan ta hanya mara kyau don jaddada yanka. Ana iya bayyana shi cikin tsari mai kyau. AT: "bari mu kashe kowane ɗayansu"
Anan "kusanci ga Allah" yana hade da tambayar shi shawara. AT: "Bari mu roki Allah me ya kamata mu yi"
Anan "hannu" yana nufin ikon kayar dasu. AT: "ba mu damar cin nasara a kansu"
Wannan yana nuna cewa Allah bai yarda ya taimaki Saul ba.
"sami wanda ya yi zunubi"
Saul ya bayyana wannan a matsayin yanayin tunanin ne saboda bai yarda cewa Jonathan yana da laifi ba.
Mutane suka yi tsit, saboda yawancinsu sun sani Yonatan ya karya rantsuwar Saul. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Mutanensa sun san wanda ke da laifi, amma babu wani daga cikinsu da ya ce wa Saul komai"
Wannan ya zama gama gari tunda sojojin Isra'ila ne kawai suka hallara. AT: "Sai ya ce wa sojojin Isra'ila da suke wurin"
Isra'ilawa a lokacin suna amfani da duwatsu na musamman da ake kira Urim da Tummim don su sami ja-gora daga Allah. AT: "Nuna mana ta hanyar Tummim"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kuri'a sun nuna cewa ko Yonatan ko Saul suna da laifi, amma sojojin ba su da laifi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sannan kuri'a ta nuna cewa Yonatan ya yi laifi"
Kuri'a ta nuna cewa Jonathan yayi zunubi.
"Faɗa mini yadda ka yi zunubi" ko "Ka gaya mini abin da ka yi wanda ba dai-dai ba ne"
Mai yiwuwa su ne 1) "Ina shirye in mutu" ko 2) "Shin na cancanci a kashe ni saboda aikata hakan?"
Saul ya yi rantsuwa ta biyu ta wauta cikin ƙasa da kwana ɗaya. AT: "Allah ya kashe ni idan ban kashe ku ba, Yonatan"
Sojojin suna kare Yonatan daga Saul.
Mutanen suka tsawata wa Saul. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Yonatan ya kammala wannan babbar nasara ga Isra'ila. Lallai bai mutu ba."
Wannan karin magana ya nuna yadda mutanen Isra'ila zasu kare Yonatan su tsare shi. Ana iya bayyana waɗannan jimla a cikin tsari mai kyau. AT: "za mu kiyaye shi daga duk wata cuta"
Saul na ɗan lokaci ya yi aiki da gaba gaɗi don ya ci nasara a kan abokan gaban Isra’ila.
"Duk inda ya tura sojojinsa"
Kalmar "hannu" tana wakiltar iko. AT: "daga ikon sarrafawa"
Wannan bayanan asali ne game da dangin Saul.
Waɗannan sunayen maza ne.
Waɗannan sunayen mata ne.
Wannan sunan mace.
Waɗannan sunayen maza ne.
"Duk rayuwar Saul"
"ya tilasta shi ya shiga cikin sojojinsa"
1Sama'ila ya cewa Saul, "Yahweh ya aiko ni in shafe ka sarki bisa mutanensa Isra'ila. Yanzu ka saurari maganganun Yahweh.2Wannan ne abin da Yahweh mai runduna ya ce, 'Na lura da abin da Amalek ya yiwa Isra'ila cikin tsayayya da su a bisa hanya, sa'ad da suka fito daga cikin Masar.3Yanzu ka je kakai hari ga Amalek ka kuma lalata duk abin da suke da shi ɗungum. Kadaka raga masu, ammaka kashe su maza da mata, yaro da jariri, saniya da tunkiya, raƙumi da jaki."'4Saul ya tattaro mutanen ya ƙidaya su a birnin Telem: mutane dubu ɗari bisa ƙafa, da mutanen Yahuda dubu goma.5Daga nan Saul ya zo cikin birnin Amalek ya kuma jira a cikin kwari.6Daga nan Saul ya cewa Keniyawa, "Ku je, ku tafi, ku fito daga cikin Amalekawa, domin kada in lalatar da ku tare da su. Domin kun nuna halin kirki ga dukkan mutanen Isra'ila, sa'ad da suka zo daga Masar." Sai Keniyawa suka wãre daga Amalekawa.7Sai Saul yakai hari ga Amalekawa, daga Habila har ya zuwa Shur, wadda ke gabas da Masar.8Daga nan ya ɗauki Agag sarkin Amalekawa da rai; gaba ɗaya ya lalatar da dukkan mutanen dakaifin takobi.9Amma Saul da mutanen suka bar Agag, duk da mafi kyau daga cikin tumaki, da shanu, da maraƙai masu ƙiba, da raguna. Kowanne abu da ke da kyau, ba su lalatar ba. Amma gaba ɗaya suka lalatar da duk wani abu wulaƙantacce marar amfani kuma.10Daga nan maganar Yahweh ta zo ga Sama'ila, cewa,11"Ya ba ni ɓacin rai cewa na naɗa Saul sarki, domin ya juya baya daga bi na bai kuma aiwatar da dokokina ba." Sama'ila ya fusata; ya yi kuka ga Yahweh dukkan dare.12Sama'ila ya farka da wurwuri domin ya sami Saul da safe. Aka cewa Sama'ila, "Saul ya tafi Kamel kuma yakafa wakansa wurin tunawa, daga nan ya juya kuma ya ci gaba zuwa Gilgal."13Daga nan Sama'ila ya zo wurin Saul, Saul kuma ya ce masa, "Mai albarka ne kai daga Yahweh! Na cika dokar Yahweh."14Sama'ila ya ce, "Daga nan mene ne wannan kukan tumakin a kunnuwa na, da kukan shanun da na ke ji?"15Saul ya maida amsa, "An kawo su ne daga Amalekawa. Domin mutanen sun keɓe mafi kyau daga cikin tumakin da shanun, domin hadaya ga Yahweh Allahnka. Sauran gaba ɗaya mun hallakar da su."16Daga nan Sama'ila ya cewa Saul, "Jira, kuma zan faɗi maka abin da Yahweh ya ce mani da daren nan." Saul ya ce masa, "Yi magana!"17Sama'ila ya ce, "Koda ya ke kai ƙarami ne a idanunka, ba an mai she ka shugaban kabilun Isra'ila ba? Daga nan Yahweh ya shafe ka sarki bisa Isra'ila,18Yahweh kuma ya aike ka bisa hanyarka ya kuma ce, 'Je kuma gaba ɗayaka hallakar da masu zunubi, Amalekawa, ka kuma yi faɗa gãba da su har sai sun hallaka.'19Me yasa baka yi biyayya da muryar Yahweh ba, amma a maimako ka ƙwato ganimaka kuma yi abin da ke mugunta a gaban Yahweh?"20Daga nan Saul ya cewa Sama'ila, "Lallai na yi biyayya da muryar Yahweh, kuma na tafi bisa hanyar da Yahweh ya aike ni. Nakamo Agag, sarkin Amalek, kuma gaba ɗaya na hallakar da Amalekawa.21Amma mutanen suka ɗauko wasu daga cikin ganimar - tumaki da shanu, abubuwa mafi kyau da aka keɓe ga hallakarwa, domin hadaya ga Yahweh Allahnka a Gilgal."22Sama'ila ya maida amsa, "Yahweh yana gamsuwa da baye-baye na ƙonawa da hadayu, fiye da biyayya da muryar Yahweh? Biyayya tafi hadaya, kuma saurare ya fi kitsen raguna.23Domin tawaye kamar zunubin tsafi ya ke, taurin kai kumakamar mugunta da ƙazanta. Sabodaka yi watsi da maganar Yahweh, shi ma ya ƙika da ga zama sarki."24Daga nan Saul ya cewa Sama'ila, "Na yi zunubi; domin nakarya dokar Yahweh da maganganunka, saboda ina jin tsoron mutanen na kuma yi biyayya da muryarsu.25Yanzu, ina roƙon kaka yafe zunubina, ka kuma juyo tare da ni domin in yi sujada ga Yahweh."26Sama'ila ya cewa Saul, "Ba zan koma tare dakai ba; domin ka yi watsi da maganar Yahweh, Yahweh kuma ya ƙika da zama sarki bisa Isra'ila."27Yayin da Sama'ila ya juya domin ya tafi, Saul ya riƙe haɓar rigarsa, ta kuma yage.28Sama'ila ya ce masa, "Yahweh ya yage sarautar Isra'ila daga gare ka a yau ya kuma bayar da ita ga makwabcinka, wani wanda ya fi ka.29Haka kuma, Ƙarfin Isra'ila ba zai yi ƙarya ba ko ya canza ra'ayinsa; domin shi ba mutum ba ne, da zai canza ra'ayinsa."30Daga nan Saul ya ce, "Na yi zunubi. Amma ina roƙon kaka darajanta ni yanzu a gaban dattawan mutanena da gaban Isra'ila. Ka sake juyowa tare da ni, domin in yi sujada ga Yahweh Allahnka."31Sai Sama'ila ya sake juyowa bayan Saul, Saul kuma ya yi sujada ga Yahweh.32Daga nan Sama'ila ya ce, "Kawo Agag sarkin Amalekawa nan wurina." Agag ya zo gare shi ɗaure cikin sarƙoƙi ya kuma ce, "Tabbas ɗacin mutuwa ya wuce."33Sama'ila ya maida amsa, "Kamar yadda takobin ka ta maida mata marasa 'ya'ya, haka mahaifiyarka za ta zama marar ɗa a cikin mata." Daga nan Sama'ila ya datse Agag gunduwa-gunduwa a gaban Yahweh a Gilgal.34Sama'ila ya tafi Rama, Saul kuma ya tafi gidansa a Gibiya ta Saul.35Sama'ila bai sake ganin Saul ba har sai ranar mutuwarsa, gama ya yi makoki domin Saul. Yahweh ya yi baƙinciki da cewa ya naɗa Saul sarki bisa Isra'ila.
Wannan na nufin sakon daga daga Yahweh. AT: "sakon Yahweh"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya. Jumla ta biyu tana ba da takamaiman bayanai game da abin da za su hallaka gaba ɗaya.
Wannan shi ne birni a cikin kudancin Yahuda.
"maza 200,000 a kafa, da kuma mutanen Yahuda 10,000"
Ƙungiyar mutanen makiyaya wacce ta kasance da aminci ga al'ummar Isra'ila
Waɗannan su ne sunayen wuraren.
Yahweh ya gaya wa Saul ya hallaka komai, amma a nan Saul ya ƙi bin umarnin Yahweh.
“Bakin takobi” yana wakiltar sojoji suka yi amfani da su a yaƙi. Anan Saul ya wakilci kansa tare da sojojinsa. AT: "sun hallakar da mutanen gaba ɗaya da takubbansu" ko "sun kashe mutanen duka da takubbansu"
Saul ya yi rashin biyayya ga Allah ta wurin barin Agag ya rayu.
Saul ya yi rashin biyayya ga Allah ta wurin kiwon dabbobi mafi kyau.
Karin magana "kalmar Yahweh ta zo ga" ana amfani da ita don gabatar da saƙo na musamman daga Allah. AT: "Yahweh ya ba da saƙo ga Sama'ila. Ya ce," ko "Yahweh ya yi magana da wannan saƙon ga Sama'ila:"
"Yi hankuri"
Saul ana yin biyayya ga Yahweh ana maganarsa kamar Saul ya juya baya daga barin bin Allah. AT: "ya daina bi na"
"bai yi biyayya ga abin da na umurce shi ba." Ya kamata Saul ya hallaka komai da kowa. Allah ya sanya doka a kan Amalek. Amma Saul ya bar waɗansu dabbobin su rayu.
"Wani ya fadawa Sama'ila"
Saul ya cika da girman kai.
Babu tabbaci idan Saul ya fahimci cewa bai yi biyayya da umurnin Allah ba don ya hallaka Amalekawa gaba ɗaya.
Sama'ila ya yi tambaya game da dalilin da ya sa Saul bai kashe Amalekawa ƙaƙaf ba.
Waɗannan su ne sautunan da waɗannan dabbobi ke yi. Yarenku na iya samun sharuɗɗa daban-daban don waɗannan.
Kalmar "su" da kalmar "mutane" a nan duka suna wakiltar sojojin Saul. Saul yana zargin mutanen ne maimakon kansa.
Saul yana jayayya cewa dabbobin don hadaya banda umarnin Yahweh don halakar da komai.
Anan gani yana wakiltar hukunci ko kimantawa. AT: "a ra'ayinku" ko "a hukuncinku"
Sama'ila ya yi amfani da wannan tambayar don ya tuna wa Saul abubuwan da Allah ya ba shi. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Yahweh ya naɗa ku sarkin kabilan Isra'ila!"
Sama'ila ya yi wannan tambayar don ya tsawata wa Saul don rashin biyayya ga Yahweh. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Ya kamata ku yi biyayya ... Yahweh!"
Sama’ila yana zargin Saul da rashin biyayya kai tsaye. Yahweh ya umarci Saul ya hallaka dukan abin da yake na Amalekawa, kada ya koma da wani sansaninsa.
Anan "gani" na nuni ga tunanin Yahweh ko ra'ayi. AT: "abin da Yahweh ya ɗauka a matsayin mugunta" ko "abin da ke mugu a cikin hukuncin Yahweh"
Wannan magana ce mai karfafawa. Babu tabbaci idan Saul ya ɗauka wannan gaskiya ne, ko kuwa kawai yana neman hujja ne don zunubinsa.
Wannan yana nuna yana canza zargin zuwa ga mutane.
Sama'ila yayi wannan tambayar don ya nanata cewa biyayya ta fi hadaya mahimmanci. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Yahweh baya jin daɗin hadayu na ƙonawa da hadayu kamar yin biyayya da muryarsa!"
Allah yana son Saul ya yi masa cikakkiyar biyayya cikin halakar Amalekawa. Babu wani abu a ƙasar da ya dace da hadayu.
Cikakken sunan "tawaye" ana iya fassara shi da kalmar aikatau. AT: "yin tawaye zunubi ne kamar yin duba"
Cikakken sunan "taurin kai" ana iya fassara shi da kalma sannan kuma za a iya fassara kalmar nan ta "mugunta" azaman sifa. AT: "taurin kai ya munana kamar aikata mugunta da aikata mugunta"
"na yanke shawara cewa ba za ku ƙara zama sarki ba"
Wannan karin magana ne wanda ke nufin ya saba umarnin. AT: "Na yi rashin biyayya ga abin da Yahweh ya umarta"
Wannan shine dalilin da Saul ya bayar don rashin biyayya ga Allah. AT: "saboda ina tsoron sojoji"
Sama’ila ya bayyana sarai cewa Saul ya fahimci cewa ya yi rashin biyayya ga Allah a lokacin da ya ceci dabbobi mafi kyau kuma bai kashe Agag ba.
Saul ya yi wannan don ya hana Sama’ila ya tafi. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Saul ya yi ƙoƙari ya hana shi ta hanyar riƙe gefen rigar Sama'ila"
Wannan yana komawa ne ga lokacin da Saul ya yaga rigar Sama'ila a cikin 1 Samuila 15:27. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "Kamar yadda zaka yayyaga rigata, Yahweh ya tsage mulkin Isra'ila"
Allah ya riga ya ƙaddara wanda zai zama sarki bayan Saul.
Anan ana kiran Yahweh “Ƙarfin Isra’ila” domin yana ba Isra’ilawa ƙarfi. AT: "Yahweh, wane ne ƙarfin Isra'ila"
An bayyana wannan a matsayin mara kyau don jaddada cewa Allah amintacce ne. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "shi ne Allah, kuma zai aikata abin da ya ce zai yi"
Wataƙila Saul ya fi son mutane su girmama shi fiye da bauta wa Allah da gaske.
Wannan yana nuna cewa Sama'ila ya canza shawara, kuma sun tafi tare zuwa inda mutane suke. AT: "Don haka Sama'ila ya amince da yin hakan, kuma suka tafi tare tare da komawa inda mutane suke"
"Sun kawo masa Agag ɗaure da sarƙoƙi sai Agag yace"
Duk waɗannan jimlolin suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana iya nufin su kasance cikin salon waƙa. AT: "Tunda kun kashe mutane, ku ma za'a kashe ku"
Sama'ila shi ne wanda ya gama wannan aiki wanda Yahweh ya umarci Saul ya yi. AT: "Sai Sama'ila ya yanyanka Agag gunduwa-gunduwa da takobinsa"
Waɗannan su ne sunayen wuraren.
Sama'ila bai sake ganin Saul ba tsawon ransa"
1Yahweh ya cewa Sama'ila, "Har yaushe zaka yi makoki domin Saul, tunda nayi watsi da shi daga zama sarki bisa Isra'ila? Ka cika ƙahonka da mai ka kuma tafi. Zan aike ka ga Yesse na Betlehem, domin na zaɓar wakaina sarki cikin 'ya'yansa maza."2Sama'ila ya ce, "Yaya zan tafi? Idan Saul ya ji haka, zai kashe ni." Yahweh ya ce, "Ka ɗauki maraƙi tare dakai ka kuma ce, 'Na zo in yi hadaya ga Yahweh.'3Ka kira Yesse zuwa hadayar, zan kuma nuna maka abin da zaka yi. Zaka shafe mani wanda zan gaya maka."4Sama'ila ya yi yadda Yahweh ya faɗi ya kuma tafi Betlehem. Dattawan birnin suna rawar jiki yayin da su ka zo suka same shi suka kuma ce, "Kana zuwa cikin salama?"5Ya ce, "Cikin salama; Na zo in yi hadaya ga Yahweh. Ku shirya ku keɓe kanku ku kuma zo tare da ni wurin hadayar." Daga nan ya ware Yesse da kuma 'ya'yansa maza ya kuma gayyace su zuwa hadayar.6Da suka zo, yakalli Iliyab ya kuma faɗi wakansa cewa shafaffe na Yahweh ba bu shakka yana tsaye a gaba na.7Amma Yahweh ya cewa Sama'ila, "Kadaka dubi siffarsa ta zahiri, ko tsawon ƙirarsa; saboda na ƙi shi. Domin Yahweh ba ya duba yadda mutum ke duba wa; mutum yanakallon siffa a zahiri, amma Yahweh yanakallon zuciya."8Daga nan Yesse ya kira Abinadab ya kuma sa ya gitta a gaban Sama'ila. Daga nan Sama'ila ya ce, "Wannan ma Yahweh bai zaɓe shi ba."9Yesse daga nan yasa Shamma ya gitta, amma Sama'ila ya ce, "Wannan ma Yahweh bai zaɓe shi ba."10Yesse yasa 'ya'yansa maza bakwai suka gitta a gaban Sama'ila. Daga nan Sama'ila ya cewa Yesse, "Yahweh bai zaɓi ɗaya daga cikin waɗannan ba."11Daga nan Sama'ila ya cewa Yesse, "Dukkan 'ya'yanka maza suna nan?" Ya maida amsa, "Akwai ƙaramin su da ya rage, amma yana lura da tumaki." Sama'ila ya cewa Yesse, "Ka aika akawo shi; domin ba za mu zauna ba har sai ya zo nan."12Yesse ya aika aka zo da shi ciki. Yanzu dai wannan ɗa jã ne da kyawawan idanu da kyakkyawar siffa. Yahweh ya ce, "Tãshi, shafe shi; domin shi ne."13Daga nan Sama'ila ya ɗauki ƙahon mai ya kuma shafe shi a tsakiyar 'yan uwansa. Ruhun Yahweh ya afko bisa Dauda daga wannan rana har zuwa gaba. Daga nan Sama'ila ya tashi ya kuma tafi Rama.14Yanzu Ruhun Yahweh ya bar Saul, ruhu mai illa kuma daga Yahweh yana azabtar da shi a maimako.15Bãyin Saul suka ce masa, "Duba, ruhu mai illa daga Allah na azabtar dakai.16Bari ubangijinmu yanzu ya umarci bãyinsa waɗanda ke tsaye a gabanka su nemo mutum wanda ya kware a kiɗin garaya. Daga nan idan ruhu mai illa daga Allah yana bisanka, zai kaɗa ta kuma zaka sami lafiya."17Saul ya cewa bãyinsa, "Ku samo mani mutum da ya iyakaɗa wa sosai ku kumakawo mani shi."18Daga nan ɗaya daga cikin samarin ya amsa, ya kuma ce, "Na ga wani ɗan Yesse Betlehemiye, wanda ya kware akaɗa wa, ƙaƙƙarfa, mutum mai ƙarfin hali, mutumin yãƙi, mai tattali a zance, mutum mai asali; kuma Yahweh yana tare da shi."19Sai Saul ya aika da manzanni wurin Yesse, ya kuma ce, "Ka aiko mani da ɗanka Dauda, wanda ke tare da tumaki."20Yesse ya ɗauki jaki danƙare da gurasa, da salkar inabi, da 'yar akuya, ya kuma aika da su tare da ɗansa Dauda wurin Saul.21Daga nan Dauda ya zo wurin Saul ya kuma shiga hidimarsa. Saul ya ƙaunace shi sosai, ya kuma zama mai ɗaukar makamansa.22Saul ya aika wa Yesse, cewa, "Bari Dauda ya tsaya a gabana, domin ya sami tagomashi a idanu na."23Duk sa'ad da ruhu mai illa daga Allah yana bisan Saul, Dauda zai ɗauki garaya ya kumakaɗa ta. Sai Saul ya wartsake ya kuma yi lafiya, kuma ruhu mai illar sai ya tafi daga gare shi.
Wannan tambayar tsawatarwa ce daga Allah. Ana iya fassara ta azaman sanarwa. AT: "Dakatar da makoki na ƙi Saul daga zama sarkin Isra'ila."
Kalmar "ƙaho" wani lokaci ana amfani da ita don "kwalba" wanda yake kama da ƙaho kuma ana amfani da shi don riƙe ruwa ko mai. An yi amfani da tukunyar mai don shafawa sarki.
Sama'ila ya yi amfani da tambaya don ya nanata cewa ya damu da zuwa Benyamin. AT: "Ba zan iya tafiya ba!" ko "Ina jin tsoron tafiya."
Wannan yana da zance a cikin ambato. Za'a iya bayyana ambaton kai tsaye azaman zance kai tsaye. AT: "ku gaya wa mutanen can cewa kun zo ne don yin hadaya ga Yahweh."
Da alama dattawan suna rawar jiki saboda sun damu da Sama'ila ya zo ya tsawata musu.
Ana iya bayyana wannan azaman cikakkiyar jimla. AT: "Ee, na zo lafiya"
Keɓe wani yana nufin shirya shi don nufin Yahweh ta hanyar tabbatar da cewa mutumin yana da tsabta bisa ga ka'idar Musa.
Anan "su" suna nufin Yesse da 'ya'yansa maza.
A nan "ya" yana nufin Sama'ila.
Yahweh yana magana akan kansa a cikin mutum na uku. AT: "Domin Ni Yahweh, ban gani ba ... Ni, Yahweh, na duba"
Wadannan sunayen biyun 'ya'yan Yesse.
An fahimci cewa Shamma ya wuce ta Sama'ila. AT: "Yesse ya sa Shamma ya wuce gaban Sama'ila" ko "Yesse sannan ya ce wa Shamma ta je wurin Sama'ila"
"Har yanzu akwai saurayi na ƙarami"
An fahimci cewa suna jira su zauna su ci abinci. AT: "ba za mu zauna mu ci ba"
Ana amfani da kalmar "Yanzu" a nan don alamar hutu a layin babban labari. A nan mai ba da labarin ya faɗi game da sabon mutum a cikin labarin.
Kalmar "jã" na nufin Dauda yana cikin koshin lafiya.
Kalmomin "yi sauri" yana nufin Ruhun Yahweh ya rinjayi Dauda. A wannan yanayin yana nufin ya ba Dauda damar cika duk abin da Yahweh yake so ya yi. Duba yadda zaka fassara makamancin magana a cikin 1 Samuila 10: 5.
Ana nuna cewa ya tashi bayan sun zauna cin abinci.
Ana amfani da wannan kalmar a nan don alamar hutu a cikin babban layin labari. A nan ne mai ba da labarin ya fara ba da sabon labarin labarin.
Wannan na iya nufin ko dai "ruhun da ke haifar da matsala" ko "muguwar ruhu."
Barorin suna kiran Saul a cikin mutum na uku "ubangijinmu." AT: "Muna roƙonka da kai, maigidanmu, ka ba da umarni"
Bayin suna kiran kansu a cikin mutum na uku "bayin ku." AT: "ka umurce mu, bayinka da suka halarci wurinka, da su duba"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "babban mayaki" ko 2) "mutum ne jarumi."
"mai hikima a magana" ko "wanda ke magana da hikima"
Anan "tare da shi" na nufin Yahweh ya taimaka ya kuma sa wa Dauda albarka.
Anan "ya zo" ana iya fassara shi da "tafi."
Cikakken sunan "sabis" za a iya bayyana shi azaman kalma. AT: "ya fara yi masa aiki"
"Dauda ya zama mai ɗaukar wa Saul makamai"
Anan “tsaya a gabana” karin magana ne wanda ke nufin ci gaba a hidimar Saul. AT: "Bar David ya zauna a cikin sabis na"
Anan “idanu” sunaye ne na gani, kuma “gani na” yana wakiltar yadda Saul yake hukunci ko kimanta Dauda. AT: "ya sami tagomashi a cikin hukunci na" ko "Na yarda da shi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kiɗan zai sanyaya Saul kuma ya bashi lafiya"
1Yanzu Filistiyawa suka tara rundunarsu domin yaƙi. Suka taru a Soko, wacce take ta Yahuda. Suka yi sansani tsakanin Soko da Azeka, cikin Ifes Dammim.2Saul tare da mutanen Isra'ila suka taru sukakafa sansani a kwarin Ila, suka jã layin dãga dominsu fuskanci Filistiyawa.3Filistiyawa suka tsaya a bisa dutse a sashen gefe, Isra'ila kuma na bisa dutse a wancan gefen a kwari da ke tsakaninsu.4Wani mutum mai ƙarfi ya fito daga cikin sansanin Filistiyawa, mutum mai suna Goliyat daga Gat, wanda tsayinsa kãmu shida ne da rabi.5Yana da hular tagulla a bisakansa, yana kuma sanye da tufafin yaƙi. Rigar nada nauyin Shekel dubu biyar na tagulla.6Yana sanye da makarin ƙafa na tagulla da kuma mãshi na tagulla a tsakiyar kafaɗunsa.7Sandar mashinsa na da girma, da tausasshen igiya domin harba takamar dirkar masaka. Kan mashinsa na da nauyin shekel na ƙarfe ɗari shida. Mai ɗaukar masa garkuwa na a gaba da shi.8Ya tsaya ya yi ihu ga sojojin Isra'ilawa, "Donme kuka fito waje kukakafa sansanin yaƙi? Ni ba Bafiliste ba ne, ku kuma ba bayi ne na Saul ba? Ku zaɓa wakanku mutum kuma bari ya sauko gare ni.9Idan ya iya faɗa da ni ya kumakashe ni, sa'an nan zamu zama bayinku. Amma idan na kãda shi na kumakashe shi, sai ku zama bayinmu ku kuma bauta mana."10Sai kuma Bafilisten ya ce, "Na ƙalubalanci rundunar Isra'ila yau. Ku ba ni wanda zamu yi faɗa tare."11Lokacin da Saul da dukkan Isra'ila suka ji abin da Bafilisten ya faɗi, sai sukakaraya da babban tsoro.12Yanzu dai Dauda ɗan Ifraimiye ne na Betlehem cikin Yahuda, mai suna Yesse. Yana da 'ya'ya maza takwas. Yesse tsohon mutum ne a cikin kwanakin Saul, tsoho ne tukub a tsakanin mutane.13Manyan 'ya'ya maza na Yesse suna tare da Saul a filin dãga. Sunayen 'ya'yansa maza uku da suka tafi bakin dãga su ne Iliyab wanda shi ne ɗan fari, na biyun Abinadab, sai na ukun Shammah.14Dauda shi ne ɗan ƙaraminsu. Yayyensa uku suka bi Saul.15Yanzu dai Dauda yana fita yana shigowa gaba da baya tsakanin rundunar Saul da kuma tumakin babansa a Betlehem, domin ya ciyar da su.16Kwana arba'in mai ƙarfin nan Bafilisten yana zuwa gaba safiya da yamma domin ya miƙakansa ga yaƙi.17Sai Yesse ya cewa ɗansa Dauda, "Ka ɗauko wa 'yan uwanka mudu 22 na wannan gasasshen hatsin da kuma wannan gurasar goma, ka kuma ɗauko su da sauri kakai su sansani zuwa ga 'yan'uwanka.18Ka kuma ɗauki curin man shanu goma ga shugabansu na dubu. Ka duba lafiyar 'yan'uwankaka kuma dawo da tabbacin suna lafiya.19'Yan'uwanka suna tare da Saul da dukkan mazajen Isra'ila a cikin kwarin Ila, suna yaƙi da Filistiyawa."20Dauda ya tashi da sassafe ya bar garken cikin hannun wani makiyayi domin ya kula da su. Ya ɗauki abincin ya tafi, kamar yadda Yesse ya umarce shi. Ya iso sansani lokacin da rundunar ke fitowa zuwa filin dãga suna sowa ta yaƙi.21Sa'an nan Isra'ila da Filistiyawa sukakafa layi domin dãga, runduna gãba da juna.22Dauda ya bar kayayyakinsa ajiya wurin maitsaron kayayyaki, ya ruga da gudu zuwa wurin rundunar, ya gaida 'yan'uwansa.23Yayin da ya ke cikin magana da su, mutumin mai ƙarfin, Bafilisten na Gat, mai suna Goliyat, ya kuma fito daga cikin rundunar Filistiyawa, ya kuma furta maganganun da ya ke furtawakamar da farko, Dauda kuwa ya ji su.24A lokacin da dukkan Isra'ila suka ga mutumin, suka yi gudu daga wurinsa kuma suka ji tsoro matuƙa.25Mazajen Isra'ila suka ce, "Ko kun ga wannan mutumin wanda ya fito? Ya fito domin ya cakuni Isra'ila. Sarki zai bai wa duk wadda yakashe shi dukiya mai yawa. kuma zai ba da ɗiyarsa gare shi ya aura, Kuma za ya raba gidan ubansa daga biyan haraji a Isra'ila."26Dauda ya cewa mutanen da ke tsaye kusa da shi, "Mene ne za a yiwa mutumin da yakashe wannan Bafilisten domin yakawar da kunya ga Isra'ila? Wane ne wannan Bafilite marar kaciya da har ya ke rena rundunar Allah mai rai?"27Sai mutanen suka furta abin da suka faɗa tun farko kuma suka ce masa, "Haka za a yiwa mutumin da yakashe shi."28Iliyab babban ɗan'uwansa ya ji sa'ad da ya yi magana da mutanen. Sai fushin Iliyab ya yi ƙuna a bisa Dauda, sai ya ce, "Mene ne dalilin da yasaka gangaro nan wurin? A hannun wane ne ka baro 'yan tumakan nan cikin jeji? Na san girman kanka, da kuma fahariyar zuciyarka; domin ka gangaro nan domin kayi kallon yaƙi ne."29Dauda ya ce, "Mene ne na yi yanzu? Ba tambayakawai na yi ba?"30Ya juya ya bar shi zuwa wurin wani, ya sake irin magana a yadda ya yi dã. Mutanen suka amsa masakamar dã.31Da aka ji maganganun da Dauda ya faɗa, sojoji suka maimaita su ga Saul, shi kuwa ya aika akakawo Dauda.32Sai Dauda ya cewa Saul. "Kada zuciyar kowanne mutum takaraya sabili da wancan Bafilisten; bawanka zai tafi ya yi faɗa da wannan Bafilisten."33Saul ya cewa Dauda, "Ba zaka iya fãɗawa Bafilisten nan ba domin ka yi faɗa da shi; gamakai matashi ne, amma shi mutum ne mayaƙi tun yana saurayi."34Amma Dauda ya cewa Saul, "Bawanka yana kula da tumakin mahaifinsa. Lokacin da zaki ko damisa ya taso ya ɗauki 'yar akuya daga cikin garken,35nakan bisu in kumakai masu farmaki, in kuma ƙubutar da shi daga bakinsa. Lokacin da zai tayar mani, nakama shi a gemunsa, na buga shi, na kumakashe shi.36Bawanka yakashe zaki da damisa. Wannan Bafilisten marar kaciya zai zamakamar ɗayansu, tunda ya ƙalubalanci rundunar Allah mai rai."37Dauda ya ce, "Yahweh ya ƙubutar da ni daga hannun zaki da kuma hannun damisa. Za ya ƙubutar da ni daga hannun wannan bafilisten." Sa'an nan Saul ya cewa Dauda, "Je ka, bari kuma Yahweh yakasance tare dakai."38Saul ya sanya wa Daudakayan yaƙinsa. Yasa masa hular tagulla akansa, ya kuma sanya masa mayafin wayoyi.39Dauda ya ɗaura takobinsa a rigar yaƙi. Amma yakasa tafiya ciki, domin baya yi koyi da su ba. Sai Dauda ya cewa Saul, "Ba zan iya fita in yi faɗa da wannan kaya ba, gama ban yi koyo da su ba." Saboda haka Dauda ya kwaɓe kayan.40Ya ɗauki sandar kiwonsa cikin hannunsa ya kuma zaɓi duwatsu biyar daga cikin rafi; ya zuba su cikin jakarsa ta kiwo. Majajjawarsa na cikin hannunsa sa'ad da ya fuskanci Bafilisten.41Bafilisten ya rugo zuwa wurin Dauda, da mai ɗaukar masa makamai a gabansa.42A lokacin da Bafilisten ya juya ya kuma ga Dauda, sai ya rena shi, gama ɗan yaro ne kawai, kuma jã, mai asalin siffa.43Sai Bafilisten ya cewa Dauda, "Ni kare ne, da zaka zo gare ni da sanduna?," sai kuma Bafilisten ya la'anci Dauda da allolinsa.44Bafilisten ya cewa Dauda, "Zo gare ni, zan kuma bada namanka ga tsunytsayen sammai ga kuma namomin jeji."45Dauda kuwa ya amsa wa Bafilisten, "Kai kana zuwa gare ni da takobi, da mashi, da kibiya. Amma na zo gare ka a cikin sunan Yahweh mai runduna, Allah na rundunar Isra'ila, wandaka rena.46Yau Yahweh zai ba ni nasara bisanka, zan kumakashe ka in kuma cire kanka daga jikinka. Yau zan miƙɑ gawawakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sammai ga kuma namomin jeji na ƙasa, saboda dukkan duniya ta san cewa akwai Allah a Isra'ila,47kuma dukkan wannan taro su san cewa Yahweh ba ya ba da nasara ta dalilin takobi ko mãshi. Gama yaƙin na Yahweh ne, kuma za ya miƙaka cikin hannunmu."48A lokacin da Bafilisten ya tashi ya kuma taso ga Dauda, sai Dauda ya rugo da sauri zuwa ga rundunar magabcin domin ya gamu da shi.49Dauda yasa hannunsa cikin jaka, ya ɗauko dutse daga ciki, sai ya jefi Bafilisten a tsakiyar goshi, sai ya faɗi a fuskarsa ƙasa.50Dauda ya ci nasara ga Bafilisten da majajjawa da dutse. Ya jefe Bafilisten ya kumakashe shi. Babu takobi cikin hannun Dauda.51Sai Dauda ya sheƙa a guje ya kuma tsaya a bisa Bafilisten ya kuma dauƙe takobinsa, ya zaro ta daga gidanta, yakashe shi, ya datse kansa da ita. A lokacin da Filistiyawa suka ga cewa mutuminsu mai ƙarfi ya mutu, suka gudu.52Sai mazajen Isra'ila da na Yahuda suka tashi da sowa, suka kuma runtumi Filistiyawa har zuwa kwari da ƙofofin Ekron. Matattun Filistiyawa suka kwanta akan hanya zuwa Sharem, hanyar zuwa Gat da Ekron.53Mutanen Isra'ila suka dawo daga runtumar Filistiyawa, suka kuma washe sansaninsu.54Dauda ya ɗauki kan Bafilisten yakawo shi Yerusalem, amma ya ajiye rigar yaƙinsa a tasa rumfar.55Da Saul ya ga Dauda ya fita gãba da Filistiyawa, ya cewa Abna, shugaban runduna, "Abna, yaron wane ne wannan matashin?" Abna ya ce, "Ranka ya daɗe, sarki, ban sani ba."56Sarkin ya ce, "Ka tambayi waɗanda suna iya sani, ɗan wane ne."57Da Dauda ya dawo daga kisan Filistiyawan, Abna ya ɗauke shi, yakawo shi wurin Saul tare dakan Bafilisten a cikin hannunsa.58Saul ya ce masa, "Kai ɗan wane ne, ɗan saurayi?" Dauda ya amsa, "Ni yaron bawanka ne Yesse mutumin Betlehem."
Wannan sunan wuri ne
''Sarkar sakonnin waya'' sulke ce mai sassauƙa wacce aka rufe ta da ma'aunan kariya ko ƙananan faranti. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ya kare kansa ta hanyar sa rigar sarka mai sarkar sarka" ko "ya sa rigar sarkar sarka"
Shekel yanki ne na nauyi da-idai da kusan gram 11. AT: "kimanin kilogram 55"
Wannan karamin mashi ne wanda yake nufin jefawa.
"rike mashin dinsa"
"igiya ta birgima cikin da'ira"
"Batun mashin dinsa" ya auna kimanin kilogram 7 (domin shekel yanki ne na nauyi dai-dai da kusan gram 11).
"Me yasa kuka zo don yaƙi da mu?" Goliyat ya yi amfani da wannan tambayar don ya yi wa Isra’ilawa ba’a. AT: "Ku wawaye ne idan kuna tunanin za ku iya yin yaƙi da mu!"
Goliyat ya yi amfani da wannan tambayar don ya yi wa Isra’ilawa ba’a. Lokacin da ya ce shi Bafiliste ne, yana nuna cewa yana da ƙarfi. AT: "Ni babban Bafiliste ne, kuma ku bayin Saul kawai ne."
"Na kalubalanci sojojin Isra'ila"
Kalmomin ''karaya'' da 'tsoro ƙwarai' ma'anar abu ɗaya ne kuma suna ƙarfafa tsananin tsoronsu.
"Ya" yana nufin Yesse.
Kalmomin guda biyu ma'anar abu guda ɗaya kuma an haɗa su don girmamawa.
Abinadab na biyun, da Shamma na uku an haife shi. Wannan jimlar tana nuna tsarin haihuwa.
"Tsawon kwanaki 40"
"don nuna cewa a shirye yake ya yi yaƙi"
"kyaftin ɗin 'yan'uwanku dubu." Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) kalmar "dubu" tana wakiltar ainihin adadin sojojin da wannan kyaftin din ya jagoranta. 2) kalmar da aka fassara zuwa "dubu" ba ta wakiltar ainihin lambar, amma sunan babban rukunin sojoji ne. AT: "kyaftin ɗin 'yan'uwanku rundunonin soja"
"Binciki ku gano yadda 'yan'uwanku suke lafiya"
"dukkan sojojin Isra'ila"
"sunansa Goliyat"
"sun ja daga gaba daga layin Filistiyawa"
Sojojin suna fadin haka ne don su ja hankalin junan su ga mutumin nan Goliyat. AT: "Duba mutumin nan da ya fito!"
Wannan yana nufin sarkin Isra'ila. AT: "Sarkinmu"
Wannan yana nufin 'yar sarki.
Kalmar "gida" na nufin gida ko iyali. AT: "ba zai ƙara bukatar iyalinsa su biya haraji ba"
Ana iya bayyana wannan tare da kalmar aikatau "wulakanci." AT: "yana hana Isra'ila wulakanta ta" ko "ta hana shi wulakanta Isra'ila"
Dauda ya yi wannan don ya nuna fushinsa ga Bafilisten da yake raina rundunar Allah. AT: "Wannan Bafiliste wanda ba shi da kaciya ba tabbas ba shi da ikon da zai ƙi sojojin Allah na mai rai!"
Wannan jumlar zagi ce kuma tana nuna cewa Goliyat ba na Allah mai rai bane.
Anan ana magana da fushi kamar wuta ce da za a iya hurawa. AT: "Iliyab ya yi fushi da Dauda"
Iliyab ya yi amfani da wannan tambayar don ya nuna yana fushi da dawowar Dauda. Wataƙila yana nuna cewa Dauda ba shi da kyakkyawan dalilin zuwa. AT: "Ba ku da kyakkyawan dalilin zuwa nan"
Iliyab ya yi amfani da wannan tambayar don ya zagi Dauda ta wurin sa aikinsa ya zama ba shi da muhimmanci da kuma zarginsa da rashin kula da tumakin mahaifinsa. AT: "Kawai kuna da alhakin kula da 'yan raguna a cikin jeji. Ba ku iya ko da aiwatar da wannan aikin mai sauki!"
Waɗannan jimlolin guda biyu ma'anar abu guda ɗaya kuma an haɗa su don girmamawa.
David ya yi amfani da waɗannan tambayoyin don bayyana takaicinsa da kuma ba da hujjar kansa. AT: "Ban yi wani laifi ba. Tambaya kawai nake yi!"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Lokacin da sojoji suka ji abin da Dauda ya ce"
Zuciyar da ta kasa wakiltar firgita da rasa amincewa. AT: "Kada ku bari kowa ya firgita" ko "Kada ku bari kowa ya rasa amincewa"
Dauda ya yi magana kansa “bawanka” don girmama Saul. AT: "Ni, bawanku, zan tafi"
Dauda ya yi magana kansa “bawanka” don girmama Saul. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 17:31. AT: "Ni, bawanku, na kasance ina kiwon tumakin mahaifina"
Anan "shi" yana nufin zaki ko damisa. Wasu yare zasuyi amfani da kalmar "ta" maimakon "shi."
Anan "shi" yana nufin rago.
Dauda ya ci gaba da magana da Sarki Saul.
Dauda yana cewa zai iya kashe Bafilisten kamar yadda ya iya kashe zaki da damisa.
Damisa da zakuna suna amfani da ƙafafunsu lokacin da suke kai hari, saboda haka kalmar "gwaiwa" tana wakiltar harin ne. AT: "daga harin zaki da kuma daga harin damisa" ko "daga zaki da damisa"
Hannun Bafilisten yana wakiltar ƙarfinsa a yaƙi. AT: "ikon wannan Bafilisten" ko "Bafilisten"
"Takobin Saul a kan makamai"
Anan "ya" yana nufin Dauda
Majajjawa makami ne na jifa.
"kuma mai ɗaukar masa garkuwa yana tafe a gabansa"
"ya ƙi shi"
Anan kare yana wakiltar karamar dabba wanda mutum zai iya kashewa cikin sauƙi. Kalmar "sandunansu" tana nufin sandar Dauda kuma ta nuna ra'ayin Goliath cewa ba makami mai kyau ba ne. Goliyat ya yi amfani da wannan tambayar don ya zargi Dauda da zaginsa. AT: "Kuna zagina ta hanyar zuwa wurina da sanduna kawai kamar na kare kawai!"
Goliyat ya yi maganar kashe Dauda ya bar jikinsa a ƙasa domin dabbobi su ci shi kamar zai ba da jikin Dauda ga dabbobin. AT: "Zan kashe ku, da tsuntsayen sama da namomin jeji za su cinye jikinku"
Anan “suna” yana wakiltar ikon Allah ko hukuma. AT: "da ikon Yahweh" ko "tare da hukuma Yahweh"
"wanda ka tsokane" ko "wanda ka zagi"
Dauda ya ci gaba da magana da Goliyat.
Dauda yayi magana akan jagorantar Isra’ilawa wajen kashe Filistiyawa da barin gawarwakinsu a ƙasa domin dabbobi su cinye su kamar shi zai ba da gawar ga dabbobin. AT: "Mu Isra'ilawa za mu kashe sojojin Filistiyawa, da tsuntsayen sama da namomin duniya za su ci su"
Kalmar "duniya" tana nufin mutanen da suke duniya. AT: "dukkan mutanen duniya na iya sani"
Takobi da mashi misalai ne na makaman yaƙi. Suna wakiltar hanyoyin yaƙi na mutane. AT: "Nasarar da Yahweh ke bayarwa ba ta dogara da takobi da mashi ba" ko "lokacin da Yahweh ya ba mu nasara, bai dogara da yadda muke yaƙi ba"
An yi magana game da cin nasarar yaƙi a matsayin mallakar yaƙin. AT: "Yahweh yana ci nasara a koyaushe" ko "nasara ta Yahweh ce"
Bada Filistiyawa a hannun Isra’ila yana wakiltar taimaka wa Isra’ilawa su ci Filistiyawa a yaƙi. AT: "zai taimake mu mu ci ku"
Aya ta 50 ta taƙaita ne game da nasarar da Dauda ya yi da Goliyat. Cikakkun bayanai game da yadda ya buge Goliyat ya kashe shi a cikin 1 Sama'ila 17:48 da 17:51. Wasu yarukan basa amfani da bayanan taƙaitawa kamar wannan. A waɗancan yanayi, masu fassara na iya sake fasalin ayoyin kamar yadda suke a cikin UDB.
Dauda yayi hakan ne bayan Goliyat ya faɗi ƙasa a cikin 1 Sama'ila 17:48.
"ya dauki takobin Bafilisten." A nan kalmar "nasa" tana nufin Goliyat.
Ana iya bayyana a sarari cewa Isra'ilawa suna kashe Filistiyawa yayin da suke runtumar su. AT: "Kuma suka kashe Filistiyawa yayin da suke runtumar su, kuma gawarwakin Filistiyawa da suka mutu suna ƙasa a kan hanyar Sha'arayim"
"Isra'ilawa sun washe sansanin Filistiyawa"
"ya sanya kayan yakin Goliyat a cikin rumfansa"
Tattaunawa a cikin 1 Sama'ila 17: 55-56 ya faru ne kafin Dauda ya kashe Goliyat. AT: "Lokacin da Saul ya ga Dauda" ko "Da farko lokacin da Saul ya ga Dauda"
"tafi yaƙi da Bafilisten"
"wanene mahaifin wannan matashin"
"waye baban yaron"
"Wanene mahaifinka"
"Ubana shi ne baranka, Yesse, mutumin Betlehem"
1Bayan da ya gama magana da Saul, sai ran Yonatan ya manne wa ran Dauda, Yonatan kuwa ya ƙaunace shi kamar ransa.2Saul ya ɗauki Dauda zuwa cikin hidimarsa a wannan rana; baya barshi ya koma gidan mahaifinsa ba.3Sai Yonatan da Dauda suka yi alƙawari da juna na abokantaka domin Yonatan ya ƙaunace shi kamar ransa.4Yonatan ya tuɓe rigarsa wadda ya ke yãfe da ita ya kuma ba Dauda tare da rigar yaƙinsa, har da takobinsa, bakansa, da kuma maɗaurinsa.5Dauda ya tafi duk inda Saul ya aike shi, kuma ya ci nasara. Saul ya maida shi kai bisa mazajen yaƙi. Wannan ya ƙayatar a idanun dukkan mutanen da kuma idanun bayin Saul.6Da suka dawo daga hallaka Filistiyawan, matayen suka fito daga dukkan biranen Isra'ila, suna raira waƙa da rawa, su taryi Saul, dakacakaura, da farinciki, da kumakayan kiɗe-kiɗe.7Matayen suka riƙa yin waƙa da juna sa'ad da suke kaɗawa. Suka raira: "Saul yakashe dubbansa, Dauda kuma dubbansa goma."8Saul ya ji haushi ƙwarai, kuma wannan waƙa ta baƙanta masa rai. Ya ce, "Sun ba Dauda dubbai goma, amma ni sun ba ni dubbai kawai. To mene ne ya rage masa idan ba mulkin ba?"9Saul kuwa daga wannan rana ya fara yi wa Daudakallon rashin yarda.10washegari wani mugun ruhu daga wurin Allah ya saukar wa Saul ya kuma yi hauka cikin gidan. Sai Dauda yakaɗa garayarsa, kamar yadda ya saba kowacce rana. Saul yana ɗauke da mashi cikin hannunsa.11Saul ya jefa mashin, gama ya yi tunani, "Zan tsire Dauda ga bango." Amma Dauda ya tsira daga gaban Saul sau biyu kamar haka.12Saul ya ji tsoron Dauda, gama Yahweh na tare da shi, amma baya kuma tare da Saul.13Sai Saul ya fitar da shi daga gabansa ya kuma maishe shi shugaban dubu. Da haka Dauda ya dinga fita yana shigowa a fuskar mutanen.14Dauda ya yi nasara a dukkan hanyoyinsa, gama Yahweh na tare da shi.15Da Saul ya ga yana ci gaba, sai ya ji tsoronsa.16Amma dukkan Isra'ila da Yahuda suka ƙaunaci Dauda, gama yana fita yana shigowa a idanunsu.17Sai Saul ya cewa Dauda, "Ga babbar ɗiyata Merab. Zan baka ita ta zama matarka. Sai dai ka yi mazakutta dominaka kuma yi yaƙin Yahweh." Gama Saul ya yi tunani, "Kada hannuna ya tayar masa, amma bari hannun Filistiyawa ya sauka bisansa."18Dauda ya cewa Saul, "Ni wane ne, kuma su wane ne 'yan uwana, ko gidan mahaifina cikin Isra'ila, da zan zama suruki ga sarki?"19Amma a lokacin da Merab, ɗiyar Saul, yakamata a bada ita ga Dauda, sai aka bada ita ga Adriyel mutumin Meholat ta zama matarsa.20Amma Mikal, ɗiyar Saul, ta ƙaunaci Dauda. Suka gaya wa Saul, wannan kuma ya yiwa Saul daɗi.21Sai Saul ya ce a zuciyarsa, "Zan ba da ita gare shi, domin ta zama tarko a gare shi, kuma hannun Filistiyawa ya yi gãba da shi." Saboda haka Saul ya cewa Daudakaro na biyu, "Zaka zama surukina."22Saul ya umarce bayinsa, "Ku yi magana da Dauda a asirce, ku ce, 'Duba, sarki yana jin daɗinka, kuma dukkan bayinsa suna ƙaunar ka. To yanzu, ka zama surukin sarki."'23Saboda haka bayin Saul suka furta waɗannan maganganu ga Dauda. Sai Dauda ya ce, "Ko ƙaramin abu ne gare ku zaman surukin sarki, ganin cewar ni talaka ne, kuma ba sananne ba?"24Bayin Dauda suka mayar wa Saul da maganganun da Dauda ya faɗa.25Sai Saul ya ce, "Ku faɗi wannan ga Dauda, 'Sarki ba ya buƙatar wani sadãki, sai dai fatar loɓar Filistiyawa ɗari daya, da za a rama daga maƙiyan sarki."' Yanzu Saul ya yi tunani dai yasa Dauda ya mutu ta hannun Filistiyawa.26Da bayinsa suka gaya wa Dauda waɗannan maganganu, sai ya yiwa Dauda dai-dai ya zama surukin sarki.27Kafin waɗanan kwanaki su wuce, Dauda ya tafi tare da mazajensa ya kumakashe Filistiyawa ɗari biyu. Dauda ya dawo da fatar loɓarsu, sai aka miƙa su cikakku ga sarki, domin ya zama surukin sarki. Sai Saul ya ba Dauda Mikal ɗiyarsa ta zama matarsa.28Da Saul ya gani, ya kuma sasance da cewa Yahweh na tare da Dauda, kuma Mikal, ɗiyar Saul, ta ƙaunace shi,29Saul ya ƙara jin tsoron Dauda. Saul ya ci gaba da zama magabcin Dauda.30Sai sarakunan Filistiyawa suka fito domin yaƙi, kamar dai yadda suke fitowa, hakannan Dauda ya ke nasara fiye da dukkan bayin Saul, har sunansa ya zama abin girmamawa.
Ana magana akan abota ta kusanci kamar tana ɗaure rayukan mutane biyu. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yonatan ya ƙaunaci Dauda sosai" ko "Yonatan ya miƙa kansa ga Dauda"
Anan "ƙaunatacce" yana nufin soyayya tsakanin abokai, ba soyayya ta soyayya ba. Kalmar nan “kurwa” tana wakiltar mutum ko rayuwar mutumin. AT: "Yonatan ya ƙaunaci Dauda kamar yadda ya ƙaunaci kansa" ko "Yonatan ya ƙaunaci Dauda kamar yadda yake ƙaunar ransa"
Anan "ƙaunatacce" yana nufin soyayya tsakanin abokai, ba soyayya ta soyayya ba. Kalmar nan “kurwa” tana wakiltar mutum ko rayuwar mutumin. AT: "Yonatan ya ƙaunaci Dauda kamar yadda ya ƙaunaci kansa" ko "Yonatan ya ƙaunaci Dauda kamar yadda yake ƙaunar ransa"
"ya wadata"
Kalmomin "a idanun" da "a wurin" ma'anarsu ɗaya. Ra'ayin mutane ana magana ne a matsayin wani abu da suke ɗauka a matsayin mai kyau ko mara kyau. AT: "Wannan abin farin ciki ne a cikin ra'ayoyin dukan mutane da na barorin Saul" ko "Wannan ya faranta zuciyar dukan mutane da kuma barorin Saul"
Wannan bayani ne na gaba daya wanda yake jaddada yawan matan da suka zo daga garuruwa da yawa. AT: "daga yawancin biranen ko'ina cikin Isra'ila"
"da farin cikin kada tambura da sauran kayan kida"
Ana iya samar da kalmar daga layin da ya gabata. AT: "Dauda ya kashe dubun dubunsa"
"Sun yaba"
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Abin da kawai ya rage masa ya samu shi ne sarauta."
A nan "ruhun cutarwa" na iya nufin ko dai "ruhun da ke haifar da matsala" ko "wani mugun ruhu." Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 16:14.
"ya yi hauka"
"Yahweh yana tare da Dauda"
"Saul kuwa ya kawar da Dauda daga gabansa"
Anan "mutanen" yana nufin sojoji a ƙarƙashin umarnin Dauda. Kalmomin "sun fita" da "sun shigo" kalmomin magana ne da ke nuni da jagorantar mutane zuwa yaƙi da jagorantar su gida daga yaƙi. AT: "Dauda ya jagoranci sojojinsa zuwa yaƙi kuma ya jagorance su zuwa gida daga yaƙi"
Anan "tsaya cikin tsoro" karin magana ne wanda ke nufin tsoro. AT: "ya ji tsoron Dauda"
Anan "Isra'ila da Yahuda" suna wakiltar mutanen dukkan kabilun. AT: "duk mutanen Isra'ila da na Yahuda sun ƙaunaci Dauda"
Ana magana da cutar da wani kamar sanya hannun mutum a kan mutumin. Anan, Saul yana nufin kashe Dauda. AT: "Ba zan kasance wanda zan kashe shi ba; zan bar Filistiyawa su kashe shi"
Dauda ya yi amfani da wannan tambaya ta zance don ya nanata cewa bai cancanci zama surukin Saul ba. AT: "Ni ba kowa bane kuma dangi ko dangin mahaifina basu da mahimmanci a Isra'ila ... ga sarki."
"mijin 'yar sarki"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da ya kamata Saul ya bai wa Dauda 'yarsa Merab"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Saul ya ba ta Adriyel"
Anan "ƙaunatacce" yana nufin tana da sha'awar soyayya ga Dauda.
Anan "su" suna nufin mutanen da suka gano game da yadda Mikal take ji, ba David da Mikal ba.
"Zaka zama mijin 'yata"
"dukkan bayinsa suna sha'awar ka"
Dauda ya yi wannan tambayar don jaddada cewa bai cancanci zama surukin sarki ba. AT: "Babban al'amari ne kasancewa surukin sarki, kuma ni talaka ne kuma bashi da mahimmanci game da hakan."
Ana iya samar da fi'ili don kalma ta biyu daga na farkon. AT "Sarki ba ya son komai don amarya; yana so ne kawai ku kawo masa kaciyar 100"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "don ɗaukar fansa akan magabtan sarki"
Anan “faɗuwa” na nufin mutuwa. Jumlar "da hannu" kalma ce da ke gaya mana hanyoyin da wani abu zai faru, a wannan yanayin, Filistiyawa za su kashe Dauda. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "a sa Filistiyawa su kashe Dauda"
"Dauda da mutanensa sun ba sarki waɗannan dukka"
nan kalmomin "gani" da "sani" suna raba ma'anoni iri ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa Saul ya sani da tabbaci. AT: "Saul ya gane"
Anan “suna” magana ne na Dauda. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "don mutane su girmama David ƙwarai"
1Saul ya cewa Yonatan ɗansa da kuma dukkan bayinsa cewa su kashe Dauda. Amma Yonatan, ɗan Saul, ya yi fahariya da Dauda.2Saboda haka Yonatan ya gaya wa Dauda, "Saul mahaifina na neman yakashe ka. Saboda hakaka yi zaman tsaro da safe ka kuma ɓoye kanka a boyayyen wuri.3Zan fita in tsaya kusa da mahaifina cikin fili a indakake, zan kuma yi magana da mahaifina game dakai. Idan na ji wani abu akanka, zan gaya maka."4Yonatan ya yi maganar alheri game da Dauda ga Saul mahaifinsa ya kuma ce masa, "Bari kada sarki ya yi laifi ga bawansa Dauda. Gama ba ya yi maka laifi ba, kuma ayyukansa masu kyau sun kawo maka alheri.5Gama ya ɗauki ransa cikin hannunsa ya kumakashe Bafilisten. Yahweh yakawo babbar nasara ga dukkan Isra'ila. Ka gani ka kuma yi murna. Donme zaka yi zunubi ga jinin marar laifi da zakakashe Dauda babu dalili?"6Saul ya saurari Yonatan. Saul ya rantse, "Har ga Allah, ba zai kashe shi ba."7Sai Yonatan ya kira Dauda, sai kuma Yonatan ya gaya masa dukkan waɗannan abubuwan. Yonatan kuma yakawo Dauda wurin Saul, yana kuma tsayawa a gabansakamar dã.8Sai aka sake yin yaƙi, Dauda kuma ya fita ya yi faɗa da Filistiyawa ya kuma ci nasara da su da babbar hallaka. Suka gudu daga fuskarsa.9Wani mugun ruhu daga wurin Yahweh ya saukar wa Saul da ya ke zaune a gidansa da mashinsa cikin hannunsa, kuma yayin da Dauda ke kaɗakayan kiɗinsa.10Saul ya yi koƙarin tsire Dauda har ga bango da mashinsa, amma ya tsere daga gaban Saul, har Saul yakafe mashin cikin bangon. Dauda ya gudu ya tsere a wannan dare.11Saul ya aika da manzanni zuwa gidan Dauda su kula da shi domin yakashe shi da safe. Mikal, matar Dauda, ta ce masa, "Idan baka ceci ranka a wannan daren ba, gobe za akashe ka."12Saboda haka Mikal ta zura Dauda ta tãga. Ya tafi ya gudu, ya tsere.13Mikal ta ɗauki gunkin gida ta ajiye bisa gado. Sai ta sanya matashin kai na gashin akuya akansa, ta kuma rufe shi dakayayyaki.14Da Saul ya aika 'yan saƙo su ɗauko Dauda, ta ce, "Yana barci."15Sai Saul ya aika 'yan saƙo su ga Dauda; ya ce, "Ku kawo mani shi akan gadon, domin in kashe shi."16A lokacin da 'yan saƙon suka shigo ciki, gashi, gunkin gida na bisakan gado bisa matashin kai mai gashi na ɗan rago a bisakansa.17Saul ya cewa Mikal, "Donme ki ka ruɗe ni har ki ka bar makiyina ya tafi, har ya tsira?" Mikal ta amsa wa Saul, "Ya ce mani, 'Bar ni in tafi. Donme zan kashe ka?"18Yanzu Dauda ya gudu ya kuma tsira, ya tafi wurin Sama'ila a Rama ya kuma gaya masa dukkan abin da Saul ya yi masa. Sa'annan shi da Sama'ila suka tafi suka zauna a Nayot.19Aka gaya wa Saul, cewa, "Duba, Dauda na Nayot cikin Rama."20Sai Saul ya aika da 'yan saƙo su kamo Dauda. Da suka ga taron annabawa na annabci, Sama'ila kuma na tsaye a matsayin shugabansu, sai Ruhun Allah ya sauko bisa 'yan saƙon Saul, sai su ma suka yi annabci.21Da aka gaya wa Saul wannan, sai ya aika da wasu 'yan saƙon, sai suma suka yi anabci. Sai Saul ya sake aikawa da wasu 'yan saƙo kãro na uku, sai suma suka yi anabci.22Sai shi ma ya tafi Rama ya zo wurin rijiya mai zurfi da ke a Seku. Ya yi tambaya, "Ina Sama'ila da Dauda?" Wani ya ce, "Duba, suna a Natot cikin Rama."23Saul ya tafi Nayot a Rama. Sai Ruhun Allah ya sauko bisansa, yayin da ya ke tafiya ya yi ta anabci har ya iso Nayot a Rama.24Ya tuɓe rigunansa ya kuma yi anabci a gaban Sama'ila. Ya kwanta tsirara dukkan rana da dukkan dare. Shi yasa suke tambaya, "Wai Saul na ɗaya daga cikin annabawa ne?"
Yonatan ya ji daɗin kasancewa tare da Dauda sosai.
Yonatan yana magana kamar dai Saul wani mutum ne don ya nuna wa Saul cewa Yonatan yana daraja Saul. AT: "Kada ku yi zunubi ga bawanku"
Anan "rayuwa a hannunsa" wani karin magana ne da ke nuni da kasada da ransa. AT: "ya jefa rayuwarsa cikin haɗari"
Yonatan ya yi wannan tambayar don ya tsauta wa Saul. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Kada ku yi zunubi akan jinin marar laifi kuma ku kashe Dauda ba tare da dalili ba."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba zan kashe shi ba" ko "Ba zan kashe shi ba" ko "tabbas zan rayar da shi"
Dauda yana tare da Saul.
A nan "ruhun cutarwa" na iya nufin ko dai "ruhun da ke haifar da matsala" ko "wani mugun ruhu." Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 16:14.
jefar da mashinsa don ya ratsa ta cikin Dauda da bango
Mikal ta gaya wa Dauda
Anan "ceton ranka" karin magana ne wanda yake nufin tserewa. AT: "Idan baku kubuta ba"
Mikal ta taimaka wa Dauda ya tsere wa Sarki Saul. Tana amfani da gunkin gida don yin gadon Dauda kamar yana kwana a ciki.
Zai yiwu ma'anonin su 1) kan gunkin yana kwance kan matashin gashin akuya kuma Mikal ta sanya gunkin a cikin kayan Dauda ko 2) Mikal ta yi amfani da tufafin Dauda a matsayin bargo don ta rufe gunkin gaba ɗaya kuma ta yi "matashin kai" na akuyar gashi yayi kamar gashin Dauda wanda ya fito daga ƙarƙashin bargon tufafi.
Saul ya aikata abin da yake so ya kashe Dauda.
Dalilin da ya sa mutanen suka zaci Dauda yana cikin gado ana iya bayyanawa a sarari. AT: "Idan da gaske ba shi da lafiya da zai zo wurina, ku kawo mini gado tare da shi a ciki"
Zai yiwu ma'anonin su ne 1) Saul yana son sanin dalilin da yasa Mikal ta aikata abin da ta yi ko 2) Saul ya yi amfani da wannan tambayar don tsawata wa Mikal. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Bai kamata ka yaudare ni ba ka bar maƙiyina ya tafi, don haka ya tsere."
Ko da yake Dauda bai faɗi haka ba da gaske, Mikal ta gaya wa Saul cewa Dauda ya yi mata barazanar wannan tambayar. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Zan kashe ku idan ba ku taimake ni in tsere ba."
Dauda ya gudu zuwa wurin Sama'ila.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Wani ya gaya wa Saul"
Anan “kai” na nufin matsayi na iko. AT: "yin aiki a matsayin shugabansu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Lokacin da wani ya gaya wa Saul wannan"
Waɗannan sune sunayen wurare ne.
Wannan ya zama misali a tsakanin Isra'ilawa. Da alama mutane sun faɗi hakan ne don nuna mamakin lokacin da mutum ba zato ya yi abin da ba a taɓa yi ba. Ana iya bayyana ma'anar tambayar a bayyane. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Samuila 10:11. AT: "Wannan shine dalilin da ya sa idan mutane suka ga wani yana aikata wani abu wanda ba a zata ba, sai su ce, 'Shin Saul ma annabi ne?'"
1Sai Dauda ya gudu daga Nayot a Rama ya kuma zo ya cewa Yonatan, "Me na yi? Mene ne laifina? Mene ne zunubina ga mahaifinka, da ya ke neman ɗaukan raina?"2Yonatan ya cewa Dauda, "Sam ba haka ba ne; ba zaka mutu ba. mahaifina ba ya yin wani abu mai girma ko ƙanƙani ba tare da ya gaya mani ba. Donme mahaifina zai ɓoye mani wannan abu daga gare ni? Ba haka ba ne."3Duk da haka Dauda ya sake rantsuwa kuma ce, "Mahaifinka ya san da cewar na sami tagomashi a idanunka. Dama ya ce, 'Kada a bari Yonatan ya san wannan, don kada ya damu.' Amma tabbas tun da Yahweh na raye, kumakamar yaddakaimaka ke rayuwa, rãtakaɗan ne tsakani na da mutuwa."4Sai Yonatan ya cewa Dauda, "Duk abin daka ce, zan yi maka."5Dauda ya cewa Yonatan, "Gobe ne sabon wata, kuma yakamata in zauna wurin cin abinci da sarki. Ammaka bar ni in tafi, domin in ɓoye kaina cikin saura har kwana na uku da yamma.6Idan mahaifinka ya damu game da ni sarai, sai kace, 'Dauda ya nemi izini daga wajena domin ya tafi Betlehem birninsa. Domin lokacin hadaya ta shekara ce ga dukkan dangin.'7Idan ya ce, 'lafiya lau,' bawanka zai sami salama. Amma idan ya husata ƙwarai, to ka sani ya ƙudurci aikata mugunta.8Saboda hakaka kyauta wa bawanka. Gamaka jawo bawanka cikin alƙawari na Yahweh tare dakai. Amma idan akwai zunubi cikina, kakashe ni dakanka; gama mene ne dalilin da zai saka kawo ni ga mahaifinka?"9Yonatan ya ce, "Sam haka ba zai yiwu ba! Idan na gane mahaifina yana da niyyar cutar dakai, ba zan gaya maka ba?"10Sai Dauda ya cewa Yonatan, "wane ne zai gaya mani idan ya zama cewa mahaifinka ya amsa maka da faɗa?"11Yonatan ya cewa Dauda, "Zo, mu tafi cikin saura." Sai suka tafi cikin saura tare su biyu.12Yonatan ya cewa Dauda, "Bari Yahweh, Allah na Isra'ila, ya zama shaida. A lokacin da zan tambayi mahaifina gobe war haka, ko rana ta uku, duba, idan akwai shirin alheri game da Dauda, ba zan aika gare ka in kuma sanar dakai ba?13Idan ya gamshi mahaifina da ya cutar dakai, bari Yahweh ya yi wa Yonatan har fiye kuma idan ban sanar dakai in kuma sallame kaka tafi ba, domin ka tafi cikin salama. Bari Yahweh yakasance tare dakai, kamar yadda ya ke tare da mahaifina.14Idan ina nan da rai, ba zaka nuna mani amintaccen alƙawarin Yahweh ba, domin kada in mutu?15Kadaka datse amintaccen alƙawarinka daga gidana har abada- koda Yahweh ya datse kowanne magabcin Dauda daga fuskar ƙasa.16Saboda haka Yonatan ya yi alƙawari da gidan Dauda ya kuma ce, "Bari Yahweh ya nemi lissafi daga hannun magabtan Dauda."17Yonatan yasa Dauda ya yi rantsuwa kuma domin ƙaunar da ya ke kaunarsa, gama yanakaunarsakamar yadda ya ke kaunar ransa.18Sai Yonatan ya ce masa, "Gobe ne sabon wata. Za a yi kewarka domin mazauninka zai zama babu kowa.19Bayan ka zauna can har kwana uku, sai ka sake komawa can indaka ɓoye kanka a lokacin da al'amuran ke ci gaba, ka tsaya kusa da dutsen Ezel.20Zan harba kibiyoyi uku gefensa, kamar ina auna inda nakeso in harba.21Daga nan zan aika ɗan matashina in kuma ce masa, 'Tafi ka nemo kibiyoyin.' Idan na cewa ɗan yaron, 'Duba, kibiyoyin suna wannan gefenka; nemo su."; sai ka zo; gama akwai kariya dominka kuma ba cutarwa, na rantse da ran Yahweh.22Amma idan na ce wa matashin, 'Duba, kibiyoyin suna can gaba dakai,' sai ka yi tafiyarka, gama Yahweh ya sallame ka.23Amma batun alƙawarin da ni dakai mu ka furta, gama, Yahweh na tsakani na dakai har abada."24Sai Dauda ya ɓoye kansa cikin saura. Lokacin da sabon wata ya fito, sarkin ya zauna domin cin abinci.25Sarkin ya zauna a bisa kujerarsa, yadda ya saba, a bisa kujera ta jikin bango. Yonatan ya tashi, Abna kuma ya zauna ta gefen Saul. Amma kujerar Dauda babu kowa.26Duk da haka Saul baya ce komai ba wannan rana, domin ya yi tunani, "Wani abin ne ya faru da shi. Ba shi da tsarki; tabbas ba shi dai da tsarki."27Amma a rana ta biyu, ranar bayan sabon wata, wurin zaman Dauda babu kowa. Saul ya cewa Yonatan ɗansa, "Me yasa ɗan Yesse bai zo ya ci abinci jiya da yau ba?"28Yonatan ya amsa wa Saul, "Dauda ya nemi izini sosai daga wurina domin ya tafi Betlehem.29Ya ce, 'Na roƙe ka. Gama iyalina na da hadaya a birni, kuma ɗan'uwana ya umarce ni da in kasance. Yanzu, idan na sami tagomashi a idanunka, Na roƙe ka bari in je in ga 'yan'uwana. Saboda wannan dalili yasa bai zo kujerar sarki ba."30Sai haushin Saul ya yi ƙuna bisa Yonatan, ya kuma ce masa, "Kai ɗan lalatacciya, mace mai tayarwa! Ashe ban sani baka zaɓi ɗan gidan Yesse ga kunyarka, ga kuma kunyar tsiraicin mahaifiyarka?31Idan har ɗan Yesse na a raye a ƙasar, ko kai ko mulkinka ba zai kafu ba. To yanzu, ka aika akawo shi gare ni, gama dole ne ya mutu."32Yonatan ya amsa wa mahaifinsa, "Da wane dalili za akashe shi? Me ya yi?"33Sai Saul ya jefa mashinsa don yakashe shi. Sai Yonatan ya gane cewa mahaifinsa ya ƙudurta yakashe Dauda.34Yonatan ya tashi ya bar teburin cikin hasalar fushi baya kuma ci abinci ba a rana ta biyu ga watan, gama yana baƙinciki saboda Dauda, domin mahaifinsa ya wulaƙanta shi.35Da safe, Yonatan ya fita zuwa saura inda suka shirya su haɗu da Dauda, kuma ɗan saurayin na tare da shi.36Ya cewa ɗan saurayin, "Ka yi gudu ka nemi kibiyoyin da na harba." Yayin da ɗan saurayin ya ruga, ya harba wata kibiyar gaba da shi.37Lokacin da ɗan saurayin ya iso inda kibiyar da Yonatan ya harba ta sauka, Yonatan ya kira ɗan saurayin, ya ce, "Ba kibiyar na gabanka ba?"38Sai Yonatan ya kirawo ɗan saurayin, "Yi sauri, hanzarta, kadaka tsaya!" Sai ɗan saurayin Yonatan ya tattara kibiyoyin ya dawo wurin ubangidansa.39Amma ɗan saurayin bai san komai ba. Yonatan da Dauda ne kaɗai suka san zancen.40Yonatan ya ba ɗan saurayin makamansa ya ce masa, "Tafi, kakai su cikin birnin."41Ba da jimawa ba bayan tafiyar ɗan saurayin, Dauda ya fito daga bayan dutsen, ya kwanta fuskarsa ƙasa, ya durƙusa ƙasa har sau uku. Suka yi wa juna sumba da kuka tare, Dauda ya yi kuka sosai.42Yonatan ya cewa Dauda, "Ka tafi cikin salama, gama mu biyu mun rigaya mun rantse da sunan Yahweh muka kuma ce, 'Bari Yahweh yakasance tsakanin kai da ni, kuma tsakanin zuriyata da zuriyarka, har abada."' Sa'an nan Dauda ya tashi tsaye ya tafi, Yonatan kuma ya koma cikin birnin.
Wadannan tambayoyin guda uku suna nufin abu guda. Dauda ya yi amfani da su don ya nanata cewa bai yi wa Saul laifi ba. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Ban yi wani laifi ba. Ban yi wani laifi ba. Ban yi wa mahaifinka laifi ba. Ba shi da dalilin kashe ni."
Anan "karɓi raina" salon magana ne don "kashe ni."
Kalmomin "babba ko ƙarami" sun haɗa da komai a tsakanin. AT: "babu komai"
Yonatan ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa Saul zai gaya masa idan yana shirin kashe Dauda. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Mahaifina ba shi da dalilin ɓoye mini wannan abin!" ko "Idan wannan abin gaskiya ne, mahaifina tabbas zai sanar da ni!"
Anan idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. AT: "Na faranta maka rai" ko "ka dauke ni da kyau"
Anan "mataki tsakanina da mutuwa" karin magana ne wanda yake nuni da kusancin mutuwa. AT: "Na kusan mutuwa"
Dauda ya ce Yonatan zai yi gwaji game da Sarki Saul.
A farkon kowace wata, mutane suna yin biki tare da miƙa hadayu ga Allah.
"har zuwa yammacin jibi"
Dauda ya ci gaba da bayanin gwajin da ya gabatar.
"ya tambaye ni idan zan ba shi izinin barin"
Kalmar "ya" tana nufin Saul.
Dauda ya yi magana kansa kamar dai shi wani mutum ne don ya nuna cewa ya daraja Yonatan. AT: "Ni, bawanku, zan sami zaman lafiya"
Dauda ya ci gaba da magana da Yonatan.
Abin da mutanen biyu suka amince da shi za a iya bayyane su. AT: "Yahweh ya ji ku lokacin da zaka kulla yarjejeniya da ni cewa ni da ku koyaushe za mu zama abokai na gari"
Ana iya fassara wannan tambayari a matsayin sanarwa. AT: "to babu dalilin da zai sa ku kawo ni wurin mahaifinku"
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Lallai zan gaya muku."
"idan mahaifina yana so ya yi muku abubuwa masu kyau"
Yonatan ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa zai gaya wa Dauda idan Saul yana da niyyar cutar da shi. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "to lallai zan aiko zuwa gare ku in sanar da ku"
Wannan karin magana ne. Yonatan yayi amfani da wannan rantsuwa don girmamawa kuma yayi magana kansa kamar shi wani mutum ne. AT: "bari Yahweh ya yi mani duk wata cuta da mahaifina ya yi niyyar yi muku, har ma fiye da haka"
Yonatan ya roƙi Dauda kada ya kashe duka zuriyarsa don sauran su rage.
Yonatan ya yi wannan tambayar ne don ya tabbatar da cewa Dauda zai yi hakan. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "jna roƙon ka a nuna mini amincin Yahweh, don kada in mutu"
Kalmar "gida" na nuna mutanen da ke zaune a gidan. AT: "Iyalin Dauda"
Hannun magani ne na mutum. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Bari Yahweh ya yi amfani da maƙiyan Dauda don hukunta Dauda idan Dauda ya karya wannan alkawarin" ko 2) "Bari Yahweh ya hallaka maƙiyan Dauda."
Anan "ransa" yana nufin kansa. AT: "Yonatan ya ƙaunaci Dauda kamar yadda ya ƙaunaci kansa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mahaifina zai yi kewar ku"
Anan "kasuwanci yana cikin hannu" wani karin magana ne wanda yake nuni zuwa lokacin da komai ya faru. AT: "lokacin da komai ya faru"
"Ezel" sunan wani dutse. AT: "dutsen da mutane ke kira Ezel"
Yonatan ya ci gaba da magana da Dauda.
nan kalmar "shi" tana nufin dutsen da Dauda zai ɓoye ta.
Waɗannan suna nufin mutum ɗaya.
"to kai, Dauda, zo"
Yonatan ya ci gaba da magana da Dauda.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Yahweh mashaidi ne a tsakanina da ku" ko "Yahweh zai kalli yadda muke ɗaukan juna" ko 2) "Bari Yahweh ya zama shaida a tsakanina da ku" ko "Bari Yahweh ya kalli yadda muke mu bi da juna "
Wasu tsofaffin kofe sun "Yonatan ya zauna kusa da shi."
A dokar Musa, mutumin da ba shi da tsarki a al'adance ba zai halarci bikin ba har sai firist ɗin ya bayyana cewa ya tsarkaka. Saul ya maimaita wannan magana kamar yana ƙoƙarin shawo kansa.
"ya ce in ba shi izinin tafiya"
Anan idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 20: 3. AT: "Na faranta maka rai" ko "kun yarda da ni da kyau"
Yonathan ya yi magana game da Saul kamar dai shi wani mutum ne don ya nuna cewa yana daraja Saul. AT: "teburinku"
Anan "fushin ya ƙone" magana ne da ke nufin yin fushi ƙwarai. AT: "Saul ya yi fushi ƙwarai da Yonatan"
Wannan karin magana ne. Saul ya yi amfani da wannan kalmar a matsayin tsautawa mai tsanani ga Yonatan da kuma damuwarsa ga Dauda. AT: "Kai wawan ɗan karuwanci" ko "Kai wawa maciyi"
Saul ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa ya san cewa Yonatan da Dauda abokai ne. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Na san kun zaɓi ɗan Yesse ... tsiraicin uwa."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba za ku zama sarki ba kuma ba za ku kafa mulkinku ba"
Yonatan yana ƙoƙari ya sa Saul ya yi tunani sosai game da abin da yake yi. Ana iya fassara wannan azaman bayani, kuma kalmomin "idan za a kashe shi" ana iya fassara su cikin aiki. AT: "Ba ku da kyakkyawan dalili don kashe shi. Bai yi wani laifi ba." ko "Ba ku da cikakken dalilin kashe shi. Bai yi laifi ba."
Wannan "na biyu" lamba ce wacce take nufin biyu. AT: "rana ta biyu ta bikin sabon wata"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ya yi bakin ciki game da Dauda"
A nan "shi" yana nufin Dauda.
A nan "shi" yana nufin Yonatan.
"Yonatan ya harba kibiya sama da saurayin"
Yonatan ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa kibiyar ta fi gaban saurayin nisa. Za a iya fassara tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ya kamata ku sani cewa kibiyar ta wuce ku." ko "Kibiyar ta fi karfinka."
"ya kira saurayin, wanda yake guje masa," "yi sauri"
Dauda ya rusuna wa Yonatan, wanda har ila shi ɗan Sarki ne, wanda ya cancanci a girmama shi. Hakanan, wannan shi ne karo na ƙarshe da Dauda ya sadu da Yonatan.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Yahweh mashaidi ne a tsakanina da ku" ko "Yahweh zai kalli yadda muke ɗaukan juna" ko 2) "Bari Yahweh ya zama shaida a tsakanina da ku" ko "Bari Yahweh ya kalli yadda ku bi da juna." Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 20:22.
1Sa'an nan Dauda ya zo Nob domin ya ga Ahimelek babban firist. Ahimelek yazo domin ya taryi Dauda jikinsa na rawa ya kuma ce masa, "Donme kake kai kaɗai kuma babu wani tare dakai?"2Dauda ya cewa Ahimelek babban firist, "Sarki ya aike ni wata hidima ya kuma ce da ni, 'Kada kowa yasan komai game da abin nan da na aike ka, da kuma abin da na umarce ka.' Na aike 'yan matasan wani wurin.3Yanzu dai me kake da shi a hannu? Ba ni 'yar gurasa guda biyar, ko duk abin da ke samuwa."4Firist ya amsa wa Dauda ya kuma ce, "Babu gurasa da ba a tsarkake ba, amma akwai gurasa mai tsarki- Idan 'yan samarin sun keɓe kansu daga mata."5Dauda ya amsa wa firist, "Tabbas mata sun yi nisa da mu tun kwana uku da suka wuce, kamar yadda ya ke idan na fita. Abin da ke na mazajen an keɓe su har ma game da ɗan ƙanƙanin hidimomi. Balle irin wannan na yau lalle duk abin da suke da shi za a keɓe!"6Saboda haka sai firist ya ba shi gurasa da aka keɓe. Gama babu wata gurasa a wurin sai dai gurasar bagadi, wadda aka cire daga wurin Yahweh, domin ya sanya gurasa mai zafi a wurinta a ranar da aka ɗauke ta.7Yanzu dai ɗaya daga cikin bayin Saul yana nan a wannan rana, tsararre a gaban Yahweh. Sunansa Doweg mutumin Idom, shugaban makiyayan Saul.8Dauda ya cewa Ahimelek, "Yanzu babu wani mashi ko takobi? Domin ban kawo takobi ko makamaina tare da ni ba, domin hidimar sarki na buƙatar hanzari."9Firist ya ce, "takobin Goliyat Bafiliste, wandaka kashe a cikin kwarin Ila, tana nan nannaɗe cikin kaya a bayan falmara. Idan kana so ka ɗauki wannan, ka ɗauke ta, gama babu wani makami a nan." Dauda ya ce, "Babu wata takobi irin wannan; ba ni ita."10Dauda ya tashi ya gudu daga wurin Saul a wannan rana ya kuma tafi wurin Akish, sarkin Gat.11Bayin Akish suka ce masa, "Ba wannan ba ne Dauda, sarkin ƙasar? Ba sun yi waƙa da rawa ga juna dominsa ba, 'Saul yakashe nasa dubbai, Dauda kuma yakashe nasa dubbai goma?"12Dauda ya ajiye waɗannan maganganu cikin zuciyarsa yana kuma jin tsoran Akish, sarkin Gat.13Sai ya canza yanayinsa ya yi kamar marar hankali cikin hannuwansu; sai ya yi alamomi a bisa ƙofofin kyamaren ya kuma bar yawu na zubowa ƙasa zuwa gemunsa.14Sai Akish ya cewa bayinsa, "Duba, ku ga mutumin na hauka. Donme kukakawo shi wurina?15Ko na rasa mahaukatan mutane ne, har da zaku kawo mani wannan talikin yana yin wannan hali a gabana? Anya wannan taliki zai shigo cikin gidana?"
Wannan sunan wani wuri ne.
"Na gaya wa samarin su tafi wani wuri, kuma zan gana da su can daga baya"
Dauda yana fara sabon bangare na tattaunawar.
Anan "a hannu" yana ma'ana "akwai." AT: "Wane abinci kuke da shi da za ku ba ni?"
gurasar da firistoci ba su yi amfani da ita ba wajen bauta
Ana iya fassara wannan azaman cikakkiyar jimla. AT: "Mazajenku na iya cin shi idan ba su kwana da mata ba da jimawa ba"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "mun kiyaye kanmu daga mata"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Mazajen sun ware abin da yake nasu"
Wannan magana ce, ba tambaya ba. Ana iya fassara shi cikin tsari mai aiki. AT: "Gaskiya ne a yau za su keɓe abin da suke da shi"
Kuna iya buƙatar faɗi a sarari cewa Doweg ya ga abin da Dauda ya yi. AT: "Doweg ... makiyaya, kuma ya ga abin da Ahimelech ya yi"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Doweg yana da wasu ayyukan addini game da Yahweh don yin can. Madadin fassara: "don wani aiki a gaban Yahweh" ko 2) Yahweh ya tsare Doweg a can. AT: "saboda Yahweh ya tsare shi a can"
Anan "a hannu" yana da ma'ana "akwai." Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 21: 3. AT: "Shin kuna da mashi ko takobi da za ku iya ba ni?"
Wannan shine sunan wani wuri a cikin Isra’ila.
Suna iya yin karin magana lokacin da suka ce Dauda shine sarkin ƙasar. Sun yi amfani da wannan tambayar don nuna cewa Dauda babban maƙiyi ne kuma Akish bai kamata ya bar shi ya zauna a wurin ba. AT: "Kun san wannan David ne, wanda yake da haɗari kamar sarkin ƙasar"
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Kun san cewa lokacin da mutanen ƙasar ke rawa, suna waƙa ga juna game da shi, 'Saul ... dubbai goma?'
Anan "an ɗauka ... a zuciya" yana nufin don yin tunani sosai game da abin da aka faɗi. AT: "Dauda ya yi tunani sosai game da abin da bayin suka ce"
Anan "hannaye" sune magana ga mutum. AT: "a gabansu"
Zai yiwu ma'anonin su ne 1) Akish ya nemi bayinsa su bayyana dalilin da ya sa suka kawo Dauda gare shi ko 2) Akish yana tsawata musu da tambaya. AT: "Ya kamata ku san ba ku kawo mini shi ba."
Wannan tambayar tsawatarwa ce. AT: "Akwai wadatattun mahaukata a nan waɗanda ke ɓata lokacina. Bai kamata ku kawo wannan mutumin don ya yi kamar na a gabana ba."
1Sai Dauda ya bar can ya kuma tsere zuwa ƙogon Adullam. A lokacin da 'yan'uwansa da dukkan gidan mahaifinsa suka ji haka, sai suka gangara zuwa wurinsa.2Duk wanda ke cikin ƙunci, da duk wanda ke cikin bãshi, da kuma marar jin daɗi-dukkansu suka taru wurinsa. Dauda ya zama shugabansu. An sami mazaje kamar ɗari huɗu tare da shi.3Sai Dauda ya bar wurin zuwa Mizfa cikin Mowab. Ya cewa sarkin Mowab, "Na roƙe kaka bar mahaifina da mahaifiyata su zauna dakai har sai na san abin da Allah zai yi mani."4Sai ya bar su tare da sarkin Mowab. Mahaifinsa da mahaifiyarsa suka zauna tare da shi dukkan kwanakin da Dauda ke cikin sansaninsa.5Sai annabi Gad ya cewa Dauda, "Kadaka tsaya a sansaninka. Tashi ka kuma shiga cikin ƙasar Yahuda." Sai Dauda ya bar wurin ya kuma tafi cikin jejin Heret.6Saul ya ji cewa an ga Dauda, tare da mutanen da ke tare da shi. A yanzu dai Saul yana a Gibiya ƙarƙashin itaciyar tamarisk a Rama, da mashinsa a hannu, kuma dukkan bayinsa na tsaye zagaye da shi.7Saul ya cewa bayinsa da ke tsaye zagaye da shi, "Ku saurara yanzu, mutanen Benyamin! Ko ɗan Yesse zai ba kowannenku filayen zaitun ne? Zai maida ku dukka shugabannin dubbai da shugabannin ɗari,8domin misanyar dukkan ku don tayar mani? Babu wani daga cikin ku da ya gaya mani lokacin da ɗa na ya yi alƙawari da ɗan Yesse. Babu waninku da ya ji tausayi na. Babu waninku da ya gaya mani cewar ɗana ya zuga bawana Dauda gãba da ni. Yau ya ɓoye yana jirana domin su kai mani farmaki."9Sai Doweg mutumin Idom, wanda ya tsaya kusa da bayin Saul, ya amsa, "Na ga ɗan Yesse ya iso Nob, wurin Ahimelek ɗan Ahitub.10Ya yi addu'a ga Yahweh don ya taimake shi, kuma ya bashi guziri da kuma takobin Goliyat Bafiliste."11Sai sarki ya aiki wani domin yakawo Ahimelek Firist ɗan Ahitub da dukkan gidan mahaifinsa, su firistocin da ke a Nob. Dukkansu suka zo wurin sarkin.12Saul ya ce, "Saurara yanzu, ɗan Ahitub." Ya amsa, "Ga ni nan, ubangidana."13Saul ya ce masa, "Donme ka yi mani makirci, kai da ɗan gidan Yesse, har ka ba shi gurasa, da takobi, ka kuma yi addu'a ga Allah domin ya taimake shi, domin ya tayar mani, ya ɓoye a asirce, kamar yadda ya ke yi a yau?"14Sai Ahimelek ya amsa wa sarki ya kuma ce, "Wane ne cikin dukkan bayinka da ke amintacce kamar Dauda, wanda ya ke surukin sarki kuma shugaba bisa 'yan tsaro, kuma ana girmama shi cikin gidanka?15Yau ne na fara yi masa addu'a Allah ya taimake shi? Nesa da ni! Kada sarki ya sanya wa bawansa wani laifi ko ga dukkan gidan mahaifina. Gama bawanka bai san komai ba game da wannan batu."16Sarki ya amsa, "Dole ka mutu, Ahimelek, kai da gidan mahaifinka."17Sarki ya cewa mai tsaron da ke tsaye kusa da shi, "Ka juyaka kashe firistocin Yahweh. Domin hannunsu na tare da Dauda, kuma domin sun san ya gudu, amma ba su gaya mani ba." Amma bayin sarkin ba su iya ɗibiya hannunsu su kashe firistocin Yahweh ba.18Sa'an nan ya cewa Doweg, "Juyaka kashe firistocin." Sai Doweg Ba-Idome ya juya ya fãɗawa firistocin; yakashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke yafe da falmarar linin a wannan rana.19Dakaifin takobi, ya abkawa Nob, birnin firistocin, mazaje da mataye, yara da jarirai, kuma bijimai da jakai da tumakai yakashe su dukka dakaifin takobi.20Amma ɗaya daga cikin 'ya'yan Ahimelek ɗan Ahitub, mai suna Abiyata, ya tsere ya gudu zuwa wurin Dauda.21Abiyata ya gaya wa Dauda cewar Saul yakashe firistocin Yahweh.22Dauda ya cewa Abiyata, "Na sani a wannan ranar, da Doweg Ba-Idome ke wajen, zai faɗa wa Saul. Ni ke da laifi domin mutuwar kowanne a cikin iyalin mahaifinka!23Ka zauna tare da ni kumakadaka ji tsoro. Gama wanda ya ke neman ranka shi ke neman nawa kuma. Zaka zauna lafiya tare da ni."
Wannan sunan wani gari ne kusa da Gath.
Wannan ƙari magana ne. AT: "Mutane da yawa da suke cikin damuwa ... mutane da yawa da ba sa farin ciki"
"Dauda kuwa ya tashi daga kogon Adullam,
Dauda ya so iyayensa su zauna tare da Sarkin Mowab don kada Sarki Saul ya cutar da su. Masu fassara na iya bayyana ma'anar sa ta asali ta amfani da ra'ayoyin "zo ku zauna tare," "ku zauna tare da ku," ko "zama a nan tare da ku," kamar yadda a cikin UDB.
"tafi ƙasar ka ta ƙasar Yahuda"
Wannan sunan wuri ne.
Saul ya fi son Dauda, don haka marubucin ya ambaci sauran mutanen dabam. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "wani ya gano inda Dauda da duk mutanen da suke tare da shi suka ɓoye"
Wannan nau'in itace ne. AT: "babban itacen inuwa"
Saul ya yi amfani da wata tambaya don ya nanata cewa Dauda, wanda ya fito daga ƙabilar Yahuda, ba ya son yin wannan ga mutanen ƙabilar Benyamin. AT: "ɗan Yesse ba zai ba ku gonaki ko gonakin inabi ba."
Saul ya yi amfani da wata tambaya don ya nanata cewa Dauda, wanda ya fito daga ƙabilar Yahuda, ba ya son yin wannan ga mutanen ƙabilar Benyamin. AT: "Ba zai sanya ku shugabannin hamsin da na ɗari ɗari" (Duba: rquestion)
Wannan sunan mutum ne. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 21: 7.
Ahimelek ya yi addu'a ga Yahweh domin ya taimake shi, Ahitub kuwa ya ba Dauda.
"ta hanyar bayarwa"
"tawaye" ko "fada"
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Babu wani daga cikin barorinku da yake da aminci kamar Dauda ... gida."
Kalmar "gida" magana ne ga dangin da ke zaune a gidan. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda danginku ke girmamawa"
Ahimelek ya yi wa kansa wannan tambaya kafin Saul ya yi tambaya, sannan nan da nan ya ba da amsar. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Wannan ba shi ne karo na farko da na roki Allah ya taimaki Dauda ba."
Wannan karin magana yana nufin "Tabbas ba haka bane!"
Ahimelek ya yi magana kansa a cikin mutum na uku a matsayin "bawa". Ahimelek kuma ya kira Saul a cikin mutum na uku "sarki." Ahimelek ya yi wannan magana don girmama Saul. AT: Ina roƙon Sarki Saul, kada ku ɗauka ni, bawanku, ko kowa a gidan mahaifina da laifi. Gama ban san komai ba"
Kalmar "gida" magana ne ga dangin da ke zaune a gidan. AT: "dangin mahaifinka" ko "zuriyar mahaifinka"
"sojojin da ke tsaye a kusa da shi don kare shi"
Anan "Juya" na nufin juyawa ko juya baya ga sarki. AT: "Je ka kashe" ko "Kashe"
Kalmar "hannu" magana ne ta aikin da aka yi da hannu. AT: "bai yi komai ba don kisa" ko "ƙi kashewa"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Doweg ya kashe duk firistocin da kansa ko 2) kalmar "Doweg" wakiltar Doweg da mutuminsa. AT: "Doweg mutumin Idom da mutanensa suka juya suka kawo hari ... suka kashe"
"an kashe shi da takobi"
Nob sunan birni ne. Anan sunan "Nob" yana wakiltar mutanen wannan birnin. AT: "mutanen cikin garin Nob" ko "mutanen Nob"
Wannan sunan mutum ne.
1Aka gaya wa Dauda, "Ga shi, Filistiyawa na yaƙar Keila kuma suna washe wurin shiƙar hatsi."2Sai Dauda ya yi addu'a ga Yahweh domin taimako ya kuma tambaye shi, "Ko na tafi in kai wa waɗannan Filistiyawan farmaƙi? Yahweh ya cewa Dauda, "Tafi kakai wa Filistiyawa farmaƙi ka ƙubutar da Keila."3Mazajen Dauda suka ce masa, "Duba, muna jin fargaba a nan Yahuda. Balle wai har mu tafi Keila Gãba da rundunar Filistiyawa?"4Sai Dauda ya yi addu'a ga Yahweh domin taimako kuma. Yahweh ya amsa, "Ka tashi, gangara zuwa Keila. Gama zan baka nasara a bisa Filistiyawan."5Dauda da mutanensa suka tafi Keila suka kuma yi yaƙi da Filistiyawa. Ya kora garkunansu ya kuma buga su da babban yanka. Da haka Dauda ya kuɓutar da mazaunan Keila.6Lokacin da Abiyata ɗan Ahimelek ya gudu zuwa wurin Dauda a Keila, ya zo da falmara a hannunsa.7Aka gaya wa Saul cewa Dauda ya tafi Keila. Saul ya ce, "Allah ya ba da shi cikin hannuna. Gama yana tsare domin ya shiga cikin birnin da ke da ƙofofi da ƙyamare."8Saul ya tattara dukkan rundunarsa domin yaƙi, don ya gangara zuwa Keila, don ya kewaye Dauda da mutanensa.9Dauda na sane da cewar Saul na ƙulla cuta gãba da shi. Ya cewa Abiyata firist, "Kawo falmara nan."10Sai Dauda ya ce, "Yahweh, Allah na Isra'ila, bawanka tabbas ya ji cewa Saul na shirin zuwa Keila, ya lallatar da birnin sabili da ni.11Mutanen Keila zasu bashe ni cikin hannunsa? Saul zai gangaro, kamar yadda bawanka ya ji? Yahweh, Allah na Isra'ila, na roƙe ka, ka gaya wa bawanka." Yahweh ya ce, "Zai gangaro ya zo."12Sai Dauda ya ce, "Mutanen Keila zasu miƙa ni da mazaje na cikin hannun Saul?" Yahweh ya ce, "Zasu miƙaka."13Sai Dauda tare da mazajensa, da suke kamar ɗari shida, suka tashi suka fita daga Keila, suka kuma tafi daga wancan wuri zuwa wancan wurin. Aka gaya wa Saul da cewar Dauda ya kubce daga cikin Keila, daga nan kuma ya fãsa bin sa.14Dauda ya zauna cikin ƙarfafan wuraren tsaro cikin jeji, a cikin ƙasar duwatsu cikin hamada ta Zif. Saul ya nace da nemansa kowacce rana, amma Allah bai miƙa shi cikin hannunsa ba.15Dauda yaga cewar Saul ya fito neman ransa; a yanzu dai Dauda na cikin Hamadar Zif a Horesh.16Sa'an nan Yonatan, ɗan Saul, ya tashi ya tafi wurin Dauda a Horesh, ya kuma ƙarfafa hannunsa cikin Allah.17Ya ce masa, "Ka daka ji tsoro. Gama hannun Saul mahaifina ba zai same ka ba. Zaka zama sarki bisa Isra'ila, ni kuma zan zama na kusa dakai. Saul mahaifina shi ma ya san da haka."18Suka yi alƙawari a gaban Yahweh. Dauda ya zauna a Horesh, Yonatan kuma ya tafi gida.19Sai Zifiyawa suka zo wurin Saul a Gibiya suka ce, "Ba a wurinmu Dauda ya ke ɓuya ba cikin ƙarfafan wuraren tsaro na Horesh, a bisa tudun Hakila, wanda ya ke kudu da Yeshimon?20Yanzu ka zo, sarki! Bisa ga buƙatarka, ka zo! Namu fannin shi ne mu miƙa shi a hannun sarki."21Saul ya ce, "Bari Yahweh ya albarkace ku. Gama kun ji tausayina.22Ku tafi, ku tabbatar da hakan. Ku lura ku gane inda ya ke ɓuya da kuma wane ne ya gan shi a wurin. An gaya mani cewa yana da wayau ƙwarai.23Sai ku lura, ku kuma fahimci dukkan wuraren da ya ke ɓoye kansa. Ku dawo gare ni da tabbataccen zance, sa'an nan zan tafi tare da ku. Idan yana cikin ƙasar, zan binciko shi waje daga dukkan dubban Yahuda."24Sai suka tashi suka riga Saul zuwa Zif. Yanzu Dauda da mazajensa suna a cikin hamadar Mawon, a cikin Araba zuwa Kudu da Yeshimon.25Saul da mutanensa suka tafi neman shi. Amma aka gaya wa Dauda wannan, sai ya tafi zuwa tudun duwatsu ya kuma zauna a hamadar Mawon. Lokacin da Saul ya ji, ya runtumi Dauda zuwa hamadar Mawon.26Saul ya bi ta wancan sashen tudun, Dauda kuma da mazajensa na tafiya a wancan sashen tudun. Dauda ya hanzarta ya guje wa Saul. Da Saul da mutanensa na kewaye da Dauda da mazajensa don su kama su,27sai ɗan saƙo ya iso wurin Saul ya kuma ce, "Hanzartaka kuma zo, gama Filistiyawa sun kawo hari a ƙasar."28Saboda haka Saul ya komo daga bin Dauda ya kuma tafi gãba da Filistiyawa. Saboda haka ake kiran wurin Dutsen Tsira.29Dauda ya tafi daga nan ya kuma zauna cikin ƙarfafan wuraren tsaro na Engedi.
"Keila" sunan gari ne. Anan "Keila" tana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin. AT: "fada da mutanen Keila" (Duba: da )
raba hatsi ko tsaba, gaba ɗaya daga hatsi ko alkama ta wasu hanyoyin inji
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Za mu fi jin tsoro idan muka je Keila don yaƙi da sojojin Filistiyawa."
Marubucin ya fi mai da hankali ga Dauda, don haka waɗannan kalmomin duka mufuradi ne, kodayake mutanen Dauda sun taimake shi ya yi waɗannan abubuwa duka.
"hukuma kira"
Dauda yayi magana kamar wani don nuna girmamawarsa ga Yahweh. AT: "kamar yadda na ji ... ku gaya mani"
Anan "hannu" yana wakiltar ƙarfi ko iko. AT: "ka ba ni ga Saul"
Anan "hannu" yana wakiltar ƙarfi ko iko. AT: "ka ba ni da mutanena ga Saul"
"ya gudu daga"
Wannan shine sunan yankin da babu kowa a kusa da garin Zif.
Kalmar "hannu" magana ne ta iko. AT: "bai bar Saul ya sami iko a kan Dauda ba" ko "bai bar Saul ya yi yadda yake so tare da Dauda ba" ko "bai bar Saul ya kama Dauda ba"
Wannan karin magana ne. AT: "kokarin kashe shi"
Wannan sunan birni kusa da Zif.
Wannan karin magana ne. AT: "ya ƙarfafa shi ya dogara ga Allah"
Anan “hannu” magana ne ta Saul da ƙarfinsa. AT: "Don Saul mahaifina ba zai same ku ba" ko "Ga Saul mahaifina ba zai taɓa samun iko a kanku ba"
Wannan shi ne sunan ƙungiyar mutane daga Zif.
Ana iya fassara wannan tambayar ta zance azaman motsin rai. AT: "Dauda yana ɓoye a cikinmu a ... Yeshimon!"
Wannan shi ne sunan wani dutse a jejin Yahuda.
Wannan sunan yankin hamada ne kusa da Tekun Gishiri. Hakanan za'a iya fassara shi azaman "Jejin Yahudiya" ko "kufai."
Kalmar "hannu" magana ne ta iko. Mutane Zif suna magana da Saul kamar dai shi wani mutum ne don nuna masa cewa suna girmama shi. AT: "a ba ka David don ka iya yin duk abin da kake so tare da shi"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Ina fata Yahweh ya albarkace ku"
Cikakken sunan "tausayi" ana iya fassara shi da sifa "nau'in." Saul ya faɗi haka ne domin sun ba shi labarin Dauda kuma sun yarda su taimaki Saul su kama Dauda. AT: "kun tausaya mini" ko "kun faɗi wannan da alheri"
Waɗannan kalmomin guda biyu suna kusan kusan abu ɗaya kuma ana iya fassara su azaman yankin ɗaya. AT: "Sanin tabbas"
"wa ya ganshi"
Wannan karin magana ne. AT: "ko da zan kame kowane mutum a Yahuda" ko "a cikin duk dangin Yahuda"
Sun daina abin da suka kasance suna yi. Kada mai karatu ya yarda cewa suna zaune ne ko suna kwance.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Wani ya gaya wa Dauda cewa suna zuwa" ko "David ya san cewa suna zuwa"
Wannan shine sunan yankin da aka yashe kewaye da garin Mawon a kudancin Yahuda.
Kalmomin "sauri" da "zo" ana iya haɗa su zuwa ra'ayi ɗaya. AT: "Ku zo da sauri"
abin tunawa ko alama ce ta tserewar Dauda daga Saul
1Lokacin da Saul ya komo daga bin Filistiyawa, aka gaya masa, "Dauda na cikin Hamadar Engedi."2Sai Saul ya ɗauki mazaje zaɓaɓɓu dubu uku daga dukkan Isra'ila ya tafi neman Dauda da mazajensa a bisa Duwatsu na Awakin jeji.3Ya zo wurin mazamnin awakai nakan hanya, a inda akwai kogo. Saul ya shiga ciki don ya rufe ƙafarsa. Yanzu Dauda da mazajensa na zama a can ƙarshen ƙurewar kogon.4Mazajen Dauda suka ce masa, "Wannan ita ce ranar da Yahweh ya yi magana da ya ce maka, 'Zan bã da maƙiyanka cikin hannunka, don ka yi masa duk abin daka ga dama."' Sai Dauda ya tashi a hankali yana tafiya gaba a rarrafe ya kuma yanko sashen rigar Saul.5Daga baya sai zuciyar Dauda ta dame shi domin ya yagi sashen rigar Saul.6Ya cewa mazajensa, "Yahweh ya sauwaƙe da yiwa ubangidana haka, shafaffen Yahweh, har da zan miƙa hannu gãba da shi, ganin cewar shafaffe ne na Yahweh."7Don haka sai Dauda ya tsauta wa mazajensa da waɗannan maganganu, kuma bai bar su su kai wa Saul farmaƙi ba. Saul ya tashi, ya fita daga cikin kogon, yakama hanyarsa.8Bayan haka, Dauda shi ma ya tashi, ya fita daga cikin kogon, ya yi kira ga Saul: "Ubangidana sarki." Lokacin da Saul ya waiga bayansa, sai Dauda ya rusuna da fuskarsa ƙasa ya nuna masa bangirma.9Dauda ya ce wa Saul, "Me yasakake sauraron mutanen da ke cewa, 'Duba, Dauda yana neman ya cutar dakai?'10Yau ka ga yadda Yahweh ya miƙaka cikin hannuna sa'ad da muke a cikin kogon. Wasu suka ce mani in kashe ka, amma na bar ka. Na ce, 'Ba zan miƙa hannuna gãba da ubangidana ba; gama shafaffe ne na Yahweh.'11Duba, mahaifina, dubi sashen rigarka a hannuna. Ai ko yadda na yanki sashen rigarka amma ban kashe ka ba, kana iya fahimta da ganin cewa babu wata mugunta ko makirci cikin hannuna, kuma ban yi maka zunubi ba, ko da ya ke kana neman rainaka ɗauke.12Bari Yahweh ya shar'anta tsakanina dakai, kuma bari Yahweh ya sãka mani gãba dakai, amma hannuna ba zai tayar maka ba.13Kamar yaddakarin maganar mutanen dã ke cewa, 'Daga cikin mugu mugunta ke fitowa.' Amma hannuna ba za ya tayar maka ba.14Wane ne sarki ke fita neman sa? Wane ne kake kora? Mataccen kare! Wofi!15Bari Yahweh ya zama mai shari'a ya kuma shar'anta tsakani na dakai, ya kuma tabbatar, ya kuma tsaya mani ya kuma sa in tsira daga hannunka."16Bayan da Dauda ya gama furta waɗannan maganganun ga Saul, Saul ya ce, "Muryarka ce wannan, ɗana Dauda?" Saul ya tãda muryarsa ya yi kuka.17Ya ce wa Dauda, "Kai mai adalci ne fiye da ni. Gamaka sake biya na da alheri, inda na maido maka mugunta.18Ka furta yau yaddaka yi mani alheri, gama baka kashe ni ba lokacin da Yahweh ya miƙa ni ga jinƙanka.19Domin idan mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi ya tafi lafiya? Bari Yahweh ya sãka maka da alheri yaddaka yi mani a yau.20Yanzu, na sani tabbas zaka zama sarki kuma sarautar Isra'ila zatakafu a hannunka.21Ka rantse mani har ga Yahweh cewar ba zaka datse zuriyata bayana ba, kuma ba zaka lallatar da sunana daga gidan mahaifina ba.22Sai Dauda ya yi alƙawari ga Saul. Sa'an nan Saul ya tafi gida, amma Dauda da mazajensa suka haura zuwakagara mai ƙarfi.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "wani ya gaya masa"
Engedi wuri ne a cikin Isra’ila yamma da Tekun Gishiri inda akwai ruwa tare da busasshiyar ƙasa kewaye da shi.
mutanen da ya zaɓa saboda sune mayan sojoji
"garken tumaki"
Wannan kalmomi ne na '' sauƙaƙa kansa '' ko '' najasa '' ko kuma 'woshi hanjinsa.
Kalmar "tashi" karin magana ne ta neman aiki. AT: "Dauda ya ɗauki mataki; a hankali ya ratse"
kusanci a hankali, a hankali ko a hankali
Wannan karin magana ne. AT: "Dauda ya yi baƙin ciki saboda ya yi wani abu ba dai-dai ba"
"wanda Yahweh ya zaɓa ya shugabanci mutanensa" ko "wanda Yahweh ya naɗa sarki"
Hannun sunan magana ne na ikon haifar da cutarwa. AT: "don cutar da shi ta kowace hanya"
Ana iya fassara wannan tambaya a azaman bayani. AT: "Kada ku saurari mutanen da ke cewa, 'Duba, Dauda yana neman cutar da ku.'"
Anan “idanunku” suna wakiltar Sarki Saul. AT: "kun gani da idanunku"
Kalmar "hannu" nuna ta sarrafawa. AT: "sanya ku inda zan iya kashe ku ko in ba ku damar rayuwa"
Saul ba shi ne ainihin mahaifin Dauda ba. Dauda ya kira shi “uba” don ya nuna cewa yana daraja Saul.
Dauda yayi magana kamar mugunta da cin amana abubuwa ne na zahiri da zai iya riƙewa a hannunsa. Anan "hannu" yana wakiltar mutum mai aiki ko aikata wani abu. AT: "Ban aikata wani mugunta a kanku ba, kuma ban yi muku tawaye ba"
Hannun ya nuna ikon haifar da cutarwa. Duba yadda kuka fassara makamancin magana a cikin 1 Sama'ila 24: 5. AT: "Ba zan cutar da ku da komai ba"
Ana iya fassara wannan magana a azaman jigon suna. AT: "mutanen da suka rayu tun da daɗewa"
Wadannan tambayoyin na magana za a iya fassara su azaman maganganu. Lokacin da David yayi tambayoyin, ya sani cewa zai amsa tambayoyin da kansa. AT: "Bari in fada muku wanda sarkin Isra'ila ya fito bayansa. Bari in fada muku ko wanene kuke bi."
Kalmomin "mataccen kare" kwatanci ne ga mutum mara ƙarfi. Ana iya yin wannan jimlar cikakke. AT: "Kuna bin mutumin da ba shi da iko kamar mataccen kare"
Kalmar "ƙuma" kwatanci ce ga mutumin da wasu ba su ɗauka da muhimmanci ba. AT: "Kuna bin mutumin da bashi da mahimmanci kamar ƙuma"
Mai yiwuwa su ne 1) "ku yi abin da yake dai-dai, kuma ku nemi hujja ta" ko kuma 2) "ku ga cewa dalili na daidai ne kuma ku yi yaƙi domin ni."
Saul ya yi magana kamar Dauda ɗansa ne don ya nuna wa Dauda cewa yana ƙaunarsa.
Marubucin yayi rubutu kamar murya wata aba ce mutum zai iya ɗagawa da hannunsa. AT: "kuka da karfi"
Saul ya san cewa Dauda ya nuna cewa ya goyi bayan Sarki Saul kuma ya kasance da aminci a gare shi ta wajen kashe shi
Saul ya yarda cewa Dauda ya zaɓi nuna jinƙai kuma ya nuna amincinsa ga Sarki Saul a matsayin shafaffen Yahweh.
Inda Saul ya yi imani da cewa Dauda maƙiyinsa ne, ya fahimci cewa ko da shike Dauda zai zama sarki, Dauda ba zai karɓi gadon sarautar daga hannun Saul da ƙarfi ba, amma zai jira lokacin da Yahweh ya ƙayyade.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Mai yiwuwa su ne 1) Dauda zai sa masarautar Isra’ila ta ci gaba ta hanyar ikonsa na sarki. AT: "mulkin Isra'ila zai sami ci gaba yayin da kake mulkin Isra'ilawa" ko 2) Yahweh zai sa Dauda ya sami cikakken iko akan masarautar Isra'ila. AT: "zaku sami cikakken mulkin mulkin Isra'ila"
"ba za ku kashe 'ya'yana maza da danginsu ba." Ya kasance abu ne na yau da kullun ga sabon sarki wanda ba ya daga zuriyar gidan da ya gabata ya kashe duk ‘ya’yan tsohon sarki don hana ɗayansu ƙalubalantar shi akan kujerar sarauta.
Yana da mahimmanci ga kowane iyali a cikin Isra’ila su sami zuriya daga tsara zuwa tsara suna ɗauke da sunan dangi da gadon ƙasa. AT: "ba za ku halakar da iyalina da zuriyata ba" ko "za ku bar iyalina su rayu"
"Dauda da sojojinsa"
1Yanzu dai Sama'ila ya mutu. Dukkan Isra'ila suka taru tare suka kuma yi masa makoki, suka kuma binne shi a cikin gidansa a Rama. Sa'an nan Dauda ya tashi ya kuma tafi cikin hamadar Faran.2Akwai wani mutum a Mawon, wanda dukiyarsa na cikin Karmel. Mutumin mai arziki ne ainun. Yana da tumakai dubu uku da awakai dubu ɗaya. Yana sausayar gashin tumakinsa akamel.3Sunan mutumin Nabal, kuma sunan matarsa Abigel. Mata ce mai hikima da kyan gani. Amma mutumin mai zafin hali da mugun tafarki ne a al'amuransa. Shi daga zuriyar gidan Kaleb ne.4Dauda ya ji daga cikin hamada cewa Nabal yana sausayar gashin tumakinsa.5Don haka Dauda ya aika samari mutum goma. "Ku tafi zuwakamel, ku tafi wurin Nabal, ku gaishe shi da sunana.6Za ku ce masa, 'Ka zauna cikin wadata. Salama gare ka salama ga gidanka, kuma salama ga dukkan mallakarka.7Na ji cewakana da 'yan sausaya. Makiyayanka na tare da mu, kuma bamu cutar da su ba, basu kuma rasa komai ba cikin dukkan lokacin da suke akarmel.8Ka tambayi samarinka, zasu kuma gaya maka. Yanzu bari 'yan samarina su sami tagomashi a idanunka, gama mun kawo ga ranar buki. Na roƙe kaka bã da duk abin dakake da shi a hannunka ga bayinka ga kuma ɗan ka Dauda."9Lokacin da samarin Dauda suka iso, suka faɗi dukkan wannan ga Nabal a madadin Dauda suka kuma jira.10Nabal ya amsa wa bayin Dauda, "Wane ne Dauda, kuma wane ne ɗan Yesse? Akwai bayi da yawa da ke ƙaurace wa iyayen gidansu a wannan kwanaki.11To na ɗauki gurasata da ruwa na da namana da na yanka domin 'yan sausayata, in kuma bada su ga mutanen da ban san ko daga ina suke ba?"12Saboda haka 'yan samarin Dauda suka juya suka tafi suka kuma dawo, suka kuma gaya masa duk abin da aka ce.13Dauda ya cewa mazajensa, "Kowanne mutum ya ɗaura takobinsa." Sai kowanne mutum ya ɗaura takobinsa. Dauda shi ma ya ɗaura takobinsa. Mazajen wajen ɗari huɗu suka bi Dauda, ɗari biyu kuma suka tsaya wurin kayayyaki.14Amma ɗaya daga cikin 'yan samarin ya gaya wa Abigel, matar Nabal; ya ce, "Dauda ya aiko da manzanni daga cikin hamada domin su gaishe da ubangidanmu, amma ya zage su.15Kuma mazajen sun nuna mana alheri. Ba mu cutu ba kuma ba mu ɓatar da komai ba cikin dukkan tafiyar da muka yi da su lokacin da muke cikin filaye.16Sun zama ganuwa a garemu da rana da dare, dukkan lokutan da muke tare da su muna kula da garken.17Saboda haka ki san wannan ki kuma san abin da zaki yi, gama akwai shirin mugunta game da ubangidanmu, kuma gãba da dukkan gidansa. Shi mutum ne marar cancanta da ba mai iya shawartar sa."18Sai Abigel ta tashi da sauri ta ɗauki gurasa curi ɗari biyu, inabi kwalba biyu, tumakai guda biyar gyararru, awo biyar na busasshen hatsi, da curin kauɗar inabi guda ɗari, da wainar 'ya'yan ɓaure guda ɗari biyu, ta ɗora su bisa jakai.19Ta cewa matasanta, "Ku sha gabana, zan kuma bi ku a baya." Amma bata gaya wa mijinta Nabal ba.20Yayin da take zuwa bisa jakinta ta kuma sauka daga bakin ƙofar dutsen, Dauda da shi da mazajensa suna saukowa zuwa gare ta, ta kuma tarbe su.21Yanzu Dauda ya riga ya faɗa cewa, "Tabbas a banza na tsare dukkan mallakar wannan mutum cikin hamada, har babu abin da ya ɓace cikin dukkan abin da ke nasa, kuma sai ya sãka mani da mugunta.22Bari Allah ya yi mani haka, Dauda, fiye da haka kuma, idan war haka da safe na bar ko da namiji ɗaya wanda ke nasa."23Lokacin da Abigel ta ga Dauda, ta hanzarta ta sauko daga jakarta ta kuma kwanta a gaban Dauda da fuskarta ƙasa ta kuma rusunar dakanta zuwa ƙasa.24Ta kwanta dab da ƙafafunsa ta kuma ce, "akainakaɗai, ubangidana, laifin yakasance. Na roƙe ka bari baiwarka ta yi magana dakai, ka kuma saurari maganganun baiwarka.25Kada ubangidana ya kula da wannan talikin marar amfani, Nabal, gama yadda sunansa ya ke, haka ya ke. Nabal ne sunansa, kuma sakarci na tare da shi. Amma ni baiwarka ban ga 'yan samarin ubangidana ba, waɗandaka aiko.26Yanzu dai, ubangidana, a bisa ran Yahweh, da kuma ranka, har tun da Yahweh ya tsare ka daga zubda jini, kuma daga ramuwa domin kanka da hannunka, yanzu bari maƙiyanka, da waɗanda ke neman yin mugunta ga ubangidana, su zamakamar Nabal.27Yanzu bari wannan kyautar da baiwarka takawo ga ubangidana a ba 'yan samarin da ke biye da ubangidana.28Na roƙe ka daka gafarta wa bawanka, gama Yahweh za ya gina wa ubangidana tabbataccen gida, domin ubangidana yana yaƙin Yahweh ne; kuma ba za a sami mugunta a cikinka ba dukkan kwanakin ranka."29Koda shi ke mutane sun tashi neman ranka, duk da haka ran ubangidana za a kãre shi cikin taro na masu rai daga wurin Yahweh Allahnka; kuma za ya ɗauke rayukan maƙiyanka, kamar daga aljihu na majajjawa.30Yahweh zai aiwatar wa ubangidana komai da ya alƙawarta maka, ya kuma zaɓe ka shugaba bisa Isra'ila.31Wannan ba zai zama abin nauyi gare ka ba - cewaka zubar da jinin marar laifi, ko domin ubangidana na ƙoƙarin kuɓutar dakansa. Gama a lokacin da Yahweh zai yi wa ubangidana alheri, ka tuna da baiwarka."32Dauda ya cewa Abigel, "Mai albarka ne Yahweh, Allah na Isra'ila, shi wanda ya aiko ki da kika same ni yau.33Hikimarki mai albarka ce kuma ke mai albarka ce, domin kin tsare ni daga zubar da jini kuma daga rama wakaina da hannuna!34A gaskiya, yadda Yahweh, Allah na Isra'ila, ke raye, shi wanda ya kiyaye ni daga cutar da ke, da ba domin kin yi sauri kin zo gare ni ba, da ba za a sami wani ragowa domin Nabal ko da ɗan jariri ne zuwa wayewar gari ba."35Sai Dauda yakarɓi abin da takawo masa daga hannunta; ya ce ma ta, "Tafi cikin salama zuwa gidanki; duba, na saurari muryarki kuma na gamsu."36Sai Abigel ta koma ga Nabal; gashi kuwa, ya shirya shagali a gidansa, kamar shagali na sarki; kuma zuciyar Nabal ta shagalta cikinsa, gama ya bugu ainun. Sai ta ƙi gaya masa komai har hasken safiya.37Sai ya zamana da safe, lokacin da ƙarfin giya ya fita daga Nabal, sai matarsa ta gaya masa waɗannan abubuwan; zuciyarsa ta mutu cikinsa, sai ya zamakamar dutse.38Sai ya zama bayan kwana goma sai Yahweh yakai wa Nabal farmaƙi har yakashe shi.39Da Dauda ya ji cewa Nabal ya mutu, ya ce, "Albarka ta tabbata ga Yahweh, wanda ya ɗauki zargin zãgin da na sha daga hannun Nabal ya kuma kãre bawansa daga mugunta. Ya juyar da aikin muguntar Nabal bisakansa." Sai Dauda ya aika ya kuma yi magana da Abigel, domin ya ɗauke ta a matsayin matarsa.40Lokacin da bayin Dauda suka iso wurin Abigel akarmel, suka yi mata magana suka ce, "Dauda ya aike mu gare ki mu ɗauke ki zuwa wurinsa ki zama matarsa."41Ta tashi, ta sunkuyar dakanta zuwa ƙasa, ta kuma ce, "Duba, baiwarka baiwa ce da za ta wanke ƙafafun bayin ubangidana."42Sai Abigel ta yi sauri ta tashi, ta hawo bisa jaka tare da bayi 'yanmata biyar da ke nata waɗanda suka biyo ta; sai kuma ta biyo bayin Dauda ta kuma zama matarsa.43Yanzu dai Dauda ya ɗauko wakansa Ahinowam ta Jezril a matsayin matarsa; su biyu suka zama matansa.44Haka kuma, Saul ya rigaya ya bayar da 'yarsa, matar Dauda, ga Falti ɗan Layish, wanda mutumin Galim ne.
Wannan wataƙila batun gama gari ne. Da yawa daga cikin jama'ar Isra'ila suna wurin, amma wataƙila wasu ba su sami damar halarta ba.
Mai yiwuwa ma'anonin su ne sun binne Sama'ila 1) a garinsa na Rama ko 2) a ƙasar danginsa da ke Rama amma ba a zahiri a cikin gidan ba ko 3) a gidansa da ke Rama.
"Dauda da mutanensa suka ci gaba suka sauka"
Wannan sunan wani gari ne. Wannan ya bambanta da Tsaunin Karmel.
"aske ulu daga tumakinsa"
Wannan sunan mutum ne.
Wannan sunan mace.
Anan "gida" yana wakiltar iyali. AT: "Ya kasance daga zuriyar Caleb" ko "Ya kasance daga zuriyar Kaleb"
"ku gaishe shi kamar yadda zan gaishe shi idan ina wurin"
"Ina so ku rayu cikin wadata." Cikakken sunan "wadata" ana iya fassara shi azaman aiki. AT "Ina fata ku mallaki kyawawan abubuwa da yawa muddin kuna raye"
"Ina fatan zaman lafiya ya zo muku, da iyalanku da dukiyoyinku"
"Masu sausayar ku suna aiki" ko "masu sausayar ku suna da tumakin da za su yi musu sausaya." Dauda yana son mutanensa su yi magana don Nabal ya fahimci cewa tumakinsa suna da kyau domin mutanen Dauda sun taimaka wajen tsare su.
Dauda yana nuna yadda shi da mutanensa suka ba bayin Nabal da garkensu kariya. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "mun kiyaye su da dukiyoyinsu daga cutarwa"
Anan idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. AT: "ku faranta ran samarina" ko kuma "ku kula da samarina da kyau"
Dauda ya yi magana kamar shi ɗan Nabal ne don ya nuna cewa yana daraja Nabal, wanda ya tsufa.
"Rundunar Dauda"
"ya ba Nabal cikakken sako"
Nabal ya yi amfani da tambayoyi don ya nanata cewa ba shi da dalilin taimaka wa Dauda. Wadannan tambayoyin guda biyu ana iya fassara su azaman maganganu. AT: "Wannan Dauda ɗan Yesse da kuke magana game da shi" "Ban san shi ba." ko "Ban san ko wanene wannan Dauda ba, don haka ba zan yi kamar yadda ya ce ba. Ban san ko wanene Yesse ba, don haka ban damu da abin da zai faru da ɗansa ba. "
"maza wani da ban san inda suka fito ba" ko "mutanen da ban sani ba"
Idan ba a san takuba a cikin yarenku ba, kuna iya ɗaukar "madauri a kan takobinsa" azaman ma'anar ma'ana don shirya don yaƙi. AT: "Kowane mutum, ku shirya don yaƙ." Kuma kowane mutum ya shirya yaƙi. David ma ya shirya don yaƙi"
Sun kasance a sansanin su don hana wasu maharan satar kayan su.
Kuna iya bayyana abin da saurayin ya yi kafin ya yi magana da Abigel. AT: "Daya daga cikin bayin Nabal ya gano abin da Dauda da mutanensa suke shirin yi, don haka ya tafi wurin matar Nabal Abigel"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Babu wanda ya cutar da mu" ko "Ba mu da wata matsala"
"ba mu rasa komai ba lokacin da muke tare da su." Mutanen Dauda suka hana dabbobin daji da sauran mutane yin garken garken Nabal.
Mutanen Dauda sun kasance kamar bango a cikin birni wanda yake kare mutanen birni daga abokan gaba.
Mai maganar yana taka tsantsan kar ya ambaci wanda ke kulla mugu. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "wani yana shirin aikata mugunta ga maigidanmu"
"cewa wani ya riga ya dafa" ko "a shirye wani ya dafa"
"hatsin da wani ya dafa"
"wainar zabibi" ko "yawan zabibi
Zai yiwu ma'anonin su 1) a cikin ƙaramin, siririn gadon rafi ko 2) zuwa inda mutanen suke ɓoye.
"Dauda da sojojinsa"
Marubucin ya ba da bayanan baya kafin ya ci gaba da labarin.
Mai karatu yana bukatar fahimtar cewa Dauda ya faɗi waɗannan abubuwa kafin ya ce, "Kowane mutum ya rataye takobinsa" a cikin 1 Sama'ila 25:12.
Rubutun Ibraniyanci yana da "Allah ya bugi maƙiyan Dawuda," kuma wasu sifofin sun bi wannan. Koyaya, karatun ULB yana bin babbar al'adar Girka ta Tsohon Alkawari, kamar yadda wasu sifofin zamani keyi.
Marubucin ya gama ba da bayanan baya, don haka ya ci gaba da labarin.
Abigel tana da tawali’u kuma tana nuna cewa za ta yi biyayya ga Dauda domin shugaba ne mai iko.
Abigel tayi magana game da kanta da Dauda kamar wasu mutane biyu ne, don nuna cewa tana girmama Dauda.
Abigel ta ci gaba da ba Dauda shawara cewa kada ya rama.
Kuna iya bayyana abin da Abigel za ta yi. AT: "Amma da ... na ga ... wanda kuka aiko, da na ba su abinci"
kisan kai
Hannu magana ne ta abin da mutum yake yi da hannu. Abigel ta ɗauka cewa ya kamata Dauda ya bar Yahweh ya rama a kansa. AT: "ɗaukar fansa da kanka maimakon barin Yahweh ya yi"
Abigel tana magana kamar Yahweh ya riga ya hukunta Nabal. AT: "Ina fatan Yahweh zai hukunta maƙiyanku ... kamar yadda zai hukunta Nabal"
Abigel ta ci gaba da gaya wa Dauda kada ya yi fushi.
Abigel tayi amfani wannan magana don ta nuna girmamawa ga Dauda. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Ina rokon ka ba wannan kyautar da bawanka ya kawo wa shugabana, ga samarin" ko "Ina rokon ka bari shugabana ya ba da kyautar da bawanka ya kawo wa ubangijina, ga samarin"
Anan "gida" wani karin magana ne da ake amfani da shi don "zuriya." AT: "Yahweh zai tabbatar cewa koyaushe maigidana yana da zuriya wanda ke aiki a matsayin sarki"
"yaƙi da magabtan Yahweh"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "ba wanda zai taɓa ganin kuna aikata wani mummunan abu" ko "ba za ku taɓa yin wani abu na mugunta ba"
Abigel tayi magana game da rayuwar Dauda kamar abu ne dogo siriri wanda mutum zai iya sanyawa tare da wasu dogaye da siraran abubuwa sannan ya ɗaura su cikin ƙulla da igiya. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh Allahnku zai ɗaure ran maigidana a cikin tarin masu rai" ko "Yahweh Allahnku zai rayar da ku tare da waɗanda suke da rai"
Abigel tayi magana game da magabtan Dauda suna rayuwa kamar ƙananan abubuwa kamar dutse wanda za'a iya sawa a cikin majajjawa da harbi mai nisa. AT: "zai kashe maƙiyanku a sauƙaƙe kamar yadda mutum yakan harba dutse nesa mai nisa"
Abigel ta ci gaba da tattaunawa da Dauda.
Abigel tana faɗin cewa idan Dauda ya zaɓi yin fansa zai kasance da lamiri mai tsabta sa'ad da Yahweh ya naɗa shi sarkin Isra'ila. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Za ku yi farin ciki koyaushe kamar yadda kuka yi - cewa ba ku zubar da jinin marasa laifi ba, ko kuma saboda maigidana bai yi ƙoƙarin ceton kansa ba"
Wannan shi ne, lokacin da Yahweh ya naɗa shi sarki bayan mulkin Saul ya ƙare.
Dauda ya karɓi shawarar Abigel da kyaututtuka.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. Mai yiwuwa ma'anonin sune 1) "Na yabi Yahweh ... wanene" ko 2) "Bari duka mutane su yabi Yahweh ... wanene."
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Na gode wa Yahweh saboda ya albarkace ku ta hanyar sa ku masu hikima kuma saboda"
Dauda ya karɓi kyautar Abigel kuma ya yarda ya yi kamar yadda ta shawarce shi.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Da ban bar wa Nabal ko da ɗa namiji ba"
Wannan karin magana ne. Abigel ba ta sauke duk kyaututtuka daga jakunan kanta ba. AT: "ta karɓi duk kyaututtukan da ta kawo"
Kalmar "murya" magana ne ta saƙon da mutum yake magana da shi kuma abin da aka haɗa shi ne ga wanda yake magana. AT: "sun saurari abin da kuka gaya mani" ko "zan yi kamar yadda kuka ba ni shawara"
Nabal ya yi farin ciki ƙwarai
wayewar gari
Hukuncin Yahweh a kan Nabal
Nabal ya daina maye kuma hakan ya sa ba ya farin ciki.
Nabal bai iya motsawa ba saboda yana tsoro cewa ba shi da ƙoshin lafiya, wataƙila domin ya shanyewar jiki.
Dauda ya ce zai kāre Abigel ta wurin aurenta.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 25:32. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) AT: "Na yabi Yahweh" ko 2) AT: "Bari duka mutane su yabi Yahweh"
Wannan karin magana ne. AT: "ya kare ni bayan Nabal ya wulakanta ni"
Dauda yayi magana kamar wani mutum don nuna girmamawarsa ga Yahweh. AT: "ya hana ni aikata ayyukan muguntar"
AT: "ya yi wa Nabal abin da Nabal ya shirya yi mini"
Kuna iya bayyana bayanan da aka fahimta. AT: "ya aika da mutane don su yi magana da Abigel kuma su gaya mata cewa Dauda yana so ya ɗauke ta ta zama matarsa"
Abigel ta amsa ta rusuna. Ya kamata mai karatu ya fahimci cewa watakila ta riga ta tsaya a lokacin da maza suke magana da ita a cikin 1 Sama’ila 25:39, don haka kalmar “tashi” magana ne ta yanke shawarar yin ruku’u ƙasa.
Abigel tana magana kamar wata ce don ta nuna cewa tawali’u ne. Ta nuna cewa tana son zama sabuwar matar Dauda ta wurin miƙa wa ƙafafun bayin Dauda ƙafa. AT: "Duba, zan bauta muku, bayin maigidana Dauda, ta hanyar wanke ƙafafunku"
Kuna buƙatar bayyana abin da Abigel ta yi bayan ta tashi da kuma kafin ta hau. AT: "da sauri ta yi abin da ta buƙaci don shirya don tafiya, sa'annan ta hau"
Abigel ta hau jaki, amma barorin mata suka yi ta tafiya.
Wannan abin ya faru kafin Dauda ya auri Abigel.
Waɗannan sunayen maza ne. (Duba: tanslate_names)
Wannan gari ne a arewacin Yerusalem.
1Sai Zifiyawa suka zo wurin Saul a Gibiya suka kuma ce, "Ba Dauda yana ɓoyewa a cikin tudun Hakila ba, wanda ya ke kamin Yeshimon?"2Sai Saul ya tashi ya kuma tafi zuwa hamada ta Zif, tare da zaɓaɓɓun mutane dubu uku na Isra'ila, domin neman Dauda a cikin hamadar Zif.3Saul yakafa sansani a bisa tudun Hakila, wanda ke kafin Yeshimon, a gefen hanya. Amma Dauda na zama cikin hamadar, kuma ya ga cewa Saul na zuwa gare shi a cikin hamadar.4Sai Dauda ya aiki 'yan leken asiri kuma ya fahimci cewa tabbas Saul ya zo.5Dauda ya tashi ya kuma tafi wurin da Saul yakafa sansani; ya ga inda Saul ya kwanta, tare da Abna ɗan Nã, shugaban rundunarsa; Saul ya kwanta cikin sansanin, kuma mutanen suka zagaye shi, dukkansu suna barci.6Sa'an nan Dauda ya cewa Ahimelek Bahittiye, kuma ga Abishai ɗan Zeruwa, ɗan'uwan Yowab, "Wane ne zai tafi da ni wurin Saul a cikin sansani?" Abishai ya ce, "Ni! Zan tafi tare dakai."7Sai Dauda tare da Abishai suka tafi wurin rundunar cikin dare. Saul na barci cikin tsakiyar sansani tare da mãshinsakafe da ƙasa kusa dakansa. Abna da kuma sojojinsa suka kwanta zagaye da shi.8Sai Abishai ya cewa Dauda, "Yau Allah ya miƙa maƙiyinka cikin hannunka. Yanzu na roƙe kaka bar ni in cake shi har ƙasa da mashi da bugu ɗaya tak. Ba zan cake shi sau biyu ba."9Dauda ya cewa Abishai, "Kadaka hallaka shi; gama wane ne za ya miƙa hannunsa gãba da shafaffen Yahweh ya kuma zama marar laifi?"10Dauda ya ce, "Na rantse da ran Yahweh, Yahweh zai kashe shi, ko kuma ranar mutuwarsa ta zo, ko kuma ya tafi yaƙi ya mutu.11Bari Yahweh ya sauwaƙe mani da in miƙa hannuna gãba da shafaffe; amma yanzu, na roƙe ka, ka ɗauki mashin da ke kusa dakansa da kuma gorar ruwa, sai mu tafi."12Sai Dauda ya ɗauke mashin da gorar ruwan da ke kusa dakan Saul, suka kuma tafi. Babu wanda ya gansu ko ya san komai game da haka, ko wani ya farka, gama duk sun yi barci, gama barci mai nauyi daga wurin Yahweh ya faɗo bisansu.13Sa'an nan Dauda ya tashi ya tafi wancan ɓangaren ya kuma tsaya akan tsauni can nesa; akwai babbar rãta tsakaninsu.14Dauda ya yi kira da ihu ga mutanen ga kuma Abna ɗan Nã; ya ce, "Baka amsa ba, Abna?" Sai Abna ya amsa ya ce, "Kai wane ne da ke yi wa sarki ihu?"15Dauda ya cewa Abna, "Kai ba mutum ba ne mai ƙarfin hali? Wane ne kamarka a Isra'ila? To donme baka yi tsaron ubangidanka sarki ba? Gama wani ya shigo domin yakashe sarki ubangidanka.16Wannan abin daka yi ba shi da kyau. Na rantse da ran Yahweh, ka cancanci ka mutu domin baka yi tsaron ran sarki ubangidanka ba, shafaffe na Yahweh. Yanzu ka duba inda mashi da gorar ruwa da ke kusa dakansa suke!"17Saul ya sasance muryar Dauda ya kuma ce, "Wannan muryarka ce, ɗana Dauda?" Dauda ya ce, "Muryata ce, ubangidana, sarki."18Ya ce, "Me yasa ubangidana ke neman bawansa? Me na yi? Wacce mugunta ce ke cikin hannuna?19Yanzu saboda haka, na roƙe ka, bari ubangidana sarki ya saurari maganganun bawansa. Idan Yahweh ne ya zugaka gãba da ni, bari yakarɓi baiko; amma idan mutum ne, bari ya la'anta a fuskar Yahweh, gama yau sun kore ni waje, domin kada in manne wa gãdon Yahweh; sun ce mani, "Je ka yi sujada ga wasu alloli.'20Saboda haka yanzu, kadaka bar jinina ya zuba nesa da fuskar Yahweh; gama sarkin Isra'ila ya fito neman ƙwaro ɗayakamar yadda wani ke fita farautar makwarwa a bisa duwatsu."21Sai Saul ya ce, "Na yi zunubi. Dawo, Dauda, ɗana; domin ba zan ƙara cutar dakai ba, domin yau raina ya zama abin daraja a idonka. Duba, na yi kamar wawa kuma na yi mugun kuskure."22Dauda ya amsa ya kuma ce, "Duba, mashin ka yana nan, sarki! Bari ɗaya daga cikin samarin ka ya zo yakarɓa yakai maka.23Bari Yahweh ya sãka wa kowa bisa ga adalcinsa da amincinsa; domin Yahweh ya miƙaka cikin hannuna yau, amma ba zan bugi shafaffensa ba.24Duba, kamar yadda ranka ke da daraja a idanuna yau, bari raina ya zama da daraja a fuskar Yahweh, kuma bari ya kuɓutar da ni daga dukkan wahala."25Sai Saul ya cewa Dauda, "Bari ka yi albarka, Dauda ɗana! Lallai zaka yi manyan abubuwa kuma zaka yi nasara cikin dukkansu." Sai Dauda yakama hanyarsa, Saul kuma ya koma fadarsa.
Ana iya fassara wannan tambayar azaman motsin rai. AT: "Dauda yana ɓoye ... Yeshimon!"
Wannan sunan yankin hamada ne kusa da Tekun Gishiri. Hakanan za'a iya fassara shi azaman "Jejin Yahudiya" ko "kufai." Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 23:19.
Kalmar "tashi" karin magana ne ta neman aiki. AT: "Sai Saul ya ɗauki mataki kuma ya tafi"
mutanen da ya zaɓa saboda sun kasance manyan sojoji
"Dauda ya dauki mataki kuma ya tafi"
Waɗannan sunayen maza.
Waɗannan sunayen maza.
"Ina so in zama wanda ya sauka"
Abishai yayi magana kamar abokan gaba ƙaramin abu ne da Allah ya ba a hannun Dauda. Kalmar "hannu" na nufin ta ƙarfin da hannu zai iya aiwatarwa. AT: "Allah ya baku cikakken iko akan makiyinka"
Wannan magana da ke nufin "kisa da mashi"
"Zan kashe shi a karo na farko da na buge shi" ko "Ba zan buƙaci na buge shi a karo na biyu ba"
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. Hakanan za'a iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Ba wanda zai iya bugun shafaffen Yahweh kuma ya kasance ba shi da laifi." ko "Duk wanda ya bugi shafaffen Yahweh zai zama mai kisan kai."
"kamar yadda Yahweh yake rayuwa" ko "kamar yadda Yahweh ya yi rai"
"zai mutu ajalin mutuwa"
Hannun yana magana ne don cutarwar da hannu zai iya yi. AT: "ku aikata komai don cutarwa"
Yahweh ya sa sun yi barci mai nauyi.
Dauda ya yi amfani da tambaya don ya kunyata Abna don ya amsa. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Ka amsa mini, Abna!"
Dauda ya yi amfani da tambaya don ya tsawata wa Abna don bai kāre Saul ba. AT: "Kai mutum ne jarumi."
Dauda ya yi amfani da tambaya don ya tsawata wa Abna don bai kāre Saul ba. AT: "Kai ne mafi girman soja a Isra'ila."
Zai yiwu ma'anar su ne 1) wannan tambaya ce ta gaske kuma Dauda yana son Abna ya amsa masa ko 2) wannan tambaya ce ta magana kuma Dauda yana tsawata wa Abna. AT: "Don haka ya kamata ku kula da shugabanku sarki!"
Saul ba shine mahaifin Dauda na gaske ba. Saul ya yi magana kamar dai shi mahaifin Dauda ne don ya nuna wa Dauda cewa yana son Dauda ya amince da shi kuma ya girmama shi kamar yadda Dauda zai amince da kuma girmama mahaifinsa.
Anan Dauda yayi magana game da Saul a mutum na uku yana kiran shi "shugabana," shi kuma yana magana ne game da na uku wanda yake kiran kansa "bawansa." Dauda yayi wannan magana don ya nuna girmamawa ga Saul. AT: "Me ya sa kake, shugabana, kana bi na, bawanka?" ko "Me yasa kuke bina?"
Wannan yana magana akan mugunta kamar abu ne wanda aka riƙe a hannu. Anan "hannu" yana wakiltar mutum mai aiki ko aikata wani abu. Mai yiwuwa ma'anoni sune 1) Dauda da gaske yana son Saul ya amsa tambayar. AT: "Me na yi kuskure?" ko 2) ana iya fassara wannan tambayar ta magana a matsayin sanarwa. AT: "Ban yi kuskure ba!"
Dauda yayi magana kamar shi da sarki wasu mutane ne don girmama Saul. AT: "kai sarki na, saurari maganata"
"ya sa ka yi fushi da ni"
Kuna iya bayyana dalilin da zai ba da kyauta. AT: "Zan ba shi hadaya don haka ba zai sake sa ku yi fushi da ni ba"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "bari Yahweh ya yanke hukuncin azabtar da su"
Dauda ya yi amfani da kalmar "ƙwaro" a matsayin kwatanci ga mutum, kansa, wanda ba zai iya yin wata babbar illa ba. AT: "wannan ƙwaroa ɗaya" ko "ni, kuma ba zan iya cutar da ku ba kamar yadda ƙwaro ɗaya za ta iya"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Koma ka yi mini hidima a fada ta" ko 2) "Ka koma gidanka."
Anan idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. AT: "a yau kun ɗauki rayuwata da ƙima da daraja" ko "a yau kun nuna min cewa da gaske kuna girmama ni"
"ya kasance wauta sosai"
Kalmar "hannu" yana magana ta ƙarfin mutum. "Yahweh ya bani dama in kawo muku hari a yau" ko "Yahweh ya sanya ni a inda zan iya kashe ku a sauƙaƙe"
Anan idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. Duba yadda kayi fassarar irin waɗannan kalmomin a cikin 1 Sama'ila 26:21. AT: "Na dauki rayuwarku da matukar muhimmanci" ko "Na nuna muku a yau cewa da gaske nake girmama ku"
Anan idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. AT: "don haka Yahweh ya ɗauki rayuwata da tamani kuma" ko "don haka Yahweh ya ɗauki raina kamar yadda na ɗauki ranku da tamani"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari Yahweh ya albarkace ku"
1Dauda ya faɗi a cikin zuciyarsa, "Wata rana zan hallaka ta hannun Saul; ba abin da ya fiye mani sai in tsere zuwa ƙasar Filistiyawa; da haka Saul zai dena nema na cikin dukkan iyakar Isra'ila; ta haka zan kubce daga hannunsa."2Dauda ya tashi ya tsallaka can, shi da mazajensa ɗari shida da ke tare da shi, wurin Akish ɗan Mawok, sarkin Gat.3Dauda ya zauna tare da Akish a Gat, shi da mazajensa, kowanne mutum da iyalansa, Dauda tare da matayensa biyu, Ahinowam Yeziriya, da kuma Abigel Bakameliya, matar Nabal.4Da aka gaya wa Saul cewa Dauda ya tsere zuwa Gat, sai bai sãke neman sa ba.5Dauda ya cewa Akish, "Idan na sami tagomashi a idanunka, bari su bani wuri cikin ɗaya daga cikin biranen ƙasar, domin in zauna nan: donme bawanka za shi zauna cikin masarauta tare dakai?"6Sai Akish ya ba shi Ziklag a wannan rana; shi yasa Ziklag ta zama ta sarakunan Yahuda har wa yau.7Shekarun da Dauda ya zauna cikin ƙasar Filistiyawa shekara ɗaya ce cikakkiya da wata huɗu.8Dauda da mazajensa sukakaiwa wurare dabam dabam farmaƙi, suka hari Geshurawa, da Girziyawa, da Amalekawa; gama waɗannan al'ummai su ne asalin mazaunan ƙasar, idan kana tafiya zuwa Shur, har zuwa ƙasar Masar. Suna zama a nan wurin tun zamanun dã.9Dauda yakai wa ƙasar farmaƙi kuma bai bar namiji ko mace da rai ba; ya kwashi tumaki, da awakai, da jakuna, da raƙuma, da kumakayayyaki; sai ya dawo kuma zuwa Akish.10Akish zai ce, "Gãba da su waye yau kakai hari?" Dauda zai amsa, "Gãba da kudancin Yahuda," ko "Gãba da kudancin Yeramiyawa," ko "Gãba da kudancin Keniyawa."11Dauda bai bar namiji ko mace da rai domin yakawo su zuwa Gat ba, ya ce, "Sabodakada su yi magana game da mu, su ce 'Dauda ya yi kaza dakaza.'" Haka ya yi dukkan lokutan da ya ke zama a ƙasar Filistiyawa.12Akish ya amince da Dauda, yana cewa, "Ya sa mutanensa Isra'ilawa suna ƙyamarsa; zai zama bawana har abada."
Anan "zuciyarsa" yana magana wanda yake nufin kansa. AT: "Dauda ya yi tunani a ransa"
Kalmar "hannu" yana magana don mutum. AT: "kuɓuta daga gareshi"
"Dauda ya dauki mataki; ya wuce"
Waɗannan sunanyen maza ne.
Wannan sunan mace.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Wani ya gaya wa Saul" ko "Saul ya ji"
Anan idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 20:3. AT: "Idan na faranta muku" ko "Idan kun ɗauke ni da kyau"
Tunda Akish shine wanda zai "ba," wannan yana magana ta "Ina roƙon ka, ba ni wuri."
"ɗayan garuruwan da ke waje" ko "ɗaya daga cikin garuruwan da ke bayan birni"
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Ba na bukatar zama tare da ku a cikin birni tare da ku." ko "Ban isa in zauna anan tare da ku a cikin birin masarauta ba."
Wannan sunan birni ne a kudu maso yamma na yankin Yahuda.
kai hari da karɓar dukiya sau da yawa
Kungiyar mutanen da suke zaune a fili tsakanin Filistiya da Masar.
Anan ana amfani da "ku" azaman wakilin suna mara yankewa wanda ke nufin kowa. AT: "a kan hanyar da yawancin mutane suke zuwa Shur"
dangi daga kabilar Yahuda
ƙungiyar mutanen da suka rayu a ƙasar Midiya
ɗaya daga cikin birnin Filistiyawa biyar.
1Sai ya zama a wannan kwanaki Filistiyawa suka tara rundunar yaƙinsu domin yaƙi da Isra'ila. Akish ya cewa Dauda, "Ka san da cewar zaka fita tare da ni cikin runduna, kai da mazajenka."2Dauda ya cewa Akish, "Da haka zaka san abin da bawanka zai iya aikatawa." Akish ya cewa Dauda, "Da haka zan maishe ka mai tsarona na din-din din."3Yanzu dai Sama'ila ya mutu, kuma dukkan Isra'ila sun yi masa makoki suka kuma binne shi a Rama, a cikin birninsa. Haka kuma, Saul ya fanfari masu hurɗa da matattu ko da ruhohi.4Sai Filistiyawa suka tarakansu wuri ɗaya suka zo sukakafa sansani a Shunem; Saul kuma ya tara dukkan Isra'ila tare, suka kumakafa sansani a Gilbowa.5Lokacin da Saul ya ga rundunar Filistiyawa, sai ya ji tsoro, zuciyarsa kuma ta yi rawa sosai.6Saul ya yi addu'a ga Yahweh domin taimako, amma Yahweh bai amsa masa ba - ko ta mafarki, ko da Urim, kuma wurin annabawa ba.7Sai Saul ya cewa bayinsa, "Ku nemo mani mace wadda ta ke magana da matattu, domin in tafi wurinta in nemi shawararta." Bayinsa suka ce masa, "Duba, akwai wata mace a Endo wadda ta ke faɗin cewa tana magana da matattu."8Saul ya ɓaddakama, ya sanya wasu kaya, ya tafi, shi da mutum biyu tare da shi; suka tafi wurin matar da dare. Ya ce, "Ki duba mani, na roƙe ki, da ruhu, ki kuma kirawo mani duk wanda na faɗi maki."9Matar ta ce masa, "Duba, kasan dai abin da Saul ya yi, yadda ya kori waɗanda ke magana da matattu ko ga ruhohi. To me yasakake shirya wa raina tarko, ka sa ni in mutu?"10Saul ya rantse mata har ga Yahweh ya kuma ce, "Na rantse da ran Yahweh, babu hukuncin da zai same ki domin wannan."11Matar ta ce, "Wane ne kake so in kirawo maka?" Saul ya ce, "Kirawo mani Sama'ila."12Da matar ta ga Sama'ila, sai tayi ihu da babbar murya ta kuma yi magana da Saul, cewa, "Donme ka ruɗe ni? Gamakai Saul ne."13Sarkin ya ce ma ta, "Kada ki ji tsoro. Me kika gani?" Matar ta cewa Saul, "Na ga wani allah yana fitowa daga ƙasa."14Ya ce mata, "Yayakamaninsa ya ke?" Ta ce, "Tsohon mutum yana haurowa sama; yana sanye dakaya." Saul ya gane cewa Sama'ila ne, sai ya faɗi ƙasa fuskarsa ƙasa ya kuma nuna bangirmansa.15Sama'ila ya cewa Saul, "Donme ka dame ni har daka hauro da ni sama?" Saul ya amsa, "Na gaji sosai, Filistiyawa suna yaƙi da ni, Allah kuma ya rabu da ni kuma ya ƙi ya amsa mani, ko ta wurin annabawa, ko ta mafarkai. Saboda haka na kirawo ka, domin ka sanar da ni abin da zan yi."16Sama'ila ya ce, "Mene ne kake tambaya ta, tun da Yahweh ya bar ka, kuma ya zama abokin gãbarka?17Yahweh ya aiwatar maka da abin da ya faɗa zai yi. Yahweh ya raba mulkin daga hannunka ya kuma bayar ga wani - ga Dauda.18Domin bakayi biyayya da muryar Yahweh ba kuma baka aiwatar da fushinsa mai ƙuna bisa Amalekawa ba, shi kuma ya yi maka haka a wannan rana.19Duk da haka, Yahweh zai miƙa Isra'ila dakai cikin hannuwan Filistiyawa. Gobe kai da 'ya'yanka maza zaku kasance tare da ni. Yahweh kuma za ya miƙa rundunar Isra'ila cikin hannuwan Filistiyawa."20Sa'an nan Saul nan da nan ya faɗi da ƙarfinsa zuwa ƙasa da kuma fargaba saboda maganganun Sama'ila. Babu wani sauran ƙarfi a cikinsa, gama bai ci abinci ba dukkan yini, ko a wannan dare.21Macen ta zo wurin Saul ta ga cewa yana cikin babbar damuwa, Ta ce masa, "Duba, baiwarka ta saurari muryarka; Na ɗibiya raina a cikin hannuwana na kuma saurari maganganun daka faɗi mani.22Don haka yanzu, na roƙe ka, kai maka saurari muryar baiwarka macen, na kuma shirya maka abinci ɗan kaɗan a gabanka. Ka ci sabodaka maido da ƙarfi domin sa'ad da zakakama hanyarka."23Amma Saul bai yarda ba ya kuma ce, "Ba zan ci ba." Amma bayinsa, tare da macen, suka nace masa, ya kuma saurari muryarsu. Saboda haka ya tashi daga ƙasa ya zaunakan gado.24Matar tana da ɗan maraƙi mai ƙiba a cikin gidan; ta yi sauri ta yanka shi; ta ɗauki gari, ta cuɗa shi, ta kuma shirya gurasa da shi.25Takawo ga Saul da bayinsa, suka kuma ci. Sa'an nan suka tashi suka kuma yi tafiyarsu a wannan daren.
babban taron sojoji
Wataƙila Dauda yana son Akish ya yi tunanin cewa Dauda zai kashe Isra’ilawa da yawa, amma “abin da bawanka zai iya yi” yana iya nufin cewa Dauda yana shirin kashe Filistiyawa a maimakon haka. Gwada fassara saboda mai karatu ya iya ganin waɗannan ma'anoni guda biyu.
Marubucin yana ba da bayanan asali don shirya mai karatu don abubuwan da zasu biyo baya.
bayan da Dauda da Akish suka yi magana (1 Sama'ila 28: 2)
"ya tattara dukkan sojojinsa cikin Isra'ila tare"
waɗannan sunayen wurare ne
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna ƙarfafa tsananin tsoronsa. Anan an ambaci Saul da “zuciya”. AT: "ya firgita"
Babban firist ya ɗauki tsarkakakkun kuri'a da ake kira Urim da Tummin a cikin ƙyallensa, a cikin wata 'yar jaka ta alama, kusa da zuciyarsa.
Wannan sunan wani wuri ne.
Saul ya ɓad da kama saboda hanyar daga Gilbowa (1 Sama'ila 28:3) zuwa Endor (1 Sama'ila 28:5) ta ƙasar da Filistiyawa suna zaune a ciki. Ya yi kwana da rana ya je wurin matar bayan faɗuwar rana.
"Yi magana da matattu a gare ni"
Sauran ma'anoni masu yiwuwa sune 1) "ɗaya kamar Allah" ko 2) "alƙali" (1 Sama'ila 7:15).
Sama'ila yayi magana kamar masarautar abu ne na zahiri wanda za'a iya riƙe shi a hannu kuma wani mutum ya kama shi. AT: "an sanya ku don haka ba kwa zama sarki" ko "an nada wani mutum sarki a madadinku"
Sama’ila yayi magana kamar Isra’ilawa ƙaramar abu ce da Yahweh zai ba Filistiyawa, waɗanda yake magana da su kamar su mutum ɗaya ne. AT: "Yahweh zai ba Filistiyawa damar yin duk abin da suke so su yi muku da Isra'ilawa"
Wannan hanyar ladabi ce da za a ce Saul zai mutu. AT: "zai mutu"
Saul bai ci abinci ba a daren kafin ya yi tafiya daga Gilbowa zuwa Endor, ko da rana yayin da yake tafiya, ko kuwa da daddare ya ziyarci matar.
Wannan karin magana ne. "Zan iya mutuwa saboda na saurara" ko "Wani na iya kashe ni saboda na saurara"
Matar tana magana kamar wata ce don ta nuna cewa tana daraja Saul. Tana ambaton kanta da “muryarta” don jaddada abin da ta ce. AT: "muryata" ko "zan yi magana da ku"
ɗan maraƙi wanda aka girma kuma aka ciyar da shi don wadatar shi don biki na musamman
1Yanzu Filistiyawa sun taru tare dukkan rundunarsu a Afek; Isra'ilawa suka yi sansani kusa da magudanar ruwa da ke cikin Yezril.2Sarakunan Filistiyawa suka wuce a ɗari-ɗarinsu da kuma dubbai; Dauda da mazajensa suka wuce suna daga baya tare da Akish.3Sai sarakunan Filistiyawa suka ce, "Mene ne wannan Ibraniyawan ke yi a nan?" AKish ya cewa sauran sarakunan Filistiyawan, "Ba wannan ba ne Dauda, bawan Saul, sarkin Isra'ila, wanda ke tare da ni kwanakin nan, ko ace waɗannan shekaru, kuma ban same shi da wani laifi ba tun ranar da ya zo wurina har wa yau?"4Amma sarakunan Filistiyawa suka yi fushi da shi; suka ce masa, "Ka sa wannan mutum ya tafi, domin ya tafi wurin daka bashi, kadaka bar shi ya biyo mu zuwa filin dãga, domin kada ya juya ya zama maƙiyinmu cikin yaƙi. Don ta yaya wannan talikin zai yi sulhu da ubangidansa? Ba ta ɗaukar kawunan mutanen mu ba ne?5Ba wannan ba ne Dauda wanda aka yi wa waƙa a junansu cikin rawa, cewa, 'Saul yakashe dubbansa, Dauda kuma yakashe nasa dubbai goma'?"6Sai Akish ya kirawo Dauda ya kuma ce masa, "Na rantse da ran Yahweh, ka zama nagari, kuma fitarka da shigowarka tare da ni cikin runduna mai kyau ne a gani na; gama ban iske wani laifi gare ka ba tun randa ka zo wurina zuwa wannan rana.7Sai ka juya yanzu ka kuma tafi cikin salama, domin kada ka yi wa sarakunan Filistiyawa laifi."8Dauda ya cewa Akish, "Amma me na yi? Mene ne ka samu a cikin bawanka duk sa'ad da nake tare da kai zuwa wannan rana, da har ba zan je inyi yaƙi da maƙiyan ubangidana sarki ba?"9Akish ya amsa ya kuma cewa Dauda, "Na san da cewa kai marar laifi ne a idanuna kamar mala'ikan Allah; duk da haka sarakunan Filistiyawa suka ce, 'Ba zai haura tare da mu ba zuwa yaƙin.'10Saboda haka sai ka tashi da sassafe tare da bayin ubangidanka waɗanda suka zo tare da kai; da zarar ka tashi da asussuba ka kuma sami haske, ka tafi."11Sai Dauda ya tashi da sauri, shi da mazajensa, don su tafi da safe, su dawo ƙasar Filistiyawa. Amma Filistiyawan suka haura zuwa Yezril.
karamin rafin ruwa mai kwarara bisa dabi'a daga kasa
Rukunin ɗari ɗari da na dubbai suka wuce gaba, sa'an nan Akish da mataimakansa, sa'an nan Dauda, da mutanensa, da sauran sojojin Filistiyawa, waɗanda suke tsaron Akish.
Hanyoyin da za a iya fassara wannan tambaya ta magana a matsayin magana su ne AT: 1) "Bai kamata ku bar waɗannan Ibraniyawa, abokan gabanmu su kasance tare da mu ba." ko 2) "Ku gaya mana su wane ne waɗannan Ibraniyawa."
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Ban san komai ba game da abin da ya yi ba dai-dai ba" ko "Ina matukar farin ciki da shi"
"kada ku bari sojojinsa su shiga tare da sojojinmu a kan makiyanmu"
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. Anan “ɗaukar kawunan” yana nufin kissa don kisan kai. AT: "Hanya mafi kyau da David zai sasanta da maigidansa shine ta hanyar kashe sojojinmu!"
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Kada ku aminta da David" shi ne wanda suka raira waƙa ga juna a cikin rawa, suna cewa, "Saul ... dubun dubun! "
"Na yi farin ciki da ka fita ka shigo tare da ni da runduna ta" ko "Yana da kyau ka tafi ko'ina tare da ni da runduna na"
"duk da cewa wannan gaskiya ne, wannan ya fi mahimmanci: hakimai" ko "duk da haka, sarakuna"
"ana iya gani da asuba"
1Ya zama kuma, da Dauda da mazajensa suka iso Ziklag a rana ta uku, da Amalekawa suka kawo farmaki bisa Negeb da kuma kan Ziklag. Suka kai wa Ziklag hari, suka ƙona ta,2suka kwashe matayen da kowa da ya ke ciki, da manya da ƙanana. Ba su kashe kowa ba, amma suka kwashe suka yi tafiyarsu.3Lokacin da Dauda da mazajensa suka iso birnin, an ƙone, kuma matayensu, da 'ya'yansu maza, da 'ya'yansu mata an ɗauke su zuwa bauta.4Sa'an nan Dauda da mutanen da ke tare da shi suka tãda murya suka yi kuka har sai da babu wani sauran ƙarfi kuma da za su yi kuka.5Aka kwashe matan Dauda guda biyu, Ahinowam Yeziriya, da Abigel matar Nabal mutumiyar Karmel.6Dauda ya dãmu ƙwarai, gama mutanen suna magana game da su jefe shi da duwatsu, gama dukkan mutanen suna ɓacin rai, kowanne mutum domin 'ya'yansa maza da mata; amma Dauda ya ƙarfafa kansa cikin Yahweh, Allahnsa.7Dauda ya cewa Abiyata ɗan Ahimelek, firist, "Na roƙe ka, ka kawo mani falmara a nan wurina." Sai Abiyata ya kawo falmarar wurin Dauda.8Dauda ya yi addu'a ga Yahweh domin bishewa, cewa, "Idan na bi wannan mayaƙan, zan sha kansu?" Yahweh ya amsa, "Bi su, domin lallai za ka sha kansu, kuma tabbas za ka sake ƙwato dukkan abubuwan."9Sai Dauda ya tafi, shi da mazajensa ɗari shida waɗanda ke tare da shi; suka iso magudanar Beso, inda waɗanda aka bari suka zauna.10Amma Dauda ya ci gaba da runtumar su, shi da mazaje ɗari huɗu; gama ɗari biyu sun tsaya a baya, wato waɗanda ƙarfinsu ya gãza da baza su iya haurawa zuwa magudanar Beso ba.11Suka gamu da wani Bamasare cikin saura suka kawo shi ga Dauda; suka ba shi gurasa, ya kuma ci; suka ba shi ruwa ya sha;12sai kuma suka ba shi gutsuren wainar 'ya'yan ɓaure da curin kauɗar inabi guda biyu. Bayan da ya ci, ƙarfinsa ya dawo kuma, gama bai ci gurasa ba ko ya sha wani ruwa har kwana uku da yini uku.13Dauda ya ce masa, "Kai na wane ne? Daga ina ka fito?" Ya ce, "Ni ɗan matashin ƙasar Masar ne, bawan Ba-amaleke; ubangidana ya baro ni domin kwana uku da suka shige rashin lafiya ta same ni.14Mu ka kai farmaƙi a yankin Negeb na Keretiyawa, da abin da ya ke na Yahuda, da kuma Nageb na Kaleb, kuma muka ƙona Ziklag."15Dauda ya ce masa, "Za ka kawo ni zuwa wurin waɗannan maharan?" Bamasaren ya ce, "Ka rantse mani ga Allah da cewar ba zaka kashe ni ko ka bashe ni a cikin hannuwan ubangidana ba, ni kuma zan kawo ka wurin waɗannan maharan."16Da Bamasaren ya kawo Dauda wurin, maharan na nan barbaje a dukkan ƙasar, suna ci suna sha suna rawa saboda dukkan ganimar da suka kwaso daga cikin ƙasar Filistiyawa da kuma ƙasar Yahuda.17Sai Dauda ya kai masu hari tun daga wayewar gari har yammancin da gari ya waye. babu mutum wanda ya tsira sai dai 'yan matasa guda ɗari, waɗanda suka haura bisa raƙuma suka kuma gudu.18Sai Dauda ya maido da dukkan abin da Amalekawa suka ɗauke; kuma Dauda ya ƙubutar da matansa biyu.19Babu abin da ya ɓace, ko ƙarami ko babba, ko 'ya'ya maza ko 'ya'ya mata, ko kayan ganima, ko wani abu da maharan suka ɗauko wa kansu.20Dauda ya dawo da komai. Dauda ya ɗauko dukkan garken da kuma dabbobin, waɗanda mazajen suka koro gaba da sauran garkunan. Suka ce, "Wannan ganimar Dauda ce."21Sai Dauda ya komo wurin sauran ɗari biyun da ƙarfinsu ya gãza ba su bi shi ba, waɗanda sauran suka sa su jira a magudanar Beso. Waɗannan mazajen suka zo domin su tarbi Dauda da kuma mutanen da ke tare da shi. Da Dauda ya iso wurin mutanensu, ya gaishe su.22Sai dukkan mugayen mutanen da marasa amfani da ke cikin waɗanda suka tafi tare da Dauda suka ce, "Domin waɗannan mazajen ba su tafi tare da mu ba, ba za mu ba su komai daga cikin ganimar da muka samu ba. Sai dai kowanne ɗaya daga cikinsu ya ɗauki matarsa da 'ya'yansa, ya bishe su, su tafi."23Sa'an nan Dauda ya ce, "Ba za ku yi haka ba, 'yan'uwana, da abin da Yahweh ya ba mu. Ya kiyaye mu ya kuma bayar da maharan da suka tayar mana a hannuwanmu.24Waye zai saurari ku a kan wannan zance? Gama kamar yadda rabon kowanne da ya tafi yaƙin, haka zaya zama rabon duk wadda ya jira wurin kaya; za su sami rabo dai-dai da kowa."25Haka ya ci gaba da zama daga wannan rana har wa yau, gama Dauda ya maida haka doka da kuma ka'ida a Isra'ila.26Da Dauda ya kai Ziklag, ya aika daga cikin ganimar zuwa ga shugabannin Yahuda, zuwa ga abokansa, cewa, "Duba, ga kyauta domin ku daga ganimar maƙiyan Yahweh."27Ya kuma aika da waɗansu zuwa ga shugabannin da ke a Betel, da kuma waɗanda ke a Ramot na Kudu, kuma ga waɗanda suke daga Jattir,28kuma ga waɗanda ke cikin Arowa, kuma zuwa ga waɗanda ke a Sifmot, kuma ga waɗanda suke a Ishtemowa.29Ya kuma aika zuwa ga shugabannin da ke cikin Rakal, kuma zuwa ga waɗanda ke cikin biranen Yeramilawa, kuma ga waɗanda ke cikin biranen Kenawa,30kuma ga waɗanda ke cikin Homa, da kuma waɗanda ke zama a Borashan, ga kuma waɗanda ke cikin Atak,31ga kuma waɗanda ke cikin Hebron, ga kuma dukkan wuraren da Dauda da kansa da mazajensa ke zuwa kodayaushe.
Mai yiwuwa su ne 1) "duka mutane marasa muhimmanci da mutane masu muhimmanci" ko 2) "duka ƙanana da manyan jiki."
Waɗannan galibi sojojinsa ne.
Dauda ya sami ƙarfi a wurin Yahweh bayan harin.
Kalmar "ɓacin" kwatanci ne na sha'awar tawaye. Kalmar "ruhu" magana ne don mutum. AT: "duk mutanen sun kasance a shirye don yin tawaye ga Dauda" ko "duk mutanen sun yi murna ƙwarai"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Dauda ya yi ƙarfin zuciya domin ya san Yahweh Allahnsa zai taimake shi" ko 2) "Yahweh Allahnsa ya ƙarfafa Dauda."
Dauda ya nemi Yahweh game da farmakin da aka kai wa mutanensa.
AT: "Dauda ya yi addu'a cewa Yahweh ya gaya wa Dauda abin da ya kamata ya yi"
Sun gaji da samamen da suke kawowa yanzu suna bin Amalekawa. Ba su da ƙarfin ci gaba.
An bar shi a can don ya mutu daga ƙungiyar ɓarkewar Amalek.
Dauda ya tambayi bawan Bamasaren
ƙungiyar mayaka masu dauke da makamai wadanda suke kaiwa mutane hari ko wurare ba zato ba tsammani
Anan "hannaye" suna nufin sarrafawa. AT: "ba zaku ... keta amanar da nake da ita a gare ku ba ta hanyar barin maigidana ya sake mallake ni"
lokaci bayan rana ta faɗi har zuwa sama duhu
"Babu wani abu da Amalekites suka sata da aka rasa"
Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) "ba mutane ne marasa muhimmanci ba ko kuma manyan mutane" ko 2) "ƙanana ne a zahiri ko kuma babba." Duba yadda kayi fassarar irin waɗannan kalmomin a cikin 1 Sama'ila 30:1.
"yayi musu magana cikin fara'a"
Za a iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Ba wanda zai saurare ku a cikin wannan lamarin."
"za a tabbatar duk sun karbi kudi dai-dai"
Waɗannan su ne sunayen garuruwa.
Waɗannan su ne sunayen garuruwa.
Waɗannan su ne sunayen kungiyar mutane.
1Yanzu Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra'ila. Mazajen Isra'ila suka gudu daga fuskar Filistiyawa suka kuma faɗi matattu a Tsaunin Gilbowa.2Filistiyawa suka runtumi Saul da 'ya'yansa. Filistiyawa suka kashe Yonatan, Abinadab, da Malkishuwa, 'ya'yansa maza.3Yaƙin ya yi zafi gãba da Saul, kuma masu harbin bãka suka sha kansa. Yana cikin ƙunci da zafi sabili da su.4Sai Saul ya cewa mai ɗaukar masa makamai, "Zaro takobinka ka soke ni da ita. In ba haka ba, waɗannan marasa kaciyar zasu zo su wulaƙanta ni." Amma mai ɗaukar masa makamai ya ƙi, gama yana jin tsoro. Sai Saul ya ɗauki takobinsa ya faɗi bisanta.5Da mai ɗaukar masa makamai ya ga Saul ya mutu, sai shi ma ya ɗauki ta sa takobin ya faɗa kanta ya mutu da shi.6Haka Saul ya mutu, 'ya'yansa uku, da kuma mai ɗaukar masa makamai - waɗannan mutanen dukka suka mutu tare rana ɗaya.7Lokacin da mutanen Isra'ila da ke a wancan ɓangaren kwarin, da kuma waɗanda ke gaba da Yodan, suka ga cewa mazajen Isra'ila sun gudu, kuma Saul da 'ya'yansa maza sun mutu, sai suka ƙaurace wa ƙauyukansu suka gudu, sai kuma Filistiyawa suka zo suka zauna cikinsu.8Sai ya zama kuma washegari, da Filistiyawa suka zo domin su washe kayan matattun, sai suka ga Saul tare da 'ya'yansa maza uku sun faɗi a Dutsen Gilbowa.9Suka yanke kansa suka kuma cire kayan yaƙinsa, suka kuma aika 'yan saƙo cikin ƙasar Filistiyawa ko'ina domin su kai labarai ga haikalin gumakansu kuma ga mutanensu.10Suka ajiye rigar yaƙinsa cikin haikalin Ashtoret, kuma suka rataye jikinsa ga ganuwar birnin Bet Shan.11Lokacin da mazaunan Yabesh Giliyad suka ji abin da Filistiyawa suka yi wa Saul,12dukkan mazaje 'yan yaƙi suka tashi suka yi tafiya dukkan dare suka ɗauki jikin Saul da kuma jikkunan 'ya'yansa daga ganuwar Bet Shan. Suka tafi Yabesh suka ƙona su a can.13Sai Suka ɗauki ƙasusuwansu suka binne su a ƙarƙashin itaciyar tamarisk a Yabesh, suka yi azumi na kwana bakwai.
Wannan yakin ya samo asali ne sakamakon rikici tsakanin Dauda da Filistiyawa a cikin 1 Sama'ila 29:1. Marubucin ya gama ba da labarin Dauda wanda ya fara a 1 Sama'ila 30:1, yanzu kuma ya ba da labarin yaƙi tsakanin Isra'ilawa da Filistiyawa.
"ya kori Saul da 'ya'yansa maza uku"
Wannan karin magana ne. "Sojojin Saul sun fara rashin nasara a yakin"
Mai ɗaukar makamai ya ɗauki babbar garkuwar babban kwamandansa da wasu makamai. Ya kare kwamandan yayin yaƙi.
Ba a yi muku kaciya ba alama ce ta baƙi. AT: "waɗannan mutanen da ba a yi musu kaciya ba" ko "waɗannan mutanen da ba Isra'ilawa ba"
"ya kashe kansa da takobinsa"
ya zauna a garuruwan da Isra'ilawa suka bari
kwashe kayan yaƙin da makaman daga gawarwakin Isra’ilawa
"duk yankuna na ƙasar Filistiyawa"
"yin magana da labarai a cikin gidajen ibada da kuma mutane"
Wannan sunan wani gari ne. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 1 Sama'ila 11: 1.
"yadda Filistiyawa suka wulakanta Saul"
1Bayan mutuwar Saul, Dauda ya dawo daga harin Amelikawa ya kuma zauna a Ziglak kwana biyu.2A rana ta uku, wani mutum ya zo daga sansanin Saul da tufafinsa a yage da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dauda sai ya kwanta rub da ciki a ƙasa ya miƙe jikinsa ya yi ruku'u a gabansa.3Dauda ya ce masa, "Daga ina ka fito?" Ya amsa, "Na kubce daga sansanin Isra'ila ne."4Dauda ya ce masa, Idan ka yarda ka gaya mani yadda abubuwa suka kasance." Ya amsa, "Mutane sun gudu daga yaƙi. Da yawa sun faɗi kuma da yawa sun mutu. Saul da Yonatan ɗansa su ma sun mutu."5Dauda ya ce ma saurayin, "Yaya ka sani cewa Saul da Yonatan ɗansa sun mutu?"6Saurayin ya amsa, "Sa'a ce na ci. ya zamana ne ina kan Dutsen Gilbowa, sai ga Saul yana jingine akan mashinsa, karusai da mahaya suka kusa rutsasu.7Saul ya juya ya gan ni ya kuma kira ni da murya. Na amsa, 'Ga ni.'8Ya ce mani, "Waye kai?" Na amsa masa, 'Ni Ba-amelike ne.'9Ya ce mani, ' Idan ka yarda ka tsaya a kaina ka kasheni, gama zafin azaba ya sha kaina, amma duk da haka rai yana ciki na'10Saboda haka na tsaya a kansa na kasheshi, domin na sani ba zai rayu ba bayan ya faɗi. Sa'an nan na ɗauki kambin da ke kansa da ɗamarar da ke damtsensa kuma, na kawo su nan gunka, ubangidana."11Sai Dauda ya ƙeƙƙece tufafinsa dukkan mutanen da ke tare da shi suka yi haka su ma.12Suka yi makoki, da kuka, kuma suka yi azumi har yamma saboda Saul, domin ɗansa Yonatan, domin mutanen Yahweh, domin kuma gidan Isra'ila sabili da sun faɗi ta hannun takobi.13Dauda ya cewa saurayin, 'Daga ina ka ke?' Ya amsa, 'Ni yaron wani baƙo ne a ƙasar, Ba-amaleke."14Dauda ya ce masa, "Me ya sa ba ka ji tsoron kashe shafaffen sarki na Yahweh da hannunka ba?"15Dauda ya kira ɗaya daga cikin samarin ya ce, "Tafi ka kashe shi." Sai wannan mutumin ya tafi ya buga shi ƙasa. Sai Ba-ameliken ya mutu.16Sai Dauda ya cewa mataccen Ba'ameliken, '" Alhakin jininka na kanka domin bakinka da kansa yana shaida gãba da kai ya ce, 'Na kashe shafaffen sarki na Yahweh.'"17Sa'an nan Dauda ya yi wannan waƙar makoki game da Saul da Yonatan ɗansa.18Ya bada doka ga mutane su koyar da Waƙar Bãka ga 'ya'yan Yahuda, wanda aka rubuta a Littafin Yashar.19"Ɗaukakarki, Isra'ila, ya mutu, an yi kisa a tuddanki! Aiya jarumawa sun faɗi!20Kada ku faɗa a Gat, kada ku yi shelarsa a titunan Askelon, domin kada 'yan'matan Filistiyawa su yi farinciki, domin kada 'yan'matan marasa kaciya su yi biki.21Duwatsun Gilbowa, kada raɓa ko ruwan sama su kasance a kanku, ko gonaki masu bada hatsi domin baiko, gama a nan aka lalata garkuwar ƙarfafa. Garkuwar Saul ba a ƙara shafe ta da mai ba.22Daga jinin waɗanda aka kashe, daga jikin ƙaƙƙarfa, bãkan Yonatan bai juya ba, kuma takobin Saul bata dawo wofi ba.23Saul da Yonathan ƙaunatattu ne masu alheri a rayuwa, a mutuwarsu ba a raba su ba. Sun fi gaggafai zafin gudu, sun fi zakoki ƙarfi.24Ku 'yan'matan Isra'ila, ku yi kuka domin Saul, wanda ya suturtar daku cikin shunayya da duwatsu masu daraja da kayan zinariya masu ƙayatarwa a tufafinku.25Aiya jarumawa sun faɗi tsakiyar yaƙi! An kashe Yonatan a tuddanki,26Ina da damuwa domin ka, ɗan'uwana Yonatan. Amintacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abin al'ajibi ne, ya zarce ƙaunar mata.27Aiya jarumawa sun faɗi, makaman yaƙi kuma sun lalace!"
Wannan shi ne sunan birnin da ke kudacin Yahuda.
"Bayan kwana uku"
Cikin wannan al'ada, mutum ya yage tufafinsa ya kuma sa ƙura a kansa almace na makoki.
Wannan alamace ta biyayya ga Dauda, sarkin Isra'ila.
Ma'ana mai yiwuwa na kamar haka 1) "Da yawa an ji musu ciwo, da yawa kuma an kashe" ko 2) "Da yawa an ji musu ciwo an kuma kashe."
Wannan magana na nanata cewa mutumin bai yi shirin haduwa da Saul ba.
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) Ƙarfin Saul ya ragu kwarai da gaske, don haka sai ya yi amfani da mãshinsa don ya taimaki kansa ko 2) Saul na ƙoƙari ya kashe kansa ta wurin faɗiwa a kan mãshinsa.
Waɗannan ambaton kai tsaye ana iya bayyana su azaman magana kai tsaye. AT: "Ya tambaye ni ko ni wanene, kuma na gaya masa cewa ni Ba'amalake ne"
Waɗannan sune mutanen da Dauda ya kai musu hari a cikin 2 Sama'ila1:1.
An yi magana game azabar Saul sai ka ce wani abu ne mummuna da ta kama shi. AT: "Ina sha matuƙar azaba"
Wannan karin magana na nufin cewa yana da rai.
"ko ya aka yi zai mutu"
Dauda da mutanensa sun yayyage tufafinsu alama ce na makoki saboda da mutawar Sarki Saul.
Maganganun nan biyu a takaice na nufin abu ɗaya. Kalman nan "gida" na wakiltar zuriyar Isra'ila. Amma "mutane" da "gida" mai yiwuwa suna wakiltar sojojin Isra'ila. AT: "domin sojojin Isra'ila"
Wannan shi ne sunan Allah da ya banyana wa mutanensa cikin Tsohon Alƙawari. Duba translationWord (tW) game da yadda za a juya wannan suna Yahweh.
Anan "faɗuwa" hanya ce mai ladabi da ke nufin kashewa. Har ila yau, "takobi" yana wakiltar yaƙi. Wannan a nan yana nufin "an kashe shi." AT: "sun mutu a yaƙi" ko "abokan gaba sun kashe su a yaƙi"
Mutumin ya riga ya bayana cewa shi Ba'amaleke ne cikin 2 Sama'ila 1:8. Dauda ya yi wannan tambayar don ya tabbatar da wannan saboda muhimmancin shari'ar da Dauda zai yi wa mutum.
Ana amfani da wannan tambayar ta zance don tsawata wa mutumin. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Ya kamata ka ji tsoron Yawe, kada kuma ka kashe shafaffensa ... hannunka!"
Wannan na nufin Saul wanda Allah ya zaɓa.
Wannan jumlar na nufin cewa ka yi abu da kanka. AT: "kanka"
Wannan karin magana yana nufin "kashe shi."
A nan "jini" na nufin "zub da jini". A nan "kanka" na nufin mutumin, ma'ana kuwa ita ce ka ɗauki alhakin. AT: "Alhakin mutuwarka na wuyar ka" ko "Ka jawo wa kanka mutuwa"
A nan "bakin ka" na nufin mutumin kansa.
Dauda ya yi waƙa ta makoki saboda Saul da kuma Yonatan.
Wannan shi ne kan waƙar.
Wannan bayani ne da aka ƙãra don a gaya wa mai karatu abin da ya faru da wakar a nan gaba.
Kalmar "Yashar" na nufin "adali." AT: "Littafin Adali."
"darajar ki" na nufin Saul.
Maganan nan "jarumawan" na nufin Saul da Yonatan.
Kalmar "fãɗĩ" a nan na nufin "mutu"
Waɗannan maganganu biyu suna nifin abu ɗaya, an maimaita a matsayin wata bagaren waƙar.
Gat da Ashkelon su ne manyan biranen Filistiyawa. Filistiyawan sun kashe Saul da Yonatan.
Waɗannan maganganu biyun na nufin abu ɗaya ne, suna na kuma ruwaita shi a matsayin wata bangaren waaƙar.
Wannan magana na nufin mutanen da ba su bin Yahweh, kamar Filistiyawan.
Dauda ya yi magana kai tsaye da "Tsaunin Gilbowa" sai ka ce sun kassa kunne ga waƙarsa.
Dauda ya la'anta kasa in Sarki Saul ya mutu cikin yaƙi. Ya yi wannan duk domin ya girmama Saul, keɓaɓɓe Sarki na Allah.
Anan "jarumin" na nufin Saul. An la'anta garkuwar domin ta faɗa a ƙasa, domin kuma an wasa jinin sarkin a kan ta.
An yi garkuwar Saul da fata. Don a lura da garkuwar a kan shafe ta da mai. AT: "Babu wanda zai lura da garkuwar Saul kuma"
An bayana cewa Saul da Yonatan su na da ban tsoro, su kuma ƙarfafan jarumai ne.
An yi magana game da takobin Saul sai ka ce abu ne da ke raye, kuma zai iya dawowa da kanshi. Maimaƙon ta dawo hannun wofi, sai ta dawo ta na ɗauke da jini abokan gãban Saul.
An yi amfani da maganan nan "ba raba su" don a nanata cewa a kullayomi suna tare. AT: "har mutuwa suna tare"
An yi amgana game da Saul da Yonatan sai ka ce sun fi gaggafai sauri sun kuma fir zakoki ƙarfi.
"wanda ya tanaɗa muku sutura da kayan ado masu kyau." Waɗannan maganganu biyun suna da ma'ana kusan iri ɗaya wanda ke bayana cewa an tanaɗa wa mataye sutura masu kyau da ban sha'awa, masu tsaɗa kuma.
An ruwaita wannan a cikin aya 27 don a nanata cewa mafi kyau daga cikin mayaƙan Isra'ila sun mutum. AT: "Jarumai sun mutu a cikin yaƙi"
A nan "jarumawa" na nufin Saul da Yonatan ko kuwa dukka sojojin Isra'ila. AT: "jarumai"
Wannan wata hanya ce na faɗin cewa "sun mutu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yonatan ya mutu cikin yaƙi" ko kuwa "Abokan gãban sun kashe Yonatan"
Wannan ɓangaren waƙan Dauda ya cigaba game da Tsaunin Gilbowa kamar yadda ya fara a cikin 2 Sama'ila 1:21.
An yi amfani da kalman nan "ɗan'uwa" da nufin cewa su abokai ne na kwarai.
An yi amfani da "ƙauna" a nan da nufin abokantaka da biyayya. Biyayyar Yonatan ga Dauda ya fi biyayyar da mace ke yi wa mijinta da kuma 'ya'yanta.
1Bayan wannan Dauda ya tambayi Yahweh ya ce, 'Ko in haura zuwa ɗaya daga cikin biranen Yahuda?" Yahweh ya amsa masa, "Ka haura." Dauda ya ce, "Wanne birnin zan je?" Yahweh ya amsa, "Zuwa Hebron."2Sai Dauda ya tafi Hebron da matayensa guda biyu, Ahinowam daga Yezril, da Abigel daga Karmel, gwauruwar Nabal.3Dauda ya kawo mutanen da ke tare da shi, waɗanda kowannen su ya kawo nasa iyalin, zuwa biranen Hebron inda suka fara zaunawa.4Sa'an nan mutane daga Yahuda suka zo suka naɗa Dauda sarki bisa gidan Yahuda. Aka cewa Dauda, '"Mutanen Yabes Giliyad ne suka bizne Saul."5Sai Dauda ya aiki manzanni ga mutanen Yabes Giliyad suka kuma ce masu, "Yahweh ya albarkace ku, tunda ku ka nuna wannan riƙon amana ga ubangidanku Saul har ku ka bizne shi.6Bari yanzu Yahweh ya nuna maku alƙawarin riƙon amana da aminci. Ni kuma zan yi maku wannan alheri domin kun yi wannan abu.7Yanzu dai, bari hannuwanku su ƙarfafa; ku yi ƙarfin hali domin Saul ubangidanku ya mutu kuma gidan Yahuda sun naɗa ni shafaffen sarki bisan su."8Amma Abna ɗan Nã, sarkin yaƙin rundunar Saul, ya ɗauki Ishboshet ɗan Saul ya kuma kawo shi Mahanam,9Ya naɗa Ishboshet sarki bisa Giliyad, Ashar, Yazril, Ifraim, Benyamin, da kuma bisa dukkan Isra'ila.10Ishboshet ɗan Saul, yana da shekaru arba'in da ya soma mulki bisa Isra'ila, ya kuma yi mulki shekara biyu. Amma gidan Yahuda suka bi Dauda.11Lokacin da Dauda ke sarki cikin Hebron bisa gidan Yahuda shekara bakwai ne da wata shida.12Abna ɗan Nã, da barorin Ishboshet ɗan Saul, su ka tafi daga Mahanayim zuwa Gibiyan.13Yowab ɗan Zeruya da barorin Dauda suka fita suka gamu da su a tafkin Gibiyan. A nan suka zauna, ɗaya ƙungiyar a ɗaya gefen tafkin ɗayan kuma a ɗaya wancan gefen.14Abna ya cewa Yowab, "Bari samarin su tashi su yi gãsa a gabanmu." Sai Yowab ya ce, "Bari su tashi."15Sai samarin suka tashi suka tattaru tare, sha biyu domin Benyami da Ishboshet ɗan Saul, kuma sha biyu daga barorin Dauda.16Kowanne ya danƙe abokin gasarsa a kai ya soke gefen cikin ɗan'uwansa da takobi, sai su ka faɗi ƙasa tare. Shi ya sa aka kira wurin nan da Ibraniyanci, "Helkat Hazzurim." ko "Filin Takkuba" wanda ya ke cikin Gibiyan.17Yaƙin ya yi zafi ainun a ranar nan kuma aka buga Abna da mutanen Isra'ila a gaban barorin Dauda.18'Ya'ya maza uku na Zeruya suna wurin: Yowab, Abishai, da Asahel. Asahel mai zafin gudu da ƙafa ne kamar barewar jeji.19Asahel ya sheƙa da gudu bayan Abna ya bishi kurkusa ba ratsewa wani gefen.20Abna ya waiga bayansa ya ce, "Kai ne kuwa Asahel?" Ya amsa, "I, ni ne."21Abna ya ce masa, "Ka juya zuwa gefenka na dama ko hagunka, ka cafke ɗaya daga cikin samarin ka karɓe makaminsa." Amma Asahel ya ƙi ratsewa wani gefen.22Sai Abna ya sãke cewa Asahel, "Ka dena bi na donme zan buga ka ƙasa? Ƙaƙa kuma zan fuskanci, ɗan'uwanka Yowab?"23Amma Asahel ya ƙi ratsewa, saboda haka Abna ya soki jikinsa da kan mashinsa marar kaifi har ma mashin ya fito ta wancan gefen. Asahel ya faɗi ya mutu. Ya zamana fa duk wanda ya iso inda Asahel ya faɗi ya mutu, sai ya dakata ya tsaya shuru.24Amma Yowab da Abishai suka bi Abna. Sa'ad da rana take faɗuwa, suka iso tudun Amana, da ke kusa da Giya a hanyar da ta bi ta jejin Gibiyon.25Mutanen Benyaminu suka haɗa kansu gaba ɗaya suka goyi bayan Abna suka tsaya a kan tudu.26Sai Abna ya kira Yowab ya ce, "Dole ne takobi ya hallakar har abada? Ba ka sani zai zama da ɗaci a ƙarshe ba? Har yaushe zai zamana kafin ka gaya wa mutanenka su janye daga fafarar 'yan uwansu?"27Yowab ya amsa, "Na rantse da Yahweh, hakika da baka faɗi haka ba, da sojojina sun fafari 'yan 'uwansu har zuwa safiya!"28Sai Yowab ya busa ƙaho, mutanensa duk suka tsaya suka dena fafarar Isra'ila, kuma ba su sake yin faɗa ba.29Abna da mutanensa suka yi ta tafiya dare farai cikin Araba. Suka haye Yodan, suka yi ta tafiya dukkan safiyan nan, sa'annan ne suka kai Mahanayim.30Yowab ya juyo daga fafarar Abna. Ya tara dukkan mutanensa, cikinsu aka rasa Asahel da sojojin Dauda guda goma sha tara.31Amma mutanen Dauda sun riga sun kashe mutane 360 na Benyamin da ke tare da Abna.32Sai suka ɗauki Asahel suka binne shi cikin kabarin mahaifinsa, da ke a Baitalami. Yowab da mutanensa suka yi tafiya dare farai, gari kuma ya waye masu a Hebron.
"Bayan Dauda ya yi makokin mutuwar Saul da Yonatan a cikin yaƙi"
A wannan lokacin Dauda ya cikin birnin Ziglag. Dauda ya yi amfani da kalman nan "haura" domin Ziglag na ƙasa da Yahuda. AT: "tafi zuwa ɗaya daga cikin biranen Yahuda"
A wannan lokacin Dauda yana cikin birnin Zigkag. Mai bada labarin ya yi amfani da kalman nan "haura" saboda Ziglaga na ƙasa da Hebron. AT: "Dauda ya tafi zuwa Hebron da matansa biyu"
Cikin wannan alama sun zuɓa mai a kan Dauda don nuna cewa an zaɓe shi ya zama sarki.
An yi amfani da "gida" a matsayin "kabila" AT: "kabilan Yahuda"
Wannan sunan gari ne cikin yankin Giliyad.
Dauda ya yi magana da mutanen Yabesh Giliyad.
Sun binne Saul.
A nan "hannuwa" na nufin mutanen Yabesh Giliyad. AT: "yi ƙarfin hali"
Cikin wannan alama sun zuɓa mai a kan Dauda don nuna cewa an zaɓe shi ya zama sarki.
Waɗannan sunaye mazaje ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
An yi magana game da yin biyayya ga mulkin Dauda sai ka ce "bin" sa. AT: "kabilan Yahuda sun yi wa Dauda biyayya a matsayin sarkin su"
Anan "gida" ana amfani da ma'anar "ƙabila."
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan hanyar ladabi ce ta cewa sun mutu. AT: "dukansu sun mutu"
Wannan wata suna ne da aka bayar don a tunashe mutane abin da ya faru.
Zai zama da taimakon a bayana a fili cewa wannan yaƙi ce ƙwarai da gaske da ya shefe samarai maza. AT: "Sai sauransu sun fara yaƙi. Yaƙi ce ƙwarai da gaske a ranar"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
A nan an kwatanta Asahel da barewar, wata dabba da ke gudu sosai. AT: "Asahel ya iya guduwa sosai"
Wannan ƙaramin dabba ne mai kafa hudu, yana da dogayen kahonni biyu a kan sa, yana kuma gudu sosai.
A nan "ratsa zuwa wani gefe ba" an bayana shi hakaon don a nanata yadda ya bi sawun Abna. AT: "bishi duk inda ya tafi"
Wannan sunan mutum na miji ne.
"Ka bar bi na ... ka bar bin Abna"
Abna yana roƙon Asahel ya kashe ya kuma cafke sojan da ba zai zama da lahani kamar Abna ba. Ba ya so ya kashe Asahel. AT: "yi faɗa da wani soja ka kuma karɓi kayan yakinsa"
Ana amfani da wannan tambayar ne don gargaɗin Asahel game da haɗarin da ya fuskanta. "Bugawa ƙasa" hanya ce mai ladabi da ake cewa "a kashe." AT: "Ba na so in kashe ku"
Wannan tambayar na nanata cewa Abnar ba ya so ya yi faɗa ko kuma ya kashe Asahel domin zai ɓata dangantakansa da Yowab. A nan "fuskanci ... Yowab" karin magana ne da ke nufin cewa zai ji kunyar fuskanci Yowab. AT: "zan ji kunyar fuskanci ɗan'uwan ka Yowab"
Wannan na nufin "dakata" ko "bar bi"
Wannan na nufin wurin riƙe mashin, bai yi tsini ba har da zai iya sokin wani abu. Yana iya nufin cewa Abnar yana ƙoƙari ya hana Asahel bin sa, ba ya so ya kashe shi.
Wannan sunan mutum namiji ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
"yi ihu" ko "yi kururuwa'
Wannan tambayar na nanata cewa yaƙin ya cigaba na sawon lokaci. A nan "takobi" na nufin yaƙi. An yi magana game da kisa cikin yaƙi na nufin cewa dabbar jeji ta cinye sojojin. AT: "Ba mu bukata mu yi amfani da su takobin mu mu yi yaƙi mu kashe juna."
An yi amfani da wannan tambayar don a tilasta Yowab ya san cewa in sun cigaba da faɗa zai kai su ga shan wahala sosai. A nan "ba ɗaɗi" na nufin matuƙar wahala da zai auku. AT: "Ka san cewa ba za mu same shi da sauki ba in mun cigaba da wannan!"
An yi wannan tambayar gangancin da nufin sa Yowab ya bar yaƙi da 'yan'uwansa Isra'ilawa. An yi amfni da "'yan'uwa" a nan don ya wakilci 'yan ƙasar Isra'ila. AT: "Bar wannan don don kada ya zama lallai ga Isra'ila su kashe junansu!"
Wannan rantsuwa ce mai karfi. AT: "Tare da Allah a matsayin shaida na" ko "Allah zai tabbatar da cewa ina nufin abin da na faɗa"
Wannan magana na bayana abin da da zai faru har idan Abna bai yi hikimar yin magana ga Yowab ba.
An yi amfani da ƙaho don nuna alamar umurni ga rudunar sojojin da ke a nesa.
A nan "Isra'ila" na nufin mutanen da ke yi wa Isra'ila yaƙi. AT: "cigaba da bin Isra'ila"
Waɗannan sunayen wuraren wuri.
"mutane 360 daga Benyamin sun bi Abna." Abnar bai mutu ba.
Wannan magana na nufin "daga kabilar Benyamin."
"ɗauki gawan Asahel tare da su"
"sun sauka a Hebron da safe"
1Akwanakin nan dai aka yi dogon yaƙi tsakani gidan Saul da gidan Dauda. Gidan Dauda ya yi ta ƙara ƙarfi, amma gidan Saul ya yi ta raguwa.2Aka haifa wa Dauda 'ya'ya maza a Hebron. Ɗan farinsa Amon, da Ahinowam daga Yazril ta haifa masa.3Ɗansa na biyu, Kilyab, Abigel gwauruwar marigayi Nabal daga Karmel ta haifeshi, Ɗansa na ukun Absalom ne, ɗan Ma'aka, ɗiyar Talmai, sarki Geshu.4Ɗan Dauda na huɗu, Adonija, ɗan Hagit ne. Ɗansa na biyar Sefatiya ne ɗan Abtiyal,5na shidan, Itram ne, ɗan Egla matar Dauda. Waɗannan 'ya'ya maza aka haifa wa Dauda a Hebron.6Ya zamana fa a lokacin yaƙi tsakanin gidan Saul da gidan Dauda sai Abna ya ƙarfafa kansa a gidan Saul.7Saul na da kwarkwara wadda sunanta Risfa, ɗiyar Aya ce. Sai Ishboshet ya cewa Abna, "Me yasa ka kwana da ƙwarƙwarar mahaifina?"8Sai Abna ya husata da maganganun Ishboshet ya ce, "Ni kan kare ne na Yahuda? Yau ina nuna aminci ga gidan Saul, mahaifinka, da 'yan'uwansa, da kuma abokanansa, ta wurin yadda ban basheku ba cikin hannun Dauda. Amma yanzu kana zargi na da laifi game da wannan matar.9Bari Allah ya yi mani, Abna, harma fiye da haka, idan ban yi wa Dauda yadda Yahweh ya rantse masa ba,10a tada masarautar daga gidan Saul, a kafa kursiyin Dauda bisa Isra'ila da bisa Yahuda daga Dan zuwa Bayasheba."11Ishboshet bai iya amsa wa Abna ba koda magana ɗaya, domin yana jin tsoronsa.12Sa'an nan Abna ya aika manzanni ga Dauda su yi masa magana dominsa cewa, "Ƙasar wane ne wannan? Ka yi yarjejeniya da ni, gama hannuna na tare da kai, in kawo maka dukkan Isra'ila."13Dauda ya amsa, "Da kyau zan yi yarjejeniya da kai. Abu ɗaya na ke biɗa a gare ka shi ne cewa ba za ka ga fuskata ba sai dai da farko ka kawo Mikal, ɗiyar Saul, sa'ad da za ka zo ka gan ni."14Sai Dauda ya aika manzanni zuwa wurin Ishboshet, ɗan Saul, cewa, "Ka ba ni matata Ishboshet Mikal, wadda na biya sadakin loɓar kaciya ɗari na Filistiyawa domin ta.15Sai Ishboshet ya aika a kawo Mikal, ya kuma karɓe ta daga mijinta, Faltiyel ɗan Layis.16Mijinta ya tafi tare da ita, yana tafiya yana kuka, ya bi ta zuwa Bahurim. Sai Abna ya ce masa, "Ka koma gida yanzu." Sai ya koma.17Abna ya yi magana da dattawan Isra'ila cewa, "Da daɗewa kun yi ta ƙoƙarin ku naɗa Dauda ya zama sarki bisan ku.18Yanzu ku yi haka. Gama Yahweh ya yi magana game da Dauda cewa, 'Ta hannun bawana Dauda zan ceci mutanena Isra'ila daga hannun Filistiyawa daga kuma dukkan hannun maƙiyansu.'"19Abna kuma da kansa ya yi magana da mutanen Benyamin. Sai Abna kuma ya tafi ya yi magana da Dauda a Hebron domin ya bayyana masa dukkan abin da Isra'ila da dukkan gidan Benyamin gaba ɗaya suka yi niyar aikatawa.20Da Abna da mutanensa guda ashirin suka iso cikin Hebran domin su ga Dauda, Dauda ya shirya masu liyafa.21Abna ya bayyana wa Dauda, "Zan tashi in tattaro maka dukkan Isra'ila, ubangidana sarkina, domin su yi alƙawari da kai, domin ka yi mulki bisa dukkan abin da kake marmari." Sai Dauda ya sallami Abna, Abna kuma ya koma da salama.22Sai sojojin Dauda da Yowab suka dawo daga hari, tare da ganima mai tarin yawa. Amma Abna ba ya tare da Dauda a Hebran. Dauda ya rigaya ya sallame shi, Abna kuma ya tafi cikin salama.23Lokacin da Yowab da dukkan sojojin da ke tare da shi suka iso, aka gaya wa Yowab, "Abna ɗan Nã ya zo gun sarki, kuma sarki ya sallame shi, Abna kuma ya tafi cikin salama."24Sai Yowab ya zo wurin Sarki ya ce, "Mene ne ke nan ka yi? Duba, Abna ya zo wurin ka! Me yasa ka sallame shi, kuma ga shi ya tafi?25Baka sani ba Abna ɗan Nã ya zo domin ya yaudare ka ya kuma san shirye-shiryenka ya gane duk abubuwan da kake yi?"26Da Yowab ya bar Dauda, sai ya aika manzanni su bi Abna, suka kuma dawo da shi daga rijiyar Sira, amma Dauda bai san wannan ba.27Da Abna ya dawo Hebron, Yowab ya kai shi gefe a tsakiyar ƙofa domin ya yi magana da shi a kaɗaice. Nan Yowab ya soke shi a ciki ya kashe shi. Da haka Yowab ya ɗau fansar jinin ɗan'uwansa. Asahel.28Da Dauda ya ji wannan ya ce, "Da ni da mulkina baratattu ne a gaban Yahweh har abada game da jinin Abna ɗan Nã.29Bari alhakin mutuwar Abna ya faɗi kan Yowab da kuma dukkan gidan mahaifinsa. Bari kada a taɓa rasa a cikin iyalin Yowab wani wanda ke ɗigar miƙi ko ciwon fata ko kuma wanda ya ke gurgu kuma dole ya yi tafiya tokare da sanda ko kuma wanda takobi ya kashe shi ko wanda ya ke da rashin abinci."30Haka Yowab da ɗan uwansa Abishai suka kashe Abna, domin ya kashe ɗan uwansu Asahel a Gibiyan cikin yaƙi.31Dauda ya cewa Yowab da dukkan mutanen da ke tare da shi, "Ku kekketa tufafinku, ku sa tsumoki, ku yi makoki a gaban gawar Abna."32Sarki Dauda ya bi bayan gawar cikin tawagar makokin. Suka binne Abna a Hebron. Sarki ya yi kuka da kururuwa mai ƙara a kabarin Abna, dukkan mutane kuma su ka yi kuka.33Sarki ya yi makoki domin Abna ya yi waƙa, "Ya ƙyautu Abna ya mutu kamar yadda wawa ke mutuwa?34Ba wai an ɗaure hannuwanka ba. Ƙafafunka ba a ɗaure su da sarƙa ba. Kamar yadda mutum yakan faɗi a gaban 'ya'yan rashin gaskiya, haka ka faɗi." Sai kuma dukkan mutane suka ƙara kuka a bisansa.35Dukkan mutane suka zo su sa Dauda ya ci abinci tun da sauran rana. Amma Dauda ya rantse, "Bari Allah ya hukunta ni, ya kuma ƙara yi, idan na ci abinci ko wani abu kafin rana ta faɗi."36Dukkan mutane suka lura da ɓacin ran Dauda, suka ji daɗi, duk abin da sarki ya yi suka ji daɗin sa.37Sai dukkan mutane da kuma dukkan Isra'ila suka gane a ranar nan ba niyyar sarki ba ce a kashe Abna ɗan Nã.38Sarki ya cewa barorinsa, "Ba ku sani basarake da kuma babban mutum ne ya faɗi yau a cikin Isra'ila ba?39Yanzu na rarrauna yau, koda shi ke ni sarki ne zaɓaɓɓe. Waɗannan mutane, 'ya'yan Zeruya, sun fi kowa mugunta a gare ni. Bari Yahweh ya sãka wa mugu da hukuncin da ya cancanci muguntarsa."
An yi amfani da wannan kalmar don nuna alamar canji daga ainihin kan labarin. A nan Sama'ila ya bada bayani game da yaƙin da ta auku tsakanin Dauda da waɗanda suke goyon bayan Saul.
A nan "gida" na nufin "masu goyon baya"
Wannan magana ne da ke nufin cewa yawan mutane da suke goyon bayan Dauda suna ta ƙaruwa.
Wannan salon magana ne da ke nufin cewa yawan mutane da suke goyon bayan Saul suna ta raguwa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "matayen Dauda sun haifi 'ya'ya maza shida"
Wannan shine tsari lambar 'ya'yan Dauda maza.
Waɗannan sunayen mata ne. Su ne matayen Dauda.
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan shine tsari lambar 'ya'yan Dauda maza.
Waɗannan shi ne sunayen 'yan'yan Dauda Maza.
Waɗannan shine sunayen matan Dauda.
Wannan ya gabatar da sabon abin da ya faru cikin labarin gwagwarmaya tsakanin masu goyon bayan Dauda da iyalin Saul.
Wannan na nufin iyalin Saul da masu goyon bayansa wanda suke mulkin kayansa bayan mutuwarsa.
Wannan na nufin waɗanda suke goyon bayan Dauda.
Ƙarfin ikon Abner a kan gidan Saul ana magana da shi kamar yana da ƙarfi a zahiri. AT: "Abna ya sami ƙarin iko a kan dangi da magoya bayan Saul"
Waɗannan sunayen mata ne.
Wannan sunan namiji, ɗan Saul.
Ishboshet ya yi wannan tambayar don ya tsautawa Abna wanda ke yi kamar shi sarki ne. AT: "Ba ka da iko ka kwana da ƙwarƙwarar mahaifina!"
Wannan wata magana ne da ke nufin dangantaka ta jima'i.
Abna yayi amfani da wannan tambayar a matsayin musun zargin Ishbosheth a fusace. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Ni ba mayaudari bane mai yiwa David aiki!"
Abna yana magana game da kansa kamar kan kare, wanda Isra'ila suna duba a matsayin wanda ke biyayya ga duk wanda ya ciyar da su. A nan "na Yahuda" na nufin cewa biyayyar Abna zuwa ga Yahuda wato ida Dauda yake ba kuma gidan Saul ba. AT: "Shin, ni maci amana na Yahuda ne? ko "Ni ba maci amana da aiki wa Dauda ba!"
A nan "hannu" na wakilcin ikon yin nasara. AT: "Dauda ya ci nasara bisa"
Abna ya yi amfani da wannan tambayar don ya tsauta wa Ishboshet. Ba a tabbatar ko Abnar ya kwana da Risfa, ko ana zarginsa be ba. Ma'ana mai yiwuwa 1) Abna na da laifi AT: "Kada ka yi fushi cewa na kwana da wannan matan!" ko 2) Abna bai yi laifi ba. AT: "Kada ka yi tunani cewa na kwana da wannan matar!"
Wannan wa'adi ce ma muhimmanci a wancan lokaci. Abna yana roƙon Allah ya hukunta shi hukunci mai tsanani idan bai cika wa'adinsa ba. Mai yiwuwa harshen ku na da wata hanyar bayana wa'adi. AT: "Ina roƙon Allah ya hukunta ni idan ban yi"
A nan "gida" na nufin iyalin Saul da masu goyon bayansa da suka rayu bayan mutuwar Saul. AT: "iyalin da masu goyon bayan Saul"
Wannan magana na nufin ikon Dauda a matsayin sarki.
Wasu juyi sun ƙara "lokacin da yake Hebron" wasu kuma basa yin haka. Kuna iya ƙara jumlar idan ta kasance a cikin sigar ƙasarku.
Asalin rubutun wannan tambayar bai bayyana ba. Ma'ana mai yiwuwa su ne 1) Abna yana da ikon ya ba Dauda ƙasar. AT: "Wannan ƙasar tawa ce!" ko 2) Allah ne ya zaɓa Dauda ya yi mulkin ƙasar: AT: "Wannan ƙasar dai-dai take da ku!"
Anan “hannu” yana wakiltar taimakon Abna da yake yiwa Dauda. AT: "Zan taimake ku"
Dauda yana bayanin yanayin da zai sadu da Abna. Anan “fuska” tana nufin Dauda da kansa. AT: "ba za ku iya ganina ba sai kun kawo mini Mikal tukunna"
Wannan sunan ɗiyar Saul ne. Ita ce matar Dauda na farko.
Wannan na wakiltar yawan mazajen da Dauda ya kashe saboda Saul ya ba shi zarafi ya auri Mikal. "Fatar gaba" ita ce ninkawar fatar da ke rufe al'aurar namiji.
Faltiyel shi ne mijin Mikal na biyu. Saul ya miƙa ta zuwa gare shi bayan Dauda ya gudu daga gare Saul.
Waɗannan sunayen mutane maza ne.
Wannan suna kawye ne.
"don haka ku naɗa Dauda a matsayin sarkin ku"
A nan "hannu" na nufin iko Dauda na yi nasara bisa Filistiyawa. AT: "Zan ba wa bawa na iko zai kuma"
A nan "hannu" na nufin iko bisa Isra'ila. AT: "ikon Flistiyawa"
A nan "hannu" na nufin iko bisa Isra'ila. AT: "ikon dukkan maƙiyansu"
Waɗannan maganganu biyu na nufin zuriyar Benyamin ɗaya daga cikin kabilar Isra'ila.
Yawan mazajen da suka tare da Abna.
Wannan jumlar na nufin "dukka al'umma ta Isra'ila"
Sun rabu a matsayi abokai. Dauda bai yi fushi da Abna ba.
Waɗannan kayaki ne da aka kwashe daga wurin abokan gãba.
Abna ya riga ya koma gida.
"wani ya gaya wa Yowab"
Wannan sunan namiji ne. Shine kakan Saul.
Yowab ya yi wannan tambayar don ya tsauta wa Dauda don ya bar Abna ya tafi cikin salama. AT: "Bai kamata da ka yi wannan ba!"
Yowab ya yi wannan tambayar don ya tsauta wa Dauda don ya bar Abna ya gudu. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Abna na a nan amma har ka bar shi ya tafi!"
Yowab yana wannan tambayar don ya shawo kan Dauda cewa Abna ya shirin mugunta ga Dauda. AT: "Hakika ka san ... duk abin da kake yi."
"Sira" sunan wuri ne in da rijiyar ta ke.
Wannan na nufin ɗaya daga cikin ƙofofin ganuwar birnin a Hebron. Kamar yadda UDB ke nufin cewa ƙofofin birnin an yi su ne haɗe cikin gine-ginen ganuwar birnin. Cikin hanyar akwai ƙofofi da ke kai ga ɗakunan da ke gefen inda ake karɓan baƙi, inda kuma ake cin kasuwa ana kuma yin abubuwa dangane da shari'a. Ma yiwuwa a cikin ɗaya daga cikin waɗannan ɗakunan ne Yowab ya kashe Abna.
A nan "jini" na nufin mutuwar Asahel. AT: "mutuwar Asahel"
Wannan na nufin mutum ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
A nan "jini" na nufin mutuwa Abna. Dubi yadda ka juya magana makamancin haka cikin 2 Sama'ila 3:27. AT: "mutuwa Abna" ko "kashe Abna"
Wannan magana na nufin cewa sakamakon lafin zau faru da Yowab da iyalinsa kamar wani abu ne mai nauyi ya faɗi a kansu. AT: "sa wahala don Yowab domin kuma dukka gidan mahaifinsa"
A nan "gida" na nufin zuriya. AT: "dukka zuriyar mahaifin Yowab"
Wannan na nufin cewa dole za a sami wani da ke da damua kamar yadda aka lisafta. AT: "Bari a kullayaumi a sami"
A nan "takobi" na nufin mutuwa cikin hargitsi. AT: "mutu cikin hargitsi"
"na yunwa"
Waɗannan alama ce ta nuna makoki da kuma baƙin ciki.
Kalmomin nan "hawaye" da "kuka" a takaice na nufin abu ɗaya, na kuma nanata yadda Dauda ya yi makokin don mutuwar Abna.
An yi amfani da wannan tambayar don a nanata cewa bai ƙyautu da ya mutu ba. AT: "Bai ƙyautu Abna ya mutu cikin ƙunya ba!"
Waɗannan jumlolin na nufin zance kusan iri ɗaya. Ana iya haɗa su cikin jimla ɗaya. AT: "Haƙika kai ba barawo bane da ke a kurkuku" ko "Haƙika kai ba mai laifin ba ne"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Babu wanda ya ɗaure hannuwanka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Babu wanda ya ɗaure ƙafafunka da sarƙa"
Wannan na nufin mutanen da ke da rashin gaskiya ko mugaye. AT: "mugayen mutane"
An yi amfani da wannan zuguiguci don nuna cewa al'umma ta Isra'ila suna da nufin lura da Dauda a sa'ad da yake cikin makokin. AT: "Mutanen da yawa sun zo"
Wannan wa'adi ce ma muhimmanci a wancan lokaci. Dauda yana roƙon Allah ya hukunta shi hukunci mai tsanani in har ya ci wani abu kamin faɗiwar rana. Mai yiwuwa harshen ku na da wata hanya na bayana wa'adi. AT: "Ina roƙon Allah ya hukunta nu in"
An yi amfani da wannan tambayar don nuna yadda Dauda ya girmama Abna. A nan "faɗi" na nufin "mutu." Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "haƙika da gaske babban yarima ya mutu yau cikin Isra'ila!"
Waɗannan maganganu biyun suna nufin Abna. AT: "babban yarima"
"ba tare da rahama ba"
1Lokacin da Ishboshet, ɗan Saul, ya ji Abna ya mutu a Hebron, sai hannuwasa suka yi rauni, dukkan Isra'ila suka tsorata.2Ɗan Saul yana da mutane biyu waɗanda shugabanni ne na ƙungiyoyin sojoji. Sunan ɗayan Bãna ɗayan kuma Rekab, 'ya'yan Rimon Babirote na mutanen Benyamin (gama ana ɗaukar Birot a yankin Benyamin ta ke),3Birotiyawa sun gudu ne zuwa Gittam kuma har yau suna zama a can.4Yanzu dai, Yonatan ɗan Saul, yana da ɗa wanda gurgu ne a ƙafa. Yana da shekara biyar sa'ad da labari ya zo akan Saul da Yonatan daga Yeziril. Sai mai renonsa ta ɗauke shi don ta gudu da shi. Amma da ta ke gudu, sai ɗan Yonatan ya faɗi ya gurgunce. Sunansa Mafiboshet.5Sai 'ya'yan Rimon Babirote, Rekab da Ba'ana, suka yi tafiya cikin zafin rana zuwa gidan6Mafiboshet lokacin da ya ke hutawa da tsakar rana. Matar da ke tsaron ƙofar barci ya kwashe ta sa'ad da ta ke tankaɗen alkama, sai Rekab da Bãna suka yi sanɗo shuru suka wuce ta.7To bayan da suka shiga ɗakin, sai suka faɗa masa suka kashe shi sa'ad da ya ke ƙwance kan gadonsa. Suka yanke kansa suka tafi da shi, suka yi tafiya dukkan dare zuwa Araba.8Suka kawo kan Mafiboshet gun Dauda a Hebron, suka kuma ce da sarki, "Duba, wannan kan Mafiboshet ɗan Saul ne, maƙiyinka, wanda ya nemi ranka. Yau Yahweh ya sãka wa maigidanmu sarki gãba da Saul da zuriyarsa."9Dauda ya amsa wa Rekab da Bãna ɗan'uwansa, 'ya'yan Riman Babirote; ya ce masu, "Na rantse da ran Yahweh, wanda ya ceci raina daga kowacce wahala,10dã wani ya gaya mani; 'Duba, Saul ya mutu,' yana tsammanin ya kawo labari mai daɗi, sai na danƙe shi na kashe shi a Ziglag. Wannan shi ne ladan dana bashi don labarinsa mai daɗi.11To ba zan yi fiye da haka ba, sa'ad da mugayen mutane suka kashe mutum marar laifi a cikin gidansa a kan gadonsa, yanzu ba zan nemi jininsa daga hannunku in kuma tumbuƙe ku daga duniya ba?"12Sa'an nan Dauda ya umarci samari, suka kashe su suka yanke hannuwansu da ƙafafunsu kuma suka rataye su a gaɓar tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Mefiboshet suka binne shi a kabarin Abna a Hebron.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
A cikin wannan kalmar "hannunsa" yana wakiltar Ishboshet kansa. AT: "Ishboshet ya zama mai rauni" ko "Ishboshet ya rasa ƙarfi"
Wannan ya gabatar da Ba'ana da Rekab a cikin labarin.
Anan marubucin ya fara ba da bayanan baya game da Birot ga mai karatu. Yankin ƙasar Birot bisa ga yankin ƙasar Benyamin. (Duba: writin_background)
Waɗannan sunayen wurare ne.
Wannan aya ta dakatar da babban labarin don bayar da bayanan asali game da Mefiboshet, zuriyar Saul ta hanyar Yonatan maimakon ta Ishboshet. Mefiboshet zai zama muhimmin hali daga baya a littafin.
Wannan jumlar na nufin "ba za a iya tafiya ba."
Wannan shi ne shekarun ɗan Yonatan a lokacin mutuwar mahaifinsa.
Wannan na nufin labarin mutuwar su.
Wannan yana bayanin yadda Mefiboshet ya ji rauni don haka ya kasa tafiya.
Labarin ta koma zuwa ga ayyukan Rekab da Ba'ana wanda aka gabatar da su cikin 2 Sama'ila 4:1.
tsakiyar rana, wani ɓangare na rana lokacin da yake mafi zafi
"cire sãba daga alkama"
Wannan karin magana ne da ke nufin "ƙoƙarin kashe ka."
Wannan wa'adi ne mai nauyi da Dauda ya rantse, murdin Yahweh ne shaida. AT: "Na rantse da ran Yahweh"
A nan “rai” yana nufin Dauda da kansa. Wannan yana nufin cewa Yahweh ya rayar da Dauda. AT: "wanene ya cece ni"
An yi amfani da wannan tambayar don a nuna cewa mazajen sun yi laifi na musamman. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Kana da laifi fiye! Aiki na ne in biɗi ran sa daga gare ka in kuma tumbuƙe ka daga duniya."
Jimlar "jininsa" tana wakiltar rayuwar Ishboshet. Anan "daga hannunka" yake wakiltar Rekab da Ba'ana, 'ya'yan Rimmon na Babirote, wanda aka gabatar a cikin 2 Samuila 4: 5. AT: "na ɗauke ku alhakin mutuwar Ishboshet"
Waɗannan ayyuka ne na alama don nuna raini ga maza.
Wannan alama ce ta bada martaba ga Ishboshet. Ana iya bayana wannan a fili. AT: "sun martaba Ishboshet ta wurin zinne kansa cikin kabari"
1Sa'an nan dukkan kabilun Isra'ila suka zo gun Dauda a Hebron suka ce, "Duba mu jikinka ne da ƙashinka.2A kwanakin baya, da Saul ya ke mulki bisanmu, kai ne ka bi da rundunar yaƙi ta Isra'ila. Yahweh ya ce maka, "Za ka yi kiwon jama'ata Isra'ila, za ka kuma zama sarki bisa Isra'ila.'"3Sai dukkan dattawan Isra'ila suka zo wurin sarki a Hebron, Sarki Dauda ya yi alƙawari da su a gaban Yahweh. Suka naɗa Dauda sarki bisa Isra'ila.4Dauda yana da shekaru talatin sa'ad da ya fara sarauta, ya kuma yi mulki shekara arba'in.5A Hebron ya yi mulkin bisa Yahuda shekaru bakwai da wata shida, kuma a Yerusalem ya yi mulki shekaru talatin da uku bisa dukkan Isra'ila da Yahuda.6Sarki da mutanensa suka zo Yerusalem gãba da Yebusiyawa, mazamnan ƙasar. Suka cewa Dauda, "Ba za ka iya zuwa nan sai dai idan makafi da guragu ne za su kore ka. Dauda ba zai iya zuwa nan ba."7Duk da haka Dauda ya ci kagarar Sihiyona, wadda yanzu shi ne birnin Dauda.8A lokacin nan Dauda ya ce, "Waɗanda suka hari Yebusiyawa dole su bi ta wuriyar ruwa domin su kai ga "guragu da makafi' waɗanda su ne maƙiyan Dauda." Shi yasa mutane ke cewa, "Da 'makafi da kuma guragu' ba za su shiga fãda ba."9Sai Dauda ya zauna cikin kagara ya kira shi birnin Dauda. Ya tsare shi da gine- gine kewaye da shi tun daga waje zuwa ciki.10Dauda ya ƙasaita domin Yahweh, Allah mai runduna, yana tare da shi.11Sa'an nan Hiram sarkin Taya ya aika da manzanni gun Dauda, da itacen sida, da masassaƙa da masu fãsa duwatsu. Suka gina wa Dauda gida.12Dauda ya sani Yahweh ya naɗa shi sarki bisa Isra'ila kuma ya ɗaukaka masarautarsa sabili da mutanensa Isar'ila.13Bayan da Dauda ya bar Hebron ya zo Yerusalem, ya ƙara ɗaukar ƙwaraƙwarai da mataye a Yerusalem, aka ƙara haifa masa 'ya'ya maza da 'ya'ya mata.14Waɗannan su ne sunayen yaran da aka haifa masa a Yerusalem: Shammuwa, Sobab, Natan, Suleman,15Ibha, Elisuwa, Nefeg, Yafiya,16Elishama, Eliyada, da Elifelet17Da dai Filistiyawa suka ji cewa an naɗa Dauda sarki bisa Isra'ila, sai suka fita dukka suna nemansa. Amma Dauda ya ji abin, sai ya gangara zuwa mafaƙa.18Yanzu Filistiyawa sun rigaya sun fito sun bazu a Kwarin Refayim.19Sai Dauda ya roƙi taimako daga Yahweh. Ya ce, "Ko in hari Filistiyawa? Za ka bani nasara akan su?" Yahweh ya cewa Dauda, "Ka hare su, domin hakika zan ba ka nasara bisa Filistiyawa."20Sai Dauda ya kai hari a Ba'al Ferazim, a nan ya kayar da su. Ya ce haka, "Yahweh ya fantsamo cikin maƙiyana a gabana kamar fantsamowar ruwan ambaliya." Saboda haka sunan wurin ya zama Ba'al Ferazim.21Filistiyawa suka bar gumakunsu a nan, Dauda kuma da mutanensa suka ɗauke su suka tafi da su.22Sai Filistiyawa suka sake tasowa kuma suka ƙara bazuwa cikin Kwarin Refayim.23Sai Dauda ya sake roƙon taimako daga Yahweh. Yahweh kuma ya ce masa, "Kada ka kai hari ta gabansu, maimakon haka ka zagaya ta bayansu ku afka masu ta cikin itatuwan tsamiya.24Sa'ad da kuka ji ƙarar takawar yaƙi cikin iska da ke bugawa a ƙwanƙolin itatuwan tsamiya, sai ku kai hari da karfi. Kuyi wannan domin Yahweh ya rigaya ya sha gabanku ya hari rundunar Filistiyawa."25Sai Dauda ya yi yadda Yahweh ya umarce shi. Ya kashe Filistiyawa daga Geba har zuwa Geza.
Wannan na nufin "dangi." AT: "mun haɗa dangi da kai" ko "mu daga iyali ɗaya ne"
Wannan bayani game da tarihi. Saul sarki ne a gare su kafin Dauda.
Waɗannan jimloli guda biyu suna nufin abu ɗaya dai-dai kuma suna jaddada cewa Yahweh ya zaɓi Dauda ya zama sarki.
"shafe" alama ce na nuna cewa sun fahimci cewa Allah ya zaɓe Dauda a matsayin sarki.
Dauda da rundunar sojojin Isra'ila sun kai hari ga Yerusalem.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Idan kun zo nan, makaho da guragu ma za su iya juya ku baya"
Dauda yana magana da sojojinsa. AT: "Dauda ya ce wa sojojinsa, "Waɗanda suke so su fatattaki mutanen Yebus"
Ma'ana mai yiwuwa 1) wannan na nufin mutanen da lallai guragu ne da makafi ne ko 2) wannan magana ne da ke magana game da Yebusiyawan da ke cikin birnin Urushalima sai ka ce dukkan su marasa karfi ne ba sa kuma iya taimakon kansu.
Wannan sunan mutum ne.
waɗanda suke sassaƙa itace
wadanda suke aiki da dutse ko bulo
Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Dauda maza.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ya ƙara samun 'ya'ya maza da mata" ko "sun haifa masa 'ya'ya maza da mata"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "da matayen sa suska haifa masa" ko "da yake da shi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Isra'ila sun naɗa Dauda sarki"
Wannan magana na nufin wasu Filistiyawa da suke neman Dauda. An zuguiguta wannan don a nuna yawan Filistiyawa da suke so su ga Dauda.
Wannan sunan wuri ne. (Duba: )
Wannan sunan wuri ne. (Duba: )
Anan Dauda yayi magana game da nasarar da Yahweh ya kawo kamar ambaliyar ruwa ce wacce ta mamaye kogin ta kuma rufe ƙasar, ta haifar da halaka. AT: "Yahweh ya mamaye magabtana kamar yadda ambaliyar ruwa ta mamaye ƙasar"
Sun “tasowa” domin Filistiyawa suna zama a wuri mafi ƙasƙanci fiye da sansanin Dauda.
Wannan sunan wuri ne
Wannan karashin umurnin da Yahweh ya fara ba wa Dauda ne cikin 2 Sama'ila 5:22.
Wannan yana magana ne game da sautin ganyen da ke birgima yayin da iska ke busawa cikin su kamar karar sautin tafiya. AT: "Lokacin da iska ke busawa ta saman da itatuwan tsamiya sai yaji kamar mutane suna tafiya"
Waɗannan sunayen wurare ne.
1Dauda ya sake tattaro dukkan zaɓabbun mutanen Isra'ila, dubu talatin.2Dauda ya tashi ya tafi da dukkan mutanensa da ke tare da shi daga Bãla cikin Yahuda domin a ɗauko akwatin Yahweh daga can wanda ake kira da sunan Yahweh mai runduna, wanda ya ke zaune a kursiyi bisa kerubim.3Suka ɗora akwatin Yahweh bisa sabuwar karusa. Suka fito da shi daga gidan Abinadab, da ke kan wani tudu. Uza, da Ahiyo, 'ya'yansa, suke bi da sabuwar karusar.4Suka fito da karusar daga gidan Abinadab daga kan tudu tare da akwatin Yahweh a bisan sa. Ahiyo na tafiya a gaban akwatin.5Sai Dauda da dukkan gidan Isra'ila suka fara wasa a gaban Yahweh, suna biki tare da sassaƙaƙƙun kayayyakin waƙa, molaye, garayu, kacau-kacau, da kuge.6Da suka iso masussukar Nakon, sai sãn ya yi tuntuɓe, sai Uza ya miƙa hannunsa ya tallafi akwatin Allah, ya kuma kama shi.7Sai fushin Yahweh ya yi ƙuna a kan Uza. Allahj ya kai masa hari nan take sabili da zunubinsa. Uza ya mutu nan take da akwatin Allah.8Dauda ya yi fushi domin Yahweh ya kai wa Uza hari, ya kira sunan wurin nan Ferez Uza. Wurin nan har yau ana kiransa Ferez Uza.9Dauda ya ji tsoron Yahweh a ranan nan. Ya ce, "Ƙaƙa akwatin Yahweh zai zo gare ni."10Saboda haka Dauda bai so ya ɗauki akwatin Yahweh tare da shi zuwa cikin birnin Dauda ba. Maimakon haka, sai ya ajiye shi a gefe cikin gidan Obed Idom Bagitte.11Akwatin Yahweh ya kasance a gidan Obed Idom Bagitte wata uku. Sai Yahweh yasa masa albarka da dukkan gidansa.12Sai aka gaya wa sarki Dauda, "Yahweh ya albarkaci gidan Obed Idom da dukkan abubuwan da ke nasa saboda akwatin Yahweh" Sai Dauda ta tafi ya ɗauko akwatin Yahweh daga gida Obed Idom zuwa birnin Dauda da murna.13Lokacin da waɗanda suke ɗauke da akwatin Yahweh suka yi tafiya taki shida, sai ya yi hadayarsa da kiwataccen ɗan maraƙi.14Dauda ya yi rawa a gaban Yahweh da dukkan ƙarfinsa; yana sanye da ɗan feton lilin kaɗai.15Sai Dauda da dukka gidan Isra'ila suka ɗauko akwatin Yahweh tare da sowa da kuma ƙarar ƙahonni.16Sa'ad da akwatin Yahweh ya shigo birnin Dauda, Mikal, ɗiyar Saul, ta leƙa waje ta taga. Ta ga Sarki Dauda yana tsalle yana rawa a gaban Yahweh. Sai ta rena shi a zuciyarta.17Suka kawo akwatin Yahweh ciki suka ajeye shi a mazauninsa, a tsakiyar rumfar da Dauda ya shirya dominsa. Sai Dauda ya miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama a gaban Yahweh.18Lokacin da Dauda ya gama miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama ya albarkaci mutane a cikin sunan Yahweh mai runduna.19Sai ya rarraba wa dukkan mutane, dukkan cin-cirindon Isra'ila gaba ɗaya, maza da mata, dunƙulen gurasa, ɗan gutsuren nama, da wainar kauɗar inabi. Sa'annan dukkan mutane suka tafi, kowanne ɗayan su ya koma zuwa nasa gida.20Sai Dauda ya koma ya albarkaci iyalinsa. Mikal, ɗiyar Saul, ta fito ta taryi Dauda ta ce, "Ina misalin girmamawar da sarkin Isra'ila ya samu yau, wanda ya tsirance kansa yau a idanun bayi 'yan mata cikin barorinsa, kamar ɗaya daga cikin ashararrun mutane wanda ba ko kunya yana tsiraratar da kansa!"21Dauda ya amsa wa Mikal, "Na yi wannan a gaban Yahweh, wanda ya zaɓe ni fiye da mahaifinki fiye kuma da dukkan iyalin gidansa, wanda ya aza ni shugaba bisa mutanen Yahweh, bisa Isra'ila, A gaban Yahweh zan yi murna!22Zan zama ma da tawali'u fiye da haka, in kuma kunyata a idanuna ma. Amma game da 'yan mata bayi da kika ambata, za a girmamani."23Saboda haka Mikal ɗiyar Saul, ba ta da 'ya'ya har ranar mutuwarta.
Wannan alama ce na sabon ɓangaren labarin.
Wannan magana ne da ke wakiltar rundunar sojojin al'umma ta Isra'ila.
An nuna cewa suna ɗaukar akwatin zuwa Yerusalem. AT: "daga Ba'ala a Yahuda don ɗaukar akwatin alkawarin Allah zuwa Yerusalem"
Wannan sunan wani wuri ne.
An rubuta sunan Yahweh a kan akwatin.
"wanda ke zaune cikin wurin iko tsakanin kerubim"
Dauda da rundunar sojojin al'umma ta Isra'ila sun ɗauki akwatin alkawarin.
Waɗannan sunayen mutanen maza ne.
Wannan na wakliltar mutanen Isra'ila. AT: "dukka sauran mutanen Isra'ilawa da ke tare da shi"
Wannan sunan mutum namiji ne.
Anan ana maganar "fushin Yahweh" kamar wuta ce.
Uzza ya yi zunubi don ya taɓa akwatin saboda Yahweh ya ummurta cewa kada kowa ya taɓa akwatin.
Wannan sunan wuri ne. Mai fassarawa na iya ƙara alamar hasumiya da ke cewa, "Sunan nan "Ferez Uzza" na nufin "hukuncin Uza.'"
Wannan na nufin har zuwa lokacin da aka rubuta.
An yi amfani da wanna tambayar don a nanata cewa yana tsoron kai akwatin zuwa Yerusalema. AT: "ina tsoron kawo akwatin Yahweh tare da ni zuwa Yerusalem."
Wannan sunan mutum namiji ne.
A nan "shi" na nufin Obed Idom Bagitte
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutanen sun gaya wa Sarki Dauda"
A nan "gida" na wakiltar iyali. AT: "Obed Idom da Iyalinsa"
Yerusalem ta fi kusan kowane wuri a cikin Isra’ila, don haka ya zama dai-dai ga Isra’ilawa su yi maganar hawa Yerusalem da sauka daga gare ta. AT: "kai akwatin alkawari na Allah" ko "ɗauki akwatin alkawari na Allah."
Rawa a nan alamace sujada cikin fariciki ga Yahweh.
tufafin da aka yi daga igiyoyi
A nan "gida" na wakiltar mutanen Isra'ila. AT: "dukka sauran Isra'ilawan tare da shi"
Kalman nan "yanzu" alama ce da ke nuna cewa an yanke labarin. A nan mai ba da labarin ya yi bayani game da Mikal.
Mikal ɗiyar Sarki Saul ne kuma ita matar Dauda ce. Duba yadda ka juya wannan cikin 2 Sama'ila 3:12.
A nan "zuciyar" na wakiltar tunani ko motsin rai. AT: "ta dube shi da wulakanci" ko "ta yi masa izgili"
"ga Yahweh"
A albarkaci "cikin sunan Yahweh mai runduna" na nufin a sa albarka da ƙarfin Yahweh da kuma ikonsa ko a matsayin wakilinsa.
dunƙulen gurasa da aka yi da busasshiyar inabi
A nan "fito" ana iya juya shi kamar "tafi"
Wannan magana ne. Mikal tana nufin wani abu ne daban da abin da ta faɗa, ba ta kuma gaskata cewa Dauda ya yi abin girmamawa. Mikal ta yi magana cikin rashin bada girma ga sarki Dauda game da kayan rawarsa da kuma halin.
Anan “idanun bayi mata” suna wakiltar kuyangin mata. AT: "a gaban bayi mata"
Mikal ta kwatanta Dauda da wanda ke bayana kansa a fili da kuma mutane wawayu
Anan "naku" yana nufin Mikal.
A nan "mutanen Yahweh" da "Isra'ila" na nufin abu ɗaya.
Dauda yana da ban dariya kuma yana nufin akasin abin da ya faɗa. Bai yarda da abin da ya yi da gaske ba a ƙasƙantar da shi ba ko kuma abubuwan da ya yi a nan gaba za a manta da su.
A nan "a idanuna ma" na wakiltar abin da mutum ke duba ko tunani game da wani abu. AT: "zan dubi kaina a matsayin wanda aka kunyata" ko "zan dubi kaina a matsayin wawa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Amma game da bayi 'yan mata da ki ka ambata za su girmama ni"
1Ya zamana sa'ad da sarki yana zaune cikin gidansa, kuma Yahweh ya bashi hutu daga dukkan maƙiyansa kewaye,2sarki ya cewa annabi Natan, "Duba, ina zaune cikin gidan sida, amma akwatin Yahweh yana zaune a cikin tsakiyar rumfa."3Sai Natan ya cewa sarki, "Je ka, ka yi abin da ke zuciyarka, gama Yahweh yana tare da kai."4Amma a daren nan maganar Yahweh ta zo gun Natan cewa,5"Ka tafi ka gaya wa bawana Dauda, "Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗi: Zaka gina mani gida inda zan zauna a ciki?6Gama ban taɓa zama a cikin gida ba daga ranar da na fitar da mutanen Isra'ila daga Masar har zuwa rana ta yau; maimakon haka ina ta yawo a cikin rumfa, a rumfar sujada.7A dukkan wuraren dana yi yawo a cikin mutanen Isra'ila, na taɓa gaya wa wani ɗaya daga cikin shugabannin Isra'ila wanda na naɗa ya yi makiyayancin mutanena Isra'ila, cewa, "Donme ba ka gina mani gidan itatuwan sida ba?'"'8Yanzu dai, ka gaya wa bawana Dauda, "Wannan shi ne abin da Yahweh mai runduna ya ce: "Na ɗauko ka daga makiyaya, daga bin tumaki, domin ka zama mai mulki bisa mutanena Isra'ila.9Na kasance tare da kai duk inda ka tafi. Na datse dukkan maƙiyan ka daga gaban ka. Yanzu zan sa sunanka ya shahara kamar sunayen shahararrun nan na duniya.10Zan sanya wa mutanena Isra'ila wuri, zan kuma kafa su a can, domin su zauna a mazaunin kansu kuma ba za a ƙara wahalshe su ba. Mugayen mutane ba za su ƙara zambatar su ba, kamar yadda suka yi a dã,11kamar yadda suke ta yi daga ranar dana umarci alƙalai su kasance bisa mutane na Isra'ila. Yanzu zan ba su hutawa daga dukkan magabtansu. Bugu da ƙari, "Ni, Yahweh, na furta maka cewa zan yi maka gida.12Sa'ad da kwanakinka suka cika kuma ka kwanta tare da ubanninka, zan tada wani daga zuriyar ka a bayan ka, wanda zai fito daga cikin jikinka, kuma zan kafa mulkinsa.13Shi zai gina gida domin sunana, kuma ni zan kafa kursiyin mulkinsa har abada.14Zan zama uba a gare shi, shi kuma zai zama ɗana. Idan ya yi zunubi, zan hore shi da sandar mutane da kuma bulalar 'ya'yan mutane.15Amma alƙawarin amincina ba zai barshi ba, kamar yadda da na ɗauke shi daga Saul, wanda na kawar daga gabana.16Gidanka da mulkinka za a tabbatar har abada a gabanka. Kursiyinka zai tabbata har abada.'"17Natan ya yi magana da Dauda ya kuma gaya masa dukkan maganganun nan, ya kuma gaya masa game da wahayin dukka.18Sai sarki Dauda ya shiga ciki ya zauna a gaban Yahweh ya ce, "Wane ne ni, Yahweh Allah, kuma mene ne iyalina har daka kawo ni ga haka?19Yanzu dai wannan ƙaramin abu ne a idonka, Ubangiji Yahweh. Har ma ka yi magana game da iyalin bawanka a kan lokatai masu zuwa, ka kuma nuna mani tsararraki masu zuwa, Ubangiji Yahweh!20Me kuma ni, Dauda, zan ce maka? Ka girmama bawanka, Ubangiji Yahweh.21Sabili da maganarka, domin kuma ka cika nufinka, ka yi wannan babban abu kuma ka bayyana shi ga bawanka.22Saboda haka kai mai girma ne, Ubangiji Yahweh, domin babu wani kamar ka, kuma babu wani Allah sai kai, kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.23Wacce al'umma ce kamar mutanenka Isra'ila, al'umman nan guda ɗaya a duniya wadda, kai Allah, ka je ka fanshe mu domin kanka? Ka yi wannan domin su zama mutanenka, domin ka yiwa kanka suna, ka kuma yi manyan al'amura dana ban tsoro domin ƙasarka. Ka kori al'ummai da gumakunsu daga gaban mutanenka, waɗanda ka kuɓutar da su daga Masar.24Ka kafa Isra'ila a matsayin mutanenka har abada, kuma kai, Yahweh, ka zama Allahnsu.25Saboda haka yanzu, Yahweh Allah, bari alƙawarin da ka yi game da bawanka da iyalinsa ya tabbata har abada. Ka yi yadda ka faɗa.26Bari sunanka ya zama da girma har abada, domin mutane su ce, Yahweh mai runduna shi ne Allah na Isra'ila,' sa'an nan gidana ni, Dauda, bawanka ya tabbata a gaban ka.27Domin kai, Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ka bayyana wa bawanka cewa za ka gina masa gida. Shi yasa, ni, bawanka, na sami ƙarfin hali in yi addu'a gare ka.28Yanzu dai, Ubangiji Yahweh, kai ne Allah, maganganunka abin dogara ne a gare su, kuma ka yi wannan alƙawari mai ƙyau ga bawanka.29Yanzu dai, bari ya gamsheka ka albarkaci gidan bawanka, domin ya dawwama a gabanka har abada. Domin kai, Ubangiji Yahweh, ka faɗi waɗannan abubuwa, da kuma albarkarka gidan bawanka zai zama da albarka har abada."
Ana amfani da wannan jumlar a nan don alamar farkon sabon ɓangaren labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
"bashi hutu daga duk makiyansa da ke kewaye da shi." Anan "hutawa" suna ne na ƙarshe. AT: "ya sa ƙungiyoyin mutane makiya suka daina kai wa Isra'ila hari"
Sida wani nau'in itace ne wanda aka san shi da ƙarfinsa. Idan kuna da kwatankwacin irin bishiyar a al'adunku, zaku iya amfani da wannan sunan, in ba haka ba zaku iya sake amfani da wannan. AT: "Ina zaune a cikin gida mai ƙarfi, madawwami"
Rumfar gidaje ne na ɗan lokaci. Idan baku da tanti a cikin al'adunku, zaku iya kalman wannan daban. AT: "akwatin alkawarin Allah yana zaune a wani wuri na ɗan lokaci"
Anan “zuciya” tana wakiltar hankali. AT: "ku yi abin da kuke ganin ya kamata ku yi"
Anan "tare da kai" yana nufin Allah yana taimakawa da kuma albarkaci Dauda.
Karin magana "kalmar Yahweh ta zo ga" ana amfani da ita don gabatar da saƙo na musamman daga Allah. AT: "Yahweh ya ba Natan sako. Ya ce," ko "Yahweh ya yi magana da wannan saƙon ga Natan:"
Yahweh yayi amfani da wata tambaya don ya nanata cewa ba Dauda bane zai gina gida ga Yahweh. Ana iya fassara wannan tambaya azaman sanarwa. AT: "Ba za ku gina mini gida ba"
Yahweh yayi amfani da tambaya don jaddada cewa bai taɓa tambayar wani daga cikin shugabannin Isra’ila ya gina masa gida ba. AT: "Ban taɓa cewa komai ga kowane shugaban Isra'ila ba"
Waɗannan shugabanni na Isra'ilawa ana maganarsu kamar makiyaya ne kuma mutanen tumaki ne.
Idan Yahweh ya yiwa shugabannin wannan tambaya, da ya yi amfani da tambaya don ya tsawata musu don ba su gina masa gidan itacen ssida ba. Amma, Yahweh ya fada a baya cewa bai yi musu wannan tambayar ba. AT: "Ya kamata ku gina mini gida na itacen sida."
Yahweh ya bayyana alkawuransa ga Sarki Dauda ta bakin annabi Natan.
Wannan baya nufin "a wannan lokacin," amma ana amfani dashi don jan hankali zuwa mahimmin batun da ke biyo baya.
Yahweh yana faɗa wa annabi Natan abin da zai faɗa wa Dauda.
Anan "tare da kai" yana nufin cewa Yahweh ya taimaka kuma ya albarkaci Dauda.
An yi maganar Yahweh wanda ke halakar da maƙiyan Dauda kamar dai Yahweh zai yanke su, kamar yadda mutum zai yanke yanki ko yanke reshe daga itace.
Anan “suna” yana wakiltar mutuncin mutum.
Yahweh ya ci gaba da bayanin alkawuransa ga Sarki Dauda ta bakin annabi Natan.
"Zan zabi wuri"
An yi maganar Yahweh yana sa mutane su zauna a ƙasar dindindin da amintattu kamar zai dasa su a cikin ƙasar. (Duba: fig_metaphor)
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba wanda zai taɓa damunsu"
"daga lokaci"
Bayan da mutanen Isra’ila suka shiga cikin ƙasar Kan’ana kuma kafin su sami sarakuna da za su mallake su, Allah ya naɗa shugabanni da ake kira “alƙalai” don su ja-gorance su a lokacin wahala.
"Zan baku aminci daga dukkan makiyanku." AT: "Zan sa duk makiyinka ya daina kawo muku hari"
Anan kalmar "gidan" yana nufin kakannin Dauda suna ci gaba a matsayin sarakunan Isra'ila. A cikin 2 Sama'ila 7: 4 Yahweh ya tambayi Dauda idan shi ne zai gina wa Yahweh gida. A can “gida” yana wakiltar haikalin. Idan yarenku yana da kalmar da zata iya bayyana duka ra'ayoyin, yi amfani da shi a nan da kuma cikin 2 Sama'ila 7: 4.
Yahweh ya ci gaba da bayanin alkawuransa ga Sarki Dauda ta bakin annabi Natan.
Waɗannan jimlolin biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma an haɗa su don ƙarfafawa. Dukansu hanyoyi ne masu ladabi don magana akan mutu da mutuwa.
An yi magana game da sanya Yahweh daga zuriyar Dauda kamar Yahweh zai ɗaga shi ko ɗaga shi.
Wannan karin magana ne wanda ya nufin mutumin zai zama zuriyar Dauda.
Anan “kursiyi” yana wakiltar ikon mutum ya yi sarauta. AT: "Zan sanya mulkinsa a Isra'ila ya dawwama har abada"
Annabcin da ke 2 Sama'ila 7: 12-14 yana nufin Suleman, ɗan Dauda. Amma, fannonin annabcin za su cika ta wurin Yesu. Don haka, a nan ya fi kyau fassara kalmomin "uba" da "ɗa" tare da kalmominku na yau da kullun don mahaifa da ɗansu.
Yahweh ya gama kwatanta alkawuransa ga Sarki Dauda ta bakin annabi Natan.
Kalmar "aminci" suna ne wanda ba a fahimta wanda za'a iya bayyana shi da "aminci mai kauna." AT: "Ba zan taɓa daina ƙaunarsa da aminci kamar yadda na daina son Saul ba"
A nan kalmar "gida" tana wakiltar zuriyar Dauda, waɗanda za su yi sarauta kamar sarakuna. Anan "masarauta" na nufin abu ɗaya kamar "gida." Hakanan za'a iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Za ku rayu har in ga na kafa danginku da mulkinsu kan Isra'ilawa har abada"
Anan “kursiyi” yana wakiltar ikon yin sarauta kamar sarki. AT: "Zan sa zuriyarku su mallaki Isra'ila har abada"
Dauda ya yi wannan tambaya don ya bayyana zurfin motsin da ya ji daga jin shelar Yahweh. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Ni da iyalina ba mu cancanci wannan girmamawar ba, ya Yahweh Allah."
Anan gani yana wakiltar hukunci ko kimantawa. AT: "a cikin hukuncinku"
Dauda ya yi amfani da wannan tambaya don jaddada cewa ba shi da sauran abin da zai faɗa wa Yahweh. AT: "Babu sauran abin da zan iya fada muku."
"Saboda abin da kuka alkawarta za ku yi"
"don cim ma abin da kuka shirya yi"
An yi amfani da kalmar "da kunnuwanmu" don ƙarfafawa. AT: "kamar yadda mu da kan mu muka ji"
Dauda yayi amfani da wata tambaya da ya jaddada cewa babu wata al'umma kamar Isra'ila. AT: "Babu wata al'umma kamar jama'arku Isra'ila, al'umma guda a duniya wanda ku, Allah, kuka tafi kuka ceci kanku."
Dauda ya ci gaba da magana da Yahweh.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki.AT: "kuna iya aikata abin da kuka alkawarta mini da iyalina, kuma mai yuwuwar alkawarinku ba zai taba canzawa ba"
Anan "gida" yana wakiltar iyali. AT: "iyalina"
"Na aminta da abinda kake fada"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "zaku ci gaba da albarkar iyalina har abada"
1Bayan wannan ya zamana Dauda ya hari Filistiyawa ya kuma ci su, Sai Dauda ya karɓe Gat da ƙauyukanta daga karkashin linzamin Filistiyawa.2Sa'an nan ya buga Mowabawa, ya gwada mutanensu da igiya ta wurin sasu su kwanta a ƙasa. Ya gwada layi biyu da zai kashe, layi ɗaya mai tsawo sosai da zai bari da rai. Haka Mowabawa suka zama bayi ga Dauda suka biya shi haraji.3Dauda ya buga Hadadeza ɗan Rehob, sarkin Zoba, sa'ad da Hadadeza ya ke tafiya garin ya mai da mulkinsa na dã wajen Kogin Efratis.4Dauda ya ƙwace karusai daga gunsa guda 1,700 da matafiya a ƙasa dubu ashirin. Dauda ya yanke jijiyar ƙafafun dawakai masu jan karusai, amma ya bar wasu domin karusai ɗari.5Lokacin da Armeniyawa na Damaskus suka zo su taimaki Hadadeza sarkin Zoba, Dauda ya kashe Armeniyawa mutum dubu ashirin da biyu.6Sai Dauda ya ajiye ƙungiyoyin sojojinsa a Aram ta Damaskus, kuma Armeniyawa suka zama bayinsa suna biyan haraji. Yahweh ya ba Dauda nasara duk inda ya tafi.7Dauda ya ɗauko garkuwoyin zinariya da suke kan bayin Hadadeza ya kawo su Yerusalem.8Daga Beta da Berotai, biranen Hadadeza, Sarki Dauda ya kwaso tagulla masu ɗumbun yawa.9Da Tou, sarkin Hamat, ya ji Dauda ya kayar da dukkan rundunar Hadadeza,10Tou ya aika Hadoram ɗansa gun Sarki Dauda ya gaishe shi ya kuma sa masa albarka, domin Dauda ya yi yaƙi gãba da Hadadeza ya kuma ci shi, domin kuma a dã Hadadeza ya yi yaƙi gãba da Tou. Hadoram kansa ya zo tare da kayayyakin azurfa, zinariya, da tagulla.11Sarki Dauda ya ƙeɓe waɗannan kayayyaki domin Yahweh, su azurfa da zinariya daga dukkan al'umman da ya ci da yaƙi -12Aram, Mowab, da mutanen Ammon, da Filistiyawa, da Amelik, tare kuma da dukkan kayayyakin ganima na Hadadeza ɗan Rehob sarkin Zoba.13Sunan Dauda ya shahara sa'ad da ya komo daga bugun Armeniyawa cikin Kwarin Gishiri, da su da mutanensu dubu goma sha takwas.14Ya ajiye ƙungiyoyin sojoji cikin dukkan yankin Idom, dukkan Idomiyawa suka zama bayi gare shi. Yahweh ya ba Dauda nasara duk inda ya tafi.15Dauda ya yi mulki bisa dukkan Isra'ila, ya kuma aikata adalci da gaskiya ga dukkan mutanensa.16Yowab ɗan Zeruya shi ne shugaban rundunar yaƙi, Yehoshafat ɗan Alihud kuwa shi ne magatakarda.17Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyata su ne firistoci, Seraya ne marubuci.18Binaya ɗan Yehoyaida shi ne mai lura da Keretiyawa da Feletiyawa, 'ya'yan Dauda su ne manyan hakimai masu ba sarki shawara.
Anan Dauda ya wakilci sojojinsa. AT: "Dauda da sojojin sa sun kai hari ga"
A nan "ya" na nufin Dauda wanda ke wakiltar sojojinsa. AT: "Sa'an nan sun ci nasara"
A nan "layi" "igiya" ne. Dauda ya sa sojojin sun kwanta a ƙasa don a gwada ya kuma kasa su cikin ƙungiyoyi uku. An kashe mutanen a ciki kashi biyu, an kuma bar na ukun a raye.
Anan duka "Dauda" da "Hadadeza" suna wakiltar rundunarsu. AT: "Dauda da rundunarsa sun ci sojojin Hadadeza"
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan sunan wata yanki ne a cikin Aram.
"don dawo da iko kan yanki" ko "don sake kwace yanki"
"sojojin ƙafa 20,000"
Wannan al'ada ce inda ake yanke jijiyoyin baya na kafafu don dawakai ba za su iya gudu ba.
"ajiye shi sosai" ko "an sami isa sosai"
A nan Dauda na wakiltar sojojinsa. AT: "Dauda da sojojinsa sun kashe"
"mazajen Arameniyawa 22,000"
"ya umarci manyan kungiyoyin sojojinsa da su ci gaba da zama a Aram"
A nan Dauda na wakiltar sojojinsa.
Waɗannan sunayen wurane ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan sunan wurin ne.
A nan "Dauda" na wakiltar rundunar sojojinsa. AT: "Rundunar sojojin Dauda sun ci nasara"
"da Amalekawa"
Waɗannan sune kayaki da sojojin suka kwashe daga wurin mutanen da suka yi nasara bisan su.
A nan "suna" na nufin Dauda ya shahara. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Dauda ya shahara sosai"
Wannan sunan wurin ne. Ainihin wurin ba a sani ba.
"mazaje 18,000"
"Ya ummurci ƙungiyoyin sojojinsa su tsaya cikin dukkan yankin Idom"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Magatakarda mutum ne da ke magana da mutanen ya na kuma gaya musu sanarwai na sarkin. AT: "Ahilud shi ne maishaidi"
Waɗanan sunayen ƙungiyar mutane ne. Waɗannan sune masu tsaron Dauda.
1Dauda yace, "Akwai ko ɗaya wanda ya rage cikin iyalin Saul wanda zan nuna masa alheri sabili da Yonatan?"2Akwai wani bawa cikin iyalin Saul mai suna Ziba, aka kuma kira shi ga Dauda. Sarki ya ce masa, "Kai ne Ziba," Ya amsa, "I. Ni ne bawanka."3Sai sarki yace, "Babu ko ɗaya da ya rage daga iyalin Saul wanda zan nuna masa alherin Allah." Ziba ya amsa wa sarki, "Yonatan har yanzu yana da ɗa, wanda yana da gurguntaka."4Sarki ya ce masa, "Ina ya ke." Ziba ya amsa wa sarki ya ce, "Duba, yana cikin gidan Maki ɗan Ammiyel a Lo Deba."5Sa'an nan Sarki Dauda ya aika a ka fito da shi daga gidan Maki ɗan Ammiyel a Lo Deba.6Sai Mefiboshet ɗan Yonatan ɗan Saul, ya zo gun Dauda ya russuna fuskarsa ƙasa ya girmama Dauda. Dauda ya ce, '"Mefiboshet," Ya amsa, "Duba, ni baranka ne!"7Dauda ya ce masa, "Kada ka ji tsoro, gama hakika zan nuna maka alheri sabili da Yonatan mahaifinka, kuma zan mayar maka dukkan ƙasar kakanka, za ka kuma ci kullum a teburina."8Mefiboshet ya russuna ya ce, "Wane ne ni baranka, da za ka dube ni da tagomashi mataccen kare kamar ni?"9Sai sarki ya kira Ziba, baran Saul, ya ce masa, "Duk mallakar Saul da iyalinsa na ba jikan ubangidanka.10Da kai, da 'ya'yanka maza, da kuma barorinka dole ku noma masa gonakansa dole kuma ku yi masa girbi domin jikan ubangidanka ya sami abinci. Gama dole Mefiboshet, jikan ubangidanka, ya riƙa ci kullum a teburina." Ziba yana da 'ya'ya maza goma sha biyar da barori ashirin.11Sai Ziba ya cewa sarki, bawanka zaiyi dukkan abin da ubangijinsa sarki ya dokaci bawansa." Sarki ya ƙara da cewa, "Game da Mefiboshet zai riƙa ci a teburina, kamar ɗaya daga cikin 'ya'yan sarki."12Mefiboshet yana da wani ɗa ƙarami mai suna Mika, Duk waɗanda suke zauna a gidan Ziba barori ne na Mefiboshet.13Sai Mefiboshet ya zauna a Yerusalem, kullum kuwa ya na ci a teburin sarki, koda shi ke gurgu ne a dukkan ƙafafunsa biyu.
"domin ƙaunar da nake yi wa Yonatan"
Wannan sunan mutum ne.
Ziba ya kira kansa "bawanka" don nuna bangirma ga Dauda.
AT: "Zan yi alheri kamar yadda na yi wa Allah alkawari zan zama"
"wanda ƙafafunsa suka lalace." Kalmar "ƙafa" a nan tana nufin ikon tafiya. AT: "wanda ya kasa tafiya"
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan sunan wuri ne.
An fahimci cewa Dauda ya aika da masu kai sako
Ana iya juya kalman nan "zo" kamar "je"
Mefiboshet ya dubi kansa kamar "bawan ka" don nuna bangirma ga Dauda.
"saboda ina ƙaunar mahaifin Yonatan"
Anan "teburina" yana wakiltar kasancewa tare da Dauda ko a gabansa. Cin abinci tare da sarki a teburinsa babban abin girmamawa ne. AT: "koyaushe zaku ci abinci tare da ni"
Wannan tambaya tana nuna cewa Mefiboshet ya fahimci cewa bai da muhimmanci sosai don sarki ya kula da shi. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Ni kamar mataccen kare ne. Ban cancanci ku tausaya min ba."
Anan Mefiboshet yana wakiltar layin Saul, kuma ya kamanta kansa da “mataccen kare.” Karnuka dabbobi ne masu taurin kai, ba a kulawa da su, kuma ba su da wata mahimmanci. Za'a dauki mataccen kare koda bashi da mahimmanci. AT: "irin wannan mutum kamar ni wanda ba shi da daraja kamar mataccen kare"
Anan "yanzu" yayi hutu a cikin babban layin labari. Mai ba da labarin ya ba da bayanan baya game da Ziba.
'ya'ya maza 15 da barori 20
Ziba yana kiran kansa "baranka" kuma yana kiran Dauda "shugabana." AT: "Ni, bawanka zai yi duk abin da kai, ya sarki, ka umurce ni da yi"
Wannan shi ne sunan ɗan Mefiboshet.
A nan "gida" na nufin iyali. AT: "dukka iyalin Ziba"
"duka kafafunsa sun lalace." Anan "ƙafa" tana wakiltar ikon tafiya. AT: "ko da yake ya kasa tafiya"
1Ananan da jimawa sai sarkin mutanen Ammon ya mutu, kuma ɗansa Hanun ya zama sarki a madadinsa.2Dauda ya ce, "Zan nuna alheri ga Hanun ɗan Nahas, kamar yadda mahaifinsa ya nuna mani alheri." Sai Dauda ya aiki barorinsa su kai ta'aziya ga Hanun domin mahaifinsa. Barorinsa suka shiga ƙasar mutanen Ammon.3Amma shugabannin mutanen Ammon suka cewa Hanun ubangijinsu, Kana tsammani da gaske Dauda ya ke girmama mahaifinka saboda ya aiko mutane su yi maka ta'aziya? Ba Dauda ya aiko barorinsa domin su dubi birnin ba, su san shi, domin su hallaka shi?"4Sai Hanun ya ɗauki barorin Dauda, ya aske rabin gemunsu, ya yanke rigunansu har zuwa ɗuwawunsu, a sa'annan ya sallame su suka tafi.5Da suka labarta wa Dauda wannan, ya aika domin ya sadu da su, domin mutanen sun kunyata ainun. Sarki ya ce, "Ku dakata a Yeriko har sai gemunku ya toho, sa'annan ku dawo.6Lokaci da mutanen Ammon suka ga sun zama abin ƙyama ga Dauda, sai suka aika manzanni suka kuma yi hayar Aremiyawan Bet Rehob da Zoba, da sojoji 'yan tafiya a ƙasa dubu ashirin, da sarkin Mãka mai dubun mutane, da mutanen Tob masu mutane dubu goma sha biyu.7Da Dauda ya ji haka, sai ya aiki Yowab da dukkan rundunar sojoji.8Ammonawa suka fito suka ja dagar yaƙi a mashigar ƙofar garinsu, Aremiyawan Zoba kuwa da na Rehob, da kuma mutanen Tob da Mãka, suka tsaya su kaɗai a filaye.9Da Yowab ya ga dagar yaƙi biyu sun fuskance shi gaba da baya, sai ya zaɓi ƙwararrun mayaƙa na Isra'ila ya jera su gãba da Aremiyawa.10Sauran rundunar kuwa, ya bashe su ƙarƙashin jagorancin Abishai ɗan'uwansa ya sa kuma suka ja dagar yaƙi gaba da rundunar Ammon.11Yowab ya ce, Idan Aremiyawa suka sha ƙarfi na, sai kai Abishai ka ƙwace ni, amma idan rundunar Ammon suka sha ƙarfinka zan zo in ƙwace ka.12Ku ƙarfafa, mu kuma nuna kanmu masu ƙarfi ne domin mutanenmu da kuma biranen Allahnmu, gama Yahweh zai yi abin da ke da kyau domin nufinsa.13Sai Yowab da sojojin rundunarsa suka tashi zuwa yaƙi gãba da Aremiyawa waɗanda dole suka gudu daga gaban rundunar Isra'ila.14Da rundunar Ammoniyawa suka ga Aremiyawa sun gudu, sai suma suka gudu daga Abishai suka koma cikin birni. Sai Yowab ya dawo daga fafarar mutanen Ammon ya koma Yerusalem.15Da Aremiyawa suka ga Isra'ila na cinsu, suka sake tattara kansu.16Sai Hadareza ya aika sojojin Aremiya su zo daga ƙasar ƙetaren Kogin Yuferetis. Suka zo Helam da Shobak, sarkin yaƙi na rundunar Hadareza ya shugabance su.17Da aka gaya wa Dauda wannan, sai ya tara dukkan Isra'ila gaba ɗaya, suka haye Yodan, suka iso Helam. Aremiyawa suka ja dagar yaƙi gãba da Dauda suka yaƙe shi.18Aremiyawa suka gudu a gaban Isra'ila. Dauda ya kashe mahayan karusai ɗari bakwai na Aremiyawa, da dubu arba'in na mahaya dawakai. Shobak sarkin yaƙin rundunarsu aka ji masa rauni, ya mutu a nan.19Sa'ad da dukkan sarakunan da ke barorin Hadareza suka ga Isr'ila ta ci su, sai suka biɗi sulhu da Isra'ila suka zama bayinsu. Sai Aremiyawa suka ji tsoron su ƙara taimakon mutanen Ammon.
Waɗannan sunayen maza.
Shugabannin sun yi amfani da tambaya don ba sarki shawara cewa kada ya amince da Dauda. AT: "Ba daidai ba ne ku yi tunanin ...kai! "
Anan "shi" yana nufin birni wanda yake wakiltar mutanen da suke zaune a wurin. AT: "domin cin nasara a kanmu"
Wannan aikin an yi shi ne don cin fuska don wulakanta maza.
A nan "ainun" wani karin magana ne da ke nufin "sosai."
An fahimci cewa ya kamata su koma Yerusalem.
Maganar "zama ƙanshi" kalma ce ta "sun zama abin ƙyama." AT: "sun zama abin ƙyama kamar warin David"
Waɗannan su ne sunayen wuraren.
Anan "birni" yana nufin Rabbah, babban birin Ammonawa
Yaƙin da Aremiyawa da Ammonawa ya ci gaba.
"Ya sanya Abishai ɗan'uwansa ya shugabanci sauran sojoji"
Yowab ya shirya sojoji don yaƙi.
Anan "ni" yana nufin Yowab. Yowab da Abishai suna wakiltar kansu da sojojinsu. AT: "a gare mu, to, ku, Abishai, da rundunarku dole ne su cece mu"
Anan Abishai ya wakiltar kansa da sojojinsa. AT: "daga Abishai da sojojinsa"
Anan "birni" yana nufin Rabbah, babban birnin Ammonawa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da Aremiyawa suka ga Isra'ilawa suna fatattakarsu"
Waɗannan sunayen maza.
Wannan sunan wani wuri ne.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Lokacin da Dauda ya ji wannan"
Anan "Isra'ila" tana wakiltar sojojin Isra'ila. AT: "ya tattara duka sojojin Isra'ila tare"
Anan Dauda ya wakiltar kansa da sojojinsa. AT: "akan Dauda da sojojinsa kuma ya yaƙi su"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ya gane cewa Isra'ilawa sun ci su da yaƙi"
1Ya zamana da bazara, lokacin da sarakuna ke tafiya yaƙi, sai sarki Dauda ya aiki Yowab, da barorinsa, da dukkan rundunar Isra'ila. Suka ragargaza rundunar Ammon, suka kafa wa Rabba sansani. Amma Dauda ya zauna a Yerusalem.2A na nan wata rana da yammaci, Dauda ya tashi daga gadonsa yana tafiya a kan soron fadarsa, Daga nan ya hango wata mata wadda take wanka, matar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai abar sha'awa.3Sai Dauda ya aika ya kuma tambayi mutane waɗanda suka san wani abu game da matar. Sai wani ya ce, "Ashe wannan ba Batsheba ce ba, ɗiyar Eliyam, kuma ashe ba matar Yuriya ba ce Bahitte?"4Dauda ya aika manzanni, aka ɗaukota, ta shiga ciki wurinsa sai ya kwana da ita (gama ba ta daɗe da tsarkake kanta daga hailarta ba). Sa'an nan ta koma gidanta.5Matar ta yi ciki sai ta aika aka gaya wa Dauda; ta ce, "Ina da ciki."6Sai Dauda ya aika wurin Yowab, "Ka aiko mani Yuriya Bahitte. Sai Yowab ya aika wa Dauda Yuriya.7Da Yuriya ya iso, Dauda ya tambaye shi yadda Yowab ya ke, yadda rundunar take, da kuma yadda yaƙin ke tafiya.8Dauda ya cewa Yuriya, "Ka gangara zuwa gidanka, ka wanke ƙafafuwanka." Sai Yuriya ya bar fadar sarki, sai sarki ya aika wa Yuriya kyauta bayan tafiyarsa.9Amma Yuriya ya yi barci a ƙofar fadar sarki tare da dukkan barorin maigidansa, bai kuwa gangara zuwa gidansa ba.10Da aka gaya wa Dauda, "Yuriya bai gangara zuwa gidansa ba." Dauda ya cewa Yuriya, "Ashe ba yanzu ka dawo daga tafiya ba, me yasa ba ka tafi gida ba?"11Yuriya ya amsa wa Dauda, "Akwatin alƙawari, da Isra'ila da Yahuda suna zaune cikin rumfa, maigidana kuma Yowab da barorin maigidana sun kafa sansani a fili. Ƙaƙa fa zan tafi cikin gidana in ci in sha in kuma kwana da mata ta? Na rantse da ranka, ba zan yi wannan abu ba."12Sai Dauda ya cewa Yuriya, "Ka zauna a nan gobe zan barka ka tafi." Sai Yuriya ya zauna a Yerusalem ranar nan da kashegari kuma. Lokacin da Dauda ya kira shi, ya ci ya sha a gabansa,13Dauda ya bugar da shi. Da yamma Yuriya ya fita ya je ya kwanta a gadonsa tare da barorin maigidansa bai gangara zuwa gidansa ba.14Saboda haka da safe Dauda ya rubuta wa Yowab takarda, ya ba da ita ta hannun Yuriya.15Dauda ya rubuta cikin wasiƙar cewa, "A sa Yuriya a gaba in da yaƙi yafi zafi sosai, sa'an nan ku janye daga gare shi, domin a buge shi ya mutu."16Sa'ad da Yowab ya kafa wa birnin daga, ya sa Yuriya a inda ya sani ƙarfafan sojojin abokan gaba za su yi yaƙi.17Da mutanen garin suka fito suka gwabza yaƙi da rundunar Yowab, waɗansu sojojin Dauda suka faɗi, kuma Yuriya Bahitte shi ma aka kashe shi a wurin.18Da Yowab ya aika saƙo ga Dauda yadda dukkan abu ya gudana a yaƙin,19ya umarci manzon cewa, '"Sa'ad da ka gama faɗin komai game da yaƙin ga sarki,20mai yiwuwa sarki ya husata, ya kuma ce maka, "Me ya sa kuka matsa kusa da birnin kuka yi yaƙi? Ba ku sani za su yiwo harbi daga garun ba?21Wa ya kashe Abimelek ɗan Yerubeset? Ba wata mace ce ta jeho dutsen niƙa daga kan garu a kansa ba, sai ya zo ya mutu a Tebez? Me ya sa kuka matsa kurkusa da garun?' Sa'an nan dole za ka amsa, "Bawanka Yuriya Bahitte shi ma ya mutu.'"22Sai manzon ya tashi ya tafi wurin Dauda ya faɗa masa dukkan abin da Yowab ya aike shi ya faɗa.23Sai manzon ya cewa Dauda, "Abokan gãba suka fi mu ƙarfi da fari; suka fafaremu har zuwa jeji, amma muka kora su baya har zuwa ƙofar gari.24Sai maharbansu suka harbi sojojinka daga kan garu, aka kashe waɗansu barorin sarki, shi ma baranka Yuriya Bahitte an kashe shi."25Sai Dauda ya cewa manzon, "Ka faɗa wa Yowab wannan, 'Kada ka da mu, 'Kada ka bar wannan ya ɓata maka rai, gama takobi ya kan hallakar da wannan da kuma wancan. Ka matsa wa birnin lamba da yaƙi, ku kãda shi,' ka kuma ƙarfafa shi."26Sa'ad da matar Yuriya ta ji cewa Yuriya mijinta ya mutu, ta yi makoki sosai domin mijnta.27Sa'ad da makokinta ya wuce, Dauda ya aika aka ɗaukota aka kawota gida a fãdarsa, ta zama matarsa ta kuma haifa masa yaro. Amma abin da Dauda ya yi ya baƙanta wa Yahweh rai.
"Hakan ya faru ne a lokacin bazara." Wannan yana gabatar da sabon abu a layin labarin.
"a lokacin shekara"
Dauda ya aike su yaƙi. Ana iya bayyana wannan a sarari. Kalmar "nasa" tana nufin Dauda. AT: "Dauda ya aika da Yowab, da barorinsa, da dukan sojojin Isra'ila zuwa yaƙi"
"sojojin Ammonawa"
Matar ba ta kan rufin, za ta yi wanka a waje a farfajiyar gidanta. AT: "matar da take wanka a farfajiyar gidanta"
Dauda yana ƙoƙari ya gano ko wacece matar. Kalmar "shi" tana nufin Dauda, amma alama ce ta manzon da Dauda ya aika. Manzo ya nemi mutane game da ita. AT: "manzon ya tambayi mutanen da suka san ta game da wacece ita"
Wannan tambaya tana ba da bayani kuma ana iya rubuta shi azaman bayani. AT: "Wannan ita ce Batsheba ... kuma ita matar Uriah Bahitte."
Da gaske ne Dauda ya aiki manzanni, suka ɗauke ta suka kawo shi wurinsa. AT: "sun kawo ta wurinsa"
Ta shigo fadarsa da cikin dakin kwanan shi. AT: "ta zo wurin da yake"
A nan kalmar “aika” na nufin cewa ta aika ɗan saƙo don ta gaya wa Dauda cewa tana da ciki. AT: "ta aika da saƙo ga Dauda, kuma manzon ya gaya wa Dauda cewa tana da ciki"
A nan kalmar “aika” na nufin Dauda ya aika da manzo. AT: "Sai Dauda ya aika da manzo"
Dauda yana tambaya ko Yowab da sojojin suna cikin koshin lafiya da kuma game da ci gaban yaƙi. AT: "idan Yowab yana cikin koshin lafiya, da sauran sojoji suna cikin koshin lafiya, da yadda yaƙin ke gudana"
Zai yiwu ma'anar kalmar "sauka" ita ce 1) gidan Yuriya yana a wuri mafi ƙanƙanta fiye da gidan sarki ko 2) gidan Yuriya ba shi da muhimmanci sosai fiye da gidan sarki. AT: "Je gidanku"
Wannan jumlar ta magana don dawowa gida don hutawa dare bayan aiki duk rana. AT: "hutawa dare"
Dauda ya aika wani ya kawo wa Yuriya. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "sarki ya aiki wani don ya kai wa Yuriya kyauta"
Kalmar "nasa" tana nufin Yuriya kuma kalmar "maigida" tana nufin Dauda.
Ana amfani da wannan tambaya ne don nuna mamakin Dauda cewa Yuriya bai ziyarci matarsa ba. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Bayan kun dawo daga wannan doguwar tafiya, ya kamata ku gangara zuwa gidanku."
Wannan yana nufin rundunarsu. AT: "sojojin Isra'ila da na Yahuda"
Ana amfani da wannan tambaya ne don jaddada ƙiwarYuriya game da ziyartar matarsa kuma ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Ba daidai ba ne na shiga gidana ... tare da matata yayin da sauran sojoji a cikin runduna na cikin haɗari."
Yuriya ya rantse da alkawari mai ƙarfi cewa ba zai koma gida wurin matarsa ba muddin sauran sojoji suna yaƙi. Ya yi wannan alkawarin ne ta hanyar kwatanta gaskiyar alkawarinsa da tabbaci cewa sarki yana raye. AT: "Na yi alkawari da gaske ba zan yi haka ba"
"Yuriya ya ci ya sha tare da Dauda"
Kalmomin "hannun Yuriya" yana nufin Yuriya kansa. AT: "ya aika da Yuriya da kansa don ya sadar da shi a gare shi"
"a fagen daga inda yakin yafi kamari"
"ka umarci sojoji su juya baya daga gare shi"
"yana iya yi rauni kuma ya kashe"
Ana iya bayyana kalmar "kafa" da kalmomin aiki "kewaye" da "hari." AT: "rundunarsa sun kewaye da afkawa birni"
Kalmar "fadi" hanya ce mai ladabi don nufin sojojin da aka kashe. AT: "An kashe sojojin Dauda" ko "sun kashe wasu sojojin Dauda"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ciki har da Yuriya Bahitte" ko "kuma mutanen garin sun kashe Yuriya Bahitte"
Kalmomin "aika saƙon" yana nufin cewa ya aika ɗan saƙo don ba da rahoto. AT: "Yowab ya aika da manzo wurin Dauda don ya ba da rahoto"
Yowab ya ce Dauda na iya tsawata masa ta hanyar yin waɗannan tambayoyin. Waɗannan tambayoyin ana iya rubuta su azaman maganganu. AT: "Bai kamata ku kusanci birni don yin yaƙi ba. Ya kamata ku san cewa za su yi ta harbi daga bango."
Wannan yana nufin mazajen gari suna harbi da kibiyoyi akan abokan gaba daga saman garun garin. AT: "harba kibau daga saman bangon birni"
Yowab ya ce Dauda na iya tsawata masa ta hanyar yin waɗannan tambayoyin. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Ku tuna yadda aka kashe Abimelek ɗan Yerubeset!"
Yowab ya ce Dauda na iya tsawata masa ta hanyar yin waɗannan tambayoyin. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Ka tuna ya mutu a Tebez lokacin da wata mata ta ɗora masa dutsen niƙa a saman bangon."
Yowab ya ce Dauda na iya tsawata masa ta hanyar yin waɗannan tambayoyin. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Bai kamata ku je kusa da bango ba!"
"ƙofar gari"
"maharba sun harba kibiyoyi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "sun kashe wasu bayin sarki"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "sun kashe bawanka Yuriya Bahitte"
Anan "takobi" yana nufin mutumin da ya kashe wani da takobi. Kashe wani da takobi ana maganarsa kamar takobi yana “cin” mutane. AT: "don mutum ɗaya ana iya kashe shi da takobi kamar yadda aka kashe wani mutum" ko "don kowane mutum zai iya mutuwa a yaƙi"
"Fada ko da karfi"
Anan marubucin yayi magana game da kukan nata sosai kamar dai yana da zurfin ciki. AT: "ta yi kuka sosai" ko kuma "ta yi kuka sosai"
A nan kalmar "aika" na nufin cewa ya aiko ɗan saƙo don ya zo da ita ya kawo ta wurinsa. AT: "Dauda ya aika mata da manzo ya kawo ta gida"
1Sa'an nan Yahweh ya aiki Natan wurin Dauda. Ya tafi wurinsa ya ce, "A kwai waɗansu mutum biyu cikin wani birni. Ɗaya mutumin mai arziƙi ne ɗayan kuwa matalauci.2Mai arziƙin na da tumaki masu tarin yawa a garkunansa,3amma talakan nan ba shi da komai sai dai wata 'yar ƙaramar tunkiya, wacce ya saya ya yi kiwonta. Ta yi girma tare da shi da kuma yaransa. Har ma 'yar tunkiyar takan ci tare da shi ta kuma sha daga moɗarsa, takan yi barci cikin hannuwansa har ma kamar ɗiya take a gunsa. '4Wata rana wani baƙo ya zo gun mutumin nan mai arziƙi, amma mai arziƙin nan bai so ya ɗauki dabba daga cikin nasa garken domin ya ciyar da shi ba. Mai makon haka ya ɗauki 'yar tunkiyar matalaucin nan ya yi wa baƙon abinci da ita.5Dauda ya husata ƙwarai gãba da mutumin nan mai arziƙi, sai ya tasar wa Natan da ihu,6"Na rantse da ran Yahweh, mutumin da ya yi wannan ya cancanci mutuwa. Dole ya biya ninki huɗu tamanin 'yar tunkiyan nan domin ya yi wannan domin kuma bai ji tausayin matalaucin nan ba.7Sai Natan ya cewa Dauda, "Kai ne mutumin! Yahweh, Allah na Isra'ila, ya ce, 'Na naɗa ka sarki bisa Isra'ila, na kuma kuɓutar da kai daga hannun Saul.8Na baka gidan ubangidanka, da matan ubangidanka a hannnuwanka. Na kuma ba ka gidan Isra'ila da Yahuda. Idan dã waɗannan sun yi ƙanƙanta dana ba ka waɗansu abubuwa ƙari bisansu.9To me yasa ka raina dokokin Yahweh, har ka aikata abin da ke na mugunta a idonsa? Ka kashe Yuriya Bahitte da takobi ka ɗauki matarsa ta zama matarka. Ka kashe shi da takobin rundunar Ammon.10Saboda haka yanzu takobi ba zata taɓa rabuwa da gidanka ba, domin ka rena ni ka ɗauki matar Yuriya Bahitte ta zama matarka.'11Yahweh ya ce, "Duba, zan tayar maka da masifa gãba da kai daga cikin gidanka. A idanunka, zan ɗauki matanka in ba da su ga maƙwabcinka, zai kwana da matanka rana katã.12Gama ka yi naka zunubin a asirce, amma ni zan yi wannan a gaban duk Isra'ila, rana katã.'"13Sai Dauda ya cewa Natan, "Na yiwa Yahweh zunubi." Natan ya amsa wa Dauda, "Yahweh ma ya shafe zunubinka. Ba za a kashe ka ba.14Duk da haka, domin ta wurin yin wannan ka rena Yahweh, yaron da za a haifa maka hakika zai mutu."15Sa'an nan Natan ya bar shi ya tafi gida. Yahweh ya kai wa yaron da matar Yuriya ta haifa Dauda hari, da matsanancin ciwo.16Dauda ya roƙi Yahweh domin yaron. Dauda ya yi azumi ya shiga cikin ɗaki ya kwanta a ƙasa dukkan dare.17Dattawan gidansa suka tashi suka tsaya a gefensa, domin su tashe shi daga ƙasa, amma yaƙi ya tashi kuma ya ƙi ya ci tare da su.18Sai ya zamana a rana ta bakwai yaron ya mutu. Barorin Dauda suka ji tsoron su gaya masa cewa yaron ya rasu, domin sun ce, "Duba, sa'ad da yaron ke raye mun yi masa magana bai saurari muryar mu ba. Me zai yiwa kansa idan muka ce masa yaron ya mutu?!"19Amma da Dauda ya ga barorinsa suna raɗa da junansu, Dauda ya gane yaron ya mutu. Ya cewa barorinsa, "Yaron ya mutu?" Suka amsa, "Ya mutu."20Sai Dauda ya tashi daga ƙasa ya wanke kansa, ya shafa mai, ya canza rigunansa. Ya tafi zuwa rumfar sujada ta Yahweh, ya yi sujada a can, sa'an nan ya dawo fadarsa. Da ya buƙata, sai suka sa abinci a gabansa, ya kuma ci.21Sai barorinsa suka ce masa, "Me yasa ka yi haka? Ka yi azumi da kuka saboda yaron, sa'ad da ya ke da rai, amma da yaron ya mutu, ka tashi ka ci abinci."22Dauda ya amsa, "Sa'ad da yaron ke da rai na yi azumi da kuka. Na ce, 'Wa ya sani watakila Yahweh zai yi mani alheri, ya bar yaron da rai?'23Amma yanzu ya mutu, to donme zan yi azumi? Zan iya komo da shi da rai ne? Ni zan je gunsa, amma shi ba zai komo wuri na ba."24Dauda ya ta'azantar da Batsheba matarsa, ya shiga wurinta, ya kwana da ita. Daga baya ta haifi yaro, aka sa wa yaron suna Suleman. Yahweh ya ƙaunace shi25ya kuma aika da saƙo ta hannun annabi Natan cewa a sa masa suna Yedidiya, domin Yahweh ya ƙauna ce shi.26Yanzu dai Yowab ya yi yaƙi gãba da Rabba, birnin masarautar mutanen Ammon, ya kama kagararta.27Sai Yowab ya aiki manzanni ga Dauda ya ce, "Na yaƙi Rabba, na kuma kama mashigar ruwan birnin.28Yanzu fa ka tattaro sauran rudunar ka kafa wa birnin sansani ka ci shi, domin in na ci birnin, za a kira shi da sunana."29Sai Dauda ya tattaro dukkan rundunar ga baki ɗaya suka tafi Rabba; suka yaƙi birnin, suka ci shi.30Dauda ya cire kambin zinariya da ke kan sarkin - nauyinsa talanti guda ne na zinariya, akwai wani dutse mai daraja a cikinsa. Aka ɗora wannan kambi a kan Dauda. Sa'an nan ya fito da ganimar birnin masu ɗumbun yawa.31Ya fitar da mutanen da ke cikin birnin, ya tislasta masu su yi aiki da zartuna, faretani, da gatura; ya kuma sa su su yi aiki a maginar tubali. Dauda ya tilasta wa dukkan biranen mutanen Ammon su yi wannan aiki tuƙuru. Sai Dauda da dukkan rundunarsa suka koma Yerusalem.
ɗan rago
Wannan yana nufin kusancin wannan mutumin da karamin ragonsa. AT: "ya ƙaunace shi kamar ɗaya daga cikin 'ya'yansa mata"
Ya kasance ga baƙonsa ya ci abinci. AT: "don baƙonsa ya ci abinci"
Anan marubucin ya bayyana yadda Dauda ya yi fushi sosai kamar dai jikinsa yana da zafi a zahiri saboda fushinsa. AT: "Dauda ya fusata da" ko "Dauda ya yi fushi ƙwarai"
Wannan yana nufin cewa Dauda ya yi magana cikin fushi ga Natan.
Adadin da aka bukaci attajiri ya biya ga talakan ya ninka na ɗan ragon sau huɗu. "Dole ne ya biya talakawa sau huɗu farashin ragon"
Anan kalmar "hannu" tana nufin iko. AT: "daga ikon Saul"
Anan Yahweh ya bayyana Dauda yana da matan ubangidansa kamar matansa, da cewa suna "a hannunsa." AT: "matan maigidanku a matsayin na ku"
Anan Yahweh yayi magana game da yadda ya ba Dauda ikonsa a matsayin sarki a kan Isra'ila da Yahuda kamar dai ya ba shi gidajen Isra'ila da na Yahuda a matsayin kyauta. Maganar "gidan" na nufin "mutanen." AT: "Na kuma ba ku iko a matsayin sarki a kan Isra'ila da Yahuda"
"da ban baku abin da ya isa ba"
Ana amfani da wannan tambaya don tsawata wa Dauda. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Bai kamata ka raina" ba kuma bai kamata ka aikata abin da ke mugu a gabansa ba! "
Dauda bai kashe Yuriya da kansa ba, maimakon haka ya shirya don a kashe shi a yaƙi. Kalmomin "da takobi" suna wakiltar yadda Yuriya ya mutu a yaƙi. AT: "Kun shirya Uriya Bahitte ya mutu a yaƙi"
Dawuda bai kashe Yuriya da kansa ba, maimakon haka ya shirya don a kashe shi a yaƙi lokacin da Isra’ilawa suke yaƙi da Ammonawa. Kalmomin "da takobi" yana nufin yadda ya mutu a yaƙi. AT: "Kun shirya masa ya mutu a yaƙi da sojojin Ammonawa"
A nan kalmar "takobi" tana nufin mutanen da ke mutuwa a yaƙi. Hakanan, "gidan" Dauda yana nufin zuriyarsa. AT: "wasu daga cikin zuriyarku za su mutu koyaushe a yaƙi"
Anan "gidan" Dauda yana nufin danginsa. AT: "daga cikin danginku"
Anan an ambaci Dauda da idanunsa don jaddada abin da zai gani. AT: "Yayin da kuke kallo"
Wannan jumlar tana magana ne game da mutanen Isra'ila suna da masaniya game da abin da ya faru da matansa kamar dai duk sun shaida hakan da gaske.AT: "a gaban duk jama'ar Isra'ila" ko "kuma duk mutanen Isra'ila za su san da shi"
Yahweh ya gafarta wa Dauda zunubinsa. Wannan ana maganarsa anan kamar Yahweh yana wucewa akan zunubinsa kamar dai wani abu ne wanda yayi tafiya dashi kuma yayi watsi dashi. AT: "an gafarta"
Kalmomin "an haifa muku" yana nufin cewa jaririn Dauda ne. AT: "ɗanka da za a haifa"
Anan marubucin yayi magana ne game da Yahweh yana sa jariri ya kamu da rashin lafiya kamar yadda Yahweh ke kaiwa yaro hari. AT: "Yahweh ya wahalar da yaron cewa ... kuma ba shi da lafiya "ko kuma "Yahweh ya sa jaririn ya ... zama mai rashin lafiya"
"kuma ya bukace shi da ya tashi daga bene
Ana kiran bayin anan da muryoyinsu don jaddada cewa suna magana. AT "bai saurare mu ba"
Bayin suna yin wannan tambaya don nuna tsoronsu. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Muna tsoron kada ya cutar da kansa idan muka gaya masa cewa yaron ya mutu!"
"ya fahimta"
Waɗannan ayoyin suna ƙunshe da tambayoyin magana waɗanda ke jaddada cewa Dauda ya gane cewa Yahweh ya bar wannan ya faru.
Dauda ya yi wannan tambayar don tausayawa cewa babu wanda ya san ko Yahweh zai bar yaron ya rayu. Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ba wanda ya san ko Yahweh zai yi mani alheri ko a'a don yaron ya rayu."
Dauda ya yi wannan tambayadon jin tausayin cewa ba shi da dalilin yin azumi. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Yanzu da ya mutu ba zai da wani amfani ba yin azumin ba kuma."
Dauda yana nuna cewa zai je inda ɗansa yake idan ya mutu. AT: "Lokacin da na mutu zan je inda yake"
Dukansu kalmomin "sun shiga wurinta" da kuma kalmar "kwanciya da ita" suna nufin Dauda yana yin lalata da Batsheba kuma yana nanata abin da suka yi. AT: "ya yi lalata da ita"
Anan “kalma” tana nufin saƙon da Yahweh ya gaya wa Natan ya gaya wa Dauda. AT: "ya aika Nathan ya gaya masa"
Wannan wani suna ne na ɗan Dauda, Suleman, wanda Yahweh ya zaɓa masa.
"Yowab kuwa ya aiki manzanni wurin Dauda su ce masa."
"Auke" wuri ko alama yana nufin karɓar iko da shi. AT: "sun karɓi ikon samar da ruwan garin"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane za su sanya masa suna"
dutse mai daraja irin su lu'u-lu'u, yaƙutu, shuɗin safiya, emerald, ko opal
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sun sanya kambin a kan kan Dauda"
Anan marubucin yayi magana ne game da Dauda lokacin da yake magana da gaske game da sojojin Dauda. AT: "sun fito da ita"
Dauda bai fito da mutanen da kansa ba; sai ya umarci sojojinsa da su fito da su. AT: "Dauda ya umarci sojojinsa su fito da mutanen"
Wannan yana nufin mutanen da ke cikin birane. AT: "dukkan mutanen biranen Ammonawa"
1Ya zama fa bayan wannan sai Amnon ɗan Dauda, ya yi sha'awar 'yar'uwarsa Tama kyakkyawa wanda ubansu ɗaya ne, amma 'yar'uwar Absalom ce uwa ɗaya uba ɗaya, shi ma ɗaya ne daga cikin 'ya'yan Dauda maza.2Amnon ya jarabtu har ya kama ciwo saboda 'yar 'uwarsa Tama. Ita kuwa budurwa ce, a ganin Amnon ba zai taɓa yiwuwa ya yi ma ta wani abu ba.3Amma Amnon ya na da wani aboki mai suna Yonadab ɗan Shimeya, ɗan'uwan Dauda. Yehonadab wani mutum ne mai hila.4Yehonadab ya cewa Amnon, "Me yasa ga ka ɗan sarki, kake damuwa kowacce safiya? Ba za ka gaya mani ba?" Amnon ya amsa masa, "Ina ƙaunar Tamar, 'yar 'uwar ɗan'uwana Absalom."5Sai Yonadab ya ce masa, "Ka kwanta a gadonka ka yi kamar baka da lafiya. Sa'ad da mahaifinka zai zo ganin ka, ka tambaye shi, "Idan ka yarda ka aiko Tama 'yar'uwata ta ba ni wani abu in ci, bari ta girka shi a gaba na, domin in gan shi in kuma ci shi daga hannunta?'"6Sai Amnon ya kwanta kamar ba shi da lafiya. Da sarki ya zo domin ya dube shi, Amnon ya cewa sarki, "Idan ka yarda ka aiko 'yar'uwata Tama ta yi mani ɗan abinci saboda rashin lafiyata domin in ci daga hannunta.'"7Sai Dauda ya aika saƙo ga Tama a fãdarsa, cewa, "Ki tafi yanzu gidan ɗan'uwanki Amnon ki shirya masa abinci."8Sai Tama ta tafi gidan ɗan'uwanta Amnon in da ya ke kwance. Sai ta ɗauki ƙullu ta cuɗa ta yi waina a idonsa, sa'an nan ta toya.9Ta ɗauki kaskon kuma ta ba shi wainar, amma ya ƙi ci. Sa'an nan Amnon ya cewa waɗanda ke wurinsa, '"Kowa ya fita waje, ku ba ni wuri." Sai kowanne ɗayan su ya fita daga gare shi.10Sai Amnon ya cewa Tama, "Kawo abincin nan ɗakina domin in ci daga hannunki." Sai Tama ta ɗauki wainar da ta yi, ta kawo ta cikin ɗakin Amnon ɗan'uwanta.11Da ta kawo masa abincin, sai ya cafke hannunta ya ce mata, "Ki zo, ki kwana da ni, 'yar uwata."12Ta amsa masa, "A'a, ɗan'uwana, kada ka matsa mani, domin ba makamancin abu haka da ya kamata ya faru a Isra'ila. Kada ka yi wannan abin kunya!13Ƙaƙa zan rabu da kunyata? Kai kuma fa? Za ka zama kamar ɗaya daga cikin sakarkaru na Isra'ila! Yanzu fa in ka yarda ka yiwa sarki magana, ba zai hana ka ni ba."14Duk da haka Amnon ya ƙi ya saurare ta. Tun da ya fi Tama ƙarfi, sai ya kama ta ya kwana da ita.15Sa'an nan Amnon ya ƙi Tama da mummunar ƙiyayya. Ya ƙi ta fiye da yadda dã ya yi sha'awarta. Amnon ya ce mata,16"Tashi ki tafi." Amma ta amsa masa, "A, a! Wannan babbar muguntar sallamata in tafi ta fi muni da abin da ka yi mani!" Amma Amnon bai saurare ta ba.17Maimakon haka, sai ya kira baransa ya ce, "Ka fitar da wannan mata daga gabana, ka kulle ƙofar a bayanta."18Sai baransa ya fitar da ita ya kulle ƙofar a bayanta. Tama ta na saye da wata taguwa mai ado sosai domin 'ya'yan sarki mata waɗanda budurwai ne suna yin shiga irin haka.19Tama ta baɗa toka a kanta ta keta taguwarta. Ta ɗibiya hannayenta a kanta ta tafi, tana rusa kuka sa'ad da take tafiya.20Absalom ɗan'uwanta ya ce mata, "Ko ɗan'uwanki Amnon ya sadu da ke ne? Amma yanzu ki yi shuru, 'yar uwata. Shi ɗan'uwanki ne. Ka da ki riƙe wannan a zuciya." Haka Tama ta zauna ita kaɗai a gidan wanta Absalom.21Sa'ad da Sarki Dauda ya ji dukkan waɗannan abubuwa, sai ya husata ƙwarai.22Absalom bai cewa Amnon komai ba, gama Absalom ya ƙi shi sabili da abin da ya yi mata da yadda ya kunyatar da 'yar'uwarsa Tama.23Ya zama fa bayan shekara biyu cur, Absalom na da masu sausayar tumaki da ke aiki a Bãl Hazor, wadda ke kusa da Ifraim, Absalom kuma ya gayyaci dukkan 'ya'yan sarki maza su ziyarci wurin.24Absalom ya tafi wurin sarki ya ce, "Duba yanzu, bawanka yana da masu sausayar tumaki. Idan ka yarda bari sarki da barorinsa su zo tare da ni, bawanka."25Sarki ya amsa wa Absalom, "A'a, ɗana kada dukkanmu mu tafi domin za mu wahalshe ka." Absalom ya ƙarfafa sarki, amma bai yarda ya tafi ba, sai dai ya albarkaci Absalom.26Sai Absalom ya ce, "In ba haka ba, idan ka yarda bari ɗan'uwana Amnon ya je tare da mu." Sai sarki ya ce masa, "Donme Amnon zai je tare da ku?"27Absalom ya matsa wa Dauda, sai ya bari Amnon da dukkan 'ya'yan sarki maza su tafi tare da shi.28Absalom ya dokaci barorinsa cewa, "Ku saurara sosai. Sa'ad da Amnon ya soma buguwa sosai da ruwan inabi, kuma sa'ad da zan ce maku, 'Ku hari Amnon,' sai ku kashe shi. Kada ku ji tsoro. Ba nine na dokace ku ba? Ku yi ƙarfin hali ku yi mazakutta."29Sai barorin Absalom suka yiwa Amnon yadda aka dokace su. Sai dukkan 'ya'yan sarki maza suka tashi, kowanne mutum ya haye bisa alfadarinsa ya tsere.30Ya zamana fa, lokacin da suke kan hanya, sai labari ya kai wurin Dauda cewa, "Absalom ya kashe dukkan 'ya'yan sarki maza kuma babu ko ɗaya da ya rage a cikinsu."31Sai sarki ya miƙe ya kekketa tufafinsa, ya kwanta a ƙasa; dukkan barorinsa suka tsaya nan da tufafinsu a yayyage.32Yehonadab ɗan Shimeya, ɗan'uwan Dauda, ya amsa ya ce, "Kada ubangidana ya gaskata cewa sun kashe dukkan samari waɗanda 'ya'yan sarki maza ne, gama Amnon ka ɗai ya mutu. Absalom ya ƙudura wanna abu tun daga randa Amnon ya ɓata 'yar'uwarsa Tama.33Saboda haka fa, kada maigidana sarki ya riƙe wannan rahoto a zuciyarsa har da zai gaskata cewa dukkan 'ya'yan sarki maza suka mutu, gama Amnon ne kaɗai ya mutu."34Absalom ya gudu. Wani bawa da ke tsaro ya tada idanunsa ya ga mutane da yawa suna zuwa a kan hanya a gefen dutse yamma da shi.35Sai Yonadab ya cewa sarki, "Duba, 'ya'yan sarki maza suna zuwa. Ya yi dai-dai da yadda bawanka ya faɗa."36Ya zama fa sa'ad da ya gama magana sai 'ya'yan sarki maza suka iso suka tada muryoyinsu suka yi kuka. Sarki da dukkan barorinsa ma suka yi kuka mai zafi.37Amma Absalom ya gudu ya tafi gunTalmai ɗan Ammihud, sarkin Geshu. Dauda ya yi ta makokin ɗansa da daɗewa.38Sai Absalom ya gudu ya tafi Geshu, inda ya kasance har shekara uku.39Ran Sarki Dauda ya yi marmarin ya tafi ya ga Absalom, gama ya ta'azantu game da Amnon da mutuwarsa.
"Hakan ya faru ne bayan wannan." Ana amfani da wannan jumlar don gabatar da sabon abu zuwa layin labarin.
Amnon da Tama mahaifinsu ɗaya amma ba uwa ɗaya suke ba.
Absalom da Tama mahaifinsu ɗaya da mahaifiyarsu.
Amnon ya yi takaici saboda yana son ya kwana da Tama ƙanwarsa. AT: "Amnon ya yi takaici saboda sha'awar 'yar uwarsa Tamar har ya ji ciwo"
Waɗannan sunayen maza ne. Shimeya ɗan'uwan Dauda.
mai dabara ko yaudara
Wannan tambaya ta buƙata ce don Yehonadab ya gaya masa dalilin da ya sa yake baƙin ciki. Ana iya rubuta shi azaman bayani. AT: "Shin ba za ku gaya mani dalilin da ya sa kuka baƙin ciki ba?" ko "Ina roƙon ka, faɗa mini abin da ya sa kuka baƙin ciki."
Wannan wataƙila buƙata ce don ta ba shi abinci da kansa. AT: "kila baya son ta saka abincin a bakin sa ...a sanya ta ta yi min hidima da kaina"
Abincin ba don rashin lafiyarsa ba ne, a'a ma domin shi ne, saboda ba shi da lafiya. Jumlar "a gabana" buƙata ce ga Tama ta shirya abincin a gabansa. AT: "a gabana saboda ba ni da lafiya"
Wannan yana nufin cewa ya aika ɗan saƙo don ya yi magana da Tama. AT: "Dauda ya aika manzo"
Wannan yana nufin Tama ta yi burodi a gabansa. AT: "a gabansa"
"Fita daga wurin wani" na nufin barin su. AT: "Don haka kowa ya bar shi"
Wannan ita ce buƙata don Tama ta ba shi abincin da kansa. AT: "kuma ku bauta min"
Tana nufin yin lalata da shi. AT: "kar ku tilasta min in yi lalata da ku"
abun kunya sosai
Tama ta ci gaba da magana da Amnon.
Tama ta yi wannan tambaya ce don jaddada irin kunyar da za ta ji idan ta kwana da shi. Tama tayi maganar kawar da kunyarta kamar dai makiyi ne ko azabar da take buƙatar tserewa daga gareta. AT: "Idan kun yi haka, dole ne in jure rashin kunya a duk inda na je"
Ana iya bayyana kalmar "wannan babbar mugunta" azaman aiki. AT: "Zai zama ummunan abu ne ya sa na tafi! Zai zama mafi muni"
Wannan yana nufin kulle ƙofar don kar ta sami damar sake dawowa. AT: "kulle ƙofar don kar ta sake dawowa"
Waɗannan ayyukan makoki ne da baƙin ciki a cikin al'adun Isra'ilawa. AT: "sanya toka a kanta kuma ta yayyaga rigarta don nuna cewa tana baƙin ciki sosai. Sa'an nan don nuna ɓacin ranta, sai ta ɗora hannayenta bisa kai"
Wannan ita ce hanyar ladabi da za a tambaya ita ce Amnon ya yi lalata da ita. AT: "Shin Amnon ɗan'uwanka ya kwana da kai?"
Maganar "riƙe wannan a zuciya" na nufin "damuwa da shi." AT: "Kada ku damu da abin da ya faru"
Wannan yana bayanin cewa shekaru biyu duka sun shude kuma suna gabatar da taron na gaba a layin labarin. Jumlar “cikakkun shekaru” na nufin cewa sun cika shekaru.
Waɗannan mutane ne da suke yanke ulu daga tunkiya.
Wannan sunan wani wuri ne.
Babban ɗan na iya wakiltar mahaifinsa sau da yawa a cikin al'adun Isra'ilawa. Amnon shi ne ɗan farin Dauda.
Dauda ya sani Amnon ba abokin Absalom ba ne.
Anan marubucin yayi magana game da Absalom yana roƙon Dauda ya bar Amnon ya zo kamar yana matsa masa lamba ne. AT: "Absalom ya roƙi Dauda don Amnon ya zo"
Absalom ya yi wannan tambaya ce don ya nanata cewa za a zarge shi da kashe Amnon saboda yana ba su umarni. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Na umarce ku da yin haka." ko "Ni zan kasance da laifin kisan shi saboda na umurce ku da yin haka."
Wannan yana nufin 'ya'yan sarki waɗanda suka bar bikin.
"Ya faru ne." Ana amfani da wannan jumlar a nan don gabatar da taron na gaba a layin labarin.
Anan ya ce labarin ya zo, amma da gaske wani ya zo ya gaya wa Dauda labarin. AT: "cewa wani ya zo ya ba da labarin ga Dauda yana cewa"
Ya yi waɗannan abubuwa ne don ya nuna cewa yana baƙin ciki sosai. AT: "ya yayyaga tufafinsa, ya jefar da kansa a ƙasa yana mai baƙin ciki"
"Maigidana, kada ka yi imani"
Wannan ita ce hanyar ladabi da cewa Amnon ya yiwa 'yar uwarsa fyade.
Maganar "ɗauki abu a zuciya" na nufin "damuwa da shi." AT: "ku damu da wannan rahoton"
Wannan yana nufin cewa bawan yana sa ido ga abokan gaba yayin da yake tsaron bangon garin. AT: "wanene ke tsaro" ko "wanene ke tsaron bangon birni"
A nan ana magana da 'ya'yan da ke kuka kamar muryoyinsu wani abu ne da suka ɗaga sama. AT: "ya yi ihu"
Waɗannan sunayen maza.
Anan an ambaci Dauda da hankalinsa don ƙarfafa tunaninsa. AT: "Sarki Dauda ya dade"
"saboda bai ƙara yin baƙin ciki ba game da mutuwar Amnon." Wannan yana nufin shekaru uku bayan Absalom ya gudu zuwa Geshur.
1Yanzu fa Yowab ɗan Zeruya ya fahimci cewar ran sarki na marmarin ganin Absalom.2Yowab ya aika da kalmar saƙo a Tekowa yasa a kawo masa mace mai hikima. Ya ce mata, "Ina roƙonki kiyi kamar kina makoki kisa tufafin makoki. Ina roƙon ki kada ki shafa mai a jikinki, amma kiyi kamar mace wadda ta daɗe tana makoki domin matacce.3Daga nan sai ki je wurin sarki kiyi magana da shi game da abin da zan kwatanta." Sai Yowab ya faɗa mata maganganun da za ta faɗi a wurin sarki.4Sa'ad da matar nan daga Tekowa ta yi magana da sarki, sai ta kwanta da fuskarta a ƙasa ta ce, "Ka taimake ni, ya sarki."5Sarki ya ce mata, "Me ya faru?" Sai ta amsa, "Gaskiyar ita ce ni gwauruwa ce, maigidana kuma ya mutu.6Ni baiwarka, ina da 'ya'ya biyu, sun yi faɗa tare a cikin saura, ba kuwa wani wanda zai raba su. Ɗaya ya bugi ɗayan har ya kashe shi.7Yanzu duk zuriyar sun tashi gãba da baiwarka, su ka ce, 'Ki ba mu mutumin da ya kashe ɗan'uwansa cikin hannunmu, domin mu kashe shi, domin biyan ran ɗan'uwansa wanda ya kashe.' Da haka kuma za su hallaka magajin. Ta yin haka za su ɓice wutata da ta rage, kuma ba za su bar wa maigidana suna ko zuriya a doron ƙasa ba."8Sai sarki ya cewa matar, "Ki tafi gidanki, kuma zan umarta ayi wani abu domin ki."9Sai matar nan ta Tekowa ta amsa wa sarki, "Ya shugabana, sarki, bari alhakin laifin ya komo kaina da gidan iyalin mahaifina. Sarki da kursiyinsa basu da laifi."10Sai sarki ya amsa, duk wanda ya ce maki wani abu, ki kawo shi wurina, ba zai ƙara taɓa ki ba."11Daga nan sai ta ce, "Ina roƙon ka, bari sarki ya tuna da Yahweh Allahnka, domin kada mai ɗaukar fansar jini ya ƙara hallakar da wani, domin kada su hallaka ɗana." Sai sarki ya amsa, "Bisa ran Yahweh, babu gashin ɗanki ko ɗaya da zai faɗi ƙasa."12Daganan sai matar ta ce, "In ka yarda bari baiwarka ta sake yin magana ga shugabana sarki." Ya ce, "Ci gaba da magana"13Sai matar ta ce, "Donme ka kutta wannan maƙida gãba da mutanen Allah? Gama ta wurin faɗin wannan, sarki ya zama kamar wani mai laifi, saboda sarki bai sake dawo da korarren ɗansa gida ba.14Gama dukkan mu dole mu mutu, kuma muna kama da ruwan da aka zubar a ƙasa, wanda ba za a sake tattara shi ba. Amma Allah ba zai ɗauki rai ba; maimakon haka, ya kan nemi hanya domin waɗanda aka kora su dawo.15Yanzu fa, ganin yadda na zo in faɗi wannan abu ga shugabana sarki, saboda mutane sun sa na ji tsoro. Sai baiwarka ta ce a ranta, 'yanzu zan yi magana da sarki. Maiyiwuwa ne sarki ya aikata bisa ga roƙon baiwarsa.16Watakila sarki zai saurare ni kuma ya ceci baiwarsa daga hannun mutumin da zai hallaka ni da ɗana tare, daga cikin gãdon da Allah ya ba mu.'17Daga nan baiwarka ta yi addua, ta ce, Yahweh, in ka yarda bari maganar shugabana sarki ta ba ni sauƙi, gama kamar yadda mala'ikan Allah ya ke, haka shugabana sarki ya ke wajen faɗin abu mai kyau daga mugunta.' Bari Yahweh Allahnka ya kasance tare da kai."18Daga nan sarki ya amsa wa matar ya ce, 'Ina roƙon ki kada ki ɓoye mani komai da zan tambaye ki." Sai matar ta amsa ta ce, 'Yanzu bari shugabana sarki ya yi magana."19Sai sarki ya ce "Ko hannun Yowab bai tare da ke cikin dukkan al'amarin nan?" Sai matar ta amsa ta ce, "Bisa ga ranka, ya shugaba sarki, ba wani ko ɗaya da zai kuɓuta daga hannun dama ko hagu daga duk wani abin da shugabana sarki ya faɗi. Gama bawanka Yowab ne ya umarce ni ya kuma gaya mani dukkan abubuwan da baiwarka ta faɗi.20Bawanka Yowab ya yi wannan domin ya canza yanayin abin da ya ke faruwa. Shugabana kuma yana da hikima, hikima irinta mala'ikan Allah, kuma ya san dukkan abin da ya ke faruwa a cikin ƙasa."21Sai sarki ya cewa Yowab, Yanzu fa ka duba, zan yi wannan, jeka fa, ka komo da saurayin nan Absalom."22Sai Yowab ya kwanta da fuskarsa ƙasa cikin darajantawa da godiya ga sarki. Yowab ya ce, "Yau bawanka ya sani cewa Na sami tagomashi a idonka, ya shugabana, sarki, da shi ke sarki ya aikata bisa ga roƙon bawansa."23Sai Yowab ya ta shi, ya tafi Geshu, kuma ya zo da AbsalomYerusalem.24Sarki ya ce, "Zai iya komawa gidansa, amma ba lallai ya ga fuskata ba." Absalom ya dawo gidansa, amma bai ga fuskar sarki ba.25Yanzu kuwa a cikin dukkan Isra'ila babu wanda ake yabo domin kyansa fiye da Absalom. Daga tafin sawunsa zuwa bisa kansa babu wani aibi a cikinsa.26Sa'ad da ya aske gashin kansa a ƙarshen kowacce shekara, saboda ya kan yi masa nauyi, yakan auna gashin kansa, ya kan kai kimanin awo ɗari biyu, bisa ga mizanin ma'aunin sarki.27An haifa wa Absalom 'ya'ya uku maza da 'ya mace ɗaya, sunanta Tama. Ita kyakkyawar mace ce.28Absalom ya zauna cikakkun shekaru biyu a Yerusalem, ba tare da ganin fuskar sarki ba.29Daga nan Absalom ya aika a kira Yowab domin ya aike shi wurin sarki, amma Yowab ya ƙi zuwa wurinsa. Har yanzu Absalom ya sake aikawa karo na biyu, duk da haka Yowab ya ƙi zuwa.30Domin wannan Absalom ya ce da barorinsa, "Duba, gonar Yowab tana kusa da tawa, ga shi yana da bali a wurin. Ku je ku sa mata wuta."31Sai barorin Absalom suka sawa gonar wuta. Daga nan sai Yowab ya tashi ya zo wurin Absalom a gidansa, ya ce masa, "Donme barorinka suka sawa gonata wuta?"32Absalom ya amsa wa Yowab, "Duba na aika maka cewa, ka zo nan domin in aike ka wurin sarki ka ce, "Donme na dawo daga Geshu? ya fi mani sauƙi a ce har yanzu ina can. Yanzu bari in ga fuskar sarki, idan bani da gaskiya, bari ya kashe ni.'"'33Sai Yowab ya je wurin sarki ya faɗa masa. Sa'ad da sarki ya kira Absalom, sai ya sunkuyar da fuskarsa har ƙasa a gaban sarki, sarki kuwa ya sumbaci Absalom.
Ana amfani da wannan kalmar a nan don alamar hutu a cikin babban layin labari. Anan marubucin ya faɗi game da sabon mutum a cikin labarin.
Duba yadda zaka fassara sunan wannan mutumin a cikin 2 Samaila 2:13
Wannan yana nufin Yowab ya aika da saƙo wurin Tekowa ya sa ya komo da wata mata a wurinsa. Ana iya rubuta wannan ta hanyar aiki. AT: "ya aika wani da sako zuwa ga Tekowa kuma ya sa ya dawo da mace mai hikima"
Ta yi hakan ne don ta nuna girmamawa da biyayya ga sarki. AT: "ta nuna girmamawa ga sarki ta hanyar kwanciya a ƙasa"
"Daya daga cikin 'ya'yana ya buge dayan da wani abu"
"iyalina duka"
Idan suka kashe ɗan'uwan mai laifi babu ɗan da zai bar gadon dukiyar. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "idan suka yi wannan, za su lalata magajin danginmu"
Anan matar tana nufin ɗanta tilo da yake raye kamar shi ɗan wuta ne. Tana magana ne game da mutanen da ke kashe ɗanta kamar dakatar da ƙona garwashin. AT: "Ta wannan hanyar zasu kashe ɗa tilo da na rage"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "ba za su bar wa mijina suna ko zuriyata ba"
"a cikin ƙasa." Wannan jimlar ta kwatancen tana nanata cewa layin gidan ba zai ci gaba a duniya ba bayan mijinta ya mutu. "Doron ƙasa" yana nufin ƙasa da mutane suke tafiya a kanta.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT "Zan kula da wannan al'amarin a gare ku"
Wannan yana nufin cewa idan mutane suka ce sarki bai yi daidai ba don taimaka wa dangin matar cewa kada sarki ya yi laifi. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "idan kowa ya zarge ku saboda taimaka wa danginmu, za a iya ɗaukar iyalina a matsayin masu laifi maimakon"
nan kalmar “kursiyi” tana nufin duk wanda ya zama sarki a bayansa daga baya. AT: "Sarki da zuriyarsa" ko "Sarki da danginsa"
Anan ana maganar barazanar ana magana ne gaba ɗaya. AT: "ya tsoratar da ku" ko "yayi muku barazanar"
Anan Dauda yayi magana game da mutumin da baya mata barazana ko cutar da ita, ta hanyar cewa mutumin ba zai taɓa ta ba. An nuna cewa Dauda ba zai ƙyale mai yi mata barazanar ya sake damun ta ba. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "Zan tabbatar bai sake yi muku wata barazana ba"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Kalmar "kira zuwa ga hankali" ita ce karin magana ma'anar yin addu'a. AT: "Ina roƙon ka, ku yi addu'a ga Yahweh Allahnku" ko 2) Anan "ku tuna" yana nufin tunawa kuma yana nuna cewa bayan ya tuna Yahweh zai yi alkawari da sunansa. AT: "Da fatan za ku yi alkawari da sunan Yahweh Allahnku"
Wannan yana nufin mutumin da yake so ya rama mutuwar ɗan’uwan da ya mutu. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "mutumin da yake son rama mutuwar ɗan uwana ɗana"
Ma'anar cewa ba za a cutar da danta ba, wanda aka kara ta hanyar cewa ba zai rasa ko da gashin kansa ba. AT: "ɗanka zai kasance da cikakkiyar aminci"
Matar ta yi wannan tambayar don ta tsawata wa Dawuda game da yadda ya bi da Absalom. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Abin da kuka faɗa yanzu ya tabbatar da cewa ba ku yi kuskure ba."
Matar tana kwatanta sarki da wanda yake da laifi don nuna cewa yana da laifi ba tare da faɗi kai tsaye ba. AT: "sarki ya bayyana kansa mai laifi"
"dansa wanda ya koreshi"
Anan matar tayi maganar mutum yana mutuwa kamar ruwa ne ake zubewa a kasa. AT: "Dukanmu dole ne mu mutu, kuma bayan mun mutu ba za a sake dawo da mu da rai ba"
Matar tana nuna cewa ya kamata Dauda ya dawo da ɗansa kansa. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Allah ya dawo da wani wanda ya kora kuma ya kamata ku yi ma ɗanku haka"
Ana iya samar da bayanan da aka fahimta. AT: "saboda mutane sun tsoratar da ni cewa na zo"
Anan an kwatanta Dauda, sarki, da “mala’ikan Allah.” AT: "don sarki kamar mala'ikan Allah ne domin dukansu sun san yadda ake faɗi alheri da mugunta"
Anan kalmar "hannu" tana nufin tasirin Yowab. AT: "Shin Yowab bai taɓa rinjayar ku ba a duk wannan" ko "Shin Yowab ya aiko ku nan don ku faɗi waɗannan abubuwa"
Anan matar ta bayyana wahalar magana da sarki da kuma hana shi gano gaskiyar ta hanyar kwatanta shi da wani mutum da ba shi da tserewa ta kowace hanya. AT: "babu wanda zai iya hana ku sanin gaskiya"
Matar ta gwada hikimar Dauda da hikimar mala'ika don ta nanata yadda yake da hikima. AT: "kai mai hikima ne, kamar mala'ikan Allah"
Yowab ya yi wannan don girmama sarki.
Jumlar "samu tagomashi" karin magana ne wanda ke nufin yarda da wani. Hakanan, “idanu” magana ne na gani, kuma gani yana wakiltar hukunci ko kimantawa. AT: "kun yarda da ni" ko "kun yarda da ni"
"ka aikata abin da na ce ka yi"
Anan kalmar "fuska" tana nufin sarki da kansa. AT: "amma ba zai gan ni ba ... king sarki"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane sun yaba wa Absalom saboda kyawunsa fiye da yadda suka yaba wa wani"
Wannan yana nufin duka mutumin ba shi da aibi. AT: "Babu wani aibu a jikinsa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Absalom yana da 'ya'ya maza uku da mace ɗaya"
Anan “fuskar sarki” tana nufin sarki da kansa. AT: "sarki"
Anan "kalma" ishara ce ta "saƙo." Wannan yana nufin cewa ya aika da saƙo wurin Yowab tare da roƙo. AT: "Absalom ya aika da saƙo ga Yowab yana tambayarsa"
An nuna cewa Absalom yana son Yowab ya zo wurinsa don ya gan shi kuma ya yi roƙo a gare shi don a ba shi damar zuwa ganin sarki. Cikakkiyar ma’anar wannan ana iya bayyana ta a sarari. AT: "ya zo gare shi kuma ya yi masa roƙo domin ya ga sarki"
Absalom yana girmama sarki. AT: "sunkuyar da kai ƙasa don girmama sarki"
Wannan yana nuna cewa sarki ya gafarta kuma ya mayar da Absalom. Cikakkiyar ma’anar wannan ana iya bayyana ta a sarari.
1Ana nan bayan wannan kuma Absalom ya shirya karusa da dawakai domin kansa, tare da mutane hamsin masu gudu a gabansa.2Absalom zai tashi da wuri ya tsaya a bakin hanya mai zuwa ƙofar birni, sa'ad da kowanne mutum ya ke da matsalar da za a kawo wa sarki domin shari'a, daga nan sai Absalom ya kira shi ya ce, "Daga wanne birni ka zo?" sai mutumin ya amsa, "Bawanka daga ɗaya daga cikin kabilun Isra'ila ya ke."3Sai Absalom ya ce masa, Duba, maganarka tana da kyau da kuma gaskiya, amma sarki bai sanya kowa da zai ji maganarka ba."4Absalom ya ƙara da cewa, "Ina ma da ni aka sanya in zama alƙali cikin ƙasar, domin kowanne mutum da ke da kowacce irin matsala ko dalili ya zo wurina, kuma zan yi masa adalci!"5Ya zama kuwa idan kowanne mutum ya zo wurin Absalom domin ya girmama shi, Absalom ya kan miƙa hannunsa ya kama shi ya yi masa sumba.6Absalom ya aikata wannan ga dukkan Isra'ila musamman wanda ya zo wurin sarki domin shari'a. Da haka Absalom ya sace zukatan mutanen Isra'ila.7Ana nan bayan shekaru huɗu sai Absalom ya cewa sarki, "Ina roƙonka ka yardar mani in tafi in cika wa'adin da na yiwa Yahweh cikin Hebron.8Gama bawanka ya yi wa'adi lokacin da nake zama a Geshu cikin Aram, cewa, 'Idan ya tabbata Yahweh ya sake dawo da ni Yerusalem, daga nan zan yi wa Yahweh sujada.'"9Sai sarki ya ce masa, "Tafi lafiya" Sai Absalom ya tashi ya tafi Hebron.10Amma Absalom ya aika da masu leƙen asirin ƙasa cikin dukkan kabilun Isra'ila, ya na cewa, da zarar kun ji busar ƙaho, daga nan dole ku ce, 'Absalom ne sarki cikin Hebron.'"11Mazaje ɗari biyu suka ta fi tare da Absalom daga Yerusalem, waɗanda aka gayyata. Sun tafi cikin rashin sanin su, ba su da masaniyar abin da Absalom ya rigaya ya shirya.12Lokacin da Absalom ke cikin miƙa hadayu, ya aika a kirawo Ahitofel daga garinsa a Gilo. Shi ne mai ba Dauda shawara. Makircin Absalom kuwa ya yi ƙarfi, gama mutanen da ke bin Absalom kullum sai ƙaruwa suke yi.13Wani ɗan saƙo ya zo wurin Dauda ya ce, "Zukatan mutanen Isra'ila sun koma wajen Absalom."14Sai Dauda ya cewa dukkan bayinsa da e tare da shi a Yerusalem, "Tashi bari mu gudu, in ba haka ba a cikinmu babu wanda zai kuɓuta daga hannun Absalom. Mu hanzarta tashi, kada ya same mu da sauri, kuma ya kawo bala'i a kanmu ya bugi birnin da kaifin takobi.15Bayin sarki suka cewa sarki, "Duba, bayin sarki a shirye suke su yi duk iyakar abin da shugabanmu sarki ya ayyana."16Sarki ya fita dukkan iyalinsa kuma suka bi shi, amma sarki ya bar mata goma, waɗanda ƙwaraƙwarai ne domin su kula da fãda.17Bayan da sarki ya fita tare da dukkan mutanen da ke bayansa, suka tsaya a gida na ƙarshe.18Dukkan rundunarsa suka tafi tare da shi, a gaban sa kuma dukkan Keretawa, da dukkan Feletawa, da dukkan Gittiyawa - mutum ɗari shida waɗanda suka bi shi tun daga Gat.19Sa'an nan sarki ya cewa Ittai Bagitti, "Donme za ka zo, tare da mu? Ka koma ka zauna tare da sarki Absalom, gama kai baƙo ne ɗan bauta kuma, ka koma wurinka.20Da ya ke jiya kaɗai ka tafi, donme zan sa ka kai da komowa tare da mu? Gashi kuwa ban ma san inda zan tafi ba. Don haka sai ka juya ka koma ka ɗauki 'yan ƙasarka. Bari bangirmanka da aminci su tafi tare da kai."21Amma Ittai ya amsa wa sarki ya ce, "Na rantse da ran Yahweh, da ran shugabana sarki kuma, hakika duk wurinda shugabana sarki ya tafi, can ne kuma bawanka za shi, ko ya kai ga rayuwa ko ga mutuwa."22Sai Dauda ya cewa Ittai, "Jeka ka ci gaba tare da mu" Sai Ittai Bagitti ya haye tare da sarki, da dukkan mutane da dukkan iyalin da ke tare da shi.23Dukkan ƙasar kuwa ta yi kuka da babbar murya yayin da dukkan mutane suka ratsa ta hayin kwarin Kidron, sarki ma da kansa ya haye. Dukkan mutane suka yi tafiya a ƙasa zuwa wajen hanyar jeji.24Har su Zadok da dukkan Lebiyawa, masu ɗauke da akwatin alƙawarin Allah, suna wurin. Suka ajiye akwatin Allah a ƙasa, Abiyata ya bi su. Suka jira har saida dukkan mutane suka gama fitowa daga cikin birni.25Sai sarki ya cewa Zadok, "Ka ɗauki akwatin Allah ka mai da shi cikin birni. Idan na sami tagomashi a idon Yahweh, zai komo da ni nan, ya kuma sake nuna mani akwatin da wurin zamansa.26Amma idan ya ce, "Ba na jin daɗinka,' Duba Ina nan, bari ya yi mani abin da ya ga ya yi masa kyau."27Sai sarki ya cewa Zadok firist, kai ba mai gani ba ne? Ka koma cikin birni lafiya, da 'ya'yanka biyu tare da kai, Ahimãz ɗanka, da Yonatan ɗan Abiyata.28Duba, a wurin mashigai na jeji zan jira har sai magana ta zo daga gare ku ka sanar da ni."29Sai Zadok da Abiyata suka ɗauki akwatin alƙawari na Allah suka mai da shi cikin Yerusalem, suka kuma zauna can.30Amma Dauda ya haura ba takalmi yana kuka har zuwa Dutsen Zaituna, kuma ya rufe kansa. Kowanne mutum cikin mutanen da ke tare da shi ya rufe kansa, suka hau suna kuka yayin da suke tafiya.31Sai wani ya faɗawa Dauda ya ce, Ahitofel na cikin masu maƙida da Absalom." Dauda ya yi addu'a ya ce, "Ya Yahweh, ina roƙonka ka juyar da shawarar Ahitofel ta zama wawanci."32Ana nan sa'ad da Dauda ya kai kan hanya, inda a ke yiwa Allah sujada, Hushai Ba'arkite ya zo ya sadu da shi da yagaggar tufa da ƙura a kansa.33Dauda ya ce masa, "I dan za ka yi tafiya tare da ni, za ka zama nawaya a gare ni.34Amma idan ka juya cikin birni ka ce da Absalom, 'Zan zama bawanka, ya sarki, kamar yadda na zama bawan mahaifinka a kwanakin baya, haka kuma yanzu zan zama bawanka,' ta haka za ka ruɗar da shawarar Ahitofel domina.35Ba za ka tafi tare da Zadok da Abiyata firist tare da kai ba? Zai zama kuwa duk abin da ka ji a fadar sarki, dole ka faɗawa Zadok da Abiyata firist.36Duba can suna tare da 'yayansu biyu, Ahimãz ɗan Zadok da Yonatan ɗan Abiyata. Dole ta hannunsu za ku aiko mani da dukkan abin da kuka ji."37Sai Hushai, abokin Dauda, ya zo cikin birni yayin da Absalom ya kai kuma ya shiga cikin Yerusalem.
Ana amfani da wannan jumlar don gabatar da taron na gaba a layin labarin.
Waɗannan mutane za su yi gudu a gaban karusai don girmama Absalom. AT: "tare da maza hamsin don gudu a gabansa don girmama shi"
An nuna cewa mutumin ya faɗi batunsa ga Absalom. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Absalom zai tambaye shi menene matsalar sa, sannan mutumin zai bayyana wa Absalom dalilin da ya sa ya nemi adalci. Daga nan Absalom zai ce masa"
Waɗannan kalmomin suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani dasu tare don jaddada cewa shari'arsa mai kyau ce.
"Ji" shari'a na nufin saurarenta da yanke hukunci game da ita. AT: "don yanke hukunci game da shari'arku" ko "don kula da shari'arku"
Wannan aikin gaisuwa ce ta abokantaka. AT: "ku gaishe shi a matsayin aboki ta hanyar rungumar shi da sumbanta"
Wannan jumla yana nufin Absalom ya shawo kan mutanen su zama masu aminci a gare shi maimakon na Dauda. Anan marubucin yayi maganar yadda mutane suka zama masu biyayya ga Absalom da cewa ya sata zukatansu. AT: "Ta wannan hanyar, Absalom ya shawo kan mutanen Isra'ila da su yi masa aminci"
Wannan yana nufin shekaru hudu bayan ya koma Yerusalem. AT: "shekaru huɗu bayan Absalom ya koma Yerusalem, ya"
"zuwa Hebron can can cika wa'adin da na yi wa Yahweh"
"Absalom ya tafi"
Anan wuraren da kabilun Isra’ila suka zauna ana kiransu ƙabilun kansu. AT: "a ko'ina cikin ƙasar kabilun Isra'ila"
"ana busa ƙaho"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda ya gayyata"
"tafi babu laifi"
Wannan yana nufin cewa ya aika da saƙo don ya je wurin Ahitofel ya dawo da shi wurinsa. AT: "ya aika da manzo don ya je ya samo Ahithophel wanda yake"
Anan an ambaci mutanen ta “zukatansu” don jaddada amincinsu ga Absalom. AT: "Mutanen Isra'ila suna da aminci ga" ko "Mutanen Isra'ila suna bin bayan"
Anan Dauda yayi magana game da Absalom da mutanen da suke tare da shi da kansa "Absalom" saboda mutanen suna bin ikon Absalom. AT: "kuɓuta daga Absalom da mutanensa ... tare da mutanensa za su hanzarta ... kuma za su kawo"
"Birni" sunan birni ne wanda yake nufin mutanen da ke cikin birnin. “Bakin takobi” wani maganin sirri ne wanda ke nufin takubban Isra’ilawa kuma ya nanata cewa sun kashe mutanen a yaƙi. AT: "zai afkawa mutanen garinmu kuma ya kashe su da takubbansu"
Anan kalmar "kiyaye" na nufin kulawa. AT: "don kula da gidan sarauta"
Wannan yana nufin gidan karshe da zasu zo yayin barin garin. AT: "a gidan karshe yayin da suke barin garin"
Waɗannan sunayen mutanen da kungiyoyin ne. Fassara sunayen kamar yadda zaka yi a cikin 2 Sama'ila 8:18 da 2 Samaila 6:10.
"Mazaje 600"
Wannan sunan mutum ne.
Wannan tambaya ta jaddada Dauda baya son Ittai ya zo. Ana iya fassara wannan tambaya azaman sanarwa. AT: "Ba na son in sa ku ku yi ta yawo tare da mu."
Wannan ni'ima ce da Dauda yake yi masa. AT: "Bari Yahweh ya kasance mai aminci da aminci a gare ku koyaushe"
Anan mai magana yayi alkawalin da gaske. Zai gwada gaskiyar da zai cika alkawarinsa da tabbaci cewa Yahweh da sarki suna da rai. AT: "Na yi alkawari da gaske cewa rayayyen Yahweh da sarki"
"koda za'a kashe ni ina mai goya maka baya"
Da yawa mutane daga cikin Isra'ilawa suka yi kuka da ƙarfi lokacin da suka ga sarki yana tafiya. Anan an gamsu wannan da cewa duk ƙasar tayi kuka. AT: "Duk mutanen da ke kan hanyar sun yi kuka" ko "Da yawa daga cikin mutanen sun yi kuka"
Wannan sunan wani wuri ne kusa da Yerusalem.
Anan “idanun Yahweh” suna nuni ga tunanin Yahweh da ra’ayinsa. Idan ka "sami tagomashi" a wurin wani yana nufin sun yarda da kai. AT: "Yahweh ya yarda da ni"
"inda gabansa yake." Akwatin alkawarin alama ce ta kasancewar Yahweh. Wannan yana nufin wurin da akwatin yake. AT: "inda aka ajiye shi"
Wannan sunan mutum ne.
Ana amfani da wannan tambaya ta zance don tsawata wa Zadok kuma ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Za ku iya gano abin da ke faruwa."
Wannan yana nufin shi aika saƙo zuwa ga sarki. AT: "har sai kun aiko manzo zuwa gare ni don ya sanar da ni"
A nan sarki ya nuna cewa zai karɓi saƙo wanda zai sanar da shi game da abin da ke faruwa a Yerusalem. AT: "don fada min abin da ke faruwa a Yerusalem"
sanye da takalmi
Wannan alama ce ta makoki da kunya. AT: "kansa ya rufe cikin makoki"
Dauda yana roƙon Yahweh ya mai da shawarar Ahitofel wauta da rashin amfani. AT: "Ya Yahweh a bar duk wata shawara da Ahithophel ya bayar na wauta ne da rashin nasara"
Ana amfani da kalmar "saman ko kan" a nan saboda Dauda ya hau kan tudu kuma yana saman tudu. AT: "a saman tudu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "inda mutane suka taɓa bautar Allah"
David yana ba da shawarar ga Hushai cewa ya ƙi duk abin da Ahitofel ya ba shi shawara. AT: "kuna iya yi min hidima ta hanyar adawa da shawarar Ahitofel"
Dauda ya yi wannan tambaya don ya gaya wa Hushai cewa ba zai kasance shi kaɗai ba. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Zadok da Abiyata firistoci za su kasance a wurin don su taimake ku."
Wannan magana ce gaba ɗaya. Yana nufin dukkan mahimman abubuwa da abubuwan fahimta da yake ji, ba kowace kalma ɗaya yake ji ba.
1Sa'ad da Dauda ya hau har ya wuce kan tudu kaɗan, Ziba bawan Mefiboshet ya gamu da shi da jãkai guda biyu labtattu; a kansu kuwa dunƙulen gurasa guda ɗari biyu na curin kauɗar inabi ɗari, da curin 'ya'yan itacen ɓaure ɗari, da salkar ruwan inabi.2Sarki ya cewa Ziba, "Donme ka kawo waɗannan abubuwa?" Ziba ya amsa ya ce, "Jakai domin iyalin sarki ne su hau, gurasa da wainar itacen ɓaure domin mutanenka su ci, ruwan inabi kuma domin duk wanda ya sũma a cikin jeji ya sha."3Sarki ya ce, Ina jikan shugabanka?" Ziba ya amsa wa sarki ya ce, "Duba, ya tsaya baya cikin Yerusalem, gama ya ce, 'Yau gidan Isra'ila za su mayar mani da sarautar mahaifina.'"4Daga nan sai sarki ya cewa Ziba, "Duba, dukkan abin da ke mallakar Mefiboshet yanzu naka ne,'" Sai Ziba ya amsa, na sunkuya cikin bangirma gare ka, ya shugabana, sarki. Bari in sami tagomashi a idanunka."5Sa'ad da sarki Dauda ya gabato Bahurim, wani mutum daga gidan iyalin Saul ya zo, sunansa Shimei ɗan Gera. Ya fito yana tafiya yana la'antarwa.6Ya jefi Dauda da duwatsu har da shugabannin sarki, duk da sojoji da masu tsaro da ke hannun damansa da hannun hagu.7Shimei ya yi kira cikin la'antarwa, "Tafi daga nan, mutumin banza, mutumin jini!8Yahweh ya sãka wa dukkanku domin jinin iyalin gidan Saul, wanda kake mulki a matsayinsa. Yahweh ya bada mulkin a cikin hannun Absalom ɗanka. Gashi yanzu kuma ka hallaka saboda ka zama mutum mai zubda jini."9Daga nan sai Abishai ɗan Zeruya ya cewa sarki, "Donme wannan mataccen karen zai la'anta shugabana sarki? Ina roƙonka ka yardar mani in haye in fille masa kai."10Amma sarki ya ce, "Ina ruwana da ku, ku 'ya'yan Zeruya? Mai yiwuwa yana la'antani saboda Yahweh ne ya ce masa, "La'anta Dauda.' Wane ne zai ce masa, 'Donme kake la'antar sarki?'"11Sai Dauda ya cewa Abishai da dukkan bayinsa, "Duba, ɗana, wanda aka haifa daga cikin jikina, yana so ya ɗauki raina. Balle wannan mutumin Benyamin da ke marmarin ganin hallaka ta, Ku ƙyale shi kawai ku bar shi ya yi ta la'antarwa, gama Yahweh ne ya umarce shi.12Maiyiwuwa Yahweh ya duba irin gagarumin baƙincikin da ke kaina, ya sãka mani da alheri saboda la'antarwar da ya yi mani yau."13Hakanan Dauda da mazajensa suka yi tafiya kan hanya, Shimei kuma ya zaga gefen gangaren tudu, yana tafiya yana la'antarwa yana jifansa da duwatsu yana zuba masa turɓaya yayin da ya ke tafiya,14Daga nan sarki da dukkan mutanen da ke tare da shi suka zo da gajiya, can ya huta lokacin da suka tsaya da dare.15Absalom kuwa da dukkan matanen Isra'ila waɗanda ke tare da shi, suka zo Yerusalem, Ahitofel kuma na tare da shi.16Ya zama kuwa sa'ad da Hushai - Ba'arkite, abokin Dauda, ya zo wurin Absalom Hushai ya cewa Absalom, "Ran sarki ya daɗe! Ran sarki ya daɗe!"17Absalom ya cewa Hushai, "Wannan ita ce biyayyarka ga abokinka? Donme ba ka tafi tare da shi ba?"18Hushai ya cewa Absalom, "A'a! maimakon haka, shi wanda Yahweh da wannan jama'a da dukkan mutanen Isra'ila suka zaɓa, shi ne mutumin da ni zan zama nasa, kuma zan zauna tare da shi.19Kuma, wanne mutum zan bautawa? Ba gaban ɗansa ya kamata in yi bautar ba? kamar yadda na yi bautar gaban mahaifinka, hakanan zan yi bautar a gabanka."20Sa'an nan Absalom ya cewa Ahitofel sai ka ba mu shawara game da abin da za mu yi."21Ahitofel ya amsa wa Absalom, "Ka je ka kwana da bayin matan mahaifinka waɗanda ya bari domin su kula da fãda, daga nan dukkan Isra'ila za su ji ka zama abin ƙyama ga mahaifinka. Daga nan hannuwan dukkan waɗanda ke tare da kai za su yi ƙarfi."22Sai suka baza wa Absalom rumfa a bisa fãda, Absalom kuwa ya kwana da mata bayin mahaifinsa a idanun dukkan Isra'ila.23Ya zama kuwa shawarar da Ahitofel ya bayar a waɗannan kwanaki ta zama kamar wadda mutum ya ji daga bakin Allah da kansa. Haka dukkan shawarar Ahitofel ta zama a wurin Dauda da Absalom.
"Burodi guda 200" ... 100 gungu " ... 100 curin" (Duba: tranlsate_numbers)
Waɗannan jimlolin suna nufin zabibi ko ɓaure da aka matse tare.
"fatar giya mai cike da ruwan inabi"
Wannan yana nufin mutanen Isra'ila. AT: "mutanen Isra'ila"
Samun zuriyar Saul da aka ba shi izinin yin magana ana magana da shi azaman mayar da mulkin ga danginsu. AT: "zai ba ni damar yin mulkin da kakana ya mulka"
Ziba ba ya durƙusawa a gaban sarki lokacin da yake magana a nan. Wannan yana nufin cewa zai bauta wa sarki da irin tawali'un da zai nuna idan a zahiri yana ruku'u a gabansa. AT: "Zan yi muku biyayya da tawali'u"
Kalmomin "sami tagomashi" na nufin yarda da wani. Hakanan, “idanu” sunaye ne na gani, kuma gani yana wakiltar hukunci ko kimantawa. AT: "Ina son ku faranta mini rai" ko "Ina son ku da ku yarda da ni"
Waɗannan sunan gari ne. Fassara sunan wannan garin kamar yadda kayi a cikin 2 Samuila 3:16.
Waɗannan sunayen maza.
"duk da cewa akwai"
mutumin da yake mugu, mai laifi ko mai karya doka
Anan "jini" yana nufin duk mutanen da yake da alhakin kashe su a yaƙi. AT: "mai kisan kai"
Yahweh yana saka musu ta wurin horon su. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Yahweh ya hukunta"
Anan “jini” yana nuni ga mutanen da aka kashe daga dangin Saul. Sarki shine sanadin mutuwar su. AT: "don kashe yawancin dangin Saul"
Dauda ya yi sarauta a kan mutanen da Saul ya taɓa sarauta. AT: "a wurin wa kuka yi mulki a matsayin sarki"
Anan "hannu" yana nufin sarrafawa. AT: "a cikin ikon Absalom"
Abishai ya yi wannan tambayar ne don ya nuna fushinsa ga mutumin. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Wannan mataccen kare ba zai yi magana da sarki ta wannan hanyar ba."
A nan ana bayyana mutumin da cewa ba shi da daraja ta hanyar kwatanta shi da mataccen kare. AT: "wannan mutumin banza"
An yi wannan tambayar ta magana don gyara 'ya'yan Zeruya. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Ba na son sanin abin da kuke tunani!"
An faɗi wannan azaman tambaya don jaddada cewa amsar ita ce "babu kowa." Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "'Ba wanda zai iya tambayarsa 'Me ya sa kuke zagin sarki?'"
Dauda ya bayyana ɗan nasa wannan don ya jaddada kusancin da ke tsakanin uba da ɗansa. AT: "ɗana na kaina" ko "ɗana ƙaunataccena"
Wannan hanya ce mai ladabi don koma wa kashe wani. AT: "yana so ya kashe ni"
David ya yi amfani da wannan tambayar don ya nuna cewa bai yi mamaki ba cewa mutumin yana so ya kashe shi. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Tabbas wannan mutumin Benyamin yana son halakata!" ko "Ban yi mamakin wannan mutumin Benyamin yana son halakata ba kuma!"
A nan kalmar "bar shi kawai" na nufin hana shi daga abin da yake yi. AT: "Kada ku hana shi la'ana ta"
Anan Dauda yayi magana game da wahala kamar dai dabba ce mai haɗari da mutumin Benyamin ya saukar masa.
Shimai yana tafiya dai-dai da na Dauda da mutanensa, amma Shimei yana kan tudun.
Wadannan tambayoyin an yi su ne don sukar Hushai. Ana iya fassara su azaman sanarwa. AT: "Ka kasance aboki mai aminci ga Dauda; ya kamata ka tafi tare da shi."
Anan Hushai yana nufin Absalom a cikin mutum na uku da ya cire girman kansa kuma ya ɗora shi ga Yahweh da mutanen da suka zaɓe shi. Ana iya rubuta wannan a mutum na biyu. AT: "kai ne wanda ... kai ne mutumin ... tare da kai"
Hushai yayi waɗannan tambayoyin ne don ya nanata cewa yana so ya bauta wa Absalom. Ana iya rubuta su azaman sanarwa. AT: "Ya kamata in bauta wa ɗan Dauda kawai, don haka zan yi aiki a gabansa." ko "Ya kamata in bauta maka, domin kai ɗan Dauda ne."
Ahitofel ya yi magana game da Absalom wanda ya ɓata wa mahaifinsa rai kamar zai zama abin ƙanshi mai daɗi da wari. AT: "ka zama mai zafin rai ga mahaifinka" ko "ka wulakanta mahaifinsa"
Anan aka ambaci mutanen da suka bi Absalom da hannayensu. Labarin zai ƙarfafa amincin mutane ga Absalom ya kuma ƙarfafa su. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Labarin wannan zai ƙarfafa amincin duk waɗanda suka bi ku"
Wannan yana nufin cewa mutane suna iya ganin rumfar kuma Absalom yana tafiya yana fita daga cikin rumfar tare da matan. Maganar "duk Isra'ila" ta zama gama gari, don kawai mutanen da ke kusa da gidan sarauta ne za su iya ganin ta. AT: "inda Isra'ilawa zasu ganshi ya shiga rumfar"
A nan marubucin ya kwatanta yadda mutane suka amince da shawarar Ahitofel da yadda za su amince da shawara kai tsaye daga Allah. AT: "Yanzu mutane sun aminta da shawarar Ahitofel a waccan zamanin kamar yadda za su amince da shi idan ya zo"
A nan bakin Allah yana wakiltar kansa kuma yana ƙarfafa jawabinsa. AT: "kamar dai Allah ne ya faɗi hakan da bakinsa" ko "kamar dai mutum ya ji maganarsa da kansa Allah"
1Daga nan sai Ahitofel ya cewa Absalom, "Yanzu bari in zaɓi maza dubu goma sha biyu, kuma zan tashi in fafari Dauda yau a daren nan.2Zan auka masa lokacin da ya yi raụni ya gaji in kuma ba shi mamaki da tsoro. Mutanen da ke tare da shi za su gudu, sarki kaɗai zan buge.3Zan dawo da dukkan mutane a gare ka. kamar amaryar da ke zuwa wurin mijinta, daga nan dukkan mutane za su zauna lafiya ƙarƙashinka."4Abin da Ahitofel ya faɗi ya faranta wa Absalom rai da dukkan dattawan Isra'ila.5Daga nan sai Absalom ya ce, yanzu ku kira Hushai Ba'akite shima, bari mu ji abin da ya ce."6Sa'ad da Hushai ya zo wurin Absalom, Absalom ya bayyana masa abin da Ahitofel ya faɗi sai ya tambayi Hushai, "Ko za mu iya yin abin da Ahitofel ya ce? In ba haka ba sai ka faɗi shawararka."7Sai Hushai ya cewa Absalom, "Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokacin ba ta da kyau."8Hushai ya ƙara da cewa, "Ka san mahaifinka da mazajensa jarumawa ne masu ƙarfi, kuma suna da zafin rai, kamar damisar da a ka ƙwace wa 'ya'yanta a cikin saura. Mahaifinka mayaƙine, ba zai kwana tare da mutane a daren nan ba.9Duba, yanzu haka mai yiwuwa yana wurin ɓuya cikin wasu ramummuka ko a wani wuri. Za ya zama kuwa idan aka kashe waɗansu mutanenka a farkon harin, iyakar wanda yaji zai ce, 'An yi yanka tsakanin sojojin da ke bin Absalom.'10Daga nan har su sojoji masu ƙarfin zuciya, waɗanda zukatansu suna kama da zuciyar zaki, za su ji tsoro domin dukkan Isra'ila sun sani cewa mahaifinka jarumi ne, kuma mutanen da ke tare da shi suna da ƙarfi ƙwarai.11Shawarata a gare ka ita ce a tattara dukkan Isra'ila a gare ka, daga Dan zuwa Biyasheba, kamar yashin da ke bakin teku yawa, kai kuwa da kanka ka tafi yaƙi.12Daga nan zamu abka masa a wurin da za a same shi, za mu rufe shi kamar yadda raɓa take faɗowa ƙasa. Ba za mu bar ko ɗaya daga cikin mazajensa, ko shi kansa, da rai ba.13Idan ya toge cikin birni, daga nan dukkan Isra'ila za su kawo igiyoyi zuwa ga birnin nan kuma za mu jãshi zuwa cikin rafi, har da ba za a tarar da ko ƙanƙanen dutse ɗaya a wurin ba."14Daga nan sai Absalom da dukkan mazajen Isra'ila suka ce, shawarar Hushai Ba-arkite tafi shawarar Ahitofel." Yahweh ya wajabta ƙin amincewa da shawara mai kyau ta Ahitofel domin a kawo hallakarwa a kan Absalom.15Daga nan sai Hushai ya cewa Zadok da Abiyata firistoci, "Ahitofel ya ba Absalom da dattawan Israi'ila irin wannan shawarar, amma ni na bada wata shawarar dabam.16Yanzu kuwa, sai ku tafi da sauri ku sanar da Dauda; ku ce masa, 'Kada ku yi sansani a daren yau a mashigan Araba, amma ta ko ƙaƙa ka haye, in ba haka ba za a haɗiye sarki da dukkan mutanen da ke tare da shi."17Yanzu Yonatan da Ahimãz suna zama a maɓuɓɓugar En-Rogel. Wata mace baiwa takan je ta sanar da su abin da ya kamata su sani, domin bashi yiwuwa su ɗauki kasadar a yi ta ganinsu suna tafiya cikin birni. Idan saƙo ya zo sukan je su faɗa wa sarki Dauda.18Amma wani saurayi ya gan su a wannan lokacin sai ya faɗa wa Absalom. Sai Yonatan da Ahimãz suka fita a gaggauce suka zo gidan wani mutum a cikin Bahurim, wanda ya ke da rijiya a harabar gidansa, inda suka sauka ciki.19Matar mutumin kuma ta ɗauki murfin rijiyar ta rufe bakin rijiyar da shi, ta zuba hatsi a kai, ba wanda ya san cewa Yonatan da Ahimãz suna cikin rijiyar.20Mutanen Absalom suka zo wurin matar gidan suka ce, "Ina Ahimãz da Yonatan?" Sai matar tace masu, "Sun haye rafi." Bayan da suka dudduba ko'ina ba su same su ba, sai suka koma Yerusalem.21Ya zama kuwa bayan da suka tafi sai Yonatan da Ahimãz suka fito daga cikin rijiyar. Suka tafi su kai wa sarki Dauda rahoto; suka ce masa, "Ku tashi ku haye ruwa da sauri saboda Ahitofel ya bada irin wannan shawarar game da ku."22Daga nan sai Dauda ya tashi da dukkan mutanen da ke tare da shi, suka haye Yodan. Kafin wayewar hasken safiya babu ko ɗaya daga cikin su da ya kasa hayewa Yodan.23Sa'ad da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya yiwa jãkinsa sirdi ya tafi. Ya koma gida cikin nasa birni, ya kimtsa al'amuransa, kuma ya rataye kansa. Ta haka ya mutu aka kuma bizne shi cikin kabarin mahaifinsa.24Daga nan sai Dauda ya zo Mahanayim. Absalom kuma, ya hayeYodan, shi da dukkan mazajen Isra'ila tare da shi.25Absalom kuma yasa Amasa shugaban rundunar yaƙi maimakon Yowab. Amasa ɗan Yeta Isma'ile, wanda ya kwana da Abigel wadda take ɗiyar Nahash 'yar'uwar Zeruya uwar Yowab.26Daga nan Isra'ila da Absalom suka kafa sansani cikin ƙasar Giliyad.27Ya zama kuwa sa'ad da Dauda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabbah na Ammonawa, da Maki ɗan Amiyel daga Lo Deba, da Barzillai Bagiliye daga Rogelim,28suka kawo tabarmin kwanciya da barguna, da masakai da tukwane, da alkama, garin bali, gasasshen hatsi, wake, da ganye,29zuma, da mai, tumaki da manshanu, domin Dauda da mutanen da ke tare da shi su ci. Mutanen nan suka ce, "Mutanen nan suna jin yunwa, da gajiya, da ƙishi a cikin jeji."
Waɗannan kalmomin ma'anar abu ɗaya ne asali kuma ana amfani dasu tare don ƙarfafa raunin Dauda. AT: "mai rauni"
Anan ana iya bayyana kalmar "tsoro" da sifa "ji tsoro." AT: "zai ba shi mamaki kuma ya ba shi tsoro"
Ana nuna cewa yana nufin kashe sarki. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Zan kashe sarki kawai"
Wannan yana nufin duk mutanen da suke tare da Dauda. AT: "dawo da duk mutanen da suke tare da shi"
Anan Ahitofel yayi maganar farin cikin mutane ta hanyar kwatanta shi da farin cikin amarya. AT: "kuma za su zo da farin ciki, kamar amarya tana farin ciki idan ta zo wurin mijinta" ko "kuma za su zo da farin ciki"
Fushin sojoji a nan ana kwatanta su da na uwa mai kai wanda aka sauke da sasa. AT: "suna cikin fushi, kamar uwa mai ɗauke da ɗiyar da aka ƙwace sa" ko "suna da tsananin fushi"
Wannan yana nufin cewa nasa ya yi yaƙe-yaƙe da yawa kuma ya san hanyoyin yaƙi sosai. AT: "ya yi yaƙe-yaƙe da yawa"
Wannan wani wurin ne da zai iya ɓoyewa. AT: "ko a ɓoye a wani wuri"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da sojojinsa suka kashe wasu mutanenku"
Kalmar "yanka" na nufin abin da ya faru inda aka kashe mutane da yawa ta hanyar zalunci. Ana iya bayyana wannan azaman kalma. AT: "An kashe yawancin sojoji da ke bin Absalom" ko "Sojojin abokan gaba sun kashe da yawa daga cikin sojojin da ke bin Absalom"
A nan ana nufin sojoji ta hanyar "zukatansu." Hakanan, jaruntakar ƙarfin su idan aka kwatanta da ta zaki. AT: "wadanda suka yi jarumtaka kamar zakuna" ko "wadanda suka yi jarumtaka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Hakanan, a nan "duk Isra'ila" suna wakiltar sojojin Isra'ila ne kawai. AT: "cewa ku tattara duka sojojin Isra'ilawa"
Wannan kalmar tana nufin daga iyakar arewacin Isra'ila zuwa iyakar kudu. AT: "daga duk al'ummar Isra'ila"
Wannan karin gishiri ne inda ake kwatanta dukkan yashi a bakin teku da yawan sojojin Isra'ila. AT: "da yawa waɗanda da ƙyar za a iya kirga su"
Jumlar "da mutum" na nufin tafi da kanka ba aika wani ba maimakon haka. AT: "sa'annan ka jagorance su zuwa yaƙi"
An bayyana sojojin Absalom da suna rufe sojojin Dauda kamar yadda raɓa take rufe ƙasa da safe. AT: "za mu mamaye da kuma fatattakar sojojin Dauda gaba ɗaya"
Ana amfani da wannan jumlar mara kyau don girmamawa kuma ana iya bayyana ta cikin kyakkyawar siga. AT: "Za mu kashe kowane ɗayan mutanensa"
Duk waɗannan kalmomin suna nufin Dauda. AT: "Dauda kansa"
Wannan yana nufin cewa sojoji za su rurrushe ganuwar birni su ja gutsun su zuwa kogi. AT: "zai lalata garin kuma ya ja duwatsu zuwa ga kogi da igiyoyi"
Wannan karin gishiri ne don bayyana yadda zasu rusa garin kwata-kwata. Ba zai share kowane ƙaramin dutse daga cikin birnin ba. AT: "har sai garin ya lalace gaba ɗaya"
AT: "don mutanen Isra'ila su ƙi kyakkyawar shawarar Ahitofel"
'Kawo' wani abu akan wani yana nufin haifar da hakan garesu. AT: "don haifar da bala'i ga Absalom"
Wannan jumlar, ma'anar "kamar wannan," tana nufin abin da Ahitofel ya ba Absalom tun da farko a cikin 2 Sama'ila 17: 1.
Mashigan wani yanki ne mara zurfin kogi inda mutane zasu iya wucewa. Araba ita ce ƙasar da ke gefen Kogin Yodan.
Wannan yana nufin tabbatar da cewa kayi wani abu. AT: "tabbatar da" ko "tabbatar da cewa kun kasance"
Anan an bayyana sarki da jama'arsa da ake kashewa kamar cewa maƙiyinsu ya haɗiye su. AT: "za a kashe sarki"
Anan ana maganar "sakon" kamar yana zuwa musu, alhali da gaske mace ce ta zo sannan ta kawo saƙo. AT: "Lokacin da ta kawo musu saƙo"
"lokaci daya"
An nuna cewa sun gano cewa saurayin ya gaya wa Absalom game da zuwan su can. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Yonatan da Ahima'az sun gano abin da saurayin ya yi, sai suka tafi"
Wannan sunan karamin gari ne.
"sun saukar da kansu sun buya"
A nan “ruwan” yana nufin Kogin Yodan. AT: "haye da sauri kan kogin"
Karin magana "irin wannan da irin wannan" ana amfani da shi a wurin bayanan da mai karatu ya riga ya sani. Anan ana nufin abin da Ahitofel ya shawarci Absalom ya fara a cikin 2 Samaila 17: 1. Ana iya bayyana wannan bayanin a sarari. AT: "ya ba da shawara cewa Absalom ya tura shi tare da sojoji don su kawo muku hari yanzu"
Ana amfani da wannan jumlar mara kyau don jaddada cewa duk sun haye kogin. Ana iya bayyana shi a cikin tsari mai kyau. AT: "Da gari ya waye kowannensu ya haye Kogin Yodan"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Absalom bai bi shawararsa ba"
Ya shirya wa mutuwarsa ta hanyar gaya wa danginsa abin da za su yi bayan ya mutu. AT: "ya shirya wa mutuwarsa"
"Kuma wannan shi ne yadda"
Waɗannan sunayen wurane ne.
Waɗannan sunayen maza.
Waɗannan sunayen mata.
Waɗannan sunayen maza.
Tabarmin wani abu ne mai laushi da za'a kwana akansa, kuma bargo mayafin mayafi ne.
cikin bukatar ruwa ko wani abin sha
1Dauda ya ƙidaya sojojin da ke tare da shi ya naɗa shugabanni na dubbai da na ɗarurruka a bisansu.2Daga nan Dauda ya aika da rundunar soja, ɗaya bisa uku ƙarƙashin, umarnin Yowab, waɗansu kashi uku kuma ƙarƙashin umarnin Abishai ɗan Zeruya, ɗan uwan Yowab, har yanzu wani kashi na uku kuma ƙarƙashin umarnin Ittai Ba-gitte. Sarki kuma ya cewa rundunar yaƙi, "Lallai zan fita tare daku da kaina, nima."3Amma mazajen suka ce, "Ba dole sai ka je yaƙi ba, gama idan mun gudu ba za su kula da mu ba, ko idan rabin mu sun mutu ba za su kula ba. Amma darajarka a bakin zambar goma tamu ce! Domin wannan ya fi kyau kai ka kasance da shirin yi mana taimako daga cikin birni."4Sai sarki ya amsa masu, "Zan yi duk abin da ku ka ga yafi maku kyau." Sarki ya tsaya a bakin ƙofar birni yayin da dukkan rundunar yaƙi suka fita ɗari-ɗari da dubu-dubu.5Sai sarki ya umarci Yowab, Abishai, da Ittai cewa, "kuyi a hankali da saurayin nan, da Absalom, sabili da ni." Dukkan mutane sun ji cewa sarki ya ba shugabanni wannan umarni game da Absalom.6Rundunar yaƙi suka fita zuwa cikin filin karkara garin suyi yaƙi da Isra'ila; yaƙin ya bazu zuwa cikin kurmin Ifraim.7Rundunar yaƙin Isra'ila sun sha kãshi a wurin a hannun sojojin Dauda; a rannar kuwa aka yi kisa mai yawa a wurin an kashe mazaje dubu ashirin.8Faɗan ya bazu ko'ina cikin ɓangaren ƙasar, mazajen da kurmi ya cinye suka fi waɗanda suka mutu ta kaifin takobi.9Ya kasance kuwa Absalom ya gamu da waɗansu sojojin Dauda. Absalom yana tafiya kan alfadarinsa, alfadarin kuwa ya shiga ƙarƙashin cikin rassa masu kauri na itacen rimi, itacen kuwa ya kama kansa cikin rassan. Yana reto tsakanin sama da ƙasa alfadarin da ya ke haye akai kuwa ya ci gaba da tafiya.10Wani mutum daya gani sai ya fada wa Yowab, "Duba, na ga Absalom rataye a itacen rimi!"11Yowab ya ce da mutumin daya faɗa masa game da Absalom, "Duba! ka ganshi! donme ba ka buge shi a ƙasa ba? Ai da na baka azurfa goma da ɗammara."12Sai mutumin ya amsa wa Yowab, "Koda na karɓi shekel ɗin azurfa dubu, duk da haka bazan miƙa hannuna gãba da ɗan sarki ba, domin mun ji umarnin da sarki ya ba ku, Abishai da Ittai cewa, 'kada kowa ya taɓa saurayin nan Abasalom.'13Da na yi kasada da raina ta wurin ƙarya (kuma babu abin da ke ɓoye a wurin sarki), da ka yashe ni,"14Daga nan sai Yowab ya ce, "Ba zan jira ka ba." Sai Yowab ya ɗauki mãshi uku cikin hannunsa ya caka su cikin zuciyar Absalom, yayin da ya ke da rai ya ke kuma rataye a itacen rimi.15Daga nan majiya ƙarfi guda goma masu ɗauke da sulken Yowab suka kewaye Absalom, suka buge shi, suka kashe shi.16Yowab ya busa ƙaho, rundunar yaƙi suka dawo daga runtumar Isra'ilawa, gama Yowab ya rinjayi mutane.17Suka ɗauki Absalom suka jefa shi cikin babban rami a cikin kurmin; suka bizne jikinsa cikin ƙarƙashin babban tarin duwatsu, sa'an nan dukkan Isra'ila suka gudu, kowanne mutum zuwa nasa gida.18Yanzu kuwa, lokacin da Absalom ya ke da rai, ya gina wa kansa babban ginshiƙin dutse cikin kwarin sarki, gama ya ce, "Bani da ɗan da zai ɗauki suna na wanda za a tuna da ni." Ya kira ginshiƙin da sunansa, ana kiran sunansa Surar Absalom har wa yau.19Sa'an nan Ahimãz, ɗan Zadok ya ce, "Bari in gudu yanzu in kai wa sarki labari mai daɗi, yadda Yahweh ya kuɓutar da shi daga hannun abokan gabarsa."20Yowab ya amsa masa, "Ba kai ne za ka zama mai ɗaukar labari yau ba; amma wata rana za ka kai. Yau ba za ka kai kowanne labari ba gama ɗan sarki ya mutu."21Sai Yowab ya cewa Ba-kushi, "Jeka ka faɗa wa sarki abin da ka gani. Sai Ba-kushi ya sunkuyar da kansa gaban Yowab, sai ya ruga.22Daga nan sai Ahimãz ɗan Zadok ya sake cewa Yowab, ba tare da la'akari da komai zai faru ba, ina roƙon ka ka bar ni in ruga in bi Ba-kushen."Yowab ya amsa, donme kake so ka ruga, ɗana? Ganin ba za ka sami wa ta ladar kai labarin ba?"23Kome ya faru, in ji Ahimãz, "Zan ruga" Yowab ya amsa ya ce masa, "Ruga." Sa'an nan Ahimãz ya ruga ta hanyar fili, ya tsere wa Ba-kushen.24Dauda kuwa yana zaune tsakanin ƙofofi biyu na ciki da na waje. Mai tsaro kuma ya hau benen ƙofa har zuwa cikin rufin garu ya tãda idanunsa. Da ya duba, sai ga wani ya sheƙo a guje shi kaɗai.25Sai mai tsaron ya tada murya ya faɗa wa sarki. Sai sarki ya ce, "Idan shi kaɗai ne, akwai labari a bakinsa." Mai gudun ya zo kurkusa kuma dab da birnin.26Sai mai tsaron ya lura da wani mutum kuma yana gudu, sai mai tsaron ya kira mai kula da ƙofa; ya ce, "Duba, ga wani mutum kuma yana gudu shi kaɗai," Sai sarki ya ce, "Shi ma yana kawo labari."27Sai mai tsaron ya ce, "A ganina irin gudun na gaban nan ya yi kama da gudun Ahimãz ɗan Zadok." Sarki ya ce, "Shi nagarin mutum ne, yana zuwa da labari mai daɗi."28Daga nan sai Ahimãz ya yi kira ya cewa sarki, "Komai lafiya lau ne" kuma ya sunkuyar da kansa da fuskarsa gaban sarki har ƙasa ya ce, "Mai albarka ne Yahweh Allahnka! Ya ba da mutanen da su miƙar da hannayensu gãba da shugabana sarki."29Sai Sarki ya amsa, "Ko saurayin nan Absalom yana lafiya?" Ahimãz ya amsa ya ce, lokacin da Yowab ya aike ni, bawan sarki, wurinka, ya sarki, na ga babban hargitsi, amma ban san ko mene ne ba."30Sai sarki ya ce, "Juya gefe ka tsaya nan." Sai Ahimãz ya juya ya tsaya cik.31Nan da nan Ba-kushen ya zo ya ce, "Akwai albishir mai daɗi domin shugabana sarki, gama Yahweh ya ɗaukar maka fansa yau daga dukkan waɗanda suka tayar maka."32Daga nan sai sarki ya cewa Ba-kushen, ko lafiya dai da saurayin nan Absalom?" Ba-kushen ya amsa, maƙiyan shugabana sarki, da dukkan waɗanda suka tayar maka domin su cutar da kai, "Su zama kamar yadda saurayin nan ya ke."33Daga nan sarki ya yi juyayi mai zurfi, ya tafi ya hau kan ƙofar bene ya yi kuka. Yayin da ya ke baƙinciki yana tafe yana cewa "ɗana Absalom, ya ɗana, Absalom! Da ma ni ne na mutu a madadinka, Absalom, ɗana, ɗana!"
Dauda bai ƙidaya mutanen duka ba, amma waɗansu mutane suka ƙidaya. AT: "Dauda ya yi umarni don a ƙidaya sojojin da suke tare da shi kuma ya sanya" ko "Dauda ya tsara sojojin da suke tare da shi kuma ya naɗa su"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) waɗannan lambobin suna wakiltar ainihin adadin sojojin da waɗannan kaftin ɗin suka jagoranta. AT: "shugabannin sojoji 1,000 da shugabannin sojoji 100" ko kuma 2) kalmomin da aka fassara a matsayin "dubbai" da "ɗaruruwan" ba sa wakiltar ainihin lambobi, amma sunaye ne na manya da ƙananan ƙungiyoyin soja. AT: "shugabannin sojoji na manyan rundunonin soja da shugabannin kananan rundunonin sojoji"
Kyaftin mutum ne wanda yake da iko akan ƙungiyar sojoji.
Wannan yana nufin cewa zai fita tare da su zuwa yaƙi. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Ni da kaina zan tafi tare da ku zuwa yaƙi" ko "Ni da kaina zan tafi tare da ku zuwa yaƙi"
Kalmar "rabi" tana nufin daya cikin biyu dai-dai.
Wannan yana nufin cewa sojojin abokan gaba suna tunanin kashe David wanda ya fi daraja fiye da kashe sauran mutanen 10,000. Lambar 10,000 a nan ƙari ce da aka yi amfani da ita don jaddada adadi mai yawa na mutane. AT: "sun gwammace su kashe ku fiye da kashe mu 10,000" ko "kashe ku ya fi daraja a gare su fiye da kashe yawancinmu"
Dauda zai iya taimaka musu daga gari ta hanyar yi musu nasiha da kuma aika mutane su taimake su. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "cewa ku tsaya anan garin ku aiko mana da taimako"
"Saboda ni, kada ka cutar da saurayin, Absalom." Kalmomin "a hankali" na nufin kyautatawa wani kuma ba cutar da shi ba.
Wannan yana nufin cewa sun fita sun yi yaƙi da su a yaƙi. AT: "ya fita zuwa karkara ya yi yaƙi da Isra'ila"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "A can sojojin Dauda suka ci sojojin Isra'ila"
taron da aka kashe mutane da yawa ta hanyar zalunci
Anan "gandun daji" an bayyana shi kamar yana da rai kuma zai iya aiki. "Takobi" yana nufin sojojin Dauda waɗanda suka yi yaƙi da takuba. AT: "abubuwa masu haɗari a cikin gandun daji sun kashe mutanen da suka fi sojojin Dauda waɗanda aka kashe da takubansu"
Wannan lamari ne da ya faru yayin yakin. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Yayin yakin, Absalom ya gamu da wasu daga sojojin Dawuda"
Absalom yana da dogon gashi wanda ya kamu a rassan itacen. AT: "an kama gashinsa a rassan itacen"
"a cikin iska"
Wannan tambaya ta magana tana nufin ya kamata ya kashe shi. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. Maganar "bugi ƙasa" na nufin kisa. AT: "Ya kamata ku buge shi ƙasa!" ko "Ya kamata ku kashe shi nan da nan!"
Kalmomin "mika hannuna" na nufin kai hari. AT: "da ba za a auka wa ɗan sarki ba"
Anan "shafar" yana nufin "cutarwa." AT: "Babu wanda ya isa ya cutar da shi" ko "Kada ku cutar"
Anan mutumin yayi magana game da yadda sarki ya san kusan duk abin da ke faruwa kamar dai komai abu ne na zahiri ya san wurin. AT: "babu abin da sarki bai sani ba" ko "sarki yana jin labarin duk abin da ya faru"
Yowab yana nufin kada ya ci gaba da magana da mutumin. AT: "Ba zan sake ɓata lokacin magana da ku ba"
Anan zuciyar Absalom tana nufin kirjinsa ko na sama. AT: "kirji"
Wannan ya bayyana abin da Yowab ya umarta ta busa ƙaho. AT: "Sai Yowab ya busa ƙaho don kiran sojoji, kuma sojojin suka komo daga bin Isra'ila"
Bayan sun sanya gawarsa a cikin ramin sai suka rufe shi da tarin duwatsu. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "sun lullube gawarsa da tarin tarin duwatsu" (Duba: explicit)
Anan “duka Isra’ila” na nufin sojojin Isra’ila. AT: "yayin da duk sojojin Isra'ila suka gudu"
Wannan sunan wani wuri ne.
Absalom yayi amfani da kalmar "sunana" don yana nufin kansa da danginsa. AT: "don ci gaba da suna na, wanda mutane zasu tuna ni da ita"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "don haka mutane suka kira shi Surar Absalom daga wannan ranar zuwa"
A nan Ahima'az ya yi maganar gudu don ya je ya gaya wa sarki kyakkyawan labari kamar bisharar abu ne da yake ɗauka. AT: "ku gudu ku gaya wa sarki labari mai daɗi"
Anan "hannu" yana nufin sarrafawa. AT: "ikon makiyansa"
"wanda ya bada labari"
Yowab yana gaya masa ya je ya faɗa wa sarki labarin yaƙi.
Anan ana maganar mai gadin da yake son ganin wani abu kamar ya ɗaga idanunsa. AT: "an duba bayan gari"
Anan sarki yayi magana game da mutumin da yake da sako kamar cewa labarin abu ne zaune a bakinsa. AT: "yana da labarai da zai gaya mana"
Mai tsaron ya kwatanta yadda mutumin ya gudu da yadda Ahima'az yake gudu don a nuna cewa watakila shi ne. AT: "Ina jin mutumin da ke gudu a gaba shi ne Ahima'az ɗan Zadok, saboda yana gudu kamar Ahima'az"
Ya yi wannan don girmama sarki. AT: "Ya sunkuyar da kai gaban sarki fuskarsa a ƙasa don girmama sarki"
"Yabi Yahweh." Anan “albarka” na nufin yabo.
Anan Ahima'az yayi maganar mutanen da ke adawa da sarki kamar suna ɗaga hannuwansu a gabansa. AT: "mutanen da suka yi adawa da yaƙi da maigidana sarki"
Wannan yana nufin cewa mutane suna yin kamar abubuwa ba dai-dai bane.
"Motsa daga kan hanya" ko "Ka tsaya gefe"
Wannan yana nufin adawa. AT: "akasi"
Ba-kushen yana amfani da kwatanci a matsayin hanyar ladabi don gaya wa sarki cewa Absalom ya mutu. Ana iya bayyana wannan kai tsaye. AT: "Ina son duk makiyanku ... su mutu kamar yadda saurayin ya mutu"
"bai ji daɗi sosai ba"
1Aka faɗa wa Yowab cewa, "Duba, sarki yana kuka yana makoki domin Absalom."2Wato nasara ta ranar nan ta koma makoki ga dukkan jama'a, gama jama'a sun ji cewa a ran nan sarki yana makoki saboda ɗansa."3Ya zama lallai ga sojoji su saɗaɗa shiru cikin birni a wannan ranar, kamar mutane masu jin kunya su kan sace jiki sa'ad da suka gudu daga yaƙi.4Sarki ya rufe fuskarsa ya yi kuka da babbar murya, "Ya ɗana Absalom, Absalom, ya ɗana, ya ɗana!"5Yowab ya shigo cikin gida wurin sarki ya ce masa, "Yau ka kunyatar da fuskokin dukkan sojoji, waɗanda suka ceci ranka yau, da rayukan 'ya'yanka maza da mata, da rayukan matanka, da rayukan matanka bayi,6saboda kafi ƙaunar waɗanda suke ƙinka, kuma kana ƙin masoyanka. Gama yau ka nuna cewa Hafsoshi da sojoji ba komai bane a gare ka. Yau na gaskanta da Absalom ya rayu, dukkan mu kuma da mun mutu, wannan da ya faranta maka rai.7Yanzu fa sai ka tashi ka fita kayi magana mai daɗi ga sojojinka, gama na rantse da Yahweh, idan baka tafi ba, babu wanda zai zauna tare da kai a daren nan. Wannan zai fi maka muni cikin dukkan bala'o'in da suka faru da kai daga ƙuruciyarka zuwa yau."8Sa'an nan sarki ya tashi ya zauna a ƙofar birni, aka faɗa wa dukkan jama'a, cewa, "Duba fa, ga sarki can yana zaune a cikin ƙofa." Daga nan sai dukkan mutane suka zo gaban sarki. Isra'ila kuma suka gudu, kowanne mutum ya tafi gidansa.9Dukkan mutane kuma suna ta muhawara da juna cikin dukkan kabilun Isra'ila suna cewa, "Sarki ya cece mu daga hannun abokan gabanmu, ya kuma cece mu daga hannun Filistiyawa yanzu kuma ya gudu daga ƙasar saboda Absalom.10Absalom kuma wanda muka sarautar da shi bisa kanmu, ya mutu cikin yaƙi, Yanzu fa donme bama cewa komai game da dawo da sarki?"11Sarki Dauda ya aika wurin Zadok da Abiyata firist cewa, 'Kuyi magana da dattawan Yahuda cewa, donme kune na ƙarshe wajen dawo da sarki fãdarsa, da shi ke sarki ya sami tagomashi daga dukkan Isra'ila, a dawo dashi fãdarsa?12Ku 'yan'uwana ne, ƙashina ne da namana. Donme ku ne na ƙarshen dawo da sarki?'13Ku cewa Amasa, 'Kai ba ƙashina bane da kuma namana? Allah ya yi mani haka, ya kuma ƙara mani, idan ba ka zama shugaban runduna ta ba daga yanzu zuwa nan gaba a madadin Yowab.'"14Kuma ya rinjayo da zukatan dukkan mutanen Yahuda kamar zuciyar mutum guda, sai suka aika wa sarki cewa, "Ka dawo, kai da dukkan mutanenka."15Sai sarki ya dawo, ya zo Yodan. Mutanen Yahuda kuma suka zo Gilgal don su tarbi sarki, daga nan suka kawo sarki ƙetaren Yodan.16Shimei ɗan Gera, Benyamine, wanda ya zo daga Bahurim, ya hanzarta ya sauko tare da mutanen Yahuda domin taryar sarki Dauda.17Akwai mutanen Benyamin dubu goma tare da shi, da Ziba bawan Saul, da kuma 'ya'yansa goma sha biyar da barorinsa ashirin tare da shi.18Suka haye taYodan a gaban sarki. Suka haye domin su kawo iyalin sarki domin ya yi abin da ya yi masa kyau. Shimei kuma ɗan Gera ya sunkuya a gaban sarki tun kafin ya fara haye Yodan.19Sai Shimei ya cewa sarki, "Kada, shugabana, ya same ni da laifi ko ya tuna da taurin kan da bawanka ya yi a ranar da shugabana sarki ya bar Yerusalem. In ka yarda, kada sarki ya ajiye wannan a zuciyarsa.20Gama bawanka ya sani na yi zunubi. Duba, shi yasa na zo yau a matsayin na fari daga cikin dukkan iyalin Yosef na zo domin in taryi shugabana sarki."21Amma Abishai ɗan Zeruya ya amsa ya ce, "Ba za a kashe Shimei ba saboda wannan, saboda ya la'anta shafaffe na Yahweh?"22Daga nan sai Dauda ya ce, "Me zanyi da ku, ku 'ya'yan Zeruya, da yau za ku zama maƙiyana? Za a kashe wani mutum yau a cikin Isra'ila? Gama bana sani cewa yau ni ne sarki bisa Isra'ila ba?"23Sarki kuwa ya cewa Shimei, "Ba za ka mutu ba" Sai sarki ya yi masa alƙawari tare da rantsuwa.24Daga nan sai Mefiboshet ɗan Saul ya zo domin ya tarbi sarki. Bai kuwa gyara ƙafafunsa ba, ko ya aske gemunsa, ko ya wanke tufafinsa tun daga lokacin da sarki ya tashi har ranar daya dawo cikin salama.25Ya zama kuwa sa'ad da ya zoYerusalem domin ya tarbi sarki, sarki ya ce masa, "Donme ba ka tafi tare da ni ba, Mefiboshet?26Sai ya amsa, "Ya shugabana sarki, bawana ya ruɗe ni, gama Na ce, bari in yi ma jakina sirdi, domin in hau in tafi tare da sarki, gama bawanka gurgu ne.'27Bawana Ziba yaci zarafina, bawanka, a wurin shugabana sarki. Amma shugabana sarki kamar mala'ikan Allah ya ke. Don haka, sai ka yi duk abin da kaga ya gamshe ka.28Gama duk iyalin gidan mahaifina sun zama matattun mutane gaban shugabana sarki, amma ka sanya bawanka a cikin masu ci a teburinka. Wanne 'yanci nake dashi kuma da zan ƙara yiwa sarki kuka?"29Daga nan sarki ya ce masa, "Donme ka ƙara wani abu kuma? Na yanke shawarar cewa kai da Ziba za ku raba gonakin."30Sai Mefiboshet ya amsa wa sarki, "I, bari ya ɗauka duka, da shi ke shugabana sarki ya dawo gidansa lafiya."31Daga nan sai Barzillai Bagiliye ya zo daga Rogelim ya haye Yodan tare da sarki, domin ya raka shi hayin Yodan.32Yanzu dai Barzillai ya tsufa ƙwarai, shekarunsa tamanin. Ya tanadarwa sarki abin zaman gari lokacin da ya ke zaune a Mahanayim, gama shi mai arzaki ne.33Sarki ya ce da Barzillai, "Sai ka haye tare da ni, ni kuwa zan tanada maka ka zauna tare da ni a Yerusalem."34Barzillai ya amsa wa sarki, "Sauran kwanaki nawa suka rage cikin shekarun rayuwata, da zan haura tare da sarki zuwa Yerusalem?35Shekaruna tamanin. Zan iya banbance tsakanin abu mai kyau da mugu? Ko bawanka zai iya ɗanɗana abin da nake ci ko abin da nake sha? Yanzu zan iya jin kowacce muryar mawaƙa maza da waƙar mata? Donme bawanka za ya zama nawaya ga shugabana sarki?36Bawanka yana so ya haye Yodan kaɗai tare da sarki. Donme sarki zai saka mani da irin wannan ladar?37Ina roƙonka ka bar bawanka ya koma gida, domin in mutu cikin birnina a kabarin mahaifina da mahaifiyata. Amma ka duba, ga bawanka Kimham. Bari ya haye tare da shugabana sarki, kayi masa abin da ya yi maka kyau."38Sarki ya amsa ya ce, "Kimham zai haye tare da ni, kuma zan yi masa abin da kake so, iyakar abin da kake nema kuma a gare ni, zan yi maka."39Daga nan sai dukkan mutane suka haye Yodan, sarki ma ya haye, sai sarki ya sumbaci Barzillai ya kuma albarkace shi. Daga nan sai Barzillai ya koma gidansa.40Sai sarki ya haye zuwa Gilgal, Kimham kuma ya haye tare da shi. Dukkan jama'ar Yahuda kuma suka ƙetarar da sarki, da rabin jama'ar Isra'ila kuma.41Nan da nan sai dukkan mutanen Isra'ila suka fara zuwa wurin sarki suka ce da sarki, "Donme 'yan'uwanmu, mutanen Yahuda, suka sace ka suka kawo sarki da iyalinsa hayin Yodan, da dukkan mazajen Dauda tare da shi?"42Sai mutanen Yahuda suka amsa wa mutanen Isra'ila suka ce, domin sarki danginmu ne na kusa. donme kuke fushi game da wannan? Mun ci wani abin da ya zama lallai sarki dole ya biya? Ko ya ba mu wasu kyaututtuka?"43Sai mutanen Isra'ila suka amsa wa mutanen Yahuda, "Mu na da kabilai goma da suke dangantaka da sarki, 'yancin da muke dashi wurin Dauda yafi naku. Donme ku ka rena mu? Ba shawarar mu aka fara ji ba ta dawo da sarkinmu?" Amma kalmomin mutanen Yahuda sun fi kalmomin mutanen Isra'ila zafi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Wani ya gaya wa Yowab"
Ana amfani da kalmar "Duba" anan don jawo hankalin wani game da abin da za'a faɗa a gaba. AT: "Saurara, sarki yana kuka"
Wannan yana nufin cewa duka sojojin sun yi baƙin ciki maimakon yin biki. AT "Don haka maimakon yin murnar nasara a wannan ranar, duk sojojin sun yi baƙin ciki"
Marubucin ya kwatanta hanyar da sojoji suka sata cikin gari da yadda sojoji suke yin ɓoye lokacin da suke guduwa daga yaƙi. Wannan yana nanata cewa an sa su sun ji kunya. AT: "kamar yadda mutanen da suka gudu daga yaƙi za su ɓuya saboda kunya"
Wannan hanya ce ta nuna baƙin ciki da baƙin ciki. AT: "Sarki ya nuna alhinin sa ta hanyar rufe fuskarsa"
Anan ana kiran sojojin ta fuskokinsu don jaddada yadda zasu ɓoye fuskokinsu saboda kunya. AT: "Kun sa duk sojojinku sun ɓoye fuskokinsu cikin kunya yau" ko "Kun sa duk sojojin ku don jin kunya a yau"
Wannan jimlar ƙari ce, amma tana nuna ƙimar darajar da Dauda ya nuna wa sojojin. AT: "sunada ƙima a wurin ku"
Mai magana yana ba da halin kwatanci.
Yowab yana rantsuwa sosai. AT: "Na rantse, lalle da Yahweh yana raye"
Wannan yana nufin cewa idan Dauda ya tafi kawai sojojinsa zasu kasance tare da shi. AT: "kawai idan kun tafi wani daga cikin mutanenku zai kasance tare da ku"
Wannan magana ce gaba ɗaya. Yana nufin yawancin maza. Ana iya bayyana shi cikin tsari mai aiki. AT: "da yawa daga cikin mutanen da suke wurin sun ji wasu suna faɗin"
Ana amfani da kalmar "Duba" anan don jawo hankalin wani game da abin da za'a faɗa a gaba. AT: "Saurara, sarki yana zaune"
Anan "Isra'ila" na nufin sojojin Isra'ilawa waɗanda suka bi Absalom. AT: "Kuma kowane sojan Isra'ila ya gudu zuwa gidansa" ko "Kuma duk sojojin Isra'ila sun gudu zuwa gidajensu"
Anan “hannu” na nufin sarrafawa. AT: "daga ƙarƙashin ikon maƙiyanmu" ko "daga ikon abokan gabanmu" (Duba: fgis_synecdoche)
Anan “hannu” na nufin sarrafawa. AT: "daga ƙarƙashin ikon Filistiyawa" ko "daga ikon Filistiyawa"
Wannan yana nufin cewa ya bar ƙasar yana tsere wa Absalom. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "daga ƙasar da ke tsere daga Absalom"
Wannan yana nufin suyi la'akari da dawo da Dauda yanzu tunda Absalom ya mutu. Ana iya rubuta tambayar azaman sanarwa. AT: "ya kamata mu kasance game da dawo da sarki."
An yi wannan tambayar ta lafazi don tsawata wa dattawan Yahuda. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Ya kamata ku kasance farkon wanda ya fi dacewa da sarki kuma kuka dawo da shi fada, ba mutanen Isra'ila ba."
Za a iya nuna kalmar "magana" tare da kalmar "faɗi". AT: "tunda duk Isra'ila suna magana mai kyau game da sarki kuma suna son kawowa" ko "tunda abin da mutanen Isra'ila ke faɗi yana cikin yardar sarki, a kawo"
Sarki yana amfani da waɗannan zuwa jimloli don jaddada cewa suna da alaƙa da juna. Kasancewa ko kasancewa da nama ɗaya kwatanci ne na kasancewa ga iyali ɗaya ko ƙabila ɗaya. AT: "Ku 'yan'uwana ne, kuma muna da nama da ƙashi ɗaya" ko "Ku ne' yan'uwana, dangi na kusa"
Wannan ita ce tambaya ta biyu ta magana a nan kuma ma tsawatarwa ce ga dattawan Yahuda. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Ya kamata ku kasance farkon, ba na ƙarshe ba, don dawo da sarki."
Wannan karin magana ne da ke nufin don Allah ya kashe shi. AT: "Allah ya kashe ni"
Anan ana kiran amincin maza a matsayin "zukatansu." AT: "ya sami aminci"
Wannan yana magana ne game da maza a haɗe cikin aminci ga sarki kamar dai su mutum ɗaya ne masu hankali ɗaya. AT: "kuma sun kasance a hade tare" ko "sun kasance a hade cikin aminci ga sarki"
Wannan yana nufin cewa sun aika da saƙo zuwa ga sarki. AT: "Sun aika da saƙo zuwa ga sarki"
"1,000 maza ...15 'ya'ya maza ... 20 bayin"
Wannan yana nufin cewa sarki yana nan kuma yana sane da abin da ke faruwa. AT: "a wurin da sarki yake"
Wannan yana nufin "don tunawa." AT: "ku tuna"
"dauki abu a zuciya" yana nufin yin tunani game da wani abu da gaske ko kuma damuwa da shi. AT: "kada a dame shi" ko "a manta da shi"
Abishai ya yi fushi da Shimei don ya zagi Dauda kuma yana ba da shawarar cewa a kashe shi. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Ya kamata a kashe Shimei saboda ya la'ana shafaffen Yahweh."
Wannan yana nufin Dauda. Yana nufin shi ne mutumin da Yahweh ya naɗa sarki. AT: "mutumin da Yahweh ya shafe a matsayin sarki"
Dauda yayi amfani da wannan tambaya tsawata wa Abishai. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Ba mu da wani abu da yake a tare da ku, ya ku 'ya'yan Zeruya! Ba ku da cikakken dalilin da zai sa ku zama magabtana a yau."
Dauda yayi amfani da waɗannan tambayoyin don ci gaba da tsawatar da Abishai. Waɗannan tambayoyin za a iya rubuta su azaman maganganu. AT: "Babu wanda za a kashe a yau a cikin Isra'ila, saboda yau nine wanda yake sarautar Isra'ila duka."
"Bai kula da ƙafafunsa ba." Ƙafafun Mefiboshet sun kasance marasa ƙarfi. Wannan jumlar tana nufin cewa bai kula da ƙafafunsa da kyau ba.
Dauda yana tambayar Mefiboshet me ya sa bai tafi tare da Dawuda ba yayin da Dauda da dukkan mutanen da suka biyo shi suka bar Yerusalem. AT: "Me ya sa ba ku tafi tare da ni ba lokacin da na bar Yerusalem, Mefiboshet?"
Anan an kwatanta hikimar Dauda da hikimar mala'ika. AT: "maigidana sarki yana da hikima kamar mala'ikan Allah"
Wannan yana nufin aikata abin da kuke ganin shine dai-dai. AT: "ku aikata abin da kuka yi imani shine abin da ya dace a yi"
Mefiboshet yayi magana game da yadda danginsa suka cancanci kisan kamar an riga an kashe su kuma sun mutu. AT: "duk gidan mahaifina sun cancanci maigidana sarki ya ba da umarnin a kashe su"
Mefiboshet yayi amfani da wannan tambayar ta lafazin don jaddada cewa bashi da ikon neman komai daga sarki. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Saboda haka, ba ni da ikon in nemi sarki ya yi mini wani abu." (Duba: rquestion)
Dauda yayi amfani da wannan tambayar ta zance don gaya masa cewa baya buƙatar ci gaba da magana game da rikicinsa da Ziba. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Ba kwa buƙatar yin bayanin wannan gaba." ko "Tabbas ba kwa buƙatar cewa komai."
"Shekaru 80"
"ya samar da abin da sarki yake bukata"
Anan Barzillai yana nufin ya tsufa kuma babu wani dalili da zai sa shi ya bi Dauda. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Tabbas ba zan rayu ba shekaru da yawa. Babu wani kyakkyawan dalili da zai sa in tafi tare da sarki zuwa Yerusalem." (Duba: fgis_rquestion)
Barzillai yayi amfani da tambayoyi don jaddada dalilin da yasa baya son zuwa Yerusalem. Anan "mai kyau" da "mara kyau" suna nufin abin da yake kyawawa da wanda kyawawa ba. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Ba zan iya bambance tsakanin abin da yake kyawawa da wanda kyawawa ba."
Barzillai yayi amfani da tambayoyi don jaddada dalilin da yasa baya son zuwa Yerusalem. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Ba zan iya jin daɗin ɗanɗanar abin da nake ci da abin da nake sha ba."
Barzillai ya yi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa ba ya son ya zama nauyi ga sarki. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Kada bawanka ya tafi tare da kai ya zama maka nauyi."
Barzillai ya yi amfani da wannan tambaya don jaddada cewa bai san dalilin da yasa sarki zai saka masa da wannan hanyar ba. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Ban san dalilin da yasa sarki zai saka min da wannan lada mai girma ba"
Barzillai ya nemi a bar Kimham ya maye gurbinsa maimakon Dauda.
Wannan sunan mutum ne.
Wannan ba yana nuna cewa yana son ya mutu kusa da kabarinsu ba ne, a'a, yana so ya mutu a garin da aka binne su. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "inda kabarin mahaifina da mahaifiyata suke" ko "inda aka binne mahaifina da mahaifiyata"
Wannan yana nufin ƙetare Kogin Yodan. AT: "Ku bar shi ya haye Yodan" (Duba: fgis_ellipsis)
Wannan yana nufin ƙetare Kogin Yodan. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Kimham zai haye kogin tare da ni"
Suka haye Kogin Yodan. AT: "ya haye kogin zuwa Gilgal"
"Dukkan sojojin Yahuda da rabin sojojin Isra'ila sun kawo sarki a kan"
Mutanen Isra’ila sun yi amfani da wannan tambayar don su nuna cewa suna jin mutanen Yahuda sun ci amanarsu. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Bai dace ba cewa 'yan'uwanmu, mutanen Yahuda, waɗanda ba su goyi bayan ku sarki ba, sun sami damar dawo da ku da danginku ƙetaren Kogin Yodan."
Mutanen Yahuda sun yi wannan tambaya don su tsawata wa mutanen Isra'ila. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Amma ba ku da dalilin da za ku damu game da wannan."
Mutanen Yahuda suka yi tambaya don a nuna cewa ba su karɓi kome daga wurin sarki ba. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Sarki bai taba biyan kudin abincinmu ba, kuma bai taba ba mu wata kyauta ba."
"muna da wata da'awa mafi girma ga Dauda fiye da ku." Zai iya zama da kyau a bayyana a fili abin da kasancewa da “ƙarin dama” ke nufi. AT: "muna da damar da za mu bauta wa sarki kuma mu kasance tare da sarki fiye da ku"
Mutanen Isra'ila sun yi wannan tambaya don tunatar da mutanen Yahuda. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Mu ne farkon wanda ya ba da shawarar mu dawo da sarki!"
Anan "kalmomi" na nufin maganar maza. AT: "Mutanen Yahuda sun yi magana mafi zafi fiye da mutanen Isra'ila."
1Ya kasance kuma a wannan wurin akwai wani mai tada hankali sunansa Sheba ɗan Bikri, Benyamine. Sai ya busa ƙaho ya ce, "Ba mu da rabo cikin Dauda ba mu kuwa da gãdo cikin ɗan Yesse, bari kowanne mutum ya koma gidansa, Isra'ila,"2Sai dukkan mutanen Isra'ila suka yashe da Dauda suka bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka bi sarkinsu kurkusa, daga Yodan har zuwa Yerusalem.3Lokacin da Dauda yazo fãdarsa a Yerusalem, sai ya ɗauki matan nan goma bayi waɗanda ya bari su kula da fãda, ya sa su cikin gida yasa a kula da su, ya biya buƙatunsu, amma bai ƙara kwana da su ba. An kulle su har ranar mutuwarsu, suna zama kamar gwamraye.4Daga nan sai sarki ya ce da Amasa, ka kira mazajen Yahuda tare cikin kwana uku; dole kai ma ka kasance, a nan,5Sai Amasa ya tafi ya kira mutanen Yahuda tare, amma ya jinkirta ya wuce lokacin da sarki ya sanya dominsa.6Sai Dauda ya ce da Abishai, "Yanzu Sheba ɗan Bikri za ya yi mana ɓarnar da ta fi wadda Absalom ya yi. Ka ɗauki bayin shugabanka, sojojina, ka bi bayansu, in ba haka ba zai iya samun birane masu ganuwa ya ɓace mana da gani."7Sai mutanen Yowab suka bi bayansa, da su da Keretawa da su da Feletawa, da dukkan jarumawa. Suka fita Yerusalem suka bi Sheba ɗan Bikri.8Yayin da suke a babban dutsen da ke a Gibeyon, Amasa ya zo ya tarbe su, Yowab kuwa yana saye da tufafinsa na yaƙi, wanda ya haɗa da ɗammara kewaye da ƙugunsa da takobin yaƙi ɗaure da shi. Ya yin da ya ci gaba da tafiya sai takobin ya faɗi.9Sai Yowab ya ce da Amasa, "Lafiya kake, ɗan'uwana?" Yowab ya kama Amasa wajen gemunsa da hannunsa na dama don ya yi masa sumba.10Amasa bai kula da takobin da ke cikin hannun Yowab na hagu ba. Yowab ya daɓa wa Amasa a ciki 'yan hanjinsa suka faɗi a ƙasa. Yowab bai sake bugunsa ba, Amasa kuwa ya mutu. Yowab da Abishai ɗan'uwansa suka bi Sheba ɗan Bikri.11Sai ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya wajen Amasa, mutumin ya ce, "Wanda ya ke wajen Yowab da wanda ke wajen Dauda, bari ya bi Yowab."12Amasa ya kwanta yana ta birgima cikin jini a cikin tsakiyar hanya. Yayin da mutumin yaga dukkan jama'a sun tsaya cik, sai ya ɗauki Amasa ya kawar dashi daga kan hanya zuwa cikin saura. Ya jefa mayafi a kansa saboda ya ga duk wanda ya zo sai ya tsaya a kansa.13Bayan da aka kawar da Amasa a kan hanya, dukkan mutane suka bi bayan Yowab, wajen bin Sheba ɗan Bikri.14Sheba ya ratsa dukkan kabilun Isra'ila zuwa Abel ta Bet Maka, da zuwa dukkan kasar Beriyawa, waɗanda suka tattaru domin bin Sheba.15Suka kama shi suka kafa masa sansani cikin Abel ta Bet Maka. Suka tãra tulin tudun ƙasa gãba da birnin da ganuwar. Dukkan jama'ar da ke tare da Yowab suka bubbuge ganuwar suka rushe ta.16Sa'an nan wata mace mai hikima tayi kuka daga cikin birni ta ce, "Ku ji, ina roƙon ku kuji, Yowab, ka matso kusa da ni domin in yi magana da kai."17Sai Yowab ya je kusa da ita, sai matar ta ce, kai ne Yowab?" Sai ya amsa ya ce, "Ni ne," Sa'an nan ta ce masa, ka saurari kalmomin baiwarka," Ya amsa ya ce, Ina ji."18Sai ta ce, kwanakin dã an saba cewa, 'Lallai sai ka nemi shawara a Abel.' Wannan shawarar kuwa takan kawo ƙarshen al'amarin.19Mu ne ɗaya daga cikin birni da ke da salama da aminci a cikin Isra'ila. Ka na ƙoƙarin ka hallaka birni wanda ya ke uwa a cikin Isra'ila. Donme za ka haɗiye gãdon Yahweh?"20Sai Yowab ya amsa ya ce, "Hakika ba zai faru ba, bari ya zama nesa daga gare ni, da zan haɗiye ko in hallakar.21Wannan ba gaskiya ba ne. Amma wani mutum daga duwatsun ƙasar Ifraim sunan sa Sheba ɗan Bikri, ya ɗaga hannunsa sama gãba da sarki, gãba da Dauda. Shi kaɗai za a bayar ni kuwa zan janye daga birnin." Sai matar ta cewa Yowab, "Za a jefa maka kansa ta bisa ganuwa."22Daga nan sai matar taje wurin dukkan jama'a cikin hikimarta. Suka yanke kan Sheba ɗan Bikri, suka jefa shi waje wurin Yowab. Daga nan sai ya busa ƙaho mutanen Yowab suka bar birnin, kowa ya koma gidansa. Sai Yowab ya komaYerusalem wurin sarki.23Yanzu fa Yowab yana kan rundunar yaƙi ta Isra'ila, Benaiya kuma ɗan Yehoyida yana bisa kan Keretawa da Feletawa.24Adoram yana bisa mutane masu yin aikin dole, Yehoshafat kuma ɗan Ahilud shi ne magatakarda.25Sheba kuma marubuci da Zadok da Abiyata su ne Firistoci.26Ira Bajairi kuma babban mai yin hidima ga Dauda
Wannan yana nufin garin Gilgal.
Waɗannan sunayen maza ne.
Duk wadannan maganganun guda ɗaya suke nufi. Sheba yana jaddada cewa shi da kabilun Isra’ila ba su da wata dangantaka da Dauda. AT "Gadon Dauda da dangin mahaifinsa ba namu bane" ko "Ba mu daga cikin Dauda da dangin mahaifinsa"
Anan jimlar "kiyaye" na nufin kulawa. AT: "don kula da gidan sarauta"
Idan gida "a tsare yake" yana nufin an sanya mai gadi a gidan. AT: "a cikin gida kuma sanya mai tsaro a wurin"
Wannan yana nufin cewa ba a ba su izinin barin gidan ba. AT: "an rufe su a cikin gidan"
Wadannan mata ne wadanda mazajensu suka mutu.
Wannan shi ne shugaban sojojin Dauda. Duba yadda zaka fassara sunan wannan mutumin a cikin 2 Samaila 17:25.
"kara cutar da mu"
Kalmomin "sojoji na" ya bayyana wane "bayin." Dauda ya kira kansa a matsayin "maigidanka" a matsayin hanya ta yau da kullun ta yin magana da wanda ba shi da iko sosai.
"bi bayan"
Wannan yana nufin cewa Sheba da mutanensa za su shiga waɗannan garuruwan don ɓoyewa daga sojojin Dauda. Kalmar "ya" wakiltar Sheba amma tana nufin dukka shi da mutanensa. AT: "shi da mutanensa za su ɓuya a cikin garuruwa masu garu" ko "shi da mutanensa za su nemi mafaka a garuruwa masu garu"
Anan Dauda yana nufin rundunarsa ta wurin ganinsu don ƙarfafawa cewa Sheba da mutanensa za a ɓoye kuma sojojin Dauda ba za su iya kame su ba. AT: "daga gare mu"
"Lokacin da Yowab da mutanen Yahuda suke"
Yowab ya bar takobin ya faɗi don ya wautar da Amasa don ya yi tunani cewa shi Yowab ba shi da makami, don haka Amasa ta ƙyale shi ya yi tafiya kusa da shi. AT: "ya bar takobin ya faɗi a ƙasa don haka Amasa ya zaci ba shi da makami"
Amasa ɗan ɗan 'yar'uwar mahaifiyar Yowab ne.
Wannan hanya ce ta gama gari ga maza don gaishe da junan su.
"hanji ya zube"
Kasancewa "don" wani yana nufin tallafawa su. AT: "wanda ya goyi bayan Dauda" ko "wanda ya kasance mai aminci ga Dauda"
"Amasa kwance kwance cikin jininsa." Amasa na iya kasancewa har yanzu yana raye yana birgima cikin jininsa, amma mai yiwuwa ya mutu a wannan lokacin. An bayyana ta wannan hanya don nuna yadda jikinsa yake da tsananin tsoro. AT: "Amasa ya mutu a cikin jininsa"
Wannan yana nufin sun daina tafiya kuma suna kallon gawar Amasa. AT: "duk mutanen sun tsaya cak suna kallon gawar" amea tsaye kusa da shi ya tsaya cak, yana kallon gawar "
Anan "Sheba" yana nufin duka shi da sojojinsa. AT: "Sheba da rundunarsa" ko "Sheba da mutanensa"
Dukansu sunayen Habila da Bet Ma'aka suna nufin wuri ɗaya kuma ana iya haɗa su. Birni ne, kusa da kabilar Dan.
Wannan sunan kungiyar mutane.
"kuma ya bi Sheba"
"Yowab da sojoji suka riske shi"
Wannan yana nufin cewa sun yi amfani da batako don fasa bangon. Ragon ragowa itace sare ne ko babban katako mai kaifi ƙare ko ƙarshen da aka rufe da ƙarfe. Maza da yawa suka riƙe shi wanda zai iya ƙarshen ƙarshen bango. AT: "anyi amfani da rago don buga bango"
Matar tana kiran kanta "bawanka." Wannan hanyar ladabi ce don magana da wanda ke da iko
"wannan shawarar za ta magance matsalar"
Wannan ya bayyana biranen. AT: "mafi yawan birni masu aminci da aminci a Isra'ila"
Wannan yana magana ne game da mahimmancin wannan birni a tsakanin al'ummar Isra'ila kamar uwa ce da ake girmamawa sosai. AT: "birni da kowa a cikin Isra'ila yake girmamawa kamar na mahaifiyarsa" ko "garin da ke da matukar mahimmanci kuma Isra'ila ke girmamawa"
Anan matar ta yi amfani da tambaya don nuna wa Yowab abin da bai kamata su yi ba. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Kada ku halakar da garin da yake gadon Yahweh!"
Ya sake maimaita wannan maganar don jaddada cewa wannan wani abu ne wanda ba zai taɓa yi ba. AT: "Gaskiya ne, da gaske, ba zan taɓa ba"
Wannan yana nufin yin tawaye da yaƙi da wani. AT: "ya yi adawa" ko "yana tawaye ga"
Yowab yana neman mutanen birni su sakar masa Sheba. AT: "Bada wannan mutumin mana" ko "Ka ba mu wannan mutumin"
Anan "Ni" yana nufin Yowab da sojojinsa. AT: "Za mu janye daga garin"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Za mu jefa kansa"
"Yanzu" yana nuna hutu a layin babban labari. Wannan sabon sashin yana ba da bayanan baya game da mutanen da suka yi wa Sarki Dauda aiki.
1A cikin zamanin Dauda aka yi yunwa shekara uku akai akai, Dauda kuwa ya nemi fuskar Yahweh. Sai Yahweh ya ce, "Wannan yunwar tana kan ka ne saboda Saul da iyalinsa masu kisa, saboda ya kashe Gibiyonawa."2Yanzu fa Gibiyonawa ba daga jama'ar Isra'ila bane, amma daga wajen sauran Amoriyawa ne. Mutanen Isra'ila sun rantse masu ba za su kashe su ba, amma saul ya yi ƙoƙari ya kashe su dukka a cikin himmarsa domin mutanen Isra'ila da Yahuda.3Sai Dauda ya kira mutanen Gibiyonawa ya ce masu, "Me zan yi domin ku? Ta yaya zan yi kaffara, domin ku albarkaci mutanen Yahweh, waɗanda suka gãji alherinsa da alƙawarai?"4Gibiyonawa suka ce masa, ba zancen azurfa ko zinariya tsakanin mu da Saul ko iyalinsa. Kuma ba domin mu za a kashe kowanne mutum a cikin Isra'ila ba." Dauda ya amsa, "Duk abin da za ku roƙa, shi ne abin da zan yi maku."5Sai suka amsa wa sarki suka ce, mutumin da ya yi ƙoƙarin ya kashe mu dukka, wanda ya ƙulla mana makirci, wanda da yanzu an hallaka mu, mu rasa wuri a tsakanin iyakar Isra'ila.6Bari a bamu mutum bakwai daga cikin zuriyarsa, mu kuwa za mu rataye su ga Yahweh cikin Gibiya ta Saul, zaɓaɓɓe na Yahweh." Sai sarki ya ce, "Zan ba ku su."7Amma sarki ya keɓe Mefiboshet ɗan Yonatan ɗan Saul, saboda rantsuwar Yahweh da ke tsakanin su, tsakanin Dauda da Yonatan ɗan Saul.8Amma sarki ya ɗauki 'ya'ya biyu na Rizfa ɗiyar Ayiya, 'ya'yan da ta haifawa Saul, sunayen 'ya'ya biyun data haifa su ne, Armoni da Mefiboshet; Dauda kuma ya ɗauki 'ya'ya biyar na Mirab ɗiyar Saul, waɗanda ta haifawa Adriyel ɗan Barzillai Meholatiye.9Ya miƙa su cikin hannun Gibiyonawa. Suka rataye su a kan dutse, gaban Yahweh. Dukkan su bakwai ɗin suka mutu tare. Sun mutu a lokacin girbi, kwanakin farko ne a farkon kakar bali.10Daga nan sai Rizfa ɗiyar Ayiya ta ɗauki tsummoki ta shimfiɗa wa kanta su a bisa dutsen, gefen gawarwakin, daga farkon kãka har lokacin da ruwan sama ya sauko a kansu. Bata bari tsuntsayen sararin sama su dame su da rana ba, ko namomin jeji da dare.11Aka faɗa wa Dauda abin da Rizfa ɗiyar Ayiya, baiwar matar Saul, ta yi.12Sai Dauda ya tafi ya ɗauki ƙasusuwan Saul da ƙasusuwan Yonatan ɗansa daga hannun mutanen Yabesh Giliyad, waɗanda suka sace a wurin filin Bet - Shan, inda Filistiyawa suka rataye su, bayan da Filistiyawa suka kashe Saul a Gilbowa.13Dauda ya kawar da ƙasusuwan Saul da ƙasusuwan Yonatan ɗansa, suka kuma tattara ƙasusuwan mutane bakwai waɗanda aka rataye su kuma.14Suka bizne ƙasusuwan Saul da Yonatan ɗansa cikin ƙasar Benyamin cikin Zela cikin kabarin Kish mahaifinsa. Suka aikata dukkan abin da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya amsa addu'o'insu domin ƙasar.15Daga nan sai Filistiyawa suka je su sake yin yaƙi da Isra'ilawa. Sai Dauda ya sauka da shi da mutanensa su yi yaƙi da Filistiyawa. Amma gajiyar yaƙi ta sa Dauda ya yi suwu.16Ishbi-Benob na zuriyar ƙattin nan wanda nauyin mashinsa ya yi nauyin shekel ɗari uku na tagulla, yana kuma ɗauke da sabuwar takobi, ya yi nufin ya kashe Dauda.17Amma Abishai ɗan Zeruya ya ceci Dauda, ya bugi Bafilisten nan, ya kashe shi. Daga nan mazajen Dauda suka rantse masa, cewa, "Ba zaka ƙara tafiya yaƙi tare da mu ba, domin kada ka ɓice fitilar Isra'ila."18Bayan wannan kuwa aka sake yin yaƙi da Filistiyawa a Gob, lokacin da Sibbekai Bahushati ya kashe Saf, wanda ke ɗaya daga cikin zuriyar Refayim.19Ya zama kuma aka sake yin yaƙi da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Yayir mutumin Betlehem ya kashe Goliyat Bagittiye, wanda mãshin sa yana kama da dirkar masaƙa.20Ya zama kuma aka sake yin yaƙi a Gat inda akwai wani mutum mai tsayin gaske a kowanne hannunsa yana da yatsu shida a kowacce ƙafa kuma yana da yatsu shida, dukka ashirin da huɗu kenan. Shi ma har yanzu daga zuriyar Refayim ne.21Sa'ad da ya zazzagi Isra'ila, Yonatan ɗan Shimeya, ɗan'uwan Dauda, ya kashe shi.22Waɗannan su ne zuriyar Refahayim na Gat an kashe su ta hannun Dauda da kuma ta hannun sojojinsa.
Anan “fuska” magana ne ta kasancewar Yahweh. Wannan yana nufin Dauda ya yi addu'a ga Yahweh don amsa game da yunwa.
Saul ya kashe Gibiyonawa da yawa, zuriyar Saul kuwa suna da laifi saboda wannan zunubi.
Anan "Yanzu" yana nuna hutu a layin babban labari. Wannan yana ba da bayanan baya game da Gibiyonawa.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri daya. AT: "Me zan yi don kawar da wannan zunubin, don ku albarkaci mutanen Yahweh, waɗanda suka gaji nagartarsa da alkawuransa?"
"Kuɗi ba zai magance matsalar ba"
"wanene ya yi mana niyya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ku bar mutanenku su ba mu zuriyarsa bakwai"
"za mu kashe su ta hanyar rataya"
Saul mutumin Gibiya ne.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda Yahweh ya zaɓa"
Waɗannan sunayen maza ne.
Anan "hannun Gibiyonawa" suna wakiltar ikon mutanen Gibiyon.AT: "Ya ba su ga Gibiyonawa"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Gibiyonawa sun kashe su"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Wani ya gaya wa Dauda"
Jabesh wani gari ne a cikin yankin Giliyad. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sama'ila 2: 4.
Wannan yanki ne kusa da ƙofar gari inda mutane suke kasuwanci iri-iri.
Wannan sunan wani wuri ne.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda Gibiyonawa suka kashe ta hanyar ratayewa"
Wannan sunan wani gari a Benyamin.
Wannan sunan mutum ne.
"Mahaifin Saul"
Wannan sunan mutum ne.
“Fitilar Isra’ila” magana ne da ke nuni ga shugabancin Dauda da kuma ra’ayin cewa idan Dauda ya mutu, mutanen Isra’ila ba za su sami jagora ba.
Wannan jumlar ta nuna farkon sabon sashin labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
Wannan sunan wani gari ne.
Waɗannan sunayen maza ne.
Lokacin da mutum yake sakar zane zai rinka gudanar da zaren ta ƙugiyoyin da ke haɗe da manyan sanduna da ake kira "katakon masaka." Wannan yana nufin mashin Goliyat ya fi na mashin da yake ci.
Anan "ta hannun" yana nufin "ta hanyar". Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Dauda da sojojinsa sun kashe su"
1Dauda ya yi amfani da waɗannan kalmomi ya raira waƙa ga Yahweh a ranar da ya cece shi daga hannun dukkan abokan gabarsa, da kuma hannun Saul.2"Ya yi addu'a ya ce, Yahweh shi ne dutsena, da kagarata, shi wanda ya cece ni.3Allah shi ne dutse na. A cikinsa na sami mafaka, garkuwata da ƙahon cetona, hasumiyata mai tsawo, mafakata kuma, shi ne wanda ya cece ni daga tashin hankali.4Zan kira bisa Yahweh, wanda ya isa a yabe shi, kuma zan tsira daga hannun maƙiyana.5Gama ambaliyun mutuwa sun kewaye ni, haukan ruwayen hallakarwa sun tsoratadda ni.6Igiyoyin lahira sun kewaye ni; tarkunan mutuwa sun kama ni.7A cikin ƙuncina na kira Yahweh; Na kira Allahna; daga cikin haikalinsa ya ji muryata, kira na na neman taimako ya kai cikin kunnuwansa.8Sa'an nan ƙasa ta girgiza ta yi makyarkyata. Tussan sammai suka girgiza aka motsa su, saboda Allah ya yi fushi.9Hayaƙi ya fito daga hancinsa, wuta mai cinyewa ta fito daga bakinsa. Ta kunna gawayi ta wurinsa.10Ya buɗe sammai ya sauko ƙasa, duhu baƙiƙƙirin yana ƙarƙashin sawayensa.11Ya hau bisa Kerub, ya tashi. A bisa fukafukan iska aka ganshi.12Ya kuma maida duhu rumfa kewaye da shi, manyan hadura na tattaruwa cikin sararin sammai.13Daga sheƙin hasken gabansa gawayin wuta suka faɗo.14Yahweh ya yi tsawa daga sammai. Maɗaukaki ya tada muryarsa.15Ya harba kibawunsa, ya tarwatsa maƙiyansa - curirrikan walƙiya kuma sun tarwatsa su.16Sa'an nan hanyoyin ruwa suka bayyana; harsasun duniya suka tonu a kukan tsautawar Yahweh, da jin hucin numfashi daga hancinsa.17Daga bisa ya kai ƙasa; Ya riƙe ni! Daga cikin ruwaye masu yawa ya jawo ni.18Ya cece ni daga wurin maƙiyina mai ƙarfi, daga hannun waɗanda suka ƙi ni, gama sun fi karfina.19Suka afko mani a ranar masifata, amma Yahweh shi ne abin dogarata.20Ya kuma kawo ni waje a buɗaɗɗen wuri. Ya cece ni saboda yana murna da ni.21Yahweh ya sãka mani bisa ga ma'aunin adalcina; ya sãke gyara ni bisa ga tsabtar hannuwana.22Gama na kiyaye hanyoyin Yahweh ban kuma juya wa Allah baya ba ta wurin aikata mugunta.23Gama dukkan shari'unsa na adalci suna gabana; game da zancen farillansa kuma, ban rabu da su ba.24Marar laifi nake a gabansa, na kuma kiyaye kaina daga zunubi.25Domin wannan Yahweh ya sabunta ni ya sãka mani bisa ga adalcina, bisa ga matsayin tsabtata a idonsa.26Ga mai aminci, ka nuna kanka mai aminci ne; ga mutumin da ya ke marar laifi, zaka nuna kanka marar laifi.27Ga mai tsabta, ka zama da tsabta, amma ga fãsiki ka zama a murɗe.28Ka ceci rauna nan mutane, amma idanun ka na gãba da masu girmankai, kuma ka kawo su ƙasa.29Gama kai ne fitilata, Yahweh. Yahweh ya haskaka duhuna.30Gama ta wurinka zan iya zarce taron yaƙi; ta wurin Allahna nake tsallake ganuwa.31Domin Allah, hanyarsa cikakkiya ce. Shi garkuwa ne ga dukkan waɗanda suka nemi mafaka a cikin sa.32Gama wane ne Allah sai Yahweh? Wane ne dutse kuma sai Allahnmu?33Allah shi ne mafakata, yana kuma bida mutum marar laifi cikin hanyarsa.34Yana maida ƙafafuna suyi sauri kamar na naman jeji, ya kuma sanya ni a bisa dogayen tuddai.35Yana koyar da hannuwana domin yaƙi, damtsuna kuma su tausa baka na jan ƙarfe.36Ka kuma bani garkuwar cetonka, tagomashinka ya maishe ni mai girma.37Ka sanya wuri mai faɗi ƙarƙashin sawayena, santsi bai kwashe ƙafafuna ba.38Na fafari maƙiyana na kuma hallaka su. Ban juya ba har sai da suka hallaka.39Na cinye su na ragargaza su; ba za su tashi ba. Sun fãɗi ƙarƙashin sawayena.40Ka sanya ƙarfi a jikina kamar ɗammara domin yaƙi; waɗanda suka tayar mani ka sanya su ƙarƙashina.41Ka bani bayan maƙiyana' da wuyansu; Na datse wuyan waɗanda suka ƙi ni.42Sun yi kuka domin neman taimako, amma ba wanda ya cece su; sun yi kuka ga Yahweh, amma bai amsa masu ba.43Na buge su da kyau na niƙesu kamar turɓaya a ƙasa, na tattake su kamar laka na watsar da su cikin tituna.44Ka kuma ƙwatoni daga husumar mutanena. Ka kiyayeni a matsayin shugaban al'ummai. Mutanen da ban sani ba sun yi mani hidima.45Baƙi sun russuna mani dole. Da jin labarina, sun yi mani biyayya.46Baƙi sun fito daga wurin ɓuyarsu suna rawar jiki.47Yahweh mai rai ne! Bari a yabi dutsena. Bari Allah ya ɗaukaka, dutsen cetona.48Wannan shi ne Allah wanda ke tabbatar da sakayya domina, shi wanda ke ƙasƙantar da al'ummai ƙarƙashina.49Ya kuɓutar da ni daga hannun maƙiyana. Tabbas, ka ɗaukaka ni bisa kan waɗanda suka tayar mani. Ka kuɓutar da ni daga masu son cutar da ni.50Domin wannan Zan yi godiya gare ka, Yahweh, a tsakanin al'ummai; Zan raira waƙoƙin yabbai ga sunanka.51Allah ya bayar da babban ceto ga sarkinsa, yana nuna alƙawarin biyayya ga shafaffe na sa, ga Dauda da zuriyarsa har abada."
Waƙar Dauda ga Yahweh ta fara. Yana amfani da kwatankwacinsa don ƙarfafa abin da yake faɗa.
Wannan ci gaba ne daga abokan gaba ɗaya zuwa takamaiman maƙiyin Dauda, Sarki Saul.
Wannan magana yana nuna ci gaba daga wani sashi, "dutse," zuwa gaba ɗaya, "sansanin soja." An gina sansanin soja da manyan duwatsu da yawa. Wannan yana nufin Yahweh yana da ƙarfin kare mutanensa daga cutarwa.
Waƙar Dauda ga Yahweh ta ci gaba. Yana amfani da kwatankwacinsa don ƙarfafa abin da yake faɗa.
Dukkanin wadannan maganganu alamu ne na karfi da karfin Allah. Suna nanata ikon Allah na kare da ceton mutanensa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanene ya cancanci karɓar yabo"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "zai cece ni daga magabtana"
Waƙar Dauda ga Yahweh ta ci gaba. Yana amfani da kwatankwacinsa don ƙarfafa abin da yake faɗa.
Dauda ya kamanta miyagun mutanen da suke so su kashe shi da ambaliyar ruwa da ke shirin nutsar da shi. Waɗannan jimlolin suna da ma'anoni iri ɗaya kuma ana amfani dasu don ƙarfafawa.
Wannan hoto ne na ambaliyar ruwa da ke tafe da sauri wanda ke lalata komai a cikin hanyar su.
Dauda yayi magana akan mutuwa da Lahira kamar mutane ne waɗanda suke ƙoƙari su kama shi kamar yadda maharbi yake kama dabbobin. Waɗannan jimlolin suna da ma'anoni iri ɗaya kuma ana amfani dasu don ƙarfafawa.
"A cikin babbar matsalata"
Dauda yana magana ne game da haikalin sama inda Yahweh yake zaune. Har yanzu ba a gina haikalin duniya ba.
Anan baƙon ma'anar "kunnuwansa" na nufin Yahweh da kuma jin kiran da Dauda ya yi don taimako. AT: "ya ji addu'ata don neman taimako"
Waƙar Dauda ga Yahweh ta ci gaba. Yana amfani da kwatankwacinsa don ƙarfafa abin da yake faɗa.
Wannan ita ce amsawar Yahweh ga kiran Dauda na neman taimako daga maƙiyansa. Dauda ya yi amfani da hotunan duniya suna girgiza don jaddada tsananin fushin Yahweh.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "saboda fushin Allah ya girgiza su"
Anan an kwatanta fushin Yahweh da wuta, wanda ke sa garwashin wuta da ƙuna. AT: "Harshen bakinsa ya sanya garwashin wuta" ko "Ya kuma aika garwashin wuta daga bakinsa"
Dauda ya bayyana hanyar Yahweh na ceton Dauda daga abokan gabansa kamar hadari mai hadari da ke tattare da wuri. Wannan yana nanata ikon Allah da fushinsa.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Ya bayyana a fukafukan iska"
Anan duhun da Yahweh ya halitta ana kwatanta shi da rumfar wacce ta ɓoye shi gaba ɗaya. AT: "Ya ɓoye kansa a cikin duhu"
Zai yiwu ma'anonin su 1) "Daga haskensa ya aiko da garwashin wuta" ko 2) "Daga haskensa ya aiko walƙiya"
Dauda ya bayyana Yahweh yana yin waɗannan ayyukan mutum zai yi.
Waƙar Dauda ga Yahweh ta ci gaba. Yana amfani da kwatankwacinsa don ƙarfafa abin da yake faɗa.
Lokacin da Yahweh ya yi ihu a cikin yaƙin da ya yi wa magabtan Dauda, ana kwatanta shi da ikonsa don haifar da rikici a cikin zurfin zurfin teku da ƙasa. Wannan yana nuna girman ikonsa da fushinsa mai zafi.
Dauda ya kwatanta fushin Yahweh da motsin ƙasa mai hargitsi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Tsawatarwar Yahweh, numfashin hancinsa, ya bayyana tushen duniya "
Dauda ya kamanta abokan gaba da ambaliyar da ke barazanar nutsar da shi.
Maƙiyan Dauda sun yi ƙarfi sosai. Yana yabon Allah domin ya kubutar da shi daga duk makiyansa
Waƙar Dauda ga Yahweh ta ci gaba. Yana amfani da kwatankwacinsa don ƙarfafa abin da yake faɗa.
"Maƙiyana sun yi yaƙi da ni lokacin da nake cikin babbar matsala"
"amma Yahweh ya taimake ni"
Wannan yana nufin wurin da babu hatsari kuma abokan gaba ba zasu iya kama shi ba.
Anan "tsarkin hannuwana" na nufin daidai da "adalci." AT: "saboda na bi dokokinsa"
Dauda ya ci gaba da waƙarsa ga Yahweh.
Anan "hanyoyin Yahweh" yana nufin yadda Yahweh yake son mutanensa suyi aiki. Wannan yana nufin Dauda ya aikata abin da Yahweh ya umarta.
Wannan yana nufin Dauda yana karantawa koyaushe yana tunani game da ƙa'idodin Allah.
Wannan yana nufin zabar kada ayi zunubi ga Yahweh.
Anan "tsabtar kaina" na nufin dai-dai da "adalcina." AT: "saboda ya san cewa na aikata abin da ya umarta"
Dauda ya ci gaba da waƙarsa ga Yahweh.
Anan "karkatacciyar hanya" na nufin wayo ko dabara, kuma "karkatacciyar hanya" na nufin juyawa daga abin da yake mai kyau da daidai. Wannan yana nufin Allah mai hikima ne a yadda yake ma'amala da mugaye.
A nan kalmomin "idanunku" na nuni ga abin da Yahweh yake gani. Wannan yana nufin Yahweh yana kallon mai girman kai.
"ka lalata girman kansu"
Wannan magana yana kwatanta Yahweh da fitila, wanda ke nufin ya ba Dauda haske kuma ya taimaka masa ya ga lokacin da abubuwa suke kamar ba su da bege.
Anan "shingen shinge" na iya nufin ƙungiyar sojoji ko zuwa bangon dutse. Ko ta yaya yana nufin Allah ya sa Dauda ya ci nasara a kan maƙiyansa.
David yana karin magana don jaddada taimakon Yahweh. AT: "Zan iya hawa ta bangon da ya kewaye garinsu"
"Duk abin da Yahweh ya faɗa gaskiya ne"
Dauda ya ci gaba da waƙarsa ga Yahweh.
Dauda ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa babu wani Allah sai Yahweh. Waɗannan ana iya fassara su azaman maganganu. AT: "Yahweh shi kaɗai ne Allah. Allahnmu shi kaɗai ne dutse."
Yahweh yakan kiyaye amintacce, ya kuma kawar da duk wani abin da zai cutar da shi.
Anan an kwatanta ƙafafun Dauda da na barewa ta amfani da ƙari. Yahweh ya ba Dauda ƙarfi don motsawa da sauri kuma ya samar da wurare masu tsaro don kariya da hutawa.
Ƙarfin mutum ne kawai zai iya yin amfani da bakan da aka yi da ƙarfe.
Dauda ya ci gaba da waƙarsa ga Yahweh.
Dauda ya gwada ikon Yahweh don ceton shi da garkuwar da ke kare soja daga maƙiyinsa.
Allah ya amsa addu'ar Dauda ya bashi albarka da nasara a kan makiyansa.
Yahweh ya sa Dauda a cikin amintattu inda maƙiyansa ba za su iya kama shi ba. Anan yana nufin kansa da “ƙafafunsa” don ƙarfafa ikonsa na tsayawa tabbatacce.
"ka kori makiyana"
Anan Dauda ya kwatanta kansa da dabbar daji. AT: "Na hallakar dasu kwata-kwata kamar dabbar daji tana cinye abincinta"
Dauda ya ci gaba da waƙarsa ga Yahweh.
Anan an kwatanta ƙarfin da Ubangiji yake bayarwa da ɗamara don yaƙi wanda ya ba Dauda damar yin manyan abubuwa.
"ka taimake ni na kayar da wadanda suka yaki ni"
Matsalolin da ka iya yiwuwa su ne 1) Dauda yana ganin bayan abokan gaba yayin da suke guduwa ko 2) Dauda ya sa ƙafarsa a bayan wuyan maƙiyinsa bayan ya kayar da shi.
Lokacin hukuncin Yahweh ya zo a kan su.
Wannan yana nufin cewa Dauda ya hallaka maƙiyansa gabaki ɗaya. Waɗannan jimlolin guda biyu "kamar ƙura a ƙasa" da "kamar laka a tituna" suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani da su don ƙarfafawa.
Dauda ya ci gaba da waƙarsa ga Yahweh.
Wannan yana nufinga waɗanda ke cikin Isra'ilawa waɗanda suka yi tawaye ga Sarki Dauda.
"Ka sanya ni mai mulkin al'ummai." Anan "al'ummai" na nufin wasu al'ummomi banda Isra'ila.
"Baƙon mutane"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT "Baƙi sun sunkuya a gare ni"
Waɗannan jimlolin suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani da su don ƙarfafawa. Wadannan za'a iya bayyana su a cikin aiki. AT: "Bari kowa ya yabi dutsena. Bari kowa ya ɗaukaka Allah"
"wanda ya sanya mutanen wasu al'ummomi karkashin mulkina"
"ka cece ni daga makiya na kuma ka girmama ni"
Dauda ya kammala waƙarsa ga Yahweh.
Anan magana "suna" yana nufin sunan Yahweh.
Anan Dauda na iya nufin alkawuran da Yahweh ya yi a cikin 2 Sama'ila 7: 8.
1Yanzu fa waɗannan su ne ƙarshen zantattukan Dauda - Dauda ɗan Yesse, mutumin da aka girmama ƙwarai, shi wanda ya ke shafaffe daga Allahn Yakubu, mawaƙi mai daɗi na Isra'ila.2"Ruhun Yahweh ya yi magana da ni, maganarsa kuma tana kan harshena.3Allah na Isra'ila ya faɗi, Dutsen Isra'ila ya ce mani, 'Shi wanda ya ke mulkin mutane cikin adalci, mai yin mulki cikin tsoron Allah.4Zai zama kamar hasken safiya sa'ad da rana take fitowa, safiyar da babu giza-gizai, sa'ad da ɗanyar ciyawa take tsirowa daga ƙasa ta wurin hasken rana bayan saukowar ruwan sama.5Hakika ba haka iyalina suke a gaban Allah ba? Ko bai yi madawwamin alƙawari da ni, shimfiɗaɗɗe bisa ga ƙa'ida ya tabbatar ta kowacce hanya ba? Ko bai ƙara cetona ba kuma ya biya kowanne muradina ba?6Amma marasa amfani za su zama kamar ƙayayuwa da za a zubar, gama ba za su tattaru da hannu ɗaya ba.7Mutumin daya taɓa su dole ya yi amfani da makamin ƙarfe ko mashi mai tsini. Dole a ƙone su sarai a wurin da suka kwanta."8Waɗannan su ne sunayen shahararrun sojojin Dauda: Yeshbal mutumin Hakmoniya shugabane na sojoji masu ƙarfi. Ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci ɗaya.9Bayansa kuma sai Eliyazar ɗan Dodai Ba'ahotiye, ɗaya daga cikin jarumawa uku na Dauda. Yana nan lokacin da suka rena Filistiyawa da suka tattaru tare don suyi yaƙi, lokacin da mutanen Isra'ila sun rigaya sun bar wurin.10Eliyaza ya tashi tsaye ya bugi Filistiyawa har hannunsa ya gaji hannunsa kuma ya liƙe wa takobinsa. Yahweh ya kawo babbar nasara a wannan ranar. Jama'a suka koma bayan Eliyaza, domin kawai su tuɓe jikuna.11Bayansa kuma sai Shamma ɗan Agee, Harariye. Filistiyawa suka taru a filin dagar yaƙi, mutane kuwa suka gudu daga gabansu.12Amma Shamma ya tsaya a tsakiyar yankin ƙasar ya kuma kareta. Ya kashe Filistiyawa, Yahweh ya kawo babbar nasara.13Uku daga cikin su talatin sojojin suka gangaro zuwa wurin Dauda a lokacin girbi, zuwa kogon Adullam. Rundunar Filistiyawa sunyi sansani cikin kwarin Refim.14A lokacin nan Dauda yana cikin kagararsa, a kogo, yayin da Filistiyawa kuma suka kafu a Betlehem.15Dauda ya ji ƙịṣḥi ya ce, "Ina ma wani zai bani ruwa daga rijiyar da ke a Betlehem, rijiyar da ke kusa da ƙofa!"16Sai jarumawannan uku suka fasa rundunar Filistiyawa suka ɗebo ruwa daga rijiyar da ke Betlehem, wadda ke kusa da ƙofa. Suka ɗauki ruwan suka kawowa Dauda, amma yaƙi sha, Maimakon haka sai ya zuba wa Yahweh.17Daga nan sai ya ce, "Bari wannan ya yi nesa da ni, Yahweh, har da zan sha wannan. Zan sha jinin mutanen da suka sadaukar da rayukansu?" Domin wannan bai yarda ya sha ba, Waɗannan su ne al'amuran da jarumawan nan uku suka yi.18Abishai ɗan'uwan Yowab, ɗan Zeruya, shi ne babba cikin su uku. Ya taɓa yin yaƙi da mashinsa ya kuwa kashe mutum ɗari uku. An sha ambatonsa tare da sojojin nan guda uku.19Ba shi ya fi ukun suna ba? An sanya shi shugabansu. Duk da haka, sunansa ba a kwatanta shi da darajar sauran sojoji ukun.20Benaiya daga Kabzeyel shi ɗa ne wurin Yahoiyada; shi mutum ne mai ƙarfi wanda ya yi manyan abubuwa na kasada. Ya kashe 'ya'ya biyu na Ariyel na Mowab. Ya kuma shiga cikin rami ya kashe zaki a lokacin dusar ƙanƙara.21Kuma ya kashe wani Bamasare mutum mai daraja. Bamasaren yana da mashi a hannunsa, amma Benaiya ya yi yaƙi dashi da sanda kawai, ya fizge mashin a hannun Bamasaren sa'an nan ya kashe shi da mashinsa.22Benaiya ɗan Yehoiyada ya yi waɗannan ayyukan kasada, an lissafa sunansa cikin sunayen jarumawannan uku.23An mutumta shi fiye da sauran sojojin nan talatin gaba ɗaya. Amma bai kai sauran sojojin nan uku masu ƙarfi ba. Duk da haka Dauda ya sa shi a bisa matsaransa.24Mutum talatin ɗin sun haɗa da: Asahel ɗan'uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,25Shamma Baharodiye, Elika Baharodiye,26Helez Bafaltiye, Ira ɗan Ikkesh Batekoyi,27Abiyeza Ba'anatote, Mebunnai Bahushatiye,28Zalmon Ba'ahohite, Maharai Banetofatiye;29Heleb ɗan Bãna, Banetofatiye, Ittai ɗan Ribai daga Gibiya ta Benyamin,30Benaiya Bafiratoniye, Hiddai na wajen kwarin Gãsh.31Abi albon Ba'arbatiye, Azmabet Babarhumi,32Eliyaba Bashãlboniye 'ya'yan Yashen, Yonatan ɗan Shamma Baharariye;33Ahiyam ɗan Sharar Ba'arariye,34Elifelet ɗan Ahasbai Ma'akatiye, Eliyam ɗan Ahitofel Bagilone,35Hezro Bakarmile, Fãrai Ba'abite,36Igal ɗan Natan daga Zoba, Bani daga kabilar Gad.37Zelek Ammoniye, Naharai Baberote masu ɗaukarwa Yowab kayan yaƙi ɗan Zeruya,38Ira Ba'i tire, Gareb Ba'itire,39Yuriya Bahittiye dukkan su talatin da bakwai
Wannan shine farkon sabon sashin littafin.
Wannan yana nufin abin da Dauda zai ce a cikin 2 Sama'ila 23: 2-7.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutumin da Allah na Yakubu ya girmama sosai kuma ya shafe shi"
Wannan shine mutumin da yake rubuta zabura ko waƙoƙi.
Anan "a kan harshena" na managa don Dauda yana magana. AT: "ya ba ni saƙo in yi magana"
Wannan ya ci gaba da kalmomin Dauda na ƙarshe.
Anan "Allah na Isra'ila" dai-dai yake da "Dutsen Isra'ila." Kalmomin guda biyu suna faɗin abu ɗaya. Dauda ya gwada Allah da dutse don ya nanata ikonsa na kāre mutanensa.
Waɗannan jimlolin guda biyu duk suna cewa sarki zai girmama Allah kuma ya aikata abin da Allah yake so.
Anan Allah yana kwatanta sarki da hasken safiya da rana bayan ruwan sama. Duk waɗannan hanyoyi ne na faɗin wannan sarki zai zama abin farin ciki ga Allah da kuma albarka ga mutane. Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani da su don ƙarfafawa. AT: "Zai kasance mai faranta rai ga duka"
Anan Dauda yana cewa ya yarda da Allah. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Iyalina hakika haka suke a gaban Allah!"
Dauda ya yarda cewa Allah ya yi alkawari da shi. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Lallai ya yi ... hanya. "
Dauda yayi imanin cewa Allah zai taimake shi koyaushe kuma zai sa shi ya ci gaba. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Yana ƙarfafata kuma yana ba ni duk abin da nake so."
Wannan ya kammala kalmomin Dauda na ƙarshe.
Anan ana kwatanta mugaye da ƙayoyi marasa amfani. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Amma mugu ya kasance ba shi da daraja kuma yana da haɗari kamar ƙaya muke jefawa"
"saboda babu wanda zai iya ɗaukarsu da hannunsa ba tare da ƙayayyar ta cutar da shi ba"
"Inda aka samo ƙaya, a can ne dole ne a ƙone su." Wannan yana nufin Allah zai halakar da mugaye.
Wannan sunan mutum ne. Sauran fassarorin suna karanta Yosheb Basshebet, Yashobeyam, Ishba'al, ko Ishboshet saboda yawancin kofe na da irin waɗannan bambancin. Masu fassara na iya zaɓar faɗin wannan a cikin rubutun ƙafa zuwa fassarar su
Wannan sunan kungiyar mutane. AT: "ɗan Hakmon"
Wannan ya ci gaba da jerin manyan sojojin Dauda.
Wannan yana nufin cewa sojojin sun dawo bayan Eliyaza ya dawo daga yaƙi. AT: "Sojojin Isra'ila sun koma fagen fama bayan Eliyaza ya riga ya ci nasara a yaƙi"
"kawai su dauki abin da suke so daga gawarwakin makiya"
Wannan ya ci gaba da jerin manyan sojojin Dauda.
"filin da wani ya shuka lentil"
iri iri, wanda aka ci kamar wake
"sojojin Isra'ila sun gudu"
"kogo kusa da garin Adullam." Adullam yana kusa da Betlehem.
Wannan sunan wani wuri ne. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sama'ila 5:18.
"Wasu sojojin Filistiyawa suna iko da ƙauyen Betlehem"
"yaƙi hanyarsu ta hanyar abokan gaba sojojin"
Dauda ya kwatanta ruwan da jini domin mutanen sun saka kasada da ransu don su kawo masa ruwan. Yana amfani da tambaya don jaddada wannan. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Shan wannan ruwan zai zama kamar shan jinin waɗannan mutanen da suka sadaukar da rayukansu don kawo mini shi."
Waɗannan sunayen maza. Fassara su kamar yadda yake a cikin 2 Sama'ila 2:18.
Wannan yana nufin Abishai shine shugaban jarumawa uku ɗin da suka je suka samo wa Dauda ruwa.
Ana amfani da wannan tambayar don jaddada yadda ya shahara. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Har ma ya shahara fiye da ukun."
Wannan sunan birni ne.
Waɗannan sunayen maza.
"aikata waɗannan ayyuka masu girma"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane suna yabon sa kamar yadda suka yaba wa jaruman uku"
ƙungiyar sojoji masu lura da Dauda
Wannan jerin manyan sojoji ne na Dauda.
"Manyan sojoji 30 da suka shahara"
Wannan ya ci gaba da jerin manyan sojojin Dauda.
Wannan ya ci gaba da jerin manyan sojojin Dauda.
Wannan ya kammala jerin manyan sojoji na Dauda.
"akwai 37 dukka"
1Fushin Yahweh ya sake ƙuna akan Isra'ila, ya kuma iza Dauda akansu ya ce, "Jeka ka ƙidaya Isra'ila da Yahuda."2Sarki ya ce da Yowab shugaban runduna, wanda ya ke tare dashi, "Ka tafi cikin dukkan kabilun Isra'ila, daga Dan zuwa Biyasheba, ka ƙirga dukkan mutane, domin in san jimillar dukkan mutane da suka cancanta domin yaƙi."3Yowab ya cewa sarki, "Bari Yahweh Allahnka ya riɓanɓanya mutane sau ɗari, kuma bari idanun sarki shugabana ya ga faruwar haka. Amma donme shugabana sarki ya ke son wannan?"4Duk da haka maganar sarki ta zama ita ce ta ƙarshe akan ta Yowab da sauran shugabannin rundunar yaƙi. Sai Yowab da sarakunan rundunar yaƙi suka fita daga gaban sarki domin su ƙirga yawan mutanen Isra'ila.5Suka haye Yodan suka sauka kusa da Arowa, hannun dama ga birnin da ke cikin kwari. Daga nan suka yi tafiya zuwa Gad har zuwa Yazer.6Suka zo Giliyad da kuma ƙasar Tahtim Hodshi, daga nan sai Dan yăn da kewayen wajen Sidon.7Suka zo kagarar Taya da dukkan biranen Hibiyawa dana Kan'aniyawa. Daga nan suka fita zuwa Negeb cikin Yahuda a Biyasheba.8Ya yin da suka je dukkan ƙasar, sai suka dawo Yerusalem a ƙarshen watan tara da kwana ashirin.9Yowab ya bada rahoton jimillar yawan mayaƙa ga sarki. Akwai mutum 800,000 a cikin Isra'ila jarumawa masu zarar takobi, mazajen Yahuda kuma su 500,000 ne.10Daga nan sai zuciyar Dauda ta soke shi bayan ya lissafta mutanen. Sai ya ce da Yahweh, "Na yi babban zunubi ta wurin yin wannan. Yanzu fa, Yahweh, ka ɗauke laifin bawanka, gama na aikata wauta ƙwarai."11Sa'ad da Dauda ya tashi da safe, sai maganar Yahweh ta zo wurin annabi Gad, mai duba, na Dauda cewa,12"ka je kace da Dauda: 'Wanan shi ne abin da Yahweh ya ce: "'Ina miƙa maka abu uku, sai ka zaɓi ɗaya cikinsu.""13Sai Gad ya je wurin Dauda ya ce masa, "Ko shekaru uku na yunwa su zo maka cikin ƙasarka, ko kuwa zaka yi ta gudu wata uku daga abokan gabarka suna bin ka? ko kuwa za ayi annoba kwana uku a cikin ƙasarka? Yanzu sai kayi shawarar amsar da zan maida wa shi wanda ya aiko ni."14Sai Dauda ya cewa Gad, "I na cikin babbar damuwa." Bari mu faɗa cikin hannun Yahweh da mu faɗa cikin hannun mutum, gama ayyukan jinƙansa da girma suke."15Sai Yahweh ya aika da annoba kan Isra'ila daga safe zuwa lokacin da aka sanya, mutane dubu saba'in suka mutu daga Dan zuwa Biyasheba.16Lokacin da mala'ika ya miƙa hannunsa wajen Yerusalem domin ya hallakata, Yahweh ya canza tunaninsa game da ɓarnar, ya ce da mala'ikan da ke hallakar da mutanen, "Ya isa! Sai ka janye hannunka yanzu." A wancan lokacin mala'ikan Yahweh yana tsaye a masussukar Arauna Bayebushe.17Dauda ya yi magana da Yahweh da ya ga mala'ikan da ya bugi mutanen, ya ce, "Na yi zunubi, kuma na yi aikin shiririta. Amma tumakin nan me suka yi? Ina roƙon ka bari hannunka ya hukunta ni da iyalin mahaifina!"18Ran nan sai Gad ya zo wurin Dauda ya ce masa, "Ka hau ka gina bagade ga Yahweh a masussukar Arauna Bayebushe."19Dauda kuwa ya hau kamar yadda Gad ya faɗa masa ya yi, kamar yadda Yahweh ya umarta.20Arauna ya duba ya ga sarki da bayinsa suna isowa. Sai Arauna ya fito ya sunkuyar da kansa ga sarki da fuskarsa a ƙasa.21Daga nan sai Arauna ya ce, "Donme shugabana sarki ya zo wurina, bawansa?" Dauda ya amsa, "Domin in sa yi masussukarka, domin in gina bagadi ga Yahweh, domin a iya kawar da annoba cikin mutane."22Arauna ya cewa Dauda, "Ka ɗauke ta kamar ta ka, ya shugabana sarki. Ka yi dukka abin da ka ga dama. Duba, ga shanu domin hadaya ta ƙonawa da kayan masussuka da karkiyoyin shanu domin itace.23Dukkan waɗannan, sarkina, Ni, Arauna, zan ba ka." Sai ya ce da sarki, "Bari Yahweh Allahnka ya karɓe ka."24Sai sarki ya cewa Arauna, "A'a, lallai sai dai mu yi ciniki in saye ta. Ba zan miƙa hadayar ƙonawa ga Yahweh ta kowanne abin da ban biya ba." Dauda ya sayi masussukar da shanun akan awo hamsin na azurfa.25Dauda ya gina wa Yahweh bagadi a wurin ya miƙa ƙonannun hadayu, da hadayun zumunta. Da haka suka roƙi Yahweh a madadin ƙasar, ya kuma sa annobar ta tsaya a ko'ina cikin Isra'ila.
Kalmar "ƙonewa" na nufin kunna wuta. Anan an kwatanta fushin Yahweh da na wuta. AT: "fushin Yahweh ya fara zafi kamar wuta"
"ya sa Dawuda ya yi tsayayya da su"
A cikin dokar Musa, Allah ya hana sarakunan Isra’ila yin ƙidayar mazaje masu yaƙi. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari.
Wannan jimlar tana amfani da sunaye biyu masu suna Dan, a can arewa mai nisa, da kuma Biyasheba, a kudu mai nisa, don wakiltar ƙasar baki ɗaya.
Wannan yana nufin ƙidaya duk mazan banda waɗancan maza da suka yi ƙuruciya, suka tsufa, ko kuma ba sa iya yaƙi.
Wannan yana nufin "samar da karin mutane 100 ga kowane mutum guda daya da yake yanzu."
Yowab da sauran shugabannin sojojin sarki Dawuda ba su iya shawo kan Dawuda ya ƙidaya ba.
Wannan jimlar tana wakiltar umarnin sarki ne a gare su. AT: "abin da sarki ya umarta"
"Yowab da shugabannin sojoji suka haye"
Wannan birni ne a gefen arewacin Kogin Arnon.
Wannan garin ne a cikin Gad.
Wannan na iya nufin garin Kadesh a cikin ƙasar Hittiyawa.
"Yowab da shugabannin sojoji sun tafi"
"Watanni 9 da kwana 20"
Yowab kuwa ya faɗa wa sarki yawan mutanen da suka isa yaƙi.
Wannan sunan yana nufin mutanen da suke a shirye don yin yaƙi.
Anan, “zuciya” ta motsin zuciyar Dauda da lamirinsa. AT: "Dauda ya ji da laifi"
Dauda ya kira kansa "bawanka." Wannan hanyar ladabi ce don magana da wanda ke da iko.
Karin magana "kalmar Yahweh ta zo ga" ana amfani da ita don gabatar da saƙo na musamman daga Allah. Duba yadda kuka fassara wannan karin magana a cikin 2 Sama'ila 7: 4. AT: "Yahweh ya ba da sako ga annabi Gad, mai ganin Dauda. Ya ce," ko "Yahweh ya yi wannan saƙon ga annabi Gad, mai ganin Dauda:"
Wannan yana nufin Gad babban annabin ne a cikin masarautar.
"Ina cikin mummunan matsala"
Anan "hannaye" suna nufin iko ko sarrafawa. AT: "Bari Yahweh ba mutane su hukunta mu ba"
Wannan shine lokacin da Allah ya yanke shawarar zai dakatar da annoba.
"mutane 70,000"
Anan kalmar "hannu" yana nufin ikon mala'ikan. AT: "mala'ikan na gab da halakar da mutanen Yerusalem"
Wannan yana nufin cewa Yahweh ya dakatar da muguntar da yake barin mala'ikan ya yi. AT: "Yahweh ya yi baƙin ciki game da cutar"
Kalmar "hannu" yana nufin ikon mala'ikan. AT: "Kada ku sake cutar da su"
Wannan sunan mutum ne.
Waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya kuma ana haɗa su don ƙarfafawa. AT: "Na yi zunubi ƙwarai"
David ya yi amfani da tambaya kuma ya kamanta mutane da tumaki don ya nanata cewa ba su yi wani laifi ba. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Waɗannan talakawan ba su yi laifin komai ba."
A nan kalmar "hannu" yana nufin iko. AT: "Da fatan za a azabtar da ni"
Yana nuna ban girma da kuma daraja ga sarki.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "domin Yahweh ya cire wannan annoba daga mutane"
Anan gani yana wakiltar hukunci ko kimantawa. AT: "abin da kuke tsammani mai kyau ne" ko "abin da ke mai kyau a cikin hukuncinku"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Zan gabatar da ... wani abu da na biya"
Anan kalmar "ƙasa" tana nufin mutanen Isra'ila. AT: "a madadin mutanen Isra'ila"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ya tsare annobar da ta kasance a kan Isra'ila" ko "Allah ya kawar da annobar daga Isra'ila"
1Sa'ad da Sarki Dauda ya tsufa sosai, suka lulluɓe shi da barguna amma bai ji ɗumi ba.2Sai bayinsa suka ce, "Bari mu samo wa shugabanmu sarki wata budurwa domin ta yi wa sarki hidima ta kula da shi. Ta kwanta a damatsen shugabanmu sarki domin ya ji ɗumi."3Suka bincika cikin dukkan lungunan Isra'ila, sai suka samo Abisha Bashunamiye su ka kawo ta wurin sarki. Budurwar kyakkyawa ce ƙwarai.4Ta yi wa sarki hidima ta lura da shi, amma sarkin bai kwana da ita ba.5A wannan lokacin Adonija ɗan Haggit ya ɗaukaka kansa, cewa, "Ni zan zama sarki." Ya shirya wa kansa karusai da mahaya, mazaje hamsin su wuce gabansa.6Babansa bai dame shi ba da cewa, "Meyasa ka yi wannan ko wancan?" Adonija ma kyakkyawan mutum ne ƙwarai, shi aka haifa bayan Absalom.7Ya haɗa kai da Yowab ɗan Zeruyiya da Abiyata firist. Suka bi Adonija suka taimaka masa.8Amma Zadok firist da Benayiya ɗan Yehoiada da Natan annabi da Shimai da Reyi da jarumawan da ke tare da Dauda ba su bi Adonija ba.9Adonija ya yi hadayar tumaki da bijjimai da kiwatattun shanu kusa da dutsen Zohelet, wanda ke daura da En Rogel. Ya gayyaci dukkan 'yan'uwansa, 'ya'yan sarki da dukkan mazajen Yahuda da bayin sarki.10Amma Natan annabi da Benayiya da mazajen Suleman ɗan'uwansa bai gaiyace su ba.11Sai Natan ya yi wa Batsheba uwar Suleman magana, cewa, "Ba ki ji cewa Adonija ɗan Haggit ya zama sarki ba, kuma ba da sannin Dauda shugabanmu ba?12Bari in ba ki shawara yanzu domin ki ceci ranki da na ɗanki Suleman.13Ki je wurin sarki Dauda, ki ce, shugabana, ba ka yi rantsuwa ga baiwarka ba, cewa, "Babu shakka Suleman ɗanki shi ne zai yi sarauta bayana, ya zauna kan kursiyina ba?" Me ya sa Adonija ke mulki?'14Sa'ad da ki ke magana da sarki, zan zo in tabbatar masa da maganganunki."15Sai Batsheba ta tafi ɗakin sarki. Sarki ya tsufa ƙwarai, Abisha Bashunamiya tana yi wa sarki hidima.16Batsheba ta sunkuya ta kwanta a gaban sarki. Sarki ya ce da ita, "Me ki ke so?"17Ta ce da shi, "Shugabana, ka rantsewa baiwarka da Yahweh Allahnka, cewa, 'Babu shakka Suleman ɗanki, shi zai yi mulki baya na, shi zai zauna a kursiyina?'18To yanzu ka ga, Adonija ne sarki, kai kuma shugabana sarki ba ka sani ba.19Ya yi hadaya da bijjimai da kiwatattun shanu da tumaki da yawa, kuma ya gayyaci dukkan 'ya'yan sarki da Abiyata firist da Yowab shugaban sojoji, amma bai gayyaci Suleman bawanka ba.20Game da kai shugabana sarki, dukkan idanun Isra'ila kai suke kallo, suna jira ka ce da su ga wanda zai yi mulki a bayana, shugabana.21Idan kuwa ba haka ba, zai zama bayan da shugana sarki ya yi barci tare da ubanninsa, ni da ɗana Suleman za a mai da mu kamar 'yan ta'adda."22Tana cikin magana da sarki, sai Natan annabi ya shigo.23Barori suka ce da sarki, "ga Natan annabi ya zo." Sa'ad da ya shigo gaban sarki, ya kwanta da fukarsa a ƙasa a gaban sarki.24Natan yace, "Shugabana sarki, ka ce Adonija zai yi mulki bayana, shi zai zauna kan kursiyina ne?'25Gama ya tafi yau ya yi hadaya da bijjimai da kiwattatun shanu da tumaki da yawa, kuma ya gayyaci dukkan 'ya'yan sarki da shugaban sojoji da Abiyata firist. Suna ci suna sha a gabansa, suna cewa, 'ranka ya daɗe sarki Adonija!'26Amma ni, bawanka da Zadok firist da Benaiya ɗan Yehoiada da bawanka Suleman bai gayyace mu ba.27Shugabana ya yi haka ba tare da ya gaya mana bayinka ba, wanda zai zauna a kan kursiyinsa?"28Sai sarki ya amsa ya ce, "kira mani Batsheba ta dawo." Ta zo gaban sarki ta tsaya.29Sarki ya yi alƙawari ya ce, "Da ran Yahweh wanda ya cece ni daga dukkan wahalhalu,30kamar yadda na rantse maku da Yahweh, Allah na Isra'ila, cewa, 'Suleman ɗanki, shi zai yi mulki bayana, zai zauna kan kursiyna, zan yi haka yau."31Sa'an nan sai Batsheba ta sunkuya da fuskarta a ƙasa ta kwanta gaban sarki ta ce, "Ranka ya daɗe shugabana, sarki Dauda!"32Sarki Dauda yace, "A kira mani Zadok firist da Natan annabi da Benayiya ɗan Yahoiada." Sai su ka zo gaban sarki.33Sarki ya ce, "ku tafi da barorin shugabanku, ku sa Suleman ya hau alfadarina ku kai shi Gihon.34Bari Zadok firist da Natan annabi su shafe shi ya zama sarki akan Isra'ila su busa ƙaho su ce, 'Ranka ya daɗe sarki Suleman!'35Sai ku biyo shi, ya zo ya zauna kan kursiyina; domin shi ne zai gaje ni. Na naɗa shi ya zama sarki bisa Isra'ila da Yahuda."36Benayiya ɗan Yehoiada ya amsawa sarki ya ce, "Bari ya zama haka! Yahweh Allah na shugabana sarki, ya tabbatar da shi.37Kamar yadda Yahweh ya kasance da shugabana sarki, bari ya kasance da Suleman, kursiyinsa ya ɗaukaka fiye da kursiyin shugabana sarki Dauda."38Sai Zadok firist da Natan annabi da Benayiya ɗan Yehoiada da Keretawa da Feletiyawa suka je suka ɗora Suleman akan alfadarin Sarki Dauda; suka kawo shi Gihon.39Zadok firist ya ɗauko ƙahon mai daga cikin rumfa ya shafe Suleman. Sa'an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka ce, "Ranka ya daɗe sarki Suleman."40Sa'an nan dukkan mutane suka biyo shi suna busa sarewa suna farinciki da murna sosai, har ƙasa ta girgiza saboda ƙararsu.41Adonija da bãƙinsa da ke tare da shi suka ji sa'ad da suka gama ciye-ciye. Sa'ad da Yowab ya ji ƙarar ƙahon ya ce, "Me ya sa a ke hargowa a cikin birni?"42Yana cikin magana Yonatan ɗan Abiyata firist ya zo. Adonija yace, "Shiga, kai mai aminci ne ka kuma kawo labari mai daɗi."43Yonatan yace da Adonija, "Shugabanmu sarki Dauda ya sa Suleman ya zama sarki,44kuma sarki ya aiko shi tare da Zadok firist da Natan annabi da Benayiya ɗan Yehoiada da Keretawa da Feletiyawa. Sun sa Suleman ya hau alfadarin sarki.45Zadok firist da Natan annabi sun shafe shi ya zama sarki a Gihon, sun taho daga can su na murna, saboda haka birni ya cika da hargowa. Wannan ita ce hayaniyar da ka ke ji.46Kuma, Suleman yana zaune akan kursiyin mulki.47Bayan haka, barorin sarki sun zo suna sawa sarki Dauda albarka suna cewa, 'Bari Allahnka ya sa sunan Suleman ya fi naka.' Sai sarki ya sunkuya akan gado.48Sai sarki ya ce, 'Albarka ga Yahweh Allah na Isra'ila, da ya bada wanda zai zauna akan kursiyina yau, kuma idona yana gani.'"49Sai dukkan bãƙin Adonija suka firgita. Suka tashi tsaye kowa ya bi hanyarsa.50Adonija yana jin tsoron Suleman, ya je ya riƙe ƙahonin bagadi.51Sai aka gaya wa Suleman cewa, Duba, Adonija yana jin tsoron sarki Suleman, gama gashi can ya na riƙe da ƙahonin bagadi, yana cewa, 'Bari sarki Suleman ya rantse mani cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba."'52Suleman yace, "Idan zai nuna kansa mutumin kirki, ko gashin kansa ba zai faɗi a ƙasa ba, amma idan aka sami mugunta a wurinsa to zai mutu."53Sarki Suleman ya aika mutane suka saukar da Adonija daga bagadi. Ya zo ya russana a gaban Suleman, Suleman ya ce da shi, "Tafi gidanka."
suka sa barguna masu yawa akan sarkin Dauda domin ya ji ɗumi
"barorin sarki suka bincika"
Wannan gaba ɗaya ne. AT: "a dukkan ƙasar Isra'ila"
Wannan sunan mace ne.
mutun ɗan ƙasar shunem
"sarki Dauda"
Haggit matar Dauda ce.
"ya fara taƙama"
Wadannan mazajene wadanda suke hawan karusai wanda dawakai suke ja.
wadannan mazajen za su je gaban karusan su shirya hanya dominsu su kuma kare su.
"bai taɓa damin shi ba. Bai ma taɓa tambayanshi ba" ko "bai taɓa son ya ɓata masa rai ba, saboda haka bai ma tambayeshi ba"
wannan tambayar habaici ne da mahaifi zai ya hori yaronsa. AT: "ka san abin da kayi ba dai_dai bane."
Dauda shine mahaifin Absalom da Adonijah, amma kowa da mahaifiyarsa. An haifi Absalom, san nan Adonijah.
"Adonija ya tattauna nufinsa da Yowab"
Waɗannan sunan maza ne.
" goyon baya da taimakon Adonija" ko "alkawarin goyon baya da taimakon Adonija"
"maraƙai da aka ba abinci mai yawa don suyi kiba" ko " 'yan maruƙa da aka ba wa kulawa ta musamman domin ayi hadaya"
wannan dutsen ne kusa da Yerusalem.
wannan sunan maɓulɓular ne inda mutane suke samun ruwa.
wannan gaba daya ne.
wannan jimlar biyun na nufin mutane daya
wanan jimlar biyun na nufin mutune daya
manufar wannan tambayan shine don a gabatar da bayanan da Nathan yake so ya gaya wa Batsheba. AT: "kayi kamar baka ji ... shi ba" ko " kaji ... kuwa?"
"cewa yaron Haggit Adonija yana ƙoƙarin ya zama sarki"
Mahaifiyar Adonija kuma matar Dauda.
Annabi Natan ya ci gaba yayi magana da batsheba.
manufan wannan tambayar domin a tunashe Dauda abin da yayi wa Batsheba alkawari. AT: "ka yi rantsuwa ga baiwarka ... kursiyi,"
Batsheba tayi magana da Dauda kamar wata dabam ne ta nuna tana girmama Dauda. AT: "ga ni, baiwarka"
zama a kan kursiyi tabbatarwa ce za ka zama sarki. AT: "zai zama sarki kamar yadda nake"
Batsheba zata yi amfani da tambaya don Dauda ya saurareta. " daga nan, Adonija ya dena mulki."
"ka gaya masa abinda ka faɗa gaskiya ne"
"ɗakin da sarki yake barci"
wannan budurwa ce wadda bawan sarki ya kawo domin ta ringa kulawa dashi.Translate as in 1:3.
"kanta kusa da kasa a gaban sarki"
"Me zanyi maki?"
kalmar "kai" anan na nuna. AT: "kai da kanka ka rantse "
Batsheba tayi magana kamar wata dabam ta nuna tana girmama shi. Translate as in 1:13. AT: "Ni, baiwarka"
Wannan sunan Allah ne da ya bayyana kansa ga mutanensa a tsohon alkawari. See the translationWord page about Yahweh domin yadda zamu fassara shi.
zama a kan kursiyi tabbatarwa ce za ka zama sarki. translate as in 1:13. AT: "shi zai zama sarki kamar yadda nake"
Batsheba tayi ci gaba magana da sarki Dauda.
"ka saurari abinda nake shirin gaya maka"
"bijimai da yawa, kiwatattun shanu, da tumaki"
Batsheba ta ci gaba magana da sarki Dauda.
Anan"ido" na nufin mutanen. wannan dukka ne. AT: "dukkan mutanen Isra'ila na kallon ka"
zama a kursiyi tabbatarwa ce ka za ka zama sarki. Irin wannan kalmar ya bayyana a 1:13 AT: "zai zama sarki"
Batsheba tayi magaana da sarki kamar tana maganaa kansa ta nuna tana girmama shi. AT:"bayan ka yi barci da ubanninka"
Wannan wata ta fadi "mutuwa."
wanna za a iya fassara shi gaba gaɗi AT: "sabon sarki zai mai da ɗana Solomon da ni kamar 'yan ta'adda" (Duba: )
Annabi Natan ya yi magana da sarki Dauda
"sunkuya kasa sosai"
Annabi Natan ya ci gaba magana da sarki
wannan za'a iya fassara shi magana da ba miƙaƙƙiya ba AT: "kace Adonija zai yi mulki bayana, kuma zai zauna kan kursiyina?"
zama a kan kursiyi tabbabtarwa ce za ka zama sarki. Translate as in 1:13. AT: "zai zama sarki kamar yadda nake"
Adonija me yi wuwa ya zauna a wurin cin abinci inda zai iya kallon dukkan wadanda ya gayyata lokacin da suke ci suke sha. Asalin batun shi ne mutanen da Natan ya ba wa suna su na tare da Adonija kuma suna yin buki tare. AT: "ci da sha tare da shi" ko "ci da sha inda zai iya ganinsu"
Annabi Natan ya ci gaba magana da sarki Dauda.
Natan na nufin Dauda mutum na uku. wannan wani hanya ne na girmama sarki. za'a iya faɖin shi a mutum na biyu. AT: "ka yi, shugabana sarki, yi haka ba tare da gaya mana, bayinka,wanda zai zauna a kursiyin bayanka?"
zama a kursiyi tabbatarwa ce za ka zama sarki. Irin wannan ya fito a 1:13. AT: "wanda zai zama sarki baya shi"
Sarki Dauda ya yi wa Batsheba alkawari.
"Ta zo gaban sarki" ko "ta dawo wurin sarki"
"yin alkawarin rantsuwa"
zama a kan kursiyi tabbatarwa ce zaka zama sarki. Irin wannan ya fito a 1:13. AT: "zai dauke wurina kuma zai zama sarki kamar yadda nake"
Batsheba ta san Dauda ba zai rayu har abada ba; wannan wata hanya ce ta ce masa shi sarki ne mai adalci.
Sarki Dauda ya shafe Sulaiman ya zama sarki.
Dauda yayi magana game da shi kamar yana magana da wani dabam sai Zadok, Nathan, da Benaiyezasu tuna cewa Dauda har yanzu sarki ne.AT: "bawana"
Wannan sunan maɓulɓular ruwa ne.
Sarki Dauda ya ci ga ba da magana a madadin Sulaiman kamar wanda zai zama sarki
Kalmar "zauna a kan kursiyi" ana amfani dasu adon tabbatar war zama sarkia 1:13, 1:15, da 1:28. Anan Dauda ya yi magana da Sulaiman yana ganin sa kamar ya riga ya zauna akan kursiyin.
Sun yarda kuma zasu yi abinda sarki Dauda ya ce.
Benaiya yayi magana da sarki Dauda kamar yana magana da wani dabam ya nuna ya girmama sarki Dauda. AT: "Ya shugabana da sarkina,Yahweh Allahnka ya tabbatar"
Benaiya yayi magana da sarki Dauda kamar yana magana da wani dabam ya nuna ya girmama sarki. AT: "ya kasanca tare da shugabana sarki, bari"
Kalmar "kursiyi" tabbatarwa ce ga ko
Benaiya yayi magana da sarki Dauda kamar yana magana da wani dabam ya nuna yã girmama sarki Dauda. AT: "kursiyinka shugabana sarki Dauda"
Mutanen Isra'ila suka shafe Sulaiman ya zama sarki bisan Isra'ila
Wannan sunan ƙungiyar mutane ne.
Wannan sunan maɓulɓular ne, inda ruwa mai kyau yake fitowa daga ƙasa.
Wannan na nufin firist ya ɗauko ƙahon keɓaɓɓen dabba cike da mai da aka ajiye shi a rumfa ta musamman ta Yahweh.
ma'ana ana shi ne 1) ƙahon dabba da aka cika da mai ko 2) wani ma'auni daya zama a madadin ƙahon, amma mutanen suna kiran shi ƙaho, AT: "ɗaukan ma'aunin mai"
Dukka gaba ɗaya.
Adonija yaji amo mai ƙara sai ya jira labaran
Adonija ya ji Sulaiman ne sabon sarki.
Wannan sunan ƙungiyar mutane ne.
Yonatan ya ci gaba da magana da Adonijagame da Sulaiman
ma'ana anan shine 1) wadannan kalmomi tabbatarwa ne na zama sarki. AT: "yanzu shi sarki ne" ko 2) Sulaiman yanzu na zama a kan kursiyi zahiri. Irin wannan ya bayyana a 1:35.
Wata ma'ana 1) wannan kalmomi tabbatarwa zama sarki ne. AT: "mutumin zai zama sarki kamar yadda nake" ko 2) Sulaiman na zama a kan kursiyin a zahiri. Irin wannn ya bayyana a 1:35.
Adonija ya fara jin tsoron Sulaiman.
wata ma'ana shine "suka fara yin ayyuka da sauri"
"ƙahon bagadin" yana kamanta ƙarfi da kariyar Yahweh, amma saboda Adonija yaje wurin rumfa da za'a iya gani domin ya dauki ƙahon da za'a iya gani fassara wannan a zahirance.
Wata ma'ana anan shine "Adonija ... ya tafi sauri"
Barorin suka yi ma sarki Sulaiman magana kamar suna yi wa wani dabam magana su na nuna suna yi ma sarki Sulaiman magana. AT:"yana jin tsoron su, sarki Sulaiman"
Adonija yayi magana da kansa kamar yana magana da wanidon mutane su ce yana biyayya da sarki Sulaiman. AT:"ba zai kashe ni ba"
Sulaiman ya kuɓutar da ran Adonija.
Wannan fifita magana ne don a ce Sulaiman zai bar Adonija a raye. AT: "ko gashin kansa ba zai fadi ƙasa ba" ko "zan sa shi ya zame a kãre"
wakilin suna "mugunta" za'a iya fassara shi a matsayin aiki. A na maganar sa kamar wani abu da za'a iya samun sa a ma'auni.za'a iya fassara shi a abinda da za'a iya yi. AT: "ya yi mugunta"
1Sa'ad da ranar mutuwar Dauda ta gabato, ya umurci ɗansa, Suleman cewa,2"ina bin hanyar dukkan duniya, ka ƙarfafa, ka nuna kanka namiji.3Ka kiyaye dokokin Ubangiji Allahnka, ka yi tafiya cikin hanyoyinsa, ka kiyaye farillansa da dokokinsa da shawarwarinsa da alƙawaransa, kana kiyaye abin da da aka rubuta cikin dokokin Musa domin ka wadata cikin dukkan abin da ka ke yi, a dukkan inda ka nufa,4domin Yahweh ya cika maganarsa wadda ya faɗi game da ni, cewa, 'Idan 'ya'yanka suka lura da tafarkinsu, suka yi tafiya a gabana da aminci da dukkan zuciyarsu da dukkan ransu, ba za ka rasa mutum akan kursiyin Isra'ila ba.'5Ka san abin da Yowab ɗan Zeruya ya yi ma ni da abin da ya yi wa jami'an sojojin Isra'ila su biyu, Abna ɗan Ner da Amasa ɗan Yatar waɗanda ya kashe. Ya zubar da jinin yaƙi cikin salama, ya sa jinin yaƙi akan ɗamarar da ke ƙugunsa da takalman da ke ƙafafunsa.6Ka yi da Yowab bisa ga hikimar da ka koya, amma kada ka bari furfurarsa ta tafi kabari cikin salama.7Duk da haka, ku yi mutunci ga 'ya'yan Barzilai Bagilide, ku bar su su zauna a cikinku su ci a teburinka, gama sun je wurina sa'ad da na gudu daga wurin ɗan'wanka Absolom.8Duba, Shimai ɗan Gera mutumin Benyamin ta Bahurim yana tare da ku, wanda ya zage ni, ya wulaƙanta ni, ya zazzage ni ranar da na je Mahanayim. Ya zo ya tarbe ni a Yodan, na rantse masa da sunan Yahweh cewa, 'Ba zan kashe ka da takobi ba.'9Kada ka bar shi ya tafi ba tare da ka hore shi ba. Kana da hikima ka san yadda za ka yi da shi. Ka sa furfurarsa ta faɗi cikin jini."10Sa'an nan Dauda ya yi barci tare da ubanninsa aka bizne shi a birnin Dauda.11Dauda ya yi mulki a Isra'ila shekaru arba'in, shekaru bakwai ya yi mulki a Hebron, a Yerusalem kuma ya yi mulki shekaru talatin da uku.12Suleman ya zauna akan kursiyin Dauda ubansa, mulkinsa kuwa ya kahu da ƙarfi ƙwarai.13Sai Adonija ɗan Haggit ya zo wurin Batsheba uwar Suleman. "Ta ce da shi cikin salama ka zo?" Ya ce, cikin salama ƙwarai."14Ya ce, ina da wani abu da zan faɗa maki." Sai ta ce, "To ka faɗi."15Adonija yace, "Kin san mulkin nawane, dukkan Isra'ila sun yi zaton ni zan zama sarki. Amma abubuwa sun canza, an ba ɗan'uwana sarauta, kuma wannan daga Yahweh ne.16Zan roƙi abu ɗaya a wurin ki, kada ki juya mani baya, Batsheba ta ce, "Ka faɗi."17Ya ce, "Ki yi magana da Suleman sarki, na san ba zai ƙi jin maganar ki ba, ki ce da shi ya ba ni Abishag Bashunamiye ta zama matata.18Batsheba ta ce, "Ya yi kyau, zan yi magana da sarki."19Sai Batsheba ta je wurin sarki ta faɗa masa maganar da Adonija ya yi. Sarki ya je ya tarbe ta, ya russana a gabanta. Sa'an nan ya zauna a kan kursiyinsa kuma ya sa aka kawo wa mamar sarki kujera. Ta zauna a hannun damarsa.20Ta ce da shi, "Zan roƙi wani ɗan abu daga wurinka, na sani ba za ka ƙi ba." Sai sarki ya ce, "Ki roƙa mama, ba zan ƙi ba."21Ta ce, "Ka bari a ba Adonija ɗan'uwanka Abishag Bashunamiye ta zama matarsa."22Sarki Suleman ya amsa ya ce da mamarsa, "Meyasa ki ka ce a ba Adonija Abishag Bashunamiye ta zama matarsa? Meyasa ba ki ce a ba shi mulkin ba kuma gama shi yayana ne - ne dai, domin Abiyata firist, ko domin Yowab ɗan Zeruya?"23Sarki Suleman ya rantse da sunan Yahweh, ya ce, "Bari Allah ya yi mani fiye da haka, idan Adonija ba a bakin ransa ya faɗi wannan magana ba.24Yanzu da ran Yahweh, wanda ya sa ni a kan kursiyin Dauda mahaifina, ya yi gida domina, babu shakka yau za a kashe Adonija."25Sarki Suleman ya aiki Benayiya ɗan Yehoiada, ya nemi Adonija ya kashe shi.26Sa'an nan sarki ya ce da Abiyata firist, ka tafi Anatot, ga gonakinka, kaima ka isa mutuwa, amma ba zan kashe ka a wannan lokaci ba, domin ka ɗauki akwatin Ubangiji Yahweh a gaban Dauda mahaifina, ka sha wahala kamar yadda mahaifina ya sha."27Ta haka Suleman ya kori Abiyatar daga zama firist na Yahweh, domin maganar da Yahweh ya faɗi a Shilo game da gidan Eli ta cika.28Sai maganar ta zo ga Yowab saboda ya goyi bayan Adonija, ko da ya ke bai goyi bayan Absolom ba. Sai Yowab ya gudu ya shiga rumfar Yahweh ya kama ƙahonin bagadi ya riƙe.29Sai aka gaya wa Suleman sarki, cewa ga Yowab can cikin rumfar Yahweh, sai ya ce da Benayiya ɗan Yehoiada, "Je ka same shi ka kashe shi."30To sai Benayiya ya zo rumfar Yahweh, ya ce masa, "Sarki ya ce, 'ka fito"' Yowab ya amsa ya ce, "A'a ni zan mutu a nan." Sai Benaiya ya koma ya gaya wa sarki, cewa, Yowab yace, Yana so ya mutu a kan bagadi."31Sai sarki ya ce da shi, yi yadda ya faɗi. Kashe shi ka ɗauke shi, ka bizne domin a kawar da jinin da Yowab ya zubar ba dalili daga gidan mahaifina.32Yahweh ya sa jininsa ya koma kansa, gama ya sami mutane biyu waɗanda sun fi shi, kuma sun fi shi sarki, ya kashe su da kaifin takobi. Wato Abna ɗan Na shugaban sojojin Isra'ila da Amasa ɗan Yeter shugaban sojojin Yahuda, ba tare da sanin mahaifina sarki Dauda ba.33Bari jininsu ya dawo kan Yowab da zuriyarsa har abada. Amma ga Dauda da zuriyarsa da gidansa da kursiyinsa, bari salama daga Yahweh ta kasance har abada."34Sai Benayiya ya je ya sami Yowab, ya far masa ya kashe shi. A ka bizne shi a gidansa cikin daji.35Sarki ya sa Binayiya ɗan Yehoiada ya zama shugaban sojoji maimakon sa, ya kuma sa Zadok firist a gurbin Abiyata.36Sai kuma sarki ya aika a ka kira Shimai, yace masa, "Ka gina gida domin kanka a cikin Yerusalem ka zauna nan, kada ka bar wurin ka je ko'ina.37Duk randa ka fita ka wuce kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu. Kuma jininka zai koma kanka."38Sai Shimai ya cewa sarki abin da ka faɗi ya yi kyau. Kamar yadda shugabana sarki ya faɗi, haka bawanka za ya yi." Daga nan Shimai ya zauna a Yerusalem kwanaki da yawa.39Amma bayan shekaru uku, bayin Shemai guda biyu suka guda suka je wurin Akish ɗan Ma'aka, sarkin Gat. A ka gaya wa Shimai, cewa, duba, bayinka "biyu fa sun koma Gat."40Sai Shimai ya tashi, ya sa sirdi a kan jakinsa, ya je wurin Akish a Gat neman bayinsa. Ya dawo da bayinsa daga Gat.41Sa'ad da a ka gaya wa Suleman, cewa Shimai ya fita daga Yerusalem ya je Gat ya dawo,42sarki ya aika a ka kira Shimai ya ce da shi, "Ba na sa ka yi rantsuwa da Yahweh ba na shaida maka, cewa, 'Ka sani duk randa ka bar nan ka je wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba.'? Ka ce mani, 'abin da ka faɗi ya yi kyau.'43To meyasa ba ka cika alƙawarinka ga Yahweh ba, da abin da na umurce ka?"44Sa'an nan sarki ya cewa Shimai, "Ka sani cikin zuciyarka dukkan muguntar da ka yi wa mahaifina Dauda. To Yahweh zai sa muguntarka ta koma kanka.45Amma sarki Suleman zai zama mai albarka, kursiyin Dauda kuma zai tabbata a gaban Yahweh har abada."46Sa'an nan sarki ya ummurci Benayiya ɗan Yehoiada. Ya fita waje ya kashe Shimai. Haka mulkin ya tabbata a hannun Suleman.
wannan wata hanya ce ta cewa "zan mutu."
sauran zantuttuka za'a cika su a. AT: "ka nuna wa kowa kai namiji ne" ko kuma "ka zo yadda kowa da kowa zai san cewa kai mutumin kirki ne"
tafiya cikin akan hanya shine yake nuna yadda mutun yake rayuwarsa. AT: "ka yi rayuwa yadda ya umurceka"
"yi nasara" ko kuma "yi da kyau"
"yin dukkan abinda ya yi alkawari zai yi"
Yahweh yana magana da Dauda, kuma kalmomin "kai" da kuma "na ka" yana nufin Dauda.
Yahweh yana magana da Dauda, kuma kalman "Ni" na nufin Yahweh.
habicin "da dukkan ... zuciyarsu" yana nufin "dukka-dukka" da kuma "da dukkan ... ransu" yana nufin "a dukkan ... inda suka kasance." AT: "a dukkan inda suka kasance" ko kuma "da dukkan ƙarfinsu"
kalman "kursiyi" laƙabi ne ga sarki wanda ya zauna a kursiyi. AT: "zuriyarka ba za su daina zama sarakuna a Isra'ila ba" za'a iya bayyana shi da armashi. AT: "wani daga cikin zuriyarka zai zama sarki."
sarki Dauda ya ci gaba da gaya wa Sulaiman yadda zai yi jagorancin Isra'iala.
Dauda na nufin abu ɗaya har sau biyu. AT: "abin da Yowab ... ya yi ma ni - shi ne, abin da ya yi"
wata ma'ana 1) "ka kashe mutanen nan lokacin salama kamar kana kashe su a yaƙi" ko kuma "ka ɗauki fansa akan mutanen nan a lokacin salama domin sun kashe mutane a yaƙi"
wata ma'ana 1) Yowab yana kusa da mutanen nan lokacin da ya kashe su har jinisu ya fallatsa a jikin ɗanmararsa da kuma a jikin takalmansa ko kuma 2) kalmar "jini" na wakiltar wanda ake zargi da aikin kisa, da kuma ɗammararsa da takalmansa su na wakiltar ƙarfin ikon Yowab a matsayin shugaban yaƙi, Dauda na cewa haka saboda Yowab na da laifin kisan kai, bai can-canta ya zama shugaban yaƙi da. saboda haka yana da kyau a fassara shi zahiri.
"ku tabbata Yowab ya mutu mutuwar dole kafin ya tsufa."
Sarki Dauda ya ci gaba da gaya wa Sulaiman yadda zai yi jagorancin Isra'ila
sunan na miji
Teburi wakilin ne na gidan da teburi yake. AT:"ka marabcesu su ci a gidanka"
Sarki Dauda ya ci gaba da gaya wa Sulaiman yadda zai yi jagorancin Isra'ila.
sunan mazaje
Zuriyar Benyami
sunayen wurare
za'a iya bayyana amarshin. AT: "ka tabbata ka hukunta shi"
Jini wakilin ne na mutuwar tashin hankali, da kuma kai wakili ne na da dukkan mutum. AT:"ka tabbata ya mutu mutuwar tashin hankaki"
Dauda ya mutu kuma Sulaiman ya gaje shi a matsayin sarkin Isra'ila.
Mutuwar Dauda anan ana maganarsa kamar ya kwanta barci. AT: "mutu"
Za'a iya bayyana wannan a armashi. AT: "Dauda ... aka kuma bizne shi"
"shekarun da Dauda ya yi mulki a Isra'ila" ko kuma "Dauda ya yi mulki a Isra;ila na"
kursiyin na wakiltar ikon mulki sarki. AT: "ya zama sarki, kamar yadda mahaifinsa Dauda yake"
Wannan za'a iya fassara shi a armashin. AT: "Yahweh ya kafa mulkin Sulaiman" ko kuma "Yahweh yasa Sulaiman ya shugabanci gaba ɗaya na mulkin"
Adonija ya zo yayi magana da Batsheba.
" ba tare da shirin kawa hargitsi ko tada fitina"
wannan gaba ɗaya ne.
"abin da muke sa zuciya faru bai faru ba"
wannan za'a iya fassara shi a armashi. AT: "Yahweh ya ba ɗan'uwana mulkin" ko kuma "ɗan'uwana ya zama sarki"
Adonija tattauna bukatunsa da Batsheba.
juya wa fuskar wani wakili ne na ƙin duban wani, wanda in an bi ta wata hanya shine ƙin yin abin da wannan mutum ya roƙa. AT: "ba za ka ƙi kayi abin da na roƙa ba ,,, ba zan ƙi yin abin da kika roƙa ba"
(Duba: 1:3)
Batsheba taje wurin sarki da roƙon Adonija.
"sarki ya miƙe tsaye" daga inda yake zaune a kan kursiyinsa.
wannan za'a iya fassara shi d armashi. AT:"gayawa wani ya kawo kursiyi"
Batsheba
juya wa wani bay wakili ne na ƙin duban wani, wanda in an bi ta wata hanya wakiline na ƙin yin abin da wannan mutum ya roƙa. AT: "ba za ka ƙi abin da na roƙa ba ... ba zan ƙi yin abin da kika roƙa ba" Irin wannan kalmar ana samunta a 2:16.
wannan za a fassara a. AT: "Ka bar Adonija ... ya auri Abisha Bashunamiya" ko kuma "ka ba Adonija Abisha bashunamiya ... a matsayin matarsa"
Sarki Sulaiman ya bayar da amsa ga roƙon Adonija
Sarki Sulaiman ya ji haushin roƙon mahaifiyarsa. AT: "bai yi dai_dai ba ki tambamya ... Adonija! wannan ɗaya ne da tambayar masa mulkin kuma ... Zeruya!"
wannan habaici ne. AT: "Allah na da gaskiya ya kashe ni-har ma ya yi min abin da ya fi haka muni-idan ban kashe Adonija ba domin ya yi wannan roƙo"
Sarki Sulaiman ya kashe Adonija.
kalmar "kursiyi"na nufin ikon Sulaiman don jagoranci da aka bashi daga Yahweh,
Anan "gida" na nufin zuriyar da Yahweh ya ba Sulaiman, wanda zai ci gaba da mulki bayan shi.
Sulaiman ya sallami Abiyatar daga zama firist.
Abiyatar ya sha wahala tare da Sarki Dauda kafin Dauda ya zama sarki.
Kalmar "shi" na nufin Sarki Sulaiman.
Kalmar "Shi" na nufin Yahweh.
Sarki Sulaiman ya umarci Benaiya ya kashe Yowab
"Yowab ya ji abin da Sulaiman ya yi bayan ya zama sarki"
ƙahonni na bagadi na nuna ikon Yahweh da kariyarsa.
za a fassara wannan a. AT:"wani ya gaya wa sarki Sulaiman da cewa Yowab ya gudu"
Benaiyaya je ya kashe Yowab
Anan "gida" na wakiltyar zuriyar Dauda shi kuma "jini" na wakiltar laifi. AT: "bizne shi ka kuma cire min da iyalina laifin kisan da Yowab ya yi ba dalili" ko kuma "bizne shi. ka yi haka domin kada Yahweh ba zai ɗuki fansa a kaina da iyalin mahaifina masu laifi domin Yowab ya kashe mutane ba dalili"
Sarki Sulaiman ya yi bayanin dalilin da ya sa Yowab zai mutu
Kalmar "shi" na nufin Yowab. "jini" na wakiltar kisa. da kuma, habaicin "jini ya koma kan" na nufin mutumin ya cancanci a ganshi a matsayin mai kisan kai. AT: "Yowab ya kashe mutane, kuma ina son Yahweh ya ɗauki fansa akan abin da ya yi"
Wadannan kalmomi na nufin abu ɗaya ne suna nanatawa cewa Abnar da Amasa sun fi Yowab tsarki.
Kalmar "jini" wakilin ne na kisan kai. da kuma, habaici "jini ya koma kansa" yana nufin mutumin a ɗauke shi mai kisan kai. AT: "ina son Yahweh ya ya ɗauki Yowab da zuriyarsa masu laifin kisan kai"
Kalmar "gida" da "kursiyi" wakilai ne na iyali da mulki. AT: "ga zuriyar Dauda da kuma mulkinsa"
Benaiya ya kashe Yowab yã kuma zama shugaba na sojojin Sulaiman.
wannan za a iya cewa. AT: "suka bizne Yowab a gidansa"
Gidan wakili ne na ƙasa wadda ginin ke bisa. 'ya'yan Isra'ilawa suna bizne mutune a cikin kabari. AT: "in da iyalin sa suke zama"
Sarki Sulaiman ya ce wa Shemai ya tsaya a Yerusalem ko kuwa Shemai zai mutu.
Anan "jini" wakili ne na laifi da kuma kai wakili ne na mutun gaba ɗaya. AT: "zaka a ɗauki hukunci mutuwarka a kanka"
Shemai ya bar Yerusalem.
sunan mazaje
Birnin Filistiyawa
Wannan habaici ne. "Shemai da sauri"
Sarki Sulaiman ya hukunta Shemai don barin Yerusalem.
za a iya cewa. AT: "wani ya gaya wa Sulaiman"
Sulaiman ya na tunashe da Shemai akan abinda Shemai ya yi alkawari. AT: "ka sani sosai na sa ka rantse ... cewa, 'sani ... mutu'!"
Sarki Sulaiman ya furta hukunci akan Shemai don barin Yerusalem.
ko kuma 1) Sulaiman yana tambayan amsa ko 2) AT: "kayi kuskure da ka karya alkawarinka ... kai."
Anan kai na wakiltar mutumin, da kuma muguntar an faɗe shi kamar abu mai ƙarfi ko kuma mai ruwa-ruwa da za a iya sa wa wani a kai. AT: "za a ɗauki hukunci mutuwarka akanka"
Sarki Sulaiman ya ba da umarni a kashe Shemai.
Anan "kursiyin Dauda" na nufin iko da ayyukan Duada da kuma dukkan zuriyarsa har abada.
amfani da "hannu" na wakiltar ikon Sulaiman da kuma ƙarfin sa.
1Suleman ya yi yarjejeniya da Fir'auna sarkin Masar ta dalilin aure. Ya ɗauko ɗiyar Fir'auna ya kawo ta cikin birnin Dauda har sai lokacin da ya gama ginin gidansa da gidan Yahweh da ganuwar da ta kewaye Yerusalem.2Mutane suna ta miƙa hadayu a wurare masu bisa, saboda ba a gina gida saboda sunan Yahweh ba tukuna.3Suleman ya nuna ƙauna ga Yahweh ta wurin tafiya cikin tafarkun mahaifinsa Dauda, sai dai shi ma ya miƙa hadaya kuma ya ƙona turare a wurare masu bisa.4Sarki ya je Gibiyon domin ya miƙa hadaya a can, domin can akwai wurare masu bisa sosai. Suleman ya miƙa hadayu dubu a kan bagadi.5Yahweh ya bayyana ga Suleman a cikin mafarki a Gibiyon, ya ce, "Ka roƙa! Mene ne zan ba ka?"6Sai Suleman yace, "Ka nuna girman alƙawarinka da jinƙai da aminci ga bawanka, mahaifina Dauda, saboda ya yi tafiya a gabanka cikin aminci da tsarki da gaskiya cikin zuciyarsa. Ka riƙe wannan alƙawarin da aminci da ka ba shi ɗa wanda zai zauna a kan kursiyinsa yau.7Yanzu fa, ya Yahweh Allahna, ka sa bawanka ya zama sarki a maimakon mahaifina Dauda, ko da ya ke ni ɗan yaro ne. Ban san yadda zan fita ko in shiga ba.8Bawanka yana cikin tsakiyar mutane waɗanda ka zaɓa, mutane masu yawa da sun fi gaban a lisafta ko a ƙidaya su.9Ka ba bawanka zuciya mai fahimta domin ya hukunta mutanenka, domin in gane bambanci tsakanin abu mai kyau da mummuna. Gama wane ne zai iya hukunta wannan jama'a taka mai yawa haka?"10Wannan roƙo na Suleman ya gamshi Ubangiji.11Sai Allah ya ce da shi, "Saboda ka roƙi wannan, ba ka roƙi tsawon rai ba, ko dukiya ko ran maƙiyanka ba, Amma ka roƙi fahimta domin ka gane gaskiya,12duba zan yi maka dukkan abin da ka roƙa a gare ni. Na ba ka zuciya mai hikima da ganewa, ba a yi wani mai hikima kamar ka a dã ba, ba kuma za a sami wani mai hikima kamar ka ba a nan gaba bayanka.13Kuma na ba ka har ma abin da ba ka roƙa ba, dukiya da martaba, yadda ba za a sami wani kamar ka ba a cikin sarakuna dukkan kwanakin ranka.14Idan ka yi tafiya cikin hanyoyina da farillaina da dokokina kamar yadda Dauda mahaifinka ya yi tafiya, zan haskaka kwanakinka."15Sai Suleman ya farka, ashe mafarki ya yi. Ya zo Yerusalem ya tsaya a gaban akwatin alƙawarin Ubangiji. Ya miƙa hadayu na ƙonawa da na salama kuma ya yi liyafa domin dukkan bayinsa.16Sai ga waɗansu mata biyu karuwai suka zo gabansa suka tsaya.17Sai ɗaya matar ta ce, "Ya shugabana, ni da wannan matar muna zama a gida ɗaya, ni da ita muka haihu a gidan.18Bayan na haihu da kwana uku, wannan matar kuma sai ta haihu. muna tare. Ba kowa tare da mu sai mu biyu a gidan.19Sai ɗan wannan matar ya mutu cikin dare saboda ta kwanta a kansa.20Sai ta tashi cikin tsakiyar dare ta ɗauke ɗana daga kusa da ni, domin baiwarka ta yi barci, ta kwantar da shi a ƙirjinta, sai ta kwantar da nata mataccen ɗan a ƙirjina.21Sa'ad da na tashi da safe domin in shayar da ɗana sai na ga ya mutu. Amma da na dube shi da kyau da safe, sai na ga ba ɗana ba ne wanda na haifa."22Sa'an nan sai ɗaya matar ta ce, "Ba haka ba ne, ɗan mai rai nawa ne ke kuma mataccen ne naki." Sai ɗaya matar ta ce, "A'a mataccen ne naki mai ran kuma shi ne ɗana." Haka suka yi ta magana a gaban sarki.23Daga nan sarki yace, "Ke kin ce, "Wannan ɗana ne mai ran, kuma naki ne mataccen,' ɗayar kuma ta ce, 'A'a, ɗanki shi ne mataccen, ɗana kuma shi ne mai ran."'24Sai sarki yace, "Ku kawo mani takobi." Sai aka kawo wa sarki takobi.25Daga nan sarki ya ce, "Ku raba ɗan mai rai kashi biyu, ku ba wannan mata rabi, rabi kuma ga ɗayar."26Sai ɗaya matar wadda ɗanta ne ya ke da rai, ta yi magana ta ce da sarki, gama zuciyarta ta cika da tausayi saboda ɗanta, ta ce, "Aiya, shugabana, a ba ta ɗan mai rai kada a kashe shi." Amma ɗaya matar ta ce, "Ba zai zama naki ko nawa ba. A raba shi."27Sai sarki ya yi magana ya ce, "Ku ba da ɗan mai rai ga matar ta farko, kada ku kashe shi, ita ce mahaifiyarsa."28Sa'ad da dukkan Isra'ila suka ji wannan hukunci, suka ji tsoron sarki, saboda sun ga hikimar Yahweh na tare da shi domin yanke hukunci.
Sulaiman ya auri masar.
Sulaiman ya zama surukin Fir'auna sarkin masar kuma sarakan biyu su aiki tare su kuma yaƙi abokan gãbansu.
ta na nan har yanzu a birnin Dauda bayan ya gama gini.
"majami'a"
za iya cewa. AT: "ba wani wanda ya gina gida"
Kalmar "suna" wakili ne na mutum, da kuma "saboda suna" na nufin yin sujada ga wani. AT: "yadda mutane za su yi wa Yahweh sujada"
yadda wani ya yi rayuwa ana misalta shi da tafiya cikin tafarki. AT: "biyayya da umarnin da mahaifinsa Dauda ya bar masa"
Allah ya tambayi Sulaiman abin da zai yi wa Sulaiman.
"wurin keɓaɓɓe domin mika hadayu" ko kuma "bagadi mafi mahimmanci"
"ka tambayeni dukkan abin da ka ke so ni kuma zan baka." ko kuma "menen ka ke so? ka tambaya ni kuma zan baka."
Sulaiman ya amsawa Allah tambayarsa.
"kana da aminci ga alkawarinka"
tafiya kwatancine na yadda wani yayi rayuwa. Wakilin suna "aminci," "tsarki," da kuma "gaskiya" za a fassara a matsayin mai kara armashi. AT: "saboda da yana da aminci da tsarki, da shi mai gaskiya ne"
mutum mai adalci ake magana da cewa mai gaskiya cikin zucuyarsa. AT: "kuma shi mai adalci ne" ko kuma "ya faɗi gaskiya kuma ya yi abin da ke dai_dai"
"ɗan" Sulaiman ne.
"ya yi mulki a madadinsa"
"yanzu." Sulaiman na magana ba ga rana ɗaya ba, amma ga dukkan shekarun da ya yi yana mulkin.
Sulaiman ya tambayi hikima.
Sulaiman ya yi magana kamar shi wani mutum ne dabam don girmama Yahweh. AT: "ni"
Sulaiman na cewa shi kamar yaro ne wanda bai kai mahaifinsa sani ba.
wannan kwatanci ne na rashin sanin komai akan abin da ya kamata yayi. AT: "ban san yadda yakamata na yi abu ba" ko ku a "ban san yadda zan zama sarkin ba"
Sulaiman ya yi tambaya ya buga ƙusa cewa ya san cewa ba wanda zai iya jagoranci. AT: "wanene zai iya hukunta wannan jama'a taka mai yawa haka."
Allah ya ba Sulaiman hikima da sauransu.
"rai" wakili ne na ikon kashewa. AT: "ikon kashe maƙiyanka"
"zan yi abin da ka roƙe ni in yi in ka yi mani magana"
zuciya wakili ne na abin da mutum ya yi tunani ya kuma sa ran samu. AT: "na maisheka ka zama mai hikima da gane abubuwa masu yawa"
rayuwar wani a na kwatanta shi da tafiya cikin tafarki mai kyau. AT: "yi rayuwa yadda nake son ka kayi ka kuma kiyaye" (Duba:metaphor)
"kwanaki" na nufin rayuwar Sulaiman. AT: "zan sa ka kayi tsawon rai"
Kalmar "duba" na nuna Sulaiman ya ga wani abu mai ƙayatarwa
karuwai biyu suka tambayi Sulaiman ya yi masu hukunci.
karuwi biyun suka ba Sulaiman labari.
yana da mahimmanci a ce hakan yasa yaron ya mutu. AT: "ta yi kuskuren murginawa a kan yaron ta har ya mutu"
matar ta yi magana kamar ba akanta take magana ba don girmama sarki. AT: "ni" (Duba: pronouns)
karuwan biyu suka ci gaba da gaya wa Sulaiman labarinsu.
Haka yana nufin ta ba ma yaronta madara daga nononta
"gaban Sulaiman" ku kuma "inda Sulaiman zai iya ji da ganin su"
Sulaiman ya yanke wa mata biyun hukunci.
Asalin mahaifiyar ta roƙi sarki kada a kashe shi.
Zuciyar ana kwatanta ta da ma'auni kuma tawali'u kamar wani abu mai ƙarfi. AT: "tana ƙaunar yaronta"
Dukkan Isra'ila na nufin gaba ɗaya.
1Suleman shi ne sarki a bisa dukkan Isra'ila.2Waɗannan su ne jami'ansa: Azariya ɗan Zadok shi ne firist.3Elihoref da Ahija 'ya'yan Shisha su ne magatakarda, Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubuci.4Benayiya ɗan Yehoiada shi ne shugaban sojoji. Zadok da Abiyata su ne firistoci.5Azariya ɗan Natan shi ne shugaban ma'aikata. Zabud ɗan Natan shi ma firist ne kuma abokin sarki.6Ahisha shi ne sarkin gida. Adoniram ɗan Abda shi ne shugaban masu aikin ƙarfi.7Suleman ya na da jami'ai goma sha biyu a dukkan Isra'ila waɗanda su ke tanada abinci domin sarki da mutanen gidansa. Kowanne mutum zai kawo abincin wata ɗaya a shekara.8Ga sunayensu: Ben Hur shi ne mai kula da tudun Ifraim;9Ben Deker shi ne a Makaz da Sha'albim da Bet Shemesh da Elon Bet Hanan;10Ben-Hesed a Arubbot (shi a ka damƙawa Sokoh da dukkan ƙasar Hefa);11Ben Abinadab shi ne cikin dukkan Nafot Dor (Tafat ɗiyar Suleman ita ce matarsa);12Ba'ana ɗan Ahilud ya na cikin Ta'anak da Megiddo da dukkan Bet Shan, wato kusa da Zaretan gangaren Yeziriyel, daga Bet Shan zuwa Abel Meholah har zuwa ɗaya gefen na Yokmiyam;13Ben Geber cikin Ramot Giliyad (shi aka danƙawa garuruwan Ja'ir ɗan Manasse waɗanda ke cikin Giliyad yankin Argob na wanda ke cikin Bashan ma nasa ne, manyan birane sittin masu ƙofofin jan ƙarfe);14Abinadab ɗan Iddo cikin Mahaniyam;15Ahima'az cikin Naftali (kuma ya auri Basemat ɗiyar Suleman ta zama matarsa);16Ba'ana ɗan Hushai cikin Asha da Bi'alot;17Yehoshafat ɗan Faruya cikin Issaka;18Shimei ɗan Ela, cikin Benyamin;19da Geber ɗan Uri cikin ƙasar Giliyad, da ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa da Og sarki Bashan, kuma shi ne kaɗai jami'in da ke cikin ƙasar.20Yawan Yahuda da Isra'ila yana kama da yashin teku. Su na ci suna sha suna jin daɗi.21Suleman ya yi mulki kan dukkan mulkoki tun daga Kogi har zuwa ƙasar Filistiyawa da iyakar Masar. Suna bautawa Suleman suna kawo masa gaisuwa dukkan kwanakinsa.22Abincin gidan Suleman na rana ɗaya shi ne bahu talatin na niƙaƙƙen gari da kuma tsaba bahu sittin,23da bijimai masu ƙiba guda goma da shanu guda ashirin daga makiyaya, da tumaki ɗari, banda barewa da gadã da namijin barewai, da kaji masu mai.24Gama shi ne ya ke mulkin dukkan yankin da ke hayin Kogi, tun daga Tifsa har zuwa Gaza, a bisa dukkan sarakunan da ke hayin Kogi, kuma yana da salama a kowanne gefe.25Yahuda da Isra'ila sun sami tsaro har kowanne mutum yana zuwa gonarsa ta inabi da ta ɓaure, tun daga Dan zuwa Biyasheba a dukkan kwanakin Suleman.26Suleman yana da ɗakunan dawakai dubu arba'in domin karusansa, da masu hawan dawakai mutum dubu goma sha biyu.27Waɗannan jami'ai suna tanado abinci domin sarki Suleman da dukkan wanda ya zo ya ci a teburin sarki, kowanne mutum da watansa, ba su bari an rasa komai ba.28Kuma suna kawo hatsi da ciyawa saboda dawakan da suke jan karusai, kowanne mutum bisa ga iyawarsa.29Allah ya ba Suleman ƙasaitacciyar hikima da fahimta, faɗin ganewarsa yana kama da yashin da ke bakin teku.30Hikimar Suleman ta fi ta dukkan mutanen gabas da dukkan hikimar Masar.31Hikimarsa ta fi ta dukkan mutane - ya fi Etan Ba-ezrahi hikima harma da Heman da Kalkol da Darda 'ya'yan Mahol - ya zama sananne a dukkan al'umman da ke kewaye.32Ya faɗi misalai dubu uku, ya yi waƙoƙi dubu da biyar.33Ya yi bayani a kan tsire-tsire da itacen sidar da ke Lebanon har zuwa waɗanda suke fitowa a jikin bangon ɗaki. Ya yi bayani a kan namun daji da tsuntsaye da kifaye.34Mutane sukan zo daga wurare daban-daban domin su ji hikimar Suleman. Sukan zo daga wurin dukkan sarakunan da suka ji hikimar Suleman.
Wannan shine farkon jerin jami'an Sulaiman.
sunan mazaje
jerin sunayen jami'an Sulaiman ya ci gaba.
sunayen mazaje
za a iya cew AT: "mazajen da Sulaiman ya matsa wa su yi masa aiki"
ci gaba da jerin jami'an Sulaiman:
wadannan sunayen mazaje ne ku kula idan kaga "Ben" kafin suna yana nufin "yaron" to "Ben Hur" yana nufin "yaron Hur."
"shi aka damƙawa birnin tudu ... shi aka damƙawa Makaz ...shi ak damKawa Arubbot"
wannan sunan wurare ne.
Jerin sunayen jami'an Sulaiman ya ci gaba, da kuma jeren wuraren da aka sa su aiki ya ci gaba.
sunan mazaje
"shi aka damƙawa dukkan gundumar Dor ... shi aka damƙawa Ta'anac ... shi aka damƙawa Ramot Giliyad ... shi aka damƙawa Mahaniyam"
sunan macem ne (Duba: translate _names)
sunan wurare
Jeren sunayen jami'an Sulaiman ya ci gaba da wuraren da suke aiki
sunan mazaje
"wanda aka damƙawa Naftali ... wanda aka damƙawa Asha ... wanda aka damƙawa Issaka"
sunan mace
sunayen yare na 'yan'yan Isra'ila
sunan wani ɓangare na wata ƙasa
jeren sunayen jami'an Suaiman ya ci gaba da wurin da aka damƙa masu.
sunan mazaje
ƙasar gãdoaka bata suna na wani daga cikin 'ya'yan Isra'ila
sunan wani ɓangaren ƙasa
"ƙasar da tun shekarun farko take ta Sihon"
sunan ƙungiyar mutane
Anan "ƙasar" na nufin ƙasar Yahuza; jami'ai da suka wuce sun zauna a wurare da yawa na Isra'ila.
mai magana yayi amfani da kwatanci ya ce akwai mutane da yawa da ba za a iya ƙidayawa dukka ba. kalmar "Yahuza" da kuma "Isra'ila" wakili ne na mutanen da suke a Isra'ila. AT: "akwai mutane da yawa a Isra'ila da Yahuza kamar yadda yashi yake a bakin teku" ko kuma "akwai mutane da yawa a Isra'ila da Yahuza fiye da yadda mutum zai iya ƙirgawa"
"kogin ifiritus" (UDB)
buhu gwaji ne na bushesshen abu da aka sashi a cikin musamman a cikin leda sai a dinke.
dabbobi masu ƙafa huɗu da suke gudu sosai
barewa wanda yafi guda ɗaya (barewai)
"tsuntsaye wadanda mutane suka kiwata domin suyi kiba"
sunan wani ɓangare na ƙasa
kalmar "Yahuza" da kuma "Isra'ila" wakilai ne na mutanen Yahuza da Isra'ila.
"kowanne iyali su na da lambu da itacen inabi dana ɓaure," Wannan ya nuna mutanen na rayuwa cikin salama da kwanciyar hankali, tunda ba yaƙi ko wahala wajen shuka itatuwa kuma suiyi girma.
wannan na wakiltar dukkan ƙasar Isra'ila daga Dan a kudu da arewa.
"ya zo ya ci da Sarki Sulaiman" ko kuma "wanda Sarki Sulaiman ya gayyata ya zo ya ci tare da shi"
Sulaiman yasa kowanne daga cikin jami'ai goma sha biyun nan kamar yadda yake a 4:7 su kawo masa abinci watanni da dabam-dabam.
wannan za a iya ce wa. AT: "sun tanadar da dukkan abin da Sulaiman yake buƙata"
Allah ya ba Sulaiman hikima da sanin da kuma fahimtar abubuwa da yawa kamar Allah na ba Sulaiman wani abu na hannu da za a iya gani. wakilin suna "hikima" da "fahimta" za a iya dassara shi a matsayin aiki. AT: "Allah ya sa Sulaiman ya fahimci abubuwa da kuma hikima"
Sulaiman ya na fahimtar abubuwa da yawa. Wakilin suna "faɗin"za a iya cewa ita mai ƙara armashi ce. AT: "Sulaiman ya iya fahimtar faɖin abubuwa da yawa"
"Sulaiman yana da hikima fiye da dukkan masu hikima na duniya"
wannan na nufin mutane dake a gabashin Isra'ila irinsu Arabia da Mesopotamiya
sunayen mazaje
Wadannan kalmomi sun haɗa merism da ya hada dukkan itatuwa. AT: "itacen sidar ... Ɗoɗɗoyan jeji" ko kuma "babban itacen ... ƙaramin itacen jeji"
1Hiram sarkin Taya ya aiki barorinsa wurin Suleman saboda ya ji an naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa; gama Hiram mai ƙaunar Dauda ne.2Suleman ya aika da magana zuwa ga Hiram, cewa,3"Ka sani mahaifina Dauda bai iya gina gida domin Yahweh Allansa ba, saboda yaƙe-yaƙen da suka kewaye shi, gama a lokacinsa Yahweh na ta sa abokan gabarsa a ƙarƙashin tafin sawunsa.4Amma yanzu, Yahweh ya ba ni hutawa a kowanne gefe. Ba abokin gãba kuma babu annoba.5To yanzu na yi niyya in gina haikali domin sunan Yahweh Allahna, kamar yadda Yahweh ya yi magana da mahaifina Dauda cewa, 'Ɗanka wanda zan sa a kan kursiyin mulki ya gaje ka, shi ne zai gina haikali domin sunana.'6To yanzu sai ka ba da umurni a saro mani itacen sida daga Lebanon. Bayina za su haɗu da bayinka, kuma zan biya bayinka dai-dai bisa ga abin da ka yarda da shi. Domin ka san a cikin mu ba wanda ya iya yankan katako kamar Sidoniyawa."7Lokacin da Hiram ya ji maganar Suleman, ya yi murna ƙwarai da gaske, ya ce, "Bari albarka ta kasance ga Yahweh yau, saboda ya ba Dauda ɗa mai hikima a kan jama'arsa mai girma."8Hiram ya aika da magana zuwa ga Suleman, cewa, "Na ji saƙon da ka aiko wurina. Zan ba ka dukkan katakon sida da na fir yadda ka ke bukata.9Bayina za su kawo itatuwan daga Lebanon zuwa teku, zan sa a ɗaɗɗaure su yadda za a iya sawo su a teku yadda ka ke so in yi, zan sa a yayyanka su domin ka ɗauko. Zan so ka bada abinci domin iyalin gidana.10Haka Hiram ya ba Suleman dukkan katakon sida da fir yadda ya bukata.11Suleman ya ba Hiram bahu dubu ashirin na alkama da mai wanda a ka tace garwa ashirin domin abincin gidansa, haka Suleman ya ba Hiram shekara biye da shekara.12Yahweh ya ba Suleman hikima, kamar yadda ya yi alƙawari. Salama ta kasance tsakanin Suleman da Hiram, suka ƙulla amana.13Sarki Suleman ya sa wa Isra'ilawa aikin dole. Mutanen da a ka sa aikin dolen sun kai dubu talatin.14Ya aika su Lebanon, mutum dubu goma an sa kowanne wata, wata ɗaya suna Lebanon, wata biyu kuma su na gida. Adoniram ya shugabanci waɗanda a ka sa su yi aikin dole ɗin.15Suleman yana da mutum dubu saba'in masu ɗaukar kaya, dubu takwas da kuma masu saro dutse cikin tsaunuka,16ban da haka Suleman yana da mutum 3,300 jami'ai ne na ma'aikata kuma masu duba ma'aikata.17Bisa ga ummurnin sarki, suka sassaƙo manyan duwatsu masu ƙwari domin a kafa tushen haikali.18Haka masu gini na wajan Suleman da na wajan Hiram da Gebalawa suka saro katakan suka shirya su tare da duwatsun domin ginin haikali.
Sulaiman yayi magana da Sarkin Hiram game gina haikali
"Hiram shi amini ne na ƙwarai da Dauda" (UDB)
A sa abokan gaba a ƙarƙashin ƙafa na nufin a ci su da yaƙi. AT: "Yahweh na taimakon Dauda ya ci abokan gabansa da yaƙi" ko kuma "Dauda na ta aiki tunda Yahweh na bashi nasara bisa abokan gãbansa"
Kalmar "suna" wakili ne na mutum, da kuma "domin suna" yin sujada ga wani. an fassara shi a 3:1. AT: "yadda mutane suke yi wa Yahweh sujada"
wata ma'ana anan shi ne "saboda yaƙe_yaƙen da magabtansa suka kewaye shi da shi" ko kuma "yana yaƙar abokan gaba ta kowacce hanya"
wannankakashin ƙafa wakili ne na jagoranci a akan mutum gaba ɗaya. AT: "Yahweh na taimakon Dauda ya ci nasara akan magabtansa gaba ɗaya"
Sulaiman ya ci gaba da yi wa sarki Hiram magana game da ginin haikalin
Kafin Sulaiman ya zama sarki, Sarki Dauda da mutanen Isra'ila su na ta faman yaƙi, amma yanzu Sarki Sulaiman da mutanen suna hutu a kuma cikin lokacin salama.
babu mutane masu sa wata cuta ko wata halitta mai kawa cuta. wannan za a iya faɖin shi. AT: "mun kuɓuta daga abokan gãban mu daga kuma halitta mai sa annoba"
magabta
taron da ke harfar da wata cuta ga mutane da dukiyarsu
wannan domin a jaddada kalmar da ta biyo. "ka saurara wannan shine abin da nake so nayi:" ko kuma "saboda abinda Yahweh ya yi mani, wannan ne abin da zan yi"
Kalmar "suna" wakili ne na mutum. AT: "in da Yahweh Allahna zai zauna ... in da zan zauna"
Ana "kursiyi" na nufin mulki a matsayin sarki. AT: "zan sa ya zama sarki ya gaje ka"
Sulaiman ya ci gaba da magana da sarki Hiram game da ginin haikali.
"ma'aikatanka sun fi nawa iya yanka katako"
"mutanen Sidon"
Sarki Hiram ya amsa wa Sulaiman.
"abin da Sulaiman ya ce"
wannan za ba shi armashi a ce. AT: "Na yabi Yahweh yau"
Sida wani irin itace ne mai mutuƙar mahimmanci da ake amfani da shi ayi ginin haikali.
Sarki Hiram ya ci gaba da yin magana da Sulaiman.
"ka ɗaure su a tare yadda zasu yi ninƙaya tare "
za a iya ce wa AT: "ma'aikatana sun kunce su daga zama wuri ɗaya"
"za ka iya yin abinda nake so" ko kuma "za ka biya ni"
Kalmar "fir" na nufin itatuwa da yawa, har ma da itacen sid
wannan busheshen ma'auni ne inda ma'aunin mai kuma mai lema ne. bai kai yadda ake so a gwada ba. UDBya ɗauki baƙo mai ilimi.
"dukkan shekara"
Sulaiman ya matsawa mutane su gina haikali.
"matsawa mutane a dukkan ƙasar Isra'ila su yi aiki"
yana nufin, akwai ƙungiyoyi guda uku da suke karɓe_karɓe wata ɗaya suna labanon wata biyu a gida.
kowacce ƙungiya ta ma'aikatan na yin wata ɗaya a lebanon wurin aiki wata biyu kuma a gida tare da Isra'ilawa.
za a iya cewa. AT: "mutanen da Sulaiman ya ke matsawa su yi masa aiki" (Duba: activepassive)
Sulaiman ya ci gaba da matsawa mutane su gina haikali.
"abu mai nauyi akan wani da ba zai iya cirewa ba"
"mutane da suke shiga cikin tsaunuka su sare dutse"
Sulaiman ya ci gaba da matsa wa mutane su gina haikali.
"sassaƙa babba, duwatsu masu kyau daga cikin tsauni a kuma yanka su su yi kyau"
Mutane daga birnin Gebal
1Suleman ya fara gina haikalin Yahweh. Hakan ya faru a shekara ta 480 bayan dawowar 'ya'yan Isra'la daga Masar, a cikin shekara ta huɗu ta mulkin Suleman a bisa Isra'ila cikin watan Zif wato wata na biyu.2Haikalin da Sarki Suleman ya gina wa Yahweh, ratarsa kamu sittin ne, faɗinsa kamu ashirin ne, tsawonsa kuma kamu talatin ne.3Ratar shirayin da ke ƙofar haikalin kamu ashirin ne, dai-dai suke da faɗin haikalin, a gaban haikalin kuma ta kai kamu goma.4Ya yi wa gidan tagogi waɗanda faɗinsu daga ciki ya fi daga waje.5Ya gina ɗakuna kewaye da ɗakin taro, ɗakuna sun kewaye ɗakuna na ciki da na waje. Ya gina ɗakuna a kowanne gefe.6Bene na can ƙasa kamu biyar ne faɗinsa, na tsakiya kuma kamu shida ne a faɗi, na uku kuma kamu bakwai ne faɗinsa. Domin a kewaye da bangon gidan ya yi matokarai a bangon gidan a kowanne gefe domin kada a kafa wani abu a bangon gidan.7An gina gidan da sassaƙaƙƙun duwatsun da a ka shiryo a mahaƙar duwatsu. Sa'adda a ke ginin gidan ba a ji ƙarar gatari ko guduma ba.8A fuskar kudu ta haikalin an yi wurin shigowa daga ƙasa, a ka yi matakalu suka yi sama zuwa tsakiya, suka tafi har zuwa hawa na uku.9Haka Suleman ya gina haikalin ya gama shi; ya rufe gidan da matokarai da katakai na sida.10Ya yi ɗakuna a jikin ɗakunan taro na haikali, kowanne tsawonsa kamu biyar ne; a ka jingina su jikin gidan da katakai na sida.11Sai maganar Yahweh ta zo ga Suleman, cewa,12"Game da gidan da ka ke ginawa, idan ka kiyaye farillaina ka yi adalci, ka kiyaye dokokina ka yi tafiya a cikin su, sa'an nan zan tabbatar maka da alƙawarin da na yi wa Dauda mahaifinka.13Zan zauna cikin mutanen Isra'ila, ba zan yashe su ba."14Haka Suleman ya gina gidan ya gama shi.15Sa'an nan ya gina bangaye na ciki da falankai na sida. Ya rufe gidan da katakai tun daga ƙasa har sama, daɓen kuma ya rufe shi da falankai na fir.16Daga bayan gidan ya gina waɗansu ɗakuna masu kamu ashirin da katakai na sida tun daga ƙasa har sama. Ya gina wani ɗaki can ciki, shi ne wuri mafi tsarki.17Babban ɗakin, wato wuri mai tsarki wanda ke gaban wuri ma fi tsarki, tsawonsa kamu arba'in ne.18Akwai itacen sida a gidan, wanda a ka sassaƙa shi kamar ƙwarya a buɗe da furanni. Dukka sida ne a ciki. Ba bu aikin duwatsu da ake gani a ciki.19Suleman ya yi wani ɗaki can ciki domin a ajiye akwatin Yahweh a ciki.20Ratar ɗakin na can ciki kamu ashirin ne, faɗinsa kamu ashirin tsawonsa ma kamu ashirin ne. Suleman ya shafe bangayen da zinariya tsantsa bagadin kuma ya rufe shi da itacen sida.21Suleman ya shafe haikalin da zinariya tsantsa, ɗaki na can ciki kuma ya yi masa dajiya da zinariya, ya shafe gabansa da zinariya.22Ciki dukka ya shafe shi da zinariya har sai da a ka gama haikalin dukka. Bagadi na ɗaki na can ciki kuma ya shafe shi da zinariya.23Suleman ya yi sifofi biyu na kerubim da itacen zaitun, domin ɗaki na can ciki masu tsawon kamu goma.24Kowanne fiffike na kerub ɗin tsawonsa kamu biyar ne. Ya zama daga ƙarshen wannan fiffike zuwa ƙarshen wancan ya zama kamu goma kenan.25Ɗayan kerub ɗin ma faɗin fiffikensa kamu goma ne. Dukkan kerubim ɗin dai-dai suke da juna ba wanda ya fi wani.26Tsayin kerub ɗaya kamu goma ne haka kuma na ɗayan kerub ɗin.27Suleman ya ajiye kerubim ɗin a ɗaki na can ciki. Suka buɗe fukafukansu na wannan ya taɓa wancan bango, na wancan kuma ya taɓa wancan bango. Fukafukansu suna taɓa juna a cikin wuri mafi tsarki.28Suleman ya shafe kerubin ɗin da zinariya.29Bangayen ɗakin an zane su da yatsun kerubim da ganyen dabino da buɗaɗɗun furanni tun daga ciki har waje.30Ƙasan gidan Suleman ya shafe shi da zinariya tun daga ɗakuna na ciki har zuwa na waje.31Ɗaki na ciki Suleman ya yi masa ƙofofin shiga da itacen zaitun. Dogaran ƙofar da ginshiƙansu suna da aiyanannun sassa guda biyar.32Haka ya yi ƙofofi biyu na itacen zaitun, ya sa a ka zana kerubim da ganyen dabino da furanni buɗaɗɗu. Ya shafe su da zinariya, kuma ya yayyafa zinariya a kan kerubim ɗin da kuma ganyen dabinan.33Ta haka Suleman ya yi wa haikalin ƙofofin shiga da itacen zaitun da aiyanannun sassa guda huɗu34da ƙofofi biyu na itacen fir. Ɓangare biyu na wannan ƙofa a kan naɗe su haka ma ɓangare biyu na waccan ƙofa a kan naɗe su.35Ya zana kerubim da ganyen dabino da furanni buɗaɗɗu a kansu, ya shafe zanen da zinariya dai-dai wa daida.36Ya gina farfajiya ta ciki da layika guda uku da sassaƙaƙƙen dutse da ginshiƙai na sida.37An kafa tushen gidan Yahweh a cikin shekara ta huɗu, a watan zif.38Cikin shekara ta goma sha ɗaya, a watan Bul wato wata na takwas a ka gama gidan, yadda a ke so tsarinsa ya kasance duka. Suleman ya ɗauki shekara bakwai yana ginin haikalin.
taƙaitaccen jerin yadda haikalin zai zama
yana da kyau a bayyana saboda mai karatu ya gane waɗansu mutane sun taimaki Sulaiman yin aikin.
waɗannan su ne 480 - 4.
"Zif" sunan wata na biyu ne na kalandar Ibraniyawa. A kwanakin ƙarshe na watan 4 da kuma kwanakin farko na watan 5 na kalandar turawa.
rata shine 46centimeters, AT: "27.6 mita tsawonsa, 9.2 mita faɗi, da kuma 13.8 mita tsawo"
mai bayanin ya ci gaba da jerin girman haikali.
wurin gini da aka yi shi layi da kuma rumfa da ta haɗa ka ta kuma kai wurin shiga haikalin. wannan ratar shirayin an haɗa shi da farkon katanga da ya zagaye haikalin.
kamun kamu 46 centimita. AT: "9.2 mita ...4.6 mita"
Mai bayani ya ci gaba da jera girman haikalin.
ya gina ɗakuna a wajen-wajen haikalin kewaye da shi.
wannan yana nufin ɗaki na kowanne bene na ginin.
kamun kamu 46 centimeta. AT: "misalin 2.3mita ... misali 2.8 mita ... misalin 3.2 mita"
ya yi ƙafafu a kewaye da asalin ginin domin ya tallafi ginshiƙan ƙananan ɗaki.
matokarai wasu manya gungume na masu nauyi da ake tallafar gini dashi.
Anan "ginin" na nufin gidan Allah, haikali.
sassaƙa wurin ne da mutane suke yanka ƙatu dutse daga tsauni su gyara su da kayan sassaƙa har su yi sumul-sumul. Bayan sun sassaƙo su daga masassaƙa sai su kawo su haikali.
akwai hawa uku. wasu yaren na kiransu"hawan ƙasa" "hawa na farko," da kuma "hawa na biyu."
yana da kyau mu bayana saboda maimkaratu ya gane cewa Sulaiman ba shi kaɗai ya gina haikaalin ba.
matokara wani gungumen ita ce ne da ake sa ya tallafi gini. An fassara a 6:5.
katako mai faɗi na itace an yi amfani da shi a ƙasa da katanga.
waɗannan ɗakunan ɗaya ne da na wanda aka yi maganarsa a 6:5.
wannan na bayyana katangar da ta haɗu ta yi wannan ɗaki. AT: "katanga ta ciki da ta yi ɗaki na ciki"
kamu 46 santimita. AT: "2.3 mita"
Kalmar "ginshiƙi" haɗa itacen da ake amfani da shi a gini, kamarsu matokarai da falanki
wannan wakili ne da yakegabatar da wani abu da Allah ya faɗa waannabawans ko mutanensa. AT:"Yahweh ya faɗi wannan saƙo" ko kuma "Yahweh ya faɗi wadannan kalmomi"
Kalmar "tafiya" wakili ne na "rayuwa" ko kuma "biyayya." AT: "kullum kana kiyaye farillaina"
ku muce 1) "ka yi biyayya da dukkan dokokina" ko kuma 2) "ka yi wa mutanen da kake mulki adalci."
waɗanan kalmomi na nufin abu ɗayakuma sun jaddadamuhimmancin yin biyayya da dokokin Allah. AT: "a hankali kana kiyaye dukkan abinda na umarceka.
"zan dukkan abin da na yi wa mahaifinka Dauda cewa zan yi maka"
yana da kyau mu bayyana saboda mai karatu ya gane cewa Sulaiman ba shi kaɗai ya yi ginin haikalin ba.
"a ciki"
wani itace da ake amfani dashi wajen gina haikali. (Dubi: translare_unknown)
"ya gina ɗaki kamu ashirin"
"asalin ɗaki"
wani irin ciyawa ne da ya fito kasa
"babban fure" ko kuma "furunni da aka buɗe"
"9.2 mita"
wannan bagadin za a ringa amfsani dashi don ƙona turare
"shafe" (UDB)
"Bagadin turare na shiga can ciki"
"itace daga itacen zaitun"
kamu 46santimeti. AT:"4.6 mita ... 2.3 mita"
filin da ke tsakanin wanan fiffike zuwa wancan fiffike
"yadda ake auna girman wani abu"
ya na da matuƙar muhimmanci mu fassara saboda mai karatu ya gane cewa Sulaiman ba shi kaɗai ya yi aiki ginin ba.
wani hanya ne na faɗarwurin mafi tsarki na ibada
"a rufe wani abu da wani" (UDB)
ya na da matuƙar muhimmanci mu fassara saboda mai karatu ya gane cewa Sulaiman ba shi kaɗai ya yi aiki ginin ba.
a yi abu a zãne wanda zai bada ma'ana
a rufe wani abu da wani
ya na da matuƙar muhimmanci mu fassara saboda mai karatu ya gane cewa Sulaiman ba shi kaɗai ya yi aiki ginin ba.
dogarai wadanda suka gindaya ƙyauren kofa ko taga
haƙora kamar zira kwallon a dukkan sassa biyar
"a rufe wani abu" (UDB)
"Sulaiman kuma ya yi ƙofofin shiga na itacen zaitun, da aiyananun sassa guda huɗu da ƙofofi huɗu na itacen fir, a wuri ɗaya"
haƙora kamar zira kwallo
hakan ya na nuna kowacce Ƙofa tana da sassa biyu da suka haɗu da juna saboda a dinga ninke su tare.
ya na da matuƙar muhimmanci mu fassara saboda mai karatu ya gane cewa Sulaiman ba shi kaɗai ya yi aiki ginin ba.
Ginshiƙi wani gungume itace ne maik nauyi da ake amfani da shi a tallafi gini. an sake fassara shi a 6:5.
Kalmar "huɗu" da kuma "goma sha ɗaya" na nufin "4" da kuma "11." Ya na da kyau ka yi bayanin dalilan da yasa mai rubutun ya ƙidaya shekarun. AT: "shekara ta huɗu bayan Sulaiman ya zama sarki ... shekara ta goma sha ɗaya bayan Sulaiman ya zama sarki"
"haikali" (UDB)
"zif" sunan wata ne na biyu a cikin kalandar Ibraniyawa. yana nan ta wurin ƙarshen watan huɗu da farkon watan biyar na kalandar turawa. yadda yake a 6:1.
"Bul" wata ne na tkwas a cikin kalandar Ibraniyawa. yana nan a ƙarshen watan octoba a kuma farkon watan nowamba a kalandaer turawa.
dai-dai a ce. AT: "sun gama gina kowanne ɓangare na gidan. Sun gina shi dai-dai yadda Sulaiman ya umarce su su gina"
yana da matuƙar muhimmanci a bayyanawa mai karatucewa wasu mutane sun taimaki Sulaiman yin aikin.
1Suleman ya ɗauki shekaru goma sha uku yana ginin fadarsa.2Ya gina fada ta jejin Lebanon. Tsawonta kamu ɗari ne, faɗinta hamsin ratarta kuma kamu talatin ne. Fadar an gina ta layi huɗu da ginshiƙai na sida da kalankuwa a kan ginshiƙan.3An rufe gidan da sida wanda ya kwanta a kan kalankuwoyin. Kalankuwoyin kuma ginshiƙai sun tallabe su.4Akwai kalankuwoyi arba'in da biyar, kowanne layi yana da goma sha biyar. Akwai kalankuwoyi a layuka uku.5Tagogin kuma suna duban junansu a layuka uku, dukkan ƙofofin tsawo da fãɗi bai ɗaya ne an yi masu kalankuwoyi kuma suna duban junansu layi uku.6Akwai baranda mai tsawon kamu hamsin faɗinta kuma kamu talatin, a gaba an yi kwararo mai ginshiƙai da rufi.7Suleman ya yi ɗakin kursiyinsa inda zai riƙa yin hukunci, wato ɗakin shari'ar adalci. An rufe dukkan daɓen shi da sida.8Gidan da Suleman zai zauna kuma yana wani ɓangare na fãdar, an gina shi kamar yadda a ka gina ɗakin shari'ar. Ya yi wani gida kamar haka saboda ɗiyar Fir'auna wadda ya ɗauko ta zama matarsa.9Gine-ginen an yi masu ado da duwatsu masu tsada waɗanda a ka sassaƙa su dai-dai a ka goge su a kowanne gefe. An yi amfani da duwatsun tun daga tushen ginin har zuwa sama, a waje kuma har zuwa babban ɗakin shari'a.10An kafa tushen gidan da manyan duwatsu masu tsada ratar su kamu takwas ne zuwa goma.11A sama an yi ado da duwatsu masu tsada waɗanda a ka sassaƙo su dai-dai wa daida, kuma da kalankuwa ta sida.12Katafaren ɗakin taron da ya kewaye fadar ya na da layuka uku na sassaƙaƙƙen dutse da kalankuwa ta sida kamar wanda ya ke cikin haikalin Yahweh da wurin shan iskarsa.13Sarki Suleman ya aika a ka kawo Huram daga Taya.14Huram ɗan wata gwauruwa ne ta kabilar Naftali, babansa kuma mutumin Taya ne, shi gwani ne a aikin tagulla. Huram yana cike da hikima da fasaha da basirar yin babban aiki da tagulla. Ya zo wurin sarki Suleman domin ya yi wa sarki aikin tagulla.15Huram ya tsara ginshiƙai biyu na tagulla kowanne tsawonsa kamu goma sha takwas ne kaurinsu kuma kamu goma sha biyu.16Ya kuma yi zankaye biyu da za a sa a kan kowanne ginshiƙi. Tsawon kowanne zanko kamu biyar ne.17Ya yi aikin raga da sarƙa ya yi wa zankayen ado don a sa su can saman ginshiƙan, guda bakwai ya yi domin kowanne zanko.18Haka Huram ya yi layika biyu na tagulla kewaye da ginshiƙan ya yi wa zankayensu ado.19Zankayen da ke kan ginshiƙan wurin shan iskar ya yi masu ado da furanni, kowanne fure, tsawonsa kamu huɗu.20Zankayen da ke kan ginshiƙan nan biyu, an yi masu 'yan kwararo-kwararo guda ɗari biyu kewaye da su a can ƙoli.21Ya ɗaga ginshiƙan wurin shan iska na haikali. Ginshiƙi na hannun dama ya ba shi suna Yakin, ginshiƙi na hannun hagu kuma ya ba shi suna Bo'aza.22A bisa ginshiƙan akwai ado mai kama da furanni. Haka aka tsara ginshiƙan.23Huram ya yi wani teku na zubi, kamu goma daga wannan gefe zuwa wancan. Tsawonsa kamu biyar ne, kewayensa kuma talatin.24A ƙarƙashin tekun na zubi ya yi butoci kamu goma, ya yi su lokacin da ya ke yin tekun na zubi ya yi su tare.25Ya ɗora tekun a bisa bijimai goma sha biyu, uku suna duban arewa, uku suna duban yamma, uku suna duban kudu, uku kuma suna duban gabas. aka ɗora "Tekun" a kansu, dukkan su cibiyoyinsu suna daga ciki.26Kaurin tekun kamar tafin hannu ya ke, an yi masa baki kamar na ƙoƙo, kamar fure ya na sheƙi. Tekun ya na ɗaukar ruwa garwa dubu biyu.27Huram ya yi diraku goma na tagulla. Ratar kowacce dirka kamu huɗu ne, faɗinta ma kamu huɗu, tsawonta kuma kamu uku.28Aikin dirakun shi ne, suna da mahaɗai a tsakaninsu,29kan dirakun da mahaɗarsu akwai zakuna da bijimai da kerubim. A saman zakunan da bijiman akwai zãnen furanni.30Kowacce dirka ta na da ƙafafu huɗu na tagulla, kusurwoyinta huɗu suna da matokarai saboda bangajin. Matokaran an yi su da zanen furanni a gefen kowacce ɗaya.31Bakinsu buɗe ya ke kamar kwano, faɗinsa kamu ɗaya da rabi ne, yana da kambi kamu ɗaya. A bakin su akwai zane-zane, kuma gefensu yana da tsawo da fãɗa bai ɗaya ba zagayayye ya ke ba.32Ƙafafunsu huɗu suna daga ƙarƙashinsu, abin da ya riƙe su kuma yana cikin dirkar. Tsayin gargaren kamu ɗaya da rabi ne.33Ƙafafunsu gargare kama da gargaren karusa. Abubuwan da suke riƙe da su da wayoyinsu ƙarfe ne na zubi.34An yi wurin kamawa huɗu ga kowacce dirka waɗanda suke liƙe a jikinsu.35a kan kowacce dirka an yi kambi rabin zurfinsa rabin kamu. Saman inda ta tsaya da gefenta haɗe su ke.36Jikin matokaran da gefensu, Huram ya zana zakuna da kerubim da ganyen dabino ya rufe inda ƙofofi suke ya zagaye su da furanni.37Yadda ya yi matokaran dukkan su zubinsu iri ɗaya ne girman su da tsarin su dukka ɗaya ne.38Huram ya yi bangazai goma, kowannen su zai ɗauki ruwa garwa goma. Kowanne bangaji kamu huɗu ne kuma ya sa bangaji ɗaya a bisa matokaran su goma.39Ya yi matokarai biyar daga kudu suna fuskantar haikalin, biyar kuma daga arewa su masu na fuskantar haikalin. Ya sa "Tekun" a kusurwar gabas, yana fuskantar kudu da haikalin.40Huram ya yi bangazai da moɗa da tasoshin yayyafawa. Daga nan ya gama dukkan aikin da zai yi wa Sarki Suleman cikin haikalin Yahweh.41Ginshiƙan biyu suna kama da zankayen da suke kan waɗancan ginshiƙan guda biyu. Ya yi zane guda biyu kamar tasoshi ya sa su domin su yi wa zankayen ado.42Ya yi zãne-zãne ɗari huɗu saboda sahu biyu na kayan adon da ya yi (layi biyu na zãne-zãne domin su rufe zankayen da suke a kan ginshiƙan guda biyu da);43matokaran su goma da bangajin nan guda goma na bisa matokaran.44Ya yi tekun da bajiman nan goma sha biyu da ke ƙarƙashinsa;45da tukwanen da moɗayen da bangazayen da dukkan sauran kayan aikin. Huram ya yi wa Sarki Suleman, su saboda haikalin Yahweh.46Sarki ya sa a zuba su filin Yodan a ƙasar yumɓu da ke tsakanin Sokot da Zaretan.47Suleman bai auna kayan aikin ba domin yawansu ya fi gaban aunawa, nauyin tagullar kuma ba za a iya auna su ba.48Dukkan kayan da ke cikin haikalin Yahweh Suleman ya yi su da zinariya: bagadi na zinariya da teburi wanda za a ajiye keɓaɓɓiyar gurasa.49Sandunan ajiye fitilu, biyar a hannun dama biyar kuma a hannun hagu, a gaba cikin ɗaki na can ciki an yi su da zinariya tsantsa da furannin da fitilun da yatsun dukka na zinariya ne.50Kofinan da abubuwan kashe fitila da cokula da bangazaye da abubuwan ƙona turare dukka an yi su da zinariya tsantsa. Sakatu na ɗaki na can ciki wato wuri mafi tsarki da ƙofofin babban ɗakin taro na haikali dukka da zinariya aka yi su.51Da haka aka gama dukkan aikin da Sarki Suleman ya yi domin gidan Yahweh. Sai Suleman ya kawo abubuwan da mahaifinsa Dauda ya keɓe, azurfa da zinariya da kayan ɗaki ya sa su a cikin ɗakin ajiya a gidan Yahweh.
ma rubuci ya na magana akan fãdar sarki
Saboda Sulaiman sarki ne, sauran jama'a suka yi masa aikin.
idan yarenku bashi da kalmar "fada," za ka iya sa shi a matsayin "gida" ko kuma "babban gida."
"gidan ana kiransa gidan jejin Lebanon"
kamu shine 46 santimita. AT: "46 mita ... 23 mita ... 13.8 mita"
Ginshiƙi gungume ne mai nauyi da ake tallafar bango da rufi da shi.
an bayar da su bayanai game da fadar Lebanon.
ko kuma mu ce. AT: "kafintocin sun yi rafta daga sida zuwa falanki suka kuma haɗa su da ginshian" (Duba: figs:activepassive)
wani gungumen itace ne da ake amfani da shi a tallafi rafta.
"yana da tsari na madubi" (UDB)
ma rubuci ya yi magana akan baranda na ginshiƙin ginin.
wasu tarin shafika, tazara ɗaya tsakaninsu da juna
kamu shi ne 46 santimita. AT: "23mita ... 13.8 mita"
wani sashi ne na gini da ake yi da ginshiƙan da kuma jinka da ke kai da ke kuma haɗe da ƙofar shiga ginin. Dubi yadda za'a juya wannan a 6:3
ma rubucin ya yi bayani akan ɗakin haikalin.
ku kuma mu ce 1) "Sulaiman ya gina gida inda zai kafa kursisyinsa" 2) "Sulaiman ya sa ma'aikatansa su ka gina gida da ake kira gidan gidan kujerar sarki."
ko kuma mu ce. AT: "ma'aikatan suka rufe dukkan daɓen da itaceb sida"
wanna ya na nufin dukkan daɓen. AT: "daga wannan bangon zuwa wancan"
an ci gaba da bayanai game da fadar
ko kuma muce. AT: "Sulaiman ya ba wani ya zana hoton gidan da zai zauna, a wani ɓangaren fada, a wuri ɗaya"
ma rubucin na bayani game da duwatsun da aka yi amfani dasu wurin gini.
ma iya cewa. AT: "maginan sun yi wa ginin ado da sassaƙaƙƙun duwatsu masu tsada"
ma iya cewa. AT: "sassaƙaƙƙun duwatsu, masu tsada suka kuma goge"
ma iya cewa. AT: "ma'aikatan sun yi amfani da waɗannan duwatsu"
ma rubucin ya jaddadacewa ma'aikatan sun yi amfani da duwatsu masu tsada tun daga ginshiƙin har zuwa dukkan ginin.
mã iya cewa. AT: "ma'aikatan sun kafa tushen"
kamu 46 santimita. AT: "kamar 3.7 mita"
katako wani dogon itace ne da ake amfani da shi a tallafi gini
Translate a 6:36.
Huram ya ƙarɓi gayyatar Sulaiman don ya zo Yerusalem.
Gwauruwa mata ce wadda mijin ta ya mutu, ta haka muka san mahaifinsa ya mutu.
ma iya cewa. Kalmar "hikima da basira" suna nufin abu ɗaya kuma ana amfani da su a tare domin a jaddada. Yahweh ya ba da wannan abu ana magana kamar sunwani abu ne mai ƙarfi ko mai ruwa-ruwa da za a iya zuba wa a wani abu. AT: "Yahweh ya ba Huram hikima da basira da kuma fasaha"
kamu 46 santimita. AT: "kamar 8.3 mita ... 5.5 mita ... 2.3 kamu"
da'ira tazara ce ko gwaji a abu zagayeyyen.
a do akan kowacce tushe biyun nan
sun goge tagullar saboda nuna hasken rana. "kalar tagulla" (UDB)
"ƙarfe da aka gicciya maƙale su tare da kuma ƙarfe sara harhaɗa su tare"
Rumman 'ya'yan itace ne mai ƙarfi, jan fata da kuma iri mai yawa a ciki. Huram bai yi amfani da asalin rumman ya yi adon ginshikin ba. ya yi rumman da tagulla.
furenni ciyayi ne da fulawar su ta buɗe daga wannan ƙarshe zuwa wanncan. Ma iya cewa. AT: "Huram ya yi adon zankayen ... da furannin tagulla, tsawaonsu kamu huɗu"
fassara"ginshiƙi" a 7:6
kamu 46 santimita. AT: "kusan 1.8 mita"
"rumman ɗari biyu" Rumman 'ya'yan itace ne mai ƙarfi, jar fata da 'ya'ya masu yawa a cikinsa. Fassara a 7:18 (Dubi: tran slate_numbers)
yana da matuar mahimmmanci a fassara cewa Huram ba shi kaɗai ya yi aikin ba mutane sun taimake shi.
Ma iya cewa. AT: "sunan ginshiƙin hannun dama Yakin"
ma iya cewa. AT: "sunan ginshiƙin na hannun hagu Bo'aza"
ma iya cewa. AT: "Huram ya tsara ginshiƙan" ko kuma "mutanen Huram sun tsara ginshiƙan"
wannan yana nufi tanki na tagulla ko kuma bangaji wanda zai iya ɗaukar ko riƙe ruwa.
Huram ya narker da tagulla ya kuma yi shi kamar gini.
kamu santimita. AT: "4.6 mita .... 2.3 mita ... 13.8 mita"
"daga farko zuwa ƙarshe"
zagaye tazara ne ko gwajin wani abu a zagaye.
masaki abu ne mai ƙarfi, zagayayyen itace da yake girma a reshe.
ma iya ce. AT: "lokacin da Huran ya ke yin teku"
wannan yana nufin tanki na tagulla ko kuma bagaji wanda zai iya riƙe ruwa.
"a tsaya akan wani abu"
ma iya cewa. AT: "ma'aikatan Huram sun ɗora tekun akan tagulla"
wannan bayan dabba ne mai ƙafa huɗu aka yanke kwata.
ma iya cewa. AT: "Huram ya sa bakin tekun ya zama kamar bakin kofi, don ya gyara wajen kamar furanni"
garwa wani abu ne da yake da daukan 22 lita. AT: "2,000 garwa" ko "44,000 lita"
kamu shine 46 santimita. AT: "kamar 1.8 mita ... kamar 1.4 mita"
haka yana nuna ma rubucin zai bayyana dirga a kalmar da zata biyo.
akwai yankin siffa mai ado a jikin zaki, bijimai da kuma kerubin da aka daura aa gefen dirakun.
Anan "zanẽ" yana nufin karkataccen_ siffa na tagulla.
akwai kusurwa ɗaya a kowanne ƙafa. AT: "ƙafafu guda huɗu da kuma kusurwa biyu"
"kwana ta kowacce dirka"
kowacce matokaran an sa mata rabin furanni masu ado. ma iya cewa. AT: "Huram ya sa matokaran da karkataccen siffa"
kamu shine 46 santimita. AT: ""kamar 70 santimita ... kamar 50 santimita"
Anan "kambi" na nufin zagayayyen bangaren dirka buɗaɗɗen wurin da aka sa shi a cikin bangajin.
"kuma gefensu yana da tsawo da fãɗa bai ɗaya" wannan maganar ya koma 7:27 inda aka fara maganar dirka.
Anan kalmar "su" na nufin kusuwoyin. Kalmar "gidaje" na nufin wurin da aka sa kusurwoyin.
kamu shine 46 santimita. AT: "kamar 70 santimita"
ma iya cewa. AT: "Huram yayi gargaren kamar gargaren karusai"
Anan "su" na nufin gargare
"Akwai abin da aka tanadar domin kanawa a jikin dirkar"
kamu shi ne 46 santimita. AT: "santimita ashirin da uku faɗi"
ma iya cewa. AT: "Huram ya sa matokaran da da kambin a kowacce dirka"
kalmar "su" na nufin kerubim, zakoki da kuma ganyen dabino
kalmar "furanni" na nufin karkataccen_ siffa na tagulla. ma iya cewa. AT: "akwai furanni kewaye da su" (Duba: activepassive)
ma iya cewa. AT: "Huram ya yi dukkan dirkakokin iri ɗaya"
"dukkan dirkokin tsawonsu da girmansu ɗaya"
garwa ma'aunine na abu mai ruwa-ruwa da ke ɗaukar kusan 22 lita. AT: "kamar 88lita" ko "kamar 90 lita"
kamu shine 46 santimita. AT: "kamar 1.8 mita"
"kwanar kudu maso gaban na haikalin"
tasa - tasoshin an yi masu siffa kamar kwano.
"aka gicciya ƙarfen ya yi tsiri sosai"
"400 rumman." Rumman 'ya'yan itace mai ƙarfi jar fata da 'ya'ya masu yawa a ciki. fassar a 7:18.
anan kalmar "shi" ta na nufin Huram da masu taimakonsa.
"dukkan sauran kayan aiki"
tagulla da an goge domin ya ɗauko hasken rana
ya na da mutuƙar muhimmanci a bayana wa mai karutu cewa sauran mutane sun taimaka wajen yin aikin.
"ƙasar da ba gini a kanta ko lambu kusa da Yodan"
suna yen birane
ko da yake Sulaiman ba shi ya yi aikin da kansa ba. AT: "Sulaiman bai sa Huram da ma'aikatansa su gwada kayan aikinba"
ma iya cewa. AT: "ba wanda zai iya auna nauyin tagulla"
ya na da mutuƙar muhimmanci a bayana wa mai karutu cewa sauran mutane sun taimaka wajen yin aikin.
ma iya cewa. AT: "inda firistoci za su ringa ɗora keɓaɓɓan burodi "
"furanni" da "fitilu" ɓangare ne na sandunan ajiye fitilu.
ma iya cewa. AT: "ma'aikatan sun yi kofinan ... da zallar zinariya"
ma iya cewa. AT: "sun yi abubuwan kashe fitilu ... da zinariya"
ana "abubuwab rufe" na nufin 1) abubuwan da ake rufe ƙofa dashi, 2) ginshiƙin da aka maƙala ƙofa akai.
ma iya cewa. AT: "ma'aikatan sun gama aikin da Sarki Sulaiman ya sa su su yi domin gidan yahweh"
1Sa'an nan Suleman ya tattara dukkan dattawan Isra'ila da shugabannin kabilu da shugabannin iyalai na mutanen Isra'ila a gabansa a Yerusalem, domin ya kawo akwatin alƙawarin Yahweh daga birnin Dauda wato Sihiyona.2Dukkan jama'ar Isra'ila suka taru a gaban Suleman a wurin liyafar, a cikin watan Itanim, wato wata na bakwai.3Dukkan dattawan Isra'ila da firistoci suka ɗauki akwatin.4Suka kawo akwatin Yahweh da rumfar taruwa da dukkan kaya masu tsarki da suke cikin rumfar. Firistoci da Lebiyawa ne suka kawo waɗannan kaya.5Sarki Suleman tare da dukkan taron Isra'ila suka zo gaban akwatin, suna miƙa hadayar tumaki da bijimai waɗanda ba su ƙidayuwa.6Firistoci suka kawo akwati na alƙawarin Yahweh suka sa shi a wurinsa, cikin ɗaki na can cikin gidan, wato wuri mafi tsarki a ƙarƙashin fukafukan kerubim.7Gama fukafukan kerubim ɗin sun kai wurin da akwatin ya ke, kuma sun rufe akwatin tare da sandunan da a ke ɗaukar sa.8Sandunan suna da tsawo sosai har ana iya ganin su daga wuri mafi tsarki a gaban ɗaki na can ciki, amma ba za a iya ganin su daga waje ba. Suna nan har zuwa yau.9Babu kome a cikin akwatin sai dai allunan nan na dutse da Musa ya sa ciki a Horeb, sa'ad da Yahweh ya yi alƙawari da mutanen Isra'ila lokacin da suka fito daga ƙasar Masar.10Ya zama lokacin da firistocin suka fito daga wuri mai tsarki sai girgije ya cika haikalin Yahweh.11Firistoci ba su iya tsayawa su yi hidima ba saboda girgijen. Gama darajar Yahweh ta cika gidansa.12Sa'an nan Suleman yace, "Yahweh ya ce zai zauna a cikin baƙin duhu,13Amma na gina maka wuri mai ƙawa, wurin da za ka zauna har abada."14Sa'an nan sarki ya juya ya sa wa taron jama'ar Isra'ila albarka sa'ad da jama'ar Isra'ila suke a tsaye.15Ya ce, "Bari a yi yabo ga Yahweh Allah na Isra'ila wanda ya yi magana da mahaifina Dauda, kuma ya cika da hannunsa, cewa,16'Tun ranar da na kawo Isra'ila jama'ata daga Masar, ban zaɓi birni da zan gina gida domin in sa sunana a ciki ba. Na dai zaɓi Dauda ya yi mulkin jama'ata Isra'ila.17Yana dai cikin zuciyar Dauda mahaifina ya gina gida domin Yahweh Allah na Isra'ila.18Amma Yahweh ya ce da Dauda mahaifina, 'Ya yi kyau da ka ke da tunani a zucyarka domin ka gina ma ni gida.19Duk da haka ba za ka gina gidan ba, sai dai ɗanka wanda za a haifa ma ka shi ne zai gina gida domin sunana.'20Yahweh ya cika maganar da ya faɗi gama na taso a matsayin mahaifina Dauda, kuma ina zaune a kan kursiyi na mulkin Isra'ila kamar yadda Yahweh ya yi alƙawari. Na gina gida domin sunan Yahweh Allah na Isra'ila.21Na yi wa akwati wuri wanda a cikin sa alƙawarin Yahweh ya ke, wanda ya yi wa ubanninmu lokacin da ya fito da su daga ƙasar Masar."22Suleman ya tsaya a gaban akwatin Yahweh, gaban taron jama'ar Isra'ila ya buɗe hannuwansa zuwa sama.23Ya ce, "Yahweh, Allah na Isra'ila, babu wani Allah kamar ka a bisa cikin sama ko a nan ƙasa wanda ke riƙe alƙawarinsa da aminci zuwa ga bayinka waɗanda suke tafiya a gabanka da dukkan zuciyarsu;24kai wanda ya riƙe alƙawarin da ka yi wa bawanka Dauda mahaifina. I, ka faɗi da bakinka kuma ka cika da hannunka, kamar yadda ya ke a yau.25To yanzu dai, Yahweh, Allah na Isra'ila, ka cika alƙawarin da ka yi wa bawanka mahaifina Dauda, sa'ad da ka ce, 'Ba za ka rasa mutum wanda zai zauna a bisa kursiyin Isra'ila ba, idan dai zuriyarka za su yi hankali su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi tafiya a gabana.'26To yanzu dai Allah na Isra'ila, ina roƙon alƙawarin da ka yi wa bawanka Dauda mahaifina, ya zama gaske.27Amma gaskiya ne Allah zai zauna a ƙasa? Da ya ke dukkan duniya da sama ba za su iya riƙe ka ba, balle fa wannan haikalin da na gina!28Duk da haka, Yahweh, Allahna, ka yarda da wannan addu'a da roƙo na bawanka; ka saurari kuka da addu'ar da bawanka ya yi a gabanka yau.29Bari idanunka su zama a buɗe zuwa wannan haikali dare da rana, wanda ka yi magana a kansa cewa, 'Sunana da kasancewata za su zauna a can'- domin ka ji addu'o'in da bawanka zai yi a wurin nan.30Ka ji roƙon bawanka da na jama'ar Isra'ila sa'ad da muke yin addu'a a wannan wuri. I, ka ji daga wurin da ka ke, daga sama, kuma sa'ad da ka ji, ka yi gafara.31Idan wani mutum ya yi wa maƙwabcinsa zunubi, aka nemi da ya rantse da alƙawari, idan ya zo ya yi rantsuwa da alƙawari a gaban bagadinka a wannan gida,32ka ji daga sama ka yi wa bayinka hukunci, ka hukunta mai laifi ka sa abin da ya yi ya koma kansa, ka baratar da mai adalci ka yi masa sakamako saboda adalcinsa.33Idan abokin gãba ya yi nasara a kan bayinka jama'ar Isra'ila saboda suka yi maka zunubi, idan sun juyo sun kira sunanka a wnnan haikali, suka yi addu'a suka roƙi gafara -34idan ka yarda, ka ji daga sama ka gafarta zunubin jama'arka Isra'ila; ka dawo da su ƙasar da ka bayar ga kakanninsu.35Idan sama ta rufe babu ruwa, saboda mutanenka sun yi ma ka zunubi - idan su ka yi addu'a su na fuskantar wannan wuri, su ka kira sunanka kuma su ka juwo daga zunubinsu, bayan ka wahalshe su -36sai ka ji daga sama ka gafarta zunubin bayinka da na mutanen Isra'ila, sa'ad da ka koya masu hanyoyi masu kyau da ya kamata su bi. Ka aiko da ruwa a ƙasar da ka ba mutanenka gãdo.37A misali yunwa ta zo ƙasar ko cuta ko annobar gonaki ko cutar fatar jiki, ko fãri ko tsutsotsi, a misali kuma a ce abokin găba zai kawo hari a ƙasarsu, ko annoba ko wani ciwo -38A misali kuma wani ya yi addu'a ko roƙo ko dukkan jama'arka Isra'ila - kowanne ɗayansu yana sane da annobar a cikin zuciyarsa, idan suka tada hannuwansu zuwa wannan haikali.39Sai ka ji daga sama inda ka ke zaune, ka yi gafara kuma ka sãka wa kowanne mutum bisa ga dukkan abin da ya yi; ka san zucyarsa saboda kai kaɗai ne ka san dukkan zukatan mutane.40Yi haka domin su ji tsoron ka muddin suna zaune a ƙasar da ka bayar ga kakanninmu.41Har yanzu, game da baƙo wanda ba na cikin jama'arka Isra'ila ba ne: idan ya zo daga wuri mai nisa saboda sunanka -42gama za su ji labarin sunanka mai girma da hannunka mai iko da hannunka wanda ka tayar, idan ya yi addu'a yana fuskantar wannan haikali,43idan ka yarda, ka ji daga sama inda ka ke zaune, ka yi bisa ga abin da baƙon ya roƙe ka. Ka yi haka domin dukkan mutanen duniya su san ka su ji tsoron sunanka, kamar yadda jama'arka Isra'ila suke yi. Ka yi haka domin su san da sunanka a ke kiran wannan gida da na gina.44Idan jama'arka suka je yaƙi da abokan gaba, ta kowacce hanya ka aike su, Yahweh, idan suka yi addu'a suna fuskantar wannan birni wanda ka zaɓa da wannan gida da na gina domin sunanka.45Sai ka ji addu'arsu da roƙonsu daga sama ka yi taimako.46A misali idan suka yi maka zunubi, tun da ya ke ba wanda ba ya yin zunubi, a misali idan ka yi fushi da su, ka bashe su ga abokin găba, abokin găba ya kwashe su zuwa ƙasarsu, ko da nesa ko kusa.47A misali idan suka gane suna cikin ƙasar bauta, a misali idan suka tuba suka roƙi tagomashi a wurin ka daga ƙasar waɗanda suka bautar da su. A misali idan suka ce, 'Mun yi wauta mun yi zunubi. Mun yi aikin mugunta.'48Amisali idan suka juwo gare ka da dukkan zuciyarsu da dukkan ransu a cikin ƙasar abokan gãbarsu waɗanda suka kwashe su, idan suka yi addu'a suna fuskantar ƙasarsu, suna fuskantar birnin da ka zaɓa da wannan gida da na gina domin sunanka.49Sai ka ji addu'arsu da roƙonsu na neman taimako daga sama inda ka ke, ka dai-daita al'muransu.50Ka gafartawa mutanenka zunubin da suka yi maka da dukkan zunubansu da suka ƙetare dokokinka. Ka ji tausayin mutanenka a gaban abokan gãbarsu, domin abokan găbarsu su ji tausayin mutanenka.51Su mutanenka ne da ka zaɓa, waɗanda ka kuɓutar daga Masar kamar daga cikin tanderu inda a ke narkar da ƙarfe.52Ina roƙon idanunka su buɗe ga roƙon bawanka da roƙe-roƙen mutanenka Isra'ila, ka ji su daga ko'ina suka yi kuka gare ka.53Gama ka keɓe su daga dukkan mutanen duniya su zama na ka, su kuma karɓi alƙawuranka, Yahweh Ubangiji, kamar yadda ka bayyana ta wurin bawanka Musa sa'ad da ka kawo ubanninmu daga Masar, Ubangiji Yahweh."54Haka ya zama sa'ad da Suleman ya gama yin addu'a da dukkan roƙon da zai yi zuwa ga Yahweh, ya tashi daga gaban bagadin Yahweh, daga yin durƙusonsa a kan guiwoyinsa da ta da hannuwansa zuwa sama.55Ya miƙe ya sa wa dukkan taron jama'ar Isra'ila albarka da babbar murya, cewa,56yabo ga Yahweh wanda ya ba mutanensa Isra'ila hutawa, ya cika alƙawuransa. Ko kalma ɗaya ba a rasa ba cikin dukkan alƙawura masu kyau da Yahweh ya yi da bawansa Musa.57Yahweh ya kasance tare da mu, kamar yadda ya kasance tare da kakanninmu, kada ya bar mu ko ya yashe mu,58ya sa zuciyarmu ta manne masa, mu rayu cikin dokokinsa da ka'idodinsa da farillansa, waɗanda ya umurci ubanninmu.59Bari waɗannan maganganu da na faɗi, na yi roƙo ga Yahweh, su zauna a kusa da Yahweh Allahna, dare da rana, domin ya yi taimako cikin al'amuran bawansa da al'amuran jama'arsa Isra'ila a kowacce rana;60domin dukkan mutanen duniya su sani Yahweh shi ne Allah kuma ba bu wani Allah!61Saboda haka zuciyarku ta yi aminci ga Yahweh Allanmu, ku kiyaye farillansa da dokokinsa, kamar a yau."62Sai sarki tare da dukkan Isra'ila suka miƙa hadayu ga Yahweh.63Suleman ya miƙa baye-baye na zumunci waɗanda ya yi wa Yahweh: bijimai dubu ashirin da biyu da tumaki 120,000. Haka sarki da dukkan Isra'ila su ka keɓe gidan Yahweh.64A wannan ranar ne kuma sarki ya keɓe filin da ke tsakiya a gaban haikalin Yahweh. Gama a nan ne sarki ya miƙa baye-baye na ƙonawa, baye-baye na hatsi da kitsen baye-baye na zumunta, saboda bagadin da ya ke gaban Yahweh bai kai girman da zai ɗauki baikon ba, wato baye-baye na hatsi da kitsen baye-baye na zumunta.65Haka sarki ya yi liyafa a wannan lokaci da dukkan Isra'ila tare da shi, babban taro. Tun daga Lebo Hamat har zuwa iyakar Masar, suna gaban Ubangiji Allah kwana bakwai da waɗansu kwana bakwai kuma, wato kwana goma sha huɗu kenan dukka.66A kan rana ta takwas ya sallami mutanen, suka sa wa sarki albarka kowanne ya tafi gidansa da murna da farinciki saboda abubuwa masu kyau waɗanda Yahweh ya yi wa Dauda bawansa, da Isra'ila, mutanensa.
"an kira dukkan shugabannin Isra'ila"
wannan zai iya nufin 1) ga mutanen da Sulaiman ya kira su zuwa Yerusalem ko kuma waɗanda aka jeraa 8:1 ko kuma 2) gaba ɗayan waɗanda suka yije Yerusalem domin biki, ba lailai maza kaɗai ba kowa da kowa indai ya je biki kuma shi ɗan Yerusalem ne.
wannan ya na nufin ma bikin , wadda aka fi sani da bikin alfarwa ko wurin zaman (UDB).
"Itanim" wata ne na bakwai na kalandar Ibraniyawa. yana nan a ƙarshe watam satumba da kuma farkon aktobaa kalandar turawa.
wannan kalmar jimla ce.
ma iya cewa. AT: "tumaki da yawa da bijimai fiye da yadda za a iya ƙirgawa"
"cikin ɗakin na can cikin gidan ... shine, a wuri mafi tsarki -a ƙakashir"
ma iya cewa. AT: "sandunan da firistoci suka ɗauko shi"
ana iya ce. AT: "ba wanda zai iya ganin su"
wannan na nufin ranar da mai rubutu ya yi rubutun.
wannan jimlar ana amfani da ita a fara farkon kowanne taro a labari. idn yarenka yana yin haka, zaka iya yin amfani da shi anan.
Sulaiman ya yi magana da Yahweh kamar yana magana da wani dabam domin girmamawar da ya yi ma Yahweh.
gini mai kyau inda wani mai mutuƙar muƙami ke zama
wannan gaba ɗaya ne.
ma iya cewa: AT: "yabi Yahweh, Allahn Isra'ila"
hannun wakili ne na ikon da ke cikin hannun. AT: "cikin hannunsa"
Kalmae "suna" wakili ne na mutum, da kuma "ga ... suna" na nufin yi ma mutum ɗin sujada. irin wannan ya fito a 3:1. AT: "don haka mutane su yi mani sujada"
abin da Dauda yaso an kwatantashi kamar wani abu da yake a ma'auni da kuma zuciyar kamar ma'auni. AT: "Dauda mahaifina ya sa a zuciyarsa ... sa ran yin haka"
Kalmar "suna" wakili ne na mutum, " domin ... suna" na nufin yi ma wani sujada. Irin ta ta bayana a 3:1. AT: "in da mutane za su yi wa Yahweh sujada ... in da mutane za su yi mani sujada"
"saboda ka sa rai"
"domin ka na so ka yi haka"
muna iya cewa. AT: "wanda zai zama ɗanka" ko kuma "wanda za ka zama uba a gare shi"
wannan habaici ne. AT: "ya yi dukkan abin da ya ce zai yi kamar yadda ya faɗa"
tsawo wakili ne na iko. AT: "na sami ikon da mahaifina Dauda yake da shi"
kursiyi wakiline na ayyukan wanda yake zaune akan kursiyi. AT: "ina mulkin Isra'ila"
Kalmar "suna" wakili ne na mutum, da kuma "domin ... suna" na nufin yi ma mutumin sujada. yadda yake a 3:1. AT: "yadda mutane za su yi wa Yahweh sujada"
allon dutsen da Yahweh ya yi rubutun dokoki ana magana kamar sune dokokin da kansu. AT: "allon dutsen da Yahweh ya rubuta dokokin alkawarin"
wannan gaba ɗaya ne.
yadda mutum yayi rayuwa ana misaltashi da yadda yake tafiya a kan hanyar da ke dai-dai. AT: "" tafya a gabanka da dukkan zuciyarsu kamar yadda kake so su yi
hannun wakili ne na iko. AT: "da ƙarfin ikon ka ka cika abinda ka ce"
kursiyin wakili ne na wanda ya zauna akan kujerar mulki. AT: "ka yi mulkin Isra'ila"
yadda mutum yayi rayuwa ana misaltashi da yadda yake tafiya a kan hanyar da ke dai-dai. AT: "" tafya a gabanka da dukkan zuciyarsu kamar yadda kake so su yi
ma iya cewa 1) Sulaiman na yin tambaya da gaske kuma yan buƙatar amsa ko 2) tambayar ba ya buƙatar amsa amma Sulaiman na jaddada cewa Allah ya fi ƙarfin ya zauna da ikonsa kuma ya fi ya a duniya. AT: "amma ba zai yiwu a ce Allah zai zauna a duniya ba! "
Ana Sulaiman yayi magana da Allah a fakaice. AT: "amma za ka yi" (Duba: 123person)
"abin da nakekkarin faɗa na da matuƙar mahimmanci" ko kuma "gaskiyar shi ne"
"kai, don haka wannan haikalin da na gina ba zai iya ba"
Wannan kalmar "addu'a" da "roƙo" na nufin abu ɗaya kuma suna jaddada shi mai adalci ne kuma ya yi roƙonsa. Sulaiman ya yi magana da kansa a matsayin "bawanka" domin girmama Yahweh. wannan za a iya faɗar gaba gaɗi. AT: "yi min biyayya, bawanka, kamar yadda na yi roƙo"
Kalmar "kuka" da "addu'a" na nufin abu Ɗaya kuma na jaddada gaskiyar kuma ya tambayi Yahweh ya taimakeshi. Sulaimanya na magana da kansaa matsayin "bawanka" ya nuna girmamawa ga Yahweh. wannan za a iya yin sa gaba gaɗi. AT: "ka saurare ni, bawanka, idan na kira ka yau domin taimako"
idanu wakili ne na abin da ido ya gani. AT: "bari ka gani"
wannan kalma ce mai haɗa. AT: "dukkan lokacin" ko kuma "ci gaba"
wadannan kalmomi a tare sun jaddada Yahweh zai dauwama a haikalin.
Sulaiman ya yi magana game da kansa a matsayin "bawanka" ya nuna ya na girmama Yahweh. wannan za a faɗe ji gaba gaɗi. AT: "ni, bawanka, zan yi addu'a"
Sulaiman ya yi magana "bawanka" domin nuna girmamawa ga Yahweh. ma iya cewa wannan gaba gaɗi. AT: "ka saurari roƙona da na jama'arka Isra'ila"
ma iya cewa. AT: "wani na buƙatarsa ya rantse"
anan "kai" na nufin mutum ɗumgun. AT: "A kansa"
"abashi abin da ya cancanta saboda adaicinsa"
ma iya cewa. AT: "magabta sun ci nasara akan jama'arka Isra'ila"
ko kuwa 1) "sun furta cewa sun yi maka zunubi" 2) "sun yabe ka" ko 3) "sun ce za su yi maka biyayya daga yanzu."
wakilin suna "gafara" za mu iya fassara shi a matsayin aiki. AT: "Sun roƙe ka ka gafarta masu"
sama ɗin ana magana kamar wani gini ne inda Allah ya ɓoye ruwan sama. AT: "ba ka bar ruwan sama ya faɗo ba"
ko kuwa mã ce 1) "sun furta sun yi maka zunubi" ko kuwa 2) "sun yabe ka" ko 3) "sun furta za su yi maka biyayya daga yanzu." fassarar a 8:33.
yadda wani yayi rayuwa a kwatanta shi da yin tafiya cikn tafarki mai kyau. AT: "Yadda ya kamata su bi"
waɗannan kalmomin manoma ne da yake nufin mutuwar amfanin gona ko daga ruwan sama kaɗan ko me yawa.
"fãri" wasu irin bãbe da yake kawo ta'adi ta wurin cinye amfanin gona. kalmar "tsutsotsi" na bayyani lokacin da fãrin suke ƙanana.
ma iya cewa. AT: "mutum, ko dukkan mutanenka Isra'ila, suka yi addu'a da roƙo"
kalmar "addu'a" da "roƙo" na nufin abu ɗaya kuma yana jaddada cewa mutuminmai gaskiya ne ya yi roƙo akwai misalin ta a 8:27. AT: "roƙo"
ko mu ce 1) "ya san zunubin a cikin zuciyarsa" ko 2) "ya sani a zuciyarsa cewa annoban sakamako ne na zunubinsa."
kalmar da aka fassara "sama" na nufin inda Allah yake. wannan kalmar zata iya zama "sarari," ya dangata da maganar . Kalmar "sammai" na nuna dukkan abubuwan da muke gani a nan duniya, ya haɗa da rana, wata, taurari. Ya sake haɗa da talikan sama, kamar su duniyan sama, da ba zamu iya gani daga nan duniya ba. . Kalmar "sarari" na nufin shuɗin abinda muke gani a saman duniya da yake da gajimare da kuma iskar da muke shaƙa. ko da yake ana cewa rana da wata "su ma a sarari suke." . A wasu wurare a littafi mai-tsarki, kalmar "sam" zata iya nufin ko sarari ko kuma in da Allah yake. . Idan "sama" anyi amfani dashi a kalmance, ba ana nufin Allah ne ba. Misali, inda matiyu yayi magana game da "mulkin sama" yana magana ne gane da mulkin Allah shawarar wajen fassara: . Idan "sama" an yi amfani da da shi a kalmance, za a iya fassara shi da "Allah." . Gama "mulkin sama" a littafin matiya, yana da kyau a ajiye kalmar "sama" tunda yana da bambanci da bisharar matiyu . Kalmar "talikan sama" za a iya fasara su da "rana, wata,da taurari" ko "dukkan taurarin duniya." . Jimlar "taurarin sama"za a iya fassara su da "taurarin cikin sama" ko kuwa "taurarin cikin duniyoyin sam" ko "taurarin sama" (Duba kuma: mulkin Allah) goyon baya daga littafi mai-tsarki . 1 Sarakuna 08:22-24 . 1 Tassalonikawa 01:8-10 . 1 Tasalonikawa 04:17 . Mai-maitawar Shari'a 09:01 . Afisa 06:9 . Farwa01:01 . Farawa 07:11 . Yahaya 03:12 . Yahaya 03:27 . Matiyu 05:18 . Matiyu 05:46-48 Kalman ƙididdiga: . ƙarfi: H1534, H6160, H6183, H7834, H8064,H8065, G932, G2032, G3321, G3770, G3771, G3772
Mulkin Allah, mulkin sama
1 Sarakuna 4:2 1 Sarakuna 14:11 1 Sarakuna 23:7 1 Sarakuna 37:9 1 Sarakuna 42:11 JERIN KALMOMI
Dukkan wadanna na nufin ka zama rayayye a jiki, ba matacce ba. za a iya amfani dasu a kalmance a ace rayuwa ta ruhaniya. Wadannan tattaunawa ce game da abin da ake nufi da rayuwa "ta jiki" da "ta ruhaniya."
Rayuwa ta jiki
Rayuwa ta jiki shi kasancewar ruhun a cikin jikin. Allah ya numfasa rai cikin jikin Adumu, say ya zama rayayye.
"Rai" kuma za iya zama kamar mutum "an ceci rai".
Wasu lokuta "rai" na nufin ƙalubalai na rayuwa, "ya ji daɗin rayuwarsa."
Ko kuma yadda wani ya yi rayuwa "ƙarshen rayuwarsa"
Kalmar "raye" na nufin rayuwa ta jiki kamar "mahaifiyata tana nan har yanzu a raye." Yana kuma nuna in da mutum yake zauna "su na zauna a birni"
A littaf mai-tsarki "rai" har yanzu ana misalta shi ra'ayin "mutuwa."
Rayuwa ta ruhaniya
Mutum yana da rai na ruhaniya idan ya yarda da Yesu. Allah ya canza rayuwar wannan mutumin da ruhu mai-tsarki da yake raye a cikinsa.
Ana kiran wannan "rai na harabada" don ba ya ƙare wa.
Abokin gaban rayuwa ta ruhaniya shi ne rayuwa ta shine mutuwa ta ruhaniya, wadda yake nufin rabuwa da Allah da kuma ɗanɗana hukunci na harabada. Kalmar ƙididdiga:
Ya danganta da shafin, "rai" za a iya fassara shi da "kasance wa" ko "mutum" ko "rai" ko "kasancewa" ko "ɗanɗanawa."
Kalmar "rai" za a iya fassara shi da "daumawa" ko "zama" ko "wanzu."
Magana "ƙarshen rayuwar shi"za a iya fassara shi da "idan ya daina rayuwa."
Maganar "ceci rayuwarsu' za a iya fassara shi da "bar su su rayu" ko "kada ka kashe su."
maganar "sun sadaukar da rayuwar" za a iya fassara ta da "sun sa kansu a hatsari" ko "sun yi wani abu da ya kusa kashe su."
idan wani ɓangare na littafi mai-tsarki ya yi magana akan rayuwa ta ruhaniya, £rai£ zai iya zama "rayuwa ta ruhaniya" ko kuma "rai na harabada," ya danganta da shafin.
maganar "rayuwa ta ruhaniya" zamu fassar shi da da "Allah na sa mu zama a rayea ruhaniya" ko "sabon rai ta wurin ruhun Allah-" ko "rayuwa ta cikin cikinmu."
ya danganta da wurin, maganar "ta na bada rai" za a iya fassara shi da "dalilin rayuwa" ko "ba da rai na harabada" ko "dalilin yin rayuwa na harabada." (Duba kuma: mutuwa, harabada) Goyan bayan littafai-tsarki:
2 Bitrus 01:03
Ayyukan manzanni 10:42
Farawa 02:07
Ibraniyawa 10:20
Irimiya 44:02
Yahaya 01:04
Alkalawa 02:18
Luka 12:23
Matiyu 07:14
. Mai ƙarfi: H1934, H2416, H2417, 2421, H2425, H5315, G198, G222, G227, G806, G590
mutuwa, mutuwa, mutu, mutu, matacce,*
1 Sarakuna 1:10 1 Sarakuna 3:1 1 Sarakuna 8:13 1 Sarakuna 17:9 1 Sarakuna 27:1 1 Sarakuna 35:5 1 Sarakuna 44:5
A gafarta ma wani shine kada a tuna da laifins kuma ko da sun sake yin laifi. "gafara" yanayi ne gafartawa wani. . Gafartawa wani shi ne ƙin hukunta wannan mutum domin abin da yayi marar kyau. , za a yi amfani da shi a kalmance a ce "share" kamar yadda yake a "yafe bashi." . Idan mutane suke furta zunubansu, Allah ma ya yafe masu saboda mutuwar Yesu ta hadaya a gicciye. . Yesu ya koya wa almajiransa su gafarta wa juna kamar yadda shi ma ya yafe masu. Kalmar "gafarta" ta na nufin a yafe kada a hukunta wani saboda laifinsa. . Wannan kalmar ya na da ma'ana guda da "gãfarta" amma zai haɗa da ma;ana na baya na shirin ƙin hukunta wani mai laifi. . A kotin shari;a alkari zai iya gafarta wa wani wanda aka same shi da aikata laifi. . Koda yake muna da laifin zunubi, Yesu ya gafarta mana daga hukunci shiga gidan wuta, ta wurin mutuwar hadaya da yayi a gicciye. Kalman ƙididdiga: , ya danganta da ya danganta da muhallin "gafarta" za a iya cewa "gafara" ko "shafe" ko "a saki" ko "kada a riƙe wani." . Kalmar "gafara" za a iya fassara shi da jimlar "rashin riƙon fushi" ko "furta wani marar laifi" . Idan yaren yana da kalmar don shawarar da an riga an yanke a gafarta, wannan zai fi a fassara "gafara." (Duba kuma: laifi) Goyon bayan littattafan littafi mai-tsarki: . Farawa 50:17 . Lissafi 14:17-19 . Alkalawa 29:20-21 . Yoshua 24:19-20 . 2 Sarakuna 05:17-19 . Zabura 025:11 . Zabura 025:17-19 . Ishaya 55:6-7 . Ishaya 40:02 . Luka 05:21 . Ayyukan Manzanni 08:22 . Afisawa 04:31-32 . Kolosiyawa 03:12-14 . 1 Yahaya 02:12 Kalmomin ƙididdiga: . H5546, H5547, H3722, H5375, H5545, H5547, H7521, G859, G863, G5483
laifi, laifufuka
1 Sarkuna 7:10 1 Sarkuna 13:15 1 Sarkuna 17:13 1 Sarkuna 21:5 1 Sarkuna29:1 1 Sarkuna 29:8 1 Sarkuna 38:5
Kalmar "sakamako" na nufin abindamutum ya samun a saboda wani aiki da yayi ko mai kyau ko mara kyau. Ba wani "sakamako" shi ne aba wani wani abu da ya cancanta. . Sakamako zai iya zaman abu mai kyau da mutum ya samu saboda yayi biyayya da Allah ko yayi wani aiki mai kyau. . Wani lokacin sakamako zai iya zama mummuna sabili da rashi biyayya, irin su "sakamakon masu mugunta" a wannan muhallin "sakamako" na nufin hukuncin da wani ya ƙarɓa saboda aikata zunubi. Kalman ƙididdiga: . Ya danganta da muhallin, kalmar "sakamako" za a iya fassara shi da "biya" ko "hukunci." . A "saka" wani za a iya fassara shi da "biya" ko "hukunci"ko "ba da abin da ya cancanta" . ka tabbata fassarar wannan bai zama ɗaya da haƙƙi ba. Sakamako ba wai ya tsaya ga karɓar kuɗi bayan ka yi aiki ba. (Duba kuma: hukunci) Goyon bayan littafi mai-tsarki: . Alkalawa 32:06 . Ishaya 40:10 . Luka 06:35 . Markus 09:40-41 . Matiyu 05:11-12 . Matiyu 06:3-4 . Zabura 127:3-5 . Wahayin Yahaya 11:18 Kalmomi: . Ƙarfi: H319, H866, H868, H1576, H1578, H1580, H4909, H4991, H5023, H6118, H6468, H6529, H7938, H7939,H7999, G469,G514, G591, G2603, G3405, G3406, G3408Duba kuma: hukunci, hukunta, hukunci, ana hukunci, hukunci,ba hukunci
A ckin littafi mai-tsarki kalmar "zuciya" ana amfani da a kalmance da nufin tunanin mutum, jinsa, ra'ayi ko so. . A sami "zuciya mai ƙarfi" abu mai yi wuwa ne ya na nufin mutum ya ƙiyin biyayya da Allah. . Maganar "da dukkan zuciyata" ko "da zuciyata gaba ɗaya" na nufin yin abu ba tunanin wani abu dabam, da dukkan mika kai da ra'ayi. . Maganar "ɗauke shi a zuciya" na nufin yin abu da hankalta da yi wa wani. . Kalamar "karyayyiyar zuciya" na bayyana mutum mai baƙin ciki. Mutumin an zalince shi sosai a cikin zuciyarsa. Kalmar ƙididdiga: . Wasu harsuna suna amfani da sassan jiki dabam irin su "ciki" ko "ƙoda" sun kamanta wannan. . Wasu harsunan kuma zasu iya amfani da wani abu dabam su bayaya wanna wani kuma ya bayana wani. . Idan "zuciya" ko wani sassa bashi da wannan ma'anar, sauran harsuna kan iya sa shi kamar "tunane-tunane" "yadda ka ke jin abu" . Ya kuma danganta da muhallin, "da dukkan zuciyata" "da zuciyata ɗumgum" za a iya cewa "da dukkan ƙarfina" ko "dukka-dukkan mika kai" "dukka" ko "miƙa kai." . Maganar "a ɗau hakuri" za a ce "ka bi shi a hankali" ko "yi tunani a hankali" . Maganr "ƙarfin-zuciya" za shi ma iya fassara shi da "tawayen na taurin kai" ko "rashin yin biyayya" ko " ci gaba da ƙin yi wa Allah biyayya." . Yadda za mu fassara "karyayyiyar zuciya" sun haɗa da "bakin ciki" ko "jin haushi sosai a zuciya." (Duba kuma: ƙarfi) Goyon baya littattafn littafi mai-tsarki: . Yahaya 03:17 . 1 Tassalonikawa 02:04 . Ayyukan Manzanni 08:22 . Ayyukan Manzanni 15:09 . Luka 08:15 . Markus 02:06 . Matiyu 05:08 . Matiyu 22:37
. Ƙarfafa: H1079, H2436, H2504, H2910, H3519, H3629, H3820, H3821, H3823, H3824, H3825, H3826, H4578, H5315, H5640, H7130, H7307, H7356, H7907, G674, G1282, G1271, G2133, G2588, G2589, G4641, G4698, G5590
ƙarfi, kara ƙarfi, mafi ƙarfi, taurare, taurara, taurare, yana taurare,
Kalmar "tsoro" ko "jin tsoro" na nufin jin wani abu a jikin ka da shi da daɗi lokacin da ya sami hari daga maƙiya. . Kalmar "tsoro" za iya zama matuƙar biyayya da bamgirma ga mutum wanda yana da iko. . Jimlar "tsoron Yahweh" da kuma "tsoron Allah" da "tsoron Ubangiji" na nufin matuƙar biyayya ga Allah da kuma nuna biyayyarnan ta wurin kiyaye dokokinsa. Wannan tsoron yana tasiri indan ka san cewa Allah mai-tsarki ne kuma ya tsani zunubi. . Littafi mai tsarki ya koyar da cewa dukkan wanda yake jin tsoron Yahweh zai zama mai hikima. Kalmar ƙididdiga: . Ya danganta da yanayin kalmar "tsoro" za a iya fassara shi da "jin tsoro" ko "matuƙar biyayya" ko "ban girma" ko kuma "zama cikin ɗar-ɗar". . Kalmar "tsoro" ma iya cewa "razana" ko "firgita" "mai jin tsoro" . Jimlar "tsooron Allah ya zo masu" za a fassara shi "farat ɗaya sai suka ji matuƙar tsoro da ban girma ga Yahweh" ko kuma "nan take sai suka yi mamaki ƙwarai suka girmama Allah" ko "anan take sai suka ji matuƙar tsoron Allah" (saboda ƙarfin ikonsa). . Jimlar "kada kuji tsoro" za a iya fassara shi da "ka da kuji tsoro" ko "ku daina jin tsoro." . Ku tuna jimlar "tsoron Yahweh" bai faru a tsohon alkawari ba. Jimlar "tsoron Ubangiji" ko kuma "tsoron Ubangiji Allah" aka yi amfani da shi. (Duba kuma:mamaki,tsöro, Ubangiji, iko, Yahweh) Goyon bayan littafan littafi mai-tsarki: . Yahay 04:18 . Ayyukan Manzanni 02:43 . Ayyukan Manzanni 19:15-17 . Farawa 50:17 . Ishaya 11:3-5 . Ayuba 06:14 . Yonah 01:09 . Luka 12:05 . Matiyu 10:28 . Karin magan 10:24-25
. ƙaƙƙafa: H367, H926, H1204, H1481, H1672, H1674, H1763, H2119, H2296, H2727, H2729, H2730, H2731, H2844, H2849, H2865, H3016, H3025, H3068, H3372, H3373, H3374, H4032, H4034, H4035, 4116, H4172, H6206, H6342, H6343, H6345, H6427,H7264,H7267, H7297, H7374, H7461, H7461, H7493, H8175, G870, G1167, G1168, G1169, G1630, G1719, G2124, G2125, G2962, G5398, G5399, G5400, G5401
mamaki, al'ajabi, mamkin, mamaki,mamaki, mamaki,mamaki, mai ban mamaki,mãmãki, mamakai, rikice,tsõro, madalla, ubangiji, Ubangijin, Ubangiji, Shugaba, shugaban, alamar ban tsoro, alamomin ban tsoro, iko, iko, ikoki, iko sosai, mai iko, Yahweh
wadannan jimla ɗin na nufin abu ɗaya kuma suna nufin ikon Allah.
wannan za a iya cewa. Jimlar "kira da sunan ka" na nuna mutumin ya mallaki gidan. AT: "ka mallaki gidan nan da na gina"
Lokacin da Sulaiman ya ke magana, wannan yanayin ba su faru ba tukuna, ammam Sulaiman ya na sa rai zasu faru a gaban. Kayi amfani da harshenka kayi magana game da al'amuran da zasu faru nan gaba.
Kalmar "suna" wakili ne na mutum, da kuma "domin ... suna" na nufin yin sujada. Irinta ta bayyana a 3:1. AT: "yadda mutane zasu yi sujada"
Kalmar "addu'a" da "roƙo" na nufin abu ɗaya kuma ya jaddada cewa 'ya'yan Isra'ila masu gaskiyane lokacin da suke roƙo. An sake bayyanata a 8:27. AT: "roƙonsa"
Lokacin da Sulaiman yake magana, wannan yanayin bai faru ba tukuna, amma Sulaiman ya san za su faru a gaba. Yi amfani da wanna a harshenka domin kayi magana game da abu mai zuwa.
Ma iya cewa. AT: "inda magabtansu suka kai su bauta"
Mutane waɗanda suka kama wasu a 'yan sarƙa
Waɗannan jimloli guda biyu na nufin abu ɗaya. Dukkansu gaba ɗaya suna jaddada yadda muguntar mutanen nan yake.
Kalmar na nufin abu ɗaya kuma na jaddada yadda mutanen suka yi zunubi.
Habaicin "da dukkan ... zuciya" na nufin "gaba ɗaya" da "da dukkan ... rai" na nufin "da dukkan ... kasancewa." Waɗanan jimla guda biyu na da ma'ana guda ɗaya. Fassara a 2:1. AT: "da dukkan kasancewar su" ko "da dukkan ƙarfinsu"
"lokacin da suke raye a cikin ƙasar"
"fuskantar ƙasar su." Wanna na nufin Isra'ila.
Kalmar "suna" wakili ne na mutum da "domin ... suna" na nufin yin sujada ga mutumin. Sun bayyana a 3:1. AT: "Yadda mutune zasu yi maka sujada"
Kalmomin biyu "addu'a" da "roƙo" abu ɗaya ne. Dukka suna jaddada mutanen sunyi roƙo da laulausan lafazi ga Yahweh. Ya bayyana a 8:27.
Sulaiman sau biyu yana roƙon Yahweh ya gafarta zunuban mutanen. Wannan ya jaddada na ciyar roƙonsa.
Wannan za a iya cewa. AT: "tanderu inda mutane suke narka ƙarfe"
Ido wakili ne na mutum. AT: "Duba:"
Kalmomin biyu "addu'a" da "roƙo" abu ɗaya ne. Dukka suna jaddada mutanen sunyi roƙo da laulausan lafazi ga Yahweh. Ya bayyana a 8:27.
Ma iya cewa. AT: "yabi Yahweh"
Ma iya cewa. AT: "Yahweh ya sa dukkan kalma na alkawaransa masu kyau ta tabbata"
Wanna jimlar na nufin abu ɗaya ne kuma yana jaddada Sulaiman ya son Yahweh ya kasance tare da mutunen.
Son farantawa wani ana faɗarsa kamar manne zuciyarka ga wancan mutumin. AT: "ka sa mu so faranta masa"
Anan "a hanyoyinsa" habaici ne da yake nuna yadda yake so mutanen su yi rayuwarsu. AT: "yi rayuwa yadda ya umarcemu"
Ana nufin "dukkan lokaci" ko "a yi ta ci gaba."
"su zama masu miƙa kai ɗumgun"
Yadda mutane sukeyin rayuwa ana mislata shi da tafiya a hanyar da ke dai-dai. AT: "kullum kuna kiyaye farillansa"
Hakan na nufin 1) ga mutanen da Sulaiman ya kira zuwa Yerusalem wadanda aka jerasu a 8:1, ko 2) waɗanda suka je Yerusalem domin bukin, ba wai ga bawai ma zaunan Isra'ila ba.
"bagadi na tagulla da ke gaaban Yahweh." Tunda haikalin madauwamar Yahweh ce a wurin mutanensa, bagadin ana misalta shi gabansa.
Hakan na nufin 1) ga mutanen da Sulaiman ya kira zuwa Yerusalem wadanda aka jerasu a 8:1, ko 2) waɗanda suka je Yerusalem domin bukin, ba wai ga bawai ma zaunan Isra'ila ba.An sake faɗin ta a 8:62.
"kwan 7 ... kwana 7 ... kwana 14"
Kalmar "takwas" shi ne"8."
Kalmomin na nufin abu ɗaya ne an haɗa su ne don a jaddada.
1Bayan da Suleman ya gama ginin gidan Yahweh da fădar sarki, kuma bayan da ya gama dukkan abubuwan da ya ke so ya yi,2Sai Yahweh ya bayyana ga Suleman sau na biyu, kamar yadda ya bayyana gare shi a Gibiyon.3Daga nan Yahweh ya ce da shi, "Na ji addu'arka da roƙon da ka yi zuwa gare ni. Na keɓe wannan gida, wanda ka gina, domin kaina, in sa sunana a wurin. Idanuna da zuciyata za su kasance a wurin kowanne lokaci.4A gare ka kuma, idan ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dauda mahaifinka ya yi cikin aminci da sahihancin zuciya, ka na yin biyayya ga dukkan abin da na ummurce ka ka na kiyaye farillaina da shari'una,5zan tabbatar da mulkinka a kan Isra'ila har abada, kamar yadda na yi wa Dauda mahaifinka alƙawari, cewa, 'Ba za a taɓa rasa zuriyarka a kan kursiyin Isra'ila ba.'6Amma idan ka fanɗare, ko kai, ko 'ya'yanka, ba ku kiyaye dokokina da farillaina waɗanda na shimfiɗa a gabanka ba, idan ku ka je ku ka bauta wa waɗansu alloli ku ka russana masu,7zan kawar da Isra'ila daga ƙasar da na ba su, wannan gida kuma wanda na keɓe domin sunana, zan kawar da fuskata daga gare shi, Isra'ila kuma za su zama misali da abin ba'a da abin raini ga dukkan mutane.8Wannan haikali kuma zai zama tarin juji, dukkan wanda ya wuce ta kusa da shi zai kaɗu ya yi ajiyar zuciya. Zai yi tambaya haka, 'Me ya sa Yahweh ya yi haka ga wannan ƙasa da wannan gida?'9Waɗansu za su amsa da cewa, 'Saboda sun watsar da Yahweh Allahnsu, wanda ya fito da kakanninsu daga ƙasar Masar, sun koma ga waɗansu alloli sun russana masu sun yi masu sujada. Shi ya sa Yahweh ya auko masu da wannan masifar.'"10Ya zama shekaru ashirin bayan da Suleman ya gama gine-ginen nan biyu, wato haikalin Yahweh da fãdar sarki.11Hiram sarkin Taya ya tanadawa Suleman sida da itatuwan fir da zinariya da dukkan abin da Suleman ya bukata-sai sarki Suleman ya ba shi birane ashirin cikin ƙasar Galili.12Sai Hiram ya zo daga Taya domin ya ga biranen da Suleman ya ba shi, amma ba su gamshe shi ba.13Hiram yace, "Waɗanne irin birane ne waɗannan da ka ba ni, ɗan'uwana?" Hiram ya ce da su ƙasar Kabul, haka a ke kiran su har yau.14Dã ma Hiram ya aika wa sarki zinariya awo 120.15Wannan shi ne dalilin aikin dole wanda sarki Suleman ya sa a yi: wato a gina haikalin Yahweh da fãdarsa, kuma a gina Millo da garun Yerusalem da kuma kariya ta Hazor da Maggido da Gezer.16Fir'auna sarkin Masar ya je ya kama Gezer. Ya ƙone ta ya karkashe Kan'aniyawan cikin birnin. Sai Fir'auna ya ba ɗiyarsa matar Suleman, biranen a matsayin kyautar aure.17Haka Suleman ya sake gina Gezer da Bet Horon ta gangare,18da Ba'alat da Tamar a ƙasar Yahuda cikin jeji,19da biranen da ya ke da su na ajiya da na karusansa da na mahaya dawakinsa da dukkan abin da ya yi sha'awar ginawa a Yerusalem domin jin daɗinsa a Lebanon da dukkan ƙasashen da su ke ƙarƙashin mulkinsa.20Game da mutanen da su ka rage na wajen Amoriyawa da Hittiyawa da Ferizziyawa da Hiwiyawa da Yebusiyawa waɗanda ba sa cikin mutanen Isra'ila ba,21da zuriyarsu waɗanda mutanen Isra'ila ba su iya hallakawa duka ba, Suleman ya sa su ka zama masu aikin tilas haka kuwa su ke har yau.22Amma Suleman bai sa mutanen Isra'ila aikin tilas ba. Maimakon haka sai ya sa suka zama sojojinsa da bayinsa da jami'ansa da jami'an karusansa da mahaya dawakinsa.23Suleman ya na da jami'ai masu hidimar lura da masu duba aiki, yawan su shi ne 550, su ne suke lura da mutanen da suke yin aiki.24Ɗiyar Fir'auna ta tashi daga birnin Dauda ta koma gidan da Suleman da ya gina mata, sa'an nan Suleman ya gina Millo.25A shekara sau uku Suleman ya ke miƙa baye-baye na ƙonawa da baye-baye na salama a kan bagadin da ya gina wa Yahweh, a gaban Yahweh ya ke ƙona su da turare. Ya gama haikalin yanzu yana amfani da shi.26Sarki Suleman kuma ya yi tashar jiragen ruwa a Eziyon Geber wadda ta ke kusa da Elat a bakin Jan Teku a ƙasar Idom.27Hiram ya aiko bayinsa zuwa tashar Suleman, masu tuƙin jirgi waɗanda suka saba da teku tare da bayin Suleman.28Suka je Ofir da bayin Suleman. Suka kawowa Suleman zinariya awo 420 daga can.
Sulaiman yaron sarki Dauda ne. Mahaifiyarsa ita ce Batsheba. . Sulaiman ya zama sarki, Allah ya tambayi dukkan abibda ya ke so. Don haka Sulaiman ya tambayi hikima na mulkin mutanen da gaskiya da kuma adalci. Allah yaji daɗin abinda ya roƙa ya bashi hikima da kuma dukiya mai yawa. . Sulaiman kuma an san shi da wanda ya gina ƙaton haikali a Yerusalem. . Ko da yake Sulaiman yayi mulkinsa da kyau da hikima a shekara ta farko ta mulkinsa, daga baya ya yi wautar auren baƙin mataye ya koma bautawa gunkinsu. . Saboda rashin amincin Sulaiman bayan mutuwarsa Allah ya raba masarautar Isra'ila kashi biyu, Isra'ila da kuma Yahuza. Waɗannan mulkoki biyu suna gãba da juna. (Kalmar ƙididdiga: trnaslate_names how to translates names) (Duba kuma: Batsheba, Dauda, Isra'ilawa, Yahuza, Mulkin Isra'ila, haikali) Nusar littafi mai-tsarki: . Ayyukan Manzanni 07:47-50 . Luka 12:27 . Matiyu 01:7-8 . Matiyu 06:29 . Matiyu 12:42 Kalmomi: . ƙaƙƙarfa: H8010, G4672
Isra'ila, Isra'ilawa, Haikali
1 Sarkuna 17:14 1 Sarkuna 18:1 1 Sarkuna 18:2 1 Sarkuna 18:3 1 Sarkuna 18:4
Kalmar "gida" an yi amfani da shi a kalmance a littafi mai-tsarki . Wasu lokatai kalmar "iyali" du on nufin mutane da suke zama gida ɗaya. . "gida" na nufin zuriyar mutum ko saura 'yan'uwa. Misali " gidan Dauda" na nufin dukkan zuriyar Sarki Dauda. . Kalma "gidan Allah" da "gidan Yahweh" na nufin alfarwa ko kuma haikali. Wannan maganar za a iya cewa in da Allah yake ko dauwama. . A Ibraniyawa 3, "gidan Allah" an yi amfani da shi a kwatancin ga mutanen Allah ko, gaba ɗaya, ga dukkan abu da haɗa da Allah. . Jimlar "gidan Isra'ila" n nufin dukkan ƙasar Isra'ila a bambamce ga ƙabilar kudu na mulkin Isra'ila. Kalmar ƙididdiga: . Ya danganta da muhallin, "gida" za a iya fassara shi da "iyali" ko "mutane" ko "iyali na jini" ko "zuriya" "haikali" ko "wurin zama" . Kalmar "gidan Dauda" za a iya fassara ta da "mutanen Dauda" ko "iyali Dauda" ko "zuriyar Dauda." wasu maganganun za a iya fassara su ta haka. . Hanyoyi da dama da za a iya fassara "gidan Isra'ila" shine "mutanen Isra'ila" ko "zuriyar Isra'ila" ko "Isra'ilawa" . Kalmar "gidan Yahweh" zai zama "haikalin Yahweh" ko "wurin da ake yi wa Yahweh sujada" ko "wurin da Yahweh ya ke gamu da mutanensa" ko "wurin zaman Yahweh" . "gidan Allah" za a iya fassara shi kamar na Yahweh. (Duba kuma: Dauda, Zuriya, Gidan Allah, Iyali, Mulkin Isra'ila, Alfarwa, Haikali, Yahweh) Nusar littafan littafi mai-tsarki: . Ayyukan Manzanni 07:42 . Ayyukan Manzanni 07:49 . Farawa 39:04 . Farawa 41:40 . Luka 08:39 . Matiyu 10:06 . Matiyu 15:24
. ƙaƙƙarfa: H1004, H1005, G3609, G3613, G3614, G3624
sauko, saukowa, saukowa, sauka, zuriya, zuriyoyi, gidan Allah, gidan Yahweh, iyali, iyalai, alfarwa, haikali, Yahweh
Kalmar "Yahweh" ya zo daga kalmar da take nufin "zama" ko "wanzu." . Wasu ma'anonin "Yahweh " sun hada "Shi ne" ko "Ni Ne" ko "Wanda yasa ya zama." . Wannan sunan ya na nuna Allah koyaushe yana a raye kuma zai ci gaba da rayuwa harabada. . Bin al'ada, yawancin fassarar sun yi amfani da "Ubangiji" a mai ma kon "Yahweh" wannan al'adun sun sa mutanen Yahuda sun fara manta wa da yadda ake furta kalmar "Yahweh" suka fara cewa "Ubangiji" dukkan inda kalmar "Yahweh" a littafi mai tsarki sabon fassarar littafi mai tsarki suna rubuta "UBANGIJI" da babban baki don su nuna ban girma na musamman su kuma rarrabe shi da kalmar ubangiji don ba abu ɗaya bane. . Su ULT da UST a kowanne lokaci suna fassara shi a matsayin "Yahweh" kamar yadda yake a Ibraniyanci na tsohon alkawari. . A tsohon alkawari duk inda Allah zai yi magana gama da Shi kansa yana kiran sunan sa ne maimakon wakilin suna. . Ta wurin ƙara wakilin "NI" ULT sun nuna cewa Allah ne yake magana. Kalmomin ƙididdiga: . "Yahweh" za a iya fassara shi da kalma ko jimla "NI NE" ko "Rayayye" ko "Shi wanda yake a raye" . Wanna za a rubuta ta hanya ɗaya wadda take nuna ana magana da "Yahweh" ne. . Wasu majami'u ba sa son suyi amfani da kalmar "Yahweh" maimakon haka suna yi amfani da "UBANGIJI" abin rikitrwa anan shine idan ana kartawa jama'a dukka ɗaya ne da Ubangiji Yahweh da kuma ubangijin laƙabi. . Ya fi kyau a sa sunan ""Yahweh a duk inda ya kamata, amma wasu masu fassarar sun zaɓi su sa wakilin suna a wasu wurare domin wurin ya zama da ganewa sosai. . mu ringa sa shi kamar haka "wannan ne abin da Yahweh ya ce." (Dubi kuma:, how to translate names) (ka sake duba: Allah, ubangiji, Ubangiji, Musa, Bayyana.) Nusar littafan littafi-tsarki: . 1 Sarkuna 21:20 . 1 Sama'ila 16:07 . Daniel 09:03 . Ezikiyel 17:24 . Farawa 02:04 . Farawa 04:3-5 . Farawa 28:13 . Yowel 11:12 . Ishaya 10:04 . Ishaya 38:08 . Ayuba 12:10 . Yoshu'a 01:09 . Makoki 01:05 . Liviticus 25:35 . Malachi 03:04 . Mika 02:05 . Mika 06:05 . Lissafi 08:11 . Zabura 124:03 . Rut 01:21 . Zakariya 14:5
. ƙaƙƙarfa: H3050, H3068, H3069
Allah, Ubangiji, iyayen giji, Ubangiji, Shugaba, Shugabanni, sir, Bayyana, bayanai, an bayyana, wahayi
1 Sarakuna 9:14 1 Sarakuna 13:4 1 Sarakuna 13:5 1 Sarakuna 16:1 1 Sarakuna 19:10
Kalmar "Sarki" na nufin mutum wanda shine sarki mai mulki birnin, jiha, ko ƙasa. . Sarki ana zaɓen sa ne ya yi mulki saboda dangantakarsa da sauran sarakai da suka yi mulki. . Ida sarki ya mutu yawanci lokuta babban yaronsa ne ke gadarsa. . A zamanin dã, sarki yana da iko sosai akan mutanensa da yake mulkinsu. . Ba kowannen lokaci ba kalmar "sarki" ana kiran wand ba sarki na gaskiya ba, irinsu "sarki Hiridus" a sabon alkawari. . A littafi mai-tsarki, Allah ana kiransa sarki wanda ke mulkin mutanensa. . "Mulkin Allah" na nufin Allah na mulkin mutanensa. . Yesu an kira shi "sarkin yahudawa" ko "sarkin Isra'ila" ko "sarkin sarakuna" . Idan Yesu ya dawo zai yi mulki na harabada bisan dukkan duniya. . Wannan kalmar za a iya ce "mafificin sarki" ko "sarkin da ba irinsa" ko "maɗaukakin mai mulki" . Jimlar "sarkin sarakuna" za a iya ce "sarki wanda yake mulki mbisa dukkan sauran sarakuna" ko "maɗaukakin mai mulki da yake da iko bisan sauran masu mulki." (Duba kuma: iko, Hiridus Antipas, mulki, mulkin Allah) Nusar littattafan littafi mai-tsarki: . 1 Timoti 06:15-16 . 2 Sarakuna 05:18 . 2 Sama'ila 05:03 . Ayyukan Manzanni 07:9-10 . Ayyukan Manzanni 13:22 . Yahaya 01:49-59 . Luka 01:05 . Luka 22:24-25 . Matiyu 05:35 . Matiyu 14:09
. ƙaƙƙarfa: H4427, H4428, H4430, G935, G936
iko, ikoki, mulki, mulkoki, mulkin Allah, mulkin sama
1 Sarakuna 8:6 1 Sarakuna 16:1 1 Sarakuna 17:5 1 Sarakuna 16:18 1 Sarakuna 21:6 1 Sarakuna48:14
Kalmar "Fada" gini ne inda sarki da iyalinsa da bayinsa suke zama. . Babban firist shi ma yana zama a harabar fada, yadda aka faɗa a sabon alkawari. . Fadar ƙawatacciyar ƙofa, da kyawawa gini da kayayyaki. . Ginin da kayayakin fadar an yi su ne da duwatsu da ko itace, kuma an shafe su tagullada itace mai tsada da kuma hauren giwa. . mutane da yawa suna zama suna aiki a fadar, wanda ya kunshi gine gine da yawa da harabu. (Duba kuma: haraba, babban firist, sarki) Nusar littattafan littafi mai-tsarki: . 2 Tarihi 28:78 . 2 Sama'ila 11:2-5 . Daniyal 05:5-6 . Matiyu 26:3-5 . Zabura 046:08
. ƙaƙƙarfa: H759, H1002, H1004, H1055, H1406, H1964, H1965, G833, G933, G4232
kotu, kotu, haraba, harabobu, babban firist, shugaban firist, sarki, sarakuna, mulki, mulkoki, mulki, sarakuna fiye
Gibiyon gari ne da ake samunsa kusan kilomita 13 arewamaso yamma a Yerusalem. mutanen gari gibiyon suna gibiyawa. . Lokacin da gibiyawa suka ji labaarin yadda Isra'ilawa suka lalata ƙasar Yerikoda Ai,sai suka tsoro. . Sai Gibiyawa suka zo wurin shugabannin Isra'ila a Gilgal suka ce wai sun ne daga ƙasa mai nisa. . Shugabannin Isra'ila suka yarda da ƙaryar da suka yi masu har suka ƙulla alkawari da su cewa ba za su kashe su ba amma zasu kare su. (Duba kuma: Gilgal, Yericho, Yerusalem) Nusar littattafan littafi mai-tsarkk: . 1 Tarihi 08:29 . 1 Sarakuna 03:4-5 . 2 Sama'ila 02:12-13 . Yeshu'a 09:3-5
. Ƙaƙƙarfa: H1391, H1393
1 Sarakuna 15:6 1 Sarakuna 15:7 1 Sarakuna 15:8
Kalmar "addu'a" da "roƙo" na nufin abu ɗaya kuma yana jaddada Yahweh ya gane roƙon Sulaiman na gaskiya ne. kamar a 8:27. AT: "roƙon ka"
Sunan wakili ne na mutum. AT: "ka dauwama ka kuma mai shi na ka harabada"
"idanu" da "zuciya" wakili ne na mutum. AT: "zan kare in lura da shi"
Yadda mutum yake rayuwa ana kwatantashi da tafiya a cikin tafarki mai kyau. AT: "idan ka yi rayuwa yadda nake so kayi, kamar yadda mahaifinka Dauda ya yi"
Waɗannan jimlolin na nufin abu guda kuma suna jaddada yadda amincin Dauda yake.
A nan "kursiyi" na nufin yin mulkinsa. AT: "daular ka" da "mulkinka"
Yin jagorancin mulki ana magana da shi kamar mutum ne zaune akan kursiyin. za a iya ce. AT: "zai mulki Isra'ila kullum"
A nan kalmar "dokoki" da "farillai" na nufin abu ɗaya kuma yana jaddada dukkan abin da Yahweh ya umarta.
Wannan jimla na nufin abu ɗaya aka haɗa su tare don jaddada.
A nan kalmar "suna" wakili ne namutum wanda wani abu na sa ne. AT: "keɓe shi domina"
Wakilin suna "gani" za a iya bayana ta da kalmar aiki "gani" duban wani abu shine wakilin na kãre shi. AT: "zan sa shi a inda ba zan ringa ganinsa ba" ko "zan kawar da shi yadda ba zan ƙara ganin sa"
"wannan haikalin za a rushe shi da sauran da ya ragu kuma zai zama tãrin dutse mai girma"
Wannan za a iya sa shi akalmar aiki. AT: "zai yi mamaki ya kuma yi tsaki"
Waɗannan jimla na nufin abu ɗaya. jimlar "rusuna masu" na nuna motsin jiki idan mutane suna sujada.
wannan ana amfani da shi a fara farkon labari. I dan harshenku ya na da hanyar faɗin sa, sai ka sa su anan
"bayan shekara 20"
ya na da kyau ma bayyana wa mai karatu cewa Sulaiman ba shi kaɗai yi aikin gini ba sauran mutane sun taimakeshi.
Hiram ya kwaɓi Sulaiman. AT: "wannan birane da ka bani ba su da amfani."
za a iya faɗin wannan a matsayin aiki. AT: "mutane suna ta kiransa har gobe"
awo wani ɓangaren ne mai nauyi kusan 34 kilogiram. AT: "kamar 4000 kilogiram na tagulla"
"dalilin da sarki Sulaiman ya so mutane su yi aiki"
ko kuwa muce 1) "a gina tireshi" ko kuma 2) "a gina ƙasar" (UDB).
Mutumin wakili ne na sojan da yake ba umarni. AT: "sojojin fir'auna, sarkin masar, ya je sama"
ya na da kyau a bayyana wa mai sauraro ya sani wa su mutane sun taimake shi yin ginin.
Kalmar "mutane" ko "ƙungiyar jama'a" na nufin ƙungiyar jamaa'a da suke yin yare ɗaya,al'adunsu kuma ɗaya. Jimlar "mutanen" yana nufin tarowan mutane a wani wuri ko kuma wani biki na musanman. . Lokacin da ubangiji ya ware "mutanen" domin kansa, yana nufin ya zaɓi waɖansu mutane da suka zama nasa suka bauta masa, . A littafi mai tsarki, ƙungiyar mutanennyawan cin lokaci suna zama da kakanni ɗaya kuma suna zama a tare gari gudu. . Ya danganta da muhallin, jimlar irin ta "mutanenka" zai iya zama"ƙungiyar mutanenka" or "iyalinka" ko "'yan'uwanka." . Kalmar "mutane" ana amfani dashi dukkan ƙungiyar mutane ta duniya. Wani lokaci ya na magana da mutanen da ba Isra'ilawa ne ba kuma ba su bautawa Yahweh. A wasu fassarar littafi mai tsarki kalmar "kasa" ana amfani da haka. Kalmomin ƙididdiga: . Kalmar "ƙungiyar mutane" za a iya fassara shi da "babban iyali" ko "zuriya" ko "ƙungiyar yare". . Jimlar irinta "mutane na" za a iya fassara ta da "'yan 'uwana" ko "ƙungiyar mutane" ya danganta da context. . jimlar "mutanen" za a iya fassara shi da "mutanen da suke zaune a" ko kuma "mutane ƙabilar" ya danganta ko sunan mutum ko wuri ne ya biyo baya. . "Dukkan mutanen duniya" za a ce "dukkan mai rai na duniya" ko kuma "dukkan mutum na duniya" ko "dukkan mutane" . Jimlar "mutane" za a iya fassara "ƙungiyar mutane" ko kuma "wadansu mutane" ko kuma "tattaruwar mutane" ko "iyalin mutane" (Duba kuma: zuriya, ƙasa, ƙabila, duniya) Nusar littattafan littafi mai tsarki: . 1 Sarakuna 08:51-53 . 1 Sama'ila 08:07 . Mai-maitawar Sharia28:09 . Farawa 49:16 . Rut 01:16 Kal
. ƙaƙafa: H249, H523, H524, H776, H1121, H1471, H3816, H5712, H5971,H5972, H6153, G1074, G1085, G1218, G1484, G2560, G2992, G3793
sauka, sauka, sauka, saukowa, zuriya, zuriyarsa, ƙasa, ƙasashe, ƙabilar, ƙabilai, ƙabilai, mutanen ƙabila, duniya, duniyanci.
1 Sarakuna 14:2 1 Sarakuna 21:2 1 Sarakuna 42:8 1 Sarakuna 42:10 1 Sarakuna 48:11 1 Sarakuna 50:3
Amoriyawa sune mutane masu ƙarfi sosai waɗanda su zuriya ce daga daga jikan Nuhu ka'ana. . sunan su na nufin "manya", wanda ya ke nufin yanki duwatsu in da suke rayuwa, ko kuma an san su da tsawo sosai. . Amoriyawan suna rayuwa a dukkan ɓangaren rafin Yodan. Birnin Ai Amoriyawa suka gaje shi. . Allah ya nufi "zunubin Amoriyawa" wanda ya haɗa da bautar gumaka da ayyukan zunubi. . Yeshu'a ya yi jagorancin Isra'ilawa suka lalatar da Amorikawa, kamar yadda Allah ya umarcesu su yi. Nusar litattafan littafi mai tsarki: . Amos 02:09 . Ezekiyel 16:03 . Farawa 10:16 . Farawa 15:14-16 . Yeshu'a 09:10
. Ƙaƙƙarfa: H567
1 Sarakuna 15:7 1 Sarakuna 15:8 1 Sarakuna 15:9 1 Sarakuna 15:10
Hittiyawa su ne zuriyar Hamta wurin ɗansa ka'ana. sun zama babban daula ana samun su a inda yanzu ake kira turkiya da kama arewacin pakistan. . Ibrahim ya sa yi yanki dukiya a wurin Epiron da Hittiyawa domin ya bisne matarsa Saratu. A ƙarshe Ibrahim da yawancin zuriyarsa aka bizne su a wurin. . Mahaifan Isuwa sun yi bakin ciki kwarai sa'adda ya auri mata biyu daga matan Hittiyawa. . Wani daga cikin mayaƙan Dauda sunan sa Uriya ɗan Hittiyawa. . Wasu daga cikin baƙin matan da Sulaiman ya aura Hittiyawa ne. Waɗannan matan suka juya zuciyar Sulaiman daga bin Allahnsa saboda gumakan da suka zo da shi suna bauta masa. . Hittiyawa sai suka zama barazana ga Isra'ila, a fili har ma a ruhaniyance. (Duba kuma: zuriya, Isuwa, baƙi, Ham.) Nusar littafi mai tsarki: . 1 Sarakuna 09:20-21 . Fitowa 03:7-8 . Farawa 23:11 . Farawa 25:10 . Yeshu'a 01:4-5 . Nahemiya 09:08 . Lissafi 13:27-29
. Ƙaƙƙarfa: H2850
sauko, sauko, saukowa, saukowa, zuriya, zuriya, baƙo,baƙi, baƙunta, baƙi, baƙi, baƙo, cikakken mulki, mai girma,mai girma, iko, aiyukan iko
Firiziyawa su waɗansu ƙungiyar mutane nea kasar kan'ana, kaɗan daga cikin labarin su ne aka faɗi game da kakaninsu ina ko wannan ɓangaren ƙasar kan'ana suke zama. . Firiziyawa an yi maganarsu sosai a tsohon aikawari littafin Muhukunta, inda aka ce firiziyawa sun auratayya da Isra'ilawa har sun rinjaye su su bautawa gumakansu. . yana da kyau musan da cewa zuriyar "Firiziyawa", ba ɗaya bane da Firizziyawa. Saboda haka dole ne mu nuna bambancin ta wurin rubutasu saboda mu sani. (Shawara ga mai fassara: How to translate names) (Duba kuma: Kan'ana, allolin ƙarya) Nusar littatafan littafi mai tsarki: . 1Sarakuna 09:20-21 . 2 Tarihi 08:7-8 . Fitowa 03:16-18 . Farawa 13:07 . Yehu'a 03:9-11
. Ƙaƙƙarfa: H6522
allah, allahn ƙarya, alloli, allahiya, gunki, gumaka, mashirki, mashirkiya, gumaka, shirka
Hiwiyawa suna ɗaya daga cikin ƙungiyar mutane bakwai da suke zama a kan'ana. . Dukkan waɗannan ƙungiyoyi har da Hiwiyawa zuriyar ne daga kan'ana, wanda shi jikan Nuhu. . Shekem Hiwiyawa ya yi Dina fyaɗe, 'yan'uwanta suka kashe Hiwiyawa da yawa don ɗaukar fansa. .Lokacin da Yeshu'a ke jagorantar Isra'ilawa su mallaki ƙasar kan'ana, Isra'ilawa suna yaudarar su cikin alkawari Hiwiyawa mai makon cin nasara akan su.
(Duba kuma: Kan'ana, Haman, Huhu, Shekem) Nusar littattafan littafi mai tsarki: . 2 Tarihi 08:7-8 . Fitowa 03:7-8 . Farawa 34:02 . Yeshu'a 09:1-2 . Mahukunta 03:1-3
. Ƙaƙƙarfa: H2340
Yebusiyawa mutane ne a ƙungiya da su ke zama a ƙasar kan'ana. Su mutane ne daga zuriyar Ham ɗan kan'ana. . Yebusiyawa na zama a ƙasar Yebusiya, daga baya an canza sunan ƙasar zuwa Yerusalem da sarki Dauda ya ci ƙasar da yaƙi. . Malkizadak, sarkin salem, shi ɗan asalin Yebusiyawa. (shawara ga mai fasara: how to translate names) (Duba kuma: Kan'ana, Ham, Yerusalem, Malkidak) Nassoshin Littafin Mai tsarki: . 1 Tarihi 01:14 . 1 Sarakuna 09:20-21 . Fitowa 03:7-8 . Farawa 10:16 . Yeshuwa 03:9-11 . Mahukunta 01:20-21
. Ƙaƙƙarfa: H2982, H2983
Kalmar "Isra'ila" sunane da Allah ya ba Yakubu. Yana nufin "ya yi faɗa da Allah." . Zuriyar Yakubu wanda an fi sanin su da "mutanen Isra'ila" ko kuma "ƙasar Isra'ila" ko kuma "Isra'ilawa." . Allah ya yi alkawarinsa da mutanen Isra'ila. Su zaɓaɓɓun mutanen sa ne. . Ƙasar Isra'ila ya haɗa da dukkan ƙabilai goma sha biyu na Isra'ila. . Nna da nan bayan Sarki Sulaiman ya mutu, aka raba Isra'ila kashi biyu, kudancin aka kira shi "Yuhuza" arewacin kuma aka kira shi "Isra'ila" . Daga nan "Isra'ila" za a iya fassara shi da "mutanen Isra'ila" ko kuma "ƙasar Isra'ila" ya danganta da mahallin. (Duba kuma: Yakubu, Mulikin Isra'ila, Ƙasar Yahuza, ƙabilai goma sha biyu na Isra'ila) Nassoshin littafi mai tsarki: . 1 Tarihi 10:01 . 1 Sarakuna 08:02 . Ayyukan Manzanni 02:36 . Ayyukan Manzanni 07:24 . Ayyukan Manzanni 13:23 . Yahaya 01:49-51 . Luka 24:21 . Markus 12:29 . Matiyu 27:09 . Filibiyawa 03:4-5
. Ƙaƙƙarfa: H3478, H3479, H3481, H3482, G935, G2474, G2475
ƙasa, ƙasashe, ƙabilai goma sha biyu na Isra'ila, ƙabilai goma sha biyu
1 Sarakuna 8:15 1 Sarakuna 9:3 1 Sarakuna 9:5 1 Sarakuna 10:1 1 Sarakuna 14:12 1 Sarakuna 15:9 1 Sarakuna 15:12 1 Sarakuna 16:16 1 Sarakuna 43:6
"Zuriya" wani ne wanda ya ke da dangantaka da jini na wani da yayi zamaninsa ya wuce. . Misali, Ibrahim ɗan'uwan Nuhu ne. . zuriyar mutum sune yaransa, jikokinsa, tab-taɓa kunnensa da sauransu. Yakubu zuriyarsa su ne ƙabilai goma sha biyu na Isra'ila. . Kalmar "fitowa daga" wata hanya cwe ta ce wa "zuriyar" kamar "Ibrahim ya fito daga zuriyar Nuhu." wannan za a iya cewa "daga iyalin." (Duba kuma: Ibrahim, kakanin, Yakubu, Nuhu, ƙabila goma ta Isra'ila). Nassosin littafi mai tsarki: . 1 Sarakuna 09:4-5 . Ayyukan Manzanni 13:23 . Mai-Mia tawar Shari'a 02:20-22 . Farawa 10:1 . Farawa 28:12-13
Ƙaƙƙarfa: H319, H1004, H1121, H1323, H1755, H2232, H2233, H3205, H3211, H3318, H3409, H4294, H5220, H6849, H7611, H8435, G1074, G1085, G4690
kakanni, kakanni, uba, ubanni, ubanta, uba, kakanni, kakanni, kaka, ƙabilai goma sha biyu na Isra'ila, ƙabilai goma sha biyu na 'ya'yan Isra'ila, ƙabilai goma sha biyu
1 Sarakuna 2:9 1 Sarakuna 4;9 1 Sarakuna 5:10 1 Sarakuna 17:7 1 Sarakuna 18:13 1 Sarakuna 21:4 1 Sarakuna 48:13
Kalmar "aiki" nanufin yin aiki tuƙuru kuma kowanne iri ne. . Gaba ɗaya, aiki duk wani abu ne da yake bukatar ƙarfi. za a iya kuma cewa abunnan wahala ce. . Ma'aikaci shi ne mutumin da ke yin aikin. . A turance kalam "lebo" ana anfani da shi ace matsayin Naƙuda. Sauran yare zai zama dabam. . Yadda zamu fassara "lebo" zai haɖɖa da "aiki" "aikin wahala," "aikin tsanani," "yin aiki tuƙuru." (Duba kuma: wahala, lebo, zafi) Nasosin littafi mai tsarki: . 1 Tasalonikawa 02:09 . 1 Tasalonikawa 03:05 . Galatiyawa 04:10-11 . Yakubu 05:04 . Yahaya 04:38 . Luka 10:02 . Matiyu 10:10
. Ƙaƙƙarfa: H3018, H3021, H3022, H3205, H4522, H4639, H5447, H5450, H5647, H5656, H5998, H5999, H6001, H6089, H6468, H6635, G75, G2038, G2040, G2041, G2872, G2873, G4866, G4904
ƙarfi, ƙarfi, mai ƙarfi, ƙarfi, ƙarfi, ƙarfi, aiki, aiki, aikin zafi, zafin haihuwa, zafin haihuwar yara
"Sulaiman bai matsa wa mutanen Isra'ila aiki ba"
"su ɗari biyar da hamsin da biyar"
wa su am'anoni 1) "gina tsarin ɗakunan" ko kuma 2) "gina bolar" (UDB). duba yadda ka fassara "Millo" a 9:15.
An fassara shi 8:64.
Sulaiman wakili ne na mutanen da ya gayyato su yi aikin. AT: "ma'aikatansa sun gama aikin haikalin"
ya na da muhimnci a bayana cewa Sulaiman ba shi kaɗai ya gina haikalin ba mutane sun taimakeshi.
"ƙungiyar jiragen ruwa masu yawa"
Awo na nufin 34 kilogiram. AT:"kamar 14 kilogiram na zinariya"
1Sa'ad da sarauniyar Sheba ta ji labarin Suleman ya zama sananne game da sunan Yahweh, sai ta zo ta gwada shi da tambayoyi masu wuya.2Ta zo Yerusalem da raƙuma da yawa, da raƙuman da aka ɗorowa kayan yaji da zinariya mai yawa da duwatsu masu daraja da yawa. Sa'ad da ta zo sai ta gayawa Suleman dukkan abin da ke cikin zuciyarta.3Suleman ya amsa dukkan tambayoyinta. Ba wani abu da ta tambaya wanda Suleman bai ba da amsarsa ba.4Sa'ad da sarauniyar Sheba ta ga dukkan hikimar Suleman da fãdar da ya gina,5da abincin da ke kan teburinsa da wurin da bayinsa suke zama da ayyukan da bayinsa suke yi da tufafinsu, da masu yi ma sa hidima da yadda ya ke miƙa baye-baye na ƙonawa, sai ta zama ba ta da sauran ƙarfi.6Ta ce da sarki, "Rahoton da na ji a ƙasata game da maganarka da hikimarka gaskiya ne.7Ban gaskata da abin da na ji ba sai da na zo nan, yanzu idanuna sun gani. Ko rabin hikimarka da wadatarka ma ba a gaya mani ba! Sunanka ya wuce abin da na ji.8Matanka masu albarka ne, bayinka waɗanda suke tsayawa a gabanka kullum, masu albarka ne saboda suna jin hikimarka.9Yabo ga Yahweh Allahnka wanda ya yi farinciki da kai ya sa ka a bisa kursiyin Isra'ila. Saboda Yahweh ya ƙaunaci Isra'ila har abada ya sa ka zama sarki domin ka yi masu hukunci da adalci!"10Ta ba sarki awo 120 na zinariya da kayan yaji da yawa da duwatsu masu daraja. Ba a ƙara ba sarki Suleman kayan yaji masu yawa fiye da wanda sarauniyar Sheba ta ba shi ba.11Jiragen ruwa na Hiram da suka kawo zinariya daga Ofir, daga Ofir ɗin kuma sun kawo itacen almug mai yawa da duwatsu masu daraja.12Sarkin ya yi ginshiƙai na itacen almug a haikalin Yahweh da fãdar sarki, kuma ya yi wa mawaƙa molaye da girayu. Ba a ƙara ganin itacen almug da yawa haka ba har zuwa yau.13Sarki Suleman ya ba sarauniyar Sheba dukkan abin da ta nuna sha'awa a kai da dukkan abin da ta roƙa, ƙari a kan kyautar da ya riga ya ba ta saboda karamci. Sai ta koma ƙasarta tare da bayinta.14Nauyin zinariyar da ta zo wa Suleman a cikin shekara ɗaya awo 666 ne,15ban da zinariyar da "yan kasuwa da fatake suka kawo. Dukkan sarakunan Arebiya da hakiman ƙasar masu ka kawo wa Suleman zinariya da azurfa.16Sarki Suleman ya yi manyan garkuwoyi ɗari biyu na gogaggiyar zinariya. Kowaccen su an yi ta da awo ɗari shida na zinariya.17Ya kuma yi waɗansu garkuwoyi ɗari uku na gogaggiyar zinariya, awon zinariya uku suka shiga kowacce garkuwa; sarki ya sa su can cikin fadar da ta ke a jejin Lebanon.18Kuma sarki ya yi wani babban dakalin mulki na hauren giwa ya shafe shi da zinariya mafi kyau.19Dakalin yana da matakalai shida, bayan shi kuma shan ƙwai ne a can sama. Kowannen su yana da wurin ajiye hannu a gefe, akwai zakuna biyu a tsaye gefen wurin ajiye hannun.20Zakuna goma sha biyu suna tsaye a kan matakalun, ɗaya a kan kowacce matakala. Babu wata masarautar da take da dakali kamar sa.21Dukkan kofinan sha na sarki Suleman na zinariya ne, dukkan kofinan sha da suke fãdar da ke cikin jejin Lebanon na zinariya ne tsantsa. Ba na azurfa ko ɗaya domin a zamanin Suleman azurfa ba ta da daraja.22Sarki ya na da jiragen ruwa masu yawo a kan teku, tare da jiragen Hiram. Sau ɗaya a cikin shekara uku jiragen ruwan sukan kawo zinariya da azurfa da hauren giwa da buka da ɗawisu masu daraja.23Sarki Suleman ya fi dukkan sarakunan duniya arziki da hikima.24Kowa da kowa a duniya suna so su zo wurin Suleman domin su ji hikimar da Yahweh ya sa cikin zuciyarsa.25Waɗanda ke zuwa su na kawo haraji, na santulan azurfa da zinariya, da kayan sawa da sulke da kayan yaji da dawakai da alfadarai, shekara biye da shekara.26Suleman ya tara karusai da mahaya dawaki. Ya na da karusai 1400 da mahaya dawaki dubu goma sha biyu waɗanda ya ajiye su a biranen da a ka ajiye karusai shi kansa kuwa ya na cikin Yerusalem.27Sarki ya na da azurfa a Yerusalem kamar yawan duwatsun da suke a doron ƙasa. Yana da itatuwan sida da yawa kamar yadda itatuwan ɓaure suke a cikin fadama.28Suleman ya na da dawakai da aka kawo daga Masar da Kilikiya. Abokan cinikin sarki sukan saye su garke-garke kowanne garke bisa ga farashinsa.29Akan sayo karusai daga Masar kowacce akan awo ɗari shida na azurfa, dawaki kuma akan 150 kowanne. Akan sayar da wasu da yawa daga cikin su ga sarakunan Hittiyawa da Siriya.
Ma'ana mai yiwu wa 1) "Sulaiman ya yi sunan da ya kawo wa Yahweh ɗaukaka" 2) "sunan da Yahweh ya ba Sulaiman"
wanna na gaba ɗaya ne. AT: "dukkan abinda ya ke so ya sani"
ma'ana mai yiwu wa su ne 1) "yadda bayinsa suke zauna zagaye da teburin" ko 2) "in da bayinsa suke zama."
Habaici ne. AT: "ta yi mamaki sosai"
"na ji lokacin da nake a ƙasa ta"
A nan kalmar "hikima" na nufin kalmar "kalmar." AT: "maganarka ta hikima" .
Idon wakili ne na mutum. AT: "na gani"
wannan za a iya cewa da kuma faɗin shi. AT: "mutane sun gaya min kaɗan ne kawai"
Wannan habaici ne. AT: "waɗanda kullum su na gabanka domin su yi ma ka bauta"
Wannan ma iya cewa. AT: "bari mutune su yabi Yahweh Allahnka"
Kurisyin wakiline na sarki wanda ya ke zaune a kai. AT: "wanda ya mai she ka sarkin Isra'ila"
Awo ya kai 34 kilogiram. AT: "kamar 4000 kilogiram na zinariya" (Duba: trnaslate_bweight)
ma iya cewa 1) "ba wanda ya sake ba sarki kayan yaji kamar wanda sarauniya Sheba ta bashi"n
Ya na da kyau mu bayyana wa mai karatu cewa ba Sarki Sulaiman kaai ya yi aikin ba mutane sun taimakeshi. AT: "sarki ya nsa mutanen sa suka yi" AT: "Duba:"
wani irin itace ne, zai iya zaman mai ƙanshi sosai
za mu iya cewa. AT: "ba wanda ya ƙara ganin irin wannan yawan"
Wannan na nufin har zuwa rana da marubucin ke rubutu.
Waɗannan jimlolin na nufin abu ɗaya kuma aka haɗa su tare don a jaddada.
"saboda a matsayinsa na sarki yana da komai"
"kowacce shekara" (UDB). Wannan na nufin kowacce shekara ta mulkin Sulaiman, ba wai ga abu ɗaya ba.
Awo na nufin nauyin abu kamar 34 kilogiram. AT: "kusan 23000 kilogiram na zinariya"
yana da mahimmanci a bayayyawa mai karatu cewa Sulaiman ba shi kaɗai ya yi aikin ba mutane sun taimakeshi. AT: "mutanen Sarki SUlaiman sun yi"
"200 manya kariya"
Awo abin gwada nauyin ne ya kai kamar 11 giram. AT: "kamar 6.6 kilogiram na zinariya"
Saboda da kalmar "shekel" bai bayyana anan a Ibraniyanci ba, waɗansu juyi suna gani suke maimakon mu sa bekah, wanda shi ya yi dai-dai da rabin shekel. Duk juyin da yake wannan tsammani zai ba da lissafi dai-dai da kilogiram uku
yan ada kyau ma nuna wa mai karatu cewa Sulaiman ba shi kadai ya yi aikin ba waɗansu mutane sun taimakeshi. AT: "mutanen sarkin sun yi"
"300 garkuwa"
Awo na nufin nauyi kusan 600 giram. AT: "kusan 1.8 kilogiram na zinariya"
"Gidan wanda ake kiransa gidan jejin lebanon." an fassara shi a 7:1
ya na da kyau mu nuna wa mai karatu cewa sarki ba shi kaɗai ya yi aikin ba mutane sun taimakeshi. AT: "mutanen sarki su ka yi"
Hauren giwa abu mai ƙarfi ne, fari daga tozo ko kuma haƙorin wata dabba.
"gidan da ake kira gidan jejin lebanon." Fassararsa na 7:1
Hauren giwa abu mai ƙarfi ne, fari daga tozo ko kuma haƙorin wata dabba. An fassara shi a 10:18.
Waɗannan dabbobi na rayuwa jeji ne a afirica. A ƙarshen ƙafafunsu akwai abin da yake kamar hannun mutm da ƙafa, suna da bindi mai tsawo. Wasu mutane suna kwatanta gwaggon biri da tsulan biri.
Wanan gaba ɗaya ne. AT: "mutane na daga ko'ina" ko "mutane daga wuri dabam-dabam"
Zuwa wurin mutum wakili ne na samun zarafin yi wa mutum magana ko sauraronsa. AT: "su zo masu sauran Sulaiman" ko "su na son zuwa wa Sulaiman ziyara"
Zuciyar wakili ne na abinda mutum yake tunani yake kuma faɗa kamar ma'ajiyace. Wakilin suna "hikima" ana maganar sa kamar abinda za a iya sawa a ma'ajiya kuma za a iya fassara shi da mai kara armashi. Zai iya zama wakilin mutum ko kalmar da mutum ya faɗa. AT: "su ji hikimarsa, wadda Allah ya bashi" ko kuma "su ji yadda Allah ya mai she shi mai hikima" ko kum "su ji faɗar kalmomin hikima wanda Allah ya bashi"
"1,400 karusai da 12,000 mahaya"
Za mu iya cewa. AT: "da fatakensa su ka kawo daga masar"
Za mu iya cewa. AT: "fatakensa su ka sayo karusai"
Awo na nufin nauyin abu ne kusan 11 giram. AT: "kusan 6.6 kilogiram na azurfz ... kusan 1.7 kilogiram"
"600 awo na azurfa"
Za mu iya cewa. AT: "fatakensa suka sa suka sayar da waɗannan da yawa"
1Yanzu sarki Suleman ya kaunaci baƙin mata: ɗiyar Fir'auna, da matan Mowabawa, da Ammonawa da Idomawa da Sidoniyawa da Hittiyawa.2Su na daga al'ummai waɗanda Yahweh ya ce da mutanen Isra'ila, "Ba za ku shiga cikinsu ba da aure, ko su zo cikinku, domin lallai za su juyar da zukatanku ga allolinsu." Amma duk da wannan Suleman kuwa ya ƙaunaci waɗannan mata.3Suleman ya na da gimbiyoyin mata ɗari bakwai da kuma ƙwaraƙwarai ɗari uku. Matayensa su ka juyar da zuciyarsa.4Gama sa'ad da Suleman ya tsufa, sai matansa su ka juyar da zuciyarsa zuwa bin wasu alloli; bai miƙa dukkan zuciyarsa ga Yahweh Allahnsa ba, kamar zuciyar Dauda mahaifinsa.5Gama Suleman ya bi Ashtoret, gunkin Sidoniyawa, ya kuma bi Molek, wato gunkin Ammonawa.6Suleman ya yi abin da ke mugu a fuskar Yahweh; bai bi Yahweh da zuciya ɗaya ba, ba kamar yadda mahaifinsa Dauda ya yi ba.7Sai Suleman ya gina masujadai domin Kemosh, kyamattacen gunkin Mowab, akan dutsen gabashin Yerusalem, da kuma domin Molek, da kyamataccen gunkin mutanen Amonawa.8Ya kuma gina masujadai domin dukkan baƙin mata, waɗanda su ke ƙona turare da hadayu ga allolinsu.9Yahweh kuwa ya yi fushi da Suleman, domin zuciyarsa ta rabu daga gare shi, Allah na Isra'ila, ko da ya ke ya bayyana a gare shi sau biyu,10ya kuma umarce shi akan wannan abu, da kada ya bi wasu allolin. Amma bai yi biyayya da wannan umarni na Yahweh ba.11Saboda haka Yahweh ya ce da Suleman, "Domin ka yi wannan ka kuma ƙi kiyaye alƙawari da ka'idodina waɗanda na umarceka, hakika zan tsaga mulkin daga gare ka in ba baranka.12Amma, saboda mahaifinka Dauda, ba zan yi ba a lokacin rayuwarka, amma zan tsaga ta daga hannun ɗanka.13Duk da haka ba zan ƙwace dukkan mulkin ba, zan ba kabila ɗaya ga ɗanka, saboda bawana Dauda, don kuma Yerusalem, wanda na zaɓa."14Sai Yahweh ya ta da abokin gãba ga Suleman, Hadad Ba'idome. Shi kuma daga iyalin sarautar Idom ne.15Gama sa'ad da Dauda yana cikin Idom, Yowab shugaban sojoji ya tafi don ya bizne matattu, kowanne mutum wanda aka kashe a Idom.16Yowab da dukkan Isra'ila su ka tsaya a Idom wata shida har sai da ya kashe mazajen Idom.17Amma an ɗauki Hadad tare da wasu Idomawa ta wurin bayin mahaifinsa zuwa Masar, tun lokacin da Hadad yana karamin yaro.18Su ka bar Madayana su ka zo Faran, daga nan su ka ɗauki mutane tare da su zuwa Masar, wurin Fir'auna sarkin Masar, wanda ya ba shi gida da kuma ƙasa da abinci.19Hadad kuwa ya sami tagomashi ƙwarai a fuskar Fir'auna, saboda haka Fir'auna ya bashi mata, ƙanwar matarsa, wato ƙanwar Tafenes sarauniya.20'Yar'uwar Tafenes ta haifa wa Hadad ɗa. Suka sa masa suna Genubat. Tafenes ta yi renon sa a fadar. Genubat ya zauna a fadar Fir'auna a cikin yaran Fir'auna.21A lokacin da ya ke a Masar, Hadad ya ji labari Dauda ya rasu aka kuma rufe shi tare da kakanninsa, Yowab shugaban sojoji kuma ya mutu, sai Hadad ya cewa Fir'auna, "Ka yardar mani in tashi, in koma ƙasata."22Sai Fir'auna ya ce masa, "Amma me ka rasa a nan har da ka ke neman komawa ƙasarka?" Hadad ya amsa, "Ba bu kome, idan ka yarda bar ni in koma.23Allah kuma ya ta da wani abokin gãba ga Suleman, Rezon ɗan Eliyada, wanda ya zo daga wurin maigidansa Hadadezar sarkin Zobah.24Rezon ya tattaro wa kansa mutane har ya zama shugaba akan kananan mayaƙa, bayan da Dauda ya ci nasara akan mutanen Zobah. Rezo ya mulki Damaskus.25Ya zama abokin gãbar Isra'ila dukkan kwanakin Suleman, tare da wahalar da Hadad ya kawo. Rezon ya ƙi mutanen Isra'ila ƙwarai, ya yi mulkin Aram.26Sai Yerobowam ɗan Nebat, Ba'ifraime na Zeredan, ma'aikacin Suleman ne, wanda sunan mahaifiyarsa Zeruya, wadda mijinta ya rasu, shi ma ya tayar wa sarki.27Dalilin da ya sa ya tayar wa sarki shi ne domin Suleman ya gina masujada a Millo ya kuma gyara garun birnin Dauda mahaifinsa.28Yerobowam ƙaƙƙarfan mutum mai fasaha. Suleman ya ga saurayi ne mai himma, sai ya sa shi shugabanci akan dukkan aikin gidan Yosef.29A wanan lokacin, sai Yerobowam ya fita daga Yerusalem, annabi Ahijah mutumin Shilo ya same shi a hanya.30Yanzu kuwa Ahijah ya na saye da sabuwar riga tare da mutune biyu kaɗai a filin. Sai Ahijah ya kama sabuwar rigar da ya sa, ya kyakketa kashi goma sha biyu.31Ya cewa Yerobowam, "Ɗauki kyalle goma, gama haka Yahweh, Allahn Isra'ila, ya faɗa, 'Duba, zan yaga mulkin daga hannun Suleman zan kuma ba da kabilu goma a gare ka32(amma Suleman zai sami kabila ɗaya, saboda bawana Dauda, ɗaya kuma saboda Yerusalem - birnin da na zaɓa daga cikin dukkan kabilan Isra'ila),33domin sun rabu da ni su na bauta wa Ashtoret gunkiyar Sidoniyawa, Kemosh allahn Mowab, da Milkon allahn mutanen Ammonawa. Ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ko su yi abin da ke dai-dai a idanuna da kiyaye dokokina da ka'idodina, kamar yadda Dauda mahaifinsa ya yi.34Duk da haka ba zan ɗauke dukkan mulkin daga hannun Suleman ba. A maimakon haka zan sa shi ya yi mulki dukkan kwanakin rayuwarsa, saboda bawana Dauda wanda na zaɓa, wanda ya kiyaye umarnina da dokokina.35Amma zan ɗauke mulkin daga hannun ɗansa, zan ba da shi gare ka, kabilu goma.36Zan ba da kabila ɗaya ga ɗan Suleman, saboda bawana Dauda wanda kullum yana riƙe fitila a gabana a Yerusalem, birnin da na zaɓa in sa sunana.37Zan ɗauke ka, za ka yi mulki ka cika dukkan buƙatarka, kuma za ka zama sarki akan Isra'ila,38Idan za ka saurari dukkan abin da zan umarce ka, idan kuma ka bi hanyata ka yi abin da ke dai-dai a idanuna, ka kiyaye dokokina da umarnina, kamar yadda Dauda bawana ya yi, sai in kasance tare da kai zan sa gidanka ya kahu, kamar yadda na sa gidan Dauda, zan ba da Isra'ila a gare ka.39Zan hori zuriyar Dauda, amma ba har abada ba."40Suleman kuwa ya yi ƙoƙarin kashe Yerobowam. Amma Yerobowam ya tashi ya tsere zuwa Masar, wurin Shishak sarkin Masar, ya zauna a can har mutuwar Suleman.41Kamar sauran abubuwa game da Suleman, dukkan abin da ya yi da hikimarsa ba a rubuta su a littafin ayyukan Suleman ba?42Suleman ya yi mulki a Yerusalem akan dukkan Isra'ila har shekaru arba'in.43Ya mutu tare da kakaninsa kuma aka bizne shi a birnin Dauda mahaifinsa. Rehobowam ɗansa ya zama sarki a gurbin mahaifinsa.
Waɗanan sunan mutane.
Kalmar "yanzu" anyi amfani dashi a nuna tsaiko daga asalin labarin inda mai bada labirin ya fara wani ɓangaren na labarin.
A "juya zuciyar wani" shine a gamsar da don ya chanza ra'ayinsa.AT: "a juyar da kai ka bautawa allolinsu"
"700 gimbiyoyi da kuma 300 ƙwarƙwarai" (Duba: trnsalate_numbers)
A "juyar da zuciyar wani" shine a gamsar da wani ya canza ra'ayinsa. AT: "juyar da zuciyarsa daga Yahweh" ko kuma "ja ra'ayinsa ya daina bautawa Yahweh"
A "miƙa" zuciyarka na nufin bayar da dukkan biyayya da mika kai. AT: "bai mika kai gaba ɗaya ba ... kamar Dauda"
Waɗannan sunan allolin ƙarya ne.
Wannan sunan ƙungiyar mutane ne. (Duba: trnaslate_names)
Jimlar "a gaban" na nufin ra'ayin wani. AT>~: "abinda Yahweh ya ke ganin muguntane"
"Milkom" wani sunan gunkin ne a turance "Molech."
Waɗannan sunan allolin ƙarya ne.
A nan kalmar "ga su" na nufin ɗakin gunki da Sulaiman ya gina
Kalmar "zuciyarsa ta juye" na nufin ya daina mika kai da kuma yin biyayya. AT: "Sulaiman ya daina yi wa Yahweh sujada"
"Yahweh ya bayyana ga Sulaiman har sau biyu"
A "tsaga" shine a cire abu da ƙarfi. Wannan kamar mutum ya yaga yankin kaya. AT: "zan ɗauke mulkin daga gare ka da ƙarfi"
Kalmar "hannu" na nufin mai iko, iko, da kuma ƙarfin mulki. AT: "ikon ɗanka"
Wannan suna na miji ne.
Wannan tunani abu da ya faru a baya.
Kalmar "dukkan Isra'ila" na nufin sojojin Isra'ila. AT: "Yowab da dukkan sojojin Isra'ila"
Wannan ma iya cewa. "amma bayin mahaifin Hadad suka ɗauke shi tare da wasu Edomawa"
Wannan ɓangaren ya ci gaba da bayanai na baya wanda ya faru a 11:14.
Kalmar "su" ta na nufin Hadad da sauran Edomawa kamar yadda aka faɗi a 11:14.
Wannan sunan wurare ne.
Wannan sunan mace ne.
Wannan sunan mace ne.
Wannan sunan maza ne.
Wannan wata hanya ce ta cewa Dauda ya mutu. AT: "Dauda ya mutu"
Wannan sunan mutane ne.
Wannan sunan wurare ne.
"Dauda" na nufin dukkan ƙarfin Dauda. AT: "lokacin da sojojin Dauda suka ci yaƙi"
A nan kalmar "kwanaki" na nufin wasu lokuta da kuma "Sulaiman" na nufin dukkan abubuwan da suke a ƙarƙashin ikonsa. AT: "dukkan lokacin da Sulaiman ya ke da iko"
"Rezon ya ƙi mutanen Isra'ila kwarai da gaske"
Wannan sunan mazaje ne.
Wannan sunan wurare ne.
Wannan sunan mace ne.
Kalmar "hannu" na nufin iko, ƙarfin iko, mai iko dukka. Jimlar "tayar wa" na nufin ƙin wani ta wurin yi amfani da iko, ƙarfin iko da kuma dukkan iko. Wannan wakiline da ake amfani dashi a matsayin habaici. AT: "tayarwa mulkin"
An fassara "Millo" a 9:15.
wasu ma'anoni 1) "babban mayaƙi" ko kuma 2) "mutumin da zai iya" (UDB) ko kuma 3) "mutum mai kuɗi da kuma tasiri"
"ya maishe shi shugaba"
Kalmar "aiki" na nufin dukkan aikin da Sulaiman ya sa mutane su yi domin gwamnatinsa. Wannan wakili ne.
Wanan na nufin zuriyar Yosefwaɗanda sune mutane na ƙabilar Ifraimu da Manasa. Wannan wakili ne.
Wannan suna na miji ne.
Shilonawa ƙungiyar mutane ne.
A nan kalmar "shi" na nufin Ahijah.
A ana "yaga ... daga" wakili ne da yake nuna cire abu da ƙarfi. Wannan ya na kama da mutun ya kama yanki kaya ya yaga. AT: "ka cire mulkin da ƙarfi" Duba yadda aka fassara shi a 11:11.
A nan "hannu" waakili ne da ke nuni da iko, dukkan iko, da kuma ƙarfin iko. AT: "ƙarfin ikon Sulaiman"
Sunan "Sulaiman" anan wakili ne na zuriyarsa. AT: "'ya'yan Sulaiman za su samu" ko kuma "zuriyar Sulaiman za su samu"
"Ido" anan wakili ne na ra'ayi ko batu na wani. Wannan habaici ne da ake yinsa sosai. AT: "abin da nake ganin sa dai-dai ne"
Waɗannan sunan allolin ƙarya ne.
Ahijah ya ci gaba da gayawa Yerobawam abinda Yahweh yace.
A nan kalmar "Ni" na nufin Yahweh.
A nan kalmar "hannu" wakili ne na ikon, ƙarfin iko, da kuma dukkan iko. AT: " da ga ƙarfin ikon Sulaiman"
A nan kalmar "kai" na nufin Yerobawam.
Kalmar "fitila" wakili ne da yake nufin tasirin wani da jagoranci. AT: "kullum zan sami zuriyar da zai yi mulki a matsayin mai tasiri da kuma mai jagoranci don a kiyaye dokokina tare da iyalan Dauda"
Ahijah ya ci gaba da gaya wa Yerobawam abin da Yahweh ya ce.
A nan kalmar "zan" na nufin Yahweh da kuma "ka" na nufin Yerobawam.
Kalmar "Ido" wakili ne na ra'ayi da batu na wani. wannan habaici ne da aka fi amfani da shi. Ka san yadda zaka fassara wannan a 11:31.
rabin zancen nan "gina gida" wakili ne na kafa zuriya daga wannan lokacin. AT: "zan kafa maka mulki mai dauwama"
Wannan sunan na miji ne.
za a iya maganan wannan a aiki da kuma sa ran amsa ɗin ya zama mai kyau. Tambaya ɗin ma bata buƙatar amsa kuma ana amfani da ita a jaddada abu. AT: "za ku iya samun su a littattafan ayyukan Sulaiman."
1Rehobowam ya tafi Shekem, domin dukkan Isra'ila sun tafi Shekem su maida shi sarki.2Ya zamana sa'ad da Yerobowam ɗan Nebat ya ji wannan (domin shi yana Masar, inda, ya gudu daga gaban sarki Suleman), don Yerobowam ya na zaune a Masar.3Sai su ka aika a kirawo shi, Yerobowam tare da dukkan taron mutanen Isra'ila suka zo suka ce da Rehobowam,4'"Mahaifinka ya nawaita mana. Yanzu sai ka rage mana wahalar aikin da tsohonka ya nawaita a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka."5Yerobowam ya ce da su, "Ku tafi har nan da kwana uku, sai bayan kwana uku ku dawo wuri na." Sai mutanen su ka tafi.6Sarki Rehobowam kuwa ya yi shawara tare da dattawa waɗanda suka tsaya tare da Suleman mahaifinsa a lokacin da ya ke da rai, sai ya ce masu, "Wacce shawara za ku ba ni don in amsa wa mutanen nan?"7Su ka yi magana da shi, suka ce, "Idan za ka zama bara yau ga waɗannan mutane sai ka bauta masu, ka kuma amsa masu da magana mai kyau, su kuwa kullum za su zama barorinka."8Amma Rehobowam ya yi watsi da shawarar da dattawan mutanen su ka ba shi, sai ya yi shawara tare da matasan mutane waɗanda su ka yi girma tare da shi.9Ya ce masu, "Wacce shawara za ku ba ni don in amsa wa mutanen nan da suka yi magana da ni cewa, 'Ka rage wahalar da tsohonka ya aza mana?'"10Matasan waɗanda su ka yi girma tare da Rehobowam su ka yi magana da shi, cewa, "Yi magana da mutanen nan waɗanda suka faɗa maka mahaifinka Suleman ya nawaita masu amma sai kai ka sauwaƙa masu. Sai ka ce da su, 'Karamin yatsana ya fi ƙugun mahaifina kauri.11To yanzu, ko da mahaifina ya wahalar da ku da bauta, zan ƙara maku nawayar. Mahaifina ya hore ku da bulala, amma ni zan hore ku da kunamai.'"12Sai Yerobowom da dukkan mutane suka zo wurin Rehobowom a rana ta uku, kamar yadda sarki ya umarta a lokacin da ya ce, "Ku dawo wurina a rana ta uku."13Sarki ya amsa wa mutanen da zafi, ya kuma yi watsi da shawarar da dattawa suka ba shi.14Ya yi masu magana bisa ga shawarar matasa; ya ce, "Mahaifina ya nawaita maku, amma ni zan ƙara nawaita maku. mahaifina ya yi maku horo da bulala, amma ni zan yi maku da kunamai."15Haka nan kuwa sarki bai saurari mutanen ba, gama wannan al'amarin ya zama haka bisa ga shirin Yahweh, akan yadda zai cika maganar da ya faɗa ta wurin Ahijah Bashiloniye zuwa ga Yerobowom ɗan Nebat.16Sa'ad da dukkan mutane Isra'ila suka ga sarki bai saurare su ba, sai mutanen suka amsa masa suka ce, "Mene ne rabonmu da Dauda? Ba mu da gãdo a cikin ɗan Yesse! Ku tafi rumfunanku, Isra'ila. Yanzu ka duba gidanka, Dauda." Isra'ila suka koma rumfunansu.17Amma mutanen Isra'ila waɗanda suka zauna a biranen Yahuda, Rehobowom ya zama sarkinsu.18Sai sarki Rehobowom ya aiki Adoniram, wanda ya ke shi ne shugaban aikin tilas, amma dukkan Isra'ila suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu. Sarki Rehobowom da gaggawa ya hau karusarsa ya tsere zuwa Yerusalem.19Mutanen Isra'ila kuwa suka tayar wa gidan Dauda har zuwa wannan rana.20Ya zama haka dukkan Isra'ila suka ji Yerobowom ya komo, sai suka aika a kirawo shi ga taron, suka naɗa shi sarki akan dukkan Isra'ila. Babu wanda ya bi iyalin Dauda, sai dai kabilar Yahuda.21Da Rehobowom ya komo Yerusalem, ya tara dukkan mutanen gidan Yahuda da kabilar Benyamin; suka kai mayaƙa 180,000 mutanen da aka zaɓa sojoji, da za su yi faɗa gãba da gidan Isra'ila, domin su komar da su a ƙarƙashin mulkin Rehobowom ɗan Suleman.22Amma maganar Allah ta zo ga Shemayya, mutumin Allah; ta ce,23"Faɗa wa Rehobowom ɗan Suleman, sarkin Yahuda, da Benyamin da sauran jama'a, ka ce,24"Yahweh ya ce wannan: Ba za ka yi yaƙi ko faɗa da 'yan'uwanku mutanen Isra'ila ba. Kowannenku ya koma gidansa, gama wannan al'amari ya faru ne daga gare ni.'" Sai suka saurari maganar Yahweh, suka juya suka koma hanyarsu, suka yi biyayya da maganarsa.25Sai Yerobowom ya gina Shekem a ƙasar tudu ta Ifraim, ya zauna a can. Ya fita daga can ya gina Feniyel.26Yerobowam kuwa ya yi tunani a cikin zuciyarsa, '"Yanzu mulki fa zai koma gidan Dauda.27Idan waɗannan mutanen suka ci gaba da miƙa hadiyu a haikalin Yahweh a Yerusalem, sai zuciyar waɗannan mutane su juya su yi gãba da maigidansu, Reroboam sarkin Yahuda. Za su kashe ni su koma wurin Rehobowom sarkin Yahuda."28Sai sarki Yerobowom ya nemi shawara ya siffanta 'yan maruka biyu da zinariya; ya cewa mutane, "Zai yi maku wuya don ku yi ta tafiya zuwa Yerusalem. Duba, ga waɗannan allolinku, ya Isra'ila, waɗanda suka fito da ku daga ƙasar Masar."29Ya sa siffar ɗaya a Betel ɗaya kuma a Dan. Wannan abu ya zama zunubi.30Mutane suka tafi wurin ɗaya ko ɗayan, dukka suka kama hanya zuwa Dan.31Yerobowom ya gina masujadai a tuddai, ya kuma sa firistoci a cikin dukkan mutanen, waɗanda ba 'ya'yan Lebi ba.32Yerobowom kuma ya sa a yi idi a watan takwas, ran goma sha biyar ga wata, kamar yadda ake yin idi a Yahuda, ya tafi bagadi. Ya yi kuma a Betel, hadayun siffofin maruƙan da ya yi a Betel ya sa firistoci a masujadan da ya gina.33Yerobowom ya tafi gaban bagaden da ya gina a Betel a rana ta goma sha biyar ga wata na takwas, a watan ya shirya a tunaninsa; ya yi biki don mutanen Isra'ila ya kuma tafi bagade ya ƙona turare.
A nan "Isra'ila" wakili ne na mazajen Isra'ila da zasu iya yaƙi. "dukkan Isra'ila" fifita su ne waddan yake nufin kusan dukkan mazajen Isra'ila. AT: "dukkan mazajen Isra'ila za su zo"
Wannan jimlar ana amfani da shi a fara in da aikin ya fara. Idan harshen ka yana da yadda za a sa shi, sai ka yi amfani da shi
Waɗannan sunan mazaje ne.
A nan kalmar "shi" na nufin Yerobawam.
Kayan mai nauyi wakili ne na aiki mai wahalar gaske da kuma neman wani abu. AT: " bamu wahala sosai" ko kuma "matsa maana muyi aiki da wahala kwarai"
A "tsaya a gaban" habaici ne na bautawa sarki a gabansa. AT: "dattawan da suka ba Sulaiman shawara" ko kuma "dattawan da suka saurari Sulaiman"
A "rage wahala" wakili ne da yake nufin ɗauke nauyi. AT: "kada ka wahalshe mu yadda mahaifinka yayi" ko kuma "kada ka matsa mana aikin dole yadda mahaifinka yayi"
Wannan na nufin Yerobawam ya fi mahifinsa tsanani da razanarwa. AT: "abin da zan yi in maida kayanku ya ƙara nauyi zan yi"
Wannan wakilin ma nufa shirin Yerobawam na musguna wa mutanen yafi abin da mahaifinsa ya yi. AT: " Mahaifina ya hore ku da bulala, amma ni zan hore ku da hukunci mafi tsanani"
Kalmar "kunama" na nufin 1) saƙa da ƙarfe mai tsini aski a ƙarshe 2) wani halitta kamar gizo-gizo da yake da dafi mai tsanani
Kaya mai nauyi wakili ne na aikin wahala da kuma danginsu. Duba yadda aka fassara su a 12:3. AT: "ya wahallshe ku" ko kuma "ya matsa maku aikin dole"
Wannan wakilin ma nufa shirin Yerobawam na musguna wa mutanen yafi abin da mahaifinsa ya yi. Kamar yadda yake a 12:10 AT: " Mahaifina ya hore ku da bulala, amma ni zan hore ku da hukunci mafi tsanani"
Wannan habaici ne kuma zamu iya sa shi a aikatau. AT: "Yahweh yasa abubuwa su faru haka"
Waɗannan sunan mazajene.
wannan suna ƙungiyar mutane ne na garin Shiloh.
A nan "Isra'ila" wakili ne na dukkan mutanen Isra'ila da zasu iya yin yaƙi. "dukkan Isra'ila" mafifinci ne wanda yake nuna dukkan mutanen Isra'ila. AT: "dukkan mutanen Isra'ila"
"Rabo" wakili ne ma'ana abinda wani zai samu. Wannan tambayar za'a iya fassara shi a saukaƙe. AT: "ba mu da rabo a iyalin Dauda."
"Ɗan Yesse" wakili ne na Dauda, ɗan Dauda. "gãdo" wakili ne na mutanen da suka rage a gidan Dauda. AT: "ba abin da zamu yi da zuriyar Yesse (Duba:"
"Rumfuna"wakili ne na nuna wurin zaman wani. AT: "ku koma gidanku mutanen Isra'ila"
"gida" wakili ne na Ikon Dauda. AT: "yanzu ka kula da mulkinka, zuriyar Dauda"
wannan sunan na miji ne.
A nan "Isra'ila" wakili ne na dukkan mutanen Isra'ila da zasu iya yin yaƙi. "dukkan Isra'ila" mafifinci ne wanda yake nuna dukkan mutanen Isra'ila. AT: "dukkan mutanen Isra'ila"
A nan "gida" wakili ne na iyalin Dauda. AT: "sarkin ya sauka daga Dauda"
"yau" wakili ne na wasu lokutai, lokaci. A nan yana nuna lokacin da mai rubutun yake rubutawa. AT: "zuwa lokacin mai rubutu"
Wannan jimlar an yi amfani da ita a fara farkon wani labari mai muhimmanci. idan yarenku yana da wata hanya tayin haka, za ku iya yi amfani da shi anan.
"dukkan Isra'ila" wannan fifita abu ne don ace dukkan mazajen da suka isa su wakil ci sauran jama'ar. AT: "da dukkan shugabannin Isra'ila su ka ji"
"Isra'ila" na nufin kudancin ƙabilai goma da suka yi wa Yerobawam tawaye. AT: "sarkin dukkan ƙabilu goma na Isra'ila"
"zuriyar Dauda"
A nan "gida" wakili ne na ƙabila ko kuma zuriya. Anan "ƙabila" na magana ne musamman da sojojin da suke cikin wannan ƙabila. AT: "dukkan sojoji daga ƙabilar Yahuda da Benyamin"
"Isra'ila" na nufin kudancin ƙabilai goma da suka yi wa Yerobawam tawaye. AT: "sarkin dukkan ƙabilu goma na Isra'ila"
Wannan habaici ne da ake amfani da shi a faɗi abin da Allah ya ce wa annabawan sa ko mutanensa. AT: "Alla ya ba wannan saƙo ya ce" ko kuma "Allah faɗi waɗannan kalmomi ... ya ce"
wannan sunan na miji ne.
Maganar "mutumin Allah" hanya ce mai bangirma ta kira annabin Yahweh. AT: "mutumin Allah" ko kuma "annabin Allah"
"gida" wakili ne na zuriyar Yahuda. AT: "dukkan mutane daga ƙabilar Yahuda da benyamin"
Kalmar ";yanuwa" da "mutane" su abu biyu ne da su ke nufin mazaje daga ƙabilai goma na arewaci ya kuma jaddada dangantaka ta iyali tsakaninsu da ƙabilar Yahuda da Benyamin.
za a iya ce wa wannan AT: "saboda na maida wannan abin ya faaru"n (Duba:activepassive)
"Zuciya" wakili ne na laamiri na ciki na mutum, tunani, izawa ko abin da ya ji. AT: "tunani cikin zuciyarsa"
A nan "gida" wakili ne na iyali ko zuriya. AT: "sarki ya tashi daga Dauda"
Kalmar "waɗannan mutane" na nufin mutanen arewacin ƙabilu goma na ISra'ila.
"zuciya" wakili ne na biyayya da ƙauna . AT: "biyayyar waɗannan mutane"
Wannan jimlolin na nufin abu ɗaya an haɗa su ne domin a jaddada tsoron Yeroboam don mutanen zasu juya wurin shi a matsayin sarki.
"ku" wakili ne na kakannin mutanen. AT: "kawo kakanninku"
Ma'aikatan da suka yi wannan bisa ga umarnin Yeroboam an nuna su a wakilin na sunan Yeroboam da kansa. AT: "ma'aikatan Yeroboamsun gina gidaje a tuddai"
Wanan bayanin yana magana cewa gidajen gidan sujada ne. ma'anar wannan maganar zai zama. AT: "gidajen sujada a kan tuddai"
"ya naɗa mazaje su zaman firist"
wannan wata na takwas na kalandar Ibraniyawa. Kwana na goma sha biyar kusa da farko nowamba a kalandar turawa. AT: "a kwana na goma sha buyar na watan takwas"
"su ka je" habaici ne na zuwa wuri mai tsarki su yi sujada tunda alfarwar an yi ta ne akan tuddai. AT: "mika hadayu akan alfarwar"
"su ka je" habaici ne na zuwa wuri mai tsarki su yi sujada tunda alfarwar an yi ta ne akan tuddai. AT: "mika hadayu akan alfarwar"
"a watan ya shrya"
1Mutumin Allah ya fito daga Yahuda ta wurin maganar Yahweh zuwa Betel. Yerobowom yana tsaye kusa da bagadin ƙona turare.2Ya yi kuka akan wannan mugunta ta bagadi ta wurin maganar Yahweh: "Bagadi, bagadi! Wannan shi ne abin da Yahweh ya fada, 'Duba, mai suna Yosiya za a haife shi a iyalin Dauda, da kai zan yi hadayun firistoci na masujadan tuddai waɗanda za su ƙona turare a kanka. A kanka kuma za su ƙona ƙasusuwan mutane.'"3Sai mutumin Allah ya ba da alamar ranar, cewa, "Wannan shi ne alamar da Yahweh ya yi magana: 'Duba, za a rushe bagadin, za a kuma watsar da tokar waje.'"4Da sarki ya ji abin da mutumin Allah ya ce, sai ya yi kuka akan bagadin da ya ke Betel, Yerobowam ya miƙa hannunsa daga bagadin, cewa, "Ku kama shi. "Sai hannun da ya miƙa akan mutumin ya bushe, domin bai iya komo da shi ba.5(Aka rushe bagadin aka kuma zubar da tokar bagadin, alamar da mutumin Allah ya ba da bisa ga maganar Yahweh.)6Sarki Yerobowom ya amsa ya ce da mutumin Allah, "Ka yi roƙo domin in sami tagomashi a wurin Yahweh Allahnka kuma ka yi addu'a domina, saboda ya warkar da hannuna." Mutumin Allah ya yi addu'a ga Yahweh, hannun sarki kuwa ya dawo gare shi kuma, dai-dai kamar yadda ya ke a dã.7Sarki ya ce da mutumin Allah, "Ka zo gida tare da ni ka shakata, zan ba ka lada."8Mutumin Allah kuwa ya ce da sarki, "Ko da za ka ba ni rabin mallakarka, ba zan tafi tare da kai ba, ko in ci abinci ko in sha ruwa a wannan wurin ba,9gama Yahweh ya umarce ni ta wurin maganarsa, 'Ba za ka ci gurasa ko ka sha ruwa, ko ka koma ta hanyar da ka zo ba.'"10Haka kuwa mutumin Allah ya koma ta wata hanya dabam zuwa gidansa ba ta hanyar da ya zo Betel ba.11To akwai wani tsohon annabi wanda ke zaune a Betel, ɗaya daga cikin 'ya 'yansa maza ya tafi ya faɗa masa dukkan abubuwan da mutumin Allah ya yi a wannan rana a Betel. 'Ya'yansa kuwa suka faɗa wa mahaifinsu maganar da mutumin Allah ya faɗa wa sarki.12Mahaifinsu ya ce da su, "Wacce hanyar ya bi ya tafi?" 'Ya'yansa sun ga hanyar da mutumin Allah daga Yahuda ya bi ya tafi.13Ya ce da 'ya'yansa ku ɗaura wa jaki shimfiɗa domina." Sai suka ɗaura wa jaki shimfiɗa, shi kuwa ya hau ya tafi.14Tsohon annabin ya bi bayan mutumin Allah har ya same shi yana zama a ƙarƙashin itacen rimi; ya ce masa, "Kai ne mutumin Allahn nan da ya zo daga Yahuda?" Ya amsa, "I, ni ne."15Sai tsohon annabi ya ce da shi, "Zo gida tare da ni ka ci abinci."16Mutumin Allah ya amsa, ba zan koma tare da kai ba ko kuwa in shiga tare da kai, ko kuwa in ci abinci ko in sha ruwa tare da kai a wannan wuri,17gama umarni gare ni ta wurin maganar Yahweh, 'ba za ka ci wani abinci ko ka sha ruwa a wurin ba, ko ka koma ta hanyar da ka zo.'"18Sai tsohon annabin ya ce da shi, "Ai ni ma annabi ne kamar ka, mala'ika ya yi magana da ni ta wurin maganar Yahweh, cewa, 'Ka zo da shi tare da kai cikin gidanka, don ya ci abinci ya sha ruwa.'" Amma ƙarya ce tsohon annabin ya ke faɗa wa mutumin Allah.19Saboda haka sai mutumin Allah ya koma tare da tsohon annabi ya ci abinci ya kuma sha ruwa a gidansa.20Ya yin da suka zauna a tebur, sai maganar Yahweh ta zo ga annabi wanda ya komo da shi,21sai ya kira mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda, cewa, "Yahweh ya ce, 'Domin ka yi rashin biyayya da maganar Yahweh, ba ka kuma kiyaye umarnin Yahweh Allahnka da ya ba ka ba,22amma ka komo ka ci abinci ka sha ruwa a wannan wurin wanda Yahweh ya faɗa ma ka kada ka ci abinci ko kuwa ka sha ruwa, saboda haka ba za a bizne jikinka a kabarin ubanninka ba.'"23Bayan da ya ci abinci, ya kuma sha, sai annabin ya ɗaura wa jakin mutumin Allah sirdi, da kuma mutumin da ya komo tare da shi.24Sa'ad da mutumin Allah ya tafi, sai zaki ya gamu da shi a hanya ya kashe shi, ya bar gawar akan hanya. Sai jakin ya tsaya a gefenta, haka nan ma zaki ya tsaya kusa da gawar.25Sa'ad da mutane da ke wucewa ta wurin suka ga an yar da gawar akan hanya, zaki kuma ya tsaya a gefenta, suka zo suka faɗa a cikin birnin da tsohon annabi ya ke.26Sa'ad da annabi wanda ya komo da shi daga hanyar ya ji, sai ya ce, "Wannan mutumin Allah ne wanda bai yi biyayya da maganar Yahweh ba. Saboda haka Yahweh ya ba da shi ga zaki, wanda ya yayyage shi, ya kuma kashe shi, kamar yadda maganar Yahweh ta gargaɗe shi."27Sai tsohon annabi ya yi magana da 'ya 'yansa maza, cewa, "Ku ɗaura wa jakina sirdi," su kuma suka ɗaura wa jakin sirdi.28Ya tafi ya sami gawar an bar ta a hanya, jakin da zaki su na tsaye a gefen gawar. Zaki bai ci gawar ba, ko ma ya farma jakin.29Annabin ya ɗauki gawar mutumin Allah, ya ɗora ta akan jaki, ya komo da ita. Ya zo da ita birninsa ya yi makoki ya bizne shi.30Ya bizne gawar a cikin kabarinsa, suka yi makoki domin sa, cewa. "Kaito, ɗan'uwana!"31To bayan da ya bizne shi, tsohon annabin ya faɗa wa 'ya'yansa maza, cewa, "Sa'ad da na mutu, ku bizne ni a cikin kabari inda aka bizne mutumin Allah. Ku sa ƙasusuwana a kusa da nasa.32Gama an furta saƙon maganar Yahweh, a bagadin da ke Betel da kuma dukkan gidajen da ke kan tuddai a biranen Samariya, abin da lallai zai faru."33Bayan wannan Yerobowom bai juyo daga muguwar hanyarsa ba, amma ya naɗa firistoci don masujadai da ke kan tuddai a cikin dukkan mutane. Duk wanda ya ke so sai ya karɓe shi a matsayin firist.34Wannan abu ya zama zunubi ga iyalin Yerobowam ya yi dalilin da aka hallaka iyalinsa aka kuma shafe su kakaf daga fuskar duniya.
Maganar anan shine Yahweh ya aiki mutumin Allahn zuwa Betel. wannan ma iya ceaw. AT: "Yahweh ya aiki mutumin Allah daga Yahuda zuwa Betel"
wannan wani laƙabi ne na annabi. AT: "Annabi"
"zo daga Yahuda"
A nan "furci" na nufin saƙon Yahweh. AT: "saƙon yahweh"
A nan "shi"na nufin mutumin Allah.
Annabin ya yi magana akan bagadin kamar mutum ne wanda zai iya jin shi. Ya faɗi haka sau biyu domin ya jadddada.
A nan "iyalin Dauda" na nufin zuriyar Dauda. Zamu iya ƙara mashi armashi mu ce AT: "zuriyar Dauda za su sami ɗa su sa masa suna Yosiya"
A nan "su" na nufin Yosiya da mutanen da ke tare da shi.
za mu iya cewa. AT: "Yahweh zai rushe bagadin tokar kuma za a watsar a ƙasa"
za a iya fassara wanna a ce. AT: "Yahweh ya busar da hannun da ya miƙa akan mutumin"
"ya bushe" ko kuma "ya zama shanyayye" (UDB)
za a iya fassara wanna. AT: "Yahweh kuma ya rushe bagadin"
za a iya fassara wannan a ce. "kamar yadda mutumin Allah ya faɗa ta wurin mamganar Yahweh a matsayin alama" (Duba:
A nan "magana" na nufin saƙon Yahweh. AT: "saƙon Yahweh"
Sunan nan "tagomashi" za a iya cewa shi kalmar aiki ne. AT: "ka yi roƙo domin Yahweh Allahnka ya ba ni tagomashi"
za a iya cewa. AT: "domin Yahweh ya warkar da hannuna"
za a iya cewa. AT: "Yahwehbya warkar da hannun sarki kuma ya koma kamar yadda yake a dã"
Kalmar "shakata" na nuna wakilin suna. AT: "ka zo gida tare dani ka ci abinci"
"rabin gidanka"
"ka da ka ci abinci, sha ruwa, ko koma ta hanyar da ka zo"
""ya koma ta hanya da dabam
Wannan na nufin bayyayni da'yan'yansa suka faɗa wa maifinsu hanyar da mutumin Allah ya bi.
Wannan na nufin a sa mahauni a bayan dabba yadda mutum zai iya zama ya yi tafiya da dabbar.
Wannan na nufin annabin da ke zama a Betel.
"tsohon annabin ya ce wa mutumin Allah"
"mutumin Allahn ya amsa"
"tafi gidanka"
"a Betel"
za a iya cewa. AT: "Yahweh ya umarceni ta wurin maganarsa"
Wannan habaici ne ma'ana Yahweh ya faɗa. Anan "faɗa" na wakiltar saƙon Yahweh. Duba yadda yake a 6:11. AT: "ta wurin sakon yahweh"
"mala'ika ya kawo mani saƙon Yahweh"
Wannan habaici ne ma'ana Yahweh ya faɗa. Anan "faɗa" na wakiltar saƙon Yahweh. Duba yadda yake a 13:14. AT: "ta wurin sakon yahweh"
Bayyanin na nuna har yanzu suna ci suna sha a teburin. AT: "lokacin da suke ci suke sha a tebur"
Wannan habaici ne ma'ana Yahweh ya faɗa. Anan "faɗa" na wakiltar saƙon Yahweh. Duba yadda yake a 13:14. AT: "ta wurin sakon yahweh"
Kalmar "shi" na nufin mutumin Allah.
"ya yi magana da ƙarfi ga mutumin Allah"
"domin ba ku yi biyayya da maganar Yahweh ba"
Wannan na nufin ya sa wa jakin shimfiɖda a bayasa domin mutumin Allah ya sau. Duba yadda ya ke a 13:11.
za a iya ƙarya wa wannan armashi a ce. AT: "ya bar jikin sa akan hanya"
"gawa, matacce, mushe"
A nan "faɗa" na nuna abin da suka gani akan hanya AT: "su ka zo suka faɗi abin da suka gani"
"gawa, matacce, mushe"
"kwance akan hanya"
"a raba abu da ƙasa"
"gawa, matacce, mushe"
A nan "su" na nufin annabi da yaransa.
Kalmar "kaito" anan na nufin baƙin ciki mai tsanani.
A namn kalmar "shi" na nufin annabin da kuma kalmar "ya" na nufinmutumin Allah.
Anan "ƙasusuwana" na nugin dukkan jiki. AT: "kwantar da gawata kus da ƙasusuwansa"
Ma'anar wannan bayanin shine waɗannan gida sujada ne. AT: "gidajen sujada a bisa tuddai"
za mu iya ƙara masa armashi mu ce. AT: "iyalin Yerobowam sun yi zunubi saboda waɗannan abubuwa"
wannan jimlar na nufin Yerobowam ya shirya matsafa kuma ya zaɓi firistoci.
za mu iya cewa. AT: "saboda wanna Allah ya hallaka da kuma shafe iyalan Yerobowam"
Wannan na nufin kusan abu ɗaya. AT: "a hallakarsa da su gaba ɗaya"
1A lokacin nan Abija ɗan Yerobowom ba shi da lafiya sosai.2Yerobowom ya cewa matarsa, "Idan kin yarda ki tashi ki bad da kamarki, don ka da a gane ke matata ce, ki tafi Shilo, domin Ahija annabi yana can, shi ne wanda ya ce mani zan zama sarki akan waɗannan mutane.3Tare da ke ki ɗauki malmalar abinci goma, da waina da kurtun zuma, ki tafi wurin Ahija. Zai faɗa ma ki abin da zai faru da yaron."4Matar Yerobowom kuwa ta yi haka; ta tashi ta tafi Shilo har ta iso gidan Ahija. Yanzu Ahija ba ya gani; saboda ya rasa gani don tsufa.5Yahweh ya cewa Ahija, "Duba, ga matar Yerobowom ta na zuwa ta nemi shawara daga gare ka akan ɗanta, domin ba shi da lafiya. Ka ce haka, da haka da ita, gama sa'ad da ta zo, za ta nuna kamar ita wata mace ce dabam."6Sa'ad da Ahija ya ji motsin takawarta a bakin kofa, ya ce, "Ki shigo ciki, matar Yerobowam. Meyasa ki ke yi kamar ba ke ce ba? An aiko ni gare ki da labari mara daɗi.7Tafi, ki faɗa wa Yerobowam cewa Yahweh, Allah na Isra'ila ya ce, 'Na ɗaukaka daga cikin mutane na sa ka zama shugaba akan mutanena Isra'ila.8Na yage mulki daga iyalin Dauda na baka, duk da haka ba ka zama kamar bawana Dauda ba, wanda ya kiyaye umarnina ya bi ni da dukkan zuciyarsa, ya yi abin da ke dai-dai a idanuna.9Maimako haka, ka aikata mugunta, fiye da dukkan waɗanda suka riga ka. Ka yi waɗansu alloli, ka yi siffofi na zubi ka tsokane ni in yi fushi, ka jefar da ni a bayanka.10Saboda haka, duba, zan kawo masifa a iyalinka; zan datse daga gare ka kowanne ɗa namiji a Isra'ila, ko bawa ko 'yantacce, zan ƙori iyalinka gaba ɗaya, kamar mutum wanda ya ƙone juji kurmus.11Duk wanda ya ke na iyalinka wanda ya mutu a birni karnuka su cinye shi, wanda kuma ya mutu a fili tsuntsayen sammai su cinye shi, gama ni, Yahweh na faɗa.12Ki tashi, matar Yerobowom ki koma gidanki; ya yin da ƙafarki ta shiga birni, yaron Abija zai mutu.13Dukkan mutanen Isra'ila za su yi makoki dominsa za a bizne shi. Shi kaɗai ne daga iyalin Yerobowom wanda zai je kabari, gama shi kaɗai ne, daga cikin gidan Yerobowom, aka sa me shi da aikata abu mai kyau a fuskar Yahweh, Allah na Isra'ila.14Haka nan Yahweh zai ta da wani sarki a Isra'ila wanda zai yanke iyalin Yerobowom a wannan rana. Yau ita ce wannan rana, yanzun nan.15Gama Yahweh zai hukunta Isra'ila kamar yadda akan girgiza iwa a ruwa, zai tuge Isra'ila daga wannan ƙasa mai kyau wadda ya ba kakanninsu. Zai watsar da su bayan Kogin Yufiretis, domin sun yi wa kansu turaku na Ashera domin su tsokani Yahweh ya yi fushi.16Zai bayar da Isra'ila domin zunuban Yerobowom, zunuban da ya aikata, ta wurin sa Isra'ila su yi zunubi.17Sai matar Yerobowom ta tashi ta tafi, ta zo Tirza. Tana zuwa bakin ƙofar gidanta kenan, yaron ya mutu.18Dukkan Isra'ila su ka bizne shi, suka yi makoki dominsa, kamar yadda aka faɗa masu ta wurin maganar Yahweh wanda ya yi magana ta wurin bawansa Ahija annabi.19Game da sauran abubuwa akan Yerobowom, yadda ya yi yaƙe-yaƙensa da sarautarsa, duba, an rubuta su a cikin littafin tarihin sarakunan Isra'ila.20Yerobowom ya yi mulki shekaru ashirin da biyu sa'an nan ya rasu tare da kakaninsa, ɗansa Nadab ya gaji sarauta a matsayin mahaifinsa.21Yanzu Rehobowom ɗan Suleman ya yi mulki a Yahuda. Rehobowom yana da shekare arba'in da ɗaya sa'ad da ya zama sarki, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai a Yerusalem, birnin da Yahweh ya zaɓa daga dukkan kabilun Isra'ila in da ya sa sunansa. Sunan mahaifiyarsa kuwa Na'ama Ammoniya.22Yahuda ta yi abin da ke mugu a fuskar Yahweh; suka tsokane shi ya yi fushi saboda zunuban da suka aikata, fiye da abin da kakanninsu suka yi.23Gama suma sun gina wa kansu wuraren tsafi, ginshiƙan dutse da turken Ashera a kan kowanne tudu mai tsawo da ƙarƙashin kowanne koren itace.24Akwai kuma karuwan tsafi a ƙasar. Suka yi abubuwan bankyama kamar al'ummai da Yahweh ya kawar daga wurin mutanen Isra'ila.25Wannan ya faru a shekara ta goma sha biyar ta mulkin Rehobowom da Shishak sarkin Masar ya gãba da Yerusalem.26Ya kwashe dukiyar gidan Yahweh, da dukiyar gidan sarki. Ya ɗauke kome da kome ya tafi da shi; ya kuma ɗauki garkuwoyin zinariya waɗanda Suleman ya yi.27Sarki Rehobowom ya yi garkuwoyin tagulla ya sa a hannun shugabannin masu tsaro, waɗanda ke tsaron ƙofar gidan sarki.28Ya zamana duk lokacin da sarki zai shiga gidan Yahweh, matsara za su ɗauke su; sai su kawo su a gidan tsaro.29Game da sauran abubuwa akan Rehobowom, dukkan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuda.30Kullum ana ta yin yaƙi tsakanin Rehobowom da Yerobowom.31Rehobowom kuwa ya yi barci tare da kakaninsa aka kuma bizne shi tare da su a birnin Dauda. Sunan mahaifiyarsa kuwa Na'ama daga Ammoniyawa. Abija ya gaji sarauta a matsayin mahaifinsa.
"Ka fito ba yadda mutane suka saba ganinka ba"
za mu iya ce wa. AT: "ba wanda zai gane ki"
A nan kalmar "duba" na nufin "ka bada hankalin ka ga wannan abin."
Wakilin suna "shawara" za a iya fassara a matsayin aikatau. AT: "zuwa ta tambayeka"
kalmar "haka da haka" na nuna Yahweh ya faɗa wa Ahijah abin da zai ce. AT: "ga ya mata wannan maganar"
Wannan tambayar na nuna cewa Ahijah yasan ta ḅad da kama ne. AT: "ki daina nu ke wata dabam ce, na san ko ke wacece."
za mu iya cewa. AT: "Yahweh ya ce in baki labari mara daɗi"
"na ɗaukaka ka"
Allah ya cire yawancin mulkin kamar mutum na yage yanki kaya.
"yi min biyayya"
Idanun na wakiltar gani, gani kuma na wakiltar tunani ko kuma hukunci. AT: "abin da na hukunta gaskiya ne" ko kuma "abin da nake ganin gaskiya ne"
Yerobowam ya yi wa Yahwehrashin biyayya kamar mutum wanda ya yarda abu wanda ba shi da sauran amfani. AT: "ya ƙi ni gaba ɗaya"
"ka mai da hamkali." wannan kalmar ana ƙara shi ne a nuna abin da zai biyo baya mai matuar mahimmanci ne.
Waɗanan jimloli guda biyu na nufin abu ɗaya kuma ana amfani da su a jaddada abu.
Yahweh ya yi maganar hallaka iyalin Yerobowam da kuma hani shi samun zuriya kamar yana yanke su, kamar wanda yake yanke rassan itace. AT: "zan datse daga gare ka kowanne ɗa namiji a Isra'ila"
Wannan ya haɗa da cire zuriyar Yerobowam gaba ɗaya da kuma ƙone bola ne da aka haɗa da tattaka, bushesshe, aka ƙone ƙurmus.
za mu iya cewa. AT: "karnuka za ci duk wanda ya mutu a iyalinka"
za mu iya cewa. AT: "tsuntsayen sama za su ci duk wanda ya mutu a fili"
Kalmar "ƙafa" wakili ne na dukkan mutum. AT: "idan kika shiga birnin"
wannan gaba ɗaya yana nufin mutane arewacin mulkin Isra'ila. AT: "mutanen Isra'ilawa"
"a bizne shi a kabari"
Kalmar "gida" a nan wakili ne na "iyali." AT: "dukkan iyalin Yerobowam"
Gababn Yahweh na wakiltar hukuncin Yahweh. Z a mu iya cewa. AT: "ko Yahweh, Allahn Isra'ila, zai samu dukkan abinda ya hukunta dai-dai"
Marubucin na magana ne da sabon sarkin Isra'ila yana hallakar da iyalin Yerobowam da kuma hana shi samun zuriyakamar wanda yake yanke rassa daga bishiya. AT: "hallakar da zuriyar Yerobowam"
marubucin anan ya yi amfani da wannan ya nuna yadda Yahwehzai kawo hukunci a kan mutanen Isra'ila. AT: "Yahweh zai hukunta mutanen Isra'ila kamar yadda ake girgiza iwa a ruwa"
za mu iya cewa. AT: "kamar rafin ruwa yana girgiza iwa"
Yahweh ya misalta Isra'ilawa kamar tsire wanda zai cire shi har da sauyar sa. AT: "zai cire mutanen Isra'ila daga wannan ƙasa mai kyau"Duba:
"kaca-kaca da su"
Wannan suna birni ne inda Yerobowam ke zama.
Wannan an haɗa shi gaba ɗaya ne ma;ana mutanen Isra'ila suka bizne shi suka yi masa makoki. AT: "mutane da yawa na Isra'ila su na wurin ya yinda aka bizne shi, mutanen Isra'ila kuma suka yi makoki"
za mu iya cewa. AT: "kamar yadda Yahweh faɗa musu"
A nan "magana" na wakiltar saƙon Yahweh. AT: "saƙon Yahweh" ko kuma "saƙon Yahweh"
"duba"
za a iya cewa. AT: "za ku iya samun su a rubuce a"
Wannan na nuna labarin da ya faru a baya.
shekara biyu - "shekara 22"
Mutuwar Yerobowam ana maganarsa kamar ya kwanta barci. Duba yadda aka fassara shi a 2:10. AT: "mutuwa"
shekara ɗaya ... shekara goma sha bakwai- "shekara 41 ... shekara 17"
A nan "sa sunansa" wakili ne na "dauwama" na nufin wurin da ake yi wa Yahweh sujada. AT: "in da za a dauwama" ko "in da za a yi sujada."
A nan kalmar "sa" na nufin Yehobowam.
wannan sunan mace ne.
A nan "Yahuda" na wakiltar mutanen Yahuza. AT: "mutanen Yahuda su ka yi"
"fuskar" Yahweh na nufin hukunci ko kimantawa . Duba yadda aka fassara shi a 11:5. AT: "abin da ke mugu a hukuncin Yahweh" ko kuma "abinda Yahweh ya ce mugu ne"
sunan "fushi" za a iya fassara shi a matsayin siffa. AT: "sun sa shi ya yi fushi"
"kakanni"
Kalmar "suma" anan ta na nufin 'ya'yan Yahuda.
"sun gina domin amfanin su"
Wannan za iya zama fifitawa da yake nuna akwai wurare da yawa na sujada ga allolin ƙarya a dukkan ƙasar. AT: " a kan kowanne tudu mai tsawo da ƙarƙashin kowanne koren itace"
(karuwan addini) ko "karuwai mazaje." Wannan na nufin mazaje karuwai waɗanda suka ba da kansu ga bautar gumaka.
A nan "al'ummai" na wakiltar mutane na wancan wurin. AT: "dukkan abin ban ƙyama da mutanen suka yi, waɗanda"
Wannan na nufin shekara ta biyar ta mulkin sarki Rehobowam. AT: "a shekara ta biyar da Rehobowam ya ke sarki"
"Shishak sarkim masar" wakili ne na Shishak tare da sojojin masar. AT: "Shishak sarkin masar da sojojin sa, su ka zo gaba da Isra'ila"
Wannan sunan na miji ne. Duba yadda aka fassara shi 11:40.
Wannan habaici ne wanda yake nufin takawa gãba da ko kuma kai hari. AT:
Wannan na gaba ɗaya ne da yake nuna dukkan wani abu matuƙar mahimmancida za a iya samu an ɗauke. AT: "ya ɗauke abubuwa masu muhimmanci da yawa"
kalmar "ya" na nufin Shishak da dukkan sojojin da suke tare da shi. AT: "Shishak da sojojinsa sun ɗauka"
A nan "Sulaiman" na nufin masu sana'a waɗanda suka yi aiki da Sulaiman don yin garkuwa. AT: "da Sulaiman ya sa ma;aikatansa suka yi"
Ana "sarki Rehobowam" na wakiltar mutumin da da ya yi aiki da shi wajen yin garkuwar. AT: "mutanen sarki Rehobowam sun yi garkuwa"
"a wurin garkuwa ta zinariya"
A nan "hannu" kula da ayyuka. AT: "ka sa ya zama aikin shugabanninsu"
A nan "ƙofa" na nufin wurin shiga. AT: "waɗanda ke tsaron ƙofar gidan sarki"
"matsara za su ɗauki garkuwa na zinariya"
za mu iya cewa ko kuma mu sa rai amsar ta zama gaskiya. tambayar ba ya buƙatar amsa kuma anyiamfani da shi domin a jaddada. AT: " an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuda." ko kuma "za ku iya karanta game da su a littafin tarihin sarakunan Yahuda."
Wannan na nufin littattafan da ba a amfani da su yanzu.
"akwai yaƙi kullum" ko "kwai yaƙi da ya daɗe"
Sunan sarakunan na nufin cewa akwai yaƙi tsakanin sojojin Rehoboam da Yeroboam. at: "sojojin Rehobowam da sojojin Yeroboam suna ta faɗa kullum-kullum"
mutuwar Rehoboam an yi maganarsa kamar ya kwanta barci. Duba yadda aka fassara shi a 2:10. AT: "mutuwa"
za mu iya cewa. AT: "mutane suka bizne shi"
Wannan sunan mace ne. Duba yadda aka fassara shi a 14:21.
"Ahija yaron Rehoboam"
Jimlar "a matsayinsa" wakili ne ma'ana "maimakonsa." AT: "ya zama sarki a maimakon Rehoboam"
1A shekara ta goma sha takwas ta sarki Yerobowom ɗan Nebat, Abija ya fara sarauta akan Yahuda.2Ya yi mulki shekaru uku a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Ma'aka. Ita ɗiyar Abishalom ce.3Shi ma ya yi tafiya a cikin dukkan irin zunubai da tsohonsa ya yi a lokacinsa; bai ba Yahweh Allahnsa dukkan zuciyarsa ba kamar yadda Dauda kakansa ya yi ba.4Duk da haka, saboda Dauda, Yahweh Allahnsa ya ba shi fitila a Yerusalem ta wurin ba ɗansa ya gaje shi saboda ya ƙarfafa Yerusalem.5Allah ya yi wannan domin Dauda ya yi abin da ke dai-dai a idanuwansa; a cikin dukkan kwanakin ransa, bai juya daga kowanne umarnin da aka ba shi ba, sai dai akan Yuriya Bahitte.6Yanzu akwai yaƙi a tsakanin Abija ɗan Yerobowom dukkan kwanakin rayuwar Abija.7Kamar sauran ayyukan Abija, duk da abubuwan da ya yi, ba suna rubuce a cikin littafin tarihi na sarakunan Yahuda ba? Akwai yaƙi tsakanin Abija ɗan Yerobowom.8Abija ya barci tare da kakaninsa, su ka bizne ne shi a birnin Dauda. Asa ɗansa ya zama sarki a maimakon mahaifinsa.9A cikin shekara ta ashirin ta sarautar Yerobowom sarkin Isra'ila, Asa ya fara sarauta a Yahuda.10Ya yi shekaru arba'in da ɗaya yana sarauta a Yerusalem. Sunan kakarsa kuwa Ma'aka, yar Abishalom.11Asa ya yi abin da ke dai-dai a idanun Yahweh, kamar yadda Dauda, kakansa ya yi.12Ya kori karuwai matsafa daga ƙasar ya kuma cire dukkan gumakun da kakaninsa suka yi.13Ya kuma fitar Ma'aka da kakarsa, daga zaman sarauniya, domin ta yi ƙazamar siffa daga turken Ashera. Asa ya sassare ƙazamar siffar ya ƙone ta a Kwarin Kidron.14Amma ba a kawar da wuraren tsafi na tuddai ba. Duk da haka, Asa ya ba Yahweh dukkan zuciyarsa a dukkan kwanakinsa.15Ya kawo abubuwan da mahaifinsa ya keɓe da kuma azurfa da zinariya da kwanoni waɗanda shi kansa ya yi a cikin gidan Yahweh.16Akwai yaƙi tsakanin Asa da Ba'asha sarkin Isra'ila, dukkan kwanakinsu.17Ba'asha sarkin Isra'ila, ya kai wa Yahuda yaƙi ya gina Rama, don ya hana kowa ya fita ko kuma ya shiga ƙasar Asa sarkin Yahuda.18Sai Asa ya kwashe dukkan azurfa da zinariya da suka rage a ɗakunan ajiya na gidan Yahweh, da na ɗakin ajiyar fãdar sarki. Ya sa su a cikin hannuwan barorinsa su kai su ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda ke zaune a Damaskus. Ya ce.19"Bari mu ƙulla alƙawari tsakani na da kai, kamar yadda ya ke tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, na aika maka da kyautar azurfa da zinariya. Ka karya alƙawarinka da Ba'asha sarkin Isra'ila, domin ya bar ni."20Ben-Hadad kuwa ya saurari sarki Asa ya kuma aika shugabanin sojojinsa su ka yi yaƙi da biranen Isra'ila. Suka yi faɗa da Iyon da Dan da Abe ta bet Ma'aka, da dukkan Kenneret tare da dukkan ƙasar Naftali.21Da Ba'asha ya ji wannan, sai ya daina ginin Rama ya koma Tirzah.22Sa'an nan sarki Asa ya yi jawabi ga dukkan mutanen Yahuda. Ba wanda aka ɗauke wa. Suka tafi su ka ɗauki duwatsu da katakai a Ramah waɗanda Ba'asha ke gina birnin. Sai sarki Asa ya yi amfani da kayan ginin ya gina Geba ta Benyamin da Mizfa.23Sauran dukkan abubuwa a game da Asa, dukkan ƙarfinsa, dukkan abubuwan da ya yi, da biranen da ya gina, ba su na nan ba a rubuce a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda?24Amma lokacin tsufansa, sai ya sami ciwo a ƙafafunsa. Asa ya rasu tare kakaninsa aka kuma bizne shi tare da su a cikin birnin Dauda mahaifinsa. Yehoshafat ɗansa ya zama sarki a matsayinsa.25Nadab ɗan Yerobowom ya fara sarauta a Isra'ila a shekara ta biyu ta sarki Asa na yin mulkin a Yahuda; ya yi sarautar Isra'ila shekaru biyu.26Ya yi mugunta a fuskar Yahweh ya yi tafiya a hanyar da mahaifinsa ya yi a cikin zunubinsa, ya jagoranci Isra'ila su yi zunubi.27Ba'asha ɗan Ahiji, na iyalin Issaka, ya yi wa Nadab maƙarƙashiya; Ba'asha kashe shi a Gibbeton wadda ke ta Filistiyawa, gama Nadab da dukkan Isra'ila sun kewaye Gibbeton da yaƙi.28A cikin shekara ta uku da sarki Asa ke mulkin Yahuda, Ba'sha ya kashe Nadab ya kuma zama sarki a gurbinsa.29Nan da nan da ya zama sarki, Ba"asha ya kashe dukkan iyalin Yerobowom. Bai bar kowa ba a zuriyar Yerobowom wanda ke numfashi ba; a wannan hanya ya hallakar da gidan sarautarsa, kamar yadda Yahweh ya faɗa ta wurin bawansa Ahija mutumin Shilo,30domin zunuban Yerobowom wanda ya yi da kuma zunubin da ya sa mutanen Isra'ila suka yi, don ya tsokani Yahweh, Allah na Isra'ila ya yi fushi.31Kamar sauran abubuwa a kan Nadab, da dukkan abin da ya yi, ba suna a rubuci ba a cikin littafin tarihi na ayyukan sarakunan Isra'ila?32Akwai yaƙi tsakanin Asa da Ba'asha sarkin Isra'ila a dukkan kwanakinsu.33A cikin shekara ta uku da Asa sarkin Yahuda, Ba'asha ɗan Ahija ya fara sarauta akan dukkan Isra'ila a Tirza ya kuma yi mulki sheraka ashirin da huɗu.34Ya yi abin da ke na mugunta a fuskar Yahweh ya kuma bi hanyar Yerobowom da kuma zunubin da ya sa Isra'ila suka yi.
Wannan na nufin shekara ta goma sha takwas. AT: "bayan Yeroboam ya yi sarautar ta kusan shekara goma sha takwas"
"a shekara ta 18" (Duba: trans;late-names)
Tafiya na wakiltar rayuwa, tafiya cikin zunubi na nufin aikata waɗannan zunubai.AT: "Ahija ya ci gaba da yin dukkan zunubai"
Tunda waɗannan ayoyi na magana da sarakuna da yawa. Zai taimaka a sa sunan mahaifin Ahija. Wannan bayanin zai kawo haske. AT: "cewa mahaifinsa, Rehoboam, ya aikata kafin lokacin Ahija"
Wannan jimlar ya wakilci lokacin da yake sarki. Ma'anar wannan zai fi kawo haske. AT: "kafin Ahija ya zama sarki"
Zuciya na wakiltar dukkan jiki. AT: "Ahija bai miƙa kai ba ... kamar Dauda"
Kalmar "fitila" na wakiltar zuriya wanda zai zama sarki kamar Dauda. AT: "ya ba Dauda zuriya da zai zma sarki kamar yadda Dauda yake"
"da ya tada Ahija ɗansa ya gaje" ko kuma "da ya ba Ahija ɗa"
Idanu anan na wakiltar gani, gani kuma na wakiltar tunani ko hukunci. AT: "abin da Yahweh ya hukunta ya zama gaskiya" ko kuma "abin da Yahweh ya sa ya zama gaskiya"
Kalmar "kwanaki" na wakiltar wasu loƙuta. AT: "dukkan lokacin da Dauda ya yi rayuwa" ko "gaba ɗaya rayuwar Dauda"
Juya wa daga umarni na wakiltar rashin yin biyayya da umarni. AT: "Dauda bai ƙi yin biyayya da dukkan abinda Allah ya umarceshi ba"
Wannan hanya ce ta gaba ɗaya a nuna halin da ake ciki da Yuriya. za a fi nuna shi da kyau abin da al'amarin ya ƙunsa. AT: "sai dai abinda ya yi wa Yuriya Bahitte" ko kuma "sai da ya sa a kashe Yuriya Bahitte"
Suan "Rehoboam" da "Yeroboam" na wakiltar sojojin gidan sarakunan na biyu. Rehoboam mahaifin Ahija ne. AT: "tsakanin sojojin Rehoboam da na Yerobowam"
Kalmar "kwanaki" na wakiltar wa su lokuta. AT: "a dukkan lokutan da Ahija ya yi" ko kuma "gaba ɗaya rayuwarsa"
wanna tambaya tana amfani ne ta wurin labari ko tuni ga mai karatu cewa bayanai ga me da Ahija yana a cikin wannan littafin. Duba yadda aka fassara shi a 14:29. Wannan tambayar marar buƙatar amsaza a iya fassara shi. AT: "an rubuta su a a littafin tarihin sarakunan Isra'ila."
za a iya fassara shi a AT: "wani ya rubuta a ba suna rubuce a cikin littafin tarihi na sarakunan Yahuda ba?."
Sunan "Ahija" da "Yerobowam" na wakiltar sojojinn waɗannan sarakuna. AT: "tsakanin Abija da Yeroboam."
A nan kamar kwantar da hankali barci na wakiltar mutuwa. AT: "Ahija ya mutu kamar yadda kakaninsa suka yi" ko "kamar kakaninsa, Ahija ya mutu"
Jimlar "a madadinsa" wakili ma'ana "maimakonsa." AT: "ya zama sarki a maimakon Ahija"
Wannan na nufin shekara ashirin na mulkin Yerobowam. AT: "bayan Yerobowam ya yi mulkin Isra'ila na kusan shekara ashirin"
shekara ɗaya-"shekara 41" (Duba: transalate_numbers)
Ido ana na nufin gani, gani kuma na nufin hukunci. Yahweh ya gani kuma ya yarda da aikin Asa. AT: "abin da Yahweh ya hukunta za ma gaskiya" ko kuma "abin da Yahweh ya gani gaskiya"
wannan na nufin karuwai waɗanda suka mika kansu ga yi wa gumaka sujada kuma dukka maza ne. AT: "karuwan addini" ko "karuwai da suke yi wa gumaka aiki" ko "karuwai mazaje"
Tunda Asa ya ke sarki, zai iya gaya wa 'yan majalisarsa su sassare siffar. AT: " Asa ya sassare ƙazamar siffar" ko "Asa ya sa su ka sassare ƙazamar siffar"
Za mu iya bayyana wannan da gaba gaɗi. AT: "amma Asa bai sa mutanen su kawar da wuraren tuddai ba"
Zuciya anan na wakiltar mutum. AT: " Asa ya ba da dukkan zuciyarsa "
Wannan na nufin wasu lokuta da Asa ya rayu. AT: "gaba ɗaya rayuwar Asa" ko kuma "dukkan kwanakin Asa"
Kalmar "kwanaki" wani lokaci, da kuma "dukkan kwanakinsu" na nufin dukkan lokacin da Asa da Ba'asha suke sarauta. AT: "dukkan lokacin da suke mulkin Yahuda da Isra'ila"
"kai wa Yahuda hari"
Ya na nuna cewa sojojin Ba'asha sun kama Rama. Ma'anar wannan maganar shine. AT: "kamawa da tsare Rama"
Sa abu a hannun su na wakiltar ba su waɗannan abubuwa. ya na nuna za yi abu da shi yadda mai shi yake so suyi. Asalin ma'anar shi ne. AT: "ya miƙa shi a ikon bawansa"
Ya yi magana da su ta wurin bawansa. Asa ya gaya wa bawansa abinda zai faɗa wa Ben-Hadad kuma ya faɗa. ma'ana anan shine. AT: "Asa ya gaya wa bawansa ya ce wa Ben-Hadad" ko "ta wurin bawansa Asa ya ce wa Ben-Hadad" (Duba: da
Alkawari tsakani mutum biyun ya nuna sun ƙulla yarjejeniya tsakaninsu. AT: "bari mu ƙulla alkawari da juna" ko "bari mu yi yarjejeniya ta salama"
Wannan habaici ne. Anan kalmar "duba" na ƙara jadda abinda zai biyo baya kuma tabbatar da abin da aka faɗa. AT: "tabbatarwar zan yi yarjejeniya dan kai"
Karya alkawari na nufin fasa shi kuma rashin yin abinda wani ya ce zai yi. AT: "Ka fasa alƙawarinka da Ba'asha sarkin Isra'ila," k "ka da ka yi biyayya da Ba'asha sarkin Isra'ila kamar yadda ka yi masa alkawari"
Asa ya so Ben-Hadad ya kai hari Isra'ila. Ben-Hadad zai yi haka in ya karya alkawarin sa da sarkin Isra'ila. Ma'anar wannan shine. AT: "Ka karya alƙawarinka da Ba'asha sarkin Isra'ila, ka kai masa hari"
Jimlar an yi amfani da a fara farkon labari. Idan harshen ka na da wata hanya ta sa su. za ku iya sa su.
sarkin Ba'asha ya yi wannan ta wurin ga ya wa ma'aikatansa suyi. AT: "ya ce wa ma'aikatansa su daina gina Rama"
Wannan sunan birni ne. Duba yadda aka fassara shi a 14:17.
za a iya bayyana wannan a ce. AT: "kowa da kowa ya yi biyayya da sarwar sarki"
Wannan tambayar an yi ta ne ko a faɗa ko a tunasheda mai karatu bayanai game da Ahijana nan a wannan littafin. Duba yadda aka fassara a 14:29. wannan tambayar da bata buƙatar amsa za a iya cewa. AT: "ba su na nan ba a rubuce a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda?"
za a iya fassara wannan gaba gaɗi. AT: "wani ya rubuta a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.?"
Barci anan kalmace ta kwantar da hankali da yake nufin mutuwa. AT: "Asa ya mutum kamar yadda kakaninsa suka mutu"
za mu iya sa shi a aikatau. AT: "suka bizne shi da kakaninsa"
Kalmar "mahaifi" a nan na nufin kakanni. AT: "Sarki Dauda, kakaninsa"
Sauran sura 15 da 16 na magana akan sarakunan Isra'ila. Wannan labarin ya faru tun Asa sarkin Yahuda ya na da rai.
Wannan na nufin shekara ta mulkin Asa. Ma'anar wannan zai zama. AT: "lokacin da Asa yake mulkin Yahuda kusan shekaru biyu"
"Nadab ya yi sarautar Isra'ila shekaru biyu"
fuskar Yahweh na nufin hukuncin Yahweh. AT: "abinda yake mugu a hukuncin Yahweh" ko "abinda yahweh ya ga mugu ne"
Tafiya anan na nufin rayuwa. AT: "ya yi irn abinda mahaifinsa ya yi"
Tafiya cikin zunubinsa na nufin yin zunubi a hanyoyi dabam da wanda mahaifinsa ya bi ya yi zunubi. AT: "ya yi zunubi a hanyarsa" (Duba: metaphor)
jagorancin mutane su yi wani abu na wakiltar jan hankalinsu su yi shi. AT: "ta yin zunubi ya rinjayi Isra'ila su ka yi zunubi"
"a sirrance aska shirya a kashe sarki Nadab"
Wannan sunan birni ne.
Wannan jimlar "dukkan Isra'ila" gaba ɗaya ne da yake wakiltar dukkan sojojin Isra'ila. AT: "Nadab da sojojin Isra'ila masu yawa" ko "Nadab da sojojin Isra'ila"
"sun kewaye Gibbeto, domin mutanen Gibbeto su miƙa kai a gare su"
Jimlar "a gurbinsa" kwatanci da yake nufin "maimakonsa." AT: "ya zama sarki maimakonsa"
Wanan jimla guda biyu na nufin abu ɗaya an haɗa su ne a jaddada cewa zuriyarsa dukka an kashe su.
Yeroboam shine mahaifin sarki Nadab.
Numfashi na wakiltar zama a raye. AT: " Bai bar kowa ba a zuriyar Yeroboam wanda ke numfashi ba"
"gidan sarautar Yeroboam"
A 14:9 Yhaweh ya yi magana ta wurin annanbinsa Ahija ya gaya wa Yeroboam cewa zai hallaka iyalinsa.
"Ahija wanda ya ke daga Shilo"
Sunan "zunubi" za a iya sa shi a aikatau "zunubi." AT: "saboda Yeroboam ya yi zunubi ya jagoranci Isra'ilawa su ma suka yi zunubi"
jagorantar mutane su yi wani abu dai-dai yake da jan hankalinsu su yi wani abu. AT: "ta ha ya rinjayi Isra'ila su ka yi zunubi"
Wannan tambayar an yi ta ne ko a faɗa ko a tunasheda mai karatu bayanai game da Ahijana nan a wannan littafin. Duba yadda aka fassara a 14:29. wannan tambayar da bata buƙatar amsa za a iya cewa. AT: "ba su na nan ba a rubuce a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda?"
za a iya cewa. AT: " wani ya ya rubuta wannan a littafin tarihin sarkunan Isra'ila."
Kalmar "kwanaki" na wakiltar wasu lokuta da "dukkan kwanakinsu" na nufin dukkan lokutan da Asa da Ba'asha suke sarauta. Duba yadda aka fassara shi a 15:16. AT: "dukkan lokacin da suka yi mulkin Yahuda da Isra'ila"
Wannan sura ya yi magana yadda Ba'asha ya zama sarki a 15:27. Waɗannan ayoyi sun fara faɗa game da Ba'asha sarkin Isra'ila.
Wannan sunan birni ne. Duba yadda aka fassara shi a 14:17.
Fuskar Yahweh na wakiltar hukuncin Yahweh. AT: "abinda ke mugun ta hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ga mugunta ne"
Tafiya anan na wakiltar yadda wani ya yi rayuwa. AT: "ya yi abu ɗaya da Yeroboam yayi"
ko muce "sa" da "shi" na nufin 1) Ba'asha ko 2) Yeroboam.
Jagorantar mutane su yi wani abu na wakiltar jan hankalinsu su yi shi. AT: "ta yin zunubi, ya ja hankalin Isra'ila su ka yi zunubi"
1Maganar Yahweh ta zo ga Yehu ɗan Hanani akan Ba'asha, cewa,2"Ko da ya ke na ɗauke ka daga cikin ƙura, na maishe ka shugaba akan mutanena Isra'ila, kai kuwa ka yi tafiya irin ta Yerobowom ka sa mutanena Isra'ila sun aikata zunubi, suka sa na yi fushi saboda zunubansu.3Duba, zan shafe Ba'asha da iyalinsa gaba ɗaya, zan maida iyalinka kamar iyalin Yerobowom ɗan Nebat.4Karnuka ne za su cinye kowanne mutum da ke na Ba'asha idan ya mutu a birni, tsuntsayen sama kuma ne za su cinye kowanne mutum da ya mutu a saura."5Sauran ayyuka akan Ba'asha, da abubuwan da ya yi, da ƙarfinsa, ba suna a rubuce a littafin tarihi na sarakunan Isra'ila ba?6Ba'asha ya yi barci aka kuma bizne shi tare da kakanninsa a Tirzah, Ela ɗansa kuma ya zama sarki a gurbinsa.7Sai maganar Yahweh ta zo wurin annabi Yehu ɗan Hanani akan Ba'asha da iyalinsa, duka kuma saboda dukkan mugutar da ya aikata a fuskar Yahweh, har ya yi fushi da ayyukan hannuwansa, kamar iyalin Yerobowom, kuma saboda ya hallaka dukkan iyalin Yerobowom.8A shekara ta ashirin da shida da Asa ke mulkin Yahuda, Ela ɗan Ba'asha ya fara sarauta akan Isra'ila a Tirzah; ya yi sarauta shekaru biyu.9Bawansa Zimri, shugaban rabin karusansa ya yi masa maƙarƙashiya. Sa'ad da Ela ya ke Tirzah, ya sha ya bugu a gidan Arza, wanda ya ke lura da fada a Tirzah.10Zimri ya tafi cikin gidan, ya buge shi har ya kashe shi, a shekara ta ashirin da bakwai ta mulkin Asa sarkin Yahuda, ya zama sarki a gurbinsa.11Da Zimri ya fara sarauta ya zauna akan kujerar mulki, yakashe dukkan iyalin Ba'asha. Bai bar namiji ko ɗaya a raye ba dangi ko abokai.12Haka Zimri ya hallaka dukkan iyalin Ba'asha, bisa ga maganar da Yahweh wanda ya faɗa akan Ba'asha ta bakin annabi Yehu,13saboda dukkan zunuban Ba'asha da zunuban Ela ɗansa su ka yi, da wanda su ka sa Isra'ila su ka yi, don sun tsokani Yahweh, Allah na Isra'ila, ya yi fushi da gumakunsu.14Game da sauran ayyukan Ela, da dukkan abin da ya yi, ba suna a rubuce a cikin littafin tarihi na sarakunan Isra'ila ba?15A shekara ta ashirin da bakwai da sarki Asa ke mulkin Yahuda, Zimri ya yi sarauta kwana bakwai a Tirzah. A lokacin nan sojoji sun yi sansani a Gibbeton, wanda ta ke ta Filistiyawa.16Sojojin da suka yi sansani a wurin suka ji an ce, "Zimri ya shirya makirci ya kashe sarki." A wannan rana a sansanin, dukkan mutanen Isra'ila suka naɗa Omri, shugaban sojojin, sarkin Isra'ila.17Omri kuwa ya tafi daga Gibbeton da dukkan mutanen Israila tare da shi, su ka kewayeTirzah da yaƙi.18Da Zimri ya ga an ci birnin sai ya tafi ya shiga hasumiyar da ta ke a fãdar sarki, ya sawa fãdar ginin wuta ta cinye duk da shi, ta wannan hanyar ya mutu a zafin wuta.19Wannan ya faru saboda da zunuban da ya aikata ta wurin aikata mugunta a fuskar Yahweh, ya bi hanyar Yerobowam da zunuban da ya sa mutanen Isra'ila suka yi zunubi.20Game da sauran ayyuka akan Zimri da makircin da ya aiwatar, ba a rubuce su ke ba a cikin littafin tarihi na sarakunan Isra'ila?21Sai mutanen Isra'ila suka rabu gida biyu. Rabin mutanen suka bi Tibni ɗan Ginat, don su naɗa shi sarki, rabi kuma suka bi Omri.22Amma mutane waɗanda suka bi Omri suna da ƙarfi fiye da mutanen da suka bi Tibni ɗan Ginat. Sai Tibni ya mutu, Omri kuwa ya zama sarki.23Omri ya fara sarauta akan Isra'ila a shekara ta talatin da ɗaya ta Asa sarkin Yahuda, ya yi shekaru goma sha biyu yana sarauta. Ya yi shekaru shida yana mulki a Tirzah.24Ya sayi tudun Samariya daga Shemer akan talanti biyu na azurfa. Ya gina birni a tudu aka kira sunansa birnin Samariya, bayan sunan Shemer, mai tudun.25Omri kuwa ya aikata mugunta a fuskar Yahweh, ya yi mugunta fiye da dukkan waɗanda suka riga shi.26Gama ya yi tafiya a dukkan hanyoyin da Yerobowom ɗan Nebat da irin zunubansa wanda ya sa Isra'ila suka yi zunubi, suka sa Yahweh, Allah na Isra'ila, fushi don gumakunsu na wofi.27Game da sauran ayyuka wanda Omri ya yi, da ƙarfinsa da ya nuna, ba suna nan a cikin littafin tarihin sarakunan Isra'ila ba?28Omri kuwa ya yi barci, aka bizne shi tare da kakaninsa a Samariya, Ahab ɗansa ya zama sarki a gurbin mahaifnsa29A shekara ta talatin da takwas ta Asa sarkin Yahuda, Ahab ɗan Omri ya fara sarauta a Isra'ila. Ahab ɗan Omri ya yi mulkin Isra'ila a Samariya shekaru ashirin da biyu.30Ahab ɗan Omri ya yi abubuwan da ke mugunta a fuskar Yahweh, fiye da dukkan waɗanda su ka riga shi.31Da ya ke Ahab abu ne mai sauki a gare shi ya bi zunuban Yerobowom ɗan Nebat, sai ya auro matarsa Yezebel 'yar Etba'al, sarkin Sidon; ya je yana bauta wa Ba'al, yana kuma yi masa sujada.32Ya gina bagadi domin Ba'al a gidan Ba'al, wanda ya gina a Samariya.33Ahab kuma ya yi turken gunkiyar nan Ashera. Ahab dai ya yi abin da zai tsokani Yahweh Allah na Isra'ila, zuwa fushi fiye da dukkan sarakunan Isra'ila waɗanda suka riga shi.34A lokacin sarautar Ahab, Hiyel na Betel ya gina Yariko. Hiyel ya sa tushen birni da farashin ran Abiram, ɗan farinsa; Segub, ɗan autansa, ya rasa ransa a lokacin da ya ke gina ƙofofin birnin, ta cikin ajiye maganar Yahweh wanda ya yi magana ta wurin Yoshuwa ɗan Nun.
Wannan habaicin na nufin maganar Yahweh. Duba yadda aka fassara shi a 6:11. AT: "Yahweh ya faɗi saƙonsa"
Wannan saƙon Allah ne da Yehu zai ba Ba'asha. Kalmar "ka" na nufin Ba'asha
"na ɗauke ka daga cikin ƙura." zama cikin ƙura a ƙasa na wakiltar rashin amfani. Dauke wani na nufin sa shi ya zama mai amfani. AT: "na ɗauke ka daga wuri marar amfani ƙwarai" ko "lokacin da baka da iko ko rinjaye wurin mutane, na mai da kai mai amfani"
Tafiya na wakiltar rayuwa. Yeroboam da Ba'asha dukka sun yi zunubi. Ma'anar wannan shi ne. AT: "ka yi irin abinda Yeroboam ya yi" ko "ka yi zunubi kamar yadda Yeroboam ya yi zunubi"
Yahweh ya ci gaba da gayawa Ba'asha abinda zai yi masa.
Yahweh na magana da Ba'asha, kuma jimlar "iyalinsa"na nufin iyalin Ba'asha. Za mu iya fassara shi kalmar "kai" da "naka". AT: "ka saurara, zan share ka da iyalinka gaba ɗaya"
share wa na nufin hallakarwa. AT: "zan hallakar gaba ɗaya"
Wannan tambayar an yi ta ne ko a faɗa ko a tunasheda mai karatu bayanai game da Ahijana nan a wannan littafin. Duba yadda aka fassara a 15:31. wannan tambayar da bata buƙatar amsa za a iya cewa. AT: "ba su na nan ba a rubuce a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda?"
za a iya cewa. AT: "wani ya rubuta game da shi a littafin tarihi na sarakunan Isra'ila ba?."
Barci kalma ce ta kwantar da hankali da yake wakiltar mutuwa. AT: "Ba'asha ya mutu kamar yadda kakaninsa suka yi" ko "kamar kakaninsa, Ba'asha ya mutu"
za a iya sa shi a aikatau. AT: "mutane suka bizme shi"
Wannan sunan birni ne. Duba yadda aka fassara shi a 14:17
Jimlar "a gurbinsa" kwatanci ne na "maimakon shi." AT: "ya zama sarki a maimakon Ba'asha"
Wannan habaici ne aka yi amfani da shi a gabatar da wani abu da Allah ya gaya wa annabawan sa ko mutanen sa. Duba yadda aka fassara shi a 6:11. AT: "Yahweh ya yi maganar" ko "Yhaweh ya yi faɗi waɗannan kalmomi"
Fuskar Yahweh wakili ne na hukuncin Yahweh. AT: "dukkan muguntar da Ba'asha ya yi a hukuncin Yahweh" ko "dukkan abubuwan da Ba'asha ya yi da Yahweh ya ga mugunta ne"
sunan "fushi" za a iya sa yi a fayyace "fushi." AT: "saboda a sa Yahweh ya yi fushi" ko "cewa sun sa Allah ya yi zunubi"
Hannu na wakiltar Ba'asha ko ayyukansa. AT: "ayyukan da Ba'asha yayi"
Wannan sunan birni ne. Duba yadda aka fassara shi a 14:17.
"bawan Ela Zimri"
Kalmar "karusai" anan na wakiltar sojojin waɗanda suke hawan karussa. AT: "shugaban rabin direbobin karusansa"
Wannan habaici ne. AT: "shan giya da yawa sha ya sa shi ya bugu" ko "buguwa"
Lura da iyalin wakili ne na zama shugaba na abubuwa a gidan Sarki Ela. AT: "wanda ke lura da al'amuran gidan sarki Ela"
"kai hari da kuma kashe shi"
Wannan "a gurbinsa" kwatanci ne na ma'anar "a maimakon sa." AT: "ya zama sarki a maimakon Ela"
Wannan na nufin ya kashe dukkan mazaje da yara maza. AT: " bai bar ko na miji ɗaya a raye ba"
"saƙon Yahweh" ko "saƙo daga Yahweh"
Magana "daga" na nufin gaya wa annabin ya faɗa annabin kuma yana faɗa. AT: "da Yahweh ya gaya wa Yehu ya faɗa akan Ba'asha"
jagorantar mutane su ui wani abu shine rinjayar su suyi. AT: "sun rinjayi Isra'ila su yi zunubi"
Allah ya yi fushi da mutanen saboda sun bautawa gumaka. Ma'anar wannan shine. AT: "sun sa Yahweh, Allahn Isra'ila, ya yi fushi saboda sun yi wa gumak sujada"
A nan kalmar "Isra'ila" na nufin dukkan ƙabilai goma sha biyu da suka fito daga Yakubu.
Wannan tambaya ce aka yi amfani da ita ko a faɗa ko kuma tunashe da mai karatu cewa bayani game da Ela yana waɗansu littafi. Wannan tambayar da bata ɓuƙatar amsa za a iya cewa. Duba yadda aka fassara shi a 15:31. AT: "an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila."
za a iya bayyana wanna a matsayin aikatau. AT: "wani ya rubuta su a littafin tarihin na sarakunan Isra'ila."
Wannan sunan sunan birni ne. Duba yadda aka fassara shi a 14:17.
Kalmar "sojoji" na nufin sojojin mulkin Isra'ila.
Wannan sunan birnni ne. Dubi yadda aka fassara shi a 15:27.
za a iya sa shi a aikatau. AT: "16Sojojin da suka yi sansani a wurin suka ji an ce"
Yawancin lokaci an yi amfani da shi, ya na wakiltar sojojin Isra'ila. Anan kalmar "dukka" gaba ɗaya ne da yake nufin "mafi mahimmanci." AT: "dukkan sojojin Isra'ila" ko "mafi muhimmanci a cikin sojojin Isra'ila" ko "sojojin Isra'ila"
za mu iya cewa. AT: "cewa Omri da sojojin sun ɗauke birnin"
Fuskar Yahweh na wakilta hukuncin Yahweh. AT: "abinda ya ke mugu a idon Yahweh" ko "abinda Yahweh ya Dauka ya mugunta"
A nan tafiya na nufin rayuwa. AT: "yin irin abin da Yeroboam ya yi"
Jagorantar mutane su yi wani abu na wakiltar rinjayarsu su yi. AT: "saboda ya rinjayi Isra'ila su yi zunubi"
Cin amana na nufin shirin Zimri na kashe Ela, sarkin Isra'ila. Ma'anar wannan shi ne. AT: "yadda ya shirya wa sarkin Ela" ko "yadda ya kashe sarkin Isra'ila"
Wannan tambaya ce aka yi amfani da ita ko a faɗa ko kuma tunashe da mai karatu cewa bayani game da Zimri yana waɗansu littafi. Wannan tambayar da bata ɓuƙatar amsa za a iya cewa. Duba yadda aka fassara shi a 14:29. AT: "an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila."
za a iya cewa. AT: "wani ya rubuta game da su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila."
A nan "bi" na nufin goyon baya ko son su mai da shi sarki. AT: "goyon bayan Tibni ɗan Ginat, rabi kuma suka goyi bayan Omri" ko "son su mai da Tibni ɗan Ginat sarki, rabi kuma suna son sa Omri sarki"
"sun yi rinjaye akan mutanen da suka bi Tibni"
Wannan sunan birni ne. Duba yadda yake a 14:17.
Wannan sunan na miji ne.
Za ka iya canza wannan zuwa ma'auni na zamani. AT: "68 kilogiran azurfa"
Kalmar "ya" na nufin Omri. Ya umarci mutane su gina birnin. AT: "Omri ya sa mutanen sa su gina birnin" ko "Omri ya yi bada umarni, mutanensa suka gina birnin"
Wannan habaici ne ma'ana "a girmama Shemer" ko "domin mutana su tuna da Shemer"
Fuskar Yahweh na nuna hukuncin Yahweh. AT: "abinda yake mugu a hukuncin Yahweh" ko "abinda Yahweh ya ga mugunta ne"
Tafiya na wakiltar rayuwa. AT: "ya yi dukkan abin da Yeroboam ɗan Nebat ya yi"
Wa su ma'anoni sune "sa" da "nasa" na nufin 1) Ba'asha 2) Yeroboam.
Waɗansu ma'anoni sune tafiya cikin zunubinsa 1) yin zunubi kamar yadda Yeroboam yayi. AT: "yayi zunubi kamar yadda Yeroboam ya yi" 2) zunubi kullum. AT: "ya na zunubi kullum"
Jagorancin mutane su yi zunubi na wakiltar rinjayar zuwa zunubi. AT: "zunubinsa, ta haka ya rinjaye Isra'ila suka yi zunubi" ko "ta yin irin wannan zunubin, ya rinjayi mutane su ka yi zunubi."
Allah ya yi fushi da mutanen saboda sun yi wa gumaka sujada. Duba yadda aka fassara irin wannan jimlar a 16:11. AT: "a sa Yahweh, Allah na Isra'ila, fushi saboda sun yi wa gumaka na wofi sujada"
Kalmar "wofi" anan na tunashe da mutanen cewa gumaka wofi ne saboda ba za su iya yin komai ba. AT: "gumakansu, waɗanda wofi" ko "gukansu, waɗanda wofi ne"
a nan kalmar "Isra'ila" na nufin dukkan ƙabilai goma sha biyu da suka fito da Yakubu.
Wannan tambaya ce aka yi amfani da ita ko a faɗa ko kuma tunashe da mai karatu cewa bayani game da Omri yana waɗansu littafi. Wannan tambayar da bata ɓuƙatar amsa za a iya cewa. Duba yadda aka fassara shi a 15:31. AT: "an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila."
za a iya cewa. AT: "wani ya rubuta game da su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila."
Kalmar kwantar da hankali "barci" anan na wakiltar mutuwa. AT: "Omri ya mutu kamar yadda kakaninsa suka mutu" ko "kamar kakanisa, Omri ya mutu"
Jimlar "a gurbinsa" kwatanci ne na "a maimakonsa." AT: "ya zama sarki maimakonsa"
Fuskar Yahweh na wakiltar hukuncin Yahweh. AT: "abin da ka mugu a hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ga muguntane"
Ya nuna Ahab na shirin yin mummunan zunubi. Ma'anar wannan maganar zai iya AT: "kamar Ahab yana ganin cewa ya yi tafiya a zunubin Yeroboam ɗan Nebat bai ishe ba"
Wannan habaici ne. Jimlar "ga Ahab" ya ga ko ya yi tunani wani abu. AT: "da yake Ahab abu ne mai sauki " ko "Ahab na ganin bai isa ba"
"abu da bai isa ba" ko "kaɗan"
Tafiya a zunubin Yeroboam na nufin yin zunubi yadda Yeroboam ya yi. AT: "yin zunubi yadda Yeroboam ɗan Nebat yayi"
Waɗannan jimloli na nufin abu ɗaya. Jimlar "yi masa sujada" nu nuna yadda mutane suke sunkuyawa suyi sujada.
A nan kalmar "Isra'ila" na nuna ƙasar Isra'ila, wanda ya haɗa da ƙabilai goma sha biyu.
A nan kalmar "Isra'ila" na nuna mulkin Isra'ila, wanda ya ƙunshi ƙabilai goma.
Sakamakon ginin birnin an yi maganar shi kamarwani farashi ne da za a biya. AT: "sakamakon zunubinsa shi ne ɗansa Abiram, ya mutu"
Mutuwa an yi maganar ta kamar ya rasa ransa AT: "Segub, ɗan autansa, ya rasa ransa"
"da ya ke gina ƙofofin birnin"
"bisa ga maganar Yahweh "
A nan kalmar "Yahweh" na nufin saƙo. AT: "saƙon yahweh"
Magana "ta" wani na wakiltar gaya wa wani ya faɗa da kuma mutumin da zai yi. AT: "wadda Yahweh ya sa Joshua ɗan Nun ya faɗa"
1Iliya Batishbe, daga Tishbi a Giliyad, ya ce da Ahab, "Kamar yadda Yahweh, Allah na Isra'ila ya ke raye wanda nake tsaye a gabansa, ba za a yi raɓa ko ruwan sama a waɗannan shekaru sai da faɗata."2Maganar Yahweh ta zo ga Iliya, cewa,3"Tashi daga nan ka tafi wajen gabas; ka ɓoye kanka a rafin Kerit, gabashin Yodan.4A can zai zamana inda za ka riƙa samun ruwan sha daga rafin, na kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can."5Iliya kuwa ya tafi, ya yi yadda Yahweh ya umarta. Ya tafi ya zauna a rafin Kerit, gabas da Yodan.6Hankaki kuwa suka riƙa kawo masa abinci da nama da safe abinci da nama da maraice, yana shan ruwa daga rafin.7Amma bayan wani ɗan lokaci sai rafin ya ƙafe saboda ba a yin ruwan sama a ƙasar.8Sai maganar Yahweh ta zo ga Iliya, cewa.9"Tashi ka tafi Zarefat, wadda da ta ke ta Sidon, ka zauna a can. Duba, na umarci wata mace gwauruwa ta ciyar da kai."10Shi kuwa ya tashi ya tafi Zarefat, sa'ad da ya isa ƙofar birnin sai ga wata gwauruwa a wurin ta na tattara itace. Sai ya kira ta ya ce, "Idan kin yarda ki kawo mani ɗan ruwa in sha."11Tana juyawa za ta tafi ta kawo masa ruwan sha kenan, sai ya kira ta ya ce, "Idan kin yarda ki ba ni ɗan abinci a hannunki."12Sai ta amsa, "Kamar yadda Yahweh Allahnka ya ke da rai, ba ni da abinci, sai dai ɗan garin da ya ragu a tukunya da ɗan man da ke cikin kwalba. Ga ni, ina tattara yan itatuwa biyu don in je in girka shi domin ni da ɗana, mu ci, mu mutu."13Iliya ya ce mata, "Kada ki ji tsoro. Tafi ki yi yadda na ce, amma ki fara yi mani gurasa kaɗan tukuna ki kawo mani. Sa'an nan ki yi wa kanki da ɗanki.14Gama Yahweh Allah na Isra'ila, ya ce, 'Garin da ya ke a tukunyarki ba zai ƙare ba, ko da man ma ba zai dena zubuwa ba, sai dai ranar da Yahweh ya aiko da ruwan sama a duniya."15Ta tafi ta yi yadda Iliya ya faɗa mata. Ita da Iliya da sauran yan gidan, sun ci har kwanaki da yawa.16Garin bai ƙare ba, kwalbar man ma bata dena zubuwa ba, kamar yadda maganar Yahweh ta ce, kamar kuma yadda Iliya ya faɗa.17Bayan waɗannan abubuwa sai ɗan macen, matar wadda take da gidan, ya yi ciwo. Ciwonsa kuwa ya tsananta har ba sauran numfashi a cikinsa.18Sai mahaifiyar yaron ta ce da Iliya, "Me ya haɗa ni da kai, ya mutumin Allah? Ka zo gare ni ne don ka tuna ma ni da zunubina ka kuma kashe ɗa na?"19Sai Iliya ya amsa ma ta, "Ki ba ni ɗanki." Ya ɗauki yaron daga hannuwanta, ya kai shi a ɗaki inda ya ke zama, ya kwantar da yaron akan gadonsa.20Ya yi kuka ga Yahweh ya ce, "Yahweh Allahna, ka kuma kawo masifa akan gwauruwar nan wadda na ke zaune wurinta, ta wurin kashe mata ɗa?21Sa'an nan Iliya ya kwanta ya miƙe akan yaron sau uku, ya kuma yi kuka sosai ga Yahweh ya ce, "Yahweh Allahna, ina roƙonka, idan ka yarda bari ran yaron nan ya komo gare shi."22Yahweh kuwa ya saurari muryar Iliya; ran yaron ya komo gare shi sai ya farfaɗo.23Iliya ya ɗauki yaron daga ɗakinsa ya kawo shi ya kai shi cikin gida; ya bada yaron ga uwar ya ce, "Ki gani, ɗauki yaronki yana da rai." Matar kuwa ta cewa Iliya,24"Yanzu na sani kai mutumin Allah ne, kuma maganar Yahweh kuwa da ke cikin bakinka gaskiya ce."
Wannan sunan ƙungiyoyin mutane ne daga Tishbi.
Wannan sunan gari ne a yankin Gileyad.
Wannan jimlar ratsuwa ce a jaddada abin da za a ce gaskiya.
Wannan habaici ne ma'ana "a bauta". AT: "wanda na ke bautawa"
ɗigon ruwa da yake saukowa akan tsirai da dare
Wannan habaicin na nufin Allah ya yi magana. yadda aka fassara shi a 6:11. AT: "Yahweh ya faɗi saƙonsa"
Wanan sunan wa ƙaramin rafi ne.
Wannan jimlar an yi amfani da shi a gabatar da yadda Yahweh zai lura da Iliya lokacin fãri. AT: "a can"
manyan, baƙaƙen tsuntsaye
A nan "kalmar" na wakiltar Yahweh da kansa. AT: "yadda Yahweh ya umarta"
Wannan sunan wani ƙaramin rafi ne. An fassara shi a 17:2.
"a yankin" ko kuma "a wancan ƙasa"
Wannan habaici ne ma'ana Allah ya yi magana. Duba yadda aka fassara shi a 6:11. AT: "Yahweh ya faɗi saƙonsa"
A nan kalmar "shi" na nufin Iliya.
Wannan gari ne. (Duba: trnaslate_names)
Kalmar "Duba" a nan ya ƙara jaddada abin da zai biyu baya.
Wannan jimla rantsuwa ce da ta jaddada cewa abin da za a ce gaskiya.
"abinci kaɗan"
"garin alkama" Wannan abinda ake amfani da shi a yi burodi.
Kalmar "gani" anan ta ƙara jaddada abin da zai biyo baya.
Wannan zai iya zama 'yan itatuwa biya ko 'yan itatuwa. (Duba: trnaslate_numbers)
Ya nuna cewa za su mutu saboda basu da sauran abinci. AT: "da zamu ci bayan nan, yunwa ya kashe mu"
Ya na nuna cewa za a sami garin alkama da mai da za a sake yin wani.
Wannan habaici ne ma'ana Yahweh ya sa a yi ruwan sama. AT: " Yahweh ya sa aka yi ruwan sama"
Harshe na ainahi ya ce, "da ita da shi da 'yan gindata suka ci har kwanaki da yawa." ba a gane ko wanene "shi" ba. Zai iya zama 1) iliya, gwauruwa, suka ci har kwanaki da yawa ko 2) gwauruwar, ɗanta, da dukkan wanda ke raye a gidanta suka ci har kwanaki da yawa ko 3) Iliya, gwauruwa, da dukkan rayayye na gidanta suka ci har kwanaki da yawa.
zai iya yiwuwa "'yan gidanta" sune 1) 'ya yan gwauruwan 2) mutanen da suke zama a gidanta amma ba a sa su a cikin labarin ba ko 3)'ya'yanta da sauran rayayyu da suke zama a gidanta.
A nan "magana" na wakiltar Yahweh da kansa. AT: "kamar yaddad Yahweh ya ce"
"ɗan macen, wadda take da gidan"
Wannan wata hanya ce ta cewa yaron matar ya mutu. AT: "ya daina numfashi" ko "ya mutu"
Jimlar "mutumin Allah" wani suna ne na annabi.
Wannan na nufin zunubi gaba ɗaya ba wai wani zunubi dabam ba. AT: "zunubina"
A nan "ya'' na nufin Iliya.
A nan "sa" na nufin Iliya.
Wasu ma'anoni 1) Iliya na yin tambaya sosai. AT: "don me za ka sa gwauruwa da nake zama da ita ta sha wuya har ma da kashe ɗanta" 2) Iliya ya yi amfani da tambaya ya nuna baƙin cikinsa. AT: " lailai, ba za ka sa gwauruwa da na ke zama da ita ta sha wahala har ma da kashe yaronta"
Don sa gwauruwa ta sha wahala an yi maganarsa kamar "masifa" abu ne da aka ɗora wa gwauruwar.
A nan "kuma" ƙari akan masifar da fãri ya kawo.
Wannan habaici ne. AT: "kwanta a kan yaron"
A nan "murya" na wakiltar abinda Iliya ya yi addu'a akai. AT: "Yahweh ya amsa addu'ar Iliya"
Waɗannan jimloli guda biyu na nufin abu ɗaya. AT: "yaron ya dawo da rai " ko "yaron yansake rayuwa"
A nan "sa" na nufin Iliya.
Kalmar "ki gani" anan ya na jan hankalinmu mu gane bayani na bammamaki da ya biyo baya.
A nan "magana" na nufin saƙon Yahweh. Kuma "baki" na wakiltar abinda Iliya ya ce. AT: "saƙon da ka faɗa daga Yahweh gaskiya ce"
1Bayan kwanaki masu yawa sai maganar Yahweh ta zo ga Iliya, a shekara ta uku ta farin, cewa,2"Tafi, ka nuna kanka ga Ahab zan aiko da ruwan sama a ƙasar." Iliya kuwa ya tafi ya nuna kansa ga Ahab; yanzu kuwa yunwa ta tsananta a Samariya.3Ahab ya kira Obadiya, wanda ya ke shugaban fada. Obadiya kuwa yana girmama Yahweh sosai,4domin lokacin da Yezebel ta karkashe annabawan Yahweh, Obadiya ya kwashe annabawa ɗari ya raba su hamsin, hamsin ya ɓoye su a kogo, ya ciyar da su da gurasa ya kuma shayar da su.5Ahab ya cewa Obadiya, "Tafi cikin ƙasar nan duk inda maɓuɓɓugar ruwa da fadamu suke. Watakila ma sami ciyawa mu ceci rayukan dawakai da alfadarai, don kada mu rasa dukkan dabbobin nan."6Saboda haka suka raba ƙasar a tsakaninsu suka shige ta su duba inda ruwa ya ke. Ahab ya bi ɗaya hanyar da kansa Obadiya kuma ya tafi wata hanyar.7Sa'ad da Obadiya ya ke tafiya a hanya, Iliya ya yi kaciɓus da shi. Obadiya ya gane da shi sai ya russana a ƙasa. Ya ce, "Kai ne shugabana Iliya?"8Iliya ya amsa masa. "Ni ne. Tafi ka faɗa wa shugabanka, 'Duba, Iliya na nan.'"9Obadiya ya amsa, "Wanne zunubi na yi, har da za ka bada bawanka a cikin hannun Ahab, domin ya kashe ni?10Kamar yadda Yahweh Allahnka ya ke raye, babu wata al'umma ko mulki da shugabana bai aika mutane a nemo ka ba. Duk wata al'umma ko mulki suka ce, 'Iliya ba ya nan,' Ahab ya sa su ɗauki rantsuwa ba su same ka ba.11Amma yanzu ka ce, "Tafi, faɗa wa shugabana cewa ga Iliya a nan.'12Ya yin da na tafi daga wurin ka, Ruhun Yahweh ya kai ka wurin da ban sani ba. Don haka idan na tafi na faɗa wa Ahab, idan kuma bai same ka ba, zai kashe ni. Ko da ya ke ni bawanka, ina bauta wa Yahweh tun daga kuruciyata.13Ashe ba a faɗa maka ba, shugabana, abin da na yi a lokacin da Yezebel ta kashe annabawan Yahweh, abin da na yi na ɓoye annanbawan Yahweh ɗari na raba su hamsin hamsin a kogo na kuma ciyar da su da gurasa da ruwa?14Yanzu kuwa ka ce da ni, "Tafi in faɗa wa shugabana ga Iliya a nan,' ai zai kashe ni."15Sai Iliya ya amsa, "Kamar yadda Yahweh mai runduna ya ke da rai, wanda nake tsaye a gabansa, hakika zan nuna kaina ga Ahab yau."16Saboda haka sai Obadiya ya tafi ya sadu da Ahab, ya faɗa masa abin da Iliya ya ce. Sai sarki ya tafi ya sadu da Iliya.17Lokacin da Ahab ya ga Iliya, ya ce masa, "Kai ne? wanda ke kawo wahala ga Isra'ila!"18Iliya ya amsa, "Ba ni ne na kawo wahala a Isra'ila ba, amma kai da iyalin mahaifinka su ne waɗanda suka jawo wahala ta wurin ƙin bin umarnan Yahweh kuna bin Ba'aloli.19Yanzu sai, ka aika da magana a tattara mani dukkan Isra'ila a Tsaunin Karmel, tare da annabawan Ba'al 450 da ɗari huɗu na annabawan Ashera waɗanda ke ci a teburin Yezebel."20Sai Ahab ya aika da magana ga dukkan mutanen Isra'ila da su tara annabawa gaba ɗaya a Dutsen Karmel.21Iliya ya zo kusa da dukkan mutane ya ce, "Har yaushe ne za ku ci gaba da canza tunaninku? Idan Yahweh ne Allah, ku bi shi. Amma idan Ba'al shi ne Allah, sai ku bi shi." Duk da haka mutane ba su amsa masa da magana ba.22Sai Iliya cewa mutane, "Ni, kaɗai ne na rage a matsayin annabin Yahweh, amma annabawan Ba'al su ɗari huɗu da hamsin.23Ku ba mu bijimai biyu. Bari su zaɓi ɗaya bijimin don kansu su yanyanka gunduwa gunduwa, su shimfiɗa su akan itacen, kada a sa masa wuta a ƙarƙashinsa.24Sai ku yi kira ga sunan allahnku, ni ma zan yi kira ga sunan Yahweh, duk Allahn da ya amsa da wuta bari ya kasance Allah. "Dukkan mutane suka amsa suka ce, "Wannan ya yi kyau."25Sai Iliya yace da annabawan Ba'al, "Ku zaɓi bijimi ɗaya domin kanku ku kuma shirya shi da farko, gama kuna da mutane da yawa. Sa'an nan ku yi kira ga sunan allahnku, amma kada kuma fa ku sa wuta a ƙarƙashi bijimin."26Suka ɗauki bijimin da aka ba su suka shirya shi, suka yi kira da sunan Ba'al tun daga safe har rana ta yi tsaka, suna cewa, "Ba'al, ka ji mu mana." Amma babu wata murya, ko wani da ya amsa. Suka yi ta rawa a kewayan bagadin da suka gina.27Da rana ta yi tsaka sai Iliya ya yi masu ba'a ya ce, "Ku yi ihu da ƙarfi! Shi allah ne! Watakila ya yi tafiya da nisa, ko watakila yana barci ne, sai ku tashe shi."28Suka yi ihu da ƙarfi sosai, suna kuma tsattsaga jikunansu, kamar yadda suke yi, tare da takubba da mãsu, har jini yana ta zuba daga jikunansu.29Da tsakar rana ta wuce, sai su kai ta yin sambatu har lokacin baikon hadayar yamma, amma ba bu wata murya ko wani wanda ya amsa; babu wani wanda ya kula da roƙe -roƙensu.30Sai Iliya yace da dukkan mutane, "Ku zo kusa da ni," dukkan mutane kuwa suka zo kusa da shi. Ya gyara bagadin Yahweh wanda aka lalatar.31Iliya ya ɗauko duwatsu goma sha biyu bisa ga yawan 'ya 'yan Yakubu, ga Yakubu wanda maganar Yahweh ta zo, cewa, "Isra'ila ne zai zama sunanka."32Tare da duwatsun ya gina bagadi da sunan Yahweh, ya kuma haƙa rami babba sosai kewaye da bagadin isasshe da zai ci durom biyu na hatsi.33Ya shirya itacen wuta, ya yanyanka bijimin gunduwa gunduwa, ya shimfiɗa shi bisa itacen. Ya ce, "Ku cika tuluna da ruwa a kwarara akan hadaya ta ƙonawar da kuma kan itacen."34Ya kuma ce, "Ku yi haka har sau lokaci na biyu," Suka yi haka a lokaci na biyu. Ya ce, "Su sake yi a lokaci na uku," suka yi haka a lokaci na uku.35Ruwa kuwa ya malale bagadin, ya kuma cika ramin.36Ya zama kuwa a lokacin miƙa hadaya ta maraice, sai Iliya annabi ya matso kusa ya ce, "Yahweh, Allah na Ibrahim, na Ishaku da Isra'ila, bari ya zama sananne a wannan rana cewa kai ne Allah a Isra'ila, ni kuma bawanka ne, na yi waɗannan abubuwa dukka bisa ga maganarka.37Ka ji ni, Yahweh, ka ji ni, saboda waɗannan mutane su san ka, kai ne Yahweh, Allah, kai ne kuma ka juyo da zuciyarsu gare ka kuma."38Sai wutar Yahweh ta faɗo, ta cinye hadaya ta ƙonawa, duk da itacen, da duwatsun da kurar, ta kuma lashe ruwan da ya ke cikin ramin.39Sa'ad da dukkan mutanen suka ga wannan, suka russana suka sunkuyar da kai suka ce, "Yahweh, shi ne Allah! Yahweh, shi ne Allah!"40Iliya kuma ya ce masu, "Ku kama annabawan Ba'al. Ka da ku bar ko ɗaya daga cikinsu ya tsere." Sai suka kama su, Iliya ya kai annabawan Ba'al rafin Kishon, ya karkashe su a can.41Iliya ya cewa Ahab, "Tashi, ka ci ka sha, gama akwai motsin saukowar ruwan sama."42Sai Ahab ya haura don ya ci ya sha. Iliya ya tafi can konkoli Karmel, ya zauna a ƙasa ya haɗa kai da gwiwa.43Ya ce da baransa, "Ka tafi ka duba wajen teku." Baran ya tafi ya duba, ya ce, "Ba bu kome." Sai Iliya ce, "Tafi kuma, har sau bakwai."44A zuwa na bakwai sai ya ce, "Na ga wani ɗan girgije yana zuwa daga teku, karami kamar tafin hannun mutum." Iliya ya amsa, "Tafi ka faɗa wa Ahab, 'Ya shirya karusarsa ya kuma gangara domin kada ruwan sama ya tsaida shi.'"45Ya zamana fa jim kaɗan sai sararin sama ya yi baƙi ƙirin da giza-gizai da iska, aka yi ruwan sama mai yawan gaske. Ahab ya hau ya tafi wurin Yezriyel,46amma hannun Yahweh yana tare da Iliya. Ya sha ɗammara ya sheka a guje ya riga Ahab isa Yezriyel.
"magana" wakili ne na abinda mutum ya ce. Duba yadda aka fassara shi a 6:11. AT: "Yahweh ya faɗi maganarsa"
"Ya sa aka yi ruwan sama"
Kalmar "yanzu" an yi amfani da shi a kawo tsaiko a asalin labari. A nan marubuci ya nunamatashiyar bayanai game da yadda yunwa ta tsanantawa Samaria. (Duab: writingz-background)
Kalmar "yanzu" an yi amfani da shi a kawo tsaiko a asalin labarin. A nan marubuci ya yi magana game da sabon mutum a labarin.
"100 annabawa ya ɓoye su a ƙungiyance hamsin, hamsin"
Wannan jimlar biyu na magana akan abu ɗaya. AT: "mu ceci dawakai da alfadarai daga mutuwa"
Jimlar "da kansa" na jaddada Ahab da Obadiya sun tafi ta hanya dabam-dabam, ba wai lailai ba kowa tare da Ahab. AT: "Ahab ya jagoranci ƙungiya a ɓangare ɗaya, Obadiya ya jagoranci ƙungiya a ɗaya ɓangaren"
A nan kalmar "shugaba" an yi amfani da ita a nuna girmamawa.
A nan kalmar "shugaba" na nufin Ahab.
Kalmar "duba" anan ta ƙara jaddada akan abinda zai biyo.
Obadiya ya yi wannan tambayar ya jaddada hatsari akansa saboda fushin sarki Ahab akan Iliya. AT: "ban ɓata maka ba ... da zai kashe ni."
"hannu" wakili ne na iko. AT: "ka ba da bawanka ga Ahab"
Obadiya ya nuna kansa a matsayin bawan Iliya domin ya girmama Iliya.
Wanna rantsuwa ne a jaddada abin da zai biyo gaskiya ce.
za a iya cewa "shugabana ya aiki mazaje"
wannan jimlar na jaddada hatsarin abinda Iliya ya ke faɗa wa Obadiya ya yi.
za mu iya cewa. "haƙaƙa an faɗa maka game da abind nayi ... da gurasa da ruwa!"
A nan kalmar "shugaba" kalmar ban girma ce ga Iliya.
"100 na annabawan Yahweh a ƙungiya hamsin- hamsin"
An fassara wannan a 18:9.
A nan "shugaba" na nufin sarki Ahab.
Wannan ratsuwa ne a jaddada cewa abin da za a faɗa gaskiya ne.
A "tsaya gaban" habaici ne na zama a gaban wani kuma a shirye a bauta masa. AT: "wanda nake bautawa"
"Obadiya ya faɗa wa Ahab abinda Iliya ya faɗa masa ya ce"
Ahab ya yi tambayar domin jaddada wasu game da kowanene Iliya. AT: "to kana nan, Kaine mai jawowa Isra'ila wahala!"
Wannan gaba ɗaya ne ana nufin shugabanni da mutane na ƙabilai goma na arewacin mulkin.
"annabawa ɗari huɗu da hamsin"
"magana" wakili ne naabinda mutum ya ce. Wannan bayani na da ake yin amfani da shi a yawancin lokuta. AT: "aika wa da saƙo"
Iliya ya yi wannan tambayar da begen mutane za su yanke shawara. AT: "an daɗe ana cutarku."
"ban ce komai ba" ko "na yi shiru"
Kalmar "Ni" an mamatashi don a jaddada.
"suna" wakili ne na Daukaka da girmama wani "kira ga" na nuna roƙo. AT: "ka kira allanka ... kira Yahweh"
"dakkan mutane su ka ce, 'wannan abu mai kyau ayi ne."
"ku sa ya yi dai-dai domin hadaya"
A nan kalmar "ku" na nuna da yawa.
"annabawan ba'al suka ɗauki bijimin"
za a iya cewa. AT: "bijimin da wani ya ba su"
Waɗannan jimloli na nufin abu ɗaya kuma suna nufin da jaddada cewa ba wani da ya amsa addu'ar annabawan ƙarya. AT: "amma Ba'al bai amsa ko yin wani abu ba"
"ƙila" ko "ta iya yiwuwa"
Habaicin na da ban sha'awa a a nuna bayani mummuna. Iliya yayi amfani da wannan ya zagi ba'al da sarcasm. AT: "a bayan ɗaki"
zamu iya cewa. AT: "sai kun tashe shi" ko "sai ya farka"
"sun ci gab da yin abu kamar namomin jeji." annabawan suka ci gaba da yin abu mara kan gado ko na hauka. A nan suna kiran Ba'al da rawa, ihu,ihuda ƙarfi da tsattsaga jikunan su da wuƙaƙe.
"a miƙa hadayar yamma"
Waɗannan jimlolin suna maganar abu ɗaya ne kuma suna ƙara jaddada cewa ba wanda ya amwsa addu'o'in annabawan ƙarya. AT: "amma Ba'al ba ce ko yi komai ba ko kuma ya kula da roƙe-roƙensu"
an fassara wannan a 18:25.
"duwatsu 12"
"suna" wakili ne na girmamawa da darajartawa. wasu ma'anonin sune 1) "a girmama Yahweh" ko 2) da ikon Yahweh.
abin sa ruwa ƙaramin
durom wani ma'auni ne da zai iya cin kusan 7.7 lita. AT: "kusan lita 15 na hatsi"
"akan alfarwa" inda ya sa itacen za mu iya cewa a nan. AT: "ya sa itacen domin wuta akan alfarwa"
"tuluna 4"
An fassara shi a 1 Kings 18:30
Wannan magana ana amfani da shi nuna gagarumin lokaci mai ma'ana na kwanaki a labarin. Idan yarenka yana da hanyar sa shi, za ka iya sa wa anan.
A nan "Isra'ila" na nufin Yakuba. Allah ya canza sunan Yakubu zuwa Isra'ila (Farawa32:28), da Allah ya sa wa ƙasar Yakubu sunan zuriyar "Isra'ila."
za mu iya cewa. AT: "bari mutanen nan su sani yau"
Wannan maganar an maimaita ta domin a jaddada roƙon Iliya ga Yahweh.
" ka juyo da zuciyarsu kuma.''" wakili ne na soyayya da biyayya na mutane. AT: "ka sa su zama masu yi maka biyayya kuma"
"wutar Yahweh ta zo ƙasa"
wutar an kwatanta ta da mutum wanda ya ke jin ƙishirwa.
Wannan maganar an maimata ta domin a jaddada.
"rafi" karamin wurin ruwa ko inda ruwa ke zama.
"na ji kamar za a yi ruwan sama sosai"
Wannan ya nuna yanayi da ake yin addu'a.
Kalmar "bakwai" za a iya barin su lambobi "7" AT: "sau bakwai"
Daga nesa, jido za a iya rufe shi da tafin hannun mutum.
Wannan maganar an yi amfani da shi a fara inda sabo salo na aiki ya fara. idan yarenka na da wata hanya ta sa wannan ka iya yi amfani da shi.
A nan kalmar "hannu" wakili ne na ƙarfi. AT: "Yahweh ya ba da ƙarfin sa ga Iliya" (Duba:
Iliya ya sa dogon ɗammarasa a ƙugun sa saboda ƙafafunsa su sami sararin gudu.
1Ahab ya faɗa wa Yezebel dukkan abin da Iliya ya yi da yadda ya kashe dukkan annanbawa da takobi.2Sai Yezebel ta aika wurin Iliya, cewa, "Bari alloli su yi mani, harma fiye kuma, idan ban mai da ran ka kamar ran ɗaya daga waɗannan annanbawa gobe a dai-dai wannan lokacin ba."3Sa'ad da Iliya ya ji haka, ya ji tsoro, ya tsere domin ransa ya zo Biyasheba, wadda take ta Yahuda, ya bar baransa a can.4Amma shi da kansa ya yi tafiyar yini guda cikin jeji, ya zo ya zauna a gindin itacen aduwa. Ya yi roƙo domin kansa yadda zai mutu, ya kuma ce, "Ya isa haka, yanzu, Yahweh; ɗauke raina, gama ban fi kakannina ba."5Sai ya kwanta ya yi barci a gindin itace aduwa. Farat sai mala'ika ya taba shi, ya ce masa, "Tashi ka ci abinci."6Da Iliya ya duba, kusa da kansa sai ga gurasa ana gasawa akan garwashi da butar ruwa. Ya ci, ya sha, ya koma ya kwanta kuma.7Mala'ikan Yahweh kuma ya sake zuwa sau na biyu ya taɓa shi, ya ce, "Tashi ka ci abinci, gama tafiyar za ta yi maka yawa.8Sai ya tashi ya ci ya sha, ya sami ƙarfin tafiya da wannan abincin har kwana arba'in dare da rana zuwa Horeb, wato tsaunin Allah.9Ya tafi wani kogo a can ya tsaya a cikinsa. Sai maganar Yahweh ta zo wurinsa ta ce da shi, "Me kake yi a nan, Iliya?10Iliya ya amsa, "Ni mai kishi domin Yahweh, Allah mai runduna ne, gama mutanen Isra'ila suka manta da alƙawarin ka, suka lalata bagadanka, suka kuma karkashe annanbawanka da takobi. Yanzu ni kaɗai na rage da ba su kashe ba, suna ma ƙoƙarin su ɗauke raina."11Yahweh ya amsa, "Tafi ka tsaya akan tsauni a gabana." Sai ga Yahweh yana wucewa, babbar iska mai ƙarfi ta tsaga duwatsun, ta kuma farfasa shi rugu rugua gabanYahweh, amma Yahweh ba ya cikin iskar. Bayan iskar sai girgizar ƙasa ta zo, amma Yahweh ba ya cikin girgizar ƙasar.12Bayan girgizar kuma sai wuta, amma Yahweh ba ya cikin wutar. Daga nan bayan wutar, sai natsastsar ƙaramar murya.13Sa'ad da Iliya ya ji muryar, sai ya rufe fuskarsa da alkyabbarsa, ya fita, ya tsaya a bakin kogon. Sai murya ta zo gare shi ta ce, "Me ka ke yi a nan, Iliya?14Iliya ya amsa, "Ni na zama mai kishi domin Yahweh, Allah mai runduna ne, amma mutanen Israel sun karya alƙawarinka, suka lalata bagadannka suka kuma karkashe annabawanka da takobi. Yanzu ni, kaɗai na rage suna ma ƙoƙarin su ɗauki raina.15Sai Yahweh yace da shi, "Tafi, ka juya akan hanyarka ta jeji kusa da Damaskus, idan ka isa can za ka zuba wa Hazayel mai, ka keɓe shi, ya zama sarkin Aram,16za ka kuma keɓe Yehu ɗan Nimshi ya zama sarkin Isra'ila, za ka kuma zuba wa Elisha ɗan Shafat na Abel Mehola mai ya zama annabi a gurbinka.17Zai kasance Yehu zai kashe duk wanda ya tsere daga takobin Hazayel, Elisha zai kashe duk wanda ya tsere daga takobin Yehu.18Amma zan barwa kaina mutum dubu bakwai na Isra'ila don kaina, waɗanda ba su russuna wa Ba'al da gwiwonsu ba, ba su kuma sumbace shi da bakunansu ba."19Iliya fa ya tashi daga wurin ya sami Elisha ɗan Shafat, wanda ke noma da shanun huɗa karkiya goma sha biyu, shi kansa kuma yana huɗa da karkiyar sha biyu. Iliya ya bi ta kusa da Elisha ya jefa masa alkyabbarsa.20Sai Elisha ya bar shanun noman, ya sheka da gudu gun Iliya ya ce, "Idan ka yarda bari in sumbaci mahaifina da mahaifiyata, in yi bankwana da su, sa'an nan in zo in bi ka." Sai Iliya ya ce da shi, "Koma, amma ka yi tunanin abin da na yi maka."21Elisha ya komo daga wurin Iliya ya kama shanun noman, ya yanka dabbobin, ya dafa namansu da itace daga karkiyoyin. Sai ya ba mutane suka ci. Sa'an nan ya tashi, ya bi Iliya, ya zama mai taimakonsa.
Wannan kwantanci an yi amfani da shi ay rantsuwa mai ƙarfi ainun. "bari alloli su kashe ni, su ma yi abin da yafi haka muni"
"idan ba zan kashe ka kamar yadda ka kashe waɗannan annabawan ba"
"ya tashi tsaye"
Kalmar "kansa" an yi amfani da ita a nanata shi kaɗai ne. AT: "ya yi tafiya shi kaɗai na yini ɗaya"
"itacen aduwa" bishiyace da take girma a sahara.
"ya yai addu'a cewa bari ya mutu"
"waɗannan bala'in ya yi mani yawa, Yahweh"
za mu iya cewa. AT: "gurasa da wani ya dafa akan dutse"
"abin zuba ruwa"
"zai zama maka da wahala ƙwarai."
"wannan abincin ya ba shi karfin yin tafiya kwana 40 da yini 40"
A nan kalmar "a can" na nufin dutsen Horeb. Kogo wani buɗaɗɗen wuri ne a cikin dutse ya zai kai mutum daki.
Habaicin na nufin maganar Yahweh "maganar" wakili ne da yake wakiltar saƙo. "Yahweh ya yi magana ya ce masa." Duba yadda aka fassara shi a 6:11.
Yahweh ya faɗi haka ya tsautawa Iliya ya kuma tuna masa aikin da ke a gabansa. AT: "nan ba wurin da ya kamata ka zama ba ne, Iliya."
A nan kalmar "Ni" an maimaiya shi domin a jaddada.
"gabana" habaicin na tsaya a gabana. AT: "a kan dutsen a gabana"Duba:
"ya rufe fuskarsa da alkyabbarsa" Alkyabba wani dogon igiya na, yankin kaya da zai iya rufe dukkan jiki.
"sai ya ji murya"
An fassara shi a 19:9.
A nan kalmar "Ni" an mai-maita ta domin a jaddada.
"annabi a madadinka"
wannan maganar an yi shi ne a gabatar da abinda zai kasance idan Iliya ya yi abinda Yahweh ya umarceshi ya yi. "abinda zai faru shi ne"
"takobi" wakili ne na kisa kamar a yaƙi. AT: "duk wanda Hazazel bai kashe da takobi ba"
A nan kalmar "zan" da kuma "kaina" na nufin Yahweh. AT: "zan cece su daga mutuwa"
"mutum 7,000"
"rusuna" da "sumbata" wakilai ne na yadda mutane suke yi su bautawa gumaka. An haɗa su domin a jaddada. AT: "waɗanda basu rusuna su bauta da sumbatar Ba'al ba" ko kuma "waɗanda basu yi wa Ba'al sujada ba"
wannan sunan na miji ne.
"shanun huɗa karkiya 12"
Kalmar "kansa" na nuna cewa Ilisha na huɗa da karkiyar ƙarshe, sauran mutne kuma suna yi da sauran goma sha ɗayan.
Kalmar "ya" na nufin Ilisha.
Ilisha yaba da dafaffen nama ga mutanen birnin.
1Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tara dukkan sojojinsa. Akwai sanannun sarakuna talatin da biyu da suke tare da shi, da dawakai da karusai. Ya haura ya kai wa Samariya hari ya kuwa yi yaƙi da ita.2Ya aika da jakadu zuwa cikin birni wurin Ahab sarkin Isra'ila, ya ce da shi, "Ben Hadad ya ce wannan:3Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Matanka da 'ya'yanka, masu kyau, nawa ne.'"4Sarkin Isra'ila ya amsa ya ce, "Ya kasance kamar yadda ka ce, shugabana, sarki. Ni da dukkan abin da na ke da shi naka ne."5Jakadun suka dawo kuma suka ce, "Ben-Hadad ya ce wannan, 'Na aika maka da magana cewa dole ka ba ni azurfarka, da zinariyarka, da matanka da 'ya'yanka.6Amma zan aiko barorina wurinka gobe a dai-dai wannan lokacin, za su bincike gidanka da gidajen barorinka. Za su kwashe duk abin da ka ke da shi daga hannuwanka su ɗauke abubuwan da suka gamshi idanuwansu.'"7Sai sarkin Isra'ila ya kirawo dukkan dattawan ƙasar ga baki ɗaya ya ce, "Idan kun yarda ku duba yadda wannan mutum ya ke neman rikici. Ya aiko wuri na domin in ba shi matana da 'ya'yana da azurfa da zinariyata, ni kuwa ban yardar masa ba."8Dukkan dattawa da dukkan mutane suka cewa Ahab, "Kada ka saurare shi ko ka da mu da abin da ya ke so."9Ahab ya ce da jakadun Ben-Hadad, "Ku faɗa wa shugabana sarki, 'Na yarda da dukkan abin da ka aiko barorinka su yi da farko, amma ba zan yarda da wannan buƙatar ta biyu ba.'" Jakadun kuwa suka koma da wannan amsa ga Ben-Hadad.10Sai Ben-Hadad ya sake aikawa da saƙonsa ga Ahab, ya ce, "Bari alloli su yi mani haka harma fiye idan tokar Samariya ba za ta isa domin dukkan mutane waɗanda suka biyo ni kowannensu ya sami ɗan kaɗan ba.11Sarkin Isra'ila ya amsa ya ce, "Ku faɗa wa Ben-Hadad, 'Ba wani wanda ya ke adali da zai sa sulke ya yi fahariya kamar ya ci yaƙin.'"12Ben-Hadad ya ji wannan saƙo sa'ad da ya ke sha, shi da sarakuna da ke ƙarƙashinsa waɗanda suke cikin rumfunoni. Ben-Hadad ya umarce mutanensa, "Kowa ya tsaya a wurinsa domin yaƙi. "Suka shirya kansu suka tsaya domin yaƙin ya fada wa birnin.13Sai ga wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra'ila ya ce, "Yahweh ya ce, "Ka ga wannan babban taron sojoji? Duba, zan ba da su a hannunka yau, za ka sani ni ne Yahweh.'"14Ahab ya amsa, "Wane ne zai yi jagorar babbar rundunar?" Yahweh ya amsa ya ce, "Ta wurin matasan ofisoshi waɗanda su ke yi wa gwamnonin larduna hidima." Sai Ahab ya ce, "Wane ne zai fara yaƙin?" Yahweh ya amsa, "Kai ne."15Sai Ahab ya tara matasan ofisoshi waɗanda suke yi wa gwamnonin larduna hidima. Su ɗari 232. Bayansu kuma ya tara dukkan sojoji da dukkan rundunar yaƙIn Isra'ila, jimilla dubu bakwai.16Suka tafi da tsakar rana. Ben-Hadad yana a buge da abin sha a rumfa, shi da sarakunan da ke ƙarƙashinsa su talatin da biyu waɗanda suke goyan bayansa.17Matasan ofisoshi waɗanda suke yi wa gwamnonin larduna hidima suka fara wucewa gaba. Sai Ben-Hadad ya ji labari ta wurin waɗanda ya aike su, "Mutane na zuwa daga Samariya."18Ben-Hadad yace, "Ko da sun zo don salama ko da yaƙi, ku kama su da rai."19Matasan ofisoshi waɗanda suke wa gwamnonin larduna hidima sun fita daga birnin sojoji kuma suna bin su.20Kowa ya kashe abokin gãbarsa, Aremiyawa suka gudu. Isra'ila kuwa suka rutume su. Ben-Hadad sarkin Aram ya tsere akan doki tare da mahayan dawakai.21Sarkin Isra'ila ya fita ya ƙwace dawakai da karusai, ya kashe Aremiyawa masu yawa.22Sa'an nan annabi ya je wurin sarkin Isra'ila ya ce da shi, "Tafi, ka ƙarfafa kanka, ka fahimci shirin abin da zaka yi, gama da juyuwar shekara sarkin Aram zai zo maka da harin yaƙi."23Barorin sarkin Aram suka ce da shi, "Na su allahn allah ne na tuddai. Don haka suka fi mu ƙarfi. Amma yanzu bari mu yi yaƙi da su a kwari, ba bu shakka za mu fi su ƙarfi.24Dole ka yi wannan: ka fitar da sarakuna daga matsayinsu na shugabanci ka maida hafsoshin sojoji a mamadinsu.25Ka tara sojoji kamar yawan waɗanda ka rasa-dawakai domin dawakai da karusai domin karusai, mu kuma za mu yi yaƙi da su a kwari. Babu shakka za mu yi ƙarfi fiye da su." Ben-Hadad ya saurari shawararsu ya yi yadda suka ba da shawarar.26Bayan farkon sabuwar shekara, Ben-Hadad ya tara Suriyawa su ka haura zuwa Afek su yi yaƙi da Isra'ila.27Mutanen Isra'ila suka taru aka ba su guzuri da za su yi yaƙi da su. Mutanen Isra'ila suka kafa sasani a gabansu kamar kananan garkuna biyu na awaki, amma Aremiyawa suka cika ƙasar.28Sai mutumin Allah ya zo kusa ya yi magana da sarkin Isra'ila ya ce, "Yahweh ya ce: 'Gama da ya ke Aremiyawa sun ce Yahweh shi allah na tuddai ne, amma ba shi ne allah na kwari ba, zan ba da dukkan wannan babban taron sojojin nan a hannunka, za ka sani Ni ne Yahweh.'"29Sojojin suka kafa sansani daura da juna har kwana bakwai. A rana ta bakwai ɗin yaƙi ya fara. Mutanen Isra'ila suka kashe Aremiyawa nan ƙafa100,000 a rana ɗaya.30Sauran suka gudu zuwa Afek, cikin birni, garun kuma ya faɗo akan mutune dubu ashirin da bakwai waɗanda suka rage. Ben-hadad kuwa ya gudu ya shiga cikin birni, cikin ƙuryar ɗaki.31Barorin Ben-Hadad suka ce da shi, "Duba yanzu, mun ji cewa sarakunan gidan Isra'ila sarakuna ne masu jinƙai. Idan ka yarda bari mu sa tufafin makoki mu ɗaura igiyoyi a kawunanmu, mu tafi wurin sarkin Isra'ila. Watakila zai bar ka da rai."32Sai suka sa tufafin makoki suka ɗaura igiyoyi a kawunansu suka tafi wurin sarkin Isra'ila suka ce, "Baranka Ben-Hadad ya ce, 'Idan ka yarda ka bar ni da rai.'" Ahab yace, "Har yanzu yana da rai? Shi ɗan'uwana ne."33Yanzu mutanen suna sauraro kowace alama daga wurin Ahab, sai su yi saurin amsa masa, "I, ɗan'uwanka Ben-Hadad yana da rai." Sai Ahab ya ce, "Ku tafi ku kawo shi." Sai Ben-Hadad ya zo wurin sa, Ahab ya sa ya shiga da shi cikin karusarsa.34Ben-Hadad ya ce da Ahab, "Zan dawo maka da biranen da tsohona ya ƙwace daga wurin tsohonka, kai kuma za ka yi kasuwanci a Damaskus, kamar yadda tsohona ya yi a Samariya." Ahab ya ba shi amsa, "Zan bar ka, ka tafi a kan alƙawari." Ahab ya yi alƙawari da shi, sa'an nan ya bar shi ya tafi.35Sai ga wani mutum, ɗaya daga cikin 'ya'yan annabawa, ya ce da ɗaya daga abokansa annabawa bisa ga maganar Yahweh, "Idan ka yarda ka buge ni." Amma mutumin ya ƙi ya buge shi.36Sai annabin ya ce da abokinsa annabi, "Da ya ke ba ka yi biyayya da muryar Yahweh ba, da zarar ka tashi daga wurina, zaki zai kashe ka." Da ya tashi daga wurinsa kuwa zaki ya zo ya gamu da shi, ya kashe shi.37Annabin kuma ya sami wani mutum ya ce, "Idan ka yarda ka buge ni." Mutumin kuwa ya buge shi har ya ji masa ciwo.38Sai annabin ya tafi ya jira sarki a hanya; ya bad da kama, ya rufe idanunsa da ƙyalle.39Sa'ad da sarki ya ke wucewa, sai annabi ya kira sarki ya ce, "Ni baranka na tafi wurin yaƙi mai zafi, sai soja ya tsaya ya kawo mani abokin gãba ya ce, 'Kula da wannan mutum. Idan wani abu ya sa ya tsere, za ka ba da ranka domin ransa, ko kuma ka biya talanti ɗaya na azurfa.'40Gama da ya ke baranka yana fama da kai da kawowa, abokin gãbar soja ya tsere." Sai sarkin Isra'ila ya ce da shi, "Wannan shi ne irin hukuncin da zan yi - kai da kanka ka shawarta haka."41Sai annabi ya yi sauri ya cire ƙyalle daga idanunsa, sarkin Isra'ila ya gane, ashe ɗaya daga cikin annabawa ne.42Annabin ya cewa sarki, "Yahweh ya ce, 'Da ya ke ka bar shi ya tafi daga hannunka mutum wanda na ƙaddara ga mutuwa, ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka kuma maimakon mutanensa.'"43Sarkin Isra'ila kuwa ya tafi gidansa da baƙinciki, a Samariya.
Wannan sunan na miji ne.
ƙananan sarakuna-"sanannu sarkuna 32"
"sarakunan da suke mulkin ƙananan ƙungiyoyin mutane"
Wannan habaici ne ya nuna yarjejeniya. AT: "na yarda da kai"
"gobe war haka a dai-dai lokacin da yake yanzu"
"gamshe su" wakili ne na neman wani abu da son sa. AT: "dukkan abin da ya gamshe su"
"ƙasar" wakili ne na dukkan mutanen da suke a raye a can. AT: "na mutanen Isra'ila"
"kun yarda" habaicine ma'ana ku duba da kyau. AT: "ka lura da sosai"
za a iya nuna wannan. AT: "na yarda da buƙatarsa"
wannan rantsuwa ce da jaddadawa mai ƙarfi. Duba yadda aka fassara shi a 19:1.
Ben-Hadad na faɗin cewa sojojinsa za su hallaka komai da komai a samariya.
Wannan yana yi ne na bada shawara. "sa sulke" wakili ne na yin shiri domin yaƙi. "ku faɗawa Ben-Hadad, 'ka da ka yi fahariya kamar kaci yaƙin da baka yi ba tukuna."
Kalmar "sai ga" ya na jijjiga mu muyi bayyana ta ba zata na sabon mutum a labarin. Yarenka zai iya samun hanyar yin wannan.
Yahweh ya yi tambaya ya jaddada faɗi da ƙarfin sojojin Ben-Hadad. AT: "dubi wannan taron sojoji."
Kalma "duba" yan jijjigamu mu maida hankali ga abin mamakin da zai biyo baya.
A nan kalmar "hannu" na nufin iko. AT: "baka nasara bisa waɗannan sojoji"
Ahab ya bar kalmar 'za ka yi haka' AT: "da ga wa ka yi?"
"Ahab ya kira zaman dukkan sojoji"
"ɗari biyu da talatin da biyu"
Wannan maganganun na nufin abu ɗaya kuma an sa su domin a jaddada.
"7,000"
A nan kalmar "su" na nufin sojojin Isra'ila.
ƙananan sojoji guda biyu-ka fassara wannan kamar yadda kayi a 20:1.
za mu iya cewa. AT: "waɗanda Ben-Hadad ya aika suka faɗa masa"
"yan leƙen asiri" wasu sojoji ne da aka aika su samu labari game da abokan gãba.
Mun fahimta cewa Ben-Hada na magana da sojojinsa . AT: "Ben-Hadad ya ce da sojojinsa"
A nan "sun" da "su" na nufin sojojin Isra'ilawa.
"matasan ofisoshin Isra'ilawa ... sojojin Isra'ilawa suka bi su"
"Isra'ila" wakiline na sojojin ƙasar Isra'ila. AT: "mazaje na sojojin Isra'ila su ka runtume su"
"sarki" wakiline na sarki da dukkam sojojin da ke bauta ƙarƙashinshi. AT: "sarkin Isra'ila da sojojinsa suka fita suka kai hari"
"kanka" na nufin wakilin sojojin sarki. AT: "ku ƙarfafa sojojinku"
Kalmaomi biyu na nufin abu ɗaya an haɗa su domin a jaddada. AT: "ƙudura"
wadansu ma'anoni 1) "a lokaci farkon shekara" (UDB) ko 2) "baɗi i war haka."
Kalmar "mu" da "mu" na nufin bayin sarki, da sojojin dukka gaba ɗaya.
"dole ka cire sarakuna talatin da biyu waɗanda suke mulikin dakarai"
Wanan sunan birni ne.
"Isra'ila" na nufin sojojinsu. AT: "su yi yaƙi da sojojin Isra'ila"
za mu iya ceaw. AT: "sojojin Isra'ila kuma suka taru wuri ɗaya, shugaban ya basu guzirin yaƙi" (Duba:activepassive)
Wannan ya kwatanta sojojin Isra'ilawa kamar garkunan awaki biyu. AT: "sojojin Isra'ilawa sun fito ƙanana kuma raunana kamar garkunan awaki."
Wannan wani sunan ne na annabi. AT: "annabi" (UDB)
A nan kalmar "hannu" na nufin iko. AT: "ba ka nasara akan wannan babban taron sojojin"
"kwanaki 7"
"dubu ɗari"
"masu takawa a ƙasa" sojojin waɗanda suke takawa a ƙafa.
maganar "sauran" ma ɗauka "na sojojin Aremiyawa." AT: "sauran sojojin Aremiyawa"
dubu bakwai-"27,000"
wannan ya jaddada abin da za su. AT: "saurara" ko "a mai da hankaliga bainda zamu faɗa maku"
Alama ce ta miƙa kai.
Ahab ya yi wannan tambaya ya nuna mamaki. AT: "na yi mamaki har yanzu yana da rai!"
"ɗan'uwa na" wakaili ne na wani da yake abokin mai kyau. AT: "shi kamar ɗan'uwa yake a wurina"
kalmar "yanzu" ba wai ya na nufin "a wannan lokaci," amma anyi amfani da shi a ja hankali game da abinda zai biyo baya.
"alama" wakili ne na aiki da ya bada ma'ana. AT: "ko yayi wani abu da zai sa su ce Ahab na shirin yin jinkai"
"ɗan ƙungiyar annabawa"
"maganar" wakiline na saƙo. AT: "yadda Yahweh ya gaya masa yayi"
"muryar" wakili ne na abinda Yahweh ya umarta. AT: "ba ka yi wa Yahweh biyayya ba"
Kalmar "Sarki" na nufin mutum wanda shine sarki mai mulki birnin, jiha, ko ƙasa. . Sarki ana zaɓen sa ne ya yi mulki saboda dangantakarsa da sauran sarakai da suka yi mulki. . Ida sarki ya mutu yawanci lokuta babban yaronsa ne ke gadarsa. . A zamanin dã, sarki yana da iko sosai akan mutanensa da yake mulkinsu. . Ba kowannen lokaci ba kalmar "sarki" ana kiran wand ba sarki na gaskiya ba, irinsu "sarki Hiridus" a sabon alkawari. . A littafi mai-tsarki, Allah ana kiransa sarki wanda ke mulkin mutanensa. . "Mulkin Allah" na nufin Allah na mulkin mutanensa. . Yesu an kira shi "sarkin yahudawa" ko "sarkin Isra'ila" ko "sarkin sarakuna" . Idan Yesu ya dawo zai yi mulki na harabada bisan dukkan duniya. . Wannan kalmar za a iya ce "mafificin sarki" ko "sarkin da ba irinsa" ko "maɗaukakin mai mulki" . Jimlar "sarkin sarakuna" za a iya ce "sarki wanda yake mulki mbisa dukkan sauran sarakuna" ko "maɗaukakin mai mulki da yake da iko bisan sauran masu mulki." (Duba kuma: iko, Hiridus Antipas, mulki, mulkin Allah) Nusar littattafan littafi mai-tsarki: . 1 Timoti 06:15-16 . 2 Sarakuna 05:18 . 2 Sama'ila 05:03 . Ayyukan Manzanni 07:9-10 . Ayyukan Manzanni 13:22 . Yahaya 01:49-59 . Luka 01:05 . Luka 22:24-25 . Matiyu 05:35 . Matiyu 14:09 Kalmomi: . ƙaƙƙarfa: H4427, H4428, H4430, G935, G936 Duba kuma: iko, ikoki, mulki, mulkoki, mulkin Allah, mulkin sama Misalai: 1 Sarakuna 8:6 1 Sarakuna 16:1 1 Sarakuna 17:5 1 Sarakuna 16:18 1 Sarakuna 21:6 1 Sarakuna48:14
Annabin ya na nuna kansa ne a fakaice don nuna girmama wa.
"zafin yaƙi" habaici ne a nuna abinda da dukkan zuciyarsa yaƙi mai firgitarwa. AT: "a inda yaƙi ya yi zafi sosai"
"daga nan za ka mutu a maimakonsa"
talanti ma'auni ne na nauyi dai-dai da 34 kilogiram. AT: "34 kilogiram na azurfa"
Wanan habicin na nufin yin aiki da yawa ko rashin samun lokacin kanka. AT: "yin wasu abubuwan dabam" (UDB)
A nan kalmar "hannu" wakili ne na iko. AT: "sallama" ko "saki ran wani"
"zaka mutu a maimakonsa, mutanenka za su mutu a maimakon mutanensa"
1A wani lokaci kuma, Nabot Bayezrile yana da gonar inabi a Yezriyel, kusa da fãdar Ahab, sarkin Samariya.2Ahab ya yi magana da Nabot cewa, "Ka ba ni gonar inabinka, don in mai da ita lambu, domin gonar tana kusa da gidana. Ni kuwa zan ba ka wata gonar inabin mai kyau, ko kuma idan kana so, sai in biya ka tamanin kuɗinta."3Amma Nabot ya amsa wa Ahab, "Yahweh ya sawwake in ba ka gãdon kakannina."4Ahab ya koma fãdarsa da baƙinciki, saboda amsar da Nabot Bayezrile ya ba shi da ya ce, "Ni ba zan ba ka gãdon kakannina ba." Ya zauna akan gado, ya juya fuskarsa, ya ƙi cin kowanne abinci.5Yezebel matarsa ta zo wuinsa, ta ce da shi, "Me ya sa zuciyarka ta da mu, har ka ƙi cin kowanne abinci?"6Ya amsa mata, "Domin na yi magana da Nabot Bayezrile, na ce masa, 'Ya ba ni gonar inabinsa don in saya, idan ya yarda, zan ba ka wata gonar inabin ta zama ta ka.' Sai ya amsa mani, 'ba zan ba ka gonar inabina ba.'"7Yezebel matarsa ta amsa masa, "Ba kai ne ka ke mulkin Isra'ila ba? Tashi ka ci abinci; bari zuciyarka ta yi farinciki, zan samar maka gonar inabin Nabot Bayezrile."8Yezebel ta rubuta wasiƙu da sunan Ahab, ta hatimce su da hatiminsa, sa'an nan ta aika da su zuwa ga dattawa da mawadata masu kuɗi waɗanda suke zaune tare da shi a taruruka, da waɗanda suke zama kusa da Nabot.9Ta rubuta a wasiƙun, cewa, "A yi shelar azumi, a sa Nabot a gaban mutane.10A kuma sa 'yan iskan mutane biyu su yi ta zarginsa, su riƙa cewa, 'Ka zagi Allah da sarki.'" Sa'an nan ku tafi da shi waje, ku jajjefe shi da duwatsu har ya mutu.11Mutanen birnin da dattawa da masu arzaki da ke zaune a birnin Nabot, suka yi yadda Yezebel ta sa su yi, kamar yadda aka rubuta a wasiƙun da ta aika masu.12Su kuwa suka yi shelar azumi, suka zaunar da Nabot a gaban mutane.13Sai mutune biyu suka zo, suka zauna a gaban Nabot suka yi ta shaidar zur akan Nabot a gaban mutane, cewa, "Nabot ya zagi Allah da sarki." Sai suka ɗauke shi wajen birni suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu.14Dattawa suka aika da magana ga Yezebel, cewa, "An jajjefe Nabot da duwatsu ya mutu."15Yayin da Yezebel ta ji labari an jajjefe Nabot da duwatsu har ya mutu, sai ta ce da Ahab, "Tashi ka mallaki gonar inabin Nabot Bayezrile wadda ya ƙi ya ba ka, ka ba shi kuɗi, gama Nabot ba shi da rai, ya mutu."16Da Ahab ya ji labarin Nabot Bayezrile ya mutu, sai ya tashi ya gangara zuwa gonar inabin Nabot Bayezrile ya ɗauke ta ya mallake ta.17Sai maganar Yahweh ta zo ga Iliya Batishbe, cewa,18"Tashi ka tafi ka sadu da Ahab sarkin Isra'ila, wanda ya ke zaune a Samariya. Yana cikin gonar inabin Nabot, inda ya tafi don ya mallake ta.19Dole ka yi magana da shi ka ce Yahweh ya ce, 'Ka yi kisa, ka kuma ɗauki abin da ya mallaka? Sai ka faɗa masa Yahweh ya ce, 'A wurin da karnuka suka lashe jinin Nabot, a nan ne kuma karnuka za su lashe jininka, i, jininka.'"20Ahab ya ce da Iliya, "Ka same ni ko, maƙiyina?" Iliya ya amsa, na same ka, gama ka bada kanka ga aikata abin da ke mugunta a fuskar Yahweh.21Yahweh yace wannan da kai: 'Duba, zan kawo maka masifa, in shafe ka, in datse daga gare ka kowanne ɗa namiji bawa ko 'yantarcen mutum a Isra'ila.22Zan sa iyalinka kamar iyalin Yerobowam ɗan Nebat, su kuma zama kamar iyalin Ba'asha ɗan Ahija, saboda ka sani har na yi fushi, ka kuma sa mutanen Israila sun yi zunubi.'23Yahweh kuma ya sake yin magana akan Yezebel, cewa, 'Karnuka za su cinye Yezebel a gefen katangar Yezriyel.'24Duk wanda ya ke na Ahab da zai mutu a birni karnuka ne za su cinye shi, tsuntsayen sararin sama ne kuma za su cinye duk wanda ya mutu a saura."25Babu wani kamar Ahab, da ya ba da kansa ga aikata mugunta a fuskar Yahweh, wanda matarsa Yezebel ta zuga shi yin zunubi.26Ahab ya yi abin banƙyama ƙwarai saboda ya bi gumaka, kamar yadda Amoriyawa suka yi, waɗanda Yahweh ya kore su a gaban mutanen Isra'ila.27Da Ahab ya ji waɗannan kalmomi, ya yage tufafinsa ya sa na makoki a jikinsa, ya yi azumi, ya kuma kwanta a tsummokaran makoki, ya zama da damuwa.28Sai maganar Yahweh ta zo ga Iliya Batishbe, cewa,29"Ka ga yadda Ahab ya ƙasƙantar da kansa a gabana? Da ya ke ya ƙasƙantar da kansa a gabana, ba zan kawo masifar a zamaninsa ba; sai dai a zamanin ɗansa ne, zan kawo masifar a cikin iyalinsa."
Wanna magana ya kawo mafarin labari ya kuma nuna waɗanan tarihi sun faru daga baya, ba wai Nabot ya sami gonar inabin ba. idan yarenka yana da yadda za a sa forkon labari zaka iya amfani dashi anan. AT: "wannan ne abinda ya faru daga baya"
wannan suna mutum ne daga Yezrile.
"Samariya'' ita ce kai ta na mulkin Isra'ila anan tana wakiltar dukkan ƙasar. AT: "sarkin Isra'ila" (Duba: synecdoche)
Wannan maganar rantsuwa ce a jaddada abinda zai biyo ba zai faru ba. AT: "saboda Yahweh ya hana, ba zan baka ba''
Gonar da kakaninsa suka ƙarba a matsayin dukiya ana maganar ta kamarnshi ne gãdo. AT: "in ba ka gonar da kakanni na suka karɓa a matsayin gãdo"
A nan "zuciya" na nufin dukkan mutum tausaya. AT: "don me ka ke fushi"
Yezebel ta yi wannan mummunan maganar da baya buƙatar amsa ta kwaɓi Ahab. za a iya fassara shi. AT: "har yanzu kana mulkin Isra'ila!" *
A nan "zuciya" na nufin dukkan mutum da tausaya. AT: "yi faincki" ko "yi murna"
ma'ana 1) ta rubuta sunan Ahab a wasiƙar. AT: "rubuta wasiƙa da sa hannun Ahab" 2) kalmar suna wakili ne na iko. AT: "rubuta wasika a madadin Ahab"
kalmar "mawadata" na nufin mutane masu kaɗi AT: "mawadata da suka zauna da Nabot"
sa Nabot ya zauna a maɗaukakin wuri an yi maganarsa kamar a sa ya zauna can saman sauran mutane da suke zama tare da shi. AT: "sa Nabot ya zauna a maɗaukain wuri fiye da sauran mutane"
"su yi masa zaidar zur"
Kalmar "arziki" na nufin masu kuɗi. AT: "masu arzaki da ke zaune a birnin Nabot"
za mu iya cewa. AT: "yadda ta rubuta a cikin wasiƙar" (Duba_ activepassive)
sa Nabot ya zauna a kujerar ɗaukaka ana maganarsa kamar asa Nabot ya zauna can saman sauran mutane. Duba yadda aka fassara shi a 21:8. AT: "sa Nabot ya zauna a wurin ɗaukaka fiye da saura"
"zauna inda Nabot zai iya ganin su"
A nan kalmar "su" na nufin mutanen birnin.
za a iya cewa. AT: "mun jejjefe Nabot ya kuma mutu"
za mu iya cewa. AT: "mutanen sun jejjefi Nabot ya kuma mutu"
maganganu biyun na nufin abu ɗaya kuma sun jaddada bayanin Yezebel. "Nabot ya mutu!"
Wannan maganar na nufin Yahweh ya yi magana ko y aika da saƙo. Duba yadda aka fassara shi a 6:11. AT: "Yahweh ya faɗi wannan saƙo" ko "Yahweh ya faɗa"
Yahweh ya yi wannan tambayar ya tsawata wa Ahab. AT: "ka kashe Nabot ka sa ce gonar inabinsa!"
Wannan am maimaita saboda a jaddada.
Ahab ya yi wannan tambayar ya nuna damuwar sa akan Iliya. Cewa Iliya "ya samu" Ahab na nufin Iliya ya gane ayyukan Ahab,ba wai don y gane inda yake na sarari. AT: "ka same ni, maƙiyi na!" ko "ka game abinda na yi maƙiyina"
Mutum wanda ya sa kansa ga aikata mugunta an yi maganarsa kamar ya kai kansa kasuwa ya sayar domin aikata mugunta. AT: "ka bada kanka ga aikata mugunta"
Maganar, "a fuskar" na nufin ra'ayin wani. Duba yadda aka fassara shi a 11:5. AT: "abin da Yahweh ya ce mugunta ne"
"saurara" ko "mai da hankali ga abinda nake shirin gaya maka"
Yahweh ya yi maganar hallaka iyalin Ahab da kare da bga samun zuriya kamar zai cinye shi da wuta da kuma yanke su kamar wadda yake yanke rassan itace. AT: "kashe dukkan 'ya'ya maza naka a Isra'ila, bayi ko 'yantattu"
Yahweh za hallak iyalin Ahab kamar yadda ya hallaka iyalin Yeroboam da Ba'asha.
"dukkan iyalin gidan Ahab"
Mutum wand ya ba da kansa ga aikata mugunta an yi maganarsa kamar wanda ya siyar da kansa ga aikata mugunta. Duba yadda aka fassara shi a 21:19. AT: "wanda ya miƙa kansa ga aikata mugunta"
Maganar "a fuska" na nufin ra'ayin wani. Duba yadda aka fassara shi a11:5. AT: "abinda Yahweh ya ce mugunta ne"
A nan "isra'ila" na nufin dukkan ƙabilai goma sha biyu na ba wai na arewacin kaɗai ba. AT: "cire su daga gaban mutanen Isra'ila" ko "kore su daga gaban mutanen Isra'ila"
Wannan maganar na nufin Yahweh ya yi magana ko y aika da saƙo. Duba yadda aka fassara shi a 6:11. AT: "Yahweh ya faɗi wannan saƙo" ko "Yahweh ya faɗa"
Allah ya yi amfani da tambaya ya nuna wa Iliya cewa damuwan Ahab gaskiya ne . AT: "na ga yadda Ahab ya ƙasƙantar da kansa gabana" ko "dubi yadda Ahab ya ƙasƙantar da kansa gabana."
A nan kalmar "kwanaki" na nuna dukkan kwanakin mutum a duniya. AT: "lokacin rayuwarsa ... lokacin rayuwar ɗansa"
1Shekaru uku da suka wuce ba a yi yaƙi tsakanin Aram da Isra'ila ba.2Sai a cikin shekara ta uku ɗin, Yehoshafat sarkin Yahuda ya tafi wurin sarkin Isra'ila.3Sarkin Isra'ila ya ce da barorinsa, "Ko kun san Ramot Giliyad tamu ce, amma ba ma yin komai domin mu ƙwace ta daga hannun sarkin Aram?"4Ya ce da Yehoshafat, "Za ka tafi tare da ni zuwa yaƙi a Ramot Giliyad?" Yehoshafat ya amsa wa sarkin Isra'ila, "Ni kamar ka ne, mutanena kuma kamar mutanenka ne, dawakaina suna kamar naka ne."5Yehoshafat ya cewa sarkin Isra'ila, "Idan ka yarda ka nemi shawara daga Yahweh duk abin da za ka yi tukuna."6Sai sarkin Isra'ila ya tara annabawa wuri ɗaya, mutane ɗari huɗu ne, ya ce da su, "In tafi in yi yaƙi a Ramot Giliyad, ko kuwa kada in tafi?" Suka ce, "Ka haura, gama Ubangiji zai ba da ita a hannun sarki."7Amma Yehoshafat ya ce, "Ba wani annabin Yahweh ne a nan wanda za mu nemi shawara daga wurinsa?8Sarkin Isra'ila ya cewa Yehoshafat, "Da sauran mutum ɗaya wanda za mu iya mu nemi shawara daga Yahweh da zai taimaka, Mikaiya ɗan Imla, amma ina ƙinsa gama bai taɓa yin wani annabcin alheri a kaina ba, amma sai dai na masifa." Amma Yehoshafat ya ce, "Kada sarki ya ce haka."9Sa'an nan sarkin Isra'ila ya kirawo wani bafade, ya bada umarni, "Kawo Mikaiya ɗan Imla, yanzu a nan."10Ahab sarkin Isra'ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zaune akan gãdon sarautarsu saye da tufafinsu a dandalin ƙofar Samariya, da dukkan annabawa suna ananbci a gabansu.11Zedekiya ɗan Kena'ana ya yi wa kansa ƙahonin ƙarfe, ya ce, "Yahweh ya faɗi wannan: 'Tare da waɗannan za ka tunkuyi Aremiyawa har su hallaka.'"12Dukkan annabawan suka yi annabci iri ɗaya, cewa, "Ka haura zuwa Ramot Gileyad, zaka yi nasara, domin Yahweh zai ba da ita a hannun sarki."13Ɗan saƙo wanda ya tafi ya kira Mikaiya ya yi magana da shi, cewa, duba yanzu, maganar annabawa abubuwa ne mai kyau ga sarki da baki ɗaya. Idan ka yarda bari maganarka ta zama kamar tasu ka faɗi abu mai kyau."14Mikaiya ya amsa, "Kamar yadda Yahweh ke raye, ga abin da Yahweh ya ce da ni zan faɗa."15Da ya zo gaban sarki, sarki ya ce da shi, "Mikaiya, mu tafi Ramot Giliyad don yaƙi, ko a'a?" Mikaiya ya amsa masa, "Ka haura za ka yi nasara, Yahweh zai ba da ita a hannun sarki."16Sarki ya ce masa, "Sau nawa zan neme ka da ka rantse za ka faɗa mani kome idan ba gaskiya ba, da sunan Yahweh?"17Mikaiya ya ce, "Na ga dukkan Isra'ila a warwatse akan tuddai, kamar tumaki waɗanda ba su da makiyayi, Yahweh ya ce, "Waɗannan ba su da makiyayi. Bari kowanne mutum ya koma gidansa da salama."18Sarkin Isra'ila ya cewa Yehoshafat, "Ban faɗa maka ba, ba zai yi wani annabcin alheri a kaina ba, amma sai dai na masifa?"19Mikaiya yace, "Saboda haka ka ji maganar Yahweh: na ga Yahweh yana zaune a kursiyansa tare da dukkan mala'ikun sama suna tsaye wajen damarsa da hagunsa.20Yahweh yace, 'Wa zai yaudari Ahab, ya tafi ya faɗawa Ramot Giliyad?' Ɗaya daga cikin su ya faɗi wannan, wani kuma ya faɗi abu kaza.21Sai wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Yahweh, ya ce, 'Ni zan yaudare shi.' Yahweh ya ce da shi, 'Ta ya ya?'22Sai ruhun ya amsa, 'Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakin dukkan annabawansa. 'Yahweh ya amsa, 'Kai za ka iya yaudarsa, za ka kuma yi nasara sosai. Tafi yanzu ka yi.'23Duba yanzu, Yahweh ya sa ruhun ƙarya a bakin dukkan waɗannan annabawansa, Yahweh kuma ya zartar maka da masifa."24Sai Zedekiya ɗan Kan'ana ya zo kusa ya mari Mikaiya a kumatu, ya ce, "Wacce hanya Ruhun Yahweh ya bar ni har ya zo wurinka ya yi magana da kai?"25Mikaiya yace, "Duba, za ka sani a ranar nan, lokacin da ka gudu ka shiga har ƙuryar ɗaki don ka ɓuya."26Sarkin Isra'ila ya ce da baransa, "Ku kama Mikaiya, ku kai shi wurin Amon, gwamnan birni, da Yowash, ɗana.27Ku ce da shi, 'Sarki ya ce, a jefa wannan mutum a kurkuku a riƙa ciyar da shi da waina kaɗan da ruwan sha kaɗan, har sai na komo lafiya.'"28Sai Mikaiya yace, "Idan har ka dawo lafiya, Yahweh bai yi magana da ni ba." Ya ƙara da cewa, "Ku saurari wannan, dukkan ku mutane."29Ahab sarkin Isra'ila, da Yehoshafat sarkin Yahuda, sun tafi Ramot Giliyad.30Sarkin Isra'ila ya ce da Yehoshafat, "Zan bad da kamata in tafi wurin yaƙi, amma kai ka sa tufafin sarautarka." Sai sarkin Isra'ila ya bad da kamarsa ya tafi wurin yaƙi.31Yanzu sarkin Aram ya rigaya ya umarci shugabannin karusan yaƙinsa su talatin da biyu, cewa, "Kada ku yi yaƙi da kowa komai matsayin sojojinsa. Sai dai sarkin Isra'ila kaɗai."32Sa'ad da shugabannin karusai suka ga Yehoshafat sai suka ce, "Babu shakka wannan shi ne sarkin Isra'ila." Sun juya don su yi yaƙi da shi, Yehoshafat kuwa ya yi ihu.33Da shugabannin karusan yaƙi suka gane ba sarkin Isra'ila ba ne, sai su ka juya suka dena binsa.34Sai wani mutum ya shilla kibiya kawai, sai ta sami sarkin Isra'ila a tsakanin ƙafar sulkensa. Ahab ya ce da mai kora karusarsa, "Ka juya ka ɗauke ni daga yaƙin nan gama an yi mani rauni sosai."35A ran nan yaƙi ya yi tsanani ƙwarai, aka tallafi sarki a cikin karusarsa a gaban Aremiyawa. Ya mutu da yamma. Jinin yana fitowa daga raunin da aka yi masa yana zuba a cikin karusar.36A lokacin faɗuwar rana aka yi wa sojoji shelar cewa, "Kowanne mutum ya koma birninsa kuma kowanne mutum ya koma jiharsa.37Sarki Ahab ya mutu, aka kawo shi Samariya, su ka bizne shi.38Su ka wanke karusarsa a tafkin Samariya, karnuka su ka lashe jininsa (wannan shi ne wurin da karuwai su ke yin wanka a tafkin) kamar yadda Yahweh ya furta.39Game da sauran al'amuran Ahab da dukkan abin da ya yi, da gidan da ya gina na hauren giwa da biranen da ya gina, ba suna rubuce a littafin tarihin sarakunan Isra'ila ba?40Ahab ya yi barci tare da kakaninsa, Ahaziya ɗansa ya zama sarki a gurbin mahaifinsa.41Yehoshafat ɗan Asa ya fara sarauta a Yahuda a shekara ta huɗu ta Ahab sarkin Isra'ila.42Yehoshafat yana da shekaru talatin da biyar sa'ad da ya fara sarauta, ya yi sarauta a Yerusalem yana da shekaru ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba 'yar Shilhi.43Ya yi tafiya cikin hanyoyi irin na Asa, mahaifinsa; bai karkace daga gare su ba; ya yi abin da dai-dai a fuskar Yahweh. Duk da haka ba a ɗauke wuraren tsafi na tuddai ba. Mutanen sun ci gaba da miƙa hadayu da ƙona turare a tuddan.44Yehoshafat ya yi zaman salama da sarkin Isra'ila.45Sauran ayyuka game da Yehoshafat, da ƙarfin da ya nuna, da yadda ya yi yaƙi, ba suna rubuce a littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?46Ya kori sauran karuwai daga ƙasar waɗanda suna nan tun zamanin mahaifinsa Asa.47Babu sarki a Idom, amma wakili ne ya yi mulki a wurin.48Yehoshafat ya yi jiragen ruwa, za su tafi Ofir domin zinariya, amma ba su iya tafiya ba, gama jiragen sun farfashe a Eziyon Geber.49Sai Ahaziya ɗan Ahab ya ce da Yehoshafat, "Ka bar barorina su tafi tare da naka a cikin jirage." Amma Yehoshafat bai yarda ba.50Yehoshafat ya yi barci tare da kakaninsa aka bizne shi a wurin su a birnin Dauda, kakansa; Yahoram ɗansa ya zama sarki a gurbin mahaifinsa.51Ahaziya ɗan Ahab ya fara sarauta a kan Isra'ila a Samariya a shekara ta goma sha bakwai ta Yehoshafat sarkin Yahuda, ya yi sarauta shekara biyu a Isra'ila.52Ya yi abin da ke mugu a fuskar Yahweh, ya yi tafiya ta hanyar mahaifinsa, a cikin hanyar mahaifiyarsa, da hanyar Yerobowom ɗan Nebot, wanda ya sa Isra'ila yin zunubi.53Ya bauta wa Ba'al ya yi masa sujada, ya kuma tsokani Yahweh na Isra'ila ya yi fushi, kamar yadda mahaifinsa ya yi.
"shekara 3"
Maganar an yi amfani da shi a nan a fara farkon labari. Idan harshen ka na da wata hanyar yin wannan, za ka iya duba yin anfani da shi a nan.
Ahab ya yi wannan tambayar ya jaddada cewa ya kamata da sun riga sun ƙwace Ramot da Gileyad. AT: "Ramot Gileyad tamu ce, amma ba ma yin komai domin mu ƙwace ta daga hannun sarkin Aram?"
A nan kalmar "hannu" na nufin iko. AT: "mu ɗauke shi daga jagorancin sarki Aram"
Yehoshafat ya gaya wa Ahab cewa da shi, da mutanensa da dawakansa na Ahab ne, ma'ana Ahab zai iya shugabantarsu yadda ya so. AT: "Ni, sojojina, da dawakaina naka ne ka yi amfani da su ta kowacce hanya"
"mazaje 400"
A nan kalmar "hannu" na nufin iko. AT: "gama Ubangiji zai ba da Ramot da Gileyad a hannun sarki.'' "
Yehoshafat na nufin Ahab a fakaice don nuna girmamawa. AT: "ka da ka ce haka"
"ya yi wa kansa ƙahonin ƙarfe"
Matakan annabawan wakili ne na kwatancin yadda Ahab zai ci Aremiyawa da yaƙi. Sojojin Ahab za su yi nasara da babban ƙarfi, kamar bijimi na faɗa da wani dabba.
Hallakar da maƙiyina magana da shi kamar yana cinye su. za a iya cewa. AT: "har sai ka cinye su" or "har ka hallakar da su"
A nan kalmar "hannu" na nufin iko. AT: "ku bar sarki ya ci su"
"saurar" ko "mai da hankali akan abinda zan gaya maka"
Annabawa na faɗin abu ɗaya kamar sun yi magana da abu ɗaya. Maganar "maganar annabi" na nufin saƙon da annabin ya faɗa. AT: "annabawan sun faɗi abu ɗaya mai kyau ga sarkin"
A nan kalmar "su" na nufin "maganar annabi." AT: "bari abinda ka ce ya zama aabinda sukaa ce"
kalmar"su" na nufin Ahab, Yehoshafat, da sojojin su amma ba ga Mikaiya ba.
A nan kalmar "hannu" na nufin iko. AT: "zai bar sarkin ya ci su"
Ahab ya tambayi a cikin baƙin ciki ya kwaɓa mikaiya. AT: "yawancin lokaci ... a sunan Yahweh."
A nan kalmomin "suna" na nufin iko. AT: "a matsayin mai wakiltar Yahweh"
a nan "dukkan Isra'ila" na nufin sojojin Isra'ila. AT: "na ga dukkan sojojin Isra'ila"
sojojin ana kwatanta su da tumaki da ba su da mai kiwo saboda makiyayinsu, sarkin, ya mutu.
Yahweh ya yi magana game da sarki kamar shi ne makiyayi. kamar yadda makiyayi yake da hakkin lura da kare tumakin, sarki ma haƙƙinsa ne ya lura da mutanensa. AT: "waɗannan mutane ba su da mai jagoranci"
ahab ya tambayi ya jaddada cewa ya faɗi gaskiya game da Mikaiya. AT: "na gaya maka ... sai dai masfa!"
mutuwar Ahab a yaƙi an yi maganar kamar zai faɗi. AT: "zai mutu at Ramot Gileyad"
"ɗaya ... da wani" na nufin rundunar mala'iku biyu ku uku na samaniya waɗanda suke amsa tambayoyin Yahweh a ayar da ta wuce.
A nan kalmar "ruhu" na nufin halin annabawan da kuma kalmomin "bakin" na nufin abinda za su ce. AT: "ka sa dukkan annabawansa su faɗi ƙarya"
"sosai." kalmar "duba" anan ta ƙara jaddada abin da ya biyo baya.
A nan kalmar "ruhu" na nufin halin annabawan da kuma kalmomin "bakin" na nufin abinda za su ce. AT: "ka sa dukkan annabawansa su faɗi ƙarya"
Zadakiya ya yi wannan tambaya ta zagi da tsawata wa Mikaiya. AT: "ka da ki yi tunanin ruhun Yahweh ya bar ni in yi maki magana!"
"saurara" ko "mai da hankali ga abin da zan gaya maka"
"za ka san amsaw tambayarka." kamar Zadakiya tambayar shi marar buƙatar amsa fassara shi a matsayin bayani, wannan maganar za a iya fassara ta ba da bayani a fakaice. AT: "za ka san cewa ruhun Yahweh ya yi magana da ni"
Wannan ya bayyana wani abu da ba zai faru ba. Yahweh ya riga ya faɗa wa Mikaiya cewa sarkin ba zai dawo lafiya ba.
Ahab sarki ne mai mugunta wanda yayi mulkin arewacin mulkin Isra'ila daga 875 zuwab854BC. . Srki ahab ya rinjaye mutanen Isra'ila su bautawa gumaka. . Annabi Iliya ya fuskanci Ahabya gaya masa za a yi fãri mai tsananina tsowon shekara uku da rabi a matsayin hukuncin zunubin da sarki ahab yasa suka yi. . Ahab da matarsa Yezebel sun yi mugayen abubuwa, har da yin amfani da ikonsu su kashe mutane marasa laifi. (shawarar fassara: How To Translate names) (Duba: Ba'al, Iliya, Yezebel, mulkin Isra'ila, Yahweh) Nasosin littafin mai tsarki: . 1 Sarakuna 18:1-2 . 1Sarakuna 20:1-3 . 2 Tarihi 21:06 . 2 Sarakuna 09:08
. Ƙaƙƙarfa: H256
Yahweh
1 Sarakuna 19:2 1 Sarakuna 19:3 1 Sarakuna 19:5
Yehoshafat sunan waɗansu mutanem biyu n a tsohon juyi. . Wanda aka fi sani da wannan sunan shine Yehoshfat sarki na huɗu na da ya yi mulkin Yahuda. . Ya kawo salama tsakanin Yahuda da Isra'ila ya kuma hallakar da allolin ƙarya. . Ɗayan Yehoshafat "marubuci" na Sulaiman da Dauda. Aikinsa ya haɗa da rubuta takardu wa sarki ya sa hannu da kuma rubuta tarihi mai muhimmanci da ya faru a mulkin. (shawarar fassara: How To Translate_names) (Duba kuma: bagadi, Dauda, allolin ƙarya, Isra'ilawa, Yahuda, firistoci, Sulaiman)
. 1 Tarihi 03:10-12 . 1 Sarakuna 04:17 . 2 Tarihi 17:01 . 2 Sarakuna01:17 . 2 sama'ila 08:15-18 . Matiyu 01:7-8
. Ƙakƙarfa: H3092, G2498
alfarwa, alfarwai, allah, allahn ƙarya, alloli, allahiya, bautar gumaka, mai bautawa gumaka, Isra'ila, Isra'ilawa, Firist, firistici, firistoci
Ƙabilar Yahuda sun fi yawa a cikin ƙabilai goma sha biyu na Isra'ila. Mulkin Yahuda ya ƙumshi ƙabilar Yahuda da t Binyaminu. . Bayan sarki Sulaiman ya mutu, ƙasar Isra'ila ta rabu kashi biyu. Mulkin Yahuda na kudancin ana samun su a yamma da tekun gishiri. . Kai na mulkin Yahuda shi ne Yerusalem. . Sarakuna takwas na mulkin Yahuda su ka yi biyayya da Yahweh suka jagorancin mutanesu su bautawa Yahweh. Sauran sun yi mugunta suka sa mutanen bautar gumaka. . Sama da shekara 120 bayan Asiriya ta ci Isra'ila da yaƙi (kudancin mulkin), Yahuda an ci shi ne ta wurin ƙasar babila. Mutanen Babila sun hallakar da komai har ma sun ɗauki waɗansu mutanen IUsra'ila su zama bayinsu. (Duba Kuma: Yahuda, tekun gishiri) Nassoshin littafi mai_tsarki: . 1 Samaa'ila 30:26-28 . 2 sama'ila 12:08 . Yusha'u 05:14 . Irmiya 07:33 . Alkalawa 01:16-17
. Ƙaƙƙarfa: H4438, G3063
1 Sarakuna 18:7 1 Sarakana 18:10 1 Sarakuna 18:13 1 Sarakuna 20:1 1 Sarakuna 20:5 1 Sarakuna 20:6 1 Sarakuna 20:9
Rama wani birni ne a tudun Giliyad kusa da rafin Yodan. Ana kuma kiran shi Rama ta Giliyad. . Rama tana Isra'ila ne a cikin ƙabilar Gad kuma ana yi masa laƙabi da birnin tsibiri . sarki Ahab na Isra'ila da sarki Yehoshafat na Yahuda su ka yi yaƙi da sarkin Aram a Rama. an kashe Ahab a wannan yakin. . Wasu lokuta sarki Ahaziya da sarki Yoram suka yi ƙoƙarin su ɗauke Rama da ga hannun sarki Aram. (Shawarar fassara: Translate Names) (Duba kuma: Ahab, Ahaziah, Aram, Gad, Yehoshafat, Yehu, Yoram, yordan, rafi Yodan, Yahuda, tsibiri) Nasosin littafi mai tsarki: . 1 Tarihi 06:73 . 1 Sarakuna 22:03 . 2 Tarihi 18:03 . 2 Sarakuna 08:28-29
. Ƙaƙƙarfa: H7216, H7418, H7433
gudun hijira
Gileyad sunan wani yanki ne na gabas masu duwatsu sosai a gabas da rafin Yodan inda Isra'ilawa ƙabilar Gad, Ru'ubainu da manasse suke. . Yankin ana kuma kiranshi da "birnin tudu na Gileyad" ko "dutsen Gileyad" . "Giliyad" kuma sunan mazaje da yawa ne a tsohon alkawari. ɗaya daga cikin waɗannan mazaje jika ne na Manasse. Wani kuma mahaifin Yafta.
(Duba kuma: Gad, Yafta, Manasse, Ru'ubainu, ƙabilai goma sha biyu an Isra'ila )
1 Tarihi 02:22 1 sama'ila 11:01 Amos 01:03 Mai-maitawar Shari'a 02:36-37 Farawa 31:21 Farawa 37:25-26 Kalmomin bayani: Ƙaƙƙarfa: H1568, H1569 Duba kuma ƙabilai goma sha biyu na Isra'ila, ƙabilai goma sha biyu na 'ya'yan Isra'ila, ƙabilai goma sha biyu
Kalmar "sarauta" na nuna mutane ko abubuwa da suke da halaƙa da sarki ko gimbiya. . Msalin abubuwa da za a iya kira sarauta sun haɗa da kayan sarki, fada, kursiyi da rawani. . sarki ko sarauniya a kullum suna zama a fada. . sarki yakan sa wasu irin kaya masu ƙayatarwa ana kiransu "rigan sarauta." kuma kayan sarki shuɗi ne, . a sabon alkawari masu ana kiransu "'ya'yan sarki" ko "firist da suke yi wa Allah mai rai hidima" . Kalmar sarauta za a iya fassara ta kuma da "masu dangantaka da sarki" (Duba kuma: sarki, fada,firist, shuɗi, sarauniya,kayan sarauta.) Nassoshin littafi mai tsarki: 1 sarakuna 10:13 2 Tarihi 18:28-30 Amos 07:13 Farawa 49:19-21
Ƙaƙƙarfa: sarki, sarakuna, mulki, mulkoki, mai sarauta, fada, fadodi, firist, firistoci, firistoci,shuɗi, sarauniya, sarauniyoyi,kayansarauta,
Kayan sarauta dogo ne mai dogon hannu da mace ko na miji zai iya sawa yana nan kamar alkyaba. . kayan sarauta gaban su a buɗe ne kuma ana ɗaure su daga baya zuwa gaba ta wurin ƙugu da igiya. za su iya zama dogaye ko gajeru. . shuɗin kaya ana sa su ne ga jinin sarauta, mai kuɗi Nasaoshin littafi mai tsarki: Fitowa 28:4-5 Farawa 49:11-12 Luka 15:22 Matiyu 27:27-29
Ƙaƙƙarfa: H145, H155, H899, H1545, H2436, H2684, H3671, H3801, H3830, H3847, H4060, H4254, H4598, H5497, H5622, H6614, H7640, H7757, H7897, H80071, G1746, G2067, G2440, G4749, G4016, G5511
sarauta, ma sarauta, sarkuna
shugabanin sojoji guda biyu-"shugabanin 32"
ta wurin furta komai matsayin sojansa, sarkin na nufin dukkan sojoji. AT: "ka da ku yaƙi kowanne soja"
Wanna maganar an yi amfani da shi a fara farkon labari. Idan hasrshenk a na da yadda yake sa wa ka iya amfani da shi.
ma'ana 1) ya yi shi rin harbar soja bai san da cewa Ahab ne ba 2) ya shilla kibiyar ba tare da nufin harbin wani ba.
za mu iya cewa. AT: "wani ya riƙe sarkin a cikin karusansa"
a nan kuka na nufin Sojoji da ke kuwwa. AT: "sojoji suka fara kuwwa"
waɗannan maganganun na nufin abu ɗaya kuma an haɗa su don a nanata abu.
za mu iya cewa. AT: "sojojinsa suka kawo jikinsa samariya"
"mutane suka bizne shi"
A nan "kamar yadda Yahweh ya furta" na nufin Yahweh da kansa. AT: "kamar yadda Yahweh ya furta. "
za mu iya cewa misalai amsar mai kyua ce. Tambayar bata buƙatar amsa ay amfani da ita a jaddada abu. Duba yadda aka fassara shi a 15:31. AT: "su na a rubuce a littafin tarihin Isra'ila." ko "za ku iya karanta su a littafin tarihi na sarakunan Isra'ila"
mutuwar Ahab an yi maganasa kamar ya na barci ne. dabu yadda aka fassara shi a 21:10. AT: "mutuwa"
shekara biyar-"shekara 35"
shekara ashirin da biyar-" shekara 25"
Rayuwar mutum ana fassara shi da tafiya kamar mutumin nan ya yi tafiya a hanya. AT: "ya yi abu iri ɗaya da Asa mahaigfinsa, ya yi"
A nan "fuska" na wakiltar gani da ra'ayin Yahweh an fassara kamar yana ganin abin. AT: "abinda Yahweh ya ga mugunta ne"
za mu iya cewa. AT: "bai ɗauke wuraren tuddai ba" (Duba: activepassive)
za mu iya cewa misalai amsar mai kyua ce. Tambayar bata buƙatar amsa ay amfani da ita a jaddada abu. Duba yadda aka fassara shi a 14:29. AT: "su na a rubuce a littafin tarihin Isra'ila." ko "za ku iya karanta su a littafin tarihi na sarakunan Isra'ila"
za mu iya cewa. AT: "jiragen sun farfashe" (Duba: )
mutuwarYehoshafat an yi maganasa kamar ya na barci ne. dabu yadda aka fassara shi a 2:10. AT: "mutuwa"
za mu iya cewa. AT: "aka bizne shi"
"ya yi mulki shekara biyu"
Ra'ayin Yahweh akan wani abu ana maganarsa kamar ganin wannan abin. AT: "abinda Yahweh ya ga mugu ne"
Rayuwar mutum ana fassara shi da tafiya kamar mutumin nan ya yi tafiya a hanya. AT: "ya yi abu iri ɗaya da Asa mahaigfinsa, ya yi"
A nan kalmar "Isra'ila" na nufin ƙabilai goma na arewaci da ya kafa mulkin Isra'ila.
Kalmar "bauta" da "sujada" na nufin abu ɗaya.
A nan kalmar "Isra'ila" na nufin dukkan ƙabilai goma sha biyu na zuriyar Yakubu.
1Mowab ta tayar wa Isra'ila a bayan mutuwa Ahab.2To sai Ahaziya ya faɗo daga sakatar gidan samansa a Samariya, har ya yi rauni. Sai ya aika 'yan saƙo ya ce da su, "Ku je ku tambayi Ba'al Zebub, allahn Ekron, ko zan warke daga wannan raunin."3Amma mala'ikan Yahweh yace da Iliya Batishbe, "ka tashi ka je ka sadu da 'yan saƙon sarkin Samariya, ka tambaye su, ko domin ba Allah ne a Isra'ila shi ya sa kuka je kuka tuntuɓi Ba'al Zebub, allahn Ekron?4Domin haka Yahweh ya ce, ba za ka sauko daga wannan gadon da ka hau ba; a maimakon haka za ka mutu.'"' Daga nan sai Iliya ya tafi.5Bayan 'yan saƙon sun dawo wurin Ahaziya, sai ya ce da su, "Meyasa ku ka dawo?"6suka ce da shi wani mutum ne ya zo ya gamu da mu ya ce mana, ku koma wurin wanda ya aiko ku ku ce da shi, "Yahweh ya faɗi wannan; Ashe babu Allah ne a Isra'ila da ka aika 'yan saƙo Ekron su tambayi Ba'al Zebub? saboda haka ba za ka tashi daga gadon jinyarka ba, a maimakon haka hakika zaka mutu."""7Ahaziya yace da 'yansaƙonsa "wanne irin mutum ne shi, mutumin da ya zo wurinku ya faɗa muku wannan magana"?8Suka ce da shi yana saye da rigar da a ka yi da gasusuwa da kuma ɗammara ta fata a kwankwasonsa," sai sarkin ya amsa ya ce Iliya ne Batishbe."9Sai sarki ya aika jami'ai da sojoji hamsin wurin Iliya. Jami'an suka je wurin Iliya a inda ya ke zaune a saman dutse. Jami'an suka yi magana da shi cewa, "Kai mutumin Allah, sarki ya ce ka sauko ƙasa."10Iliya ya amsa ya ce da jami'an, "In ni mutumin Allah ne, bari wuta tasauko daga sama ta ƙone mutanenku guda hamsin." Wuta ta sauko daga sama ta ƙone mutanensa hamsin tare da shi.11Sai sarki Ahaziya ya sake yin aike wurin Iliya da wata runduna ta mutum hamsin tare da hafsa. shi ma wannan hafsan ya sake cewa da Iliya, "Kai mutumin Allah, sarki ya ce ka sauko da sauri."12Iliya ya amsa ya ce da su, in ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta ƙone ku tare da mutanenka guda hamsin." Sai wuta ta sake saukowa daga sama ta ƙone shi tare da mutanensa guda hamsin.13Sarki kuma ya sake aikawa da ƙungiya ta uku tare da mazaje hamsin mayaƙa. wannan hafsan sai ya je ya durƙusa a gwiwarsa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce da shi, "kai mutumin Allah ina roƙonka bari raina da na waɗannan sojoji hamsin ya sami daraja a gabanka.14Hakika wuta ta sauko daga sama ta ƙone rundunoni guda biyu na farko tare da hafsoshinsu, amma yanzu ina roƙo bari raina ya zama da daraja a gabanka."15Sai mala'ikan Yahweh yace da Iliya, "Ka sauka ƙasa tare da shi. kada ka ji tsoronsa." Sai Iliya ya tashi ya sauka ya tafi tare da shi zuwa wurin sarki.16Can sai Iliya ya ce da Ahaziya, "Wannan shi ne abin da Yahweh ya ce, 'Ka aika manzanni su tambayi Ba'al Zebub allan Ekron. Shin domin ba bu Allah ne a Isra'ila wanda zaka tambaya domin samun sadarwa? to yanzu hakika ba zaka sauko daga gadon da ka hau ba hakika za ka mutu."17Don haka sarki Ahaziya ya mutu bisa maganar Yahweh wadda Iliya ya furta. Sai Yorom ya gaji sarautarsa, a shekara ta biyu ta Yehoram ɗan Yehoshafat sarkin Yahuda, saboda Ahaziya ba shi da ɗa.18Game kuma da sauran abubuwa game da Ahaziya, ashe ba a rubuta su a littafin ayyukan sarakunan Isra'ila ba?
"ƙasar mowab"
Gidan saman an gina shi ne a saman soron fadar. Ragar an yi ta ne da abubuwa sirara an yi masu ado an gicciya sa da juna su bada murfin taga. AT: "tagar itace ta shinfidar fada"
Wannan sunan Allah ne da ya bayyana kansa ga jama'arsa a Tsohon Alƙawari. Duba translationWord shafi dame da Yahweh don ganin yadda za a fassara wannan.
Wannan na nufin mutum da ga garin Tishba.
Wannan tambayar ba ta buƙatar amsaan yi ta ne a tsauta masu don sun tuntuɓi Ba'al-Zebub. Za a iya rubuta wannan a matsayin sanarwa. Saboda da sun san akwai Allah na Isra'ila. AT: "ku wawaye! Kun san akwai Allah a Isra'ila, amma kuna yi kamar baku sani ba da kuka aikeni in tyuntuɓi Ba'al-Zebub, allahn Ekron!"
Kalmar "tuntuɓa" a sami ra'ayin wani game da tambaya.
Wannan saƙon Yahweh ne zu ga sarki Ahaziya. AT: "Don haka Yahweh ya ce wa sarki Ahaziya"
Lokacin da aka ji wa sarki Ahaziya rauni, an ɗora shi akan gado. Yahweh ya ce ba zai warke ba ba zai tashi daga gadon ba. AT: "ba za ka warke ba, ba zaka tashi daga gadon da kake kwance a kai ba"
Bayan gamu wa da Iliya, bayan 'yan saƙon sun dawo wurin sarki maimakon zuwa Ekron.
Wannan tambayar ba ta buƙatar amsaan yi ta ne a tsauta masu don sun tuntuɓi Ba'al-Zebub. Za a iya rubuta wannan a matsayin sanarwa. Saboda da sun san akwai Allah na Isra'ila. AT: "ku wawaye! Kun san akwai Allah a Isra'ila, amma kuna yi kamar baku sani ba da kuka aikeni in tyuntuɓi Ba'al-Zebub, allahn Ekron!"
Lokacin da aka ji wa sarki Ahazariya rauni, an ɗora shi akan gado. Yahweh ya ce ba zai warke ba ba zai tashi daga gadon ba. Duba yadda aka fassara shi a 1:3. AT: "ba za ka warke ba, ba zaka tashi daga gadon da kake kwance a kai ba"
Ma'anar mai yiwuwa sune: 1) wannan maganar ya yi ne akan shi da yake da gasusuwa kamar yasa rigan fata. AT: "yana da gasusuwa sosai" ko 2) "kayansa anyi su ne daga gashin dabbobi"
Sarki ya aika shuganni jami'ai da sojoji da mutane hamsin su kawo Iliya wurinsa. AT: "sai sarki ya aika shugabannin da sojoji hamsin su kawo Iliya"
"sojoji 50"
Shugabannin suka kira Iliya mutumin Allah, amma sarki da shugabanni basu nuna wa Iliya alamar ban girma. In ni mutumin Allah ne, Iliya yace bari wuta tasauko daga sama, wannan zai nuna cewa Iliya mutumin Allah kuma ya cancanci girmamawa daga gare su. AT: "Idan ni mutumin Allah, bari wuta tasauko daga sama" ko "Idan ni mutumin Allah ne kamar yadda kunka ce, bari wuta tasauko daga sama"
Wannan na nufin wutar ta sauko daga Allah. AT: "wuta daga Allah"
"jarumawa 50" ko "sojoji 50"
"ya roƙe shi"
Shugaban sojojin cewa bayinsa bayin Iliya ne ya nuna masa girmama wa. AT: "sojojin na hamsin"
Anan kalmar "gaban" Iliya na wakiltar hukuncinsa ko kimantawa.. Shugaban sojojin na roƙon Iliya ya bar su a raye. AT: "ina roƙon ka ka kula da raina ... zama mai daraja a gare ka amma ba kashe mu ba"
Wannan tambayar ba ta buƙatar amsaan yi ta ne a tsauta masu don sun tuntuɓi Ba'al-Zebub. Za a iya rubuta wannan a matsayin sanarwa. AT: "Dole ne a yi tunanin cewa babu wani Allah a cikin Isra'ila wanda zaku nemi bayani!"
"abinda Yahweh ya faɗa wa Iliya cewa Iliya ya faɗi"
Wannan ya nuna lokacin da Yehoram ya fara mulkida ya nuna loƙutan da sarkin Yahuda ya yi mulki. AT: "a shekara ta biyu ta Yehoram ɗan Yehoshafat yake sarautar Yahuda"
Za a iya wanna tambaya azaman wata sanarwa ko a ckin tsari mai aiki. AT: "an rubuta su ... Isra'ila."
1To sai ya zama a lokacin da Yahweh zai ɗauki Iliya zuwa sama ta guguwa, da Iliya ya rabu da Elisha zuwa Gilgal.2Iliya ya ce da Elisha "ka jira nan ina roƙonka domin Yahweh ya aike ni zuwa Betel, Elisha ya ce da shi "Muddin Yahweh na raye, kana kuma raye, ba zan bar ka ba." To sai suka tafi Betel tare.3"Ya'yan annabawa da ke a Betel suka zo wurin Elisha suka ce da shi, Ko ka san Yahweh zai ɗauke shugabanka daga gare ka yau?" Elisha ya amsa masu, i na sani, amma kada ku yi magana tukuna."4Iliya ya ce da shi, Elisha ka jira a nan, Domin Yahweh ya aike ni Yeriko." Sai Elisha ya amsa, "Muddin Yahweh na raye, kai kuma kana raye, ba zan rabu da kai ba." Domin haka suka tafi Yeriko.5Sai 'ya'yan annabawa da ke a Yariko suka zo wurin Elisha suka ce da shi, "Ko ka san cewa yau Yahweh zai ɗauke shugabanka da ga gare ka? "Elisha ya amsa, "I na sani, amma ka da ku yi maganar tukuna."6Sai Iliya ya ce da shi, "Ka tsaya nan, domin Yahweh ya aike ni Yodan.'" Elisha ya amsa, Muddin Yahweh na raye, kai kuma kana raye, Ba zan rabu da kai ba." domin haka su biyun suka tafi.7Can an jima sai 'ya'yan annabawa hamsin suka tsaya a gefensu da ɗan nisa su kuma biyun suka tsaya a gefen Yodan.8Iliya ya cire tufafinsa, ya naɗe shi sai ya bugi ruwa da shi. sai rafin ya rabu biyu ta kowanne gefe su biyu suka taka sandararriyar ƙasa suka ƙetare.9Bayan sun ƙetare, sai Iliya ya ce da Elisha, "ka roƙi abin da zan yi maka kafin a ɗauke ni daga gare ka." Elisha ya amsa, ina roƙo a ba ni riɓi biyu na ruhunka ya sauko a kaina."10Iliya ya amsa, "Ka roƙi abu mai wuya. amma duk haka, in ka gan ni a lokacin da aka ɗauke ni daga gare ka, wannan zai faru sabo domin ka, amma in ba haka ba, ba zai faru ba."11Da suka ƙara tafiya suna magana, sai ga karusai na wuta da dawakai na wuta suka baiyana, waɗanda suka raba tsakanin su, Iliya ya tafi sama ta guguwa.12Da Elisha ya gani ya yi kuka, ya ce "Babana, Babana, karusai na Isra'ila da mahaya dawakansu!" Bai ƙara ganin Iliya ba, sai ya ɗauki tufafinsa ya keta su biyu.13Sai ya ɗauki alkyabar Iliya da ta faɗo masa, ya koma ya tsaya a bakin Yodan. Ya bugi ruwan da tufafin Iliya wanda ya faɗo ya ce, "Ina Yahweh, Allah na Iliya?"14Bayan ya bugi ruwan sai ruwan ya rabu biyu ta kowanne gefe sai Elisha ya ƙetare.15Lokacin da 'ya'yan annabawa da ke Yeriko suka ga ya ƙetaro daga wurinsu, suka ce "Ruhun Iliya ya sauko akan Elisha!" Sai suka zo domin su tare shi, suka sunkuyar da kawunansu a ƙasa a gabansa.16Suka ce da shi, Duba yanzu a cikin barorinka akwai mazaje hamsin majiya ƙarfi. Ka bar su su je su nemo shugabanka, ƙila ko Ruhun Yahweh ya ɗauke shi ya kai shi bisa wasu duwatsu, ko kuma waɗansu kwarurruka." Elisha ya amsa ya ce kada ku aike su."17Amma bayan sun matsa masa sai ya ji nauyi, ya ce "ku aike su." Suka aiki mazaje hamsin suka yi ta nema har kwana uku amma basu same shi ba.18Suka dawo wurin Elisha, a lokacin da yake a Yeriko, sai ya ce da su, "Ashe ban ce da ku kada ku je ba'?"19Mutanen birnin suka ce da Elisha, "Duba muna roƙon ka, halin da muke ciki a garin nan yana da faranta rai sosai kamar yadda shugabana ya gani, amma ruwan ba shi da kyau ƙasar kuma ba ta bada hatsi."20Elisha ya amsa, "Ku samo mini sabon daro ku sa gishiri a cikinsa," domin haka suka kawo masa daro.21Sai Elisha ya fita ya tafi mafitar ruwan rafin ya sa gishirin a cikinsa; sai ya ce ga abin da Yahweh ya ce, na warkar da waɗannan ruwaye. daga yanzu ba za a sami mutuwa ko rashin 'ya'ya ba a cikin ƙasar.'"22Domin haka ruwan ya gyaru har ya zuwa yau, ta wurin maganar Elisha.23Sai ya tafi can zuwa Betel. Lokacin da yake tafiya akan hanya, sai samari suka fito daga birni suka yi masa ba'a; suka ce da shi, "Kai mai saiƙo ka tafi, kai mai saiƙo ka tafi!"24Sai Elisha ya duba gefensa ya gan su; Sai ya yi kira ga Yahweh ya la'antasu. Sai matan damisa guda biyu suka fito daga kogo suka raunata samari guda arba'in da biyu.25Daga nan sai Elisha ya bar wurin ya tafi Tsaunin Karmel, daga can kuma sai ya koma Samariya.
"Don haka ya faru." Ana amfani da wannan kalmar don gabatar da taron na gaba a cikin labarin.
ƙaƙƙarfar iska da take juyawa kusa da kusa
"Muddin Yahweh na raye, kana kuma raye" A nan Elisha ya kwatanta cewa haƙiƙa Yahweh da Iliya na raye lailai ne abinda yake cewa. Wannan wata hanyar ce ta yi alkawarin rantsuwa. AT: "na rantse maka"
Wannan ba lailai 'ya'yan annabawa na cikinsu ba, amma, suma wata ƙungiyar annabawa ce. AT: "ƙungiyar mazaje annabawa"
"Lokaci da Iliya da Elisha suka zo kusa da Yeriko, 'ya'yan annabawa da suke a can suka ce wa Elisha"
"'ya'yan annabawa 50" (Duba: transate_numbers)
Wanann na nufin suna tsaye suna fuskantar su. AT: "suka tsaya su na fuskantarsu" ko "suka tsaya suna kallonsu"
wani yankin kaya da ake amfani da shi kamar gyale
"Sai ruwan Kogin Yodan ya rabu biyu ta kowanne gefe su biyu suka taka sandararriyar ƙasa suka ƙetare."
"a gefen dama da gefen hagu." Wannan na nufin dama da hagu na inda Iliya ya buga ruwa.
"ya faru"
Wannan na nufin tsallake Kogin Yodan. AT: "tsallake Kogin Yodan"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "kafin Yahweh ya ɗauke ni daga gareka"
A nan ruhun Iliya na nufin iko na ruhaniya. AT: "ninkin ikonka na ruhaniya"
Kalmar "duba" a nan na jijjiga mu ma maida hankali ga bayani na bammamaki da zai biyo baya.
A nan kalmar "na wuta" na nufin suna kewaye da wuta. AT: "karusai kewaye da wuta dawakai na wuta na ja"
"an ɗauke shi zuwa sama ta guguwa."
Elisha yana kiran Iliya shugabansa mai mutuntawa.
Mutane za su iya keta kayansu alamar bakin ciki ko makoki AT: "keta su kashi biyu ya nuna ɓacin ransa"
Elisha na tambaya ko Yahweh na tare da shi kamar yadda ya kasance da Iliya. AT: "Yahweh, Allahn Iliya ko kana tare da ni?"
Rafin ya rabu biyusain Elisha ya yi tafiya zuwa ɗaya gefen akan sandararriyar ƙasa, yadda ya yi lokacin da yana tare da Iliya.
Suna nuna masa girmamawa da kuma karban shi a matsayin sabon shugabansu.
Anan "ruhun Iliya" na nufin ikon sa na ruhaniya. Wannan ya yi maganar Elisha ya sami wannan iko na ruhaniya kamar wani abu ne da za'a iya ganinsa ya sauko masa. AT: "Elisha ya sami iko na ruhaniya irin wanda Iliya yake dashi" ko "Ikon ruhaniya da Iliya yake da shin yanzu ya koma kan Elisha"
Waɗannan mutanen na nufin kansu da suka ce ce "mazaje hamsin majiya ƙarfi." AT: "Duba yanzu, mu mazaje ne majiya ƙarfi guda hamsin kuma mu naku ne. Ku bar mu muje"
"mazaje majiya ƙarfi 50"
'Ya'yan annabawan suka yi ta tambayar Elisha har sai da ya yi fushi ya ce "a'a." AT: "Suka yi ta tambayar Elisha har sai da ya yi fushi ya yi musun roƙonsu, don haka"
Elisha ya yi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa ya riga ya gaya masu abin da zai faru. Za a iya wannan a matsayin sanarwa. AT: "na gaya maku kada kuje, domin ba za ku same shi ba!"
"shugabannin birnin"
Hakan na nuna birnin an sa shi a wuri mai kyau. AT: "birnin nan yana wuri mai kyau" ko "wannan birnin ya na matsaya mai kyau"
Mutanen suna nufin Elsha anan a matsayi "shugabana" domin girmamawa.
"ba da 'ya'ya masu kyau"
Wannan ya yi magana akan Yahweh zai warkar da ruwa mara kyau kamar ya riga ya yi. AT: "sa ruwan su zama da kyau sosai" (Duba: metaphor)
Wannan na nufin abubuwan da ruwa mara kyau za mi iya cewa. AT: "ba bu sauran mutuwa ko matsala da gonar inabinmu da ya ke zuwa ta dalilin wannan ruya" ko "daga yanzu wannan ƙasar zata 'ya'ya ruwan kuma zai bada rai"
Za a iya fadin wannan a matsayin aikatau. AT: "ruwan ya zama warkakke koda yaushe"
Ma'ana wannan shi ne abu da ya daɗe a yana yin da yke ciki har na tsawon wasu koƙuta. AT: "ta wurin kalmar da Elisha ya faɗa, kuma ruwan za zauna mai kyau"
An yi amfani da kalmar "haura" a nan saboda Betel ta fi girma sama da Yeriko.
Samarin sun so Elisha ya ya tafi ya bar su sai suka nuna ta wurin cewa "ka tafi." AT: "barnan"
masu saiƙo basu da koda da gashi ko guda ɗaya a kansu. Samari suna yi wa Elisha ba'a don yana da saiƙo.
"samarin 42"
1A shekara ta sha takwas ta Yohoshafat sarkin Yahuda, Yoram ɗan Ahab ya fara mulkin Isra'ila a Samariya; ya yi mulki na shekaru sha biyu.2Ya yi abin da ke mugu a gaban Yahweh, amma ba kamar mahaifinsa da mahaifiyarsa ba; domin ya kawar da masujadar Ba'al da mahaifinsa ya gina.3Duk da haka ya riƙe zunubin Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi, bai kauce daga gare su ba.4Sai Mesha sarkin Mowab ya yi sausayar tumaki. Ya ba sarkin Isra'ila raguna 100,000 da kuma fatun raguna 100,000.5Amma bayan Ahab ya mutu, sai sarkin Mowab ya tayar wa sarkin Isra'ila.6Domin haka sarki Yoram ya gudu daga Samariya a wancan lokacin domin ya shirya sojojin Isra'ila domin yaƙi.7Sai ya aika da saƙo ga Yohoshafat sarkin Yahuda, cewa, Sarkin Mowab ya tayar mani. Ko za ka tafi tare da ni yaƙi gãba da Mowab?" Yehoshafat ya amsa, "Zan je. Ni ma kamar ka ne, mutanena kuma kamar mutanenka ne, dawakaina kamar dawakanka ne."8Sai ya ce, "Ta wacce hanya zamu kai masu hari?" Yehoshafat ya amsa, "Ta hanyar jejin Idom."9To sai sarakunan Isra'ila da Yahuda dana Idom suka yi ta kai da kawowa har tsawon kwanaki bakwai. Babu ruwan sha domin sojojinsu, babu kuma domin dawakansu ko kuma sauran dabbobi.10To sai sarkin Isra'ila ya ce, Me kenan? ko Yahweh ya tattaro sarakuna guda uku ya bashe su a hannun Mowab ne?"11Amma Yehoshafat ya ce, Ko babu wani annabin Yahweh ne, da zamu tambayi Yahweh ta wurinsa?" Sai ɗaya daga cikin barorin sarkin Isra'ila ya amsa ya ce, "Eleisha ɗan Shafat yana nan, shi ne ya zuba ruwa a hannun Iliya."12Yehoshafat ya ce Maganar Yahweh na tare da shi." Domin haka Yehoshafat sarkin Isra'ila da sarkin Idom suka tafi wurinsa.13Elisha yace da sarkin Isra'ila, Me zan yi da kai? Ka tafi wurin annabawan mahaifinka da mahaifiyarka." Sai sarkin Isra'ila ya ce da shi, A'a domin Yahweh ya kira waɗannan sarakuna guda uku tare domin ya bashe su a hannun Mowab."14Elisha ya amsa, Muddin Yahweh na raye a gaban wanda nake tsaye, tabbas in da ba domin ina ganin darajar kasancewar Yehoshafat sarkin Yahuda ba, da ba zan ji ku ko in dube ku ba.15Amma yanzu ka kawo mani makaɗi."Sai mai kiɗa ya yi kiɗa, sai hannun Yahweh ya zo kan Elisha.16Ya ce Yahweh ya faɗi wannan, 'Ka sa tsirai su fito daga wannan kwarin.'17Domin Yahweh ya faɗi wannan, Ba zaka ga iska ba, ko kuma ka ga ruwan sama ba, amma wannan rafin zai cika da ruwa, zaku kuma sha, kai da bisashenka da dukkan dabbobinka.'18Wannan abu ne mai sauƙi a gaban Yahweh, Zai kuma ba ka nasara akan Mowabawa.19Za ka kai hari akan ƙayatatcen birni da kowanne birni ku sare kowacce bishiya mai kyau, ku kuma busar da kowanne wuri mai fid da ruwa, ku kuma mayar da kowanne wuri kufai da duwatsu."20Da safe a kusan lokacin miƙa hadaya, sai ga ruwa daga wajejen Idom; sai ƙasar ta cika da ruwa.21To bayan duk Mowabawa sun ji cewa sarakuna sun zo su yaƙe su, sai suka tattara kansu, duk waɗanda kan iya ɗaukar makami, sai suka tsaya akan iyaka.22Suka tashi da sassafe rana kuma ta haskaka. Da Mowabawa suka ga ruwa kusa da su, ya zama ja kamar jini.23Sai suka ce "Wannan jini ne! Hakika an hallaka sarakuna, sun kuma karkashe juna! To yanzu Mowab, ku mu je mu kwashe su ganima!"24Bayan sun zo sansanin Isra'ilawa, Isra'ilawa suka ba su mamaki suka hari Mowabawa, waɗanda suka tsere daga gabansu. Sojojin Isra'ila suka kori Mowabawa daga ƙasar, suka karkashe su.25Suka rushe biranen, da kuma duk wani yankin ƙasa kowannen su ya dinga tura dutse har sai da suka rufe birnin suka cike kowanne kwari na ruwa, suka cinye kowanne ɗan itaciya. Amma sojojin saye da kayan yaƙi suka sake kai hari a kansa.26Bayan sarki Mesha na Mowab ya ga ya yi rashin nasara, sai ya ɗauki mayaƙa masu sara domin su hari sarkin Idom, amma suka kasa.27Sai ya ɗauki babban ɗansa, wanda zai yi sarauta bayansa, ya miƙa shi a matsayin baiko na ƙonawa akan ganuwa. Domin haka aka sami babbar hasala gãba da Isra'ila, sojojin Isra'ila kuma suka rabu da sarki Mesha suka koma ƙasarsu.
Wannan na nuna lokacin da Yoram ya fara mulki an fara da tsawon lokacin da sarki mai mulki ya yi. Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "a shekara ta goma sha takwas ta Yehoshafat ya yi yana mulki"
"shekara ta 18"
Wasu loƙuta wannan mutumin ana kiransa "Yehoram." Wannan ba mutum ɗaya bane da wanda aka yi maganarsa a 2 Sarakuna 1:17 mai suna "Yehoram."
Anan "gaban" yana wakiltar tunanin Yahweh ko hukuncinsa . AT: "abin da Yahweh ya ga mugunta ne" ko "abin da mugunta ne a hukuncin Yahweh"
Wannan nuna irin muguntar da ya yi amma bai kai mahaifansa. AT: "amma bai yi mugunta kamar muguntar da mahaifinsa da mahaifiyar sa suka yi"
Masujadar ana amfani da ita wajen yi wa Ba'al sujada ko da yake ba'a san yadda take ba. AT: "kawar da masujadar Ba'al"
Wannan karin magana ne. A nan "riƙe" na nufin a ci gaba da yi. AT: "ya ci gaba da yin zunubin"
Wannan sunan mutum ne.
"Juyawa yayi" karin magana ne da ga wani abu habaici neda yake nufin a daina yi. AT: "bai daina yin zunubi ba"
Mesha ya ba sarkin Isra'ila waɗannan abubuwa domin mulkinsa ya ƙarƙashin ikon sarkin Isra'ila. ma'anar wanna zai zama. Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "duk shekara ana matsa masa ya ba sarkin Isra'ila raguna 100,000 da kuma fatun raguna 100,000 saboda mulkin sa na ƙarƙashin ikon sarkin Isra'ila"
"shirya sojojin Isra'ila domin yaƙi." A nan "dukkan Isra'ila" na nufin dukkan sojojin Isra'ila. AT: "shirya sojojin Isra'ila domin yaƙi"
Sarki Yoram ya ci gaba da yin magana da sarki Yehoshafat.
Kalmar "ka" na nufin Yehoshafat, amma ma nan nufin shi da sojojinsa. Anan "Mowab" na nufin "sojojin Mowab" AT: "Kai da sojojinka za ku bini mu yi yaƙi gãba da sojojin Mowab?"
Yehoshafat yana cewa shi da sojojinsa za su yi yaƙi da sarki Yoram gãba da Mowab. AT: "za mu tafi da kai"
Yehoshafat na gaya wa Yoram ya yi amfani da shi, mutanen sa, da sojojinsa don biyan buƙatunsa. Ya yi wannan maganar kamar su na Yoram ne. Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "Mu na a shirye muyi dukkan abinda ka ke son muyi. Sojojina da dawakaina a shirye suke su taimakeka"
"shiga ta cikin jejin Idom"
Wannan na nufin sarakuna tare da sojojin su. AT: "sarakunan Isra'ila da sojojinsa tafi dare da sarkin Yahuda da sojojinsa da kuma sarkin Idom da sojojinsa"
Ma'nar mai yiwuwa sune: 1) sarakuna ba su da tabbacin inda za su je don haka sauya aikibla sau da yawa or 2) sarakuna sun san inda za su je, kuma suka tafi kusa da Mowab.
Baka ne da aka yi shi kamar rabin da'i'ra.
Za a iya bayyana wa. AT: "ba su sami ruwa ko kaɗan ba"
Sarki yayi amfani da wannan tambayar don jaddada yadda mummnan yanayin su yake. Za a iya wannan a matsayin sanarwa. AT: "Shi ya duba kamar Yahweh zai ba da damar Mowab ya kama dukkan uku na mu"
A nan "Mowab" na nufin sojojin sa. Kuma "hannun Mowab" na nufin ikon sojojin Mowab. AT: "ya bashe mu a sarrafawan Mowab" ko "sojojin Mowab za su ci nasara akan mu"
Yehoshafat ya yi amfani da tambayar don nuna cewa ya tabbata cewa akwai annabi a can da kuma gano inda yake. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Tabbas akwai wani annabin Yahweh a nan! Ku faɗa mini inda ya dace, saboda haka za mu iya neman Yahweh ta wurinsa."
Wannan sunan mutum ne.
Wannan ma’anar yana nufin cewa shi mataimakan Iliya ne. Bayanin “zuba ruwa a hannu” kwatankwacin ɗaya daga cikin hanyoyin da ya bauta wa Iliya. AT: "wanda ya kasance mataimaki ga Iliya"
Wannan yana nufin cewa shi annabi ne kuma Yahweh yana faɗa masa abin da zai faɗa. AT: "Yana magana da abin da Yahweh ya ce masa ya faɗi"
Sun tafi su ga Elisha kuma sun yi shawara da shi game da abin da ya kamata su yi. Cikakken ma'anar wannan bayanin ana iya bayyana shi sarai. AT: "ya je ya ga Elisha don tambayarsa abin da ya kamata su yi"
Elisha ya yi amfani da wannan tambaya don ya nanata cewa shi da sarki ba su da komai iri ɗaya. Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin bayani. AT: "Ba ni da abin yi da ku." ko kuma "Ba ni da abin da ya yi dai-dai da ku." (Duba: rquestion)
A nan "hannun Mowab" yana nufin ikon Mowab. AT: "a ba da su ga hannun Mowab" ko "a bar su sojojin Mowab su kama su"
"Na sani Yahweh Mai Runduna yana raye, wanda nake tsaye a gabansa, tabbas ne." Anan Elisha ya gwada tabbacin cewa Yahweh yana raye da tabbacin cewa, in ba don Yehoshafat ba yana nan, ba zai kula da Yoram ba. Wannan wata hanya ce ta cika alkawari. AT: "Na rantse da Yahweh Mai Runduna, wanda nake tsaye a gabansa, ina yi muku alƙawarin idan ya kasance"
Anan ga Yahweh ana magana da shi kamar yana tsaye a gabansa. AT: "Wanda nake bauta wa"
Za a iya rubuta wannan azaman sanarwa tabbatacce. AT: "Ban kula da ku ba kawai saboda ina girmama gaban Yehoshafat, sarkin Yahuda"
Anan an ambaci Yehoshafat da gabansa. AT: "Na girmama Yehoshafat"
Waɗannan kalmomin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani da su tare don ƙarfafa cewa ba zai kula da Yoram ba. AT: "Ba zan kasance da wata ma'ana a kanku ba"
"Kuma ya faru cewa"
wani da yake kiɗa garaya
Anan “hannun” Yahweh yana nufin ikonsa. AT: "ikon Yahweh ya hau kan Elisha"
Kabarin dogo ne mai tsayi da ma’aikatan suka tono a cikin ƙasa don ɗaukar ruwa.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Zan cika kwarin kogin da ruwa"
Wannan na nufin shan ruwan da Yahweh yake bayarwa. AT: "zaku sha ruwan"
Gaban Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh ko tantancewa. AT: "Yahweh yana ɗaukar wannan a zaman abu mai sauki da ake yi" ko "Wannan abu ne mai sauƙi ga Yahweh yayi"
Birni mai garu yana da kariya sosai daga abokan gaba ta abubuwa kamar su katanga mai kyau ko wuri mai sauƙi wanda ba za'a iya kiyaye shi ba.
Wannan yana nufin sanya dutse a cikin ƙasa mai daɗi saboda haka yana da wahala a yi amfani da shi. Ana iya bayyana ma'anar wannan bayani a sarari. AT: "lalata kowane yanki mai kyau ta hanyar rufe su da duwatsun"
"ruwa ya fara guduna"
"ba da daɗewa ba ƙasar ta cika da ruwa"
ƙasa
Wannan kalmar ana amfani da ita anan don alamar hutu a cikin babban labarin. Anan marubucin ya faɗi bayanin asalin game da sojojin Mowab waɗanda ke shirin haɗuwa da sarakunan ukun da rundunarsu a yaƙi.
Anan "makamai" yana wakiltar iyawar yin yaƙi. AT: "duk mazan da zasu iya yaƙi"
Anan kalmar "sarakuna" tana nufin duka sarakuna da sojojinsu. AT: "sarakuna sun zo da rundunansu" ko "sarakuna da sojojinsu sun zo"
Wannan yana gwada kamannin jan ruwa zuwa launi da jini. AT: "ya yi ja kamar jini"
Sojojin suna kiran kansu a nan "Mowab." AT: "Sojojin Mowab"
"sace kayansu." Bayan dakaru sun ci nasara a kan abokan gabansu, za su washe garuruwansu ta hanyar washe duk abin da ya rage da muhimmanci.
Anan "Isra'ila" yana nufin sojojin Isra'ila ne kawai ba ga al'ummar Isra'ila gaba ɗaya ba. AT: "yankin da sojojin Isra'ila suka kafa alfarwansu"
Anan "Isra'ilawa" suna nufin sojoji ne kawai na Isra'ila kuma ba duka al'ummar Isra'ila ba. AT: "sojojin Isra'ila sun yi mamaki"
"suka guda da ga garesu"
Wannan shi ne babban birnin Mowab.
Ganuwar da gine-ginen birnin an yi su da dutse. Ana iya bayyana ma'anar wannan a sarari. AT: "har yanzu suna da bango na dutse da ginegine a wurin"
"Majajjawa" wani yanki ne na fata tare da igiya mai tsayi a kowane ƙarshen abin da mutum zai iya sanya dutse ko wani ƙaramin abu mai wuya ya jefa shi nesa mai nisa.
Fassara sunan wannan sarkin kamar yadda kayi a 2 Sarakuna 3:4.
"ya ga an ci sojojinsa"
"masu takkuba 700"
sojojin da suke yaƙi da takkubi
"tilasta musu hanya." Akwai sojoji da yawa da suke yaƙi a fagen fama wanda hakan ya sa ya zama da wuya a motsa duk da cewa taron.
Sarki Mesha ya ƙone ɗansa da wuta har ya mutu. Ya yi wannan don miƙa wa Kemosh, gunkin Mowab.
Anan ana iya bayyana kalmar "fushi" azaman fi'ili. Akwai hanyoyi biyu don wanda ya yi fushi a nan: 1) Sojojin Mowab. AT: "Don haka sojojin Mowab sun yi fushi da Isra'ila sosai" ko 2) Allah. AT: "Saboda haka Allah ya yi fushi da Isra'ila"
1Sai matar ɗaya daga cikin 'ya'yan annabawa ta zo tana kuka da Elisah, tana cewa, "Baranka mai gidana ya mutu, kuma ka sani baranka ya ji tsoron Yahweh. To wanda ke binsa bashi ya zo ya kwashe 'ya'yana maza guda biyu su zama bayinsa.'2'Sai Elesha ya ce da ita "Me ki ke so in yi maki? Ki faɗa mani abin da ki ke da shi a cikin gida? "Ta ce, baiwarka ba ta da komai a cikin gida, sai 'yar tukunya ɗaya ta mai."3Sai Elisha yace, "Ki je ki aro tuluna daga maƙwabtanki, tulunan da ba komai a ciki. Ki aro gwargwadon yadda za ki iya arowa.4Dole ne ki shiga ɗaki ki kulle ƙofa da ke da iyalanki sai ki zuzzuba mai a cikin dukkan tulunan; sai ki kawar da waɗanda suka cika."5Sai ta bar wurin Elesha ta kulle ƙofa ita da 'ya'yanta suka kawo mata tulunan, ta kuma cika su da mai.6Da tulunan suka cika, ta ce da ɗanta "Ka ƙaro mani wani tulun." Amma ya ce da ita, "Babu sauran tuluna." Sai man ya dena tsiyayowa.7Sai ta zo ta faɗawa damutumin Allah. Ya ce "Je ki sayar da man; ki biya bashinki, sauran sai ki gudanar da rayuwarki tare da 'ya'yanki da shi."8Wata rana Elisha ya je Shunem inda wata mata mai muhimmanci ke zama; Ta roƙe shi ya ci abinci tare da ita. Sau da dama Elisha yakan wuce ta wurin, ya kan bi ta wurin ya ci abinci.9Sai matar ta ce da mijinta, "Duba, yanzu na gane wannan mutum mai tsarki ne na Allah wanda yake wucewa kullun.10Sai mu yi masa ɗan ɗaki a saman rufi domin Elisha, sai mu sa gado a cikin ɗakin da teburi da kujeru da fitila. Domin in ya zo wurin mu, sai ya zauna a can."11To da ranar ta zo da Elisha ya tsaya a can, sai ya shiga can ya huta.12Elesha yace da Gehazi baransa, "Ka kira wannan Bashumaniye." Bayan ya kira ta, ta tsaya a gabansu.13Elisha yace da shi, "Ka ce da ita, kin sha duk wannan fama domin ki kula da mu. Me zamu yi maki? Ko ma yi magana da sarki ko kuma da Kwamandan soja?'" Ta amsa "Ina zama a cikin mutanena."1414 Domin haka Elisha yace,"To me za mu yi mata?" Gehazi ya amsa, "Hakika ba ta da ɗa Mai gidanta kuma ya tsufa."15Domin haka Elisha ya amsa, "Kira ta." Bayan ya kira ta, sai ta tsaya a ƙofa.16Elisha ya ce shekara mai zuwa war haka za ki riƙe ɗa." Ta ce, "A'a ya shugabana da kuma mutumin Allah, kada ka yi wa baiwarka ƙarya."17Amma matar ta yi ciki sai ta haifi ɗa a dai-dai lokacin da Elisha ya faɗa mata.18Bayan yaron ya yi girma, sai ya tafi wurin mahaifinsa wata rana, wanda ya ke tare da masu girbi. Sai ya ce da babansa, "Kaina, kaina."19Mahaifinsa ya ce da bayinsa, "Ku kai shi wurin mahaifiyarsa."20Lokacin da bayin suka ɗauki yaron suka kawo shi wurin mahaifiyarsa, yaron ya zauna a gwiwarta har tsakar rana daga nan sai ya mutu.21Sai matar ta tashi ta kwantar da yaron a gadon mutumin Allah, ta kulle ƙofa, ta fita.22Ta kira maigidanta, ta ce, "Ina roƙo ka aiko mani da ɗaya daga cikin bayi da kuma ɗaya daga cikin jakunan domin in yi sauri zuwa wurin mutumin Allah sa'an nan in dawo."23Maigidanta ya ce donme ki ke so ki je wurinsa yau? Ba sabon wata ba ne ko kuma Asabar ba. "Sai ta amsa, "Komai zai yi dai-dai.24" Sai ta ɗaura wa jaki sirdi ta ce da bayinta, "Ku kora shi da sauri; kada ku sausauta har sai na ce ku yi haka."25To sai ta tafi ta je wurin mutumin Allah a Tsaunin Karmel. Lokacin da mutumin Allah ya hange ta daga nesa, sai ya ce da Gehazi baransa, "Duba ga matar nan Bashunamiya tana tafe.26Ka ruga a guje ka tambaye ta, ko komai lafiya yake game da ita da maigidanta da kuma ɗanta?"' Ta amsa, "Ba damuwa."27Lokacin da ta zo wurin mutumin Allah akan dutsen sai ta kama ƙafafunsa, sai Gehazi ya zo zai ture ta amma mutumin Allah ya ce "Ka ƙyale ta, domin hankalinta a tashe yake Yahweh kuma ya ɓoye mani al'amarin, bai kuma faɗa mani komai ba."28Daga nan sai ta ce, "Na roƙe ka ɗa ne, ya shugaba na, Ashe ban ce kada ka yaudare ni ba?"29Sai Elisha ya ce da Gehazi, "Maza shirya ka riƙe sandana a hanunka. Ka je gidanta. "In ka gamu da wani in ya gaishe ka kada ka amsa, kada ka amsa masa. Ka ɗora sandana a fuskar yaron."30Amma mahaifiyar yaron ta ce, "Muddin Yahweh na raye, kana kuma raye, ba zan bar ka ba."Saboda haka Elisha ya tashi ya bi ta.31Gehazi ya ruga kafin su kai ya ɗora sandan a fuskar yaron, amma yaron bai iya ji ko kuma ya yi magana ba. Saboda haka Gehazi ya dawo ya gamu da su, ya ce da Elisha "Yaron bai farfaɗo ba."32Lokacin da Elisha ya shiga gidan yaron a mace yake, yana kuma kwance akan gado.33Sai Elisha ya shiga ya kulle ƙofa da yaron ya yi addu'a ga Yahweh.34Sai ya hau ya kwanta akan yaron; ya sa bakinsa a bakinsa, idonnsa a idonsa, hannunsa a hannunsa. Sai ya miƙe akan yaron sai jikinsa ya yi ɗumi.35Sai Elisha ya tashi ya zagaya ɗakin ya sake kwantawa akan yaron ya miƙe, sai yaron ya yi atishawa sau bakwai, sai ya buɗe idonsa!36Sai Elisha ya kira Gehazi ya ce da shi "Ka kira Bashunamiye!" Sai ya kira ta, da ya kira ta, da ta shiga ɗakin sai Elisha ya ce da ita "Ɗauki ɗanki."37Sai ta kwanta a ƙafafunsa fuskarta a ƙasa, daga nan sai ta ɗauki ɗanta ta fita.38Sai Elisha ya sake zuwa Gilgal. Akwai yunwa kuma a ƙasar, 'ya'yan annabawa kuma na zaune a gabansa. Ya ce da baransa. "Ka ɗora babbar tukunya ka dafa miya domin 'ya'yan annabawa."39Ɗaya daga cikinsu ya tafi saura domin ya samo ganyayen abinci sai ya samon ganyen inabi mai guba ya tara shi da yawa ya cika haɓar rigarsa, Suka yayyanka suka zuba a cikin abincin, amma ba su san irin su ba.40Sai suka zuba masu abinci su ci, can suna cikin cin abincin sai suka yi kuka suka ce "Da guba a cikin tukunyar!" Domin haka basu ƙara cin abincin ba.41Amma Elisha ya ce "Ku kawo mani gãri." Sai ya zuba a tukunyar ya ce, ku zuba wa mutane su ci, daga nan ba a sami wata guba a cikin tukunyar ba.42Sai wani mutum ya zo daga Ba'al Shalisha wurin mutumin Allah ya kawo masa curin gurasar sha'ir guda ashirin a cikin jakarsa daga cikin girbinsa, da kuma sababbin zargankun hatsi. Ya ce, "Ka ba mutane wannan domin su ci."43Bayinsa suka ce "Ƙaƙa zamu ba da wannan ga mutane ɗari?" Amma Elisha yace "Ku ba su wannan domin su ci, domin Yahweh ya ce, 'Za su ci su kuma bar saura.'"44Sai bayinsa suka ajiye shi a gabansu; suka ci suka bar saura, kamar yadda maganar Yahweh ta alkawarta.
Wannan baya nuna cewa su 'ya'yan annabawa ne, amma cewa su wani rukuni ne na annabawa. Duba yadda zaka fassara wannan kalmar a 2 Sarakuna 2: 3. AT: "annabawa"
"Mijina, wanda ya kasance bawanka"
mutumin da ya ba wasu mutane kuɗi
Matar ta ambaci kanta a matsayin bawan Elisha don nuna masa girmamawa.
Wannan ƙari ne. Abinda kawai yake da muhimmanci shi ne ta kasance kwalbar mai.
Wannan yana nufin shiga cikin gidansu. Ana iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayanin a bayyane. AT: "dole ku shiga cikin gidan ku"
"garewani" ko "kwalbar"
Wannan na nufin Elisha. AT: "Elisha, mutumin Allah"
Wannan karin magana ne. Yana nufin yin amfani da kuɗin don siyan abubuwan da suke buƙata, kamar abinci da sutura. Watau fassarar: "Ku yi amfani da ragowar kuɗin don ku da 'ya'yanku don abin da kuke buƙatar rayuwa"
Wannan sunan birni ne.
Wannan na nufin ta roƙe shi ya bi ta gidan ta ya ci abinci. AT: "ta tambayeshi ya bi ta gidanta ya ci abinci"
"tafiya ya bi ta Shumen"
"Yanzu na gane"
"wanda yake yin tafiya akai-akai"
Mata mai muhimmanci ta ci gaba da magana da mai gidanta game da Elisha.
A nan "mu" na nufin mata mai muhimmanci da mai gidanta.
Wannan sunan namiji ne.
"Kira wannan Bashumaniya." Wannan na nufin matar Shumem da Elisha ya ke zama da ita.
Kalmomin "tafi ga wannan matsala" kalma ce da ke nufin yin ƙoƙari sosai don yin wani abu. AT: "Kun yi ƙoƙari sosai don kula da mu" ko "Kun yi aiki tuƙuru don kula da mu"
An a iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Me za mu iya yi maku"
Anan Elisha yana tambayarta ko tana son shi ya yi magana da sarki ko kuma shugaban sojoji don neman wata buƙata ta. Za a iya bayyana ma'anar wannan tambayar a bayyane. AT: "Shin za mu iya neman ku"
Matar tana nufin cewa bata da buƙata tana da abubuwan da take buƙata saboda iyalinta suna lura da ita, AT: "iyali na ne zaye dani domin suna lura da ni, bani da buƙatar komai."
"Gaya mata ta zo ta gani"
"bayan Gehazi ya kira ta"
Wannan na nufin murfin ƙofa. AT: "murfin ƙofa"
"yaron ki"
Matar ta yi amfani da waɗannan sunaye ta na nufin Elisha.
Matar na nufin ita baiwar Elisha ce domin girmamawa.
"a daidai lokacin daya ne a shekara mai zuwa"
"bayan yaron ya fara girma" ko "lokacin da yaron ya girma"
Yaron ya faɗi haka ne saboda kansa ya ji rauni. Ana iya bayyana ma'anar wannan a sarari. AT: "Kaina na ciwo! Kaina na ciwo!"
Anan ga gwiwar macen tana nufin cinyarta. Ta riƙe ɗanta a cinyarta har ya mutu. AT: "ta riƙe ta a cinyarta har tsakar rana sannan ya mutu"
Wannan shi ne gado a ɗakin da ta shirya wa Elisha lokacin da yake tafiya cikin Shunem. (Duba: explicit)
Matar ta ce wa mijinta za ta je wurin Elisha amma ba ta ce za ta tafi ba domin ɗansu ya mutu. Wannan bayyananniyar bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "in yi sauri wurin mutumin Allah sannan in dawo. Amma ba ta gaya wa mijinta cewa ɗansu ya mutu ba"
Matar ta faɗi haka, sanin hakan zai kasance idan mijinta ya aikata yadda ta buƙata. Ana iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayanin a bayyane. AT: "Komai zai zama dai-dai idan kun yi yadda na roƙa"
Matar ba ita tasa sirdin a jakin ba, bayinta suka sa mata. AT: "ta sa bayinta suka sa mata sirdi a jaki"
"Ta yi tafiya zuwa Tsaunin Karmel inda Elisha, mutumin Allah yake"
"Tun tana can nesa, sai Elisha ya gan ta zuwa"
"Lafiya dai" ko "Ee, komai ya yi kyau"
"Tsaunin Karmel"
Wannan ya nuna cewa ta durƙusa ko a kwance a ƙasa a gaban shi kuma ta kama ƙafafunsa. AT: "Ta faɗi a ƙasa a gabanta kuma ta sanya hannayenta a ƙafafunta"
Elisha ya iya ganin matar ta yi fushi amma Yahweh bai bayyana masa dalilin matsalar nata ba.
Matar tana amfani da waɗannan tambayoyin ne domin nuna cewa tana cikin fushi game da abin da ya faru. Tana magana ne game da tattaunawar da ta yi da Elisha lokacin da ya gaya mata cewa za ta haifi ɗa. Waɗannan tambayoyin ana iya rubuta su azaman sanarwa. AT: "Ban nemi ku ba ni ɗa ba, amma na neme ku kada ku yi mini ƙarya!"
"Ku shirya don tafiya"
Elisha yana son Gehazi ya yi tafiya da sauri, ba tare da ya tsai da magana da kowa ba.
"Muddin Yahweh na raye, kana kuma raye" Wannan ya nuna cewa mahaifiyar tana rantsuwa. Uwar ta gwada tabbacin cewa Yahweh da Elisha suna da rai da tabbacin abin da take faɗi. Wannan wata hanya ce ta cika alkawari. AT: "Na yi alkawarin cewa"
Wannan yana nuna cewa yaron bai da rai. Ana iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayanin a bayyane.AT: "amma yaron bai nuna wata alama ta rayuwa ba"
Anan an mutu ana maganar barci. AT: "har yanzu ya mutu"
"Sai Elisha ya je da kansa cikin ɗakin da aka sa yoron, ya rufe ƙofa"
"kwantawa akan yaron kuma"
"matar Bashunamiya"
Matar ta kwanta a ƙasa a gaban Elisha don nuna ban girma da kuma nuna godiya. AT: "Sai ta kwanta a ƙasa a gaban Elisha ta nuna godiyarta"
Wannan abincine da ake dafawa da nama da ganyaye da ruwa a tukunya.
Waɗannan kayan lambu suna girma daji, ma'ana wani bai shuka su ba.
Ya ɗaga ƙarshen rigarsa zuwa kugu, don neman wurin ɗaukar kaya mafi yawa fiye da yadda yake iya ɗauke da hannuwansa kawai.
Tunda basu san wane irin gurnani suke ba basu san ko lafiyarsu ci ba. Cikakken ma'anar wannan bayanin ana iya bayyana shi sarai. AT: "amma ban san ko suna da kyau ko ba su ci ba"
"suka zuba miyar a kwanoni"
Wannan yana nuna cewa akwai wani abu a cikin tukunyar da zai iya kashe su, ba wai cewa akwai wani abu da ya mutu a cikin tukunyar. AT: "akwai wani abu a cikin tukunyar da zai kashe mu"
"ya ƙara shi a miyar a cikin tukunya"
"ba su abincin"
Wannan sunan birni ne.
"curi 20"
"da aka yi da hatsi na sabon girbi"
"sabon kan hatsi." Wannan na nufin hatsi sabon girbi.
Mutumin yayi amfani da wannan tambayar don nuna cewa wannan bai isa gurasar da za a ciyar da mutum dari ba. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Wannan bai isa ya ciyar da mutum ɗari ba!"
"mazaje 100"
Anan ana kiran Yahweh da abin da ya faɗa. Wannan kalmar tana nuni ne ga Yahweh da kansa. AT: "Yahweh"
1Na'aman kwamadan sojan sarkin Aram, yana da girma da ƙima a gun shugabansa, saboda shi Yahweh yakan ba Aram nasara. Hakannan shi mutum ne mai ƙarfi da kuma ƙarfin halin, amma shi kuturu ne.2Aremiyawa suka kai hari runduna runduna suka ɗauki wata yarinya daga ƙasar Isra'ila, ta yiwa matar Na'aman hidima.3Sai yarinyar ta ce shugabarta, "Na so a ce shugabana tare yake da annabin da ke a Samariya! To zai warkar da shugabana daga kututtarsa."4Sai Na'aman ya je ya faɗa wa sarki abin da yarinyar da ta zo daga ƙasar Isra'ila ta faɗa.5Saboda haka sarkin Aram ya ce, "Yanzu ka tafi, zan kuma aika da wasiƙa zuwa ga sarkin Isra'ila." Sai Na'amam ya tafi ya ɗauki talanti goma na azurfa, da tsabar zinariya dubu shida, da kuma sauyin sutura guda goma.6Hakannan ya kai wa sarkin Isra'ila wasiƙar da ta ce, Lokacin da wannan wasiƙa ta zo wurinka, za ka ga cewa na aiko da barana Na'aman zuwa wurinka domin ka warkar da shi daga kuturtarsa."7Bayan sarkin Isra'ila ya karɓi wasiƙar ya karanta ta sai ya keta tufafinsa ya ce, "Ni Allah ne da zan iya rayarwa ko in kashe, da wannan mutum zai so in warkar da mutum daga kuturtarsa? Da alama yana neman jayayya da ni."8To bayan Elisha mutumin Allah ya ji cewa sarkin Isra'ila ya keta tufafinsa, sai ya ce "Me yasa ka keta tufafinka? Ka bar shi ya zo wurina yanzu zai kuma sani akwai annabi a Isra'iula."9Sai Na'aman ya je da karusarsa ya tsaya a ƙofar gidan Elisha.10Elisha ya aika masa da 'yan saƙo gare shi cewa. "Ka je ka yi nutso sau bakwai a kogin Yodan, jikinka zai dawo, zaka kuma tsaftata.11Amma Na'aman ya fusata ya tafi ya ce, "Duba na yi zaton tabbas zai zo wurina ya tsaya ya kira sunanYahweh Allahnsa, ya kuma ɗaga hannunsa a wurin ya warkar da kuturtar tawa,12Ashe kogunan Abana da na Farfar wato kogunan Damaskus, basu fi duk waɗannan ruwayen na Isra'ila tsafta ba?" Sai ya juya cikin matuƙar hasala.13Sai bayin Na'aman suka zo kusa suka yi magana da shi, "Babana, in da annabin ya ce ka yi wani abu mai wuya ashe ba za ka yi ba? Amma me ya fi wannan da ya ce maka, "Ka yi nutso ka tsarkaka?'"14Daga nan sai ya gangara ya je ya yi nutson sau bakwai a kogin Yodan ya yi biyayya ga ummarnin mutumin Allah. Sai jikinsa ya dawo kamar na jariri sabuwar haihuwa, ya kuma warke.15Sai Na'aman ya koma wurin mutumin Allah shi da rundunarsa, ya ce "Duba yanzu na sani babu wani Allah a duk duniya sai a Isra'ila. To yanzu sai ka karɓi kyautai daga wurin baranka",16Amma Elisha ya ce "Muddin Yahweh wanda nake tsaye a gabansa na raye ba zan karɓi komai ba," Na'aman ya matsa wa Elisha ya karɓa amma Elisha ya ƙi karɓa.17To sai Na'aman yace, "In ba za ka karɓa ba sai a ba baranka kayan takarkari na kayan alatu, domin daga yanzu baranka ba zai miƙa hadaya ta ƙonawa ga wani allah ba sai ga Yahweh.18Ka gafarci baranka, wato a lokacin da sarkina ya je gidan Rimmon domin ya yi sujada a can, ya kuma lashe hannuna na kuma sunkuya a gidan Rimmon, ina roƙon Yahweh ya gafarci baranka akan wannan."19Elisha yace da shi, "Ka tafi da salama." Sai Na'aman ya tafi.20Ya ɗan yi nisa kenan, lokacin da Gehazi baran Elisha mutumin Allah ya ce a ransa, Duba, shugabana ya kyale Na'aman ɗin nan mutumin Aremiya bai karɓi kyautai da ya ya kawo daga hannunsa ba. Muddin Yahweh na raye zan bi shi in karɓi wani abu daga wurinsa."21Sai Gehazi ya bi Na'aman. Da Na'aman ya ga wani na biye da shi, sai ya dirgo daga karusa domin ya tare shi ya ce, "In ce ko lafiya?"22Gehazi yace, "Lafiya ƙalau. Ubangidana ne ya aiko ni, cewa, 'Duba, yanzunan ya yi baƙi daga ƙasa mai duwatsu ta Ifiraim samari biyu na 'ya'yan annabawa. Ina roƙo ka ba su jaka biyu na zinariya, da kayan alfarma guda biyu."23Na'aman ya amsa, "Ina murna sosai in ba ka talanti biyu." Na'aman ya bukaci Gehazi kuma ya ɗaure talanti biyu na azurfa a cikin jaka biyu, da riguna biyu, sai ya ɗora su akan bayinsa biyu, waɗanda ke ɗauke da jaka na azurfa a gaban Gehazi.24Bayan Gehazi ya zo wurin duwatsu, sai ya karɓe jaka na azurfa daga hannunsu ya ɓoye su a cikin gida; ya sallami mutanen, suka tafi.25Bayan Gehazi ya shiga ciki ya tsaya a gaban shugabansa, Elisha yace da shi, "Daga ina ka dawo, Gehazi?" Ya amsa, "Baranka bai je ko'ina ba."26Elisha yace da Gehazi, "Ashe ruhuna baya tare da kai ne a lokacin da mutumin ya juyo da karusarsa domin ya gamu da kai? Ko wannan ne lokacin karɓar kuɗi da sutura da man zaitun da garkar inabi, da tumaki da bijimai, da bayi maza da mata?27To kuturtar Na'aman za ta koma kanka da kuma zuriyarka har abada." Sai Gehazi ya fita daga gabansa a kuturce fari fat kamar auduga.
"gani." "Ra'ayin" sarki yana wakiltar abin da yake tunani game da wani abu. AT: "a cikin ra'ayin sarki"
A nan "Aram" na nufin sojojin Aremiya. AT: "sabo da Na'aman, Yahweh ya yi ta ba sojojin Aremiya nasara"
A nan "Aremiyawa" na nufin sojojin Aremiya.
"a ƙananan ƙungiya suna kai hari." Wannan na nufin a kai hari a ƙungiya kanana.
Yarinyar daga Isra'ila, wadda sojojin Aremiya suka ɗauko, ta yi magana da matar Na'aman.
A nan "shugabana" na nufin Na'aman.
Sarki zai ba Na'aman wasiƙa don ya tafi tare da shi zuwa ga sarkin Isra'ila. AT: "Zan aika da wasiƙa tare da kai"
Za a iya rubuta shi da kayyayakin gwaji na zamani. AT: "330 kilogiram na azurfa, 6,000 tsabar zinariya"
Waɗannan kyaututtuka ne daga sarkin Aram zuwa sarkin Isra'ila. AT: "ya ɗauki goma ... kayayyaki, wannan kyauta ne ga sarkin Isra'ila"
Sau da yawa mutane za su kwashe tufafinsu idan suna cikin tsananin damuwa. AT: "ya yayyage tufafinsa don nuna bacin ransa"
Sarki ya yi amfani da wannan tambaya don ƙarfafa cewa roƙon Sarkin Aram abin ƙyama ne kuma abin da ba zai iya yi ba. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "sarkin Aram dole ne ya yi tunanin ni wani bawan Allah ne, mai iko akan mutuwa da rayuwa! Yana so in warke wannan mutumin na kuturta, amma ba zan iya yin hakan ba."
Sarkin Isra'ila bai yarda da buƙatar neman warke Naamam ba ne ainihin dalilin wasiƙar. Ya yi tunanin ainihin dalilin shi ne a fara faɗa. AT: "Da alama yana neman uzurin ne don fara faɗa da ni"
Elisha ya yi magana sarkin Isra'ila game da Na'aman
Elisha ya yi amfani da wannan tambayar don nuna wa sarki cewa ba ya buƙatar damuwa da tsaga tufafinsa. AT: "Babu buƙatar baƙin ciki da tsage kayanku."
Ana iya rubuta wannan cikin tsari mai aiki. Watau fassarar: "Namanku zai yi kyau" ko "jikika zai sami lafiya"
Wannan yana nufin cewa ba zai sake zama ƙazanta ba. Ana maganar mutumin da Allah ya ɗauke shi a ruhaniya ko ƙazanta ta ruhaniya kamar dai mutumin ba shi da tsabta a zahiri. Allah ya ɗauka mutumin da ke da kuturta kamar ƙazanta da ƙazanta.
Ana amfani da wannan kalmar a nan don jan hankalin wani zuwa abin da ake faɗi na gaba. AT: "Saurara"
A nan Yahweh na nufin ta wurin sunansa. AT: "Yahweh''
"a kan wurin cutar" ko "akan kuturtata"
Na'aman ya yi amfani da wannan tambayar don nuna cewa Abana da Farfar sun fi Kogin Yodan kyau. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Abanah da Farfar Rafuka, a ƙasata ta Aram, sun fi kowane ɗayan rafin Isra'ila!
Waɗannan su ne sunayen rafuka ne.
Na'aman yayi amfani da wannan tambayar don ya jaddada da cewa zai iya wanka a cikin kogin cikin sauƙi. Ya yi imanin cewa wanka a cikinsu zai iya warkar da shi kamar yadda wanka a Kogin Yodan zai iya yi. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Ya kamata in yi wanka a cikin su in warke!" ko "Zan iya a sauƙaƙe na yi wanka a cikin su kuma in warke!"
"ya yi fushi sosai lokacin da ya koma"
Barorin sun nuna girmamawa ga Na'aman ta wurin kiransa "uba na".
Bawan ya yi amfani da wannan tambayar don tsauta wa Na'aman a hankali. AT: "babu shakka da kun aikata shi!"
Bawan yana gwada yadda yafi da cewa Na'aman ya zama mai biyayya ga wata doka mai sau tunda yana son yin biyayya da abu mai wuya. AT: "Yaya za ku fi so ku yi biyayya" ko "Shin bai kamata ku fi yarda da yin biyayya ba"
Bawan ya yi amfani da wannan tambayar don tabbatar wa Na'aman cewa ya kamata ya bi umarnin Elisha. Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin bayani. AT: "sai ka zama a shirye ka kiyaye da ya ce da kai, ka nutso ka tsarkaka."
"Elisha, mutumin Allah"
Wannan ya kwatanta sumul-sumul din jikin Na'aman bayan an warkar da shi aka kwatantata shi dana ƙaramin yaro. AT: "Jikinsa ya dawo kuma ya yi taushi kamar fatar ƙaramin yaron" ko "Fatarsa ta warke kuma ta yi laushi kamar ta ƙaramin yaro"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "kuturta ta tafi"
"Allah na Isra'ila ne kaɗai Allah mai gaskiya!"
"Na dai san yadda Yahweh yake raye, wanda nake tsaye a gabansa." Anan Elisha ya gwada tabbacin cewa Yahweh na da rai da tabbacin cewa ba zai sami kowace kyauta daga Na'aman ba. Wannan wata hanya ce ta cika alkawari. AT: "Na rantse da Yahweh, a gaban wanda na tsaya a wurin, ina yi muku alƙawarin zan kasance"
A nan bautawa Yahweh ana maganarsa a matsayin tsayawa a gabansa. AT: "wanda na bautawa"
Wannan na nufin ba zai ƙarɓi kyautar ba. AT: "ba zan ƙarɓi wata kyauta ba"
Ana iya samar da bayanin da aka fahimta. AT: "Idan ba ku karɓi kyaututtukan da na kawo muku ba"
Wannan za a iya bayyana a cikin aiki daga. AT: "bari in sami"
Na'aman yana roƙon ya ɗauki ƙasa daga Isra'ila ya sa a cikin jaka don alfadarai biyu don ɗaukar gidansa tare da shi. Daga nan ya shirya gina bagade a ƙasa. AT: "kamar ƙasa da Isra'ila take da alfadarai biyu za su iya ɗauka, don haka zan iya gina bagade ga Yahweh"
Na'aman ya kira kansa bawan Elisha ya girmama shi.
Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa tabbatacce. AT: "ba zai miƙa hadaya ta ƙonawa ko hadaya ga wani allah ba sai Yahweh" ko "ba kawai zai miƙa hadayun ƙonawa da na sadaka ga Yahweh ba"
Wannan na nufin sarkin Aram, sarkin da Na'aman yake yi wa aiki.
"yana goyon bayan kansa a madina." Wannan yana nufin cewa Na'aman ya taimaki sarki lokacin da ya durƙusa a gidan Rimmon domin sarki ya tsufa ko ba shi da lafiya.
"ka tafi gida kuma kada ka damu" ko "ka tafi ba tsoro"
"Na'man ya tafi"
Wannan kalmar anyi amfani da ita a ja hankalin wani ga abinda za a ce a gaba. AT: "Saurara"
"ya bar Na'aman mutumin Aremiya haka kawai"
"saboda bai karɓa ba"
Anan ana nufin Na'aman da hannunsa don ƙarfafa aikin bayarwa. AT: "daga gare shi"
Anan Gehazi ya gwada tabbacin cewa Yahweh yana da rai da tabbacin abin da ya yanke shawarar yi. Wannan wata hanya ce ta cika alkawari. AT: "Na rantse da Yahweh, Na yi alkawari"
Gehazi yana roƙon Na'aman ya ba shi waɗannan abubuwan domin ya ɗauke su ya ba wa annabawan. AT: "Ina roƙo ka ka ba ni gwanin zango da wasu tufafi biyu na ba su"
Za a iya rubuta wannan da ma'auni na zamani. AT: "kilogiram 34 na zinariya"
Za a iya rubuta wannan a ma'auni na zamani. Wannan awon na zinariya ne. AT: "awo biyu na zinariya" ko "kilogiram 68 na zinariya"
"ba su"
Na'aman ya buƙaci shi ya ɗauki kyautan. AT: "Na'aman ya buƙaci Gehazi ya ɗauki kyautan"
Gehazi ya kira kansa bawan Elisha.
Elisha ya yi amfani da wannan tambayar don jaddada da cewa Yahweh ya ba shi damar ganin abin da Gehazi ya yi. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Ya kamata ku fahimci cewa ruhuna zai iya ganinku lokacin da Na'aman ya dakatar da karusarsa ya yi magana da ku."
Elisha yayi amfani da wannan tambayar don nuna cewa wannan ba lokacin ba da kyaututtuka bane. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Wannan ba lokacin karɓar kuɗi ba ne ... barori mata."
Wannan ya yi maganar Gehazi da zuriyarsa yana samun kuturta kamar an cire kuturta daga Na'aman kuma aka ba Gehazi. AT: "Kai da zuriyarka za su sami kuturta, kamar yadda Na'aman ya kamu da kuturta"
Wannan maganar "gabansa" na nufin inda Elisha zai iya ganinsa. Wannan na nufin ya fita daga ɗakin da inda Elisha yake. AT: "lokacin da Gehazi ya fita, da ga "
Kuturta na sa jiki fari. A nan Gehazi farin kuturta Gehazi an kwatantashi da farin auduga. AT: "da fata da tayi fari kamar auduga"
1'Ya'yan annabawa suka ce da Elisha, "Wurin da muke zama tare da kai ya gaza mana dukkanmu.2Muna roƙo ka bar mu mu je Yodan, sai kowannen mu ya saro itace a can, sai mu gina wurin da zamu zauna." Elisha ya amsa, "To ku je"3Ɗaya daga cikinsu ya ce, "Ina roƙo ka tafi tare da barorinka." Elisha ya amsa "za ni."4To sai ya tafi tare da su, a lokacin da suka fara saran itatuwan.5Amma a lokacin da ɗayansu ke sara sai kan gatarin ya faɗa a cikin ruwa; sai ya yi waiyo ya ce "Ya shugabana, aro shi aka yi!"6Sai mutumin Allah yace, "A ina ya faɗa?" Mutumin ya nuna wa Elisha wurin. Sai ya saro 'yar tsafga, ya jefa ta cikin ruwa, sai ta sa ƙarfen ya ɗago sama.7Elisha yace, "Ka ɗauko shi." Sai mutumin ya ɗauko shi.8Sai sarkin Aram ya shirya kai hari kan Isra'ila. ya tuntuɓi barorinsa, cewa, "Sansanina ga yadda zai kasance da kuma inda zai kasance."9Sai mutumin Allah ya aika wurin sarkin Isra'ila, cewa, "Ka yi hankali kada ka wuce ta wurin nan, domin Aremiyawa suna gangarawa can."10Sai sarkin Isra'ila ya aika da saƙo can game da abin da mutumin Allah ya faɗa masa ya kuma gargaɗe shi. Ba sau ɗaya ko sau biyu ba duk lokacin da sarki zai wuce wurin yana cikin tsaro.11Sarkin Aram ya da mugame da wannan gargaɗi, sai ya kira bayinsa ya ce da su, "Ba za ku faɗa mani wane ne daga cikinmu ya ke goyon bayan sarkin Isra'ila ba"12Sai ɗaya daga cikin bayin ya ce, "Ba haka ba ne shugabana, sarki, domin Elisha annabi na Isra'ila ne ya faɗawa sarkin Isra'ila maganar da ka faɗa a ɗakin kwananka!"13Sarki ya amsa, "ku je ku duba inda Elisha yake domin in aika da mutane su kamo shi." An faɗa masa, "Duba yana a Dotan."14Domin haka sarki ya aika mahaya dawakai da karusai da sojoji masu yawa zuwa Dotan. Suka zo da dare suka kewaye birnin.15Da baran mutumin Allah ya tashi da asuba ya fita waje, sai ga rundunonin sojoji da karusai da mahaya dawakai sun kewaye birnin. Baransa ya ce da shi, "Ya shugabana! Me za mu yi?"16Elisha ya amsa, "Kada ka ji tsoro, domin waɗanda ke tare da mu sun fi waɗanda ke tare da su."17Elisha ya addu'a ya ce, "Yahweh, ina roƙonka ka buɗe idanunsa domin ya gani." Sai Yahweh ya buɗe idanun baran, Sai ya ga tsaunin na cike da dawakai da karusai na wuta kewaye da Elisha!18Lokacin da Aremiyawa suka zo gare shi, Elisha ya yi addu'a ga Yahweh ya ce, "Ka bugi mutanen nan da makanta, ina roƙonka." Sai Yahweh ya makantar da su, kamar yadda Elisha ya roƙa.19Sai Elisha ya ce da Aremiyawa, "Ba wannan ba ce hanyar, ba kuma wannan ba ne birnin. Ku biyo ni zan kai ku wurin mutumin da ku ke nema." Sai ya kai su Samariya.20Bayan sun zo Samariya, Elisha yace, "Yahweh, ka buɗe idanun mutanen nan domin su gani." Yahweh ya buɗe idanunsu, sai suka gan su a tsakiyar birnin Samariya.21Da sarkin Isra'ila ya gan su ya ce da Elisha "'Babana, in kashe su ne? In kashe sun ne?"22Elisha ya amsa, "Kada ka kashe su. Ko ka kashe bayin da ka kama da bãkanka da kuma takobinka? Ka ba su gurasa da ruwa domin su ci su sha, sai su tafi wurin shugabansu."23Sai sarki ya shirya abinci sosai domin su, bayan su ci sun sha, sai ya sallame su, suka je wurin shugabansu. Waɗannan ƙungiyoyin sojojin Aremiyawan ba su daɗe ba sosai a Isra'ila.24Bayan wannan Ben Hadad sarkin Aram ya tara dukkan sojojinsa ya kaiwa Samariya hari ya kwashe ta.25Domin haka aka yi babbar yunwa a Samariya. Duba sun washe ta har ana sayar da kan jaki tsaba tamanin na shekel, ana kuma sayar da kofin kashin kurciya a shekel biyar.26Da sarkin Isra'ila ya zo wucewa ta gefen katanga sai wata mata ta yi masa kuka, cewa, "Ka yi temako shugabana, sarki."27Ya ce, "Idan Yahweh bai taimake ki ba, ta yaya zan taimake ki? Ana samun wani abu ne daga masussuka ko kuma daga wurin matsar ruwan inabi?"28Sarki ya ci gaba, "Me ke damun ki?" Ta amsa, "Wanan matar ta ce da ni, 'Ki ba ni ɗanki domin mu dafa mu ci yau, gobe kuma sai mu ci ɗana."'29Domin haka muka dafa ɗana mu ka cinye shi, da gari ya waye na ce da ita, "Ki bada ɗanki domin mu cinye shi, amma ta ɓoye ɗanta."30To bayan sarki ya ji maganar wannan mata, sai ya keta tufafinsa (yana wucewa gefen katanga) sai mutane suka gan shi saye da tufafin makoki a jikinsa.31Sai ya ce "Dama Allah ya yi mini haka, in har kan Elisha ɗan Shafat ya tsaya a kansa yau."32Amma Elisha na zaune a gidansa, dattawa kuma na zaune tare da shi. Sai sarki ya aika manzo ya zo wurinsa, amma da manzon ya zo wurin Elisha, sai ya ce da dattawan, "Dubi yadda wannan ɗan mai kisan kai ya aika a sare mani kai? Duba lokacin da manzon ya zo, kulle ƙofa kulle ƙofar a hana masa shiga. Ashe ba ƙarar sawun mai gidansa na biye da shi ba?"33Yana cikin yi masu magana sai ɗan saƙo ya zo wurinsa. "Sarki ya ce, "Duba wannan matsala daga wurin Yahweh ta zo. Donme kuma zan ƙara jiran Yahweh?"
Wannan ba wai yana nufin 'ya'yan su na cikinsu ba. amma, suma ƙungiya ce ta annabawa. Duba yadda aka fassara a 2 Sarakuna 2:3. AT: "ƙungiyar mazaje annabawa"
Wannan yana nufin yankin da ke gabar Kogin Yodan. AT: "bari mu tafi gefen Kogin Yodan"
A nan wani daga cikin 'ya'yan annabawa na nufin kansa da bawan Elisha domin girmamawa.
Elisha ya tafi da annabawan saran itatuwa.
Kan gatari na nufin ƙarfen mai kaifi. Wannan na nufin ya fita daga ƙotar ya faɗa cikin ruwa. AT: "kan gatarin ya ifta daga hannun ya faɗa cikin ruwa."
Mutumin ya fadi hakan ne don nuna cewa ya fusata da takaici. Idan kuna da wata hanyar da za ku iya bayyana waɗannan motsin zuciyarku a yarenku, zaku iya amfani da shi anan.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Na aro shi"
"Sai Elisha, mutumin Allah, ya tambaya"
Allah ya yi amfani da Elisha don yin al'ajabi. Kan gatarin ya taso saman ruwan ya na lilo yadda 'ya'yan annabawan za su iya sa hannun su su ɗauka.
"ya sa ƙarfen na lilo saman ruwa"
"kan gatarin." Kan gatarin anyi shi ne da ƙarfe.
"A lokacin da sarkin Aram yake yaƙi da Isra'ila"
Wannan kalmar ana amfani da ita anan don alamar hutu a cikin babban labarin. Anan marubucin ya fara ba da sabon ɓangaren labarin.
Sarkin Aram kuwa yana gaya wa masu ba shi shawara inda za su kafa sansanin. A nan kalmar "irin wannan kuma irin wannan" wata hanya ce da za a koma zuwa bayanin wurin da sansanin sansanin ba tare da an rubuta ta ba. Idan wannan aikin bai fassara da kyau zuwa yarenku ba wannan ana iya rubuta shi azaman magana kai tsaye. AT: "ya gaya musu inda zango sansanin zai kasance"
"Elisha mutumin Allah"
Elisha ya san takamaiman wurin da Aramiyawa za su kafa sansaninsu kuma ya shawarci sarkin Isra'ila don sojojinsa su guji yankin.
Wannan na nufin wurin da Elisha ya gaya wa sarki a 2 Sarakuna 6:8.
Elisha zai yi gargaɗi ga sarki a ina sojojin Aramiya za su kawo hari domin ya faɗakar da mutane kafin a kai harin. AT: "Elisha ya gargaɗi sarkin Isra'ila ta wannan hanyar sau da yawa kuma jama'ar Isra'ila sun sami damar zauna lafiya"
Sarkin Aram ya ɗauka akwai wani mahaukaci a cikin sojojinsa da yake ba da labarin sarkin Isra'ila. Yayi amfani da wannan tambayar don ya gano ko wanene ma'asumi. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Ku gaya mini wanne ne ga sarkin Isra'ila!" ko kuma "ku gaya mini wanene a cikinku yake bayyana wa sarkin Isra'ila shirinmu!”
"Kasancewa ga wani" yana nufin kasancewa da aminci ga wannan mutumin. A wannan yanayin, yana nufin cewa za su ba da bayanai don taimakawa sarkin Isra'ila. AT: "yana taimaka wa sarkin Isra'ila" ko "yana da aminci ga sarkin Isra'ila"
Bawan yana cewa babu wani daga cikin sojojin sarki da yake ba da labarin ga sarkin Isra'ila. AT: "Ba namu bane"
Wannan na nufin sarkin Aram.
"abinda ka faɗa a sirrin ɗakin ka"
Sarki yana shirin aiko mutanen su kama shi. Sarki bai yi shirin kama shi da kansa ba. AT: "Zan iya aika mutane su kama shi"
Wannan kalmar an yi amfani da ita a ja hankalin sarki game da abinda za a faɗa a gaba. AT: "Saurara"
Wannan sunan birni ne.
Wannan na nufin sarki Aram.
"ya tashi da asuba ya fita waje, sai ya ga"
Bawan ya koma cikin gidan ya gaya wa Elisha abinda ya gani. AT: "bawan ya koma ciki kuma ya ce wa Elisha"
"Kasance tare da wani" a cikin yaƙi yana nufin yin yaƙi don ɓangarensu. AT: "waɗanda suke goyon bayanmu a cikin yaƙi sun fi waɗanda suke goyon bayansu"
Elisha yana rokon cewa bawansa na iya ganin abubuwan da wasu mutane ba za su iya gani ba, wato dawakai da karusai na wuta da ke kewaye da su. AT: "sa shi iya gani"
"kama yana gani. Abinda ya gani shine"
Kalmar "duba" anan na nuna yadda bawan yayi mamaki da abin da ya gani.
"gefen tsaunin na rufe da dawakai"
Wannan na nufin birnin da Elisha ke zama. AT: "kewaye da birnin da Elisha ke zama"
Wannan na mufin sojojin Aramiya.
"Ka sanya mutanen nan su makance!" Wannan yana nuna Yahweh ne wanda yasa basu iya gani sosai.
Elisha ya rikitar da Aramiyawa ta hanyar gaya musu cewa ba su shiga garin da suke nema ba. AT: "Wannan ba ita ce hanyar ba, ba kuma wannan garin da kuke nema ba"
"Hakan ya faru" ko "To,"
Elisha yana roƙon Yahweh ya sa mutanen su sake gani a fili. AT: "ƙyale mutanen nan su gani"
Yahweh ya sa mutanen suka sake gani. AT: "Yahweh ya kawar da makantarsu" ko "Yahweh ya sa suka gani sarai"
Kalmar ''Duba'' anan na nuna Aramiyawa sun yi mamakin abinda suka gani.
"lokacin da ya ga sojojin Aramiyawa"
Sarkin na magana da Elisha annabi ya ki shi ''baba'' a nuna girmamawa.
A nan sarkin Isra'ila na nufin sojojin sa kamar kansa. AT: "in sa sojojina su kashe waɗannan sojojin abokan gaba?"
Elisha ya na amsa tambayar sarkin Isra'ila.
Elisha ya yi amfani da wannan tambayar don tsauta wa sarki ya kuma ce masa kada ya kashe waɗannan mutanen. Kalmomin "takobi da baka" kalmomi ne na yaƙe-yaƙe waɗanda sojoji suke amfani da takuba da baka da kibau. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Ba za ku kashe mutanen da kuka kama a yaƙi ba, don haka kar ku kashe waɗannan mutanen." )
Waɗannan makaman da ake anfani da su ne a yaƙi. AT: "a yaƙi da takobinka da bakanka"
A nan "gurasa" na nufin abinci. AT: "ka ba su abinci da ruwa domin su ci su sha,"
Wannan na nufin sarkin Aram.
Sarki yasa bayinsa su su shirya masu abinci. Bai shirya abincin da kansa ba. AT: "Sai sarkin yasa bayinsa suka shirya masu abinci da yawa"
"Waɗannan ƙungiyoyin"
Wannan na nufin ba su sake kai wa Isra'ila hari da wuri ba. AT: "suka daina kai wa ƙasar Isra'iala hari na ɗan tsawon lokaci"
Sunan sarkin Aram. Ma'anar sunan sa shine "ɗan Hadad."
Sarki da sojojinsa sun kai hari Samariya. AT: "Sun kai hari Samariya"
Kalmar "duba" anan na nuna yadda bawan yayi mamaki da abin da ya gani.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "kan jaki ya kai"
"zinariya 80"
Wannan za a iya auna shi a ma'auni na zamani. AT: "kashi huɗu na lita" ko "kwata ta lita"
"kashi 4." Wannan ɓangare ne na kashi huɗu na abu.
Kalmomin da babu za a iya ƙarawa. AT: "kashin kurciya ana sayar dashi a" ko "kashin kurciya ya kai naira"
"tafiya a saman katangan birni"
Matar ta kira sarki da suna shugaba ta nuna girmamawa.
"Sarkin Isra'ila ya amsa wa matar,"
Sarki ya yi amfani da wannan tambaya don gaya wa matar cewa ba zai iya taimakon ta ba. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Idan Yahweh ba ya taimaka muku, to ba zan iya taimaka muku ba."
Sarki ya yi amfani da wannan tambaya don nuna cewa babu abinci. A nan masussukar ma'anar hatsi ce da ruwan inabin yana nufin ruwan inabin. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Babu wani abu da yake zuwa daga masussukar ko matattar ruwan inabin." ko "Ba abinci da za a girbe, ko 'ya'yan inabi domin yin ruwan inabin."
"Sarkin ya ce." Wannan na nuna sun ci gaba da magana.
"mun dafa"
Kalmar "kalmomin" yana ga abin da matar ta faɗi. AT: "ta ji matar tana faɗi abin da ita da sauran matan suka aikata"
Sarkin ya keta rigarsa ta waje ya nuna ɓacin ransa. AT: "ya keta tufafinsa dan baƙin ciki"
Ya kasance yana yawo a jikin bango lokacin da matar ta kira shi cikin 2 Sarakuna 6:24. Yanzu ya ci gaba da tafiya da shi.
Ya sa tsummoki har ma don abin da aka sa masa, sarkin ya nuna cewa ya yi baƙin ciki kwarai da gaske. AT: "yana da tsummoki a ƙarƙashin mayafin jikinta, a jikin fatarsa" ko "yana sanye da tsummokaran a ƙarƙashin tufafinsa saboda ya fusata"
Sarki yana cewa yana fatan Allah zai hukunta shi har ma ya kashe shi idan annabi Elisha bai mutu ba saboda abubuwan da suka faru a cikin Samariya. AT: "Allah ya yi mini azaba ya kashe ni"
Wannan na nuni ga Elisha yana mutuwa, musamman a fille kansa. AT: "idan ba a kashe Elisha ɗan Shafat a yau ba" ko "idan sojojina ba su buge Elisha ɗan Shafat a yau"
"Kasancewa a gaban sarki" yana nufin kasancewa ɗaya daga cikin bayinsa. AT: "Sarkin Isra'ila ya aiki ɗaya daga cikin bayinsa a matsayin manzo"
Anan Elisha yana magana da dattawan tun kafin manzan sarki ya iso. AT: "lokacin da manzon ya kusan isa, sai Elisha ya ce wa dattawan"
Elisha ya yi amfani da wannan tambaya don ya jawo hankali ga manzannin da kuma zagi sarki. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Duba, wannan ɗan mai kisan kai ya aiko wani ya cire mini kai!"
Wannan yana nuna cewa sarkin Isra'ila yana da halayen mai kisan kai. AT: "wannan mutumin da ya yi kama da mai kisan kai" ko "wannan mai kisan kai"
An fahimci cewa ya aiko da mutum. AT: "ya aika wani zuwa"
Wannan yana nufin fille kansa. AT: "a datse kaina" ko "a fille kaina"
Elisha ya yi amfani da wannan kalma a nan don jawo hankalin dattijon game da abin da ya faɗi. AT: "Saurari abin da nake so kuyi: yaushe"
Idan an kulle kofa ga wani yana nufin yana rufe kuma ba za su shiga ta ciki ba. AT: "kulle ƙofar don kada ya shiga"
Elisha ya yi amfani da wannan tambaya don tabbatar wa dattawan cewa sarki ba ya zuwa kusa da shi. Wannan tambaya ana iya rubuta ta azaman bayani. AT: "Sautin ƙafafun maigidansa yana hannun dama." ko kuma "Sarki zai zo da wuri bayan ya dawo."
Kalmar "ga shi" tana faɗakar da mu game da isowar manzo.
Dan saƙon ya iso, sarki kuma kamar yadda Elisha ya faɗa zai yi. Kalmomin "sun sauko gare shi" yana nufin cewa sun isa wurin da yake. AT: "manzo da sarki sun iso"
"Lallai wannan matsala." Kalmar "duba" a nan yana ƙara ƙarfafawa ga abin da ya biyo baya. Kalmomin "wannan matsala" tana nufin yunwar Samariya da wahala da ta haddasa.
Wannan sarki yayi amfani da wannan tambaya don nuna cewa bai yi imani da cewa Yahweh zai taimake su ba. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Don me zan ci gaba da jiran Yahweh ya taimake mu?" ko kuma "Ba zan ƙara jiran taimako daga wurin Yahweh ba!
1Elisha yace, ka ji maganar Yahweh, wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗa: gobe kamar i yanzu a ƙofar shiga Samariya za a sayar da kofin garin alkama a shekel ɗaya, awo biyu na sha'ir a shekel,'"2Sai hafsan da aka aiko wurin Elisha ya ce da mutumin Allah, "Ko da ma ace Yahweh zai buɗe sakatun sama, wannan abin zai faru? "Elisha ya amsa, "Duba za ka ga abin na faruwa da idonka amma ba za ka ɗanɗana ko kaɗan daga cikinsa ba."3To akwai mutun huɗu da ke da ciwon kuturta a wajen ƙofar birni. Sai suka cewa juna, "Domin me za mu yi ta zama a nan har mu mutu?4In mun ce za mu cikin birni yunwar na can, za mu kuma mutu a can. Bari mu je sansanin Aremiyawa. In sun bar mu da rai mu rayu, in kuma zamu mutu mu mutu a can, amma ko da ma mun tsaya a nan zamu mutu. To yanzu sai mu je sansanin Aremiyawa. In sun bar mu da rai to, za mu rayau, in kuma sun kashe mu mutuwa kawai zamu yi."5To sai suka tashi da almuru suka nufi sansanin Aremiyawa; da suka isa tsakiyar wurin ba kowa a sansanin ba ko mutun ɗaya a wurin.6Domin Ubangiji yasa sojojin Aremiyawa su ji ƙarar karusai da ƙarar mahayan dawakai da kuma babbar ƙarar rundunar soja, suka ce da junansu. "Sarkin Isra'ila ya yi hayar sarakunan Hitiyawa da na Masar domin su kawo mana hari."7Domin haka sojoji suka ruga da almuru; suka bar rumfunansu, da dawakansu, da jakunansu da sansanin kamar yadda yake suka gudu domin su tsirar da ransu.8Lokacin da mutanen da ke da kuturta suka shiga tsakiyar sansanin suka shiga wata rumfa suka ci suka sha, suka kwashi shekel da zinariya da azurfa da da suturu suka tafi da su suka ɓoye su suka sake dawowa suka shiga wani sansanin suka kwashi ganima daga can suka tafi suka ɓoye ta.9Daga nan suka ce da juna, "Ba mu yin abin da ke dai dai ba yau. wannan ranar ta kai soƙo mai daɗi ce, amma munyi shiru game da batun. In mun jira har gari ya waye za mu fuskaci horo. To yanzu, ku zo mu je mu faɗa wa dukkan gidan sarki."10Sai suka tafi suka kira masu tsaron ƙofar birnin. Suka faɗa masu cewa, Mun je sansanin Aremiyawa, amma ba kowa a can, ba kuma motsin kowa, amma akwai dawakai a ɗaure, da jakai a ɗaure da kuma rumfunan kamar yadda suke."11Daga nan sai masu tsaron ƙofofin suka baza labarin, daga nan sai aka faɗa a cikin dukkan gidan sarki.12Sai sarki ya tashi da dare ya ce da bayinsa, "Yanzu zan faɗa maku abin da Aremiyawa suka yi mana. Sun sani muna jin yunwa, to sai suka bar sansanin suka je suka ɓuya a cikin sauruka. Suna cewa, "in sun fito wajen birnin, zamu kama su da rai, mu shiga cikin birnin."'13Ɗaya daga cikin bayin sarki ya ce, "'Ina roƙonka ka bar waɗansu mutane su ɗauki dawakai biyar da suka rage a birnin. Su kamar sauran yawan Isra'ila ne da suka ragu - domin da yawansu sun mutu; sai mu aike su mu gani."14Sai suka kwashi karusan dawakai guda biyu, sai sarki ya aike su su bi Aremiyawa cewa, "Ku je ku gani."15Sai suka tafi har zuwa Yodan, hanyar kuma ta cika da suturu birjik da kuma kayayyakin da Aremiyawa suka warwatsar cikin saurinsu. Sai manzannin suka dawo suka faɗawa sarki.16Sai mutane suka fita suka kwashi ganimar sansanin Aremiyawa. Domin haka aka sayar da awon alkama a shekel ɗaya da kuma awon sha'ir biyu a shekel, kamar dai yadda maganar Yahweh ta faɗa.17Sai sarki ya sa wannan hafsan da ya aika ya zama mai kula da ƙofar, sai mutane suka tattake shi a ƙofar. Ya mutu kamar yadda mutumin Allah ya faɗa, a lokacin da sarki ya zo wurinsa.18Haka ya kasance kamar yadda mutumin Allah ya faɗa wa sarki, cewa, war haka a ƙofar shiga Samariya, za, a sayar da awo biyu na sha'ir a shekel, awo ɗaya na alkama kuma a shekel."19Wannan hafsan ya ce da mutumin Allah, "Duba ko da Yahweh zai sa sakatun sama su buɗe, ko wannan zai faru?" Elisha ya ce, "Duba za ka gani yana faruwa a idanunka, amma ba za ka ci daga cikinsa ba."20Wannan shi ne hakikanin abin da ya faru da shi, domin mutane sun tattake shi a bakin ƙofa, ya kuma mutu.
An ɗauka cewa Isra'ilawa za su biya kuɗi kaɗan ƙasa da wannan kayan da aka ba su. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "mutane za su sayar da mudu na lallausan gari na shekel da mudu biyu na sha'ir a shekel"
Anan kalmar "awo" tana fassara kalmar "seah," sati guda ce na busassun ma'aunin dai-dai da lita 7. AT: "lita 7 na garin alkama ... lita 14 na sha'ir"
Ana magana da babban shugaban wanda ya kasance mai taimaka wa sarki game da shi kamar mutum ne wanda sarki ya jingina hannunsa. AT: "shugaban ɗin da ke kusa da sarki" ko "shugaban wanda shi ne mai taimaka wa sarki"
Yahweh yana sa saukar ruwan sama mai yawa domin ya sa amfanin gona ta yi magana kamar ana buɗe sakatun a sama wanda yake zubo da ruwan sama. AT: "ko da Yahweh zai sa aka yi ruwan sama mai yawa daga sama"
Hafsan yayi wannan tambaya ne don nuna rashin yardarsa. Wannan tambaya za a iya fassara a matsayin bayani. AT: "wannan ba zai taɓa faruwa ba!"
Kalmomin "da idanka" ya nanata cewa tabbas shugaban zai ga abubuwan da Elisha ya annabta. AT: "da kanka za ku kalli waɗannan abubuwa suna faruwa"
"amma ba za ka ci ko kaɗan daga cikin garin alkamarba ko sha'ir"
Wannan kalmar ana amfani da ita anan don alamar hutu a cikin babban labarin. Anan marubucin ya fara ba da sabon ɓangaren labarin.
Duk da cewa akwai maza guda huɗu, da alama ɗayansu ne ke yin wannan tambaya. Tambayar yana jaddada cewa bai kamata su aikata wannan ba. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Tabbas kada mu zauna anan har sai mun mutu"
Mazajen guda huɗu masu kuturta suna cewa Aramiyawa ta yiwu su basu abinci ko su kasu, kuma wannan mutuwar ba komai bace tunda ko anan ma zamu mutu.
Wannan na yamma bayan faɗuwar rana, amma kafin gari ya yi duhu.
"gefen"
Sojojin Aramiyawa kuwa suka ji amon sowa da take kama da babban mayaƙa suna gab da fuskantar yaƙi. Wannan ba ainihin runduna ba ce, amma Ubangiji ya sa sun ji wannan karar.
"sojojin Aram suka ce wa junansu"
Anan kalmar "sarakuna" tana wakiltar sarakuna da sojojinsu. AT: "runtunan Hittiyawa da Masarawa"
"su yaƙe mu" ko "su kawo mana hari"
Wannan shi ne abin da ya faru bayan da Ubangiji ya sa sojojin Aram su yi tunanin sun ji babbar rundunar abokan gaba suna gab da zango.
Wannan na yamma bayan faɗuwar rana, amma kafin gari ya yi duhu.
Wannan yana nufin abubuwa ne wanda sojojin da aka ci nasara kan karba daga wata rundunar da suka ci nasara. A nan yana nufin "azurfa da zinariya da tufafi."
"har safiya"
Wani wanda yake azabtar da mutanen hudun ana magana dashi kamar azaba shine mutumin da ya kama su. AT: "mutane za su yi mana horo" ko "wani zai yi mana horo"
Anan kalmar "gidan" tana wakiltar mutanen da ke zama a gidan sarki. AT: "gaya wa sarki da mutanensa"
Ana iya bayyanar da bayanan dalla-dalla a sarari. AT: "kamar yadda suke yayin da sojoji suke har yanzu"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "sai mutane suka ba da labari a cikin gidan sarki" ko "sannan mutane suka faɗa wa sarki da waɗanda ke cikin fadarsa"
"suna shirin yi mana" ko "sun yi yaudarar mu"
Wannan yana nufin cewa za su kama mutanen ba su kashe su ba.
Yawancin dawakan Isra'ilawa sun mutu saboda yunwar. Ana iya bayyana ma'anar wannan a sarari. AT: “dawakai cikin birni da suka rage da rai”
Mazajen da zasu je sansanin Aramiyawa za sun raba abubuwan dai-dai da sauran da suka rage a birni. Ta yi wu su mutu saboda yunwa, ko kuma Aramiyawa su kashe su.
Bayani mai gamsarwa game da abin da ya ke so ya gani na iya bayyana a sarari. AT: “gani ko abin da waɗannan kutaren suka faɗi gaskiya ne”
Bayani mai gamsarwa game da abin da sarki ya so su gani za a iya bayyana shi a sarari. AT: "Ku je ku duba ku gani ko abin da waɗannan kutaren suka faɗi gaskiya ne"
"Suka bi hanyar sojojin Aramiyawa suka bi har hanyar Kogin Yodan"
Wannan ƙari ne mai nuna cewa mazan sun ga waɗannan abubuwan sun watse a hanya yayin da suke tafiya. AT: "tufafi da kayan aiki suna kan hanya"
Wannan yana nufin ɗaukar abubuwa daga sojojin da aka yi nasara.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Don haka mutane suka sayar da mudu na lallausan gari na shekel da mudu biyu na sha'ir a bakin shekel"
Anan "kalma" tana wakiltar Yahweh. Fassarar ta dabam: "kamar yadda Yahweh ya faɗa"
Taron mutanen na ta suari su je ga abincin a sansani sai suka kãda hafsan suka tattake shi ya mutu.
A cikin wannan ayar, marubucin ya taƙaita abin da ya faru ta hanyar maimaita abubuwan da ya faru a cikin 2 Sarakuna 7: 1.
"Game da wannan lokacin gobe"
A nan kalmar "awo" an fassara ''seah'' wanda shi ne ma'aunin ya kusan lita 7. AT: ''14 lita sha'ir ... lita 7 na garin alkama''
"sosai". Kalmar "duba" anan a jaddada abinda ya biyo baya.
Yahweh yana sa saukar ruwan sama mai yawa domin ya sa amfanin gona ta yi magana kamar ana buɗe sakatun a sama wanda yake zubo da ruwan sama. AT: "ko da Yahweh zai sa aka yi ruwan sama mai yawa daga sama"
Hafsan yayi wannan tambaya ne don nuna rashin yardarsa. Wannan tambaya za a iya fassara a matsayin bayani. AT: "wannan ba zai taɓa faruwa ba!"
Kalmomin "da idanka" ya nanata cewa tabbas shugaban zai ga abubuwan da Elisha ya annabta. AT: "da kanka za ku kalli waɗannan abubuwa suna faruwa"
"amma ba za ka ci ko kaɗan daga cikin garin alkamarba ko sha'ir"
1To sai Elisha ya yi magana da matar da ya komar da ɗanta da rai. Ya ce da ita, "Ki tashi, da dukkan gidanki, zauna a duk inda za ki zauna a wata ƙasa, domin Yahweh ya saukar da yunwa a wannan ƙasa har tsawo shekaru bakwai."2Sai matar ta tashi ta yi biyayya da maganar mutumin Allah. Ta tafi da ita da mutanen gidanta zuwa ƙasar Filistiyawa har tsawon shekaru bakwai.3To a ƙarshen shekaru bakwai da wannan mata ta komo daga ƙasar filistiyawa, ta je wurin sarki ta roƙe shi domin gidanta da kuma ƙasarta.4To sarki na magana da Gehazi baran mutumin Allah, cewa "Ina roƙo ka faɗa mini dukkan manyan abubuwan da Elisha ya yi."5A lokacin da yake faɗa wa sarki yadda Elisha ya komar da ran yaron da ya mutu, sai wannan dai matar ta zo ta roƙi sarki saboda gidanta da kuma ƙasarta. Gehazi yace, "Shugabana, sarki, ga matar da kuma ɗan nata, da Elisha ya mayar wa da rai."6Lokacin da sarki ya tambayi matar game da ɗanta, ta yi masa bayani. Sai sarki ya sa wani hafsa dominta ya ce, "Ka ba ta duk abin da ke nata da kuma dukkan girbin gonarta tun daga ranar da ta bar ƙasar har ya zuwa yanzu."7Sai Elisha ya zo Damaskus. Inda Ben Hadad sarkin Aram ke ciwo. Sai aka faɗa wa sarki cewa, "Mutumin Allah ya zo nan."8Sai sarki yace da Hazayel, "Ɗauki kyauta a hannunka ka je wurin mutumin Allah, ka tuntuɓi Yahweh ta wurinsa, cewa 'Ko zan wartsake daga wannan rashin lafiyar?"'9To sai Hazayel ya tafi wurinsa da kyauta ta kowanne abu mai kyau na Damaskus, ya ɗora wa raƙuma arba'in. Sai Hazayel ya zo ya tsaya a gaban Elisha ya ce "Ɗanka Ben Hadad sarkin Aram ne ya aiko ni gare ka, cewa 'ko zan warke daga wannan rashin lafiyar?"'10Elisha ya ce da shi, "Ka je ka ce da Ben Hadad, 'Hakika za ka warke; amma Yahweh ya nuna mani cewa hakika zai mutu."11Sai Elisha ya ƙarfafa Hazayel har sai da ya ji kunya, mutumin Allah kuma ya yi kuka.12Hazayel ya tambaya, "Meyasa ka yi kuka, ya shugabana?" Ya amsa, "Saboda na san irin muguntar da zaka yi wa mutanen Isra'ila. Za ka ƙone hasumayoyinsu da wuta, za ka kuma kashe samarinsu da takobi, zaka kuma daddatsa 'yan ƙananansu, za ka kuma feɗe matayensu masu juna biyu."13Hazayel ya masa, "Wane ne baranka, da zai yi wannan babban abu? Ai shi kare ne kawai. Elisha ya amsa, Yahweh ya nuna mani cewa za ka yi sarautar Aram.14Daga nan Hazayel ya rabu da Elisha ya komo wurin mai gidansa, wanda ya ce da shi "Me Elisha ya faɗa maka?" ya amsa, ya faɗa mani hakika za ka warke."15To washegari Hazayel ya ɗauki bargo ya tsoma shi a ruwa, ya shimfiɗa shi a kan fuskar Ben Hadad da haka ya mutu. Sai Hazayel ya zama sarki a maimakon sa.16A shekara ta biyar ta sarautar Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra'ila, Yahoram ya fara sarauta. Shi ɗan Yehoshafat ne sarkin Yahuda. Ya fara sarauta a lokacin da Yehoshafat ke sarautar Yahuda.17Yahoram yana da shekaru talatin da biyu a lokacin da ya fara sarauta, ya yi sarauta ta shekaru takwas a Yerusalem.18Yahoram ya bi tafarkin sarakunan Isra'ila, kamar yadda gidan Ahab ya yi; domin ya auri 'yar Ahab a matsayin matarsa, ya kuma yi abin da ke mugu a gaban Yahweh.19Duk da haka, saboda baransa Dauda bai so ya hallaka Yahuda ba, tun da ya yi masa alƙawari cewa har kullum ba za a rasa wanda zai yi sarauta daga zuriyarsa ba.20A kwanakin Yahoram, sai Idom ta tayar wa mulkin Yahuda, suka kuma naɗa wa kansu sarki. Sai21Yahoram ya tsallake shi da hafsoshinsa da dukkan karusansa. Sai ya tashi da duhu ya kai hari ya washe Idomawa, waɗanda suka kewaye shi da kuma hafsoshin karusai. Sai sojojin Yaharom suka tsere gidajensu.22To da haka Idom ta tayar wa mulkin Yahuda har ya zuwa yau. Libna ita ma ta tayar alokaci guda.23To game da sauran abubuwa game da Yahoram, da duk abin da ya yi, ashe ba a rubuce suke a littafin ayyukan sarakunan Yahuda ba?24Yahoram ya mutu ya huta tare da ubanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dauda. Daga nan ɗansa Ahaziya ya zama sarki a madadinsa.25A shekara ta sha biyu ta Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra'ila, da Ahaziya ɗăn Yehoram, sarkin Yahuda, suka fara mulki.26Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu lokacin da ya fara sarauta; ya yi sarautar shekara ɗaya a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Ataliya; Ita 'yar Omri ce, sarkin Isra'ila.27Ahaziya ya bi tafarkin gidan Ahab; ya yi abin da ke mugu a gaban Yahweh, kamar dai sauran abin da Ahab ya yi, domin Ahaziya suruki ne ga gidan Ahab.28Ahaziya ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab, domin su yi yaƙi gãba da Hazayel, sarkin Aram, a Ramot Giliyad. Aremiyawa suka yi wa Yoram rauni.29Sarki Yoram ya koma gida domin ya warke a Yazriyel daga raunin da aka yi masa a Rama, a lokacin da ya yi yaƙi da Hazayel sarkin Aram. Sai Ahaziya ɗan Yahoram sarkin Yahuda, ya tafi Yezriyel domin ya ga Yoram ɗan Ahab, saboda an yi wa Yoram rauni.
Wannan kalmar ana amfani da ita anan don alamar hutu a cikin babban labarin. Anan marubucin ya fara ba da sabon ɓangaren labarin.
Labarin wannan matar da yaronta yana nan a 2 Sarakuna 4:8.
"ya sa ya dawo da rai"
Tashi anan shi ne mutum ya dakatar da abin da yake yi ya fara yin abin da ya kamata ya yi. AT: "tashi daga inda suke"
"Elisha, mutumin Allah"
Wannan na nufin sarkin Isra'ila.
Yayin da matar ta tafi, gidansu da kayan sa ba a sikeli ba. Tana roƙon a mayar musu da ita. Cikakken ma'anar wannan bayanin ana iya bayyana shi sarai. AT: "don a mayar mata da gidanta da kayan ta"
Wannan kalmar anan anyi amfani da ita a kawo tsaikon labarin. Anan marubucin ya bamu matashin bayanin game da abinda sarki yake yi yayin da matar ta iso.
"ya sa yaron da ya mutu ya dawo da rai"
Bayan da matar ta tafi, gidan ta da dukiyoyinta an kwashe. Tana roƙon a maido mata da shi. ma'anar wannan bayanin za a iya cewa. AT: "domin gidanta da dukiyarta a maido mata"
Wannan na maganar labarin ɗanta yana mutuwa kuma Elisha ya ta da shi daga rai. Ana iya bayyana ma'anar wannan bayanin a bayyane. AT: "game da abin da ya faru da ɗanta"
Wannan ma'anar tana nufin yawan kuɗin gonakin gonakin nata da ya cancanci yayin da ta tafi. AT: "Duk ribar da aka samu daga girbin gonakinta"
Wannan sunan sarkin Aram. Sunansa yana nufin "ɗan Hadad." Duba yadda zaka fassara sunan mutumin a cikin 2 Sarakuna 6:24.
Wannan sunan na mutum ne.
Hazayel zai ɗauki kyautai, ba wai guda ɗaya ba. AT: ""ɗauki kyaututtuka da yawa"
Kalmomin "a hannunka" ma'ana kalma ce a gare shi domin ɗaukar kyautai tare da shi. AT: "tare da kai"
"ka roƙi Elisha ya roƙi Yahweh"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "wanda raƙuma arba'in suka ɗauka"
''raƙuma 40''
Ben Hadad ba da gaske bane ɗan Elisha, amma Hazayel ya kira shi don ya nuna kusanci tsakanin su. AT: "Ben Hadad, sarkin Aram, wanda yake kamar ɗanka gare ka"
"har sai Hazayel ya ji kunya"
Hazayel na nufin Elisha yadda zai girmama shi.
Allah ya nuna wa Elisha abinda zai faru a gaba.
Kalmar '''kai'' na wakiltar Hazayel kuma na nufin shi da sojojin da ke ƙarƙashin ikon sarkin. AT: "zaka sa ya faru" ko "za sa sojojinka"
Kalmar "ku" tana wakiltar Hazayel amma a nan yana nufin sojojinsa ne ba ga Hazayel da kaina ba. AT: "Sojojinka za ku kafa ... sojojinku za su kashe"
"murkushe 'yayansu." Wannan mummunan bayanin sojoji ne da ke kashe yara.
Wannan na nufin samarin za su mutu a yaƙi. Takobi shine makamin da aka fi amfani da shi ya yaƙi. AT: "za ka kuma kashe samarinsu a yaƙi"
Wannan na nufin yanka cikinsu. AT: "za ka kuma feɗe cikin matayensu masu juna biyu.'' da takobi"
Hazayel ya ambaci kansa a nan bawan Elisha. Hazayel ya yi amfani da wannan tambaya don ƙarfafa cewa bai yi tunanin zai iya yin munanan ayyukan da Elisha ya faɗi ba. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Ba zan taɓa iya yin waɗannan manyan abubuwan ba." ko "Wanene ni, da zan sami ikon yin irin waɗannan abubuwan?"
"wannan mummunan abu." A nan kalmar "babba" tana nufin wani abu wanda ke da babban tasiri kuma mummunan aiki.
Hazayel yana magana ne game da kansa. Yayi magana game da karancinsa da rashin tasiri ta hanyar kwatanta kansa da kare. Anan kare yana wakiltar dabba mai ƙarancin ƙarfi. AT: "Ni mai rauni ne kamar kare" ko "Ba ni da ƙarfi kamar dabba mara ƙarfi"
maganar "shugabansa" na nufin Ben Hadad.
Wannan yana nuna cewa Ben Hadad ya sha wahala a ƙarƙashin bargon rigar. Cikakken ma'anar wannan bayanin ana iya bayyana shi sarai. AT: "fuska. Ben Hadad bai iya yin numfashi ba, har ya mutu"
Yehoram ya zama sarkin Yahuda.
Wannan yana nuna tsawon lokacin da Yehoram ya fara sarautar Yahuda ta wurin faɗi tsawon lokacin da Yehoram, sarkin Isra'ila na yanzu yake sarauta. AT: "A cikin shekara ta biyar ta Yoram ɗan Ahab ya zama sarkin Isra'ila" ko "A shekara ta biyar ta mulkin Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra'ila"
"shekara ta 5"
Yehoram, ɗan Yehoshafat, ya zama sarkin Isra'ila.
"shekaru 32"
Anan "tafiya" karin magana ne nuna yadda ya rayu da sarauta a matsayin sarki. A wannan lokacin a tarihi, sarakunan Isra'ila na baya-bayan nan sun zama mugayen sarakuna. Cikakken ma'anar wannan bayanin ana iya bayyana shi sarai. AT: "Yehoram shi ne sarki mugunta, kamar yadda sauran sarakunan Isra'ila waɗanda suka yi sarauta a gabansa"
A nan "gidan" Ahab na nufin iyalansa gidan Ahab da zuriyarsa ta yanzu. Ahab shi surukin Yehoram. AT: "kamar yadda sauran iyalan Ahab suke yi"
Yehoram ya auri 'yar sarki Ahab.
Gaban Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh ko tantancewa. AT: "abin da ke mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ɗauka mugunta ne"
A nan "Yahuda" wata alama ce ta mutanen da ke zaune a can. AT: "halakar da mutanen Yahuda"
"tunda Yahweh ya faɗa wa Dauda cewa zai ba Dauda zuriya a koyaushe." Wannan na nufin alkawarin da Yahweh ya yi wa Dauda cewa zuriyarsa za su mallaki Yahuda koyaushe. Ana iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayanin a bayyane. AT: "tunda ya faɗa wa Dauda cewa zuriyarsa za su yi mulkin Yahuza koyaushe"
"Idom sun yi tawaye"
Anan kalmar "hannun" tana nufin sarrafawa Yahuda, kuma "Yahuda" yana nufin musamman ga sarkin Yahuda. AT: "sarrafawa sarkin Yahuda"
"sun zaɓi sarki su mulkesu"
Abin da aka "tsallake" za a iya bayyana a sarari. AT: "Sai Yehoram ya tsallake layin abokan gaba"
"Sai, da duhu, ya tashi"
A nan kalmar "shi" na wakiltar Yehoram da kuma na nufin shi da kansa da hafsoshinsa. AT: "shi da hafsoshinsa"
Sarki Yoram na Yahuda ya mutu kuma ɗansa Ahaziya ya zama sarki.
Saboda haka bayan haka, Idom ba ta ƙara mallakar Yahuba ba, kuma har yanzu tana haka"
A nan "Yahuda" na nufin sarkin Yahuda. AT: "mulkin sarkin Yahuda" ko "ikon sarkin Yahuda"
har lokacin da aka rubuta wannan littafi
Libna ta tayar wa sarkin Yahuda kamar yadda Idom tayi. AT: "kamar wancan lokacin, Libna tayi tawaye ga sarkin Yahuda"
Wannan su ne biranen Yahuda wanda asalinsa Yahuda ne. A nan "Libna" yana nufin mutanen da suke zaune a can. AT: "Mutanen Libna"
"Don ƙara karantawa game da tarihin Yehoram da abin da ya yi,"
Ana amfani da wannan tambaya don ko dai sanar da ko kuma tunatar da masu karatu cewa bayanin game da Yehoram yana cikin wannan littafin. AT: "waɗannan abubuwan an rubuta su ne ... Yahuza." ko "wani ya rubuta game da su ... Yahuda."
Anan "an huta" hanya ce ta ladabi da ake magana akan wanda yake mutuwa. Bayan ya mutu, an binne gawarsa a dai-dai wurin da kakannin kakanninsa. Ana iya bayanin kalmar "an binne" a cikin tsari mai aiki. AT: "Yehoram ya mutu kamar yadda kakanninsa suka mutu, suka binne shi tare da kakanninsa"
"sai Ahaziya, ɗan Yehoram, ya zama sarki bayan ya mutu"
Ahaziya ya zama sarkin Yahuda.
Wannan ya bayyana tsawon lokacin da Ahaziya ya fara sarauta a matsayin sarkin Yahuda ta hanyar faɗi tsawon lokacin da Yehoram, sarkin Isra'ila na yanzu yake sarauta. AT: "A shekara ta goma sha biyu ta Yoram ɗan Ahab ya zama sarkin Isra'ila"
"shekara 12"
"shekaru 22"
Ataliya sunan mace ne. Omri sunan mace ne.
A nan "tafiya" na nufin yanayin rayuwarsa. AT: "Ahaziya yayi rayuwa irin ta sauran"
A nan "gida" Ahab na nufin iyalinsa. AT: "iyalin Ahab"
Gaban Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh ko tantancewa. AT: "abin da ke mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ɗauka mugunta ne"
Wannan ya bayyana dangantakar Ahaziya da Ahab. Mahaifin Ahaziya ya auri 'yar Ahab. Ana iya bayyana ma'anar wannan a sarari. AT: "ɗan surukin Ahab" ko "jikan Sarki Ahab"
Sunayen sarakunan nan uku suna nufin rundunarsu da ke rakiyar su. AT: "Rundunar Ahaziya ta haɗa kai da rundunar Yoram na Isra'ila don su yi yaƙi da rundunar Hazayel na Aram"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "don warkarwa" ko "don murmurewa"
A nan "Hazayel" na nufin shi da sojojinsa. AT: "sojojin Hazayel sarkin Aram"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Aramiyawa sun raunata Yoram"
1Sai annabi Elisha ya kira ɗaya daga cikin 'ya'yan annabawa ya ce da shi, "Ka shirya domin tafiya, ka riƙe wannan 'yar kwalbar man ka tafi Ramot Giliyad2lokacin da ka je sai ka nemi Yehu ɗan Yehoshafat ɗan Nimshi, sai ka shiga ciki ka sa shi ya tashi daga abokan taraiyarsa ka bi da shi can cikin lalloki rumfa3Sai ka ɗauki kwalbar ka tsiyaya masa mai aka ce Yahweh ya faɗi wannan: "Na keɓe ka ka zama sarkin Isra'ila" daga nan sai ka buɗe ƙofa ka yi sauri ka gudu, kada ka yi jinkiri.4Sai saurayin, wato matashin annabin, ya tafi Ramot Giliyad.5Da ya isa sai ga hafsoshin sojoji na zaune. Sai matashin annabin ya ce, "Na zo wurin ɗaya daga cikinku, ne hafsoshi." Yehu ya amsa, Ga wa daga cikinmu?" Matashin annabin ya amsa "Gareka, hafsa"6Sai Yehu ya tashi ya shiga cikin gida, sai annabin ya zuba masa mai a kã yace da Yehu, "Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: 'Na keɓe ka ka zama sarki akan mutanen Yahweh, Isra'ila.7Dole ne ka kashe iyalin Ahab shugabannka, domin in yi ramako akan bayina annabawa, da kuma jinin dukkan bayin Yahweh waɗanda Yezebel ta kashe.8Domin dukkan iyalan Ahab za su lalace zan kuma datse dukkan 'ya'ya maza na zuriyar Ahab ko shi bawa ne ko kuma mai 'yanci.9Zan mayar da gidan Ahab kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat, kamar kuma gidan Ba'asha ɗan Ahija.10Karnuka kuma za su ci naman Yezebel a Yezriyel kuma ba za 'a sami wanda zai bizne ta ba.'" Daga nan sai annabin ya buɗe ƙofar, ya gudu.11Sai Yehu ya fito waje zuwa wurin bayin shugabansa, sai ɗaya daga cikinsu ya ce da shi, "Ko dai lafiya? Meyasa wannan mahaukacin ya zo wurinka?" Yehu ya amsa musu, "Kun san irin mutumin da irin abin da ya ke faɗi."12Suka ce, "Wannan ƙarya ne. Ka faɗa." Yehu ya amsa, "Ya faɗa mani abu kaza da kaza, hakan nan ya ce 'Ga abin da Yahweh yace: Na kebe ka ka zama sarkin Isra'ila."'13Sai dukkan su suka yi sauri suka tuɓe rigarsa ta waje suka sa ta ƙarƙashin Yehu akan matakan. Suka hura kakaki suka ce, "Yehu sarki ne."14Ta haka Yehu ɗan Yehoshafat ɗan Nimshi suka ƙulla maƙarƙashiya kan Yoram. A lokacin, Yoram yana kare Ramot Giliyad, shi da dukkan Isra'ila, saboda Hazayel sarkin Aram,15amma sarki Yoram ya koma Yezriyel domin ya warke daga raunin da Aremiyawa suka yi masa, lokacin da suka yi faɗa da Hazayel sarkin Aram. Yehu yace da bawan Yoram, "In wannan shi ne ra'ayinka, to kada kowa ya tsira ya fita daga birnin, saboda aje a faɗi labarin a Yezriyel."16Sai Yehu ya tuƙa karusa zuwa Yezriyel; Yoram yana shaƙatawa a can. Sai Ahaziya sarkin Yahuda ya zo domin ya ga Yoram.17Ɗan tsaro na tsaye akan hasumaya a Yezriyel, sai ya ga rundunar Yehu da ya matso kusa; sai yace, "Na ga kungiyar mazaje na zuwa." Yoram yace, "Ka kwashi mahayin dawakai, ka aike shi wurinsu; ka ce da shi ya tambaye su 'Kuna zuwa da salama ne?"'18Sai ya aika mutumin akan doki ya koma ya tare shi; sai ya ce, sarki ne ya faɗi wannan: 'Kuna zuwa da salama ne?"' Sai Yehu yace, "Me zaku yi da salama? Ka juya ka biyo ni."Sai ɗan tsaron ya faɗa wa sarki, "Ɗan saƙon ya same shi, amma ba zai dawo ba."19Sai ya sake aikar mutum na biyu ya sake komawa akan doki, wanda ya zo wurinsu ya ce, "Sarki ya faɗi wannan: 'Kuna zuwa da salama ne?'" Yehu ya amsa "Me za ku yi da salama? ka juyo ka biyo ni."20Sai wannan manzon ya sake mayar da amsa, "Ya same su, amma ba zai dawo ba. Domin hanyar da ya ke tuƙa dawakan ita ce Yehu ɗan Nimshi ya bi; kuma yana tuki a sukwane."21Sai Yoram yace, "Ka shirya karusata." Suka shiya karusarsa, sai Yoram sarkin Isra'ila da Ahaziya sarkin Yahuda suka fita akan dawakai, kowa da karusarsa domin su gamu da Yehu. Suka same shi a mallakar Nabot Bayezriyile.22Da Yoram ya ga Yehu, sai ya ce, "Yehu kana zuwa da salama ne?" Ya amsa, "Wacce salama kuma ke a can bayan akin zina da maitanci na mahaifiyarka Yezebel sun yi yawa?"23Sai Yoram ya juya karusarsa ya tsere ya ce da Ahaziya, "Akwai tashin hankali Ahaziya."24Daga nan Yehu ya ɗauko bakãnsa da cikkakken ƙarfinsa ya harbi Yoram a tsakanin kafaɗunsa; kibiyar ta bi ta zuciyarsa, sai ya faɗi a cikin karusarsa.25Sai Yehu yace da Bidkar hafsansa, "Ciro shi ka jefar da shi a filin Nabot Bayezriyile. Tuna da yadda muka bi babansa Ahab, Yahweh ya ajeye hukuncinsa a kansa:26'Jiya na ga jinin Nabot da kuma jinin 'ya'yansa - inji Yahweh - kuma hakika zan sa ka biya shi a wannan fili - inji Yahweh. Yanzu, sai ka ciro shi ka jefar da shi a filin, bisa ga maganar Yahweh."27Da Ahaziya sarkin Yahuda ya ga wannan, sai ya gudu daga hanya zuwa Bet Haggan. Amma Yehu ya bi shi, ya ce "Shi maku kashe shi a cikin karusarsa," sai suka harbe shi kusa da Gur, wadda ke wajen Ibliyam. Ahaziya ya gudu zuwa Megiddo ya mutu a can.28Bayin suka ɗauke gawarsa a cikin karusa zuwa Yerusalem suka bizne shi a maƙabarta tare da ubanninsa a birnin Dauda.29A shekara ta sha ɗaya ne ta Yoram ɗan Ahab Ahaziya ya fara mulkin Yahuda,30Da Yehu ya zo Yezriyel, Yezebel ta ji labari, sai ta yi kwalliya ta yi wa idonta zane ta gyara gashinta, ta duba ta taga.31A lokacin da Yehu ke shiga ƙofar ta ce da shi, "Kana zuwa da salama ne, kai Zimri, an kashe shugabanka ne?"32Yehu ya dubi tagar ya cewa, "Ke tare da ni? Ke?" Sai bãbãni biyu ko uku suka duba waje.33Sai Yehu yace, "Ku wurgo ta ƙasa." Sai su ka wurgo Yezebel ƙasa, har jininta ya fallatsa a bango da kuma jikin dawakai, Yehu kuma ya tattake ta da ƙafafu.34Da Yehu ya shiga fãdar sai ya ci ya sha. Ya ce, "Duba yanzu ku ɗauki wannan la'anarniyar matar ku bizne ta, domin ita 'yar sarki ce."35Sai suka tafi domin su bizne ta, amma ba su tarar da komai nata ba sai ƙoƙon kanta da ƙafa da tafin hannuwa.36Sai suka dawo suka faɗa wa Yehu. Ya ce, "Wannan maganar Yahweh ce wadda annabi Iliya Batishbe, ya faɗa, cewa 'A filin Yezriyel karnuka za su cinye gangar jikin Yezebel,37gangar jikin Yezebel kuma za ta zama kamar ɗan kututture a cikin filaye a ƙasar Yezriyel, domin kada wani ya iya cewa, "Wannan ce Yezebel.'"'
Wannan baya nuna cewa su 'ya'yan annabawa ne, amma a'a, cewa su wani ƙungiya ne na annabawa. Duba yadda zaka fassara wannan kalmar a 2 Sarakuna 2: 3. AT: "ƙungiyar annabawa"
Jumlar "a hannunka" tana nufin ɗaukar kwalbar tare da shi. AT: "tare da kai"
fassarar wannan sunan ɗaya ne da yadda aka fassara shi a 2 Sarakuna 8:28.
Wannan na nufin Yehoshafat mahaifin Yehu ne kuma Nimshi mahaifin Yehoshafat.
Wannan mutane ne da Yehu yake zama da su.
"je tare da shi ka" ko "tafi da shi ka"
"ɗakin sirri"
Marubucin yayi amfani da kalmar “duba” wajen jan kunne zuwa abin da ya biyo baya. Idan kana da hanyar yin hakan cikin yaren ku, zaku iya amfani dashi anan.
Yehu kuwa yana zaune yana ɗaya daga cikin hafsoshin. Kuna iya gabatar da Yehu zuwa layin labarai anan idan wannan ya zama dole cikin yaren ku. AT: "Yehu da wasu hafsoshin sojoji suna zaune tare"
Kalmar "mu" na nufin Yehu da sauran hafsoshin sojoji.
Saurayin annabin ya ci gaba da faɗawa Yehu, wanda aka shafe shi a matsayin sarkin Isra'ila.
Anan "jinin" annabawan da bayin yana nufin mutuwar su. AT: "Zan iya ɗaukar fansar mutuwar bayina annabawa da dukan bayin Yahweh" ko "don in azabta su saboda kisan bayina annabawa da kuma dukkan bayin Yahweh"
Za'a iya samar da kalmomin da aka fahimta. AT: "ɗauki ramakon jinin"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "wanda Yezebel ta umarci barorinta su yi kisan" ko "wanda Yezebel ya ba da umarnin kisansa"
Wannan na nufin Yezebel ta ba da umarni a kashe mutanen nan. AT: "faɗi daga Yezebel" ko "ta umarnin Yezebel"
Anan don "yanke" yana nufin a kashe. AT: "Gama dukkan gidan Ahab zai halaka, kuma zan sa a kashe kowane ɗa na cikin danginsa" ko kuma "Kowane ɗayan cikin gidan Ahab zai mutu, gami da kowane ɗa namiji"
Ana amfani da wannan kalmar don nunawa ga kowane namiji, amma yana ƙayyade "yaro" don jaddada cewa ya haɗa da yara. AT: "kowane namiji"
Saurayin annabin ya ci gaba da faɗa wa Yehu maganar Yahweh wanda ya naɗa ya zama sarkin Isra'ila.
Wannan yana nufin cewa Allah zai hallakar da Ahab da iyalinsa kamar yadda ya hallaka Yeroboam da Ba'asha da danginsu. AT: "Zan kawar da gidan Ahab kamar yadda na kawar"
Ana amfani da wannan kalmar a cikin wannan ayar sau uku. Kowane lokaci, kalmar "gidan" tana nufin "dangi" mutumin da aka ƙayyade. AT: "iyalin"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan na nufin karnuka za su ci gawar Yezebel. AT: "karnuku za su ci gawar Yezebel"
Wannan na nufinn ofisoshin da suke bautar sarki Ahab.
"marar hankali"
Yehu ya ce shi saurayin annabi ne kuma duk sun san nau'ikan abubuwan da annabawan samari ke fadi. AT: "Kun san irin abubuwan da annabawan saurayi kamarsa suke faɗi"
"gaya mana abinda yake cewa"
"ya yi magana game da wani abu"
A cikin wannan al'ada, sanya sutura a ƙasa wata hanya ce ta girmama sarki, don ƙafafunsa ba su taɓa ƙazantar da ƙasa ba. AT: "ya tuɓe rigunansu na cikin ya sa a gaban Yehu don ya ci gaba"
Ba kowane mutum ne ke busa kaho ba. Wataƙila mutum ɗaya ne kaɗai ke busa ƙaho. AT: "wani ya busa ƙaho kuma dukansu suka ce"
Fassara sunan wannan mutumin kamar yadda kayi a 2 Sarakuna 9:1.
Wannan kalmar ana amfani da ita anan don alamar hutu a cikin babban labarin labarin. Anan marubucin ya faɗi bayanin asalin yadda Yoram ya ji rauni kuma ya tafi ya murmure a Yezriyel.
Waɗannan suna magana ne kawai da rundunar Isra'ilawa, ba ga kowane mazaunan Isra'ila ba. AT: "shi da sojojinsa" ko "shi da sojojin Isra'ila"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "don murmurewa daga"
Wannan ya nuna yana rauni a cikin yaƙi tare da Aramiyawa. AT: "raunukan da Yoram ya samu yayin yaƙin tare da sojojin Aram"
Wannan na nufin Hazayel da sojojinsa. AT: "yaƙi da Hazayel sarkin Aram da sojojinsa"
Fassara sunan wannan mutumin kamar yadda ka fassara a 2 Sarakuna 8:7.
Wannan yana nufin sojoji waɗanda suke tare da Yoram ne a Ramot Giliyad.
"Idan kun yarda da ni" Yehu ya yi amfani da wannan kalmar wajen magana idan mutane suna goyon bayan shi sarki kuma ya yanke shawara. AT: "Idan da gaske kuna son in zama sarkin ku"
Wannan yana nufin gaya wa Yoram da rundunarsa na shirin Yehu. AT: "don faɗakar da sarki Yoram da rundunarsa a Yezriyel"
Ana amfani da kalmar "yanzu" a nan don alamar hutu a cikin babban labarin. Anan marubucin ya faɗi bayanin asalin game da Ahaziya wanda ya ziyarci Joram.
''mai gadi''
''Yehu da mutanensa tun suna da nisa''
Yehu yayi amfani da wannan tambayar don gaya wa manzon cewa ba damuwarsa ba idan ya zo cikin salama ko a'a. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Ba damuwa ku idan na kasance cikin salama!" ko "ba a gare ku ku san ko na zo cikin salama ba!"
Mai tsaro ya faɗa wa sarki Yoram cewa mutumin da ya aiko ba ya zuwa tare da martani ga tambayar sarki.
"Sai sarki Yoram ya aiki manzo na biyu, wanda yake a kan doki, wanda ya tafi ya tarye Yehu da sojojinsa"
Yoram ya riga ya aiki mutum ɗaya. Wannan shine na gaba. AT: "mutum na 2"
Wannan na iya bayyana cikin tsari mai aiki. AT: "Domin direban karusai yake tuƙi kamar yadda Yehu ɗan Nimshi yake tuƙa"
"kowane a cikin karusarsa"
"Lokacin da suka isa wurin Yehu, ya kasance a"
Wannan sunan na mutum ne.
Wannan na nufin mutum daga Yezriyel
Yehu yayi amfani da wannan tambaya don nuna dalilin da ya sa bai shigo lafiya ba. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ba za a sami kwanciyar hankali ba muddin mahaifiyar Yezebel ta aikata kuma tana ba da bautar gumaka sosai ta hanyar karuwanci da maita."
"ya juya karusarsa ya yi ƙoƙarin tserewa"
cuta ko yaudara
"da dukkan ƙarfin sa" ko "da dukkan ikon sa"
Yoram ya mutu sakamakon harbi da kibiya. AT: "Yoram ya faɗi a cikin karusarsa"
Wannan sunan na mutum ne.
"ciro gawarsa ya jefar" ko "ɗauki gawarsa ya jefar"
"tunawa"
Wannan yana nuna cewa sun hau cikin karusar a bayan karusar Ahab. AT: "a bayan karusar mahaifinsa Ahab"
"Yahweh ya faɗi wannan annabcin a kan Ahab"
A nan "jini" na nufin "kisan kai" AT: "kisan Nabot da kisan 'ya'yansa"
Wannan yana nufin zai azabtar da Ahab kamar yadda ya cancanci masifar da ya aikata. AT: "Zan ba ku abinda kuka cancanci muguntar da kuka yi"
"ciro gawar Yoram ku jefar dashi a wannan filin, filin Nabot"
"domin cika annabcin da aka yi mana magana"
Ga abin da ya faru da Ahaziya, sarkin Yahuda, bayan Yehu ya kashe Yoram.
"duba abinda ya faru da Yoram"
Wannan sunayen wurare ne.
Kalmar "kusa" yana nufin cewa sun hau tudu yayin tafiya akan hanyar Gur. AT: "akan hanyar zuwa Gur"
"kakaninsa"
Wannan yana bayanin lokacin da Ahaziya ya fara sarauta ta wurin faɗi tsawon lokacin da sarkin Isra'ila na yanzu yake mulki. AT: "A shekara ta goma sha ɗaya ta sarautar Yoram ɗan Ahab ya zama sarkin Isra'ila"
''shekara 11''
"sa kayan kwalliya, sa kanta ya kyan gani"
Yezebel ta yi amfani da wannan tambaya don tuhumar Yehu da bai zo cikin salama ba. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Babu shakka kun shigo cikin aminci, ya kai Zimri, mai kisan shugabanka!"
Anan Yezebel ta kira Yehu "Zimri" don ta ce shi mai kisan kai ne. Zimri shi ne shugaban sojojin Isra'ila wanda ya kashe sarkin Isra'ila saboda yana son ya zama sarki. AT: "kun kashe shugabanka, kamar yadda Zimri ya kashe shugabansa"
Wannan sunan na mutum ne.
Kasancewa "ta kasance tare da wani" yana nufin kasancewa da aminci a gare su da tallafa musu. AT: "Wanene mai aminci a gare ni"
Yehu yana gaya wa babanni ya jefa Yezebel ta taga.
Sai bãbã suka jefa Yezebel waje ta sakata ta mutu da ta bugi ƙasa.
Wannan yana nuna cewa ya hau dawakansa a jikin ta. AT: "Dawakan Yehu waɗanda suke jan karusarsa suna tattake gawarta a ƙafafunsu"
Kalmomin "gani yanzu don" yana nufin a ba da hankalin ku ga duk abin da aka ƙayyade. AT: "Yanzu je wurin"
Tunda Yezebel 'yar sarki ce, ya wajaba a binne ta yadda ya kamata. AT: "saboda ita 'yar sarki ce don haka ya kamata a binne ta yadda ya kamata" (Duba: )
"ba su sami gangar jikinta ba" Wannan za a iya bayyana shi da kyau. AT: "duk abin da suka iske jikin ta sun kasance"
tafi hannun shine ɓangaren ciki na hannu.
Wannan na nufin wani daga garin Tishbe.
Wannan na maganar gudawar Yezebel ta watse cikin saura kamar suna digo ne a gona. Tunda sassan jikinta sunyi kankanta kuma suka shimfiɗa babu wani abu da za'a tattara kuma za'a binne shi. AT: "jikin Yezebel za a gutsuttsura shi a zubar kamar kashi a saura, yadda ba wanda zai gane yace."
"taki" wannan na magana da kashi da ake amfani dashi a matsayin taki.
"domin babu wanda zai iya sanin jikinta." ko "saboda haka ba wanda zai iya faɗi wannan Yezebel."
1Ahab yana da zuriya saba'in a Samariya. Yehu ya rubuta wasiƙu ya aika da su Samariya, ga shugabannin Yezriyel, haɗe da dattawa da 'yan tsaro na zuriyar Ahab, cewa,2"Zuriyar shugabanku na tare da ku, kuma kuna da karusai da dawakai da ƙayatattun birane da makamai.3Domin haka da zarar wannan wasiƙa ta same ku, sai ku zaɓi wanda yafi cancanta daga cikin zuriyar shugabanku ku ɗora shi akan gadon sarautar mahaifinsa, ku kuma yi yaƙi domin gidan sarautar shugabanku."4Amma suka tsorata suka ce da junansu, "Duba sarukuna biyu ma ba su iya ja da Yehu ba. To yaya zamu iya ja da shi?"5Daga nan sai wanda ke shugabantar fãdar, da mai kula da birnin da kuma dattawan da kuma masu renon yara, suka sake mayar da magana ga Yehu, cewa, "Mu bayinka ne. Za mu yi duk abin da ka umarce mu. Baza mu naɗa kowa a matsayin sarki ba. Ka yi abin da ka ga ya yi maka kyau a idanunka."6Sai Yehu ya rubuta wasiƙa ta biyu zuwa gare su, cewa, "In kuna tare da ni, in kuma za ku ji muryata, dole ne ku ɗauko wanda yake shi ne shugaban zuriyarku ku zo da shi Yezriyel gobe war haka." To sai zuriyar sarkin, su saba'in, suka zama manyan mutane masu daraja a birnin waɗanda suke kula da su7To da wasiƙa ta zo gare su, sai suka kama 'ya'yan sarki suka karkashe su, mutane saba'in, suka ɗauki kawunansu suka aikawa da Yehu a Yezriyel.8Sai manzo ya zo wurin Yehu, ya ce, "Sun kawo kawunan 'ya'yan sarki maza." Sai ya ce ku ajiye su a mazubin a ƙofar shiga har sai gari ya waye."9Da safe sai Yehu ya fito ya tsaya ya ce da dukkan mutane, "Ba ku da laifi. Na shirya makirci kan shugabana na kuma kashe shi, amma wane ne ya kashe dukkan waɗannan?10To yanzu sai ku san cewa ba wani sashe na maganar Yahweh, da aka faɗa game da gidan Ahab, da zai faɗi ƙasa, domin Yahweh ya yi abin da ya faɗa ta bakin bawansa Iliya."11Sai Yehu ya karkashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezriyel, ya kuma kashe mutanensa masu muhimmanci, da abokansa na ƙut da ƙut, da firistocinsa, har ta kai ga ba wanda ya ragu.12Sai Yehu ya tashi ya tafi; ya tafi zuwa Samariya. Da ya je Bet Eked ta makiyaya,13sai ya tarar da 'yan'uwan Ahaziya sarkin Yahuda. Yehu yace da su "Ku su wane ne?" Suka ce, "Mu 'yan'uwan Ahaziya ne, kuma zamu mu gai da 'ya'yan sarki ne da kuma 'ya'yan Sarauniya Yezebel."14Yehu ya ce da mutanensa, "Ku kama su da ransu." Sai suka kama su da ransu suka karkashe su a ramin Bet Eked, dukkan mutanen arba'in da biyu ne. Bai bar ko ɗaya daga cikinsu da rai ba.15Da Yehu ya bar wurin, sai ya tarar da Yonadab ɗan Rekab yana zuwa domin ya same shi. Yehu ya gaishe shi ya ce da shi, "Ko zuciyarka na tare da ni, kamar yadda zuciyata ke tare da taka?" Yonadab ya amsa, "Tana nan." Yehu ya amsa, "In tana nan, ka ba ni hannunka." Sai Yonadab ya ba shi hannunsa, sai Yehu ya ɗauke shi a cikin karusarsa.16Yehu ya ce, "Ka zo tare da ni ka ga himmata domin Yahweh." Sai ya tafi da Yonadab yana tuƙi tare da shi a karusarsa.17Da ya zo Samariya, sai Yehu ya karkashe duk waɗanda suka ragu daga zuriyar Ahab a Samariya, har sai da ya kashe duk wani mai jinin sarauta na iyalin Ahab, kamar dai yadda maganar Yahweh ta faɗa ta wurin Iliya.18Sai Yehu ya tattara dukkan mutane wuri ɗaya ya ce da su, "Ahab ya bauta wa Ba'al ɗan kaɗan, amma Yehu ya fi bauta masa ya yawa.19To yanzu sai ku kirawo mani dukkan annabawan Ba'al, da duk masu bautarsa, da duk firistocinsa. Kar ku rage ko da guda ɗaya, domin ina da babbar hadaya da zan miƙa ga Ba'al. Duk wanda bai zo ba za, a kashe shi." Amma Yehu ya yi wannan yaudarar ne domin ya kashe duk masu bauta wa Ba'al.20Yehu yace, "Ku shirya lokaci da za mu yi taruwa domin Ba'al." Domin haka suka yi sanarwar ta.21Sai Yehu ya aika a ko'ina cikin dukkan Isra'ila sai duk masu bautar Ba'al suka zo, har ba waninsu da bai zo ba. Suka zo masujadar Ba'al, ta kuma cika maƙil.22Yehu yace da mutane masu, kula da ma'ajiyar kayan firistoci, "Ku fito da tufafi domin duk masu bautar Ba'al." Sai mutumin ya fito da tufafi dominsu.23Sai Yehu ya tafi tare da Yonadab ɗan Rekab zuwa gidan Ba'al, ya ce da masu bautar Ba'al, "Ku bincika ku tabbatar cewa ba wani daga cikin masu bautar Yahweh a cikinku, amma sai dai masu bautar Ba'al kaɗăi."24Sai suka shiga domin su miƙa hadayu da baiko na ƙonawa. Sa'an nan Yehu ya zaɓi mutane tamanin da ke tsaye a waje, ya ce da su, "In wani ya bar mutanen nan da na kawo ya kuɓuta to a bakin ransa, zan kashe wanda ya yi sakaci har wani ya gudu a madadin wancan da ya gudu."25To nan da nan da Yehu ya gama miƙa hadaya da baiko na ƙona wa, ya ce da 'yan tsaro da hafsoshi, "Ku shiga ku kashe su. Kar ku bar wani ya fito waje." Domin haka suka karkashe su da kaifin takobi, da 'yan tsaro da hafsoshin suka jejjefar da su waje suka shiga can ƙuryar ɗakin gidan Ba'al.26Suka mummurgina duwatsun ginshiƙan gidan Ba'al suka ƙone su.27Suka kuma kakkarya ginshiƙan Ba'al, suka hallakar da gidan Ba'al suka mayar da shi makewayi wanda har yanzu haka wurin ya ke.28Da haka Yehu ya hallakar da bautar Ba'al daga Isra'ila.29Amma Yehu bai ƙyale zunubin Yerobowom ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi - wato bautar ɗan maraƙin zinariya a Betal da Dan.30Domin haka Yahweh yace da Yehu, "Saboda ka yi abin da ke dai dai a idona, ka kuma iy wa gidan Ahab gwargwadon abin da ke a zuciyata, zuriyarka zasu yi mulkin Isra'ila har ya zuwa tsara ta huɗju."31Amma Yehu bai da muya yi tafiya bisa tafarkin Yahweh, Allah na Isra'ila, da dukkan zuciyarsa ba. Bai kuma bar zunubinYarobowam ba, ta haka ya sa Isra'ila yin zunubi.32A waɗancan kwanakin Yahweh ya fara yanke sassa daga Isra'ila, sai Hazayel ya ci Isra'ila akan iyakokin Isra'ila,33daga gabashin Yodan, dukkan ƙasar Giliyad da ta Gadiyawa da ta Rubenawa da ta Manassawa, daga Arowa wadda ke a Kwarin Arno har ya zuwa Giliyad da kuma zuwa Bashan.34Game kuma da sauran abubuwa game da Yehu, da kuma duk abin da ya yi da dukkan ikonsa, ashe ba a rubuta su a cikin ayukan sarakunan Isra'ila ba?35Yehu ya yi barci tare da ubanninsa, suka kuma bizne shi a Samariya. Sai Yehoahaz ɗansa ya zama sarki a madadinsa.36Tsawon lokacin da Yehu ya yi mulkin Isra'ila a Samariya shi ne shekaru ashirin da takwas.
''zuriya 70''
Wannan yana nuna cewa Yehu ya aiki manzo don isar da haruffan. AT: "Yehu ya rubuta wasiƙu ya aika da wani manzo don ya aika da su a Samariya"
wasiƙun ya cewa "shugabanku "
Anan, zama a kan kursiyin sarki yana nufin a nada shi sarki. AT: "ku naɗa shi sarki a matsayin mahaifinsa"
"Amma suka tsorata kwarai da gaskiya"
"sarukuna biyu , Yoram da Ahaziya"
Anan "tsayawa" yana nufin samun ikon jimrewa a lokacin wahala. AT: "ba zai iya jure wa Yehu ba" ko "ba zai iya tsayayya da Yehu ba"
Zuriya sun yi amfani da tambaya don nuna cewa ba za su iya tsayayya da Yehu ba. AT: "Ba za mu iya tsayayya da shi ba ko ɗaya!" ko kuma "Ba za mu iya tsayayya da shi ba!"
lokaci ta 2"
Kasancewa "tare da wani" yana nufin kasancewa da aminci a gare su da tallafa musu. AT: "amintacce a gare ni"
ku ji ku yi biyayya
Anan "muryar" Yehu tana nufin abin da yake faɗi. AT: "ga abin da nake faɗi"
Wannan yana nufin kashe su da cire kawunansu. AT: "ku kashe zuriyar shugabanku ku kuma yanke kawunan ku"
Wannan yana nuna cewa suna kulawa da su kuma suna koya masu. AT: "wanda ke kiwon su" ko "waɗanda ke lura da su"
Wannan yana nuna cewa sun aiko mutane ne don isar da kwandunan. AT: "Ya aika mutane su kai su Yehu"
"na zuriyar Ahab"
"Yehu ya fito zuwa ƙofar shiga gari ya tsayaa gaban mutanen"
Za a iya bayyana a fili abin da ba su da laifi daga. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) "Ba ku da laifi game da abin da ya faru da Yoram" ko 2) wannan yana nuna cewa ba a ɗauki alhakin mutuwar iyalin Yoram ba. AT: "Ba ku da laifi game da abin da ya faru da Yoram da iyalinsa" ko "Ba ku kuɓuta daga wannan batun ba"
Yehu ya yi amfani da wannan kalma a nan don jawo hankalin mutane don mai da hankali ga abin da ya faɗi a gaba. AT: "Ji" ko "Ji maganata "
Yehu ya yi amfani da tambaya don sa mutane su yi tunani sosai game da lamarin. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) AT: "amma mutanen Samariya suna da alhakin kashe zuriya 70 na Ahab" ko 2) AT: "amma nufin Yahweh ne na waɗannan mutanen su mutu"
"fahimta" ko "zama sane da gaskiyar cewa"
Wannan yana maganar duk abin da Yahweh ya faɗa zai faru kamar dai abu ne wanda bai mutu ba ya faɗi ƙasa. AT: "Babu wani ɓangaren kalmar Yahweh ... da zai faɗi" ko "kowane sashin maganar Yahweh ... zai faru"
Wannan yana magana game da Yahweh wanda ya sa aka kashe zuriyar Ahab kamar ya kashe su da kansa. AT: "Yahweh ne ya sa abin ya faru"
Wannan yana nuna cewa duk an kashe su. AT: "har sai an kashe su duka" ko "har sai dukkan su sun mutu"
Wannan shi ne wurin da ake kiwon tumaki.
"zuwa ziyara"
'ya'yan sarki Ahaziya
Wannan yana nufin kama su, amma ba kashe su ba. AT: "Ku kama su" ko "Kama su"
Wannan za a iya bayyana shi da kyau. AT: "Ya kashe su dukka"
Wannan sunan mutum ne.
Anan “zuciyar” mutum tana nufin amincin su. Idan amincin mutum yana tare da wani, wannan yana nuna cewa suna da aminci ga mutumin. AT: "Shin za ku kasance da aminci a gare ni, kamar yadda zan kasance amintacce a gare ku? ... 'Zan yi.'"
"Idan haka ne, sanya hannunka a cikin nawa" ko "Idan haka ne, bari mu girgiza hannu." A cikin al'adu da yawa, lokacin da mutane biyu suka girgiza hannu, yana tabbatar da yarjejeniyarsu.
Kalmar "himma" za a iya bayyana azaman ƙiba. AT: “ga yadda nake kishin gaskiya”
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "don cika annabcin da Iliya ya faɗi, wanda Yahweh ya yi masa"
"ya kirawo dukkan mutane kuma ya kawo su inda yake"
"bauta masa da yawa fiye da Ahab"
Wannan yana nuna cewa idan basu zo ba za'a kashe su. AT: "Zamu zartar da duk wanda bai zo ba"
Wannan yana nufin tsarawa da shirya wani lokaci don wani abu. Don haka za su shirya wa Ba'al taro. AT: "Shirya"
Wannan yana nuna cewa ya aiko da manzannin su dauki wannan sako a duk fadin kasar. AT: "Sai Yehu ya aiko da manzannin" ko "Sai Yehu ya aiko da saƙo"
Wannan za a iya bayyana shi da kyau. AT: "shi ya sa kowane mai bauta wa Ba'al ya kasance a wurin" ko kuma "kowane mutum ya zo"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "sun cika shi"
Anan "don kiyaye" wani abu yana nufin kulawa da shi da kuma kulawa da shi. AT: "wanda ke lura da rigar firist" ko kuma "wanda ya kula da tufafin firist"
"Yehu yace da matanen da ke cikin haikali bautar Ba'al"
"amma kawai masu bautar Ba'al suke nan"
Anan "hannayen" maza suna magana akan "sarrafawa". Ta hanyar kasancewa a kusa da haikalin suna cikin kulawa da halin da ake ciki kuma yana kan su ko mutane sun sami damar tserewa ko a'a. AT: "Idan ɗayan waɗannan mutanen da na kawo muku ikon tserewa" ko "Idan kowane ɗayan mutanen da ke cikin ya tsere"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. Wannan ita ce hanya mai ladabi don nuna mutumin da aka kashe. AT: "Zamu dauki ransa" ko kuma "za mu kashe shi"
Wataƙila kuna buƙatar bayyana cewa Yehu ya fito daga haikalin kafin ya yi magana da mai tsaron. AT: "ya koma waje da haikalin Ba'al ya ce wa masu tsaro da hafsoshi"
Mutanen suka yi amfani da takobi don kashe masu bautar Ba'al. Wannan magana tana nufin takobinsu. AT: "da takobinsu"
Wannan yana nufin jefa gawawwakin mutane daga haikalin. AT: "sun jefar da gawawwakinsu daga haikalin"
"sanya shi ɗakin bayan gida". Wurin bayan gida shi ne gidan wanka, ko kuma wurin bayan gida, yawanci don zango ko gine-ginen da ake amfani da su don sojoji.
Wannan yana maganar Yehu yana yin irin zunubin da Yerobowam ya yi, kamar dai zunuban zunubin Yehu bai bar wurin ba. AT: "bai daina aikata irin zunuban da Yerobowam ɗan Nebat ya yi ba"
Anan "Isra'ila" na nufin mutane da ke zama a wurin. AT: "zunubin mutanen Isra'ila"
"ka yi abin" ko "aiwatar"
Idanu suna wakiltar gani, da gani suna wakiltar tunani ne ko hukunci. AT: "abin da na yanke hukunci dai-dai ne" ko "abin da na ga dai-dai ne"
Wannan yana nufin dansa, jikan, jikan, kuma jikan. AT: "zuwa tsara ta 4" ko "don ƙarin ƙarni huɗu"
Anan "tafiya" yana nufin "rayuwa." AT: "Yehu bai mai da hankali ya yi rayuwa bisa ga dokar Yahweh ba"
Don "nisanta" daga wani abu na nufin dakatar da aikata shi. AT: "Yehu bai daina yin zunubi a cikin hanyoyin guda ɗaya kamar na Yerobowam ba"
"ya fara sa yankin da Isra’ila ke iko da shi ya zama ƙarami”
"sassa na kasa"
Anan "Hazayel" yana nufin kansa da sojojinsa. AT: "Hazayel da sojojinsa" ko "Sarki Hazayel da sojojinsa na Aramiyawa"
"daga kasar da ke gabashin Yodan"
Waɗannan sunayen wurare ne.
Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin bayani. Duba yadda aka fassara wannan magana a cikin 2 Sarakuna 1:18. AT: "An rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila."
Wannan yana nuna cewa Jehu ya mutu. Wannan yana magana akan binne shi inda aka binne kakanninsa kamar yana bacci tare da su. AT: "Yehu ya mutu, suka binne shi a Samariya, inda suka binne kakanninsa" wannan na nufin Yehu ya mutu. wannan na bayani ne da cewa an binne shi da kakaninsa.
wannan sunnan mutum ne
"Yehu ya yi sarautar Isra'ila a Samariya shekara ashirin da takwas"
"shekaru 28"
1To da Ataliya, mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta kashe duk 'ya'yan gidan sarauta.2Amma Yehosheba, 'yar sarki Yahoram da 'yar'uwar Ahaziya, ta ɗauki Yo'ash ɗan Ahaziya ta ɓoye shi daga cikin 'ya'yan sarki waɗanda aka kashe, tare da mai renonsa; ta sa su a ɗakin kwana. Suka ɓoye shi domin kada Ataliya ta gan shi ta kashe shi.3Yana tare da Yahosheba a ɓoye a gidan Yahweh har tsawon shekaru shida, a lokacin da Ataliya ke sarautar ƙasar.4A shekara ta bakwai, Yeho'iada ya aika da saƙonnin ya kuma fito da kwamandojin na ɗari-ɗari na Karitawa wato wata ƙungiyar mayaƙa ta gidan sarauta da 'yan tsaro ya kawo su wurinsa, cikin haikalin Yahweh. Ya yi yarjejeniya da su, ya kuma sa su su rantse a gidan Yahweh. Daga nan sai ya nuna musu ɗan sarki.5Ya umarce su, da cewa, "Wannan shi ne abin da tilas za ku yi. Kashi uku daga cikinku waɗanda ke zuwa da ranar Asabaci za su yi tsaron gidan sarki,6kashi uku su tsaya a Ƙofaf Sur, kuma kashe uku su tsaya a ƙofar bayan gidan 'yan tsaro."7Sauran ƙungiyoyin guda biyu da ba ku yin hidima da ranar asabar, dole ne ku yi tsaron gidan Yahweh domin sarki.8Dole ne ku kewaye sarki kowanne mutum da makaminsa a hannunsa, duk wanda ya shigo wurinku sai ku kashe shi. za ku kasance tare da sarki a lokacin da ya fita da lokacin da ya dawo ciki.9Sai kwamandojin ɗari-ɗari suka yi biyayya da duk abin da Yeho'iada ya firist ya ba da umarni. Kowannen su ya ya kwashi mutanensa, waɗanda ke zuwa hidima da Asabaci, da waɗanda ke zuwa daina hidima da Asabaci; suka zo wurin Yeho'iada firist.10Sai Yeho'iada firist ya ya ba kwamandojin ɗari-ɗari mãsu da garkuwoyi na sarki Dauda da kuma waɗanda ke gidan Yahweh.11Saboda haka 'yan tsaron suka tsaya, kowanne da makaminsa a hannunsa, daga gefen dama na haikalin zuwa gefen hagun na haikalin, kusa da bagadi da kuma haikalin, suna kewaye da sarki.12Sai Yeho'iada ya kawo ɗan sarki Yo'ash, ya sa masa kambi a kansa, ya kuma ba shi sharruɗan yarjejeniya. Sai suka naɗa shi sarki suka kuma shafe shi da mai. Suka tafa hannuwansu suka ce, "Ran sarki ya daɗe!"13Da Ataliya ta ji hayaniya ta 'yan tsaro da ta mutane, sai ta zo wurin mutane a gidan Yahweh.14Tana dubawa sai ga sarki a tsaye a jikin ginshiƙin, kamar yadda al'adar ta ke, da hafsoshi da masu hura ƙahonni na tare da sarki. Dukkan mutanen ƙasar na murna suna hura ƙahonni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta yi ihu tana cewa, "Cin amanar ƙasa! Cin amanar ƙasa!"15Sai Yeho'iada firist ya bada umarni ga kwamandoji na ɗari ɗari masu shugabantar sojojin cewa, "Ku kawo ta a tsakanin rundunarku. Kuma duk wanda ya biyo ta, ku kashe shi da takobi. Domin firist ya ce, "Kada ku kashe ta a gidan Yahweh."16Domin haka suka ja ta da ta kai dai dai inda dawakai ke shiga wurin 'yan tsaron fãda a can aka kashe ta.17Sai Yeho'iada firist ya yi yarjejeniya da tsakanin Yahweh da sarki da kuma mutane, cewa za su zama mutanen Yahweh, hakannan kuma tsakanin mutane da sarki.18Domin haka dukkan mutanen ƙasar suka tafi gidan Ba'al suka rurrushe shi. Suka bubbuge bagadin Ba'al da gumakansa rugu rugu, suka kuma kashe Mattan firist na Ba'al a gaban bagadojin. Sai Yeho'iada firist ya naɗa 'yan tsaro a haikalin Yahweh.19Sai Yeho'iada ya kwashi kwamandojin ɗari ɗari da Karitiyawa, mayaƙan fãda, da 'yan tsaro, da dukkan mutanen ƙasar tare suka ka kawo sarki daga gidan Yahweh suka tafi gidan sarki ta hanyar ƙofar 'yan tsaro. Sai Yo'ash ya hau gadon sarauta.20Domin haka duk mutanen ƙasar suka yi murna, sai birnin ya sami kwanciyar hankali bayan an kashe Ataliya da takobi a gidan sarki.21Yo'ash yana da shekaru bakwai a lokacin da ya fara sarauta.
"ya zama sane cewa ɗanta ya mutu"
Ataliya bai kashe yaran da kansu ba. AT: "Ta umarci barorinta su kashe duk mutanen gidan Ahaziya wanda zai iya zama sarki"
"ta ɗauki Yo'ash ƙaramin ɗan Ahaziya, ya ɓoye shi da baiwarta a cikin ɗakuna a haikali. Don haka ba a kashe shi ba"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Yowash da Yehosheba sun ɓoye shi a cikin gidan Yahweh tsawon shekaru shida yayin da Ataliya ta mallaki ƙasar"
An ci gaba da labarin abin da ya faru bayan an ɓoye Yowash ɗan sarki Ahaziya a cikin haikalin bayan an kashe sauran zuriyar Ahaziya.
"A shekara ta bakwai na mulkin Ataliya " ko a shekara ta bakwai da Ataliya ke mulki"
babban firist
Kalmomin "kwamandojin na ɗari-ɗari " wataƙila lakabi ne na babban jami'in sojan sama. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) kalmar "ɗaruruwan" tana wakiltar dai-dai adadin sojojin da kowane ɗaya daga cikin waɗannan shugabannin ya jagoranta. AT: "kwamandojin sojoji 100" ko 2) kalmar da aka fassara a matsayin "ɗaruruwan" ba wakiltar adadi dai-dai bane, amma sunan rukunin sojoji ne. AT: "kwamandojin rundunonin soja"
Wannan sunan wani rukunin masu tsaron sarki ne.
Yeho'iada babban firist ya sa sojojinsa su zo wurin sa a haikali. AT: "ya kawo su wurinsa cikin haikalin Yahweh"
Sai Yeho'iada ya faɗa musu ɗan Yowash ɗan sarki, yana da rai.
Yeho'iada ya ci gaba da ba da umurni ga sojojin da za su kāre Sarki Yowash.
Dole ne su yi tsaro don manufar kare sarki daga cutarwa. AT: "don kare sarki Yowash"
"Duk wanda yayi ƙoƙari ya wuce ka yayin da kake kare Sarki Yowash." Matsayi yana nufin layin sojoji.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "dole ne ku kashe shi"
Waɗannan abubuwa guda biyu nuni da duk abin da sarki yake yi. AT: "Dole ne ku kasance kusa da sarki koyaushe"
"Kowane kwamanda"
"waɗanda ke ajiye gidan Yahweh"
Yeho'iada babban firist ya kawo Yowash ɗan sarki Ahaziya, daga cikin haikali inda aka yi rainonsa a ɓoye
"ya gabatar masa da littafin doka"
Firist ɗin ya zuba mai a kan Yowash kamar yadda alama ce ta sarki yanzu. AT: "zuba wani mai na zaitun a kan Yowash"
Wannan yana nufin hayaniyar da sojoji duka ke yi.
"ta zo inda mutane suka taru a haikali"
"Lokacin da ta iso, ta yi mamakin ganin Sarki Yowash a tsaye"
"a jikin ginshiƙin na cikin haikali"
"wanda shine wurin da sarki ya saba zama"
Ta yayyage tufafin ta don ta bayyana cewa tana matukar fushi da fushi.
"Ku mayaudara ne! Kun ci amanar ni!"
An ɗauka cewa mutumin da ya bi ta yana ƙoƙarin taimaka mata. AT: "Duk wanda ya bi ya yi ƙoƙarin kubutar da ita"
Wasu juyi sun fassara wannan kamar yadda "masu gadi suka kama ta suka dauke ta zuwa fada, zuwa wurin da dawakai suka shiga farfajiyar.
"ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da jama'a"
Wannan jeri ne na nuna cewa gungun mutane sun rushe haikalin Ba'al. AT: "adadi mai yawa na mutanen ƙasar"
"haikalin Ba'al"
Wannan sunan wani firist na miji ne.
Suna ɗauke da sabon sarki, Yowash, daga haikali zuwa fāda.
suka ka kawo sarki daga haikali zuwa gidansa
"birnin yana cikin nutsuwa" ko "birnin yana cikin kwanciyar hankali"
"Yowash yana da shekaru 7"
1A shekara ta bakwai ta Yehu, sarautar Yo'ash ta fara; ya yi sarauta tsawon shekaru arba'in a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ta Biyasheba.2Yoash ya yi abin da ke nagari a gaban Yahweh a dukkan lokaci, saboda Yeho'iada firist yana yi masa gargaɗi.3Amma ba a kawar da manya manya wurare ba. Har yanzu mutane na yin hadaya da ƙona turare a manyan wurare.4Sai Yo'ash yace da firistoci, "Dukkan ƙuɗaɗen da aka kawo a keɓaɓɓen wuri a cikin gidan Yahweh, wannan kuɗin da kuɗaɗen da aka tsara wa mutane - ko kuɗin da aka karɓa a wurin ƙidaya ne, ko kuma kuɗin da aka karɓa saboda wa'adi ne, ko kuma kuɗin da aka tara ta wurin yadda Yahweh ya zuga mutanensa -5sai firistoci su karbi kuɗin daga ɗaya daga cikin ma'ajiyarsu su gyara duk wata ɓarna da suka gani a cikin haikali."6Amma a shekara ta ashirin ta sarautar sarkin Yo'ash, firistoci ba su gyara komai ba a cikin haikalin.7Sai sarki Yo'ash ya kira Yeho'iada firist da kuma sauran firistoci, ya ce da su, "Meyasa baku gyara komai a cikin haikalin ba? To yanzu kada ku ƙara ɗaukan kuɗi daga masu biyan harajinku, amma ku ɗauki wanda aka karɓa ku ba waɗanda za su yi gyaran haikalin."8Sai firistoci suka yarda cewa ba za su ƙara karɓar kuɗi daga wurin mutane domin gyaran haikali da kansu ba.9A maimakon, Yeho'iada firist ya ɗauki mazubi ya yi masa huduwa a ƙasa, ya ajiye shi kusa da bagadin, daga gefen dama dai-dai inda mutane ke shiga gidan Yahweh. Sai firistoci da ke kula da ƙofar shiga haikalin suka zuba dukkan kuɗin da aka kawo gidan Yahweh.10Da zarar sun ga akwai kuɗi da yawa a cikin mazubin, sai marubuta na sarki da manyan firistoci su zo su zuba kuɗin a jakkuna sai su ƙirga kuɗin da aka samu a haikalin Yahweh.11Suka ba da kuɗin da aka tattaro daga hannun mutane masu kula da haikalin Yahweh. Suka biya masu aikin katako da magina waɗanda suka yi aiki a haikalin Yahweh,12haka kuma masu sayo katakai da yankawa, da masu sassaƙa duwatsu, domin gyaran haikalin Yahweh, da kuma duk abin da ake bukatar a biya shi.13Amma kuɗin da aka kawo cikin haikalin Yahweh ba a biya domin aikin yin kofin zinariya da fitilu da kwangiri da kakaki, ko kuma duk wani aiki na azurfa ba.14Sun bada kuɗin ga waɗanda suka yi aikin gyaran gidan Yahweh.15Haka kuma, basu bukaci kuɗi domin su biya masu biyan ma'aikata ba, domin waɗannan mutanen suna da aminci.16Amma kuɗin baiko na hadayar laifi da kuma na hadayar zunubi ba a kawo su zuwa cikin haikalin Yahweh ba, domin na firistoci ne.17Sai Hazayel sarkin Aram ya kai hari kan Gat ya kuma kame ta. Sai ya Hazayel ya juyo domin ya kawo hari Yerusalem.18Sai Yo'ash sarkin Yahuda ya ɗauke duk abubuwan da Yehoshafat da Yehoram da Ahaziya mahaifinsa da sarkunan Yahuda suka keɓe, da dukkan zinariya da aka samu a ɗakin ajiya na gidajen Yahweh da na gidan sarki ya aika da su wurin Hazayel sarkin Aram Sai Hazayel ya fita daga Yerusalem.19Game kuma da sauran abubuwa game da sarki Yo'ash da duk abin da ya yi, ashe ba a rubuta su a cikin littafin ayukan sarakunan Yahuda ba?20Sai barorinsa suka tashi suka haɗa kai suka shirya maƙarƙashiya; suka kai hari ga Yo'ash a Bet Millo, a kan hanyar da ta gangara zuwa Silla.21Jozabad ɗan Shimeyet da Yehozabad ɗan Shomar, bayinsa suka kai masa hari, ya kuma mutu. Suka bizne Yo'ash tare da kakanninsa a birnin Dauda, Amaziya, ɗansa ya zama sarki a madadinsa.
"A shekara ta 7 ta mulkin Yehu bisa Isra'ila"
"Yowash ya fara sarautar a Yahuda"
Wannan sunan mace ne.
"Zibiya, daga birnin Biyasheba"
Idanu suna wakiltar gani, da gani suna wakiltar tunani ne ko hukunci. AT: "abin da Yahweh yake hukunci dai-dai ne" ko "abin da Yahweh yake ɗauka dai-dai ne"
"koyar da shi"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Amma mutanen ba su hallakar da wuraren tsafin na tuddai ba"
Yawheh ya hana mutane yin bauta a wannan wuraren. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "Mutane sun ci gaba da zuwa wuraren da ba su yarda da Yahweh, don yin hadayu da ƙona turare"
Wannan yana nufin kuɗin da mutane suka bayar don tallafawa haikalin. Wannan kuɗin ya zo a cikin nau'i uku waɗanda aka bayyana a cikin sauran jumla.
Wannan na nufin kuɗin da mutane suka bayar kyauta ga Yahweh.
"a lokacin da Yowash ya yi sarauta shekara ashirin da uku"
Yowash ya yi wannan tambaya don ya tsauta wa firistoci. AT: "Da yakamata ku kasance kuna gyaran haikalin!"
"biya ma'aikatan da zasu yi gyare-gyare"
"A maimakon firistoci da suka karɓi kuɗin, Yeho'iada"
"daga gefen dama dai-dai inda a ke shiga haikali"
"saka a jakkuna" ko "saka a cikin akwatin"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "kuɗin da mutane suka kawo"
Yawancin juyi suna sanya wannan a cikin tsari mai ma'ana kamar "kirga kuɗin ku saka shi cikin jaka."
"kirga"
Anan "hannaye" suna nufin mazan. AT: "ga maza"
"wanda ya gyara haikalin"
mutanen da suke yin kuma gyara abubuwan da aka yi da itace
mutanen da suka gina tare da dutse
mutanen da suka sare dutse cikin dai-dai gimra da sifa
"biya duk gyaran da ake buƙata"
"ba a kashe don biyan kowane irin haikalin ba"
Waɗannan abubuwa ne da firistoci za su yi amfani da su don hidimomin haikali daban-daban, kamar hadayu ko ɓukukuwa.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ba su nemi mutanen da suka karɓi kuɗin kuma suka biya ma'aikatan don gyaran don yin lissafin kuɗin"
don ajiye lissafin yawan ƙudade da aka karba kuma aka kashe
An ɗauka cewa ba a yi amfani da wannan kuɗin don gyaran ba. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ba su yi amfani da kuɗin don hadaya ta laifi da hadayu na zunubi don biyan diyya don haikalin Yahweh ba"
Wannan yana nufin sojojin Hazayel da kuma Hazayel. AT: "Hazayel, sarkin Aram tare da rundunarsa sun kai hari ... Daga nan sai suka juya zuwa wurin yaƙi"
"sha kashi kuma ya yi iko da shi"
Waɗannan sarakunan Yahuda ne da suka gabata.
"sadaukar"
"zinariya da aka adana a ɗakin ajiya na gidajen"
Kyaututtukan da Yowash ya ba Hazayel sun shawo kansa kada ya kai wa Yerusalem hari. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "Don haka Hazayel ya daina kai wa Yerusalem hari kuma ya tafi"
Ana amfani da wannan tambaya don tunatar da mai karatu cewa an rubuta waɗannan abubuwan. Duba yadda ake fassara wannan kalmar a 2 Sarakuna 8:23. AT: "An rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuda."
Ba a san wurin wannan wurin ba.
Waɗannan sunayen mutane ne.
"a wurin da aka binne kakanninsa"
"ya zama sarki na gaba na Yahuda"
1A shekara ta ashirin da uku na Yo'ash ɗan Ahaziya sarkin Yahuda, Yehoahaz ɗan Yehu ya fara mulki akan Isra'ila da Samariya; ya yi mulkin har tsawon shekaru goma. sha bakwai.2Ya kuwa yi abin mugunta a fuskar Yahweh da bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi; kuma Yehoahaz bai juya baya daga hakan ba.3Fushin Yahweh ya yi ƙuna gãba da Isra'ila, sai ya ci gaba da bada su ga hannun Hazayel sarkin Aram da kuma ga hannun Ben Hadad ɗan Hazayel.4Saboda haka Yehoahaz ya yi kira ga Yahweh, sai Yahweh ya saurare shi domin ya ga danniyar da ake yi wa Isra'ila, yadda sarkin Aram ya ke zaluntarsu.5Don haka sai Yahweh ya ba Isra'ila maceci, sai suka kuɓuta daga ƙasar Aramiyawan, sai mutanen Isra'ila suka fara zama a gidajensu kamar yadda suke a dã.6Duk da haka, ba su kauce daga zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra'ila suka yi zunubi, kuma suka ci gaba a cikin su; kuma gunkiyar Asherah tana nan a Samariya.7Aramiyawan suka bar Yehoahaz da mahayan dawakai hamsin ne kawai da karusai goma da dakarai dubu goma, gama sarkin Aram ya halakar da su kamar ƙaiƙai a lokacin casa.8Akan sauran zantuttukan game da Yehoahaz kuwa, da dukkan abin da ya yi da ikonsa, ba an rubuta su littafin tarihin sarakunan Isra'ila ba?9Sai Yehoahaz ya kwanta tare da kakaninsa, aka kuwa bizine shi a Samariya. Yohoash ɗansa ya zama sarkin da ya gaje shi.10A shekara ta talatin da bakwai na Yo'ash sarkin Yahuda, mulkin Yohoash ɗan Yahoahaz ya fara kan Isra'ila a Samariya; ya yi mulki shekara goma sha shida.11Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh. Bai bar ko wani abu daga zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, ta yadda ya sa Isra'ila ta yi zunubi, amma ya yi tafiya cikinsu.12A batun sauran zantuttukan da suka shafi Yohoash, da dukkan abin da ya yi, da ikonsa ta yadda ya yaƙi Amaziya sarkin Yahuda, ba an rubuta su cikin littafin tarihin sarakunan Isra'ila ba?13Yohoash ya kwanta tare da kakaninsa, sai Yerobowam ya zauna a kursiyinsa. An bizne Yohoash a Samariya tare da sarakunan Isra'ila.14Sai Elisha ya yi rashin lafiya da ciwon da yasa ya mutu daga baya, don haka sai Yohoash sarkin Isra'ila ya zo gare shi ya yi kuka a kansa. Ya ce, "Babana, babana, karusan Isra'ila da mahayan dawakanta suna ɗaukan ka!"15Elisha yace masa, "Ɗauki baka da kibbau," sai Yo'ash ya ɗauki baka da wassu kibbau.16Elisha ya cewa sarkin Isra'ila, "Ka sa hannuwanka a bakan," sai ya sa hannuwansa a nan. Sai Elisha ya dafa hannuwansa a hannuwan sarkin.17Elisha yace, "Buɗe tagar da ke wajen gabas," sai ya buɗe ta. Sa'annan Elisha yace, "Harba!", sai ya harba. Elisha yace, "Wannan kibiyar nasarar Yahweh ce, kibiyar nasara akan Aram, gama za ka kai wa Aramiyawan hari a Afek har sai ka yi kaca kaca da su."18Sai Elisha yace, "Ɗauki kibau," sai Yo'ash ya ɗauke su. Ya cewa sarkin Isra'ila, "Ka caki ƙasa da su," sai ya caki ƙasa sau uku, sa'annan ya tsaya.19Amma mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, "Da ka bugi ƙasa sau biyar ko shida. Sa'annan da ka kai wa Aram hari har sai ka hallakar da ita, amma yanzu za ka kai wa Aram hari sau uku ne kawai."20Sai Elisha ya mutu, kuma aka bizne shi. Sai gungun Mowabawa suka mamaye ƙasar a farkon shekara.21Sa'ad da suke bizne wani mutun, suka ga gungũn Mowabawa, sai suka jefar da gangar jikin cikin kabarin Elisha. Da zarar mutumin ya taɓi ƙasussuwan Elisha, sai ya farfaɗo ya miƙe tsaye da kafafunsa.22Hazayel sarkin Aram ya muzguna wa Isra'ila dukkan kwanakin Yehoahaz.23Amma Yahweh ya yi alheri ga Isra'ila, ya kuma ji tausayin su ya kuma kula da su, saboda alƙawarinsa ga Ibrahim, Ishaku da Yakubu. Don haka Yahweh bai hallakar da su ba, haka kuma bai kore su daga gare shi ba.24Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben Hadad ɗansa ya gaji sarautarsa.25Yehoash ɗan Yehoahaz ya karɓi biranen daga Ben Hadah ɗan Hazayel wanɗanda Yehoahaz mahaifinsa ya ƙwato ta yaki. Yehoash ya kai masa hari sau uku, kuma ya karɓe biranen Isra'ila.
"Bayan Yowash ya yi mulkin Yahuza kusan shekara 23"
"mulkin mulkin Isra'ila daga Samariya"
"Yehoahaz ya yi mulkin har tsawon shekaru 17"
Gaban Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh ko tantancewa. AT: "abin da ke mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ɗauka mugunta ne"
Anan ana dakatar da zunubinsa ana maganarsa kamar ya juya baya garesu. Hakanan za'a iya bayyana wannan ta ingantaccen tsari. AT: "Yehoahaz bai daina aikata zunuban Yerobowam ba" ko kuma "Yehoahaz ya ci gaba da yin zunubai iri ɗaya kamar Yerobowam"
Ana magana da fushin Yahweh da Isra'ila game kamar wuta ce mai ƙonewa. AT: "Yahweh kuwa ya yi fushi da Isra'ila"
Anan "su" yana nufin Isra'ila kuma "hannu" yana nufin ikon sarrafa su. AT: "ya bar Hazayel sarkin Aram, da Ben Hadad, ɗansa, su ci nasara da Isra'ilawa sau da yawa a cikin yaƙi"
"ya yi addu'a ga Yahweh"
Waɗannan jumla guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma ana maimaita su don girmamawa. Sunan da ake nunawa "zalunci" yana ma'ana dai-dai da "sarkin Aram yana zaluntar su." AT: "ya ga yadda Sarkin Surm yake zaluntar Isra'ila"
"wani ya cece su"
Anan "hannun" yana nufin ikon sarrafa su. AT: "ya ba su ikon samun 'yanci daga ikon Aram"
An daina yin zunubi ana maganar kamar sun bar zunubai ne. Wannan za a iya bayyana shi da kyau. AT: "Isra'ila ba ta daina aikata irin zunuban da Yerobowam ya yi ba" ko kuma "Isra'ila ta ci gaba da yin zunubi iri ɗaya kamar yadda Yerobowam ya yi"
"iyalin Yerobowam"
"ya ci sojojin Yehoahaz"
Sojojin Aramiyawa sun ci rundunar Isra'ila da yaƙi har abin ya ragu, har ya zama kamar ƙaiƙayi ne kamar alkama, wanda ma'aikata za su yi ta ci a lokacin girbi. AT: "ya murƙushe su kamar yadda ma'aikata ke murƙushe ƙafar ƙafafunsu a lokacin girbi"
Ana amfani da wannan tambaya don tunatar da mai karatu cewa ayyukan Yehoahaz ya rubuta a cikin wani littafi. Duba yadda aka fassara wannan magana a cikin 2 Sarakuna 1:18. AT: "An rubuta su a littafin al'amuran sarakunan Isra'ila."
Wannan ita ce hanyar nuna ladabi da ya ce ya mutu.
"Bayan Yowash ya yi mulkin Yahuza kusan shekara 37"
"Yehowash ɗan Yehoahaz ya ci sarautar Isra'ila a Samariya"
Wannan sarki ne a Isra'ila wanda mahaifinsa shi ne Yehoahaz.
Anan “fuskar” yana wakiltar tunanin Allah ne. AT: "Ya aikata abubuwan da Yahweh ya ɗauke su mugunta ne”
"wannan Yerobowam ya sa Isra'ila su yi zunubi"
A nan ana magana da ƙarfin rundunar Yehowash kamar yadda ƙarfin Yehowash. AT: "ikon da sojojinsa suka nuna lokacin da suka yi yaƙi da rundunar Amaziya sarkin Yahuda"
Ana amfani da wannan tambaya don tunatar da mai karatu cewa ayyukan Yehoahaz ya rubuta a cikin wani littafi. Duba yadda aka fassara wannan magana a cikin 2 Sarakuna 1:18. AT: "An rubuta su a littafin al'amuran sarakunan Isra'ila."
Anan "ya zauna a kan kursiyinsa" yana nufin hukuncin sarki. AT: "Yerobowam ya zama sarki a bayansa" ko "Yerobowam ya fara sarauta bayansa"
"yi kuka domin Elisha ba shi da lafiya"
Elisha ba mahaifin sarki na zahiri bane. Sarki Yowash ya yi amfani da wannan kalmar a matsayin alamar girmamawa.
Wannan ishara ne game da Iliya zai tafi sama cikin 2 Sarakuna 2:11-12. Yowash yayi amfani da wannan kalmar wajen cewa Elisha zai mutu. AT: "Karusan Isra'ila da mahayan dawakai sun ɗauke ka zuwa sama"
Wannan yana nufin mutanen da suka kori karusai. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: “mahayan karusai”
Elisha ya cigaba da magana da sarki Yowash
"bude wannan taga da ke fuskantar gabas" ko "bude wannan taga zuwa gabas"
Tunda yake wannan ya faru bayan Yowash ya ɗauki baka da kibau, wataƙila bawa ya buɗe taga. AT: "Don haka wani bawa ya buɗe shi"
Za'a iya bayyana alakar dake tsakanin kibiya da nasara a bayyane. AT: "Wannan kibiya wata alama ce daga Yahweh cewa ita ce za ta ba ka nasara a kan Aram" ko "Wannan kibiya tana misalin nasarar da Yahweh zai ba ka a kan Aram"
Wannan wani birni ne a kasar Isra'ila.
"Amma Elisha yayi fushi da sarki Yowash"
"har sai kun halakar da ita gaba ɗaya" ko "har sai an shafe su gaba ɗaya"
Wannan kalma alama ce ta karya a cikin babban labarin. Wannan sabon sashin yana ba da bayanan baya don ɓangaren labarin da ya biyo baya.
"kowace shekara a lokacin bazara"
"Sa'ad da yadda wasu Isra'ilawa suka binne gawar mutum"
Ana iya bayyana shi sarai cewa suna tsoron Mowabawa. AT: "sai suka ga wasu gungun Mowabawa suna zuwa kusa da su, sai suka firgita"
"kabarin da aka ɓinne Elisha"
Anan "mutumin" yana nufin gawar tasa. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "Da zaran jikin mamacin ya taɓa ƙasusuwan Elisha"
"mutumin da ya mutu ya sake rayuwa kuma ya tashi"
Zai zama da amfani a rarabe wannan jumlolin zuwa wasu kananan sasa. AT: "Amma Ubangiji ya yi wa mutanen Isra'ila alheri sosai. Ya taimaka musu"
Alkawarin Yahweh shi ne dalilin da bai hallaka Isra'ila ba. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "Wannan shi ne dalilin da Yahweh bai hallaka su ba" ko "Saboda alkawarinsa, Yahweh bai hallaka su ba"
An yi magana game da yadda Yahweh ya ƙi jin daɗin cewa ya kori Isra’ilawa daga inda yake. AT: "Bai ƙi su ba"
Waɗannan sunayen sarakuna ne.
"Yehowash ya karɓi biranen Isra'ila wanda Ben-hadad ya ƙwace"
1A shekara ta biyu ta Yehoash ɗan Yehoahaz, sarkin Isra'ila, Amaziya ɗan Yo'ash, sarkin Yahuda, ya fara mulki.2Yana shekara ashirin da biyar sa'ad da ya fara sarauta; ya yi mulki na tsawon shekara ashirin da tara a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Yehoaddan, ta Yerusalem.3Ya yi abin da ke da kyau a fuskar Yahweh, duk da haka ba kamar Dauda mahaifinsa ba. Ya yi dukkan abin da Yo'ash, mahaifinsa, ya yi.4Amma ba a kawar da wuraren yin tsafi a tuddai ba. Mutane dai suka yi ta miƙa hadaya da ƙona turare a tuddan tsafi.5Sai ya zamana sa'ad da mulkinsa ya kafu sosai, sai ya kashe barorin da suka kashe mahaifinsa sarki.6Duk da haka bai kashe 'ya'yan masu kisan ba; maimakon haka, ya yi aiki bisa ga abin da ke rubuce a shari'a, a cikin Littafin Musa, kamar yadda Yahweh ya umurta, cewa, "Ubanni bai wajaba a kashe su saboda "ya'yansu ba, ko kuma a kashe 'ya'yan saboda iyayensu ba. Maimakon haka, duk mutumin da ya yi laifi lallai ne a kashe shi domin nasa zunuban."7Ya kashe sojoji dubu goma na Idom a Kwarin Gishiri; ya kuma cafko Sela a yaƙi ya kira ta Yoktil, kuma haka ake kiranta har wa yau.8Sa'an nan Amaziya ya aiko da manzanni ga Yehoash ɗan Yehoahaz ɗan Yehu sarkin Isra'ila, cewa, "Ka zo, mu sadu da juna ido da ido a yaƙi."9Amma Yehoash sarkin Isra'ila ya aike manzani su mayar da Amaziya sarkin Yahuda, cewa, "'Yar ƙaya da ke Lebanan ta aiko da saƙo ga itacen al'ul a Lebanan, cewa, 'Ki ba da ɗiyarki ga ɗa na don aure,' amma naman jeji a Lebanan ya wuce ta wurin ya tattaka ƙayar.10Hakika ka kai wa Idom hari, kuma zuciyarka ta ɗaga ka sama. Ka yi fahariya da nasararka, amma ka zauna a gida, gama donme zaka sawa kanka matsala ka faɗi, da kai da Yahuda tare da kai?"11Amma Amaziya bai saurara ba. Saboda haka Yehoash sarkin Isra'ila ya kai hari kuma shi da Amaziya sarkin Yahuda sun sadu da juna ido da ido a Beth Shemesh, wadda ke ta Yahuda.12Isra'ila ta kãda Yahuda, kuma kowanne mutun ya gudu gida13Yehoash sarkin Isra'ila, ya kamo Amaziya, sarkin Yahuda ɗan Yehoash ɗan Ahaziya, a Beth Shemesh. Ya zo Yerusalem ya rushe bangon Yerusalem daga Ƙofar Ifraim zuwa Ƙofar Kwana, mai nisan mita ɗari da tamanin.14Ya ɗauke dukkan zinariya da azurfa da dukkan abubuwan da aka samu a gidan Yahweh, da abubuwa masu daraja na fãdar sarki, tare da mutanen da aka ba da su jingina, sai ya koma Samariya.15Game da sauran zantuttukan da suka shafi Yehoash kuwa, dukkan abin da ya yi da ikonsa da yadda ya yi yaƙi da Amaziya sarkin Yahuda, ba an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila ba?16Sa'an nan Yehoash ya yi barci tare da kakaninsa kuma aka bizne shi a Samariya tare da sarakunan Isra'ila, kuma Yerobowam, ɗansa, ya zama sarki a madadin sa.17Amaziya ɗan Yo'ash, sarkin Yahuda, ya yi shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehoash ɗan Yehoahaz, sarkin Isra'ila.18Game da sauran zantuttuka da suka shafi Amaziya, ba an rubota su a littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?19Suka yi maƙarƙashiya gãba da Amaziya a Yerusalem, sai ya gudu zuwa Lakish. Ya gudu zuwa ga Lakishna, amma an aiko da maza su bishi har Lakish su kashe shi a wurin.20Suka dawo da shi akan dawakai, sai aka bizne shi tare da kakaninsa a birnin Dauda.21Dukkan mutanen Yahuda suka ɗauki Azariya, wanda ke shekara goma sha shida, suka maida shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.22Azariya ne wanda ya gina Elat ya maida ita ta Yahuda, bayan Sarki Amaziya ya kwanta da kakaninsa.23A shekara ta goma sha biyar ta sarautar Amaziya ɗan Yo'ash sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yehoash sarkin Isra'ila ya fara sarauta a Samariya; ya yi mulki shekara arba'in da ɗaya.24Ya aikata mugunta a fuskar Yahweh. Bai kauce wa dukkan zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi.25Ya maida iyakar Isra'ila daga Lebo Hamath zuwa Tekun Arabah, bisa ga bin umurnai na kalmar Yahweh, Allahn Isra'ila, wanda ya faɗa ta wurin bawansa Yona ɗan Amittai, annabin nan da ke daga Gat Hefa.26Gama Yahweh ya ga azabar da Isra'ila ke ciki, kowa yana cikin tsananin wahala, da bawa da sakakke, kuma babu maceci don Isra'ila.27Saboda haka Yahweh ya ce ba zai shafe sunan Isra'ila daga ƙarƙashin sammai ba; maimakon haka, Ya cece su ta hannun Yerobowam ɗan Yehoash.28Game da sauran zantuttukan da suka shafi Yerobowam, da dukkan abin da ya yi da ikonsa, da yadda ya yi yaƙi ya ƙwato Damaskus da Hamath, waɗanda ke na Yahuda a dã, domin Isra'ila, Ba an rubuta su a littafin abubuwan da suka faru da sarakunan Isra'ila ba?29Yerobowam ya kwanta da kakaninsa, tare da sarakunan Isra'ila, sai Zekariya ɗansa ya zama sarki a madadinsa.
"A lokacin da Yehowash ɗan Yehowahaz ya yi sarautar Isra'ila shekara biyu."
"Amaziya ɗan Yowash, sarkin Yahuda, ya fara mulki"
"Yana da shekara 25 lokacin da ya zama sarki"
"ya kasance sarki a Yerusalem shekaru 29"
Anan “idanun Yahweh” suna nufin gabansa, idanunsa kuma suna nufin hukuncinsa. AT: "Amaziya ya aikata abubuwa da yawa waɗanda suka faranta wa Yahweh rai, amma bai aikata abubuwa da yawa waɗanda suka gamshi Yahweh kamar yadda Sarki Dauda ya yi ba"
An ci gaba da labarin yadda Amaziya ya yi a matsayin sarkin Yahuda.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. An yi amfani da masujadai don bautar arna. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "Amma bai kawar da masujadai ba"
An yi amfani da masujadai don bautar arna. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "an miƙa hadaya da ƙona turare ga gumakan arna a wuraren tsafin tuddai"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "da zarar Amaziya ya tabbatad da mulkin sarautarsa da ikon sarauta"
Wataƙila Amaziya ya umarci wasu mutane su kashe jami'ai. AT: "ya sanya bayinsa su kashe ma'aikanta"
Mai ba da labari ya ba da labarin abin da sarki Amaziya ya yi bayan an kashe mahaifinsa Sarki Yowash.
Sarki Amaziya bai umarci barorinsa su kashe 'ya'yan mutanen da suka kashe mahaifinsa ba. Idan kuwa zai sa a kashe su ko da yake, zai umarci barorinsa su yi shi, da ba shi kansa ya yi ba. AT: "Amma bai gaya wa bayinsa su kashe waɗannan 'ya'yan masu kisan"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Mutane ba za su kashe ubanni don zunuban yaransu ba, kuma kada su kashe 'yan yaran saboda zunubin iyayensu"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "kowane mutum dole ne ya mutu saboda zunubin sa"
Wannan sunan wani waje ne wanda yake kudu da Tekun Mutu.
Sun sake sunan birnin Sela. Sabuwar suna Yoktil.
Anan "junan su" sun hada sojojin su. AT: "Sai Amaziya ya aika da jakadu zuwa wurin Sarki Yehoash na Isra'ila, yana cewa, 'Ka zo nan ka bar sojojinmu da junanmu yaƙi.'"
Wannan hoton kalma ne da tatsuniya. Itatuwan sida ya yi girma kuma ƙaya ce babba da daraja. Jehoash ya kamanta kansa da itacen sida da Amaziya da ƙaho kuma ya gargaɗi Amaziya kada ya kai hari. Idan kuna da kwatankwacin wannan a cikin yaren ku, zaku iya amfani dashi.
Wannan lafazin kai tsaye ana iya bayyana shi azaman magana kai tsaye. AT: "yana roƙon itacen sida don ya aurar da ɗan 'yarsa ga ɗan' ɗaya"
Wannan shi ne kashedin gargaɗin da Yehowash ya aika wa Amaziya. "Amaziya, hakika kun ci Idom"
"Ka gamsu da nasarka"
Yehoash ya yi amfani da wannan tambaya don gargaɗin Amaziya kada ya kai masa hari. AT: "don kada ka jawo wa kanka matsala kuma a sha kaye"
Anan "saurare" yana nufin yin biyayya ga gargaɗin. AT: "Duk da haka, Amaziya bai yi biyayya da gargaɗin Yehoash ba"
Waɗannan sojojin waɗannan sarakuna sun tafi yaƙi da su. AT: "Yehoash da sojojinsa suka tafi don su yi yaƙi da Amaziya da sojojinsa, suka kuma haɗu da juna"
Wannan gari ne, cikin ƙasar Yahuda, kusa da iyaka Isra'ila.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Isra'ila ta ci Yahuda"
"Dukkan mutanen Yahuda suka gudu zuwa gida"
Wannan shi ne abin da ya faru bayan sojojin Isra'ila sun ci mutanen Yahuda a Bet Shemesh.
Anan "Ya" yana nufin Yehoash da sojojinsa. AT: "Yehoash tare da sojojinsa sun zo ... Sojojin Yehoash sun ɗauke"
Waɗannan sunayen ƙofofin a bangon Yerusalem.
"kimanin mita 180 "
Wannan yana nuna cewa Yehowash ya buƙaci ya ɗauki waɗannan masu garkuwa da mutane don hana Amaziya sake kai hari. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "su kuma suka kwashi wasu fursunoni zuwa Samariya don tabbatar da Amaziya ba zai haifar musu da wata matsala ba"
Ana amfani da wannan tambaya don tunatar da mai karatu cewa ayyukan Yehoahaz ya rubuta a cikin wani littafi. Duba yadda aka fassara wannan magana a cikin 2 Sarakuna 1:18. AT: "An rubuta su a littafin al'amuran sarakunan Isra'ila."
Wannan ita ce hanya mai ladabi da za a ce ya mutu. AT: "Yehowash ya mutu"
"ya zama sarki a bayansa"
Ana amfani da wannan tambaya don tunatar da mai karatu cewa an rubuta waɗannan abubuwan. Duba yadda ake fassara wannan kalmar a 2 Sarakuna 8:23. AT: "An rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuda."
Maƙarƙashiya shi ne rufin asiri don cutar da wani ko wani abu. AT: "Wasu mutanen a Yerusalem sun yi wa maƙarƙashiya gaba da Amaziya"
Wannan birni ne, a kudu Yahuda.
Mutanen da suka shirya maƙirkishiyan suka aike da waɗansu mutane don su bi Amaziya zuwa Lakish.
Wannan shine abin da ya faru bayan mutuwan Amaziya.
Suka kawo gawar Amaziya a kan dawakai.
Wannan janar ne. Wataƙila wasu mutane ba sa son shi ya zama sarki. AT: "Mutanen Yahuda sun ɗauki Azariya wanda ke shekara 16, suka maida shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya"
Azariya bai yi wannan kaɗai ba. AT: "Azariya ne ya ba da umarnin a sake gina Elat" ko "Azariya ce ta lura da sake gina Elat"
"mayar da shi zuwa ga Yahuda"
Wannan wata hanya ce ta waƙa ta ce ya mutu.
A shekara ta 15 na Amaziya
"shekaru 41"
An daina yin zunubi ana maganar barin hanya. Wannan za a iya bayyana shi da kyau. AT: "Bai daina aikata zunubai iri ɗaya irin na Yerobowam ba" ko kuma "Ya ci gaba da aikata zunubai iri ɗaya kamar Yerobowam"
Ana kiran wannan birni Hamat.
"Jar Tekun"
Wahala da ke da wuya ana maganarta kamar tana da dandano mai ɗaci. AT: "yana da wuya"
"babu wanda zai ceci Isra'ila"
Ana hallakar da Isra'ila sarai kamar yadda Yahweh ya keɓe su da mayafi. AT: " halaka su gaba ɗaya"
Anan "sunan Isra'ila" yana wakiltar Isra'ila duka da mazaunanta. AT: "jama'ar Isra'ila"
"a duniya"
Anan "hannun" kalmar ne don iko. Hakanan, “Yehoash” yana wakiltar Yehoash da rundunarsa. AT: "ya baiwa Sarki Yerobowam da rundunarsa su cecesu"
Ana amfani da wannan tambaya don tunatar da mai karatu cewa ayyukan Yerobowam ya rubuta a cikin wani littafi. Duba yadda aka fassara wannan magana a cikin 2 Sarakuna 1:18. AT: "An rubuta su a littafin al'amuran sarakunan Isra'ila."
Wannan ita ce hanya mai ladabi da za a ce ya mutu, aka binne shi. AT: "Yerobowam ya mutu, aka binne shi a inda aka binne sauran sarakunan Isra'ila"
1A shekara ta ashirin da bakwai ta sarautar Yerobowam, sarkin Isra'ila, Azariya ɗan Amaziya sarkin Yahuda ya fara mulki.2Azariya yana shekara goma sha shida sa'ad da ya fara mulki, kuma ya yi sarauta ta shekara hamsin da biyu a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya, kuma ita daga Yerusalem take.3Ya yi abin da ke dai-dai a idanun Yahweh, kamar yarda mahaifinsa Amaziya ya yi.4Sai dai, wuraren tsafin kan tuddai ba a rusa su ba. Mutanen dai na miƙa hadaya da ƙona turare a saman tuddai.5Yahweh ya addabi sarkin da kuturta har zuwa ranar mutuwarsa kuma ya yi ta zama a gidan da aka ware ne. Yotam, ɗan sarki, ya shugabanci gidan ya kuma yi mulkin mutanen ƙasar.6Game da sauran zantuttukan da suka shafi Azariya da dukkan abin da ya yi, ba an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?7Saboda haka Azariya ya yi barci tare da kakaninsa; su ka bizne shi tare da kakaninsa a birnin Dauda. Yotam, ɗansa ya zama sarki a madadinsa.8A shekara ta talatin da takwas ta Azariya sarkin Isra'ila, Zekariya ɗan Yerobowam ya yi mulki a Isra'ila ta Samariya na wata shida.9Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh, kamar yadda mahaifansa suka yi. Bai kauce daga zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi.10Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla wa Zekariya maƙarƙashiya, ya kai masa hari a Ibleam, ya kashe shi. Sai ya zama sarki a madadinsa.11Game da sauran zantuttukan da suka shafi Zekariya, An rubuta su a littafin abubuwan da suka faru da sarakunan Isra'ila.12Wannan ne batun da Yahweh ya faɗa wa Yehu, cewa, "Zuriyarka za su zauna a gadon sarautar Isra'ila har zuwa tsara ta huɗu." Abin da ya faru kenan13Shullum ɗan Yabesh ya fara mulki a shekara ta talatin da tara na Azariya sarkin Yahuda, kuma ya yi mulki na wata ɗaya a Samariya.14Menahem ɗan Gadi ya tafi can daga Tirza zuwa Samariya. a wurin ya kai wa Shullum ɗan Yabesh hari, a Samariya. Ya kashe shi ya kuma zama sarki a madadinsa.15Game da sauran zantuttuka da suka shafi Shallum da maƙarƙashiya da ya shirya, a rubuce suke a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. Sa'an nan16Menahem ya kai hari a Tifsa da dukkan waɗanda ke wurin da iyakar wuraren Tirzah, saboda ba su ba shi zarafin shiga birnin ba. Sai ya kai mata hari ya kuma feɗe dukkan mata masu junabiyu a ƙauyen nan.17A shekara ta talatin da tara ta Azariya sarkin Yahuda, Menahem ɗan Gadi ya fara mulki a kan Isra'ila, Ya yi mulkin shekara goma a Samariya.18Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh. Gama a dukkan rayuwarsa, bai kauce daga zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi.19Sa'an nan Ful sarkin Asiriya ya zo gãba da ƙasar, sai Menaham ya bai wa Ful talanti dubu na azurfa, saboda Ful ya taimaka da gudumawa domin masarautar Isra'ila ta ƙarfafa a hannunsa.20Manehen ya ƙarbi wannan kuɗin daga Isra'ila ta wurin neman awo hamsin na azurfa daga dukkan atajiri domin ya bai wa sarkin Asiriya. Don haka Sarkin Asiriya ya juya baya kuma bai zauna cikin ƙasar ba.21Game da sauran zantuttukan da suka shafi Manahem, da dukkan abin da ya yi, ba a rubuce suke a litaffin tarihin sarakunan Isra'ila ba?22Sai Manahem ya yi barci tare da kakaninsa, kuma Fekahiya ɗansa ya zama sarki a madadinsa.23A shekara ta hamsin ta Azariya sarkin Yahuda, Fekahiya ɗan Menahem ya fara mulki a Isra'ila cikin Samariya; ya yi mulki shekara biyu.24Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh. Bai juya daga zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ta wurin hakan ya sa Isra'ila ta yi zunubi.25Fekahiya yana da hafsa mai suna Feka ɗan Remaliya, wanda ya ƙulla masa maƙarkashiya. Tare da mutane hamsin na Giliyad, Feka ya kashe Fekahiya da kuma Argob da Ariye a Samariya, a cikin sansanin hasumayar fadar sarki. Feka ya kashe Fekahiya ya kuma zama sarki a madadinsa.26Game da sauran zantuttuka da suka shafi Fekahiya da dukkan abin da ya yi, a rubuce suke a littafin tarihin sarakunan Isra'ila.27A shekara ta hamsin da biyu na Azariya sarkin Yahuda, Fekah ɗan Remaliya ya fara mulki akan Isra'ila cikin Samariya; ya yi mulki shekara ashirin.28Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh. Bai kauce daga zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi.29A kwanakin Feka sarkin Isra'ila, Tiglat Filesa sarkin Asiriya ya zo ya ɗauki Ijon da Abel Bet Ma'aka da Janoya da Kedesh da Hazor da Giliyad da Galili da dukkan ƙasar Naftali. Ya ɗauki mutanen zuwa Asiriya.30Don haka Hosheya ɗan Elah ya shirya maaƙarƙashiya găba da Feka ɗan Remaliya. Ya kai masa hari ya kuma kashe shi. Sa'an nan ya zama sarki a madadinsa, a shekara ta ashirn ta yotam ɗan Uzziya.31Game da sauran zantuttukan da suka shafi Feka da dukkan abin da ya yi, a rubuce suke a littafin tarihin sarakunan Isra'ila.32A shekara ta biyu ta Peka ɗan Remaliya, sarkin Isra'ila, Yotam ɗan Azariya, sarkin Yahuda ya fara mulki.33Yana da shekara ashirin da biyar a sa'ad da ya fara mulki; Ya yi mulki shekara goma sha shida a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Yerushah; Ita ɗiyar Zadok ce.34Yotam ya yi abin da ke da kyau a fuskar Yahweh. Ya bi misalin dukkan abubuwan da mahaifisa Azariya ya yi.35Duk da haka, ba a ƙwato wuraren tsafin kan tuddai ba. Mutanen na yin hadaya da ƙona turare a samman tuddai, Yotam ya gina ƙofarta bisa ta gidan Yaweh.36Game da sauran zantuttukan da suka shafi Yotam, da dukkan abin da ya yi, ba a rubuta su a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?37A kwanakin nan ne Yahweh ya fara aiko da Rezin sarkin Aram da Peka ɗan Remaliya gaba da Yahuda.38Yotam ya kwanta da kakaninsa a birnin Dauda, kakansa. Sa'an nan Ahaz ɗansa ya zama sarki a madadinsa.
Za a iya bayyana hakan a sarari cewa wannan ne shekara ta ashirin da bakwai ta mulkinsa. AT: "A shekara ta 27 na mulkin Yerobowam"
Wannan sananne ne ga sarki yau yau da sunan "Uziya."
Wannan sunan mahaifiyar Azariya.
"Azariya yayi abin da ke dai-dai"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "ba wanda ya ɗauke masujadai" ko kuma "Azariya bai da kowa ya ɗauke masujadan wuraren nan ba"
Kalmar "gida" tana nufin mutanen da ke zaune a gidan sarki. Saboda Azariya kuturu ne, dole ne ya zauna a wani gida daban. Sai ɗansa Yotam shi ne shugaban gidan sarki.
Ana amfani da wannan tambayar don ko sanar da masu karatu ko kuma cewa bayanin game da Azariya yana cikin wannan littafin. Hakanan za'a iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 8:23. AT: "An rubuta su ... Yahuda." ko "zaku iya karanta game da su ... Yahuda."
Barci yana wakiltar mutuwa. AT: "Azariya ya mutu kamar yadda kakanninsa suka yi" ko "kamar kakanninsa, Azariya ya mutu"
"iyalansa su ka bizne shi tare da kakaninsa"
Kalmomin "a madadinsa" yana nufin "a maimakon sa." AT: "ya zama sarki maimakon Azariya"
Za a iya bayyana hakan a sarari cewa wannan ne shekara ta talatin da takwas ta mulkinsa. AT: "A shekara ta 38 ta sarautar Azariya sarkin Yahuda"
Yerobowam shi ne Sarkin Isra'ila na biyu, yana da suna. Shi ɗan Yoash sarki ne.
Samariya ita ce birnin da Zakariya yake zaune a lokacin da yake sarkin Isra'ila. AT: "ya zauna a Samariya kuma ya yi sarauta bisa Isra'ila na wata shida"
Ganin Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 3: 2. AT: "abin da ke mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ɗauka mugunta ne"
Komawa daga zunubai yana nuna ƙin aikata waɗannan zunuban. AT: "Zekariya bai ƙi aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba" ko kuma "Ya yi zunubi kamar yadda Yerobowam ɗan Nebat ya yi zunubi"
Wannan Yerobowam shi ne sarki na farko na ƙabilu goma na arewa waɗanda suka zama masarautar Isra'ila.
Anan kalmar "Isra'ila" tana wakiltar mutanen mulkin Isra'ila. AT: "wanda ya sa mutanen Isra'ila su yi zunubi"
Waɗannan sunayen mutane ne.
"a kan Sarki Zekariya"
Wannan shi ne sunan gari ne.
"Sai Shallum ya ci sarautar a maimakon Zekariya"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Kuna iya karanta game da su a littafin al'amuran sarakunan Isra'ila"
Za a iya fayyace sarai cewa abubuwan da suka faru a cikin aya ta 10 sun cika kalmar Yahweh. AT: "Abin da ya faru da Zekariya bisa ga maganar Yahweh ne" ko "Abin da ya faru da Zekariya ya cika kalmar Yahweh"
Zama a kan kursiyin yana wakiltar kasancewa sarki. AT: "Zuriyar ku za su zama sarakunan Isra'ila har tsara ta huɗu"
Za a iya bayyana hakan a sarari cewa wannan ne shekara ta talatin da tara ta mulkinsa. AT: "a shekara ta 39 ta sarautar Azariya Sarkin Yahuda"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Samariya ita ce birnin da yake zaune a lokacin da yake mulkin Isra'ila. AT: "Shallum ya zauna a Samariya ya yi mulkin Isra'ila wata ɗaya kawai"
Kalmomin "a madadinsa" na nufin "a maimakon sa." AT: "ya zama sarki a maimakon Shallum"
Zai iya bayyana a fili abin da wannan maƙarƙashiyar ta kasance. AT: "yadda ya shirya kashe Sarki Zekariya" ko "da yadda ya kashe Sarki Zekariya"
Wannan sunan birni ne. Wasu juyi suna da "Taffua," wanda shi ne sunan wani birni.
Za a iya bayyana hakan a sarari cewa wannan ne shekara ta talatin da tara ta mulkinsa. AT: "A shekara ta 39 ta sarautar Azariya sarkin Yahuda"
Ganin Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 3: 2. AT: "abin da ke mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ɗauka mugunta ne"
AT: "Duk tsawon lokacin da ya rayu"
Kalmomin "Ful sarkin Asiriya" yana wakiltar Ful da rundunarsa. AT: "Ful sarkin Asiriya ya zo tare da rundunarsa zuwa ƙasa"
Ful sunan wani mutum wanda ya kasance sarkin Asiriya. Shi kuma sunan Tiglat-Fileser.
Kalmomin "gãba da" karin magana ne ma'anar kai hari ne. “ƙasar” tana nufin ƙasar Isra’ila kuma tana wakiltar mutanen da suke zama. AT: "ya zo da rundunarsa don su yi yaƙi da Isra'ila"
"Talanti 1000 na azurfa." Kuna iya juyar da wannan zuwa ma'aunin zamani. AT: "kilo talatin da dubu uku na azurfa" ko "ton dubu talatin da uku na azurfa"
AT: "domin Ful ya goyi bayan shi"
Samun mulkin a hannunsa yana wakiltar mulkin. AT: "don ƙarfafa mulkinsa a kan masarautar Isra'ila"
"Ya karɓi wannan kuɗin daga Isra'ila"
Kuna iya juyar da wannan zuwa ma'aunin zamani. AT: "giram ɗari shida na azurfa" ko "kashi uku bisa ɗari na kilo na azurfa"
Ana amfani da wannan tambayar don ko sanar da ko kuma tunatar da masu karatu cewa bayanin game da Menahem yana cikin wannan littafin. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 1:18. AT: "An rubuta su a littafin abubuwan da sarakunan Isra'ila suka yi."
Barci yana wakiltar mutuwa. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 10:35. AT: "Menahem ya mutu kamar yadda kakanninsa suka yi" ko "kamar kakanninsa, Menahem ya mutu"
Wannan sunnan mutum ne. (Duba:
Ana iya furta wannan a sarari da cewa wannan shine shekaransa sa na hamsin na mulkinsa. AT: "A shekara ta 50 na mulkin Azariya sarkin Yahuda"
Ganin Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 3: 2. AT: "abin da ke mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ɗauka mugunta ne"
Barin zunubai yana nuna ƙin aikata waɗannan zunuban. AT: "Fekahiya bai ƙi aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba" ko kuma "ya yi zunubi kamar yadda Yerobowam ɗan Nebat ya yi zunubi"
Anan kalmar "Isra'ila" tana wakiltar mutanen mulkin Isra'ila.
Waɗannan sunayen mutane ne.
"An yi niyyar kashe Fekahiya a asirce"
"mutane 50"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Kuna iya karanta game da su a littafin al'amuran sarakunan Isra'ila"
Ana iya bayyanawa sarai cewa wannan shekara ce ta hamsin da biyu ta mulkinsa. AT: "A shekara ta 52 ta sarautar Azariya sarkin Yahuda"
Ganin Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh Duba yadda kuka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 3: 2. AT: "abin da ke mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ɗauka mugunta ne"
Komawa daga zunubai yana nuna ƙin aikata waɗannan zunuban. AT: "Feka bai ƙi aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba" ko kuma "Ya yi zunubi kamar yadda Yerobowam ɗan Nebat ya yi zunubi"
Ana iya bayyana hakan a sarari da cewa ana nufin kwanakin mulkin Feka. AT: " A kwanakin mulkin Feka sarkin Isra'ila" ko "A wancan lokacinda Feka ya zama sarki a Isra'ila.
A cikin 2 Sarakuna 15:19 an kira wannan mutumin "Ful."
Waɗannan su ne sunayen biranen ko yankuna.
Anan "ya" yana nufin Tiglat Filesa kuma yana wakilta shi da rundunarsa. Caraukar mutane zuwa Asiriya alama ce ta tilasta musu su tafi Asiriya. AT: "Shi da rundunarsa sun tilasta mutane su tafi Asiriya
Ana iya bayyanawa a fili waɗanne irin mutane ne waɗannan. Watau fassarar: "mutanen waɗancan wuraren" ko "jama'ar Isra'ila"
Waɗannan sunayen mutane ne.
"Hosheya kuwa ya kai wa Feka hari, ya kashe shi"
Ana iya bayyanawa sarai cewa wannan shekara ce ta ashirin ta sarautarsa. AT: "A shekara ta 20 ta mulkin Yotam ɗan Uziya"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Kuna iya karanta game da su a littafin al'amuran sarakunan Isra'ila"
Ana iya bayyana hakan a sarari cewa wannan ne shekara ta biyu ta mulkinsa. AT: "A shekara ta 2 ta mulkin Feka ɗan Remaliya, sarkin Isra'ila"
"Yotam ɗan Azariya, sarkin Yahuda ya zama sarki a Yahuda"
"Yana da shekara 25 ... shekaru 16"
Wannan sunan mace ne.
Idanu suna wakiltar gani, da gani suna wakiltar tunani ne ko hukunci. AT: "abin da ke dai-dai cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ga dai-dai ne"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "ba wanda ya ɗauke masujadai" ko "Yotham ba shi da kowa ya ɗauke masujjada."
Kasancewa yana wakiltar rushewa. AT: "ba a lalata su ba"
"Yotam ya gina" yana wakiltar Yotam yana sa ma'aikatansa su gina shi. AT: "Yotam ya sa ma'aikatansa su gina ƙofar ta sama"
Ana amfani da wannan tambayar don ko dai sanar da ko kuma tunatar da masu karatu cewa bayanin game da Yotam yana cikin wannan littafin. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 8:23. AT : "An rubuta su a littafin abubuwan da sarakunan Yahuda suka yi."
Wannan sunan mutum ne.
Barci yana wakiltar mutuwa. AT: "Yotam ya mutu kamar yadda kakanninsa suka yi" ko "Kamar kakanninsa, Yotam ya mutu"
Kalmomin "a madadinsa" na nufin "a maimakon sa." AT: "ya zama sarki maimakon Yotam"
1A shekara ta goma sha bakwai ta Feka ɗan Remaliya,2Ahaz ɗan Yotam sarkin Yahuda, ya fara mulki, kuma ya yi mulki shekara goma sha shida a Yerusalem. Bai yi abin da ke dai-dai a fuskar Yahweh Allahnsa ba, kamar yadda Dauda kakansa ya yi ba.3Maimakon haka, ya yi tafiya a hanyar sarakunan Isra'ila; hakika, ya sa ɗansa a wuta domin hadaya ta ƙonawa, yana bin ayyukan ban ƙyama na al'ummai, waɗanda Yahwe ya fitar daga gaban mutanen Isra'ila.4Ya miƙa hadayu da kuma ƙona turare awurare bisa tuddai da ƙarƙashin kowanne koren Itace.5Sa'an nan Rezin, sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, sarkin Isra'ila, ya zo Yerusalem ya kawo hari. Suka tunkari Ahaz, amma ba su iya mamayar sa ba.6A lokacin nan, Rezin sarkin Aram ya maido Elath domin Aram ya kori mazajen Yahuda daga Elat. Sa'an nan Aramiyawa suka zo gun Elat inda suka zauna har yau.7Sai Ahaz ya aiki manzanni ga Tiglat Filesa sarkin Asiriya, cewa, "Ni baranka ne da ɗanka. Ka zo ka cece ni daga hannun sarkin Aram da hannun sarkin Isra'ila, waɗanda suka kawo mani hari."8Sai Ahaz ya ɗauki azurfa da zinariyan da aka tarar a gidan Yahweh da na cikin kayayyaki masu daraja na fãdar sarki ya aikar da su kyauta ga sarkin Asiriya.9Sa'an nan sarkin Asiriya ya saurare shi, kuma sarkin Asiriya ya farmaƙi Damaskus, ya mamaye ta, ya kuma ɗauke mutanenta ya kai su zaman bauta a Kir. Ya kuma kashe Rezin sarkin Aram.10Sarki Ahaz ya tafi Damaskus ya sadu da Tiglat Filesa sarkin Asiriya. A Damaskus ya ga wani bagadi. Ya aika wa Yuriya firist irin fasalin bagaden da yanayinsa da zane domin dukkan aikin da ake bukata.11Don haka Yuriya firist ya gina bagaden da zai zama kamar tsarin da sarki Ahaz ya aiko daga Damaskus. Ya gama shi kafin sarki Ahaz ya dawo daga Damaskus.12Sa'ad da sarki ya zo daga Damaskus ya ga bagaden; sarkin ya kusanci bagaden ya kuma yi bayarwa akan sa13Ya yi hadayarsa ta ƙonawar da hadayarsa ta hatsi, ya zubo hadayarsa ta sha, ya yayyafa jinin hadayarsa ta zumunci a bagaden.14Bagaden tagulla wanda ke gaban Yahweh - ya kawo shi daga gaban haikalin, daga tsakanin bagaden da haikalin Yahweh ya sa shi a gefen arewacin bagadensa15Sai sarki Ahaz ya umurci Yuriya firist, cewa, "A babban bagaden ka ƙona baikon ƙonawa na safe da baikon hatsi na yamma, da kuma baikon na ƙonawa na sarki da baikon hatsinsa, da baikon na ƙonawa na dukkan mutanen ƙasar, da baikon hatsinsu da baikon shansu. Ka yayyafa jinin akan dukkan baiko na ƙonawa, da dukka jinin hadayar. Amma bagadin tagulla zai zama nawa domin neman shawara don jagoranci."16Yuriya firist kuwa ya yi abin da sarki Ahaz ya umurta.17Sa'an nan sarki Ahaz ya ciro dakalan da darunan da suke bisansu; ya kuma ɗauke babban daron daga bijimin tagullar da ke ƙarƙashinsa ya sa shi a daɓen dutse.18Ya cire hanyar da aka killace ta Asabaci wanda aka gina a haikalin, tare da ƙofar dake waje ta shigar sarki zuwa haikalin Yahweh, saboda sarkin Asiriya.19Game da sauran zantuttukan da suka shafi Ahaz da abin da ya yi, ba a rubuce suke cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?20Ahaz ya kwanta da kakaninsa aka kuma bizne shi tare da kakaninsa a birnin Dauda. Hezekiya ɗansa ya zama sarki a madadinsa.
Zai iya bayyana a fili cewa wannan shekara ta goma sha bakwai ta mulkinsa. AT: "A shekara ta 17 ta mulkin Feka ɗan Remaliya"
Waɗannan sunayen mutum ne.
Idanu suna wakiltar gani, da gani suna wakiltar tunani ne ko hukunci. AT: "abin da ke daidai cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh Allahnsa ya ga ya yi dai-dai"
Dauda ya yi abin da ya dace.
Yin tafiya yana wakiltar halaye da ayyuka. AT: "Sarki Ahaz ya yi yadda sarakunan Isra'ila suka yi" ko "ya aikata abubuwan da sarakunan Isra'ila suka yi"
Anan "bin" yana wakiltar aikata abin da wasu sukeyi. AT: "kwafa abubuwa masu banƙyama da sauran al'umman suka yi, al'ummai"
Kalmar "al'ummai" tana wakiltar mutanen wasu al'ummai. Anan yana nufin mutanen al'umman da suka rayu a waccan ƙasar. AT: "mutanen wasu al'ummai"
Waɗannan alumman ƙasar sun gudu kamar yadda Isra'ilawa suka koma ƙasar. Ana iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "a gaban mutanen Isra'ila da suka koma cikin ƙasa" ko "kamar yadda mutanen Isra'ila suka koma ƙasar"
Waɗannan wurare ne waɗanda al'ummomin sauran al'ummai ke bauta wa allolinsu na ƙarya.
Ahaz ya kasance a Yerusalem. Anan "Ahaz" yana wakiltar kansa da kuma mutanen da suke tare da shi tare da shi. AT: "kewaye garin tare da Ahaz a ciki" ko "kewaye Ahaz da sauran waɗanda ke tare da shi"
A nan "Aram" yana wakiltar mutanen da suke zaune a can. AT: "sun koma hannun Elat na mutanen Aram"
Wannan sunan birni ne.
"tilasta wa mutanen Yahuda su bar Elath"
Wannan yana nufin zuwa lokacin rubuta wannan littafin.
A cikin 2 Sarakuna 15:19 an kira wannan mutumin "Ful." Duba yadda zaka fassara sunan shi a 2 Sarakuna 15:29.
Kasancewa bawan da ɗa yana wakiltar miƙa wuya ga ikon wani. AT: "Zan yi maka biyayya kamar nima bawanka ne ko danka"
Hannun magana ce wacce take wakiltar iko. AT: "daga ikon sarkin Aram da ikon sarkin Isra'ila"
Sarakunan da suka kai harin Ahaz suna wakiltar sojojin waɗanda sarakunan suke yi wa Ahaz da jama'arsa. AT: "waɗanda suka yi karo da ni da rundunarsu" ko "waɗanda sojojinsu suka yi karo da ni"
Kalmar “sarki” tana wakiltar sarki da sojojinsa. Hakanan, Damaskus tana wakiltar mutanen da suke zama. AT: "sarkin Asiriya da rundunarsa sun yi yaƙi da mutanen Damaskus"
Kashe mutane yana wakiltar tilasta musu su tafi. Watau fassarar: "ya sa mutane su zama fursunoni ya tilasta su zuwa Kir"
Ma'anar mai yiwuwa sune 1) wannan sunan gari ne ko 2) wannan kalma tana nufin "birni" kuma yana nufin babban birnin Asiriya.
Wannan za a iya fassara shi a cikin aiki mai aiki. AT: "duk umarnin da ma'aikatan suka buƙaci don gina shi"
Wannan shi ne abin da Sarki Ahaz ya yi bayan ya dawo daga Damaskus don ya ziyarci sabon bagaden da Uriya firist ya gina masa.
"Sarki Ahaz ya miƙa hadayar ƙonawarsa"
Wannan yana nufin bagaden da Sarki Ahaz ya ce Uriya ya gina.
Duk waɗannan maganganun suna faɗi inda bagadin tagulla yake. Suna nufin wuri guda ne.
Wannan yana nufin sabon bagaden da Ahaz ya ce Uriya ya gina.
Sa’ad da Ahaz ya ce “sarki” da “nasa,” yana nufin kansa ne. Sarki ya ba da hadayunsa na musamman. AT: "hadaya ta ƙonawa da hadaya ta gari" ko "hadaya ta ƙonawa ta sarki da hadaya ta gari"
"motsi yana tsaye" ko "katunan." Waɗannan ƙafafun suna da ƙafafun a ƙafafunsu don a motsa su.
"ya kuma cire babban kwano." “Teku” babban katako ne ko kwanon ruwa da aka yi da tagulla.
Abin da ya sa suka yi wannan za a iya bayyana a sarari. AT: "don gamsar da sarkin Asiriya"
Ana amfani da wannan tambayar don ko sanar da ko kuma tunatar da masu karatu cewa bayanin game da Ahaz yana cikin wannan littafin. Hakanan za'a iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 8:23. AT "an rubuta su a abubuwan da sarakunan Yahuda suka yi." ko "wani ya rubuta game da su a littafin ... Yahuda."
Barci yana wakiltar mutuwa. AT: "Ahaz ya mutu kamar yadda kakanninsa suka yi" ko "kamar kakanninsa, Ahaz ya mutu"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. Watau fassarar: "mutane sun binne shi tare da kakanninsa"
Kalmomin "a wurinsa" magana ne mai ma'ana "a maimakon sa." AT: "ya zama sarki maimakon Ahaz"
1A shekara ta goma sha biyu ta Ahaz sarkin Yahuda, mulkin Hosheya ɗan Elah ya fara, ya yi mulki a Samariya akan Isra'ila na shekara tara.2Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh, duk da haka ba kamar sarakunan Isra'ila waɗanda suka gabace shi ba.3Shalmaneser sarkin Asiriya ya kai masa hari, kuma Hosheya ya zama baransa ya kawo masa haraji.4Sa'an nan sarkin Asiriya ya gano cewa Hosheya na ƙulla maƙarƙshiya gãba da shi, don Hoshiya ya aiko manzanni ga So sarkin Masar; haka kuma, babu kyautar da ya miƙo wa sarkin Asiriya, kamar yadda ya saba yi shekara da shekara. Saboda haka sarkin Assiriya ya kulle shi ya ɗaure shi a kurkuku.5Sa'an nan sarkin Asiriya ya kai hari a ko'ina a ƙasar, ya kuma kai wa Samariya hari ya mamaye ta shekara uku.6A shekara ta tara ta Hosheya, sarkin Asiriya ya ɗauki Samariya ya kuma ɗauki Isra'ila zuwa Asiriya. Ya sa su a Halah, a harabar Kogin Gozan, da kuma cikin biranen Medeyawa.7Mãmewar ta faru ne saboda mutanen Isra'ila sun yi zunubi ga Yahweh Allahnsu, wanda ya kawo su daga ƙasar Masar, daga ƙarƙashin hannun Fir'auna sarkin Masar. Mutanen suna bautawa waɗansu alloli ne8kuma suna tafiya cikin ayyukan al'umman da Yahweh ya kora daga mutanen Isra'ila, da kuma cikin ayyukan sarakunan Isra'ila da suka yi.9Mutanen Isra'ila sun yi wa Yahweh Allahnsu abubuwan da ba dai-dai ba a asirce. Sun gina wa kansu manyan wurare a dukkan biranensu, daga hasumiya zuwa birni mai garu.10Suka kuma kafa ginshiƙai da sandunan Ashera a ko'ina bisan tudu da ƙarƙashin dukkan koren itace.11A wurin suka ƙona turare cikin dukkan wurare masu bisa, kamar yarda al'ummai suka yi, waɗanda Yahweh ya fitar da su kafin su. Isra'ilawa sun aikata mugayen abubuwan da suka zuga Yahweh ga fushi,12sun bauta wa gumaka, irin waɗanda Yahweh ya ce masu, "Ba za ku yi wannan abin ba."13Duk da haka Yahweh ya yi shaida ga Isra'ila da kuma ga Yahuda ta wurin kowanne annabi da kowanne mai gani, cewa, "Ku juyo daga hanyoyin mugunta ku tsare dokokina da farillaina, kuma ku yi hankali da tsare dukkan dokokin da na ummurce ubanninku, da waɗanda na aiko maku ta hanun barorina annabawa."14Amma ba za su saurara ba; maiimakon haka suka taurare kamar ubanninsu waaɗnda ba su da aminci cikin Yahweh Allahnsu.15Suka ƙi dokokinsa da alƙawarin da ya yi da kakaninsu, da ummurnan alƙawarin da ya ba su. Suka bi ayyuka marasa amfani kuma su kansu suka zama marasa amfani. Suka bi al'umman arnan da ke kewaye da su, waɗanda Yahweh ya ummurce su kada su kwaikwaye su.16Suka ƙyale dukkan dokokin Yahweh Allahnsu. Suka ƙera sifofin zubi na ƙarfe na 'yan muruƙa biyu domin su bauta masu. Suka yi sandan Ashera, kuma suka bautawa dukkan taurari na sama da Ba'al.17Suka sa 'ya'yansu maza da 'ya'yansu mata cikin wutan, suka yi duba da tsubbace tsubbace, suka sayar da kansu don su yi abin da ke mugu a fuskar Yahweh, kuma suka sa shi shi ya yi fushi.18Saboda haka Yahweh ya yi matuƙar fushi da Isra'ila ya cire su daga gabansa, Babu wanda aka bari ban da ƙabilar Yahuda ita ƙaɗai.19Ko Yahuda ma ba su tsare dokokin Yahweh Allahnsu ba, amma maimakon haka suka bi abin da Isra'ila ta yi.20Sai Yahweh ya ƙi dukkan zuriyar Isra'ila; ya wahalshe su ya bada su ga hannun waɗanda za su ɗauki mallakarsu a matakin ganima, har sai da ya watsar da su daga fuskarsa21Y a yago Isra'ila daga sarautar ta layin Dauda, suka kuma maida Yerobowam ɗan Nebat ya zama sarki. Yerobowam ya kawar da Isra'ila daga bin Yahweh ya sa suka aikata gagarumin zunubi.22Mutanen Isra'ila kuwa suka bi dukkan zunuban Yerobowam kuma ba su kauce daga yin su ba,23saboda haka Yahweh ya cire Isra'ila daga fuskarsa, kamar yadda ya faɗa ta wurin barorinsa annabawa cewa zai yi. Saboda haka aka ɗauke Isra'ila daga tasu ƙasar zuwa Asiriya, kuma haka yake har wannan rana24Sarkin Asiriya ya kawo mutane daga Babila da Kutha da Avva da Hamat da Sefabayim, sai ya sa su a biranen Samariya a madadin mutanen Isra'ila. Suka mamaye Samariya suka zauna a biranenta.25Ya kasance a farkon zamansu a wurin ba su girmama Yahweh ba. Sai Yahweh ya aiko da Zakunan da suka kashe waɗansu daga cikinsu.26Sai suka yi magana da sarkin Asiriya, cewa, "Al'umman da ka ɗauke su ka sã a biranen Samariya ba su san ayyukan da allahn ƙasar ke buƙata ba. Saboda haka a aiko da zakuna a cikinsu, kuma, duba, zakunan na karkashe mutane a wurin saboda basu san ayyukan da allahn ƙasar ke buƙata ba27Sa'an nan sarkin Asiriya ya ummurta, cewa, "Ɗauki ɗaya daga cikin firistocin wurin waɗanda ka kawo su daga wurin, kuma sai ya je ya zauna a wurin, ya kuma bari a koyar da su ayyukan da allan ƙasar ya sa a yi."28Sai ɗaya daga cikin firistocin da aka ɗauko daga Samariya ya zo ya zauna a Betel; ya koya masu yadda za su girmama Yahweh.29Kowacce kabila sun yi alloli na kansu, kuma suka sa su a wuraren da Samariyawa suka yi - kowacce kabila a biranen da suke zama.30Mutanen Babila suka yi Succot Benot; mutanen Kuta suka yi Nergal; mutanen Hamat suka yi Ashima;31Avvitawa suka yi Nibhaz da Tartak. Sefavitawa suka ƙone 'ya'yansu a wuta ga Adrammelek da Anammelek, allolin Sefavitawa.32Suka girmama Yahweh, kuma suka naɗa firistocin manyan wuraren daga cikinsu, waɗanda ke yin masu hadaya a masujadai na tuddan wuraren.33Suka girmama Yahweh suka kuma bauta wa alloli na kansu, bisa ga al'adar al'umman da aka kawar.34Har wa yau suna ci gaba da al'adun dã. Basu girmama Yahweh, ko su bi farilla da umurni da doka, ko dokokin da Yahweh ya ba mutanen Yakubu - wanda ya kira Isra'ila ba -35kuma wanda Yahweh ya yi alƙawari ya kuma ummurce su, "Kada ku ji tsoron waɗansu alloli, ko ku russunar da kanku gare su, ko ku bauta masu ko ku yi masu hadaya.36Amma Yahweh, wanda ya fito da ku daga ƙasar Masar da iko mai girma da dantse a ɗage, shi ne wanda za ku girmama; gare shi ne za ku yi ruku'u, kuma gare shi za ku yi hadaya.37Da Farillan da ummurnan da attaura da dokokin da ya rubuta domin ku, za ku tsare su har abada. Saboda kada ku ji tsoron waɗansu alloli,38kuma alƙawarin da na yi da ku, ba zaku mance ba; kuma ba za ku girmama waɗansu alloli ba.39Amma Yahweh Allahnku shi ne wanda za ku girmama. Zai ƙuɓutar da ku daga ikon maƙiyanku."40Ba za su saurara ba, saboda sun ci gaba da yin abin da suke yi a baya.41Don haka al'umman sun ji tsoron Yahweh suka kuma bauta wa ƙerarrun sifofinsu, kuma 'ya'yansu suka yi hakan kuma - kamar yadda 'ya'yan 'ya'yansu suka yi. Suka ci gaba da yin abin da kakaninsu suka yi har wa yau.
Hoshea ya zama sarkin masarautar arewa ta Isra'ila.
Wannan sunan mutum ne.
Samariya ita ce babban birnin Isra'ila.
Bai yi biyayya da dokokin Yahweh ba kamar yadda aka ba Musa. "A gaban" magana ta hukunci ko ra'ayi. AT: "mugunta ga Yahweh"
Wannan sunan mutum ne.
Hoshea kuwa ya yi yadda Sarkin Asiriya ya umarta a kawo masa kuɗi don kada sarki ya hallaka Isra'ila.
Wannan sunan mutum ne.
"kowace shekara"
"saka Hosheya a kurkuku"
sanya sojoji a kusa da garin don tilasta shi ya mika wuya
Sunan "Isra'ila" magana na nufin mutanen da suke zama a wurin. AT: "ya ɗauki mutanen Isra'ila zuwa Asiriya"
Waɗannan sunayen wurare ne.
Wannan shi ne sunan mai mutane kungiyar ne.
Wannan na nufin kama Isra'ilawa da Asiriyawa.
"Hannu" magana ne don sarrafa, izna ko iko. AT: "sarrafawar"
"Tafiya" magana ne ga hanyoyi ko tsarin halayen mutane da suke amfani da su a rayuwar su. AT: "yin ayyukan"
Waɗannan kalmomin yana nuna cewa bautar gumakan ƙarya sun yaɗu. AT: "a kan tsaunuka masu tsayi da ƙarƙashin dukkan koren itace"
Labarin ya ci gaba da taƙaita hukuncin Yahweh a kan Isra'ila.
Hanyoyi masu yiwuwa na bayar da wannan: 1) "sun aikata mugayen abubuwa marasa yawa waɗanda suka sa Yahweh ya yi fushi" ko 2) "aikata mugayen abubuwa masu yawa waɗanda suka sa Yahweh ya yi fushi"
Abin da Yahweh ya yi musu gargaɗi ne
Yahweh ya yi magana ta bakin annabawa.
"Ku daina aikata muguntar da kuka kasance kuna aikatawa"
Annabawan Yahweh ne ya aiko su don su tunatar da jama'ar Allah da umarnansu ko kuma yi musu dã'a.
Sun ƙi yarda su bi dokokin Allah kuma suka dogara ga Yahweh a matsayin Allahnsu.
Sun ƙi yin biyayya ga dokokin Allah.
Sun bi ayyukan mutanen da suke kewaye da su.
"kar a kwafa"
Sifofin zubi na ƙarfe shi ne abubuwa ne da aka sanya ta hanyar zuba baƙin ƙarfe mai narkewa a cikin nau'i don yin sifa.
yayi amfani da sihiri wajen faɗi abin da zai faru a gaba
Don "sayar da kansu" magana ne don aikata gaba ɗaya don yin abin da mugunta. AT: "sun ba da kansu ga yin abin da Yahweh ya ce mugaye ne"
"Wuri" magana ne ta kasancewa daga hankalin Yahweh don haka bai daina kula da su ba. AT: "cire su daga hankalin sa" (Duba: metonymy)
AT: "mutanen Yahuda"
"Yahweh ya hori Isra'ila"
"Hannun" magana ne don sarrafa, iko ko izni. AT: "mika su ga waɗanda suka washe dukiyoyinsu"
"gabansa" magana ne don kulawa da kulawa. AT: "har sai ya kawar da su duka" ko "har sai sun daina kasancewa a gabansa"
"Ya yago" anan wani magana ne na cirewar tashin hankali. AT: "Yahweh ya kawar da jama'ar Isra'ila"
"daga mulkin zuriyar Dauda"
"ya juya Isra'ila daga bin Yahweh"
"Isra’ilawa ba su daina aikata waɗannan zunubai ba” ko kuma “ba su daina aikata waɗancan zunubai ba”
"Wuri" a nan wani magana ne don kulawa da kulawa. AT: "saboda haka Yahweh ya kawar da jama'ar Isra'ila daga hankalin shi da kulawa"
Hukuncin Yahweh ya ci gaba da sabuwar mazaunan Asiriyawa waɗanda ke yin addininsu na arna.
Waɗannan wurare ne a daular Asiriya.
"A lokacin da waɗannan mutanen suka fara zama a wurin"
"Mutanen da kuka ƙaura daga wasu ƙasashe, kuka aika zuwa biranen Samariya"
"ba ku san yadda za ku bauta wa Allahn da Isra'ilawa suke bauta wa a cikin wannan ƙasa ba"
"Ɗauki firist wanda ya komo daga Samariya a can"
"bari firist ɗin Samariya ya koyar da mutanen da ke zama a yanzu"
Waɗannan sunayen alloli ne, namiji da mace.
Waɗannan sune sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen mutane da kungiyoyin.
"suka ba da 'ya'yansu nasu" ko "ƙona 'ya'yansu a cikin wuta a matsayin hadaya"
Wannan yana nufin mutanen arna ne waɗanda sarkin Asiriyawa ya koma biranen Samariya.
"Suna ci gaba da rayuwa iri ɗaya kamar yadda suke a da"
Mutanen suna sha'awar neman Yahweh ne kawai. Ba su da sha'awar ko basu san Yahweh ba yana sha'awar hulɗa da su.
Kalmomin "ɗaga hannu" ta nuna iko da ma'ana dai-dai wannan abu "babban iko." AT: "da iko sosai"
"yi musu biyayya"
"Saurara" a nan wani misali ne don kulawa da aiki akan umarnin. AT: "Ba su yi biyayya"
Waɗannan alumman sun yi tsoron Yahweh ne kawai har zuwa ga sun gamsar da shi kamar yadda suka yi da allolinsu.
"kuma sun ci gaba tun daga wannan lokacin." Kalmomin "wannan rana" tana nufin lokacin da marubucin ya rayu.
1Yanzu a shekara ta uku na Hosheya ɗan Ela, sarkin Isra'ila, Hezekiya ɗan Ahaz, sarkin Yahuda ya fara mulki.2Yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki shekara ashirin da tara a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Abija; ita ɗiyar Zekariya ce.3Ya yi abin da ke dai-dai a fuskar Yahweh, ya na bin misalin dukkan abubuwan da Dauda, kakansa ya yi.4Ya kawar da tuddan wurare, ya rusar da ginshiƙan dutse, ya farfashe sandan Ashera. Ya kakkarya tagullar macijin da Musa ya yi, saboda a kwanakin dã mutanen Isra'ila suna ƙona mata turare; a na kiran ta "Nehushtan."5Hezekiya ya dogara ga Yahweh, Allahn Isra'ila, saboda bayansa babu wani kamarsa a cikin sarakunan Yahuda, koma a cikin waɗanda suka gabace shi.6Gama ya manne wa Yahweh. Bai daina binsa ba gama ya kiyaye dokokinsa, waɗanda Yahweh ya ummurci Musa.7Saboda haka Yahweh yana tare da Hezekiya, kuma duk inda ya je ya wadata. Ya yi wa sarkin Asiriya tawaye kuma bai bai bauta masa ba.8Ya kai wa Filistiyawa hari har Gaza da iyakar da ke kewaya, daga hasumiyar zuwa birni mai garu.9A shekara ta huɗu na Hezekiya, wadda ke dai-dai da shekara ta bakwai ta Hosheya ɗan Elah sarkin Isra'ila, Shalmanesar sarkin Asiriya ya kawo wa Samariya hari ya mamaye su.10A ƙarshen shekaru uku suka ɗauke ta, a shekara ta shida na Hezekiya, wanda ke shekara ta tara ta Hosheya sarkin Isra'ila; a wannan hanyar kuwa aka kame Samariya.11Sai sarkin Asiriya ya ɗauki Isra'la zuwa Asiriya ya sa su a Halah da kuma a kogin Habor a Gozan da biranen Medeyawa.12Ya yi wannan ne saboda ba su yi biyayya da muryar Yahweh Allahnsu ba, amma sun wofintar da ƙudurorin alkawarinsa, dukkan abin da Musa bawan Yahweh ya ummurta. Suka ƙi su ji ko su aikata shi.13Sa'an nan a shekara ta goma sha huɗu ta Sarki Hezekiya, Senakerib sarkin Asiriya ya kai wa dukkan birane masu garu na Yahuda hari ya kuma danƙe su.14Saboda haka Hezekiya sarkin Yahuda ya aika wa sarkin Asiriya, wanda ke Lakish da kalma, cewa, "Na yi maka laifi. Ka janye daga gare ni. Duk abin da ka ɗora mani zan ɗauka." Sarkin Asiriya kuwa ya umarci Hezakiya sarkin Yahuda ya bada talanti ɗari uku na azurfa da talatin na zinariya masu yawa.15Sai Hezekiya ya ba shi dukkan azurfan da ke gidan Yahweh da na cikin ma'aji na fãdar sarki.16Sa'an nan Hezekiya ya ciro zinariyar da ke ƙofofin haikalin Yahweh da kuma daga madogaran da aka kafa; ya ba da zinarin ga sarkin Assiriya.17Amma sarkin Asiriya ya shiryo gagarumin sojojinsa, Ya aiki Tartan da Rabsaris da babbar rundunar sojojin daga Lakish zuwa ga Sarki Hezekiya a Yerusalem. Suka yi tafiya ta hanyoyin su ka kai wajen Yerusalem. Suka nufi kududdufi na sama wurin kwanciyar ruwa, wanda ke a kan kwaruwa zuwa wurin wanki, suka tsaya ta wurin.18Sa'ad da suka yi kira ga Sarki Hezekiya, Eliyakin ɗan Hilkiya, wanda ke wakilin gidan da Shebna magatakarda da Yowa ɗan Asaf, mai rubutun rohoto suka je su sadu da su.19Sai shugaban rundunar sojojin ya ce masu su faɗa wa Hezekiya abin da sarki mai girma, sarkin Asiriya, ya faɗa: "Mene ne masomin karfin halinka?20Kana faɗin kalmomi marasa amfani ne kawai, cewa akwai tarayya da ƙarfi domin yaƙi. Ga wa kake dogara? har da za ka tayar mani?21Duba, ka dogara ga sandan tafiya na raunannan ciyayin Masar, amma idan mutum ya manne mata, za ta haɗu da hannunsa ta soke shi. Wannan ne abin da Fir'auna sarkin Masar ya ke ga duk wanda ya dogara gare shi.22Amma idan ka ce mani, 'Muna dogara ga Yahweh Allahnmu ne,' ba shi ne wanda Hezekiya ya ɗauke masa wuraren sama da bagaden ba, ya kuma cewa Yahuda da Yerusalem, 'Lallai sai kun yi sujada a gaban bagaden nan a Yerusalem'?23Yanzu dai, ina so in yi maka gudunmawa daga ubangijina sarkin Asiriya. Zan baka dawakai dubu biyu, idan za ka samar masu mahaya.24Ta yaya zaka ma iya karawa da mafi ƙanƙantar shugaban sojojin ubangijina? Ka bada ƙarfinka ga Masar domin karusai da mahaya!25Na taɓa zuwa nan in yi yaƙi in hallka ta ba tare da Yahweh ba? Yahweh ya ce mani, 'Ka kai wa ƙasar nan hari ka hallaka ta."'26Sa'an nan Eliyakim ɗan Hilkaya da Shebna da Yowa suka cewa shugaban rundunar, "In ka yarda ka yi magana da harshen Aramayik, don shi muka gane. Kada ka yi magana da mu da harshen Yahuda a kunnen mutanen da ke a bangon."27Amma shugaban rundunar ya ce masu, Ba maganar da ubangijina ya aike ni ga ubangijinku in faɗa kenan ba? Ba shi ya aiko ni wurin mazan da ke zaune a bangon, waɗanda za su ci kaãshinsu su kuma sha fitsarinsu tare da ku ba?"28Sa'an nan shugaban rudunar sojojin ya tsaya ya yi kira da babbar murya a harshen Yahudawa, cewa, "Ku saurari maganar sarki mai girma, sarkin Asiriya.29Sarkin ya ce, 'Kar ka bar Hezekiya ya ruɗe ka, gama ba zai iya ya ƙubutar da kai daga ikona ba.30Kada ku yarda Hezekiya yasa ku dogara ga Allah, cewa, "Hakika Yahweh zai cece mu, kuma ba za a ba da wannan birnin ga hannun sarkin Asiriya ba.""31Kada ku saurari Hezekiya, gama ga abin da sarkin Asiriya ya ce: 'Ku yi amana da ni ku kuma zo gare ni. Sa'an nan kowannen ku zai ci daga tasa kuringar inabi da itacen ɓaurensa ya kuma sha daga cikin randarsa.32Zaku yi haka har lokacin da zan zo in ɗauke ku in kaiku wata ƙasa mai kama da taku, ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, ƙasar gurasa da lambuna, ƙasar itatuwan zaitun da zuma, saboda ku rayu kar ku mutu.' Kada ka saurari Hezekiya sa'ad da yake ƙoƙarin rinjayarku, cewa, 'Yahweh zai cece mu.'33Ko akwai wani daga cikin allolin mutanen da ya ceto su daga hanun sarkin Asiriya?34Ina allolin Hamat da Arfad? Ina allolin Sefabayim da Hena da Ivvah? Sun ceto Samariya daga hannuna ne?35A cikin allolin ƙasashe, akwai wani allahn da ya ceci ƙasarsa daga ikona? Ta yaya Yahweh zai ceci Yerusalem daga ikona?"36Amma mutane suka yi shiru basu ce uffan ba, domin sarki ya bada umarni, "Kada ku amsa masa."37Sai Eliyakim ɗan Hikiya, wanda ke shugabantar gidan; Shebna magatakarda; da Yowa ɗan Asaf, mai ɗaukan rohoto, suka zo wurin Hezikiya da tufafinsu a yage, suka bada rahoto gare shi kan maganganun babban hafsan.
Hezekiya ya zama sarki bisa Yahuda a maimakon tsohonsa sarki Ahaz.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan sunan mace.
"A idanun" a nan magana ne don kulawar Yahweh da kulawa. AT: "Sarki Hezekiya ya yi abin da yake dai-dai ga Yahweh" ko "Hezekiya ya aikata abin da Yahweh ya ce dai-dai ne"
"Hezekiya ya kawar da wuraren tsafi na kan tuddai, ya rurrushe duwatsun tunawa, ya kuma farfashe sandan Ashera"
Ana iya fassara wannan sunan "Tagulla Maciji Tsafi."
Don "riƙe" magana ne don kasancewa da aminci da haɗin kai. AT: "Hezekiya ya kasance da aminci ga Yahweh" ko "Hezekiya ya kasance da aminci ga Yahweh"
"duk inda Hezekiya ya tafi ya yi nasara"
birni mai bango kewaye da shi
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan shi ne sunan mai mutane kungiyar.
"Saboda haka sarkin Asiriya ya umarci sojojinsa su kwato Isra'ilawa daga gidajensu, ya sa su zauna a cikin Asiriya"
"Murya" magana ne ta saƙon game da umarnin Yahweh. AT: "umarnin Yahweh"
Wannan sunan birni ne.
Biranen da ke da bango kewaye da su don kariya. Duba yadda zaka fassara "birni mai garu" a cikin 2 Sarakuna 18: 8.
"Zan biya muku duk abin da kuka nema daga gare ni"
Wannan shi ne wurin da ke cikin fãdar inda aka adana kuɗi da abubuwa masu mahimmanci.
Senakirib kuwa ya aika da runduna daga sojojinsa zuwa Yerusalem don su gana da sarki Hezekiya, tare da wakilai masu suna Tartan da Rabsaris.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Sarkin Asiriya
Sarkin Asiriya
Sarkin Asiriya ya kwatanta Masar da sanda mai rauni; kuna tsammanin hakan zai tallafa muku lokacin da kuka jingina shi, amma maimakon haka sai ya faskara kuma ya yanke muku. AT: "mai rauni daga Masar"
Wannan tambaya ta tabbata cewa masu sauraro sun san amsar kuma ana amfani dasu don girmamawa. AT: "Kuna buƙatar tuna cewa shi ne wanda manyan wurarensa ... Yerusalem"!
Ya yi wannan tambayar don ya jaddada cewa sojojin Hezekiya ba su da albarkatun da za su yi yaƙi. Yana kuma amfani da ƙari wajen yin ba'a ga rundunar Hezekiya. AT: Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) "Ba za ku iya yin nasara ko da ɗaya daga cikin mafi girman sojojin sarki ba." ko 2) "Ba za ku iya kayar da rukunin sojojin sarki ta hannun babban jami'insa ba."
Yayi wannan tambayar domin ya jaddada cewa Yahweh yana bayan nasarar sa don yin biyayya da umarnin rusa Isra'ila. AT: "YAhweh da kansa ya ce mana mu zo nan mu lalatar da ƙasar nan!"
"A cikin kunnuwa" magana ne don iya sauraro. AT: "saboda mutanen da suke tsaye a bangon birni za su ji ta kuma su ji tsoro"
Yana yin waɗannan tambayoyin yana zaton masu sauraron sun san amsoshin don jaddada manufarsu ta lalata da wulakanci shugabannin da mutanen Yerusalem. AT: "Maigidana bai aiko ni da kai da maigidanka ba, har ma don in yi magana da mutanen da ke wannan birni, waɗanda za su sha wahala tare da kai lokacin da za su ci ɗakinsu kuma su sha fitsarinsu don su rayu."
"Ikona" magana ne ta saboda ikon sarki. AT: "daga kansa" ko "daga ikon runduna"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Yahweh ba zai taɓa barin sojojin sarkin Asiriya su ci wannan birni ba"
"Ku fito daga cikin birni ku mika wuya gareni" ko "Ku yi yarjejeniya da ni in yi salama, ku fito daga cikin birni zuwa wurina"
Wadannan hanyoyin abinci da ruwa sune kalmomin tsaro da yalwa. Wannan ma hanya ce ta gama gari da aka bayyana wannan ra'ayin.
Yayi wannan tambayar domin girmamawa saboda sun san amsar. AT: "Babu wani gumakan mutanen da ya ceci su ... Asiriya."
Yayi wannan tambayar domin girmamawa saboda sun san amsar. AT: "Na halakar allolin Hamat da Arfad!"
Yayi wannan tambayar domin girmamawa saboda sun san amsar. AT: "Babu wata hanyar da Yahweh zai iya ceton Yerusalem daga ƙarfi na."
"wanda ya jagoranci faɗar sarki"
"mai rike da tarihi"
1Sai ya zamana sa'ad da sarki Hezekiya ya ji rohotonsu, ya yayyaga tufafinsa, ya rufe kansa da tsumma, ya je gidan Yahweh.2Ya aiki Eliyakim, wanda ke lura da gidan, da Shebna magatakarda, da dattawan firistoci, dukkan su saye da tufafin tsumma, ga annabi Ishaya ɗan Amoz.3Suka ce masa, "Hezekiya ya ce, 'wannan ranar ta ƙunci da tsutawa da bankunya, gama 'ya'ya sun kai lokacin haifuwa amma babu ƙarfi domin haifar su.4Yana yiwuwa Yahweh Allahnka zai ji dukkan kalmomin shugaban rundunar, wanda sarkin Asiriya ubangijinsa ya aiko don ya jã da Allah, ya kuma tsauta wa kalmomin da Yahweh Allahnka ya ji. To ka ɗaga murya cikin addu'arka domin ragowar da ke nan har yanzu.""5Saboda haka barorin sarki Hezekiya suka zo wurin Ishaya,6sai Ishaya ya ce masu, "Ku faɗawa shugabanku: 'Yahweh ya ce, "Kada ku ji tsoron kalmomin da kuka ji, waɗanda barorin sarkin Asiriya suka yi mani rashin kunya.7Duba, zan sa wani ruhu a cikinsa, sai ya ji wani rohoto ya koma zuwa ƙasarsa. Zan sa ya fãɗi ta takobi a nasa ƙasan.""'8Sa'an nan shugaban rundunan ya komo ya tarar sarkin Asiriya yana yaƙi da Libna, gama ya ji wai sarkin ya tashi daga Lakish.9Sa'an nan Senakirib ya ji cewa Tirhaka sarkin Kush da Masar sun yi shiri su yaƙe shi, sai ya aiki manzanni kuma ga Hezekiya da saƙo:10"Ku cewa Hezekiya sarkin Yahuda, 'Kada ka bar Allahnka wanda ka dogara gare shi ya ruɗe ka, cewa, "Ba zan ba da Yerusalem ga hannun sarkin Asiriya ba."11Duba, ka ji abin da sarkin Asiriya ya yi wa dukkan ƙasashe da ya hallakar da su sarai. To za ka kuɓuta?12Allolin al'ummai sun kuɓutar da su ne, al'umman da ubannina suka hallakar wato Gozan da Haran da Rezef da mutanen Eden a Tel Assar?13Ina sarakunan Hamat da na Arfad da na biranen Sefabayim da Ivvah?"'14Hezekiya ya karɓa wasiƙar daga manzannin ya karanta ta. Sai ya haura zuwa gidan Yahweh ya shinfiɗa ta a gabansa.15Sa'an nan Hezekiya ya yi addu'a a gaban Yahweh ya ce, '"Yahweh mai runduna, Allahn Isra'ila, Kai da ke zaune bisan kerubim, kai kaɗai ne Allah akan dukkan mulkokin duniya. Ka yi sammai da duniya.16Ka kasa kunnenka, Yahweh, ka saurara. Ka buɗe idanuwanka Yahweh, ka gani, ka kuma ji kalaman Senakerib, waɗanda ya aiko don ya yi wa Allah mai rai ba'a.17A gaskiya, Yahweh, sarakunan Asiriya sun hallakar da al'ummai da ƙasashensu.18Suka sa allolinsu cikin wuta, gama su ba alloli ba ne amma aikin hannuwan mutane ne, katako da dutse kawai. Don haka Asiriyawan suka hallaka su.19Yanzu, Yahweh Allahnmu, I na roƙe ka, ka cece mu, daga ikonsa, saboda dukkan mulkokin duniya su sani cewa kai, Yahweh, kai kaɗai ne Allah."20Sa'an nan Ishaya ɗan Amoz ya aiko da saƙo ga Hezekiya, cewa, "Yahweh, Allahn Isra'ila ya faɗi, 'Saboda ka yi addu'a gare ni game da Senakerib sarkin Asiriya, Na ji ka.21Wannan ita ce maganar da Yahweh ya faɗa game da shi: "Budurwan nan ɗiyar Sihiyona ta rena ka tana kuma yi maka dariyar reni. Ɗiyar Yerusalem na girgiza maka kanta.22Wane ne ka saɓa wa ka kuma yi wa reni? Wanda kuma ka ɗaukaka muryarka ka ɗaga idanuwanka cikin taƙama gãba da shi? Gãba da Mai Tsarkin Isra'ila!23Ta manzaninka ka saɓa wa Ubangiji, har ka ce, 'Tare da ɗumbin karusaina na kai duwatsu mafi tsawo, mafi tsawon tudddai ta Lebanan. Zan datse dogayen itatuwan sida da zaɓaɓɓun itatuwan Sifires a wurin. Zan shiga cikin manisancin kurminta, da dajinta da ya fi bada 'ya'ya.24Na gina rijiyoyi na kuma sha ruwan baƙuwar ƙasa. Na busar da dukkan kogunan Masar a ƙarƙashin tafin ƙafafuna.'25Ba ka taɓa jin yadda na ƙudura shi da daɗewa ba, na kuma yi shi tun zamanin zamanai ba? Yanzu zan aiwatar da shi. Kana nan domin rage birane masu wadata su zama kufai.26Mazaunansu, masu ƙarancin ƙarfi, suna a warwatse, kuma an kunyata su. Su ganyaye ne a fili, koriyar ciyawa, ciyawa a rufi ko a fili, da aka ƙone kafin ta yi girma.27Amma na san yadda kake zama a ƙasa da fitarka da shigarka, da tawayenka gãba da ni.28Saboda tayarwarka gãba da ni, kuma saboda taƙamarka ta kai kunuwana, zan sa ƙugiya a hancinka, da linzami a bakinka; zan komo da kai baya ta inda ka iso."29Wannan zai zama alama a gare ka: wannan shekarar za ku ci abin da ke girma a jeji, a shekara ta biyu kuma, abin da ya fita daga nan. amma a shekara ta uku kuma dole ka shuka ka girba, ka shuka gonakin inabi ka ci 'ya'yan itatuwansu30Ragowar gidan Yahuda da suka rayu za su sake yin saiwa su yi "ya'ya.31Gama daga Yerusalem za a fito da ragowa, daga Tsaunin Sihiyona waɗanda suka tsira za su zo. Himmar Yahweh mai runduna za ta yi haka.32Saboda haka Yahweh ya faɗi haka game da sarkin Asiriya: "Ba zai zo cikin birnin ko ya harba kibiya a nan ba. Ko kuwa ya zo gabansa da garkuwa ko ya gina sansani gãba da shi ba.33Ta hanyar da ya zo, ta nan kuma zai tafi; ba zai shiga wannan birnin ba - wannan furcin Yahweh ne."34Gama zan kãre wannan birnin in kuɓutar da shi, domin kaina da kuma domin bawana Dauda."'35Sai ya zamana a daren nan da mala'ikan Yahweh ya je ya kai hari ga sansanin Asiriyawa, ya sa sojoji 185,000 suka mutu. Sa'ad da mazaje suka tashi da sassafe, sai ga gawawwaki kwance ko'ina.36Saboda haka Senakerib sarkin Asiriya ya bar Isra'ila ya tafi gida ya zauna a Nineba.37Bayan 'yan lokuta ƙaɗan, yayin da yake yin sujada a gidan allansa Nisrok, sai 'ya'yansa Adrammalek da Shareza suka kashe shi da takobi. Sa'an nan suka tsere zuwa ƙasar Ararat. Sai Esarhadon ɗansa ya zama sarki a madadinsa
Wannan wani hanya ce na cewa "haikalinYahweh."
Dukkan waɗannan sunayen mutane ne
"Hezekiya ya aiki Eliyakim"
"dukkan su na sanye da tufafin tsumma"
Anan "rana" na wakiltar a wani lokaci. AT: "wannan lokacin ƙunci ne"
Wannan karin magana ne da ke bayyana mutanen da shuganansu sun zama masu kumamaci har basu da karfi da zasu yaki abokan gaba.
"Kalmomi" na nufin ga saƙon da ke cikin wannan kalmomi. AT: "dukkan saƙon"
"Zan sarrafa halin sarkin Asiriya, don haka idan ya sami rahoto, zai so ya koma ƙasarsu"
"Zan rinjayi tunanin sa" ko "Zan sa shi yin wani ra'ayi daban." Anan “ruhu” mai yiwuwa yana nufin halinsa ne da tunanin sa, maimakon nuna ruhu.
"Fãɗi da takobi" magane ne don kashe shi. AT: "Zan sa shi ya mutu da takobi" ko kuma "Zan sa wasu mutane su kashe shi da takobi"
"wakilin shugaban Asiriya a hannun sarki"
"gano cewa sojojin Asiriyawa suna yaƙi"
Waɗannan sunayen biranen a masarautar Yahuda.
Waɗannan sunayen mutane ne.
"sun shirya sojojinsa don su yaƙi ga Asiriyawa"
"saboda haka Senakirib ya aika"
Wannan shi ne saƙon da Senakirib, sarkin Asiriya, ya aika wa sarki Hezekiya.
"Kada ku gaskata Allahnku wanda kuke dogara dashi. Yana kwance lokacin da yake faɗi"
"Hannu" shi ne magana don sarrafa, izni ko iko. AT: "ikon mulkin Asiriya"
"Ku lura, kun dai ji" ko "Tabbas kun ji." Anan "duba" aka yi amfani dashi don jan hankalin abin da yake shirin faɗi na gaba.
Senakirib yayi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa Allah ba zai iya ceton su ba. AT: "Allahnku ba zai kuɓutar da ku ba." ko kuma "Ba za ku iya kuɓuta ko dai ba!"
Saƙon Senakirib ga Sarki Hezekiya ta ci gaba.
Wannan tambaya ta tabbata cewa Hezekiya ya san amsar kuma yana ba da muhimmanci. AT: "Allolin al'ummai, al'ummai sun ... lalace" "Gozan ... Assar" "hakika ba su kubutar da su ba!"
"sarakunan Asiriya na baya" ko "sojojin tsoffin sarakunan Asiriya"
Waɗannan duk sunayen wurare ne.
Wannan yana nufin wasiƙar da Senakirib Sarkin Asiriya ya aika wa Hezekiya 2 Sarakuna 19:8.
Wataƙila kuna buƙatar fayyacewa cewa kerubobin su ne waɗanda suke kan akwatin alƙawarin. Marubutan Littafi Mai Tsarki sukan yi magana game da akwatin alƙawari kamar dai shi ne matasin ƙafar Yahweh wanda ya hau ƙafafunsa yayin da yake zaune a kursiyinsa a sama. AT: "Ku waɗanda ke zaune a kursiyinku a saman kerubobin a kan akwatin alƙawari"
Sarki Hezekiya ya ci gaba da yin addu'a ga Yahweh bayan ya sami wasiƙar daga hannun Senakirib Sarkin Asiriya.
Kalmomin "Juya kunnenka" da "saurare" suna nufin abu ɗaya ne kuma ƙara girmamawa ga roƙon. AT: "Ya Yahweh, don Allah ka saurari abin da yake faɗi"
Kalmomin "Buɗe idanunku" da "gani" suna nufin abu ɗaya kuma ƙara ƙarfafawa ga roƙon. AT: "Ya Yahweh, don Allah a kula da abin da ke faruwa"
"Sarakunan Asiriya sun ƙona gumakan sauran al'umma"
"Asiriyawa sun lalata duka al'ummai da alloli" gumakan "
"Ina rokonka"
"daga ikon Sarkin Asiriya" ko "daga sojojin Sarkin Asiriya"
"Yarinya budurwa" anan magana ne don mutanen Yerusalem kamar suna ƙarami, mai kauri da kyau. An yi amfani da kalmar 'yar' don ba da halaye na sirri ga biranen wasu marubutan Littafi Mai Tsarki. AT: "kyawawan mutanen Yerusalem"
Duk waɗannan jumlolin sun yi niyyar bayar da ma'ana iri ɗaya.
"Ɗiyar" ita ce magana don mutanen Yerusalem. AT: "Mutanen birnin Yerusalem"
Wannan matakin kwatanci ne na nuna girman kai ga girman Asiriyawa. AT: "ya raina ku"
Yahweh yana amfani da tambayoyi don tsauta wa Sennakerib. AT: "Ka ƙasƙantar da ni ko kuma an kalle shi da girman kai, bayani ga Allah na Isra'ila, Yahweh."
Wannan shi ne jawabin da Yahweh ya faɗa wa bakin annabi Ishaya, zuwa ga sarki Hezekiya game da sarki Sennakerib.
"saɓa" shi ne tsayayya a fili ko izgili.
Waɗannan alherin da Sennakerib ya yi kawai zai zama rundunar sojojinsa za su iya cika shi. Kalmar suna "Na" tana wakiltar shi da rundunarsa.
Wannan abin alfahari ne da Sennakerib yana da sojoji da yawa har ƙafafunsu suka bushe ruwa sa’ad da suka haye wani kogi. Wannan ƙari ne don ƙarfafa yawan sojojin da yake da shi. AT: "Kuma ta hanyar tafiya cikin rafin Masar, mun bushe su duka!"
Wannan ya ci gaba da maganar Yahwehi ya faɗa wa bakin annabi Ishaya, game da sarki Hezekiya da sarki Sennecherib.
Don yin ma'anar wannan tambaya mai ƙarfi cewa mai sauraro ya san amsar. AT: "Tabbas kun san yadda ... lokuta."
Wannan yana ci gaba da amfani da misalai idan aka kwatanta raunana waɗanda Asiriyawa suka ci gaba zuwa tsire-tsire mai rauni a cikin mawuyacin yanayi don haɓaka cikakke. AT: "kamar ciyawa kafin ta girma" ko "kamar ciyawa kafin ta yi girma"
"fushin fushi game da ni"
"Kunnuwa" magane ne don sauraro ko ji. AT: "saboda na ji maganganunku masu girman kai"
"ƙugiya" da linzami
Ishaya a nan yana magana ne da sarki Hezekiya.
"yayi girma ba tare da an dasa shi ba"
Wannan kwatancin yana kwatanta maido da ragowar zuwa tsiro waɗanda ke ɗauka kuma suna haifar da sakamako. AT: "Mutanen Yahuda waɗanda suka dawwama za su komar da rayuwarsu da wadatarsu" ko "Mutanen da suka ragu a cikin Yahuda za su yi arziki su sami yara da yawa"
"Babban karfi na Yahweh zai sa hakan ta kasance"
Wannan shi ne ƙarshen saƙon da Ubangiji ya faɗa, ta bakin annabi Ishaya zuwa ga Sarki Hezekiya.
"Kibiya" yana wakiltar duk kayan aikin yaƙi da lalata. AT: "kuma ba wani gwagwarmaya a nan"
"kuma ba za su ƙara gina manyan tuddai na ƙasa ba daga bangon birni don ba su damar kai harin a cikin birnin"
Yahweh yayi magana da kansa da sunan don ya tabbatar da gaskiyar abin da yake faɗa. AT: "Wannan shi ne abin da Yahweh ya ayyana" ko "wannan ne abin da Ni, Yahweh, na ayyana"
"saboda darajar kaina da kuma saboda abin da na yi wa Sarki Dauda alkawari, wanda ya bauta mini da kyau"
"Hakan ya faru"
"sojoji dubu ɗari da tamanin da biyar"
"Lokacin da mutanen da suka ragu da rai sun tashi"
Waɗannan sunayen mutane ne.
1A kwanakin nan Hezekiya ya yi rashin lafiya har ya kusa da mutuwa. Saboda haka annabi Ishaya ɗan Amoz, ya zo gare shi, ya ce masa, "Yahweh ya ce, 'Ka shirya gidanka; gama zaka mutu, ba zaka rayu ba."'2Sa'an nan Hezekiya ya juya fuskarsa ga bango ya yi addu'a ga Yahweh yana cewa,3"In ka yarda Yahweh, ka tuna da yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukkan zuciyata, da kuma abubuwan masu kyau da na yi a fuskarka." Sai Hezekiya ya yi kuka.4Kafin Ishaya ya fita cikin tsakiyar fãdar, maganar Yahweh ya zo gare shi, cewa,5"Ka juya baya, ka cewa Hezekiya, shugaban mutanena, 'Wannan shi ne abin da Yahweh, Allahn Dauda kakanka na asali, ya ce: "Na ji addu'arka, na ga hawayenka. Ina gab da warkar da kai a rana ta uku, kuma za ka haura zuwa gidan Yahweh.6Zan ƙara shekaru goma sha biyar ga rayuwarka, zan kuɓutar da wannan birnin daga hannun sarkin Asiriya, kuma zan kare birnin nan domin kaina domin kuma bawana Dauda"""7Sai Ishaya yace, "Ka ɗauki curin ɓaure."Su ka yi haka suka sa a marurunsa, sai ya samI lafiya.8Hezikiya ya cewa Ishaya, "Mene ne zai zama alamar cewa Yahweh zai warkar da ni, da kuma zai sa ni in je haikalin Yahweh a rana ta uku?"9Ishaya ya amsa, "Wannan ne zai zama alama dominka daga Yahweh, cewa Yahweh zai yi abin da ya faɗa. Inuwa ta yi gaba da taki goma, ko ta yi baya da taki goma?"10Hezekiya ya amsa, "Abu mai sauki ne ga inuwa ta yi gaba da taƙi goma. A'a, bari Inuwa ta yi baya da taƙi goma."11Sai annabi Ishaya ya yi kira ga Yahweh, sai ya komo da inuwar taƙi goma baya, daga inda ta motsa a matakalin Ahaz.12A lokacin nan Marduk-Baladan ɗan Baladan sarkin Babila ya aika da wasiƙu da kyautai ga Hezekiya, gama ya ji cewa Hezekiya ba shi da lafiya.13Hezekiya ya saurari wasiƙun nan, sai ya nuna wa manzaNnin dukkan fǎda da abubuwa masu daraja da azurfa da zinariya da kayan ƙanshi da mai, mai daraja da gidan ajiyar kayan yaƙi da dukkan abin da ke samuwa a gidajen ajiyarsa. Babu wani abu a gidansa, ko a mulkinsa, da Hezekiya bai nuãna masu ba.14Sa'annan annabi Ishaya ya zo wurin sarki Hezekiya ya tambaye shi, "Mene ne waɗannan mazajen suka ce maka? Daga ina suka fito?" Hezekiya ya ce, "Sun zo daga ƙasa mai nisa ta Babila."15Ishaya ya tambaye shi, "Mene ne suka gani a gidanka?" Hezekiya ya amsa, "Sun ga kome a gidana. Babu wani abu cikin abubuwa masu daraja da ban nuna masu ba."16Sai Ishaya ya cewa Hezekiya, "Ka saurari maganar Yahweh:17'Duba, ranakun na kusatowa da kowanne abu a fǎdarka, da abubuwan da kakaninka suka ajiye har zuwa yau, za a ɗauke su zuwa Babila. Babu abin da zai rage, inji Yahweh.18'Ya'yan da aka haifa maka waɗanda kai da kanka kake mahaifinsu - za a ɗauke su, zasu kuma zama bãbãni a fãdar sarkin Babila."'19Sa'annan Hezekiya ya cewa Ishaya, "Maganar Yahweh da ka faɗa tana da kyau." Saboda yana tunanin, "Ba za a sami salama da zaman lafiya a kwanakina ba?"20Game da waɗansu zantuttuka da suka shafi Hezekiya, da dukkan ikonsa da yadda ya yi tafki da wuriyar ruwa, da yadda ya kawo ruwa cikin birnin - ba a rubuce suke cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?21Hezekiya ya yi barci tare da kakaninsa, sai Manasse ɗansa ya zama sarki a madadinsa.
"Gidan" magana ne ga abin da ke ƙarƙashin ikon Hezekiya. AT: "Ka ba da umarnin ƙarshe ga danginka da gwamnatinka"
Wannan hanya ce ta gama gari, karin magana, da roƙon Yahweh ya tuna. AT: "tuna"
Wannan karin magana ne. AT: "ya rayuwata"
Anan gani yana wakiltar hukunci ko kimantawa. AT: "a hukuncin ku"
"Kalma "maganar" tana wakiltar saƙon da Yahweh ya saukar wa Ishaya. Wannan ita ce hanyar gama gari, karin magana. AT: "Yahweh ya faɗi maganarsa"
Kashi na biyu yana ƙarfafa bangare na farko don yin saƙo guda ɗaya. AT: "Na ji addu'arku kuma na ga hawayenku"
"kwana biyu daga yanzu". Ranar da Ishaya ya faɗi wannan ita ce ranar farko, don haka “rana ta uku” zata zama dai-dai da “kwana biyu daga yanzu.”
Maganar Yahweh zuwa ga Sarki Hezekiya ta hannun annabi Ishaya ya ci gaba.
"shekaru 15"
"Hannun" yana magana don ƙarfi, iko da sarrafawa. AT: "daga sarrfawan sarkin Asiriya"
"manna da aka yi da curin ɓaure"
"Barorin Hezekiya sun yi haka, suka sa liƙa a kan ciwon na Hezekiya"
Za'a iya bayyana asalin "inuwar" a sarari. AT: "Shin kana son Yahweh ya sanya inuwa ta hanyar hasken rana ta lalacewa a matakalar zuwa gaban matakai goma ko komawa zuwa matakai goma?" .
Wannan magana tana nufin “matakin Ahaz” a cikin 2 Sarakuna 20:11. Wannan wata hanya ce ta musamman da aka gina wa Sarki Ahaz a hanyar da matakan sa suka nuna a dai-dai lokacin da rana take haskakawa yayin da rana take haskawa. Ta wannan hanyar, staircase ɗin ya ba da labari don lokacin.
Me yasa "abu ne mai sauki" za'a iya bayyana a sarari. "Abu ne mai sauki ka sa inuwa ta motsa matakai goma, domin wannan abu ne da ya dace a yi shi"
Wannan wata hanya ce ta musamman da aka gina wa Sarki Ahaz a hanyar da matakan sa suka nuna a dai-dai lokacin da rana take haskakawa yayin da rana take haskawa. Ta wannan hanyar, staircase ɗin ya ba da labari don lokacin. AT: "matakan da aka gina wa sarki Ahaz"
Wannan sunayen sarkin Babila da yayansa maza.
"la'akari da waɗannan haruffa" ko "sun ji saƙon daga sarkin Babila"
Anan "Babu wani abu ... bai nuna masu ba" wani ƙari ne wanda aka yi amfani da shi don ƙarfafawa. Wannan yana nuna cewa Hezekiya ya nuna musu dukkan kyawawan abubuwansa. Wannan za a iya bayyana shi da kyau. AT: "Hezekiya ya nuna masa duk abin da yake da muhimmanci a cikin gidansa da kuma cikin mulkinsa"
Wannan yana nuni ga mutanen da aka aika wa Sarki Hezekiya tare da sako da kuma kyaututtuka daga Merodak Baladan.
Hezekiya ya maimaita irin wannan ra'ayin a cikin hanyoyi biyu don ƙarfafa ma'anarsa.
"Ba komai" da "ba" su fasa wa juna fita don tabbatar da ra'ayin ya zama dai-dai. Ana amfani da wannan ƙari don ƙarfafawa. AT: "Na nuna musu gaba daya kyawawan abubuwan na"
Abin da ya sa Ishaya ya yi magana za a iya bayyana a sarari. AT: "Saboda haka, Ishaya ya san Hezekiya ya kasance wauta ne ya nuna wa mutanen duka abubuwansa masu tamani, sai Ishaya ya ce masa"
"saƙon Yahweh"
"Ku saurare ni, wata rana wani lokaci zai zo" An yi amfani da "duba" don jan hankalin abin da Ishaya yake shirin gaya wa Hezekiya.
"Kwanaki" yana magana na nufin ga komawa zuwa lokacin da ba a bayyana ba.
"Saboda Hezekiya yayi tunani"
Hezekiya ya yi wannan tambaya domin ƙarfafa sanin sanin amsar. AT: "Na iya tabbata cewa za a sami kwanciyar hankali da kwanciyar hankali a cikin kwanakinina."
Ana amfani da wannan tambaya don tunatar da mai karatu cewa an rubuta waɗannan abubuwan. Duba yadda ake fassara wannan kalmar a 2 Sarakuna 8:23. AT: "An rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuda."
1Manasse na da shekaru goma sha biyu sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki shekaru hamsin da biyar a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.2Ya yi aikin mugunta a gaban Yahweh, kamar abubuwan banƙyama na al'umman da Yahweh ya kora a gaban mutanen Isra'ila.3Gama ya sake ginin wuraren bisa da Hezekiya mahaifinsa ya rurrushe, sai ya gina bagadi domin Ba'al, ya yi sandan Ashera, kamar yadda Ahab sarkin Isra'ila ya yi, ya kuma russuna wa dukkan tauraron sammai ya yi masu sujada.4Manasse ya gina bagadai a cikin gidan Yahweh, ko da yake Yahweh ya ummurta, "A Yerusalem ne sunana zai kasance har abada."5Ya gina bagadi domin dukkan taurarin sammai a filayen ciki biyu da ke gidan Yahweh.6Ya sa ɗansa ya wuce ta wuta, ya yi sihiri da dubã da ma'amula da waɗanda ke magana da matattu da waɗanda ke magana da ruhohi. Ya yi mugunta da yawa a gaban Yahweh, yana sa shi yin fushi.7Sarrafaffiyar siffa ta Ashera da ya yi, ya sata a gidan Yahweh. A game da wannan gidan ne Yahweh ya yi magana da Dauda da Suleimanu ɗansa; ya ce: "A wannan gidan da kuma Yerusalem ne, inda na zaɓa daga dukkan ƙabilun Isra'ila, da zan sa sunana har abada.8Ba zan sa ƙafafun Isra'ila su ƙara fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, Idan har zasu kula su yi biyayya da dukkan abin da na ummurce su, su kuma bi dukkan dokokin da bawana Musa ya Ummurce su."9Amma mutanen ba su ji ba, Manasse kuma ya jagorance su ga yin aikin mugunta fiye da al'umman da Yahweh ya hallakar a gaban mutanen Isra'ila.10Sai Yahweh ya yi magana ta wurin bayinsa annabawa, cewa,11"Saboda Manasse sarkin Yahuda ya yi waɗannan abubuwan banƙyama, ya kuma aikata mugunta fiye da dukkan abin da Amoriyawan da suke gabaninsa suka yi, ya kuma sa Yahuda ya yi zunubi da gumakansa,12don haka Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka: Duba, Ina gab da kawo bala'i a Yerusalem da Yahuda wanda duk wanda ya ji abin, dukkan kunuwansa za su ƙaɗu.13Zan miƙa a saman Yerusalem layin magwajin da zan gwada Samariya, da layin ma'aunin gwada gidan Ahab; Zan share Yerusalem fes-fes, kamar yadda mutum ke wanke kwano, yana share ta da kuma goge ta yana juya ta ko'ina.14Zan jefar da ragowar gãdona in ba da su ga hannun maƙiyansu. Za su zama waɗanda aka yi wa laifi da ganima ga dukkan makiyansu,15saboda sun yi abin mugunta a gabana, suka kuma zuga ni ga fushi, tun daga ranar da kakaninsu suka fito daga Masar, har yau."16Haka kuma, Manasse ya zub da jinin adalai da yawa, har sai da ya cika Yerusalem daga gefe ɗaya zuwa wani gefen da mutuwa. Banda zunubin da ya sa Yahuda suka yi, sa'ad da suka yi mugunta a gaban Yahweh.17A game da sauran zantuttukan da ya shafi Manasse da dukkan abin da ya yi, da zunuban da ya aikata, ba a rubuta su cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?18Manasse ya yi barci tare da kakaninsa aka bizne shi a lanbun gidansa, a lanbun Uzza. Amon ɗansa ya zama saki a madadinsa.19Amon na da shekaru ashirin da biyu sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki shekaru biyu a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet; ita ɗiyar Haruz na Jotba ne.20Ya yi akin mugunta a gaban Yahweh, kamar yanda Manasse mahaifinsa ya yi.21Amon ya bi dukkan hanyar da mahaifinsa ya yi tafiya ya kuma bauta wa gumakan da mahaifisa ya bauta wa, ya yi masu ruku'u.22Ya ƙi Yahweh, Allah na ubanninsa, bai kuma yi tafiya a hanyar Yahweh ba.23Barorin Amon suka shirya maƙarƙashiya gãba da shi suka kashe shi a cikin gidansa.24Amma mutanen ƙasar suka kashe dukkan waɗanda suka yi wa sarki Amon maƙarƙashiya, sai suka maida Yosiya, ɗansa sarki a madadinsa.25Game da sauran zantuttukan da suka shafi Amon da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?26Mutanen suka bizne shi a kabarinsa cikin lambun Uzza, sai Yosiya ɗansa ya zama sarki a madadinsa.
Mahaifiyar Sarki Manasse
Gaban Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh ko tantancewa. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 3: 2. AT: "abin da ke mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ɗauka mugunta ne"
Wata ma'anar mai yiwuwa ita ce "gami da abubuwa masu ƙyama."
Da Manasse ya umarci ma'aikatansa su yi masa ginin. AT: "ya sake gina masujadai a ciki ... ya gina bagadai don Ba'al, ya yi sandan Ashtora" ko "ya sa ma'aikatansa su sake gina masujadai ... ya sa su gina wa bagadai don Ba'al, sun yi sandan Ashtora"
Labarin mulkin Sarki Manasse ya ci gaba.
Sunan magana ne ta mutum. AT: "Yerusalem ita ce ta har abada zan sanar da ni"
Hakan yana nuna cewa ya gina waɗannan bagadan ne domin mutane su iya yin hadayu su kuma yi wa taurari sujada. Hakanan, da ba zai gina waɗannan bagadai da kansa ba, a maimakon haka ya umarci ma'aikatansa su yi. AT: "Ya sa ma'aikatansa su gina bagadan a farfajiya biyu na haikalin Yahweh domin mutane su bauta wa taurari su kuma miƙa musu hadayu"
Wataƙila kuna buƙatar fayyace abin da ya sa ya sa aka jefa ɗansa cikin wuta da abin da ya faru bayan ya yi hakan. AT: "Ya ƙone ɗansa har ya mutu a matsayin hadaya ga alolinsa"
"nemi bayyani daga"
Gaban Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh ko tantancewa. Duba yadda zaka fassara irin wannan magana a cikin 2 Sarakuna 3: 2. AT: "abubuwa da yawa da suka yi mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abubuwa da yawa waɗanda Yahweh ya lamurta mugaye ne"
Labarin mulkin Sarki Manasse ya ci gaba.
Wataƙila Manasse bai yi aikin ba. Barorin sa za su yi aikin. AT: "da Manasse ya umarci barorinsa su yi"
Anan Yahweh ya sa "sunan" a cikin haikalin yana nuna shi a matsayin wurin da za a yi masa sujada. AT: "Ina son mutane su bauta mini har abada"
Kafafunsa magana ne na nufin wani mutum. AT: "jama'ar Isra'ila" ko "Isra'ilawa"
A nan "al'ummai" na nufin mutanen da suka rayu a ƙasar Kan'ana kafin Isra'ilawa su zo. AT: "har ma fiye da mutanen da Yahweh ya hallaka yayin da mutanen Isra'ila suka ci gaba a cikin ƙasar"
Wannan fassara ya fahimci wannan kalmar "don haka... yace" ya zama waɗannan annabawa. Wata ma'anar na iya zama cewa Yahweh na ambaton shi kansa kamar wani mutum : "gunki. Don haka Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka ... Duba"
Motsi jiki kwatanci ne na motsin zuchi da ya haifar da shi. AT: "duk wanda ya ji abin Yahweh yayi, dukkan kunuwansa za su ƙaɗu.
Kalmomin "layin aunawa" da "layin ma'aunin" magana ne ga matsayin da Yahweh yake amfani da shi don yanke hukunci a kan mutane. AT: "ku yi hukunci a kan Yerusalem ta hanyar da na yi amfani da ita lokacin da na yanke hukuncin Samariya da gidan Ahab"
Samariya ita ce babban birni kuma tana wakiltar dukkan mutanen Isra'ila. AT: "gãba da jama'ar Isra'ila"
kayan aiki da aka yi da nauyi mai nauyi da igiya na bakin ciki wanda aka yi amfani dashi don nuna idan bango yana madaidaiciya
"Zan watsar" ko "Zan ƙi"
Anan "hannun" abokan gaba suna nufin sarrafawan abokan. AT: "bari abokan gabansu su ci su kuma su mallaki ƙasarsu"
"Hakanan, Manasse" ko "Bugu da ƙari, Manasse"
Kalmomin "zubar da jini marasa laifi" kalmomi ne na kashe mutane da ƙarfi. Zai fi kyau a fassara wannan don mai karatu ya fahimci cewa wasu mutane sun taimaka wa Manas yin hakan. AT: "Manasse ya umarci sojojinsa su kashe mutane da yawa marasa laifi"
Wannan kalmonin yana nuna yawan mutanen da Manasse ya kashe a duk Yerusalem. Ana iya bayyana sunan "mutuƙar" a matsayin "mutanen da suka mutu." AT: "akwai mutane da yawa da suka mutu ko ina a cikin Yerusalem"
Wannan za a iya bayyana da shi a aikace kuma ya ɗauka cewa amsa tabbatacciya ce. Tambayar yana da magana kuma ana amfani dashi don girmamawa. Duba yadda ake fassara wannan kalmar a 2 Sarakuna 8:23. AT: "An rubuta su ... Yahuda." ko "za ku same su ... Yahuda."
Ma’anoni masu ma’ana su ne 1) “lambun da ya kasance mallakar wani mutum mai suna Uzza” ko 2) “Lambun Uzza.”
Waɗanan sunayen mutane ne.
Wannan sunan na mace ne
Wannan sunan birni ne.
Kalmar "mugunta" ana iya fassara shi kamar wannan jumla "abubuwan ke ...mugu. Anan "gaban" Yahweh na nufin yadda yake hukumci ko zartas da muhimam abubuwa. Fassara wannan kamar yadda ka yi a 2 Sarakuna 3:1. AT: "abubuwan da Yahweh ya kira su mugunta" ko " abubuwan da Yahweh ya na dubban su a matsayin mugunta.
"ya bi dukkan hanyoyin da mahaifinsa ya bi." Ana magana da hanyar da mutum yake rayuwa kamar wanda yake tafiya akan hanyar. AT: "ya rayu gaba ɗaya yadda mahaifinsa ya rayu"
"Ya rabu da Yahweh ko "bai mai da hankali ga Yahweh ba"
"Mun yi shiri tare da yin aiki tare don cutar da shi"
Wannan na asali ne. AT: "wasu daga cikin mutanen Yahuda"
"Mun yi shirye-shirye kuma munyi aiki tare don cutarwa." Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 21:23.
Wannan za a iya bayyanar da shi a aikace mai aiki kuma yana ɗaukar cewa amsa tabbatacciya ce. Tambayar yana da magana kuma ana amfani dashi don girmamawa. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 8:23. AT: "An rubuta su ... Yahuda." ko "za ku same su ... Yahuda."
Ma’anoni masu ma’ana su ne 1) “lambun da ya kasance mallakar wani mutum mai suna Uzza” ko 2) “Lambun Uzza.” Ka ga yadda ka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 21:18.
1Yosiya yana da shekaru takwas sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki shekaru talatin da uku a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Yedida (Ita ɗiyar Adayiya na Bozkat ce).2Ya yi abin da ya dace a gaban Yahweh. Ya yi tafiya a hanyar Dauda kakansa, bai kuma kauce mata zuwa dama ko hagu ba.3Sai ya zamana a shekara ta goma sha takwas ta sarki Yosiya, ya aike Shafan ɗan Azaliya ɗan Mashullam, magatakarda, zuwa gidan Yahweh, cewa,4"Jeka wurin Hilkiya babban firist ka gaya masa ya ƙirga ƙuɗin da aka kawo cikin gidan Yahweh, wanda masu gadin haikali suka tara daga mutane.5A ba da shi ga hannun ma'aikatan da ke lura da gidan Yahweh, su ba ma'aikatan da ke gidan Yahweh domin su yi gyare-gyare a haikali.6Su bada ƙuɗi ga kafintoci da magina, a kuma sayi katakon timba a buga dutse domin gyaran haikali."7Amma babu bukatar rohoton kashe kuɗin da aka ba su, saboda sun yi aiki da shi cikin aminci.8Hilkiya babban firist ya cewa Shafan magatakarda, "Na sami littafin dokoki a gidan Yahweh." Sai Hilkiya ya ba da littafin ga Shafan, sai ya karanta shi.9Shafan ya je ya kai littafin gun sarki, ya kuma sanar da shi, cewa, "Barorinka sun kashe kuɗin da aka samu a haikali kuma sun ba da shi ga hannun ma'aikatan da ke shugabancin lura da gidan Yahweh."10Sa'annan Shafan magatakarda ya faɗa wa sarkin, "Hilkiya firist ya ba ni littafi." Sai Shafan ya karanta wa sarki.11Sai ya zamana sa'ad da sarki ya ji kalmomin dokokin, sai ya yayyaga tufafinsa.12Sarkin ya ummurci Hilkiya firist da Ahikam ɗan Shafan da Akbor ɗan Mikayiya da Shafan magatakarda da Asayiya bawansa cewa,13"Ku je ku ji daga wurin Yahweh domina da mutanen da dukkan Yahuda, saboda kalmomin wannan littafin da aka samo. Gama fushin Yahweh a gare mu na da girma saboda kakanninmu ba su saurari kalmomin wannan littafin don yin biyayya game da dukkan abin da aka rubuta game da mu ba."14Sa'an nan Hilkiya firist da Ahikam da Akbor da Shafan da Asayiya suka je wurin annabiya Hulda, matar Shallum ɗan Tikvah ɗan Harhas, mai tsaron ɗakin da ake ajiyan sutura (tana zaune a Yerusalem a yankin sabon birnin), sai suka yi magana tare da ita.15Ta ce masu, "Wannan ne abin da Yahweh, Allahn Isra'ila, ya faɗI: 'Gaya wa mutumin da ya aike ki gare ni,16Ga abin da Yahweh ya faɗi: 'Duba, zan auko da bala'i ga wannan wurin tare da mazaunansa, bisa ga dukkan abin da aka rubuta a littafin da sarkin Yahuda ya karanto.17Saboda kun yashe ni kuka kuma ƙona turare ga waɗansu alloli, don su tsokane ni ga yin fushi da dukkan ayyukan da suka yi - don haka na fito da wutar hasalata gãba da wannan wurin, kuma ba za ta mutu ba."'18Amma ga sarkin Yahuda, Wanda ya aike ku ku nemi nufin Yahweh, ga abin da zaku ce masa: "Yahweh, Allah na Isra'ila ya faɗi haka: 'game da kalmomin da ka ji,19saboda zuciyarka ta yi taushi, ka kuma yi tawali'u a gaban Yahweh, sa'ad da ka ji abin da na faɗa gãba da wannan wurin da mazaunansa, akan yadda zasu zama kango da la'ana, saboda kuma ka yayyaga tufafinka ka yi kuka a gabana, Ni kuma na saurare ka - wannan furcin Yahweh ne.20Duba, Zan tara ka ga kakanninka, kuma za a tara ka ga kabarinka cikin salama. Idanuwanka baza su ga dukkan masifun da zan auko da su akan wurin nan ba.""" Sai mazajen suka mayar da saƙon ga sarki.
shekaru 31"
Wannan sunan mace ne.
Wannan sunan mutum ne.
Wannan sunan gari ne a Yahuda.
Anan “idanu” suna wakiltar tunanin Yahweh ne ko abin da ya yi la’akari da wani abu. AT: "Ya aikata abin da Yahweh ya ga ya yi dai-dai ne" ko kuma "Ya aikata abin da yake dai-dai bisa ga Yahweh"
"Ya bi duk al'amuran da kakanninsa Dauda ya yi" Aikin Yosiya kamar yadda ya yi an ambaci kamar yana tafiya a kan hanya guda ko kuma kamar yadda Dauda ya yi. AT: "Ya yi rayuwar da kakannin Dauda ya yi" ko kuma "Ya bi gurbin Dauda wanda ya kasance"
Yin biyayya ga Yahweh cikakke ana maganarsa kamar mutum yana kan madaidaiciyar hanya kuma bai juyo ba. AT: "bai yi wani abu da zai ɓata wa Yahweh rai" ko kuma "ya yi biyayya da dukan dokokin Yahweh”
Idan yarenku yana da hanyar da zai nuna alamar sabon ɓangaren labarin, la'akari da amfani da shi anan.
"shekara ta 18"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Anan "gidan Yahweh" da "haikalin" suna nufin abu ɗaya.
An yi amfani da kalmar "haura" saboda haikalin Yahweh ya fi tsayi fiye da inda sarki Yosiya yake. AT: "Ku tafi wurin Hilkiya"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "masu gadin haikalin da suka tara kuɗin daga hannun mutane sun kawo cikin haikalin Yahweh"
Anan "hannun" yana wakiltar masu aiki gaba ɗaya. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ka gaya wa Hilkiya ya ba da kuɗin ga ma'aikatan"
Saƙon daga Sarki Yosiya zuwa Hilkiya, babban firist, ya ci gaba.
Anan "su" yana nufin ma'aikatan da ke lura da gidan Yahweh cikin 2 Sarakuna 22:5.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ma'aikatan da ke lura da aikin ba lallai ne su ba da rahoton yadda suka yi amfani da kuɗin da masu gadin haikalin suka ba su ba"
"saboda sun yi amfani da kudin da gaskiya"
Wataƙila an rubuta waɗannan dokoki a kan littafi. Littafin gungura wani nau'in littafi ne da aka yi da doguwar takarda, papyrus ko fata.
Anan "hannun" yana wakiltar masu aiki gaba ɗaya. AT: "an ba shi ga ma'aikatan"
Anan "kalmomi" suna wakiltar saƙon doka ne. AT: "Na ji dokokin da aka rubuta a littafin" ko "sun ji dokokin da aka rubuta a cikin littafin"
Wannan aikin alama ne wanda ke nuna tsananin baƙin ciki ko makoki. (Duba: ranslate_symaction)
Waɗannan sunayen mutane ne.
An bayyana a sarari a cikin 2 Sarakuna 22:14 cewa sarki yana nufin mazan su je wurin matar annabiya na Yahweh don sanin nufin Allah.
Anan "kalmomi" suna wakiltar dokoki. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "dokoki a cikin wannan littafin da Hilkiya ya samo"
Ana magana da fushin Yahweh kamar wutar da take ci. AT: "Gama Yahweh yana fushi da mu sosai"
Wannan yana nufin dokar da aka baiwa Isra'ila. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "duk abin da Musa ya rubuta a cikin dokar da ya kamata mu yi" ko "duk dokokin da Allah ya ba ta hannun Musa ga Isra'ila"
Wannan sunan mace ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) mutumin da ya kula da tufafin da firistoci suka sa a haikalin ko 2) mutumin da ya kula da tufafin sarki.
Anan "kashi na biyu" yana nufin sabon ɓangaren birni wanda aka gina a gefen arewacin Yerusalem. Hakanan, "na biyu" shine tsari na 2. AT: "Ta yi zama a Yerusalem a cikin sabon ɓangaren birni" ko "ta zauna a cikin sabon sashin Yerusalem"
Anan “mutumin” yana nufin Sarki Yosiya.
An yi maganar Yahweh da ke sa mugayen abubuwa su faru kamar yadda masifa ita ce abin da zai iya kawowa wurin. AT: "Zan sa ummunan abubuwa su faru ga wannan wurin da waɗanda suke zaune"
"zuwa Yerusalem." Wannan yana nufin birnin Yerusalem wanda ke wakiltar ƙasar Yahuda dukka. AT: "ga Yahuda"
Saƙon da Yahweh ya aika wa sarki Yosiya ta hannun Hulda, annabiya, ya ci gaba.
Ana magana da fushin Yahweh kamar wutar da take ci. AT: "fushina a kan wannan wuri kamar wuta ne wanda ba za a iya kashe shi ba"
Anan "wuri" yana wakiltar mutanen da ke zama a Yerusalem da Yahuda. AT: "waɗannan mutane"
Anan "kalmomi" yana wakiltar saƙon da Hulda ya faɗa kawai. AT: "Game da sakon da kuka ji"
Anan "zuciya" tana wakiltar yanayin mutum ne. Jin ana magana ana maganar kamar zuciya tana da taushi. AT: "saboda kun ji tausayi" ko "saboda kun tuba"
Za a iya bayyana sunayen sunaye "lalacewa" da "la'ana" azaman tsofaffen magana da kuma fi’ili. AT: "da zan mai da ƙasar kufai, ina la'anta ta"
Yahweh yayi magana da kansa da sunan don ya tabbatar da gaskiyar abin da yake faɗa. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 19:33. AT: "Wannan shi ne abin da Yahweh ya ayyana" ko "wannan ne abin da Ni, Yahweh, na ayyana"
Shi ne karshen saƙon Yahweh ga sarki Yosiya ta hannun annabiya Hulda.
Bayanan biyu suna ma'ana dai-dai da wancan. Hanyoyi masu mutunci sune na cewa zai mutu. AT: "Don haka zan bar ka ka mutu, a binne ka cikin salama"
Anan "bazai gani ba" yana wakiltar rashin fuskantar wani abu. AT: "Ba za ku dandana ba"
An yi magana da Yahweh na haddasa mummunan abubuwa kamar da masifa wani abu ne da Yahweh zai kawo wurin. AT: "Mummunan abubuwa da zan sa in faru a wannan wuri"
1Sa'an nan sarki ya aiko da manzanni waɗanda suka tara masa dukkan dattawan Yahuda da Yerusalem.2Sai sarki ya haura zuwa gidan Yahweh da dukkan mazaunan Yahuda da Yerusalem da ke tare shi, da firistoci da annabawa da dukkan mutane, daga ƙanƙani zuwa babba. Sai ya karanta dukkan kalmomin littafin Alƙawarin da aka samu a gidan Yahweh a kunnuwansu.3Sarkin ya tsaya a gefen ginshiƙi ya yi alƙawari ga Yahweh cewa zai bi Yahweh ya kiyaye dokokinsa, da ummurnansa da farillansa, da dukkan zuciyarsa da dukkan ransa, ya kuma ka'idantar da kalmomin alƙawarin da aka rubuta a wannan littafin. Saboda haka mutanen suka yarda su tsaya akan alƙawarin.4Sa'an nan sarki ya ummurce Hilkiya babban firist da firistoci da ke ƙarƙashinsa da masu tsaron ƙofa su fitar da tasoshin da aka yi wa Ba'al da Ashera daga haikalin Yahweh, da dukkan taurarin sama. Ya ƙone su a bayan Yerusalem a filayen Kwarin Kidron, sa'an nan ya kwashe tokarsu zuwa Betel.5Ya kuma kawar da firistocin gumaka waɗanda sarakunan Yahuda suka naɗa don a ƙona turare a wuraren tuddai a biranen Yahuda da kewayen Yerusalem - waɗanda suka ƙona turare ga Ba'al, da rana da wata da duniyoyi da dukkan taurarin sama.6Ya fitar da sandan Ashera daga haikalin Yahweh, wajen Yerusalem zuwa Kwarin Kidron ya ƙona shi a wurin. Ya buge ta har ga ƙura ya zubar da ƙurar cikin kaburburan talakawa.7Ya rusa ɗakunan karuwai matsafa waɗanda ke a haikalin Yahweh, inda matan ke saƙa tufafin Ashera.8Yosiya ya fitar da dukkan firistoci daga biranen Yahuda ya ƙazantar da tuddan wuraren da firistoci ke ƙona turare, daga Geba zuwa Biyasheba. Ya rurrushe tuddan wuraren a kofofin da ke mashigin ƙofofin Yoshuwa (gwamnan birnin), a gefen hagu na ƙofar birnin.9Ko da shike ba a bar firistocin waɗannan tuddan wuraren su yi aiki a bagadin Yahweh a Yerusalem ba, sun ci gurasa mara yisti cikin 'yan'uwansu maza.10Yosiya ya ƙazantar da Tofet, wanda ke cikin Kwarin Ben Hinom, saboda kar kowa ya sa ɗansa ko ɗiyarsa bi ta wuta a matsayin hadaya ga Molek.11Ya ɗauki dawakan da sarakunan Yahuda suka miƙa wa rana, Suna nan a wurin a ƙofar haikalin Yahweh kusa da ɗakin Natan-Melek shugaban shirayin da ke cikin farfajiya. Yosiya ya ƙona karusan rana.12Sarki Yosiya ya rurrusa bagadan da ke bisa rufin benen Ahaz, waɗanda sarakunan Yahuda suka yi, da bagaden da Manasse ya yi a farfajiya biyu ta haikalin Yahweh. Yosiya ya rugurguza su ya jefar da su a Kwarin Kidron,13Sarkin ya rurrushe tuddan wuraren tsafi da ke gabashin Yerusalem kudu da dutsen hallaka wanda Suleman sarkin Isra'ila ya gina wa Ashtoret da ƙazantacciyar gunkiyar Sidoniyawa; don Kemosh, ƙazantaccen gunkin Mowab; kuma na Molek, da ƙazantaccen gunkin Amonawa.14Ya rurrushe ginshiƙai na dutse rugu-rugu ya kuma sassare sandunan Ashera sa'an nan ya rufe wuraren da ƙasussuwan mutane.15Yosiya ya rurrushe bagadan da ke a Betel kakaf da wuri mai tudu da Yerobowam ɗan Nebat (wanda ya sa Isra'ila ta yi zunubi) ya gina. Ya kuma ƙona bagadin da wuri mai tudu, ya buge shi har ga ƙura, ya ƙona sandan Ashera.16Yayin da Yosiya ya dubi dukkan kewayen, sai ya gano kaburburan da ke kan tuddu, ya aika maza su kwaso ƙasusuwan daga kaburburan; sai ya ƙona su a bagadin, wanda ya ƙazantar da shi. Wannan bisa ga maganar Yahweh ce wadda mutumin Allah ya faɗa, mutumin da ya faɗi waɗannan abubuwan tuntuni.17Sa'an nan ya ce, "Wanne kabari ne waccan da na gani?" Mutanen birnin suka gaya masa, "Waccan ne kabarin mutumin Allah da ya zo daga Yahuda, ya yi magana akan abubuwan nan da kayi gãba da bagaden Betel."18Sai Yosiya ya ce, ku bar shi kawai. Kada kowa ya motsa ƙasusuwansa, sai suka bar ƙasusuwansa tare da na annabin da yazo daga Samariya.19Sa'an nan Yosiya ya cire dukkan gidajen wuraren kan tudu da ke a Samariya, wanda sarakunan Isra'ila su ka yi, da ya sa Allah ya yi fushi. Ya yi masu dai-dai da abin da aka yi a Betel.20Ya yayyanka dukkan firistocin tuddan wuraren akan bagadan sai ya ƙona ƙasusuwan mutane akan su. Sa'an nan ya koma Yerusalem.21Sa'an nan Sarkin ya ummurci dukkan mutane cewa, "Ku kiyaye bikin Ƙetarewa ga Yahweh Allahnku, kamar yadda aka rubuta a Littafin Alƙawari."22Irin hidimar bukin nan ba a taɓa yinsa ba tun daga kwanakin da alƙalai suka yi mulkin Isra'ila, ko dukkan kwanakin sarakunan Isra'ila ko Yahuda.23Amma a shakara ta goma sha takwas ta sarki Yosiya an yi bikin wannan Ƙetarewa na Yahweh a Yerusalem.24Yosiya kuwa ya kori dukkan mabiya waɗanda ke magana da matattu ko ruhohi. Ya kuma kori kawunan gidaje da gumaka da dukkan abubuwan banƙyama da ake gani a Yahuda da Yerusalem, saboda a ka'idantar da kalmomin dokokin da aka rubuta a littafin da Hilkiya firist ya samo a gidan Yahweh.25Kafin Yosiya, ba a yi wani sarki kamarsa, wanda ya juyo ga Yahweh da dukkan zuciyarsa da dukkan ransa da dukkan ƙarfinsa ba, wanda kuma ya bi dukkan dokokin Musa. Ba a kuwa yi wani sarki kamar Yosiya ba a bayansa.26Duk da haka, Yahweh bai juya baya daga zafin fushinsa ba, wanda ya yi gãba da Yahuda saboda dukkan abubuwan da Manasse ya yi na sashi shi ya yi fushi.27Saboda haka Yaweh ya ce, "Zan kuwa kawar da Yahuda daga fuskata, kamar yadda na tsige Isra'ila, zan kuma jefar da birnin da na zaɓa, Yerusalem, da kuma gidan da nace, 'Sunana zai kasance a wurin.'"28Game da sauran zantuttukan da suka shafi Yosiya da dukkan abubuwan da ya yi, ba a rubuce suke a littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?29A kwanakinsa, Fir'auna Neko, sarkin Masar, ya je yaƙi da sarkin Asiriya a kogin Yuferatis. Sarki Yosiya ya je ya sami Neko a yaƙi, sai Neko ya kashe shi a Megiddo.30Sai baran Yosiya ya ɗauke shi a karusa daga Megiddo, ya taho da shi Yerusalem ya bizne shi a nasa kabarin. Sa'an nan Mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoahaz ɗan Yosiya, suka shafa masa mai, suka mai da shi sarki a madadin mahaifinsa.31Yehoahaz yana da shekaru ashirin da uku lokacinin da ya fara mulki, ya yi mulkin shekaru uku a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Hamutal; ita ɗiyar Irmiya na Libna ne,32Yehoahaz ya yi aikin mugunta a gaban Yahweh, kamar dukkan yadda kakaninsa suka yi.33Fir'auna Neko ya ɗaure shi a Ribla, a ƙasar Hamat, saboda kar ya yi mulkin Yerusalem. Sa'an nan Neko ya yi wa Isra'ila tarar talanti ɗari na azurfa da talanti ɗaya na zinariya.34Fir'auna Neko ya sa Eliyakim ɗan sarki Yosiya ya zama sarki a madadin mahaifinsa, sai ya canza masa suna zuwa Yehoiakim. Amma ya ɗauki Yehoahaz zuwa Masar har Yehoahaz ya mutu a can.35Yehoiakim ya biya azurfa da zinariya ga Fir'auna. Don ya iya yin yadda Fir'auna yake so, Yehoiakim ya sa ƙasar biyan haraji kuma ya tilasta kowanne mutum daga cikin mutanen ƙasar ya biya da azurfa da zinariya bisa ga yanayin tsarinsu.36Yehoiakim yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya fara mulki, kuma ya yi mulki na shekara goma sha ɗaya a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Zebida ɗiyar Fediya na Ruma.37Yehoiakim ya yi akin mugunta a fuskar Yahweh, kamar yadda kakaninsa suka yi.
Wannan janar ne. AT: "da yawa wasu mutane" wannan asalin ne
Wannan magana kai ya hada da kowa a tsakanin. AT: "daga ƙarami mai mahimmanci zuwa mafi mahimmanci"
"Sai sarki ya karanta da babbar murya domin su ji"
A cikin 2 Sarakuna 22: 8 ya faɗi cewa Hilkiya ya sami littafin. Ana iya fassara wannan cikin tsari mai aiki. AT: "da Hilkiya ya samu" ko "abin da suka samu"
Ana magana da hanyar da mutum yake rayuwa kamar wanda yake tafiya akan hanyar, da kuma "bin mutum" wani ma'anar ne don aikata abinda wancan mutumin yayi ko yana son wasu suyi. AT: "yin biyayya ga Yahweh"
Waɗannan kalmomin duk suna da ma'ana guda ɗaya. Tare suna jaddada duk abin da Yahweh ya umarta a cikin doka.
Ma’anar kalmar “tare da dukkan zuciyarsa” na nufin “gaba ɗaya” kuma “da dukan ransa” na nufin “tare da kasancewarsa duka”. Waɗannan jumla guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. AT: "da dukkan kasancewarsa" ko "da dukkan ƙarfinsa"
Ana iya fassara wannan cikin tsari mai aiki. AT: "wannan littafin ya ƙunshi"
Wannan akrin magana tana nufin "yi biyayya da ka'idodin alkawari."
"da sauran firistocin da suka yi masa hidima"
mutanen da ke tsaron kofofin zuwa haikalin
"don haka mutane zasu iya amfani dasu don su bauta wa Ba'al ... don haka mutane zasu iya amfani dasu su bauta wa dukkan taurari"
Kalmar "shi" yana nufin Yosiya. Da zai umurci ma'aikatansa su yi waɗannan abubuwan. Wataƙila Hilkiya da firistocin da suka taimaka masa sun yi waɗannan abubuwan. AT: "ya sa su ƙone su ... kuma su ɗauka"
Waɗannan sunayen wurare ne.
"a matsayin wata hanyar bauta wa Ba'al, rana da wata, taurari, da dukan taurari" a matsayin hanyar bauta ga Ba'al, da rana da wata da duniyoyi da dukkan taurarin sama
Wannan yana ci gaba da sanar da abin da sarki Yosiya ya yi saboda saƙon Yahweh.
Kalmar "shi" yana nufin Yosiya. Da zai umurci ma'aikatansa su yi waɗannan abubuwan. Hilkiya da firistocin da suka taimake shi sun aikata waɗannan abubuwa. AT: "Ya sa su fito da su ... su ƙone shi ... Ya sa su doke shi ... kuma su jefa"
"suka sanya tufafi"
Yosiya zai umarci ma’aikatansa su yi waɗannan abubuwan. Wataƙila Hilkiya da firistocin da suka taimaka masa sun yi waɗannan abubuwan. AT: "Ya umurce su su kawo ... kuma su ƙazantar ... Ya sa su lalace"
Waɗannan sunayen wurare ne.
"mai mulkin garin mai suna Yoshuwa" ko kuma "shugaban birni mai suna Yoshuwa." Wannan wanin Yoshuwa daban ne daga Yoshuwa a littafin Tsohon Alkawari na Yoshuwa.
A nan "'yan'uwa" suna nufin 'yan'uwansu firistoci waɗanda suke aiki a haikali.
Waɗannan sunayen wurare ne.
"Ka sa ɗansa ko 'yarsa a cikin wuta ka ƙone su kamar hadaya ga Molek"
Zai iya zama mafi kyau don fassara don mai karatu ya fahimci cewa wasu mutane, wataƙila Hilkiya da "firistocin da ke ƙarƙashinsa"
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) dawakai na hakika ko 2) gumakan dawakai.
Anan "wanda aka bayar" yana wakiltar sadaukarwa don ibada. AT: "ya kasance yana bauta wa rana"
Wannan sunan mutum ne.
Yosiya zai umarci ma’aikatansa su yi waɗannan abubuwan. Wataƙila Hilkiya da firistocin da suka taimaka masa sun yi waɗannan abubuwan. AT: "Sarki Yosiya ya umarce su da su lalace ... Ya sa su fashe ... ya jefa su"
Wannan sunan wuri ne. Duba yadda zaka fassara wannan a 2 Sarakuna 23:4.
"ya rufe ƙasa da ƙasusuwa na mutane don haka mutane ba za su iya amfani da shi a matsayin gidan ibada ba"
Zai iya zama mafi kyau don fassara don mai karatu ya fahimci cewa wasu mutane, wataƙila Hilkiya da "firistocin da ke ƙarƙashinsa"
"ya faɗi cewa waɗannan abubuwan zasu faru"
alama ko mutum-mutumi wanda ke girmama. Kabari wata irin abin tunawa ce.
"Saboda haka ba su taɓa kasusuwa ba da ƙasusuwa na"
Zai iya zama mafi kyau don fassara don mai karatu ya fahimci cewa wasu mutane, wataƙila Hilkiya da "firistocin da ke ƙarƙashinsa"
"abin da ya yi "
Wataƙila kuna buƙatar bayyana abin da ya sa ya ƙone ƙasusuwa. "ya ƙone ƙasusuwan mutane a kansu don kada wani ya sake yin amfani da su"
"dole ne ku kiyaye bikin Ƙetarewa"
Ana iya fassara wannan cikin tsari mai aiki. AT: "Zuriyar Isra'ila ba su yi bikin Idin Ƙetarewa ta babbar hanya a lokacin ba"
Sunan "Isra'ila" magana ne don "zuriyar Isra'ila."
"lokacin da jama'ar Isra'ila suke da nasu sarki kuma jama'ar Yahuda suna da nasu sarki"
Ana iya fassara wannan cikin tsari mai aiki. AT: "Mutanen Yahuda sun yi wannan Idin Ƙetarewa na Yahweh"
"tilasta wa waɗancan ... ruhohi barin" ko "sun yi wata doka cewa waɗancan ... ruhohi dole ne su fita"
abubuwan da mutane basuyi imani ba suna da iko na musamman
"wanda ya ba da kansa ga Yahweh gaba ɗaya"
"Tun daga wannan lokaci babu wani sarki da ya yi kama da Yosiya"
Marubucin ya yi amfani da wannan kalma don nuna cewa duk da waɗannan abubuwan da Yosiya ya yi kyakkyawa ne, amma Yahweh ya yi fushi da Yahuda.
Wuta kwatanci ne na fushi, fara wuta wata alama ce ta yin fushi. Ana iya fassara kalmar "fushi" mai ma'ana azaman mai ma'ana. AT: "Yahweh bai daina kasancewa mai zafin rai ba saboda yana fushi da fushinsa"
"sun yi ne don sa shi fushi"
"daga inda nake" ko "daga kasancewa kusa da ni"
Sunan magana ne don girmamawar da ya kamata mutane su ba wa mutumin. AT: "Mutane za su bauta mini a can"
Wannan za a iya bayyanar da shi a aikace kuma ya ɗauka cewa amsa tabbatacciya ce. Tambayar yana da magana kuma ana amfani dashi don girmamawa. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 8:23. AT: "kuna iya neme su ... Yahuda."
"A zamanin Yosiya, Fir'auna Neko, sarkin Masar"
Wannan sunan mutum ne.
Wannan sunan birni ne.
"shekaru 23"
Wannan sunan mace ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Gaban Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh ko tantancewa. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 3: 2. AT: "abin da ke mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ɗauka mugunta ne"
Kasancewa cikin "sarƙoƙi" yana nuna kamawa da ɗaurin kurkuku. AT: "saka shi a kurkuku"
"tilasta wa mutanen Yahuda su ba shi"
"Yehoaikim ya tara haraji daga mutanen da suka mallaki ƙasa"
"mutanen ƙasar Yahuda." Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) "mutanen da suka rayu a ƙasar Yahuda" ko 2) "mafi ƙarfi da ƙarfi da ƙarfi daga waɗanda suka zauna a cikin Yahuda."
Wannan sunan mace ne.
Wannan sunan mutum ne.
Wannan sunan wuri ne.
Gaban Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh ko tantancewa. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 3: 2. AT: "abin da ke mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ɗauka mugunta ne"
1A kwanakin Yehoiakim, Nebukadnezza sarkin Babila ya kai wa Yahuda hari; Yehoiakim ya zama bawansa na shekaru uku. Sa'an nan Yehoiakim ya juya ya tayar wa Nebukadnezza.2Yahweh ya aiko da Yehoiakim, maharan Kaldiyawa da Aramiyawa da Mowabawa da Amoniyawa, ya aike su gãba da Yahuda su hallakar da shi. Wannan ya zo dai-dai ne da maganar Yahweh da aka faɗa ta barorinsa annabawa.3Hakika ta bakin Yahweh ne wannan ya zo ga Yahuda, ya cire su daga fuskarsa, saboda laifofin Manasse, dukkan abin da ya yi,4kuma saboda zub da jinin bayin Allah da ya yi, gama ya cika Yerusalem da jinin adalai, Yahweh bai yi niyar gafarta hakan ba.5Game da sauran zantuttukan da suka shafi Yehoiakim, da dukkan abubuwan da ya yi, ba a rubuce suke a littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?6Yehoiakim ya yi barci tare da kakaninsa, sai Yehoiacin ɗansa ya zama sarki a madadinsa.7Sarkin Masar bai sake fita ƙasarsa ya kai wa wani hari ba, saboda sarkin Babila ya ƙwato dukkan ƙasashen da ke ƙarƙashin sarkin Masar, daga rafin Masar har zuwa kogin Yuferatis.8Yehoiacin ya na da shekaru goma sha takwas yayin da ya fara mulki a Yerusalem; ya yi mulkin wata uku a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Nehushta; ɗiyar Elnatan na Yerusalem.9Ya yi aikin mugunta a gaban Yahweh; ya yi dukkan abubuwan da mahaifinsa ya yi.10A lokacin nan ne sojojin Nebukadnezza sarkin Babila suka kai wa Yerusalem hari, suka kewaye birnin da yaƙi,11Nebukadnezza ya zo birnin yayin da sojojinsa ke kewaye da shi,12sai Yehoiacin sarkin Yahuda ya je ya tari sarkin Babila, shi da mahaifiyarsa da barorinsa da 'ya'yansa da hafsoshinsa. Sarkin Babila ya kama shi a shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa.13Nebukadnezza ya ɗauki dukkan abubuwa masu daraja na gidan Yahweh, da waɗanda ke fãdar sarki. Ya farfashe dukkan tasoshin zinariyar da sarki Suleman ya yi a haikalin Yahweh, kamar yadda Yahweh ya ce zai faru.14Ya ɗauki 'yan zuwa zaman talala daga dukkan Yerusalem, da dukkan shugabanin da dukkan mayaƙa da kamammu dubu goma da dukkan 'yan fasaha da maƙera. Babu wanda aka bari sai fakirai na ƙasar.15Nebukadnezza ya ɗauki Yehoiacin zuwa zaman talala a Babila. da kuma mahaifiyar sarki da matansa da hafsoshi da manyan mazajen ƙasar. Ya ɗauke su zuwa zaman talala daga Yerusalem zuwa Babila.16Dukkan mayaƙa dubu bakwai da masu sana'a da maƙera dubu ɗaya dukkansu ƙarfafa ne da suka isa zuwa yaƙi - sarkin Babila ya kawo waɗannan mutanen ga zaman talala a Babila.17Sarkin Babila ya sa Mataniya, ɗan'uwan mahaifin Yehoiacin, ya zama sarki a madadinsa ya kuma canza masa suna zuwa Zedekiya.18Zedekiya yana da shekaru ashirin da ɗaya yayin da ya fara mulki; ya yi mulki shekaru goma sha ɗaya a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Hamutal; ita ɗiyar Irmiya na Libna ne.19Ya yi aikin mugunta a gaban Yahweh; ya yi dukkan abin da Yehoiakim ya yi.20Ta dalilin fushin Yahweh ne, dukkan waɗannan abubuwan suka faru a Yerusalem da Yahuda, har sai ya kore su daga gare shi. Sa'an nan Zedekiya ya yi tayar da gãba da sarkin Babila.
"A lokacin da Yehoiakim yake mulkin Yahuda"
Wataƙila kuna buƙatar fayyace abin da ya faru bayan Nebuchadnezzar ya kai wa Yahuda hari. AT: "an kai wa hari kuma aka ci nasara kan Yahuda"
Ana iya fassara wannan cikin tsari mai aiki. AT: "Wannan bisa ga maganar Yahweh ne bayinsa annabawa suka faɗa" ko "Wannan shi ne dai-dai abin da Yahweh ya faɗa wa bayinsa annabawa cewa za su faru"
Wasu juyi suna da, “Tabbas saboda fushin Yahweh ne,” wanda yake daidai da karanta ainihin rubutun. Idan masu fassarar suna da damar jujjuya fassarori a cikin manyan yaruka a yankin su, tabbas ya kamata su bi yadda suka zaɓi.
Anan "baki" yana wakiltar umarnin Yahweh. AT: "kamar yadda Yahweh ya umarta"
"rabu da su" ko "halakar da su"
Jini magana ce ta rayuwar marasa laifi, kuma zubar da jini kalma ce ta kisan mutane marasa laifi. AT: "Ya kashe mutane da yawa marasa laifi a cikin Yerusalem"
An rubuta wannan azaman tambayoyin magana ne saboda a lokacin da aka rubuta wannan mutanen sun riga sun san da wannan bayanin. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. Ana iya fassara shi cikin tsari mai aiki. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 8:23. AT: "Lallai an rubuta su ... Yahuda." ko "zaku iya nemo su ... Yahuda"
Barci magana ce ta mutuwa. AT: "ya mutu, aka binne shi tare da kakanninsa"
"Sarkin Masar bai fito daga ƙasarsa ya ƙara yin yaƙi da sauran gungun mutane ba"
Wannan sunan na mace ne.
Wannan sunan mutum ne.
Gaban Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh ko tantancewa. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 3: 2. AT: "abin da ke mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ɗauka mugunta ne"
Anan "dukka" asalinsu ne. Yana nufin yayi irin zunubin da mahaifinsa yayi. AT: "ya aikata irin zunuban da mahaifinsa ya yi"
Wataƙila kuna buƙatar fayyace dalilin da ya sa Yehoiachin ya fita ya sadu da Nebukadnezza. AT: "Yehoiachin, sarkin Yahuda, tare da mahaifiyarsa, da bayinsa, da shugabanninsa, da shugabanninsa, suka tafi inda sarkin Babila yake, don mika wuya gare shi"
"Bayan da sarkin Babila ya yi sarauta sama da shekara bakwai, ya kama Yehoiachin"
Kuna iya son fassara wannan don mai karatu ya fahimci cewa wataƙila Suleman ya sami wasu sun taimaka masa ya yi wannan.
Anan "Yerusalem" ma'anar kalmomin ne ga mutanen da suka rayu a wurin. Kuma, "dukka" halitta ce. Yana nufin duk mahimman mutane AT: "Nebukadnezza ya kwashe dukan manyan mutane daga Yerusalem"
"mutanen da suka san yadda ake yin da kuma gyara abubuwan da aka yi daga ƙarfe"
Wannan za a iya fassara shi azaman ingantaccen bayani. AT: "Kawai mafi talauci a ƙasar har yanzu sun ci gaba da zama a can"
"7,000 ... 1,000"
Wannan sunan mutum ne.
"21 ... 11"
Wannan sunan mace ne.
Wannan sunan wuri ne.
Gaban Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh ko tantancewa. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 3: 2. AT: "abin da ke mugunta cikin hukuncin Yahweh" ko "abin da Yahweh ya ɗauka mugunta ne"
1Sai ya zamana a shekara na tara a mulkin Zedekiya, a wata na goma, a rana ta goma ga watan, Nebukadnezza sarkin Babila ya zo da dukkan sojojinsa gãba da Yerusalem. Ya yi sansani kusa da ita, ya gina kagarai kewaye da ita.2Saboda haka aka kewaye birnin da yaƙi har shekara goma sha ɗaya na mulkin Zedekiya.3A rana ta tara na watan huɗu na shekarar, yunwa ta yi tsanani a birnin har babu abinci domin mutanen ƙasar.4Sa'an nan aka shigo birnin, sai dukkan masu yaƙin suka gudu ta ƙofar dake tsakanin katangu biyu, ta lambun sarki, ko da shike Kaldiyawa suna kewaye da birnin. Sarki ya yi ta wajen Araba.5Amma sojojin Kaldiyawa suka yi fakon sarki Zedekiya har suka mamaye shi a filayen kwarin Kogin Yodan kusa da Yeriko. Dukkan sojinsa kuwa suka warwatsu daga gare shi.6Suka kamo sarkin suka kai shi gun sarkin Babila a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.7Game da 'ya'yan Zedekiya maza kuwa, an yayyanka su a gabansa. Sa'annan ya ƙwaƙule masa idanunsa, ya ɗaure shi da sarƙa ta tagulla, ya kai shi Babila.8Yanzu kuwa a wata na biyar, a rana ta bakwai ga watan, wanda ke a shekara ta goma sha tara ta mulkin Nebukadnezza sarkin Babila, Nebuzaradan, baran sarkin Babila da kuma shugaban masu gadin sarki, ya zo Yerusalem.9Ya ƙona gidan Yahweh da fãdar sarki da dukkan gidajen Yerusalem; ya kuma ƙone dukkan manyan gine-ginen birnin.10Game da garun kewaye da Yerusalem kuwa, dukkan sojojin Babilan da ke ƙarƙashin shugaban sun rurrushe su.11Game da sauran mutanen da aka bari a birnin da waɗanda suka tafi wurin sarkin Babila, da sauran ragowar mutanen - Nebuzaradan, shugaban masu gadin sarki, ya ɗauke su zuwa zaman talala.12Amma shugaban masu gadin sarki ya bar waɗansu matalautan ƙasar su ci gaba da aikin lambuna da filaye.13Game da ginshiƙan tagulla da ke gidan Yahweh, da dakalansu da takwanniyar ruwa da ke cikin gidan Yahweh, Kaldiyawa sun ragargaza su su ka kuma ɗauke tagullan su ka kai su Babila.14Kaldiyawan kuma su ka kwashe tukwane da manyan cokula da hantsuka da cokula da dukkan tasoshin tagulla waɗanda firistoci ke aiki da su a haikali - Kaldiyawa sun tafi da su dukka.15Tukwanen da ake amfani da su domin cire tokar bagaden darurruka da aka yi da zinariya da azurfa - shugaban masu gadin sarkin ya kwashe su dukka ya tafi da su.16Ginshiƙan biyu kuwa da takwanniyar ruwa da dakalan da Suleman ya yi domin gidan Yahweh suna ƙunshe da tagulla da yawa da ba a iya aunawa.17Tsawon ginshiƙi na farkon kamu goma sha takwas ne. dajiyar tagulla akan ginshiƙin kamu uku ne, wadda aka kewaye da raga da rumman, kuma dukka da tagulla aka yi su. Ɗaya ginshiƙin da ragarsa na dai-dai da ta farkon.18Shugaban masu gadin sarkin ya ɗauki Serayiya babban firist da Zefaniya da firist na biyun da mutun uku masu tsaron ƙofa.19Daga birnin kuwa ya ɗauki waɗansu manyan sojoji da mashawartan sarki guda biyar waɗanda ba a tafi da su ba duk ya kamo ya tsare su don kada su gudu. Ya kuma kamo babban sojan da ke shugabancin ɗaukan sojoji aiki, tare da mutum sitin kuma da ke cikin birnin.20Sa'an nan Nebuzaradan, shugaban masu gadin sarki, ya ɗauko su ya kai wa sarkin Babilan a Ribla.21Sarkin Babila ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat. Ta haka Yahuda ya bar ƙasarsa zuwa zaman bauta.22Game da mutanen da suka rage a ƙasar Yahuda, waɗanda Nebukadnezza sarkin Babilan ya bari, ya sa Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, shugabancin su,23Yanzu kuwa da dukkan shugabanin sojojin, su da mazajensu, suka ji sarkin Babila ya maida Gedaliya gwamna, sai suka je wurin Gedaliya a Mizpa. Waɗannan mazajen su ne Isma'il ɗan Netaniya da Yohanan ɗan Kariya da Serayiya ɗan Tanhumet Banetofate da Ya'azaniya ɗan Ma'akatite - su da mazajensu.24Gedaliya ya yi amana da su da mazajensu, ya ce da su, "Kada ku ji tsoron shugabanin Kaldiyawa. Ku zauna a ƙasar ku yi wa sarkin Babilan hidima, kuma kome zai yi maku kyau."25Amma ya zamana dai a watan bakwai Isma'il ɗan Netaniya ɗan Elishama, daga iyali mai martaba, ya zo ya da mutum goma ya kai wa Gedaliya hari. Gedaliya ya mutu, tare da mutum goma na Yahuda da Babilonawan da ke tare da shi a Mizfa.26Sa'an nan dukkan mutanen, daga mafi ƙanƙanta zuwa masu muhiminci, da dukkan shugabani sojojin, suka tashi suka tafi Masar, saboda suna tsoron Babilonawan.27Ya zamana daga baya a shekara ta talatin da bakwai na zaman talalar Yahoiacin sarkin Yahuda, a wata na goma sha biyu, sai Awel Marduk sarkin Babilan ya saki Yahoiacin sarkin Yahuda daga kurkuku. Wannan ya faru ne a shekarar da Awel- Marduk ya fara mulki.28Ya yi maganar kirki da shi ya kuma ba shi wurin zaman da ya fi na waɗansu sarakunan da ke tare da shi a Babila.29Awel-Marduk ya cire wa Yahoiacin tufafin kurkuku, har Yahoiacin ya ci gaba da liyafa a teburin sarki dukkan rayuwarsa.30Ana kuwa biyansa albashin abinci dukkan kwanakin rayuwarsa.
Wannan shi ne watan goma na kalandar Ibraniyanci. Rana ta goma ta kusan ƙarshen Disamba a kalandar Yammaci. Wannan lokacin sanyi ne lokacin da za'a iya samun ruwan sama da dusar ƙanƙara.
Sunan "Yerusalem" wata ma'ana ce ga mutanen da ke zaune cikinta. AT: "ya zo tare da sojojinsa duka don su yi yaƙi da mutanen Yerusalem" ko "suka zo tare da sojojinsa duka don cinye Yerusalem"
Ana iya fassara wannan cikin tsari mai aiki. AT: "Sa’an nan sojojin Babilawa suka rushe cikin birni"
"dukkan mayaƙa"
"ta amfani da ƙofar"
Wasu fassarorin suna amfani da "Kaldiyawa" wasu kuma suna amfani da "Babilawa." Dukansu kalmomin suna nufin kungiyan mutane ɗaya ne.
"Sarki Zedekiya kuma ya gudu, ya tafi wurin"
Ana iya fassara wannan cikin tsari mai aiki. AT: "Sojojinsa duka sun gudu daga gare shi" ko "Kaldiyawa sun kori dukkan sojojinsa"
Wannan sunan wani wuri ne.
"sun yanke shawarar abin da za su yi don a hukunta shi"
Idanun suna kwatanci ne ga dukan mutum. AT: "sun tilasta wa sarki Zedekiya ya lura da yadda suka kashe 'ya'yansa"
"Nebukadnezza ya buɗe idanun Zedekiya." Zai fi kyau a fassara don mai karatu ya fahimci cewa wasu mutane na iya taimaka wa Nebukadnezza yin wannan.
Wannan shi ne watan biyar na kalandar Ibraniyanci. Rana ta bakwai tana gab da ƙarshen Yuli a kalandar Yammaci.
Wannan sunan mutum ne.
"Abin da ya faru ke nan ke faruwa da dukkan bangon da ke kewaye da Yerusalem: dukka"
"waɗanda suke bin umarnin"
"Wannan shi ne abin da ya faru da sauran mutane ... birnin"
"mutanen da suka rage a cikin birni"
"ya bar birnin ya tafi ya kasance tare da sarki
"Wannan shi ne abin da ya faru da ginshiƙan tagulla ... gidan Yahweh: Kaldiyawa"
"gutsuttsura su" ko "gasa su cikin kananan guda"
"waɗanda firistoci suka yi amfani da shi a cikin haikalin"
Wataƙila kuna buƙatar bayyana abin da toka ake magana akan. AT: "tukwane da aka yi amfani da su don cire toka daga bagadin"
"Babban kwanun na tagulla." Duba yadda ka fassara wannan a 2 Sarakuna 25:13.
Tsayin kamu na daidai da rabin mita 46 ne. AT: daidai da mita 8.3 ... da mita 1.4"
"Na tagulla gaba daya"
Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 25: 8.
Wannan sunnan mutum ne.
Waɗannan kalmomin suna nuni ne da Zafaniya. Wata ma'anar da ta yiwu ita ce "firist a ƙarƙashin Serayiya."
Duba yadda zaka fassara wannan a cikin 2 Sarakuna 7:10.
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) jami'in ya tilasta wa mutane su zama sojoji ko 2) jami'in ya rubuta sunayen mutanen da suka zama sojoji.
Wannan hanya ce ta ladabi da ake cewa "kashe su." Zai fi kyau a fassara domin mai karatu ya fahimci cewa wasu mutane na iya taimaka wa sarki yin wannan.
"Don haka aka fitar da jama'ar Yahuda daga ƙasarta"
Yahuda, sunan mutane kungiyar ne, da yake magana ne ga mutane da kansu. AT: "mutanen Yahuda sun fita daga ƙasarsu"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan yana nufin mutumin da ke daga zuriyar wani mutum mai suna Netofa.
Wannan yana nufin mutumin da ya fito daga wani wuri da ake kira Ma'aka.
Wannan shi ne watan bakwai a kalandar Ibraniyanci. Yana cikin ƙarshen satin Setumba da kuma farkon sashin Oktoba akan kalandar Zamani.
Wannan sunan mutum ne.
Wannan janar ne. AT: "mutane da yawa"
Wannan hadin kai ne wanda ke nufin "kowa." AT: "daga ƙarami mai mahimmanci zuwa mafi mahimmanci" ko "kowa da kowa"
"shekara 37"
Wannan shi ne watan goma sha biyu na kalandar Ibraniyanci. Ranar ashirin da bakwai tana gab da farkon watan Afril a kalandar Yammaci.
Wannan sunan mutum ne.
Ba da wuri mai kyau a teburin cin abinci alama ce ta girmama shi. AT: "mafi daraja fiye da sauran sarakuna"
Aikin cire Yehoiachin tufafin kurkuku na wakiltar sanya shi mai yantace mutum ne.
"tare da sarki da dogaransa"
Ana iya fassara wannan cikin tsari mai aiki. AT: "Sarki ya tabbatar cewa yana da rabon abinci na yau da kullum"
"Kudi don siyan abinci"
1Adamu, Set, Enosh,2Kenan, Mahalalel, Yared,3Enok, Metusela, Lamek.4'Ya'yan Nuhu su ne Shem, Ham da Yafet.5'Ya 'yan Yafet su ne Gomer, Magog, Madai, Yaban, Tubal, Meshek, Tiras.6'Ya'yan Gomer su ne Ashkenaz, Rifat da Togarma.7'Ya 'yan Yaban su ne Elisha, Tarshish, Kitiyawa, da Rodanawa.8'Ya'yan Ham su ne Kush, Masar, Fut da Kan'ana.9'Ya'yan Kush su ne Seba, Habila, Sabta, Ra'ama da Sabteka.10'Ya'yan Ra'ama su ne Sheba da Dedan. Kush ya zama mahaifin Nimrod, wanda shi ne ya fara zama jarumi a duniya.11Masar ya zama mahaifin mutanen Ludawa, da Anamawa, da Lehabawa, da Naftuhawa, da12Fatrusawa, da Kasluhawa (daga wannan tushen Filistiyawa suka fito), da Kaftorawa.13Kan'ana ya zama mahaifin Sidon, ɗan farinsa, da kuma Hitiyawa.14Shi ne ya zama kakan Yebusawa, Amoriyawa, Girgashawa,15Hibiyawa Arkiyawa, Siniyawa da16Arbiyawa, Zemarawa, da Hamatawa.17'Ya'yan Shem su ne Elam, Ashur, Arfazad, Lud, Aram, Uz, Hul, Geter, da Meshek,18Arfazad shi ne ya zama mahaifin Shela, Shela kuma ya zama mahaifin Eber.19Eber na da 'ya'ya biyu. Sunan ɗayan Feleg, gama a zamaninsa ne duniya ta rabu. Sunan ɗan'uwansa Yoktan.20Yoktan ya zama mahaifin Almodad, Shelef, Hazamavet, Yera,21Hadoram, Uzal, Dikla,22Obal, Abimayel, Sheba,23Ofir, Habila, da Yobab, duk waɗannan daga zuriyar Yoktan ne.24Shem, Arfazad, Shelah,25Eber, Feleg, Rewu,26Serug, Nahor, Tera,27Abram shi ne Ibrahim.28'Ya'yan Ibrahim su ne Ishaku da Isma'il.29Waɗannan su ne 'ya'yansu: Ɗan farin Isma'il Nebayot ne, sa'an nan Kedar, Adbeel, Mibsam,30Mishma, Duma, Massa, Hadad, Tema,31Yetur, Nafish, da Kedema. Waɗannan su ne 'ya'yan Isma'il.32'Ya'yan Ketura, ƙwarƙwarar Ibrahim su ne Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa. 'Ya'yan Yokshan su ne Sheba da Dedan.33'Ya'yan, Midiyan su ne Efa, Efer, Hanok, Abida, da Elda'ah. Dukkan waɗannan zuriyar Ketura ne.34Ibrahim ya zama mahaifin Ishaku. 'Ya'yan Ishaku su ne Isuwa da Isra'ila.35'Ya'yan Isuwa su ne Elifaz, Ruwel, Yewush, Yalam, da Kora.36'Ya'yan Elifaz su ne Teman, Omar, Zefo, Gatam, Kenaz, Timna da Amalek.37'Ya'yan Ruwel su ne Nahat, Zera, Shamma, da Mizza.38'Ya'yan Seyir su ne Lotan, Shobal, Zibiyon, Ana, Dishon, Ezer, da Dishan.39'Ya'yan Lotan su ne Hori da Homam, Timna 'yar'uwar Lotan ce.40'Ya'yan Shobal su ne Alban, Manahat, Ebal, Shefo, da Onam. 'Ya'yan Zibiyon su ne Aiya da Ana.41Ɗan Ana shi ne Dishon. 'Ya'yan Dishon su ne Hemran, Eshban, Itran, da Keran.42'Ya'yan Ezer su ne Bilhan Za'aban, Ya'akan da Akan. 'Ya'yan Dishan su ne Uz da Aran.43Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a ƙasar Idom kafin wani sarki ya yi mulki bisa Isra'ilawa. Bela ɗan Beyor, sunan birninsa Dinhaba ne.44Da Bela ya mutu, Yobab ɗan Zera na Bozra ya yi mulki a gurbinsa.45Da Yobab ya mutu, Husham na ƙasar Temanawa ya yi mulki a gurbinsa.46Da Husham ya mutu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan a ƙasar Mowab, ya yi sarauta a gurbinsa. Sunan birninsa Avit.47Da Hadad ya mutu, Samla na Masreka ya yi sarauta a gurbinsa.48Da Samla ya mutu, Shawul na Rehobot wadda a kan kogin ya yi sarauta a gurbinsa.49Da Shawul ya mutu, Ba'al-Hanan ɗan Akbor ya yi mulki a gurbinsa.50Ba'al-Hanan ɗan Akbor ya mutu, Hadar ya yi mulki a gurbinsa. Sunan birninsa Fawu. Sunan matarsa Mehetabel ce ɗiyar Matred ɗiyar Me Zahab.51Hadad ya mutu, shugaban iyalin Idom su ne Timna, Alba, Yetet,52Ohalibama, Elah, Finon,53Kenaz Teman, Mibza,54Magdiyel, da Iram. Waɗannan su ne shugabannin a Idom.
Wasu juyi da ta kumshi ULB da UDB, sun hada '"Ya'yan" domin ya bayyana hakan cewa Shem, Ham, da Yafet 'yan'uwan juna ne kuma ya'yan Nuhu ne. In ba haka ba, mai karatu zai yi zaton cewa kowanensu na wakiltar tsararaki daya nesa da Nuhu, da kakaninsu.
Waɗannan suna jerin sunayen kakanine. Idan yaren ku na da takamen hanyar da za ku sa alama irin wanan jerin, zaku iya amfani da shi anan.
Fassara waɗannan sunayen mutane ta yadda zaka fassara sunayen a yarenka. Waɗannan duka sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutanen da kungiyoyin.
Wannan sunan wani lokaci ana rubuta shi "Rodanim" kamar yadda yake cikin UDB.
Waɗannan sunayen mutane ne.
AT: "kakannin Filistiyawa"
Wannan sunan mutum ne.
Waɗannan sunayen mutanen da kungiyoyi ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
"Husham, daga ƙasar kakanin Temanawa in da suke zama, ya yi mulki a gurbinsa."
Wannan sunan ƙungiyoyin mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan sunan wurare ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
1Waɗanan su ne 'ya'yan Isra'ila maza: Ruben, Simiyon, Lebi, Yahuda, Issaka, Zebulun,2Dan, Yosef, Benyamin, Naftali, Gad da Asha.3'Ya'yan Yahuda su ne Er, Onan, da Shela, waɗanda ɗiyar Shuwa ta haifa masa Bakan'aniye. Er ɗan farin Yahuda, mugu ne a gaban Yahweh, sai Yahweh ya kashe shi.4Tama, surukarsa, ta haifa masa Ferez da Zara. Yahuda yana da 'ya'ya biyar maza.5'Ya'yan Ferez su ne Hezron da Hamul.6'Ya'yan Zera su ne Zimri, Etan, Heman, Kalkol, da Darda su biyar cur.7Ɗan Karmi shi ne Akar, wanda ya kawo matsala ga Isra'ila lokacin da ya saci abubuwan da aka keɓe domin Yahweh.8Ɗan Etan shi ne Azariya.9'Ya'yan Hezron su ne Yeramil, Ram, Kaleb.10Ram ya zama mahaifin Aminadab, Aminadab ya zama mahaifin Nashon, shugaba ne cikin zuriyar Yahuda.11Nashon ya zama mahaifin Salmon, Salmon ya zama mahaifi Bo'aza.12Bo'aza ya zama mahaifin Obed, Obed ya zama mahaifin Yesse.13Yesse ya zama mahaifin ɗan farinsa Eliab, Abinadab na biyu, Shimeya na uku,14Netanel na huɗu, Raddai na biyar,15Ozem na shida, sai Dauda na bakwai.16'Yan'uwansu mata su ne Zeruyiya da Abigel. 'Ya'yan Zeruyiya su ne Abishai, Yoab da Asahel, su uku.17Abigel ta haifi Amasa, mahaifinsa Yeter ne Ba'isma'ile.18Kaleb ɗan Hezron ya haifi 'ya'ya daga matarsa Azuba, da kuma Yeriyot. 'Ya'yansa maza su ne Yesher, Shobab, da Ardon.19Azuba ta mutu, sai Kaleb ya auro Efrat, wacce ta haifa masa Hur.20Hur ya zama mahaifin Uri, Uri kuma ya zama mahaifin Bezalel.21Daga baya Hezron (da ya cika shekaru sittin) ya auri ɗiyar Makir, mahaifin Giliyad. Ita ta haifa masa Segub.22Segub ya zama mahaifin Yayir, wanda ya mallaki birane ashirin da uku a ƙasar Giliyad.23Geshur da Aram suka ci garin Yayir da Kenat, har da garuruwa sittin na kewaye. Duk waɗannan mazauna zuriyar Makir ne, mahaifin Giliyad.24Bayan mutuwar Hezron, Kaleb ya kwana da Efrata, matar Hezron mahaifinsa. Ta haifa masa Ashhur, mahaifin Tekowa.25'Ya'yan Yeramil, ɗan farin Hezron, su ne Ram ɗan fari, Buna, Oren, Ozem, da Ahija.26Yeramil ya na da wa ta mata, wadda ta ke da suna Atara. Ita ce uwar Onam.27'Ya'yan Ram, ɗan farin Yeramel, su ne Ma'az, Yamin, da Eker.28'Ya'yan Onam su ne Shammai da Yada. 'Ya'yan Shammai su ne Nadab da Abishur.29Sunan matar Abishur Abihel ne, ta kuma haifa masa Ahban da Molid.30'Ya'yan Nadab su ne Seled da Affayim, amma Seled ya mutu ba shi da 'ya'ya,31'Ɗan Affayim kuwa Ishi ne. Ɗan Ishi shi ne Sheshan. Ɗan Sheshan shi ne Ahlai.32'Ya'yan Yada, ɗan'uwan Shammai, su ne Yeter da Yonatan. Yeter ya mutu ba shi da 'ya'ya.33'Ya'yan Yonatan su ne Felet da Zaza. Waɗannan su ne zuriyar Yeramil.34Sheshan ba shi da 'ya'ya maza, sai dai mata. Sheshan ya na da bawa, Bamasare, mai suna Yarha.35Sai Sheshan ya ba baransa Yarha ɗiyarsa ta zama matarsa. Ita ce ta haifa masa Attai.36Attai ya zama mahaifin Natan, Natan ya zama mahaifin Zabad.37Zabad ya zama mahaifin Eflal, kuma Eflal ya zama mahaifin Obed.38Obed ya zama mahaifin Yehu, kuma Yehu ya zama mahaifin Azariya.39Azariya ya zama mahaifin Helez, Helez ya zama mahaifin Eleyasa.40Eleyasa ya zama mahaifin Sismai, Sismai kuma ya zama mahaifin Shallum.41Shallum ya zama mahaifin Yekamiya, Yekamiya kuma ya zama mahaifin Elishama.42'Ya'yan Kaleb, ɗan'uwan Yeramil, su ne Mesha ɗan farinsa, wanda shi ne mahaifin Zif. Ɗansa na biyu, Maresha, shi ne mahaifin Hebron.43'Ya'yan Hebron su ne Kora, Taffuwa, Rekem, da Shema.44Shema ya zama mahaifin Raham, mahaifin Yorkiyam. Rekem ya zama mahaifin Shammai.45Ɗan Shammai kuwa shi ne Mawon, Mawon shi ne mahaifin Bet Zur.46Efah, ƙwarƙwarar Kaleb, ta haifi Haran, Moza, da Gazez. Haran ya zama mahaifin Gazez.47'Ya'yan Yahdai su ne Regem, Yotam, Geshan, Felet, Efah da Sha'af.48Ma'aka, ƙwarƙwarar Kaleb, ta haifi Sheber da Tirhanah.49Ita ce kuma mahaifiyar Sha'af mahaifin Madmanna, Sheva mahaifin Makbena da mahaifin Gibeya. Ɗiyar Kaleb ita ce Aksah. Waɗannan su ne zuriyar Kaleb.50Wàɗannan su ne 'ya'yan Hur, ɗan farinsa daga Efrata: Shobal mahaifin Kiriyat Yerim,51Salma mahaifin Betlehem da kuma Haref mahaifin Bet Gader.52Shobal mahaifin Kiriyat Yerayim yana da zuriya: Harowe, rabin jama'ar Manahatawa,53da kuma iyalin Kiriyat Yerayim: na Itirawa da na Futiyawa, da na Shumatawa da Mishrayawa. Daga waɗannan ne Zoratawa da Eshtawolawa suka fito.54Waɗannan su ne dangogin Salma: Betlehem, Netofatawa, Atrot Bet Yowab, da rabin Manahatawa - Zoritawa,55dangogin marubuta waɗanda suka zauna a Yabez: Tiratawa, Shimiatawa, da Sukatawa. Waɗannan su ne Kenitawa zuriyar da suka fito daga Hammat, kakan Rekabawa.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan shine sunnan Yahweh wanda ya bayyana wa mutanensa a cikin Tsohon Alƙawali. Duba shafin fassarar kalma game da Yahweh dangane da yadda ake fassara wannan.
"ta haifa masa ya'ya maza Ferez da Zara"
AT: "bisa lafazin Yahweh"
Wannan yana nufin Yahweh ya yarda a kashe Er.
Wannan yana nufin matar ɗansa ne.
"yaro na biyu ... yaro na uku"
Wannan na nufin cewa Yeter zuriyar Ishma'il ne.
AT: "ta haifi"
"ta haifi"
"ta haifi"
Wannan sunan mace ce.
Duba:
Duba:
"ta haifi"
Duba:
Duba:
Juyi da yawa sun gane hurɗoɗin da ke tsakanin waɗannan mutanen a hanyoyi dabam-dabam. Wasu masu fassara sun yarda cewa "baban Hebron ... baban Raham, baban Yorkim ... baban Shammai" na nufin "tushen dangin Hebron," etc. Wasu juyi asu iya ɗaukar wannan fassarar.
Duba:
Duba:
"ta haifi"
Wadannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen kabilai ne.
Waɗannan sunayen kabilai ne.
1Waɗannan su ne 'ya'yan Dauda da aka haifa masa a Hebron: ɗan fari shi ne Amnon, ta wurin Ahinowam daga Yezriyel; na biyun shi ne Daniyel, ta wurin Abigel daga Karmel;2na ukun shi ne Absalom, wanda uwarsa ita ce Ma'aka, ɗiyar Talmai sarkin Geshur. Na huɗun shi ne Adonijah ɗan Haggit;3na biyar shi ne Shefatiya ta wurin Abital; na shida shi ne Itreyam ta wurin Egla matarsa.4Waɗannan shida aka haifa wa Dauda a Hebron, inda ya yi sarauta shekaru bakwai da wata shida. Sa'an nan ya yi sarauta a Yerusalem shekaru talatin da uku.5Waɗannan 'ya'ya maza huɗu ta wurin Batsheba ɗiyar Ammiyel aka haifa masa su a Yerusalem: Shamuwa, Shobab, Natan, da Suleman.6Wasu 'ya'ya maza na Dauda su ne: Ibhar, Elishuwa, Elifelet,7Nogah, Nefeg, Yafiya,8Elishama, Eliyada da Elifelet.9Waɗannan su ne 'ya'yan Dauda maza, banda 'ya'yan da ƙwaraƙwarai suka haifa masa. Tamar 'yar'uwarsu ce.10Ɗan Suleman shi ne Rehobowam. Ɗan Rehobowam shi ne Abiya. Ɗan Abiya shi ne Asa. Ɗan Asa shi ne Yehoshafat.11Ɗan Yehoshafat shi ne Yehoram. Ɗan Yehoram shi ne Ahaziya. Ɗan Ahaziya shi ne Yo'ash.12Ɗan Yo'ash shi ne Amaziya, Ɗan Amaziya shi ne Azariya. Ɗan Azariya shi ne Yotam.13Ɗan Yotam shi ne Ahaz. Ɗan Ahaz shi ne Hezekiya. Ɗan Hezekiya shi ne Manasse. Ɗan14Manasse shi ne Amon. Ɗan Amon shi ne Yosiya.15Ga 'ya'yan Yosiya na farkon shi ne Yohanan, ɗansa na biyu Yaho'iakim, ɗansa na uku Zedekiya, ɗansa na huɗu Shallum.16'Ya'yan Yeho'akim su ne Yeho'iacin da Zedekiya.17'Ya'yan Yaho'iacin, ɗan bautar talala, su ne Sheltiyal,18Malkiram, Fedayiya, Shenazza, Yekamiya, Hoshama da Nedabiya.19'Ya'yan Fedayiya su ne Zerubabel da Shimei. 'Ya'yan Zerubabel su ne Meshullam da Hananiya; Shelomit 'yar'uwarsu ce.20Wasu 'ya'yansa maza biyar kuwa su ne Hashuba, Ohel, Berekiya, Hasadiya, Yushab-Hesed.21'Ya'yan Hananiya su ne Felatiya da Yeshayiya. Ɗansa shi ne Refayiya, waɗansu sauran zuriyoyin su ne Arnan, Obadiya, da Shekaniya22Ɗan Shekaniya shi ne Shemayiya. 'Ya'yan Shemayiya su ne Hattush, Igal, Bariya, Niyariya, da Shafat.23'Ya'yan Niyariya guda uku su ne Eliyonai, Hizkiya, da Azrikam.24'Ya'yan Eliyonai su bakwai ne su ne Hodabiya, Eliyashib, Felayiya, Akkub, Yohanan, Delayiya da Anani.
Dauda ɗan Yesse, daga zuriyar Yahuda. (Duba: 2:15)
Waɗannan sunayen mata ne.
Waɗanan sunayen mutane ne.
Wannan mutumin yana da suna iri ɗaya da annabi Ba'isra'ile, amma wani daban ne.
A na iya fassara shi a zaman bayani dabam. AT: "Dauda yayi sarauta a can shekara bakwai da wata shida."
Waɗanan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan ne farkon lissafin zuriyar Dauda da suka zama sarakuna.
Suleman yana da ɗa fiye da daya. Haka ma sauran maza suke a lissafin. AT: "Suleman shine mahaifin Rehobowam. Rehobowam shine mahaifin Abija"
Wannan wani sunna ne na Uziya, sunnan da aka fi sani na sarki.. Mai fassara yana iya yanke shawarar amfani da sunnan "Uziya" a ko'ina wa wannan sarkin.
Wannan ya ci gaba da lissafin zuriyar Dauda da suka zama sarakuna. Ka yi da wannan bayani kamar yadda ka yi a farko a 3:10.
Wannan shi ne sunan mutum.
Wannan ya ci gaba da lissafin zuriyar Dauda da suka zama sarakuna. Ka yi da wannan bayani kamar yadda ka yi a farko a 3:10.
Waɗannan sune sunayen mazaje.
Wasu juyi suna amfani da "Yekoniya" wanda ya banbanta da "Yahoyachin."
Wannan na iya zama taken da aka bawa Yahoyachin domin an kai shi bauta. duk da haka wasu juyi suna daukar kalmar kamar "Assir," sunan daya daga cikin 'ya'yansa maza.
Wannan mutumin yana da suna iri ɗaya kamar Annabi Obadiya amma wannan wani ne daban.
Juyi daban-daban sun sanya waɗannan mutane a cikin hurɗoɗi daban-daban da juna, sobada Ibraniyanci bai yi bayanni sosai game da su ba.
Waɗannan sune sunayen mazaje.
1'Zuriyar Yahuda su ne Ferez, Hezron, Karmi, Hur da Shobal.2Shobal shi ne mahaifin Reyayiya. Reyayiya shi ne mahaifin Yahat. Yahat shi ne mahaifin Ahumai da Lahad. Waɗannan su ne dangogin Zoratawa.3Waɗannan su ne kakannin dangogin da ke cikin birnin Itam: Yezriyel, Ishma, da Idbash. Sunan 'yar'uwarsu Hazzelelfoni.4Feniyel shi ne kakan dangoginn da ke cikn birnin Gedor. Ezer shi ne na asalin dangogin da ke cikin Hushah. Waɗannan su ne zuriyar Hur, ɗan farin Efrata kuma shi ne asalin Betlehem.5Ashur mahaifin Tekowa ya na da mata biyu, Helah da Na'arah.6Na'arah ta haifa masa Ahuzzam, Hefa, Temeni, Hahashtari. Waɗannan su ne 'ya'yan Na'arah.7'Ya'yan Helah su ne Zeret, Zohar, Itnan,8da Koz wanda ya zama mahaifin Anub da Hazzobeba, da dangogin zuriyar da suka fito daga Ahahel ɗan Harum.9Yabez ya sami girmamawa fiye da 'yan'wansa. Mahaifiyarsa ta kira shi Yabez. Ta ce, "Domin na haife shi cikin azaba."10Yabez ya kira bisa sunan Yahweh na Isra'ila ya ce, "Idan da za ka albarkace ni da gaske, ka faɗaɗa mani iyakata, hannunka ya kasance tare da ni. Idan ka yi haka ka kare ni daga cuta, domin in 'yantu daga azaba!" Sai Yahweh ya amsa addu'arsa.11Kaleb ɗan'uwan Shuhah shi ne mahaifin Mehir, wanda shi ne mahaifin Eshton.12Eshton shi ne mahaifin Bet Rafa, Faseya, da Tehinna, wanda shi ne mahaifin Ir Nahash. Waɗannan su ne mutanen da suka zauna a Reka.13'Ya'yan Kenaz su ne Otniyel da Serayiya. 'Ya'yan Otniyel su ne Hatat da Meyonotai.14Meyonotai ya zama mahaifin Ofra, Serayiya ya zama mahaifin Yowab wanda ya kafa Ge-Harashim, mutanen masassaƙa ne.15'Ya'yan Kaleb 'ɗan Yefune su ne Iru, Elah da Na'am. Ɗan Elah shi ne Kenaz.16'Ya'yan Yehallelel su ne Zif, Zifa, Tiriya da Asarel.17'Ya'yan Ezrah su ne Yeter, Mered, Efer, da Yalon. Matar Mered Bamasariye ta haifi Miriyam, Shammai, da Ishba, wanda shi ne mahaifin Estemowa.18Waɗannan su ne 'ya'yan Bitiya, ɗiyar Fir'auna, wadda Mered ya aura. Matar Mered Bayahude ta haifi Yarid, wanda shi ne mahaifin Gedor; Haba, wanda ya zama mahaifin Soko; da Yekutiyel, wanda shi ne ya zama mahaifin Zanowa.19Matar Hodiya 'yar'uwar Naham, tana da 'ya'ya maza biyu, ɗaya daga cikinsu ya zama mahaifin Keila Bagarme. Ɗayan kuwa shi ne Eshtamowa Bamaakate.20'Ya'yan Shimon su ne Amon, Rinna, Ben-Hanan da Tilon. 'Ya'yan Ishi su ne Zohet da Ben-Zohet.21Zuriyar Shela ɗan Yahuda su ne Er mahaifin Leka, La'ada mahaifin Maresha da dangogin da ke sana'ar linin a Bet Ashbiya,22Yokim, mutanen Kozeba, da Yo'ash da Saraf, da ya yi mulki a Mowab da Yashubi Lehem. (Wannan labari daga daɗaɗen rubutu ne.)23Waɗannan su ne maginan tukwane da suka zauna a Netayim da Gedera, suka yi wa sarki aiki.24Zuriyar Simiyon su ne Nemuyel, Yamin, Yarib, Zera da Shawul.25Shallum ɗan Shawul ne, Mibsam ɗan Shallum ne, kuma Mishma ɗan Mibsam ne.26Zuriyar Mishma su ne ɗansa Hamuyel, Zakur jikansa da Shimei tattaɓa kunnensa.27Shimei yana da 'ya'ya goma sha shida da 'ya'ya mata shida. Ɗan'uwansa bai haifi 'ya'ya da yawa ba, saboda haka dangoginsu ba su yi yawa kamar mutanen Yahuda ba.28Su ka zauna a Biyasheba, Molada, da kuma Hazar Shuwal.29Sun kuma zauna a Bilha, Ezem, Tolad,30Betuwel, Horma, Ziklag,31Bet Markabot, Hazar Susim, Bet Biri, da Sha'arayim. Waɗannan su ne biranensu har ya zuwa mulkin Dauda.32Ƙauyukansu biyar su ne Itam, Ain, Rimmon, Token, da Ashan,33da dukkan ƙauyukan da ke kewaye har zuwa Baalat. Waɗannan su ne mazauninsu, kuma suka adana tarihin zuriyarsu a rubuce.34Shugabannin dangi su ne Meshobab, Yamlek, Yosha ɗan Amaziya,35Yowel, Yehu ɗan Yoshibiya ɗan Serayiya ɗan Asiyel,36Eliyonai, Ya'akoba, Yeshohaiya, Asayiya, Adiyel, Yesimiyel, Binayiya37da Ziza ɗan Shifi ɗan Allon ɖan Yedayiya ɗan Shimri ɗan Shemayiya.38Waɗannan da aka ambata da sunaye shugabanni ne cikin dangoginsu, dangoginsu kuma su ka ƙaru ainun.39Su ka tafi kusa da Gebor, yamma da kwari, domin su nemi makiyaya saboda garkunansu.40Suka kuwa sami makiyaya mai dausayi. Ƙasar mai girma ce, ba fitina ga kuma salama. Dã Hamawa suka zauna a wurin.41Waɗannan da aka lisafta da sunaye sun zo ne a zamanin Hezekiya sarkin Yahuda, suka hari mazaunin Hamawa da na Mewunawa, waɗanda su ke a wurin. Suka hallakar da su gaba ɗaya suka gãje wurin sabili da sun sami makiyaya mai dausayi domin garkunansu.42Mutane ɗari biyar daga kabilar Simiyon su ka tafi Tsaunin Seyir, tare da shugabaninsu Felatiya, Niyeriya, Refayiya, da Uzziyel 'ya'yan Ishi.43Suka ci sauran Amelikawa 'yan gudun hijira, suka zauna a can har zuwa yau.
Waɗannan sunayen mutane ne.
An kira garin da sunan mutanen da ke zaune a garin wato Zora.
Waɗannan sunayen birane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan sunan mace ce.
"Fenuwel da Ezer kakan su shine Hur." Wannan ya nuna jerin waɗanda zasu biyo baya.
Bisa ga fahimta wadannan sunayen mutane. Koda yake wasu juyi sun fahimce su a matsayin sunayen zuriya wanda ta samo asali daga ɗan Ashur.
Waɗannan sunayen mata ne.
AT: "ta haifa masa 'ya'ya maza"
Za a iya fara sabuwa bayyani a nan. "Koz ya zama kakan Harum da zuriyar da suka fito daga Ahahel ɗan Harum"
Wannan sunnan mutum ne.
AT: "ka ƙara mani gonaki"
Ma'ana mai yiwuwa sune hannun Allah na wakiltar 1) kiyayewarsa, 2) ikonsa, ko 3) kariyarsa. AT: "ka bishe ni" ko "ka ba ni nasara" ko "ka ƙare ni." Za a iya fassarar shi kamar "ka kassance tare da ni."
"Yayi masa kamar yadda ya roƙa a cikin addu'ar sa"
Waɗannan sunayen mutane ne
"Tehinna wanda ya kafa garin Nahash"
Wannan sunan Birni ne.
Wannan sunan wuri ne.
Zai zama da taimako a yi hawan aya kuma a haaɗa aya 15 tare da 13 tunda Kenaz dangin Yefhunne ne da kuma Kaleb.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Ge-Harashim na nufin "Kwarin Kwararu." A na iya fassara ma'anar sunan ko ana iya bayyaninsa tare da bayani. AT: "Ge-Harashim, wanda ya ke nufin 'Kwarin Kwararu'. A na kiranta haka saboda mutunenta masu tsarafa ƙarafuna ne."
mutane da suka shahara a ƙira ko gine ginen abubuwa.
Bayanin da ke a 4:17 an sake shirya shi don a iya gane ma'anar da sauƙi.
Kalman nan "waɗannan" na nufin Miriyam, Shammai, da Ishba. Su ne 'ya'yan Bitiya haifa ma mijinta Mered.
Wannan sunan mace ce.
Wani daga rukunin mutanen Garmawa.
Wani daga yankin Ma'akatiya wanda ake kira Ma'akat.
Waɗannan sunayen mutane ne.
wani irin yaddin zani
mutane da ke ginin tukwane dag yumɓu
Waɗannan sunayen ɓirane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
'ya'yan ɗanka.
'ya'ya maza 16 da 'ya'ya mata 6.
Waɗannan sunayen garuruwa ne.
Lissafin biranen da zuriyar Simiyon suka zauna ya ci gaba.
Waɗannan su ne sunayen birane.
Lissafin biranen da zuriyar Simiyon suka zauna ya ci gaba.
Waɗannan sunayen ƙauyuka ne.
Wannan sunan gari ne. Ana kuma kiran sa Ba'alat.
Waɗannan mutanen shugabanni ne.
Yawan mutane a zuriyar su ya ƙaru sosai.
Wannan sunan gari ne.
wanni ɓangaren gona inda dabbobi ke kiwo a ciyawa
mai yawa sosai
zuriyar Ham
Wannan sunan kungiyar mutane. AT: "zuriyar Mewun"
"mutane 500"
Waɗannan sunayen mutane ne.
"Amelikawa 'yan gudun hijira da suka rage"
mutanen da aka tilastawa su bar gidajen kasarsu
"daga wancan lokacin har zuwa yau"
1'Ya'yan Ruben ɗan farin Isra'ila - Ruben shi ne ɗan farin Isra'ila, amma aka ba da girman ɗan farinsa ga 'ya'yan Yosef ɗan Isra'ila domin Ruben ya ƙazantar da gadon mahaifinsa. Saboda haka ba a lisafta shi a matsayin ɗan fãri ba.2Yahuda shi ne mafi ƙarfi cikin 'ya'uwansa, shugaba kuma zai fito da ga cikinsa. Amma albarkar ɗan fari na Yosef ne -3'ya'yan Ruben ɗan farin Isra'ila su ne Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.4Waɗannan su ne zuriyar Yowel: Ɗan Yowel shi ne Shemayiya. Ɗan Shemayiya shi ne Gog. Ɗan Gog shi ne Shimei.5Ɗan Shimei shi ne Mika. Ɗan Mika shi ne Reyayiya. Ɗan Reyayiya shi ne Ba'al.6Ɗan Ba'al shi ne Bira, wanda Tilgat Filesa sarkin Asiriya ya kai su bautar talala. Bira shugaba ne cikin kabilar Ruben.7Waɗannan su ne 'yan'uwan Bira cikin dangoginsu ga yadda aka lisaftasu cikin rubutun tarihin asali: Yeyel shi ne babba, Zekariya, da8Bela ɗan Azaz ɗan Shema ɗan Yowel. Suka zauna a Arowa, har can nesa da Nebo da Ba'al Meyon,9daga gabas kuma har zuwa goshin jejin da ya miƙe zuwa Kogin Yuferatis. Wannan ya zama haka domin suna da garken dabbobi da yawa a ƙasar Giliyad.10A zamanin Saul, kabilar Ruben ta faɗa wa Hagarawa ta ci su. Suka zauna a rumfunan Hagarawa a dukkan ƙasar da ke gabashin Giliyad.11'Yan kabilar Gad suka zauna kusa da su, a cikin ƙasar Bashan har zuwa Saleka.12Shugabanninsu su ne Yowel, wanda shugaba ne, da Shafan shi ma wani shugaba ne, da Yanai da Shafat a Bashan.13'Yan'uwansu ta wurin iyalan mahaifisu su ne Mika'el, Meshulam, Sheba, Yorai, Yakan, Ziya, da Eber - su bakwai cur.14Waɗannan mutane da aka ambata a baya su ne zuriyar Abihal, Abihal ɗan Huri ne, Huri ɗan Yarowa ne. Yarowa ɗan Giliyad ne. Giliyad ɗan Mika'el ne. Mika'el ɗan Yeshishai ne. Yeshishai ɗan Yahdo ne. Yahdo ɗan Buz ne.15Ahi ɗan Abdiyel ɗan Guni, shugaba ne a iyalin mahaifinsa.16Sun zauna a Giliyad, da Bashan da cikin garuruwanta da kuma cikin dukkan makiyayan ƙasar Sharon har zuwa goshin iyakarta.17An rubuta waɗannan dukka bisa ga tarihin asali a kwanakin Yotam sarkin Yahuda da kuma Yerobowam sarkin Isra'ila.18Rubenawa da Gadawa, da rabin kabilar Manasse su na da jarumawa dubu arba'in da hudu gwanayen mayaƙa, ɗauke da garkuwa da takobi da masu harbi da baka.19Suka kai hari ga Hagarawa, Yetur, Nafish, da Nodab.20Suka sami taimakon yin yaƙi da abokan gabarsu daga Mai iko dukka. Da haka ne, su ka ci Hagarawa da dukkan waɗanda ke tare da su. Wannan ya faru domin Isra'ilawa sun yi kuka ga Allah cikin yaƙin, ya kuma sauraresu domin sun dogara gareshi.21Suka washe dabbobinsu, tare da raƙuma dubu hamsin, tumaki 250,000, jakai dubu biyu, da mazaje 100,000.22Sabili da Allah ya yi yaƙi domin su, suka kashe maƙiyansu da yawa. Suka zauna a ƙasarsu har lokacin zuwa bautar talala.23Rabin kabilar Manasse suka zauna a ƙasar Bashan har zuwa Ba'al Harmon da Senir (wato Tsaunin Harmon).24Waɗannan su ne shugabannin gidajen ubanninsu: Efer, Ishi, Eliyel, Azriyel, Irmiya, Hodabiya, da Yadiyel. Waɗannan ƙarfafa ne kuma jarumawan mutane ne, shahararrun mutane, shugabannin gidajen ubanninsu.25Amma suka yi rashin aminci ga Allahn kakanninsu. A maimako, sai suka yi sujada ga allolin mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallakar a gabansu.26Allah na Isra'ila ya zuga Ful sarkin Asiriya (ana kiransa Tilgat Filesa sarkin Asiriya). Ya kwashe waɗannan zuwa bautar talala Rubenawa, da Gadawa da rabin kabilar Manasse. Ya kawo su Halah, Habor, Hara, har kuma ya zuwa kogin Gozan, in da suke zaune har wa yau.
Kalmar nan "yanzu" ana amfani da ita anan don alamar canji daga jerin zuriya zuwa bayyanin asali game da Ruben.
"amma aka ba da girman ɗan farinsa ga 'ya'yan Yosef, wani ɗan Isra'ila kuma"
Wannan zance ta ladabi don yin magana game da yadda Ruben yayi lalata da matar mahaifinsa ta biyu. Babban gado shi ne wurin da mutun da matarsa zasu kwana tare.
"Labarin tarihin iyalin bai lisafta Ruben a matsayin ɗan fãri ba"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan na iya fara sabuwar jumla." An lissafta su bisa ga littafin asalinsu"
rubutu da ke nuna yadda mutane a cikin iyali suke da alaƙa da juna
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen ɓirane ne.
Waɗannan sunayen kungiyoyin mutane ne.
Wannan sunan gari ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
AT: " ɓabilar Gadawa sun zauna"
yankin kasar da dabbobi ke kiwo a ciyawa
AT: "An lissafta su bisa ga asalinsu" ko " kuma jerin sunayen asalin zuriyarsu ne"
Ba a bayyana adadin mutanne da ake magana a kansu ba.
Wannan na nufin mutane daga ƙabilar Ruben.
Wannan na nufin mutane daga ƙabilar Gad.
sojoji dubu arba'in da hudu" ko "sojoji 44,000"
An bayyana sojojin kamar wadda suka kware a yaki ta hanyar makamam da suka dauka. AT: "An horar da su a cikin hanyoyin yaƙe yaƙe sosai"(Duba: da )
Waɗannan sunayen ƙungiyar mutane ne.
"Isra'ilawa sun yi ta rokon Allah domin taimako"
AT: "Isra'ilawa sun kama Hagarawa "
"raƙuma 50,000"
"jakai 2000"
Allah ya taimaka a yaki ana kwatanta shi kamar soja wanda yayi yaƙi a bakin daga. AT: "Don Allah ya taimake su"
Waɗannan sunayen tsaunuka ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen kungiyoyin mutane ne.
Waɗannan sunayen garuruwa ne.
Wannan sunan koji ne.
1'Ya'yan Lebi su ne Geshon, Kohat, da Merari.2'Ya'yan Kohat su ne Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel.3'Ya'yan Amram su ne Haruna, Musa da Miriyam. 'Ya'yan Haruna su ne Nadab, Abihu, Eliyeza da Itama.4Eliyeza ya zama mahaifin Finehas sai kuma Finehas ya zama mahaifin Abishuwa.5Abishuwa ya zama mahaifin Bukki. Sai Bukki ya zama mahaifni Uzzi.6Uzzi ya zama mahaifin Zerahiya, Zerahiya yazama mahaifni Merayot.7Merayot ya zama mahaifni Amariya, Amariya ya zama mahaifni Ahitub.8Ahitub ya zama mahaifin Zadok, Zadok ya zama mahaifin Ahima'az.9Ahima'az ya zama mahaifin Azariya, Azariya ya zama mahaifin Yohanan.10Yohanan ya zama mahaifin Azariya wanda ya yi hidima a haikalin da Suleman ya gina a Yerusalem.11Azariya ya zama mahaifin Amariya kuma Amariya ya zama mahaifin Ahitub.12Ahitub ya zama mahaifin Zadok, Zadok ya zama mahaifin Shallum.13Shallum ya zama mahaifin Hilkiya, Hilkiya ya zama mahaifin Azariya.14Azariya ya zama mahaifin Serayiya, sai kuma Serayiya ya zama mahaifin Yozadak.15Aka kama Yozadak aka tafi da shi a tsare lokacin da Yahweh ya aika Yahuda da Yerusalem bautar talala ta hannun Nebukadnezza.16'Ya'yan Lebi su ne Gashom, Kohat, da Merari.17'Ya'yan Gashom su ne Libni, da Shimei.18'Ya'yan Kohat su ne Amram, Izar, Hebron da Uzziyel.19'Ya'yan Merari su ne Mali da Mushi. Waɗannan ne suka zama kabilar Lebiyawa bisa ga gidajen ubanninsu.20Zuriyar Gershon ya soma da ɗansa Libni ɗan LIbni kuwa Yahat ne. Ɗansa kuwa Zimma ne.21Ɗansa Yohat ne. Ɗansa Iddo ne. Ɗansa Zera ne. Ɗansa Yeyaterai ne.22Zuriyar Kohat: Ɗansa shi ne Aminadab. Ɗansa kuwa shi ne Kora. Ɗansa shi ne Assir.23Ɗansa shi ne Elkana. Ɗansa shi ne Abiyasaf. Ɗansa shi ne Assir.24Ɗansa shi ne Tahat. Ɗansa shi ne Uriyel. Ɗansa shi ne Uzziya. Ɗansa shi ne Shawul.25'Ya'yan Elkana su ne Amasai, Ahimot, da wani ɗa kuma da aka kira Elkana.;26Ɗansa shi ne Zofai. Ɗansa shi ne Nahat.27Ɗansa shi ne Eliyab. Ɗansa shi ne Yeroham. Ɗansa shi ne Elkana.28'Ya'yan Sama'ila su ne ɗan farinsa Yowel, da Abiya na biyu.29Ɗan Merari shi ne Mahli. Ɗansa shi ne Libni. Ɗansa shi ne Shimei. Ɗansa shi ne Uzza.30Ɗansa shi neShimeya. Ɗansa shi ne Haggiya. Ɗansa shi ne Asayiya.31Waɗannan su ne sunayen mutanen da Dauda ya sa su bisa hidimar waƙa a haikalin Yahweh, bayan da akwatin alƙawari ya sami hutawa a wurin.32Suka yi hidima ta wurin waƙoƙi a gaban rumfar sujada, rumfar taruwa, har sai da Suleman ya gina haikalin Yahweh a Yerusalem. Suka aiwatar da hidimarsu bisa ga umarnin da aka ba su.33Waɗannan su ne suka yi hidima da 'ya'yansu. Daga dangogin Kohatawa aka sami Heman mawaƙi. Ga kakanninsa idan an koma lokacin baya: Heman ɗan Yowel ne. Yowel ɗan Sama'ila ne.34Sama'ila ɗan Elkana ne. Elkana ɗan Yeroham ne. Yeroham ɗan Eliyel ne. Eliyel ɗan Towa ne.35Towa ɗan Zuf ne. Zuf ɗan Elkana ne. Elkana ɗan Mahat ne. Mahat ɗan Amasai ne. Amasai ɗan Elkana ne.36Elkana ɗan Yowel ne. Yowel ɗan Azariya ne. Azariya ɗan Zefaniya ne.37Zefaniya ɗan Tahat ne. Tahat ɗan Assir ne. Assir ɗan Ebiyasaf ne. Ebiyasaf ɗan Kora ne.38Kora ɗan Izar ne. Izar Kohat ne. Kohat ɗan Lebi ne. Lebi ɗan Isra'ila ne.39Abokin Heman Asaf ne, shi ya tsaya a hannun damarsa. Asaf ɗan Berekiya ne. Berekiya ɗan Shimeya ne.40Shimeya ɗan Mika'el ne. Mika'el ɗan Ba'asiya ne. Ba'asiya ɗan Malkiya ne.41Malkiya ɗan Etni ne. Etni ɗan Zera ne. Zera ɗan Adaya ne.42Adaya ɗan Itam ne. Itam ɗan Zimma ne. Zimma ɗan Shimei ne.43Shimei ɗan Yahat ne. Yahat ɗan Geshon ne. Geshon ɗan Lebi ne.44A hannun hagun Herman akwai abokansa su ne "ya'ya Merari. Su ne waɗannan Etan ɗan Kishi. Kishi ɗan Abdi ne. Abdi ɗan Malluk ne.45Malluk ɗan Hashabiya ne. Hashabiya ɗan Amaziya ne. Amaziya ɗan Hilkiya ne.46Hilkiya ɗan Amzi ne. Amzi ɗan Bani ne. Bani ɗan Shemer ne.47Shemer ɗan Mahli ne. Mahli ɗan Mushi ne. Mushi ɗan Merari ne. Merari ɗan Lebi ne.48Aka ba abokan aikinsu Lebiyawa dukkan hidimar rumfar sujada, gidan Yahweh.49Haruna da 'ya'yansa suka yi hidimar miƙa baye-baye bisa bagadi domin baye-bayen ƙonawa; da kuma baiko bisa bagadin turare domin dukkan aiki a wuri mafi tsarki. Waɗannan baye-baye suka yi kaffara domin Isra'ila, bisa ga dukkan abin da bawan Allah Musa ya umurta.50Zuriyar Haruna kenan bi da bi: Ɗan Haruna shi ne Eliyeza. Ɗan Eliyeza shi ne Fenihas. Ɗan Fenihas shi ne Abishuwa.51Ɗan Abishuwa shi ne Bukki. Ɗan Bukki shi ne Uzzi. Ɗan Uzzi shi ne Zerahiya.52Ɗan Zerahiya shi ne Merayot. Ɗan Merayot shi ne Amariya. Ɗan Amaraiya shi ne Ahitub.53Ɗan Ahitub shi ne Zadok. Ɗan Zadok shi ne Ahima'az.54Ga wuraren da aka ba zuriyar Haruna su zauna, wato, zuriyar Haruna waɗanda ke daga dangin Kohatawa (rabo na fari nasu ne).55Aka ba su Hebron a ƙasar Yahuda da kuma makiyayarta,56amma jejin birnin da ƙauyukansa aka ba Kaleb ɗan Yefunne.57Aka ba zuriyar Haruna: Hebron (birnin mafaƙa), da Libna da makiyayarta, Yattir, Estomawa da makiyayarta,58Hilen da makiyayarta, da Debir da makiyayarta.59Aka ba zuriyar Haruna: Ashan da makiyayarta, Yutta da Bet Shemesh da makiyayarta;60daga kabilar Benyamin aka ba su Geba da makiyayarta, Alemet da makiyayarta, da Anatot da makiyayarta. Dukkan biranen iyalen Kohat guda goma sha uku ne.61Ga sauran zuriyar Kohat ta wurin kuri'a aka ba su birane goma daga rabin kabilar Manasse.62Ga zuriyar Gershon a cikin dangoginsu da bam da bam aka ba su birane goma sha uku daga cikin kabilar Issaka, Asha, Naftali, da rabin kabilar Manasse a Bashan.63Aka ba zuriyar Merari birane goma sha biyu dangi bayan dangi, daga kabilar Ruben, Gad da Zebulun.64Sai mutanen Isra'ila suka bada waɗannan birane da makiyayarsu ga Lebiyawa.65Aka ba su ta wurin ƙuri'a garuruwan da aka zana a baya daga kabilun Yahuda, Simiyon da Benyamin.66Ga wasu dangogin Kohatawa aka bada birane daga gundumar Ifraim.67Aka basu: Shekem (birnin mafaƙa) da makiyayarta a ƙasar duwatsu ta Ifraim, Gezer da makiyayarta,68Yokmiyam da makiyayarta, Bet Horon da makiyayarta,69Aijalon da makiyayarta, da Gat Rimmon da makiyayarta.70Rabin kabilar Manasse suka ba Kohatawa: Aner da makiyayarta da Bileyam da makiyayarta. Waɗannan suka zama mallaƙar sauran dangogin Kohatawa.71Zuriyar Geshon daga dangogin rabin kabilar Manasse, aka ba Golan a Bashan da makiyayarta da Ashtarot da makiyayarta.72Kabilar Issaka ta ba zuriyar Geshon: Kedesh da makiyayarta, Daberat da makiyayarta,73Ramot da makiyayarta, da Anem da makiyayarta.74Daga kabilar Asha Issaka ta karɓi: Mashal da makiyayarta, Abdon da makiyayarta,75Hukok da makiyayarta, da Rehob da makiyayarta.76Suka karɓa daga kabilar Naftali: Kedesh a Galili da makiyayarta, Hammon da makiyayarta, Kiriyatayim da makiyayarta.77Ga sauran zuriyar Merari aka ba su daga kabilar Zebulun: Yokheyam, Kartah, Rimmono da makiyayarta da Tabor da makiyayarta;78daga na kabilar Ruben a hayin Yodan a Yeriko, a gabashin kogin: Beza a cikin jeji da makiyayarta, Yahza da makiyayarta,79Kedemot da makiyayarta, da Mefa'at da makiyayarta.80Daga kabilar Gad, Lebiyawa suka karɓi: Ramot a Giliyad da makiyayarta, Mahanayim da makiyayarta,81Heshbon da makiyayarta, da Yazer da makiyayarta.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
An kwatanta ikon rundunar sojojin Nebukadnezza da wani bangare na jiki
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
ɗa na biyu da aka haifa
"mutanen Isra'ila suka ajiye akwatin alƙawari a wurin"
AT: "mawaƙan sun yi biyayya da umarnin Dauda"
"Waɗannan ne mawaƙan"
Waɗannan sunnan wani kungiyar mutane ne.
Waɗannan sunnayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
"abokan aikinsa"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Ikon mutun ya dangana ga inda yake tsaye. hanun dama alama ne na inda mutane masu mulki ke tsayawa.
AT: "tsaye a hannun hagun Heman"
"abokan aikinsa"
AT: "Aikinsu abokan aikinsu ne, Lebiyawa, su yi" haka"
AT: "Waɗannan baye-baye suka yi domin a kaffara don zunubin mutanen Isra'ila"
Duba:
AT: "Waɗannan sune zuriyar Haruna"
AT: "Ga wuraren da aka ba zuriyar Haruna, dangin Kohatawa, suka zauna (an jefa kuri'a domin tabbatar da inda zasu zauna)"
Duba yadda ka juwa wannan a 6:33.
AT: "Aka ba su Hebron"
ƙasar da ciyawa da dabbobi ke ci.
Duba:
Duba:
AT: "Suna da birane 13"
"Zuriyar Gershon a cikin dangogin aka ba su birane 13"
Duba yadda ka juya wannan a 6:1.
AT: "garuruwan nan daga"
Duba:
Duba yadda ka juwa wannan a 6:33.
Duba:
Duba:
Duba yadda ka juya wannan a 6:1.
Duba:
Duba:
Bayyanin da ke cikin 6:77 an sake tsara shi saboda a fahimci ma'anar sa cikin sauƙi.
Duba:
1'Ya'yan Issaka huɗu su ne: Tola, Fuwa, Yashub, da Shimron.2'Ya'yan Tola su ne; Uzzi, Refayiya, Yeriyel, Yahmai, Ibsam, da Sama'ila. Su ne shugabannin gidajen ubanninsu, daga zuriyar Tola an lissafa su cikin jarumawa a zamanin su. Sun kai mutum 22,600 a cikin zamanin Dauda.3Dan Uzzi shi ne Izrahiya. 'Ya'yansa su ne Mika'el, Obadiya, Yowel da Ishiya, dukkansu biyar ɗin shugabannin zuriya ne.4Tare da su kuma suna da taron rundunar yaƙi zambar talatin da shida, bisa ga tsarin dake na dangogin kakanninsu, gama suna da mata yawa da 'ya'ya.5'Yan'uwansu, mayaƙan mutane daga dukkan kabilar Issaka, suna da jarumawa dubu tamanin da bakwai, bisa ga lissafin tarihin asalinsu.6'Ya'yan Benyamin uku su ne Bela, Beker, da Yediyayel.7'Ya'yan Bela guda biyar su ne Ezbon, Uzzi, Uzziyel, Yerimot, da Iri. Su sojoji ne kuma shugabannin gidajen ubanninsu. Mutanen su sun kai 22,034 mayaƙan mutane, bisa ga jerin lissafin dangogin kakanninsu.8'Ya'yan Beka su ne Zemirah, Yo'ash, Eliyeza, Eliyonai, Omri, Yeremot, Abijah, Anatot, da Alemet. Dukkan waɗannan 'ya'yansa ne.9Lissafin dangoginsu yakai 20,200 shugabannin gida idajen ubanninsu kuma jarumawa.10Ɗan Yediyel shi ne Bilhan. 'Ya'yan Bilhan su ne Yewush, Benyamin, Ehud, Kena'ana, Zetan, Tarshish, da Ahishaha.11Dukkan waɗannan 'ya'yan Yediyayel. Jerinsu cikin zuriyarsu sun kai 17,200 shugabannin gidajen ubanninsu kuma mayaƙa maza da su ka cancanci hidimar soja.12(Shuffitawa da Huffitawa 'ya'yan Ir, da Hushitawa ɗan Aher ne.)13'Ya'yan Naftali su ne Yahziyel, Guni, Yezer, da Shillem. Waɗannan su ne jikokin Bilha.14Manasse ya na da ɗa mai suna Asriyel, wanda ƙwarƙwararsa Ba'aramiye ta haifa. Ta kuma haifi Makir, mahaifin Giliyad.15Makir ya ɗauko mace daga wurin Huffitawa da Shuffitawa. Sunan 'yar'uwarta shi ne Ma'aka. Wata zuriyar Manasse kuma shi ne Zelofihad, wanda 'ya'yansa mata ne kaɗai.16Ma'aka matar Makir, ta haifa masa ɗa ta kira shi Feresh. Sunan ɗan'uwansa kuma shi ne Sheresh, 'ya'yansa kuma Ulam da Rakem.17'Ɗan Ulam kuma shi ne Bedan. Waɗannan su ne zuriyar Giliyad ɗan Makir ɗan Manasse.18'Yar'uwar Giliyad Hammoleket ta haifi Ishhod, Abiyeya, da Mahla.19'Ya'yan Shemida su ne Ahiyan, Shekem, Likhi, da Aniyam.20Zuriyar Ifraim su ne kamar haka: ɗan Ifraim shi ne Shutela. Ɗan Shutela shi ne Bered. Ɗan Bered shi ne Tahat. Ɗan Tahat shi ne Eleyada. Ɗan Eliyada shi ne Tahat.21Ɗan Tahad shi ne Zabad. Dan Zabad shi ne Shutela. (Ezer da Eleyad mutanen Gat ne suka kashe su, mutanen da aka haifa cikin ƙasar, lokacin da suka je su sace masu shanunsu.22Ifraim mahaifinsu ya yi makoki dominsu kwanaki da yawa, 'ya'uwansa kuma suka zo don su ta'azantar da shi.23Ya kwana da matarsa. Sai ta yi ciki ta haifi ɗa. Ifraim ya kira shi Beriya, saboda masifa ta zo wa iyalinsa.)24Ɗiyarsa ita ce Sheerah, wadda ta gina Runtse da Sama Bet Horon da Uzzen Sheerah.25Ɗansa shi ne Refha. Ɗan Refha shi ne Reshef. Ɗan Reshef shi ne Tela. Ɗan Tela shi ne Tahan. Ɗan Tahan shi ne Ladan.26Ɗan Ladan shi ne Ammihud. Ɗan Ammihud shi ne Elishama.27Ɗan Elishama shi ne Nun. Ɗan Nun shi ne Yoshuwa.28Mallakarsu da mazaunansu Betel ne da ƙauyukansu na kewaye. Suka miƙa ta gabashi zuwa Na'aran da yammaci zuwa Gezar da ƙauyukansu, zuwa Shekem da ƙauyukansu zuwa Ayyah da ƙauyukansu.29Akan iyaka da Manasse su ne Bet Shan da ƙauyukansu, Ta'anak da ƙauyukansu Megiddo da ƙauyukansu, da Dor da ƙauyukansu. A cikin waɗannan garuruwa zuriyar Yosef ɗan Isra'ila suke zaune.30'Ya'yan Asha su ne Imna, Ishba, Ishbi, da Beriya. Serah 'yar'uwar su ce.31'Ya'yan Beriya su ne Heber da Malkiyel, shi ne mahaifin Birza'it.32'Ya'yan Heber su ne Yaflet, Shomer da Hotman. Shuwa 'yar'uwarsu ce.33'Ya'yan Yaflet su ne Fasak, Bimhal, da Ashbat. Waɗannan su ne 'ya'yan Yaflet.34Shomer, ɗan'uwan Yaflet, yana da 'ya'ya kamar haka: Roga, Hubba, da Aram.35Ɗan'uwan Shemer, wato Helem, yana da 'ya'ya kamar haka: Zofa, Imna, Shelesh, da Amal.36'Ya'yan Zofa su ne Suwa, Harnefa, Shuwal, Beri, Imrah,37Bezer, Hod, Shamma, Shilsha, Itran, da Beera.38'Ya'yan Yeter su ne Yefunne, Fisfa, da Ara.39'Ya'yan Ulla su ne Ara, Hanniyel, da Riziya.40Duk waɗannan zuriyar Ashar ne. Su ne kakannin dangogi, shugabannin gidajen ubanninsu, fitattun mutane, mayaƙan mutane, sarakuna a cikin shugabanni. Sun kai su dubu ashirin da shida mazaje da suka cancanta domin yin hidimar aikin soja, bisa ga jerin lissafinsu.
Duba: da
"Dukan su sun kai dubu ashirin da biyu da dari shida"
AT: "a rayuwar Dauda"
"A cikin su kuma suna"
zambar sojojin yaƙi dubu sittin - "zambar sojoji 36,000 ne shirye domin yaki"
Duba: da
"ubanninsu" ko "kakanninsu"
Duba: da
Waɗannan sunayen mutane ne.
"Lissafin zuriyarsu sun kai dubu goma sha bakwai da ɗari biyu."
Waɗannan sunayen zuriyar ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
AT: "'ya'ya maza na ɗan Bilha"
Duba:
"AT: "ƙwarƙwararsa Ba'aramiye ta haifa"
Duba:
Duba:
AT: "Mutanen Gat, asalin mutanen ƙasar ne, suka kashe Ezer da Eleyad"
"yanuwansu ne suka je su sace shanun mutanen Gat"
"Sai ta yi ciki ta haifi ɗa. "
"bashi suna"
Wannan sunan mutum ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Duba:
Duba:
AT: "gidaje na a"
"A cikin waɗannan garuruwa zuriyar Yosef, ɗan Isra'ila, suke zaune"
Duba:
Duba:
Duba:
Duba:
"mutane masu martaba"
mazaje dubu shida ne aka lissafa da suka cancanta su yi hidimar aikin soja, bisa ga jerin lissafinsu - AT: "Bisa ga lissafin zuriyar, sun kai mazaje 26,000 da suka cancanta domin yin hidima a aikin soja"
1'Ya'yan Benyamin biyar su ne Bela ɗan farinsa, Ashbel, Aharan,2Nohah, da Rafa.3'Ya'yan Bela su ne Adda, Gera, Abihud,4Abishuwa, Na'aman, Ahowa,5Gera, Shefufan, da Huram.6Waɗannan su ne zuriyar Ehud shugabannin gidajen ubanninsu domin mazaunan Geba, waɗanda aka tilasta masu su tafi Manahat:7Na'aman, Ahiyah, da Gera. Na ƙarshen, Gera, ya jagorance su cikin tafiyarsu. Shi ne mahaifin Uzza da Ahihud.8Shaharayim ya zama mahaifni 'ya'ya cikin ƙasar Mowab, bayan ya saki matansa Hushim da Ba'ara.9Ta wurin matarsa Hodesh, Shaharayim ya zama mahaifin Yobab, Zibiya, Mesha, Malkam,10Yewuz, Shakiya, da Mirma. Waɗannan su ne 'ya'yansa, shugabanni cikin gidajen ubanninsu.11Ya rigaya ya zama mahaifin Abitub da Elfa'al ta wurin Hushim.12'Ya'yan Elfa'al su ne Eber, Misham, da Shemed (wanda ya gina Ono da Lod tare da ƙauyukan da ke kewaye da su).13Akwai kuma Beriya da Shema. Su ne shugabannin zuriyar da suke zama cikin Aijalon, waɗanda suka kori mazaunan Gat.14Beriya yana da waɗannan 'ya'ya: Ahio, Shashak, Yeremot,15Zebadiya, Arad, Eder,16Mika'el, Ishfa, da Yoha.17Elfa'al yana da waɗannan 'ya'yan: Zebadiya, Meshullam, Hizki,18Heber, Ishmerai, Izliya, da Yobab.19Shimei yana da waɗannan 'ya'yan: Yakim, Zikri, Zabdi,20Eliyenai, Zilletai, Eliyel,21Adayiya, Berayiya, da Shimrat.22Shashak yana da waɗannan 'ya'yan: Ishfan, Eber, Eliyel,23Abdon, Zikri, Hanan,24Hananiya, Elam, Antotijah,25Ifdeyiya, da Fenuwel.26Yeroham na da waɗannan 'ya'yan: Shamsherai, Shehariya, Ataliya,27Ya'areshiya, Iliya da Zikri.28Waɗannan su ne shugabannin gidajen ubanninsu da suka zauna cikin Yerusalem.29Yeyil, mahaifin Gibiyon, sunan matarsa ita ce Ma'aka, ya zamna cikin Gibiyon.30'Ɗan farinsa shi ne Abdon, sai Zur, Kish, Ba'al, Nadab,31Gedor, Ahiyo, da Zeker.32Wani daga cikin 'ya'yan Yeyil shi ne Miklot, wanda ya zama mahaifin Shimeya. Sun zauna kusa da 'yan'uwansu cikin Yerusalem.33Ner shi ne mahaifin Kish. Kish shi ne mahaifin Saul. Saul shi ne mahaifin Yonatan, Malki-Shuwa, Abinadab, da Esh-Ba'al.34'Ɗan Yonatan shi ne Merib-Ba'al. Merib-Ba'al shi ne mahaifin Mika.35'Ya'yan Mika su ne, Fithon, Melek, Tareya, da Ahaz.36Ahaz ya zama mahaifin Yehoada. Yehoada shi ne mahaifin Alemet, Azmabet da Zimri, Zimri shi ne mahaifin Moza.37Moza shi ne mahaifin Bineya. Bineya shi ne mahaifin Rafa. Rafa shi ne mahaifin Eliyasa. Eliyasa shi ne mahaifin Azel.38Azel yana da 'ya'ya shida: Azrikam, Bokeru, Ishmail, Sheyariya, Obadiya, da Hanan. Dukkan waɗannan 'ya'yan Azel ne.39'Ya'yan Eshek, da ɗan'uwansa, su ne Ulam ɗan farinsa, Yewush na biyu, da Elifelet na uku.40'Ya'yan Ulam mayaƙa ne da maharba. Suna da 'ya'ya da jikoki da yawa, jimillarsu 150. Dukkan waɗannan daga zuriyar Benyamin suke.
Duba: da
Duba:
"ana bukatar su tafi" ko "tilas su tafi"
Waɗannan sunayen maza ne.
Waɗannan sunayen mata ne.
AT: "Shaharayim da matarsa Hodesh ne ke da yaran maza."
Waɗannan sunayen maza ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Duba:
Bayannin a cikin 8:14 an sake shirya shi domin a iya fahimta da sauƙi.
Bayanin a cikin 8:19 an sake shirya shi domin a iya fahimta da sauƙi.
Bayanin a cikin 8:22 an sake shirya shi domin a iya fahimta da sauƙi.
Duba:
Kalmomin nana "kawunana zuriyoyin" da "shugabanin" na nufin abu ɗaya.
Duba:
A nan "maihaifin" na nufin jagaron wannan birnin Gibiyon. AT: "Yeyil, shugaban Gibiyon, ya zauna a Gibiyon sunan matarsa ita ce Ma'aka"
"Ɗan farin Yeyil"
Duba:
Duba:
Duba: da
AT: "Yewush ɗä na biyu, da Elifelet ɗä na uku"
AT: "Suna da jimillar 'ya'ya da jikoki ɗari da hamsin"
1Haka dukkan Isra'ila aka rubuta su bisa ga tarihin asalinsu. An rubuta su cikin littafin sarakunan Isra'ila. Amma game da Yahuda, an ɗauke su zuwa bauta cikin Babila saboda zunubinsu.2Na farko da suka zauna cikin biranensu su ne waɗansu Isra'ilawa, firistoci, Lebiyawa da bayin haikali.3Waɗansu zuriyar Yahuda, Benyamin, Ifraim, da Manasse sun zauna cikin Yerusalem.4Waɗanda suka zauna sun haɗa da Utai ɗan Ammihud ɗan Omri ɗan Imri ɗan Bani, ɗaya daga cikin zuriyar Ferez ɗan Yahuda.5A cikin Shelonawa su ne Asayiya ɗan fari da 'ya'yansa kuma.6A cikin zuriyar Zera akwai Yewuel. Yawan zuriyarsu ta kai 690.7Daga zuriyar Benyamin akwai Sallu ɗan Meshullam ɗan Hodabiya ɗan Hassenuya.8Akwai kuma Ibneyiya ɗan Yeroham; Elah ɗan Uzzi ɗan Mikri; da Meshullam ɗan Shefatiya ɗan Rewuel ɗan Ibnijah.9'Yan'uwansu da ke rubuce cikin tarihin asalinsu sun kai 956. Dukkan waɗannan mutanen shugabanni ne cikin zuriyar kakanninsu.10Firistoci su ne Yedayiya, Yeho'iarib, da Yakin.11Akwai kuma Azariya ɗan Hilkiya ɗan Meshullam ɗan Zadok ɗan Meraiyot ɗan Ahitub, shugaba a cikin gidan Allah.12Akwai Adayiya ɗan Yeroham ɗan Fashur ɗan Malkijah. Akwai kuma Ma'asai ɗan Adiyel ɗan Yahzera ɗan Meshullam ɗan Meshillemit ɗan Immer.13'Yan'uwansu, da suke shugabanni cikin gidajen kakanninsu, sun kai 1,760. Mutane ne da suka iya aiki cikin gidan Allah.14A wajen Lebiyawa, akwai Shemaiya ɗan Hasshub ɗan Azrikam ɗan Hashabiya, daga zuriyar Merari.15Akwai kuma Bakbakkar, Heresh, Galal, da Mattaniya ɗan Mika ɗan Zikri ɗan Asaf.16Akwai kuma Obadiya ɗan Shemaiya ɗan Galal ɗan Yedutun; and Berekiya ɗan Asa ɗan Elkana, wanda ya zauna a ƙauyukan Netofatawa.17Matsaran ƙofa su ne Shallum, Akkub, Talmon, Ahiman, da zuriyarsu. Shullam shi ne shugabansu.18Dã suna tsaro a ƙofar sarki ta wajen gabas domin sansanin zuriyar Lebi.19Shallum ɗan Kore ɗan Ebiyasaf, wanda a matsayinsa na ɗan Kora, da 'yan'uwansa daga gidan mahaifinsa, su Korawa, suna bisa aikin hidima, su na kula da ƙofar rumfa, kamar yadda kakanninsu suka kula da sansanin Yahweh, suna kuma tsaron wurin shiga.20Finehas ɗan Eliyeza shi ne shugabansu a dã, Yahweh kuma yana tare da shi.21Zekariya ɗan Meshelemiya shi ne mai tsaron ƙofar shiga haikali, "rumfar taruwa."22Dukkan waɗanda aka zaɓe su matsaran ƙofofi sun kai 212. An rubata sunayensu cikin lissafin mutane cikin ƙauyukansu. Dauda da Sama'ila mai gani sun sanya su cikin muƙamansu na amana.23Da su da 'ya'yansu sun kula da ƙofofin gidan Yahweh, wato rumfar sujada.24An sanya matsran ƙofofi a dukkan kusurwoyi huɗu, wajen gabas, yamma, arewa, da kudu.25'Yan'uwansu, da ke zaune a ƙauyukansu, sun zo domin kewayawa na kwana bakwai, a juyi.26Amma shugabannin matsara huɗu, wato Lebiyawa, an sanya su kula da ɗakuna da ɗakunan ajiya cikin gidan Allah.27Sukan tsaya dukkan dare a wurarensu kewaye da gidan Allah. Domin suke da haƙƙin kula da shi. Za su buɗe shi kowacce safiya.28Waɗansun su suna kula da kayan haikali; suna ƙirga su yayin da aka kawo su ko aka fitar da su.29Waɗansu kuma an sanya su kula da abubuwa masu tsarki, kayayyaki, da kayan da aka tanada, waɗanda sun haɗa da gari mai laushi, ruwan inabi, mai, da turaren ƙonawa, da kayan yaji.30Waɗansu 'ya'yan firistoci sukan haɗa kayan yaji.31Mattitiya, ɗaya daga cikin Lebiyawa wanda ɗan fari ne a wurin Shallum Korahiye, shi ne ke ɗauke da nawayar shirya gurasa domin baye-baye.32Waɗansu 'yan'uwansu, zuriyar Kohatawa, su ne masu kula da yin gurasa, su shirya kowacce Asabaci.33Mawaƙa da shugabannin gidajen ubannin Lebiyawa sun zauna cikin ɗakuna a wuri mai tsarki lokacin da ba su da wani aiki, domin dole su aiwatar da nasu ayyuka dare da rana.34Waɗannan shugabannin gidajen ubannin cikin Lebiyawa ne, kamar yadda ya ke a jere cikin rubutaccen tarihin asalinsu. Suna zama cikin Yerusalem.35Mahaifin Gibiyon, Yeyiyel, sunan matarsa itace Ma'aka, ya zauna cikin Gibiyon.36'Dan farinsa shi ne Abdon, ɗansa shi ne Zur, Kish, Ba'al, Ner, Nadab,37Gedor Ahiyo, Zekariya da Miklot.38Miklot shi ne mahaifin Shimeyam. Sun zauna kusa da 'yan'uwansu cikin Yerusalem.39Ner shi ne mahaifin Kish. Kish mahaifin Saul. Saul mahaifin Yonatan, Malki-Shuwa, Abinadab, da Esh-Ba'al.40Ɗan Yonatan shi ne Merib-Ba'al. Merib-Ba'al shi ne mahaifin Mika.41'Ya'yan Mika su ne Fithon, Melek, Tareya, da Ahaz.42Ahaz shi ne mahaifin Yada. Yada shi ne mahaifin Alemet, Azmabet, da Zimri. Zimri shi ne mahaifin Moza.43Moza shi ne mahaifin Bineya. Bineya shi ne mahaifin Refayiya. Refayiya shi ne mahaifin Eliyasa. Eliyasa shi ne mahaifin Azel.44'Ya'yan Azel shida su ne Azrikam, Bokeru, Ishma'el, Sheyariya, Obadiya, da Hanan. Waɗannan su ne 'Ya'yan Azel.
Tarihin asalinsu na nufin tarihin kabila ko kakannin mutum.
Wannan littafin ya rigaya ya bata.
Duba: da
Wannan sunan wata ƙungiyar mutane ne daga zuriyar Shelah.
Duba:
Duba:
Duba: da
AT: "Waɗannan mutane ne da suka iya aiki cikin gidan Allah"
"ɗaya daga cikin zuriyar"
Wannan sunan wani ƙungiyar jama'ane.
Duba:
"Masu gadi" ko "masu tsaron ƙofa"
Waɗannan jumlolin na nufin wurin shigar ƙofar rumfa, ko alfarwa.
"shugaban matsaran"
Duba:
AT: "Lissafin mutanen ƙauyukansu ya ƙunshi sunayen mazaje"
"zuriyarsu"
AT: "an sanya matsaran a ƙofar shigar gari"
AT: "zagaye duka"
"'yan'uwan masu gadi"
kewayewa, bi da bi - AT:" zasu zo su taimaka na tsawon kwana, bi da bi"
AT:" kula da ɗakuna"
"Wasu masu tsaro"
AT: "sun ƙirga rubuce rubucen da muta suka fitar, kuma suka ƙirga rubuce rubucen yayin da aka dawo da su"
AT: "a kula da" ko "a lura da"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen ƙungiyoyin mutane ne.
Duba shafi na fassara saboda wannan kalmar "gurasa" domin bayani a kan "gurasan kasancewa."
"ba sai sun yi wani aiki ba"
AT: "dole su aiwatar da nasu ayyukan"
AT: "Lissafin tarihin iyali ya shafi sunayen waɗannan shugabannin gidajen Lebiyawa"
Duba:
Ambatar Gibiyon na farko ana magana ne a kan mutum, na biyu kuma ɓirni ne.
Duba:
Duba: da
1Yanzu fa Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra'ila. Kowanne mutumin Isra'ila ya gudu daga gaban Filistiyawa su ka faɗi matattu a kan Tsaunin Gilbowa.2Filistiyawa suka runtumi Saul da ɗansa kusa kusa. Filistiyawa suka kashe Yonatan, Abinadab, da Malki-Shuwa, 'ya'yansa.3Yaƙi ya tsananta gãba da Saul ƙwarai, maharba kuma sun cim masa, kuma suka yi masa rauni.4Daga nan sai Saul ya ceda mai ɗaukar masa makamai, "Ka zare takobinka ka kashe ni da ita. In ba haka ba, waɗannan marasa kaciyar za su zo su zage ni." Amma mai ɗaukar makamansa yaƙi, domin yana jin tsoro ƙwarai. Sai Saul ya ɗauki takobinsa ya faɗi a kanta.5Sa'ad da mai ɗaukar makamansa ya ga Saul ya mutu, shi ma sai ya faɗi a kan takobinsa ya mutu.6Da haka Saul ya mutu, da 'ya'yansa uku. Dukkan iyalin gidansa suka mutu tare.7Sa 'ad da kowanne mutum a Isra'ila da ke cikin kwari yaga cewa sun gudu, kuma Saul da 'ya'yansa sun mutu, sai suka bar biranensu suka gudu. Daga nan sai Filistiyawa suka zo suka zauna cikinsu.8Ya zama kuwa washegari, sa'ad da Filistiyawa suka zo su ɗauki kayan matattu, sun tarar da Saul da 'ya'yansa matattu a Tsaunin Gilbowa.9Suka tuɓe shi suka ɗauki kansa da kayan yaƙinsa. Suka aikar da saƙo ko'ina cikin Filisitaya a kuma kai labarin ga gumakansu da mutane.10Suka sa kayan yaƙinsa cikin haikalin allolinsu, suka kafe kansa a gidan Dagon.11Sa'ad da dukkan mutanen Yabesh Giliyad suka ji dukkan abin da Filistiyawa suka yi wa Saul,12dukkan maza mayaƙa su ka je suka ɗauki jikin Saul da na 'ya'yansa, suka kawo su Yabesh. Suka bizne ƙasusuwansu ƙarƙashin itacen rimi cikin Yabesh suka yi azumi kwana bakwai.13Saul ya mutu saboda ya yi rashin amincin ga Yahweh. Bai yi biyayya ga umarnan Yahweh ba, amma ya nemi shawara a wurin wata mai yin magana da matattu.14Bai nemi shawara daga wurin Yahweh ba, shi yasa Yahweh ya kashe shi ya mayar da mulkin ga Dauda ɗan Yesse.
Duba:
AT: "Sojojin Isra'ila suka gudu daga"
AT: "Ya mutu"
Wannan kalmar "marasa kaciya" a nan zargi ne wanda ke nuna cewa mutanen ɓare ne kuma basu da wani dangantaka da Allah.
AT: "ya kashe kanshi da shi"
AT: "kuma 'ya'yansa uku suka mutu"
AT: "Sa'ad da mutanen a Isra'ila"
"zauna a cikin ɓiranen Isra'ila"
AT: "ɗauki duk wani kaya mai daraja daga jikin matattu"
Saul da 'ya'yansa sun matattu "
AT: "Filisitayawa sun cire komai daga jikin Saul"
"Filisitayawa sun sa kayan yaƙin Saul"
Wannan sunan wani gunki ne.
Duba: da
AT: "Sa'ad da dukkan mutanen Yabesh Giliyad suka ji dukkan abin da sojojin Filistiyawa" (Duba: da )
AT: "jikunnansu" ko "sauransu"
Wannan ra'ayi ko shawarwara ne game da abin da mutun zai yi.
AT: "yace yana magana da matattu"
AT: "ya bada mulkin mutanen Isra'ilai ga"
1Daga nan si dukkan Isra'ila suka zo wurin Dauda a Hebron suka ce, "Duba, mu ƙashinka da namanka ne.2Cikin kwanakin dã, lokacin da Saul ya ke sarki a bisanmu, kai ne ka ke jagorancin mutanen Isra'ila. Yahweh Allahnka ya ce maka, 'Za ka yi kiwon mutanena Isra'ila, kuma zaka zama mai mulki bisan mutanena Isra'ila.""3Dukkan dattawan Isra'ila suka zo wurin sarki a Hebron, Dauda ya yi alƙawari da su gaban Yahweh. Suka ƙeɓe Dauda sarki a bisan Isra'ila. Ta haka maganar Yahweh wadda Sama'ila ya furta ta zama gaskiya.4Dauda da dukkan Isra'ila suka je Isra'ila (wato, Yebus). Yebusawa mazaunan ƙasar, su na can.5Mazaunan Yebus suka ce da Dauda, "Ba za ka zo nan ba."6Amma Dauda ya ci kagarar Sihiyona, wato, Birnin Dauda. Dauda ya ce, "Duk wanda ya fara bugun Yebusawa zai zama shugaban yaƙi." Yowab ɗan Zeruya ya fara kai hari, aka mai she shi ya zama shugaba.7Daga nan Dauda ya fara zama cikin kagara. Sai suka kira ta birnin Dauda.8Ya gina garu kewaye da birnin daga Millo da baya zuwa kewayan bangon. Yowab ya gina sauran birnin.9Dauda ya zama babba ya ƙasaita saboda Yahweh mai runduna yana tare da shi.10Wɗannan su ne shugabanni ƙarƙashin Dauda, waɗanda su ka taimaki mulkin Dauda ya zama da karfi, tare da dukkan Isra'ila, suka sa shi ya zama sarki, da biyayya da maganar Yahweh game da Isra'ila.11Waɗannan su ne jerin ƙwararrun sojojin Dauda: Yashobeyam, ɗan Bahakmonite, shi ne hafsan ofisoshi. Ya kashe mutum ɗari uku da mashin sa a lokaci ɗaya.12Bayan sa sai Eliyeza ɗan Dodo, Ba'ahohite, ɗaya daga cikin jarumawan nan uku.13Yana tare da Dauda a Fas Dammim, a wurin Filistiyawa suka taru domin yaƙi, inda akwai yankin ƙasa mutane kuma suka gudu daga gaban Filistiyawa.14Suka tsaya a tsakiyar filin. Suka kãre shi suka kuma kashe Filistiyawa da yawa Yahweh kuma ya cece su da babbar nasara.15Daga nan mutum uku cikin talatin suka tafi wurin Dauda cikin dutse, a kogon Adullam. Mutanen Filistiyawa suka yi sansani a cikin Kwarin Refayim.16A lokacin nan Dauda yana cikin kagara, a kogo, yayin da Filistiyawa suka kafa sansanin su a Betlehem.17Dauda ya ji ƙishin ruwa sai ya ce, "Da ma wani zaya bani ruwa in sha daga rijiyar da ke a Betlehem, rijiyar dake a bakin ƙofa!"18Sai jarumawan nan uku suka kụtsa cikin rundunar Filistiyawa suka ɗebo ruwa daga cikin rijiyar Betlehem, rijiyar da ke bakin ƙofa. Suka ɗauko ruwan suka kawo wa Dauda, amma yaƙi shan sa. Maimakon haka, ya tsiyaye shi ga Yahweh.19Sai ya ce, "Yahweh, ya nisantarda wannan daga gare ni, da zan sha wannan ruwan. Zan sha jinin mutane waɗanda su ka sadaukar da rayukansu?" Saboda sun sa ran su cikin haɗari, Dauda ya ƙi shan ruwan. Wannan shi ne abin da jarumawan nan uku suka yi.20Abishai ɗan'uwan Yowab, shugabane na jarumawan uku. Ya taɓa amfani da mãshin sa ya kashe mutum ɗari uku. An faɗe shi cikin su ukun nan.21A cikin ukun ɗin ya sami girmamawa riɓi biyu har ya zama shugabansu. Ko da shike baya ɗaya daga cikin su.22Benaiya ɗan Yeho'iada ya zama da ƙarfi daga Kabzeel wanda ya yi manyan abubuwa. Ya kashe 'ya'ya biyu na Ariyel mutumin Mowab. Ya kuma sauka cikin rami ya kashe zaki lokacin sanyin dusar ƙanƙara.23Har ya kashe Bamasare, tsawon mutumin ya kai kamu biyar. Bamasaren yana da babban mãshi misalin itacen sãƙa amma ya je wurin sa da sanda kawai. Ya fizge mãshin daga hanun Bamasaren ya kashe shi da mãshinsa.24Benaiya ɗan Yeho'iada ya yi waɗannan ayyuka, an sanya sunansa tare da jarumawan uku.25An mutunta shi fiye da sojojin nan talatin gaba ɗaya, amma ba kamar ƙwararrun sojojin nan uku ba. Duk da haka Dauda ya sanya shi shugaba akan matsaransa.26Jarumawan mutanen su ne: Asahel ɗan'uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo na Betlehem,27Shammot Baharore, Helek Bafelone,28Ira ɗan Ikkesh Batekoye, Abiyeza Ba'anatote,29Sibbekai Bahushate, Ilai Ba'ahohite.30Maharai Banetofate, Heled ɗan Baanah Banetofate,31Ittai ɗan Ribai na Gibiya na zuriyar Benyamin, Benaiya Bafiratone,32Hurai na kwarurrukan Ga'ash, Abiyel Ba'arbate,33Azmabet Baharume, Eliyaba Basha'albone,34'ya'yan Hashem Bagizoniye, Yonatan ɗan Shagi Baharare,35Ahiyam ɗan Sakar Baharare, Elifal ɗan Ur,36Hefar Bamekarate, Ahija Bafelone,37Hezro Bakarmele, Na'arai ɗan Ezbai,38Yowel ɗan'uwan Natan, Mibhar ɗan Hagri,39Zelek Ba'moniye, Naharai Baberote (mai ɗaukar wa Yowab makamai ɗan Zeruyiya)40Ira Ba'itriye, Gareb Ba'itriye,41Yuriya Bahitte, Zadab ɗan Ahlai,42Adina ɗan Shiza Barubeniye (shugaban Rubenawa) da mutum talatin tare dashi,43Hanan ɗan Ma'aka da Yoshafat Bamitiniye,44Uzziya Ba'ashterate, Shama da Yeyiyel 'ya'yan Hotam Ba'arowaye,45Yediyayel ɗan Shimri, Yoha (ɗan'uwansa Batize),46Eliyel Bamahabe, Yeribai da Yoshabiya 'ya'yan Elna'am, Itma Bamowabe,47Eliyel, Obed, da Ya'asiel Bamezobate.
AT: "mu 'yan'uwanka ne" ko "kakaninmu ɗaya da kai"
"maganar Yahweh"
Duba:
AT: " Amma sojojin Dauda sun ci yaƙi"
AT: "kuma sun kira shi birnin Dauda"
AT: "sai Dauda ya maida Yowab shugaban yaƙi"
AT: "Isra'ila sun ƙara wa ganuwa da ke kewaye da birnin ƙarfi"
Wannan na nufin ganuwa a Yerusalem wanda ake zaton Yebusawa ne suka gina.
Duba: da
AT: "shugabanni da ke a ƙarƙashin Dauda, "
AT: "waɗanda su ka taimaki mulkin Dauda ya zama da ƙarfi"
AT: "a lokaci ɗaya"
"da kashe Filistiyawa da yawa." -
Duba:
"3 cikin 30"
"Filistiyawa sun tsayad da sojoji a Baitalami"
"jarumawan nan 3"
Wannan jumlolin na magane ne akan rijiya daya. Ɗayan ya bayyana inda rijiyar yake a Baitalami.
AT: "Allah, kada ka bar ni in sha wannan irin hadaya saboda sojoji na!"
Duba:
"manyan mayaƙan nan uku"
AT: Abishai shugabane na a cikin su manyan mayaƙan nan uku"
Duba:
AT: "Benaiya ya sadu da Bamasaren"
AT: "mãshi mai girma sosai"
Duba:
"sananne ne shi kamar manyan jarumawan 3"
AT: "An mutunta shi fiye da sojojin nan talatin gaba ɗaya, amma ba kamar ƙwararrun sojojin nan uku ba"
Duba:
Duba:
Duba:
Duba:
Duba:
"mutum talatin tare dashi"
Duba:
1Waɗannan su ne waɗanda suka zo wurin Dauda a Ziklag, tun lokacin da bai iya tsayawa gaban Saul ɗan Kish ba. Suna cikin sojoji, mataimakan sa a cikin yaƙi.2Maharban baka ne kuma sukan harba ta dama da hagu sukan jefa dutse da majaujawa wajen harbin kibiya da baka. Su mutanen Benyamin ne, mutanen kabilar Saul.3Sarki shi ne Ahiyaza, sai Yowash, dukkan su 'ya'yan Shema'ah Bagibeyate. Akwai Yeziyel da Felet, 'ya'yan Azmebet. Akwai kuma Berakah, Yehu Ba'anatote,4Ishmaiya Bagibiyone, sojane cikin talatin ɗin (Kuma shugaban talatin ɗin); Irmiya, Yahaziyel, Yonanan, Yozabad Bagaderate.5Eluzai, Yerimot, Beyaliye, Shemariya, Shefatiya Baharufiye,6Koratawa, Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezar, Yashobeyam, da7Yowela da Zebadiya, 'ya'yan Yeroham na Gedor.8Waɗansu Gadawa su ka haɗu da Dauda a kagara cikin jeji. Su jarumawa ne, Horarru domin yaƙi, waɗanda sun iya garkuwa da mashi; fuskokinsu kamar na zakuna. Sauri gare su kamar bareyi a kan duwatsu.9Akwai Ezer shugaba, Obadiya na biyu, Eliyab na uku,10Mishmanna na huɗu, Irmiya na biyar,11Attai na shida, Eliyel na bakwai,12Yonatan na takwas, Elzabad na tara,13Irmiya na goma, Makbannai na sha ɗaya.14Waɗannan 'ya'yan Gad shugabannin runduna ne. ƙaraminsu shi ke jagorancin ɗari, babbansu shi ke jagorancin dubbai.15Sun ƙetare Yodan cikin wata na fari, sa'ad da ya yi ambaliya ya kori dukkan waɗanda suke zama cikin kwarurruka, dukka da na wajen gabas da na wajen yamma.16Waɗansu mutanen Benyamin da na Yahuda suka zo kagara wurin Dauda.17Dauda ya fita domin ya tarye su ya yi masu jawabi yace: "Idan kun zo wurina da salama ku taimakeni, za ku iya haɗa hannu da ni. Amma idan kun zo ne domin ku bashe ni ga abokan gãba ta, bari Allah na kakanninku ya gani ya tsauta maku, gama ban yi wani abin da ba dai-dai ba."18Sa'an nan sai Ruhu ya sauko kan Amasai, wanda ya ke shugaban talatin ɗin. Amasai ya ce, "Mu na ka ne, ya Dauda. Wajen ka mu ke, ya ɗan Yesse. Salama, bari salama ta kasance ga duk wanda ya taimakeka. Bari salama ta kasance ga masu taimakonka, gama Allahnka ya na taimakonka." Daga nan Dauda ya karɓe su ya sa su zama shugabanni akan jama'arsa.19Waɗansu daga Manasse ku ma suka koma wajen Dauda sa'ad da ya zo tare da Filistiyawa domin ya yi yaƙi da Saul. Duk da haka ba su taimaki Filistiyawa ba, saboda shugabannin Filistiyawa sun tuntuɓi junansu sa'an nan suka sallame shi. Suka ce, "Zai koma wajen ubangidansa Saul zai jawo haɗari ga rayukanmu."20Da ya je Ziklag, mutanen Manasse da su ka haɗa hannu da su su ne Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika'el, Yozabad, Elihu, da Zilletai, shugabanni na dubbai na Manasse.21Sun taimaki Dauda yaƙi da taron mahara, gama su jarumawa ne. Daga baya su ka zama shugabanni cikin runduna.22Yau da gobe, mutane suka yi ta zuwa wurin Dauda domin su taimake shi, har aka sami babbar rundunar soja, kamar rundunar sojojin Allah.23Wannan shi ne lissafin sojoji masu makamai domin yaƙi, waɗanda suka zo wurin Dauda a Hebron, domin su juyar da mulkin Saul zuwa gare shi, domin tabbatar da maganar Yahweh.24Daga Yahuda waɗanda suke ɗauke da garkuwa da mãshi sun kai 6,800, a shirye domin yaƙi.25Daga zuriyar Simiyon sun kai jarumawa 7,10026Daga zuriyar Lebiyawa sun kai mayaƙa 4,600.27Yehoyada shi ne shugaban zuriyar 'ya'yan Haruna tare da shi akwai mutum 3,700.28Tare da Zadok saurayi, ƙaƙƙarfa, mutum mai ƙarfin hali, sun kai shugabanni ashirin da biyu daga iyalin mahaifinsa.29Daga Benyamin, kabilar Saul, sun kai dubu uku. Yawancinsu suka zama da biyayya ga Saul har zuwa lokacin nan.30Daga Ifraim sun kai mayaƙa 20,800, suna cikin gidajen mahaifansu.31Daga rabin kabilar Manasse akwai mutane dubu goma sha takwas waɗanda suka zo domin su naɗa Dauda sarki.32Daga Issaka, akwai shugabanni ɗari biyu masu gane zamanai sun san abin da ya kamata Isra'ila su yi. Dukkan 'yan'uwansu suna ƙarƙashin mulkinsu.33Daga Zebulun akwai mayaƙa dubu hamsin, shiryayyu domin yaƙi, da dukkan makaman yaƙi, a shirye suke suyi biyayya da zuciya ɗaya.34Daga Naftali akwai shugabanni dubu, tare da su kuma mutum dubu talatin da bakwai tare da garkuwa da mãsu.35Daga Danawa akwai mutane 28,600 shiryayyu domin yaƙi.36Daga Asha akwai mutane dubu arba'in shiryayyu domin yaƙi.37Daga ɗaya ƙetaren Yodan, daga Rubenawa, Gadawa, da rabin kabilar Manasse, akwai mutane 120,000 shirye domin kowanne irin yaƙi.38Dukkan waɗannan sojojin, shiryayyu ne domin yaƙi, sun zo Hebron da tsayayyar manufa wato su naɗa Dauda sarki bisa Isra'ila.39Dukkan sauran Isra'ila kuma sun amince ya zama sarki. Suna can tare da Dauda kwana uku, suna ci da sha, gama 'yan'uwansu sun aike su da guzuri.40Har yanzu kuma, waɗanda ke kusa da su, kamar su Issaka da Zebulun da Naftali, sun kawo abinci akan jakuna da raƙuma, alfadarai, da shanu, guzurin gari, kauɗar 'ya'yan ɓaure, ruwan inabi, mai, shanu, da tumaki, gama Isra'ila tana murna.
Duba:
AT: "A lokacin da bai iya tsayawa ba a gaban"
AT: "Kayan yaƙinsu sun ƙunshi baka, kuma sun iya harbi da hannun dama da na hagu"
Duba:
"sojoji talatin 30"
Duba:
Duba:
AT: "Suna da sauri sosai"
Waɗannan ƙananan dabbobi ne masu falala da sauri, mai kama da barewa.
Duba:
An lissaffa waɗannan mazajen bisa ga sugabancinsu. "2nd ... 11th ...
Wannan na nufin cewa ƙaraminsu shi ne ya jagorancin sojoji 100.
Wannan na nufin cewa mafi girman ƙungiyar da shugaban ya jagoranta shi ne 1,000.
AT: "mutanen daga ƙabilar Benyamin da na Yahuda"
Duba:
AT: "Ruhun ya bashi iko"
Jumlolin biyu na nufin abu ɗaya wanda ya nuna miƙa kai su bi Dauda.
Duba:
"fiye da mazaje 1,000"
AT: "Kungiyar Jama'a da fashi a ko ina a cikin kasar"
AT: "Kowanne rana"
Kwatanta yawan sojojin Dauda da rundunar sojojin Allah na mala'iku.
Duba:
AT: "a ba da mulkin Saul zuwa ga Dauda"
"maida maganar Yahweh" ko "cika maganar Yahweh"
Duba: da
Duba: and See:
Duba yadda ka fassara wannan a cikin 1 Tarihi 5:18.
Duba:
Duba:
AT: " riƙe dukkan irin makamai
AT: "shirye shirye"
"kwana 3"
1Dauda ya tuntuɓi shugabanni na mutum dubbai da na ɗaruruwa, tare ta kowanne shugaba.2Dauda ya ce da dukkan taron Isra'ila, "Idan kun ga ya yi maku kyau, idan kuma wannan ya zo ne daga wurin Yahweh Allahnmu, bari mu aika da 'yan saƙo ko'ina ga 'yan'uwanmu, waɗanda suka rage cikin dukkan lardunan Isra'ila, ga Firistoci da Lebiyawa waɗanda suke cikin garuruwansu. Bari a sanar da su cewa su haɗa kai da mu.3Bari mu kawo akwatin Allahnmu gare mu, gama ba mu nemi nufinsa a cikin kwanakin mulkin Saul ba."4Dukkan taron jama'a suka yarda da waɗannan abubuwa, saboda ya yi dai-dai a idanun dukkan mutane.5Dauda fa ya tara dukkan Isra'ila tare, daga Shihor Kogi a cikin Masar zuwa Lebo Hamat, domin kawo akwatin Allah daga Kiriyat Yeyarim.6Dauda da dukkan Isra'ila suka hau zuwa Baalah, wato Kiriyat Yeyarim, wanda ke na Yahuda, domin daga can za a ɗauko akwatin Allah, wanda ake kira da sunan Yahweh, wanda ya ke zaune yana mulki akan Kerubim7Sai suka sanya akwatin Allah akan sabon keken shanu. Sun fito da shi daga gidan Abinadab. Uzza da Ahiyo suna kula da keken shanun.8Dauda da dukkan Isra'ila suna murna a gaban Allah da dukkan ƙarfinsu. Suna waƙa da garayu da molaye, kugenni, da kakaki9Sa'ad da suka zo masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa domin ya riƙe akwatin, saboda shanun sun yi tuntuɓe.10Daga nan fushin Yahweh ya yi ƙuna akan Uzza, Yahweh ya kashe shi domin Uzza ya miƙa hannunsa ya taɓa akwatin. Ya mutu a wurin a gaban Allah.11Dauda ya yi fushi saboda Yahweh ya abkawa Uzza. Ana kiran wannan wurin Ferez Uzza har wa yau.12Dauda ya ji tsoron Allah a wannan rana. Ya ce, "Ya ya zan kawo akwatin Allah in dawo da shi gidana?"13Dauda bai gusar da akwatin zuwa birnin Dauda ba, amma ya sa shi a gefe cikin gidan Obed Idom Bagittiye.14Akwatin Allah ya kasance cikin gidan Obed Idom har wata uku. Yahweh ya albarkaci gidansa da dukkan abin da ya mallaka.
Sojojin suna da shugabanai wanda ke jagoran rundanar sojoji daban daban. AT: "fiye da mutane 1,000 da na 100"
A nan "Ido" kwatanci ne na tunani da ra'ayin mutane. AT: "dukan mutanen sun yi tunani da cewa waɗannan abubuwan ne suka dace a yi"
Duba:
Wannan wani suna ne na Kiriyat Yeyirim.
Duba:
Wannan wani keke ne da dabbobi da ba a taɓa amfani da su ba ke ja.
Duba:
AT: "Yahweh ya yi fushi mai ƙuna a kan Uzza"
"a gaban Allah"
Duba yadda aka fassara wannan a 1 Chron. 4:42
Duba:
AT: "wata 3"
1Daga nan Hiram sarkin Taya ya aika da 'yan saƙo wurin Dauda, da itatuwan Sida, kafintoci da magina. Su ka gina masa gida.2Dauda kuwa ya sa ni Yahweh ya tabbatar da shi zama sarki akan Isra'ila, kuma mulkinsa zai ɗaukaka sama domin taimakon mutanensa Isra'ila.3A cikin Yerusalem, Dauda ya auri waɗansu mata, ya zama mahaifin waɗansu 'ya'ya maza da 'ya'ya mata.4Waɗannan su ne 'ya'yan da aka haifa masa cikin Yerusalem: Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,5Ibha, Elishuwa, Elfelet,6Noga, Nefeg, Yafiya,7Elishama, Biliyada, da Elifelet.8Sa'ad da Filistiyawa su ka ji cewa an keɓe Dauda ya zama sarki bisa Isra'ila, dukka suka fita suna neman sa. Amma Dauda ya ji labarin sai ya fita ya yi yaƙi da su.9Filistiyawa sun rigaya sun kawo hari cikin kwarin Refayim.10Daga nan Dauda ya nemi taimako a wurin Allah. Ya ce, "Ko zan iya kai wa Filistiyawa hari? Za ka bani nasara akan su?" Yahweh ya ce masa, "Kai masu hari, gama lallai zan ba she su gare ka."11Sai suka zo Ba'al Ferazim, a can ya yi nasara da su. Ya yaba ya ce, "Yahweh ya fasa abokan gãbata ta hannuna, kamar fasuwar ambaliyar ruwa." Sunan wannan wurin ya zama Ba'al Ferazim.12Filistiyawa suka bar allolinsu a wurin, Dauda kuma ya umarta a ƙone su.13Filistiyawa suka sake kai hari a cikin kwari.14Dauda ya sake neman taimako a wurin Allah. Allah ya ce masa, ba za ka kai hari ta gabansu ba, amma ka kewaye su ta itatuwan balsam sai ka kai masu hari ta baya."15Sa'ad da ka ji motsin tafiya cikin iska ta itatuwan balsam, daga nan sai ka kai hari da ƙarfi. Ka yi haka gama Allah ya rigaya ya tafi a gabanka domin ya bugi rundunar Filistiyawa."16Dauda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi. Ya ci nasara da rundunar Filistiyawa tun daga Gibiyon har zuwa Gezar.17Daga nan sunan Dauda ya bazu zuwa ko'ina cikin dukkan ƙasashe, Yahweh kuma ya sa dukkan ƙasashe su ji tsoron sa.
Waɗannan mutane ne da aikinsu shi ne ƙirar abubuwa da katako.
AT: "Yahweh ya ɗaukaka mulkin Dauda domin ya taimaka wa mutanensa Isra'ila"
Duba:
AT: "mutanen Isra'ila sun keɓe Dauda ya zama sarki"
Wannan sunan wani wuri ne.
AT: "bani nasara a kan su"
Wannan sunan wani wuri ne.
Wannan na nufin kayayyakin Dauda. AT: "amfani da sojojin na"
AT: "a ƙone allolinsu na karya"
"Kwarin Refayim"
AT: "hari ta gabansu"
AT: "je ta cikin itatuwan balsam kuma ka kai masu hari ta baya"
Wannan wani irin itace ne.
Allah ya ci gaba da amsa tamboyoyin Dauda.
AT: "ya rigaya ya tafi a gabanka domin yayi yaƙi dominka"
Wannan sunan wani gari ne.
AT: "Mutane daga nesa sun ji game da nasarar Dauda a kan Filistiyawa.
1Dauda ya gina wa kansa gidaje a cikin birnin Dauda. Ya shirya rumfa saboda akwatinin Yahweh inda a ka ajiye shi.2Sa'an nan Dauda yace, "Lebiyawa ne kaɗai za su ɗauki akwatin Yahweh, domin su aka zaɓa su ɗauki akwatin Yahweh, su yi masa hidima har abada."3Sa'an nan Dauda ya tattara dukkan Isra'ila a Yerusalem domin a kawo akwatin Yahweh wurin da ya shirya masa.4Dauda ya tattara zuriyar Haruna da Lebiyawa.5Daga zuriyar Kohat akwai shugaba wato Yuriyel, da 'yan'uwansa mutum 120.6Daga zuriyar Merari akwai shugaba wato Asayiya, da 'yan'uwansa mutum 220.7Daga zuriyar Geshon akwai shugaba wato Yowel, da 'yan'uwansa mutum 130.8Daga zuriyar Elizafan, akwai shugaba wato Shemaiya, da 'yan'uwansa mutum 200.9Daga zuriyar Hebron akwai shugaba wato Eliyel, da 'yan'uwansa mutum tamanin.10Daga zuriyar Yuziyel akwai shugaba wato Amminadab da 'yan'uwansa mutum 112.11Dauda ya kira Zadok da Abiyata firistoci da Lebiyawa wato su, Yuriyel da Asayiya da Yowel da Shemaiya da Eliyel da Amminadab.12Ya ce da su, "Ku ne shugabannin Lebiyawa. Ku tsarkake kanku, ku da 'yan'uwanku domin ku kawo akwatin Yahweh, Allah na Isra'ila a wurin da na shirya domin sa.13Ba ku ne ku ka ɗauke shi da farko ba. Shi ya sa Ubangiji Yahweh ya yi fushi da mu domin ba mu bi farillansa ba."14Sai firistoci da Lebiyawa suka tsarkake kansu domin su iya ɗauko akwatin Yahweh, Allah na Isra'ila.15Haka Lebiyawa suka ɗauko akwatin Yahweh, Allah na Isra'ila, a bisa kafaɗunsu da sandunan, kamar yadda Musa ya umurta - suna bin ka'idojin da aka shimfiɗa a maganar Yahweh.16Dauda ya yi magana da shugabannin Lebiyawa su sa 'yan'uwansa su zama mawaƙa, da kayan waƙoƙi, wato su garayu da molaye da kugenni, suna kaɗa su da ƙara sosai suna tada muryoyinsu suna murna.17Sai Lebiyawa suka naɗa Heman ɗan Yowel da wani cikin 'yan'uwansa, wato Asaf ɗan Berekiya. Daga cikin 'yan'uwansu, wato daga zuriyar Merari suka naɗa Itam ɗan Kushaiya.18Tare da su akwai 'yan'uwansu aji na biyu: wato su Zekariya da Ya'aziyel da Shemiramot da Yehiyel da Unni da Eliyab da Benaiya da Ma'aseiya da Mattitiya da Elifelehu da Miknaiya da Obed Idom da Yehiyel masu tsaron ƙofa.19Mawaƙan suka zaɓi Heman da Asaf da Itam su zama masu kaɗa kugenni masu ƙara na tagulla.20Zekariya da Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma'sseiya da Benaiya su ne masu kiɗan girayu, da aka shirya wa Alamot.21Mattitiya da Elifelehu da Mikneiya, Obed Idom, Yeyiyel da Azaziya suka bi da hanya tare da kiɗin girayu da aka shirya wa Sheminit.22Kenaniya, shugaban Lebiyawa shi ne kuma shugaban mawaƙa saboda shimai koyar da waƙa ne.23Berekiya da Elkana su ne masu tsaron akwati.24Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zekariya, Benaiya da Eliyeza, firistoci, su ne masu busa ƙaho a gaban akwatin Yahweh. Obed Idom da Yehiyel kuma su ne masu tsaron akwatin Yahweh.25Sai Dauda da dattawan Isra'ila da shugabannin dubbai suka tafi don su ɗauko akwatin alƙawarin Yahweh daga gidan Obed Idom da murna.26Sa'an nan, Yahweh ya taimaki Lebiyawan da suka ɗauko akwatin alƙawarin Yahweh, suka miƙa hadaya ta bijimai bakwai da raguna bakwai.27Dauda ya sa riga ta linin, haka kuma Lebiyawan da suka ɗauki akwatin da mawaƙa da Kenaniya shugaban mawaƙan. Dauda kuma yana saye da falmara ta linin.28Haka dukkan Isra'ila suka kawo akwatin alƙawarin Yahweh da shewa ta farinciki, da ƙarar ƙahonni da kugenni da girayu da molaye.29Amma sa'ad da akwatin alƙawarin Yahweh ya shigo birnin Dauda, Mika'el ɗiyar Saul ta leƙa ta taga. Sai ta ga sarki Dauda yana rawa yana jin daɗi. Sai ta rena shi a cikin zuciyarta.
AT: "Mutane sun gina wa Dauda gidaje"
AT: "bada doka a shirya wuri mai daraja"
AT: " Dauda ya bada doka ga dukkan mutanen Isra'ila su taru wuri ɗaya.
Duba: da
mutane da suke a iyali ɗaya ko yare
Duba: da
Duba:
AT: "Na dokace Lebiyawa su shirya"
"Ba ku ɗauke akwatin ba kafin"
AT: "ba mu tambaye shi ba don umurni"
AT: "horar da mu"
Duba:
AT: "raira waƙa"
AT: "iko na ƙasa" ko "na biyu"
mutane masu tsaron ƙofa
Duba:
Duba yadda ka fassara wannan a 13:7.
"bi da sauran mawaƙan" ko "bi da waƙoƙi"
Duba:
AT: "fiye da mutane 1,000"
Wannan sunan mutum ne.
AT: "Dauda, Lebiyawan, da mawaƙan, duka sun sa linin mai kyau"
Wanan wanin yaddin riga ne mai haske da kuma ƙarfi.
Wannan sunan mutun ne.
AT: "Dukkan taron Isra'ila suka kawo akwatin Yahweh daga gidan Obed Idom zuwa Yerusalem"
AT: "kamar yadda mutanen suka kawo akwatin alƙawarin na Yahweh zuwa ɓirnin Dauda"
Wannan sunnan matar Dauda ne.
AT: "ta rena shi sosai a cikin tunanin ta"
1Su kawo akwatin Yahweh suka sa shi a tsakiyar rumfar da Dauda ya kafa domin sa. Sa'an nan suka yi baye-baye na ƙonawa da baye-baye na zumunta a gaban Yahweh.2Sa'ad da Dauda ya gama yin hadayu na ƙonawa da baye - baye na zumunta, ya sa wa mutanen albarka a cikin sunan Yahweh.3Ya ba kowanne mutum namiji da mace dunƙulen gurasa da yankan nama da curin kauɗar inabi.4Dauda ya sa waɗansu cikin Lebiyawa su yi hidima a gaban akwatin Yahweh, su yi farinciki da godiya su yi yabo ga Yahweh, Allah na Isra'ila.5Waɗannan Lebiyawa su ne Asaf, shi ne shugabansu da Zekariya, Yaaziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benaiya, Obed Idom da Yeyiyel. Waɗanna su ne za su kiɗa girayu da molaye. Asaf shi ne zai kiɗa kugenni da ƙara sosai.6Benaiya da Yahaziyel firistoci su ne za su yi ta busa ƙahonni, a gaban akwatin alƙawari na Allah.7A wannan rana Dauda ya fara sa Asaf da 'yan'uwansa su rera wannan waƙa ta godiya ga Yahweh.8Ku yi godiya ga Yahweh, ku kira bisa sunansa, ku sanar da ayyukansa a cikin al'ummai.9Ku rera gare shi, ku rera yabbai gare shi, ku faɗi dukkan ayyukansa na mamaki.10Ku yi fahariya cikin sunansa mai tsarki; bari zuciyar waɗanda suke neman Yahweh ta yi murna.11Ku nemi Yahweh da ƙarfinsa; ku nemi kasancewarsa a kullun.12Ku tuna aiyukan ban mamakin da ya yi, da al'ajibansa da dokokin bakinsa,13ku zuriyar Isra'ila bayinsa da ku mutanen Yakubu, zaɓaɓɓunsa.14Shi ne Yahweh, Allahnmu, dokokinsa suna cikin dukkan duniya.15Ku tsare alƙawarinsa a zukatanku har abada da maganar da ya umurta ga dubun tsararraki.16Yakan tuna alƙawarin da ya yi da Ibrahim da wa'adin da ya yi wa Ishaku.17Wannan shi ne ya tabbatar wa Yakubu ya zama ka'ida, ga Isra'ila kuma alƙawari na har abada.18Ya ce, "Zan ba ku ƙasar Kan'ana a matsayin rabonku na gădo."19Lokacin da ba su da yawa, 'yan ƙalilan, kuma baƙi a cikin ƙasar.20Suka yi yawo daga wannan al'umma zuwa waccan, daga wannan mulki zuwa wani.21Bai yarda wani ya tsanance su ba; ya ma hori sarakuna saboda su.22Ya ce, "Kada ku taɓa shafaffuna, kada ku cuci annabawana."23Ku rera ga Yahweh, ku duniya dukka, ku yi shelar cetonsa kowacce rana.24Ku shaida ɗaukakarsa a cikin al'ummai, ayyukansa na mamaki a cikin dukkan al'immai.25Gama Yahweh mai girma ne, a yabe shi ƙwarai, a ji tsoron sa fiye da dukkan alloli.26Gama dukkan alloli na al'ummai gumaka ne, Amma Yahweh, shi ne ya hallicci sammai.27Daraja da martaba na tare da shi. Iko da farinciki na wurinsa.28Ku bayar ga Yahweh, ku kabilun duniya, ku bayar da daraja da iko ga Yahweh!29Ku ba Yahweh darajar da ta dace da sunansa. Ku kawo masa baiko ku zo gabansa. Ku durƙusa ga Yahweh a cikin martabarsa mai tsarki.30Ku yi rawar jiki a gabansa ku duniya dukka. Duniya ta kahu, ba za ta iya girgiza ba.31Bari sammai su yi murna, bari duniya ta yi farinciki, a cikin al'ummai bari su ce, "Yahweh ne ya ke mulki."32Bari teku ya yi ruri, abin da ya ke cika shi kuma ya yi sowa ta farin ciki. Bari filaye su yi farinciki tare da dukkan abin da ke cikin su.33Bari itatuwan da ke cikin jeji su yi sowa ta farinciki a gaban Yahweh, gama yana zuwa domin ya hukunta duniya.34A yi godiya ga Yahweh, gama nagari ne shi, alƙawarinsa na jinƙai ya tabbata har abada.35Sai ku ce, "Ka cece mu, ya Allah na cetonmu. Ka tattara mu, ka kuɓutar da mu daga sauran al'ummai, domin mu ba da godiya ga sunanka mai tsarki da ɗaukaka cikin yabonka."36A yi yabo ga Yahweh, Allah na Isra'ila har abada abadin. Dukkan mutane suka ce, "Amin" yabo ga Yahweh.37Sai Dauda ya bar Asaf da 'yan'uwansa a gaban akwatin alƙawari na Yahweh, su yi ta yin hidima a gaban akwatin, dai-dai da buƙatar kowacce rana.38Obed Idom haɗe da 'yan'uwan nan sittin da takwas. Obed Idom ɗan Yedutun tare da Hosah su ne masu tsaron ƙofa.39Zadok da abokan aikinsa firistoci kuma suka yi hidima a rumfar Yahweh a can tudun Gibiyon.40Su riƙa miƙa baye-baye na ƙonawa a kan bagadi babu fasawa safe da yamma, bisa ga abin da ke rubuce a cikin shari'ar Yahweh, wadda ya ba Isra'ila umarni.41Heman da Yedutun su na tare da su da kuma waɗanda a ka kira sunayensu a ka zaɓe su, su ba da godiya ga Yahweh saboda alƙawarinsa da amincinsa sun tabbata har abada.42Heman da Yedutun su ne za su lura da waɗanda za su busa ƙahonni da kugenni da sauran kayan kiɗin da a ke amfani da su lokacin da a ke rera waƙoƙi na saduda. 'ya'yan Yedutun su na tsaron ƙofa.43Daga nan dukkan jama'a su ka koma gidajensu, Dauda kuma ya koma gida domin ya sa wa mutanensa albarka.
wani ɓangare, na dunƙulen gurasa
Wannan busassun 'ya'yan itace ne, ƙaramin 'ya'yan itace da ke girma a itacen inabi.
Duba:
Duba yadda ka fassara wannan a 13:7.
Wannan yana nufin ranar da aka maida akwatin alƙawari daga gidan Obed Idom zuwa Yerusalem.
AT: "waƙa ta godiya ga Yahweh"
kuyi addu'a wa Yahweh"
AT: "a cikin wanda Allah ya ke"
AT : "bari waɗanda suke so su san Yahweh da kyau"
AT: "Ku tuna abubuwan ban mamaki"
AT: "da yayi magana "
Waɗannan jumloli na nufin anu daya kuma ana anfani da shi maimaici.
AT: "dokokinsa domin dukkan mutanen duniya ne.
AT: "Tuna da alkwarin Yahweh"
"tsararraki 1000"
AT: "Yahweh ya kan tuna"
"a matsayin rabonku"
"Yahweh ya faɗi wannan a lokacin da Isra'ila suna ƙaramin ƙungiyar mutane"
"baƙi a cikin ƙasar"
Wannan jumloli biyu na nufin abu ɗaya, ya nuna yadda Isra'ila suka yi yawo.
Duba:
Kowanne abu a duniya na ba Allah ɗaukaka"
AT: "kowacce rana"
AT: "Daraja da martaba dukka na tare da shi."
AT: "Yahweh ya nuna Iko da farin ciki a fili."
"Ku yabi Yahweh don"
"ya dace ko ya isa ya karbi"
AT: "Nuna ban girma yayin da kuka yi tunanin sa"
AT: "Bari kowa a ko ina su yi farinciki.
AT: "Teku zai yi babban ƙara"
AT: "halittun cikin teku"
An yi maganan itatuwa a nan kamar mutun wanda zai yi sowa ta farinciki.
AT: "har abada"
AT: "Mutanen" ko "kowanne mutun da ke wurin "
Duba:
AT: "kamar yadda ake buƙatar kowacce rana bisa ga shari'ar Musa"
AT: "yi hidima kusa da rumfar Yahweh"
Duba:
"Firistoci"
Duba:
suba yadda ka fassara wannan a 13:7.
1Ya zama bayan da sarki ya kimtsa a gidansa, sai ya ce da annanbi Natan, "Duba ni ina zaune a cikin gidan sida, amma akwatin alƙawarin Yahweh yana zaune a rumfa."2Natan yace da Dauda, "Ka yi abin da ya ke a zuciyarka, gama Yahweh yana tara da kai."3Amma a wannan daren maganar Yahweh ta zo wurin Natan, cewa,4"Je ka, ka gaya wa Dauda bawana, 'ga abin da Yahweh ya ce: 'Kai ba za ka gina mani gidan da zan zauna ba.5Gama ba a gida ni ke zama ba tun daga ran da na kawo Isra'ila har zuwa yau. Sai dai a rumfa na ke zama da rumfar sujada a wurare dabam-daban.6A cikin dukkan wuraren da na zaga cikin Isra'ila, na taɓa yi wa wani cikin shugabannin da na sa, cewa, "Me ya sa ba ka gina mani gida na sida ba?""'7To yanzu, ka gaya wa bawana Dauda, 'Ga abin da Yahweh mai Runduna ya ce: Na ɗauko ka daga wurin kiwo, daga bin tumaki, domin ka yi mulkin jama'ata Isra'ila.8Ina tare da kai dukkan inda ka tafi, na kuma datse dukkan maƙiyanka daga gabanka, kuma zan sa ka yi suna, kamar sunan waɗanda suke manya a duniya.9Zan zaɓi wuri domin jama'ata Isra'ila, domin su zauna a wuri na kansu, don kada su ƙara samun tashin hankali. Mutane masu mugunta ba za su ƙara musguna masu yadda suka yi a dã ba,10kamar yadda su ka yi sa'ad da na umurci alƙalai su shugabanci jama'ata Isra'ila. Zan ladabtar da dukkan maƙiyanka. Har yanzu, ina gaya ma ka, Ni Yahweh, zan gina maka gida.11Za ya zama idan kwankinka suka cika da za ka tafi wurin ubanninka, zan tada zuriyarka a bayanka, wani daga cikin zuyarka, zan kafa masarautarsa.12Shi zai gina mani gida, kuma zan kafa kursiyinsa har abada.13Zan zama uba a gare shi, shi kuma zai zama ɗana. Ba zan ɗauke alƙawarin amincina daga gare shi ba kamar yadda na ɗauke daga wurin Saul, wanda ya yi mulki kafin ka.14Zan ɗora shi bisa gidana cikin masarautata har abada, kursiyinsa kuma zai tabbata har abada.'"15Natan ya yi magana da Dauda, ya baiyana masu dukkan waɗannan maganganu, ya kuma gaya masa game da wahayin gabaɗaya.16Sai Dauda ya shiga ciki ya zauna a gaban Yahweh; ya ce, "Wanene ni, Ubangiji Yahweh, menene kuma iyalina, da ka kawo ni a wannan matsayi?17Gama wannan ƙaramin abu ne a wurin ka Yahweh. Ka yi magana a kan iyalin bawanka game da babban lokaci mai zuwa, ka kuma nuna wa bawanka tsararraki na gaba, Allah Yahweh.18Ni Dauda, me kuma zan ce da kai? Ka ɗaukaka bawanka. Gama ka darajanta bawanka sosai.19Yahweh, saboda bawanka, kuma domin ka cika nufinka, ka yi wannan babban abu na baiyana ayyukanka masu girma.20Yahweh, ba wani kamar ka, kuma ba wani Allah ban da kai, kamar yadda mu ke ji koyaushe.21Gama ina wata al'umma kamar jama'arka Isra'ila, waɗanda ka kuɓutar daga Masar domin su zama mutanenka, su yi suna domin ka ta wurin aiyukanka masu girma da ban razana? Ka kori al'ummai daga gaban mutanenka, waɗanda ka kuɓutar daga Masar.22Ka sa Isra'ila sun zama mutanenka har abada, kuma kai, Yahweh ka zama Allahnsu.23To yanzu, Yahweh, ka bari alƙawarin da ka yi game da bawanka da iyalinsa ya tabbata har abada. Ka yi kamar yadda ka ce.24Sunanka ya tabbata har abada ya yi girma domin mutane su ce, 'Yahweh mai Runduna shi ne Allah na Isra'ila,' gidana kuma ni, Dauda ya tabbata a gabanka har abada.25Gama kai, Allahna, ka baiyanawa bawanka za ka gina gida domin sa. Shi ya sa ni bawanka, na sami ƙarfin in yi addu'a zuwa gare ka.26To yanzu, Yahweh, kai Allah ne, ka kuma yi wannan kyakkyawan alƙawari ga bawanka:27Gama ya gamshe ka, ka albarkaci gidan bawanka ya kasance a gabanka har abada. Kai Yahweh, kai ne ka albarkace shi, kuma zai zama mai albarka har abada."
zama da farin ciki da wadata, ba tare da marmarin son a yi gaba ba ko a canza.
An ɗauki katako daga sida ya zama katakon gini mafi kyau.
An bayyana Dauda da wannan gaɓan jiki da ke da alaka da emoshen. AT: "ka yi abin da ya ke a zuciyarka"
"Allah yayi ƒaɗi kalmarsa"
AT: "na kawo Isra'ila zuwa ƙasar alƙawari daga Masar"
AT: "Da ka gina mani gida na itace mai tsada
Aikin Dauda na maƙiyayi na nufin inda yake kiwon tumaki. AT: "Na ɗauko ka daga wurin kiwo"
Duba yadda ka fassara wannan kalmar a 4:39.
Allah ya ci gaba da bada saƙon da Natan zai faɗa wa Dauda.
A lokacin kwanaki na tsararaki na nufin ranaku da suka wuce. AT: "da na umurce ku" ko "daga tsara da na umurce ku"
Yahweh na nufin zai bawa Dauda jikoki su yi mulki a Isra'ila, kwatanci da zai gina mashi gida.
Rayuwa na nufin yan kwanaki. AT: "lokancin da ka mutu"
A sa wani ya zama shu ana nufin tada su su je gaba
Ikon mulki kamar sarki an bayyana shi ta wurin da sarki ya ke zama.
Ana kwatanta 'yancin sarki yayi mulki ta wurin da yake zama. AT: kuma 'yancinsa na mulki"
"ya gaya mashi"
"Dauda ya ce"
Dauda yayi waɗannan tambayoyi domin ya nuna godiya ga Allah domin ya zaɓi ya albarkace shi duk da bai dace ba.
"Dauda yayi waɗannan tambayoyi domin ya nuna godiya ga Allah. AT: "Idan zan fadi wani abu domin nuna godiya, duk da ban san abin da zan faɗa ba."
AT: "riba ta"
AT: "ka kuɓutar daga bauta a Masar"
Kalman nan "girma" da "razana" na nufin abu daya yana nanata muhinmancin girma. AT: ayyuka masu ban razana"
AT: "ya ci gaba har abada"
Kasancewa da yara da gina iyali na nufin gina gida.
AT: "kasancewa da isasshen ƙarfin hali"
Na nufin abu ɗaya, an maimaita shi a nan don nanatawa
1Bayan wannan sai Dauda ya kai wa Filistiyawa hari kuma ya yi nasara a kan su. Ya ƙwace Gat da ƙauyukanta daga ƙarƙashin mulkin Filistiyawa.2Daga nan ya yi nasara da Mowab, Mowabawa suka zama bayin Dauda suka biya haraji gare shi.3Sa'an nan Dauda ya yi nasara da Hadadezer sarkin Zoba a Hamat, sa'ad da Hadadezer ya ke tafiya domin ya kafa mulkinsa a Kogin Yuferatis.4Dauda ya ƙwace masa karusai dubu da mahaya dawaki dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu ashirin. Dauda ya yaiyanke jijiyoyin gwuiwoyin dukkan dawakan da ke jan karusai, amma ya rage waɗanda za su ja karusai ɗari.5Sa'ad da Aramiyawan Damaskus suka zo domin su taimaki Hadadezar sarkin Zoba, Dauda ya kashe mutanen Aramiyawa dubu ashirin da biyu.6Sai Dauda ya kafa zangon sojoji a Aram ta Damaskus. Aramiyawa suka zama bayinsa suka kawo masa gaisuwa. Dukkan inda Dauda ya je, Yahweh yana ba shi nasara.7Dauda ya ɗauko garkuwowin zinari waɗanda bayin Hadadezar ke ɗauke da su ya kawo su Yerusalem.8Dauda ya ɗauko tagulla da yawa daga Tibhat da Kun biranen Hadadezar. Da wannan tagullar ne Suleman ya yi "Teku" na tagulla da ginshiƙai da sauran kayan aiki na tagulla.9Sa'ad da Tou sarkin Hamat ya ji labarin Dauda ya yi nasara da dukkan sojojin Hadadeza sarkin Zoba,10Sai Tou ya aika ɗansa Hadoram ya je ya gaida sarki Dauda ya sa masa albarka, saboda Dauda ya yi yaƙi da Hadadeza kuma ya yi nasara da shi, saboda Tou ya yi yaƙi da Hadadeza. Kuma Tou ya aika Dauda abubuwa daban-daban na zinariya da azurfa da tagulla.11Sarki Dauda ya keɓe waɗannan kaya ga Yahweh tare da dukkan azurfa da zinariyar da ya samo daga dukkan al'ummai: wato Idom, Mowab, da mutanen Ammon da Filistiyawa da Amelikawa.12Abishai ɗan Zeruyiya ya kashe Idomawa dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.13Ya kafa zangon sojoji a Idom, dukkan Idomawa suka zama bayin Dauda. Yahweh ya ba Dauda nasara a dukkan inda ya je.14Dauda ya yi mulkin dukkan Isra'ila, kuma ya yi gaskiya da adalci ga dukkan mutane.15Yowab ɗan Zeruyiya shi ne shugaban sojoji, Yehoshafat ɗan Ahilud kuma shi ne marubuci.16Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyata su ne firistoci, Shabsha ne marubuci.17Benaiya ɗan Yehoiada shi ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, 'ya'yan Dauda kuma su ne manyan masu ba da shawara.
"Bayan da Allah yayi alƙawari ya albarkaci Dauda"
Wannan sunan mutum ne.
Wannan suna ƙasa ne.
"karusai 1,000"
"mahaya dawaki 7,000)
"ya kashe 22,000"
rundunonin sojoji da aka sa a wani ɓangare.
Duba yadda ka fassara sunan shi a 18:3.
Waɗannan sunayen birane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
"yaƙi tare da"
"Idomawa 18,000"
Wannan sunnan kwari ne da ke tsakanin Idom da Yahuda in da ake gamuwa domin yaƙi.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wasu juyi sun daidata wannan da cewa Ahitub da Ahimelek manyan firistoci ne.
Waɗannan sunayen mutane da ƙungiyoyi ne.
1Daga baya sai Nahash, sarkin mutanen Amon, ya mutu, ɗansa ya gaje shi.2Dauda yace, "Zan yi mutunci ga Hanum ɗan Nahash, saboda mahaifinsa ya nuna mutunci gare ni." Sai Dauda ya aika manzanni su yi masa gaisuwa game da mahaifinsa. Bayin Dauda suka shiga ƙasar Ammoniyawa suna je wurin Hanum domin su yi masa gaisuwa.3Amma sarakunan Ammoriyawa suka ce da Hanum, "Ka na tsammani Dauda girmama mahaifinka ya ke yi da ya aiko mutane su yi maka gaisuwa? Ba leƙen asiri ya kawo su domin su duba ƙasar nan da nufin su kaɓantar da ita ba?"4Sai Hanun ya kama bayin Dauda ya yi masu aski, ya yayyanke rigunansu har zuwa kwankwaso sa'an nan ya sallame su.5Sa'ad da suka yi wa Dauda bayani ya aika a ka tarbe su, saboda sun kunyata ƙwarai. Sarki yace da su, "Ku tsaya a Yeriko sai gemunanku sun fito, sa'an nan ku dawo."6Da Ammoniyawa suka ga sun maida kansu abin ƙyama ga Dauda, Hanun da Ammoniyawa suka aika da dubban awon azurfa domin su gaiyato karusan Arameyawa da mahaya dawaki daga Nahariyam da Ma'aka da Zoba.7Su ka gaiyato karusai dubu talatin da biyu tare da sarkin Ma'aka da mutanensa, waɗanda suka zo suka yi zango kusa da Medeba. Ammoniyawa suka tattaro daga biranensu, suka fito domin a yi yaƙi.8Da Dauda ya ji haka, sai ya aiki Yowab tare da dukkan sojojinsa su je su same su.9Mutanen Ammon su ka fito suka ja layi a ƙofar birni domin yaƙi, su kuma sarakunan da suka zo suka zauna cikin fili su kaɗai.10Lokacin da Yowab ya ga layin yaƙi na fuskantar sa gaba da baya, daga cikin mutanen Isra'ila ya zaɓi waɗansu gwanayen yaƙi ya shirya su, domin su kara da Arameyawa.11Sauran sojojin kuma ya ba da su ga Abishai ɗan'uwansa, domin ya sa su kara da sojojin Ammon.12Yowab yace, "Idan Arameyawa suka fi ƙarfi na, to kai Abishai, sai ka kuɓutar da ni. Amma idan sojojin Ammoniyawa suka fi ƙarfin ka to, ni zan zo in kuɓutar da kai.13Ka ƙarfafa, bari mu yi ƙarfin hali saboda mutanenmu kuma saboda biranen Allahnmu, gama Yahweh zai yi abin da ya gamshe shi."14Sai Yowab da sojojinsa suka nausa domin su yi yaƙi da sojojin Arameyawa, waɗanda aka tilasta wa su gudu a gaban sojojin Isra'ila.15Sa'ad da sojojin Ammon suka ga Arameyawa sun gudu, suma sai suka gudu daga wurin Abishai ɗan'uwan Yowab suka koma cikin birni. Daga nan Yowab ya koma daga wurin mutanen Ammon ya kuma koma Yerusalem.16Lokacin da Arameyawa suka ga Isra'ilawa sun yi nasara a kansu, sai suka nemi taimako daga ƙetaren Kogin Yuferatis, tare da Shofak shugaban sojojin Hadadeza.17Sa'ad da Dauda ya ji haka, sai ya tattara dukkan Isra'ila, suka haye Yodan, suka je wurin su. Ya shirya sojoji domin su yi yaƙi da Arameyawa, suka kuwa yi faɗa da shi.18Arameyawa suka gudu daga gaban Isra'ila, Dauda kuwa ya kashe sojojin karusan Arameyawa dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba'in. Ya kuma kashe Shofak shugaban sojojin.19Da dukkan sarakuna, wato bayin Hadadeza suka ga Isra'ila sun ci nasara a kan su, suka nemi salama da Dauda suka bauta masa. Sai ya zama mutanen Aram ba su ƙara marmarin su taimaka wa Amoniyawa ba.
Waɗannan sunayen mutane ne.
AT: "Zan yi alheri ... yayi alheri"
AT: "Kada ka gani cewa Dauda na girmama babankadomin ya aika mutane su yi maka ta'aziya."
"sutura"
"ya aika wasu 'yan saƙo su ƙarfafa su"
Kalmar nan abin "kyama" na nufin abu mai wari, wannan ya kwatanta Amoniyawa kamar wani abu da ake kyamarsa ko ba a buƙata.
Waɗannan sunayen birane ne.
"ya ji cewa Amoniyawa suna zuwa domin su yi yaƙi"
"yayi yaƙi da su"
Wannan sunan ɗan'uwan Yowab ne.
"kasance da ƙarfin hali"
AT: "bari mu nuna gabagadi".
AT: "sun matsa kusa zuwa yaƙi" ko "sun kusanci maƙiyan sojoji domin su yi yaƙi"
"Arameyawa sun gane"
ƙarin sojoji"
AT: "Arameyawa sun yaƙi Dauda da sojojinsa"
"kashe 7,000"
"40,000 sojojin ƙasa"
1Da lokaci ya yi sa'ad da sarakuna su kan tafi yaƙi, sai Yowab ya jagoranci sojoji suka je suka ragargaza ƙasar Amoniyawa. Ya ja daga a Rabba. Dauda kuma na Yerusalem. Yowab ya kai wa Rabba hari, ya yi nasara a kanta.2Dauda ya ɗauke rawanin sarkinsu daga kansa, sai ya tarar ya kai nauyin awo ɗaya na zinariya, kuma da duwatsu masu daraja a cikin sa. A ka ɗora rawanin a kan Dauda, kuma ya kawo ganima mai yawa daga birnin.3Ya fito da mutanen daga cikin birni ya tilasa su yi aiki da zartuna da ƙarafa masu tsini na aiki da gatura. Dauda ya sa dukkan mutanen da ke cikin biranen Ammon su yi wannan aikin. Daga nan Dauda da dukkan sojojin suka dawo Yerusalem.4Bayan wannan sai ya zama yaƙi ya ɓarke a Gezer da Filistiyawa. Sibbekai Bahushate ya kashe Siffai, wani daga cikin kabilar Refiyam, daga nan sai a ka ladabtar da Filistiyawa.5Sai ya zama a wani yaƙi kuma da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya'ir mutumin Betlehem ya kashe Lahmi ɗan'uwan Goliya mutumin Gat, wanda makamin mãshinsa ya yi kamar turken masaƙa.6A wani yaƙin kuma a Gat, a ka sami wani mutum mai tsawo ƙwarai, wanda ya ke da yatsu shida a kowanne hannunsa da kuma yatsu shida a kowacce ƙafarsa. shi ma daga Refiyam ya ke.7Da ya yi wa sojojin Isra'ila ba'a, Yehonadab ɗan Shemiya ɗan'uwan Dauda ya kashe shi.8Waɗannan zuriyar Refiyam na Gat ne, suka kashe su da hannuwan Dauda da sojojinsa.
"ragargaza ƙasar" Wannan na nufin yanayi wadda sojoji zasu lalata ƙasar in da abokan gaba ke noman abinci.
AT: "mutanen Dauda suka ɗora rawanin a kan shi"
Ana maganar mutanen ta sunayen biranensu. AT: "Dauda ya buƙaci dukkan mutanen biranen"
Waɗannan sunayen birane ne.
Wadannan sunayen mutane ne.
ka tilastawa wani ko wani abu ta ƙarfi.
Wannan suna ne da aka bawa wasu jinsin mutane da ke da tsayi, da ƙarfi .
Waɗannan sunayen mutane ne.
Dauda da sojojinsa na nufin wannan gaɓa na jiki da suke amfani da shi domin su riƙe taƙobi. AT: "Dauda da sojojinsa suka kashe jikokin Refiyam"
1Wani magafcin Isra'ila ya taso ya iza Dauda ya ƙidaya mutanen Isra'ila.2Sai Dauda yace da Yowab da manyan sojoji, "Ku je ku ƙidaya mutanen Isra'ila tun daga Biyasheba har zuwa Dan, ku kawo mani rahoto, domin in san yawansu."3Sai Yowab ya ce, "Dama Yahweh ya sa sojojinsa su fi haka yawa sau ɗari. Amma shugabana sarki, dukkan su ba bauta maka su ke yi ba? Me ya sa shugabana ya ke so a yi haka? Yaya za a kawo laifi a Isra'ila?"4Amma maganar sarki ta rinjayi Yowab. To, sai Yowab ya fita ya zagaya dukkan Isra'ila. Daga nan ya dawo Yerusalem.5Yowab ya kawo wa Dauda rahoton yawan sojoji. A Isra'ila masu zarar takobi su ne 1,100,000. A Yahuda kaɗai akwai sojoji 470,000.6Amma ba a ƙidaya Benyamin da Lebi tare da su ba, saboda Yowab bai ji daɗin maganar da sarki ya yi ba.7Yahweh bai ji daɗin wannan aikin ba, saboda haka sai ya buga Isra'ila.8Dauda ya ce da Yahweh, "Na yi zunubi mai girma da na yi haka. Yanzu, ka ɗauke zunubin bawanka gama na yi wauta ƙwarai."9Yahweh yace da Gad, annabin Dauda,10"Je ka ka ce da Dauda, 'Ga abin da Yahweh yace, ina ba ka zaɓi guda uku, sai ka zaɓi ɗaya daga cikin su."11Sai Gad ya je wurin Dauda ya ce da shi, "Ga abin da Yahweh ya ce, 'Ka zaɓi ɗaya cikin waɗannan:12yunwa ta shekaru uku ko wata uku na ƙanƙanci a hannun abokan gãbarka ko kuwa Yahweh ya bi ka da takobinsa har kwana uku, wato annoba ta afko cikin ƙasar, mala'ikan Yahweh ya bi ko'ina cikin ƙasar Isra'ila yana ta hallaka mutane.' To yanzu, sai ka yi tunani ka ba ni amsar da zan kai wa wanda ya aiko ni."13Sai Dauda yace da Gad, "Ina cikin babbar damuwa! Gara in faɗa cikin hannun Yahweh da in faɗa cikin hannun mutum, gama jinƙansa yana da yawa ƙwarai."14Sai Yahweh ya aiko da annoba a ƙasar Isra'ila, har mutum dubu saba'in suka mutu.15Sa'an nan Yahweh ya aiko mala'ika ya hallaka Yerusalem. Yana kusa da ya hallaka ta, sai Yahweh ya canza niyyarsa. Ya ce da mala'ikan mai hallakarwa, "Ya isa! Ka mayar da hannunka."A wannan lokacin, mala'ikan Yahweh yana tsaye masussukar Ornan Bayebushe.16Dauda ya tada ido, ya ga mala'kan Yahweh yana tsaye tsakanin sama da ƙasa, da takobi a zare cikin hannunsa ya ɗaga shi a kan Yerusalem. Sai Dauda ya ce da dattawa, ku sa tufafin makoki, ku kwanta da fuskokinku a ƙasa.17Dauda ya ce da Yahweh, "Ba ni ne na ba da umarnin a ƙidaya sojoji ba? Ni ne na yi wannan aikin mugunta, amma waɗannan tumaki, me suka yi? Yahweh Allahna! Ka sa hannunka ka buga ni, ni da iyalina, amma kada ka bari annobar ta zauna a kan mutanenka."18Sai mala'ikan Yahweh ya umurci Gad ya ce da Dauda, Dauda ya je ya ginawa Yahweh bagadi a masussukar Ornan Bayebushe.19Sai Dauda ya tafi ya yi kamar yadda Gad ya dokace shi a cikin sunan Yahweh.20Lokacin da Ornan ke sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala'ikan. Sai shi da 'ya'yansa su huɗu, suka ɓoye kansu.21Lokacin da Dauda ya zo wurin Ornan, sai Ornan ya duba ya ga Dauda. Sai ya bar wurin sussukar ya faɗi da fuskarsa a ƙasa a gaban Dauda.22Sa'an nan Dauda ya ce da Onan, "Ka sayar mani da wannan masussuka domin in gina wa Yahweh bagadi. Zan biya gaba ɗaya domin a cire annobar daga cikin jama'a."23Ornan ya ce da Dauda, "Ka ɗauke ta kamar taka ce, ya shugabana sarki. Ka yi abin da ka ga dama da ita. Duba, zan ba ka bijimaina domin hadaya ta ƙonawa, sandunan fyaɗi kuma ka yi makamashi da su, alkama kuma domin hadaya ta tsaba, zan ba ka su dukka."24Sarki Dauda yace da Ornan, "A'a gara dai in saya in biya. Ba zan ɗauki kayanka in yi hadaya ta ƙonawa ga Yahweh ba, ba tare da ya shafe ni da komi ba."25Sai Dauda ya sayi wurin a bakin zinariya awo ɗari shida.26Sai Dauda ya gina wa Yahweh bagadi a wurin, ya miƙa baye-baye na ƙonawa da baye-baye na zumunta. Ya yi kira ga Yahweh, ya kuwa amsa masa da wuta daga sama a kan baye-baye na ƙonawar.27Sa'an nan Yahweh ya umurci mala'ikan, mala'ikan kuma ya mayar da takobinsa cikin kubenta.28Da Dauda ya ga Yahweh ya amsa masa a masussukar Ornan Bayebushe, sai ya yi hadayar a wurin nan take.29A wannan lokaci wurin taruwa na Yahweh wanda Musa ya yi a cikin Jeji da bagadi domin baye-baye na ƙonawa suna can kan tudun Gibiyon.30Duk da haka, Dauda ba zai iya zuwa can domin ya nemi nufin Yahweh ba, saboda yana jin tsoron takobin mala'kan Yahweh.
Kassance da girma na bayyana da kasance da iko sosai. AT: "Abokin gaban Isra'ila ya kasance da iko sosai"
Yowab ya bayyana marmarisa na sojojin su fi haka yawa sau ɗari su kuma kassance da iko.
AT: Amma shugabana sarki, dukkan su sun bauta maka ai. Bai kamata shugabana ya nemi wannan ba? Za ka kawo laifi a Isra'ila don marmarin son ikon sojoji."
Wannan na maganar umurnin sarki Dauda ya zama maganar karshe domin ba zai zake umurninshi ba bayan ya bada ita. AT: Umurnin sarki ba zai chanza ba"
An bayyana sojojin Isra'ila ta wurin zare takobinsu domin yaƙi.
AT: "Amma Yowab bai ƙidaya mutane daga ƙabilar Lewi sa Benyamin ba.
"wannan aikin" na nufin yunƙurin Dauda domin ya ƙidaya mutanen Isra'ila da zasu yi yaƙi.
an bayyana gafara kamar an ɗauke laifin. AT: "gafarta mani"
Wannan hanya ce ta sassauci da ke bayyana cewa abokin gaba ya kashe wani.
AT: "kashewa"
AT: "Gara in zo cikin sarrafawar Yahweh, da in faɗa cikin sarrafawar mutane, gama ayyukan jinƙansa na da yawa ƙwarai."
"mutum 70,000 suka mutu"
Ya canza shawararsa.
AT: "shirye suyi yaƙi"
AT: "Ni ne na ba da umarnin a ƙidaya sojoji"
AT: "basu yi komai ba da zaka hore su"
Duba yadda ka fassara sunansa a 21:13.
AT: "kamar yadda Gad, ke magana ikon Yahweh, ya gaya wa Dauda ya yi."
Waɗannan jumlolin ya bayyana cewa Ornan ya durkusa a ƙasa. Durkusawa a gaban wani alama ne na nuna bangirma da ƙasƙanci. Durkusawa sossai alama ne na kaskanci da nuna bangirma sossa.
AT: "Zan biya gaba ɗaya darajar masussuƙar ƙasar"
AT: "Ka ɗauke shi kamar kyauta ne"
Fahimtan Dauda na bayyana yadda yake gani. AT: "abin da ka ga yayi kyau"
"shekel na zinariya 600"
"Ya yi addua'a ga Yahweh domin taimako"
AT: "mala'ikan ya daina kashe mutane"
"Allah ya gaya ma shi abinda za ya yi"
AT: "yana jin tsoro cewa mala'ikan Yahweh zai kashe shi"
1Sai Dauda yace, "A nan gidan Yahweh Allah zai kasance, tare da bagadin ƙona baye-baye na Isra'ila."2Sai Dauda ya umurci bayinsa su tattaro baƙin da ke zaune a ƙasar Isra'ila. Ya sa su zama masu sassaƙo duwatsu, su sassaƙo tubulan duwatsu waɗanda za a gina gidan Yahweh da su.3Dauda kuma ya ba da ƙarafa masu tarin yawa domin a yi ƙusoshi saboda ƙofofi da ƙyamarensu da tagulla. Ya kuma ba da tagulla mai yawan da ba za a iya aunawa ba,4da itacen sida fiye da yadda za a iya ƙirgawa. (Sidoniyawa da mutanen Taya suka kawo wa Dauda gumaguman sida da yawa domin ya ƙidaya.)5Dauda ya ce ɗana Suleman yaro ne, bai ƙware ba tukuna, kuma gidan da za a gina wa Yahweh dole ne ya zama mai daraja sosai, domin ya zama da daraja ya yi suna a dukkan ƙasashe. Saboda haka zan yi shiri domin gininsa." Saboda haka, Dauda ya yi gagarimin shiri kafin mutuwarsa.6Sai ya kira Suleman ɗansa ya umurce shi ya gina gida saboda Yahweh, Allah na Isra'ila.7Dauda yace da Suleman, "Ɗana, na yi niyya ni da kaina in gina gida saboda sunan Yahweh, Allahna.8Amma Yahweh ya zo wuri na ya ce, 'Ka yi yaƙe-yaƙe da yawa ka zubar da jini. Ba za ka gina gida domin sunana ba, domin ka zubar da jini da yawa bisa ƙasa a idanuna.9Duk da haka, za ka sami ɗa wanda zai zama mutum mai salama. Zan ba shi hutawa daga dukkan maƙiyansa a kowanne sashi. Sunansa zai zama Suleman, kuma zan ba da salama da kwanciyar rai ga Isra'ila a kwanakinsa.10Shi ne zai gina mani gida, zai zama ɗa a gare ni, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan tabbatar da kursiyin mulkinsa bisa Isra'ila har abada.'11To yanzu, ɗana, Yahweh ya kasance tare da kai ya ba ka nasara. Za ka ginawa Yahweh Allahnka gida kamar yadda ya ce.12Bari Yahweh ya ba ka fahimi da hangen gaba, domin ka yi biyayya da dokar Yahweh Allahnka, sa'ad da ya ɗora ka bisa shugabancin Isra'ila.13Za ka yi nasara idan ka lura ka yi biyayya da farillai da dokokin da Yahweh ya ba Musa game da Isra'ila. Ka ƙarfafa, ka yi ƙarfin zuciya, kada ka karaya.14Yanzu ka duba, na yi baban ƙoƙari, na yi tanaji domin gidan Yahweh, zinariya awo 100,000, azurfa awo milyan ɗaya, da tagulla da ƙarafa masu tarin yawa. Na kuma tanaji katako da dutse. Na sani dole sai ka ƙara a kan su.15Kana da ma'aikata da yawa: masu sassaƙar dutse da magina da kafintoci da ƙwararru ga aikin hannu da yawa a kowanne fanni,16waɗanda za su iya yin aiki da zinariya da azurfa da tagulla da ƙarafa. Sai ka fara aiki, Yahweh ya kasance tare da kai."17Dauda kuma ya dokaci dukkan dattawan Isra'ila su taimaki ɗansa Suleman, da cewa,18"Yahweh Allahku yana tare da ku, kuma ya ba ku salama a kowanne sashi, ya ba da mazauna yankin cikin hannuna. An ladabtar da yankin a gaban Yahweh da mutanensa.19Sai ku nemi Yahweh Allah da dukkan zuciyarku da ranku. Sai ku tashi tsaye ku gina wuri mai tsarki na Yahweh Allah. Sa'an nan ne za ku iya kawo akwatin alƙawari na Yahweh tare da abubuwan da ke na Yahweh a cikin gidan da a ka gina domin sunan Yahweh."
Waɗannan ne mutanen da ke tattara dutwasu su sassaƙa su a daidai girma sobada magina su yi aiki gini ko na gina ganuwa.
"sakata" ko "noti." Waɗannan abubuwan ke ke haɗa abubuwa biyu.
AT: "fiye da wani zai a iya aunawa"
"fiye da wani zai a iya ƙirgawa
AT: "gidan Yahweh" ko "gidan da za a gina wa Yahweh"
"Dauda yayi kira"
"ya umurce shi ya gina ... na yi niyya ni da kaina in gina"
"ba za ka gina haikali domin girmama ni ba"
"domin na sani cewa ka kashe mutane da yawa"
Dauda ya ci gaba da gay wa Suleman abin da Yahweh ya gaya mashi.
Wannan na nufin a kowanne wuri kewaye da Isra'ila.
"yayin da ya yi mulkin Isra'ila"
Allah zai bi da Suleman kamar shi ɗan Allah ne.
Dauda ya ci gaba da magana da Suleman.
Dauda yayi amfani da wannan domin gabatar da wani abu mai muhimmanci da yake so ya faɗa.
AT: "bari ka yi nasara ta wurin bi da aikin ginin"
"a lokacin da ya maida ka sarkin Isra'ila"
Dauda ya ci gaba da magana da Suleman.
Wannan ya gabatar da wani abu mai muhimmanci da Dauda yake so ya faɗa.
"1,000,000"
Dauda ya ci gaba da magana da Suleman.
Dukkansu ma'aikata ne masu sassaƙar dutse su kuma shirya su domin magina su yi amfani da shi domin gine gine da ginin ganuwowi.
Waɗannan mutane ne da ke aiki da kataƙo.
"ya ba ku salama daga yaƙi a kowanne sashi wa Isra'ila"
"Ya bani iko bisa kowane mutum da ke zaune a yankin mu"
"haikalin da za a gina domin ɗaukaka Yahweh"
1Sa'ad da Dauda ya tsufa, yana kusa da ƙarshen rayuwarsa, sai ya naɗa ɗansa Suleman ya zama sarkin Isra'ila.2Ya tattara dukkan shugabannin Isra'ila, tare da firistoci da Lebiyawa.3Lebiyawa kuwa masu shekaru talatin da ma sama da haka, aka kidaya su, sun kai jimillar dubu talatin da takwas.4'"Dubu ashirin da huɗu daga cikin su za su yi hidimar gidan Yahweh, sai kuma dubu shida za su zama ma'aikata da alƙalai.5Dubu huɗu kuwa za su zama matsara ƙofofi da dubu huɗu kuma za su zama masu yabon Yahweh da kayayyakin bushe-bushe da kaɗe-kaɗe waɗanda za su yi yabo," Dauda ya ce.6Ya raba su kashi kashi bisa ga 'ya'yan Lebi: Geshon, da Kohat da Merari.7Daga zuriyar kabilar Geshon, akwai Ladan da Shimei.8Akwai 'ya'ya maza uku na Ladan: su ne Yehiyel shi ne shugaba da Zetam da Yowel.9Akwai 'ya'ya uku maza na Shimei, su ne Shelomit da Heziyel da Haran. Waɗannan su ne shugabannin kabilar Ladan.10Akwai 'ya'ya huɗu maza na Shimei, su ne Yahat, Ziza, Yewush da Beriya.11Yahat shi ne babba, Ziza shi ne na biyu, amma Yewush da Beriya ba su da 'ya'ya maza da yawa, saboda haka sai aka ɗauke su a matsayin kabila ɗaya tare da yin ayyuka iri ɗaya.12Akwai 'ya'ya maza huɗu na Kohat su ne Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel.13Waɗannan 'ya'ya maza na Amram su ne Haruna da Musa. Haruna aka zaɓa aka kuma ƙeɓe shi domin ya tsarkake abubuwa mafi tsarki, shi da kabilarsa su riƙa ƙona turare a gaban Yahweh, su yi masa hidima, su riƙa sa albarka da sunansa har abada.14Amma Musa mutumin Allah, da 'ya'yansa maza aka ɗauke su a matsayin Lebiyawa.15'Ya'yan Musa maza kuwa su ne Geshon da Eliyeza.16A zuriyar Geshon Shebayel ne babban ɗansa.17Zuriyar Eliyeza Rehabiya ne ɗansa. Eliyeza ba shi da 'ya'ya maza, amma Rehabiya na da zuriya mai yawa.18Ɗan Izhar shi ne Shelomit na shugaba.19Zuriyar Hebron su ne Yeriya, babbansu, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da kuma Yekameyam na huɗu.20'Ya'yan Uzziyel maza kuwa su ne Mika ne babban da Ishija na biyu.21'Ya'yan Merari maza su ne Mali da Mushi. 'Ya'yan Mali maza su ne Eliyeza da Kish.22Eliyeza kuwa ya rasu ba shi da ko 'ya'ya maza. Yana da 'ya'ya mata ne kaɗai.23'Ya'ya maza na Kish ne suka aure su. 'Ya'yan Mushi uku maza su ne Mali, Eder da Yerimot.24Waɗannan su ne zuriyoyin Lebiyawa bisa ga dangoginsu. Su ne shugabannin, da aka lasafta aka jera su bisa ga sunaye, su ne dangogin da suka yi hidimar aiki a cikin gidan Yahweh, daga shekaru ashirin zuwa gaba.25Gama Dauda ya ce, '"Yahweh, Allah na Isra'ila, ya ba da hutu ga sauran mutanensa. Ya mai da gidansa a Yerusalem har abada.26Lebiyawa ba sauran bukatar ɗauka rumfar sujada tare da kayayyakin yin aiki a cikinta."27Gama bisa ga maganar Dauda ta ƙarshe aka kiɗaya Lebiyawa, daga mai shekaru ashirin zuwa gaba.28Aikinsu kuwa shi ne su taimaki zuriyar Haruna gudanar da aiki cikin gidan Yahweh. Su kula da farfajiyoyi da ɗakuna, da tsabtace tsarkakan dukkan abubuwa da su ke na Yahweh, da sauran ayyuka a cikin gidan Allah.29Za su kuma ɗauki nauyin kula da wajen gurasar ajiyewa da lallausan gari na baiko na gari, da waina marar gami da soyayyun baye-baye, baye-bayen da ka gauraya da mai, da dukkan ma'aunan nauyi da girma abubuwa.30Suna kuma tsaye a kowacce safiya don su yi godiya da yabon Yahweh. Suna riƙa yin wannan da maraice31da duk lokacin baikon ƙonawa suna miƙa wa Yahweh, a ranakun Asabaci da lokacin tsayuwar sabon wata da bikin ƙayyadaddun idodi. Akwai adadin lambar da za a sa bisa ga ka'ida, kullum za su bayyana a gaban Yahweh.32Su ne za su riƙa lura da rumfar taruwa, da wuri mai tsarki, za su kuma taimaki abokansu, zuriyar Haruna hidima cikin gidan Yahweh.
Dauda ya naɗa Suleman ya zama magajin shi, ya kuma tsara Firistoci da ma'aikata domin hidima a haikali.
AT: "Waɗansu mutanen Dauda sun ƙidaya Lebiyawa da ke shekara 30 da fiye da haka"
dubu tkwas - "Su 38,000 ne"
dubu huɗu - AT: "Daga waɗannan Lewiyawa, 24,000"
Waɗannan Lewiyawan na sauraron ƙararraƙi, suna kuma zartas da shari'ar bisa ga dokar Musa.
Waɗannan sunayen 'ya'yan Lewi ne.
"Jerin Lewiyawa bisa ga zuriyarsu"
Wannan ya ci gaba da lissafta Lewiyawa bisa ga zuriyarsu.
AT: "saboda haka sai Dauda ya ɗauke su a matsayin ƙabila ɗaya"
Wannan ya ci gaba da lissafta Lewiyawa bisa ga zuriyarsu.
AT : "Yahweh ya zaɓe Haruna domin ya tsarkake abubuwa mafi tsarki"
AT: "kamar waƙilin Allah ya riƙa sa masu albarka har abada"
AT: "'ya'yansa suna tare da Lewiyawa." 'Ya'yansa Musa aka ɗauke su a matsayin Lewiyawa.
Wannan ya ci gaba da lissafta Lewiyawa bisa ga zuriyarsu.
Wannan ya ci gaba da lissafta Lewiyawa bisa ga zuriyarsu.
Wannan ya ci gaba da lissafta Lewiyawa bisa ga zuriyarsu.
AT: "Waɗannan su ne sunayen dangogin Lewi da iyalensu bisa ga dangoginsu, waɗanda mutanen Dauda suka ƙirga kuma suka lissafa. Su ne shugabannin dangogin"
AT: "daga shekaru 20 da fiye da haka"
AT: "tare da dukkan kayayyakin yin aikin cikinta"
AT: "saboda maganar Dauda ta ƙarshe shine umurnw da cewa a kiɗaya Lewiyawa"
AT: "baye-bayen da wani ya sa aka gauraya da mai"
"Lewiyawa suma sun tsaya"
Waɗannan hutunan na nuna alamar farawar kowacce wata.
AT : "a duk lokacin da firistoci suna miƙa baikon ƙonawa wa Yahweh"
1Ga yadda aka raba aiki bisa ga zuriyar Haruna su ne: Nadab, Abihu, Eliyeza da kuma Itama.2Nadab da Abihu sun riga mahaifinsu mutuwa. Ba su da 'ya'ya, saboda haka Eliyeza da Itama suka shiga aikin firistoci.3Dauda, tare da Zadok, zuriyar Eliyeza da Ahimelek, da zuriyar Itama, sun karkasa su bisa ga ayyukansu na matsayin firistoci.4Akwai manyan mutane da yawa a zuriyar Eliyeza fiye da zuriyar Itama, sai suka karkasa zuriyar Eliyeza zuwa kashi goma sha shida. Sun yi wannan bisa ga shugaban dangogi da kuma bisa ga zuriyar Itamar. Waɗannan rabe rabe guda takwas ne adadinsu, bisa ga dangoginsu.5Suka karkasa su ta hanyar ƙuri'a, domin akwai ma'aikatan wuri mai tsarki da kuma ma'aikata na Allah daga zuriyar Eliyeza da kuma zuriyar Itama.6Shemaiya ɗan Netanel marubuci, Balabe, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da ma'aikata, Zadok firist, da Ahimelek ɗan Abiyata, da shugabannin firistoci da iyalan Lebiyawa. An sami dangi ɗaya ta wurin ƙuri'a daga zuriyar Eliyeza, an sake samun ɗaya daga zuriyar Itama.7Ƙuri'a ta farko ta je ga Yehoyarib, ta biyu ga Yedayiya,8ta uku ga Harim, ta huɗu ga Seyorim,9ta biyar ga Malkija, ta shida ga Mijamin,10ta bakwai ga Hakkoz, ta takwas ga Abija,11Na tara Yeshuwa, ta goma ga Shekaniya,12ta goma sha ɗaya ga Eliyashib, ta goma sha biyu ga Yakim,13ta goma sha uku ga Huffa, ta goma sha huɗu ga Yeshebeyab,14Ta goma sha biyar ga Bilga, ta goma sha shida ga Immer,15Ta goma sha bakwai ga Hezir, ta goma sha takwas ga Haffizzez,16ta goma sha tara ga Fetahiya, ta ashirin ga Yehezkel,17ta ashirin da ɗaya ga Yakin, ta ashirin da biyu ga Gamul,18ta ashirin da uku ga Delaiya, da kuma ta ashirin da huɗu ga Ma'aziya.19Wannan shi ne tsarin aikinsu, idan sun zo hidima cikin gidan Yahweh, bisa ga ka'idar da kakansu Haruna ya ba su, kamar yadda Yahweh, Allah na Isra'ila ya umarce shi.20Waɗannan su ne sauran Lebiyawa, 'ya'ya maza na wajen Amram, shi ne Shubawel; 'Ya'ya maza na Shubawel da Yedaiya.21'Ya'ya maza na Rehabiya shi ne Ishija shugaba.22Na wajen Izharawa: shi ne Shelomit; na wajen Shelomit: shi ne Yahat.23'Ya'ya maza na wajen Hebron Yeriya ne shugaba, Amariya na biyu, da Yahaziyel na uku, da Yekameyam na huɗu.24'Ya'ya maza zuriyar Uzziyel ya haɗa da Mika. Zuriyar Mika ta haɗa da Shamir.25Ɗan'uwan Mika shi ne Ishija. 'Ya'ya maza ya haɗa da Zekariya.26'Ya'ya maza na Merari su ne Mali da Mushi. Ɗan Yaaziya shi ne Beno.27'Ya'ya maza na Merari su ne Yaaziya: Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.28'Ya'ya maza na Mali su ne Eliyeza, wanda ba shi da 'ya'ya maza.29'Ya'ya maza na Kish, ɗan Kish, shi ne Yerameyel.30'Ya'ya maza na Mushi su ne Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lebiyawa bisa ga iyalansu.31Waɗannan mutane su ne ke shugabatar kowanne gidan uba da kowane ɗan 'yan'uwansu, aka jefa ƙuri'a a gaban sarki Dauda da Zadok da kuma Ahimelek, tare da shugabanni na kowanne iyalan firistoci da Lebiyawa. Suka jefa ƙuri'a kamar yadda zuriyar Haruna suka yi.
Duba yadda ka fassara wannan a 6:1.
Wannan sunan mutun ne.
"rarrba dangoginj Eliyeza da Itama bisa ga ƙungiyoyinsu"
"Dauda, Zadok , Ahimelek sukn rarraba"
"kungijoyi 16"
"Waɗannan rabe rabenguda takwas ne adadinsu, bisa ga dangogin Itama"
Wannan sunan mutun ne.
Duba yadda ka fassara wannan a 15:22.
AT: "An zabi dangi ɗaya ta wurin ƙuri'a daga zuriyar Eliyeza, an sake samun ɗaya daga zuriyar Itama"
Wannan shine tsarin hidima da Dauda, Zadok da Ahimelek suka zaɓa ta wurin kuri'a domin jikokin Eliyeza da Itama.
Wannan shine tsarin hidima da Dauda, Zadok da Ahimelek suka zaɓa ta wurin kuri'a domin jikokin Eliyeza da Itama.
Wannan shine ƙarshen tsarin hidima da Dauda, Zadok da Ahimelek suka zaɓa ta wurin kuri'a domin jikokin Eliyeza da Itama.
AT: "bin ka'idodin da kakansu Haruna ya ba su"
Wannan ya fara da jerin sunaye na 'ya'yan Lewi. Wannan jerin ya ƙare a 24:30.
Duba yadda ka fassara wannan a 6:.
Duba yadda ka fassara wannan a 23:15.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen mutanen a 23:19.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen mutanen a 23:19.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen mutanen a 23:21.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Duba yadda ka fassara sunayen waɗanna mutanen a 23:21.
Waɗannan sunayen mutane ne.
1Dauda da shugabannin Lebiyawa sun zaɓi waɗansu don aiki suna cikin 'ya'yan Asaf maza da na Heman da na Yedutun. Waɗannan mutane za su yi annabci da waɗannan kayayyakin bushe bushe irin su garayu da molaye da kuge. A nan ga adadin mutanen da suka yi wannan aikin:2Daga 'ya'yan Asaf maza, su ne Zakkur, Yosef, Netaniya da Asharela, Asaf mahaifinsu ne ya ke bi da su, shi ne kuma wanda ya ke waƙa a ƙarƙashin sarki.3Daga 'ya'yan Yedutun maza su ne Gedaliya, Zeri da Yeshayiya, Shimei, Hashabiya da Mattitiya, dukka su shida ne, mahaifinsu Yedutun ne ke kula da su, shi ne kuma mai raira waƙoƙi da garaya don godiya da yabon Yahweh.4Daga 'ya'yan Heman maza kuwa akwai Bukkiya, Mattaniya, Uzziyel, Shebuwel, Yerimot, Hananiya, Hanani, Eliyata, Giddalti, Romamti-Ezer, Yoshbekasha, Malloti, Hotir da kuma Mahaziyot.5Dukkan waɗannan 'ya'ya maza ne na Heman annabin sarki. Allah ya ba Heman 'ya'ya maza goma sha huɗu da kuma 'ya'ya mata uku don ya girmama shi.6Dukkan waɗannan suna ƙarƙashin mahaifinsu. Su mawaƙan gidan Yahweh ne, tare da kaɗa kuge da molaye da garayu kamar yadda suke aiki cikin gidan Allah. Asaf da Yedutun da Heman suna ƙarƙashin umarnin sarki.7Su da 'yan'uwansu maza horarru ne sun kuma ƙware da mawaƙa ga Yahweh jimillarsu kuwa ita ce 288.8Suka jefa ƙuri'u don ayyukansu, dukka suna kama da juna, haka ma ya ke ga yaro da babba da malami da ɗalibi.9Yanzu game da 'ya'yan Asaf maza; ƙuri'a ta farko ta faɗa a kan iyalin Yosef; ta biyu ga iyalin Gedaliya, jimilla mutane goma sha biyu ne;10ta uku ta faɗa a kan Zakkur, da 'ya'yansa da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne,11ta hudu ta faɗa ga Izri, 'ya'yansa da danginsa jimilla mutane goma sha biyu ne;12ta biyar ta faɗa ga Netaniya, 'ya'yansa maza da danginsa jimilla mutane goma sha biyu ne;13ta shida ta faɗa ga Bukkiya, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;14ta bakwai ta faɗa ga Yesarela, 'ya'yansa maza da danginsa jimilla mutane goma sha biyu na;15ta takwas ta faɗa ga Yeshayiya, 'ya'yansa dandinsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;16ta tara ta faɗa ga Mattaniya, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;17ta goma ta fada ga Shimei, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;18ta goma sha ɗaya ta faɗa ga Azarel, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;19ta goma sha biyu ta faɗa ga Hashabiya, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;20ta goma sha uku ta faɗa ga Shubayel, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;21ta goma sha hudu ta faɗa ga Mattitiya, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;22ta goma sha biyar ta faɗa ga Yerimot, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;23ta goma sha shida ta faɗa ga Hananiya, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;24ta goma sha bakwai ta faɗa ga Yoshbekasha, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;25ta goma sha takwas ta faɗa ga Hanani, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;26ta goma sha tara ta faɗa ga Malloti, 'ya'yansa da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;27ta ashirin ta faɗa ga Eliyata, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;28ta ashirin da ɗaya ta faɗa ga Hotir, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;29ta ashirin da biyu ta faɗa ga Giddalti, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;30ta ashirin da uku ta faɗa ga Mahaziyot, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne;31sai ta ashirin da huɗu ta faɗa ga Romamti-Ezer, 'ya'yansa maza da danginsa, jimilla mutane goma sha biyu ne.
Duba yadda ka fassara wannan a 13:7.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen mutanen a 16:40.
Waɗannan sunnayen mutane ne.
Wannan ya ci gaba da jerin sunnanyen shugabanin ayyukan haikali da aka fara a 25:1.
Waɗannan sunnayen mutane ne.
"'ya'ya maza 14 da 'ya'ya mata 3"
Duba yadda ka fassara waɗannan a 16:40.
"mazan sun kassance ɗari biyu da tamanin ne"
Wannan ya bayyana su da zurfi. AT: "dukkansu
Wannan ya fara lissafin kuri'ar 24 da a kada domin ɓtsarin da kowane iyali zasu yi hidima. An ƙarasa wannan jerin a 25:29.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen a 25:1.
"mutane 12"
Wannan ya ci gaba da jerin da ya fara a 25:9.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen mutanen a 1 Chron. 25:4.
Duba yadda zaka fassara waɗannan sunayen mutanen a 25:1.
Wannan ya ci gaba da jerin da ya fara a 25:9.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen mutanen a 25:1.
Wannan ya ci gaba da jerin da ya fara a 25:9.
Wannan ya nuna tsarin yadda aka zaɓi iyalen. AT: "lamba 14 ... lamba 15 ... lamba 16 ... lamba 17"
Ya ci gaba da jerin da ya fara a 25:9.
Duba yadda zaka fassara waɗannan sunayen mutanen a 25:4.
Wannan ne ƙarshen jerin da aka far a 25:9.
Duba yadda zaka fassara waɗannan sunayen mutanen a 25:4.
1A nan ga yadda aka raba masu tsaron ƙofofi: Daga Koratawa, Meshelemiah ɗan Kore ne, zuriyar Asaf.2Meshelemiya yana da 'ya'ya maza: Zekariya ne ɗan fari, Yediyayel ne na biyu, Zebadiya na uku, Yatniyel na huɗu,3Elam na biyar, Yehohanan na shida, Eliyehoyenai ne ɗa na bakwai.4Obed Idom da 'ya'ya maza su ne, na fari shi ne Shemaiya, na biyu Yehozabad, na uku Yowa, na huɗu Sakar, na biyar Netanel, shida5Ammiyel, na bakwai Issaka, na takwas Fiyuletai, gama Allah ya sa wa Obed Idom albarka.6Shemaiya shi ne ɗan farin Obed Idom ya haifi 'ya'ya maza waɗanda suka yi shugabancin iyalansu; su jarumawan mutane ne.7'Ya'yan Shemaiya maza su ne Otni, Refayel, Obed, Elzabad. Danginsa Elihu da Shemakiya suma jaruman mutane ne.8Dukkan waɗannan kabilun Obed Idom. Su da 'ya'yansu maza da dangoginsu jarumai ne masu ƙarfi da gwaninta na yin hidima. Akwai mutane sittin da biyu da suke da dangantaka da Obed Idom.9Meshelemiya yana da 'ya'ya maza da 'yan'uwa, mutane ne masu ƙarfi da gwaninta, su dukka goma sha takwas ne.10Hosa, yana cikin zuriyar Merari, yana da 'ya'ya maza, Shimri shugaba (ko da ya ke ba shi ne ɗan fari ba, duk da haka maihaifinsa ya maishe shugaba).11Hilkiya shi ne na biyu, da Tabaliya na uku da Zekariya na huɗu. Dukkan 'ya'yan Hosa maza da 'yan'uwansa su goma sha uku ne.12Waɗannan su ne rabe rabe na masu tsaron ƙofa, bisa ga shugabanninsu, da ayyuka, kamar iyalansu, da za su yi hidima a gidan Yahweh.13Sai suka jefa kuri'a yaro da babba bisa ga iyalansu, don kowacce ƙofa.14Sai ƙuri'ar ƙofar gabas, ta faɗo a kan Shelemiya. Suka kuma jefa ƙuri'a don ɗansa Zekariya, mai ba da shawara mai ma'ana, sai ƙuri'arsa ta fito don ƙofar arewa.15An sa Obed Idom ƙofar kudu, an kuma sa 'ya'yansa maza lura da ɗakunan ajiya.16Shuffin da Hosa an sa su a ƙofa ta yamma tare da Shalleket, a kan hanyar da ta haura. Aka tabbatar da masu tsaron kowanne iyali.17A gefen gabas akwai Lebiyawa shida, a gefen arewa a rana ta huɗu, a gefen kudu a rana ta huɗu, an kuma sa biyu biyu a ɗakunan ajiya.18A ɗakin shari'a da ke yamma akwai masu tsaro huɗu, a hanya guda huɗu, biyu kuma a ɗakin shari'a.19Yadda aka raba masu tsaron ƙofofin kenan. Suna cike da zuriyoyin Kora da Merari.20A cikin Lebiyawa, Ahijah ne mai kula da ma'ajin gidan Allah, da ma'ajin abubuwa da ke na Yahweh.21Zuriyar Ladan, daga zuriyar Geshon ta wurinsa da waɗanda suke shugabannin iyalan Ladan Bageshone, su ne Yehiyeli,22da 'ya'yansa maza Zetam da Yowel ɗan'uwansa, su ne ke kula da ɗakunan ajiyar gidan Yahweh.23Akwai kuma masu tsaro da aka ɗauko daga kabilar Amram, da Izhar da Hebron da kuma Uzziyel.24Shubayel ɗan Geshom ɗan Musa, shi ne babban jami'in ɗakunan ajiya.25Danginsa daga kabilar Eliyeza su ne ɗansa Rehabiya, Yeshayiya ɗan Rehabiya, Yoram ɗan Yeshabiya, Zikri ɗan Yoram, da kuma Shelomit ɗan Zikri.26Shelomit da 'yan'uwansa ne ke lura da dukkan gidajen ajiya da abubuwan da ke na Yahweh, wanda Dauda sarki, da iyalin shugabanni, da shugabannin sojoji na dubu dubu na ɗari ɗari da kuma shugabannin sojojin da aka keɓe.27Su ne kuma aka keɓe don kula da ganimar yaƙe-yaƙe domin kuma gyaran gidan Yahweh.28Su ne kuma masu lura da kowane irin abubuwa da aka keɓe ga Yahweh ta wurin annabi Sama'ila, da Saul ɗan Kish da Abner ɗan Ner da Yowab ɗan Zeruyiya. Kowanne abu da aka keɓe ga Yahweh yana ƙarƙashin kulawar Shelomit da 'yan'uwansa.29Zuriyar Izhar da Kenaniya tare da 'ya'yansa maza su ne aka danƙa wa al'amuran sasantawa na Isra'ila. Su ne shugabanni da alƙalai.30Zuriyar Hebron da Hashabiya haɗe da 'yan'uwansa, 1700 gwanayen mutane ne, su ne masu lura da ayyukan Yahweh da na sarki. Suna wajen yammacin Yodan.31Daga zuriyar Hebron, Yeriya shi ne shugaban zuriyarsa, bisa ga asalin iyalansu. A shekara ta arba'in ta sarautar Dauda sun bincika, aka tarar akwai ƙarfafan mutane, jarumawa a Yazer ta Giliyad.32Yeriya yana da 'yan'uwa har 2,700, waɗanda suke gwanaye shugabannin iyali. Dauda ya maida su masu lura da kabilar Ruben da ta Gad da kuma rabin kabilar Manasse, domin kowane abu da ke na Allah da kuma al'amuran sarki.
Wannan ya fara lissafin sunayen masu tsaron ƙofofi.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen mutanen a 9:21.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan ya fara lissafin sunayen masu tsaron ƙofofi wanda ya fara a 1 Tarihi 26:1.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen mutanen a 16:37.
Waɗannan sunnayen mutane ne.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen mutanen a 9:21.
"Dangin Shemaiya" ko "Iyalen Shemaiya"
"jimilar su dukka 18"
Wannan ya fara lissafin sunayen masu tsaron ƙofofi wanda ya fara a 1 Tarihi 26:1.
Waɗannan sunayen mutane ne.
AT: "Dukkan 'ya'yan Hosa maza da 'yan'uwansa su 13 ne"
AT: "kowane mutum" ko "dukkan mutane na kowane tsara"
AT: "A lokacin suka jefa kuri'a"
Wannan mutum ne da ke bada hukunci mai kyau a yanke hukunci.
Obed Idom shine ke da hakin lura da ƙofar kudu an kuma sa 'ya'yansa maza lura da ɗakunan ajiya.
Wannannne sunan ƙofar.
AT: "Kowane iyali na da hakin tsaron wani abu"
"Lewiyawa 6"
" mutane biyu biyu" ko "mutane 2 a kowane lokaci"
"mutane biyu suka tsare hanyar, kuma mutane biyu suka tsare ɗakin shari'a"
Yehiyeli da ya'yansa maza sune suriyar Ladan, waɗanda suka fito daga Geshon na Ladan. Yehiyeli da ya'yansa maza sune Shugabanan iyalen Ladan Bageshone. 'Ya'yansa Yehiyeli maza sune"
Zuriyar Gershon.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen mutanen a 23:7.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen mutanen a 1 Chron. 23:12.
Duba yadda ka fassara waɗannan sunayen mutanen a 23:15-17.
Waɗannan sunayen mutane ne.
"fiye da 1,000 mazaje fiye da 100 mazaje"
Waɗannan sunayen mutane ne.
"Kowanne abu da shugabanai suka keɓe "
Duba yadda zaka fassara waɗannan sunayen mutanen a 23:12.
"dubu da ɗari bakwai gwanayen mutane ne"
"ayyukan Yahweh da ayyukan sarki"
AT: "sunayensu suna cikin jerin"
"yan'uwa dubu biyu da dari bakwai"
1Wannan shi ne lissafin iyalin shugabannin Isra'ila, shugabannin sojoji na dubu dubu da ɗari ɗari, har da rudunar sojoji waɗanda suke yi wa sarki aiki ta hanyoyi dabam dabam. Kowace runduna za ta yi aiki wata wata har ƙarshen shekara. Kowanne kashi na da mutane dubu ashirin da huɗu.2A kowane kashi a wata na farko, shi ne na Yashobeyam ɗan Zabdiyel. A cikin kashinsa akwai mutane dubu ashirin da huɗu.3Yana cikin zuriyar Pezer, shi ne kuma mai lura da dukkan shugabannin sojoji a watan farko.4Bisa ga kashi wata na biyu shi ne Dodai, daga kabilar zuriya daga Ahoya. Miklot shi ne na biyu a jerin. A cikin rabonsa akwai mutane dubu ashirin da huɗu.5Shugaban ruduna a wata na uku shi ne Benaiya ɗan Yehoiada, firist ne kuma shugaba. A cikin rabonsa akwai mutane dubu ashirin da huɗu.6Wannan shi ne Benaiya wanda shi ne shugaba a cikin talatin, da kuma bisa ga talatin. Ammizabad ɗansa mana cikin rabonsa.7Shugaban sojoji a wata na huɗu shi ne ɗan'uwan Asahel Yowab. Ɗansa Zebadiya ya zama shugaba a madadinsa. A cikin rabonsa akwai mutane dubu ashirin da huɗu.8Shugaba na watan biyar shi ne Shamhut, a zuriyar Izra. A cikin rabonsa akwai mutane dubu ashirin da huɗu.9Shugaba na watan shida shi ne Ira ɗansa Ikesh, daga Tekowa. A cikin rabonsa akwai mutane dubu ashirin da huɗu.10Shugaba na watan bakwai shi ne Helez Bafelone, daga mutanen Ifraim. Rabonsa mutane dubu ashirin da huɗu ne.11Shugaba na watan takwas shi ne Sibbekai Bahushate, daga kabilar zuriya daga Zera. Rabonsa mutane dubu ashirin da huɗu ne.12Shugaba na watan tara shi ne Abiyeza Ba'anatot, daga kabilar Benyamin. Rabonsa mutane dubu ashirin da huɗu ne.13Shugaba na watan goma shi ne Maharai daga birnin Netofa, daga dangin zuriya daga Zera. Rabonsa mutane dubu ashirin da huɗu ne.14Shugaba na watan goma sha ɗaya shi ne Benaiya daga birnin Firaton, daga kabilar Ifraim. Rabonsa mutane dubu ashirin da huɗu ne.15Shugaba na watan goma sha biyu shi ne Heldai daga birnin Netofa, daga dangin zuriya daga Otniyel. Rabonsa mutane dubu ashirin da huɗu ne.16Waɗannan su ne shugabannin kabilun Isra'ila: Ga kabilar Ruben, Eliyeza ɗan Zikri shi ne shugaba. Ga kabilar Simiyonn, Shefatiya ɗan Ma'aka shi ne shugaba.17Ga kabilar Lebi, Hashabiya ɗan Kemuwel shi ne shugaba, Zadok shi ne jagora na zuriyar Haruna.18Ga kabilar Yahuda, Elihu, ɗaya daga cikin 'yan'uwan Dauda, shi ne shugaba. Ga kabilar Issaka, Omri ɗan Mika'el shi ne shugaba.19Ga kabilar Zebulun, Ishamaiya ɗan Obadiya shi ne shugaba. Ga kabilar Naftali, Yerimot ɗan Azriyel shi ne shugaba.20Ga kabilar Ifraim, Hosheya ɗan Azaziya shi ne shugaba. Ga rabin kabilar Manasse, Yowel ɗan Fedaiya shi ne shugaba.21Ga rabin kabilar Manasse a Gileyad, Iddo ɗan Zekariya shi ne shugaba. Ga kabilar Benyamin, Ya'asiyel ɗan Abner shi ne shugaba.22Ga kabilar Dan, Azarel ɗan Yeroham shi ne shugaba. Waɗannan su ne shugabannin kabìlun Isra'ila.23Dauda bai ƙidaya waɗanda shekarunsu ba su kai ashirin ba ko kuma yara, gama Yahweh ya yi alƙawarin zai sa mutanen Isra'ila su yi yawa kamar taurarin sammai.24Yowab ɗan Zeruya ne ya fara ƙidayar mutanen nan, amma bai gama ba. Sai hukunci mai zafi ya sami Isra'ila saboda wannan. Wannan ƙidayar ba a rubuta ta ba cikin Tarihin Sarki Dauda ba.25Azmabet ɗan Adiyel shi ne mai lura da ma'ajin sarki. Yonatan ɗan Uzziya shi ne mai kula da ɗakin ajiya a filaye da kuma cikin birane, har da ƙauyuka da kagaran hasumiyoyi.26Ezri ɗan Kelub shi ne mai lura da gonaki, da waɗanda suke huɗa a ƙasar.27Shimei Baramate shi ne mai kula da gonakin inabi da Zabdi Bashifime shi ne mai lura da itatuwan zaitun da inda ake ajiye kwalaben shaye-shaye.28Ga itatuwan zaitun da na ɓaure waɗanda suke a kwari shi ne Ba'al-Hanan daga Geder, kuma ɗakin ajiyar man shi ne Yowash.29Bisa ga garken shanu a Sharon shi ne Shitrai, daga Sharon kuma bisa ga garken shanu da ke cikin kwari shi ne Shafat ɗan Adlai.30Bisa ga rakuma shi ne Obil Ba'isma'ile, kuma bisa ga jakuna mata shi ne Yedaiya daga Meronot. Bisa ga tumaki shi ne Yaziz Bahagire.31Yazia Bahagire shi ne mai lura da garken. Dukkan waɗannan su ne masu lura da dukiyar sarki Dauda.32Yonatan, kawun Dauda, shi ne mai ba da shawara, tun da shi mutum ne mai ganewa shi ne kuma magatakarda. Yehiyel ɗan Hakmoni shi ne mai kula da 'ya'yan sarki.33Ahitofel shi ne mai ba sarki shawara, Hushai daga mutanen Arkite su ne masu shawara na jikin sarki.34Ahitofel ɗan Benaiya an ba da makaminsa ga Yehoiada ɗan Benaiya ta wurin Abiyata. Yowab shi ne babban shugaban sojojin sarki.
AT: "Waɗannan sune sunayen"
"ta hanyoyi dabam dabam" ko "ta hanyoyi da yawa"
"cikin shekarar dukka"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗănnan sunayen mutane ne.
"a cikin rundunar sojojisa" ko "a cikin ƙungiyar sojojinsa"
Duba yadda ka fassara waɗannan a 11:10.
"Asahel, danu'wan Yowab, shi ne shugaban sojoji a wata na huɗu."
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan sunan gari ne.
"Helez Bafelone, daga mutanen Ifrraim, shi ne shugaba na watan bakwai."
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen yarurruka ko dangogi ne.
Wannan shi ne watan goma bisa ga kalandar Yahudawa.
Waɗannan sunayen wurare ne. A lokacin ƙarshen sashin watan sha biyu da farkon sashin watn ɗaya na Kalandar Yammaci.
mutane dubu huɗu - "mutane 24,000"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
"mutane waɗanda ke da shekaru ashirin ko "ƙasa da haka"
"ka ƙara yawan mutanen Isra'ila"
AT: "Allah ya hukunta mutanen Isra'ila"
Waɗannan sunnayen mutane ne.
"mai haƙin tsaro"
"hasumiyoyi masu karfi"
Wannan na nufin gini a ciki ko cire dattin kafin a yi shukka
Wannan sunan wani wuri ne.
Wannan wani irin itace ne.
Waɗannan sunayen mutane ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
"waɗanda suke cin ciyawa a fili"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan sunan wani wuri ne.
"Waɗannan mutanen"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan sunan yaren wani dangi ne.
1Dauda ya tara dukkan shugabannin Isra'ila a Yerusalem: shugabannin kabilu da shugabannin kungiyoyi da ke yi wa sarki hidima a cikin shirin aikinsa, shugabannin dubu dubu da ɗari ɗari da manajoji bisa dukkan dukiya da mallakar sarki da 'ya'yansa da kuma fãdawa da mutane mayaƙa, tare da waɗanda suka zama mafiya fasaha.2Sai sarki Dauda ya mike tsaye ya ce, "Ku saurare ni, 'yan'uwana da jama'ata. Na yi niyya in gina haikalin akwatin alƙawari na Yahweh; wurin zaman zatin Allahnmu, na kuma riga na yi shirin ginin.3Amma Allah ya ce da ni, 'Ba za ka gina mani haikali da sunana ba, domin kai mutum ne mayaƙi, ka kuma zubar da jini.'4Duk da haka Yahweh, Allah na Isra'ila, ya zaɓe ni daga dukkan iyalin mahaifina, in zama sarkin Isra'ila har abada. Shi ne ya zaɓi kabilar Yahuda da kuma gidan mahaifina, daga cikin dukkan 'ya'ya maza na mahaifina, shi ne ya zaɓe ni in zama sarkin Isra'ila.5Daga 'ya'ya maza da yawa Yahweh ya ba ni, ya zaɓe Suleman, ɗana, ya zauna a kan gãdon sarautar mulkin Yahweh, bisa Isra'ila.6Ya ce da ni, 'Suleman ɗanka ne zai gina mani gida da farfajiyoyina, gama na zaɓe shi ya zama ɗa a gare ni, ni kuwa zan zama uba a gare shi.7Zan tabbatar da mulkinsa har abada, idan ya tsaya da gaske ya yi biyayya da dokokina da kuma ka'idodina.'8Saboda haka yanzu, a gaban dukkan Isra'ila, wannan taron Yahweh, da kuma gaban Allahnmu, dukkan ku dole ku kiyaye kuma yi ƙoƙari ku bi dukkan umarnan Yahweh Allahnku. Ku yi wannan don ku mallaki wannan ƙasar mai kyau, ku zauna a cikin ta a matsayin gãdo ga 'ya'yanku a bayanku har abada.9Amma kai, ɗana Suleman, ka yi biyayya da Allah na mahaifinka, ka bauta masa da dukkan zuciyarka da kuma yardar rai. Ka yi wannan gama Yahweh mai binciken dukkan zukata ne, ya kuma san kowanne irin nufi da tunanin kowanne mutum. Idan ka neme shi, zaka same shi, amma idan ka rabu da shi, shi ma zai yi watsi da kai har abada.10Ka lura da cewa Yahweh ya zaɓe ka domin ka gina wannan rumfa mai tsarki. Ka yi ƙarfi, ka kama yi aiki."11Sa'an nan Dauda ya ba ɗansa Suleman tsarin ginshiƙan ƙofar haikalin, da gine-ginen haikali da ɗakunan ajiya da benaye da ɗakunan ciki da ɗakunan inda ake gafarta zunubi.12Ya ba shi tsarin da ya zãna domin farfajiyoyin gidan Yahweh, da dukkan kewayen ɗakunan, da ɗakunan ajiya na gidan Allah, da ma'ajiyai domin abubuwan da ke na Yahweh.13Ya kuma ba shi ƙa'idodin domin rarraba firistoci da Lebiyawa, da dukkan hidimar da za a yi a gidan Yahweh, domin kowanne aiki na cikin gidan Yahweh.14Ya fayyace nauyin santulan zinariya domin kowanne irin aiki, nauyin santulan azurfa domin kowanne irin aiki.15Nauyin zinariya domin dukkan kayayyakin zinariya, sun haɗa da kowanne alkuki da fitilunsa da fitilar zinariya, nauyin ma'aunin kowacce fitila da maɗori, nauyin ma'aunin kowacce azurfa domin kowanne maɗorin fitila, bisa ga yadda za'a yi amfani da kowanne maɗorin fitila a cikin sujada.16Ya ba da ma'aunin zinariya da za a yi teburorin gurasar ajiyewa don kowanne teburi, da kuma ma'aunin azurfa don teburorin azurfa.17Ya bada ma'aunin zinariya tsantsa wadda za a yi cokula masu yatsu domin nama da daruna da kofuna da kwanoni da da ma'auni na yawan azurfa da za a yi kwanoni da ita.18Ya bada ma'aunin zinariya tsantsa wadda za a yi bagaden ƙona turare da ita, da kuma zinariya da za a yi tsarin kerubobin da za su miƙa fikafikansu su rufe akwatin alƙawarin Yahweh.19Dauda ya ce, "Na sa dukkan wannan a rubuce ne kamar yadda Yahweh ya umarce ni, ya kuma ba ni don in fahimci fasalin aikin filla-filla."20Dauda ya ce da ɗansa Suleman, "Ka yi ƙarfi da jaruntaka. Ka yi aikin. Kada ka ji tsoro ko ka karai, gama Yahweh Allah, Allahna, na tare da kai. Ba zai bar ka ba ko ya ƙyale ka har sai ka gama dukkan aikin hidimar haikalin Yahweh.21Duba ga, karkasuwar firistoci da Lebiyawa na nan domin yin dukkan hidima a haikalin Allah. Za su kasance tare da kai, tare kuma da dukkan gwanayen mutanen da suka yarda su taimake ka a cikin aikin da yadda za a yi hidimar. Shugabanni da dukkan mutane na shirya su bi umarninka."
Ayyuka da za a rika yi a kai a kai, misali kawace rana ko kowane wata.
"1,000 da na 100"
kalmomin nan biyu na nufin abu ɗaya kuma ya nuna dukkan malakar da sarki yake da ita.
AT: "ya mike tsaye"
Wannan jumloli biyun na magana ne a kan abu ɗaya kuma yana nanata cewa Dauda da isra'ila iyali ɗaya ne
Jumla na biyu na bayani ne akan jumla na fari. Yahweh na nufin "akwatin alƙawari" a matsayin "wurin zaman zatinsa."
AT: "haikali domina"
AT: "Ya kashe mutane"
Dauda ya ci gaba da yin magana da Isra'ila.
AT: "dukkan kasar Isra'ila" ko "dukkan Isra'ilawa"
AT: "ya yi mulki" ko "ya zama sarki"
AT: "Isra'ila, wanda shi ne mulkin Yahweh"
Dauda ya ci gaba da maga da Isra'ila.
AT: "Allah ya ce mani"
kalmar nan "gida" na nufin haikalin Yahweh.
Wannan bai nuna cewa Suleman ya zamma ɗa na haifuwa a wurin Allah ba. Amma yana nufin dangantaka tsakanin shi da Allah. AT: "Na zaɓi in yi alaƙa da shi kamar ɗa, ni kuma in zama kamar Uba a gare shi"
Waɗannan kalmomi biyu na nufin abu ɗaya, kuma yana bayani ne akan dukan abin da Yahweh ya dokace su.
Kalmar nan "kai" na nufin Dauda. AT: "Kamar yadda kake miƙa kai a kwanakin nan.
Dauda ya ci gaba da magana da Isra'ilawa.
Wannan na nufin cewa Dauda ya fara wata saɓuwar jawabi.
AT: "'ya'yanku waɗanda zasu gaje ku a bayanku"
Dauda ya ƙira kansa "mahaifinka" saboda wannan gagarumin taro ne. AT: "Allahna"
AT: "gabaki ɗaya"
AT: "yardar rai"
Waɗannan jumloli biyu na nufin abu ɗaya da kuma jaddada cewa Yahweh ya san tunanin kowane mutun.
AT: "Idan ka nemi Yahweh ya saurare ka, zai yi haka"
"ƙofar shiga" ko ƙofar haikali." "Wannan na nufin abinda yake kare rumfar da ke a ƙofar shiga haikalin.
ɗakunan ajiye abubuwa masu daraja.
Waɗannan ka'idodine na musanman game da yadda firistoci da Lebiyawa zasu yi hidima a cikin haikali.
Wannan na nufin ƙungiyoyin da aka rarraɓa firistoci da sauran ma'aikata na haikali domin kowannen su ya cika aikinsa. Duba yadda ka fassara wannan kalmar a 24:1.
AT: " tataccen zinariya" ko "zinariya mai daraja"
AT: "Na rubuta dukkan wannan"
AT: "ka taimake ni in fahimci abin"
Waɗannan kalmomi biyu na nufin abu ɗaya, ya kuma jaddada cewa dole Suleman ya kasance da karfin hali.
AT: "zai taimake ka"
Duba yadda ka fassara wannan a 28:13.
1Sarki Dauda yace da dukkan taron, "Ɗana Suleman, wanda shi kaɗai Allah ya zaɓa, sai dai saurayi ne, kuma ba shi da ƙwarewa, kuma aikin babba ne. Gama haikalin ba na mutum ba ne, amma na Yahweh Allah ne.2A halin yanzu dai na riga na yi iyakacin ƙoƙarina, har na tanada waɗannan abubuwa saboda haikalin Allahna. Na ba da zinariya saboda abubuwa na zinariya, azurfa saboda abubuwa na azurfa, tagulla saboda abubuwa na tagulla, ƙarfe saboda abubuwa na ƙarfe, itace kuwa saboda na itace. Na kuma ba da duwatsu da yawa masu daraja, da masu launi iri-iri -da kowaɗanne irin duwatsu masu daraja - da duwatsu a yalwace.3Yanzu, saboda ƙaunar da na ke da ita ta gidan Allahna, shi ya sa na bada zinariyata da azurfata don wannan aiki. Ina ƙara yin wannan dukka don in shirya wannan haikali mai tsarki,4na bada zinariya tsantsa talanti dubu uku daga Ofir, azurfa tsantsa talanti dubu bakwai, domin yin ado a bangon ginin.5Na bada zinariya saboda abubuwa da abin da za ayi da zinariya, azurfa saboda abubuwan da za a yi na azurfa, da dukkan irin abubuwa da kafintoci za su yi. Wane ne kuma ya ke da niyyar bayarwa domin Yahweh yau, ya kuma ba da kansa gare shi?6Sai aka yi bayarwar yardar rai bisa ga shugabannin iyalan kakanni da shugabannin kabilun Isra'ila da shugabannin dubbai da ɗaruruwa da kuma shugabannin da suke yi wa sarki aiki.7Suka bada saboda hidimar gidan Allah talanti dubu biyar da darik dubu goma na zinariya, da talanti dubu goma na azurfa da dubu goma sha takwas na tagulla da kuma talanti 100,000 na ƙarfe.8Waɗanda suke da duwatsu masu daraja sun bada su cikin taskar gidan Yahweh, a ƙarƙashin kulawar Yehiyel, zuriyar Gashon.9Mutane suka yi murna domin waɗannan baye-baye na yardar rai, gama sun bayar da zuciya ɗaya ga Yahweh. Sarki Dauda kuma ya yi murna ƙwarai.10Dauda ya albarkaci Yahweh a gaban dukkan taron, ya ce, "Yabo naka ne, Yahweh, Allah na kakanmu Isra'ila, har abada abadin.11Naka ne, Yahweh, girma da iko da daraja da nasara da ɗaukaka. Gama dukkan abin da ke cikin sammai da duniya naka ne. Naka ne mulki, Yahweh, kai ne maɗaukaki mai mulki a bisa komai.12Dukkan wadata da ɗaukaka suna zuwa daga gare ka, kai ka ke mulki bisa dukkan mutane. A hannunka iko da ƙarfi su ke. Kai ne ka ke da ƙarfi da iko ka sa mutane su yi girma, ka kuma bada ƙarfi ga kowane mutum.13Yanzu, ya Allahnmu, muna gode maka muna kuma yabon sunanka mai daraja.14Amma wãne ni, ko kuma mutanena da za mu iya kawo waɗannan abubuwa da yardar rai? Gama dukkan abubuwan nan sun zo daga gare ka ne, mu kuma muka ba ka abin da ke naka.15Gama mu bãƙi ne, matafiya kuma a gabanka, kamar kakanninmu. Kwanakinmu a duniya kamar inuwa ne, ba mu da begen dauwama a duniya.16Yahweh Allahnmu, dukkan wannan dukiya da muka tattara domin mu gina haikali saboda ɗaukakar sunanka mai tsarki - sun zo daga gare ka ne kuma naka ne. Na kuma sani, ya Allahna, ka kan gwada zuciya, kana jin daɗin abin da ke nagari.17Amma ni, bisa ga amincewar zuciyata, da yardar rai, na miƙa maka dukkan waɗannan abubuwa, yanzu ina dubawa da murna ganin mutanenka waɗanda suke nan da yardar su suka kawo maka kyautai.18Yahweh, Allah na Ibrahim da Ishaku da Isra'ila-kakanninmu - ka ajiye wannan har abada a cikin tunanin zukatan mutanenka. Ka bi da zukatansu zuwa gare ka.19Ka ba ɗana Suleman cikakkiyar zuciyar sha'awar kiyaye umarnanka da alƙawarin ka'idodi da dokokinka, domin ya aikata dukka waɗannan shirye-shirye na gina haikali wanda na riga na yi tanaji dominsa."20Dauda ya ce da dukkan taron, "Yanzu sai ku albarkaci Yahweh, Allahnku." Dukkan taron kuwa suka albarkaci Yahweh, Allah na kakaninsu, suka rusuna da kawunsu suka yi sujada ga Yahweh suka kuma sunkuyar da kansu a gaban sarki.21Washegari, sai suka miƙa wa Yahweh hadayu da hadayun ƙonawa gare shi. Sun miƙa bijimai dubu ɗaya, da raguna dubu ɗaya da kuma 'ya'yan tumakai dubu ɗaya, tare da hadayunsu na sha da hadayu masu yawan gaske domin dukkan Isra'ila.22A wannan rana, sun ci, sun sha a gaban Yahweh tare da bayyana murna da yabo. Sai suka sake naɗa Suleman ɗan Dauda, sarki a karo na biyu, suka shafa masa man keɓewa tare da ikon Yahweh ya zama mai mulki. Suka kuma keɓe Zadok don ya zama firist.23Sai Suleman ya zauna a kan gadon sarauta na Yahweh maimakon Dauda mahaifinsa. Ya yi wadata, kuma dukkan Isra'ila suka yi biyayya da shi.24Dukkan shugabanni da sojoji da 'ya'yan sarki suka yi alƙawari za su yi wa sarki Suleman biyayya.25Yahweh kuwa ya ɗaukaka Suleman ƙwarai da gaske a gaban dukkan Isra'ila, ya ba shi babban iko fiye da wani sarki kafin shi a Isra'ila.26Dauda ɗan Yesse ya yi mulki bisa dukkan Isra'ila.27Dauda ya yi mulki a Isra'ila har shekaru arba'in. Ya yi mulki a Hebron shekaru bakwai, sa'an nan ya yi mulki shekaru talatin da uku a Yerusalem.28Ya rasu da kyakkyawan tsufa, bayan ya ji daɗin rayuwa mai tsawo, da arziki da daraja. Suleman ɗansa ya gaje shi.29Abubuwan da sarki Dauda ya yi suna rubuce a cikin tarihin annabi Sama'ila, da annabi Natan da annabi Gad.30Abubuwan da ke rubuce su ne ayyukansa da mulkinsa, abubuwan da ya kammala da kuma waɗanda suka shafe shi da Isra'ila da dukkan mulkokin sauran ƙasashe.
Waɗannan duwatsu ne tare da laying baƙi da fari da ake amfani da su don yin kayan ado.
Wannan na nufin zane ko abin kwaikwaya da ke kyawawa kuma na ado da aka yi da duwatsu.
Dauda ya ci gaba da yin magana da mutane game da tanadin da yayi don ginin haikalin.
"3,000 talanti"
mafi inganci da zinariya mafi daraja
Duba:
Wannan ne wurin da ake adana kuɗi da abubuwa masu tamani.
Wannan sunan mutum ne.
da yardar rai ba tare da wata shakka ko jinkiri ba
AT: "Yabo naka ne, Yahweh Uban mu, Allah na kakanmu Isra'ila, har abada abadin."
Dauda ya cig aba da addu'ansa ta yabo ga Yahweh.
Kalmar nan "Iko" da "ƙarfi" na nufin abu ɗaya yana kuma bayyana girma da Ikon Yahweh.
Dauda ya ci gaba da addu'ansa ta yabo ga Yahweh.
Dauda yana nufin cewa shi da mutanensa basu cancanci yabo ba don bada wani abu ga Allah.
AT: "Ka sani mu ba ƙomai bane"
Inuwa ya kan fito ya sake ɓattawa da sauri
"domin ina so in kassance da martaba da mutumci a cikin ayuka da nake yi maka"
"ka ajiye wannan a cikin tunanin zukatan mutanenka har abada"
Duba:
kwanta rub da ciki a ƙasa domin nuna bangirma
Domin a ɗaukaka Yahweh.
Na farko an bayyana shi a 23:1.
AT: "an shafe shi domin ya mulki Isra'ila a madadin Yahweh"
AT: "amincin su"
Waɗannan jumlolin guda biyu sun jaddada cewa Suleman ya sami tagomashi na musamman daga wurin Yahweh, wanda ya sa ya zama sarki mafi girma da ƙarfi a Isra'ila.
Wannan rubutu da babu su kuma.
AT: "wani mutane ne ya rubuta ayyukansu a can"
AT: "abubuwan da suka faru a wasu al'ummomin da suka shafi Isra'ila"
1Aka ƙarfafa Suleman ɗan Dauda a cikin mulkinsa, Yahweh Allahnsa na tare da shi ya kuma sa shi ya zama da iko sosai.2Suleman ya yi magana da dukkan Isra'ila, hafsoshi dubu-dubu dana ɗari-ɗari, da mahukunta da dukkan sarakuna a Isra'ila, da shugabannin gidajen ubanni.3Suleman da dukkan taro suka tafi babban tudu a Gibiyon, domin a can ne rumfar taruwa ta Allah take, wadda Musa bawan Yahweh ya yi a cikin jeji.4Amma Dauda ya kawo akwatin alƙawari na Allah daga Kiriyat Yerim zuwa wurin da ya keɓe dominsa. Domin ya kafa mata rumfa a Yerusalem,5Bugu da ƙari bagadin jan ƙarfen da Bezalel ɗan Uri ya yi yana wurin a gaban rumfar taruwa ta Yahweh; Suleman da dukkan taron suka tafi wurinta.6Suleman ya tafi can wurin bagadi na tagulla a gaban Yahweh, wadda take a rumfar taruwa, ya miƙa baye-bayen ƙonawa guda dubu a kansa.7Allah ya bayyana ga Suleman a wannan dare ya cemasa, "ka tambaya! Me zan baka?"8Suleman ya ceda Allah, '"Ka nuna babban amintaccen alƙawari ga Dauda mahaifina, kuma ka maida ni sarkin mutanensa a madadin sa.9Yanzu, Yahweh Allah, sai ka cika alƙawarin da kayi wa mahaifina Dauda, domin ka maida ni sarki kan mutane masu ɗumbin yawa kamar ƙasa.10Yanzu sai ka bani hikima da ilimi domin in iya jagorancin mutanen nan, domin wane ne zai iya yiwa mutanenka hukunci, su da keda yawa sosai?"11Allah ya ceda Suleman, "Saboda wannan ne yake zuciyarka, kuma domin baka roƙi wadata ba, ko kuɗi, ko girma, ko kuma ran waɗanda ke ƙinka, ko kuma tsawon ranka ba, amma ka roƙi hikima da ilimi domin kanka, domin ka iya mulkin mutanena, waɗanda na maishe ka sarki a kansu, to wannan shi ne abin da zan yi.12Yanzu zan baka hikima da ilimi. Hakannan zan baka arziki da wadata da girma, da ba a taɓa samun sarki kamarka a baya ba, ba kuma za a samu a bayan ka ba."13To sai Suleman ya komo Yerusalem wuri mai tudu da kea Gibiyon, daga wurin rumfar taruwa; ya yi sarauta akan Isra'ila.14Suleman ya tattara karusai da mahayan dawakai, yana da karusai 1,400 da mahayan dawakai dubu goma sha biyu waɗanda yasa a biranen karusai da kuma tare da shi sarki, a Yerusalem.15Sarki ya samar da zinariya da azurfa birjik kamar duwatsu a Yerusalem, ya kuma samar da itacen sida sosai kamar itacen ɓaure da ke cikin kwaruruka.16Game da sayo dawakai daga Masar da Kuye domin Suleman, fatakensa ne suka sayo su daga Kuye cikin rahusa.17Suka sayo karusa daga Masar a awo ɗari shida na zinariya, da kuma doki akan shekel 150. Suka kuma sayar da wasu ga sarakunan Hitiyawa da Aremiyawa.
AT : "Suleman ya kasance da Iko a kan Isra'ila"
Wannan sunan Allah ne da ya bayyana ga mutanensa a Tsohon Alƙawali. Duba shafi na fassara game da yadda zaka fassara wannan.
AT: "Allah ya talafa mashi" ko "Allah ya taimake shi"
Karamar kauye mile 9 kudu da Yerusalem.
AT: "kafa rumfa"
Suleman ya tafi Gibiyon inda bagadi yake a rumfar taruwa.
AT: "an gama" ko "ƙarasawa"
AT: "yawan mutanen da baza a iya ƙirgawa ba" (Duba: da figss_hyperbole)
AT: "babu wanda zai iya yiwa mutanenka hukunci"
"a gaban wurin rumfar taruwa"
Wannan na magana ne a kan biranen da ke ajiye karusai .
AT: "ƙarafuna masu yawa da kuma daraja waɖanda ba safai ake samunsu ba"
AT: "itatuwa masu yawa da daraja "
1Suleman kuma ya bada umarni domin ginin gida saboda sunan Yahweh da kuma gina fãda domin masarautarsa.2Suleman yasa mutune dubu saba'in su kwaso kayayyaki, mutane dubu tamanin masu saran duwatsu a cikin tsaunuka, da kuma mutane dubu 3,600 su dinga kula da su.3Suleman ya aika da saƙo zuwa sarki Hiram na Taya cewa "Kamar yadda ka yi ga mahaifina Dauda, kana aiko masa da itacen sida domin ya gina gidan da zai zauna, to sai kayi mani haka.4Duba ina gab da gina gida saboda sunan Yahweh Allahna, in keɓe shi dominsa, in ƙona turare mai ƙamshi a gabansa, in kuma kawo gurasa ta kasancewarsa da kuma hadaya ta ƙonawa safe da yamma, da ranakun asabarci da sabobbin watanni, da kuma ayyanannun bukukuwa domin Yahweh Allahnmu. Wannan na har abada ne, domin Isra'ila.5Gidan da zan gina zai zama da girma sosai, domin Allahnmu mai girma ne fiye da dukkan wasu alloli.6Amma wane ne zai iya gina gida domin Allah, da yake duniya da dukkan sammai da kansu basu ishe shi ba? Wane ni da zan gina masa gida, ba sai dai kawai in ƙona masa hadaya ba?7To sai ka aiko mani da mutum da ya ƙware a aikin zinariya, azurfa, tagulla, jan ƙarfe, da shunayya, da ja, da shuɗin u'lu, mutum wanda ya iya dukkan ingantattatu sassaƙa. Zai kasance tare da ƙwararrun mutane waɗanda ke tare da ni a Yahuda da Yerusalem, wanda Dauda mahaifina ya yi tanadi.8Ka aiko mani da itacen sida dana sifires da algun daga Lebanon. Duba barorina zasu tafi tare da barorinka,9domin a samar da katakai sosai, domin gidan da nake shirin ginawa zai zama babba da kuma ban mamaki.10Duba zan ba barorinka mutanen da zasu saro katakan, da kuma awo dubu ashirin na niƙaƙƙiyar alkama, da awo dubu ashirin na sha'ir, da salkunan ruwan inabi dubu ashirin, da kuma santulan mai guda dubu ashirin."11Sai Hiram, sarkin Taya ya amsa a rubuce ya aika wa Suleman: "Saboda Yahweh yana ƙaunar mutanensa, sai ya naɗa ka sarki a kansu."12Bugu da ƙari Hiram yace, "Albarka ta tabbata ga Yahweh, Allah na Isra'ila, wanda ya hallici sama da duniya, wanda ya ba sarki Dauda ɗa mai hikima, da baiwa da kirki da fahimi, wanda zai gina gida domin Yahweh, da kuma fãda domin kansa.13Yanzu na aiko da mutum mai fasaha, da baiwa da fahimi, shi ne Huram-Abi.14Shi ɗan wata mata ne a cikin 'ya'yan Dan. Mahaifinsa ya zo ne daga Taya. Shi ƙwararre ne a aikin zinariya da azurfa, da tagulla, da baƙin ƙarfe, da duwatsu, da katakai, da shunayya, da shuɗi, da jan ulu, da lilin mai kyau. Hakannan kuma ƙwararre ne a fannin kowacce irin sassaƙa da zãne. Sai a samar masa wuri a cikin mutanenka ƙwararru da keyi maka aiki, da kuma na shugabana, Dauda, mahaifinka.15Yanzu kuma da alkama da riɗi, da maida ruwan inabi, wanda shugabana ya yi magana, sai ya aiko da waɗannan abubuwan ga bayinsa.16Zamu saro katako daga Lebanon, gwargwadon yawan katakon da kake bukata. Zamu kawo maka har zuwa tekun Yoffa, sai ka ɗauke su zuwa Yerusalem."17Suleman ya ƙirga dukkan baƙi da kea ƙasar Isra'ila, ya bi irin fasahar da Dauda mahaifinsa ya mora, ya ƙirga su aka sami mutum 153,600.18Yasa dubu saba'in daga cikinsu su suke ɗaukar kaya, dubu tamanin kuma masu saro katako a kan duwatsu, sai 3,600 su zama masu duba aikin da kuma sa mutanen suyi aikin
Wannan na magana ne a kan gurasa 12 da aka sa a gaban ɓagaɗi
Lokacin bukukuwa da ya zo daidai da sabon wata.
Ya nuna cewa Allahnmu mai girma ne fiye da sauran alolli.
AT: "babu wanda zai iya gina gida wa Allah domin babu abinda zai ishe shi? Ni ba komai bane! Sai dai mutumin da zai yi masa hadaya.
Wannan ne irin itacen da wata ƙila ake amfani da shi a ƙera kayan kiɗe-kiɗe.
Wannan shi ne, garin alƙama.
AT: "bada baiwar hankali"
AT: "wuri don kansa"
AT: 'yan kasashen waje, 153,600 ne"
1Sai Suleman ya fara gina gidan Yahweh a Yerusalem akan Tsaunin Moriya, inda Yahweh ya bayyana ga Dauda mahaifinsa. Ya shirya wurin da Dauda ya tsara dominsa, a masussukar Ornan na Yebusiya.2Ya fara ginin a rana ta biyu ta watan, a shekara ta huɗu ta mulkinsa.3Wannan shi ne fasalin ginshiƙin da Suleman ya kafa domin gidan Allah. ya yi amfani da tsohon salon awo, tsawonsa kamu sittin ne, sai faɗinsa kamu ashirin ne.4Awon harabar daga gaban gidan ya kai kamu ashirin, dai-dai da faɗin ginin. Tsayinsa kuma kamu ashirin ne, Suleman kuma ya dalaye cikin ginin da tsantsar zinariya.5ya yi wa rufin ainihin cikin harabar ado da sifires, waɗanda ya dalaye da zinariya mai kyau, waɗanda ya sassaƙa da itatuwan dabino da sarƙoƙi.6ya yi wa gidan ado da duwatsu masu daraja; zinariyar an samo ta ne daga Farbayim.7Hakannan ya yi daɓen ƙasa da bango, da ƙofofin da zinariya; da sassaƙaƙƙun kerubim a jikin bangayensa.8Ya gina wuri mafi tsarki. Tsawonsa ya kai awo ashirin dai-dai da faɗin ginin, haka kuma faɗin gidan shi ma kamu ashirin ne. Ya shafe shi da tsantsar zinariya dai-dai da yawan talanti dubu ɗari shida.9Nauyin awon ƙusa ya kai awo hamsin na zinariya. Ya shafe shi har sama da zinariya.10Ya yi siffofin kerubim guda biyu domin wuri mafi tsarki; masu aikin sassaƙa suka dalaye su da zinariya.11Faɗin fuka-fukan kerubobin kamu ashirin ne tsawonsu gaba ɗaya; Fuffuken kerub ɗin ya kai awo biyar a tsawo, wanda ya kai har bangon ɗakin; shi ma ɗaya fuffuken kamu biyar ne, yana taɓa fuffuken ɗaya kerub ɗin na farko.12Fuffuken ɗaya kerub ɗin ma kamu biyar ne, ya kai har bangon ɗakin; ɗayan fuffuken ma kamu biyar ne, yana taɓa fuffuken kerub na farko.13Fuka-fukan waɗannan kerubobin sun kai faɗin awo ashirin. Kerubobin suka tsaya kan ƙafafunsu, fuskokinsu na fuskantar babban ɗakin taron.14Ya mayar da labulen shuɗi, da shunayya, da jan ulu, ya sassaƙa zãnen kerubobi a kansa.15Hakannan Suleman ya kafa ginshiƙai guda biyu kowanne tsawonsa ya kai kamu talatin da biyar a tsawo, domin a gaban, abubuwan da kekansu sun kai kamu biyar na tsawo.16Ya yi sarƙoƙi domin ginshiƙan ya kuma dora su a kansu; hakannan yasa turaren ƙanshi ya haɗa su a jikin sarƙar.17Ya kafa ginshiƙan a gaban haikalin, ɗaya daga hannun hagu, ɗaya kuma daga hannun dama, yasa wa ginshiƙan hannun dama suna Yakin, na hannun hagun kuma Bo'aza.
Wannan ne Ibrahim ya bada ɗansa, Ishaku, ga Allah.
"60 ... 20"
Kamu 46 ne.
"yayi"
Wannan na bayyana harabar babban ɗaki.
Duwatsu masu daraja, masu kyau daake anfani da shi domin ado.
Kalmar da ke nufin yamma.
Wasu sun fassara wannan da cewa yana nufin tsifar kerubim da aka yarda shi a ƙarfe.
AT: yadi mai daraja" ko "ƙyaƙkyawan yadi"
1Hakanan ya yi bagadi na tagulla; tsawonsa kamu hamsin ne, faɗinsa kuma kamu ashirin ne, tsawonsa kuma goma ne.2Hakannan ya yi wani kewayayyen tafki na ƙarfe, kamu goma daga baki zuwa baki. Tsawonsa kamu biyar ne, tafkin kuma a kewaye kamu talatin ne.3A ƙarƙashin bakin tafkin akwai bijimai kewaye, kowanne awo goma, aka yi zuɓin ɗaya tare da tafkin sa'ad da aka yi zuɓin tafkin kansa.4Babban madatsar da ake kira "Tafkin" aka ɗora shi bisa bijimai goma sha biyu, uku na fuskantar arewa, uku yamma, uku kudu, uku kuma gabas. Aka ɗora "Tafkin" a bisansu kuma gadon bayansu na fuskantar ciki.5"Bangajin" ya yi kaurin damtsen hannu, kuma aka goge bakinsa kamar bakin kofi, kamar buɗewar fure. "Tafkin" yana ɗaukar kimanin garwa dubu uku ta ruwa.6Hakannan ya yi tafkuna goma domin wankin abubuwa; yasa biyar daga ɓangaren kudu, biyar kuma daga arewa; za a dinga wanke kayayyakin miƙa baiko na ƙonawa a cikinsu. Babban madatsar da aka fi sani da "Tafki" firistoci ne suke amfani da ita domin wanke-wanke.7ya yi sandunan zinariya na ajiye fitilu guda goma kuma an tsara su ne kamar yadda aka umarta; ya ajiye su a cikin haikali, biyar a hannun dama biyar a hannun hagu.8ya yi tebura goma yasa su a cikin haikalin, biyar a bangon dama, biyar a bangon hagu. Ya yi kwanonin na zinariya guda ɗari.9Bugu da ƙari ya yi harabar firistoci, da babbar haraba da kuma ƙofofi domin harabar ya kuma dalaye ƙofofinsu da tagulla.10Ya ajiye madatsar da aka sani da "Tafki" a gefen gabas na haikalin, daga gabas kuma na haikalin, yana fuskantar kudu.11Huram ya yi tukwanen, cebura na ƙarfe da kwanoni na yayyafa ruwa. Da haka Huram ya kammala aikin da ya yi wa Suleman a cikin gidan Allah:12ginshiƙai guda biyu, gammunan biyu masu fasalin kwano da kebisa ginshiƙin biyu, tsare-tsaren aikin ado biyu da aka yi domin rufe gammunan biyu masu fasalin kwano waɗanda ke bisa ginshiƙan.13Ya kuma yi siffofin ruman guda ɗari huɗu domin suturta waɗannan kayayyakin: ya kawo dozin biyu na kayan kyalli domin a adana bangazan da kekan ginshiƙan.14Hakannan ya yi matokarai domin kawo tafkunan su zauna a matokaran;15tafki ɗaya bijimai sha biyu a ƙarƙashinsa,16Hakannan da tukwanen, da ceburan, cokulan nama masu yatsu, da dukkan sauran kayayyaki da Huram-Abi ya ƙera daga gogaggiyar tagulla domin Sarki Suleman, domin gidan Yahweh.17Sarki ya ajiye su a filin Yodon filin yumɓu tsakanin Sukkot da Zaretan.18Da haka Suleman ya yi dukkan waɗannan kayyayaki cikin babbar yalwa. Hakika ba a san nauyin tagullar da aka yi aiki da ita ba.19Suleman ya yi dukkan kayan ƙawa da kecikin haikalin Allah da kuma bagadi na zinariya, da kuma teburi inda ake ajiye gurasa;20Sandunan ajiye fitilu da fitilun da aka yi domin ƙona hadaya a gaban ɗakin ƙurya - waɗannan anyi su da tsantsar zinariya ne;21Hakannan furannin, da fitilun bangazan, da cokulan da abin ƙona turare duk da zinariya tsantsa, aka yi su.22Haka kuma abin gyara fitilu, da cokula, da bangazai da abin ƙona turare duk da tsantsar zinariya aka yi su. Game kuma da ƙofar gidan, da ƙofofinsu na ciki zuwa wuri mafi tsarki da kuma ƙofofin gidan, dake, na haikalin, duk da zinariya aka yi su.
Wannan shine gefen saman kwano.
AT: "goma a kowanne kamu"
Wannan shi ne centimita takwas
AT: Bakin na da taushi, mai lankwasa baki"
Wannan daruna ne masu zurfi da ake amfani da su ayi wanki.
kwanoni da ake amfani da su a cikin gidan Allah domin yayyafa ruwa a bagadi
AT: "kwanonin"
Wannan babban kwano na ado ne da ake wanki da shi.
sauran kayan aiki ko abubuwa da ake amfani da su a bagadi
Tagulla da ma'aikata suka goge domin ya kasance da haske.
Suleman bai yi waɗannan tasoshin da kansa ba, amma ya bada umurni ne a yi su.
AT: "nauyin tagulla na da girma"
Ma'aikantan Suleman sukan yi abubuwa bisa ga umurninsa.
Dukkan kwanonin da abubuwan da ake amfani da su a gidan Allah.
Duba yadda za fassara wannan a 2:4.
1Bayan Suleman ya kammala waɗannan ayyukan domin gidan Yahweh, Suleman ya kawo kayayyakin da Dauda mahaifinsa ya keɓe saboda wannan dalilin, haɗe da zinariya da azurfa, da dukkan kayayyakin ado - ya ajiye su a ma'ajin gidan Allah.2Daga nan Suleman ya tattaro dukkan dattawan Isra'ila, da dukkan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalai na mutanen Isra'ila, a Yerusalem domin su kawo akwatin alƙawari na Yahweh daga birnin Dauda, wato Sihiyona.3Dukkan mutanen Isra'ila suka tattaru a gaban sarki a wurin bikin, wanda aka yi a wata na bakwai.4Dukkan dattawan Isra'ila suka zo, Lebiyawa kuma suka ɗauko akwatin alƙawari.5Suka kawo akwatin, da rumfar taruwa, da dukkan kayayyakin da kecikin rumfar. Sai firistoci waɗanda ke daga kabilar Lebiyawa suka kawo waɗannan abubuwa6Sarki Suleman da dukkan taron mutanen Isra'ila suka taru a gaban akwatIn, suka yi hadaya da shanu har da ba za'a iya ƙirgawa ba.7Sai firistoci suka kawo akwatin alƙawari na Yahweh a wurinsa, a can ɗaki na ƙurya na gidan, zuwa wuri mafi tsarki, a ƙarƙashin fuka-fukan kerubim.8Domin kerubim sun buɗe fuka-fukansu a kan wurin akwatin sun kuma rufe akwatin da kuma sanduna da aka ɗauko shi da su.9Sandunan suna da tsawo sosai ana ganin ƙarshensu daga wuri mai tsarki a gaban ɗaki na can ciki, amma ba za a iya ganinsu daga waje ba. Suna nan a wurin har ya zuwa yau.10Ba komai a cikin akwatin sai allunan guda biyu da Musa ya saka a Tsaunin Horeb, a lokacin da Yahweh ya ƙulla alƙawari da Isra'ila, bayan sun fito daga Masar.11Sai ya zamana bayan firistoci sun fito daga wuri mai tsarki. Dukkan firistocin da kewurin suka tsarkake kansu ga Yahweh, basu bi tsarinsu na rabe-rabensu ba.12Hakannan Lebiyawa da kemawaƙa, dukkansu har da Asaf da Heman da Yedutun da 'ya'yansu da 'yan'uwansu suka yi ado da kaya masu kyau suna kaɗa molo da garayu, da goge, sarewa, suna tsaye a gabas da bagadin. Tare da su akwai firistoci 120 suna hura kakakai.13Sai ya zamana da masu hura kakakin da mawaƙan suna waƙa tare, suna fitar da murya ɗaya domin yabo da godiya ga Yahweh. Sun tada muryoyinsu da kakakinsu da molonsu da kayan kaɗe-kaɗensu, suka kuma yabi Yahweh. Suka rera waƙa cewa, "Domin shi managarci ne domin alƙawarinsa mai aminci ya tabbata har abada." Daga nan sai gidan, wato gidan Yahweh, ya cika da girgije.14Firistoci basu iya tsayawa suyi hidima ba saboda girgijen, domin daukakar Yahweh ta cika gidan.
Wannan ne wurin da ake ajiye abubuwa ko inda ake tara abubuwa.
Wannan ne Bikin Mafaka da ake yi a ranar shabiyar ga watan bakwai a kalandar Yahudawa. Wannan na kusa da watan goma ne a kalandar Yammaci.
Duba yadda ka fassara wannan a 4:19
AT: "tumaki da shanu masu yawa"
"zuwa wurin da aka shirya masa"
Wannan na nufin zuwa lokacin da aka rubuta littafin tarihi na biyu.
Dukkansu uku suka bida sujada lokacin da Dauda ya mayar da akwatin zuwa Yerusalem. Dauda ya zabe su a matsayin Shugabanan mawaƙa.
AT: "yan'uwansu" ko "jikokinsu"
1Daga nan sai Suleman ya ce"Yahweh ya cezai zauna a cikin duhu baƙi ƙirin,2amma na gina maka wurin zama mai dacewa, wurin da zaka zauna har abada."3Bayan wannan sai sarki ya juya ya albarkaci dukkan taron mutanen Isra'ila a lokacin da taron Isra'ila ke tsaye.4ya ce dãma a yabi Yahweh na Isra'ila, wanda ya yi magana da mahaifina Dauda, ya kuma cika shi da hannunsa, cewa,5'Tun daga ranar dana fito da mutanena daga ƙasar Masar, ban zaɓi wani wuri a cikin dukkan kabilun Isra'ila domin in gina gida saboda sunana a can ba. Ban kuma zaɓi wani mutum ya zama sarkin mutanena Isra'ila ba.6Duk da haka na zaɓi Yerusalem, domin sunana ya kasance a can, na kuma zaɓi Dauda ya zama sarkin mutanena Isra'ila,'7To a cikin zuciyar mahaifina Dauda ya ƙudurta ya gina gida domin Yahweh Allah na Isra'ila.8Amma Yahweh ya cewa Dauda mahaifina in har ka ƙudurta ka gina gida domina ka kyauta daka sa wannan a zuciyarka.9Duk da haka ba kaine zaka gina gidan ba; amma ɗanka ne, wanda zai fito daga tsatsonka, shi ne zai gina gida domin sunana.'10Yahweh ya cika maganar da ya faɗa, domin ina tsayawa a maimakon Dauda mahaifina, na kuma zauna a kan gadon sarautar Isra'ila, kamar yadda Yahweh ya alƙawarta. Na kuma gina gida domin sunan Yahweh, Allah na Isra'ila.11Na ajiye akwatin alƙawari a can, wanda shi ne alƙawarin Yahweh, wanda ya yi da mutanen Isra'ila."12Suleman ya tsaya a gaban bagadi na Yahweh a gaban dukkan taron Isra'ilawa ya buɗe hannuwansa.13Domin ya yi dakali na tagulla, tsawo kamu biyar, fãɗi kamu biyar, bisansa kamu biyar. Ya ajiye shi a tsakiyar harabar haikalin. Ya tsaya a kansa ya kuma durƙusa a gaban dukkan taron Isra'ila, daga nan sai ya buɗe hannuwansa zuwa sammai.14Yace, "Yahweh, Allah na Isra'ila, ba wani Allah kamarka a sama ko a ƙasa, wanda ke cika alƙawari da madawwamiyar ƙauna ga bayinka da suka yi tafiya a gabanka da dukkan zuciyarsu;15kai wanda ka riƙe alƙawari da bawanka Dauda mahaifina, abin daka alƙawarta masa. I, kayi magana da bakinka ka kuma cikata da kanka kamar yadda ya ke a yau.16Yanzu Yahweh, Allah na Isra'ila, sai ka cika abin daka alƙawarta wa bawanka Dauda mahaifina, lokacin da kace 'Baza ka taɓa rasa wani mutun a gabana da zai zauna a kan gadon sarautar Isra'ila ba, in dai zuriyarka suka lura suyi tafiya bisa shari'ata, kamar yadda kayi tafiya a gabana.'17Yanzu, Yahweh, Allah na Isra'ila, ina roƙonka cewa ka tabbatar da alƙawarin da kayi wa bawanka Dauda.18Amma ko Allah zai yi rayuwa da mutum a duniya? duba, duniya ma kanta da sama basu isheka ba, balle kuma wannan haikalin dana gina!19Amma duk da haka ina roƙo ka girmama wannan addu'a ta bawanka, da kuma roƙonsa Yahweh Allahna; ka ji addu'a da kuma kukan da bawanka ke yi a gabanka.20Dama idanunka da kunnuwanka su kasance a buɗe rana da dare ga wannan haikalin. Wurin da kayi alƙawarin sa sunanka. Dama ka saurari addu'ar bayinka da zasu yi a wannan wurin.21To sai ka saurari roƙe-roƙen bawanka da mutanenka Isra'ila a lokacin da suka yi addu'a suna fuskantar wannan wuri. I, ka saurara daga wurin da kake zaune, daga sammai kuma bayan ka saurara, ka yi gafara.22In mutun ya yi laifi gãba da ɗan'uwansa in an bukace shi da ya rantse a gaban bagadinka a wannan gida,23to sai kaji daga sammai ka kuma hukunta bayinka, kayi wa mugu sakaiya, ka kuma ɗora masa hakinsa a kansa. Ka kuma shaida mai adalci mara laifi, ka bashi ladar aikinsa na adalci.24A lokacin da aka ci nasara kan mutanenka Isra'ila ta hannun maƙiya saboda sunyi maka zunubi, in sun juyo wurinka, suka kuma furta sunanka, suka yi addu'a, suka roƙi gafara a gabanka a wannan wuri-25to ina roƙo kaji daga sammai ka gafarta zunubin mutanenka Isra'ila; ka komo da su ƙasar daka basu, su da kakaninsu.26Idan sammai suka rufe kuma aka sami fãri saboda mutane sun yi maka zunubi - in sun yi addu'a suna fuskantar wannan wuri, suka furta sunanka, suka kuma juyo daga zunubinsu bayan ka hore su -27to sai kaji su a sama ka gafarta zunubin bayinka da mutanenka Isra'ila, lokacin daka bi da su ta hanya mai kyau da zasu bi. Ka aiko da ruwan sama a kan ƙasarka, wadda ka ba mutanenka gãdo.28Ko kuma ace ana yunwa a ƙasar, ko kuma akwai cuta, ko annoba, ko darɓa, ko funfuna; ko kuma ace a kwai magafta da suka kawo hari a ƙofofin birnin ƙasar, ko kuma wata masifa ta afko wa ƙasar ko rashin lafiya_29ko kuma ace an yi adduo'i da roƙe-roƙe ta wurin mutum ɗaya ko kuma dukkan mutanenka Isra'ila-ko kuma na sane da annobar da kuma baƙincikin a zuciyarsa lokacin da ya buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali.30sai ka saurara daga sama, a wurin da kake zama; ka gafarta ka kuma sãka wa kowanne mutum gwargwadon aikinsa; ka san zuciyarsa, domin kai kaɗai ne kasan zukatan mutane.31Kayi wannan domin su ji tsoronka, domin suyi tafiya bisa tafarkunka a cikin dukkan kwanakin da suke a wannan ƙasa daka ba kakaninsu.32Game kuma da băƙi da ba mutanenka Isra'ila ba, amma saboda girman sunanka, da hannunka mai iko, da kuma damtsenka daka miƙa - suka zo suka yi addu'a suna fuskantar wannan wuri,33to ina roƙo ka saurara daga sama, wurin da kake zama, ka kuma yi duk abin da băƙin suka roƙe ka, domin dukkan mutanen duniya su san sunanka su kuma ji tsoronka, kamar mutanenka Isra'ila, domin kuma su san wannan gidan dana gina ana kiransa da sunanka.34Ko kuma in mutanenka suka tafi yaƙi gãba da maƙiyansu, ta kowacce hanya da zaka aike su, sai kuma suka yi addu'a gare ka suna fuskantar wannan birni daka zaɓa, suna kuma fuskantar wannan wuri dana gina domin sunanka.35To sai ka saurari addu'arsu da roƙonsu ka taimake su daga sammai.36Ko kuma in sunyi maka zunubi_ tunda ya ke ba wanda baya yin zunub i- ko kuma in kayi fushi da su ka kuma miƙa su ga maƙiya, domin maƙiya su kwashe su su kaisu bauta a ƙasarsu, ko kusa ko nesa.37Daga nan a misali in sun gane cewa suna ƙasar bauta, kuma a misali in sun tuba suka kuma nemi tagomashi daga wurinka a ƙasar da suke bauta. A misali kuma idan suka ce, 'Mun yi wauta mun yi zunubi. Mun yi halin mugunta.'38A misali idan suka juyo gare ka da dukkan zuciyarsu da ransu a ƙasar da suke bauta, inda suka ɗauke su a matsayin bautar talala, a misali kuma in sun yi addu'a suna fuskantar ƙasarsu, wadda ka ba kakaninsu, da kuma birni daka zaɓa, da kuma gidan da na gina domin sunanka.39Daga nan sai kaji addu'oinsu da roƙe-roƙensu ka kuma taimake su, daga sammai a wurin da kake zama ka taimaki al'amarinsu. Ka gafarta wa mutanenka, da suka yi maka zunubi.40Yanzu, Allahna, ina roƙonka, ka buɗe idanunka, ka kuma sa kunnuwanka suji addu'ar da za a yi a wannan wuri.41Yahweh Allah, sai ka tashi daga wurin hutawarka, kai da akwatin ƙarfinka. Yahweh kasa firistocinka su rufa da cetonka, ka kuma sa tsarkakanka suyi murna kan alheranka.42Yahweh Allah, kada ka juyar da fuskar keɓaɓɓunka daga wurinka. Ka tuna da abubuwan daka alƙawarta na yin aminci ga bawanka Dauda."
AT: "wurin zama mafi ɗaukaka"
AT: "a lokacin da mutane ke a tsaye"
shi ya sa ya faru ko ya kuma tabbatar da cikan alkawalinsa.
AT: "Domin sanar da kaina a can"
AT: "abinda Dauda yake so"
Sunnan Yahweh na waƙiltar kassancewarsa.
AT: "a cikin su akwai alunnan dutse wanda yake nuna alkawarin da Yahweh yayi da mutanensa Isra'ila"
AT: "a gaban dukkan taron Isra'ilawa da suka taru a can"
Suleman ya ɗaga hannayensa kuma ya riƙe su a sama yayin da ya durƙusa yayi addu'a.
AT: "mu da muka yi abin da kake so mu yi"
Wannan yana nufin alƙawalin da Allah yayi wa Dauda da cewa ɗansa ne zai gida haikali. AT: "ka cika alƙawalinka."
Wannan roƙo ne. AT: "ka yi"
AT: "ba za ka taɓa rasa wani mutum a gaba na da zai zauna a kan gadon sarautar Isra'ila ba.
AT: "kamar yadda Dauda yayi"
AT: "Amma Allah, ba zai yi rayuwa da mutum a duniya ba"
Duba yadda ka fassara wannan a 2:6.
"Don Allah ka taimake waɗanda lokaci--- rana da dare"
AT: "wurin da kace zaka sa mutane su sanka" (Duba: metonymy)
AT: "bayan ka saurari addu'oin, don Allah ka gafarta masu zunubansu"
AT: "ta wurin horar da shi kamar yadda ya dace"
AT: "don Allah, ka ji addua'arsu"
AT: "ka yi masu alƙawali"
Wannan jumla "sammai suka rufe " na nufin babu ruwan sama da ya sauka daga sama. AT: "Idan baku bar ruwa ya sauko ba."
Da kalmomin bakunansu da ayyukansu, suka ɗaukaka Allah da ikonsa"
AT: "juyo daga muguntarsu"
AT: "bi da su ta hanyar adalci"
Ma'anar mai yiwuwa: "na san da zunubin a zuciyarsa" ko "na san da annobar da kuma baƙin cikin a zuciyarsa sobada zunubi ne"
Duba yadda ka fassara wannan a 6:12
AT: "abubuwan da yayi"
AT: "kai mai girman ne kuma mai iko"
AT: "an san gidan da sunan Yahweh, malakarka"
AT: "Mutanen sun yi gini a ƙarƙashin shugabanci na"
Duba:
maƙiya su ka kwashe suka su kaisu bauta a ƙasar maƙiyansu
Wannan na nufin Isra'ila ne. AT: "sun yi addu'a suna fuskantar ƙasarsu da ka ba wa kakaninsu"
1Da Suleman ya gama addu'a sai wuta ta sauko daga sama ta cinye baye-baye na ƙonawa da hadayu, sai ɗaukakar Yahweh ta cika gidan.2Firistoci basu iya samun damar shiga gidan Yahweh ba, saboda ɗaukakarsa ta cika gidansa.3Duk mutanen Isra'ila sun ga yadda wutar tazo daga sama ɗaukakar Yahweh kuma ta sauko a kan gidan, sai suka sunkuyar da kawunansu ƙasa a kan keɓaɓɓen dutse na sujada suka bada godiya ga Yahweh. Suka ce, "Domin shi nagari ne, domin alƙawarin amincinsa ya tabbata har abada."4Sai sarki da dukkan mutanen suka miƙa hadaya ga Yahweh.5Sarki Suleman ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin, da tumaki da awaki 120,000. Sai sarki da dukkan mutanen suka keɓe gidan Allah.6Sai firistoci suka tsaya, kowanne ya tsaya a inda ya ke hidima, hakannan Lebiyawa suna ɗauke da kayan kiɗa na Yahweh, wanda sarki Dauda ya yi domin ya riƙa yin godiya ga Yahweh ta wurin waƙa, "Domin alƙawarin amincinsa ya tabbata har abada." Sai dukkan firistoci suka hura kãkãki a gabansu, kuma sai dukkan Isra'ila suka miƙe tsaye.7Sai Suleman ya keɓe tsakiyar haikalin a gaban gidan Yahweh. A can ya miƙa baye-baye ta ƙonawa da kuma kitse na baye-baye na zumunci, domin wannan bagadi na tagulla da ya yi ya gaza ɗaukar baye-baye na ƙonawa, baye-baye ta hatsi, da kitsen.8Sai Suleman da ya yi bukin a wancan lokacin har na kwana bakwai tare kuma da dukkan Isra'ilawa, babban taro ne tun daga Lebo Hamat har zuwa iyakar Masar.9A rana ta takwas suka yi taron murna domin sun yi taron keɓe bagadi na kwana bakwai.10A rana ta ashirin da uku a wata na bakwai, Suleman ya sallami taron mutanen suka koma gidajensu da murna da farin ciki saboda alheran Yahweh daya nuna ga Dauda da Suleman da kuma Isra'ila, mutanensa.11Da haka Suleman ya kammala gidan Yahweh da kuma gidansa. Duk abin da yazo zuciyar Suleman game da gidan Yahweh da kuma gidansa ya yi su dukka.12Sai Yahweh ya bayyana ga Suleman da dare ya kuma ce da shi, "Na ji addu'arka na kuma zaɓi wannan wurin domin kaina domin ya zama gidan miƙa hadaya.13A misali da ace na rufe sammai domin kada ayi ruwa, ko kuma in umarci fări su cinye ƙasar, ko kuma idan na aiko da cuta cikin mutanena,14To indan mutanena da ake kira da sunana, zasu yi tawali'u su yi addu'a, su biɗi fuskata, su kuma juya daga mugayen hanyoyinsu, to zan ji daga sama, zan kuma gafarta zunubinsu, in kuma warkar da ƙasarsu.15Yanzu idanuna zasu zama a buɗe kunnuwana kuma zasu ji addu'o'in da za ayi a wannan wurin.16Domin yanzu na zaɓa na kuma keɓe wannan gida domin sunana ya kasance a wurin har abada. Idanuna da zuciyata zasu kasance a can kullum.17Kai kuma in zaka yi tafiya a gabana kamar yadda mahaifinka Dauda ya yi, ka kuma yi biyayya da duk abin da na umarce ka ka kuma kiyaye sharuɗana da farillaina,18To zan kafa gadon sarautarka, kamar yadda na faɗa a alƙawarina da Dauda mahaifinka, lokacin da nace, 'Ba za a taɓa rasa wani daga cikin zuriyarka ba wanda zai yi mulki a Isra'ila.'19Amma in ka juya, kayi watsi da farillaina da dokokina dana sa a gabanka, kuma idan ka juya ka bautawa gumaka ka russuna masu,20To zan tunɓuke su daga ƙasar dana basu. Wannan gidan kuma dana keɓe domin kaina zan kawar da shi daga gare ni, zan kuma maida shi abin habaici da ba'a ga dukkan al'ummai.21Koda ya ke wannan haikalin ya ƙayatu yanzu, duk wanda ya wuce ta gefensa zai razana ya yi tsaki. Zasu ce 'Me yasa Yahweh ya yi haka ga wannan gida da kuma wannan ƙasa?'22Sauran zasu amsa suce saboda sun yashe da Yahweh Allahnsu ne, wanda ya fito da kakanninsu daga ƙasar Masar, sai kuma suka kakkafa waɗansu gumaku suka russuna masu suka yi masu sujada. Shi yasa Yahweh ya aukar masu da duk wannan masifa."'
Wannan yanayi ne na addua'a. AT: "sun sunkuyar da kansu tare da fuskokinsu da ke taba gefen duwatsu."
AT: "amincin alƙawalin Allah" ko "Allah yayi alƙawa ya aunaci Isra'ila har abada"
AT: "kowanne ya tsaya a inda aka shirya masa"
AT: "ya gaza ɗaukar baye-baye na ƙonawa masu yawa"
Mutane daga dukkan Isra'ila suka zo.
Wannan babban taro ne na mussamam domin yin ibada.
"ya gama"
AT: "Na saurari addu'arka"
AT: "tsayar da ruwa"
Kalmar nan "ƙasar" yana nufin "dukkan shuke-shuke da amfanin gona.
AT: "nemi Allah" ko "nemi Allah ya saurareka"
Kalman nan "idannun" da "kunne" na nufin Allah wanda ya zaba ya gani ya kuma saurari addua'ar mu. AT: "Idanuna zasu zama a buɗe kuma kunnuwana kuma zasu ji"
"Mai kaunata, maitsaro na, da kariya na"
AT: "In zaka yi biyayya kamar Dauda, mahaifinka, ya yi"
AT: "Zan tunɓuke su daga ƙasar." An kwatantashi da tunɓuke anfanin gona daga jijiya a cikin kasa da tunɓuke mutanen Allah wato Isra'ila daga ƙasa. Sakamaƙon zai zama lalatar da kasar da kuma baƙin cikin mutane.
1Sai ya kasance a karshen shekaru ashirin da Suleman ya gina gidan Yahweh da kuma gidansa,2sai Suleman ya sake gina garuruwan da Hiram ya bayar gare shi, ya kuma zaunar da mutanen Isra'ila a cikinsu.3Sai Suleman ya kai wa Hamatzoba hari ya kuma cinye ta.4Ya gina biranen ajiya a cikin hamada, da dukkan birane ƙayatattu da ya gina a Hamat.5Haka kuma sai ya gina Bet Horon na Sama da Bet Horon na Ƙasa, birane masu tsaro mai ƙarfi tare da katangai, ƙofofi, da ƙyamare.6Ya gina Balat da dukkan biranen ma'aji da ya mallaka, da dukkan biranem domin karusansa da kuma biranen domin mahayansa, kuma ko mene ne ya yi niyar ginawa domin jin daɗinsa a cikin Yerusalem, cikin Lebanon, da kuma cikin dukkan ƙasashen da keƙarƙashin mulkinsa.7Amma game da dukkan mutanen da aka rage na wajen su Hittiyawa, da Amoriyawa, da Feriziyawa, da Hibiyawa, da kuma Yebusiyawa, waɗanda ba daga Isra'ila suke ba,8zuriyarsu da aka bari a bayansu cikin ƙasar, waɗanda mutanen Isra'ila basu hallakar ba - Suleman ya maishe su masu aikin tilas, haka suke har wa yau.9Duk da haka, Suleman bai ɗora wa jama'ar Isra'ila aikin tilas ba. A maimakon haka, suka zama sojojinsa, kwamandojinsa, da hafsoshinsa, da kuma kwamandojin karusan jarumawansa da kuma mahaya dawakansa.10Waɗannan kuma su ne manyan hafsoshin masu tafiyar da al'amuran masu kula waɗanda ke na Sarki Suleman, 250 ne suke, waɗanda suka kula da mutanen da suka yi aiki.11Sai Suleman ya fito da ɗiyar Fir'auna daga birnin Dauda zuwa gidan da ya gina mata, gama yace, "Matata bazata zauna a gidan Dauda sarkin Isra'ila ba, domin duk inda akwatin alƙawarin Yahweh ya shiga mai tsarki ne."12Sai Suleman ya miƙa baye-baye na ƙonawa ga Yahweh a bisa bagadin Yahweh daya gina a gaban Haikalin.13Ya miƙa hadayu kamar yadda ya wajaba cikin shirin kowacce rana; ya miƙa su, yana koyi da yadda aka shimfiɗa su a cikin umurnan Musa, a ranakun Asabaci, sabobbin watanni, da kuma kafaffun bikin sau uku kowacce shekara: Bikin Gurasa Mara Gami, Bikin Mako, da kuma Bikin Bukkoki.14Bisa ga dokokin mahaifinsa Dauda, Suleman ya naɗa ƙungiyoyin firistoci ga aikinsu, Lebiyawa kuma ga matsayinsu, domin suyi yabo ga Allah su kuma yi hidima a gaban firistoci, kamar yadda ya wajaba a kowacce rana. Ya kuma sa matsaran ƙofofi bisa ga tsarinsu a kowacce ƙofa, gama Dauda, mutumin Allah, ya umarta wannan.15Waɗannan mutane basu kauce daga dokokin sarki ga firistoci da Lebiyawa ba game da kowanne al'amari, ko game da ɗakunan ajiya.16Dukkan aikin da Suleman ya umartar aka gama, daga ranar da aka kafa harsashen gidan Yahweh har aka gama shi. Gidan Yahweh ya kammalu.17Sai Suleman ya tafi Eziyon Geba daga nan zuwa Elat a gaɓar teku, a ƙasar Idom.18Sai Hiram ya aika mashi da jirage da hafsoshinsa suka umarta, mazajen da suka ƙware a sha'anin teku, kuma tare da bayin Suleman suka tafi Ofir suka kuma ɗauka daga nan talanti 450 na zinariya suka kawo wurin Sarki Suleman.
AT: "Bayan shekara 20,"
Suleman yana wakiltar duk sojojin yaƙinsa. AT: "Sojojin Sulaiman sun kai hari ma birnin Hamatzoba"
Birane a Siriya
Duba:
AT: "waɗanda suka rage a cikin ƙasar"
"bayi"
Duba yadda ka fassara wannan a 5:9
Duba:
AT: "yadda ya wajaba cikin shirin kowacce rana bisa ga dokan Musa"
"mutane sun bi dokokinsa"
Waɗannan su ne garuruwa tare da bakin Tekun Reeds
"ɗari huɗu da hamsin talanti na zuriya"
1Da sarauniyar Sheba taji game da girman Suleman, sai tazo Yeruslem domin ta gwada shi da tambayoyi masu wuya. Ta zo da doguwar tawaga, tare da raƙuma ɗauke da kayayyakin ƙamshi, zinariya mai yawa, da kuma duwatsu masu daraja dayawa. Da ta iso wurin Suleman, sai ta gaya masa dukkan abin da kecikin zuciyarta.2Suleman ya bata amsar dukkan tambayoyinta; babu komai mai wuya ga Suleman; babu tambayar da bai bada amsar ta ba.3Da sarauniyar Sheba ta ga hikimar Suleman da kuma fãdar da ya gina,4abincin teburinsa, da yanayin zaman bayinsa, aikin bayinsa da kuma tufafinsu, har da masu ba shi abin sha da irin tufafinsu, da kuma baye-baye na ƙonawa daya miƙa a gidan Yahweh, sai kuma babu sauran hanzari a cikinta.5Ta cewa sarkin, "Gaskiya ne, labarin da naji cikin ƙasata game da maganganunka da hikimarka.6Ban yarda da abin da naji ba har sai da nazo nan, kuma da idanuwana na gani. Ko rabi ba a gaya mani ba game hikima da wadatarka! Ka zarce girman da naji game da kai.7Mutanenka masu albarka ne, bayinka kuma waɗanda ke tsayawa gaban ka koyaushe masu albarka ne, domin suna sauraran hikimarka.8Mai albarka ne Yahweh Allahnka, wanda ya ke jin daɗinka, wanda ya ɗora ka a bisa kursiyinsa, ka zama sarki domin Yahweh Allahnka. Domin Allahnka na ƙaunar Isra'ila, domin ya kafa su har abada, ya maishe ka sarki bisansu, domin ka aikata gaskiya da adalci!"9Sai ta ba sarki talanti 120 na zinariya da kayan ƙamshi mai yawa da kuma duwatsu masu daraja. Babu kayan ƙamshi mai yawa haka kamar wannan da sarauniyar Sheba ta ba Sarki Suleman da aka ƙara kawo masa kuma.10Bayin Hiram da bayin Suleman, waɗanda suka kawo zinariya daga Ofir, sun kawo kuma katakon algum da duwatsu masu daraja.11Da katakan algum ɗin, sarki ya yi matakalai na gidan Yahweh da kuma domin fadarsa, har kuma da garayu da molaye domin mawaƙa. Ba a taɓa ganin irin wannan katakon a ƙasar Yahuda ba.12Sarki Suleman ya ba sarauniyar Sheba dukkan abin da ta tambaya; ya bata fiye da abin da ta kawo wa sarki. Sai ta tafi ta koma ƙasarta, ita da bayinta.13Yanzu nauyin zinariyan da yazo wurin Suleman a cikin shekara ɗaya talanti 666 na zinariya ne,14ban da zinariyar da 'yan kasuwa da fatake suka kawo. Dukkan sarakunan Arabiya da gwamnoni a cikin ƙasar suka kawo zinariya da azurfa ga Suleman.15Sarki Suleman ya yi manyan garkuwoyi guda ɗari biyu na bugaggar zinariya. Awo ɗari shida na zinariya ne ya shiga kowacce ɗaya.16Ya kuma yi garkuwoyi na bugaggar zinariya guda ɗari uku. Minas uku na zinariya ne ya shiga kowacce garkuwa; sarki ya ajiye su a cikin Gida na Jejin Lebanon.17Sa'an nan sarki ya gina babban kursiyi na hauren giwa ya kuma dalaye ta da zinariya mafi kyau.18Da akwai matakalai guda shida na hawan kursiyin, kuma da kujeran ɗora ƙafa harɗe da mazamnin sarautar. A kowanne ɓangaren kursiyin akwai abin ɗora hannu da zakuna biyu tsaye kusa da kowannen su.19Zakuna goma sha biyu suna tsaye a matakalun, ɗaya a kowanne gefe na matakalai shidan. Babu wata masarautar da keda irin wannan kursiyin.20Dukkan abubuwan shan ruwan Sarki Suleman na zinare ne, kuma dukkan moɗayen shan ruwa da kea Gida na Jejin Lebanon duk na zallar zinare ne. Babu wadda suke daga azurfa domin azurfa ba abin daraja bane a kwanakin Suleman.21Sarkin yana da jiragen ruwa masu tafiya cikin teku, tare da jiragen na Hiram. Sau ɗaya a shekara uku jiragen sukan tafi su kawo zinariya, azurfa, da kuma hauren giwa, da manyan birai, da ɗawisu.22Saboda haka sarki Suleman yafi dukkan sarakunan duniya arziki da kuma hikima.23Dukkan sarakunan duniya suka nemi su ga Suleman domin su saurari hikimarsa, wadda Allah yasa cikin zuciyarsa.24Waɗanda suka kawo ziyara suka zo masa da kyautai, kayayyaki na azurfa dana zinariya, riguna, kayan yaƙi, da kayan ƙanshi, da kuma dawakai da alfadarai, shekara bayan shekara.25Suleman yana da ɗakunan dawakai har dubu huɗu da karusai, da mahayan dawakai dubu sha biyu, waɗanda ya sanya su cikin birnin karusai tare da shi kuma a cikin Yerusalem.26ya yi mulki bisa dukkan sarakuna daga Kogin Yufiretis zuwa ƙasar Filistiyawa, zuwa iyakar Masar.27Sarkin yana da azurfa cikin Yerusalem, yawansu kamar duwatsun ƙasa. Ya maida itacen sida kamar itacen durumi mai yawa da suke ƙauyuka.28Aka kawo wa Suleman dawakai daga Masar da kuma daga dukkan ƙasashe.29Game da waɗansu batutuwa game da Suleman, farko da ƙarshe, ba an rubuta su cikin Tarihi na Nathan annabi ba, cikin Annabci Ahiya Ba-shiloni, kuma a cikin Wahayin Iddo Mai duba (wanda ya sami labari game da Yerobowam ɗan Nebat)?30Suleman ya yi mulki cikin Yerusalem bisa dukkan Isra'ila har shekara arba'in.31Ya yi barci tare da kakanninsa kuma mutanen suka binne shi a cikin birnin Dauda mahaifinsa. Rehobowam, ɗansa, ya zama sarki a madadinsa.
Sheba ta ga komai na Suleman
Waɗannan masu hidima ne dake shan ruwa kafin a ba wa sarki don gudun kada sarki ya sha guba.
"babu girman kai a cikinta kuma"
AT: "yanzu na gani wa kai na"
AT: "Kana da hikima da wadata sossai"
AT: "waɗanda ke tsayawa gaban ka koyaushe domin karɓan umurni"
AT: " wanda ya ke jin daɗinka"
Wurin zinariya da ba a sani ba.
Wannan shi irin itace ne.
"An yi su da awo ɗari shida na zinariya"
Wannan wani suna ne na haƙora ko ƙahon dabba kamar giwa da wasu manyan dabba, kamar giwa ko karkanda.
AT: "saman kursiyin na a zagaye a bayan inda sarki ke zama"
Azurfa ba abin daraja bane a kwanakin Suleman har ma yana da daraja kaɗan.
Dabbobi daga nesa, mai yiwuwa a Afirika.
AT: "wanda Allah yaba shi"
AT: "kowanne shekara"
Duba:
Wannan ƙananan ɗakunan ne inda ake ajiya dawaki.
AT: "azurfa masu yawa"
AT: "mai yawa sosai"
AT: "daga dukkan wurare" "ko "daga ko'ina"
Waɗannan rubuce-rubucen da ba zama.
Shilo shi ne sunan mai mutane kungiyar.
AT: "ya rasu"
1Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukkan Isra'ila na zuwa Shekem domin a naɗa shi sarki.2Da Yerobowam ɗan Nebat ya ji wannan (domin yana cikin Masar, inda ya guje wa sarki Suleman), sai ya dawo daga Masar.3Sai suka aika aka kirawo shi, kuma Yerobowam da dukkan Isra'ila suka zo; suka yi magana da Rehobowam suka kuma ce,4"Mahaifinka yasa karkiyarmu da wuya. Yanzu kuwa, kasa aikin mahaifinka mai wuya ya zama da sauƙi, ka kuma sauƙaƙa karkiya mai nauyin da ya ɗora mana, mu kuma mu bauta maka."5Sai Rehobowam yace masu, "Ku komo gare ni bayan kwana uku." Sai mutanen suka tafi.6Sai sarki Rehobowam ya nemi shawara a wurin dattawa waɗanda suka tsaya a gaban Suleman mahaifinsa sa'ad da ya ke raye; yace, "Ta yaya zaku shawarce ni in bada amsa ga waɗannan mutanen?"7Suka yi magana da shi suka ce, "Idan kayi alheri ga waɗannan mutanen ka kuma kyauta masu, ka kuma faɗi masu maganganun alheri, sa'annan zasu zama bayin ka koyaushe."8Amma Rehobowam ya yi watsi da shawarar da dattawan suka bashi, amma ya nemi shawara daga matasa waɗanda suka girma tare dashi, waɗanda suka tsaya gabansa.9Yace masu, "Wacce shawara zaku bani, domin mu amsa ma mutanen da suka yi magana da ni suka ce, 'Ka rage mana nauyin karkiyar da mahaifinka ya ɗora mana'?"10Samarin da suka yi girma tare da Yerobowam suka yi magana dashi, cewa, "Ga yadda zaka yi magana da mutanen da suka ce maka mahaifinka Suleman yasa ƙarkiyarsu tayi nauyi, amma wai dole kasa ta zama da sauƙi. Ga abin da zaka ce masu, 'Ɗan ƙaramin yatsana yafi ƙugun mahaifina kauri.11Don haka yanzu, ko da ya ke mahaifina ya tsananta maku da karkiya mai nauyi, ni zan daɗa bisa karkiyarku. Mahaifina ya hore ku da bulala, amma ni zan hore ku da kunnamai."12Sai Yerobowam da dukkan mutanen suka zo wurin Rehobowam a rana ta uku, kamar yadda sarki ya faɗi, "Ku dawo wurina a rana ta uku."13Sai Rehobowam ya yi masu magana da zafi, ya yi banza da shawarar dattawan.14ya yi masu magana bisa ga shawarar Samarin, cewa, "Mahaifina yasa ƙarkiyarku tayi nauyi, amma zan daɗa bisanta. Mahaifina ya yi maku horo da bulala, amma ni zanyi maku horo da kunamai."15Sarki kuwa bai saurari mutanen ba, gama al'amari ne wadda ke faruwa yadda Allah ya shirya, domin Yahweh ya aiwatar da maganarsa wadda Ahiya Bashilone ya faɗi ga Yerobowam ɗan Nebat.16Lokacin da dukkan Isra'ila suka ga cewa sarki bai saurare su ba, sai mutanen suka amsa masa suka ce, "Wanne rabo muke da shi a cikin Dauda? Bamu da gãdo a cikin ɗan Yesse! Kowannenku ya koma ga rumfarsa, Isra'ila. Yanzu ka kula da naka gidan, Dauda." Sai dukkan Isra'ila suka koma rumfunansu.17Amma game da mutanen Isra'ila waɗanda ke zaune cikin biranen Yahuda, Rehobowam ya yi mulki bisansu.18Sai sarki Rehobowam ya aiki Adoniram, wanda ke lura da aikin tilas, amma mutanen suka jejjefe shi da duwatsu har ya mutu. Sarki Rehobowam ya tsere da sauri cikin karusansa zuwa Yerusalem.19Don haka Isra'ila ke tayarwa gãba da gidan Dauda har wa yau.
"dukkan mutanen al'ummar Isra'ila"
AT: "Rehobowam bai bi shawarar ba"
"Samari" ya nuna rashin hikimarsu da sani idan an kwatantasu da tsofoffi da suka shawarci Suleman.
Rehobowam ya nuna cewa yafi mahaifisa zafi
AT: "amma zan hore ku da bulala da ke da bakin karfe"
AT: "dukkan shugabannai"
"Bamu son wani abu ya haɗa mu da waɗannan jikokin sarki Dauda!"
Wannan sunan mutum ne.
Duba yadda zaka fassara a wannan a 2 Chron. 5:9
1Da Rehobowam ya isa Yerusalem, ya tattaro gidan Yahuda da Benyamin, 180,000 zaɓaɓɓun mutane waɗanda suke sojoji, suyi yaƙi gãba da Isra'ila, su maido da masarautar ga Rehobowam.2Amma maganar Yahweh tazo wa Shamayya mutumin Allah, cewa,3"Ka cewa Rehobowan ɗan Suleman, sarkin Yahuda, da dukkan Isra'ila cikin Yahuda da Benyamin,4Yahweh ya faɗi wannan, "Kada ku kai hari ko kuyi yaƙi gãba da 'yan'uwanku. Kowanne dole ya koma ga nasa gidan, domin na sanya wannan ya faru."'" Sai suka yi biyayya da maganganun Yahweh suka kuma juya baya daga harin Yerobowam.5Rehobowam ya zauna cikin Yerusalem ya kuma gina birane domin tsaro.6Ya gina Betlehem, Itam, Tekoya,7Betzur, Soko, Adullam,8Gat, Maresa, Zif,9Adorayim, Lakish, Azeka,10Zora, Ayyalon, da kuma Hebron. Waɗannan tsararrun birane ne cikin Yahuda da Benyamin.11Ya ƙarfafa wuraren tsaronsu ya sanya ofisoshi a cikinsu, tare da tanadin abinci, da mai, da inabi.12Ya sanya garkuwoyi da mãsu a cikin dukkan biranen ya kuma maida su masu ƙarfi sosai. Haka Yahuda da Benyamin suka zama nasa.13Firistoci da Lebiyawa daga cikin dukkan Isra'ila suka ƙetara zuwa gare shi daga cikin kan iyakokinsu.14Domin Lebiyawan suka bar gonakinsu na noma da kiwo da kaddarorinsu domin su zo Yahuda da Yerusalem, domin Yerobowam da 'ya'yansa maza sun kore su, don kada su sake aiwatar da ayyukan firistoci domin Yahweh.15Yerobowam ya naɗa wa kansa firistoci domin wuraren masujadai da kuma gumakan akuya da na maraƙi da ya yi.16Mutane daga dukkan kabilun Isra'ila suka biyo shi, waɗanda suka tsaida zukatansu su biɗi Yahweh, Allah na Isra'ila; suka zo Yerusalem suyi hadaya ga Yahweh. Allahn Ubanninsu.17Sai suka ƙarfafa masarautar Yahuda suka kuma sa Rehobowam ɗan Suleman ya yi ƙarfi lokacin shekaru uku, suka kuma yi tafiya shekaru uku cikin hanyar Dauda da Suleman.18Rehobowam ya ɗaukar wa kansa mata: Mahalat, ɗiyar Yerimot, ɗan Dauda, da Abihayil, ɗiyar Eliyab, ɗan Yesse.19Ta haifa masa 'ya'ya maza: Yewush, Shemariya, da Zaham.20Bayan Mahalat, Rehobowam ya ɗauki Ma'aka, ɗiyar Absalom; ta haifa masa Abiya, Attai, Ziza, da Shelomit.21Rehobowam yana ƙaunar Ma'aka, ɗiyar Absalom, fiye da dukkan matansa da ƙwaraƙwaransa (ya ɗauki mata sha takwas da ƙwaraƙwarai sittin, ya kuma zama mahaifin 'ya'ya maza ashirin da takwas da 'ya'ya mata sittin).22Rehobowam ya naɗa Abiya ɗan Ma'aka ya zama basarake, shugaba a tsakanin 'yan'uwansa; yana tunanin maida shi sarki.23Rehobowam ya yi mulki da hikima; ya baza dukkan 'ya'yansa maza cikin dukkan ƙasar Yahuda da Benyamin zuwa kowanne tsararren birni. Ya kuma basu abinci a yalwace ya kuma nemo mataye da yawa domin su.
AT: "zaɓaɓɓun sojojinsa"
AT: "Yahweh yayi magana"
Rehobowam yayi mulkin yankunan Yahuda da Benyamin.
AT: "Firistoci da Lebiyawa sun gudu zuwa Isra'ila, masarautar arewa zuwa Yahuda"
Ƙasar da ake amfani wa dabbobi.
Mutane daga ƙabilar da ke arewancin da ke bauta wa Ubangiji sun gudu zuwa Yahuda.
AT: "da ke bauta wa Yahweh"
AT: "suka kuma yi tafiya cikin hanyar Dauda da Suleman tsawon shekaru uku"
Duba:
Duba:
Duba:
1Sai ya kasance, da mulkin Rehobowam ya kafu ya kuma yi ƙarfi, sai ya watsar da shari'ar Yahweh - da dukkan Isra'ila tare da shi.2Ya faru a shekara ta biyar na sarki Rehobowam, Shishak, sarkin Masar, yazo gãba da Yerusalem, saboda mutanen sun yi rashin aminci ga Yahweh.3Yazo da karusai ɗari sha biyu da mahaya dawakai dubu sittin. Sojoji babu iyaka suka zo tare da shi daga Masar: Libiyawa, Sukkiyawa, da Kushiyawa.4Ya ƙwaci tsararrun birane da kena Yahuda ya kuma zo Yerusalem.5Yanzu Shemayya annabi yazo wurin Rehobowam da shugabannin Yahuda da suka tattaru tare a Yerusalem saboda Shishak. Shemayya yace masu, "Wannan ne abin da Yahweh ya faɗa: Kun yashe ni, don haka nima na bayar daku cikin hannun Shishak."6Daga nan shugabannin Isra'ila da sarki suka ƙasƙantar da kansu suka kuma ce, "Yahweh mai adalci ne."7Da Yahweh yaga cewa sun ƙasƙantar da kansu, maganar Yahweh tazo ga Shemayya, cewa, "Sun ƙasƙantar da kansu. Ba zan rusa su ba; zan ƙubutar da su na wani matsayi, fushina kuma ba zai zubo bisa Yerusalem ta hannun Shishak ba.8Duk da haka, zasu zama bayinsa, domin su fahimci bambanci tsakanin yi mani bauta da kuma bauta wa shugabannin sauran ƙasashen."9Sai Shishak sarkin Masar yazo gãba da Yerusalem ya kuma ɗauke taskokin cikin gidan Yahweh, da taskokin cikin gidan sarki. Ya ɗauke komai da komai; ya ɗauke garkuwoyi ta zinariya da Suleman ya yi.10Sarki Rehobowam ya yi garkuwoyi na tagulla a mamadinsu ya miƙa su kuma cikin hannuwan ofisoshin tsaro, waɗanda ke tsaron ƙofofin zuwa gidan sarki.11Sai ya kasance duk sa'ad da sarki ya shiga gidan Yahweh, matsaran zasu ɗauke su; daga nan zasu maido da su cikin gidan tsaro.12Da Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, fushin Yahweh ya juya daga gare shi, domin kada a lalatar da shi ɗungun; baya da haka, akwai sauran wasu abubuwan nagarta da ake samu cikin Yahuda.13Sai sarki Rehobowam yasa sarautarsa tayi ƙarfi a Yerusalem, haka kuma ya yi mulki. Rehobowam na da shekaru arba'in da ɗaya sa'ad da ya fara mulki, ya kuma yi mulki shekaru sha bakwai a Yerusalem, birnin da Yahweh ya zaɓa daga dukkan kabilun Isra'ila saboda yasa sunansa a wurin. Sunan mahaifiyarsa Na'ama, Ba'ammoniya.14Ya aikata abin da ke mugunta, saboda bai kafa zuciyarsa ba domin ya biɗi Yahweh.15Sauran al'amura kuwa game da Rehobowam, farko da ƙarshe, ba a rubuce suke ba a cikin rubuce-rubucen Shemayya annabi da Iddo mai dubawa, waɗanda kuma suke da lissafe - lissafen asaloli da ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam?16Rehobowam ya yi barci da kakanninsa aka kuma binne shi cikin birnin Dauda; Abiya ɗansa ya zama sarki a gurbinsa.
"Sai ya kasance" alama ne da ke nuna muhimmin abu na musamman a cikin labari. AT: A daidai lokacin da ya faru.
AT: "da dukkan Isra'ila da Yahuda sun bi shi a zunubinsa". Isra'ila kuma ta kumshi Yahuda a nan. (Duba: )
Duba:
AT: "zuwa kawo hari"
AT: "sojoji da yawa"
Duba:
AT: "na bayar daku domin bauta a cikin hannun Shishak" (Duba: )
AT: "sarki da wasu shugabanai na Isra'ila sun kaskantar da kansu. Sarki da sauran shugabanai na wakiltar dukan mutanen Isra'ila.
""Yahweh yayi maganar." Duba yadda ka fassara wannan a 11:2.
AT: "zan ƙubutar da su daga hallaka"
AT: "Ba zan yi fushi da Yerusalem ba"
AT: "miƙa su kuma cikin hannuwan kwamandoji"
AT: Yahweh waya fushi da shi kuma, don haka, bai hallaka shi gabaki ɗaya ba"
"bugu da kari"
AT: "saboda a martabashi ko yaushe a can "
AT: "ba shi da muradi da ƙarfi ya yi biyayya ga Allah"
AT: "Rehobowam ya rasu"
AT: "ya zama sarki maikakon Rehobowam"
1A cikin shekara ta sha takwas ta sarki Yerobowam, Abiya ya fara mulki bisa Yahuda.2ya yi mulki shekaru uku a Yerusalem; sunan mahaifiyarsa Ma'aka, ɗiyar Yuriyel na Gibiya. Aka yi yaƙi tsakanin Abiya da Yerobowam.3Abiya ya tafi cikin yaƙin da mayaƙa ƙarfafa, sojoji masu ƙarfin hali, zaɓaɓɓun mutane 400,000. Yerobowam yaja dagar yaƙi gãba da shi tare da zaɓaɓɓun mutane 800,000, ƙarfafa, sojoji masu ƙarfin hali.4Abiya ya tsaya a tsaunin Zemarayim, wanda ke ƙasar tudu ta Ifraim, ya kuma ce, "Ku saurare ni, Yerobowam da dukkan Isra'ila!5Baku san cewa Yahweh, Allah na Isra'ila, ya bayar da mulki bisa Isra'ila ga Dauda ba har abada, gare shi da 'ya'yansa bisa tsararren alƙawari?6Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, bawan Suleman ɗan Dauda, ya tashi da tawaye gãba da ubangijinsa.7Mutane marasa amfani, ƙasƙantattun jama'a, suka tattaru gare shi. Sun zo gãba da Rehobowam ɗan Suleman, duk da cewa Rehobowam yaro ne kuma bai da ƙwarewa kuma ba zai iya tsayayya da su ba.8Yanzu kunce wai zaku iya ƙin ikon mulkin Yahweh cikin hannun zuriyar Dauda. Ku mayaƙa ne masu yawa, tare daku kuma akwai maruƙan zinariya da Yerobowam ya yi a matsayin alloli dominku.9Ba ku kuka kori firistocin Yahweh, zuriyar Haruna, da Lebiyawa ba? Ba kun naɗa wa kanku firistoci bisa ga ɗabi'ar mutanen sauran ƙasashe ba? Duk wanda yazo ya keɓe kansa da ɗan maraƙi da raguna bakwai zai zama firist na abubuwan da ba alloli ba.10Amma mu kam, Yahweh ne Allahnmu, kuma bamu yashe shi ba. Muna da firistoci, zuriyar Haruna, suna bautar Yahweh, da Lebiyawa, waɗanda ke kan aikinsu.11Kowacce safiya da maraice suna ƙona wa Yahweh baye-baye na ƙonawa da turaren ƙamshi. Suna kuma shirya gurasar miƙawa a bisa tsastsarkan teburi; suna kuma lura da mazaunin fitila na zinariya tare da fitilunsu, domin su riƙa ci kowacce safiya. Muna kiyaye dokokin Yahweh, Allahnmu, amma kun yashe shi.12Duba, Allah yana tare da mu a bisa kanmu, kuma firistocinsa suna nan tare da kãkãki domin su busa ƙara gãba daku. Mutanen Isra'ila, kada kuyi faɗa gãba da Yahweh, Allah na kakanninku, domin baza kuyi nasara ba."13Amma Yerobowam ya shirya kwanto a bayansu; mayaƙansa suna gaban Yahuda, masu kwanton kuma a bayansu.14Da Yahuda suka waiga baya, duba, yaƙin yana gabansu kuma yana bayansu. Suka yi kuka ga Yahweh, firistocin kuma suka busa kãkãki.15Dagana mutanen Yahuda suka yi kuwwa; yayin da suka yi kuwwar, sai Allah ya mazge Yerobowam da dukkan Isra'ila a gaban Abiya da Yahuda.16Mutanen Isra'ila suka guje daga gaban Yahuda, Allah kuma ya bayar da su cikin hannun Yahuda.17Abiya da mayaƙansa suka kashe su da babban yanka; zaɓaɓɓun mutane 500,000 na Isra'ila suka fãɗi matattu.18Ta wannan hanya, mutanen Isra'ila aka kayar da su a wannan lokaci; mutanen Yahuda suka yi nasara saboda sun dogara ga Yahweh, Allah na kakanninsu.19Ya runtumi Yerobowam; Ya ɗauke birane daga gare shi: Betel da kauyukanta, Yeshana da ƙauyukanta, da Efron da ƙauyukanta.20Yerobowam bai taɓa sake samun iko ba a lokacin kwanakin Abiya; Yahweh ya buge shi, kuma ya mutu.21Amma Abiya ya zama cike da iko; ya ɗaukar wa kansa mata sha huɗu ya kuma zama mahaifin 'ya'ya maza ashirin da biyu da 'ya'ya mata sha shida.22Sauran ayyukan da Abiya ya aiwatar, ɗabi'arsa da maganganunsa an rubuta a cikin taƙaitaccen labarin Annabi Iddo.
"Maka'iya" sunan mace ce. "Yuriyel" sunan mutum ne.
AT:"Aka yi yaƙi tsakanin sojojin Abiya da sojojin Yerobowam"
"Dubu ɗari huɗu zaɓaɓɓun mutane ... dubu ɗari takwas zaɓaɓɓun mutane"
Wannan sunan wurin ne.
AT: "Ka sani sosai ... alƙawari"
AT: "masu ƙarban rashawa, ƙazantatu mutane"
"tare da Yerobowam"
Ana magana ne a kan alolli.
AT: "Kun kori ... Lebiyawa".
AT: "Kun naɗa wa ... ƙasashe"
AT: "waɗanda suke aiki"
"Gurasar halarta" gurasa ne na musamman da ake yi domin nuna alamar kassancewa da zumuntar Allah da mutanen sa.
AT: "kada kuyi tawaye da Yahweh"
AT: "hari da ba a zato a bayan sojojin Yahuda"
AT: "kira da ƙarfi ga Yahweh"
AT: "Allah ya buga"
Duba:
Waɗannan sunayen birane ne.
AT: "Yahweh ya sa Yerobowam ya kamu da ciwon, sai ya mutu"
AT: "ya auri mata goma sha huɗu"
1Abiya ya yi barci tare da kakanninsa, aka kuma bizne shi a cikin birnin Dauda. Asa, ɗansa, ya zama sarki a gurbin sa. A kwanakin sa ƙasar ta kasance shiru na shekaru goma.2Asa ya yi abin da kemai kyau da dai-dai a idanun Yahweh Allahnsa,3domin ya ɗauke bãƙin bagadai da wuraren tuddai. Ya farfasa ginshiƙan dutse ya kuma datse kafe-kafen Astarot.4Ya dokaci Yahuda su biɗi Yahweh, Allah na kakanninsu, su kuma aiwatar da shari'ar da dokokin.5Haka kuma ya ɗauke wuraren tuddai da bagadan turare daga dukkan biranen Yahuda. Masarautar ta sami hutawa a ƙarƙashin sa.6Ya gina tsararrun birane a Yahuda, domin ƙasar ta kasance shiru, kuma ba shi da yaƙi a waɗannan shekaru, saboda Yahweh ya ba shi salama.7Domin Asa ya cewa Yahuda, "Bari mu gina waɗannan birane muyi katangai kewaye da su, da hasumiyoyi, da ƙofofi, da ƙarafuna; ƙasar har wayau tamu ce, saboda mun biɗo Yahweh Allahnmu. Mun biɗo shi, kuma ya bamu salama ta kowanne gefe." Sai suka yi gini kuma suka yi nasara.8Asa na da mayaƙa da ke ɗaukar garkuwoyi da mãsu; daga Yahuda yana da mutane 300,000, daga kuma Benyamin, mutane 280,000 waɗanda ke ɗauke da garkuwoyi suna kuma jan bakkuna. Dukkan waɗannan ƙarfafa ne, mutane masu ƙarfin hali.9Zera Bakushe yazo gãba da su tare da mayaƙa sojoji miliyan ɗaya da karusai ɗari uku; yazo Maresha.10Daga nan Asa ya fita domin ya gamu da shi, suka kuma kafa dãgar yaƙi a kwarin Zefata a Maresha.11Asa ya yi kuka ga Yahweh, Allahnsa, ya kuma ce, "Yahweh, babu wani sai kai da zai taimaki wanda ba shi da ƙarfi yayin da ya ke fuskantar masu yawa. Ka taimake mu, Yahweh Allahnmu, domin mun dogara gare ka, kuma a cikin sunanka munzo gãba da wannan babban taro. Yahweh, kai ne Allahnmu; kada ka bar mutum ya yi nasara da kai."12Yahweh ya buge Kushiyawa a gaban Asa da Yahuda; Kushiyawa suka tsere.13Asa da sojojin da ketare da shi suka runtume su zuwa Gera. Kushiyawa da yawa suka fãɗi yadda basu iya murmurowa ba, domin an lalatar da su gaba ɗaya a gaban Yahweh da mayaƙansa. Mayaƙan suka kwashe ganima mai yawa.14Mayaƙan suka hallakar da dukkan ƙauyukan da ke kewaye da Gera, domin fargaban Yahweh ya sauko bisa dukkan mazaunansu. Mayaƙan suka washe dukkan ƙauyukan, kuma akwai ganima da yawa a cikin su.15Mayaƙan kuma suka hallakar da rumfar zaman makiyaya mayawata; suka kwashe ganimar tumaki masu yawa, tare da raƙuma, sa'an nan suka koma Yerusalem.
AT: "Abiya ya mutu"
AT: "A lokacin mulkinsa"
AT: "ƙasar ta kasance da salama na shekaru goma"
AT: "bisa ga Yahweh"
AT: "Asa yasa an lalatar da da wuraren bautar gumaka da bagadi da ake amfani domin bautar allolin ƙarya a Yahuda"
Duba:
AT: "Asa ya cewa mutanen Yahuda" (Duba: )
AT: "mun rigaya mun biɗi Yahweh Allahnmu ya taimake mu"
Duba: da
Wannan ne sunan birnin a Yahudah.
AT: "kada ka bar wasu mjutane suyi nasara da ku.
AT: "Kushiyawa sun mutu"
AT: "saboda mazaunan aka firgita daga Yahweh"
1Ruhun Allah yazo bisa Azariya ɗan Oded.2Ya fita ya sami Asa ya kuma ce masa, "Ka saurare ni, Asa, da dukkan Yahuda da Benyamin: Yahweh yana tare da kai, yayin da kake tare da shi. Idan ka biɗe shi, zaya samu gare ka; amma idan ka yashe shi, zai yashe ka.3Yanzu lokaci mai tsawo, Isra'ila basu tare da Allah na gaskiya, babu firist mai koyarwa, babu kuma shari'a.4Amma idan a cikin ƙuncinsu suka juya ga Yahweh, Allahnsu, suka kuma biɗe shi, sai ya samu a gare su.5A waɗannan lokuta babu salama ga wanda ya yi tafiyarsa zuwa wani wuri, ko wanda ya yi tafiya zuwa nan; maimako, manyan matsaloli na bisa dukkan mazauna ƙasashen.6Aka karya su gutsu-gutsu, al'umma gãba da al'umma, birni kuma gãba da birni, domin Allah ya azabtar da su da dukkan wahalu iri - iri.7Amma ka ƙarfafa, kada kuma ka bar hannunka ya zama kasasshe, domin aikin ka zai sami sakamako."8Sa'ad da Asa yaji waɗannan maganganu, anabcin Oded annabi, sai ya yi ƙarfin hali ya kori ƙazantattun abubuwa daga dukkan ƙasar Yahuda da Benyamin, daga kuma biranen da ya kame daga ƙasar tudu ta Ifraimu, ya kuma sake gina bagadin Yahweh, wanda ke gaban rumfar gidan Yahweh.9Ya tattaro dukkan Yahuda da Benyamin, da waɗanda ke zama tare da su - mutane daga na Ifraim da Manasse, daga kuma Simiyon. Domin sunzo daga Isra'ila zuwa gare shi babban taro, da suka ga cewa Yahweh Allahnsa na tare da shi.10Sai suka tattaru tare a Yerusalem a cikin wata na uku, a cikin shekara ta sha biyar na mulkin Asa.11Suka yi hadaya ga Yahweh a wannan rana daga cikin ganimar da suka kawo: shanu ɗari bakwai da tumaki da awaki dubu bakwai.12Suka shiga cikin alƙawari su biɗi Yahweh, Allah na kakanninsu, da dukkan zuciyarsu kuma da dukkan ransu.13Suka yarda da cewa duk wanda ya ƙi ya biɗi Yahweh, Allah na Isra'ila, za a kashe shi, ko da ƙarami ne ko babba, ko namiji ko mace.14Suka yi rantsuwa ga Yahweh da babbar murya, tare da sowa, kuma da kãkãki da ƙahonni.15Dukkan Yahuda suka yi farinciki da alƙawarin, domin sun yi rantsuwa da dukkan zuciyarsu, suka kuma biɗi Allah da dukkan buƙatunsu, kuma ya samu a gare su. Yahweh ya basu salama a dukkan kewayensu.16Ya kuma cire Ma'aka, kakarsa, daga zama sarauniya, domin tayi ƙazantaccen siffa daga wani ƙarfen Ashera. Asa ya datse ƙazantaccen siffar, ya niƙe shi zuwa turɓaya ya kuma ƙone shi a magudanar Kidron.17Amma bisan wurare ba a ɗauke su ba daga Isra'ila. Duk da haka Asa ya sadaukar da zuciyarsa gaba ɗaya dukkan kwanakinsa.18Ya kawo cikin gidan Allah abubuwan mahaifinsa da abubuwansa wanda ke na Yahweh: Kayayyakin azurfa da zinariya.19Babu sauran yaƙi kuma har shekara talatin da biyar na mulkin Asa.
AT: "Ruhun Allah ya ba Azariya ikon anabci"
AT: "Isra'ilawa sun daina bauta wa Allah"
AT: "babu firist wanda zai koya masu"
AT: "Allah ya ansawa Isra'ila da suka nemi Shi.
AT: "Wasu al'ummomi da birane sun ci nasararsu.
AT: "ya cire gumaku"
AT: "Yahweh na taimakon sa"
"Su" na nufin ƙabilu na Yahuda da Isra'ila da ke tare da Asa.
Wannan shi ne watan uku na kalandar Yahudawa. A lokacin ƙarshen sashin watan biyar da farkon sashin watan shida a kalandar Yammaci. )
"700 ... 7,000"
AT: "cikin gaskiya kuma gabaki ɗaya"
AT: "A kashe shi"
Duba yadda ka fassara wannan a 15:4
"Mutanen da yawa da suka zauna a Yahuda suka yi murna"
Duba:
AT: "gumaka"
AT: "Asa yayi biyayya kuma ya bi Yahweh gaba dukkan dukkan rayuwarsa"
AT: "haikalin Allah"
"sheraka 35"
1Cikin shekara ta talatin da shida na mulkin Asa, Ba'asha, sarkin Isra'ila, ya nuna tsageranci gãba da Yahuda ya kuma gina Rama, domin kada ya bar wani ya tashi ko ya tafi ƙasar Asa, sarkin Yahuda.2Daga nan Asa ya fito da azurfa da zinariya daga ɗakunan ajiya na cikin gidan Yahweh da gidan sarki, ya kuma aika su ga Ben Hadad sarkin Aram, wanda ke zama a Damaskus. Yace,3"Bari alƙawari ya kasance tsakani na da kai, kamar yadda ya kasance tsakanin mahaifi na da mahaifin ka. Duba, na aiko maka da azurfa da zinariya. Ka karya alƙawarinka da Ba'asha, sarkin Isra'ila, saboda ya rabu da ni."4Ben Hadad ya saurari sarki Asa ya kuma aika da shugabannin mayaƙansa gãba da biranen Isra'ila. Suka kai hari ga Iyon, Dan, Abelmayim, da dukkan biranen ajiya na Naftali.5Sai ya kasance da Ba'asha yaji wannan, sai ya dena ginin Rama, ya kuma bar aikinsa ya tsaya.6Daga nan Asa sarki ya ɗauki dukkan Yahuda tare da shi. Suka ɗauke duwatsu da katakai daga Rama wanda Ba'asha ke ginin birnin da su. Daga nan nan sarki Asa ya ɗauki waɗannan kayan gini ya yi amfani da su ya gina Geba da Mizfa.7A wannan lokaci Hanani mai gani ya tafi wurin Asa, sarkin Yahuda, ya kuma ce ma shi, "Saboda ka dogara ga sarkin Aram baka kuma dogara ga Yahweh Allahnka ba, mayaƙan sarkin Aram sun kuɓuce daga hannunka.8Kushiyawa da Libiyawa ba manyan mayaƙa ba ne, tare da karusai masu yawa da mahaya dawakai? Duk da haka, saboda ka dogara ga Yahweh, ya baka nasara a bisansu.9Gama idanun Yahweh na dubawa ko'ina cikin dukkan duniya, domin ya nuna kansa mai karfi a madadin waɗanda zukatansu ke shiryayyu zuwa gare shi. Amma ka aikata wawanci a cikin wannan al'amari. Daga yanzu zuwa nan gaba, zaka sami yaƙi."10Daga nan Asa ya fusata da mai ganin; ya sanya shi cikin kurkuku, domin ya yi fushi da shi game da wannan al'amari. A dai-dai wannan lokacin kuma, Asa ya tsananta wa wasu daga cikin mutanen.11Duba, ayyukan Asa, daga farko zuwa karshe, duba, an rubuta su cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra'ila.12A cikin shekara ta talatin da tara na mulkinsa, Asa ya kamu da cuta a ƙafafunsa; cutarsa kuwa ta yi tsanani sosai. Duk da haka, bai nemi taimako ba daga Yahweh, amma daga masu magani kaɗai.13Asa ya yi barci tare da kakanninsa; ya mutu a shekara ta arba'in da ɗaya na mulkinsa.14Suka bizne shi a nasa kabarin, wanda ya haƙa domin kansa a cikin birnin Dauda. Aka kwantar da shi cikin maɗauki da ke cike da ƙanshi mai daɗi da kayan ƙanshi daban-daban da ƙwararrun masu haɗa turare suka haɗa. Daga nan suka haɗa babbar wuta domin girmama shi.
A nan "gina" na nufin ganuwa da ke kewaye da birnin, domin kare birnin daga mahara.
AT: "kada ka kai mani hari"
AT: "aika rundunarsa su kai biranen hari"
Waɗannan sunayen ɓirane ne.
AT: "Kushiyawa da Libiyawa ba manyan mayaƙa ne, tare da karusai masu yawa da mahaya dawakai"
AT: "Yahweh na duban abubuwan da ke faruwa ko'ina a duniya"
AT: "Yahweh yayi kariya da hannunsa"
AT: "dukkan abin da yayi"
Wannan littafi ne wanda babu shi.
AT: "Asa yana da cuta a ƙafafunsa"
AT: "Asa ya mutu"
"Maɗauki wani tebur ne da ake ajiyan gawa a lokacin jana'iza"
1Yehoshafat ɗan Asa ya zama sarki a gurbinsa. Yehoshafat ya ƙarfafa kansa gãba da Isra'ila.2Ya sanya 'yan doka a cikin dukkan ƙarfafan biranen Yahuda, ya kuma kafa sansanai a cikin ƙasar Yahuda da cikin biranen Ifraim, waɗanda Asa mahaifinsa ya kame.3Yahweh yana tare da Yehoshafat saboda ya yi tafiya cikin hanyoyin farko na mahaifinsa Dauda, bai kuma biɗi ba'aloli ba.4Maimako, ya dogara ga Allah na mahaifinsa, ya kuma yi tafiya cikin dokokinsa, ba bisa ga ɗabi'ar Isra'ila ba.5Sai Yahweh ya tabbatar da mulkin a hannunsa; dukkan Isra'ila suka kawo haraji ga Yehoshafat. Yana da dukiya da daraja a yalwace.6Zuciyarsa ya sadaukar ga hanyoyin Yahweh. Ya cire wuraren tuddai da kafe-kafen Ashera daga Yahuda.7A cikin shekara uku na mulkinsa ya aika da ofisoshinsa Benhayin, Obadiya, Zakariya, Netanel, da Mikaya, su koyar a cikin biranen Yahuda.8Tare da su kuma akwai Lebiyawa: Shemayya, Nataniya, Zebadiya, Asahel, Shemiramot, Yehonatan, Adoniya, Tobiya, da Tobadoniya; tare da su kuma akwai firistoci Elishama da Yehoram.9Suka koyar a Yahuda, suna da littafin shari'ar Yahweh tare da su. Suka yi yawo cikin dukkan biranen Yahuda suka kuma yi koyarwa a cikin mutanen.10Fargabar Yahweh ya sauko bisa dukkan masarautun ƙasashen da kekewaye da Yahuda, har da ba su iya yaƙar Yehoshafat ba.11Wasu daga cikin Filistiyawa suka kawo kyautai ga Yehoshafat, da azurfa a matsayin haraji. Larabawa kuma suka kawo masa garkuna, raguna 7,700, da awaki 7,700.12Yehoshafat ya zama cike da iko sosai. Ya gina tsararrun birane da wuraren ajiya a Yahuda.13Yana da kayan biyan buƙatu masu yawa a cikin biranen Yahuda, da sojoji - ƙarfafa, mutane masu ƙarfin hali - a Yerusalem.14Ga lissafinsu an tsãra bisa ga sunayen gidajen ubanninsu: Daga Yahuda, shugabannin dubbai; Adna shugaba, tare da shi kuma mutanen yaƙi 300,000;15gaba da shi kuma Yehohanan shugaba, tare da shi kuma mutane 280,000;16gaba da shi kuma Amasiya ɗan Zikri, wanda ya miƙa kansa ya bautawa Yahweh da yardan ransa; tare da shi kuma mutanen yaƙi 200,000.17Daga Benyamin: Eliyada cike da iko mutum mai ƙwazo, tare da shi kuma 200,000 shiryayyu da bakkuna da garkuwoyi;18gaba da shi kuma Yehozabad, tare da shi kuma 180,000 a shirye shiryayyu domin yaƙi.19Waɗannan ne waɗanda suka bauta wa sarki, baya ga waɗanda sarki ya sanya a tsararrun birane a cikin dukkan Yahuda.
Ra'ayin "kansa" a nan na a matsayin sojojin sarki. AT: "ka shirya sojojin domin su yi yaki Isra'ila"
Waɗannan sansanin sojoji ne na tsaro.
Ana ambaton hali kamar yana tafiya ne. AT: "yayi tafiya a cikin adalcin kakaninsa"
Bai kuma biɗi ba'aloli ba, domin neman taimako daga garesu.
Duba yadda ka fassara wannan a 14:1
Waɗannan sunayen mutane ne.
AT: "Mutane a dukkan ƙasashen da ke kewaye da Yahuda sun tsorata da abinda Yahweh zai iya yi domin ya horar da su"
Waɗannan sunayen nutane ne.
"ban da"
1Yanzu Yehoshafat yana da dukiya da yawa da kuma girma; sai ya haɗa kai da Ahab ta wurin miƙa ɗaya daga cikin iyalinsa ya auri 'yarsa.2Bayan 'yan shekaru sai ya tafi wurin Ahab a Samariya. Ahab ya yanyanka tumaki da shanu masu yawa dominsa da kuma mutanensa da ketare da shi. Ahab yasa shi ya kai wa Ramot Giliyad hari tare da shi.3Ahab sarkin Isra'ila yace da Yehoshafat, sarkin Yahuda, "Ko za ka bini zuwa Ramot Giliyad?" Yehoshafat ya amsa masa, ni kamar ka ne, mutanena kuma kamar mutanenka ne; zamu kasance tare da kai a cikin yaƙin."4Sai Yehoshafat yace da sarkin Isra'ila, "Na roƙe ka ka fara neman maganar Yahweh domin amsarka."5Daga nan sai sarki ya tattara dukkan annabawa tare har su ɗari huɗu sai yace da su, "Ko ma iya zuwa Ramot Gileyad yaƙi, ko kuwa kada mu je?" Suka ce, "Ka kai hari, domin Allah zai bada ita a hannun sarki."6Amma Yehoshafat yace, "Babu wani annabin Yahweh da ba shi nan da zamu nemi shawara?"7Sarkin Isra'ila ya cewa Yehoshafat, "Har yanzu akwai wani da zamu nemi shawarar Yahweh, shi ne Mikaiya ɗan Imla, amma ina ƙinsa domin bai taɓa yi mini wani anabci mai kyau ba, amma kullum na mugunta ne." Amma Yehoshafat yace, "Bai kamata sarki ya faɗi haka ba."8Sai sarkin Israila ya kira hafsa yace, "Ka yi hanzari ka kawo Mikaiya ɗan Imla."9To Ahab sarkin Isra'ila da Yehoshafat sarkin Yahuda na zaune a kujerar mulki kowannensu ya yi adonsa na sarauta a filin Allah a ƙofar shiga Yerusalem, kuma dukkan annabawa na zaune a gabansu.10Sai Zedekiya ɗan Kena'ana ya yi wa kansa ƙaho na ƙarfe ya ce"Yahweh ya faɗi wannan. Da wannan zaka rarraki Aremiyawa har sai an haɗiye su.11Duk annabawan suka yi annabci iri ɗaya suna cewa ka kai hari kan Ramot Gileyad kayi nasara, gama Yahweh ya bayar da ita a hannun sarki."12Manzon da aka aika wurin Mikaiya ya yi magana da shi yace, "Duba, dukkan annabawa sun faɗi maganganu masu kyau game da sarki. Ina roƙonka kaima maganarka ta zama kamar tasu, ka faɗi abubuwa masu kyau."13Mikaiya ya amsa, "Na rantse da Yahweh abin da Allah ya faɗi shi zan faɗa."14Sa'ad da yazo wurin sarki, sarki ya ceda shi, "Mikaiya, ma iya zuwa Ramot Gileyad yaƙi, ko a'a?" Mikaiya ya amsa masa, "Ka kai hari ka kuma yi nasara! Domin zata zama babbar nasara."15Sai sarki ya ceda shi, "Har sau nawa zan buƙace ka da ka rantse ka faɗa mini gaskiya da sunan Yahweh?"16To sai Mikaiya yace, "Na ga dukkan Isra'ila a warwatse a kan tuddai, kamar tumakin da basu da makiyayi, Yahweh kuma yace, 'Waɗannan basu da makiyayi. Bari kowanne mutum ya koma gidansa cikin salama.'"17To sai sarkin Isra'ila ya ceda Yehoshafat, "Ashe ban faɗa maka cewa ba zai yi annabci mai kyau game da ni ba, amma sai na masifa?"18Sai Mikaiya ya ce yanzu dukkan ku sai ku ji maganar Yahweh: Na ga Yahweh zaune kan kursiyinsa, kuma dukkan rundunar sama na tsaye a gefen damansa da hagunsa.19Yahweh yace, Wane ne zai yaudari Ahab, sarkin Isra'ila, domin ya haura ya faɗi a Ramot Gileyad?' Wannan ya ce haka wani kuma ya ce wancan.20Daga nan sai wani ruhu ya sauko daga wurin Yahweh yace, 'zan ruɗe shi. 'Yahweh ya ceda shi ta yaya?'21Sai ruhun ya amsa, 'Zan je in zama ruhun ƙarya a bakin annabawansa dukka. Yahweh ya amsa, 'Zaka ruɗe shi, kuma zaka yi nasara. To yanzu sai ka tafi ka yi haka.'22Yanzu duba, Yahweh yasa ruhun ƙarya a bakin annabawan nan naka, Yahweh kuma ya umarta masifa dominka."23Sai Zedekiya ɗan Kena'aya, yazo gaba, ya mari Mikaiya a kunci, yace, "Ta wacce hanya Ruhun Yahweh ya barni har ya yi magana da kai?"24Mikaiya yace, "Duba za ka san haka a waccan ranar, lokacin da ka shiga lungun ɗaki domin ka ɓuya."25Sarkin Isra'ila ya ceda wanɗansu bayi, "Ku je ku kama Mikaiya ku kai shi wurin Amon gwamnan birnin, da kuma Yowash, ɗana.26kuce da shi, 'Sarki ya ceka sa wannan mutum a kurkuku ka kuma ciyar da shi da 'yar gurasa da ɗan ruwa, har sai na dawo lafiya.'"27Sai Mikaiya ya cein har ka dawo lafiya to ba Yahweh ne ya yi magana ta wurina ba." Ya ƙara da cewa, dukkan ku mutane ku ji wannan."28To sai Ahab, sarkin Isra'ila, da Yehoshafat, sarkin Yahuda, suka tafi yaƙi a Ramot Gileyad.29Sarkin Isra'ila ya ceda Yehoshafat, "Zan yi ɓadda kama in tafi yaƙin, amma kai sai ka sa rigunanka na sarauta." Sai sarkin Isra'ila ya yi ɓadda kama suka tafi yaƙin.30Shi kuma sarkin Aram ya bada umarni ga shugaban mayaƙan karusai cewa "Kada ya hari ƙananan mayaƙa sai dai sarkin Isra'ila kaɗai."31Sai ya kasance bayan shugaban mayaƙan ya ga Yehoshafat sai yace, "Wancan sarkin Isra'ila ne." Sai suka juya domin su kai masa hari, amma Yehoshafat ya ƙwala ihu, Yahweh kuma ya taimake shi. Allah ya juyar da su daga binsa.32Bayan da shugabannin yaƙin suka gane ba sarkin Isra'ila bane sai suka juya suka dena fafararsa.33Amma wani mutum ya ciro bakansa ya yi harbi a iska sai ya bugi sarkin Isra'ila a mahaɗar makamansa. Sai Ahab ya ceda mai tuƙa karusarsa, ka juya ka fitar da ni daga filin dãga, domin na sami mummunan rauni sosai."34Yaƙi ya yi zafi sosai a wannan rana, ana kuma riƙe da sarkin Isra'ila a cikin karusarsa da kefuskantar Aremiyawa har yamma. Can kusan faɗuwar rana, sai ya mutu.
AT: "ya haɗa kai da Ahab" ko "ya maida kansa abokin Ahab"
Yehoshafat ya haɗa kai da Ahab. AT: "Na miƙa kaina da sojojina a gareka don kayi amfani da mu yadda kake so"
"Na tabbata dole akwai a nan ... shawara."
Shi annabin Ubangiji ne.
Wannan yana nufin ƙahonin sa ne amma suka yi da karfe.
AT: "Za ka ci nasararsu"
AT: "Yahweh zai baku nasara"
Wannan na nufin dukkan saƙon annabawa.
AT: "da ra'ayi ɗaya" ko "kuma dukkansu sun yarda"
AT: "na tabbatar maka"
AT: "ko baza mu je ba"
AT: "Na gaya maka ka faɗa mini gaskiya da sunan Yahweh?
AT: "babu shugabanci mai kyau"
AT: "Na faɗa maka cewa ba zai yi annabci mai kyau game da ni ba, amma sai na masifa"
Wannan na nufin ka rinjayi wani ta wurin miƙa wani abu mai jan hankali.
AT: "ka ji rauni sosai" ko "ka mutu"
Wannan ya nuna cewa ra'ayi bai zo ɗaya ba
AT: "ruhun da ya iza annabawansa dukka suka fadi ƙarya"
AT: "Ka ƙadara cewa mummunan abu zai same ka"
Wannan ba shine Zedekiya da ake nufin a sama ba, amma annabi da ke biyaya da da Ahab.
AT: "Ruhun Yahweh ba zai barni har da zan yi magana da kai"
AT: "lokacin da ka gudu, a tsorace, don ka ɓoye"
Mikaiya ya sani da cewa Yahweh bai yi magana ta wurinsa ba.
AT: "yaƙi a kan"
Wannan yana nufin canza yanayin da aka saba don kada a gane.
AT: "Kada ku kai hari ga ɗaya daga cikin sojojin" d
Ba dai-dai bane aka bayyana Yehoshafat a matsayin sarkin Isra'ila saboda Ahab ya nace cewa ya sa rigunan sarauta.
AT: "Allah ya sa suka daina bin sa"
Wannan wuri ne inda makamai biyu ke haɗuwa kuma mai sauƙin kamuwa da kibiya da takobi.
1Yehoshafat sarkin Yahuda ya koma gidansa a Yerusalem lafiya.2Sai Yehu ɗan Hanani, mai duba yaje ya tare shi ya cewa sarki Yehoshafat, "Ko zaka dinga taimakon mugaye? Ko zaka ƙaunaci maƙiyan Yahweh? Domin wannan, fushi daga Yahweh na kanka.3Duk da haka akwai 'yan waɗansu halaye nagari a cikinka, domin kã kawar da sandunan Ashera daga ƙasar, ka kuma sa zuciyarka ga neman Allah."4Yehoshafat ya zauna a Yerusalem; ya kuma sake yin tafiya cikin mutanen Biyarsheba zuwa ƙasar duwatsu ta Ifiraimu ya kuma komo da su ga Yahweh, Allah na ubanninsu.5Ya sa mahukunta a cikin ƙasar a cikin dukkan tsararrun biranen Yahuda, daga birni zuwa birni.6ya ceda mahukuntan, "Ku yi la'akari da abin da zaku yi, domin ba saboda mutum kuke yin hukuncin ba, amma saboda Yahweh; yana tare daku a cikin zartar da hukunci.7Yanzu dai, sai ku bar tsoron Yahweh ya zauna a bisanku. Ku yi hankali a lokacin da kuke yin hukunci, domin babu laifofi ga Yahweh Allahnmu, kuma babu wata tara ko karɓar rashawa."8Bugu da ƙari, a Yerusalem Yehoshafat ya naɗa waɗansu daga cikin Lebiyawa da firistoci da waɗansu shugabannin kakanni na gidajen Isra'ila, da su gudanar da hukunci domin Yahweh, da kuma sasanta saɓani. Suka zauna a Yerusalem.9Ya umarce su, da cewa, "Dole ku yi hidima cikin girmamawa ga Yahweh, da kuma aminci, da kuma dukkan zuciyarku.10Duk inda akwai wani saɓani da ya zo gare ku daga ɗan'uwa da kezaune a birninsu, ko dai game da zubar da jini, ko game da dokokin da aka umarta, da sharuɗa da farillai, dole ku gargaɗe su kada su zama da laifi a gaban Yahweh, ko kuma fushi ya sauko maku daku da "yan'uwanku. Wannan zaku yi kuma ba zaku zama da laifi ba.11Duba, Amariya babban firist shi ne shugabanku a kan dukkan al'amuran Yahweh. Zebadiya ɗan Isma'ila, shugaban gidan Yahuda, shi ne ke da ragamar duk abin da ya shafi sarki. Hakannan Lebiyawa zasu zama hafsoshi suna yi maku hidima. Ku yi ƙarfin hali ku kiyaye dokokin ku, Bari Yahweh kuma ya kasance da masu aikata nagarta."
AT: "Kada ka taimaki mugaye! Ka ƙaunaci maƙiyan Yahweh!"
Duba yadda ka fassara wannan a 14:1
AT: "yanke shawara sosai"
AT: "farfado da bangaskiyarsu a cikin Yahweh"
AT: "Kuji tsoron Yahweh sa'anda kuke zartas da hukumci"
AT: "kakannin iyalan Isra'ila"
AT: "taimakawa don sasanta saɓani"
AT: "Allah zai sauko maku da fushinsa da kai da 'yan'uwanku"
Duba:
1Sai ya kasance bayan wannan, sai mutanen Mowab da Ammon, da waɗansu Meyunawa suka kawo wa Yehoshafat yaƙi.2Sai waɗansu suka faɗa wa Yehoshafat cewa, "Babbar runduna na zuwa găba da kai daga hayin Mataccen Teku, daga Idom. Duba suna nan a Hazezon Tamar," wato Engedi.3Sai Yehoshafat ya tsorata ya kuma ƙudurta ya nemi Yahweh. ya yi shelar azumi a cikin dukkan Yahuda.4Yahuda ta taru domin neman Yahweh; Suka zo su nemi Yahweh daga dukkan biranen Yahuda.5Yehoshafat ya miƙe a cikin taron mutanen Yahuda da Yerusalem, a gidan Yahweh, a gaban sabon harabar.6ya ce"Yahweh Allah na ubanninmu, ba kai bane Allah a sama? Ba kai bane mai mulkin dukkan mulkokin al'ummai? Ƙarfi da iko naka ne, domin haka ba wanda zai iya yin tsayayya da kai.7Allahnmu ashe ba kai ka kori mazaunan wannan ƙasa ba daga gaban mutanen ka Isra'ila, ka kuma bada ita har abada ga zuriyar Ibrahim?8Sun zauna a cikinta suka gina maka wuri mai tsarki a cikinsa da sunanka cewa,9'In wata masifa ta taso a kanmu - ko takobin hukunci, ko cuta, ko yunwa - zamu tsaya a gaban wannan gida, da kuma gabanka (domin sunanka na a cikin wannan gida), kuma zamu yi kuka zuwa gare ka a cikin ƙuncinmu, zaka kuma jimu ka kuma cece mu.'10Duba yanzu, ga mutanen Ammon, da Mowab, da Tsaunin Seyir waɗanda baka bari mu hallakar da su ba a lokacin da suka fito daga ƙasar Masar; a maimakon haka, Isra'ila suka juya daga wurinsu basu kuma hallaka su ba.11Dubi yadda suke sãka mana; suna tafe domin su kore mu daga ƙasar da ka bamu gãdo.12Allahnmu, ba zaka hukunta su ba? Domin bamu da ikon yin yaƙi da wannan babbar rundunar da kezuwa domin su yaƙe mu. Ba mu san abin da zamu yi ba, amma mun zuba ido gare ka."13Dukkan Yahuda suka tsaya a gaban Yahweh, duk da ƙananansu da matayensu, da yaransu.14To a cikin tsakiyar tattaruwar, sai Ruhun Yahweh ya zo kan Yahaziyel, ɗan Zakariya, ɗan Benaiya, ɗan Yeyel, ɗan Mataniya, Balebi, ɗaya daga cikin 'ya'yan Asaf.15Yahaziyel yace, "Ku saurara, ku dukkan Yahuda da mazaunar Yerusalem, da sarki Yehoshafat. Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗa maku, ' Kada kuji tsoro; kada ku karaya saboda girman wannan babbar rundunar, domin yaƙin ba naku bane na Allah ne.16Dole ne kuje ku yaƙe su gobe. Duba suna zuwa ta mashigin Ziz. Zaku same su a ƙarshen kwari kafin hamadar Yeruwel.17Ba zaku bukaci ku yi faɗa ba a wannan yaƙin. Ku tsaya a wurarenku, ku tsaya ku jira, ku ga ceton Yahweh tare daku, Yahuda da Yerusalem. Kada ku tsorata ko ku karaya. Kuje ku hare su gobe, domin Yahweh yana tare daku.'"18Yehoshafat ya sunkuyar da kansa ƙasa. Dukkan Yahuda da mazauna Yerusalem suka faɗi a gaban Yahweh, suna yi masa sujada.19Da Lebiyawa, na zuriyar Kohatiyawa, suka miƙe suka yabi Yahweh, Allah na Isra'ila, da babbar murya.20Da sassafe suka tashi suka tafi hamadar Tekowa. A lokacin da suka fita, Yehoshafat ya tashi tsaye yace, "Ku saurare ni Yahuda da ku mazauna Yerusalem! Ku dogara ga Yahweh Allahnku, zaku sami kafuwa. Ku dogara ga annabawansa, zaku yi nasara."21Bayan da ya tuntuɓi mutane, sai ya naɗa waɗanda zasu raira yabo ga Yahweh su ba shi waƙar yabo domin ɗaukakarsa mai tsarki, a lokacin da suka tafi suna tunkarar sojoji, suka ce, "Ku yi godiya ga Yahweh, domin alƙawarin amincinsa ya tabbata har abada."22Sa'ad da suka fara waƙar yabo, sai Yahweh yasa masu kwanto gãba da mutanen Ammon, da Mowab, da Tsaunin Seyir waɗanda ke zuwa domin su kawo hari ga Yahuda, aka yi nasara da su.23Domin mutanen Ammon da Mowab suka fita suka yaƙi mazaunan Tsaunin Seyir, suka karkashe su suka hallakar da su. Bayan sun hallaka mazaunan Tsaunin Seyir. Sai duk suka taimaka wajen hallaka junansu.24Sa'ad da Yahuda suka zo su dudduba hamada sai suka dubi sojojin. Duba, sun fãɗi ƙasa matattu; ba wanda ya tsira.25Yehoshafat da dukkan mutanensa suka zo domin su kwashi ganima daga gare su, sai suka sami kayayyakin da aka yi watsi da su, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka ɗebar wa kansu, fiye da yadda zasu iya ɗauka. Ya ɗauke su kwana uku kafin su iya kwashe ganimar, domin akwai ta birjik.26A rana ta huɗu sai suka taru a kwarin Beraka. A can suka yabi Yahweh, domin haka ake kiran sunan wurin "Kwarin Beraka" har ya zuwa yau.27Daga nan sai suka juya, dukkan mutanen Yahuda da na Yerusalem, Yehoshafat kuma yana yi masu jagora, suka sake koma Yerusalem da farinciki, domin Yahweh ya sake sa su suyi murna a kan maƙiyansu.28Suka zo Yerusalem zuwa gidan Yahweh da garayu, da molo, da kãkãki.29Razanar Allah ta kama dukkan mulkokin al'ummai sa'ad da suka ji Yahweh ya yaƙi maƙiyan Isra'ila.30Ta haka mulkin Yehoshafat ya zama da kwanciyar hankali, domin Allahnsa ya ba shi salama a dukkan yankunansa.31Yehoshafat ya yi mulkin Yahuda: Yana da shekaru talatin da biyar a lokacin da ya fara sarauta, ya kuma yi mulkin Yerusalem na tsawon shekaru ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba, 'yar Shilhi.32ya yi tafiya bisa tafarkin Asa, mahaifinsa, bai kuma juya ya barsu ba; ya yi abin da keda kyau a gaban Yahweh.33Duk da haka, ba a ɗauke wuraren tuddai ba. Mutanen basu juyar da zukatansu ga Allah na kakanninsu ba.34A kan kuma sauran abubuwa game da Yehoshafat, farko da ƙarshe, duba an rubuta su a cikin tarihin Yehu ɗan Hanani, wanda aka rubuta a cikin littafin sarakunan Isra'ila.35Bayan wannan Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya haɗa kai da Ahaziya, sarkin Isra'ila, wanda ya yi aikin ƙeta sosai.36Ya haɗa kai da shi domin ya yi jiragen ruwa domin zuwa Tarshish. Sun kafa jiragen a Eziyon Geba.37Daga nan sai Eliyeza ɗan Dodabahu na Maresha, ya yi annabci gãba da Yehoshafat; ya ce"Saboda ka haɗa kanka da Ahaziya, Yahweh ya rushe ayyukanka." Sai aka ragargaje jiragen domin kada a iya tafiya.
Waɗannan ƙabilu ne da ke zaune a Idom yamma da Ƙogin Yodan.
Wannan wani suna ne na Engedi.
AT: "ƙuduri"
AT: "ya nemi Yahweh ya sauraresu"
AT: "kai Allah ne a sama kuma mai mulkin dukkan sarakunan duniya."
AT: "kai ka kori mazaunan wannan ƙasa ba daga gaban mutanen ka Isra'ila, ka kuma bada ita har abada ga zuriyar Ibrahim."
AT: "kasancewarka na nan wannan gidan"
Wannan shi ne wurin da mutanen Idomawa suka zauna.
AT: Haka ne suka sãka mana don alherin da ka nuna masu; suna tafe domin su kore mu daga ƙasar ka"
AT: "don Allah ka hukunta su"
AT: "mun zuba ido gare ka domin neman taimako"
Duba yadda zaka fassara wannan a 2 Chron. 15:1
sunayen mutane.
AT: "kuje zuwa" ko "kuje filin ɗaga"
Wannan itace kwari mai zurfi tsakanin tsaunuka biyu kudu maso gabas zuwa Yerusalem.
"Allah zai yi yaƙin kuma ya ceci mutanensa"
AT: "Dukkan mutanen Yahuda"
Wadannan sunayen mutanen da zuriyar Korat da Kora.
Wannan wani gari ne a kudancin Yerusalem.
AT: " Yahweh zai taimake ku"
AT: "Idan kun dogara ga annabawansa, zaku yi nasara"
Duba yadda ka fassara wannan a 20:10
AT: "shirya kai hari mai bada mamaki"
Waɗannan jumloli biyun na nufin abu ɗaya. na biyu yana ƙarfafa na farko. AT: "a hallaka su gabaki ɗaya"
Ya zama da mamaƙi. Dukkan maƙiyan sun kashe junnansu.
Wannan jumla "sun fãɗi ƙasa" hanya ce na cewa sun mutu. AT: "sun fãɗi ƙasa matattu"
Duba yadda ka fassara wannan a 2 Chron. 5:9
Wannan na nufin dukkan mayaƙa. AT: "kowane soja na Yahuda da Yerusalem" (Duba:
Sarki Yehoshafat yayi gaban dukkan sojoji yayin da suka sake komawa Yerusalem.
"Dukkan sarakunan al'ummai suna tsoron Allah sosai"
Wannan na magana ne a kan gwamnati da mai saurata ɗaya.
AT: "ya bi tafarkin mahaifinsa"
Duba yadda ka fassara wannan a 2 Chron. 14:1
Duba yadda ka fassara wannan a 2 Chron. 16:11
Waɗannan jirage ne da ke iya tafiya a kan babban ruwa.
Duba yadda ka fassara wannan a 8:17.
Sunan mutum ne.
1Yehoshafat ya yi barci tare da kakanninsa aka binne shi tare da su a birnin Dauda; Yehoram, ɗansa, ya zama sarki a madadin sa.2Yehoram na da 'yan'uwa, ga 'ya'yan Yehoshafat: Azariya, Yehiyel, Zekariya, Azariyahu, Mika'ilu da Shefatiya. Dukkan waɗannan 'ya'yan Yehoshafat ne sarkin Isra'ila.3Mahaifinsu ya basu kyautar zinariya da azurfa masu ɗumbin yawa da sauran kayayyaki masu daraja, da ƙayatattun birane a Yahuda, amma sai ya bada gadon sarauta ga Yehoram, saboda shi ne ɗan fari.4To lokacin da Yehoram ya gãji mahaifinsa a sarauta ya kuma kafa kansa sosai a matsayin sarki, sai ya karkashe dukkan 'yan'uwansa da takobi, haka kuma da shugabannin Isra'ila da ban da ban.5Yehoram na da shekaru talatin da biyu lokacin da ya fara mulkin, ya kuma yi mulki a Yerusalem na tsawon shekaru takwas.6ya yi tafiya bisa tafarkin sarakunan Isra'ila, kamar yadda gidan Ahab ya yi, domin ya auri ɗiyar Ahab ta zama matarsa sai ya yi mugun abu a gaban Yahweh.7Duk da haka Yahweh bai so ya hallakar da gidan Dauda ba saboda alƙawarin da ya yi da Dauda; ya yi alƙawarin cewa kullum zai ba da rai a gare shi da kuma zuriyarsa.8A kwanakin Yehoram, Idom ta ɓalle daga mulkin Yahuda, suka kuma naɗawa kansu sarki.9Daga nan sai Yehoram da jarumawansa suka ƙetara da karusansa. Da duhu ya tashi ya yaƙi Idomawan da suka kewaye shi da dukkan jarumawan karusansa.10Ta haka Idom ta ci gaba da tayar wa Yahuda har wa yau. Libna ita ma sai ta tayar a lokaci guda, domin Yehoram ya rabu da Yahweh, Allah na kakanninsa.11Haka kuma, Yehoram ya gina manyan wurare a duwatsun Yahuda yasa mazaunan Yerusalem su yi rayuwa kamar karuwai, ya kuma karkatar da Yahuda.12Wasiƙa daga annabi Iliya ta zo ga Yehoram. Cewa, "Wannan shi ne abin da Yahweh, Allah na Dauda mahaifinka, ya ce: Saboda baka yi tafiya bisa tafarkin Yehoshafat mahaifinka ba, baka kuma bi tafarkin Asa sarkin Yahuda ba,13amma ka bi tafarkin sarakunan Isra'ila, ka kuma sa Yahuda da mazauna Yerusalem su zama kamar karuwai, kamar yadda gidan Ahab suka yi-saboda kuma ka kashe 'yan'uwanka a cikin iyalin mahaifinka ko mariƙa takobi da suka fi ka shahara-14Duba, Yahweh zaya kawo wa mutanenka da matanka da 'ya'yanka da mallakarka babbar annoba.15Kai kuma da kanka ka zama da matsananciyar cuta saboda cutar da kecikin hanjinka, har sai hanjinka ya fito waje saboda cutar, kwana bayan kwana."16Yahweh ya tayar da ruhun Filistiyawa da na Larabawa gãba da Yehoram waɗanda ke kusa da Kush.17Suka kawo wa Yahuda hari, suka washe ta, suka kwashe dukkan wadatarta da suka samu a gidan sarki. Suka kuma kwashe 'ya'yansa da matansa. Basu bar masa ko ɗa ɗaya ba sai dai Yehowahaz, ƙaramin ɗansa.18Bayan duk waɗannan, Yahweh ya buge shi a hanjinsa da cuta mara warkewa.19Sai ya kasance a lokacin a ƙarshen shekaru biyu, sai hanjinsa ya fito saboda rashin lafiyarsa, sai ya mutu ta wurin matsananciyar cuta. Mutanensa basu yi wata wata domin girmama shi ba kamar yadda suke yi wa kakanninsa.20Ya fara sarauta a lokacin da yake da shekaru talatin da biyu; ya yi mulkin Yerusalem na tsawon shekaru takwas, sai ya mutu ba tare da makoki ba. Suka binne shi a birnin Dauda, amma ba a maƙabartar sarakuna ba.
AT: "ya mutu"
Wannan ne birni Yerusalem.
AT: "ya ɗauki ikon mulkin mahaifinsa"
Duba yadda ka fassara wannan a 2 Chron. 20:31
AT: "bisa ga Yahweh"
AT: "A lokacin da Yehoram yake sarki"
"gaba da ikon Yahuda"
AT: "suka ƙetare iyaka zuwa Edom"
Duba yadda ka fassara wannan a 2 Chron. 5:9
Wannan sunnan wani gari ne a Yahuda
AT: "har sai cutar ta jawo maka mutuwa"
AT: "ya sa Filistiyawa da Larabawa sun yi fushi sosai da Yahuda"
AT: "ya ba shi cuta mara warkewa a hanjinsa"
AT: "a lokacin da ya dace" ko "a lokacin da ya ke dai-dai"
AT: "babu baƙin ciki"
1Mazauna Yerusalem suka naɗa Ahaziya sarki, wato ƙaramin ɗan Yehoram sarki, a madadinsa, domin rundunonin Larabawa sun kashe dukkan manyan 'ya'yansa. Domin haka Ahaziya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya zama sarki.2Ahaziya na da shekaru ashirin da biyu a lokacin da ya fara sarauta; ya yi mulkin Yerusalem shekara ɗaya. Sunan mahaifiyarsa Ataliya; ita 'yar Omri ce.3Shi ma ya bi tafarkin Ahab domin mahaifiyarsa ce ke ba shi shawara a cikin yin ayyukan mugunta.4Ahaziya ya yi abin mugunta a gaban Yahweh, kamar yadda gidan Ahab suka yi, domin su ne mashawartansa bayan mutuwar mahaifinsa zuwa hallakarsa.5Hakanan ya bi shawararsu; ya yi tafiya tare da Yerom ɗan Ahab, sarkin Isra'ila, domin su kai hari ga Hazzaiyel, sarkin Aram, a Ramot Gileyad. Aremiyawa suka yi wa Yoram rauni. `6Yoram ya komo domin ya warke daga raunukan da suka ji masa a Rama, lokacin da ya fita ya yi yaƙi da Hazeyel, sarkin Aram. Domin haka Ahaziya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya tafi can Yezril domin ya ga Yoram ɗan Ahab, domin an raunata Yoram.7To an kawo hallakar Ahaziya daga Allah a ziyarar da Ahaziya ya kai wa Yoram. A lokacin da ya isa, sai ya tafi tare da Yehoram domin su kai hari ga Yehu ɗan Nimshi, wanda Yahweh ya zaɓa ya hallakar da gidan Ahab.8A lokacin da Yehu ke aiwatar da hukuncin Allah a kan gidan Ahab, sai ya tarar da shugabannin Yahuda da kuma 'ya'yan ɗau'uwan Ahaziya suna yi wa Ahaziya hidima. Sai Yehu ya kashe su.9Yehu ya nemi Ahaziya, suka kama shi yana ɓoye a Samariya, sai suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi. Sai suka binne shi, domin sun ce, "Shi ɗan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Yahweh da dukkan zuciyarsa." Domin haka gidan Ahaziya ba shi da sauran iko yin sarautar mulkin.10Yanzu bayan Ataliya, ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta kashe dukkan 'ya'yan sarauta a cikin gidan Yahuda.11Amma Yehosheba, ɗiyar sarki, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya a asirce ta ware shi da ban da sauran 'ya'ya maza na sarki waɗanda ake shirin kashewa. Ta sa shi da kuma mai renon shi a ɗakin kwana. Da haka Yehosheba 'yar sarki Yehoram, matar Yehoida firist (domin ita 'yar'uwar Ahaziya ce) sai ta ɓoye shi daga Ataliya domin kada Ataliya ta kashe shi.12Yana tare da su a gidan Allah har tsawon shekaru shida, bayan Ataliya ta yi mulkin ƙasar.
Duba yadda ka fassara wannan a 2 Chron. 20:31
AT: "a ra'ayin Yahweh"
sunayan mutane
1A shekara ta bakwai, Yehoyida ya nuna ƙarfinsa ya shiga alƙawari da shugabannin ɗari-ɗari, Azariya ɗan Yeroham, da Isma'ila ɗan Yehohanan, da Azariya ɗan Obed, Ma'asiya ɗan Adayiya, da Elishafat ɗan Zikri.2Suka zazzaga Yahuda suka tattara Lebiyawa daga dukkan biranen Yahuda, da kuma shugabannin kabilu na gida-gidan Isra'ila sai suka zo Yerusalem.3Dukkan taron mutanen suka yi alƙawari da sarki a gidan Allah. Yehoyida ya ce da su, Duba ɗan sarki ne zai yi mulki, kamar yadda Yahweh ya faɗi game da zuriyar Dauda.4Wannan ne abin da dole zaku yi: kashi uku na firistoci da Lebiyawa da suka zo yin hidima a ranar Asabar, zasu zama masu tsaro a ƙofofi.5Kashi uku kuma su tsaya a fadar sarki, kashi uku kuma a wurin da aka kafa harsashin ƙofa. Dukkan mutane zasu kasance a harabar gidan Yahweh.6Kada ku bar kowa ya shiga haikalin Yahweh sai dai firistoci da Lebiyawan da keyin hidima kai ɗai. Zasu shiga domin an keɓe su, amma sauran dole ne su yi biyayya da umarnin Yahweh.7Dole ne Lebiyawa su kewaye sarki, kowanne na riƙe da makami a hannunsa. Duk wanda ya shigo gidan kuma sai a kashe shi. "Ku tsaya wurin sarki a lokacin da ya shigo da kuma lokacin da ya fita."8To sai Lebiyawa da dukkan Yahuda suka yi kamar yadda Yehoyida firist ya umarta. Kowannen su ya ɗauki mutanensa, masu zuwa domin su yi hidima a ranar Asabar, da kuma waɗanda ba zasu yi hidima a ranar Asabar ba, domin Yehoyida firist bai sallami kowacce runduna ba tukuna.9Sai Yehoyida firist ya kawo masu da manya da ƙananan garkuwoyi da sarki Dauda ya ajiye a gidan Allah ya ba kwamandojin.10Yehoyida ya sanya dukkan sojojin, kowanne mutum da makaminsa a hannusa, daga sashen dama na haikalin zuwa sashen hagu na haikalin, kusa da bagadin da kuma haikalin, zagaye da sarkin.11Sai suka fito da ɗan sarki suka sa masa rawani suka kuma bashi kundin dokoki na alƙawari, suka naɗa shi sarki daga nan sai Yehoyida firist da 'ya'yansa suka keɓe shi ya zama sarki suka ce, "Ranka ya daɗe sarki."12Lokacin da Ataliya ta ji hayaniyar mutanen suna yabon sarki sai ta zo cikin mutane ta shiga haikalin,13ta na dubawa sai ga sarki tsaye kan dakalin sarauta riƙe da sandar sarauta a ƙofar shiga, ga kuma kwamandoji da masu hura kakaki kewaye da sarki. Dukkan mutanen ƙasar na murna suna busa kakaki, mawaƙa suna kaɗa kayan kaɗe-kaɗe suna kuma bida waƙoƙin yabo. Sai Ataliya ta keta tufafinta tana cewa, "Cin amana! Cin amana!"14Daga nan sai Yehoyida ya ce da kwamandojin ɗari-ɗari su zo su fito da ita a kashe ta da takobi tare da duk waɗanda suka biyo ta. domin firist ya ce, "Kada ku kashe ta a cikin gidan Yahweh".15To sai suka buɗa mata hanya ta bi ta Ƙofar Doki zuwa gidan sarki a can suka kashe ta.16To sai Yehoaida da sarki da dukkan mutanen suka yi alƙawari cewa za su zama mutanen Yahweh.17Sai dukkan mutanen suka tafi gidan Ba'al suka rushe shi, suka ɓaɓɓalle bagadin Ba'al da kuma gunkinsa. Suka kashe matan firist na Ba'al a gaban waɗanan bagadan.18Yehoyida ya zaɓi shugabannin haikalin Yahweh ta wurin jagorancin firistoci, da ke Lebiyawa waɗanda Dauda ya sa domin su yi hidima a gidan Yahweh, domin su miƙa hadaya ta ƙonawa ga Yahweh tare da farinciki kamar yadda Dauda ya yi umarni, kamar yadda ya ke a rubuce a shari'ar musa.19Yehoyida ya sa 'yan tsaro a ƙofar haikalin Yahweh, domin kada duk wani marar tsarki ta kowanne fanni ya shiga.20Yehoyida ya kwashi kwamandoji da mutane ma su daraja da gwamnoni tare da shi da dukkan mutanen ƙasar. Ya kawo sarki daga gidan Yahweh, mutane suka shiga ta babbar ƙofa zuwa gidan sarki daga gidan suka zaunar da sarki akan gadon sarauta.21domin haka dukkan mutanen ƙasar suka yi murna birnin kuma ya sami kwanciyar hankali. Ataliya kuma aka kashe ta da takobi.
babban firist wanda yake aiki a haikali kuma ya yi aminci ga Allah. Si ne mashawarcin Yowash.
AT: "Mutane da yawa"
Ma'ana mai yiwuwa su ne 1) "a dukkan lokaci" ko 2) "duk inda ya tafi."
Mafi yawan mutanen sun yi biyayya da ka"idodin firit"
AT: "sun gama aikinsu a ranar Asabaci"
AT: "Ya hadace ka'idodin dokoki na alƙawari"
AT: "kusan dukkan mutanen"
AT: waɗanda su ne shugabanni cikin sojoji"
AT: "Kusan dukkan mutane da yawa suka tafi gidan Ba'al"
AT: "a ƙarkashin jagorancin firistoci"
AT: "kada duk wani marar tsarki ta kowanne fanni ya shiga"
An gina haikalin a kan tsauni mafi tsayi a Yerusalem. AT: "Ya kawo sarki daga haikali a saman tsaunin zuwa masarauta"
1Yowash yana da shekaru bakwai lokacin da ya fara mulki, ya yi mulki na tsawon shekaru arba'in a Yerusalem, sunan mahaifiyarsa Zibiya, daga Biyasheba.2Yoash ya yi abin da kenagari a gaban Yahweh a dukkan kwankin Yehoyida, firist.3Yehoyida ya aura masa mata biyu, sai ya zama uba na 'ya'ya maza da mata.4Bayan wannan Yowash ya yanke shawarar gyara gidan Yahweh.5Sai ya tara firistoci da Lebiyawa ya ce da su, "Kowacce shekara sai ku je cikin dukkan biranen Yahuda ku tattaro kuɗin da za a gyara gidan Allahnku daga dukkan mutanen Isra'ila. Ku tabbata kun fara yanzu." Lebiyawa basu yi komai ba da farko.6Sai sarki ya kirawo Yehoyida babban firist ya ce da shi, "Meyasa baka bukaci Lebiyawa su kawo haraji daga Yahuda da kuma Yerusalem ba kamar yadda Musa bawan Yahweh da kuma taron Isra'ila suka yi ba domin rumfar alƙawarin dokoki ba?"7Domin 'ya'ya maza na Ataliya wannan muguwar mata, sun rushe gidan Allah suka kuma kwashe dukkan kayayyaki masu tsarki na gidan Yahweh suka kai suka bayar ga Ba'al.8To sai sarki ya umarta, suka yi taska suka sa ta daga wajen ƙɔfar shiga gidan Yahweh.9Sai suka yi shela a cikin dukkan Yahuda da Yerusalem domin mutane su biya haraji domin gidan Yahweh harajin da Musa bawan Allah ya sa wa Isra'ila a jeji.10Dukkan shugabanni da dukkan mutane suka yi murna suka kawo kuɗi suka sa a taska har sai da suka cika ta.11To bayan an kawo taskar wurin fadawan sarki ta hannun Lebiyawa duk lokacin da suka ga taskar ta cika da kuɗi sosai a cikinta, marubutan sarki da manyan firistoci su kan zo, su ɗauke ta su kwashe sai su mayar da ita wurin da ta ke. Haka suka dinga yi kowacce rana, suka dinga tara kuɗaɗe masu yawa.12Sai sarki da Yehoyida suka ba da kuɗaɗen ga masu yin aikin hidima a gidan Yahweh. Waɗannan mutanen suka yi hayar masu aikin dutse da masu aikin katako domin su komo da gidan Yahweh, haɗe da masu aikin ƙarfe da tagulla.13To sai ma'aikatan, suka gudanar da aikin ta hannuwansu; suka tayar da gidan Yahweh suka komar da shi kamar yadda ya ke da farko, suka kuma ƙarfafa shi.14Bayan sun gama sai suka mayar da sauran kuɗin ga sarki da kuma Yehoyida. Wannan kuɗin da shi aka yi aikin kujerun gidan Yahweh, da kayayyaki wanda aka mora domin karɓar baiko- cokula da kayayyaki na zinariya da azurfa. Suka yi ta miƙa baye-baye na ƙonawa a gidan Yahweh a dukkan kwanakin Yehoyida.15Yehoyida ya tsufa yana da cikkakun kwanaki, ya mutu yana da shekaru 130.16Suka binne shi a birnin Dauda a cikin sarakuna, saboda ya yi abu mai kyau a Isra'ila, a gaban Allah da kuma gidan Allah.17To yanzu kuma bayan mutuwar Yehoyida, mutanen Yahuda suka zo domin su nuna karramawa ga sarki. Sai sarki ya saurare su.18Suka yi watsi da gidan Yahweh, Allah na kakanninsu suka bautawa gumakan Ashera da siffofinta. Fushin Allah ya auko kan Yahuda da Yerusalem saboda wannan aikin na su mara dacewa.19Duk da haka ya aiko annabawa gare su domin su sake komo da su gare shi, annabawan suka ce Yahweh na gãba da mutanen, amma suka ƙi saurara.20Sai Ruhun Allah ya zo kan Zakariya ɗan Yehoyida, firist; Zakariya ya miƙe a sama da mutanen ya ce da su, "Allah ya faɗi wannan: Me yasa ku ke aikata laifofi ga dokokin Yahweh, domin kada ku azurta? Da yake kun yi watsi da Yahweh, shima ya yi watsi da ku.21"Amma suka yi masa maƙarƙarshiya; sarki ya umarta a jejjefe shi da duwatsu a dandalin gidan Yahweh.22Ta irin wannan hali Yowash, sarki, ya jahilci kirkin da Yehoyida mahaifin Zakariya ya yi masa. A memakon haka ya kashe ɗan Yehoyida. Lokacin da Zakariya ke mutuwa ya faɗi cewa, "Dãma Yahweh ya ga wannan ya kuma sa ka bada lissafi."23To bayan kusan ƙarshen shekara, sai sojojin Aram suka tasarwa Yowash. Suka zo Yahuda da Yerusalem; suka kashe dukkan shugabannin mutane suka kuma kwashe dukkan ganimarsu zuwa ga sarkin Damaskus.24Sojojin Armeniyawa kuma suka zo da ƙaramar rundunar soja, amma Yahweh ya ba su nasara kan babbar rundunar soja, domin Yahuda ta yi watsi da Yahweh na kakanninsu. Allah na kakanninsu. Da haka Armeniyawa suka kawo hukunci a kan Yowash.25A lokacin da Armeniyawa suka fice, an yi wa Yowash mummunan rauni. Bayinsa suka yi masa maƙarƙashiya saboda ya kashe Zakariya ɗan Yehoyida, firist. Suka kashe shi a kan gadonsa; suka binne shi a birnin Dauda, amma ba a maƙabartar sarakuna ba.26Waɗannan su ne mutanen da suka yi masa maƙarƙashiya: Zabad ɗan Shimeyat mace Ba'ammoniya, da Yehozabad ɗan Shimrit, mace Bamowabiya.27To lissafin 'ya'yansa, da kuma annabci mai muhimmanci da aka yi a kansa, da kuma sake gina haikalin Allah, duba an rubuta su a cikin Littafin shashi akan sarakuna. Sai Amaziya ɗansa, ya zama sarki a madadinsa.
Duba yadda ka fassara wannan a 14:1
AT: "muddin Yehoyida firist yana raye.
AT: "nan da nan"
"Kayi mugunta. Na gaya maka cewa ka buƙaci Lewiyawa ... alƙawarin dokoki, amma baka yi haka ba."
Wannan na nufin kayayyaki da ake amfani da su a cikin haikali.
"waɗanda ke gini da dutse da kuma waɗanda ke gini da katako"
AT: "waɗanda ke aikin ƙarfe"
AT: "sunyi tare da hannuwansu"
AT: "kowane rana dukkan kwanakin Yehoida"
AT: "ya ba sarki girma"
AT: "zunubansu"
Yowash bai kasa kunne ko ya tuna babban alherin Yehoida, baban Zakariya ba.
AT: :za ka biya dukkan abubuwa marasa kyau da ka yi"
"Wannan ne littafin nan ya rigaya ya ɓace"
1Amaziya yana da shekaru ashirin da biyar a lokacin da ya fara sarauta; ya yi sarauta ta shekaru ashirin da tara a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddan ta Yerusalem.2ya yi abin da kemai kyau a gaban Yahweh, amma ba da cikakkiyar miƙa zuciya ba.3Sai ya zamana nan da nan bayan mulkinsa ya kafu sai ya kashe bayin da suka kashe mahaifinsa, sarki.4Amma bai kashe 'ya'yan waɗanda suka yi kisan kan ba. Amma ya yi kamar yadda aka rubuta cikin shari'ar Musa, kamar yadda Yahweh ya umarta, "Dole ne iyaye ba zasu taɓa mutuwa ba saboda 'ya'ya, ko 'ya'ya su mutu saboda iyayensu ba, a maimakon haka, kowa zai ɗauki alhakin zunubinsa."5Bugu da ƙari, Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya yi masu ƙidaya bisa ga kabilar kakanninsu, a ƙarƙashin jagorancin shugabannin dubu-dubu da na ɗari-ɗari da dukkan Yahuda da Benyamin. Ya ƙirga su daga 'yan shekaru ashirin zuwa sama, ya sami mutane kusan 300,000 zaɓaɓɓu domin yaƙi waɗanda zasu iya riƙe mashi da garkuwa.6Hakannan ya yi hayar mayaƙa 100,000 daga Isra'ila akan kuɗi azurfa ɗari ɗaya.7Amma sai mutumin Allah ya zo gunsa ya ce masa "Sarki kada ka bari mutanen Israi'la domin Yahweh ba ya tare da Isra'ila - ba ko ɗaya daga cikin mutanen Ifiraimu,8Amma ko dama a ce kana da ƙarfi na yi yin yaƙin Ubangiji zai rikirtar da kai a gaban maƙiya, domin Yahweh ya na da ikon taimako yana kuma da ikon rushewa."9Amaziya ya ce da mutumin Allah, "Amma me za muyi da talanti ɗari dana ba sojojin Isra'ila?" Mutumin Allah ya amsa da cewa "Yahweh zai iya baka fiye da wannan."10To sai Amaziya ya rarraba sojojin da suka zo daga Ifiraimu; ya sake aika su gida. Fushinsu ya yi zafi sosai a kan Yahuda, suka koma gida da matsanancin fushi.11Amaziya ya yi ƙarfin hali har ya tafi da mutanensa zuwa Kwarin Gishiri; a can ya karkashe sojojin Seyir guda dubu goma.12Sojojin Yahuda kuma suka kama sojoji duba goma da ransu. Suka kai su can ƙonƙolin tsauni suka tutturo su ƙasa duk suka kakkarye.13Amma sojojin da Amaziya ya komar da su domin kada su je yaƙi tare da shi, suka je suka kai hari a Yahuda daga Samariya har zuwa Betahoron. Suka kashe mutane dubu uku suka kuma kwashi ganima mai yawa.14Sai ya zamana, bayan Amaziya ya dawo daga kisan Idomawa, sai ya kwaso allolin Seyir ya maida su allolinsa. Ya russuna masu ya kuma ƙona masu turare.15Domin haka fushin Yahweh ya yi ƙuna a kan Amaziya. Ya aika masa da saƙo ta hannun annabi cewa, "Meyasa ka je ka tuntuɓi allololin da basu iya ceton mutanensu daga hannunka ba?"16To lokacin da annabin keyi masa magana, sarki ya ce da shi, "Ko mun maida kai mashawarcin sarki ne? Ka bari! donme za a kashe ka?" Daga nan sai annabin ya bari ya ce na sani Allah ya yi ƙudiri na hallakar da kai saboda ka yi waɗannan abubuwa ba ka kuma ji shawarata ba."17To sai Amaziya sarkin Yahuda ya tuntuɓi mashawartansa ya aika da 'yan saƙo zuwa ga Yehowash ɗan Yehoyahaz ɗan Yehu, sarkin Isra'ila, cewa, "Ka zo mu sadu da juna fuska da fuska a cikin yaƙi."18Amma Yehowash sarkin Isra'ila ya aika da 'yan saƙo ga Amaziya sarkin Yahuda, cewa, "Ɗan ƙaramin sassabe da kea Lebanon ya aika da saƙo ga itacen sida a Lebanon, cewa, "Ka bada 'yarka ga ɗana a matsayin mata; amma sai dabbar daji a Lebanon ta zo ta tattake ɗan sassaben.19Ka kuma ce, duba na rugurguje Idom; amma zuciyarka ta kumburaka. Ka yi taƙama da ɗaukakarka, amma ka tsaya a gida, gama donme zaka jawo wa kanka masifa da faɗuwa, kai da Yahuda tare da kai?"20Amma Amaziya ba zai saurara ba, domin wannan al'amarin daga Allah ne, domin ya miƙa Yahuda ga hannun maƙiyanta, domin sun nemi shawara daga allolin Idom.21To sai Yowash sarkin Isra'ila ya kai hari; shi da Amaziya, sarkin Yahuda, suka gamu fuska da fuska a Betshemesh, wadda take mallakar Yahuda.22A ka ragargaza Yahuda a idon Isra'ila kowa kuma ya tsere gida.23Yehowash, sarkin Isra'ila, ya kame Amaziya ɗan Yehowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, a Betshemesh. Ya kawo shi Yerusalem daga Ifiraimu ya kuma rushe ganuwar Yerusalem daga ƙofar Ifiraimu zuwa kusurwar ƙofar, tsawon kamu ɗari huɗu ne.24Ya kwashe dukkan zinariya da duk abubuwan da ya iske a gidan Allah da Obida da Idom, da kuma abubuwa masu daraja na gidan sarki, tare da kamammun yaƙi, sai ya koma Samariya.25Amaziya ɗan Yowash Sarkin Yahuda ya yi mulki na tsawon shekaru sha biyar yana mulkin Yahuda bayan mutuwar Yehoyash, ɗan Yehoyahaz, sarkin Isra'ila.26Game da sauran ayyukan Amaziya na farko da na ƙarshe duba an rubuta su a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda da Isra'ila.27Yanzu tun daga lokacin da Amaziya ya juya wa Yahweh baya, sai suka fara shirya masa maƙarƙashiya a Yeruslem. Sai ya gudu zuwa Lakish suka kashe shi a can.28Suka komo da shi a kan dawakai suka binne shi a maƙabartar kakanninsa a birnin Yahuda.
Wannan sunnan na mace ne.
Duba yadda ka fassara wannan a 14:1
Wannan na bayanni ne game da Litattafan Farawa, Fitowa, Levitikus, Lissafi, da Maimaitawar Sharia.
An lissafa sunnanyensu a litatafi na musanman.
Duba:
AT: "Fushinsu ya yi ƙunna sosai
AT: "fushi sosai"
Wannan wani ɓangare ne na Mataciyar Teku
AT: "saboda duk su mutu"
Wannan wani ƙauye ne kusa da Yerusalem a Ifriam.
AT: "kashe"
"bautawa waɖannan allolin ƙarya"
AT: "Ka je ka bauta wa allololin mutanen da basu iya ceton mutanensu daga hannunka, Sarki Amaziya"
AT: "Ba mu za kai maɓe ka ka zama ɗaya daga shawartan na ba. Ka daina magana! Idan ka sake yin magana, zan sa sojoji na su kashe ka"
Labarin misalan ɓaure ne.
Wannan ƙaramin daji ne.
Babban itace sosai. A nan na wakiltar sojan Isra'ila.
AT: "zaka jawo wa kanka masifa da faɗuwa, kai da Yahuda tare da kai"
AT: "cin nasara da"
AT: "komai da komai"
AT: "an rubuta su ... Isra'ila."
Birnin a Yahuda.
wani suna da ake kiran birnin Dauda, ko Yerusalem
1Dukkan mutanen Yahuda suka ɗauki Uziya lokacin ya na ɗan shekara sha shida suka naɗă shi sarki a madadin babansa Amaziya.2Shi ne wanda ya sake gina Ilat ya sake komo da ita Yahuda. Bayan wannan sai ya mutu tare da kakanninsa.3Uziya yana da shekara sha shida lokacin da ya fara sarauta. ya yi mulki na tsawon shekaru hamsin da biyu a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya; ita daga Yerusalem ce.4ya yi abin da kemai kyau a gaban Yahweh, ya bi misalin mahaifinsa, Amaziya, ta kowanne abu.5Yasa kansa ga tafarkin neman Allah a kwanakin Zakariya, wanda ya bashi dokoki na yin biyayya ga Allah. Da yake ya nemi Yahweh sai Yahweh ya wadata shi.6Sai Uziya ya fita ya je ya yi yaƙi da Filistiyawa, ya rushe ganuwar birnin Gat da Yamna da ta Ashdod; ya gina birane a ƙasar Ashdod da` kuma cikin Filistiyawa.7Allah ya taimake shi gãba da Filistiyawa da Larabawan da suka zauna a Gurba'al da kuma Maunayawa.8Ammoniyawa kuma su ka biya haraji ga Uziya ƙarfinsa kuma ya kai har Masar, domin yana ƙara samun iko sosai.9Bugu da ƙari kuma Uziya ya gina hasumiya a Yerusalem akan Ƙofar Kwana, a Ƙofar Kwari, ya kuma ƙayata su.10Ya kuma gina hasumiyar tsaro a jeji ya kuma haƙa rijiyoyi da yawa domin yana da dabbobi masu yawa a kwarurruka da kuma a saura. Yana da manoma da masu kula da itatuwan inabi a ƙasa mai duwatsu da kuma a filaye masu 'ya'yan itatuwa, domin ya ƙaunaci aikin gona sosai.11Kuma Uziya yana da mayaƙan sojoji da kezuwa yaƙi a ƙungiyance bisa yadda aka rarraba su bisa ga yawansu yadda Yeyil marubuci da Ma'asiya, hafsa, ƙarƙashin ikon Hananiya ɗaya daga ciki kwamandojin sarki.12Dukkan yawan shugabannin mayaƙa na kabilu shi ne 2600.13A karƙashin ikonsu kuma akwai soja guda 307,500 da keyin yaƙi da iko mai ƙarfi domin su taimaki sarki yaƙi da maƙiya.14Uziya ya shirya su - domin su zama da dukkan garkuwoyi suturun yaƙi da kwari da kibaw da duwatsun majajjawa.15A Yerusalem ya yi masu aikin ƙira da mutane masu fasaha suka samar su kasance a kan hasumiyoyin da kuma filayen dãga, domin su dinga harba kibiyoyi da kuma manyan duwatsu. Ikonsa ya kai har ƙasashe masu nisa, domin ya sami taimako sosai har sai da ya zama da iko sosai.16Amma bayan Uziya ya sami iko sosai sai zuciyarsa ta kumbura domin haka ya yi abin da ba shi da kyau; ya yi wa Yahweh Allahnsa zunubi, domin ya tafi gidan Yahweh domin ya ƙona turare akan bagadin ƙona turare.17Sai Azariya firist ya bi shi tare da shi kuma akwai firistocin Yahweh guda tamanin, waɗanda mutane ne masu ƙarfin hali.18Suka yi tsayayya da sarki Uziya, suka ce da shi, "Uziya ba aikinka bane ka ƙona turare, amma aikin firistoci ne, 'ya'yan Haruna waɗanda aka keɓe su ƙona turare. Ka fita daga wuri mai tsarki, domin kana da rashin aminci kuma Yahweh Allah ba zai girmamaka ba"19Sai Uziya ya yi fushi. yana riƙe da sandan tasar ƙona turare a hannunsa. Lokacin da yake fushi da firistoci, sai kuturta ta kama shi a goshi a gaban firistocin a gidan Yahweh, a gefen bagadin ƙona turare.20Sai Azariya da dukkan firistoci suka duba, sai, suka ga ya zama kuturu a goshinsa. Sai suka yi sauri suka fitar da shi daga can. Hakika, shima ya gaugauta fita, domin Yahweh ya buge shi.21Sarki Uziya ya zama kuturu har ya zuwa randa ya mutu, ya kuma zauna a keɓaɓɓen gida saboda ya zama kuturu, domin an fitar da shi daga gidan Yahweh. Ɗansa, Yotam, ya zama mai kula da gidan sarki, ya kuma yi mulkin mutanen ƙasar.22Game kuma da sauran abubuwa akan Uziya farko da ƙarshe, an rubuta su a cikin abin da annabi Ishaya ɗan Amoz ya rubuta.23Sai Uziya ya yi barci tare da kakanninsa aka binne shi a maƙabartar sarakuna, domin sun ce, "Shi kuturu ne." Yotam, ɗansa, ya zama sarki a madadinsa.
"16 ... 52"
Wannan ne garin Yahuda a yankin Aqaba
AT: "sarkin ya mutu"
Duba yadda ka fassara wannan a 14:1
AT: "haka kuma"
AT: "Ya ƙudurta ya gamshi"
Wannan gari ne a arewacin Yahuda.
Wannan gari ne a Arabiya.
AT: "kan iyakar Masar"
Rijiya babban ɗaki ne da aka tone a kasa wanda ake amfani da shi domin tara ruwan sama.
Garkuwa kariya ne na kai.
Wannan sutura ne ga jiki da aka yi da kayan haɗin karfe ko sarƙoƙi.
AT: "Ya zama da girman kai"
AT: "zuriyar Haruna"
Wannan kwano ne na musammam ko kwano da aka yi amfani da shi don ƙona turare.
AT: "Suka sa shi ya tafi da sauri"
AT: "Yahweh ya buge shi da cuta"
Wannan ya nuna cewa ya kuma zauna a keɓaɓɓen gida nesa da mutane.
AT: "dukkan abu"
AT: "Uziya ya mutu"
1Yotam yana da shekaru ashirin da biyar lokacin da ya fara mulki; ya yi mulki na shekaru sha shida a Yerusalem, sunan mahaifiyarsa Yerusha; ita ɗiyar Zadok ce.2Ya yi abin da kemai kyau a idon Yahweh, ya bi gurbin mahaifinsa Uziya ta kowanne abu. Ya kuma ƙi shiga wuri mai tsarki na Yahweh, amma duk da haka mutane basu daina aikin mugunta ba.3Ya gina ƙofar sama ta gidan Yahweh, akan tsaunin Ofel kuma ya yi gine-gine masu yawa.4Ya kuma yi gine-gine a ƙasa mai duwatsu ta Yahuda, a cikin daji kuma ya gina tsararrun wurare da hasumiyoyi.5Ya kuma yi yaƙi da mutanen Amon ya kuma cinye su. A wannan shekarar, dai mutanen Amon suka bashi talanti ɗari na zinariya, da awo goma na alkama, da awo goma na riɗi, haka mutanen Amon suka riƙa ba shi a shekara ta biyu da ta uku.6Sai Yotam ya zama da iko sosai saboda ya yi tafiya da ƙarfi tare da Yahweh Allahnsa.7Game kuma da sauran abubuwa game da Yotam, da dukkan yaƙe-yaƙensa, duba, an rubuta su a cikin littafin sarakunan Isra'ila da Yahuda.8Yana da shekaru ashirin da biyar a lokacin da ya fara mulki, ya yi mulki a Yerusalem na tsawon shekaru sha shida.9Yotam ya yi barci tare da kakanninsa, aka binne shi a birnin Dauda. Ahaz, ɗansa, ya gaje shi a sarauta.
Duba yadda ka fassara wannan a 14:1
AT: "haka kuma"
Wannan wani tudu ne a Yerusalem.
AT: "a shekara ta biyu da ta uku bayan da ya ci nasara a kansu"
AT: "yayi biyaya da Yahweh ba tare da ya kauce ba" ko "yayi rayuwa da miƙa kai ga Yahweh"
Wannan littafi ne wanda ya rigaya ya bace.
AT: "Yotam ya mutu"
1Ahaz na da shekaru ashirin ne sa'ad da ya fara mulki, kuma ya yi mulki na shekara goma sha shida a Yerusalem. Bai yi abin da ke dai-dai a fuskar Yahweh ba, kamar yadda Dauda kakansa ya yi,2Maimakon haka, ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra'ila; ya kuma ƙera zubin ƙarfe domin Ba'al.3Bugu da ƙari, ya ƙona turare a ƙwarin Ben Hinnom kuma yasa 'ya'yansa cikin wuta, bisa ga ayyukan ɓautar gumaka na mutanen da Yahweh ya kora daga ƙasarsu kafin mutanen Isra'ila.4ya yi hadaya da ƙona turare a wuraren bisa da kan tuddai da ƙarƙashin kowanne koren itace.5Saboda haka Yahweh Allahn Ahaz, ya bada shi ga hannun sarkin Aram. Aramiyawan suka buge shi kuma suka ɗauke daga gare shi gagarumin taron ɗaurarru, aka tafi da su Damaskus. Ahaz ma aka bada shi ga hannun sarkin Isra'ila wanda ya buge shi da mummunar kisa.6Gama Pekah ɗan Remaliya a rana ɗaya, ya kashe sojoji Yahuda 120,000, dukkansu maza masu ƙarfin hali ne, saboda sun yashe da Yahweh, Allahn kakanninsu.7Zikiri, mutum mai ƙarfi daga Ifraimu, ya kashe Ma'asiyya ɗan sarki, Azirikam, shugaban făda da Elkana, wanda ke bin sarki a muƙami.8Mayaƙan Isra'ila sun ɗauki kãmammu daga danginsu mata 200,000 da 'ya'ya maza da mata. Suka kuma kwaso ganima da yawa, wadda suka komo da su Samariya.9Amma akwai wani annabin Yahweh a wurin, sunansa Oded. Ya je ya sadu da mayaƙan da kezuwa Samariya. Ya ce masu, "Saboda Yahweh, Allahn kakanninku, na fushi daYahuda, ya bada su ga hannun ku. Amma kuka yanka su cikin harzuƙan da ta kai samma.10Yanzu kun yi niyar ku ajiye maza da matan Yahuda da Yerusalem kamar bayinku. Amma ba ku da laifin zunubanku ga Yahweh Allahnku?11To yanzu, ku saurare ni: Ku mayar da kamammun, waɗanda kuka ɗauko cikin naku 'yan'uwan, gama zafin fushin Yahweh na kanku."12Sa'annan waɗansu shugabannin mutanen Ifraimu- Azariya ɗan Yohanan da Berakiya ɗan Meshilemot da Yehizkiya ɗan Shallum da Amasa ɗan Hadlai, suka taso gãba da waɗanda suka dawo daga yaƙin.13Suka ce da su, "Kada ku kawo kamammun nan, gama kunyi niyar wani abu da zai kawo wa kanmu zunubi ga Yahweh, ya kuma ƙara a kan zunubanmu da laifofinmu, gama laifofinmu na da yawa, kuma akwai fushi mai zafi a kan Isra'ila."14Sai mayaƙan suka bar kamammun da ganimar a gaban shugabannin da dukkan taron.15Mutanen da aka kira sunansu suka tashi suka ɗauki kãmammun, suka suturad da dukkan waɗanda ke a tsirance cikinsu tare da ganimar. Suka suturad da su suka basu takalma. Suka basu abinci su ci su sha. Suka yi jinyar masu raunuka kuma suka sa masu rauni a kan jakuna. Suka komo da su ga iyalansu a Yeriko, (wadda ake kira Birnin Dabino). Sa'annan suka koma Samariya.16A wancan lokacin sarki Ahaz ya aiki manzanni zuwa sarakunan Assiriya domin neman su taimake shi.17Gama Idomawa sun sake kawo wa Yahuda hari, suna ɗaukar kamammu suna tafiya da su.18Filistiyawa kuma sun mamaye biranen da keƙwararru da na Negev ta Yahuda. Suka ɗauki Beth Shemesh, da Aijalon, da Gederot, da Soko tare da ƙauyukanta, da Timna tare da ƙauyukanta, da kuma Gimzo tare da ƙauyukanta. Suka tafi su zauna a wuraren.19Gama Yahweh ya ƙasƙantar da Yahuda saboda Ahaz, sarkin Isra'ila; domin ya yi mugunta a Yahuda kuma ya yi wa Yahweh zunubi mai nauyi.20Tiglat Filesar, sarkin Assiriya, ya zo wurinsa ya dame shi maimakon ya ƙarfafa shi.21Domin Ahaz ya ɗebo kaya daga gidan Yahweh da gidajen sarki da shugabanni, ya bada abubuwa masu daraja ga sarakunan Assiriya. Amma yin hakan bai sa yaci riba ba.22Wannan sarki Ahaz kuma ya yi zunubi ƙwarai ga Yahweh a lokacin wahalarsa.23Gama ya yi wa allolin Damaskus hadaya, allolin da suka kada shi. Ya ce, "Saboda allolin sarakunan Aram sun taimaka masu, zan yi masu hadaya, don su taimake ni." Amma su suka zama masa dalilin lalacewa da dukkan Isra'ila.24Ahaz ya tattara kayan ɗaki na gidan Allah ya datse su gunduwa-gunduwa. Ya ƙulle kofofin gidan Yahweh sai ya yi wa kansa bagadai a dukkan lungunan Yerusalem.25A kowanne birni a Yahuda ya yi wuraren tuddai na ƙone hadaya ga waɗansu alloli. Ya harzuƙa Yahweh, Allahn kakaninsa, ga fushi.26Yanzu sauran aikinsa, da dukkan hanyoyinsa, na farko dana karshe, Duba, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra'ila.27Ahaz ya kwanta da kakanninsa, kuma suka binne shi a birnin, a Yerusalem, amma ba su kawo shi cikin hurumin sarakunan Isra'ila ba. Hezekiya, ɗansa, ya zama sarki a madadinsa.
Duba yadda ka fassara wannan a 14:2
AT: "ya yi zunubi kamar yadda sauran sarakunan Isra'ila da ke a gabansa"
Wannan ƙwari ne a Yerusalem
AT: "ko ina"
AT: "ya taimake ku yin nasara a kansu"
AT: "Amma ku tuna, ku na da laifi ... ga Yahweh Allahn ku."
Wannan wani irin takalma ne.
AT: "Sun ba su kulawar asibiti"
AT: "suka sa waɗanda baza su iya tafiya ba a kan jakuna"
AT: "Yahweh ƙasƙantar da Ahaz"
Tiglat-Filesar III, wanda aka san shi da Ful.
AT: "lokacin da yake wahala"
AT: "zan yi masu hadaya"
"kayan ɗaki da wasu abubuwa"
AT: "a kowwane yanki na Yerusalem"
AT: "dukkan abubuwan da yayi"
Wannan litafin ya rigaya ya ɓace.
"Ahaz ya mutu"
1Hezekiya ya fara mulki a sa'ad da yake da shekaru ashirin da biyar da haifuwa; ya yi mulki shekara ashirin da tara a Yerusalem. Sunan mahaifiyarsa Abijah; ita ɗiyar Zakariya ce.2Ya yi abin da ke dai-dai a fuskar Yahweh kamar yadda mahaifinsa Dauda ya yi.3A shekara ta farko na mulkinsa, A wata na farko, Hezekiya ya ɓuɗe ƙofofin Gidan Yahweh ya gyaggyara su.4Ya kawo firistoci da Lebiyawa, ya tattaro su a farfajiyar gefen gabas.5ya ce da su, "Ku saurare ni, ku Lebiyawa! Ku keɓe kanku, ku kuma keɓe gidan Yahweh, Allahn kakanninku, ku cire ƙazamci daga wuri mai tsarki.6Gama kakanninmu sun kauce daga hanya suka yi mugun abu a fuskar Yahweh Allahnmu; suka yashe shi, suka juye fuskarsu daga wurin da Yahweh ke zamne, kuma suka juya ma wurin baya.7Haka kuma suka kukkulle ƙofofin rumfuna suka kakkashe wutan fitilun; basu ƙona turare ko miƙa baye-baye na ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra'ila ba.8Saboda haka fushinYahweh ya faɗo wa Yahuda da Yerusalem, kuma yasa suka zama abin razana da tsoro da ba'a, kamar yadda ku ke gani da idanunku.9Wannan shi yasa ubaninmu suka faɗi ta kaifin takobi, kuma 'ya'ya mazanmu da 'ya'ya matanmu da matayenmu suke cikin bautar talala.10Yanzu kuwa yana zuciyata in yi alƙawari da Yahweh, Allah na Isra'ila, saboda zafin fushinsa ya juya daga auko mana.11'Ya'yana maza kada ku zama da ragwanci yanzu, gama Yahweh ya zaɓe ku ku tsaya a gabansa, kuyi masa sujada, ku kuma zama barorinsa ku ƙona turare."12Sa'annan Lebiyawa suka tashi: Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya, na mutanen Kohatawa; da mutanen Merari, wato Kish ɗan Abdi, da Azariya ɗan Yahalelel; da Gershonawa, wato Yowa ɗan Zimma, da Iden ɗan Yowa;13na 'ya'yan Elizafan, Shimri da Yewuyel; dana 'ya'yan Asaf wato Zekariya da Mataniya;14na 'ya'yan Heman, Yehuwel da Shimei; da na 'ya'yan Yedutun wato Shemayya da Uziyel.15Suka tattara 'yan'uwansu maza suka tsarkake kawunansu, sai suka shiga ciki, kamar yadda sarki ya umarta, biye da maganar Yahweh, a tsabtace gidan Yahweh.16Firistocin suka je cikin gidan Yahweh domin su tsabtace shi suka fitar da dukkan kazamtar da suka samo a haikalin Yahweh, suka zuba a harabar gidan. Sai Lebiyawa suka kwashe ta suka kai waje zuwa rafin Kidron.17Sai suka fara aikin tsarkakewa a rana ta fari a watan ɗaya. A rana ta takwas ga wata suka kai shirayin Yahweh da aikin, Sa'annan bayan kwana takwas kuma suka tsarkake gidan Yahweh. A ranar sha shida ga watan ɗaya suka gama.18Sai suka tafi wurin sarki Hezekiya, a cikin fada, suka ce, "Mun tsabtace haikalin Yahweh dukka da bagadin baye-bayen ƙonawa tare da dukkan tasoshi, da kayayyaki, da teburan gurasar kasancewa, da dukkan kayayyakin da suke ciki.19Saboda haka muka shirya muka kuma tsarkake dukkan kayayyakin da sarki Ahaz ya lalatar sa'ad da ya yi aikin rashin aminci a lokacin da yake mulki. Duba, su na nan a gaban bagadin Yahweh."20Sa'annan sarki Hezekiya ya tashi da sassafe ya tattara shugabanin birnin; ya haura can zuwa gidan Yahweh.21Suka kawo bijimai bakwai da raguna bakwai da 'yan raguna bakwai da bunsura bakwai a matsayin baikon zunubi masarauta da wuri mai tsarki, domin kuma Yahuda. Sai ya umarci firistioci, wato 'ya'yan Haruna maza, su miƙa su a kan bagadin Yahweh.22Sai suka yanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a bagadin. Suka yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagadin; hakanan kuma suka yanka 'yan ragunan suka yayyafa jinin a bagadin.23Suka kawo bunsuran yin hadaya domin zunubi a gaban sarki da taron jama'a; suka ɗora hannuwansu a kansu.24Sai firistoci suka yankasu suka yi hadaya domin zunubi da jinin a bagadin domin ayi kafara saboda dukkan Isra'ila, gama sarki ya umarta ayi baiko na ƙonawa da baiko domin zunubi saboda dukkan Isra'ila.25Sai Hezekiya ya sanya Lebiyawa a gidan Yahweh tare da kuge da molaye da garayu. Suka jerasu bisa ga umarnin Dauda, da na Gad, mai gani na sarki, da annabi Nathan, gama umarnin daga wurin Yahweh ya zo ta wurin annabawansa.26Lebiyawa suka tsaya da kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Dauda, firistoci kuwa suna rike da ƙahonni.27Sai Hezekiya ya bada umarni a miƙa baiko na ƙonawa a bisa bagadin. Sa'ad da aka fara miƙa hadaya ta ƙonawa sai waƙa ga Yahweh ma ta fara tasowa tare da busa ƙaho da sauran kayan kiɗe-kiɗe dana bushe- bushe na Dauda sarkin Isra'ila.28Dukkan taron suka yi sujada. mawaƙa suka raira waƙa, masu ƙahonni su ka yi ta busawa; Aka yi ta yin haka har lokacin da aka gama miƙa hadayar ƙonawa.29Bayan da aka gama yin hadaya ta ƙonawa, sai sarki, tare da dukkan waɗanda suke tare da shi, suka sunkuya suka yi sujada.30Bugu da ƙari, sarki Hezekiya, tare da shugabanin suka umarci Lebiyawa su raira waƙar yabo ga Yahweh da kalmomin Dauda da na Asaf mai gani. Suka raira wakokin yabo tare da murna, suka sunkuya suka yi sujada.31Sai Hezekiya ya ce, "yanzu dai kun tsarkake kanku ga Yahweh. Sai ku zo kusa ku kawo hadayu da sadakoki na godiya a cikin gidan Yahweh. Sai taron suka kawo hadayu da sadakoki na godiya, kuma dukkan waɗanda suka yi niya sun kawo hadayan ƙonawa.32Jimilar hadayu na waɗanda taron suka kawo su ne bijimai saba'in da raguna ɗari da 'yan raguna ɗari biyu. waɗannan duka kuwa don hadaya ne ta ƙonawa ga Yahweh.33Tsarkakakkun baye-bayen kuwa bijimai ɗari shida da tumaki dubu uku ne.34Amma firistocin kima ne don haka suka kasa feɗe dukkan dabbobin da za a miƙa su baye-baye na ƙonawa, sai 'yan'uwansu, Lebiyawa, suka taimake su har aka gama aikin kamin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. gama Lebiyawan su na la'akari da tsarkake kansu fiye da firistocin.35Bugu da ƙari, akwai hadayu masu yawa na ƙonawa da aka yi; suka aikatu da kitse na hadaya ta salama, akwai kuma hadaya ta sha don kowacce hadaya ta ƙonawa. Da haka aka maido da hidimar gidan Yahweh.36Hezekiya ya ji daɗi, haka ma dukkan jama'a suka yi murna saboda abin da Allah ya yi wa jama'a, gama farat ɗaya aka yi aikin.
Wannan sunnan mace ne.
Duba yadda ka fassara wannan a 14:1.
Wannan shi ne watan farko na kalandar Yahudawa. A lokacin sashin ƙarshen watan uku da na farkon sashin watan huɗu a kalandar Yahudawa.
AT: "ku cire ƙazamtar" kp "ku cire dattin"
Duba yadda zaka fassara wannan a 21:6
Duba yadda zaka fassara wannan a 18:12
AT: "kamar yadda kuka gani da idannun ku"
AT: "Wannan shi ya sa kakanninmu suka mutu a yaƙi."
AT: "zai iya ƙin yin fushi da mu"
Duba:
Karamin magudanar ruwa wanda yake guduna a gefen gabas da Yerusalem. A wasu lokuta ana amfani dashi a zaman wurin zubar da shara.
Wannan na kusa da farkon watan ḥuɗu a kalandar Yammaci.
AT: "a lokacin da yayi mulkinsa"
Duba yadda zaka fassara wannan a 5:11.
Waɗannan baye-baye ne na shaidar godiya.
AT: "wanda ya yarda"
AT: "su na la'akari da bin ka'idodi na tsarkake kansu"
AT: "firistoci ɗin ya ƙona kitsen dabbobin da ke tare da waɗanda aka miƙa su don ya ajiye zumuntarsa mai kyau da Yahweh;" (UDB)
AT: "firistoci suka sake sa shi bisa ga tsari"
1Hezikiya ya aiko da saƙo ga dukkan Isra'ila da Yahuda, ya kuma rubutawa Manasa da Ifraimu wasiƙu, da cewa su zo gidan Yahweh a Yerusalem, su yi Idin Ƙetarewa ga Yahweh, Allah na Isra'ila,2Gama sarkin, da shugabaninsa da dukkan taron jama'a sun gana tare, cewa sun shirya su yi Idin Ƙetarewa a wata na biyu.3Ba su iya yinsa a lokacin da aka saba yi ba, saboda babu firistocin da suka tsarkake kansu, kuma mutane ba su tattaro kansu gaba ɗaya zuwa Yerusalem ba.4Wannan shirin kuwa ya yi dai-dai a idanuwan sarki da dukkan taron jama'a.5Saboda haka suka yarda su yi shelar umarnin a ko'ina a Isra'ila daga Biyarsheba zuwa Dan, cewa mutanen su zo su yi bikin Idin Ƙetarewa ga Yahweh, Allahn Isra'ila, a Yerusalem. Domin sun lura ba su taɓa yin sa da mutane da yawa ba, bisa ga abin da kea rubuce.6Sai masu kai saƙo suka tafi da wasiƙu daga sarki da shugabaninsa zuwa ga dukkan Isra'ila da Yahuda, da umarnin sarkin, Suka ce ku mutanen Isra'ila, ku juyo ga Yahweh, Allahn Ibrahim da Ishaku da Iara'ila. Saboda shi ma ya sake juyowa ga ragowarku da kuka kuɓuta daga hannun sarkin Assiriya.7Kada ku zama kamar kakaninku ko 'yan'uwanku maza, waɗanda suka kauce daga Yahweh, Allahn kakaninsu, har yasa ya bar su ga hallaka, kamar yadda kuka gani.8Yanzu kuwa kada kuyi taurin kai, kamar yadda kakaninku suka yi, ku miƙa kanku ga Yahweh, ku kuma zo wurinsa mai tsarki, wadda ya tsarkake har abada, kuyi sujada ga Yahweh Allahnku, saboda zafin fushinsa zai kauce daga aukowa maku.9Gama idan kuka juya baya ga Yahweh, 'yanuwanku maza da yaranku zasu sami tagomashi a gaban waɗanda suka tafi da su a matsayin kamammu, kuma zasu dawo wannan ƙasar. Gama Yahweh Allahnku mai alheri da jinkai ne kuma ba zai juya fuskarsa daga gare ku ba idan kun juyo zuwa gare shi."10Sai manzanin suka wuce daga birni zuwa birni a dukkan lardin Ifraimu da Manasa, har zuwa Zabulun, amma mutanen suka yi masu dariya da ba'a.11Ko da yake, waɗansu mutanen Asha da Manasa da Zabulun suka yi tawali'u suka zo Yerusalem.12Hannun Allah kuma ya zo ga Yahuda, ya basu zuciya daya, su yi abin da sarki da shugabanin suka umarta ta wurin maganar Yahweh.13Mutane da yawa, taron jama'a mai girma, suka taru a Yerusalem domin su yi Bikin Idin Abinci Marar Gami a wata na biyu.14Suka tashi suka cire bagadan da kecikin Yerusalem, da dukkan bagadan ƙona turare; suka zubar da su a kwarin Kidron.15Sa'an nan suka kashe ragunan Idin Ƙetarewa a rana ta huɗu ga watan biyu, Firistoci da Lebiyawa kuwa suka ji kunya, saboda haka suka tsarkake kansu suka kawo hadayu na ƙonawa a gidan Ubangiji.16Suka ɗauki gwalgwadon matsayinsu, bisa ga yadda dokar Musa, mutumin tsauni ta faɗa, Firistocin suka yarfa jinin da suka karɓa daga hannun Lebiyawa.17Gama akwai waɗansu da yawa a taron da ba su tsarkake kansu ba. Saboda haka Lebiyawan suka yanka ragunan Idin Ƙetarewa domin duk wanda ba shi da tsarki kuma ba zai iya tsarkake hadayunsa ga Yahweh ba18Gama babban taron mutane, yawancinsu daga Ifraimu da Manasa da Issaka da Zabulun, ba su tsarkake kansu ba, duk da haka suka ci abincin Idin, găba da rubutaccen umarnan. Gama Hezekiya ya yi masu addu'a cewa,19"Ubangiji Yahweh ya gafarci duk wanda ya sa zuciyarsa ga neman tsauni, Yahweh, tsaunin kakaninsa, ko bai da tsarki ta ka'idar tsarkakewa na wuri mai tsarki."20Saboda haka Yahweh ya saurari Hezekiya ya kuma warkar da mutanen.21Mutanen Isra'ila waɗanda suke a Yerusalem sun yi Idin Abinci Mara Gami da murna mai yawa har kwana bakwai. Lebiyawa da firistoci suka yabi Yahweh rana bayan rana, suna waƙa da kayayyakin kiɗe-kiɗe masu ƙara ga Yahweh.22Hezekiya ya yi magana ta ƙarfafawa ga dukkan Lebiyawan da suka gane hidimar Yahweh. Sai suka ci abinci a duk lokacin idin na kwana bakwai, suna miƙa hadayu na salama, suna ta furta zunubai ga Yahweh, tsauni na kakaninsu.23Dukkan taron jama'an kuwa suka shirya su ƙara yi bikin na kwana bakwai kuma, suka kuma yi haka da murna.24Gama Hezekiya sarkin Yahuda ya ba jama'an bijimai dubu ɗaya da tumaki dubu bakwai a matsayin baiko; shugabanin kuma suka baiwa jama'ar bijimai dubu ɗaya da tumakai da awakai dubu ɗaya. Firistoci da yawa kuma suka tsarkake kansu.25Dukkan jama'ar Yahuda, tare da firistoci da Lebiyawa, da dukkan mutanen da suka zo tare daga Isra'ila, da kuma baƙin da suka zo daga ƙasar Isra'ila da waɗanda ke zaune a Yahuda - Dukkansu sun yi farin ciki.26Saboda haka aka yi babban murna a Yerusalem, gama tun daga lokacin Suleman ɗan Dauda, sarkin Isra'ila, babu wani abu kamar haka a Yerusalem.27Sa'an nan firistoci da Lebiyawa suka tashi suka sa wa mutane albarka. Aka kuwa ji muryarsu, addu'arsu kuma ta kai sama, wuri mai tsarki da tsauni yake.
Isra'ilawa sukan yi wannan bukin bayan Idin Ƙetarewa a watan farko na kalandar Yahudawa. Wata na farko yazo dai-dai da ƙarshen watan uku da farkon watan huɗu a kalandar Yammaci.
Wannan wata na biyu ne a kalandar Yahudawa. Ƙarshen watan huɗu da kuma farkon watan biyar a kalandar Yammaci.
Duba yadda ka fassara wannan a 4:1
AT: "dukan mutanen Isra'ila"
Wannan ne mutumin da ke kai saƙo.
AT: "ya sa su su hallaka"
AT: "biyaya ga Yahweh" ko "ku miƙa kanku ga Yahweh"
Wannan wani karamin kwari ne a kwarin Kidron
Wannan na kusa da farkon watan biyar a kalandar Yammaci.
AT: "Sun tsaya a inda aka basu"
AT: "suka yanka ragunan hadayan Idin Ƙetarewa"
Wannan na magana ne a kan kayan kiɗe-kiɗe.
1Yanzu sa'ad da aka gama dukkan waɗannan, sai mutanen Isra'ila da kewurin suka fiita daga biranen Yahuda suka rurrushe ginshiƙan duwatsu suka kakkarye sandunan Ashera, suka kuma karya masujadar bisa da bagadun a dukkan Yahuda da Benyamin da Ifraim da Manasse, har sai da suka rurrusa su dukka. Sai dukkan mutanen Isra'ila suka dawo, kowanne ga nasa mallaka da nasa birnin.2Hezekiya ya rarraba ɓangarorin firistoci Lebiyawa kumaya shirya su bisa ga ɓangarorinsu, kowanne mutum da aikinsa, da firistoci da Lebiyawa. Yasa su su yi hadayun ƙonawa dana zumunci, su yi hidima, su yi godiya, su yi yabo a ƙofar haikalin Yahweh.3Ya kuma shirya sashin hadayar ƙonawa ta sarki daga mallakarsa, wato domin hadayun ƙonawa na safe dana yamma da hadayun ƙonawa domin ranakun Asabar, saɓobbin watanni, da sanyayyun bukukuwa, kamar yadda yake a rubuce a shari'ar Yahweh.4Bugu da ƙari, ya umarci mutanen da kezama a Yerusalem su bada ɓangaren da ya shafi firistoci da Lebiyawa, saboda su ci gaba da sa ƙarfi ga biyayya da doka na Yahweh.5Ba tare da ɓata lokaci ba bayan an aiko da umarnin, mutanen Isra'ila suka bayar hannu sake wato nunan fari na hatsi da sabon ruwan inabi da maida zuma da dukkan girbin gona. Suka kawo zakka na dukkan kome; waɗannan abu kuwa masu tarin yawa ne.6Mutanen Isra'ila da Yahuda waɗanda ke zama a biranen Yahuda suka kawo zakkar shanu da tumaki, da kuma zakkar abubuwa masu tsarkin da aka keɓe ga Yahweh tsauninsu, kuma suka tattaro su dami-dami.7A watan uku ne sa'ad da suka fara harhaɗa gudunmawarsu dami-dami, suka kuma gama a wata na bakwai.8Sa'an da Hezekiya da shugabanin suka zo suka ga dammunan, suka albarkaci sunan Yahweh da mutanensa Isra'ila.9Sa'annan Hezekiya ya tambayi firistocin da Lebiyawa game da dammunan.10Azariya, babban firist, na gidan Zadok, ya amsa masa ya ce, "Tun da mutanen suka fara kawo baye-baye cikin gidan Yahweh, Mun ci kuma mun sami isasshe, kuma muna da ragowa da yawa, gama Yahweh ya albarkaci mutanensa. Abin da ya rage shi ne wannan da yawa a nan."11Sa'an nan Hezekiya ya umarta ayi wuraren ajiya a gidan Yahweh, sai suka kuwa shirya wuraren.12Sa'an nan suka yi aminci suka kawo baye-bayen, zakka da abubuwan da kena Yahweh. Kononiya, Balebiye, shi ne shugaba mai lura da su, kuma Shimei, dan'uwansa ne na biye da shi.13Yehiyel, da Azaziya, da Nahat, da Asahel, da Yerimot, da Yozabad, da Eliyel, da Ismakiya, da Mahat, da Benaya na karkashin Konaniya da Shime'i dan'uwamsa, bisa ga zaɓen Hezekiya, sarki, da Azariya, mai lura da gidan Yahweh.14Kore ɗan Imna Balebiye da shugaba na ƙofar gabas, su ne masu lura da bayarwar yardar rai ga tsauni da shugabanci a kan rarrabawar baye-baye ga Yahweh da abubuwa mafi tsarki cikin baye-bayen.15A ƙarƙashinsa akwai Iden da Mini'amin da Yeshuwa da Shemaya da Amariya da Shekaniya a biranen firistocin. Suka cika ayyukan amanar shugabanci, Domin a bayar da waɗannan baye-baye ga 'yan'uwansu maza ɓangare ɓangare ga kowa da kowa.16Suka kuma ba wa mazajen da keshekara uku zuwa sama, waɗanda aka lisafta a rohotonin kakaninsu da suka shiga gidan Yahweh, kamar yadda ake bukata a kowacce rana, ayi aiki bisa ga muƙamansu da ɓangarorinsu.17Suka rarraba wa firistocin bisa ga rahotonin kakaninsu, haka kuma ga Lebiyawan da kesama da shekara ashirin ko fiye, bisa ga muƙamansu da ɓangarorinsu.18Suka haɗa da 'yan ƙananansu da matayensu da 'ya'ya mazansu da 'ya'ya matansu, a dukkan unguwan, gama su masu aminci ne ga kiyaye zaman tsarkinsu.19Gama firistocin wato zuriyar Haruna waɗanda ke filayen ƙauyukan da keta biranensu ne, ko kuwa a kowacce birni dai, akwai mazajen da aka sa da sunayesu, su bada rabo ga duk mazaje cikin firistoci, da kuma ga waɗanda aka lisafta a rahotonin kakaninsu cewa suna cikin Lebiyawa.20Hezekiya ya yi wannan a dukan Yahuda. Ya aiwatar da abin da kenagari, dai-dai, da kuma aminci a gaban Yahweh, tsauninsa,21A duk aikin da ya fara cikin hidimar gidan tsauni da dokoki da farilai, don kusantuwa da tsauninsa, ya aikata su da dukkan zuciyarsa, kuma ya yi nasara.
ko mai yiwuwa ne a ɖauke wannan kamar. AT: "kusan dukkan mutanen Isra'ila"
Hezekiya ya ɗauki nama da hatsi da aka yi amfani da shi domin hadaya ta ƙonawa a matsayin mallakarsa.
Wannan na maganar bukukuwa da ake yi a wasu lokuta.
"ɗaya cikin goma na dukkan amfanin gona"
Wata na uku a kalandar Yahudawa. Wanda yazo daidai da lokacin girbi da kuma farkon rani. Ƙarshen watan biyar da farkon watan shida a kalandar Yammaci.
Babban firist yan miƙa yatsa zuwa tarin abin da ya rege.
AT: "Hezekiya ya umarti firistoci da Lebiyawa su shirya ɗakunan ajiya a gidan Yahweh"
Waɗannan sunayen mutane ne.
"A ƙarƙashin ikonsa"
"kowa da kowa"
AT: "daga shekara uku da sama da haka"
AT: "yadda ake buƙata a kowacce rana"
1Bayan waɗannan abubuwan da amintattun ayyuka, Senakirib sarkin Asuriya, ya zo ya shiga Yahuda. Ya kafa sansani ya kai ma birane masu garu hari, da niyar ya yi kamu domin kansa.2Sa'ad da Hezekiya ya ga Senakirib ya iso kuma ya yi niyar yaƙi da Yerusalem,3sai ya yi shawara da shugabanninsa da mazajensa masu iko su tsayar da ruwayen da kefitowa daga maɓuɓɓugar da suke bayan birnin; suka taimake shi ya yi hakan.4Saboda haka mutane da yawa suka taru suka tsayar da dukkan maɓuɓɓugai da rafuffuka da kegudu ta cikin ƙasar. Su na cewa, "Me zai sa sarakunan Asuriya su zo su sami ruwa mai yawa?"5Hezekiya ya yi karfin hali ya sake gina dukkan ganuwar da aka rushe, ya gina hasumiyar da inganci, haka kuma ɗaya garun da kewaje. Ya kuwa ƙara ƙarfin Milo a birnin Dauda, ya kuma yi makamai na yaƙi da yawa da garkuwoyi.6Sai ya sa manyan sojoji su shugabanci mutane. Ya tattaro su gareshi a dandalin ƙofar birnin ya yi magana ta ƙarfafawa da su. Ya ce,7"Ku ƙarfafa da nagartaccen ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro ko ku yi fargaba saboda sarkin Asuriya da dukkan sojojin da ketare da shi, gama wani yana tare da mu wanda ya fi waɗanda ke tare da shi.8Hannun mutum ne kawai ke tare da shi, amma mu Yahweh tsauninmu yake tare da mu domin ya taimake mu ya yi mana yaƙi." Mutane kuwa suka ta'azantu da maganar Hezekiya, sarkin Yahuda.9Bayan wannan, sai Senakirib sarkin Asuriya ya aika da barorinsa zuwa Yerusalem (Yanzu dai yana a gaban Lakish, kuma dukkan mayaƙansa na tare da shi), ga Hezekiya, sarkin Yahuda da dukkan Yahuda waɗanda ke a Yerusalem. Ya ce,10Ga abin da Senakirib, sarkin Asuriya, ya ce: "Ga me kake dogara a kai don ka dage wa yaƙi kewaye da kai a cikin Yerusalem?11Ba ruɗin ku Hezekiya yake yi ba, don ya sa ku mutu da yunwa da ƙishi, sa'ad da yake gayă maku, 'Yahweh tsauninmu zai cece mu daga hannun sarkin Asuriya'?12Ba wannan Hezekiyan ba ne yake ɗauke wuraren bisansa da bagadensa ya kuma umarci Yahuda da Yerusalem, 'A kan bagadi guda ne ya wajaba ku yi sujada, a kansa ne kuma zaku ƙona hadayunku?13Ba kun san abin da ni da kakannina muka yi wa dukkan manyan mutane na waɗansu ƙasashen ba? Allolin manyan mutane na ƙasashe sun iya ceton ƙasashensu daga hannuna?14Daga cikin dukkan manyan waɗancan al'ummai waɗanda kakannina suka hallakar kakaf, da wanda ya iya ceton mutanensa daga hannuna? Donme tsauninku zai iya cetonku daga hannuna?15Yanzu fa kada ku yarda Hezekiya ya ruɗe ku ko ya ɓadda ku haka. Kada kuwa ku gaskata shi, gama ba wani tsauni na wata al'umma ko mulki wanda ya taɓa ceton mutanensa daga hannuna, ko kuma daga hannun kakannina. Wane ne tsaunin ku har da zai iya cetonku daga hannuna?"16Barorin Senakirib sun yi maganganu fiye da haka găba da Yahweh tsauni da bawansa Hezekiya.17Senakirib ya kuma rubuta wasiƙu don ya yi ba'a ga Yahweh, tsauni na Isra'ila, ya kuma yi maganar găba da shi. Ya ce, "Kamar yadda allolin al'ummai na sauran ƙasashe basu ceci mutanensu daga hannuna ba, hakanan kuma tsaunin Hezekiya ba zai iya ceton mutanensa daga hannuna ba."18Suka yi kuka da babban murya, da harshen Yahudanci, suka yi ta magana da mutanen Yerusalem waɗanda suke kan garu, don su tsoratar da su, su kuma firgita su, domin su danƙe birnin.19Suka yi magana a kan tsauni na Yerusalem kamar yadda suka yi ta magana a kan allolin waɗansu mutanen duniya, waɗanda aikin hannuwan mutane ne kurum.20Sarki Hezekiya da annabi Ishaya ɗan Amoz, suka yi addu'a saboda wannan al'amari kuma suka yi kuka zuwa sama21Yahweh kuwa ya aiki mala'ika, wanda ya karkashe mazajen yaƙi da manyan jarumawa da shugabanni na sarkin a sansanin. Saboda haka Senakirib ya koma ƙasarsa cike da kunya. Sa'ad da ya shiga gidan tsauninsa, sai waɗansu daga cikin 'ya'yan cikinsa suka kashe shi da takobi.22Ta haka Yahweh ya ceci Hezikiya da mazaunan Yerusalem daga hannun Senakirib, sarkin Asuriya, daga kuma hannun dukkan sauran, ya kuma hutar da su ta kowace ɓangare.23Mutane da yawa suka kawo wa Yahweh sadakoki a Yerusalem, da kuma abubuwa masu daraja ga Hezekiya sarkin Yahuda, saboda haka ya sami ɗaukaka a idanun dukkan sauran al'ummai tun daga lokaci nan har zuwa gaba.24A kwanakin nan kuwa Hezekiya ya yi ciwo gab da mutuwa. Sai ya yi addu'a ga Yahweh, wanda kuwa ya yi magana da shi ya ba shi alamar cewa zai warke.25Amma Hezekiya bai mayar da godiya a kan taimakon da ya ba shi ba, domin a zuciyarsa akwai girman kai. Saboda haka hasala ta auka kansa, da kan Yahuda da Yerusalem.26Duk da haka dai, daga baya Hezekiya ya ƙasƙantar da kansa saboda fahariyar zuciya da ya yi, da shi da mazaunan Yerusalem, don haka hasalar Yahweh ba ta faɗo masu ba a kwanakin Hezekiya.27Hezekiya yana da dukiya ƙwarai yana kuma da girma. Sai ya gina wa kansa taskoki inda zai ajiye azurfa da zinariya da duwatsu masu daraja da kayan yaji da garkuwoyi da dukkan tasoshi, da kwanoni masu daraja.28Yana kuma da ɗakunan ajiya na hatsi, da na ruwan inabi dana mai, da wuraren turke dabbobi na kowanne iri, yana kuma da garkuna a cikin rufar dabbobinsa.29Bugu da ƙari, ya kuma tanada wa kansa birane da mallakar garkunnan tumaki da na shanu a yalwace. Gama tsauni yaba shi wadata mai yawa.30Hezekiyan nan ne kuwa ya datse ruwan da yake gangarowa daga kogin Gihon, ya kuma kawo su su gangara zuwa wajen yammacin birnin Dauda. Hezekiya ya yi nasara da dukkan ayyukansa.31Ko da shi ke, game da jakadun hakiman Babila, waɗanda aka aika su tambaye shi game da waɗanda suka san irin abin al'ajibin da aka yi a ƙasar, sai tsauni ya ƙyale shi kurum, don ya jaraba shi ya san dukkan abin da kea zuciyarsa.32Sauran ayyukan Hezekiya da kyawawan ayyukansa, gashi an rubuta su a wahayin annabi Ishaya ɗan Amoz a littafin Sarakunan Yahuza da na Isra'ila.33Sai Hezekiya ya rasu, suka bizne shi a sashe na bisa na hurumin 'ya'yan Dauda, maza da dukkan Yahuda da mazaunan Yerusalem suka girmama shi sa'ad da ya rasu, sai Manasa ɗansa ya gaji gădon sarautarsa.
Hezekaya ne yayi waɗannan amintattun ayyukan
Sun rufe maɓuɓɓugar da ke bayan birnin don kada mutanen su samu ruwan.
Sarakunan Asiriya ba za su zo su sami ruwa ba. Masu fassara zasu so su juya "Sarkin Asiriya," za su juya shi "Sarakunan Asiriya," domin babu wani rubutu da ya shaida na "Sarki."
Duba yadda ka fassara wannan a 15:8
AT: "Hezekiya ya yi ƙarfin hali ya kuma ƙarfafa mutanen su sake gina"
Wannan ɓangaren ganuwa ne da ke da ƙarfi, ya kasance a gefen arewacin Yerusalem.
AT: "gama Allahmu yana tare da mu da yana da iko fiye da su"
AT: "ikon mutum"
Wannan wani birni ne a Yahuda
At: "Baka iya dage wa yaƙi kewaye da kai a cikin Yerusalem"
AT: "Hezekiya yana ruɗin ku ... da yake gaya maku, Yahweh ... Asiriya"
AT: "Shi wannan Hezekeya ya ɗauke"
AT: "Kun san abin da ... ƙasashen ba"
AT: "Allolin ƙungiyoyin mutanen ƙasashe sun iya ... iko"
AT: "Babu dalilin da Allahnku zai iya ... ƙarfi" (Duba:
Waɗannan jumloli biyu na nufin abu ɗaya ne. kuma yana ƙarfafa tsananin tsoro. AT: "don su ba su tsoro sosai."
AT: "Suka yi izgili da Allah na Yerusalem kamar yadda suka yi ta izgili a kan allolin waɗansu mutanen duniya" (Duba: )
AT: "roƙi Allah"
ya sha -"shan kunya" "kunya"
AT: "haikali na alollinsa"
A nan "hutu" na nufin salama. AT: "ka basu salama da dukkan makwabtan kasashe" (Duba: )
AT: "don dukkan al'ummai kewaye da su sun sani"
AT: "ya kasance da fahariya"
Duba yadda ka fassara wannan a 9:25
inda ake ajiyan ƙananan dabbobi.
Babu kuma waɗannan litattafan..
Duba yadda ka fassara wannan a 9:29
1Manasse yana da shekara goma sha biyu sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki shekaru hamsin da biyar a Yerusalem.2Ya yi abin da kemugunta a fuskar Yahweh, kamar ƙazantattun abubuwan da al'umman da Yahweh ya kore su a gaban mutanen Isra'ila.3Gama ya gina wuraren kan tudun da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe, kuma ya gina bagadai domin Ba'aloli. Ya ƙera sandunan Ashera, kuma ya russuna wa dukkan taurarin sammai ya yi masu sujada.4Manasse ya gina bagadin a gidan Yahweh, koda shi ke dai Yahweh bai umarta ba, "A Yerusalem ne sunana zai kafu har abada."5Ya gina bagadai ga dukkan taurarin sama a cikin shirayu biyun da kegidan Yahweh.6A Kwarin Ben Hinnom ya sa 'ya'yansa maza a wuta. Ya aikata tsafe-tsafen tsubbu; ya yi karatun baƙaƙen zabura; kuma ya tuntuɓi masu magana da matattu da ruhohi. Manasse aikata miyagun ayyuka da dama a fuskar Yahweh, ya kuma tsokani Yahweh ga fushi.7Sarafaffen siffar da ya yi, ya sa shi a gidan tsauni. A kan wannan gidan ne tsauni ya yi magana da Dauda da Suleman ɗansa. Ya ce, "A wannan gidan da Yerusalem ne, waɗanda na zaɓa daga dukan ƙabilun Isra'ila, cewa zan kafa sunana har abada.8Ba zan ƙara fitar da mutanen Isra'ila daga ƙasar dana ba wa kakaninsu ba, idan za su yi biyayya su kiyaye dukkan abin dana umarce su, su bi dukkan dokoki da farillai dana umarta ta hannun Musa."9Manasse ya jagoranci Yahuda da mazaunan Yerusalem ga yin mugunta fiye da al'umman da tsauni ya hallakar a gaban mutanen Isra'ila.10Yahweh ya yi magana da Manasse da jama'arsa amma babu wanda ya kula.11Saboda haka Yahweh yasa sarakunan yaƙi na sarkin Asiriya su kama Manasase su ɗaure shi da sarƙoƙin tagulla su kai shi Babila.12Sa'ad da Manasse ke shan wahala, sai ya roƙi Yahweh, tsauninsa, ya ƙasƙantar da kansa sosai a gaban tsauni na kakaninsa.13ya yi addu'a zuwa gare shi; sai ya roƙi tsauni, sai tsauni ya ji rokonsa ya komo da shi Yerusalem, ga mulkinsa. Sa'an nan ne Manasse ya sani Yahweh shi ne tsauni.14Bayan haka sai Manasse ya gina garu a bayan birnin Dauda a gefen yammacin Gihon, a kwari, zuwa Ƙofar Kifi. Ya kewaye tudun Ofel, bayan wannan kuma ya gina shi da tsayi sosai. Sa'an nan yasa sarakunan yaƙi a garuruwa masu garu na Yahuda.15Ya kwashe baƙin alloli, wato gumaku daga cikin gidan Yahweh, da dukkan bagadin da ya giggina a bisa dutse na gidan Yahweh da Yerusalem. Ya zubar da su a bayan birnin.16Ya kuma komar da bagadin Ubangiji ya miƙa hadayu na salama dana godiya a kansu; ya kuma umarci Yahuda da ta bauta wa Yahweh, tsauni na Isra'ila.17Duk da haka, jama'a suka ci gaba da miƙa hadayunsu a masujadar bisa, amma ga Yahweh, tsauninsu kaɗai.18Game da sauran ayyukan Manasse da addu'o'insa ga tsauninsa, da abubuwan da masu gani suka faɗa masa cikin sunan Yahweh, tsauni na Isra'ila, gasu, suna a rubuce cikin ayyukan sarakunan Isra'ila.19A cikin rahoton akwai tarihin addu'arsa, da yadda tsauni ya ƙarɓi rokonsa, akwai kuma rahoton dukkan zunubinsa da rashin amincinsa, da wuraren da ya gina masujada a bisa, ya kafa sandar Ashera da sarafaffun siffofi, kamin ya ƙasƙantar da kansa - suna nan a rubuce a Tarihin Masu Duba.20Haka dai Manasse ya kwanta tare da kakaninsa, suka binne shi a gidansa. Sai Amon, ɗansa, ya zama sarki a madadinsa.21Amon yana da shekara ashirin da biyu sa'ad da ya fara sarauta, ya yi shekara biyu yana mulki a Yerusalem.22Ya aikata mugunta a gaban Yahweh, kamar yadda Manasse, mahaifisa ya yi. Amon ya miƙa hadayu ga dukkan siffofin da mahaifinsa Manasse ya yi, ya bauta masu.23Bai ƙasƙantar da kansa a gaban Yahweh, kamar yadda mahaifinsa Manasse ya yi ba. Maimakon haka, shi wannan Amon fa ya ƙara yin zunubi gaba-gaba.24Sai fadawansa suka yi masa maƙarkashiya suka kashe shi a gidansa.25Amma jama'ar ƙasar suka ƙarkashe dukkan waɗanda suka yi wa sarki Amon maƙarƙashiya, sai suka naɗa Yosiya, ɗansa, ya gaji gadon sarautarsa.
Duba yadda zaka fassara wannan a 14:1
AT: "kamar ƙazantattun abubuwan da al'umman da Yahweh ya kore su a gaban mutanen Isra'ila."
AT: "Zan bayyana kaina ga mutane"
Wannan na nufin al'adar ƙona 'ya'ya da rai a matsayin hadaya zuwa ga gumaka.
Wani wuri kusa da Yerusalem da an san shi da suna Gehenna.
AT: "mutanen Yahuda da Yerusalem "
AT: "kawo masu hari ta"
AT: "kama Manasase kuma suka kai shi bauta a Babila"
Jumla na biyu na ƙara ƙarfafa jumla na farko ne wanda ya nuna zurfafan addua'an Manasse yayi. AT: "Ya yi addu'a zuwa ga Allah kuma ya roƙi Allah"
Duba:
AT: "baƙin alloli na wasu kasashe"
AT: "ya umarci jama'ar Yahuda"
Wannan tarihi ne na Isra'ila da ya rigaya ya ɓace.
Wannan tarihi ne da ya rigaya ya ɓace.
AT: "Manasse ya mutu, kuma iyalinsa sun bizine shi"
Duba yadda ka fassara wannan a 14:1
AT: "Amon ƙara yin zunubi da yawa"
"ƙulle ƙulle a sirri"
1Yosiya yana da shekara takwas sa'ad da ya fara sarauta, ya yi mulki shekara talatin da ɗaya a Yerusalem.2Ya yi abin da ke dai-dai a fuskar Yahweh, ya kuma yi tafiya a hanyoyin Dauda mahaifinsa, kuma bai juya dama ko hagu ba.3Gama a shekara ta takwas na mulkinsa, tun yana yaro ya fara biɗan tsauni na Dauda, kakansa, a shekara ta goma sha biyu ne ya fara tsarkake Yahuda da Yerusalem daga tsafin wuraren bisa da sandar Ashera da sarafaffun siffofi da zuben siffofin ƙarfe.4Mutanen suka rurrusa bagadan Ba'alolin a gabansa; ya rurrusa bagadan turaren da kebisansu. Ya karya sandar Ashera da saraffaffun sifoffi da siffofin ƙarafuna har suka ragargaje zuwa ƙura. Ya yayyafa ƙurar a kan kaburburan waɗanda suka yi masu hadaya.5Ya ƙona kasusuwan firistocinsu a bagadansu. Ta haka ya tsarkake Yahuda da Yerusalem.6Ya yi haka kuma a biranen Manasa da Ifraimu da Saminu har zuwa Naftali da lalatattun wurare da kekewaye da su.7Ya rusar da bagadan; ya ragargaza sandar Ashira da sarafaffun siffofi zuwa gǎri, ya kuma rurrusa bagadan turare a dukkan ƙasar Isra'ila; sa'an nan ya koma Yerusalem.8Yanzu a shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, bayan Yosiya ya tsarkake ƙasar da haikalin, ya aiki Shafan ɗan Ma'aseya da gwamnan birnin da Yowa ɗan Yowahaz magatakarda, da su gyaggyara gidan Yahweh tsauninsa.9Suka je wurin Hilkaya, babban firist, suka danƙa masa kuɗin da aka kawo gidan Yahweh wanda Lebiyawa da masu gadin ƙofofi suka tara daga Manasse da Ifraimu, daga dukkan ragowar Isra'ila, daga dukkan Yahuda da Benyamin da kuma daga mazaunan Yerusalem.10Suka danƙa kuɗin ga mazan da kelura da gidan Yahweh. Waɗannan mazan ne ke biyan ma'aikatan da ke gyaggyarawa da adana haikalin.11Suka biya kafintoci da magina kuɗin da zasu sayi sassaƙaƙƙen duwatsu da katakai domin yin tsaiko kuma da tankaru don gine- ginen da waɗansu sarakuna na Yahuda suka bar su suka lalace.12Mazajen sun yi aikin da aminci. Masu shugabancinsu su ne Yahat da Obadiya wato Lebiyawa, 'ya'yan Merari; da Zekariya da Meshullam, daga 'ya'ya mazan Kohatawa. Sauran Lebiyawan waɗanda dukkansu ƙwararrun mawaƙa ne, sun yi shugabancin ma'aikatan.13Waɗannan Lebiyawan ne ke shugabancin masu ɗaukan kayan gini da duk sauran ma'aikata daban-daban. Akwai kuma Lebiyawan da kemasu rubuce=rubuce da masu gudanar da shugabanci da masu gadin ƙofofi.14Sa'ad da suka kawo kuɗin da aka kawo gidan Yahweh, Hikaya firist ya samo littafin shari'a ta Yahweh wanda aka bayar ta wurin Musa.15Hikaya ya cewa Shafan magatakarda, "Na sami littafin shari'a a gidan Yahweh." Hikaya ya kawo littafin ga Shafan.16Shafan ya kai ma sarki littafin, ya kuwa ba shi rahoto, cewa, "Barorinka na yin dukkan abubuwan da aka basu amanan yi.17Suka tattaro kuɗin da aka samu agidan Yahweh, sai suka bayar da shi ga hannun shugabannin lura da mazan aikin."18Shafan magatakarda ya faɗa wa sarki, "Hilkaya firist ya ba ni littafi." Sa'an nan Shafan ya karanta wa sarkin.19Ya zamana kuwa a sa'an da sarki ya ji kalmomin shari'a, sai ya yayyage tufafinsa.20Sarkin ya umarce Hilkaya da Ahikam ɗan Shafan da Abdon ɗan Micah da Shafan magatakarada da Ashaya, baransa, cewa,21"Ku je ku bincika nufin Yahweh domina, da kuma domin waɗanda aka bar su a Isra'ila da Yahuda, saboda kalmomin littafi da aka samo. Gama yana da girma, hasalar Yahweh da aka zubo mana. yana da yawa, saboda kakaninmu basu saurari kalmomin wannan littafi ba don su yi biyayya da dukkan abin da aka rubuto cikinta."22Saboda haka Hilkaya, da waɗanda sarki ya umarta, suka je wurin annabiya Huldah, matar Shallum ɗan Tokhat ɗan Hasra, mai lura da tufafin firistoci (tayi zama a Yerusalem a Gunduma ta Biyu), sai suka yi magana da ita haka.23Sai ta ce masu, "Ga abin da Yahweh, tsaunin Isra'ila, ya ce: "Gaya wa mutumin da ya aiko ku wuri na,24Ga abin da Yahweh ya faɗi: Duba. 'Ina gab da kawo bala'i a nan wurin da kan mazaunanta, dukkan la'anonin da aka rubuta a littafi da suka karanta a gaban sarkin Yahuda.25Saboda sun ƙi ni kuma sun ƙona turare ga waɗansu alloli, saboda su zuga ni ga fushi da dukkan ayyukan da suka aikata- Don haka fushi na zai zubo a wannan wurin, kuma ba za a datse shi ba.'26Amma ga sarkin Yahuda, wanda ya aiko ku ku tambayi Yahweh abin da zai yi, ga abin da zaku gaya ma sa, 'Yahweh, tsauni na Isra'ila ya faɗi haka: Game da maganganun da ka ji,27saboda baka taurare zuciyarka ba, kuma ka ƙasƙantar da kanka a gaban tsauni sa'ad da ka saurari maganganu game da wannan wurin da mazaunanta, kuma domin ka ƙasƙantar da kanka a gaba na, ka yayyaga taufafinka ka yi kuka a gabana, Ni kuma na saurare ka - wannan furcin Yahweh ne -28duba, Zan tattara ka da kakaninka. Za a tattara ka zuwa kabarinka cikin salama, kuma idanuwanka ba za su ga bala'in da zan kawo a wurin nan da mazaunanta ba." Mazajen nan suka kai wa sarki wannan saƙon.29Sa'an nan sarkin ya aiko manzanni su tattaro dukkan dattawan Yahuda da Yerusalem tare.30Sa'an nan sarkin ya haura zuwa gidan Yahweh, da dukkan mazajen Yahuda da mazaunan Yerusalem, da firistoci da Lebiyawa da dukkan mutane, daga manya zuwa ƙanana. Sa'an nan ya karanto ga saurarawarsu dukkan kalamomin littafin Alƙawari da aka samo a gidan Yahweh.31Sarkin ya tsaya a wurinsa ya yi alƙawari a gaban Yahweh, ya yi tafiya bisa ga jagorancin Yahweh, ya kuma kiyaye dokokinsa da farillansa da umarnansa, da dukkan zuciyarsa da dukkan ransa, ya yi biyayya da maganganun alƙawari da kea rubuce a wannan littafi.32Ya sa dukkan waɗanda aka same su a Yerusalem da Benyamin su tsaya a kan alƙawarin. Mazaunan Yerusalem sun yi aiki cikin biyayya ga alƙawarin tsauni, tsauni na kakanninsu.33Yosiya ya ɗauke dukkan ƙazamtattun abubuwa daga ƙasashen da suke na mutanen Isra'ila. Ya sa kowa a Isra'ila ya bauta wa Yahweh, tsauninsa. Gama a dukkan kwanakinsa, ba su juya daga bin Yahweh, tsaunin kakaninsu ba.
Duba yadda ka fassara wannan a 14:1
AT: "kuma bai yi rashin biyayya ga Allah ba" ko "yayi biyayya ga dukan dokokin Allah"
AT: "har suka ragargaje yadda iska zai iya kwashen su"
AT: "sun lalace gabaki ɗaya" (Duba: )
Duba:
"suka danƙa masa haƙin lura da kuɗi"
AT: "suka bari su ruɓe"
Duba:
AT: "Waɗannan Lebiyawan ne ke shugabancin mutanen da k kowanne irin aikin gini."
Duba:
AT: "dukkan abubuwan da ka basu amanan yi"
AT: "Suka taru"
wannan jumlar shaida ne; yana nuna cewa abinda ya biyo baya na da muhimminci a wannan labarin. AT: "Yanzu, ka lura da abinda ya faru a gaba:"
Duba:
AT: "Ka tambayi Yahweh abinda yake so in yi"
AT: "bisa ga abinda aka rubata a litafin"
Duba:
AT: "mai lura da tufafin firistoci"
AT: "sai suka yi magana da ita kamar haka"
"sun ba ni haushi"
"Ana maganar emoshen kamar fushi a Littafi Mai Tsarki kamar ruwa. AT: "saboda haka zai zama kamar wuta da na zuba a kansu, babu abinda zai hana wutan"
AT: "Yahweh, Allah na Isra'ila ya faɗi haka: Game da maganganun da ka ji, don zuciyarka na da taushi - ka yarda ka canza"
Wannan alama ce ta tuba da tsoro.
AT: "za ka mutu"
AT: "ba za ka ɗanɗana ba"
AT: "kowa da kowa"
AT: "karanto masu"
AT: "tsayawa a inda ya saba tsayawa a kofar shiga haikali"
Waɗannan jumlolin biyu karin magana ne da ke nufin mutum gaba ɗaya. AT: "tare da dukkan kansa" ko "dukkan zuciyarsa."
"duk waɗanda ya zauna a Yerusalem da Benyamin"
AT: "a yi biyayya da alƙawarin"
Waɗannan ne allolin da ke abin kyama ga Allah.
1Yosiya ya kiyaye Idin Ƙetarewa ga Yahweh a Yerusalem, kuma suka kashe 'yan ragunan Idin a rana ta goma sha huɗu ga wata na fari.2Ya sa firistocin a matsayinsu ya ƙarfafa su a cikin hidimar gidan Yahweh.3Ya cewa Lebiyawan da suka koyar da dukkan Isra'ila waɗanda aka keɓe ga Yahweh, "Ku sa akwati mai tsarki a gidan da Suleman ɗan Dauda, sarkin Isra'ila ya gina. Kada ku dinga ɗaukar sa a bisa kafaɗunku kuma. Yanzu ku bauta wa Yahweh tsauninku, ku yi wa mutanensa Isra'ila hidima.4Ku shirya kanku ta sunayen gidajen kakaninku da ɓangarorinku, bisa ga rubutaccen umarnin Dauda, sarkin Isra'ila, da ta Suleman, ɗansa.5Ku tsaya a wuri mai tsarki, kuna ɗaukan matsayinku tare da ɓangarorin 'yan'uwanninku maza ta cikin gidajen kakaninku da zuriyoyin mutane, kuna kuma ɗaukan matsayinku tare da ɓangarorinku ta cikin gidajen kakaninku na Lebiyawa.6Ku kashe 'yan ragunan Idin Ƙetarewa, ku tsarkake kanku, ku shirya ragunan domin 'yan'uwanku maza, kuyi bisa ga maganar Yahweh da aka bayar ta hannun Musa."7Yosiya ya baiwa dukkan mutane 'yan raguna dubu talatin da 'yan awakai daga turkuna domin baikon Idin Ƙetarewa ga dukkan waɗanda suka kasance. Ya kuma bada bijimai dubu talatin; waɗannan daga mallakar sarki ne.8Shugabaninsa sun bayar da baikon yardar rai ga mutane da firistoci da Lebiyawa. Hilkaya da Zekariya da Yehiyel da manyan ma'aikatan da kelura da gidan tsauni, sun ba firistoci baikon ƙananan shanu 2,600 da bijimai ɗari uku domin Idin Ƙetarewa.9Konaniya kuwa da Shemaya da Netanel, 'yan'uwansa maza, da Hashabiya da Ye'iyel, da Yozabad, waɗanda ke shugabancin Lebiyawa, sun ba Lebiyawan baiko domin Idin Ƙetarewa ƙananan shanu dubu da bijimai ɗari biyar.10Don haka aka shirya hidimar, sai firistocin suka tsaya bisa ga matsayinsu, da Lebiyawan ta ɓangarorinsu, cikin yin biyayya da umarnin sarki.11Suka kashe 'yan ragunan Idin Ƙetarewa, sai firistoci suka zuba jinin da suka karɓo daga hannun Lebiyawan, sai Lebiyawan suka feɗe 'yan ragunan.12Suka cire hadayun ƙonawa, don su rarraba su ga ɓangarorin gidajen kakanin mutanen, suƙa miƙa su ga Yahweh, kamar yadda aka rubuta a cikin littafin Musa. Suka yi haka kuma da bijiman.13Suka gaggasa 'yan ragunan Idin Ƙetarewan da wuta bisa ga umarni. Game da tsarkakkun baye-bayen, suka dafa su cikin ruwa a tukwane daban-daban, suka kuma ɗauka da sauri suka kai wa dukkan mutane.14Suka shirya baye-baye daga baya domin kansu da firistocin, saboda firistocin, wato zuriyar Haruna, suna fama da miƙa hadaya ta ƙonawa da kitsen har sai dare ya yi, saboda haka Lebiyawan sun shirya baye-bayen domin kansu da firistoci, zuriyar Haruna.15Mawaƙan, zuriyar Asaf, suna wurin, bisa ga bishewar Dauda da Asaf da Heman da Yedutun mai duba na sarki, kuma masu tsaro suna a kowacce ƙofa. Ba za su taɓa barin wurin tsayawarsu ba, saboda 'yan'uwansu Lebiyawa sun shirya abu dominsu.16Don haka, a lokacin nan dukkan hidimar Yahweh ana yi domin bikin Idin Ƙetarewa ne da miƙa baye-bayen ƙonawa a bagaden Yahweh, kamar yadda sarki Yosiya ya umarta.17Mutanen Isra'ilan da suka kasance sun kiyaye Idin Ƙetarewa a lokacin, sa'an nan kuma da Shagulgulan Gurasa Marar Gami na kwana bakwai.18Irin wannan bikin Idin Ƙetarewan ba a taɓa yin sa a Isra'ila ba tun daga kwanakin su annabi Sama'ila, ba kuwa wani daga cikin sauran sarakunan Isra'ila da ya yi hidimar bikin Idin Ƙetarewa kamar yadda Yosiya ya yi, tare da firistoci da Lebiyawa da dukkan mutanen Isra'ilan da suka kasance, kuma da mazaunan Yerusalem.19Wannan Idin Ƙetarewa an kiyaye shi ne a shekara ta goma sha takwas na mulkin Yosiya.20Bayan dukkan wannan, bayan Yosiya ya shirya haikalin bisa ga tsari, Neko, sarkin Masar, ya hauro ya yi faɗa da Karkemish a Kogin Yuferetis, sai Yosiya ya je ya yi faɗa da shi.21Amma Neko ya aiko wakilai gun sa, cewa, "Mene ne zan yi da kai, sarkin Yahuda? Ba na zuwa găba da kai yau, amma găba da gidan da nake yaƙi da su. tsauni ya umarce ni da in yi sauri, saboda haka ka janye daga shisshigi da Allah, wanda ke tare da ni, don zai iya hallaka ka."22Koda shi ke, Yosiya ya ƙi ya juyo daga gare shi. Ya ɓoye kamaninsa don ya yi yaƙi da shi. Bai saurari maganar Neko da ta zo daga bakin Allah ba; sai ya je ya yi faɗa a Kwarin Megiddo.23Jarumawa suka harbi Yosiya, sai sarki ya cewa barorinsa, "Ku tafi dani, gama na sami mumunar rauni,"24Sai barorinsa suka ɗauke shi daga karusar, suka sa shi a karusa ta biyu. Suka kai shi Yerusalem, inda ya mutu. Aka binne shi a wurin binne kakaninsa. Dukkan Yahuda da Yerusalem suka yi makoki domin Yosiya.25Irimiya ya yi makoki domin Yosiya; dukkan mazaje da mata mawaƙa suna maƙoƙi game da Yosiya har yau. Waɗannan waƙoƙin suka zama al'ada a Isra'ila; Suna a rubuce a waƙoƙin maƙoƙi.26Game da sauran abubuwan da suka shafi Yosiya, da nagargarun ayyukansa da ya yi cikin biyayya da abin da kea rubuce a shari'ar Yahweh -27kuma dukkan ayyukansa, daga farko zuwa karshe, na a rubuce cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra'ila.
Wata na farko a cikin kalandar Yahudawa. Rana ta goma sha huɗu na kusa da farkon watan huɗu a kaladar Yammaci.
AT: "Ya gaya wa firistoci ayyukan da zasu yi"
AT: "mutanen sun yi gini a ƙarkashin shugabancin sarki solomon"
AT: "ƙabilunku da iyalanku"
"mai tsarki" na nufin wuri mafi tsarki a cikin haikali. AT: "dauki matsayin ka a cikin haikali"
Wannan na nufin aikin da aka ƙungiyoyin wa kowanne Balewi.
Duba: da
Wannan 'ya'yan awaki ne.
"sun shirya komai domin hidimar Idin Ƙetarewa."
"jinin da Lewiyawa suka ba su"
"suka dafa"
Duba:
Duba yadda ka fassara wannan a 30:16
Dukkan abubuwan da ke da alaƙa da hadaya da bautan Yahweh a lokacin Idin Ƙetarewa ya zama sujada "hidima".
Farkon yin amfani da sunan al'ummar Isra'ila gabaki ɗaya, amma amfani da sunan na biyu na nufin musamman ga yarurrukan arewa da mulkin Isra'ila
Duba:
AT: "farfado da tsarin sujada a haikali"
AT: "Babu dalilin da zai sa ka kai mani hari , sarkin Yahuda"
AT: "Ba na faɗa da ƙasar ka"
AT: "gãba da Babila, gãba waɗanda nake yaƙi da su"
"ya yi yaƙi da sojojin Babila"
"daga Allah" ko "Allah ya fada masa"
Duba yadda ka fassara wannan a 5:9
1Sa'an nan mutanen ƙasar suka ɗauki Yehowahas ɗan Yosiya, suka maida shi sarki a madadin mahaifinsa a Yerusalem.2Yehowahas yana da shekara ashirin da uku sa'ad da ya fara mulki, ya kuma yi mulki watanni uku a Yerusalem.3Sarkin Masar ya cire shi a Yerusalem, ya sa wa ƙasar tara na talenti ɗari na azurfa da talenti ɗaya na zinariya.4Sarkin Masar ya maida Iliyakim, ɗan'uwansa, sarki a kan Yahuda da Yerusalem, (ya sauya wa Iliyakim suna zuwa Yehoyakim). Sa'an nan Neko ya ɗauki ɗan'uwan Iliyakim Yehowahas ya kawo shi Masar.5Yehoyakim yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya fara mulki, kuma ya yi mulki shekara goma sha ɗaya a Yerusalem. Ya yi abin mugunta a fuskar Yahweh Allahnsa.6Sa'an nan Nebukadnezar, sarkin Babila, ya kai masa hari ya ɗaure shi da sarƙoƙi ya kai shi Babila.7Nebukadnezar kuma ya ɗauki waɗansu kayayyakin gidan Yahweh zuwa Babila, ya sa su a fadarsa a Babila.8Game da sauran zantattukan da suka shafi Yehoyakim, abubuwan ƙazamtar da ya yi, da abin da aka samo găba da shi, gashi, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra'ila. Sa'an nan Yehoyakin, ɗansa, ya zama sarki a madadinsa.9Yehoyakin yana da shekara takwas sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki wata uku da kwana goma a Yerusalem. Ya yi abin da kemugunta a fuskar Yahweh.10Da bazara, Sarki Nebudkanezar ya aiki mazaje aka kawo shi Babila, tare da abubuwa masu daraja daga gidan Yahweh, sai ya maida Zedekiya, danginsa, sarki a kan Yahuda da Yerusalem.11Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki shekara goma sha ɗaya a Yerusalem.12Ya yi abin da kemugunta a fuskar Yahweh Allahnsa. Bai ƙasƙantar da kansa a gaban annabi Irimiya ba, wanda ya yi magana daga bakin Yahweh.13Zedekiya kuwa ya yi tayarwa gãba da Sarki Nebudkanezar, wanda ya sa shi rantsuwar yin biyayya gare shi da sunan Allah. Amma Zedekiya ya taurare zuciyarsa da wuyansa gãba da juyowa ga Yahweh, Allahn Isra'ila.14Bugu da ƙari, dukkan shugabannin firistocin da mutanen sun yi mummunan rashin aminci, kuma suka bi kazamtattun aikin al'ummai. Suka lalatar da gidan Yahweh wanda ya tsarkake a Yerusalem.15Yahweh, Allahn kakaninsu, ya aiko da kalma garesu ta manzaninsa a kai a kai, saboda yana da tausayi a kan mutanensa da wurin da yake zamne.16Amma sun yi ma manzanin Allah ba'a, suka yi banza da maganarsa, suka kuma wulaƙantar da annabawansa, har sai da fushin Allah ya taso gãba da mutanensa, har babu taimako game da haka.17Don haka Allah ya kawo masu sarkin Kaldiyawa, wanda ya kashe 'yan mazansu da takobi a masujada, kuma ba su ji tausayin 'yan maza ko budurwai ko tsofoffin maza ko masu farin gashi ba. Allah ya bayar da su dukka ga hannunsa.18Dukkan kayan ɗaki na gidan Allah, masu manya da ƙanana da dukiyoyin gidan Yahweh da dukiyoyin sarki da ma'aikatansa- dukkan waɗannan ya kwashe zuwa Babila.19Suka ƙona gidan Allah, suka rurrushe garun Yerusalem, suka ƙona dukkan fadodinta, kuma suka hallakar da dukkan abubuwa masu kyau a ciki.20Sarki ya ɗauke zuwa Babila waɗanda suka kuɓce wa takobi. Suka zama barori dominsa da 'ya'yansa maza har zuwa mulkin Fasha.21Wannan ya faru ne domin a cika maganar Yahweh ta bakin Irimiya, har sai ƙasar ta ji daɗin hutun Asabatunta. Ta jira Asabbatu na tsawon lokacin da take zama a yashe, don a wuce shekaru saba'in ta haka.22Yanzu kuwa a shekara ta farko ta Sairus, sarkin Fasha, domin maganar Yahweh ta bakin Irimiya ta cika, Yahweh ya zuga ruhun Sairus, sarkin Fasha, don haka ya sanar da umarni ga dukkan mulkinsa, ya kuma sa ta a rubuce. Ya ce,23Ga abin da Sairus, sarkin Fasha, ya ce: "Yahweh, Allahn sammai, ya bani dukkan mulkokin duniya. Ya umarce ni in gina gida dominsa a Yerusalem, wanda yake a Yahuda. Duk wanda ke cikinku daga dukkan mutanesa, Yahweh Allahnku, ya kasance tare da ku. Bari ya haura can zuwa ƙasar."
Duba:
Duba:
AT: "ya kawo shi Masar a matsayin fursuna"
Duba yadda ka fassara wanan a 21:6
AT: "kai hari Yerusalem"
Barorin Nebukadnezar kuma sun ɗauki.
Ana magana ne game da bautan alolli na ƙarya, da Yahweh ya ƙi.
Wannan na magana ne game da halinsa.
Duba yadda ka fassara wannan a 14:1
AT: "Bai ƙasƙantar da kansa ba kuma bai yi biyayya da Allah ba ta wurin sauraron annabi Irmiya"
"daga maganar da Allah ya bashi"
Jumloli guda biyun nan karin magana ne, dake nuna taurin kai, yana nuna taurin kan Zedekiya ga Allah.
Duba yadda ka fassara wannan a 15:8
AT: "lokuta masu yawa"
AT: "babu yadda za'a kauce mashi"
AT: "Allah ya bar sojojin Kaldiyawa su ci nasararsu."
"sojojinsa sun kwashe"
"Su" na nufin sojojin Babila.
"Sojojinsa sun ɗauke"
AT: "Ya zaɓe in umarce ma'aikata na su gina masa haikali a Yerusalem.
1A shekarar farko ta sarautar Sairus, sarkin Fasiya, Yahweh ya cika maganarsa wadda ta zo ta bakin Irmiya, wadda ta motsa ruhun Sairus. Muryar Sairus ta kai dukkan masarautarsa. Wannan shi ne abin da aka faɗa aka kuma rubuta:2"Sairus sarkin Fasiya ya ce; Yahweh, Allah na Sama, ya bani dukkan mulkokin duniya, ya kuma zaɓe ni in gina masa gida a Yerusalem a Yahudiya.3Duk wanda ya ke daga cikin mutanensa (Ubangijinsa ya kasance tare da shi) zai tafi Yerusalem ya gina gida domin Yahweh, Allah na Isra'ila, Allah da ke a Yerusalem.4Mutanen da ke kowanne sashi na mulkin inda waɗanda suka ragu ke zama sai su basu guzirin azurfa da zinariya, da mallakoki da dabbobi, da kuma kyauta ta yardar rai domin gidan Allah a Yerusalem."5Sai shugabannin zuriyar Yahuda da ta Benyamin, da firistoci da Lebiyawa, da duk waɗanda Allah ya iza ruhunsu su je su gina gidansa ya kafu.6Waɗanda ke kewaye da su suka taimaki aikinsu da azurfa da zinariya da kayayyaki, da dabbobi, da abubuwa masu daraja, da kyautai na yardar rai.7Sarki Sairus kuma ya fito da kayayyakin da ke gidan Yahweh waɗanda Nebukadnezza ya kwaso daga Yerusalem ya kuma ajiye a gidajen allolinsa.8Sai Sairus ya danƙa su a hannun Miteredat ma'aji, wanda ya ƙirga su ta hannun Sheshbazza shugaban Yahudiya.9Wannan shi ne yawansu: daro talatin na azurfa, daro dubu ɗaya na zinariya, da kuma wasu daro ashirin na sauran kayayyaki,10Tasoshi talatin na azurfa, ƙananan tasoshi na zinariya guda 410, da kuma sauran kayayyaki guda dubu.11Akwai a ƙalla kayayyakin zinariya da azurfa guda 5,400 da aka haɗa jimla dukka. Sheshbazza ya kawo dukkan waɗannan a lokacin da masu zaman talala suka fita daga Babila zuwa Yerusalem.
magana a kan farkon mulkin sarki Sairus.
Wannan shine sunan Allah wanda shi ya bayyana wa mutanensa a Tsohon Alkawari. Dubi shafin juyinKalman game da Yahweh a kan yadda za ku juya wannan.
"Yahweh yayi abinda ya ce zai yi"
cewa Jeremiya ya rubuta ko yayi magana game da.
Zuga ruhu na nufin don sa wani ya so ya yi abu. "Yahweh... ya sa Sairus ya so ya yi abu"
mutanen waɗanda ke mallakan Yahweh.
Isra'ilawa da suka zabi su zauna a inda suke su taimake wadanda suka zaɓi su je Urushalima a jiki da kuma ta kuɗi
Wannan na nufin aikin mutane a surar baya wanda Allah ya ta da
Zuga ruhu karin magana ne wanda ke sa wani ya so ya yi abu. AT: ''duka waɗanda Allah ya yi suna so su je''.
Waɗannan sunayen maza ne.
Să abu a hannun wani wata karin magana ce don kyale mutumin yayi abinda yake so yayi da abun. A nan ya kamata mai karatun ya gane cewa Sairus na zato Miteradet ya yi abinda shi Sairus ya so yayi. AT: ''să ma'aji Miteradet a cajin kula da su'' ko sa ma'aji Miteradet ya dauki nauyin su
jami'in da ke a cajin kudi
ya tabbata Sheshbazzar ya sani daidai abin da dukan
Wannan shine tsarin ƙidãyayyun abubuwan.
'nine - "30 ... 1,000 ... 29''
abubuwan da ake amfani a riƙe ruwa domin wanki
duka lambar abubuwan da aka dawo da su zuwa Urushalima daga Babila, da aka jera su a sama daban-daban.
1Waɗannan su ne mutanen lardin da suka fita daga bautar talalar sarki Nebukadnezza, wanda ya bautar da su a Babila, mutanen da suka koma biranensu na Yerusalem da kuma Yahudiya.2Sun dawo tare da Zerubbabel, Yoshuwa, Nehemiya, Serayya, da Re'elaya, Modekai, Bilshan, Misfar, Bigbai, Rehum, da Bãna. Wannan shi ne lissafin mutanen Isra'ila.3Zuriyar Farosh: 2,172.4Zuriyar Shefatiya: 372.5Zuriyar Arak: 775.6Zuriyar Fahat Mowab, ta wurin Yeshuwa da Yowab: 2,812.7Zuriyar Elam: 1254.8Zuriyar Zattu: 945.9Zuriyar Zakkai: 760.10Zuriyar Bani: 642.11Zuriyar Bebai: 623.12Zuriyar Azgad: 1,222.13Zuriyar Adonikam: 666.14Zuriyar Bigbai: 2,056.15Zuriyar Adin: 454.16Mutanen Ater, ta wurin Hezekiya: su tasa'in da takwas.17Zuriyar Bezai: 323.18Zuriyar Yorah: 112.19Mutanen Hashum: 223.20Mutanen Gibba: tasa'in da biyar.21Mutanen Betlehem: 123.22Mutanen Netofa: hamsin da shida.23Mutanen Anatot:128.24Mutanen Azmabet: arba'in da biyu.25Mutanen Kiriyat Arim, Kefira, da Birot: 743.26Mutanen Rama da Geba: 621.27Mutanen Mikmas:122.28Mutanen Betel da Ai: 223.29Mutanen Nebo: hamsin da biyu.30Mutanen Magbish: 156.31Mutanen ɗayar Elam: 1,254.32Mutanen Harim: 320.33Mutanen Lod, Hadid, da Ono: 725.34Mutanen Yeriko: 345.35Mutanen Senã: 3,630.36Sai firistoci zuriyar Yedayya na gidan Yeshuwa: 973.37Zuriyar Immer: 1,052.38Zuriyar Fashur: 1,247.39Zuriyar Harim: 1,017.40Lebiyawa zuriyar Yeshuwa da Kadmiyel zuriyar Hodabiya: saba'in da huɗu.41Mawaƙan haikali, zuriyar Asaf: 128.42Zuriyar masu kula da ƙofa: na Shallum, Ater, Talmon, Akkub, Hatita, da Shobai: 139.43Waɗanda aka sa su yi hidima a haikali: zuriyar Ziha, Hasufa, Tabbawot,44Keros, Siyaha, Fadon,45Lebana, Hagaba, Akkub,46Hagab, Shalmai, da Hanan.47Zuriyar Giddel: Gahar, Re'ayya,48Rezin, Nekoda, Gazzam,49Uzza, Faseya, Besai,50Asnah, Meyunim, da Nefusim.51Zuriyar Bakbuk: Hakufa, Harhur,52Bazlut, Mehida, Harsha,53Barkos, Sisera, Tema,54Neziya, da Hatifa.55Zuriyar bayin Suleman: zuriyar Sotai, Hassoferet, Feruda,56Jãla, Dakon, Giddel,57Shefatiya, Hattil, Fokeret Hazzebem, da Ami.58Akwai 392 jimlar zuriyar waɗanda aka sasu yi aiki a haikali da kuma zuriyar bayin Suleman.59Waɗanda suka fita Tel Melah, Kerub, Addon, da Imma - amma basu iya gane asalinsu a Isra'ila ba -60sun kai 652 in an haɗa da zuriyar Delayya, Tobiya, da Nekoda.61Hakanan, daga zuriyar firistoci: da zuriyar Habayya, Hakkoz, da Barzillai (wanda ya auro matarsa daga 'ya'yan Barzillai ta Gileyed waɗanda kuma ake kiran su da sunansu).62Sun yi ta bincika asalinsu amma basu samo su ba don haka aka cire su daga aikin firist saboda rashin tsarki.63Don haka gwamnan ya ce da su kada su ci duk wani abu mai tsarki na hadaya har sai firist da Urim da Tummin sun amince.64Aka haɗa jimlarsu dukka ta kai mutum 42,360,65ba a haɗa da bayinsu ba (waɗannan sun kai 7,337) da mazansu da matansu mawaƙan haikali sun kai (ɗari biyu).66Dawakansu: 736.67Takarkaransu: 245. Raƙumansu: 435. Jakunansu: 6,720.68Da suka je gidan Yahweh a Yerusalem, manyan ubanni suka yi bayarwa ta yardar rai don a gina gida.69Sun bayar gwargwadon iyawarsu don asusun raya aikin: suka bada awon zinariya sittin da ɗaya, da azurfa jaka dubu biyar da kuma kayan sha na firistoci guda ɗari.70To sai firistoci da Lebiyawa, da jama'a, da mawaƙan haikalin da masu tsaron ƙofofi, da waɗanda aka sa suyi hidima a haikali suka mallaki biranensu. Dukkan mutane a Isra'ila suka zauna a biranensu
Wannan ya fara tsarin sunayen mutanen da suka dawo da ga rabuwa da kasarsu..
Wannan ƙarin magana ce wanda ke nufin tafiya zuwa ga Urushalima. AT: ''koma'' ko ''dawo''
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan sunayen maza ne.
Wannan ya ci gaba tha tsarin sunayen mutane da suka dawo daga rabuwar kasarsu tare de lambar kowanne rukuni.
Waɗannan sunan maza ne.
Wannan ya ci gaba tha tsarin sunayen mutane da suka dawo daga rabuwar kasarsu tare de lambar kwanne rukuni.
Waɗannan sunan maza ne.
Wannan ya ci gaba tha tsarin sunayen mutane da suka dawo daga rabuwar kasarsu tare de lambar kowanne rukuni.
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan sunan na miji ne. Juya kamar a 2:1
Wannan ya ci gaba tha tsarin sunayen mutane da suka dawo daga rabuwar kasarsu tare de lambar kowanne rukuni.
Wadannan sunayen maza ne.
takwas - ''98''
Wannan ya ci gaba tha tsarin sunayen mutane da suka dawo daga rabuwar kasarsu tare de lambar kowanne rukuni. Kula da zura iddo a 2:21 waɗannan yanzu sune sunayen wurare daga inda suka samo asali
Wadannan sunayen maza ne.
biyar...' hamsin da shida - "95...56''
Wannan ya fara tsarin lambar mutane waɗanda magabatansu suka zauna a garuruwan Yahuda. (Dubi:
Wannan sunan wani gari ne a Yahuda.
Wannan ya ci gaba da sunayen mutane waɗanda suka dawo daga rabuwar ƙasarsu tare da lambar a kowanne rukuni wanda magabatansu suka zo daga wuraren da aka jera.
Waɗannan sunayen wurare ne.
two - ''42''
Wannan ya ci gaba da sunayen mutane waɗanda suka dawo daga rabuwar ƙasarsu tare da lambar a kowanne rukuni wanda magabatansu suka zo daga wuraren da aka jera.
Waɗannan sunayen wurare ne.
biyu - ''52''
Wannan ya ci gaba da sunayen mutane waɗanda suka dawo daga rabuwar ƙasarsu tare da lambar a kowanne rukuni wanda magabatansu suka zo daga wuraren da aka jera.
Sunayen wurare
Wannan ya ci gaba da sunayen mutane waɗanda suka dawo daga rabuwar ƙasarsu tare da lambar a kowanne rukuni wanda magabatansu suka zo daga wuraren da aka jera.
Wannan sunan wani wuri ne.
Wannan sashin ya tsara sunayen firistoci waɗanda zuriyarsu suka dawo daga rabuwar ƙasarsu tare da lambar a kowanne rukuni.
Sunayen maza.
Wannan sunan na miji ne. Juya kamar a 2:3.
"Harim" a 2:31 sunan wani wuri ne, amma a nan "Harim" sunan mutum ne.
Wannan sashin ya tsara sunayen firistoci waɗanda zuriyarsu suka dawo daga rabuwar ƙasarsu tare da lambar a kowanne rukuni.
Waɗannan sunayen maza ne.
huɗu - ''74''
waɗanda suke a cajin wanda ke shiga ta hanyar ƙõfõfin haikali
sunnan na miji. Juya kamar a 2:15.
Wannan sashin ya tsara sunayen Lewiyawa waɗanda zuriyarsu suka dawo daga rabuwar ƙasarsu.
Waɗannan sunayen maza.
Juya kamar a 2:40.
Wannan sashin ya tsara sunayen Lewiyawa waɗanda zuriyarsu suka dawo daga rabuwar ƙasarsu. Waɗannan duka sunayen maza ne.
Wannan sashin ya tsara sunayen Lewiyawa waɗanda zuriyarsu suka dawo daga rabuwar ƙasarsu. Waɗannan duka sunayen maza ne.
Wannan sashin ya tsara sunayen Lewiyawa waɗanda zuriyarsu suka dawo daga rabuwar ƙasarsu.
Wannan shine lambar dukan mutanen da ke cikin wannan rukunin waɗanda suka daga rabuwar ƙasarsu.
Wannan shine tsarin sunayen mutane wanda suka dawo zuwa Isra'ila daga birane dabn-daban na Babila amma basu iya tabbatar da gadonsu ba.
Waɗanan ne sunayen wuraren da basu zama a Babila.
sunayen maza
sunayen maza.
ragistar da ta faɗi suwaye magabatansu
''basu iya samun sunayensu ba a registar firistoci ba''
Za'a iya juya wannan a. Za'a iya juya sunan nan "Firist" kamar ''yi aiki kamar firist''. AT: ''sauran firistocin suka bi da su kamar su marasa tsabta ne basu kyalesu su ya aiki kamar firist ba''
basu chanchanta su zama firist ba
abubuwa biyu kamar ɗan lido da frisit ke amfani don ya yanke abinda Allah ke so su yi
duka kungiyoyin da suka dawo zuwa ƙasar Yahuda daga rabuwar kasarsu.
"baiwarsu mace"
'"200"
Wannan shine tsarin dabbobi tare da lambar kowanne rukuni da suka dawo tare da mutane daga rabuwar ƙasarsu
dubu ɗaya... dubu biyar... ɗari ɗaya - ''61,000 ...5,000 ... 100''
''Darik'' ƙaramin tsabar ƙudin zinari ne da ake amfani a masaruatar Fasiya.
Minas shine na'urar gwaji ne na nauyi. Na'urar ɗaya dadai take da giram 550. kullum ana nasabar minas da auna azurfa.
tufafin da ake sanyawa gaba kusa da fata
Kowa ya koma zuwa garinsu a Yudiya. Ba kowa ya zauna a Urushalima ba.
1A wata na bakwai ne bayan da mutanen Isra'ila suka dawo biranensu, inda suka tattaru a matsayin al'umma ɗaya a Yerusalem.2Yeshuwa ɗan Yozadak da 'yan'uwansa firistoci, Zerubbabel ɗan Sheltiyyel da 'yan uwansa suka tashi don su gina bagadin haikalin Allah na Isra'ila don su miƙa hadaya ta ƙonawa kamar yadda aka umarta a shari'ar Musa mutumin Allah.3Sai suka kafa bagadin a wurin tsayuwarsa, don sun firgita saboda mutanen ƙasar. Suka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Yahweh da yammaci.4Hakanan suka yi idin bukkoki kamar yadda ya ke a rubuce suka riƙa miƙa hadaya kowacce rana kamar yadda aka aiyana, ana yin kowanne aiki bisa ga ranarsa.5Bisa ka'ida, akwai baye-baye na ƙonawa ta kowacce rana da kowanne wata da kuma baye-baye na kowanne idi na Yahweh da aka aiyana tare da dukkan kyautai na yardar rai.6Suka fara miƙa baye-baye na ƙonawa ga Yahweh a rana ta farko a wata na bakwai, koda ya ke ba a kafa haikali ba tukuna.7Don haka suka bada zinariya ga masu aikin dutse da maƙera, suka bada abinci, da abin sha, da mai ga mutanen Sidon da Taya don su kawo itacen sida ta kan teku daga Lebanon zuwa Yoffa kamar yadda sarki Sairus ya bada umarni ga sarkin Fasiya.8Sa'an nan a wata na biyu na shekara ta biyu bayan sun zo gidan Allah a Yerusalem, sai Zerubbabel ɗan Sheltiyyel, Yeshuwa ɗan Yozadak, da sauran firistoci da Lebiyawa da waɗanda suka dawo daga bauta zuwa Yerusalem suka fara aiki. Suka sa Lebiyawa 'yan shekaru ashirin su kula da aikin gidan Yahweh.9Yeshuwa yasa 'ya'yansa da 'yan'uwansa, Kadmiyel yasa 'ya'yansa, (da zuriyar Hodabiya), kuma 'ya'yan Henadad da 'ya'yansu da 'yan'uwansa - dukkansu Lebiyawa ne - da suka haɗu tare wajen lura da masu yin aikin gidan Allah.10Masu ginin suka kafa harsashen ginin haikalin Yahweh. Wannan yaba firistoci da masu sa tufafinsu da kayan hurawarsu, su kuma Lebiyawa 'ya'yan Asaf suka yabi Yahweh da garaya, kamar yadda Dauda ya yi umarni.11Suka rera waƙar yabo da godiya ga Yahweh, Cewa "Shi nagari ne! Amintaccen alƙawarinsa mai aminci ga Isra'ila ya tabbata har abada."Dukkan mutane suka tada babbar murya da ƙarfi suna yabon Yahweh saboda kafa harsashin ginin haikalin da aka yi.12Amma da yawa daga cikin firistoci da Lebiyawa, da manyan ubannin shugabanni, da tsofaffin mutanen da suka ga lokacin da aka kafa harsashen ginin haikali na farko suka yi kuka da ƙarfi. Amma da yawa suka rera waƙar farinciki da murna da muryoyi masu daɗi.13A sakamakon haka mutane ba su iya tantance muryar farinciki da ta baƙinciki ba, Don mutane suna ta kuka da matuƙar farinciki, kuma an jiwo ƙararsu daga nesa.
Wannan shine watan bakwai na kalandar Yammaci. Shine a karshan kakar rani da kuma farin kakar damina. Shine a lokacin karshen watan Satumba da kuma farkon sashin watan Octoba a kalandar yammaci
mutum ɗaya yana a wuri ɗaya kuma yana da manufa ɗaya. AT: ''domin manufa ɗaya"
Wannan sunan na miji ne. Juya haka kamar a 2:36.
Wannan sunnan na miji ne.
Tashi a tsaye karin magana ne da ke nufin fara yin abu. AT: ''fara yi da kuma gina''
Za'a iya juya wannan akan kalmar aiki. Za a bukata bayyana waye ne ko kuwa ma wani abu ne Allah ya ke bada wannan Umarni. AT: kamar yadda Yahweh ya umarce su a dokokin Musa''
''suka saka bagadi a tsaye'' ko "ajiye bagadi a tsaye don ya tsaya a nan"
Wannan wata karin magana ce. AT: ''suka ji tsoro sosai''
Zai kamata ku bayyana abinda ya ke game da mutanen ƙasar da ya sa Yahudawa tsoro. AT: ''saboda sun yi tsammani ce wa mutanen ƙasar suna so su kai masu hari.
Wata abu na farko da mutanen suka yi itace mika hadayu. Anyi wannan kamin sake gina haikali.
Wannan wani biki ne da ake yi na tsawon kwanaki takwas a lokacin watan bakwai na kalandar yammaci. Shine ke haɗe tare da lokacin fitowa a lokacin da Isra'ilawa suke zama a tantuna.
Wannan shine watan bakwai na kalandar yammaci. Ranar farko na kusa da tsakiyar Satumba a kalandar yammaci.
Yahudawan sun fara bikin sujada tun kafin ma su fara gina haikalin. AT: ''basu sa tushen haikalin ba tukunna''
Wasikun da Sairus ya aika, ya bawa Yahudawa izinin sayan kaya domin aikin ginin hikali.
Wannan shine wata na biyu a kalandar Yahudawa. Wannan ne a lokacin kakar zufa a lokacin da mutane suke girbin amfanin gona. Shine lokacin karshen sashin watan Afrilu da kuma fărin watan Mayu a kalandar Yammaci.
Wannan shine a lokacin shekaran da ke bayan wanda suka dawo
Ana bukatan ku bayyana cewa babu wani gidan Allah a tsaye a lokacin da suka iso. AT: "zuwa inda gidan Allah yake tsaye" ko "zuwa ga inda za su gina gidan Allah"
Waɗannan sunayen maza ne.
"shekaru 20 na haihuwa"
Wannan sunan na miji ne. Juya kamar a 2:40.
"tushe" a nan na ya fi kawai dutsen tubalan da zasu dogarar ganuwar haikalin. Shine aka hada da dukan benen haikalin da aka sa na dutse. Wannan ke bada daman dukan masu bautar haikalin su sa igunan na musamman su kuma ajiye su da tsabta.
"rigunan su na musamman"
siriri biyu, zagayayyen farantin karfe da ake bugawa tare don su bada ƙaran sauti mai yawa (Dubi: )
Hannun sarki wata karin magana ne domin bada ikon ba da umarni. AT: "kamar yadda Dauda ... ya umarta"
Jin da kuma maganar godiya da kuma nuna godiya domin alherin daga wani.
Wannan na nufin haikali na farko da Sulemanu ya gina, gidan Allah.
Idanu na wakilta gani AT: ''a ganin su'' ko ''kuma suka gan shi''
Wannan na nufin tunani na bakin ciki da ya shafe hawaye da kuma muryoyi.
1Yanzu kuwa waɗansu abokan gãba na Yahuda da Benyamin suka ji cewa mutanen da ke ƙasar bauta sun fara gina haikali domin Yahweh, Allahn Isra'ila.2Sai suka tuntuɓi Zarubbabel da sarakunan zuriyoyin kakaninsu. Suka ce da su, "Bari mu yi gini tare da ku, gama kamar ku, muna neman Allahnku kuma mun yi hadaya gare shi tun kwanakin da Esarhadon, sarkin Asiriya, ya kawo mu nan wurin."3Amma Zarubbabel da Yeshuwa da shugabanin dangogin kakannin suka ce, "Ba ku ba ne, amma mune waɗanda tilas ne mu gina gidan Allahnmu, gama mune waɗanda zasu yi gini domin Yahweh, Allah na Isra'ila, kamar yadda sarki Sairus na Fasiya ya umarta."4Sai mutanen ƙasar suka sa hannuwan mutanen Yahuda suka raunana;5Suka sa mutanen Yahuda suka tsorata da ci gaba da yin ginin. Suka kuma ba mashawartan cin hanci don su lalatar da shirin. A wannan lokacin sun yi haka a dukkan kwanakin sarki Sairus har zuwa mulkin Dariyos sarkin Fasiya.6To sai a farkon mulkin Ahasuras suka rubuto takardar tuhuma game da mazaunan Yahuda da Yerusalem.7A kwanakin Atazazas ne Bishilam, da Mitiredat, Tabiyel da aminansu suka rubuto wa Atazazas. An rubuta wasiƙar a harshen Aramaik aka kuma fassara.8Rehum babban rundunan sojoji da Shimshaya marubuci sun rubuta haka ga Atazazas game da Yerusalem.9Sai Rehum da Shimshaya da aminansu waɗanda ke Alƙalai da waɗansu hafsoshi a gwamnati, da Fasiyawa, daga mazajen Irek da Babila da mazajen Susa (wato Ilemawa) - suka rubuta wasiƙa -10suka haɗa kai da mutane masu daraja da Ashurbanifal ya tilasta su zama a Samariya suka bi su tare da sauran waɗanda ke a Lardin Gaba da Kogin.11Wannan ne kwafin wasiƙar da suka aika wa Atazazas: "Barorinka, mazajen Lardin Gaba da Kogin, sun rubuta wannan:12Bari sarki ya sani cewa Yahudawan da suka tafi daga gareka sun taso mana a Yerusalem don su gina birnin tayarwa. Sun kammala garun da gyare-gyaren harsasun.13Yanzu kuwa bari sarki ya sani cewa idan birnin nan ya ginu kuma an kammala garun, ba zasu bayar da kuɗin fito da haraji ba, amma zasu azabtar da sarakunan.14Tabbas saboda mun ɗanɗana gishirin fãda, bai cancanci mu ga wani raini na faruwa da sarki ba. Saboda haka ne muke sanar da sarki15ka duba daga cikin rubutun kididdiga na mahaifinka don ka tabbatar da cewa wannan birnin tayarwa ne da zai azabtar da sarakuna da lardunan. Ya sha tayar da matsaloli ga sarki da kuma larduna. Ya kuma zama cibiyar tawaye tun da daɗewa. Dalilin haka ne ma aka hallakar da birnin.16Muna sanar da sarki cewa idan aka gina wannan birnin da garun, to babu wani abin da zai rage dominka a Lardin Gaba da Kogin."17Sai sarkin ya aika da amsa ga Rehum da Shimshaya da aminansu a Samariya da sauran waɗanda ke a Lardin Gaba da Kogin: "Salama gareku.18Wasiƙar da kuka aika mani an karanta an kuma fassara mani.19Don haka nasa aka yi bincike kuma na gano cewa a kwanakin baya sun yi tayarwa da rashin hankali ga sarakuna.20Sarakuna masu iko sun yi mulki a kan Yerusalem kuma sun kasance da iko a kan kowanne abu a Lardin Gaba da Kogin. Ana kuma biyansu haraji.21Yanzu kuwa a yi umarni ga waɗannan mutanen su tsaya kuma kada su gina wannan birnin sai na umarta.22Ku yi hankali kar ku yi banza da wannan. Me zai sa a bar wannan jayayyar ta yi girma ta sa mu hasara a wannan masarauta?23Sa'ad da aka karanta umarnin sarki Atazazas a gaban Rehum, da Shimshaya da aminansu, sai suka fita da sauri zuwa Yerusalem suka sa Yahudawan su tsayar da ginin.24Don haka aiki a gidan Allah a Yerusalem ya tsaya har zuwa shekara ta biyu ta mulkin Dariyos sarkin Fasiya.
Mutanen da ba yahudawa ba suka bada kansu zuwa ga gini haikalin
Ana iya juya wannan a. AT:''waddanda 'yan Babila suka raba su da kasarsu''
Sunnan na miji. Juya kamar a 2:1.
Ya yi mulki a Assuriya kafin Sairus ya yi mulki a Farisa
Sunnan na miji. Juya kamar a 2:3
Ma'ana mai yiwuwa sune 1) shugaban yahudawa ya ji cewa Sairus ya umurce su ne kawai su gina haikalin ko kuma) ginin haikalin aikin yahudawa ne kawai kuma ba wani wanda ba bayahude ba da za a kyalle ya taimaka a wurin aikin.
''mutanen da suke zaune a garin a wannan lokacin," wanda zai iya hadawa da waɗanda ba yahudawa ba da kuma iyalin yuhudawa waɗanda 'yan Babila basu sa sun rabu da kasarsu ba
ya nemi ya hana Yudiyawa (Dubi: )
mutane waɗanda suka dawo daga Babila kuma suka zauna a kasar Yahuda
"ya sa shi yadda Yudiyawa baza su iya gina haikalin yadda suka tsara ba"
Za'a iya juya wannan kalma "zargi" kamar fi'ilin nan "zargi" da kuma fi'ilin nan "rayuwa a ciki," bi da bi. Zai yiwu ku bukaci ku sa a bayyane abid da abokan gaba suka zargi Yudiyawa da shi da suka yi. AT: "rubuta wani wasika wanda suka zargi waɗanda suka yi rayuwa a Yahuda da kuma Urushalima na rashin biyayya wa sarki"
sunayen maza )
Wannan shine wasikar da aka yi magana a 4:4.
yaren da ake amfani a wannan wuri a lokacin domin harkokin kasuwanci
cikin Fasiya
sunan na miji. Juya kamar a EZR 2:1.
Sunan birane
sunan yankin kasar da ke da ya fi girma
Wannan shine sunan wani.
Wannan shine sunan lardin da ke yamma da kogin Yufiretis. Shine ke ketaren dag birnin Susa.
Ezra ya hada a rubutunsa, wadataccen wasikar da ya aika zuwa ga sarki Atazazas.
Wannan shine sunan lardin da ke yamma da kogin Yufiretis. Shine ke ketaren dag birnin Susa. Juya kamar a 4:9.
Wannan birni na nufin domin mutane wadanda suke rayuwa a ciki. AT: "birinin da suka shirya su zauna a ciki su kuma yi tawaye da ku"
"gyara tushen ginin" ko "gyara mafarin ginin"
Za'a iya juya wannna a. AT: "idan sun gina birnin kuma sun kammala ganuwar"
Kalmar nan "cuta" na nufin Yudiyawa basu kuma ba sarakunan kudi.
Ma'ana mai yiwuwa sune cewa wannan na nufin 1) marubutan suna ma sarki biyayya
Za'a iya juya wannan a, wanda a wani takaddama za ku bukaci ku bayyana a fili wanda ya hallaka birnin. AT: "' 'yan Babila su ka hallaka birnin"
Za'a iya juya wannan a. AT: "idan sun gina birnin da kuma ganuwar" kamar da kalmonin suka bayyana a 4:13.
Wannan kari ne don a sa sarki yayi tunani cewa zai rasakudin haraji da yawa idan Yudiyawa suka yi tawaye.
Za'a iya juya wannan a, wanda a wani takaddama za ku bukaci ku bayyana a fili wanda ya juya ya kuma karanta wasikar wa sarki. AT: "ni na sa bayi na su juya su kuma karanta wasikar da ku ka aiko mani"
sunan na miji. Juya kamar a 2:1.
sunan na miji. Juya kamar a 4:7.
kogin Yufiretis
Za'a iya juya wannan a. AT: "Mutanen Urushalima sun biya haraji da kuma haraji zuwa waɗannan sarakuna"
"bada doka"
"yi hankali ka yi wannan"
anyi maganar abu mai hatsari kamar shi tsiro ne da zai iya kara girma. AT: "abu mai hatsari yayi muni"
Kalmomin nan "ribar saurata na nufin don sarki shi kanshi. AT: "sanadin karin abubuwa marasa kyau su faru da sarakunan"
Za'a iya juya wannan a, wanda a wani takaddama za ku bukaci ku bayyana a fili wanda ya juya ya kuma karanta wasikar daga sarki Atazazas zuwa ga jami'ansa"
Juya kamar a EZR 2:1.
Juya kamar a EZR 4:7.
bata lokacin nan ya kai kimanin shekara shashida
1Sai annabi Haggai da Zakariya ɗan annabi Iddo suka yi annabci da sunan Allah na Isra'ila ga Yahudawa a Yahuda da Yerusalem.2Zarubbabel ɗan Sheltiyyel da Yeshuwa ɗan Yozadak suka tashi tsaye suka fara gina gidan Allah a Yerusalem tare da annabawan da suka ƙarfafa su.3Daga nan Tattenai gwamnan Lardin Gaba da Kogin, Shetar Bozenai, da abokan aikinsa suka zo suka ce masu, "Wane ne ya baku umarni ku gina wannan gidan ku kuma ƙarasa waɗannan katangun?"4Sai suka kuma ce, Mene ne sunayen mutanen da ke yin wannan ginin?"5Amma idanun Allah na kan dattawan Yahudawa kuma maƙiyansu basu tsayar da su ba. Suna jiran wasiƙar da za a aika wa sarki da kuma umarnin da za a komar masu game da wannan.6Wannan shi ne kwafin wasiƙar Tattenai wato gwamnan Lardin Gaba da Kogi, da Shetar Bozinai da tawagarsa a cikin Lardin Gaba da Kogi, wanda suka aikawa sarki Dariyos.7Sun aika da rahoto, suka rubuta wa sarki Dariyos haka, "Bari dukkan salama ta zama taka.8Bari sarki ya sani cewa mun je Yahuda gidan Allah mai Girma. Ana gininta da manyan duwatsu da katakan da aka shirya a ganuwar. Wannan aikin kuwa ana yin sa sosai da sosai, kuma yana tafiya dai-dai a hannuwansu.9Muka tambayi dattawan, 'Wa ya baku umarni ku gina wannan gida da wannan ganuwar?'10Mun kuma tambayi sunayensu domin ka iya sanin sunan kowanne mutum da ya jagorance su.11Suka amsa suka ce, 'Mu barorin wanda shi ne Allah na sama da ƙasa, kuma muna ginin wannan gida wanda aka gina a shekarun baya masu yawa a sa'ad da sarki mai girma na Isra'ila ya gina, ya kuma ƙarasa shi.12Koda ya ke, Sa'ad da kakaninmu suka sa Allah na sama ya yi fushi, sai ya bada su ga hannuwan Nebukadnezza, sarkin Babila, wanda ya rushe wannan gidan ya kuma ɗauke mutanen zuwa ɓauta a Babila.13Duk da haka, a shekara ta fari sa'ad da Sairus ya ke sarkin Babila, Sairus ya bada umarni a gina gidan Allah.14Sarki Sairus ya kuma mayar da kayayyakin zinariya da azurfa na gidan Allah da Nebukadnezza ya kawo daga haikali a Yerusalem zuwa ga haikali na Babila. Ya mayar da su ga Sheshbazza, wanda yasa ya zama gwamna.15Ya ce da shi, "Ɗauki waɗannan kayayyakin. Tafi ka aje su a haikali a Yerusalem. Bari a sake gina gidan Allah a wurin."16Sai Sheshbazza yazo ya ƙafa harsashe domin gidan Allah a Yerusalem; kuma ana kan yi, amma ba a ƙarasa shi ba.'17Yanzu kuwa, idan sarki ya yarda, sai a bincika a gidan ajiyar rahotonin dã a Babila koda akwai huƙunci daga Sarki Sairus game da gina gidan Allah a Yerusalem. To sai sarki ya aiko da ra'ayinsa gare mu.
sunayen maza
sunan na miji. juya wa kamar a
Wannan shine haikalin Allah
sunayen maza
Wannan ne sunan yankin da ke yamma da kogin Ufiretis. Shine a ƙetaren kogin, daga birnin Susa. Dubi yarda ka juya shi a 4:9.
Idanu na nufin mutum mai kallon wani mutum. AT: "Allah ne mai kallo a kan
wannan za a iya juya shi haka. AT. "domin wani ma'aikacin gwamnati ya aika wasiƙa bay zuwa gare su tare da doka"
Ezra ya hada abinda ke cikin wasiƙar zuwa ga Sarki Dariyus game da aikin su a haikalin
Wannan ne sunan lardin da shine yamma da kogin Ufiretis. Shine kogin da ke ƙetare daga birnin Susa
Wasiƙa daga Tattenai zuwa ga sarki da ya fara a 5:6 ya ci gaba
itace domin gini
"Wa ya baku izini"
Wasiƙa daga Tattenai zuwa ga sarki da ya fara a 5:6 ya ci gaba
Ma'ana mai yiwuwa su ne 1) su na kiran mutanen Yahudawa bayin na Allah ko 2) waɗanda su ka ams su na daga ƙabilar Lewi da Haruna, wanda su ne a zahiri ke da alhaƙin bautar haikali da hadayu
Wannanza a iya juya shi haka. AT: "da mai girma sarkin Israila ya gina ya kuma kawo duka kayan aiki don"
"kawo duka kayan aiki don shi"
Wasiƙa daga Tattenai zuwa ga sarki da ya fara a 5:6 ya ci gaba. Tattenai ya ci gaba da gaya wa sarki abin da Yahudawa su ka gaya ma shi farawa a 5:11
"sa Allah na sama yayi fushi sosai da mu"
hannun na nufin iko ko iko. Har ila yau, "Nebukadnezzar" na wakiltar sojojin sa. AT: "yarje wa Nebukadnezzar, sarkin Babila, da kum sojojin sa su rushe wannan gida su kuma ɗauki mutanen"
kyakketa wannan gida zuwa asa
Sairus ya bada Umurni cewa mutane su sake gina haikalin Allah
Wasiƙa daga Tattenai zuwa ga sarki da ya fara a 5:6 ya ci gaba. Tattenai ya ci gaba da gaya wa sarki abin da Yahudawa su ka gaya ma shi farawa a 5:11
Juya kamar a EZR 1:7.
Sarki Sairus ya mayar masu da abubuwan haikalin
Wanna za'a iya juya shi kamar a. AT: "Ina so Yahudawa su sake gina gidan Allah"
Wasiƙa daga Tattenai zuwa ga sarki da ya fara a 5:6 ya ci gaba. Tattenai ya ci gaba da gaya wa sarki abin da Yahudawa su ka gaya ma shi farawa a 5:11
Wannan za'a iya juya shi a. AT: "mutane su na gina shi yanzu, amma ba su gama duka aikin ba tukun na"
gina
Wasiƙa daga Tattenai zuwa ga sarki da ya fara a 5:6 ya ci gaba. Tattenai ya gama gay wa sarkin abin da Yahudawan su ka gay ma shi ya kuma tambaye sarkin don ya ga idan abin da Yahudawan su ka gaya ma shi gaskiya ne
Wannan za'a iya juya shi a. AT: "zan so ka sa wani ya yi binciken wannan al'amarin"
"idan akwai wani rejista a nan da Sarki Sairus ya bayar a sharia"
1Sai sarki Dariyos ya bada umarni a yi bincike a gidan ajiyar rahotanin dã a Babila.2A ƙasaitaccen birnin Ikbatana a Midiya aka sami takarda; wannan ne abin da aka rubuta a cikinta:3A shekara ta farko ta Sarki Sairus, Sairus ya bada umarni game da gidan Allah a Yerusalem: 'Bari gidan ya sake ginuwa domin ya zama wurin hadaya, bari a kafa harsasunsa, bari tsawonsa ya zama kamu 27, faɗinsa kamu 27,4da layin manyan duwatsu guda uku da layi ɗaya na sababbin katakai, kuma bari gidan sarki ya biya duk kuɗin da aka kashe.5Yanzu a dawo da kayayyakin zinariya da azurfa na gidan Allah wanda Nebukadnezza ya kawo Babila daga haikali a Yerusalem sai a aika da su kuma ga haikali a Yerusalem. Zaku kuwa aje su a gidan Allah.'6Yanzu Tattenai, gwamnan Lardin Gaba da Kogi da Shetar Bozinai da tawagar da ke Lardin Gaba da Kogi, ku rabu da su!7Ku bar aikin gidan nan na Allah yadda ya ke. Gwamna da dattawan Yahudawa zasu gina wannan gidan Allah a wancan wurin.8Ina umarta cewa tilas ne kuyi wannan domin waɗannan dattawan Yahudawan da suka gina wannan gida na Allah: Kuɗi daga asusun sarkin gaba da Kogi za a yi amfani da su a biya waɗannan mutanen don kada su tsayar da aikinsu.9Ko mene ne ake bukata - bijimai, ko raguna, ko 'yan raguna domin hadaya ga Allah na Sama, ko hatsi, ko gishiri, ko ruwan inabi, ko mai bisa ga umarnin firistocin Yerusalem - ku ba su waɗannan abubuwa kowacce rana babu fasawa.10Ku yi wannan domin su kawo bayarwarsu ga Allah na Sama kuma ku yi mani addu'a, sarki, da 'ya'yansa.11Ina umarta cewa duk wanda ya taka wannan doka, za a ciro ginshiƙi daga gidansa a soke shi da shi. Gidansa kuwa tilas ne a mayar da shi juji saboda wannan.12Bari Allah wanda yasa sunansa ya zauna a wurin ya cisge kowanne sarkin ko mutanen da suka ɗaga hannu su canza wannan doka, ko su lalata wannan gidan na Allah a Yerusalem. Ni, Dariyos, nake umarta wannan. Bari a yi tare da kula!"13To saboda umarnin da sarki Dariyos ya aika, Tattenai, gwamnan Lardin Gaba da Kogi da Shetar-Bozinai da abokan aikinsa, suka yi dukkan abin da Sarki Dariyos ya umarta.14Saboda haka dattawan Isra'ila suka yi ginin kamar yadda Haggai da Zakariya suka umarta ta wurin annabci. Suka gina shi bisa ga dokar Allah na Isra'ila da Sairus da Dariyos da Atazazas, sarakuna Fasiya15An kammala gidan a rana ta uku ga watan Adar, a shekara ta shida ta mulkin sarki Dariyos.16Mutanen Isra'ila da firistoci da Lebiyawa da sauran masu zaman bauta suka yi bukin keɓe gidan Allah tare da jin daɗi.17Suka ba da bijimai ɗari da raguna ɗari da 'yan raguna ɗari huɗu domin keɓe gidan Allah. Awaki goma sha biyu aka bayar a matsayin bayarwa ta wanke zunubi domin dukkan Isra'ila, ɗaya domin kowacce kabilar Isra'ila.18Suka kuma sa firistoci da Lebiyawa su rarraba wa mutanen aiki domin sujada ga Allah a Yerusalem, kamar yadda aka rubuta a Littafin Musa.19Saboda haka waɗanda suke cikin bauta suka yi bukin idin Ƙetarewa a watan huɗu.20Firistocin da Lebiyawa dukka suka tsarkake kansu suka kuma yanyanka hadayun idin Ƙetarewa domin dukkan waɗanda suka yi bauta, har da su kansu.21Mutanen Isra'ila da suka ci kaɗan daga cikin naman idin Ƙetarewa su ne waɗanda suka dawo daga bauta suka kuma raba kansu daga rashin tsarkin mutanen ƙasar suka kuma biɗi Yahweh, Allah na Isra'ila.22Cikin jin daɗi kuwa suka sha shagulgulan bukin gurasa marar gami har kwanaki bakwai, gama Yahweh ya kawo masu jin daɗi ya kuma juya zuciyar sarkin Asiriya ta ƙarfafa hannunsu a cikin aikin gidansa, gidan Allah na Isra'ila.
za a iya bayyana "bincike" tare da wannan fi'ili "bincika" ko "bincike." AT: " ba wa ma'aikatan gwamnatin sa umurni su bincika" ko "ba wa mai'aikatan gwamnatin sa umurni su yi bincike"
za'a iya bayyan abin da za su bincika a fili. AT: "ba wa ma'aikatan gwamnatin sa umurni su yi bincike su kuma gano idan akwai wani rejista da Sarki Sairus ya gaya wa Yahudawa su gina gidan Allah a Urushalima"
Wannan ne ginin da ma'aikatan gwamnatin sarki suke ajiye muhimman registar gwamnati
Wannan shi ne sunan birnin
Za'a iya nayyana wannnan a. AT: "Sun sami wani littafi
Wannan ne ya fara registar sarki Sairus na bad da umurnin cewa Yahudawa su sake gina haikalin Allah a Urushalima
za'a iya bayyan shi a fili cewa wannan shi ne farkon shekarar mulkin sa. AT: "a cikin shekarar farko na mulkin sarki Sairus"
Za'a iya bayyana shi a. AT: "Bari Yahudawa su sake gina gidan"
"kamu sittin." Zaku iya maida wannan zzuwa ga ma'aunin zamani. AT: "mita ishirin da bakwai"
Ma'ana mai yiwuwa su ne 1) wannan ya bayyana yadda za'a gina tushen. AT: "gina shi a kan shinfiɗa uku na babban duwatsu tare da shimfiɗar katako ɗaya" ko 2) Wannan ya bayyana yadda za'a gina gauwars. AT: gina ganuwar tare da shinfiɗa uku na babban duwatsu da canji tare da shifiɗar katako daya
"gidan sarki" na wakiltar dukiyar sarki Sairus a asussun ajiye ƙudin masarauta
Wannan ne ya fara registar sarki Sairus na bada umurnin cewa Yahudawa su sake gina haikalin Allah a Urushalima
Dariyus ya rubuta kai tsaye zuwa ga wannan mazan. juya sunansu kamar a 5:3 )Dubi:
Wannan shine sunan lardin that ke yamma da kogin Ufiretis. Shine a ƙetaren daga birnin Susa. Dubi yadda za ku juya shi a 4:9.
Wannan ne ya fara registar sarki Sairus na bada umurnin cewa Yahudawa su sake gina haikalin Allah a Urushalima, wanda aka fara a 6:3.
Wanna za'a bayyana shi a. AT: "yi anfani da kuɗi daga harajin sarki bayan kogin a biya waɗannan mutanen"
"Harajin sarki" na nufin harajin da mutane ke biyan sarki. AT: "kuɗi daga harajin da kuka karɓa don sarki daga mutane bayan gogin"
Za'a iya juya wannan a. AT: "Duka abin da su ke buƙata"
Wannan ne ya fara registar sarki Sairus na bada umurnin cewa Yahudawa su sake gina haikalin Allah a Urushalima, wanda aka fara a 6:3.
Za'a iya juya wanna a. AT: "na umurce ku ma'aikata gwamnati na da ku jawo katako daga gidansa ku kuma rataye shi a sama. sa'an nan su zamar da gidan shi wurin zuba datti"
dogon, itace, da ke riƙe jinkan gidan
huda ta
Ɗaga hannu na wakiltar ƙoƙarin ko ƙarfin zuciyar yin wani abu. AT: "wanda ke ƙoƙarin ya yi canji... ko a hallako" ko "wanda ke karfin zuciya a canza... ko a hallaka"
Za'a iya bayyana "doka" tare da maganan nan "abin da na wajabta." AT: "a canja abinda na rigaya na wajabta" ko " a ce na wajabta wani abu daban"
juya waɗannan sunayen mazan kamar yadda ku ka yi a 5:3.
Za'a iya juya wanna a. ya kamata ku bayyana wane gida ne suka kammala. AT: "Sun kammala gidan Allah" ko "Sun ƙãre ginin haikalin"
"Adar" suna ne na sah biyu da kuma karshen watan kalandar Yahudawa. Shine a lokacin kakar sanyi. Kwana na ukun ne kusa da tsakkiyar feb a urailu a kalandar 'yan yamma
Sarki Dariyus yayi ta mulki has tsawon shekara biyar, yanzu shine shekara na shida na mulkin sa.
An kama waɗannan mutanen ne aka kuma tafi da su Babila, amma sun dawo zuwa Urushalima. AT: "sauran mutanen waɗanda aka kai ƙamammu zuwa Babila suka kuma dawo zuwa Urushalima" ko "sauran mutanen waɗanda suka dawo daga bauta"
"bijimai 100... raguna 400"
za'a iya bayyana"aikin rarrabuwa" tare da "raba cikin aikin ƙungiyoyi." AT: "raba firistoci da kuma lawiyawa cikin aikin ƙungiyoyi"
"ƙungiyoyin da ke aiki tare"
Wannan ne farkon watan calandar Yahudawa. ranar shaɦuɗun na kusa da farkon watan Aprila a calandar yamma.
"maida kansu da tsarki." zama da tsarki na wakiltar kasancewa karɓabe a wurin Allah"
raba kansu daga dauɗar na wakiltar ƙin yin abubuwan da ke sa mutane dauɗa. AT: "Sun ƙi si yi abubuwan da mutanen ƙasar suka yi da ya maida su mara tsabta"
A nan "Dauɗa" na wakiltar kasancewa da rashin karɓuwa a wajen Allah"
Neman Yahweh na wakiltar zaɓen sani, sujada, da kuma yi mashi biyayya. AT: "ya zabi ya yi wa Allah biyayya"
juya zuciyar sarki na wakiltar sa shi tunani daban game da aiki da ke haikali. AT: "canja halin sarkin Asiriya" ko "sa sarkin Asiriya shirye"
ƙarfafa hannunsu a cikin aikin na wakiltar taimakom su yi aiki. Sarkin Asiriya yayi haka ne ta wurin gaya masu su yi aikin, da kuma tanada masu kuɗi domin aikin. AT: "don taimakon su su yi aikin gidansa" ko "ya maida shi mai yiwu wa don su yi aikin gidan sa"
Wannan na nufin ginin haikalin
1Yanzu bayan wannan, a zamanin mulkin Atazazas sarkin Fasiya, Ezra ya dawo daga Babila. Kakannin Ezra su ne kamar haka, Seraiya, Azariya, Hilkiya,2Shallum, Zadok, Ahitub,3Amariya, Azariya, Merayot,4Zerahiya, Uzzi, Bukki,5Abishuwa, Fenihas, Eliyeza, wanda shi ne ɗan Haruna babban firist.6Ezra ya dawo daga ƙasar Babila kuma ƙwararren marubuci ne cikin shari'ar Musa wanda Yahweh, Allah na Isra'ila, ya bayar. Sarki ya ba shi dukkan abin da ya ke buƙata domin hannun Yahweh na tare da shi.7Wasu daga cikin zuriyar Isra'ila da kuma firistoci, da Lebiyawa, da mawaƙan haikali, da masu tsaron ƙofa da kuma waɗanda aka shirya domin hidima a haikali suma suka tafi Yerusalem a cikin wata na bakwai na mulkin Atazazas.8Ya isa Yerusalem a wata na biyar na wannan shekara.9Ya baro Babila a rana ta ɗaya na watan farko. A rana ta ɗaya ne na watan biyar ya isa Yerusalem, tun da hannun Allah mai kyau na tare da shi.10Ezra ya kafa zuciyarsa domin ya yi bincike, ya aikata, ya kuma koyar da farillai da hukumtai da dokokin Yahweh.11Wannan shi ne umarnin da sarki Atazazas ya ba Ezra firist da kuma marubucin dokoki da farillun Yahweh domin Isra'ila.12"Sarkin sarakuna Atazazas, zuwa ga firist Ezra, marubuci na dokokin Allah na sama:13Ina bada umarni cewa kowannene daga Isra'ila cikin harabar mulkina tare da firistocinsu da Lebiyawa da ya ke da niyar tafiya zuwa Yerusalem, zaya iya tafiya da kai.14Ni, sarki, tare da mashawartana guda bakwai, muna aiken ku dukka ku bincika game da Yahuda da kuma Yerusalem bisa ga dokokin Allah, wanda ke cikin hannuwanku.15Ku dawo da azurfa da zinariyar da suka bayar da yardar rai zuwa ga Allah na Isra'ila, wanda mazauninsa ke a Yerusalem.16Ku bayar hannu sake dukkan azurfa da zinariya da dukkan Babila ta bayar kuma da dukkan abin da mutane da firistoci suka bayar hannu sake domin gidan Allah a Yerusalem.17Saboda haka ku saya da farashi cikakke shanun, da ragunan, da 'yan tumakin, da hatsi da baye-baye na sha. Ku miƙa su a bisa bagadin da ke cikin gidan Allahnku a Yerusalem.18Ku yi haka da sauran azurfar da zinariyar dukkan abin da kuka ga ya dace maku da 'yan'uwanku, domin ku gamshi Allahnku.19Ku ɗibiya kayayyakin da aka yi maku kyautarsu a gabansa domin hidima cikin gidan Allahnku a Yerusalem.20Duk wani abin da ake buƙata domin gidan Allahnku da za kuyi bukatarsa, sai a biya daga cikin ma'ajina.21Ni, sarki Atazazas, na yi umarni ga dukkan masu ajiya cikin Lardin Gaba da Kogi, da cewa dukkan abin da Ezra zai yi buƙata daga gareku bari a ba shi a cike,22har sama da talantai na azurfa ɗari, tuli buhu ɗari na hatsi, da ruwan inabi gallan ɗari, da gallan ɗari na mai, da kuma gishiri babu iyaka.23Dukkan abin da suka fito daga umarnin Allah na Sama, ka aikata da kuzari, domin gidansa. Donme ne ne hasalarsa za ta yi ƙuna a bisa masarauta ta da 'ya'yana?24Muna sanar da su game da ku da kada su ɗora maku wata tãra ko haraji ga kowanne firistoci, ko Lebiyawa, ko mawaƙa, ko masu tsaron ƙofa, ko ga mutanen da aka ba hidimar haikalin da kuma bayin gidan wannan Allah.25Ezra, ta wurin hikimar da Allah ya baka, dole ka naɗa alƙalai da masanan hikima su yiwa mutane hidima a cikin dukkan Lardin Gaba da Kogi, su kuma yi hidima ga kowannene da ya san shari'ar Allahnka. Dole kuma ka koyar da shari'ar ga dukkan waɗanda basu san dokar ba.26Ku hori duk wanda ba ya yi cikakkiyar biyayya ga shari'ar Allah ba ko shari'ar sarki ba, ko ta mutuwa, ko kora daga ƙasa, ko a ƙwace mallakarsu, ko jefawa cikin kurkuku.27Yi yabo ga Yahweh, Allahn kakanninmu, wanda ya sanya dukkan wannan cikin zuciyar sarki ya ɗaukaka gidan Yahweh cikin Yerusalem,28kuma wanda ya nuna amincin alƙawarinsa gareni a gaban sarki, da mashawartansa, da kuma dukkan majalisarsa masu iko. Na sami ƙarfafawa daga hannun Yahweh Allahna, sai na tara shugabanni daga Isra'ila su tafi tare da ni.
Assalin Ezra ya koma zuwa ga Haruna, babban firist na farko
Za'a iya bayyana daga inda Ezra ya zo a fili. AT: "Ezra ya zo Urushalima daga Babila"
Juya sunan wannan mutumin kamar yadda kuka yi a 2:1
Juya sunan wannan mutumin kamar yadda kuka yi a 2:40.
Wannan tsarin sunayen na dukan sunan maza ne.
"Sarkin ya ba Ezra duk abin da ya tambaye"
"Hannun" Yahweh na wakiltar albarkar Yahweh ko Taimakon Yahweh. AT: "albarkun Yahweh na tare da Ezra" or "Yahweh na Albarkar Ezra"
Wannan na nufin shekara ta bakwai na mulkin sarki Atazazas. AT: "a cikin shekara ta bakwai da Atazazas ke sarki
Wannan ne wata na biyar na kalandar Yahudawa. a lokacin ƙarshen sashe na Yuli da kuma farkon sashen Augusta a calandar yamma.
Wannan na kusa da tsakkiyar watan mari a calandar yamma.
"Hannu" na wakiltar ikon ko lura da Allah da ya ke anfani da shi don sakamako mai kyau
kafa zuciyarsa na wakiltar tabbacin yanke shawara ko miƙa kan sa don yayi wani abu. AT: "Ezra ya miƙa rayuwarsa ga yin karatu"
"biyayya"
Waɗannan ne dokokin da Allah ya ba wa Isra'ila ta wurin Musa
Rubutun da bi wanna bayani shi ne dokan da sarki Atazazas ya bayar
"Sarkin Sarakuna" suna ne, da ke ma'anar cewa shi ne babba cikin duka sarakuna, sarkin da sauran sarakuna suke wa biyayya. AT: "Babban sarki Atazazas" or "Atzazas, babban cikin sarakuna"
a lokutan nan mutane da ke buƙatar izinidaga sarki su tsuguna da kuma sake gina wurin da aka rushe ta wurin al'umma da ta ci nasara.
Kamar nan, "You" na nufin Ezra
Wanna na ci gaba da dokan da sarki Atazazas ya ba wa Ezra
Kalman nan "Ni" da kuma "Sarki" na nufin mutum Ɗaya ne. Sarkin na tunawa mutanen waɗanda suka ji wannan wasiƙa da cewa shi ne marubucin wasiƙar.
Za'a iya bayyana abin da za su bincike game da shi a fili. AT: "su bincike halin da ake ciki a Yahuda da kuma Urshalima, domin a koyi ko suna ko ba suwa biyayya da shari'ar Allah"
Za'a iya bayyana inda za su kawo shi a fili.
"da yardar kai" na nufin cewa ba a sa su dole su bada kuɗin ba. Sun bada shi domin sun so su yi haka. AT: "azurfar da kuma zinariyar da suka bada da yardar rai
Za'a iya nayyana shi a. AT: "abinda mutane da kuma firistoci suka bada da yardar rai"
Wannan na ci gaba da dokan da sarki Atazazas ya ba wa Ezra
maganar nan "a cike" na nufin kamar yadda wajibi ne a kammala aikin. Su ka yi anfani da azurfa da kuma zinariya don su sayi duka abin da suke buƙata domin su yi wa Allah sujada a cikin haikali. AT: "Sayi iya gwargadon shanu, raguna, hatsi, da kuma abin sha na baye baye kamar yadda ake bukatu"
maganan nan "'yan'uwan ku" na nufin mutane waɗanda ke yin aiki tare da Ezra. AT: "'yan'uwan aikin ku" ko "abokan aikin ku"
Wannan na ci gaba da dokan da sarki Atazazas ya ba wa Ezra
Za'a iya bayyana wannan a. AT: "abubuwan da muka ba ka a cikin yardar rai"
kalmar nan "Shi" na nufin Allah
Za'a iya bayyana kalmar nan "hidima" tare da kalmar nan "yi hidima" ko "amfani" "aiki" ko
Wani keɓaɓɓen wuri inda ake adana kuɗi
Wannan na ci gaba da dokan da sarki Atazazas ya ba wa Ezra
Wannan shi ne sunan Lardin da ke yamma da kogin Ufiretis. Yana ƙetaren kogi daga birnin Susa. Dubi yarda ka juya shi a 4:9
Za'a iya bayyana wannan a. "Ku ba Ezra a cike, duka abi da ya tambaye ku"
"talanta azurfa 1oo." Za ku iya maida wannan zuwa auni na zamani. AT: "3,400 talanta na azurfa" ko "uku da ɗaya-rabin ton na tsarin awo
Wannan na nufin haikalin Allah
Wannan ya ci gaba da dokar da Sarki Atazazas ya ba wa Ezra
"Muna gaya ma su ba don gabatar da wani haraji ko haraji"
mutane wadanda ke buga kayan kida
Wannan ya ci gaba da dokar da Sarki Atazazas ya ba wa Ezra
Za'a iya bayyana Kalmar nan "hikima" tare da "mai hikima" da kuma "cikin hikima." AT: "Alla ya maida kai mai hikima, don haka dole ne ka sanya alkalai da kuma masu ganewa"
Za'a iya juya wanna tare. AT: "ko ta wurin kashe su, korar su, kwace kayan su, ko daure su a kurkuku, kore su daga nan, dauki abubuwan da suka mallaka, ko sa su a kurkuku"
Ezra ya yabi Allah domin dokar da sarki Atazazas ya bayar
"saka abubuwa a zuciyar sarki na wakiltar sanya shi ya zama da wasu tunani da kuma sha'awa. AT: sanya shi ya so ya daukaka gidan Yahweh a Urushalima"
Wannan na nufin haikalin Yahweh
kasancewa da karfafa na wakiltar kasancewa da karfafa.
A nan hannun Yahweh na wakiltar abin da yayi domin ya taimaki Ezra. AT: "Domin Yahweh ya taimake ni"
1Waɗannan su ne shugabanni na kakannin iyalansu waɗanda suka baro Babila tare da ni a zamanin mulkin sarki Atazazas.2Na zuriyar Fenihas, Geshom. Na zuriyar Itamar, Daniyel. Na zuriyar Dauda, Hattush,3wanda ya zama na zuriyar Shekaniya, wanda ya zama daga zuriyar Farosh; da kuma Zakariya, kuma tare da shi akwai mazaje 150 da aka lisafta su cikin rubutattun tarihin zuriyarsu.4Na zuriyar Fahat Mowab, Elihonai ɗan Zerahiya kuma tare da shi akwai mazaje ɗari biyu.5Na zuriyar Zatti, Ben Yahaziyel kuma tare da shi akwai mazaje ɗari uku.6Na zuriyar Adin, Ebed ɗan Yonatan kuma tare da shi an lisafta mazaje hamsin.7Na zuriyar Ilam, Yeshayya ɗan Ataliya kuma tare da shi an lisafta mazaje saba'in.8Na zuriyar Shefatiya, Zebadiya ɗan Mikayel kuma tare da shi an lisafta mazaje tamanin.9Na zuriyar Yowab, Obadiya ɗan Yehiyel kuma tare da shi aka lisafta mazaje 218.10Na zuriyar Bani, Shelomit ɗan Yesofiya kuma tare da shi aka lisafta mazaje 160.11Na zuriyar Bebai, Zakariya ɗan Bebai kuma tare da shi aka lisafta mazaje ashirin da takwas.12Na zuriyar Azgad, Yohanan ɗan Hakkatan kuma tare da shi aka lisafta mazaje 110.13Waɗanda suke daga zuriyar Adonikam suka zo daga baya. Waɗannan su ne sunayensu: Elifelet, Yewuyel, tare da Shemayya kuma mazaje sittin ne suka zo tare da su.14Na zuriyar Bigbai, Uttai da Zakku kuma tare da shi aka lisafta mazaje saba'in.15Na tara matafiyan a mashigin daya tafi har zuwa Ahaba, kuma muka yi sansani a nan kwana uku. Na bincike mutanen da kuma firistoci, amma babu wani daga zuriyar Lebi a nan.16Sai na aika a kirawo mani Eliyeza, da Ariyel, da Shemayya, da Elnatan, da Yarib, da kuma Elnatan da Natan, da Zakariya da kuma Meshullam - waɗanda su ne shugabanni - da kuma Yoyarib tare da Elnatan waɗanda su ne masu koyarwa.17Daga nan sai na aike su wurin Iddo, shugaban da ke a Kasifiya. Na faɗa masu abin da zasu faɗawa Iddo da kuma danginsa, su bayi na haikali da ke zaune a Kasifiya, wato, su aika mana da bayi domin gidan Allah.18Sai suka aika mana ta hannun Allahnmu mai nagari mutum mai suna Sherebiya, mutum mai tattali. Shi daga zuriyar Mahali ne ɗan Lebi ɗan Isra'ila. Ya zo da 'ya'ya sha takwas da 'yan'uwa.19Hashabiya ya zo tare da shi. Haka kuma akwai Yeshayya, ɗaya daga cikin 'ya'yan Merari, da ɗan'uwansa tare da 'ya'yansu, dukkan su mazaje ashirin.20Cikin waɗanda aka ɗaurawa hidimar haikali, waɗanda Dauda da bayinsa suka ɗora wa haƙin yiwa Lebiyawa hidima: 220, kowanne ɗayansu aikinsa bisa ga sunansa.21Sai nayi shelar azumi a mashigin Ahaba domin mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu biɗi hanya madaidaiciya dominmu, domin ƙanananmu, da dukkan mallakarmu.22Na ji kunyar tambayar sarki sojoji ko dawakai da zasu yi tsaronmu daga maƙiya a hanya, gama mun gaya wa sarki, 'hannun Allah na bisa dukkan waɗanda suka neme shi da gaskiya, amma ƙarfinsa da fushinsa na bisa dukkan waɗanda suka manta da shi.'23Sai muka yi azumi muka nemi Allah game da wannan, muka yi roko gare shi.24Daga wannan sai na zaɓi mazaje guda sha-biyu daga cikin shugabannin firistoci: Sherebiya, Hashabiya, da kuma yan'uwansu guda goma.25Na auna masu azurfa goma, da zinariya, da kayayyaki da baye-baye na gidan Allah da sarki, da mashawartansa da kuma shugabanninsu, da dukkan Isra'ila suka bayar hannu sake.26Sai na auna cikin hannunsu azurfa talanti 650, talanti ɗari na kayayyakin azurfa, talanti ɗari na zinariya,27kwanonin zinariya guda ashirin waɗanda aka haɗa su dukka aka ƙimanta farashinsu akan sulallan zinari dubu ɗaya, da kuma a kan gogaggun tagulla biyu masu daraja kamar zinariya.28Sa'an nan na ce masu, "An keɓe ku ga Yahweh, da waɗannan kayayyakin, kuma azurfar da zinariyar dukka baiko ne na yardar rai ga Yahweh, Allah na kakaninku.29Ku kula da su ku kuma adanasu, har sai kun auna su a gaban shugabannin firistoci, da Lebiyawa, da kuma shugabannin kakannin zuriyar Isra'ila a Yerusalem cikin ɗakunan gidan Allah."30Su firistoci da kuma Lebiyawa suka yi na'am da azurfa, da zinariya da kuma kayayyakin da aka auna domin su tafi da su Yerusalem, zuwa gidan Allahnmu.31Muka fito daga mashigin Ahaba a rana ta sha biyu na watan farko domin mu tafi Yerusalem. Hannun Allahnmu na a bisanmu; ya kare mu daga hannun maƙiyanmu da kuma waɗanda suka yi niyyar yi mana kwanto a kan hanya.32Sai muka shiga Yerusalem muka kwana uku a cikinta.33Daga nan a rana ta huɗu aka auna azurfa, da zinariya, da kuma kayayyakin cikin gidan Allahnmu ta hannun Meremot ɗan Yuriya firist, kuma tare da shi akwai su Eliyeza ɗan Fenihas, Yozabad ɗan Yeshuwa, da kuma Nodiya ɗan Binnui Balebi.34Aka tabbatar da jimilla da nauyin komai. Dukkan nauyin komai aka rubuta a wannan lokacin.35Waɗanda suka komo daga bautar talala, su mutanen 'yan gudun hijira, suka miƙa ƙonannun baye-baye zuwa ga Allah na Isra'ila: raguna goma sha biyu, awakai tasa'in da shida, tumaki guda saba'in da bakwai, da kuma tunkiyoyi goma sha biyu domin hadayar zunubi. Dukkansu hadayu ne na ƙonawa na Yahweh.36Sa'an nan suka ba da umarnai na sarki ta hannun manyan shugabannin sarki da kuma gwamnonin Lardin Gaba da Kogi. Sai kuma suka taimaki jama'ar da kuma gidan Allah.
Ayoyi 2-14 tsarin sunaye ne na shugabanni da kuma magabatan su. dukan su maza ne.
Juya sunan wannan mutumin kamar yadda ka yi 2:3.
za'a iya rubuta wannan a wata magana dabam bayan "Zekariya." AT: "Hattush ne a zuriyar Shekaniya, wanda shi ne a zuriyar Parosh"
"tare da Zekariya akwai maza 150 aka jera a rikodin da ke a cikin sassalr sa
Tsarin sunayen maza ya ci gaba
"kuma tare da Eliyehoyenai maza dari biyu ne"
Juya sunnan wannan mutumin kamar yadda ka yi a 7:1.
Juya sunnan wannan mutumin kamar yadda ka yi a 8:1.
Juya sunnan wannan mutumin kamar yadda ka yi a 2:15.
Tsarin sunayen maza ya ci gaba.
Juya sunnan wannan mutumin kamar yadda ka yi a 2:3.
Wannan sunan na miji ne.
"kuma tare da Zebadiya aka jera maza tamanin"
Juya wannan kamar yadda ka yi a 2:11.
Wannan shi ne karshen tsarin sunayen maza. .
"kuma tare da Yohanan aka jera maza dari da goma
Kalman nan "wadanda" na nufin shugabannin. AT: "Shugabannin na zuriyar Adonikam"
Juya sunnan wannan mutumin kamar yadda ka yi a 2:11.
Juya sunnan wannan mutumin kamar yadda ka yi a 2:1.
Aya 16 ta kunshi tsarin sunayen maza.
Ma'ana mai yiwuwa sune cewa "hanyar ruwa" shine 1) hanyar ruwa da mutane suka gina ko 2) wani kogi na kullum. Ja'a iya juya shi a wat hanya ta duka. AT: "hanyar ruwa da ke gudana zuwa Ahaba"
Wannan sunan wani wuri ne.
Juya sunnan wannan mutumin kamar yadda ka yi a 8:12
Akwai mutane guda uku da suke da wannan sunan
wannan sunan mutumin
Kalmar nan "su" na nufin shugabannin tara da kuma malamai da aka yi rubutu game da su a 8:15. AT: "Nan gaba na aika waɗannan mutanen zuwa Iddo"
Wannan shi ne sunnan wurin.
Malmomin nan "wato shi"na gabatar da abin da ya gaya masu su fada. AT: "Na gaya masu su gaya wa Iddo... su aika mana bayi domin gidan Allah"
Waɗannan sunnan maza ne.
"Hannun mai kyau" na Allah na wakiltar alherin sa na tanada masu. AT: "Domin Allah na yi mana alheri, suka aiko mana mutum"
Wannan mutum ne mai fahimta da kuma hikima
A nan, "Isra'ila" sunan na miji ne. Sunan da Allah ya ba Yakubu kenan
mutane masu dalili musamman a cikin wani tsarin gwamnati
Wannan ne sunnan hantar ruwan da ke gudana zuwa wurin da ake kira Ahaba. Dubi yadda za ka juya Ahaba da kuma hanyar ruwa a 8:15.
Kalmar nan "nema" na wakiltar tambayar Allah ya yi masu wani abu. A nan, "madaidaiciyar hanya" na wakiltar tsira yayin da suke tafiya. AT: "tambayar Allah ya ba mu, 'yan ƙanana mu, da kuma tsirar dukan mallakar mu yayin da suke tafiya" ko " tambayar Allah ya kare mu, 'yan ƙananan mu, da kuma dukan mallakar mu yayun da muke tafiya"
Hannun Allah a bisa mutane na nufin Allah na taimakon mutane. Neman Allah karin magana ne na bauta ma shi. AT: "Allah na taimakon dukan waɗanda ke bauta mashi"
Cikekken mulkin Allah da kuma fushin sa a kan mutane na nufin don horon mutane. Mantawa da Allah karin magana ne don kin bauta ma sa. AT: "amma ya na horon dukan wadanda su ka ki su yi masa bauta"
A nan, neman Allah karin magana ne don tambayar Allah ya yi wani abu domin su. AT: "Don haka mun yi azumi da kuma tambayar Allah ya taimake mu"
Juya sunayen waɗannan mazan kamar yadda ka yi a 8:18.
"650 talanti na azurfa." za ka iya maida wannan zuwa ga auni na zamani. AT: "22,000 kilo na azurfa" ko kilo dubu ishirin da biyu na azurfa"
Za ka iya maida wannan a auni na zamani. AT: "3,400 kilo na abubuwan azurfa"
Za ku iya maida wannan zuwa auni na zamani. AT: "3,400 kilo na azurfa"
"Sulalla" shi ne ƙaramin tsabar ƙaramin Zinariya na da mutanen masarautar Fashiya ke amfani da ita. Za iya juya wannan a bisa yawan tsabar kuɗin ko nauyin su. AT: "tsabar zinariya dubu ɗaya na Fashiya" ko "takwas da ki
tagulla caƙudin jan ƙarfe ne da kuma wani ƙarfe. yana da ƙarfi fiye da zallan jan ƙarfe
"Sa'an nan na ce wa jami'an firistoci shabiyu"
a lokacin da suna isa Urushalima, za su auna azurfa, zinariya, da kuma tagulla don su nuna cewa ba su ɗauki wani domin kan su ba.
Bisa ga dokan Musa, ƙabilar Lewi na da aikin kula da haikali, mallakar haikali da kuma baye-baye
"Mun bar hanyar ruwan Ahaba" ko "Mun fara tafiya daga hayar ruwan Ahaba"
Wannan shi ne sunnan hanyar ruwan da ke gudana daga wurin da ake kira Ahaba. juya wannan kamar yadda ka yi a 8:21.
wannan shi ne farkon watan kalandar Yahudawa. rana ta shabiyu na kusa da ƙarshen watan Maris a calandar Yammaci.
Kasancewar hannun Allah a kan mutane na nufin domin Allah taimakon mutane. AT: "Allah na taimakawa mutane"
Wannan na nufin ɓarayi da kuma 'yan fashi waɗanda su ka so su kai masu hari domin taskõkin su
Za'a iya juya wannan a. AT:"jami'an firistoci shabiyu sun auna azurfan, zinariyan, da kuma abubuwan"
aka auna su waje.... cikin hannun Meremot
Waɗandan sunnayen maza ne.
Juya wannan sunan kamar yadda kayi a 2:3.
Waɗannan magana biyu na nufin mutanen Yahudawa da su ke zaman rabuwa da ƙasar su a Babila da kuma waɗanda suka bar Babila kuma suka koma Urushalima a Yudiya. AT: "Waɗanda suka koma zuwa Urushalima daga bauta a Babila, mutanen da suka rabu da ƙasar su
shida... saba'in da bakwai... shabiyu- "12, 96... 77... 12
Waɗannan sune ma'aikatan gwamnatin Babila da suke tafiyad da mutane Yamma da kogin Yufiretis, wanda ya kunshi mutanen da ke zama a Yudiya.
Wannan shi ne sunnan lardin da ke yamma da kogin Yufiretis. Shi ne a ketaren kogin daga birnin Susa. Ya kun hada da Yudiya. Dubi yadda za ka juya shi a 4:9.
haikalin
1Bayan waɗannan abubuwa sun faru, shugabanni suka same ni suka ce, "Mutanen Isra'ila, da firistoci da Lebiyawa basu keɓe kansu daga mutanen sauran ƙasashe ba da kuma abin ƙyamarsu: Kan'aniyawa da Hittiyawa da Ferizziyawa da Yebusiyawa da Ammoniyawa da Mowabiyawa da Masarawa da kuma Amoriyawa.2Domin sun ɗauki wasu daga cikin 'yan matansu da samarinsu, kuma sun hada mutane masu tsarki da sauran mutanen ƙasashen, shugabanni da magabata su ne na farko ga wannan rashin bangaskiya."3Lokacin da na ji wannan, na yayyage rigata da alkyabbata na kuma tsittsige gashin kaina da gemuna, sai na zauna a ruɗe.4Sai dukkan waɗanda suka yi rawar jiki saboda maganar Allah na Isra'ila saboda wannan rashin aminci da suka same ni lokacin da nake zaune ina jin kunya har baikon yamma.5Amma a lokacin baikon yamma sai na tashi daga matsayin ƙasƙanci a cikin rigata da alkyabbata a yayyage, na russuna da gwiwoyina, na ɗaga hannuwana zuwa ga Yahweh Allahna.6Na ce, "Ya Allahna, ina jin kunya da takaici in ɗaga fuskata gare ka, muguntarmu ta ƙaru a kanmu, kuma zunubanmu sun yi girma har sun kai sammai.7Tun daga lokacin kakanninmu har yanzu muna da babban laifi. Saboda zunubanmu, mu da sarakunanmu, da firistocinmu sun bada mu a hannun sarakunan wannan duniya, ga takobi, ga bauta, da ganima da kuma kunyatar da mu, kamar yadda muke a yau.8Amma yanzu a ƙaramin lokaci, alheri daga Yahweh Allahnmu ya zo ya bar mana ringi ya kuma bamu wuri a wurinsa mai tsarki. Wannan yasa Allahnmu ya buɗe mana idanu, ya kuma bamu 'yar wartsakewa daga bautarmu.9Domin mu bayi ne, amma duk da haka Allahnmu bai manta da mu ba amma ya cika alƙawarinsa da amincinsa a gare mu. Ya yi wannan ta wurin sarkin Fasiya domin ya bamu ƙarfi, don mu sake gina gidan Allahnmu mu kuma sake gyaransa. Ya yi wannan saboda ya bamu tsaron gina garu a Yahuda da Yerusalem.10Amma yanzu, Allahnmu, me zamu ce bayan wannan? Mun manta da umarnanka,11umarnan daka ba bayinka annabawa, daka ce, "Wannan ƙasar da kuke shiga don ku mallake ta ƙazamtaciyar ƙasa ce. Ta ƙazamtu ta wurin mutanen ƙasar da abubuwan ƙyamarsu. Sun cikata daga ƙarshe zuwa ƙarshe da abubuwansu na ban ƙyama.12Saboda haka, kada ku bada 'ya'yanku 'yan mata su auri 'ya'yansu maza; kada ku ɗauki 'ya'yansu mata don 'ya'yanku maza, kuma kada ku nemi salamarsu da jin daɗi, don zaku yi ƙarfi ku ci abu mai kyau a ƙasar, domin zaku sa 'ya'yanku su gaje ta a dukkan lokaci."13Bayan da dukkan abubuwan nan suka same mu saboda mugayen ayyukanmu da zunubanmu masu yawa - tun da kai, Allanmu, ka ɗauke dukkan laifoffinmu ka kuma bar mana ringi -14ko zamu sake karya umarninka mu kuma yi auratayya tare da waɗannan mutane da ke ƙazamtattu? Ba zaka yi fushi da mu ka shafe mu don kada a sami wani da ya rage, har babu wani da zai tsira ba?15Yahweh, Allah na Isra'ila, kai mai adalci ne, gama mun zama 'yan ringi da suka tsira a wannan rana. Duba! Ga mu nan gabanka da zunubanmu, don ba wanda zai iya tsayawa a gabanka saboda wannan.
auren mutane daga sauran kasa da kuma addinin su da aka karba
A lokacin da Ezra ya ji cewa Isra'ilawa da yawa sun auri matan kasashen waje da kuma suna bautar allolin su
Ezra na nuwa wa kowa yadda bai ji dadin yadda mutane ke yin abubuwan da ke batawa Allah rai.
hadayar da firist zai bayar kusa da lokacin da rana ke tafiya kasa
wani hanyar cewa ya na "zaune a kunyace" (9:3). '"inda na ke zaune a kasa domin nuna yadda na kunyata"
"a gwiwoyi na da kuma mika a waje makamai na tare da hannaye na da ke a bude zuwa sama
Waɗannan kalmomi hanyoyi biyu ne na maganar muguntarmu da laifinmu kamar abubuwan jiki ne da zai iya girma ya zama ya fi girma fiye da mutane. Za'a iya bayyan kalmomin nan "mugunta" da kuma "laifi" kamar sunna da siffa bi da bi. AT: "mun aikata mugayen halaye kuma muna da laifi sosai"
"lokacin da magabatanmu ke da rai"
Za'a iya juya wannan a. AT: "ka bada mu... a hannun sarakuna"
Takobi na nufin don kashe mutane, wasu mutane. Allah ya yarda mutane su kashe Yahudawa.
Za'a iya juya shi a fi'ilin magana. Allah ya yarda mutane su kama Yahudawa su kuma tafi da su daga nan.
Za'a iya juya shi a fi'ilin magana. Allah ya yarda mutane su dauki dukiyar Yahudawa.
ana maganar zabin Allah yayi alheri kamar alheri mutum ne wanda zai iya motsi. AT: "Yahweh Allahnmu ya zabi ya zama da alheri zuwa garemu da kuma"
Ana maganan amincin alkawarinsa kamar wani abu ne da wani zai iya rike wa a hannnunsa ya kuma rike wa wani ya dauka. AT: "ya bada kansa zuwa ga aminci gare mu da kuma ajiye alkawarinsa"
Sarkin bai iya ganin haikalin a zahiri ba, amma ya sani game da abin da ke faruwa a Urushalima. A nan "gani" na nufin abin da wani ya sani. AT: "domin sakin Fasiya ya sani game shi"
haikalin
Ganuwar da ke ba mutane tsaro na nufin Yahweh na tsaron mutanen sa"
"sai karshen zamanai"
Za'a iya juya kalmomin nan "ayuka" da kuma "laifi" kamar sunaye ne. AT: "domin abubuwa marasa kyau da muka yi kuma domin mu masu laifi ne sosai"
"za ka zama mai adalci idan ka kashe mu duka, amma baka horar da mu ba,amma kuma ka bar wadansun mu a raye
za'a iya juya wannan kamar zance. AT: "ba daidai bane cewa wadansun mu suka karya dokokin ka da kuma sa... mutane."
za'a iya juya wannan kamar zance.AT: "Ina tsoro cewa za ka yi haushi... tsira."
"Ka kasa kunne game da abin da na ke so in ce"
"Zaka iya gani cewa dukanmu masu laifi ne"
"ba ka tunanin cewa akwai wani mutum mara laifi"
1Sa'ad da Ezra ya ke yin addu'a da roƙon gafara, ya yi kuka har yasa kansa ƙasa a gaban gidan Allah. Sai babban taron jama'a maza da mata da yara daga Isra'ila suka taru wurinsa, don mutane na kuka mai zafi sosai.2Shekaniya ɗan Yehiyel na zuriyar Elam ya ce da Ezra, "Mun yiwa Allahnmu rashin aminci har mun auri mata bãƙi daga mutanen ƙasar waje. Amma duk da haka akwai sauran bege ga Isra'ila.3Saboda haka yanzu bari muyi alƙawari da Allahnmu mu kori dukkan matan da 'ya'yansu bisa ga umarnin shugabanni da waɗanda suke rawar jiki don umarnin Allahnmu, bari a yi haka bisa ga doka.4Tashi, domin wannan hakinka ne ka aiwatar, mu kuma muna tare da kai. Ka yi ƙarfin hali, ka yi wannan."5Ezra kuwa ya tashi, yasa shugabannin firistoci, Lebiyawa, da dukkan Isra'ila su yi alƙawarin aiki ta wannan hanyar. Saboda haka dukkansu suka ɗauki alƙawarin rantsuwa.6Sai Ezra ya tashi daga gidan Allah, ya tafi ɗakunan Yehohanan ɗan Eliyashib. Bai ci ko da gurasa ba bai kuma sha ruwa ba, tun da ya ke yana baƙinciki a kan rashin amincin waɗanda suka yi a zaman talala.7Saboda haka suka aika da magana a Yahuda da Yerusalem ga dukkan mutane da suka komo daga zaman talala su kasance a Yerusalem.8Duk wanda bai zo ba a cikin kwana uku bisa ga umarni daga shugabanni da dattawa zai rasa dukkan abin da ya mallaka za a kuma ware shi daga cikin babban taron mutanen da suka dawo daga zaman talala.9Sai dukkan mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Yerusalem a cikin kwana uku. A ranar ashirin ga watan tara. Dukkan mutanen suka tsaya a dandalin gidan Allah, suna kuma rawar jiki saboda maganar da kuma ruwan sama.10Ezra firist kuma ya miƙe tsaye ya ce, "Ku kunyi rashin aminci. Kun zauna da mata bãƙi ta haka kuka ƙarawa Isra'ila laifi.11Amma yanzu sai ku bada yabo ga Yahweh, Allah na kakanninku, ku kuma aikata nufinsa. Ku ware daga mutanen ƙasar da mata bãƙi.12Dukkan taron suka amsa da babbar murya, '"Za muyi kamar yadda ka ce.13Amma, akwai mutane da yawa, kuma lokacin marka ne. Ba mu da ƙarfin tsayawa a waje, kuma wannan ba aikin da za ayi shi a kwana ɗaya ko biyu bane, tun da mun yi babban laifi a wannan al'amari.14Saboda haka bari shugabanninmu su wakilci dukkan taron. Bari dukkan waɗanda suka bar baƙin mata su zauna a biranenmu su zo su sa lokaci tare da dattawan birni da kuma alƙalan birnin har sai fushin Allah ya huce daga kanmu.15Yonatan ɗan Asahel da Yazeyya ɗan Tikba ne basu yarda da wannan ba, da Meshullam da Shabbetai Balebi suka goyi bayansu.16Saboda haka mutane waɗanda suka komo daga zaman talala suka yi wannan. Ezra firist ya zaɓi maza, da dattawa kakanin zuriyarmu da gidaje - dukkansu kuwa ta wurin sunaye, sai suka duba al'amarin a kan rana ta farko ga wata na goma.17Sun gama binciken a rana ta farko a wata na farko ga mazajen da suke zama tare da baƙin mata.18A cikin zuriyar firistoci ma akwai waɗanda suke zama da bãƙin mata. A cikin zuriyar Yeshuwa ɗan Yehodak da ɗan'uwansa su ne Mãseyya, Eliyeza, Yarib da Gedaliya.19Suka yi niyyar sakin matansu. Tun da su masu laifi ne, suka bada baikon rago daga cikin garkensu don laifinsu.20A cikin zuriyar Imma akwai Hanani da Zebadiya.21A cikin zuriyar Harim akwai Mãseyya da Iliya da Shemayya da Yehiyel da Uzziya.22A cikin zuriyar Fashu akwai Elihonai da Mãseyya, Isma'il da Netanel da Yozabad da Elasa.23A cikin Lebiyawa akwai Yozabad da Shimei da Kelayya - wato Kelita, Fetahiya, Yahuda da Eliyeza.24a cikin mawaƙa akwai Eliyashib.25A cikin masu tsaron ƙofa akwai Shallum, Telem da Uri. A cikin sauran Isra'ilawa - a cikin zuriyar Farosh akwai Ramiya, Izziya, Malkiya, Miyamin, Eliyeza, Malkiya da Benayya.26A cikin zuriyar Elam akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot da Iliya.27A cikin zuriyar Zattu akwai Elihonai, Eliyashib, Mattaniya, Yeremot, Zabad da Aziza.28A cikin zuriyar Bebai akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai da Atlai.29A cikin zuriyar Bani akwai Meshullam, Malluk, Adayya, Yashub da Shil Yeremot.30A cikin zuriyar Fahat Mowab akwai Adana, Kelal, Benayya, Mãseyya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi da Manasse.31A cikin zuriyar Harim akwai Eliyeza, Ishiya, Malkiya, Shemayya, Shimiyon,32Benyamin, Malluk da Shemariya.33A cikin zuriyar Hashum akwai Mattenai, Matatta, Zabad, Elifelet, Yeremai, Manasse, Shimei.34A cikin zuriyar Bani akwai Mãdai, Amram, Uwel,35Benayya, Bedeya, Keluhi,36Waniya, Meremot, Eliyashib,37Mattaniya, Mattenai, da Yãsu.38A cikin zuriyar Binnuyi akwai Shimei,39Shelemiya, Natan, Adayya,40Maknadebai, Shashai, Sharai,41Azarel, Shelemiya, Shemariya,42Shallum, Amariya da Yosef.43A cikin zuriyar Nebo: Yehiyel, Matitiya, Zabad, Zebina, Yaddai da Yowel da Benayya.44Dukkan waɗannan sun auro mata bãƙi kuma suna da 'ya'ya tare da wasun su.
Ezra yayi maganar kansa kamar shi wani ne kuma.
da sauri ya tafi daga tsaye zuwa kwance fuska a ƙasa
a gaban haikalin
Juya kamar yadda ya ke a 8:4
Juya kamar yadda ya ke a 8:8
"za mu taimake ka"
Waɗannan sunan maza ne.
"ma'aikatan gwamnatin za su ɗauki dukan mallakarsu daga dukan wanda bai zo ba... kuma zai yi uzuri da su" ko "Mutanen Yahuda da kuma Urushalima za su ɗauki dukan mallakarsu daga dukan wanda ba su zo ba... kuma zai zama an cire shi"
kwana 3
"bayan kwana uku"
Wannan shi ne watan tara na Kalandar Yahudawa. ranar ishirin na kusa da tsakkiyar Disamba a kalandar yammaci
babban wanda aka ɓude tsakar gida a gaban haikali
Za'a iya juya "cin amanar ƙasa" kamar. AT: "taimaka wa abokan gaban naku mutanen"
"kuma yanzu Allah ya ɗauke mu masu laifi na munin zunubin fiye da dã
tafi daga nan zama daban daga
za'a iya juya wannan a. AT: "muna bukatar dogon lokaci mu yi dukkan wannan aikin"
Za'a iya juya wannan a. AT: "tabbateccen likacin da dattawan birbnin da kuma alƙalen birnin za su shirya"
Sunayen maza
Ma'ana mai yiwuwa sune, 1) wadannan maza basu son jami'an birnin su binciki laifukan ko) ba su so wani ya binciki auren mutane.
mutanen su binciki wandanda suka auri matan da ba Yahudawa ba
Wannan shine watan goma kalandar yammaci. Ranar farko na kusa da tsakkiyar Disemba a kalandar yammaci.
wannan shine watan goma na kalandar yammaci. Ranar farko na kusa da tsakkiyar Disamba a kalandar yammaci.
Juya kamar a 2:1
Juya kamar a 3:1
sunayen maza
Juya kamar a 8:15
Ezra ya ci gaba da tsara sunayen maza waɗanda suka auri matan da ba Yahudawa ba
sunayen maza. Juya kamar a 2:36.
sunayen maza
sunan mutum. Juya kamar a 8:8.
sunan muyum. Juya kamar a 10:18.
Ezra ya ci gaba da tsara sunayen maza waɗanda suka auri matan da ba Yahudawa ba.
sunan na miji. Juya kamar a 8:33.
sunan na miji. Juya kamar a 10:5.
sunan na miji. Juya kamar a 2:40.
sunan na miji. Juya kamar a 2:3.
sunan na miji. Juya kamar a 7:1.
Ezra ya ci gaba da tsara sunayen maza waɗanda suka auri matan da ba Yahudawa ba
sunan maza. Juya kamar a 2:7.
sunan na miji. Juya kamar a 8:8.
sunan na miji. Juya kamar a 10:20.
sunan na miji. Juya kamar a 10:5.
Ezra ya ci gaba da tsara sunayen maza waɗanda suka auri matan da ba Yahudawa ba
sunan na miji. Juya kamar a 10:18.
sunan na miji. Juya kamar a 10:26.
sunan na miji. Juya kamar a 2:31.
sunan na miji. Juya kamar a 10:26.
Ezra ya ci gaba da tsara sunayen maza waɗanda suka auri matan da ba Yahudawa ba
sunan na miji. Juya kamar a 2:19.
sunan na miji. Juya kamar a 10:26.
sunan na miji. Juya kamar a 8:12.
sunan na miji. Juya kamar a 10:30.
Ezra ya ci gaba da tsara sunayen maza waɗanda suka auri matan da ba Yahudawa ba
sunan maza. Juya kamar a 10:26.
sunan maza. Juya kamar a 10:33.
sunan na miji. Juya kamar a 8:33.
sunan na miji. Juya kamar a 10:23.
Ezra ya ci gaba da tsara sunayen maza waɗanda suka auri matan da ba Yahudawa ba
sunan na miji. Juya kamar a 10:30.
sunan na miji. Juya kamat a 2:40.
sunan na miji. juya kamar a 7:1.
1Maganar Nehemiya ɗan Hakaliya ke nan: A wata na Kislif, a shekara ta ashirin, a lokacin da nake a fãdar Shusha,2Sai wani daga cikin 'yan'uwana mai suna Hanani ya zo tare da waɗansu mutane daga Yahuda, sai na tambaye su labarin Yahudawan da suka tsira, da kuma sauran Yahudawan da ke a can, waɗanda ke a Yerusalem.3Suka ce da ni "waɗanda suka kuɓuta daga zaman bauta suna cikin babbar damuwa da wulaƙanci, saboda ganuwar Yerusalem ta karye ta faɗi, an kuma ƙone ƙofofinta da wuta"4Nan da nan bayan na ji waɗannan maganganu sai na zauna na yi kuka, har tsawon kwanaki ina damuwa da azumi a gaban Yahweh na sama.5Sai na ce Yahweh "kai ne Ubangiji Allah na sama, Allah wanda ya ke da girma da nagarta, mai cika alƙawari, mai kuma madawammiyar ƙauna ga masu ƙaunarsa da kuma kiyaye dokokinsa.6Ka ji addu'ata ka kuma buɗe idanunka, don ka ji addu'o'in bayinka da nake yi a gare ka dare da rana, don mutaten Isra'ila bayinka. Ina furta zunuban mutanen Isra'ila, waɗanda suka yi maka. Duk da ni da gidan ubana mun yi zunubi.7Mun yi aikin mugunta sosai a gabanka kuma bamu kiyaye dokokinka da farillanka waɗanda ka ba mu ba, da kuma ƙa'idojin da ka umarci bawanka Musa.8Ka tuna da abin da ka umarci bawanka Musa, cewa "In kun yi rashin biyayya, zan warwatsa ku cikin al'ummai,9amma in kun komo gare ni kuka kuma bi umarnina kuka aikata su, to ko da ya ke an warwatsa mutanenku a faɗin duniya, zan tattaro su daga can zan kuma kawo su wurin nan da na zaɓa domin sunana ya zauna."10Yanzu su bayinka ne da kuma mutanenka, waɗanda ka kuɓutar da ƙarfin ikonka da kuma ƙarfin dantsenka.11Yahweh ina roƙon ka, ka saurari addu'ar bayinka yanzu, kuma addu'ar bayinka waɗanda ke son yi maka biyayya, yanzu ka ba bawanka nasara, ka kuma ba shi tagomashi a gaban wannan mutum." Ni mai aikin shayar da sarki ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"Kislif" watan tara ne a kalandar Ibraniyawa. Wannan ƙarshen watan Nuwamba ne zuwa farkon wantan Disemba a kalandar Turawa.
Wannan na ɗaya daga cikin biranen sarautar sarakunan Fasiya, yana a ƙasar Elam. Babba ne, birni mai tsaro da kangaye masu tsawo kewaye da shi
Hanani ɗan'uwan Nehemiya ne ciki ɗaya
"Hanani yazo daga Yahuda tare da waɗansu mutane"
Waɗannan zance biyu na nufin ƙungiyar mutane ɗaya ne. Ma'anonin zasu iya zama 1) Yahudawa kima waɗanda aka kwashe zuwa bauta a Babila amma suka gudu suka koma da zama a Yerusalem ko 2) Yahudawa kima waɗanda suka gudu daga masu neman su kuma su ɗin su kai zuwa bauta a Babila kuma suka ci gaba da zama a Yerusalem. Tunda ba a tabbatar da daga wurin da suka gudo ba, zai fi kyau kada a ambaci haka a fassarar. AT: "Yahudawan da suka gudo daga bauta suka kuma rage a Yerusalem" (Duba: figs explicit)
A nan "su" na nufin Hanani da sauran mutanen da suka zo daga Yahuda.
Ana iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "sojoji sun karye ganuwar Yerusalem sun kuma ƙone ƙofofinta da wuta"
Nehemiya ya faɗi abinda yayi addu'a a kai. AT: "Sai na ce wa Yahweh"
Wannan sunan Allah ne wanda ya bayyana wa mutanensa a Tsohon Alƙawari. Duba shafin translationWord game da Yahweh domin yadda za a fassara wannan.
Tunda Nehemiya na magana ne da Yahweh, wakilan sunaye "shi" da "nashi" za a iya fassarawa a matsayin "kai" da "naka." AT: "dake ƙaunar ka suna kuma kiyaye umarnanka"
"kalle ni." A nan "buɗe idanunka" karin zance ne dake a madadin lura da wani. AT: "lura da ni"
"don ka ji addu'ar bawanka da nake yi a gare ka Ni, bawanka, ina addu'a." Kalmar "bawa" na zancen Nehemiya ne. Yadda wani zai fuskanci na gaba da shi kenan domin ya nuna tawali'u da bangirma.
Ta wurin faɗar haka yana nufin yana addu'a a lokutan rana da dare, Nehemiya ya jaddada yawan addu'ar sa. AT: "koyaushe"
A nan kalmar "gida" na a madadin iyali. AT: "Duk dani da iyalina"
Nehemiya ya ci gaba da addu'a ga Allah.
A "tuna" karin zance ne dake nufin tunawa. AT: "Idan ka yadda ka tuna"
Wakilan sunayen nan "kai" da "naka" na nufin ga Allah.
Wakilan sunayen nan "kai" da "naka" jimloli ne kuma su na nufin mutanen Isra'ila.
Yahweh yayi maganar sanya mutanen Isra'ila su zauna cikin wasu al'ummai kamar ya warwatsasu yadda wani zai warwatsa iri. AT: "Zan sa ku zauna cikin wasu al'ummai"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "ko da ya ke na warwatsa mutanenku"
Yahweh yayi maganar wuraren duniya masu nisan gaske a matsayin "a faɗin duniya." AT: "zuwa wurare masu nisan gaske"
Wannan zance na nufin Yerusalem, inda haikalin yake. AT: "zuwa Yerusalem, wurin nan da na zaɓa ... zauna"
A nan kalmar "suna" na a madadin Yahweh da kansa. AT: "wurin nan da na zaɓa domin in zauna"
Nehemiya ya ci gaba da addu'a.
An yi amfani da wannan kalma ne domin a nuna alamar dakatawa a cikin addu'ar Nehemiya. A nan ya fara roƙonsa bisa ga alƙawarin Yahweh.
Kalmar "su" na nufin mutanen Isra'ila.
A nan "hannu" na madadin ƙarfi ko iko. Tare, waɗannan kalmomi sun jaddada tsananin ikon Yahweh. AT: "ta wurin girman ikonka da babban ƙarfinka"
A nan "bawa" na nufin Nehemiya. Yadda wani zai fuskanci na gaba da shi kenan domin ya nuna tawali'u da bangirma. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 1:6.
A nan "bayi" na nufin sauran mutanen Isra'ila waɗanda suma su na addu'a ga Yahweh domin yayi aiki a madadin mutanensa kuma a madadin Yerusalem.
A nan "suna" na a madadin Yahweh da kansa. AT: "waɗanda ke son yi maka biyayya"
A nan "shi" na nufin Nehemiya, wanda ke nuna kansa a matsayin mutum na uku domin ya bayyana tawali'unsa a gaban Allah, kuma "wannan mutum" na nuna sarkin Fasiya.
Nehemiya na maganar halin sarki da yanayinsa kamar haka sarki ke fuskantar wani abu. AT: "ka kuma ba ni tagomashi a gaban wannan mutum"
Wannan asalin bayani ne game da aikin Nehemiya a fãdar sarki. Harshenka na iya kasancewa da hanya ta musamman ta shaida asalin bayani.
1A watan Nisan, a shekara ta ashirin ta sarautar Atazazas sarki, ya zaɓi ruwan inabi, sai na ɗauki ruwan inabin na ba sarki. Sai ya zamana fuskata ta ɓaci a gaban sarki kuma ban taba ɓata fuska a gabansa ba.2Amma sarki ya ce mani " me ya sa fuskarka ta ɓaci haka? Kuma gashi ba ciwo kake yi ba. Hakika wannan damuwar zuciya ce "Daga nan sai na tsorata sosai.3Na ce da sarki "Ran sarki ya daɗe! me zai hana ni baƙinciki? Da ya ke birni da maƙabartar iyayena sun zama kufai, kuma an ƙone ƙofofinta da wuta."4Sai sarki ya ce mani "Me kake so in yi?" Sai na yi addu'a ga Allah na sama.5Sai na amsa wa sarki" Idan ya gamshi sarki, in kuma na sami tagomashi a idon sarki, sai ka aike ni Yahudiya, garin maƙabartar iyayena, don in sake gina shi."6Sai sarki ya amsa mani (sarauniya kuma tana zaune a gefen sarki), "Har zuwa yaushe za ka ɗauka, kuma yaushe za ka dawo?" Bayan na faɗawa sarki lokacin da zan dawo sai ya yi farincikin aike na.7Sai na ce da sarki "Idan ya gamshi sarki, ina roƙo a ba ni wasiƙu domin gwamnonin lardin da ke gefen rafi don su bani damar wucewa ta yankunansu a kan hanyata ta zuwa Yahuda.8Kuma ina roƙo a bani wasiƙa domin in ba Asaf mai kula da mashigin dajin sarki don ya ba ni katakan da zan yi madogarai na mashigin kusa da haikalin, da kuma ganuwar birnin, da kuma ɗakin da zan zauna." To da ya ke hannun Allah na tare da ni, sai sarki ya yarda da buƙatuna.9Sai na zo wurin gwamnoni a cikin Lardi Gaba da Kogin na basu wasiƙun sarki. Sarki kuma ya haɗa ni tare da waɗansu jarumawa na sojojin dawakai.10Lokacin da Samballat Bahorine da kuma Tobiya Ba'amone bayi suka ji wannan, sai suka da mu sosai cewa wani ya zo don ya taimaki mutanen Isra'ila.11Sai na zo Yerusalem na zauna a can har kwana uku.12Sai na tashi da dare ni da mutane kima da ke tare da ni. Ban faɗa wa kowa abin da Allahna ya sa a zuciyata in yi domin Yerusalem ba. Ba dabba tare da ni, in ban da wacce na ke hawa ba.13Da duhu sai na bi ta Ƙofar Kwari, kusa da Rijiyar Dila zuwa Ƙofar Kashin Shanu, na dudduba ganuwar Yerusalem, an rushe ta kuma a buɗe take, aka kuma ƙone ƙofofinta na katakai da wuta.14Daga nan sai na je ƙofar ƙorama da kuma Madatsin ruwan Sarki. Wurin yana da matsi sosai ga dabbar da nake a kai har da za ta iya wucewa ta ciki.15To sai na tafi da duhu ta kwari na dudduba ganuwar, sai na dawo na shiga Ƙofar Kwari, ta haka na dawo.16Shugabanni basu san inda na je da kuma abin da na yi ba, kuma ban sanar da Yahudawa ba tukuna, ban kuma faɗa wa firistoci ba, hakanan ma manyan mutanen garin, da kuma sauran mutanen da suka yi aikin.17Sai na ce da su, "Kun ga masifar da muke ciki, yadda Yerusalem ta zama kufai kuma an ƙone ƙofofinta da wuta. Ku zo mu sake gina ganuwar Yerusalem, don kada mu ƙara zama abin wulaƙanci."18Na faɗa masu cewa hannun Allah na tare da mu da kuma maganar da sarki ya faɗa mani. Sai suka ce "Mu tashi mu kama ginin." Sai suka ƙarfafa hannuwansu don wannan aiki nagari.19Amma lakacin da Samballat Bahorine, da Tobiya bawan nan Ba'amone, da Geshem Balarabe suka ji labarin aikin, sai suka yi mani ba'a da reni, suka ce, "Me ku ke yi? Kuna yiwa sarki tayarwa ne?"20Sai na amsa masu na ce, "Allah na sama zai ba mu nasara. Mu bayinsa ne kuma za mu tashi muyi ginin. Amma ku baku da gãdo, ko iko, kuma baku da tarihin da zaku ce naku ne a Yerusalem".
"Nisan" sunan watan farko ne a kalandar Ibraniyawa.
"A shekara ta ashirin da Atazazas ke sarki"
An yi amfani da wannan kalma a nuna alamar yankewa daga ainihin layin labarin. A nan Nehemiya ya faɗi tushen zance game da yanayinsa a gaban sarki.
"Sai sarkin"
A nan ana nuna Nehemiya ta fuskarsa domin fuska na nuna lamirin wani. AT: "Me yasa ranka ya ɓaci"
Wannan na maganar ɓacin ran Nehemiya kamar cewa zuciyarsa ta ɓaci, tunda ana la'akari da zuciya a matsayin cibiyar lamiri. AT: "Kana cikin ɓacin rai sosai"
Yayin da Nehemiya ya shirya bada amsa, sai yaji tsoro domin bai san yadda sarki zai ɗauki abin ba.
Nehemiya yana nuna bangirma ga sarki Atazazas. A nan "ya daɗe" zarcewar zance ne dake nufin yayi tsawon rai. AT: "Ran sarki ya daɗe" ko "Dama sarki yayi tsawon rai"
A nan Nehemiya yayi amfani da tambayar barkwanci domin ya gayawa sarki dalilin baƙincikinsa. Za a iya rubuta wannan a matsayin jimla. AT: "Ina da dalilin mai kyau na yin baƙinciki."
"wurin da aka bizne kakannina"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "wuta ta ƙone ƙofofinta"
"Daga nan na maidawa sarki amsa"
A nan a idonka na nufin hukunci ko gani. AT: "a hukuncinka"
"birnin da aka bizne kakannina"
Nehemiya baiyi niyyar yin dukkan ginin ba shi kaɗai, amma zai zama shugaban aikin. AT: "don ni da mutanena mu sake gina shi"
Ana iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "ina roƙo ka ba ni wasiƙu"
Wannan ne sunan lardin da ke yamma da kogin Yufiretus. Yana daga ƙetaren kogi daga birni Shusha.
Wannan sunan mutum ne.
"Hannun" Allah na nufin "tagomashi." AT: "tagomashin Allah na tare da ni"
Samballat sunan wani mutum ne, Horonawa kuma wasu ƙungiyar mutane ne.
Wannan mutum da alamar 'yantaccen bawa ne da yanzu ya zama hafsa a Ammon. (Duba: transtlate_names)
"suka ji cewa na iso"
A nan "zuciyar" Nehemiya na nufin tunane-tunanensa da manufarsa. AT: "ya motsa ni" ko "ya bida ni"
"Ba dabbobi tare da ni"
Mutane kima suka raka Nehemiya zuwa wannan gewaya, amma yayi magana a matsayin mutum na farko saboda shine mafi muhimmanci.
"Da duhu, na fita ta Ƙofar Kwari"
karen daji
Ana kyautata zaton, ana fitar da juji daga cikin birni ta wannan ƙofar.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "wadda maƙiyan Isra'ilawa suka rushe, da ƙofofin katako waɗanda maƙiyansu suka ƙone da wuta"
Suma mutanen da suke tare da Nehemiya suka bi shi. AT: "To sai muka tafi ... muka kuma dawo"
"ta cikin Ƙofar Kwari"
Wannan na nuna sauran mutanen da daga bisani zasu sake gina ganuwoyin. AT: "sauran waɗanda daga bisani zasu yi aikin sake ginin ganuwoyin"
A nan "kun" jimla ne, yana nufin dukkan mutanen da aka ambata a Nehemiya 02:16.
"don kada mu ƙara kunyata"
"Hannun" Allah na nufin "tagomashinsa." AT: "tagomashin Allahna na tare da ni"
Wannan salon magana ne. AT: "a fara ginin"
Furcin "ƙarfafa hannuwansu" na nufin su shirya suyi wani abu. AT: "Sai suka shirya domin wannan aiki nagari"
Waɗannan sunayen maza ne. A duba yadda aka fassara wannan a Nehemiya 02:9-10.
Wannan sunan wani mutum ne.
Suna amfani da waɗannan tambayoyin barkwanci su yiwa Nehemiya ba'a. Za a iya rubuta waɗannan a matsayin furce-furce. AT: "Ku na aikata wawanci! Ku daina yiwa sarki tayarwa!"
Wannan na nufin Atazazas, sarkin Fasiya.
Wannan salon magana ne. AT: "zamu fara sake ginin"
"Amma ku baku da rabo, ko gãdo, ko asalin addini a Yerusalem"
1Eliyashib ya tashi tare da 'yan'uwansa firistoci, sai suka gina Ƙofar Tumaki. Suka keɓe ta suka sa ƙofofinta a inda suke. Suka keɓe ta har zuwa Hasumiyar Ɗari da kuma Hasumiyar Hananel.2A gaba da shi sai mutanen Yeriko suka yi aiki, a gaba da su kuma Zakkur ɗan Imri ne ya yi aiki.3'Ya'yan Hassina'a ne suka gina Ƙofar Kifi. Suka sa mata madogarai, da ƙyamarenta, da sakatunta, da mãkarenta.4Meremot ne ya gyara sashi na gaba. Shi ɗan Yuriya ne ɗan Hakkoz. Gaba da su sai Meshullam ya gyara. Shi ɗan Berekiya ne ɗan Meshezabel. Gaba da su sai Zadok ya gyara. Shi ɗan Ba'ana ne.5Gaba da su sai Tikoyitawa suka gyara, amma shugabanninsu suka ƙi yin aikin da masu duba aikinsu suka umarce su.6Yohaida ɗan Fasiya da Meshullam ɗan Besodeiya ne suka gyara Tsohuwar Ƙofa. Suka sa mata madogarai, da ƙyamarenta, da sakatunta, da mãkarenta.7Gaba da su sai Melatiya mutumin Gibiyon da Yadon mutumin Meronot, su mutanen Gibiyon da Mizfa ne, suka yi gyare-gyaren inda gwamnan Lardin Gaba da Kogi ke zama.8Gaba da shi sai Uziyel ɗan Harhahiya, ɗaya daga cikin maƙeran zinariya, ya yi gyara, Gaba da shi kuma sai Hananiya mai yin turare. Su ne suka sake gina Yerusalem da Babban Garun.9Gaba da su kuma sai Refayiya ɗan Hur ya gyara. Shi ke mulkin rabin gundumar Yerusalem.10Gaba da su sai Yedayiya ɗan Harumaf ya gyara kusa da gidansa. Gaba da shi sai Huttush ɗan Hashabniya ya gyara.11Malkiya ɗan Harim da Hasshub ɗan Fahat- Mowab suka gyara ɗaya sashin tare da Hasumiyar Matoya.12Gaba da su sai Shallum ɗan Hallohesh, shugaban sashin gundumar Yerusalem, ya yi gyara tare da 'ya'yansa mata.13Hannun da mazaunan Zanowa suka gyara Ƙofar Kwari. Suka sake gina ta suka sa ƙyamarenta, da sakatunta, da mãkarenta. Suka yi gyara har zuwa kamu dubu tun daga Ƙofar Kashin Shanu.14Malkiya ɗan Rekab, shugaban gundumar Bet Hakkerem, ya gyara Ƙofar Kashin Shanu. Ya gina ta ya sa ƙyamarenta, da sakatunta, da mãkarenta.15Shallun ɗan Kol-Hozeh, shugaban gundumar Mizfa, ya sake gina Ƙofar Ruwa. Ya gina ta ya sa murfi akan ta da ƙyamarenta, da sakatunta, da mãkarenta. Hakanan ya sake gina Shirayin Siloyam a lambun sarki, tun daga ƙasa har ya zuwa birnin Dauda.16Nehemiya ɗan Azbuk, shugaban rabin gundumar Bet Zur, ya yi gyara har zuwa wurin kabarin Dauda, zuwa madatsar ruwan da mutum ya yi, har ya kai gidan manyan mutane.17Bayansa sai Lebiyawa suka yi gyara, tare da Rehum ɗan Bani, gaba da shi kuma sai Hashabiya, shugaban rabin gundumar Keilah don gundumarsa.18Bayansa sai jama'ar ƙasarsu suka yi gyara, suka haɗa da Binuyi ɗan Henadad, shugaban rabin gundumar Keilah.19Gaba da shi sai, Ezar ɗan Yeshuwa, shugaban Mizfa, ya gyara ɗaya sashin da ke fuskantar ƙurya har kwanar garun.20Bayansa sai Baruk ɗan Zabbai ya ba da kansa domin gyaran ɗaya gefen, tun daga kwanar garun har ya zuwa ƙofar gidan Eliyashib babban firist.21Bayansa sai Meremot ɗan Yuriya ɗan Hakkoz ya gyara ɗaya gefen ƙofar gidan Eliyashib har zuwa ƙarshen gidan Eliyashib.22Gaba da shi sai firistoci, da sauran mutane daga yankin Yerusalem suka yi gyara.23Gaba da su Benyamin da Hasshub suka gyara gefen gidajensu. Gaba da su Azariya ɗan Ma'asiya ɗan Hananiya ya gyara kusa da gidansa.24Gaba da shi Binuyi ɗan Henadad ya gyara ɗaya gefen daga gidan Azariya zuwa kwanar garun.25Falal ɗan Uzai ya yi gyaran wajen kwanar bango, da kuma hasumayar da ta kai har dogon gidan sarki a fãdar tsaro. Gaba da shi sai Fedaiya ɗan Farosh ya yi gyara.26Barorin da ke zama a Ofel suka yi gyara har kusa da Ƙofar Ruwa a wajen gabas da kuma bangon da ya haɗe garin.27Daga shi sai Tekoyawa suka yi gyaran ɗaya gefen da ke kusa da babbar hasumaya har zuwa garun Ofel.28Sai firistoci suka gyara sama da Ƙofar Doki, kowanne kusa da gidansa.29Bayansu sai Zadok ɗan Immar ya gyara wajen sashen gidansa. Daga bayansa sai Shemaiya ɗan Shekaniya mai tsaron ƙofar gabas ya yi gyara.30Bayansa Hananiya ɗan Shelemiya da Hanun ɗan Zalaf na shida, ya gyara ɗaya ɓangaren. Bayansa sai Meshullam ɗan Berekiya ya gyara kusa da ɗakin da ya ke zama.31Bayansa sai Malkiya, ɗaya daga cikin maƙeran azurfa, ya yi gyara har zuwa gidan masu hidima a haikali da kuma na fataken dake haɗe da ƙofa da kuma ɗakin fira na kan kwana32Maƙeran zinariya da kuma fatake suka gyara sama da ɗakin fira da ke kwanar Ƙofar Tumaki.
"Eliyashib babban firist ya zo gaba tare da 'yan'uwansa, firistoci"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"Hasumiyar 100"
Wannan sunan hasumiya ne. Da alamar an bada sunan wannan hasumiya daga sunan wani "Hananel."
Wannan na nufin cewa mutanen sun fito daga Yeriko ne. AT: "mutane daga Yeriko"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"Suka kafa mata ƙyamare" ko "Suka sanya ƙyamare a wurinsu"
"makullanta da mãkarenta." Waɗannan ke kulle ƙofofin sarai.
Waɗannan maganganu na nufin gyara ganuwar. AT: "Meremot ne ya gyara sashi na gaba na ganuwar ... Meshullam ya gyara ganuwar ... Zadok ya gyara ganuwar ... Tikoyitawa suka gyara ganuwar"
Waɗannan mutane ne daga garin Tikoya.
Ana iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "wanda masu duba aikinsu suka umarce su da su yi"
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
Gibiyonawa da Meronotawa ƙungiyar mutane ne.
Waɗannan sunayen wurare ne
Wannan sunan lardi ne dake yamma da kogin Yufiretis. Yana ƙetaren kogi daga birnin Shusha. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Nehemiya 2:7.
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
maƙerin zinariya wani ne mai yin 'yankunne da sarkar zinariya da sauran kayan zinariya.
Waɗannan maganganu na nufin gyara ganuwar. AT: "maƙeran zinariya, suka gyara ganuwar ... Hur ya gyara ganuwar ... Harumaf ya gyara ganuwar ... Hashabniya ya gyara ganuwar"
Hananiya shima ya gyara ganuwar. AT: "gaba da shi kuma Hananiya mai yin turare ya gyara ganuwar"
sinadari na ruwa da mutane ke sanyawa a jikinsu kaɗan domin suyi ƙanshi
shugaba ko babban mai hidima
"Rabi" na nufin sashe ɗaya daga cikin sassa biyu dake dai-dai wa dai-da.
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
Waɗannan maganganu na nufin gyara ganuwar. AT: "gyara ɗaya sashin ganuwar ... gyara ganuwar, tare da 'ya'yansa mata"
Shallum shine shugaban, ba Hallohesh ba.
Wannan sunan wani mutum ne.
"mutane daga Zanowa"
Wannan sunan wani wuri ne.
"Ƙofa ta Kwari" ko "Ƙofar dake kai wa Kwari." A yi ƙoƙarin fassara wannan bayani a matsayin suna, ba kwatance kawai ba.
Suka gyara sashen ganuwar tsakanin Ƙofar Kwari da Ƙofar Kashin Shanu. AT: "Suka yi gyara har zuwa kamu dubu na ganuwar, daga Ƙofar Kwari zuwa Ƙofar Kashin Shanu"
An fahimci cewa suna gyaran ganuwar Yerusalem.AT: "Suka yi gyara har zuwa kamu dubu na ganuwar" ko "Suka sake gyara wani kamu dubu na ganuwar bayan Ƙofar Kwari"
"kamu 1,000." Za a iya rubuta wannan bisa ga gwajin zamani. AT: "mita 460"
Ana kyautata zaton, ana fitar da juji daga cikin birni ta wannan ƙofar.A yi ƙoƙarin fassara wannan bayani a matsayin suna, ba kwatance kawai ba.
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
Malkiya ne shugaba, ba Rekab.
Wannan sunan wani wuri ne.
"Ya kafa ƙyamarenta" ko "Ya sa ƙyamaren a wurinsu"
Shallun ne shugaba, ba Kol-Hozeh ba.
Wannan na nufin ganuwar na gefen Shirayin Siloyam. AT: " ganuwar da ta kewaye Shirayin Siloyam "
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
Nehemiya ne shugaba, ba Azbuk ba.
Wannan wani mutum ne daban mai suna Nehemiya baya ga marubucin littafin.
Waɗannan duka sunayen wurare ne.
Waɗannan maganganu na nufin gyara ganuwar. AT: "gyara ganuwar har zuwa wurin ... Lebiyawa suka gyara ganuwar"
"mayaƙa"
"tsayawa gundumarsa" ko "a mamadin gundumarsa"
Waɗannan maganganu na nufin gyara ganuwar. AT: "Bayansa sai jama'ar ƙasarsu suka gyara ganuwar ... gyara ɗaya sashin ganuwar"
"Bayan shi"
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
Binuyi ne shugaba, ba Henadad.
Waɗannan duka sunayen wurare ne.
Ezar ne shugaba, ba Yeshuwa.
"a gaban matakalun har ya zuwa garun"
wurin ajiyar makamai
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
Wannan na nufin gyara ganuwar. AT: "gyara ɗaya gefen ganuwar"
Waɗannan maganganu na nufin gyara ganuwar. AT: "kewaye da Yerusalem, gyara ganuwar ... Benyamin da Hasshub suka gyara ganuwar ... Azariya ... ya gyara ganuwar ... Binuyi ... ya gyara ganuwar"
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
"Bayan su ... Bayan shi"
"a gaban gidansu"
Waɗannan maganganu na nufin gyara ganuwar. AT: "Falal ya gyara ganuwar ... Farosh ya gyara ganuwar ... Barori ... suka gyara ... suka gyaran ɗaya gefen ganuwar"
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
"hasumayar da ta miƙe"
"fãdar bisa ta shugaban Isra'ila"
Wannan ne wurin da matsara ke zama.
Wannan sunan wani wuri ne.
"a gaban Ƙofar Ruwa"
"doguwar hasumiya ... doguwar hasumiya." Wannan zance "hasumayar da ta kai har" na nufin doguwar hasumiya da ta zarce daga ganuwar. Zai iya kasancewa dukkan wannan zance na maganar hasumiya ɗaya ne.
Waɗannan maganganu na nufin gyara ganuwar. AT: "firistoci suka gyara ganuwar ... ya gyara wajen sashen ganuwar ... ƙofar gabas ya gyara ganuwar ... ya gyara ɗaya ɓangaren ganuwar ... ya gyara kusa da"
Kalmar "sama" anyi amfani da ita a nan saboda gidajen firistocin suna bisa kamar hawan tudu daga Ƙofar Doki.
"a gaban gidansa"
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
Shemaiya ne mai tsaron ƙofar gabas, ba Shekaniya ba.
"wanda ke lura da ƙofar gabas" ko "wanda ke buɗewa da rufe ƙofar gabas"
"ɗa na 6" ko "ɗa na lamba 6"
"a gaban ɗakunan da yake zama." Kalmar "ya" na nufin Meshullam.
Wannan sunan wani wuri ne.
Waɗannan maganganu na nufin gyara ganuwar. AT: "ya yi gyara har zuwa ganuwar gidan ... fatake suka gyara ganuwar"
"masu sayarwa" ko "masu sana'a"
ɗakunan dake sashen bisa inda mutane ke zama
Wannan sunan wani wurin shiga ne daga ganuwar
1Da Sanballat ya ji muna yin ginin ganuwar, sai abin ya dame shi, ya fusata sosai, ya yi wa Yahudawa ba'a.2A gaban 'yan'uwansa da sojojin Samariya, sai ya ce, mene ne waɗannan kumaman Yahudawan ke yi? Ko zasu iya dawo da birni don kansu? Ko zasu miƙa hadayu? Ko zasu iya gama aikin a rana ɗaya? Ko zasu iya samun duwatsu daga tarin matattun duwatsu da aka ƙone?3Tobiya Ba'amone na tare da shi, sai ya ce, "Ai ganuwar da suke ginawa dila ma kawai in ya bi ta kan abin da suke ginawa zai rushe ganuwarsu ta dutse!"4Ya Allahnmu, ka ji yadda aka rena mu. Ka mayar masu da reninsu a kansu, ka sa a kwashe su suzama ganimar yaƙi zuwa ƙasar da zasu yi zaman jarun.5Kada ka rufe laifofinsu, kada ka shafe zunubansu daga fuskarka, don sun sa maginan sun yi fushi,6To sai muka gina katangar kuma katangar ta haɗu har ta kai rabin tsawonta, don jama'ar na da marmarin aiki.7Amma bayan Sanballat, da Tobiya, da Larabawa, da Amoniyawa, da kuma Ashdodiyawa suka ji yadda ake yin gyaran katangar Yerusalem da kuma yadda aka gyaggyara wuraren da suka lalace, sai matsanancin fushi ya kama su.8Sai duk suka haɗa baki, suka fito don su yaƙi Yerusalem, da kuma kawo rikici a cikinta.9Amma muka yi addu'a ga Allahnmu kuma muka sa masu tsaronsu dare da rana, saboda wannan maƙarƙashiyar tasu.10Daga nan sai mutanen Yahuda suka ce, "Ƙarfin ma'aikatan yana kasawa. Akwai kayayyaki da yawa da za a kwashe, kuma ba zamu iya ci gaba da ginin ganuwar ba".11Maƙiyanmu suka ce, "Ba za su gan mu ko su san lokacin da zamu auko masu mu kashe su ba, mu tsayar da aikin."12A lokacin, Yahudawan da ke zama kusa da su ne suka zo ta ko'ina suka yi magana da mu sau goma, suka gargaɗe mu akan maƙarƙashiyar da suke shirya mana.13Sai na sa mutane a gangaren ganuwar a wuraren da ke da hatsari nasa kowanne iyali da takobinsu, mãshi, da kibiya.14Daga nan sai na miƙe na duba, sai na ce da manyan mutane da shugabanni, da sauran mutanen, "Kada ku ji tsoronsu. Ku tuna da Ubangiji, wanda ya ke da girma da kuma ban razana. Ku yi yaƙi domin iyalinku da 'ya'yanku maza da mata da matayenku da kuma gidajenku."15Sai ya kasance bayan maƙiyanmu sun ji mun san shirye-shiryensu, Allah kuma ya rikirkita shirye-shiryensu, sai kowa ya koma ya kama aikin garun, kowa ga nasa aikin16Tun daga rabin barorina suka koma aikin katanngar, rabinsu kuma suka riƙe mãsu da kwalkwali da kwari, suka kuma sa sauran kayan yaƙi, shugabanni kuma na bayan mutanen Yahuda.17Mutanen dai dake aikin ginin katangar da kuma ɗauko kaya, suke kuma tsaron in da suke. Sai kowannen su ya kama aiki da hannu ɗaya, ɗaya hannun kuma yana riƙe da makami.18Kowanne mai gini kuma yana rataye da takobinsa a kwiɓi, yadda suka yi aikin kenan, mai busa ƙaho kuma yana gefena.19Sai na ce da manyan mutane da shugabannin, "Aikin babba ne kuma yanzu ya yi fãɗi, kuma mun rabu a kan garun, mun kuma yi wa juna nisa20To dole ne ku ruga inda kuka ji ƙarar ƙaho sai ku tattaru a can. Allahnmu zai yi yaƙi a madadinmu."21Da haka muka yi aiki. Rabinsu na riƙe da mãshi tun daga safe har fitowar taurari.22Hakannan sai na ce da mutanen a wancan lokacin, "Sai kowanne mutum da baransa su kwana a tsakiyar Yerusalem, don su zama masu gadi, da dare da kuma ma'aikata da rana."23To ko ni ko 'yan'uwana, ko bayina, ko masu gadi dake tare da mu ba wanda ya canza tufafin da yasa, kuma kowannen mu ya ɗauki makaminsa, ko dama ya tafi ɗebo ruwa ne.
A nan Nehemiya ya yi amfani da kalmar "da" ya nuna sabon fanni a labarin.
Waɗannan duka sunayen mutane ne.A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 2:10.
A nan "abin" na nufin da Sanballat ya sakankance cewa Yahudawa suna sake ginin ganuwar. Wannan na maganar yadda Sanballat ya husata sosai kamar ƙunar wuta. AT: "ya yi fushi sosai"
"A gaban mutanensa" ko "A gaban danginsa"
Sanballat ya yi waɗannan tambayoyi ne domin ya yiwa Yahudawa ba'a. Za a iya rubuta waɗannan a matsayin zance. AT: "Waɗannan kumaman Yahudawan ba zasu iya aiwatar da komai ba. Ba zasu iya maido da birnin ba domin kansu. Ba zasu iya miƙa hadayu ba. Ba zasu iya gama aikin ba a rana ɗaya."
"Yahudawa marasa ƙarfi"
Wannan na maganar rashin iya gama wani abu da sauri ta wurin cewa ba za a iya kammalawa ba a rana ɗaya. AT: "da sauri"
Sanballat ya sake yin wannan tambaya ne domin ya yiwa Yahudawa ba'a. Ana iya rubuta wannan a matsayin zance. AT: "Ba zasu iya maido rai ga duwatsun ba daga tarin matattun duwatsu da aka ƙone."
Wannan na maganar mutanen na sake gina birnin kamar su na maido shi da rai. AT: "maido da birnin da gina ganuwarsa daga tarin matattun duwatsu da aka ƙone"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "daga tarin matattun duwatsu da wani ya ƙone"
Sanballat ya yi ba'a game da ganuwar da zarce magana game da rashin ƙarfinta ta wurin cewa dila ma kawai zai iya rushe ta. AT: "Wannan ganuwar da suke ginawa dila ma kawai in ya bi ta kan abin da suke ginawa zai rushe ganuwarsu ta dutse"
A nan Nehemiya na addu'a ga Allah. Za a iya sanya wannan a fili a kuma rubata shi cikin alamar rufewa. AT: "Daganan nayi addu'a, 'Ka ji, Allahnmu, ... don sun sa maginan sun yi fushi.' To"
A nan kalmar "mu" na nufin Yahudawa. Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Ka ji, Allahnmu, gama maƙiyanmu sun rena mu"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "bari maƙiyansu suyi masu fashi"
Wannan magana "reni" na nufin zage-zagen Sanballat da Tobiya. A nan kalmar "kawunansu" na nufin dikkan mutanen. AT: "Ka mayar masu da reninsu a kansu" ko "Ka sanya zage-zagen su yi masu ba'a"
Wannan na maganar yafewa wani zunubansa kamar kayayyakin da aka rufe. AT: "Kada ka yafe"
Wannan na maganar mancewa da zunuban wani kamar abin da aka rubuta da za a iya sharewa. AT: "kada ka manta da zunubansu"
"sun ba maginan haushi"
"To sai muka sake gina katangar"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "muka haɗa katangar kuma katangar ta haɗu har ta kai rabin tsawonta"
"Rabi" na nufin sashe ɗaya daga cikin sassa biyu dake dai-dai wa dai-dai.
Wannan na maganar mutanen sunyi fushi sosai kamar fushinsu yana ƙuna a cikinsu. AT: "suka yi fushi sosai" ko "suka zama da hasala"
A nan "Yerusalem" na nufin mutanen da suke zama a can. AT: "gãba da mutanen Yerusalem"
"sanya mutane kewaye da ganuwar domin suyi tsaron birnin"
Kayayyakin su ne "ƙonannun duwatsu" ko "fasassun duwatsu" ko "duwatsun da basu kafuwa."
"Ba zasu ganmu muna zuwa ba har sai mun kai bayansu"
Wannan na maimakon ta kowace kafa. Kalmar "ko'ina " zarcewar zance ne dake nufin "da yawa." AT: "daga kafofi da yawa"
A nan lambar 10 anyi amfani da ita a nuna "da yawa." AT: "magana damu sau da yawa"
"a wurare marasa tsaro"
Wannan na nufin mutane da yawa daga kowanne iyali, wannan na nuna bai haɗa da mataye da yara ba. AT: "nasa mutane daga kowanne iyali"
maganar "ku tuna" na nufin tunawa. AT: "Ku tuna da Ubangiji"
"Sai ya faru cewa"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "mun san shirye-shiryensu"
"samarina suka yi aiki"
"Rabi" na nufin sashe ɗaya daga cikin sassa biyu dake dai-dai wa dai-dai.
"shugabanni kuma suka tsaitsaya bayan mutanen"
Wannan zarcewar zance ne. Ba koyaushe ba ne suka yi aiki da hannu ɗaya ba kawai, amma a koyaushe suna tare da makamansu domin su zama a shirya su kãre kansu tare da waɗanda ke kewaye da su.
A nan "Na" na nufin Nehemiya.
Waɗannan shugabannin da aka ambata a cikin Nehemiya 4:16.
A nan kalmar "babba" na nufin "mai fãɗi" ko "mai girma."
Wannan na nufin wani na busa ƙaho"
"Rabi" na nufin sashe ɗaya daga cikin sassa biyu dake dai-dai wa dai-dai.
Wannan na nufin dukkan yini, yayin da ake rana a waje. AT: "daga farkon hasken rana har zuwa farawar dare"
"safe" lokaci ne da rana take fitowa. A nan fitowar rana na maganar tasowar "safiya". AT: "tasowar rana" ko "safiya"
"cikin Yerusalem"
"tuɓe rigunanmu ba"
1Daga nan sai mazaje da matansu suka yi babban kuka kan 'yan'uwansu Yahuduwa.2akwai waɗanda suka ce "Mu da 'ya'yanmu maza da mata muna da yawa. To sai mu sami hatsin da za mu ci mu rayu."3Akwai waɗanda suka ce, muna jinginar da filayenmu da kuringar inabinmu, da gidajenmu don mu sami abinci a lokacin yunwa."4Hakannan waɗansu suka ce. '"Mun ranci kuɗi don mu biya harajin sarki saboda gonakin inabinmu.5Yanzu kuma jikkunanmu da jininmu dai-dai ya ke da na 'yan'uwanmu, 'ya'yanmu kuma dai-dai da nasu 'ya'yan. An tilasta mana mu sayar da 'ya'yanmu su zama bayi. Tuni ma aka bautar da 'ya'yanmu mata. Amma mu ba mu da iko mu yi komai sabada gonakinmu na inabi suna hannun waɗansu mutane"6Bayan na ji wannan kuka nasu da waɗannan maganganu sai na fusata sosai7Sai na yi tunani na kuma ba manyan mutane da shugabanni laifi. Na ce da su, "Kowa na neman riba a kan ɗan'uwansa." Sai na jagoranci babban taron gãba da su,8sai na faɗa masu cewa, "Mun sha fama kafin mu fito daga ƙangin bauta musamman 'yan'uwanmu Yahudawa da aka sayar a cikin al'ummai, amma sai ga shi kuna sake sayar da 'yan'uwanmu don a sake sayar da su a gare mu kuma!" Sai suka yi shiru ba wanda ya ce uffan.9Hakanan na ce da su abin da kuke yi ba shi da kyau. A she ba za ku yi tafiya cikin tsoron Allahnmu ba, don kada mu zama abin ba'a ga al'umman da ke gãba da mu ba?10Ni da 'yan'uwana da bayina ne ke basu rancen kuɗi da hatsi. Amma dole ne mu dena sa ruwa a kan wannan bashin.11Sai ku mayar masu da filayensu, da gonakin inabinsu. Da na zaitun ɗinsu, da gidajensu da kuma ƙiyasin kuɗi da na hatsi, da sabon ruwan inabi, da kuma man da kuka karɓa daga gare su."12Daga nan sai suka ce. "Za mu mayar da abin da muka karɓa daga wurinsu, kuma ba za mu karɓi komai daga wurinsu ba. Za mu yi kamar yadda ka faɗi. 'Daga nan sai na kira firistoci, na sa su rantse cewa zasu yi kamar yadda suka alƙawarta.13Sai na kakkaɓe tufafina na ce, "Ubangiji ya kakkaɓe dukiya da gidan duk wanda bai cika alƙawaransa ba. Da ma a kakkaɓe shi ya zama fanko sai taron suka amsa, "Amin," sai suka yabi Yahweh jama'ar kuma suka aikatata kamar yadda suka yi alƙawari.14To, tun daga lokacin da aka naɗa ni na zama gwamnan a ƙasar Yahuda, daga shekara ta ashirin har ya zuwa shekara ta talatin da biyu ta sarautar sarki Atazazas, ko kuma in ce shekaru sha biyu ba mu taɓa cin abincin da ake ba gwamna ba.15Amma su tsofaffin gwamnoni da suka gabace ni suka ɗora wa jama'ar ɗawainiya mai nauyi, suka kuma karɓi awo, da zinariya da kuma abincin yau da kullum, da ruwan inabi. Har ma bayinsu suka dinga ƙuntatawa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda tsoron Allah.16Na kuma ci gaba da aikin ganuwar, ba mu kuma sayi ƙasa ba, duk barorina suka taru a can don wannan aiki.17A kan teburi kuma inda Yahudawa da shugabaninsu, su 150 suke, in ban da sauran waɗanda suka zo tare da mu daga al'umman dake kewaye da mu.18Kuma kowacce rana akwai sã da aka shirya, zaɓaɓɓun tumaki guda shida, da tsuntsaye, kuma bayan kwana goma a kan kawo kowanne irin ruwan inabi, kuma duk da haka ban taɓa karɓar kuɗin abincin gwamna ba, don buƙatu sun yi wa mutane yawa.19Ka tuna da ni ya Allahna, saboda duk abin da na yi domin mutanen nan.
Tunda su na aikin ganuwa, ma'aikatan basu da isasshen lokacin aikin sayen ko noma abinci domin iyalansu. Cikakken manufar wannan magana za a samu a fili.
Wannan na nufin mazajen da suke aikin ginin ganuwar.
Wannan kalma "kuka" za a iya faɗi a matsayin kalmar aiki. AT: "suka yi kuka da ƙarfi"
"Muna ɗaukar alwashi" ko "muna bada alƙawari"
A nan Yahudawan na cewa tushen Yahudancinsu ɗaya ne da sauran Yahudawan kuma muhimmancinmu ɗaya ne da sauran. Za a iya bayyana wannan a fili a AT: "Duk da haka iyalanmu Yahudawa ne kamar sauran iyalan Yahudawa, kuma 'ya'yanmu na da muhimmanci a gare mu kamar nasu 'ya'yan"
Wannan kari ne wanda ke nufin iyalansu. AT: "iyalanmu"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Mun riga mun saida wasu 'ya'yanmu mata zuwa bauta"
Tunda gonakin mutanen da garkokinsu basu cikin ikonsu, basu iya aikin samun kuɗaɗen da zasu iya yin hidimar iyalansu ba. Cikakken bayanin wannan za a samu cikin. AT: "Amma bamu iya canza wannan yanayi ba saboda wasu ne yanzu ke mallakar gonakinmu da garkokinmu waɗanda muke buƙata domin lura da rayuwarmu"
Wannan kari ne dake nufin basu da kadarorin yin wani abu. AT: "bamu iya yi ba"
Wannan kalma "kuka" za a iya faɗi a matsayin kalmar aiki. AT: "sa'adda na ji kukansu"
Kowanne Bayahude ya sani cewa ba dai-dai ba ne a ƙarƙashin shari'a ya caji wani Bayahude bashi da ruwa. Za a sani cikakkaen fassarar wannan a. AT: "Kowannen ku na cajin ɗan'uwansa ribar bashi da ruwa, kuma wannan ba dai-dai ba ne a ƙarƙashin shari'a"
Wannan na nufin ya tattaro babban taro ya kuma gabatar da wannan ƙara a gabansu. Manufar wannan bayani za a sami cikakken fahimtar sa. AT: "Na tara babban taro na kuma kawo wannan ƙara gãba da su" ko "Na yanke masu hukunci a gaban taron"
Wannan na nufin suna saida wasu daga cikin iyalansu a matsayin bayi ga 'yan'uwansu Yahudawa. Cikakkaen ma'anar wannan bayani za a sami fahimtar sa a. AT: "Yanzu kuna saida mutanenku su zama bayi ga ga 'yan'uwanku Yahudawa, saboda daga baya su sake saida mana su"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "waɗanda mutane suka sayar a matsayin bayi ga al'ummai"
Wakilin suna "na" na nufin Nehemiya.
"Ku" a nan na nufin manyan Yahudawa.
Wannan tambayar barkwanci ca da Nehemiya ke amfani da ita yana tsawatawa manyan. Za a iya fassarawa a matsayin bayani. AT: "Ku yi tafiya cikin tsoron Allahnmu domin ku kawas da ba'ar al'umman dake maƙiyanmu."
Wannan kari ne. A nan "tafiya" na nufin halin mutum da yadda yake rayuwa. AT: "ku yi rayuwarku ta hanyar da zata gamshi Allah"
Kalmar "ba'a" na nufin "zargi" ko "ƙasƙanci" kuma za a iya bayyana ta a matsayin kalmar aiki. AT: "al'umman da ke gãba da mu ba daga yi mana ba'a" ko "maƙiyanmu al'ummai daga zarginmu"
arowa ko bayar da wani abu ga wani da sa begen biya
Wannan kowanne kuɗi, abinci, ko kadara da wani zai yadda wani ya yi aro domin ya biya bashin. Mai aron zai kasance mai arawar zai bishi bashi.
Fannin darajar bashin ne da aka caji mai aron a matsayin riba
"kuka caje su" ko "kuka sa su biya"
A nan "su" na nufin shugabannin Yahudawa
A nan kalmar "su" na nufin shugabannin Yahudawa.
shugabannin Yahudawa na cewa za su mayar da kuɗaɗen da Yahudawa talakawa suka biya a matsayin ruwan da aka caje su.
"Na" na nufin Nehemiya.
"Na kakkaɓe aljihun falmarata." Sau da yawa a Tsohon Alƙawari, ana nuna kwaikwayon rantsuwa a sarari domin a nuna shaida game da alƙawarin da aka ɗauka. Nehemiya yana nuna kwaikwayo ga shugabannin Yahudawa abin da zai faru idan suka karya alƙawarin da suka ɗauka.
A nan Nehemiya na maganar cewa Allah zai ƙwace dukkan mallakar mutum kamar ace Allah zai kakkaɓe mutum daga gidansa da mallakarsa kamar yadda Nehemiya ya kakkaɓe aljihun falmararsa. AT: "To da ma Allah ya ƙwace dukkan mallaka da gidan kowanne mutum wanda bai kiyaye alƙawarinsa ba kamar yadda na kwashe dukkan abin da ke cikin aljihun falmarata"
A nan "ni" na nufin Nehemiya
"daga shekara ta 20 har ya zuwa shekara ta 32"
"da Atazazas ke sarki "
"shekaru 12" ko "lokacin waɗannan shekaru 12." Nehemiya na ƙara shaida wannan zance ne domin ya jaddada cewa ya yi wannan ba tsayawa dukkan cikakken lokacin da yake gwamna.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "cin abincin da mutanen ke gabatarwa gwamna"
"kowace rana"
"gwamnonin da suka gabata" ko "gwamnonin da suka wuce." Nehemiya ba shine gwamnan farko ba na Yahuda.
"Amma ni ban yi haka ba, saboda tsoron Allah ban karɓi abincin ba" ko "Amma ban karɓi abincin ba saboda ina jin tsoron Allah"
"Na" na nufin Nehemiya"
Kalmar "mu" na nufin Nehemiya da barorinsa.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Na tãra dukkan barorina a can"
"suyi aiki a ganuwar"
"mazaje ɗari da hamsin"
Nehemiya ne ke da hakkin wadatar da abinci ga dukkan waɗannan mutane. Za a iya bayyana wannan a sarari. AT: "Kuma, ko wace rana a teburinmu ni ke ciyar da Yahudawa da shugabanni, mutane 150; mu na kuma ciyar da bãƙi da ke zuwa daga ƙasashen dake kewaye da mu
Wannan na nufin teburin gwamna. Teburin zumunta ne domin jama'ar gari da tattauna al'amura.
shugabannin gwamnati
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Kowacace rana ina gaya wa barorina abinda zasu shirya" ko "Kowacce rana ina gaya wa barorina su shirya abinci daga"
"zaɓaɓɓu 6 ... kwana10"
"isasshen ruwan inabi domin kowa"
"duk da haka ban taɓa tambayar kuɗin abincin gwamna ba"
Wannan kari ne. Roƙo ne ga Allah da ya yi juyayi akansa ya kuma tuna da shi. AT: "Ka tuna dani"
1To, bayan Sanballat da Tobiya da Geshem Balarabe da sauran maƙiyanmu suka ji labarin na sake gina ganuwar, ba kuma inda ya ragu a buɗe, duk da ya ke ban sa ƙyamare a ƙofofin ba,2sai Sanballat da Geshem suka aiko mani da saƙo cewa, "Ka zo mu haɗu a wani wuri a filin Ono." Amma so suke su cutar da ni.3Na aika masu da 'yan'saƙo, cewa, "Ina yin babban aiki, kuma ba zan sauko ƙasa ba. Donme aiki zai tsaya a lokacin da na bar shi na gangaro wurinku?"4Sai suka sake aiko mani da dai irin wannan saƙon har sau huɗu kuma na dinga ba su amsa da irin amsar da na saba basu a kullum.5Sanballat ya aiko bawansa gare ni da dai irin wannan saƙon a karo na biyar, da rubutu a buɗe a hannunsa.6A cikin sa aka rubuta cewa, "An ba da rahoto cikin al'ummai hakannan Geshem shi ma ya faɗa cewa, kai da Yahudawa kuna so kuyi tayarwa, don wannan ya sa kuke sake gina ganuwar. Daga cikin abin da rahoton ya ce har ma ka kusa zama sarkinsu.7Kuma ka zaɓi annabawa su yi wannan shela game da kai a Yerusalem, cewa, 'Akwai sarki a Yahuda!' Kuma ka tabbata sarki zai ji waɗannan saƙonnin. Don haka ka zo muyi magana da juna."8Sai na aika da saƙo gare shi cewa, "Ba wani abu kamar irin abin da ka ce ya faru, amma ka ƙago su ne daga cikin zuciyarka."9Don dukkansu sun so su tsoratar da mu, suna tunanin, "Za su sa hannunsu su tsai da aikin, don kada a kammala shi." Amma ya Allah ka ƙarfafa hannuwana.10Na je gidan Shemaiya ɗan Delaiya ɗan Mehetabel, wanda a gidansa aka ƙulla maƙarƙashiyar. Ya ce, "Sai mu je gidan Allah tare a cikin haikali, sai mu kulle ƙofofin haikalin don suna zuwa don su kashe ka. Da dare suna son su kashe ka."11Na ba su amsa cewa, "Ko namiji kamar ni zai iya guduwa? Ko namiji kamar ni zai iya zuwa haikali don ya tsirar da ransa? Ba za ni ciki ba."12Na gane cewa ba Allah ne ya aiko shi ba, amma ya yi anabci ne gãba da ni. Tobiya da Sanballat ne suka yi hayar sa.13Sun yi hayar sa don ya tsoratar da ni, don in yi abin da ya ce in yi zunubi, don su bani laifi har su wulaƙanta ni.14Ya Allahna ka tuna da Tobiya da Sanballat, da duk abin da suka yi. Hakannan ka tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawan da suka so su sa in tsorata.15Da haka aka kammala ginin garun a ranar ashirin da biyar ga watan Elul, bayan kwana hamsin da biyu.16Bayan duk maƙiyanmu sun ji labarinsa, sai dukkan al'umman da ke kewaye da mu suka ji tsoro sosai duk fuskarsu ta yanƙwane. Don sun san an kammala aikin ne ta wurin taimakon Allahnmu.17A wannan lokaci sai masu daraja na Yahuda suka aika da wasiƙu masu yawa ga Tobiya, wasiƙun Tobiya kuma suka zo masu.18Don akwai waɗanda ke yi masa alƙawari, don shi surukin Shekaniya ne, ɗan Ara. Ɗansa Yehohanan ya auri 'yar Meshullam ɗan Berekiya ta zama matarsa.19Sun faɗa mani labarin ayyukansa masu kyau nima kuma na bashi nawa rahoton. Tobiya ya aika mani da wasiƙu don ya firgita ni.
Waɗannan duka sunayen mutane ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 2:9-10.
Nehemiya ya shugabanci sake ginin ganuwar kuma bai gina ba da kansa. AT: "mun sake gina ganuwar .. ba mu riga mun sa"
Wannan na nufin sassan ganuwar. AT: "kowanne sassan ganuwar" ko "kowacce kafa a ganuwar birnin"
Wannan na nufin sun aiko manzo da saƙo. AT: "
Wannan sunan wani wuri ne.
Nehemiya ya shugabanci sake ginin ganuwar. Kuma bai gina ba da kansa. AT: "muna yin babban aiki"
An yi amfani da wannan tambayar barkwanci domin a ƙalubalanci roƙon Sanballat. Za a iya rubuta wannan a matsayin bayani. AT: "Ba zan bar aiki ya tsaya ba domin in gangaro wurinku"
Wannan kalma "gangaro" a nan anyi amfani da wannan kalma ne saboda sararin Ono inda ake neman Nehemiya da ya je yana kwari ne da Yerusalem.
Gane wannan saƙo daban-daban na nufin ya sha ban-ban a wata hanyar daban da saƙonnin huɗu na dã kuma, saboda haka, ayi la'akari da haka. AT: "Sanballat ya aiko bawansa gare ni da irin wannan saƙon" ko "Sanballat ya aiko bawansa gare ni ya kawo saƙo na biyar"
Wasiƙar zancen siyasa ne a buɗe. Wannan cin mutunci ne ga mai karɓar saboda saƙon a buɗe yake don kowa ya iya karantawa kuma ya baza abin da ke ciki ga dukkan mutanen lardin.
Wannan na nufin yana tare da wasiƙar a mallakarsa, amma ba lallai yana ɗauke da ita ba ga hannu a koyaushe. AT: "a cikin mallakarsa"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Jita-jita cikin lardin"
Wannan na nufin suna shirin yiwa Atazazas, sarkin Fasiya, tayarwa wanda shike mulkin Yahudawa a wannan lokaci. AT: "ana shirin yiwa Atazazas tayarwa"
"Sarki Atazazas zai ji"
"Don haka ka zo ka same mu"
A nan "na" na nufin Nehemiya kuma "shi" ga Sanballat.
"Ba wani abu kamar irin abin da ka rubuta ya faru"
A nan "zuciya" na nufin "tunani," wato, marmari da zace-zacen wani. AT: "amma daga cikin tunaninka ne ka ƙago su" ko "amma ka ƙirƙiro wannan ne daga tunane-tunanenka"
A nan "su" na nufin maƙiyan Nehemiya, Sanballat, Tobiya, Geshem, da mabiyansu. Kalmar "mu" na nufin Yahudawa.
Wannan zancen kwatance ne dake nufin cewa suna tsai da aiki a ganuwar. AT: "Ma'aikatan bisa ganuwar zasu tsai da yin aikin"
A nan Nehemiya na roƙon Allah domin ya ƙarfafa hannuwansa ta wurin roƙon sa da ya ƙarfafa "hannuwansa." AT: "Ka ƙarfafa ni" ko "Ka bani ƙarfin hali"
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
Marubucin bai faɗi dalilin da yasa ya kasance a tsare a gidansa ba, don haka zaifi kyau ace yana a gidansa amfani da kalmomi masu kyau da ake iya wa. AT: "wanda bai bar gidansa ba" ko "wanda hukuma ta umarta da ya zauna gida"
Nehemiya ya yi amfani da wannan tambayar barkwanci domin ya jaddada cewa ba zai yi abin da Shemaiya ke shawararsa ba. Za a iya rubuta waɗannan tambayoyi a matsayin bayani. AT: "Namiji kama ta ba zai gudu ba. Namiji kama ta ba zai tafi cikin haikali ba domin ya ɓoye ya tsare ransa."
"amma ya yi anabci ne domin ya yi tsayayya da ni"
Amfani da haikali a matsayin wuri domin ɓoyewa zunubi ne. Zai fi kyau a nuna wannan a bayyane. AT: "in yi zunubi ta wurin amfani da haikali ta hanyar da bata dace ba"
Wannan kari ne. AT: "saboda su ba ni mugun suna" ko "domin su faɗi rahoto marar kyau game da ni"
Wannan kari ne. AT: "Tunawa"
Wannan sunan mace ne.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "mun gama garun"
"rana ta 25 ga watan Elul." Elul shine wata na shida a kalandar Ibraniyawa.
"kwana 52"
"ba su ji daɗin kansu ba" ko "sun rasa amincewa da kansu"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Allahnmu ne ya taimake mu muka kammala wannan aiki"
Masu daraja suka aika manzanni da wasiƙu masu yawa ga Tobiya. AT: "suka aika manzanni masu yawa da wasiƙu"
A nan ana zance wasiƙun Tobiya kamar da kansu suka taka suka zo, yayin da ainihin maanzanni ne suka kawo su. AT: "Tobiya ya aika da wasiƙu" ko "Tobiya ya aika manzanni masu yawa da wasiƙu"
A duba yadda za a fassara wannan suna a Nehemiya 2:10.
Wannan na maganar waɗanda ke yiwa Tobiya aminci saboda sun ɗaukar masa alƙawari kamar alƙawarinsu wata igiya ce da ta ɗaure jikkunansu. AT: "waɗanda suka yi masa rantsuwar alƙawari" ko "waɗanda suka yi masa alƙawari kuma suke yi masa aminci"
Wannan na nufin Tobiya ya auri ɗiyar Shekaniya. Duba yadda aka fassara "Shekaniya" a cikin Nehemiya 3:29.
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
Waɗannan duka sunayen mutane ne. Duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:4.
Masu daraja na Yahuda suka gaya mani game da ayyukan Tobiya na Alheri suka kuma gaya mani game da amsoshina"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. Tobiya ya aika manzanni su kai wasiƙu ga Nehemiya. AT: "Tobiya ya aika mani da wasiƙu" ko "Tobiya ya aika manzanni su kawo mani wasiƙu"
1Bayan an gama ganuwar na kuma sa ƙofofin a wurarensu, na kuma zaɓi masu tsaron ƙofofin da mawaƙa da Lebiyawa,2na ba ɗan'uwana Hanani iko kan Yerusalem, tare da Hananiya muka kula da masarautar, don shi amintacce ne, kuma mai tsoron Allah fiye da masu yawa daga cikinsu.3Na ce da su, "Ka da ku buɗe ƙofofin Yerusalem har sai rana ta yi zafi. Lokacin da masu tsaron ƙofofin ke tsaro, zaku kulle ƙofofin kusa mãkaransu. Ku zaɓi masu gadi daga cikin mazaunan Yerusalem, waɗansu a bayan gidajensu, waɗansu kuma su tsaya inda aka sa su gadin."4Yanzu birnin yana da faɗi da kuma girma, amma kuma waɗanda ke ciki basu da yawa, kuma ba'a gama sake gina gidaje ba tukuna.5Ya Allahna ka ba ni iko in tattara mutane masu girma da shugabanni da dukkan jama'a in sa su bisa ga iyalansu. Sai na samo littafin asalin waɗanda suka dawo daga farko sai na samo wannan rubutun a cikinsa.6Waɗannan sune mutanen lardin da suka fito daga bautar talala waɗanda sarki Nebukadnezza sarkin Babila ya kwasa zuwa bauta. Sun dawo zuwa Yerusalem da Yahuda, zuwa birninsa.7Sun zo tare da Zerubbabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Azariya, da Ra'amiya, da Nahamani, da Modakai, da Bilshan, da Misferet, da Bigbai, da Nehum, da Ba'ana. Yawan mazajen mutanen Isra'ila ya haɗa da waɗannan.8Zuriyar Farosh, 2,172.9Zuriyar Shefatiya, 372.10Zuriyar Ara, 652.11Zuriyar Fahat-Mowab, zuwa zuriyar Yeshuwa da Yowab, 2,818.12Zuriyar Elam, 1,254.13Zuriyar Zattu, 845.14Zuriyar Zakkai, 760.15Zuriyar Binuyi, 648.16Zuriyar Bebai, 628.17Zuriyar Azgad, 2,322.18Zuriyar Adonikam, 667.19Zuriyar Bigbai, 2,067.20Zuriyar Adin, 655.21Zuriyar Ater na Hezekiya, 98.22Zuriyar Hashum, 328.23Zuriyar Bezai, 324.24Zuriyar Harif, 112.25Zuriyar Gibiyon, 95.26Mutane daga Betlehem da Netofa, 188.27Mazaje daga Anatot, 128.28Mutane daga Bet Azmabet, 42.29Mutanen daga Kiriyat Yeriyim, da Kefira, da Birot, 743.30Mutanen daga Rama da Geba, 621.31Mutanen Mikmas,122.32Mutanen Betal da Ai, 123.33Mutanen Nebo, 52.34Mutanen wancan Elam, 1,254.35Mutanen Harim, 320.36Mutanen Yeriko, 345.37Mutanen Lod, Hadid, da Ono, 721.38Mutanen Sena'a, 3,930.39Sai firistoci: Zuriyar Yedayya (na gidan Yeshuwa), 973.40Zuriyar Immer, 1,052.41Zuriyar Fashur, 1,247.42Zuriyar Harim, 1,017.43Sai Lebiyawa: Zuriyar Yeshuwa, na Kadmiyel, na Binuyi, da Hodiba, 74.44Mawaƙa: Zuriyar Asaf, 148.45Masu tsaron ƙofa na zuriyar Shallum, da zuriyar Ater, da zuriyar Talmon, da zuriyar Akkub, da zuriyar Hatita, da kuma zuriyar Shobai, 138.46Masu hidimar haikali: Zuriyar Ziha, da zuriyar Hasufa, da zuriyar Tabbawot,47da zuriyar Keros, da zuriyar Siya, da zuriyar Fadon,48da zuriyar Lebana, da zuriyar Hagaba, da zuriyar Shalmai,49da zuriyar Hanan, da zuriyar Giddel, da zuriyar Gahar.50Da zuriyar Riyayya, da zuriyar Rezin, da zuriyar Nekoda,51da zuriyar Gazzam, da zuriyar Uzza, da zuriyar Faseya,52da zuriyar Besai, da zuriyar Mewunim, da zuriyar Nefushesim.53Da zuriyar Bakbuk, da zuriyar Hakufa, da zuriyar Harhur,54da zuriyar Bazlut, da zuriyar Mehida, da zuriyar Harsha,55da zuriyar Barkos, da zuriyar Sisera, da zuriyar Timah,56da zuriyar Neziya, da zuriyar Hatifa.57Da zuriyar bayin Suleman: da zuriyar Sotai, da zuriyar Soferet, da zuriyar Ferida,58da zuriyar Ya'ala, da zuriyar Darkon, da zuriyar Giddel,59da zuriyar Shefatiya, da zuriyar Hattil, da zuriyar Fokeret Hazzebayim, da zuriyar Amon.60Dukkan masu hidimar haikali, da zuriyar bayin Suleman, 392.61Waɗannan su ne mutanen da suka tafi daga Tel Mela, Telkasha, Kerub, Addon, da Imma. Amma ba zasu iya ba da shaida cewa iyayensu zuriyar Isra'ila ba ne:62da zuriyar Delaiya, da zuriyar Tobiya, da zuriyar Nekoda, 642.63Waɗanda ke daga firistoci: zuriyar Habaiya, da Hakkoz, da Barzilai (wanda ya auro matarsa daga mutanen Barzillai na Giliyad ake kuma kiran su da sunansu).64Waɗannan sun binciko rubutaccen tarihinsu a cikin waɗanda aka karɓo tarihinsu bisa ga asalinsu, amma ba'a samu ba, don haka aka cire su daga aikin firist don ba su da tsarki.65Daga nan sai gwamna ya ce da su ba za a barsu su ci rabon firistoci ba na abinci daga cikin abincin hadaya har sai an sami firist tare da Urim da Tummim.66Dukkan taron baki ɗaya shi ne 42,360,67ban da barorinsu maza da mata, waɗanda daga cikinsu aka sami 7,337. Suna da mawaƙa maza da mata da suka kai 245.68Dawakansu guda 736, bijimansu 245,69raƙumansu, 435, da jakunansu, 6,720.70Waɗansu daga cikin shugabannin iyaye suka bada kyautai domin aikin. Gwamna ya bada awo dubu na zinariya, da bangaji 50, da suturar firistoci guda 530.71Waɗansu daga cikin shugabannin iyalai suka bayar da awo dubu ashirin na zinariya da awon azurfa 2,200.72Sauran jama'a suka bayar da awo dubu ashirin na zinariya, da kuma awo dubu biyu na azurfa, da suturar firistoci guda sittin da bakwai,73To sai firistoci da Lebiyawa, da masu tsaron ƙofa da mawaƙa, da waɗansu mutane da masu hidima a haikali da dukkan Isra'ila dake cikin birane. A wata na bakwai sai mutanen Isra'ila suka zauna a biranensu."
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Sa'ad da muka gama ganuwar"
Anyi wannan tare da taimakon. AT: "Ni da waɗansu muka kafa ƙofofin"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. Watakila manufofin sune: 1) Nehemiya ya zaɓe su. AT: "Na kuma sanya masu tsaron ƙofofin da mawaƙa da Lebiyawa a wuraren aikinsu" ko 2) Wani ne daban ya zaɓe su. AT: "Suka sanya masu tsaron ƙofofin da mawaƙa da Lebiyawa a wuraren aikinsu"
mutanen da aka sa a kowacce ƙofa, suke da hakkin bari a shiga cikin birni ko haikali, da buɗewa da rufe ƙofofi a wasu lokuta domin dalilan da shugaba ya sanya
makaɗa na baki dake bida sujada, cikin jerawa, da bukukuwa, suna kaɗe-kaɗe da furci dake jaddada da inganta taron
Waɗannan duka sunayen mutane ne.
"Na bada umarni ga ɗan'uwana Hanani ya zama mai hidimar kulawa"
"masu kulawa da masarautar"
"mai tsoron Allah fiye da mutane masu yawa"
Kalmar "su" na nufin Hanani da Hananiya.
Manufofin da ake zato sune 1) Hanani da Hananiya suka yi waɗannan ayyuka ko 2) Hanani da Hananiya suka yi waɗannan ayyuka da taimakon masu tsaron ƙofofin ko 3) masu tsaron ƙofofin sunyi waɗannan ayyuka ƙarƙashin shugabancin Hanani da Hananiya.
"rana ta yi tsaka a sama"
"Ku kulle ƙofofin kusa mãkaransu lokacin da masu tsaron ƙofofin ke tsaro"
"ku rufe ƙofofin ku kulle su"
"Ku sanya masu gadi daga cikin mutanen da ke zama a Yerusalem"
"wurin gadin" ko "wurin aikin"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "mutanen basu gama sake gina gidaje ba tukuna
A nan "ba ni iko" Nehemiya na nufin tunane-tunanensa da manufofinsa. A duba yadda aka fassara wannan a Nehemiya 2:12. AT: "motsa ni" ko "bida ni"
"a lissafa su ayi masu rigista"
Wannan littafi ne wanda bai wanzu ba kuma.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "aka samu cewa wani ya rubuta wannan a ciki"
"Waɗannan zuriyar lardin ne"
"suka dawo daga" ko "suka zo daga"
Wannan kari ne da ke zancen tafiya zuwa Yerusalem, wanda ke bisa tudu sama da sauran kewayen.
"waɗanda Nebukadnezza shugaban Babila ya kwasa daga ƙasar haihuwarsu zuwa bauta." Sojojin Babila suka yi haka ƙarƙashin umarnin Nebukadnezza.
Waɗannan sunayen mutane ne.
An yi ƙidaya sa'ad da Isra'ilawa suka dawo Yerusalem da farko daga bauta. Lissafin yana mamadin yawan mazajen da ke kowacce ƙungiyar iyali. Wannan jimla na gabatar da rahoton da ke surorin da ke gaba.
Nehemiya yana sake lissafa jimillar mutanen da suka dawo daga bauta. Mutanen suka yi ƙungiyar iyalai bisa ga sunayen kakanninsu. Lissafin yana mamadin lissafin yawan mazajen kowanne iyali.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"wannan, zuwa zuriyar Yeshuwa da Yowab ne"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Marubucin ya yanke wannan jimla. AT: "zuriyar Ater, wanda yake zuriyar Hezekiya ne"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Waɗannan sunayen wuraren ne a Yahuda.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Kalmar "gida" na ma'anar iyali. AT: "daga iyalin Yeshuwa"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Waɗannan ayoyi sun ci gaba da sunayen mutanen da zuriyarsu suka dawo daga bauta.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan mutum an san shi kuma da suna Si'aya a cikin Ezra 2:44.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan mutum sunan wani ne da ake kira Hassoferet a cikin Ezra 2:55
Wannan mutum sunan wani ne da ake kira Feruda a cikin Ezra 2:55
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"Sun binciko rubutaccen lissafin tarihinsu" ko " Sun nemo rubutaccen lissafin tarihinsu"
"Waɗannan" na nufin zuriyar Habaiya, Hakkoz da Barzilai. (Duba: Nehemiya 7:63)
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "amma basu sami lissafinsu ba"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. Jimlar "aikin firist" za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau "aiki a matsayin firistoci." AT: "gwamnan ya maida su kamar marasa tsarki kuma bai bar su buyi aiki a matsayin firistoci ba"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "har sai firist mai Urim da Tummim ya yadda"
Waɗannan duwatsu ne masu tsarki da firist ke ɗauke da su a ƙirjinsa kuma wasu lokutta yana amfani dasu ya nemi sanin nufin Allah.
"Dukkan ƙungiyar baki ɗaya"
"shi ne mutane 42,360"
"mawaƙa maza da mawaƙa mata"
"ɗari bakwai da talatin da shida ... ɗari biyu da arba'in da biyar ... ɗari huɗu da talatin da biyar ... dubu shida da ɗari bakwai da ashirin." Waɗannan lissafin dabbobin da aka dawo da su ne.
"manyan kakanni" ko "shugabannin dangogi"
"aka sanya cikin ma'aji"
"awo 1,000"
Awo guda sulen zinariya ne da mutanen daular Fasiya suke amfani da shi.
"bangaji hamsin." Waɗannan manyan darurruka ne.
"suturar firistoci ɗari biyar da talatin." Waɗannan karikitan suturar firistoci ne da suke sanyawa.
"awo 20,000"
"awon azurfa dubu biyu da ɗari biyu." awon maina rabin kilo ne na nauyin azurfa.
wani ƙarfe mai ƙyallin tuka, da ake amfani da shi ana sulella, kayan kwalliya, kwanoni da kambuna
"awon maina 2,000"
"suturar firistoci 67"
Wannan rahoto na nufin wasu Isra'ilawa waɗanda ba firistoci ba ne ko wasu ma'aikatan haikali.
Wataƙila ma'anonin sune: 1) dukkan ƙungiyoyin Isra'ilawa da aka lissafa a wannan aya ko 2) sauran Isra'ilawa waɗanda basu aiki a haikali.
"wata na 7" wannan watan bakwai ne na kalandar Ibraniyawa. A lokacin ƙarshen watan seftemba ne da farkon watan oktoba na kalandar Turawa.
"suka yi zamansu a biranensu"
1Sai dukkan mutane suka taru a matsayin mutum ɗaya a fili a gaban Ƙofar Ruwa. Sai suka tambayi Ezra marubuci ya kawo Littafin Shari'a na Musa, wanda Yahweh ya umarci Isra'ila.2A rana ta fari a wata na bakwai, Ezra firist ya kawo shari'a a gaban taron mutanen maza da mata, da duk waɗanda zasu iya ji su kuma fahimta.3Sai ya fuskanci filin Ƙofar Ɍuwa, sai ya yi karatu daga cikinsa tun daga asubahi har zuwa tsakar rana, a gaban dukkan maza da mata waɗanda zasu ji su kuma fahimta, kuma dukkan mutanen suka saurari karatun littafin shari'a a hankali.4Sai Ezra marubuci ya tsaya a kan dogon dakali na katako wanda mutane suka shirya saboda wannan dalilin. Waɗanda ke tsaye a gefansa su ne Mattitiya, Shema, Ananiya, Yuriya, Hilkiya, da Ma'aseiya, a gefen damarsa; da Fedaiya, Mishyel, Malkiya, Hashun, Hashbaddana, Zakariya, da Meshullum suna gefensa na hagu.5Sai Ezra ya buɗe littafin a gaban dukkan mutane, don yana tsaye ne a saman mutanen, sa'ad da ya buɗe littafin sai dukkan mutane suka miƙe tsaye.6Sai Ezra ya yi godiya ga Yahweh, Allah mai girma, sai dukkan mutane suka ɗaga hannuwansu sama suka amsa, "Amin! Amin!" Sai suka sunkuyar da kansu suka yi sujada ga Yahweh da fuskokinsu a ƙasa.7Hakannan Yeshuwa, Bani, Sherebiya, Yamin, Akkub, Shabbetai, Hodiya, Ma'aseiya, Kelita, Azariya, Yozabad, Hanan, da Felaiya - Lebiyawa - suka taimaki mutane su fahimci shari'ar, a sa'ad da mutane suke a wurarensu.8Sun karanta daga cikin littafin, Shari'ar Allah, suka faiyace ta a fili suka kuma fassarata suka bada ma'anarta ga mutane don mutane su fahimci karatun.9Nehemiya gwamna, da Ezra firist da marubuci, da kuma Lebiyawa da ke yiwa mutane fassara suka ce da dukkan mutanen, "Wannan rana ce mai tsarki ga Yahweh Allanku. Kada ku yi baƙinciki ko kuka." Don dukkan mutanen sun yi kuka bayan da suka ji manganganun shari'a.10Sai Nehemiya ya ce da su, "Kuje ku ci kitse ku kuma sami abu mai zaƙi ku sha, ku kuma aikawa waɗanda basu da abin yin bikin, don wannan rana mai tsarki ce ga Ubangijinmu. Kada ku yi alhini, don farincikin Yahweh shi ne ƙarfinku."11Sai Lebiyawa suka sa mutane su yi shiru, suna cewa, "Ku natsu! Don wannan rana mai tsarki ce. Kada ku yi baƙincikin."12Daga nan sai mutane suka tafi don su ci, su sha, su kuma yi zumunci, suyi biki cikin murna sosai saboda sun fahimci maganar da aka koyar da su.13A rana ta uku sai shugabannin iyalai da iyaye daga dukkan mutane, da firistoci, da Lebiyawa, suka taru a wurin Ezra marubuci don su sami fahimta daga manganganun shari'a.14Sai suka ga wani wuri inda Yahweh ya umarta ta wurin Musa cewa 'ya'yan Israi'la su taru a cikin bukkoki a lokacin bikin watan bakwai.15Sai suyi shela a cikin dukkan biranensu, da Yerusalem, cewa, "Kuje can ƙasa mai duwatsu, ku kawo rassan zaitun da zaitun na daji, da tuwon-biri, da na dabino, da durumi da sauran itatuwa masu rassa don ku yi bukkoki, kamar yadda ya ke a rubuce."16To sai mutanen suka fita suka samo rassan suka yi wa kansu bukkoki, dukkansu kowa da nasa rufe-rufen, da harabunsu, da kuma harabar gidan Allah, a fili a gaban Ƙofar Ruwa da kuma dandalin dake ƙofar Efiraim.17Dukkan mutanen da suka dawo daga bautar talala suka kakkafa bukkoki suka zauna a cikinsu. Don tun daga kwanakin Yoshuwa ɗan Nun har ya zuwa wannan rana mutanen Isra'ila ba su yi wannan biki ba, don haka suka yi murna sosai.18Hakanan rana bayan rana, daga rana ta fari zuwa rana ta ƙarshe, Ezra ya karanta littafin shari'ar Allah. Su kan yi bikin a kwanaki bakwai a rana ta takwas sai ayi babban taro, don nuna biyayya ga wannan umarni.
Kalmar "dukka" gamewa ne da ke nuna mutanen bakiɗaya suka zo tare. AT: "mutane dukka suka taru"
Wannan wani babban buɗewa ne ko hanyar ƙofa cikin ganuwar.
Wannan zai iya zama dukka ko sashe daga litattafai biyar na farkon Tsohon Alƙawari.
Wannan watan bakwai ne na kalandar Ibraniyawa. Rana ta farko na watan bakwai yana kusa da tsakiyar Seftemba a kalandar Turawa. AT: "A rana ta 1 na watan 7"
"kawo littafin shari'a"
Wannan zai haɗa da yaran da suka isa fahimtar abin da ake karantawa.
"Ya juya ya fuskanci filin"
A nan "daga" na nufin Littafin Shari'a na Musa.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan kalma "gaban" za a iya bayyanata tare da aikatau "duba." AT: "Kowa yaga Ezra ya buɗe littafin"
"Littafin Shari'a"
"yana tsaye ne a bisa sama da inda mutanen suke"
Mutane sun miƙe tsaye ne domin nuna bangirma ga maganar Allah.
Wannan kalma "godiya" za a iya fassarawa a matsayin aikatau. AT: "Ezra ya godewa Allah"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Kalmar 'Sun" a nan na nufin Lebiyawa.
Wannan kalma "fassarawa" da "ma'ana" za a iya fassarawa a matsayin aikatau. AT: "fassarawa a faiyace da bayyana ta"
"abin da aka karanta"
Wannan gamewar na nuna anyi babban kuka cikin mutanen. AT: "gama mutanen sunyi kuka mai zafi"
Wannan rahoto na nuna cewar an gayawa mutanen da suyi buki da abinci mai gina jiki da abubuwan sha masu zaƙi. AT: "ku ci abinci maigina jiki ku sha abu mai zaƙi"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "kada ku yi baƙinciki"
Wannan kalma "farinciki" da "ƙarfi" za a iya fassarawa a matsayin aikatau ko wakilin aiki. AT: "farinciki cikin Yahweh zai kiyaye ku: ko "zama cikin farinciki cikin Yahweh zai zama mafakarku"
"Ku yi shiru!" ko "Ku yi tsit!"
Kalmar suna "murna" za a iya bayyanawa a matsayin aikatau. AT: "yi murna sosai"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "maganar da ya bayyana masu"
"A rana ta 2" ko "washegari"
Kalmar suna "fahimta" za a iya bayyanawa a matsayin aikatau. AT: "a gane"
"watan 7." Wannan watan bakwai ne a kalandar Ibraniyawa. Lokacin ƙarshen Seftemba ne da farkon Oktoba a kalandar Turawa.
Waɗannan bukkoki ne ba dawwamammu ba da mutane ke yi da rassa da ganyen itatuwa.
"Sai su yi sanarwa"
wani irin ƙaramin itace ne mai furanni
"itatuwa masu ganyaye"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "kada ku yi baƙinciki"
"kowanne ya gina ta shi bukka"
Waɗannan wasu manyan buɗewa ne ko hanyoyin ƙofofi cikin ganuwar.
"a buɗaɗɗen wuri ta Ƙofar Ifraim"
"Daga kwanakin Yeshuwa"
A nan "Nun" sunan wani mutum ne.
Kalmar suna "murna" za a iya bayyanawa a matsayin aikatau. AT: "mutanen suka yi murna sosai"
Wannan kari na ma'anar "kowacce rana."
Wannan rahoto na zancen dukkan makon bikin. AT: "daga rana ta fari zuwa rana ta ƙarshe na makon"
"suka yi bikin" ko "suka yi shagalin bukin"
"a rana ta 8"
Wannan wani taron addini ne na musamman.
Wannan rahoto na zancen "umarni" dokar Yahweh ne game da yadda za a gama bukin bukkokin. AT: "kamar yadda Allah ya zartar da duka"
1A rana ta ashirin da huɗu a wannan watan dai sai mutanen Israi'la suka taru suna kuma yin azumi, suna sanye da tufafin makoki, suka kuma baɗa toka a kawunansu.2Zuriyar Israi'la suka keɓe kansu daga dukkan bãƙi. Suka tsaya, suka furta zunubansu, da kuma ayyukan mugunta na kakaninsu.3Suka tsaya a wurarensu, har kusan faɗuwar rana suna karanta littafin shari'ar Yahweh Allahnsu. Har kusan rabin ɗaya ranar suna ta furta zunubansu suna sunkuyawa a gaban Yahweh Allahnsu.4Sai Lebiyawa, Yeshuwa, Bani, Kadmiyel, Shebaniya, Bunni, Sherebiya, Bani, da Kenani, suka tsaya a filin suka yi kuka ga Yahweh Allahnsu.5Sai Lebiyawa, Yeshuwa, da Kadmiyel, Bani, Hashabneyya, Sherebiya, Hodiya, Shebaniya, da Fetahiya, suka ce, "Ku miƙe tsaye ku yabi Yahweh Allahnku har abada abadin." Dama su yabi sunanka maɗaukaki, kuma ya ɗaukaka fiye da dukkan albarku da yabo.6Kai ne Yahweh. Kai kaɗai. Ka yi samaniya da sammai mafiya nisa, da dukkan rundunoninsu, da duniya da duk abin da ke cikinta, da tekuna da duk abin da ke cikinsu. Ka ba dukkan su rai, kuma dukkan rundunar sama na yi maka sujada.7Kai ne Yahweh, Allahn da ya zaɓi Abram, ya kawo shi daga Ur ta Kaldiyawa ya bashi suna Ibrahim.8Ka gane cewa yana da aminci a gare ka, ka kuma yi masa alƙawari zaka bada ƙasar Kan'aniyawa, da Hitiyawa, da Amoriyawa, da Feriziyawa, da Yebusiyawa, da Girgashiyawa, ga zuriyarsa. Ka kiyaye alƙawarinka saboda kai adali ne.9Ka ga ƙuncin kakanninmu a Masar ka kuma ji kukansu a bakin Tekun Iwa.10Ka bada alamu da al'ajibai gãba da Fir'auna da dukkan bayinsa da dukkan mazaunan ƙasarsa don ka san Masarawa sun yi masu mugun hali sosai. Amma ka samarwa kanka suna wanda ya ke nan har ya zuwa yau.11Kai ne kuma ka raba teku biyu a gabansu, don su bi ta cikin tsakiyar teku a kan sandararriyar ƙasa; ka kuma kora masu runtumarsu cikin zurfafa kamar dutse a cikin ruwaye zurfafa.12Ka bida su ta wurin ginshiƙin girgije da rana, da kuma ginshiƙin wuta da dare don ta nuna masu hanyar da za su bi.13A kan Dutsen Sinai ka sauko ƙasa ka yi magana da su daga sama ka kuma ba su ka'idojinka na adalci da kuma shari'arka ta gaskiya, da farillanka da dokokinka masu kyau.14Ka koyar da su game da Asabar ɗinka mai tsarki, ka basu dokoki da farillai da shari'u ta wurin Musa bawanka.15Ka basu gurasa daga sama saboda yunwarsu, da kuma ruwa daga dutse saboda ƙishinsu, ka kuma ce da su ku shiga ku mallaki ƙasar da ka rantse za ka basu.16Amma su da kakaninmu suka nuna rashin girmamawa, suka yi taurin kai, basu saurari dokokinka ba,17Suka ƙi su saurara, kuma suka ƙi tunani a kan al'ajibanka da kayi a cikinsu, amma suka yi tayarwa, saboda tayarwarsu suka zaɓi shugaba don su koma zaman bautarsu. Amma kai Allah ne wanda ya ke cike da gafara, da alheri da tausayi, mai jinkirin fushi, mai madawwamiyar ƙauna. Baka yashe su ba.18Ko ma a lokacin da suka kafa ɗan maraƙin daga narkakken ƙarfe suka ce, 'Wannan Allahnku wanda ya fitar da ku daga ƙasar Masar,' suka kuma yi babban saɓo,19kai, cikin tausayinka, baka yashe su ba a cikin jeji. Ginshiƙin girgijen ya bi da su akan hanya bai kuma rabu da su ba da rana, hakama ginshiƙin wutar bai rabu da su ba da dare don ya haskaka masu hanyar da zasu bi.20Ruhunka manargaci ka basu don ya gargaɗe su, Baka janye mannarka daga bakunansu ba, ka kuma basu ruwa saboda ƙishinsu.21Har shekaru arba'in ka yi masu tanadi a cikin jeji, kuma basu rasa komai ba. Suturunsu basu koɗe ba ƙafafunsu kuma ba su kumbura ba.22Ka basu mulkoki da al'ummai ka ba kowannesu lungu-lungu na ƙasar. Sa'an nan suka mallaki ƙasar Sihon da sarkin Heshbon da kuma ƙasar Og sarkin Bashan.23Ka sa 'ya'yansu su yawaita kamar taurarin sama, ka kuma kawo su ƙasar da ka faɗawa ubanninsu su je su mallake ta.24Sai mutanen suka je suka mallaki ƙasar ka kuma kori mazauna ƙasar a idonsu, wato Kan'aniyawa. Ka ba da su a hannuwansu, tare da sarakunansu da mutanensu na ƙasar, don Isra'ila su yi yadda suka so da su.25Suka kame ƙayatattun birane da kuma ƙasa mai bada abinci, sun kuma mamaye gidaje cike da abubuwa kyawawa da rijiyoyin da tuni aka haƙa, da garkar inabi da ta zaitun, da itatuwa masu bada 'ya'ya sosai. Da suka ci suka ƙoshi suka yi ƙiba suka ji daɗin kansu a cikin babbar nagartarka.26Daga nan suka yi rashin biyayya a gare ka. Suka yi watsi da dokokinka. Suka karkashe annabawanka da suka gargaɗe su su komo gare ka, sun kuma yi babban aikin saɓo.27Don haka sai ka ba da su a hannun maƙiyansu, waɗanda suka wahalashe su. A cikin wahalarsu, suka yi kuka gare ka, ka kuwa ji su daga sama, Kuma saboda babban jinƙanka ka aika masu da masu kuɓutarwa waɗanda suka kuɓutar da su daga ƙasar maƙiyansu.28Amma bayan sun huta, sai suka ƙara yin aikin mugunta a gabanka, sai ka yashe su a hannun maƙiyansu suka mulke su. Duk da haka sa'ad da suka juyo suka yi kuka gare ka, ka ji su daga sama, da kuma a lokuta da yawa saboda yawan jinƙanka ka 'yanto su.29Ka gargaɗe su da su juyo ga dokokinka. Duk da haka suka yi husuma kuma ba su saurari umarnanka ba. Suka yi zunubi kan sharuɗan da ke bada rai ga wanda ya kiyaye su. Sun miƙa kafaɗunsu na taurin kai suka ƙi sauraro.30Ka yi ta watsi da su da kuma yi masu gargaɗi ta wurin Ruhunka ta hannun annabawanka. Duk da haka ba su saurara ba. Don haka sai ka miƙa su ga magabtan ƙasashensu31Amma a cikin jinƙanka mai girma baka hallakar da su dukka ba, ko kuma ka yashe su, Don kai Allah ne mai yawan jinƙai da alheri.32Yanzu saboda haka ya Allahnmu - kai mai girma ne, maɗaukaki, managarci wanda ka riƙe alƙawarinka da kuma ƙaunarka madauwamiya - kar ka bari duk wannan wahalar da ta same mu ta zama kamar 'yar ƙarama a gare ka, ga sarakunanmu, ga masu mulkinmu, da kuma firistocinmu, da annabawanmu, da iyayenmu, da dukkan mutanenka tun daga kwanakin sarakunan Asiriya har ya zuwa yau.33Kai mai adalci ne a cikin duk abin da ya same mu, don da amincinka ka bi da mu, amma muka yi aikin mugunta.34Sarakunanmu da masu mulkinmu, da firistocinmu da iyayenmu, ba mu kiyaye shari'arka ba, ko mu saurari dokokinka ko sharuɗɗan da ka gindaya mana waɗanda kuma ka gargaɗe su ba.35Koma da a cikin mulkinsu, sa'ad da suka ji daɗin babban alherinka a gare su, a wannan babbar ƙasa mai yalwa da ka basu, ba su bauta maka ba ko kuma su juyo daga mugayen hanyoyinsu ba.36Yanzu mu bayi ne a ƙasar da ka ba iyayenmu su ji daɗin yalwarta da dukkan abubauwa masu kyau da ke cikinta, yanzu mun zama bayi a cikinta!37Dukkan wadatar da ka ba mu tana hannun sarakunan da ka ɗora a kanmu saboda zunubanmu. Suna mulkin jikkunanmu da dabbobinmu yadda suka so. Muna cikin babban ƙunci.38Saboda dukkan wannan, muka yi dauwamammen alƙawari a rubuce. A kan littafin da aka hatimce akwai sunayen shugabanninmu, da Lebiyawa da firistoci."
"rana ta ashirin da huɗu a wannan wata" Wannan na wajen tsakiyar Oktoba a kalandar Turawa.
"mutanen Israi'la suka zo tare"
Wannan domin su nuna ladamarsu ne domin dukkan laifuffukan da su da kakanninsu suka yi.
'Isra'ilawa"
"basu kuma yin kowacce irin hurɗa da waɗanda ba Isra'ilawa ba"
"suka furta laifuffukan da suka yi da laifuffukan da kakanninsu suka yi"
Dukkan Isra'ilawa suka tsaya
"suna ta furta laifuffukan da suka yi"
"sujada" ko "yabo"
Wasu juyin sun fassara, "Yeshuwa, Bani ... sun tsaya a matakalun da aka gina wa Lebiyawa"
Waɗannan sunayen mazaje
A nan Lebiyawa na magana da mutanen Isra'ila.
"albarkaci Yahweh"
sunayen mazaje. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 9:3-4.
sunayen mazaje
Lebiyawa suna magana da Yahweh. " bari mutanen Isra'ila su yabi sunanka maɗaukaki, Yahweh"
runduna sojoji ne. "Rundunar sama" yana maganar misalin cewa taurari kamar su sojoji ne. Su kuma Taurarin misali ne na mala'iku masu yawa. Taurari na sujada ga Yahweh misali ne na mala'iku na sujada ga Yahweh.
Lebiyawa sun ci gaba da addu'a a gaban dukkan mutane.
"Ur, inda mutanen Kaldiyawa ke zama"
Zuciya, can cikin wani taliki, na mamadin wani taliki. AT: "Kaga cewa ya amince da kai ɗungun"
Waɗannan sunayen ƙungiyar mutane
Yahweh ya ga
Ma'anar rahoton shine Yahweh ya tashi ya yi aiki saboda Isra'ilawa sunyi kukan neman taimakon.
Annobobin sun gwada zuciyar Fir'auna, suka kuma zama shaida gãba da taurin zuciyarsa. AT: "alamu da al'ajibai da suka yi shaida gãba da Fir'auna" ko "alamu da al'ajibai da suka kayar da Fir'auna"
"dukkan Masarawa"
"sun nuna fin ƙarfi ga Isra'ilawa" ko "wulaƙanta zaɓaɓɓun mutanen Allah"
A nan "suna" na a madadin matsayi. AT: "ka yi fice yadda har yau mutane na tunawa"
Allah ya raba
a wannan zancen, marubucin ya yi bayanin cewa Allah ya jefa Masarawa cikin Teku cikin sauƙi kamar yadda wani zai jefa dutse cikin ruwa, kuma dutsen ya nutse ƙarƙashin ruwa bakiɗaya.
Yahweh ya bida
Sa'ad da Allah ya yi magana da mutanensa, ana bayanin haka kamar "saukowa" ko "saukowa daga sama." Wannan hanyar kwatance ce da cewa Allah ya bayyana ga wannan taliki. AT: "ka bayyana" ko "ka sauko daga sama"
Dukkan waɗannan maganganu na bayanin wani abu, shari'ar Musa.
Dukkan waɗannan kalmomi na nufin shari'ar Musa.
Isra'ilawa a zamanin Musa da mutanen Isra'ila bayan zamanin Musa
Ainihin zancen shine "suka taurare wuyansu." Idan yarenka na da wani kari da ake amfani da shi a gurbin taurin kai, za a iya amfani da ita a nan.
"al'ajiban da ka yi a cikinsu"
Isra'ilawa zasu san cewa wannan na maganar kakanninsu yadda suka so su koma Masar. AT: "suka zaɓi shugaba domin ya maida su Masar inda suka yi bauta"
An yi maganar marmarin yin gafara kamar wani abin ruwa ne da zai iya cika kwano. AT: "wanda ke a shirye ya yi gafara"
An yi maganar ƙauna kamar amfanin gona da Yahweh zai iya rabawa da mutane. AT: "yana ƙaunar mutanensa ƙwarai"
Yahweh bai yashe da Isra'ilawa
suka narkar da ƙarfe suka yi zube na siffar maraƙi
A duba yadda aka fassara a cikin Nehemiya 09:12.
Marubucin ya canza salon magana domin ya jaddada abubuwa kyawawa da Yahweh ya ba mutanensa. Yarenka yana iya kasancewa da wata hanyar jaddada waɗannan abubuwa.
koyar
Za a iya bayyana wannan da tarawa. AT: "ka ba su mannarka a ba rowa"
bakin na zancen talikin ɗungun. AT: "daga wurin su"
Yahweh ya ba Isra'ilawa mulkoki.
"Ya ikonta su suyi nasara da mulkoki da al'ummai
"Ya ikontasu su mallaki lungu-lungu na ƙasar"
Waɗannan sunayen sarakuna ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
Yahweh ya sa zuriyar Isra'ilawa a zamanin Musa
An yi zancen Kan'aniyawa a nan kamar wasu ƙananan abubuwa ne da wani taliki zai sanya a hannun wani taliki. A sanya wani abu a hannun wani shine aba wani iko akan wannan abin ɗungun. AT: "Ya ikonta Isra'ilawa suka shugabance su ɗungun"
Isra'ilawa a zamanin Musa suka kame
ƙasa mai albarka
ramuka a ƙasa inda mutane ke ajiye ruwa
Wannan zai iya zama zance da manufar "daina tunani game da Yahweh" ko "suka shagala."
Anyi maganar shari'a kamar wani abu marar amfani da wani zai iya wurgarwa. AT: "basu ɗauki shari'arka da daraja ba kuma basu kula da ita ba"
Isra'ilawa suka yi watsi da shari'ar Yahweh.
A nan "hannu" na a madadin iko ko mulki. AT: "kasa maƙiyansu suka kayar da su kuma suka wahalashe su"
A nan "hannu" na a madadin iko ko mulki. AT: "ka aika mutane da suka tsaida maƙiyansu daga yi masu mugunta"
A nan "sun" na nufin Isra'ilawa kuma "ka" ga Yahweh.
A nan "hannu" na a madadin iko ko mulki. AT: "ka yi watsi da su ka bar maƙiyansu suka kayar da su"
Idan yarenka na da kalmar "saurari" wadda kuma ke nufin "biyayya," ayi amfani da ita a nan.
Yahweh da kansa anyi maganarsa kamar shine ainihin dokokin da kansu. AT: "kai kodayake kana bada rai ga dukkan wanda ke biyayya da dokokinka"
Waɗannan siffofin maraƙi wanda ya ƙi mai shi yasa masa karkiya a kafaɗunsa. A nan sun zama misalin mutanen masu taurin kai. AT: "Suka zama masu taurin kai"
A nan "hannu" na a madadin iko ko mulki. AT: "A duba yadda aka fassara waɗannan kalmomi cikin Nehemiya 9:27. AT: "ka bar al'ummai maƙwaftansu su kayar da su"
Yahweh ya miƙa
"ba ka hallakasu ba"
Mai yiwu wa ne a raba wannan cikin jimloli biyu. "kar ka bari duk wannan wahalar ta zama kamar 'yar ƙarama a gare ka. Wahalar da ta same mu ... har ya zuwa yau"
Kalmar "ta zo mu" na maganar miyagun abubuwan da suka same mu kamar mutane ne da suka kawo mugunta. AT: "mugunta ... mun wahala ... abubuwan da suka wahalar da mu"
sa'ad da suka ji daɗin kyawawan abubuwan daka bayar a gare su"
"ba su yi biyayya da shari'arka ba ko koyarwarka ba"
"dukkan abubuwa masu kyau da ke cikinta" ko "dukkan abubuwa masu kyau da zamu samu a cikinta"
"Mu na biyan haraji ga sarakuna domin aikata ƙasar da ke tamu"
Sarakunan suna mulki
saboda mutanen sun yi rashin biyayya kuma Yahweh ya hore su
Mai karatun ya gane cewa mazajen sun rubuta sunayensu a littafin kafin a hatimce shi.
1A bisa takardu masu tambari akwai Nehemiya, wanda ya ke gwamna, ɗan Hakaliya da Zedekiya,2Sera'iya, Azariya, Irmiya,3Fashhur, Amariya, Malkiya,4Hattush, Shebaniya, Malluk,5Harim, Meremot, Obadiya,6Daniyel, Ginneton, Baruk,7Meshullam, Abiya, Miyamin,8Ma'aziya, Bilgai, da kuma Shemaiya. Waɗannan su ne firistocin.9Lebiyawan su ne: Yeshuwa ɗan Azaniya, Binuyi na iyalin Henadad, Kadmiyel,10da kuma sauran yan'uwansu Lebiyawa, Shebaniya, Hodiya, Kelita, Felaiya, Hanan,11Mika, Rehob, Hashabiya,12Zakkur, Sherebiya, Shebaniya,13Hodiya, Bani, da kuma Beninu.14Shugabannin mutanen su ne: Farosh, Fahat-Mowab, Ilam, Zattu, da Bani,15Bunni, Azgad, Bebai,16Adoniya, Bigbai, Adin,17Atar, Hezekiya, Azzur,18Hodiya, Hashum, Bezai,19Harif, Anatot, Nebai,20Magfiyash, Meshullam, Hezir,21Meshezabel, Zadok, da Yadduwa,22Felatiya, Hanan, Anaya,23Hoshiya, Hananiya, Hasshub,24Hallohesh, Filha, Shobek,25Rehum, Hashabna, Ma'aseiya26Ahiya, Hanan, Anan,27Malluk, Harim, da kuma Ba'ana.28Game da sauran mutanen kuwa, waɗanda suke firistoci, Lebiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, da masu hidimar haikali, da kuma dukkan waɗanda suka keɓe kansu daga mutanen ƙasashen maƙwabta suka kuma miƙa kansu ga shari'ar Allah, har da matayensu, da 'ya'yansu maza da mata, dukkan waɗanda suke da ilimi da kuma fahimta,29suka haɗu tare da 'yan'uwansu, da sarakunansu, kuma suka ɗaure kansu da la'ana da kuma alƙawarin yin tafiya bisa shari'un Allah, wadda Musa bawan Allah ya bayar, su kuma kula su kuma yi biyayya da dukkan dokokin Yahweh Ubangijinmu da kuma umarnai da kuma farillunsa.30Mun yi alƙawari ba zamu ba da 'ya'yanmu mata aure ga mazaunan ƙasar ba ko mu auro 'yan matansu ga 'ya'yanmu maza.31Mun kuma yi alƙawari idan mazaunan ƙasar suka kawo kayayyaki ko wani hatsi domin sayarwa a ranar Asabarci, ba zamu saya daga gare su ba a ranar Asabaci ko wata rana mai tsarki. Kowacce shekara ta bakwai zamu bar filayenmu su huta, kuma zamu ṣoke dukkan basusuwan da aka yi.32Mun yi na'am da dokokin bayar da ɗaya cikin uku na awo a shekara domin hidimar gidan Allahnmu,33domin tanadin gurasar wuri-mai tsarki, da kuma hatsin baiko na kullum, baye-baye na ƙonawa a ranakun Asabaci, bukukuwan sabon wata da kuma shiryayyar liyafa, da kuma baye-baye masu tsarki, da kuma baye-baye na zunubi domin yi wa Isra'ila kaffara, haka kuma domin dukkan ayyukan gidan Allahnmu.34Da firistoci da Lebiyawa da mutane suka jefa ƙuri'u domin itacen yin baiko. Ƙuri'un zasu zaɓi wane ne daga cikin iyalanmu zai kawo itace zuwa gidan Allahnmu a sanyayyun lokatai kowacce shekara, domin ƙonawa a bisa bagadin Yahweh Allahnmu, kamar yadda ya ke a rubuce cikin shari'a.35Mun yi alƙawari mu kawo nunar fari da aka shuka a ƙasarmu cikin gidan Yahweh, da kuma nunar fari na kowanne itace duk shekara.36Kamar yadda aka rubuta a shari'a, mun yi alƙawari mu kawo cikin gidan Allah da kuma ga firistoci masu hidima a can, ɗan fari cikin 'ya'yanmu da kuma na garkunan shanunmu da garkunan tumakinmu.37Zamu kawo cụrinmu na fari da kuma baye-bayenmu na hatsi, da kuma 'ya'yan kowacce itaciya, da kuma sabon inabi da kuma mai zamu kawo su ga firistoci, ga rumbunan gidan Allahnmu. Zamu kawo wa Lebiyawa zakka daga ƙasarmu domin su Lebiyawa na karɓar ɗaya daga goma daga dukkan garuruwan da muke aiki.38Firist, zuriyar Haruna, dole yana tare da Lebiyawa sa'ad da suke karɓar ɗaya daga goma. Su Lebiyawa dole su kawo ɗaya daga goma ga gidan Allahnmu zuwa cikin runbunan ma'aji.39Gama mutanen Isra'ila da kuma zuriyar Lebi zasu kawo gudumuwoyin na hatsi, da sabon inabi, da kuma mai zuwa ga runbuna inda ake ajiyar santalolin wuri mai tsarki inda firistoci masu hidima suke, da kuma matsaran ƙofa, da kuma inda mawaƙa ke zama. Ba za mu yi watsi da gidan Allahnmu ba.
An rubuta sunayen waɗannan mutane a cikin takardun. Za a bayyana wannan a fili. AT: "Bisa takardu masu tambari akwai sunayen Nehemiya ... Hakaliya" ko "Bisa takardu masu tambari akwai sunayen waɗannan mutanen Nehemiya ... Hakaliya"
An sanya tambari ga takardun bayan da aka sa hannu ga sunayen a cikin takardun.
Wasu sunyi imanin cewa Nehemiya ne ya rubuta wannan littafi kuma yana magana game da kansa ne kamar shi wani ne daban saboda lissafin na mulki ne.
Wannan suna namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 1:1.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan suna namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:23.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:11.
A waɗannan ayoyin, Nehemiya ya lissafa sunayen firistoci waɗanda suka sa hannu a takardar. (Duba: Nehemiya 10:1)
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:10.
Waɗannan sunayen mazaje ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 9:4.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:11.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:4.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:4.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:29.
Wannan na nufin lissafin mutane a baya waɗanda suka sa hannu a takardar. AT: "Waɗannan sunayen firistoci ne waɗanda suka sa hannu a takardar"
Wannan na nufin waɗanda suka sanya sunayensu bisa hatimtattun takardun. AT: "Lebiyawan suka sanya sunayensu bisa hatimtattun takardun"
Waɗannan sunayen mazaje ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:18-19.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:24.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 7:43.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 9:4.
Waɗannan sunayen mazaje ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 8:7.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 7:49.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 10:11.
Waɗannan sunayen mazaje ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:17.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:2.
Wannan na nufin waɗanda suka sanya sunayensu bisa hatimtattun takardun. AT: "Shugabannin mutanen waɗanda suka sanya sunayensu bisa hatimtattun takardun"
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:25.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:11.
Waɗannan sunayen mazaje ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 7:12.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 9:4.
Waɗannan sunayen mazaje ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 7:16-17.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya7:7.
Waɗannan sunayen mazaje ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 7:20.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 8:7.
Waɗannan sunayen mazaje ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 7:23.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 7:27.
Waɗannan sunayen mazaje ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:4.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 8:4.
Waɗannan sunayen mazaje ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:11.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:17.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 3:23.
Waɗannan sunayen mazaje ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 10:4.
Wannan sunan namiji ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 7:6.
Wannan na nufin mutanen da aka sa a kowacce ƙofa, su ke da hakkin lura da shiga birnin ko haikalin, haka nan kuma buɗewa da rufewar ƙofofin a lokutta da yanayan da aka tsaida daga shugaba. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 7:1.
Za a nemi ayi bayanin cewa waɗannan su ne masu waƙa a haikali. AT: "mawaƙan haikali"
Za a iya bayanin wannan zance. AT: "dukkan waɗanda suka isa fahimtar abin da alƙawarin biyayya da Allah ke ma'ana"
"'yan'uwansu sarakuna" ko "'yan'uwansu shugabanni." Waɗannan kalmomi na nufin mutane iri ɗaya.
Wannan na maganar mutanen sun ɗauki alƙawari da la'ana kamar alƙawarin da la'anar igiya ne dake ɗaure su. AT: "suka rantsewa kansu da alƙawari da la'ana" ko "suka ɗauki alƙawari suka kuma kira ga la'ana ta sauko masu idan suka ƙi kiyaye wa"
Wannan kari ne. AT: "su rayu ta wurin shari'ar Allah" ko "su yi biyayya da shari'ar Allah"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "wadda Musa bawan Allah ya bayar ga Isra'ila"
"su bi"
Wannan na ma'anar cewa ba zasu bar 'ya'yansu maza da mata su aure su ba. AT: "ba zamu bayar da 'ya'yanmu mata aure ga mutanen ƙasar ba ko mu ɗauko 'ya'yansu mata su auri 'ya'yanmu maza ba"
Wannan na nufin mutanen da ke zaune a ƙasar kuma basu bautawa Yahweh. AT: "mutanen wannan ƙasa da basu bautawa Yahweh"
Wakilin suna "mu" a nan ya haɗa da Nehemiya mutanen Yahudawa, amma ba makarancin wannan littafi ba.
"shekara ta 7"
Wannan kari ne. AT: "ba zamu noma gonakinmu ba" ko "ba zamu shuka wani abu ba a gonakinmu"
Wannan na ma'anar cewa ba zasu nemi waɗanda su ke bi bashi ba da su biya. AT: "zamu ṣoke dukkan basusuwa da mu ke bin mutane" ko "zamu gaya wa mutane cewa ba za bu biya mu ba kuma"
"Muka yi alƙawarin biyayya da dokokin"
Wakilin suna "mu" a nan ya haɗa da dukkan Isra'ilawa da Nehemiya banda firistoci da Lebiyawa, bai kuma haɗa da makarancin wannan littafi ba
"awo 1/3." "Na uku" na ma'anar kashi ɗaya daga cikin abin da aka kasa dai-dai gida uku. Za a iya rubuta wannan bisa ga magwajin zamani. AT: "giram 5 na azurfa"
"a biya domin kulawa da"
Wannan na nufin gurasa 12 da aka gasa ba da gamin yisti ba da ake ajiye wa a haikali ana amfani da su a nuna kasancewar Allah tare da mutanensa.
Waɗannan bukukuwa ana yin su ne sa'ad da wata ke ƙarami farkon fitowa a sararin sama.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "domin Lebiyawa su ƙona"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "kamar yadda aka rubuta"
"a cikin ƙasarmu" ko "bisa ƙasarmu"
A nan wakilin suna "mu" ya haɗa da Nehemiya da Isra'ilawa banda firistoci da Lebiyawa, kuma banda mai karatun wannan littafi
Mai yiwu wa ma'anonin sun haɗa da 1) cụrin da aka yi daga ɓarjin gari, 2) ɓarjin gari, ko 3) niƙaƙƙen hatsi.
Kalmomin "farko" an fahimce su tun daga farawar jimloli. Za a iya maimaita su. AT: "sabon inabi na farko da kuma mai" ko "mafi kyau daga sabon inabi da kuma mai"
"wuraren da ake ajiyar abubuwa a cikin haikali"
A nan "ƙasarmu" na nufin dukkan abin da ake shukawa a ƙasar. AT: "zakka daga abin da muke shukawa a ƙasar"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "mutanen suka ba su zakkar"
Wannan na nufin kashi ɗaya daga cikin kashi goma.
"runbunan ma'aji da ke cikin haikali"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: " runbuna inda firistoci ke ajiyar abubuwan da ake amfani da su a haikali"
Za a iya faɗin wannan a matsayin ƙarawa. AT: "Za mu lura da haikalin"
A nan wakilin suna "mu" ya haɗa da Nehemiya da dukkan Isra'ilawa kuma banda mai karatun wannan littafi
1Shugabannin mutanen suka zauna cikin Yerusalem, sai kuma sauran mutanen suka jefa ƙuri'u domin kawo ɗaya daga cikin goma ya zauna a Yerusalem, birni mai tsarki, sai kuma sauran kashi taran a bar su a wasu garuruwan.2Sai mutanen suka albarkaci dukkan waɗanda suka yarda su zauna a Yerusalem.3Waɗannan su ne shuagabannin lardin dake zama Yerusalem. Duk da haka, a cikin garuruwan Yahuda kowanne na zama a ƙasarsa, harma da waɗansu Isra'ilawa, firistoci, Lebiyawa, masu hidimar haikali, da zuriyar bayin Suleman.4A Yerusalem akwai mazauna waɗanda suke na zuriyar Yahuda da kuma zuriyar Benyamin. Mutanen Yahuda su ne: Atayya ɗan Uzziya ɗan Zakariya ɗan Amariya ɗan Shefatiya ɗan Mahalalel, na zuriyar Ferez.5Akwai Ma'aseiya ɗan Baruk ɗan Kol-Hoze ɗan Hazayya ɗan Adayya ɗan Yoyarib ɗan Zakariya, ɗan Bashiloni.6Dukkan 'ya'yan Ferez da suka zauna cikin Yerusalem 468 ne. Su zama shahararrun mutane.7Waɗannan su ne zuriyar Benyamin: Sallu ɗan Meshullam ɗan Yoyed ɗan Fedayya ɗan Kolayya ɗan Ma'aseyya ɗan Itiyel ɗan Yeshayya,8da waɗanda suke binsa, da Gabbai da Sallai, mutane 928.9Yowel ɗan Zikri shi ne mai kula da su, da kuma Yahuda ɗan Hassenuwa shi ya zama na biyu a shugabanci bisa birnin.10Daga firistocin: Yedayya ɗan Yoyarib, Yakin,11Serayya ɗan Hilkiya ɗan Meshullam ɗan Zadok ɗan Merayot ɗan Ahitub, babban mai kula da gidan Allah,12da kuma abokan aikinsu waɗanda suka yi aikin gidan Allah, mutane 822, tare da Adayya ɗan Yeroham ɗan Felaliya ɗan Amzi ɗan Zakariya ɗan Fashhur ɗan Malkiya.13Yan'uwansa ne shugabannin zuriya, mutane 242; da kuma Amashsai ɗan Azarel ɗan Ahzai ɗan Meshillemot ɗan Immer,14da kuma yan'uwansu, mutane 128 masu ƙarfin halin yaƙi; mai kula da su shi ne Zabdiyel ɗan Hagedolim.15Daga Lebiyawa: Shemayya ɗan Hashub ɗan Azrikam ɗan Hashabiya ɗan Bunni,16da kuma Shabbetai da Yozabad, su da ke daga wajen shugabannin Lebiyawa kuma su ne ke da haƙin aikin waje da gidan Allah.17Akwai Mattaniya ɗan Mika ɗan Zabdi, na zuriyar Asaf, shi ne jagora da ya fara bada godiya cikin addu'a, da kuma Bakbukiya, shi ne na biyu cikin yan'uwansa, da kuma Abda ɗan Shammuwa ɗan Galal ɗan Yedutun.18Dukkan Lebiyawa da ke cikin birni mai tsarki lissafinsu 284 ne.19Masu kula da ƙofa: Akkub, Talmon, kuma sauran abokan hurɗarsu, da suke kula da ƙofofi, mutane 172.20Sauran Isra'ila da kuma sauran firistoci da Lebiyawa suna cikin dukkan garuruwan Yahuda. Kowannen su na zaune a wurinsa na gãdo.21Ma'aikatan haikali suna zaune cikin Ofel, da Ziha da Gishfa su ne masu kula da su.22Babban shugaba a bisa Lebiyawan da ke a Yerusalem shi ne Uzzi ɗan Bani ɗan Hashabiya ɗan Mattaniya ɗan Mika, daga zuriyar Asaf, mawaƙa a bisa aikin cikin gidan Allah.23Suna a ƙarƙashin umarnai masu girma daga wurin sarki, kuma an bada umarnai masu tsanani ga mawaƙa yadda kowacce rana ke bukata.24Sai Fetaniya ɗan Meshezabel, daga zuriyar Zera ɗan Yahuda, ya zauna a ɓarayin sarki a game da kowanne al'amari da ya shafi mutane.25A game da ƙauyuka da kuma filayensu, wasu mutanen Yahuda sun zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da kuma cikin Dibon da ƙauyukanta, da kuma cikin Yekabzil da ƙauyukanta,26da cikin Yeshuwa, Molada, Bet Felet,27Hazar Shuwal, da kuma Biyasheba da ƙauyukanta.28Wasu daga mutanen Yahuda sun zauna cikin Ziklag, Mekona da kuma ƙauyukanta,29Enrimmon, Zora, Yamut,30Zanowa, Adullam, da kuma ƙauyukanta, da cikin Lakish da filayenta, da Azeka da ƙauyukanta. Sai suka zauna daga Biyasheba zuwa Kwarin Hinnom.31Benyamin suka zauna daga Geba, a Mikmash da Aiya, a kuma Betel da ƙauyukanta,32Anatot, Nob, Ananiya,33Ramah, Gittayim,34Hadid, Zeboyin, Neballat,35da kuma Ono kwarin maƙera.36daga cikin Lebiyawa dake zama cikin Yahuda aka sanya su kan mutanen Benyamin.
"mutanen suka jefa alamun duwatsu"
"domin kawo ɗaya daga cikin goma"
"a ƙasarsa: Isra'ilawa"
"wasu mutanen Yahuda da kuma wasu mutanen Benyamin"
"Daga zuriyar Yahuda:"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"daga zuriyar Ferez"
A cikin waɗannan ayoyin, Nehemiya ya ci gaba da lissafa shugabannin lardi waɗanda ke zaune a Yerusalem.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan na nufin mutumin da ya zo daga Shilo.
"Dukka ... ɗari huɗu da sittin da takwas ne." Perez yana da zuriya 468 da ke zaune a Yerusalem. (Duba:
"Mutane ne masu ƙarfin hali" ko "Jarumawan mutane ne"
"Waɗannan su ne wasu daga cikin zuriyar." Yarenka zai buƙaci kayi bayani cewa wannan ba lissafin dukkan zuriyar ba ne.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"mutane ɗari tara da ashirin da takwas ne."
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"'yan'uwansu" ko "danginsu"
"waɗanda su ke yin aiki a haikali." A nan "gidan" na nufin "gidan Allah" wanda aka ambata cikin ayoyin da suka gabata.
"mutane ɗari takwas da ashirin da biyu"
'yan'uwan su ne Adayya, da ɗan Yeroham (Duba: Nehemiya 11:12).
Wannan kalma zance ne domin 1) dangi Isra'ilawa ko 2) mutanen da ke aiki iri ɗaya. AT: "waɗanda ke tare" ko " abokan aiki"
"mutane ɗari biyu da arba'in da biyu"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"mutane ɗari da ashirin da takwas masu ƙarfin halin yaƙi." "Waɗannan "jarumawan yaƙi ne" ko "masu ƙarfin halin yaƙi."
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"daga wajen shugabannin Lebiyawa, su ne ke shugabanci"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wato, wanda ya bida mawaƙa.
Mai yiwuwa ma'anonin sune 1) Bakbukiya ɗan'uwan Mattaniya ne kuma na biyu a shugabanci daga Mattaniya ko 2) "Bakbukiya, wanda ya bida ƙungiyar mawaƙa ta biyu."
Bayanin na nufin birnin Yerusalem.
"lissafinsu ɗari biyu da tamanin da huɗu ne." Akwai Lebiyawa ɗari biyu da tamanin da huɗu a Yerusalem.
mutanen da aka sanya a kowacce ƙofa, su ke da hakkin bada damar shiga birnin ko haikali, haka kuma buɗewa da rufewar ƙofofin a lokutta da dalilan da shugaban ya tsãra. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 7:1.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"mutane ɗari ne da saba'in da biyu"
Waɗannan sunan wani wuri ne.
"Mai lura da"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"Sarkin ya gaya masu abin da za su yi"
Za a iya fassara wannan a matsayin aikatau. AT: "sarkin ya jaddada masu abin da za su yi da mawaƙan "
"a ɓarayin sarkin Fasiya a matsayin mashawarci game da dukkan al'amuran da suka shafi mutanen Yahudawa"
Waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen wurare ne.
A nan "su" na nufin mutanen Yahuda.
"Mutanen Benyamin suka zauna Geba, a Mikmash da Aiya"
Waɗannan sunayen wurare ne.
Wannan zai iya zama wata hanyar faɗin sunan garin Ai ne.
Mai yiwuwa ma'anonin sune 1) wannan kwatancen Ono ko 2) "Kwarin maƙera ne" ko "Kwarin Maƙera," Wani sunan ne na Ono, ko 3) Wani wuri ne daban da Ono, "da kuma Kwarin Maƙera."
"Wasu rarrabawar Lebiyawa na Yahudanci an sanya su da su zauna tare da mutanen Benyamin"
1Waɗannan su ne firistoci da Lebiyawa da suka fito tare da Zerubbabel ɗan Sheltiyel da kuma tare da Yeshuwa: Serayya, da Irmiya, Ezra,2Amariya, Malluk, Hattush,3Shekaniya, Rehum, da kuma Meremot.4Akwai su Iddo, Ginneton, Abiya,5Miyamin, Mowadiya, Bilga,6Shemayya, da Yoyarib, Yedayya,7Sallu, Amok, Hilkiya, da Yedayya. Waɗannan ne shugabannin firistoci da mataimakansu a kwanakin Yeshuwa.8Lebiyawan su ne Yeshuwa, Binuyi, Kadmiyel, Sherebiya, Yahuda, da Mattaniya, wanda shi ne shugaban waƙoƙin godiya, tare da abokan aikinsa.9Bakbukiya da Unni, su ne abokan aikinsu, suka tsaya daura da su lokacin yin sujada.10Yeshuwa shi ne mahaifin Yowakim, Yowakim shi ne mahaifin Eliyashib, Eliyashib ne Mahaifin Yowada,11Yowada ne mahaifin Yonatan, kuma Yonatan shi ne mahaifin Yadduwa.12A zamanin Yowakim waɗannan su ne firistoci, su ne shugabannin iyalai: Merayya ne shugaban Serayya, Hananiya ne shugaban Irmiya,13Meshullam shi ne shugaban Ezra, Yehohanan shi ne shugaban Amariya,14Yonatan ne shugaban Malluk, kuma Yosef shi ne shugaban Shebaniya.15Adna ne shugaban Harim, Helkai shugaban Merayot,16Zakariya shi ne shugaban Iddo, Meshullam shi ne shugaban Ginneton17Zikri shi ne shugaban Abiya. ... na Miniamim. Filtai shi ne shugaban Mowadiya.18Shammuwa shi ne shugaban Bilga, Yehonatan shi ne shugaban Shemayya,19Mattenai shi ne shugaban Yoyarib, Uzzi shi ne shugaban Yedayya,20Kallai shi ne shugaban Sallai, Eba shi ne shugaban Amok,21Hashabiya shi ne shugaban Hilkiya, da Netanel shi ne shugaban Yedayya.22A kwanakin Eliyashib, Lebiyawa Eliyashib, Yowada, Yohanan, da Yadduwa aka lisafta su a matsayin shugabannin iyalai, kuma aka lisafta firistocin a zamanin mulkin Dariyos na Fasiya.23Su zuriyar Lebi, shugabannin iyalansu aka lisafta su a cikin littafi na tarihi har zuwa kwanakin Yohanan ɗan Eliyashib.24Su shugabannin Lebiyawan su ne Hashabiya, Sherebiya, da Yeshuwa ɗan Kadmiyel, tare da abokan tarayyarsu, suna zaune daura da su domin raira waƙoƙin yabo da kuma bada godiya, suna aikinsu cikin ka'ida, suna biyayya da umarnin Dauda, mutumin Allah.25Mattaniya, Bakbukiya, Obadiya, Meshullam, Talmon, da Akkub su ne matsaran ƙofofi masu tsaro a tsaye a ɗakunan ajiya dake gefen ƙofofin.26Sun yi hidima a cikin kwanakin Yoyakim ɗan Yeshuwa ɗan Yozadak, da kuma a kwanakin Nehemiya gwamna da kuma Ezra firist da marubuci.27A lokacin keɓewar ganuwar Yerusalem, mutane suka nemi firistoci dukkan inda suke zama, suka kawo su Yerusalem su yi bikin keɓewar tare da farinciki, da godiya da kuma waƙoki tare da kuge, da molo, da giraya, da tsarkiyoyi.28Zumuntar mawaƙa suka tattaru tare daga garuruwa kewaye da Yerusalem daga kuma ƙauyuka na Netofatiyawa.29Sun kuma fito daga Bet Gilgal daga kuma filin Geba da Azmabet, domin mawaƙa sun gina wa kansu ƙauyuka kewaye da Yerusalem.30Su firistoci da Lebiyawa suka tsarkake kansu, suka kuma tsarkake mutanen, da ƙofofin, da kuma ganuwar.31Sai na sa shugabannin Yahuda suka hau kan ganuwar, na kuma shirya manyan ƙungiyoyin mawaƙa guda biyu domin su yi waƙoƙin godiya. Sashi ɗaya suka yi dama bisa ganuwar ta sashen Ƙofar Kashin Shanu.32Hoshayya da rabin shugabannin Yahuda suka tafi tare da su,33bayan su Azariya, Ezra, Meshullam,34Yahuda, Benyamin, Shemayya, da Irmiya,35da wasu 'ya'yan firistoci ɗauke da algaitu, da kuma Zekariya ɗan Yonatan ɗan Shemayya ɗan Mattaniya ɗan Mikayya ɗan Zakkur ɗan Asaf.36Da akwai waɗansu cikin 'yan'uwan Zakariya, Shemayya, Azarel, Milalai, Gilalai, Ma'ai, Netanel, Yahuda, Hanani, suna ɗauke da kayayyakin kiɗe-kiɗen Dauda mutumin Allah. Ezra marubuci na tsaye gabansu.37Daga Ƙofar Maɓulɓula suka haura kai tsaye zuwa matakalar birnin Dauda, daga matakala zuwa ganuwa a bisa fãdar Dauda, zuwa wajen Kofar Ruwa daga gabas.38Ɗaya ƙungiyar mawaƙan masu bada godiya suka tafi zuwa wancan sashen. Na bi su a bisa ganuwar tare da rabin mutanen, sama da Hasumiyar Murahu, zuwa kan Ganuwa Mai Faɗi,39da bisa Kofar Ifraim, da kuma daga Tsohuwar Ƙofa, da kuma daga Ƙofar Kifi da kuma Hasumiyar Hananel da kuma Hasumiyar Ɗari, zuwa ga Ƙofar Tumaki, sai suka tsaya a Ƙofar Matsara.40Da haka dukkan mawaƙa suka bada godiya suka ɗauki wurinsu a cikin gidan Allah, nima na ɗauki wurina tare da rabin ma'aikatan da ke tare da ni.41Sai su firistoci suka ɗauki wurin zamansu: Eliyakim, Ma'aseyya, Miniyamin, Mikayya, Elihonai, Zakariya, da kuma Hananiya, tare da ƙahonni,42da kuma Ma'aseyya, Shemayya, Eliyaza, Uzzi, Yehohanan, Malkiya, Elam, da kuma Eza, sai kuma mawaƙan suka sa aka ji su Jezrahiya kuma shi ne shugabansu.43Suka bada manyan hadayu a wannan rana, da farinciki kuma, gama Allah ya sa suka yi farinciki da murna mai girma. Haka mataye da kuma yara suka yi murna. Da haka aka ji farincikin Yerusalem daga nesa.44A wannan rana aka naɗa mutane su shugabanci ɗakunan ajiya domin gudumuwa, nunar fari, da zakka, domin su tara adadin da aka shirya bisa ga shari'a a cikinsu domin firistoci da kuma Lebiyawa. Kowannen su aka ba shi aikin noma filayen da ke kusa da garuruwan. Domin Yahuda sun yi farinciki da firistoci da kuma Lebiyawa waɗanda ke tsaye a gabansu.45Suka yi hidimar Allahnsu, da kuma hidimar tsarkakewa, haka kuma mawaƙa da matsaran ƙofofi suka yi, domin kiyaye umarnan Dauda da na Suleman ɗansa.46A tun zamanin dã, cikin kwanakin Dauda da Asaf, akwai shugabannin mawaƙa, aka yi waƙokin yabo da godiya ga Allah.47A zamanin Zerubbabel da kuma zamanin Nehemiya, dukkan Isra'ilawa suka kawo rabonsu na kowacce rana ga mawaƙa da kuma matsaran ƙofofi. Suka keɓe wa Lebiyawa rabonsu na kowacce rana, su kuma Lebiyawa suka keɓe wa 'ya'yan Haruna nasu rabon.
"Waɗanda suka iso daga Babila"
"ƙarƙashin shugabancin Zerubbabel"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Masu karatu na dã zasu iya fahimtar cewa Yeshuwa ne babban firist. AT: "Yeshuwa babban firist"
An ci gaba da lissafin da aka fãra daga cikin Nehemiya 12:1.
An ƙara waɗannan kalmomin ne domin wannan juyin. Idan aka ci gaba da lissafin da aka fãra daga cikin Nehemiya 12:1, ana iya cire waɗannan kalmomi.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Ginnetoi zai iya zama wata hanyar faɗin sunan "Ginneton"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Mai yiwuwa ma'anonin sune 1) wannan lokacin hidimar sujada ne kuma waɗannan ƙungiyoyi biyu ne na mawaƙa da masu sujada, ko 2) waɗannan ƙungiyoyi suna lura da haikali a lokutta daban-daban, ko "suna juyin aikin lura da haikalin."
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan Yeshuwa shi ne aka ambata a cikin Nehemiya 12:1.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Waɗannan sunayen iyalai ne da aka ba sunan mazajen.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Waɗannan sunayen iyalai ne da aka ba sunan mazajen.
"shi ne shugaban iyalin" ko "shi ne shugaban zuriyar"
Ginneton zai iya zama wata hanyar faɗin sunan Ginnetoi.
Mutanen da suka yi linkokin juyin Ibraniyanci sai ba su sanya sunan shugaban iyalin Miniamim ba. Sai masu fassara su yi rubutun ƙasan shafi su yi bayanin wannan. Juyin ULB ya yi amfani da haka "..." a nuna cewa sunan shugaban ya ɓace. AT: "Wani ne shugaban Miniamim"
Mowadiya zai iya zama wata hanyar faɗin sunan Mawadiya
sunayen mazaje
Mai yiwuwa wata ma'anar ita ce "har sai zamanin mulkin Dariyos"
Wannan zai iya nufin Littafin Tarihi. Marubutan sun rubuta kalmomin a cikin ayoyin da suka gabata a cikin wani littafi da aka rubuta al'amarin ranar.
Lissafin da ke haikali lissafi ne da ya kai har zuwa kwanakin Yohanan a nan ya tsaya.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan na nufin yadda suka raira wasu daga cikin waƙoƙin sujadarsu. Shugaba ko ƙungiya ɗaya zasu raira layi ɗaya, daga nan ƙungiya ɗaya ko biyu "dake tsaye daura da su" zasu raira wani layin suna mayar wa.
Sarki Dauda ya umarci Lebiyawa yadda zasu jera su kuma bida waƙoƙin sujada.
An tsaida ranar ta wurin lissafin waɗanda ke shugabancin Yahudawa a kwanakin. "sa'ad da Yoyakim ...Yozadak ke babban firist, da sa'ad da Nehemiya ke gwamn da kuma Ezra ... ke marubuci"
Mai yiwuwa ma'anonin su ne 1) "A lokacin da suka keɓe ganuwar Yerusalem" ko 2) "Domin ayi keɓewar ganuwar Yerusalem."
"gwangwani biyu, kewaye da farantin ƙarfe da ake bugawa tare domin ya bada kiɗa"
Waɗannan sunayen wurare ne.
shugabannin mutanen da ke zama lardin Yahuda
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"suka biyo bayan su"
Wasu juyin sun karanta, "daga cikin sauran firistoci da ke tare da algaitu, akwai Zekariya"
Dukkan sunayen bayan "Zekariya" kakannin Zekariya ne. Wannan lissafin ya haɗa Zekariya tare da shahararren mawaƙin nan Asaf. "Zekariya wanda ke ɗan Yonatan, wanda ke ɗan Shemayya, wanda ke ɗan Mattaniya, wanda ke ɗan Mikayya, wanda ke ɗan Zakkur, wanda ke ɗan Asaf"
"Tare da su akwai waɗansu"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"Ezra marubuci na jagorancin su"
Waɗannan sunayen buɗaɗɗun wurare ne a jikin ganuwar.
ƙungiyar masu waƙa
Nehemiya ya bi su
Waɗannan sunayen dogayen gine-gine ne inda mutane ke zaman tsaro daga haɗari.
Wannan sunan wani sashen ganuwar ne
Waɗannan sunayen buɗaɗɗun wurare ne a jikin ganuwar.
Nehemiya ke magana a nan. AT: "Ni, Nehemiya, nima na ɗauki wurina"
Waɗannan sunayen mazaje ne Waɗanda su ne firistoci a lokacin .
Wannan sunan namiji ne wanda shi ne shugaban mawaƙa.
Mai yiwuwa ma'anonin sune 1) farkon firistoci bakwai ne kawai aka lissafa daga Eliyakim zuwa Hananiya suka ɗauki ƙahonni ko 2) dukkan firistoci 15 da aka lissafa daga Eliyakim zuwa Hananiya suka ɗauki ƙahonni.
"suka raira da ƙarfi"
"farinciki mai girma"
A nan "farincikin Yerusalem" misali ne na "ihun da mutanen Yerusalem suka yi." Za a iya fassara wannan a matsayin aikatau. AT: "mutane da ke nesa da Yerusalem suka ji ihun da mutanen Yerusalem suka yi yayin da su ke shagalin"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau.Babu cikakken fahimtar wanda ya naɗa su. AT: " suka naɗa mutane su shugabanci"
abubuwan da mutane ke ba firistoci
Da alamar mutanen sun naɗa mazajen ne saboda mutanen Yahuda suna godiya domin firistoci da Lebiyawa da ke yi masu hidima.
Lebiyawa da firistocin ba wai tsaye su ke kawai ba, suna hidima bisa ga aikinsu. Za a iya bayanin ma'anar. AT: "waɗanda ke tsaye a gabansu suna bautar Allah"
Waɗannan mutane ne da aka sanya a kowacce ƙofa, su ke da hakkin bada damar shiga birnin ko haikalin, haka kuma buɗewa da rufewar ƙofofin a lokutta da dalilan da shugaban ya tsãra. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 7:1.
Wannan jimla ta nuna dalilin da yasa mutanen suka yi abin da auka yi ai cikin Nehemiya 12:45 kuma ya ƙara bamu bayani game da lokacin da Dauda ya gaya wa mutane yadda za su yi sujada a haikali.
Zerubbabel zuriyar Sarki Dauda ne kuma ɗaya daga cikin gwamnoni a lardin Yahuda.
"Dukkan Isra'ilawa suka keɓe rabo"
firistoci a Isra'ila, waɗanda zuriyar Haruna ne, ɗan'uwan Musa
1A wannan rana suka karanta Littafin Musa mutane na saurare. Aka iske a rubucce a cikinsa cewa kada wani Ba'ammone ko mutumin Mowab ya shigo cikin taron jama'ar Allah, har abada.2Dalili kuwa shi ne domin basu taryi mutanen Isra'ila da gurasa da ruwan sha ba, amma suka yiwo hayar Bala'am domin ya la'anci Isra'ila. Duk da haka, Allahnmu ya juyar da la'anar zuwa albarka.3Da dai suka ji shari'ar, sai suka ware kowanne baƙo daga Isra'ila.4Yanzu dai kafin wannan aka sa Eliyashib firist ya zama shugaban ɗakunan ajiya na gidan Allahnmu. Yana da dangantaka da Tobiya.5Eliyashib ya shirya wa Tobiya babban ɗaki na ajiya, inda dã aka ajiye hadayar gari, da ta turare, da tasoshi, da kuma zakkar hatsi, da sabon inabi, da mai, wanda aka keɓe domin Lebiyawa, da mawaƙa, da matsaran ƙofofi, da kuma gudumuwa domin firistocin.6Amma cikin dukkan wannan lokacin ba na cikin Yerusalem. Gama a cikin shekara ta talatin da biyu ta sarautar Atazazas sarkin Babila na tafi wurin sarki. Bayan lokaci kaɗan sai na nemi izinin tafiya daga wurin sarki7sai kuma na komo Yerusalem. Na fahimci muguntar da Eliyashib ya aikata da ya ba Tobiya ɗakin ajiya a cikin haikali na gidan Allah.8Na fusata ƙwarai sai na watsar da kayan ɗakin Tobiya zuwa waje daga ɗakin ajiya.9Na umarta a tsabtace ɗakunan ajiyar, na sake zuba kayayyakin gidan Allah a cikinsu, wato baye-bayen hatsi, da kuma turare.10Sai na fahimci cewa ba a ba wa Lebiyawa rabonsu ba, kuma duk sun gudu, kowannen su zuwa ga gonarsa, su Lebiyawa da mawaƙa waɗanda suka yi aikin.11Sai na yiwa shugabannin faɗa na ce, "Me ya sa aka yi watsi da gidan Allah?" Na tara su tare kowannen su a wurin aikinsa.12Sa'annan dukkan Yahuda suka kawo zakkar hatsi, sabon inabi, da kuma mai cikin ɗakunan ajiya.13Sai naɗa ma'aji bisa gidajen ajiya su Shelemiya firist da Zadok marubuci, kuma daga wurin Lebiyawa, Fedayya. Na kusa da su shi ne Hanan ɗan Zakkur ɗan Mattaniya, gama an iske su amintattu ne. Aikinsu shi ne su rarraba ragowar kayayyakin ga abokan aikinsu.14Ka tuna da ni, Allahna, game da wannan, kuma kada ka shafe sarai ayyukan alherin da na aikata sabili da gidan Allahna da kuma hidimarsa.15A waɗannan kwanakin na gani a Yahuda mutane na matsar inabi a ranar Asabaci suna kuma kawo tulin hatsi da ɗauro su bisa jakkai, da kuma inabi, da zaitun, da ɓaure, da kuma kowanne kayan nauyi, wanda suka kawo cikin Yerusalem a ranar Asabaci. Na yi tsayayya da su ganin cewar suna sayar da abinci a wannan rana.16Mutanen Tiya masu zama cikin Yerusalem suka kawo kifi da dukkan kowanne kayayyaki, suka sayar a ranar Asabaci ga mutanen Yahuda da kuma cikin birnin!17Sai na fuskanci shugabannin Yahuda kai tsaye, "Wacce irin mugunta ce haka kuke yi, ku na mai da ranar Asabaci wofi?18Ba abin da iyayenku suka yi ba kenan? Ba Allahnmu ya aiko da dukkan wannan masifar a bisanmu da kuma wannan birni ba? Yanzu kuna ƙara kawo wata hasala kan Isra'ila ta wofintar da Asabaci."19Daga nan da zarar dare ya yi a bakin ƙofofin Yerusalem kafin Asabaci, na ba da umarni a kulle ƙofofin kada kuma a buɗe su har sai bayan Asabaci. Na sanya wasu bayina a bakin ƙofofin don kada a iya shigo da kaya ciki ranar Asabaci.20'Yan kasuwa da masu sayar da kowanne irin tufafi suka taru a wajen Yerusalem sau ɗaya ko biyu.21Amma na yi masu kashedi, "Donme ku ke taruwa a wajen ganuwa? Idan kuka ƙara yin haka, zan kore ku da hannuna!" Daga wannan lokaci ba su ƙara zuwa a ranar Asabaci ba.22Sai na dokaci Lebiyawa su tsabtace kansu, su kuma zo su tsare ƙofofin, a tsarkake ranar Asabacin. Ka tuna da ni game da wannan kuma, Allahna, ka kuma yi mani jinƙai sabili da amintaccen alƙawarinka zuwa gare ni.23A waɗannan kwanaki na kuma ga Yahudawan da suka auro matan Ashdod, da Ammon, da kuma Mowab.24Rabin 'ya'yansu na magana da yaren Ashdod. Babu waninsu da zai iya magana da harshen Yahuda, amma sai ɗaya daga cikin harshen sauran mutanen kawai.25Na fuskance su kai tsaye, na kuma la'anta su, na kuma bugi wasu daga cikinsu har na tsige sumar kansu. Na sa suka yi rantsuwa ga Allah, cewa, "Ba za ku bada 'ya'yanku mata ga samarinsu ba, ko ku ɗauko wa 'ya'yanku maza 'yanmatansu, ko don kanku.26Ba haka Suleman sarkin Isra'ila ya yi zunubi ta dalilin waɗannan matayen ba? A cikin al'ummai masu yawa babu sarki kamarsa, kuma Allahnsa ya ƙaunace shi, kuma Allah ya maishe shi sarki bisa dukkan Isra'ila. Duk da haka, matayensa bãƙi suka sa yayi zunubi.27Ƙaƙa zamu saurare ku mu aikata dukkan wannan babbar mugunta, mu kuma yi rashin aminci ga Allahnmu ta wurin auro mataye bãƙi?"28Ɗaya daga cikin 'ya'yan Yowada ɗan Eliyashib babban firist surukin Sanballat Bahorone ne. Saboda haka na sa shi ya gudu daga fuskata.29Ka tuna da su, Allahna, domin sun ƙazantar da firistanci, da kuma alƙawarin firistanci da kuma Lebiyawa.30Da haka na tsabtace su daga duk abin da da ke na bãƙunci, na kuma kafa ayyukan firistoci da na Lebiyawa, kowanne ga aikinsa.31Na yi tanadi domin baikon itace a lokatansu da na nunar fari. Ka tuna da ni, Allahna, domin alheri.
"saboda mutane su saurare
"zai kuskura ya shigo cikin taron jama'ar Allah"
"saboda ba su iya shigowa cikin taron jama'ar Allah ba"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: " suka naɗa Eliyashib firist" ko "shugabannin suka naɗa Eliyashib firist"
"Eliyashib da Tobiya sunyi aiki tare ƙut da ƙut"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"Eliyashib ya shirya wa Tobiya babban ɗaki don amfaninsa"
Waɗannan mutane ne da aka sanya a kowacce ƙofa, su ke da hakkin bada damar shiga birnin ko haikalin, haka kuma buɗewa da rufewar ƙofofin a lokutta da dalilan da shugaban ya tsãra. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Nehemiya 7:1.
"Amma cikin dukkan wannan lokacin da haka ke faruwa, na bar Yerusalem"
A nan "na" na nufin Nehemiya.
Wannan ɗaki ne wanda a baya an tsarkake shi domin ajiyar kayan baiko. (Duba: Nehemiya 13:5).
Za a iya bayanin cikakken ma'anar wannan zance. Za a kuma iya fassara wannan a matsayin aikatau. AT: "mutanen ba su kuma kawo baye-bayen su da zakka na abinci zuwa ɗakunan ajiya domin firistocin haikali"
Lebiyawa da mawaƙa da ke aikin sun bar haikalin, kowanne ya tafi gonarsa"
Nehemiya ya yi tambayar barkwanci domin ya ƙalubalanci ko ya yiwa shugabannin ba'a waɗanda basu yi aikinsu ba. Za a iya fassara wannan tambaya a matsayin jimla. AT: "kun yi watsi da gidan Allah"
Sunan ƙasar mamadin mutanen ƙasar ne. Watakila wannan gabaɗaya ne. AT: "dukkan mutanen da su ke zama a Yahuda"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Za a kuma iya fassara wannan a matsayin aikatau. Jimlar "amintattu" za a kuma iya fassara wannan a matsayin aikata. AT: "Na san cewa zan amince da su"
"Allahna, ka tuna dani game da wannan"
Kalmar " matsar inabi " wata magana ce da ke nufin inabin da ke cikin kwamin dutse matsewa. Mutanen su kan tattake inabin domin su matso ruwan su yi ruwan inabi da shi. AT: "tattake inabi a cikin kwamin dutse"
tattake wani abu domin a mitsike shi ko murje shi
Wannan sunan wani birni ne.
Nehemiya ya yi amfani da tambayar barkwanci ne domin ya tsautawa shugabannin Yahuda. Za a iya fassara wannan a matsayin zance. AT: "ku na aikata mugunta ta wurin ɓata ranar Asabaci." ko "Allah zai yi maku horo domin wannan mugunta da kuka aikata, ta wurin ɓata ranar Asabaci."
Nehemiya ya yi amfani da tambayar barkwanci ne domin ya tsautawa shugabannin Yahuda. Za a iya haɗa wannan tambaya a fassara a matsayin zance. AT: "kun san cewa ubanninku sun aikata wannan, shi yasa Allah ya aiko da dukkan wannan masifa a kanmu da bisa wannan birni."
"Sa'ad da rana ta faɗi ... kuma lokaci ya yi da za a fara Asabaci"
Za a iya fassara wannan a matsayin aikatau. AT: "cewa masu tsaro su riƙa rufe ƙofofin kada kuma su buɗe su har sai"
Za a iya fassara wannan a matsayin aikatau. AT: "babu wanda zai iya shigowa da abubuwan da suke so su sayar"
"mutanen da suka kawo abubuwa daban-daban da suke so su sayar"
Nehemiya ya yi amfani da tambayar barkwanci ne domin ya tsautawa fataken ya kuma jaddada dokarsa. Za a iya fassara wannan a matsayin zance. Za a iya yin bayanin cikakken ma'anar wannan zance. AT: "Ku na taruwa a bayan ganuwar gãba da umarnina."
Kalmar "hannu" misali ne na tilastawa. AT: "Zan kore ku tilas!" ko "Zan cire ku dole!"
"Allahna, ka tuna da ni game da wannan kuma." A duba yadda aka fassara wannan irin zance a cikin Nehemiya 13:14.
Waɗannan ayoyi sun gabatar da aikin da ya biyo baya.
"Yahudawan sun auro bãƙin mataye." Allah ya hana auren gauraye. Za a iya yin bayanin cikakken ma'anar wannan zance.
Wannan sunan wani birni ne.
Waɗannan sunayen al'ummai ne.
"Sakamakon hakan, rabin 'ya'yansu "
"Na yi magana da su kai tsaye game da abin da suka yi"
Nehemiya ya bugi wasu da hannuwansa.
"Na sa suka ɗauki alƙawari a gaban Allah"
Nehemiya ya yi amfani da tambayar barkwanci ne domin ya tsautawa mazajen. Za a iya fassara wannan a matsayin zance. AT: "Kun san cewa Suleman sarkin Isra'ila ya yi zunubi ta dalilin waɗannan matayen."
Nehemiya ya yi amfani da tambayar barkwanci ne domin ya tsautawa mazajen. Za a iya fassara wannan a matsayin zance. AT: "Ba zamu saurare ku ba mu aikata dukkan wannan babbar mugunta, mu kuma yi rashin aminci ga Allahnmu ta wurin auro mataye bãƙi."
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan na nufin wanda ya fito daga birnin Bet Horon.
"Na kore shi" ko "Na sa ya bar Yerusalem"
"Ka yi tunani game da su" ko "Ka tuna da abin da suka yi." A duba yadda aka fassara wannan irin zance a cikin Nehemiya 13:14.
Sun sa an wulaƙanta firistanci kuma anyi maganar karya alƙawarin kamar sun maida firistanci, da kuma alƙawarin marasa tsafta a zahiri. AT: "sun ƙazantar da firistanci, sun kuma karya alƙawarin da ka yi da firistoci da Lebiyawa"
"Ta wannan hanya na keɓe su"
"na gaya wa firistoci da Lebiyawa abin da za su yi"
"Na shirya yadda za a tanadi itace domin baye-bayen itace"
"domin baye-bayen nunar fari a lokacin girbi"
"Ka yi tunani game da dukkan abin da na yi, Allahna, ka kuma albarkace ni saboda abubuwan alheri da na aikata." A duba yadda aka fassara wannan irin zance a cikin Nehemiya 13:14.
1A kwanakin Ahasuros (wannan shi ne Ahasuros wanda yayi mulki daga Indiya har zuwa Kush, bisa larduna 127),2a kwanakin nan Sarki Ahasuros ya zauna bisa kursiyin sarautarsa a fadar Susa.3A shekara ta uku ta sarautarsa, yayi wa dukkan sarakunansa da barorinsa biki. Mayaƙan Fasiya da Midiya da manyan sarakuna da hakimai da gamnonin larduna duk suna gabansa.4Ya nuna darajar arziƙin mulkinsa da bangirman ɗaukakar ƙasaitarsa kwanaki da yawa, har kwanaki 180.5Da kwanakin nan suka cika, sarki yayi biki kuma na kwana bakwai. Yayi bikin ne saboda dukkan mutanen da suke a fadar Susa, manya da ƙanana. Anyi wannan a farfajiyar lambu da ke a fãdar sarki.6Anyi wa farfajiyar lambun ado da labulai farare da shunayya, aka ratayesu bisa kirtani na lallausar lilin mai launin shunayya haɗe da zobban azurfa aka ɗaure ajikin ginshiƙan duwatsu masu daraja. Akwai kujeru na zinariya, dana azurfa da suke a shirayin da aka daɓe da duwatsun ado masu daraja kamar su fofari mabil, fiyel da duwatsun dakali masu launi.7Aka bada abin sha a moɗayen zinariya, kowacce moɗa daban take, kuma ga ruwan inabin sarakai a yalwace saboda tsabar alfarmar sarki.8An shayar ne bisa ga umarni, "Kada a tilasa wa kowa." Sarki ya ba fadawan fadarsa umarni suyi wa kowa yadda yake so.9Har wayau, Sarauniya Bashti ta yawa mata biki a fadar Sarki Ahasuros.10A rana ta bakwai da sarki ke jin daɗi a zuciyarsa saboda ruwan inabi, ya cewa Mehuman, Bizta, Harbona, Bigta, Abagta, Zetar, da Karkas (shugabanni bakwai da ke masa hidima),11su kawo Sarauniya Bashti a gabansa da kambin sarauta a kanta. Yana so ya nuna wa mutane da fadawansa ƙyanta, gama tana da ƙyaƙƙyawan fasali.12Amma Sarauniya Bashti taƙi zuwa bisa ga faɗar sarki sa'ad da fadawa suka je suka faɗa mata. Sai sarki ya husata ƙwarai; fushinsa yayi ƙuna a ransa.13Sai sarki yayi shawara da waɗanda aka san su masu hikima ne, sun fahimci lokatai (domin haka sarki ya saba yi ga waɗanda suka ƙware a shari'a da hukunci).14Na kusa da shi su ne Karshina, Shetar, Admata, Tashish, Meres, Marsina, da Memukan, sarakuna bakwai na Fasiya da Midiya. Suna da 'yancin shiga gun sarki, suke da mafifitan muƙamai a mulkin.15"Bisa ga shari'a me za a yiwa Sarauniya Bashti saboda taƙi yin biyayya da umarnin Sarki Ahasuros wanda ya aika mata ta hannun shugabanni?'16Sai Memukan yace a gaban sarki da fadawansa, "Ba ga sarki ne kaɗai Sarauniya Basti tayi laifi ba, amma ga dukkan fadawa da dukkan mutanen da ke a lardunan Sarki Ahasuros.17Gama wannan al'amari da sarauniya ta aikata zai zama sananne ga dukkan mata. Zai sasu rena mazajensu. Zasu ce, 'Sarki Ahasuros ya umarta a kawo Sarauniya Bashti a gabansa amma taƙi.18Kafin faɗuwar ranar yau manyan matan Fasiya da Midiya da suka ji al'amarin sarauniya zasu maimaita wa dukkan hakiman sarki haka. Wannan zai kawo reni da fushi mai yawa.19Idan ya gamshi sarki bari a aika dokar sarauta daga gareshi, a kuma rubuta a shari'ar Fasiyawa da Midiyawa da bata canzawa, cewa Bashti ba zata ƙara zuwa gaban sarki ba. Bari sarki ya bada matsayin ta ga wacce ta fita.20Sa'ad da dokar sarki ta kai ko'ina a faɗin masarautarsa, dukkan mata zasu girmama mazansu, daga manyansu har zuwa ƙananansu."21Sarki da hakimansa sun gamsu ƙwarai da wannan shawara. Sarki kuwa yayi yadda Memukan ya shawarta.22Ya aika wasiƙu zuwa dukkan lardunansa, kowanne lardi da irin rubutunsa, kowaɗanne mutane da harshensu. Ya umarta kowanne namiji ya zama shugaban gidansa. Wannan doka an bada ita a cikin harshen kowaɗanne mutane da ke cikin masarautarsa.
"A lokacin Ahasuros" ko "Sa'ad da Ahasuros ke mulki a matsayin sarki"
Wannan bayani ne na gabatarwa domin taimakawa mai karatu ya gane Ahasuros.
Lardi wani babban sashe da ake rarrabawa zuwa ƙasashe domin sauƙin mulki.
A nan "kursiyin sarauta" na nufin mulkinsa bisa masarautar. AT: "ya yi mulkin daular"
Wannan na nufin babban birni, mai ƙarfi da tsaro.
Wannan birnin sarautar sarakunan Fasiya ne.
"Bayan ya yi mulki shekaru biyu"
Da alamar wannan na nufin shugabannin sojoji. AT: "Hafsoshin sojoji"
Waɗannan kalmomi su na da kamannin ma'ana kuma su na jaddada girman sarautarsa. AT: "babbar darajar arziƙin mulkinsa"
Waɗannan kalmomi su na da kamannin ma'ana kuma su na jaddada girmansa. AT: "darajar ƙasaitarsa"
"kwanaki ɗari da tamanin"
"A ƙarshen bikin"
Wannan biki ne na biyu domin shugabannin Susa kawai. AT: "wani bikin da aka yi kwana bakwai"
"Shirayin" na ɗauke da duwatsun ado masu kaloli da aka jera da salo gwanin kyau.
Wannan wani irin dutse ne mai kalolin jã da shunayya dake haɗe da ƙananan ƙarau.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "bãƙin sun sha ruwan inabi daga moɗayen zinariya"
"sarkin ya bayar da ruwan inabin sarakai a yalwace babu rowa"
"babbar niyyar bayarwa"
"Kada a tilasa wa kowa ya sha"
Wannan zance na ma'anar cewa sarki ya ba ma'aikatansa umarni su ba dukkan bãƙi ruwan inabi iyakar yadda su ke so.
"Bayan kwana 6"
A nan "zuciya" na nufin sarki, da "jin daɗi" kari ne da ke nufin buguwa. AT: "sarkin ya bugu da ruwan inabi"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan gabatarwar zance ne da ke bayanin mazajen nan su wanene.
"kyakkyawa ce sosai"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "sa'ad da fadawan sarki suka je suka faɗa mata umarninsa"
"bisa ga umarnin"
An yi zancen zafin fushin sarki kamar a ce wuta ce da ke ƙuna a ransa. AT: "fushinsa ya yi zafi kamar wuta a cikinsa"
"waɗanda suka fahimci abubuwan da ke faruwa a rayuwarsu"
Wannan gabatarwar zance ne da ke bayanin dalilin da yasa sarki ya kira waɗannan mazaje.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Zai zama da taimako idan aka shaida wanda ya yi wannan tambaya. AT: "Sarkin yace masu, "Bisa ga shari'a ... ta hannun shugabanni?"
"Bisa ga kiyaye shari'a" ko "Bisa ga biyayya da shari'a"
Wannan sunan mutum ne.
Waɗannan ƙarin zance ne domin a jaddada yamutsin da rashin biyayyar sarauniya ya haifar.
"Za su ji haushin mazajensu su kuma rena su"
Meremot ya ci gaba da amsawa sarki.
Meremot ya yi magana da sarki a matsayin mutum na uku cikin nuna ladabi. AT: Idan ya gamshe ka mai martaba ... daga gare ka ... a gabanka ... gamshi ... dokarka ... faɗin masarautarka"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "wadda ba wanda zai iya canzawa"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Idan suka ji dokar sarki" ko "Idan suka ji abin da ka umarta"
sarari sosai
Wannan bayani ne da ke nufin kowa har kowanne ƙarshen matsayi da tsakiya. Mai yiwuwa wannan na maganar mazajen, amma zai iya zama da nufin matayen.
Lardi wani babban sashe ne da ake rarrabawa zuwa ƙasashe domin mulki. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:1.
"dukkan mazaje su ɗauki cikakken shugabanci bisa matayensu da 'ya'yansu"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "suka rubuta wannan doka"
1Bayan waɗannan abubuwa, sa'ad da fushin Sarki Ahasuros ya huce, sai ya tuna da Bashti da abin da tayi. Ya kuma tuna da dokar da ya zartar akanta.2Sai samari waɗanda ke wa sarki hidima suka ce, "Bari a madadin sarki a binciko kyawawan budurwai masu tãshe."3Bari sarki yasa shugabanni a dukkan lardunan mulkinsa, su tara dukkan kyawawan budurwai ma su tãshe a gidan mata a cikin masarauta a Susa. A sasu a ƙarƙashin shugabancin Hegai, hakimin sarki, wanda shi ne mai lura da mata, ya kuma basu kayan kwalliyarsu.4Bari yarinyar data gamshi sarki ta zama sarauniya a madadin Bashti." Wannan shawarar ta gamshi sarki, sai yayi haka.5Akwai wani Bayahude a fadar Susa mai suna Modakai ɗan Yair ɗan Shimeya ɗan Kish ɗan Benyamin.6An ɗauko shi ne daga Yerusalem tare da 'yan bautar talala waɗanda aka kwasosu tare da Yehoiachin, sarkin Yahuda, su ne Nebukadnezza sarkin Babila ya kwashe.7Yayi ta lura da Hadassa, wato Esta ɗiyar kawunsa, domin bata da uba ko uwa. Yarinyar tana da kyan fasali tana kuma da kyan fuska. Modakai ya ɗauketa a matsayin 'yarsa.8Sa'ad da aka yi shelar umarni da dokar sarki, aka kawo 'yan mata da yawa a masarautar Susa. Sai aka sasu a hannun Hegai ya kula dasu. Esta ma aka kaita fadar sarki aka sata a ƙarƙashin Hegai mai lura da mata.9'Yar yarinyar ta gamshe shi, ta kuma sami tagomashi a wurinsa. Sai nan da nan ya tanada mata kayan kwalliyarta da kuma abincinta. Ya tanada mata kuyangi bakwai daga fadar sarki, ya kuma kaita da ita da kuyanginta wuri mafi kyau a gidan mata.10Esta bata gayawa kowa su wane ne mutanenta da danginta ba, gama Modakai ya umarce ta kada ta faɗa.11Kowacce rana Modakai yana kai da kawowa a shirayin gidan da aka sa mata, domin ya san lafiyar Esta, da kuma ko me za ayi da ita.12Da lokaci yayi da kowacce yarinya zata shiga wurin Sarki Ahasuros - bisa ga ƙa'idar da ke na mata, kowacce yarinya sai ta cika watanni goma sha biyu na kwalliyar mata, wata shida tana shafe jikinta da man mur, wata shida tana shafa turare da mai -13sa'ad da yarinya mace ta shiga wurin sarki, duk abin da ranta yaso sai a bata daga cikin gidan matayen domin ta kai fãda.14Da yamma zata shiga ciki, da safe zata koma gidan matayen na biyu, a hannun Sha'ashigaz, shugaba na sarki wanda shi ke lura da ƙwaraƙwarai. Ba zata ƙara komawa wurin sarki ba sai in ko yaji daɗinta a ransa kamin ya sake kiranta.15Sa'ad da lokacin Esta ('yar Abihel kawun Modakai wanda ya ɗauke ta a matsayin 'yarsa) yazo da zata shiga wurin sarki, bata roƙi komai ba sai abin Hegai bafaden sarki, wanda shi ke kula da matayen, ya bata. A yanzu Esta ta sami farin jini wurin dukkan waɗanda suka dube ta.16Aka kai Esta wurin Sarki Ahasuros a masarautar fãda a wata na goma, wanda shi ne watan Tebet a shekararsa ta bakwai da mulki.17Sarki ya ƙaunaci Esta fiye da dukkan sauran matayen ta kuma sami karɓuwa da tagomashi daga gare shi, fiye da dukkan sauran budurwan. Sai ya ɗibiya mata kambin sarauta a kanta ya maisheta sarauniya a madadin Bashti.18Sai sarki ya yi ƙasaitaccen biki domin dukkan hakimansa da kuma barorinsa, wato, "Bikin Esta'," kuma ya tsaida biyan haraji a duk lardunansa. Ya kuma bada kyautai bisa ga falalar yalwar mulkinsa.19Ananan sa'ad da aka tara budurwai karo na biyu, Modakai ya zauna a ƙofar sarki.20Esta ba ta rigaya ta faɗa wa kowa game da 'yan uwanta ko mutanenta ba, domin Modakai ya umarceta. Ta ci gaba da bin shawarar Modakai, kamar yadda tayi lokacin daya reneta.21A kwanakin da Modakai ke zama a ƙofar sarki, hakiman sarki guda biyu, Bigtan da Teres, masu tsaron ƙofa, suka fusata suka nema su cuci Sarki Ahasuros.22Da aka bayyana wa Modakai al'amarin sai ya gaya wa Sarauniya Esta, Esta ta faɗa wa sarki a sunan Modakai.23Aka bincika rahoton aka tabbatar haka yake, sai aka rataye dukkansu biyun a bisa gungume. Aka rubuta wannan al'amari a Littafin Tarihi a gaban sarki.
Wannan ya gabatar da wani sabon al'amari da ya faru ba da daɗewa ba.
"fushin sarki ya ragu"
Wannan na nufin doka a cikin Esta 1:19-20.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "A gaya wa barorinka su binciko"
Mutanen sun yi magana da sarki a matsayin mutum na uku cikin nuna ladabi. AT: "A madadin ka"
'Yan barorin suka ci gaba da magana da sarki.
Barorin sun yi magana da sarki a matsayin mutum na uku cikin nuna ladabi. AT: "Bari ka yi ... shugabannika ... gamshe ka"
Duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:1.
inda matayen mutum mai mataye da yawa su ke zama
Wannan na nufin babban birni, mai ƙarfi da tsaro. Duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:2.
Duba yadda aka fassara sunan wannan wuri a cikin Esta 1:2.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Bari Hegai, hakimin sarki, wanda shi ne mai lura da mata, ya lura da su"
Wannan sunan mutum ne.
"Kayan kwalliya" sinadarai ne kamar su man shafawa, sabulai, ko hoda da mata ke amfani da su su na shafawa a fuska da jikinsu domin su fita da kyau.
Wannan ya gabatar da Modakai sabon mutum cikin labarin.
"Yair," " Shimeya," da "Kish" mazaje ne zuriyar da "Modakai" ya fito.
"daga zuriyar Benyamin"
Wannan tushen zance ya bayyana yadda Modakai ya zo Susa. Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Nebukadnezza sarkin Babila ya ɗauko shi da sauran 'yan zuwa bauta tare da Yehoiachin, sarkin Yahuda"
Juyin Ibraniyanci bai bar wani bayani ba sosai game da wanda ake magarsa a nan. Watakila Kish ne, wanda ya zamanto kakan-kakan Modakai. Idan game da modakai ne da kansa, to zai kasance tsoho ne sosai a lokacin al'amura game da Esta. Juyin zamani da yawa sun bar wurin ba bu bayani sosai. Kaɗan daga cikin Juyin, wanda suka haɗa da UDB, sun zaɓi su yi zaton cewa Modakai ne wanda aka ɗauko aga Yerusalem.
Wannan sunan mutum ne.
Wannan sunan Esta ne na Ibraniyanci.
"ɗan'uwansa"
"mahaifinta da mahaifiyarta sun mutu"
"ya lura da ita kamar 'yarsa"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Bayan da sarki yayi shelar cewa su je su nemo kyawawan mataye"
"sanarwa"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "suka kawo 'yammata da yawa"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Hegai ya fara kulawa da su"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Hegai mai lura da mata ya fara kulawa da Esta da aka kawota cikin fadar sarki"
Waɗannan jimloli biyu na ma'anar abu ɗaya kuma yana jaddada iya yadda ta gamshe shi. AT: "'Yar yarinyar ta gamshe shi ƙwarai"
A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:5.
"Esta"
"halin da Esta ke ciki" ko "game da lafiyar Esta"
Bayanai ne na al'adun mata waɗanda suka zama matan sarki.
"yin abu dai-dai da abinda ake bukata na mata"
abinda aka yi domin a sa 'yan mata su yi kyau sosai su kuma yin ƙamshi mai daɗi.
za a iya bayyyana wannan a bayyanau. AT: "za ta iya samun duk abin da take bukata ko so"
yi amfani da kalma ko jimla da aka yi amfani a Littafin Esta 2:3.
ya na nuna cewa safiya da ta biyo baya. Za mu iya zayyace shi, AT: "washe gari"
"wani gida daban"
"a wurin da Sha'ashigaz, ... ƙwaraƙwarai za su lura da ita"
"bincike" ko "kariya"
Wannan sunan na miji ne.
Wannan ya gabatar sa sabon fannin labarin.
Tushen rahoton zai tunawa mai karatu da Modakai ɗan'uwan Esta.
Mahaifin Esta kuma kawun Modakai
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "ta roƙi kawai abin da"
Wannan kari ne. AT: "gamshi dukkan"
"Tebet" sunan watan goma ne na kalandar Ibraniyanci. Lokacin ƙarshen watan Desemba ne da farkon watan Janwari na kalandar Turawa.
"shekara ta 7"
Wannan amfani da kalmar "ƙauna" ta soyayya ce.
Waɗannan kari suna ma'anar abu ɗaya ne su na kuma jaddada iya yadda Esta ta gamshi sarki. AT: "ta gamshe shi ƙwarai"
sarkin yayi haka ne domin ya nuna cewa yana mai da ita sarauniya.
Zai taimaka idan aka faɗi cewa sunan wannan biki ke nan. AT: "ya kira shi, 'Bikin Esta'"
"ka karɓi haraji ƙasa da yadda yake karɓa a dukkan lardunan"
"falalar yalwar da sarki kawai ke iya bada wa"
Babu cikakken bayanin lokacin da aka yi wannan taro karo na biyu, kuma donme. Saboda haka wasu juyin sun taɓa wannan wurin. Zaifi kyau idan aka fassara shi yadda yake a rubuce.
"wani lokaci kuma" ko "ƙarin lokaci"
Watakila ma'anonin su ne 1) Modakai ya zauna wurin domin ya riƙa jin labarin al'amura game da Esta daga bakin mutanen da ke wucewa ta ƙofar ko 2) "zauna a ƙofar sarki" kari ne da ke ma'anar sarki ya bada matsayin shugabanci ga Modakai.
"ƙofar zuwa fãdar sarki"
Modakai ya gaya mata cewa kada ta gaya wa kowa game da iyalinta.
Wannan na gabatar da sabon al'amari a cikin labarin.
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Sa'ad da Modakai ya gane abin da su ke shiryawa"
Wannan kari ne. AT: "a madadin Modakai"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Sarkin ya bincika rahoton ya tabbatar haka yake, sai yasa barorinsa suka rataye dukkansu biyun "
Wannan wani sassaƙaƙƙen katako ne da aka kafa ana amfani da shi wurin kashe mutane ta wurin ɗaura igiya zagaye a bisan gungumen ƙarshen igiyar kuma a ɗaure wuyansu sai a rataye su a jikin. AT: "katakon rataye mutane"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Suka rubuta wannan al'amari"
1Bayan waɗannan abubuwa, Sarki Ahasuros ya ɗaukaka Haman ɗan Hamedata Ba'agage, ya fifita matsayin ikonsa bisa kan dukkan shugabanni da ke tare da shi.2Dukkan barorin sarki da ke ƙofar sarki kulluyomi sukan durƙusa su rusuna wa Haman, gama sarki ya umarta suyi haka. Amma Modakai bai durƙusa masa ba ko kuma ya rusuna masa ba.3Sai barorin sarki da ke a kofar sarki suka cewa Modakai, "Me yasa kake rashin biyayya da dokar sarki?"4Suka yita masa magana kowacce rana, amma yaƙi ya cika burinsu. Saboda haka suka gaya wa Haman domin suga ko za a bar al'amarin game da Modakai ya zama haka, gama ya gaya musu shi Bayahude ne.5Da Haman yaga Modakai baya durƙusa ko ya rusuna masa ba, sai Haman ya cika da hasala.6Sai ya ƙudurta ba Modakai kaɗai zai kashe ba, gama barorin sarki sun gaya masa irin mutanen Modakai. Haman yana so ya hallakar da dukkan Yahudawa, mutanen Modakai, waɗanda suke cikin dukkan masarautar Ahasuros.7A cikin wata na fari (wanda shi ne watan Nisan), a shekara ta goma sha biyu ta mulkin Sarki Ahasuros, aka jefa Fur - wato ƙuri'a - a gaban Haman, domin a zaɓi rana da wata. Suka yita jefa ƙuri'a akai akai har sai data faɗa akan watan goma sha biyu (wato watan Ada).8Sa'an nan Haman ya cewa Sarki Ahasuros, "Akwai waɗansu mutane a warwatse an kuma baza su a dukkan lardunan masarautarka. Shari'arsu daban take data sauran mutane, basa kuma kiyaye dokokin sarki, sabili da haka bai kyautu ba sarki ya bar su da rai.9Idan sarki ya amince, ya bada umarni a kashe su, ni kuma zan bada talanti dubu goma na azurfa a hannun waɗanda ke tafiyar da cinikaiyar sarki, domin susa a cikin baitulmalin sarki."10Sai sarki ya tuɓe zobensa daga yatsansa ya ba Haman ɗan Hamedata Ba'agagite, maƙiyin Yahudawa.11Sarki ya cewa Haman, "Zan tabbatar an mayar maka da kuɗin da kuma mutanenka. Za ka yi abin daka gadama da su."12Sai aka kira magatakardun sarki a rana ta goma sha uku ga watan fari, aka rubuta doka game da dukkan umarnin da Haman ya bayar zuwa ga masu mulkin lardunan sarki, waɗanda suke bisa dukkan larduna, zuwa ga gwamnonin dukkan al'umma, da shugabannin dukkan mutane, ga kowanne lardi bisa ga irin rubutunsa, da kowacce al'umma kuma bisa ga harshenta. Da sunan Sarki Ahasuros aka rubuta, aka kuma hatimce shi da zobensa.13Aka aika da takardun hannu da hannu ta wurin manzanin zuwa ga dukkan lardunan sarki, domin a shafe su, a kashe, a kuma hallaka dukkan Yahudawa, samari da tsofaffi, yara da mata, rana ɗaya - a rana ta goma sha uku a watan goma sha biyu (wato watan Ada) - a kuma washe mallaƙarsu.14Sai aka sanar kowanne lardi takardar data zama shari'a. Aka sanar da dukkan mutane a kowanne lardi cewa su shirya domin wannan rana.15Manzanin suka tafi da hanzari domin su baza umarin sarki. Aka baza umarnin kuma a fadar Susa. Da sarki da Haman suka zauna domin su sha, amma birnin Susa ya ruɗe.
Wannan na gabatar da sabon al'amari a cikin labarin.
Wannan suna ne da kwatancen Haman ɗaya daga cikin shugabannin sarki.
A nan "matsayin ikonsa" na a madadin matsayi ko muƙaminsa a gwamnati. AT: "aka ɗora shi sama da sauran shugabanni" ko "aka ba shi iko fiye da dukkan sauran shugabanni"
Waɗannan ayyuka na nuna ladabi ga ikon Haman.
"suka ƙasƙantar da kansu suka kuma kwanta rib da ciki a ƙasa a gaban Haman"
"suga me Haman zai yi game da ayyukan Modakai"
Modakai ya nuna rashin bangirma ga matsayin Haman a gwamnati ta wurin ƙin yin waɗannan ayyuka.
A nan an yi zancen hasalar Haman kamar wani abin da zai iya cika shi fal. AT: "Haman ya fusata ƙwarai"
"Ya ƙi shawarar kashe Modakai kaɗai." Za a kuma iya faɗin wannan a matsayin daidaituwa. AT: "Ya ƙudurta ya kashe fiye da Haman"
"a kawas da dukkan Yahudawa" ko "a kashe dukkan Yahudawa"
"A wata na ɗaya"
"Nisan" sunan watan farko ne na kalandar Ibraniyanci. Wanda ya ke lokacin ƙarshen watan Mach da farkon watan Afril na kalandar Turawa.
"A shekara ta 12 ta Sarki Ahasuros" ko "sa'ad da Sarki Ahasuros yayi mulki wajen shekaru sha biyu"
"suka kãɗa Fur _ wato ƙuri'a _"
"watan sha biyu"
"Ada" sunan watan sha biyu ne na kalandar Ibraniyanci. Wanda ya ke lokacin ƙarshen watan Febwari da farkon watan Mach na kalandar Turawa.
"wata ƙungiyar mutane". Wannan na nufin Yahudawa a matsayin yare ɗaya.
"waɗanda ke zama wurare daban-daban"
A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:1.
Haman ya yi magana da sarki a matsayin mutum na uku cikin nuna ladabi. AT: "na ka ... kai"
"kada sarki ya bar su su da rai." Za a iya faɗin wannan a matsayin tattarawa. AT: "sarki ya cire su"
A nan "hannu" na a matsayin mutane. A "bada" kari ne da ke ma'anar a biya su. AT: "Zan biya ... ga mutanen"
"ton 330 na azurfa"
zobe na musamman da ake amfani da shi ana buga tambarin sarki a bisa shela
Ba a yi bayanin ma'anar wannan jimla ba. Watakila ma'anonin su ne 1) "Zan maida maka kuɗin" ko 2) "Ka ɗauki kuɗin ka kuma ba mutanen kamar yadda ka faɗa."
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "sarki ya kira magatakardunsa ... suka rubuta doka game da dukkan umarnin da Haman ya bayar"
Wannan watan farko ne na kalandar Ibraniyanci. Rana ta sha uku na kusa da farawar watan Afril na kalandar Turawa.
"gwamnonin larduna." A fassara "lardi" kamar a cikin Esta 1:1.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "suka rubuta dokar a sunan Sarki Ahasuros, Haman kuma ya hatimce shi da zoben sarki"
A nan "suna" na wakiltar ikon sarki. AT: "a cikin ikon"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Manzanin suka bada takardun hannu da hannu" ko "Manzanin suka bada takardun kai tsaye"
Waɗannan kalmomi na ma'anar abu ɗaya kuma su na jaddada hallakarwa ɗungun. AT: "a hallaka ɗungun"
"a rana ta goma sha uku a watan goma sha biyu"
"Ada" sunan watan sha biyu ne kuma watan ƙarshe na kalandar Ibraniyanci. Kwana na sha uku yana kusa da farawar watan Mach a kalandar Turawa.
a sace ta ƙarfi da yaji
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Shugabannin a kowanne lardi suka sa takardar ta zama shari'a."
A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:1.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "suka gaya wa dukkan mutane a kowanne lardi."
"a ranan nan"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "suka kuma rarraba dokar."
Wannan na nufin babban birni, mai ƙarfi da tsaro. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:2.
A duba yadda aka fassara wannan birnin a cikin Esta 1:2.
"yana cikin babban ruɗewa"
1Da Modakai ya ji dukkan abin da aka riga aka yi, sai ya kyekketa tufafinsa yasa rigar makoki da toka. Ya fita waje ya je tsakiyar birni, ya yita rusa kuka da bacin rai mai tsanani.2Iyakarsa bakin ƙofar sarki kaɗai, domin ba a yardar wa kowa ya wuce wurin sanye da tsummoki ba.3A kowanne lardi, duk inda umarnin da dokar sarki ya kai, Yahudawa suka yi ta makoki ƙwarai, tare da azumi, kuka da makoki. Da yawa kuma suka zauna cikin tsummoki da toka.4Da kuyangun Esta da barorinta suka zo suka faɗa mata, sarauniya ta damu ƙwarai. Ta aika wa Modakai tufafin sawa (domin ya tuɓe tsummokaransa), amma ya ƙi karɓarsu.5Sai Esta ta kira Hatak, ɗaya daga cikin wakilan sarki wanda aka sasu yi mata hidima. Ta umarce shi ya je wajen Modakai ya binciko abin daya faru da kuma ma'anar al'amarin.6Sai Hatak ya tafi wurin Modakai a dandalin birnin da ke gaban ƙofar sarki.7Modakai ya gaya masa dukkan abin daya faru da shi, da kuma jimillar azurfar da Haman ya alƙawarta zai auna ya sa a baitulmalin sarki domin a kashe Yahudawa.8Ya kuma ba shi takardar umarnin bugu na biyu a Susa domin hallaka Yahudawa. Yayi haka ne domin Hatak ya nuna wa Esta, ya kuma ba ta nawaiyar tafiya wurin sarki don ta roƙi tagomashi ta kuma nemi alfarma daga gare shi game da mutanenta.9Sai Hatak ya tafi ya faɗa wa Esta abin da Modakai yace.10Sai Esta ta yi magana da Hatak cewa ya koma wurin Modakai.11Ta ce, "Dukkan barorin sarki da mutanen lardunan sarki sun sani cewa duk wani namiji ko mace wanda ya shiga cikin farfajiyar sarki ba tare da an kira shi ba, doka ɗaya ce tak: wato dole a kashe shi - sai ko wanda sarki ya miƙa wa sandar zinariya kaɗai domin ya rayu. Ba a kira ni in je wurin sarki ba kwanakin nan talatin."12Sai Hatak ya tafi ya faɗa wa Modakai abin da Esta ta ce.13Modakai ya mayar da wannan saƙo: "Kada ki yi tsammanin saboda kina gidan sarki zaki kuɓuta fiye da sauran Yahudawa.14Idan kika yi shiru a wannan lokaci, to gudunmawa da tsira zasu zo wa Yahudawa daga wani wuri, amma ke da gidan mahaifinki zaku hallaka. Wa ya sani ko kin sami wannan matsayin mulkin saboda makamancin lokaci irin wannan?"15Sa'an nan Esta ta aika wa Modakai wannan saƙo,16"Kaje ka tattara dukkan Yahudawan da ke zaune a Susa, kuyi azumi domina. Kada ku ci ko ku sha har kwana uku, rana ko dare. Ni da 'yan matana ma zamu yi haka. Sa'an nan zan je wajen sarki, koda yake yin hakan ya saɓa wa shari'a, idan na hallaka, na hallaka."17Modakai ya tafi yayi duk abin da Esta ta faɗa masa yayi.
"ya ji game da waɗannan wasiƙu"
Waɗannan ayyuka nuna alamar tsananin damuwa ne. AT: "ya kyekketa tufafinsa yasa rigar makoki da toka domin ya nuna baƙincikinsa"
A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:1.
"Yahudawa suka yi babban makoki"
"Da yawa kuma suka zauna ƙasa, cikin tsummoki zaune cikin toka"
"barori mata da barori maza"
"domin Modakai ya sanya"
Wannan sunan namiji ne.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "ɗaya daga cikin wakilan da sarki ya sa su yi mata hidima."
"tashar birni"
A duba yadda aka fassara sunan wannan mutum a cikin Esta 3:1.
"Modakai kuma ya ba Hatak"
"ta roƙi tagomashin sarki"
Wannan karin yanayi za a iya bayaninsa cikin jimla. Zai kuma zama da taimako idan aka raba shi cikin jimloli biyu. AT: "babu wani namiji ko mace da za a bari ya shiga cikin farfajiyar sarki sai idan sarki ya gayyace su. Wanda ya karya wannan doka za a kashe shi sai wanda sarki ya miƙa wa sandar zinariya"
"kwana 30"
A nan anyi zancen "gudunmawa" da "tsira" kamar masu rai ne da ke iya tasowa. AT: "wani daban zai taso daga wani wuri ya kuma tsirar da Yahudawa"
Dalilin wannan tambaya shi ne domin Esta ta yi tunani mai zurfi game da fanninta cikin wannan al'amari. AT: "Wa ya sani, ko saboda saboda makamancin lokaci irin wannan ki ka zama sarauniya."
A duba yadda aka fassara wannan birnin a cikin Esta 1:2.
Azumi alamar aiki ne da Yahudawa ke yi sa'ad da su ke yin addu'a mai tsanani. Za a iya nuna wannan a bayyane. AT: "ku yi azumi da addu'a domina ... za mu yi azumi da addu'a"
"kwana 3"
1Bayan kwana uku, sai Esta ta saka rigunan sarauta ta tafi ta tsaya a shirayin ciki na fadar sarki, a gaban gidan sarki. Sarki yana zaune a kan kursiyinsa a masarautar gidansa, yana fuskantar kofar shiga gidan.2Lokacin da sarki ya ga sarauniya Esta tana tsaye a shirayi, sai ta sami amincewa a idanunsa. Sai ya miƙa mata sandar zinariya da ke hannunsa. Sa'an nan Esta ta matso ta taɓa kan sandar.3Sa'an nan sarki yace mata, "Mene ne kike so Sarauniya Esta? Mene ne roƙon ki? Har ma rabin masarautata, za a ba ki."4Esta tace, "Idan sarki ya yarda, bari sarki da Haman su zo yau wurin liyafar dana shirya domin sa."5Sa'an nan sarki yace, "Ku kawo Haman nan da nan, yayi abin da Esta ta ce." Sai sarki da Haman suka tafi liyafar da Sarauniya Esta ta shirya.6Lokacin da ana raba ruwan inabi a liyafar, sai sarki ya cewa Esta, "Me kike so? Za a baki. Mene ne kike roƙo? Har ma rabin masarautar, za a baki ita."7Esta ta amsa, "Abin da nike so da kuma roƙona shi ne,8idan na sami tagomashi a idanun sarki kuma idan ya gamshi sarki ya amsa roƙona kuma ya girmama roƙona, bari sarki da Haman su zo liyafar da zan shirya maka gobe, sa'an nan zan amsa tambayar sarki."9A wannan rana Haman ya tafi gida da murna da farinciki, a zuciyarsa. Amma da Haman ya ga Modakai a bakin ƙofar sarki, kuma Modakai bai tashi tsaye ba balle yayi rawar jiki a gabansa da ko wani tsoro, sai ya cika da hasala găba da Modakai.10Duk da haka Haman ya kame kansa ya tafi gidansa. Ya aika aka kira abokansa, ya kuma tattarosu da matarsa Zeresh.11Haman ya rattaba masu darajar wadatarsa, yawan "ya'yansa maza, da dukkan yawan matsayi da sarki ya girmama shi da su, da yadda yake da fifikon daya zarce na dukkan shugabanni da barorin sarki.12Haman yace, "Sarauniya Esta bata gayyaci kowa ba sai ni zan je da sarki liyafar data shirya. Har ma gobe ta sake gayyata ta in zo tare da sarki.13Amma ban ɗauki duk wannan a bakin komai ba a gareni muddin in na ganin Modakai zaune a bakin ƙofar sarki."14Sai Zeresh matarsa ta cewa Haman da dukkan abokansa. Bari a kafa wani gungume mai tsawon ƙafa hamsin. Da safe sai ka yi magana da sarki domin su rataye Modakai a kai. Sa'an nan ka tafi da murna tare da sarki wurin liyafar." Wannan ya gamshi Haman sai yasa aka kafa gungumen.
"a cikin ɗakin daga ƙofar shiga gidan" ko "kallo zuwa ƙofar shiga gidan"
Kalmar "idanu" na nufin a gabansa kuma misali ne da ke nuna darajar da ya bata. Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "ya gamsu da ita" ko "ya amince da ita"
Ya yi haka ne domin ya nuna cewa ya gamsu da ita.
Watakila ta yi haka ne domin ta nuna cewa tana bada girma ga mulkinsa kuma tana godiya domin kirkin da ya nuna mata.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Idan ki ka roƙi har ma rabin masarautata, zan baki"
Domin nuna bangirma ga sarki wasu lokutta mutane na kiran sa "ka." Za a iya fassara wannan tare da kalmar "ka" jere kuma da kalmomin da ke nuna bangirma. AT: "Ya sarki, idan ya gamshe ka, ka zo ka kuma kawo Haman ... domin ka" ko "Idan ka yarda ka yi haka, ranka ya daɗe, ka zo, bari kuma Haman ya zo da kai ... domin ka"
A duba yadda aka fassara sunan wannan mutum a cikin Esta 3:1.
Kalmar suns "so" za a iya bayyana ta tare da aikatau "roƙo" ko "buƙata"? AT: "Me kike roƙo" ko "Me kike buƙata"
Za a iya bayyana wannan a matsayin aikatau. AT: "Zan baki abin da kika roƙa" ko "Zan yi maki abin da kika roƙa"
kalmar suna "roƙo" za a iya bayyana ta tare da aikatau "so" ko "buƙata"? AT: " Me kike so" ko "Me kike buƙata"
Za a iya bayyana wannan a matsayin aikatau. AT: "Idan kika roƙi har ma rabin masarautar, zan baki ita"
Kalmomin "roƙo" da "buƙata" su na da ma'ana ɗaya. Watakila ta yi amfani da waɗannan kalmomin tare ne a matsayin wata hanyar magana da ke nuna ladabi da bangirma ga sarki.
Domin nuna bangirma ga sarki, wasu lokutta mutane basu kiransa da "ka." Za a iya fassara wannan tare da "ka" tare da wasu kalmomin da ke nuna bangirma. AT: "Idan ka gamsu da ni, Ya sarki, idan ya gamshe ka"
A nan "sami tagomashi" kari ne da ke nufin yadda da ita ko gamsuwa ta ita. "A idanun sarki" misali ne da ke wakiltar darajar ta a gare shi. AT: "Idan sarki ya daraja ni kuma ya yadda da ni" ko "idan sarki ya gamsu da ni"
Za a iya fassara wannan da kalmar "ka" tare da kalmomin da ke nuna bangirma. AT: "idan ka yadda ka zo kuma ka kawo Haman" ko "idan ka yadda ka zo bari kuma Haman ya zo tare da kai"
Za a iya fassara wannan da kalmar "ka" tare da kalmomin da ke nuna bangirma. AT: "Zan amsa tambayarka"
Tashi tsaye alamar nuna bangirma ne. Modakai bai ba Haman bangirma na musamman ba.
"Cika da hasala" na mamadin jin haushi sosai. AT: "ya fusata ƙwarai"
Za a iya fassara wannan da jimlar "Koda yake ya husata sosai"
Kame kansa na nufin ya ƙi yin wani abu da ya ke matuƙar so ya yi. Haman ya so ya nuna wa Modakai cewa ya husata sosai. AT: "Haman ya ƙi ya nuna zafin fushinsa"
Wannan sunan mace ne.
"daraja da "wadata" dukka misalan suna ne. AT: "Haman ya rattaba masu irin girman wadatarsa" ko "Haman ya rattaba masu manyan abubuwan da ya ke dasu"
Misalin suna "matsayi" za a iya bayyanawa tare da aikatau "tsaidawa." Ya na nufin sarkin ya ba shi ƙarin muhimmin aiki. AT: "Yadda sau da yawa sarkin ya ba shi matsayi kuma ya girmama shi" ko "yadda sarkin ya girmama shi sau da yawa ta wurin ba shi muhimmin aiki"
Fifikon daya zarce na mutane na a madadin mai muhimmanci fiye da su. AT: "yadda ya zama mai muhimmanci fiye da dukkan shugabanni da barorin sarki"
Za a iya fassara wannan a matsayin tattarawa. AT: "ni kaɗai"
"ba ya sa ni murna" ko "bai ƙosar da ni ba"
Wannan wani sassaƙaƙƙen katakon rataye wani ne ta wurin ɗaura igiya zagaye a bisan gungumen ƙarshen igiyar kuma a ɗaure wuyansa sai a rataye shi a jikin. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 2:23.
"Tsawon ƙafa 50" za a iya juya wannan zuwa magwajin zamani. AT: "tsawon mita ashirin da uku"
"ya gaya wa mutane su sassaƙa gungumen"
"Haman ya so wannan shawara"
1A daren nan sarki ya kasa barci. Sai ya umarci barori su kawo tarihin ayyukan mulkinsa, aka kuma riƙa karanta wa sarki da murya.2Sai aka tarar a rubuce a wurin cewa Modakai ya faɗi game da Bigtana da Teresh, fadawan sarki biyu da ke tsaron ƙofa, da suka yi ƙoƙarin su cuci Sarki Ahasuros.3Sarki ya tambaya, "Me aka yi don a bashi girma ko a maida Modakai sananne saboda yayi wannan abu?" Sai samari matasa na sarki da ke masa hidima suka ce, "Ba a yi masa komai ba."4Sarki yace, "Wa ke a shirayi?" Yanzu fa Haman ya rigaya ya shigo shirayin gidan sarki na waje domin yayi masa magana game da rataye Modakai a kan gungumen daya kafa masa.5"Barorin sarki suka ce masa, Haman yana tsaye a shirayi." Sarki yace bari ya shigo ciki."6Da Haman ya shigo, sarki yace masa, "Me za a yiwa mutumin da sarki yake jin daɗin ya girmama shi?" Sai Haman yace a zuciyarsa, "Wane ne kuwa sarki zai ji daɗin girmama shi fiye da ni?"7Haman ya cewa sarki, "Saboda mutumin da sarki ke jin daɗin girmama shi,8bari a kawo rigunan sarauta, waɗanda sarki ya taɓa sawa, da dokin da sarki ya taɓa hawa, kuma a sa masa kambin sarauta.9Sa'an nan da rigunan da dokin a ba da su ga ɗaya daga cikin manyan shugabanni. Bari su sa wa mutumin da sarki ke so ya girmama rigunan, bari kuma su bishe shi a kan dokin, a titunan birni. Bari kuma su yi shela a gabansa, "Wannan shi ne abin da ake yi wa wanda sarki ke jin daɗin girmama shi!'"10Sai sarki ya cewa Haman, "Yi hanzari ka ɗauki rigunan da dokin, kamar yadda ka faɗi kayi wa Modakai Bayahude wanda ya kan zauna a ƙofar sarki. Kada ka kasa yin ko abu ɗaya daga abin da ka faɗa."11Sai Haman ya ɗauki rigunan da dokin. Ya sanya wa Modakai rigunan ya bishe shi bisa dokin a dukkan titunan birnin. Yayi ta shela a gabansa, '"Haka ake yi wa mutumin da sarki yake jin daɗin girmama shi."12Modakai ya dawo ƙofar sarki. Amma Haman ya gaggauta zuwa gidansa, yana makoki, da kansa a lulluɓe.13Haman ya gaya wa matarsa Zeresh da dukkan abokanansa duk abubuwan da suka faru da shi. Sai mutanensa sanannu domin hikimarsu, da Zeresh matarsa suka ce masa, "Idan dai Modakai, wanda ka fara faɗuwa a gabansa Bayahude ne, ba zaka ci nasara a kansa ba, amma hakika zaka faɗi a gabansa."14Suna cikin magana da shi haka, sai ga hakiman sarki sun iso. Suka gaggauta suka tafi da Haman wurin liyafar da Esta ta shirya.
Waɗannan sunayen mazaje biyu ne. A duba yadda aka fassara sunayensu a cikin Esta 2:21.
A nan "tarar" kalma ce da ke nufin fahimci. Dukka "tarar" da "lissafta" za a iya bayyanawa a matsayin aikatau. AT: "Suka tarar cewa marubuta sun lissafta a nan" ko "suka fahimci cewa marubutan sun rubuta"
Za a iya bayyanawa a matsayin aikatau. AT: "Me na yi don a bashi girma" ko "Me muka yi don a bashi girma"
Za a iya bayyanawa a matsayin aikatau. Duk da haka zai yi kyau a sami hanyar bayani da ba zai nuna cewa kamar barorin na tuhumar sarki ba. AT: "Babu wanda ya yi wani abu domin Modakai"
A duba yadda aka fassara sunan wannan mutum a cikin [Esta 3:1]
"shirayi na farko daga waje"
Za a iya bayani a fili dalilin ratayewar. AT: "kashe Modakai ta ratayewa"
Wannan wani sassaƙaƙƙen katako ne da aka kafa ana amfani da shi wurin kashe mutane ta wurin rataye su. A duba yadda aka fassara "gungume" a cikin Esta 5:14. AT: "katakon da Haman ya kafa domin rataye Modakai"
"ginawa"
A nan sarki na maganar kansa a matsayin mutum na uku. Za a iya faɗin wannan a matsayin mutum na farko da kuma aikatau. AT: "Me zan yiwa mutumin da na ke jin daɗin in girmama shi"
Jin daɗin yin wani abu kari ne da ke nufin farincikin yin wani abu ko son yin wani abu. AT: "sarki ya ke farincikin girmamawa" ko "sarki ya ke son ya girmama"
Zuciya na mamadin tunani da hali. AT: "tunani" ko "ya cewa kansa"
Za a iya bayanin wannan a matsayin jimla. "Tabbas babu wanda sarki zai ji daɗin girmama shi fiye da ni!"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "bari wani ya kawo rigunan sarauta" ko "yagawa barorinka su kawo rigunan sarauta"
Kalmar "ya" na nufin dokin. Kambin sarauta alama ne na musamman da ke nuna iyalin sarki.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Sa'an nan bari su bada rigunan da dokin" ko "Sa'an nan a gaya masu su bada rigunan da dokin"
A gaya masu su sa wa mutumin ... cikin girmamawa, bari kuma su bishe shi"
"A gaya wa manyan shugabanni da barori su yi shela"
Kalmar "ko abu ɗaya" na jaddada cewa ya tabbatar ya yi dukkan abin da ya faɗi. Za a iya faɗi a matsayin tarawa. AT: "Ka tabbatar cewa ka yi dukkan abin da ka faɗi"
Yawanci mutane kan lulluɓe kansu ne su nuna cewa suna cikin tsananin ɓacin rai ko kunya.
A duba yadda aka fassara sunan wannan mata a cikin Esta 6:13.
Sun yi magana kamar cewa Haman da Modakai suna cikin yaƙi, kuma Haman ya fara rasa yaƙin. A nan "faɗuwa" na nuna rashin daraja da kayarwa. AT: "wanda ya riga ya ƙasƙantar da kai... babu shakka zai kayar da kai"
"ba zaka yi nasara da shi ba." Sun yi magana kamar cewa Haman da Modakai suna cikin yaƙi. A nan nasara akan wani na nufin samun girmamawa fiye da wanin. AT: "ba za ka samu girmamawa fiye da shi ba"
1Sai sarki da Haman suka tafi su yi liyafa da Sarauniya Esta.2A kan rana ta biyu, da ake bada ruwan inabi, sarki ya cewa Esta, "Mene ne roƙonki, Sarauniya Esta? Za a biya maki. Me kike tambaya? Har ma rabin masarautar ma, za a kuma baki."3Sai Sarauniya Esta ta amsa, "Idan na sami tagomashi a idanun ka, idan kuma ka yarda, bari a barni da raina - wannan shi ne roƙona, ina kuma roƙon wannan domin mutanena.4Gama an sayar damu - ni da mutanena, domin a hallaka mu, a kashe, a kuma shafe mu gaba ɗaya. Dama a ce an sayar damu ga bauta, maza da mata bayi, dana yi shuru, gama ba wani ƙunci makamancin haka da zai bada dalilin damun sarki."5Sai Sarki Ahasuros ya cewa Sarauniya Esta, "Wa ye shi? Ina za a sami wannan mutum daya ƙudurta a zuciyarsa yayi makamancin abu haka?"6Esta tace, "Mafaɗacin mutumin, wannan maƙiyi shi ne mugun nan Haman!" Sai Haman ya firgita a gaban sarki da sarauniya.7Sarki ya miƙe tsaye cikin hasala wurin shan ruwan inabin liyafar ya tafi cikin lambun fãda, amma Haman ya jira ya roƙi ransa daga Sarauniya Esta. Ya lura sarki yana niyyar zartar da hallakarwa gãba da shi.8Sarki ya komo daga lambun fãda zuwa cikin ɗakin da aka shayar da su ruwan inabi. Haman ya faɗi a kan kujerar da Esta take. Sai sarki yace, "Zai ci mutuncin sarauniya a gabana a cikin gidana?" Da zarar fitar wannan magana daga bakin sarki, sai barorin suka lulluɓe fuskar Haman.9Sai Harbona, ɗaya daga cikin hakimai da ke wa sarki hidima, ya ce, "Akwai wani gugume mai tsawon kamu hamsin kusa da gidan Haman. Ya kafa shi ne saboda Modakai, wanda yayi magana domin a kare sarki." Sarki yace, "A rataye shi a kai."10Sai suka rataye Haman bisa gungumen da ya shirya saboda Modakai. Sai hasalar sarki ya huce.
A duba yadda aka fassara sunan wannan mutum a cikin Esta 3:1.
"a wannan rana ta biyu ta bikin"
"ya yin da barorin ke zubo ruwan inabin su na ba su"
Misalin suna "roƙo" za a iya bayanin shi tare da aikatau "tambaya" ko "buƙata." AT: "Me ki ke tambaya" ko "Me ki ke buƙata"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Zan baki abin da ki ka tambaya" ko "Zan yi maki abin da ki ke tambaya"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Idan ki ka tambayi har ma rabin masarautata, zan baki ita"
A nan "sami tagomashi" kari ne da ke nufin yadda da ita ko gamsuwa ta ita. "A idanunka" misali ne da ke wakiltar darajar ta a gare shi. AT: "Idan ka daraja ni kuma ka yadda da ni" ko "idan ka gamsu da ni"
Misalin "bayar da rai" na mamadin kuɓutar da wani daga mutuwa. Wannan maganar za a iya bayanin ta a matsayin aikatau. AT: "ka ceci raina"
Misalin suna "roƙo" za a iya bayanin shi tare da aikatau "tambaya" AT: "Wannan itace tambayata"
Misalin "an sayar" na madadin yashewa. Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Gama wani ya yashe mu" ko "Gama wani ya sanya mu cikin haɗarin maƙiyanmu"
A nan dukka kalmomin uku na da ma'ana ɗaya kuma an yi amfani da su ne domin jaddadawa. Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "domin maƙiyanmu su hallaka mu, su kashe, su kuma shafe mu gaba ɗaya"
A ƙudurta a zuciya ayi wani abu kari ne da ke nufin niyyar yin wani abu. Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Ina wanda ya yi niyyar yin makamancin abu haka"
"ya ji tsoro ƙwarai"
Kasancewa cikin hasala kari ne da ke nufin jin haushi ƙwarai. AT: "Sarkin ya ji haushi ƙwarai ya kuma miƙe tsaye"
"ya roƙi Sarauniya Esta da ta ceci ransa"
A nan lura na madadin ganewa ko fahimta. AT: "Ya gane cewa anyi niyyar zartar da hallakarwa"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. Misalin suna "hallakarwa " za a iya bayyana shi da aikatau mai ƙarfi "lalatarwa" ko "kashewa." AT: "sarki yana niyyar zartar da hallakarwa gãba da shi" ko "sarki yana niyyar kashe shi"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "inda barorin suka shayar da su ruwan inabi"
dogon wurin zama inda wani zai iya zaunawa ko ya kwanta
Sarki yayi wannan tambaya ne domin ya nuna mamakinsa da haushin abin da Haman ya ke yi. Za a iya fassara wannan a matsayin jimla. AT: "Har ma yana neman ya kai wa sarauniya hari a gabana a cikin gidana!"
"kai hari ga sarauniya." Wannan wata hanyar sauƙi ce ta faɗin fyaɗe.
Fitowar zance daga baki misali ne da ke nufin yin magana. AT: "da zarar sarki ya ce haka"
Lallai sun yi haka ne saboda sun fahimci sarki yana so a kashe Haman. AT: "barorin sun lulluɓe fuskar Haman ne alamar cewa za a kashe shi"
Wannan sunan namiji ne.
Za ka iya juya "kamu hamsin" zuwa gwajin zamani. A duba yadda aka fassara wannan kalma a cikin Esta 5:14. AT: "Gungume mai tsawon mita ashirin da uku"
An yi maganar hasalar sarki kamar wata babbar wuta ce da ta zama ƙarama. AT: "Daga nan hasalar sarkin ta ragu" ko "Daga nan sarkin bai yi fushi ba sosai"
1A wannan ranar Sarki Ahasuros ya bai wa Sarauniya Esta mallakar Haman, maƙiyin Yahudawa, sai kuma Modakai ya fara hidima a gaban sarki, gama Esta ta gaya wa sarki dangartakarta da Modakai.2Sai sarki ya cire zobensa na hatimi, wanda ya karɓe daga wurin Haman, sai ya ba da shi ga Modakai. Esta ta sa Modakai ya zama mai lura da gidagen Haman.3Sai Esta ta sake yin magana da sarki. Ta kwantar da fuskartar a ƙasa tana kuka yayinda take roƙo gareshi ya kawo ƙarshen mugun shirin Haman Ba'agage, da maƙarkashiyar daya ƙulla wa Yahudawa.4Sai sarki ya miƙo sandar zinariya na sarauta ga Esta, ta tashi ta tsaya a gaban sarki.5Sai ta ce, "Idan ya gamshi sarki, kuma idan na sami tagomashi a wurinka, idan abin yayi dai-dai a ganin sarki, kuma idan na sami tagomashi a idanunka, bari a bada rubutaccen umarni da zai soke wasiƙun da Haman ɗan Hamedata Ba'agage, ya rubuta domin ya hallakar da Yahudawa waɗanda suke warwatse cikin lardunan sarki.6Gama yaya zan jimre da ganin masifar da za ta faɗo wa mutanena? Ta yaya zan iya daure wa ganin hallakarwar dangina?"7Sarki Ahasuros ya cewa Sarauniya Esta da kuma Modakai Bayahude, "Duba, na miƙa wa Esta gidan Haman, kuma sun rataye shi a bisa gungume, domin yayi shirin kaiwa Yahudawa farmaki.8Rubuta wani umarni domin Yahudawa a cikin sunan sarki a kuma hatimce shi da zoben sarki. Gama umarnin da aka riga aka rubuta da sunan sarki aka kuma hatimce shi da zoben sarki ba za a iya soke shi ba."9Sai aka kirawo magatakardan sarki a wannan lokaci, a cikin wata na uku, wanda shi ne watan Siban, a ranar ashirin da uku ga wata. Aka rubuta umarni ɗauke da dukkan abin da Modakai ya umarta game da Yahudawa. Aka rubuta zuwa ga gwamnonin larduna, su gwamnoni da shugabannin lardunar da ke zaune daga Indiya zuwa Kush, larduna 127, ga kowanne lardi aka rubuta da irin rubutunsu, da kuma ga kowaɗanne mutane cikin yarensu, da kuma ga Yahudawa da rubutunsu da yarensu.10Modakai yayi rubutu da sunan sarki Ahasuros ya kuma hatimce shi da zoben hatimin sarki. Ya aika takardun ta hannun 'yan kada ta kwana mahaya doki masu gudu sosai da ake yin anfani da su a hidimar sarki, wanda aka yi renon su daga masarauta.11Sarki ya baiwa Yahudawa na kowanne birni izinin taruwa tare a kuma yi tsayayya don kariyar rayukarsu: su shafe su gaba ɗaya, su kashe, su kuma hallakar da kowacce taruwar masu makamai daga kowaɗanne mutane, ko lardin da ke niyyar kawo masu farmaki, da yaransu da kuma matayensu, ko su kwashi dukiyoyinsu ganima.12Wannan za a aiwatar cikin dukkan lardunan sarki Ahasuros, a ranar sha uku na watan sha biyu, wanda shi ne watar Ada.13Takardar dokar za a miƙa ta a matsayin shari'a kuma za a bayyana ta a fili ga dukkan mutane. Yahudawa sai su zauna da shiri a wannan rana don ɗaukar fansa kan maƙiyansu.14Sai 'yan kada ta kwana suka hau dawakan masarauta da ake amfani dasu a hidimar sarki. Suka tafi babu ɓata lokaci. Dokar sarki kuwa aka miƙa ta daga fada a Susa.15Sai Modakai ya tashi daga gaban sarki sanye da rigunan sarauta na shuɗi da fari, tare da gagarumin kambi na zinariya da kuma alkyabba ta lillin mai ruwan shunayya, sai birnin Susa tayi sowa da kuma farinciki.16Yahudawa suka sami sauƙi da kuma farinciki, da kuma murna da kuma daraja.17A kowanne lardi da cikin kowanne birni, dukkan inda umarnin sarki ya kai, aka yi farinciki da kuma murna a tsakanin Yahudawa, aka yi biki da kuma hutu. Dayawa daga cikin mutane daban-daban a ƙasar suka zama Yahudawa, domin tsoron Yahudawa ya faɗo masu.
A duba yadda aka fassara sunan wannan mutum a cikin Esta 3:1.
Wannan zobe yana da sunan sarki ko alamarsa.Sa'ad da aka zuba ƙaron hatimcewa a bisa muhimman takardu, sai ya danna alamar a cikin hatimin. Idan takarda na da alamar wannan hatimin, mutane za su san cewa abin da aka rubuta a bisa takardar yana tare da ikon sarki kuma dole ayi biyayya. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 3:10.
Ta wurin ba da zobensa na hatimi ga Modakai, sarkin ya ba da iko ga Modakai ya rubuta muhimman takardu waɗanda mutane za su yi biyayya dole.
Wannan na maganar abubuwan da Haman ya ke da su kuma sarkin ya ba Esta.
"bara"
"Kawo ƙarshen" a nan kari ne da ke ma'anar a tsaida wani abu. AT: "a tsaida mugun shirin Haman Ba'agage" ko "a hana mugun shirin Haman Ba'agage daga faruwa"
A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 3:1.
"makircin da ya ƙirƙiro" ko "makircin da Haman ya ƙirƙiro
Ya yi haka ne ya nuna cewa ya gamsu da ita. A duba yadda aka fassara irin wannan magana a cikin Esta 5:2.
"Idan abin da na roƙa ya gamshi sarki"
A nan "sami tagomashi" kari ne da ke nufin yadda da ita ko gamsuwa ta ita. "A wurinka" misali ne "idanu", kuma idanu misali ne da ke wakiltar darajar ta a gare shi. AT: "Idan ka daraja ni kuma ka yadda da ni" ko "idan ka gamsu da ni"
"A ganin sarki" misali ne da ke wakiltar darajar ta a gare shi. AT: "idan abin da na roƙa ya yi dai-dai- a ganin sarki"
A nan "idanunka" misalin da ke nufin gani, kuma gani misali ne da ke wakiltar darajar ta a gare shi. AT: "Idan ka daraja ni kuma ka yadda da ni" ko "idan ka gamsu da ni"
a maida baya a cire ikon
Wannan sunan namiji ne.
A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:1.
Esta ta yi wannan tambaya ne ta nuna cewa ranta zai ɓaci sosai idan mutanenta suka hallaka. AT: "Ba zan iya jimre ganin masifar da za ta faɗo wa Yahudawa ba. Ba zan iya daure ganin kisan dangina ba."
Wannan na mamadin dukkan abin da Haman ya mallaka. AT: "dukkan abin da Haman ya ke da shi" ko "dukkan kadarorin Haman"
A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 6:4.
Rubuta wani abu a cikin sunsn sarki na mamadin rubutawa da izininsa, ko an wakilce shi aka rubuta.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "domin babu wanda zai soke umarnin ... zoben" ko "domin babu wanda zai goge umarnin ... zoben"
Rubuta wani abu a cikin sunsn sarki na mamadin rubutawa da izininsa, ko an wakilce shi aka rubuta.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "sarki ya kira magatakardansa."Mai karatu ya fahimci cewa ana zaton sarki ya gaya wa wani maƙaddashinsa da ya je ya zo da magatakardan tare da shi. Da zaton ba wai sarki ya yi kira da murya da ƙarfi ba domin su zo.
"Siban" sunan wata na uku ne a kalandar Ibraniyanci. Kwana na ashirin da uku yana kusa da tsakiyar watan Jun na kalandar Turawa.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Suka rubuta umarni"
"larduna ɗari da ashirin da bakwai"
"aka rubuta da salon rubutunsu" akwai ire-iren rubutu daban-daban a cikin duniya.
Rubuta wani abu a cikin sunsn sarki na mamadin rubutawa da izininsa, ko an wakilce shi aka rubuta.
mutanen da ke kai saƙo
Dokin sarauta namijin dokin sarki ne da ya zarce kowanna doki. Dawakan da ake amfani da su wajen aiwatar da hidimar sarki 'ya'yansa ne. AT: "'ya'yan dokin sarki"
"Ya gaya wa Yahudawa ... cewa ya bar su su tareu"
Wannan misali ne na tsayawa su yi yaƙi kada kuma su gudu. AT: "ku rãma"
A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 3:13.
"A ɗauki fansa kan mutane" a nan kari ne da ke ma'ana ka yi rauni ga waɗanda suka yi maka rauni. AT: "su maida yaƙi gãba da maƙiyansu"
A nan "babu ɓata lokaci" kari ne da ke ma'ana ba su yi jinkiri ba ko su tsaya. AT: "Suka tafi da hanzari"
Wannan ne birnin da fãdar sarki ta ke. A duba yadda aka fassara a cikin Esta 1:2.
"Birnin na ma'anar mutanen da ke zaune a ciki. AT: "mutanen birnin Susa suka yi sowa da kuma farinciki"
Kalmar "farinciki" na nuna sowar da suka yi. AT: "sowa cikin farinciki"
Mai yiwuwa ma'anonin su ne 1) samin sauƙi misali ne da ke nufin kasancewa da murna. AT: "suna murna da farinciki" ko 2) samin sauƙi misali ne na jin wadata da tsaro. AT: "suka ji su na da tsaro suka kuma yi farinciki"
Mai yiwuwa ma'anonin su ne 1) sauran mutane suka darjanta Yahudawa. AT: "sauran mutane suka darjanta su" ko 2) Yahudawa suka ji an darjanta su. AT: "suka ji an darjanta su"
Lardi wani babban sashe ne da ake rarrabawa zuwa ƙasashe domin mulki. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:1.
Kaiwa wurare na nufin zuwa wuraren. AT: "duka inda mutanen sarkin suka kai umarninsa"
ranar da mutane ke bukin abubuwa na musamman
Tsoron Yahudawa ya faɗo masu na nufin zama cikin tsoro ƙwarai. AT: "suka zama cikin tsoron Yahudawa ƙwarai"
1Yanzu a cikin watan sha biyu, wanda shi ne watan Ada, a ranar sha uku, lokacin da za a aiwatar da shari'a da kuma dokar sarki, a ranar da makiyan Yahudawa ke sa ran zasu sha karfinsu, aka juyad da yanayin. Yahudawa suka sha karfin waɗanda suka tsane su.2Yahudawa suka tattaru a biranensu cikin dukkan lardunan sarki Ahasuros, su tayar wa waɗanda suka so su kawo masu bala'i. Babu wanda ya iya tsayayya dasu, gama tsoronsu ya abko wa dukkan mutanen.3Dukkan shugannin lardunar, da gwamnonin lardunar, su gwamnoni, da ma'aikatan sarki, suka taimaka wa Yahudawa domin tsoron Modakai ya abko masu.4Gama Modakai ya zama mutum mai girma a gidan sarki, kuma labarinsa ya bazu a dukkan larduna, domin mutumin Modakai ya zama mai girma.5Yahudawa suka kai hari ga makiyansu da takobi, suna kisansu da hallakar da su, kuma suka yi masu yadda suka ga dama ga waɗanda suka ƙisu.6A cikin fãdar Susa da kanta Yahudawa suka kashe da kuma hallakar da mutum ɗari biyar.7Suka kashe Farshandata, Dalfon, Asfata,8Forata, Adaliya, Aridata,9Farmashta, Arisai, Aridai, da Baizata,10da kuma 'ya'ya maza na Haman ɗan Hamedata su goma, maƙiyin Yahudawa. Amma basu kwashi ganima ba.11A wannan rana jimillar waɗanda aka kashe cikin fãdar Susa, aka faɗa wa sarki.12Sai sarki ya cewa Sarauniya Esta, "Yahudawa sun kashe mutum ɗari biyar cikin fãdar Susa, har da 'ya'ya maza na Haman su goma. Mene ne kuma suka aiwatar cikin sauran lardunar sarki? Yanzu mene ne roƙonki? Za a baki. Mene ne bukatarki? Za a biya maki."13Esta tace, "Idan ya dace a ganin sarki, bari a baiwa Yahudawan da ke cikin Susa izinin aiwatar da dokar yau a gobe kuma, bari kuma a rataye gawawakin 'ya'ya maza na Haman su goma a bisa gumagumai."14Sai sarki ya umarta da a yi haka. Aka zartar da dokar a cikin Susa, aka kuma rataye 'ya'ya maza goma na Haman.15Yahudawa da ke a Susa suka taru tare a rana ta sha huɗu a watan Ada, suka kashe mutum ɗari uku cikin Susa, amma ba su kwashi ganima ba.16Sauran Yahudawa da ke a lardunan sarki suka taru tare don su kare rayukansu, sun kuma ƙuɓuta daga makiyansu suka kuma kashe mutum dubu saba'in da biyar daga waɗanda suka tsanesu, amma basu ɗibiya hannunsu bisa dukiyan waɗanda suka kashe ba.17Wannan ya faru ne a ranar sha uku na watan Ada. A rana ta sha huɗu sai suka huta suka maishe ta ranar shagali da kuma murna.18Amma Yahudawan da ke a Susa suka taru tare a ranakun sha uku da sha huɗu. A rana ta sha biyar suka ka huta suka maishe ta ranar shagali da kuma murna.19Shi yasa Yahudawan da ke ƙauyuka, waɗanda suka yi gidajensu a ƙauyukan karkara, suka maida rana ta sha huɗu na watan Ada ranar murna da kuma shagali, da kuma ranar da zasu aika wa juna kyaututtukan abinci.20Modakai ya rubuta waɗannan abubuwan ya kuma aika wasiƙu zuwa ga dukkan Yahudawan da ke cikin dukkan lardunan sarki Ahasuros, na kusa dana nesa,21yana umurtansu dasu kula su kuma kiyaye ranakun sha huɗu da kuma sha biyar na Ada a kowacce shekara.22A wannan kwanaki ne Yahudawa suka kuɓuta daga maƙiyansu, da kuma watan da baƙin cikinsu ya zama farin ciki, kuma ranar makoki ta zama ranar shagali. Zasu maishe su ranakun shagali da kuma murna, da kuma aikar da kyaututtukan abinci ga juna, da kuma kyaututtuka ga talakawa.23Sai Yahudawa suka cigaba da shagali kamar yadda suka fara, suna aiwatar da abin da Modakai ya rubuta garesu.24A wannan lokacin da Haman ɗan Hamedata Ba'agage, maƙiyin dukkan Yahudawa, ya shirya wa Yahudawa makirci don ya hallakar dasu, ya kuma jefa Fur (wato, ya jefa ƙuri'u), don ya hargitsa su ya hallakar da su.25Amma da zancen ya kai ga sarki, sai ya bada umarnai ta wasiƙu domin makircin da Haman ya ƙulla gãba da Yahudawa shi koma kansa, da kuma a rataye shi da 'ya'yansa maza a bisa gumagumai.26Saboda haka aka kira waɗannan ranakun sunan Furim, bisa ga sunan Fur. Saboda dukkan abubuwan da aka rubuta cikin wannan wasiƙa, da dukkan abin da suka gani da idanunsu ta kuma same su,27Yahudawa suka yi na'am da sababbin ranaku da al'ada. Wannan ranaku zasu zama dominsu, da kuma zuriyarsu, da kuma dukkan wanda zai haɗa kai da su. Ya kuma zama cewa za su tuna da waɗannan ranakun biyu sau biyu a kowacce shekara. Zasu kula da waɗannan ranakun a hanyoyi na musamman da kuma a lokaci ɗaya kowacce shekara.28Waɗannan ranaku za a yi bukukuwa a kuma kula dasu a kowacce tsara, da kowanne iyali, da kowanne lardi, da kowanne birni. Waɗannan Yahudawan da kuma zuriyarsu ba zasu dena tunawa da waɗannan ranakun Furim cikin aminci ba, domin kada su manta da su.29Sarauniya Esta ɗiyar Abihel da Modakai Bayahude suka yi rubutu da cikakken iko suka kuma tabbatar da wannan wasika ta biyu game da Furim.30Aka aika wasiƙu zuwa ga dukkan Yahudawa cikin larduna 127 na masarautar Ahasuros, ana yi wa Yahudawa barka na salama da gaskiya.31Waɗannan wasiƙu suka tabbatar da ranakun Furim cikin lokacinsu, kamar yadda Modakai Bayahude da Sarauniya Esta suka dokaci Yahudawa. Yahudawa suka yi na'am da wannan doka domin kansu da kuma zuriyarsu, kuma kamar yadda suka yi na'am da lokacin azumi da makoki.32Dokar Esta ta tabbatar da waɗannan sharuɗɗai game da Furim, an kuma rubuta su cikin littafi.
A duba yadda aka fassara irin wannan zance a cikin Esta 3:13.
A nan "aiwatarwa" kari ne da ke ma'anar yin wani abin da aka umarta ko shirya. Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "lokacin da mutanen su ke gab da aiwatar da shari'a da kuma dokar sarki"
Shan ƙarfin mutane kari ne da ke ma'anar kayar da su. AT: "su kayar da Yahudawa"
"aka juyad da al'amarin." Juyad da al'amarin misali ne da ke ma'anar akasin abin da aka zaci zai faru. AT: "akasin ne ya faru"
A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:1.
Tayar wa mutane zance ne da ke nufin yin yaƙi gãba da su. AT: "su yi yaƙi da maƙiyansu"
Kawo bala'i ga mutane kari ne da ke ma'anar haddasa bala'i ya faru da su. A wannan yanayin yana nufin hallakar da su. AT: "waɗanda suka nemi su hallakar da su"
Tsayayya da mutane na nufin hana harinsu. AT: "Ba bu wanda ya iya hana kai harin Yahudawa" ko "Ba bu wanda ya iya yin nasara a yaƙi gãba da Yahudawa"
Tsoron mutane ya abko masu na nufin mutane na zama cikin tsoro ƙwarai. AT: "dukkan mutanen suka zama cikin tsoron Yahudawa ƙwarai"
"gwamnonin da ke bisa larduna"
Tsoron ya abko wa mutane na nufin mutane na zama cikin tsoro ƙwarai. AT: "suka zama cikin tsoron Modakai ƙwarai"
"mai muhimmanci ƙwarai a fãdar sarki"
Labari ya bazu a dukkan wurare na nufin mutane a dukkan wuraren na sanin irin girmansa. AT: "a dukkan lardunan mutane suka san irin girmansa"
Wannan na nufin babban birni, mai ƙarfi da tsaro. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:2.
Wannan birnin sarautar sarakunan Fasiya ne. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 1:2.
"mutum 500"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
"'ya'ya maza 10"
Wannan suna ne da kwatancen Haman, ɗaya daga cikin shugabannin sarki. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 3:1.
A duba yadda aka fassara sunan wannan mutum a cikin Esta 3:1.
Wannan kalma na gaya mana game da Haman.
Sarkin ya yi wannan tambaya ne da ya nuna cewa ya tabbata Yahudawa sun kashe mutane da yawa a sauran lardunan. AT: "abin da babu shakka suka aiwatar a sauran lardunan sarkin!" ko "babu shakka sun kashe da yawa fiye ma a sauran lardunan sarki!"
Za a iya bayyana misalin suna "roƙo" tare da aikatau "tambaya" ko "buƙata." AT: "me ki ke tambaya?" ko "me ki ke buƙata?"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "zan baki abin da ki ka tambaya" ko "zan yi maki abin da ki ke buƙata"
Za a iya bayyana misalin suna "buƙata" tare da aikatau "tambaya" ko "roƙo." AT: "me ki ke tambaya?" ko "me ki ke roƙo?"
A nan "aiwatar" kari ne da ke ma'anar wani abu da aka dokatar ko shirya. AT: "gobe kuma ayi biyayya da dokar yau" ko "gobe kuma ayi abin da aka dokatar da ayi yau"
Wannan wani sassaƙaƙƙen katakon rataye wani ne ta wurin ɗaura igiya zagaye a bisan gungumen ƙarshen igiyar kuma a ɗaure wuyansa sai a rataye shi a jikin. A duba yadda aka fassara "gungume" a cikin Esta 2:23. AT: "katakon rataye mutane"
A duba yadda aka fassara irin wannan zance a cikin Esta 3:13.
Ɗora hannuwa bisa abubuwa na mamadin kwashe su. AT: "ba su ɗauki ganima ko ɗaya ba" ko "ba su ɗauki ko ɗaya daga cikin ganimar ba"
"75,000"
Ɗora hannuwa bisa abubuwa na mamadin kwashe su. AT: "ba su ɗauki ganima ko ɗaya ba" ko "ba su ɗauki ko ɗaya daga cikin ganimar ba"
"dukiyoyi" ko "kadarori"
A duba yadda aka fassara irin wannan zance a cikin Esta 3:13.
"A rana ta sha huɗu ga watan Ada Yahudawan da ke lardunan suka huta"
Za a iya faɗin dalilin da ya sa suka taru a sarari. AT: "Yahudawan da ke a Susa suka taru tare su yi yaƙi gãba da maƙiyansu"
A kiyaye rana kari ne da ke ma'anar shagali. AT: "ayi shagalin ranakun sha huɗu da kuma sha biyar na Ada a kowacce shekara"
Ya zama na mamadin ya canza. Misalin suna baƙinciki da farinciki za a iya fassarawa tare da "baƙinciki" da "farinciki." AT: "suka canza daga zama cikin baƙinciki zuwa farinciki"
Wannan wuri ya kammala yawacin labarin Esta domin a bayyana dalilin yin bikin Furim.
Wannan suna ne da kwatancen Haman, ɗaya daga cikin shugabannin sarki. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 3:1.
"Fur" kalmar Fasiya ne na "ƙuri'u." Kalmar "ya jefa ƙuri'u" ya bayyana ma'anar "ya jefa Fur."
Za a iya fassara juyin Ibraniyawa ya kasance da ma'anar, "Amma da Esta ta zo gaban sarki." Wasu juyin zamani sun ɗauki wannan fassarar.
"shi koma kansa" na ma'anar a yiwa Haman haka. AT: "makircin da Haman ya ƙulla gãba da Yahudawa bari a yi ma shi"
A kira wani abu bisa ga wani abun kari ne da ke ma'anar a bada suna irin ɗaya ko shigen suna ɗaya. AT: "Suka kira waɗannan ranaku Furim, kamar kalmar Fur"
Wannan sunan biki ne da ake yi domin tunawa da ceton mutanen Yahudawa a tsohuwar Fasiya daga shirin Haman na hallakarwa da kisan Yahudawa a rana ɗaya.
Za a iya bayani a sarari abin da "Fur" ke nufi. AT: "kalmar Fur, wadda ke ma'anar "ƙuri'a."
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Yahudawa za su kiyaye su kuma yi bukukuwan waɗannan ranaku"
Za a iya faɗin wannan da yayyarawa. AT: "a koyaushe za su kiyaye da aminci"
Esta ɗiyar Abihel ce, Esta da Modakai ne suka rubuta wasiƙar.
Mahaifin Esta da kawun Modakai. A duba yadda aka fassara wannan a cikin Esta 2:15.
"ƙarin wasiƙa"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Suka aika wasiƙu zuwa ga dukkan Yahudawa"
"larduna ɗari da ashirin da bakwai"
Misalin suna "barka" da "gaskiya" za a bayyana da. AT: "da fatan Yahudawa za su kasance cikin salama kuma mutane za su yi aminci ga Yahudawa"
Yin na'am da doka misali ne da ke nufin yadda da dokar. Misalin suna "doka" za a iya bayyanawa tare da aikatau "doka." AT: "Yahudawan suka yadda cewa su da zuriyarsu sun yadda yi bikin ranakun Furim"
Karɓar lokuttan azumi da makoki misali ne da ke ma'anar yadda da yin azumi da makoki a wasu lokutta"
1Sa'an nan Sarki Ahasuros yasa dokar haraji a ƙasar da kuma kasashen tuddai na bakin teku.2Dukkan aikin ci gaba na iko dana karfi, tare da cikakken tarihin girman Modakai ta yadda sarki ya darajartar da shi, aka rubuta su cikin littafin tarihin sarakunan Midiya da kuma Fasiya.3Modakai Bayahude ya zama na biyu bayan sarki Ahasuros ta fannin mulki. Mai girma ne cikin Yahudawa da kuma sananne cikin 'yan'uwansa Yahudawa masu yawa, gama yana kula da lafiyar mutanensa yana yin maganar salama domin dukkan mutanensa.
Sa dokar haraji na nufin a sa mutane su biya haraji. Ƙasar da kuma ƙasashen tuddai na bakin teku na nufin mutanen da ke zama a ciki, AT: "a sa mutanen da ke zama a ƙasar da kuma ƙasashen tuddai na bakin teku su biya haraji"
Misalin suna "aikin ci gaba" za a iya bayaninsa da aikatau "aiki" ko kalmar "yin manyan abubuwa. Misalin suna "iko" da "ƙarfi" za a iya fassarawa da wakilin aiki. AT: "Dukkan aikin ci gaba da ya yi saboda ikonsa da karfi" ko "Dukkan manyan abubuwan da ya yi saboda ikonsa da karfi"
An yi zancen cewa sarki ya darjanta Modakai kamar a ce sarki ya ɗaga shi sama a zahiri. AT: "cikakken labarin Modakai da yadda sarki ya darajartar da shi na da girma" ko "cikakken labarin Modakai da yadda sarki ya darajartar da shi domin manyan abubuwan da ya yi"
"mutum mafi muhimmanci bayan sarki Ahasuros"
Kalmar "'yan'uwa" na nufin mutane da ke kamarsa. AT: "Yahudawa kamarsa"
Kula da wani abu misali ne domin aiki tuƙuru domin wannan abin. Misalin suna "kula" za a iya fassarawa a matsayin kalma tare da aikatau "wadata" ko wakilin aiki "kariya." AT: "Ya yi aiki tuƙuru domin mutanensa Yahudawa su wadata" ko "Ya yi aiki tuƙuru domin mutanensa Yahudawa su kasance cikin kariya"
"ya wakilci mutanensa domin su sami salama"
1Akwai wani mutum a ƙasar Uz mai suna Ayuba; Ayuba kuwa marar laifi ne mai gaskiya, wanda ke tsoron Yahweh ya kuma juya wa mugunta baya.2A ka haifa masa 'ya'ya bakwai maza da 'yammata uku.3Ya mallaki tumaki dubu bakwai da raƙuma dubu uku da bijimai ɗari biyar da jakai ɗari biyar da kuma bayi masu yawan gaske. Shi ne ya fi girma a cikin dukkan mutanen Gabas.4An keɓe rana domin kowanne ɗă, ya yi liyafa a cikin gidansa. Sukan aika a kira 'yan'uwansu mata su uku su ci su sha tare da su.5Sa'ad da kwanakin liyafar suka ƙare, sai Ayuba ya aika su zo ya tsarkake su. Ya kan tashi da sassafe ya miƙa baye--baye na ƙonawa domin kowanne ɗaya a cikin 'ya'yansa, gama ya kan ce, "Ya yiwu yarana sun yi zunubi sun yi saɓon Yahweh a cikin zukatansu." Haka Ayuba yakan yi kullun.6A ranar da 'ya'yan Allah maza suka zo domin su bayyana kansu a gaban Yahweh. Sai Shaiɗan ma ya biyo su. Sai Yahweh yace da Shaiɗan, "Daga ina ka zo?"7Sai Shaiɗan ya amsawa Yahweh yace, "Daga garari cikin duniya da zirga--zirga a cikinta."8Sai Yahweh yace da Shaiɗan, "Ka kuwa lura da Ayuba bawana? Gama babu kamar sa a duniya, marar laifi ne kuma mutum ne mai gaskiya yana tsoron Yahweh ya juya wa mugunta baya.9Sa'annan Shaiɗan ya amsawa Yahweh yace, "Haka nan Ayuba ya ke tsoron Allah ba dalili?10Ba ka kare shi ta kowanne gefe ba, shi da gidansa da dukkan abin da ya ke da shi? K a sawa ayyukan hannuwansa albarka da shanunsa sun yaɗu da yawa a cikin ƙasa.11Amma yanzu ka miƙa hannunka ka taɓa abin da ya ke da shi dukka, ka gani idan bai la'ance ka kana gani ba."12Sai Yahweh yace da Shaiɗan, "Duba, dukkan abin da ya ke da shi na hannunka." Sai dai a kansa ne kaɗai ba zaka sa hannunka ba." Sa'annan Shaiɗan ya fita daga wurin Yahweh.13Sai ya zama a wata rana, 'ya'yansa maza da mata suna ci suna shan ruwan inabi a gidan babban wansu.14Wani ɗan aike ya zo wurin Ayuba yace, "Bijimai suna huɗa jakai kuma suna kiwo a gefensu.15Sai Sabiyawa suka auko ba zato suka kwashe su. Bayin kuma sun kashe su da kaifin takobi. Ni kaɗai ne na tsira don in gaya maka."16Yana cikin yin magana, sai wani kuma ya zo ya ce, "Wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye tumaki duk da bayin. Ni kaɗai ne na tsira don in gaya maka."17Yana cikin yin magana, sai wani kuma ya zo ya ce, "Kaldiyawa sun zo a ƙungiyoyi uku, sun kawo hari a kan raƙuman sun kwashe su. Sun kuma kashe bayin da kaifin takobi. Ni kaɗai ne na tsira don in gaya maka."18Yana cikin yin magana, wani kuma ya zo ya ce, "Ya'yanka maza da matan suna ci suna sha a gidan babban wansu.19Sai wata iska mai ƙarfi ta taso daga cikin jeji ta buge kusurwoyin gidan guda huɗu. Gidan ya faɗa a kan matasan, kuma sun mutu. Ni kaɗai ne na tsira don in gaya maka."20Sai Ayuba ya tashi, ya keta tufafinsa, ya aske kansa, ya faɗi da fuskarsa a ƙasa, ya yi wa Yahweh sujada.21Ya ce, "Sa'ad da na fito daga cikin mahaifiyata tsirara nake, kuma tsirara zan koma can. Yahweh ne ya bayar, Yahweh ne kuma ya ɗauke. Bari sunan Yahweh ya zama mai albarka."22A cikin wannan lamari dukka, Ayuba bai yi zunubi ba, bai kuma yi zargi ga Allah kan ya yi kuskure ba.
Yiwu wurare su ne: 1) wani wuri a cikin tsohon Idom gabashin Kogin Yodan ko 2) wani wuri gabashin Yufiretis a cikin Iran na zamani.
Kalmomin ''marar laifi'' da kuma ''mai gaskiya'' na da ma'anar kusan ɗaya kuma suna nanata cewa Ayuba mai adalci ne. AT: ''mutum wanda ya yi abin da ke dai-dai a gaban Allah''
''wanda ke girmama Yahweh''
A nan an yi magana akan mugunta kamar wani wuri ne da mutum zai iya guje wa zuwa, a maimakon yin ayyukan mugunta. AT: ''ya ƙi aikata mugunta''
'''ya'ya maza 7 da mata 3''
''Yana da tumaki 7,000''
''raƙuma 3,000''
''bijimai 500''
''mafi arziki'
Wannan na nufin wuraren da suke gabas da Kan'ana. AT: ''duk mutanen da ke zaune a ƙasashen da suke gabashin ƙasar Kan'ana''
Kalmar ''rana'' wataƙila na nufin ranar da suka yi bikin ranar haihuwar ɗa. Amma aƙalla yana nuni cewa dukan yayansa maza kan dauki wata rana domin yin liyafa. AT: ''A kowace ranar haihuwar ɗa, ɗa zai ba da'' ko ''Kowane ɗa kuma shi zai ba''
"Suna zama bisa al'ada kuma sun aika ... Ayuba ya saba ke ... ya saba tsarkakewa ... ya saba tun da sassafe ya miƙa ... yana al'ada yace''
Kalmar ''su'' na nufin 'ya'ya maza bakwai da 'yan mata uku amma ba su hada da Ayuba ba.
''Lokacin da liyafar suka ƙare'' ko ''Bayan liyafar''
''Ayuba ya aiki wani ya kira su zo wurinsa''
A nan ''tsarkakewa'' na nufin a roƙon Allah ya dauke dukkan wani rashin tsarki da 'ya'yan Ayuba suka jawowa kansu yayin da suke farin ciki tare. Ayuba ya yi wannan ta wurin hadaya ga Allah a kansu.
''Zukatansu'' na nufin tunaninsu. Sau da yawa irin wannan tunanin kan zo ba zato, ba da son mai yinta ba. AT: ''ya la'ance Allah a cikin tunaninsu''
''A lokacin da'' ko '' Wata rana yaushe.'' Wannan ba takamaiman rana bane amma a fili taron ya kasance koyaushe.
Wannan na nufin malaiku, hallitu na sama
''su tsaya tare a gaban Yahweh kamar yadda ya umarce su su yi.''
Wannan shi ne sunan Allah ne wanda ya bayyana wa mutanensa a cikin Tsohon Alƙawari. Duba fassara a translationWord game da Yahweh dangane da yadda ake fassara wannan.
Waɗannan kalmomin ''garari'' da ''zirga-zirga'' suna nufin ayyukan tafiye-tafiye cikin dukkan duniya domin a tabbatar da cikar. AT: ''Daga tafiya ko'ina cikin duniya''
''Ka kuwa yi tunani game da Ayuba bawana?'' A nan Allah ya fara magana da shaiɗan game da Ayuba. AT: ''Ka yi la'akari da bawana Ayuba"
Kalmomin ''mara laifi'' da ''mai gaskiya'' na da ma'ana kusa daya kuma na nanatawa cewa Ayuba adali ne. Duba yadda aka fasara wannan a Ayuba 1:1. AT: ''wanda ya yi abin da ke dai-dai a gaban Allah'' (Duba: )
''wanda ya girmama Yahweh.'' Duba yadda aka yi fassara wannan a Ayuba 1:1
''Haka nan Ayuba yana girmama Allah ba dalili?'' Shaiɗan ya amsa Allah ta wurin miƙawa da amsa tambayarsa. Ya ce Ayuba na yi wa Yahweh biyayya ne kawai domin Allah ya sa masa albarka. AT: ''Ayuba yana da dalilin yin biyayya ga Allah.''
Shaiɗan ya faɗi gaskiya don ya tabbatar da hujjojinsa. AT: ''Ka kare shi, da danginsa da duk abin da ya mallaka''
Kamar yadda shinge kamar bango ko shinge ya kewaye kuma yake kare mallakar mutum, Allah ya kewaye Ayuba da kariyarsa. AT: ''ya kare shi da gidansa da duk abin da yake nasa''
''duk abin da yake yi''
Shaiɗan yana nufin cewa idan Allah ya kai hari kan Ayuba, zai ga yadda Ayuba zai mai da martani. AT: ''Amma yanzu, idan ka miƙa hannunka taɓa duk abin da yake da shi, za ka ga zai la'anta ka a fuskarka''
''ya na da dabbobi masu yawa a cikin ƙasar
A nan ''hannu'' na nufin ikon Yahweh da aikatawa. ''Amma yanzu amfani da ikonka''
A nan ''taɓawa'' na wakiltar aikin lalatarwa ko batawa. AT: ''kai hari duk abin da yake da shi'' ko ''lalata dukan abin da yake da shi''
''kana ji.'' wannan na nufin a lokutan Yahweh ke lura.
''Kalla'' ko ''Lura da dukan abin da zan fada maka''
Anan ''hannun'' na wakiltar ikon wani don sarrafa wani abu. AT: ''kana da iko akan dukan abin da yake da shi''
''a kan ransa''
''barin Yahweh"
Wannan na nufin mutane dake a yanki a ckin zamani na Yemen. A nan yana wakiltar kungiyar maharan ko 'yan fashi.
A nan ''auko'' na nufin farmaki. AT: ''kai masu hari''
A nan bugewa na nufin kisa.
A nan ''kaifin'' na nufin gefe na takobi da ke kishe mutane, wato, ko tsinin ko gefen kaifi. Hakanan, an yi bayanin dukka takuban Sabiyawa kamar dai su takobi ɗaya ne.
''ya'' na nufin manzo farko
Wannan na nufin wani manzo. AT: ''wani manzo ya zo''
Duba yadda zaka fassara wannan a Ayuba 1:15.
A nan ''kaifi'' na nufin fannin takobi da kan kashe mutane. Duba yadda zaka fassara wannan a Ayuba 1:15.
Duba yadda zaka fassara wannan a Ayuba 1:13.
"Hadari" ko "Guguwar hamada"
"tsarin tallafi na gidan"
"Gidan ya faɗi akan ɗiyanku maza da mata"
Waɗannan ayyuka ne na makoki na al'ada, suna nuna baƙin ciki mai zurfi.
"A haifuwata, ban kawo komai a cikin duniya, kuma a mutuwata zan koma a kasa ba tare da komai ba"
"Game da duk wannan abin da ya faru"
"ka ce Allah ya yi ba dai-dai ba"
1Wata rana kuma da 'ya'yan Allah maza suka zo su baiyana kansu a gaban Yahweh. Shaiɗan ma ya biyo su don ya baiyana kansa a gaban Yahweh.2Yahweh yace da Shaiɗan, "Daga ina ka zo?" Sai Shaiɗan ya amsawa Yahweh yace, "Daga garari cikin duniya da kai da kawowa a kanta."3Yahweh yace da Shaiɗan, "Ka lura da bawana Ayuba? Gama babu kamar sa a duniya, marar laifi ne, mutum ne mai gaskiya, yana juya wa mugunta baya. Har yanzu yana nan riƙe da nagartarsa, duk da yake ka sa in yi gãba da shi, don in hallaka shi babu wani dalili."4Shaiɗan ya amsawa Yahweh yace, "Jiki magayi, tabbas mutum zai iya rabuwa da dukkan abin da yake da shi domin ya ceci ransa.5Amma ka miƙa hannunka yanzu ka taɓa ƙasusuwansa da jikinsa, ka gani idan bai la'ance ka kana gani ba."6Yahweh yace da Shaiɗan, "Ga shi, yana hannunka; ransa ne kaɗai ba zaka taɓa ba."7Daga nan sai Shaiɗan ya tafi daga gaban Yahweh. Ya bugi Ayuba da marurai tun daga tafin ƙafarsa har zuwa kansa.8Ayuba ya ɗauki ɓallin kasko yana susa da shi, kuma ya zauna a cikin tsakiyar toka.9Sai matarsa tace da shi, "Har yanzu kana nan riƙe da nagartarka? Ka la'anci Allah ka mutu."10Amma ya ce da ita, "Kina yin magana kamar yadda gaɓuwar mace ke yi. Za mu karɓi abu mai kyau daga wurin Allah mu ƙi karɓar marar kyau"? A cikin wannan lamari dukka, Ayuba bai yi zunubi da leɓunansa ba.11A na nan, sa'ad da abokan Ayuba uku suka ji dukkan wannan bala'in da ya same shi, kowannen su ya tawo daga garinsa: Elifaz Batemane da Bildad Bashune da Zofar Banamate. Suka sa lokaci domin suzo su makoki tare da shi su kuma ta'azantar da shi.12Sa'ad da suka hango daga nesa, basu iya gane shi ba. Suka tada muryoyinsu suka yi kuka; kowannen su ya keta tufafinsa ya watsa ƙura a sama dakuma bisa kansa.13Sa'an nan suka zauna a ƙasa tare da shi a ƙasa har yini uku da dare uku. Ba wanda ya yi masa magana, gama sun ga yana da baƙin ciki mai yawa.
Wadannan ayar kusan dai-dai da Ayuba 1:6-7 kuma za a iya fassara ta ta wannan hanyar.
Duba yadda zaka fassara wannan a Ayuba 1:8.
Duba yadda zaka fassara wannan a Ayuba 1:1.
"ya kasance mai sadaukarwa sosai ga yin nagarta da adalci"
''rinjayi ni ba tare ba dalili don in farmaki shi"
A nan ''hallaka'' na wakiltar ''yi talauci''. AT: ''don mai da shi talaka''
''jiki'' anan na nufin rayuwar Ayuba. AT: ''mutum zai yi komai don ceton ransa, har ma ya karɓi asarar dukiya da ƙaunatattunsa''
Shaiɗan na nufin cewa idan Yahweh ya kai hari kan Ayuba, zai ga yadda Ayuba zai mai da martani. AT: ''Amma yanzu, idan ka shimfiɗa hannunka ka taɓa ƙasusuwansa da jikinsa, za ka ga zai la'anta ka a fuskarka''
Duba yadda zaka fassara a wannan a Ayuba 01:11.
A nan ''taɓa'' na wakiltar aikin cutarwa. At: ''kai har''
Wannan na wakiltar jikin Ayuba.
Wannan na nufin a lokacin da Allah yake kula. AT: ''a cikin jin ku''
Duba yadda zaka fassara wannan a Ayuba 1:12.
''ya sa Ayuba ya wahala sosai da marurai mai raɗiɗi''
Wataƙila wannan na nufin wurin da aka zubar da datti kuma ake ƙonawa. Kasancewa a irin wannan wurin na nuna alamar baƙin ciki mai zurfi. AT: "zama akan datti''
Za a iya rubuta wannan tambaya a matsayin wata sanarwa. AT: ''Bai kamata har yanzu ku riƙe nagartarka ba''
''Ki Allah''
''kina magana da hanyar wawa mace ta yi magana''
Za a iya rubuta wannan tambaya a matsayin wata sanarwa. AT: ''Lallai ne mu karɓi mai kyau da kuma mara kyau daga wurin Allah.''
Wannan na wakiltar duk kyawawan abubuwan da Allah ya bamu.
Wannan na wakiltar munanan abubuwa da Allah yayi ko kuma ya bamu damar kwarewa.
A nan ''leɓe'' na wakiltar magana ne. AT: ''yin zunubi ta wurin magana gaba da Yahweh''
Elifaz, Bildad da Zofar sunayen mazaje ne. Teman wani birni a cikin Idom ne. Mutanen Shuh sune zuriyar Ibrahim da Ketura. Na'ama wani birni ne a Kan'ana.
'"an yarda a kan lokaci''
A nan kalmomin ''makoki tare da'' da ''ta'azantar'' na da ma'ana kusan ɗaya. Abokai sun yi ƙoƙarin ta'azantar da Ayuba ta wurin makoki da shi. AT: "don yin baƙin ciki tare da Ayuba domin ya taimaka da ya sauƙaƙa wahalarsa''
Wannan kalmar na nufin ''sun duba da kyau'' ko ''sun kalla da lura.''
Wataƙila wannan na nufin cewa abokan Ayuba basu iya gane shi da farko, da suka hango shi daga nesa. Ayuba ya yi dadan da wanda aka saba saboda damuwarsa da kuma marurai da suka rufe jikinsa. AT: ''da kyar suka gane shi''
A nan ''tada muryoyi'' na nufin sun yi ƙara. AT: ''sun yi ihu da ƙarfi'' ko ''sun yi kuka da ƙarfi''
Wannan alama ce ta baƙin ciki.
Waɗannan alamun makoki ne.
1Bayan wannan, Ayuba ya buɗe bakinsa ya la'anci ranar da aka haife shi.2Ya ce:3"Bari ranar da a ka haife ni ta lalace, kuma da daren aka ce, 'an ɗauki cikin yaro.'4Bari ranar ta zama baƙa; Dãma kada Yahweh ya tuna da ita daga sama, kada ma rana ta yi haske a kanta.5Dãma duhu da inuwar kwarin mutuwa su maishe ta tasu. Dãma girgije ya tsaya a kan ta, dãma kowanne abu mai sa rana ta yi baƙi ya ba ta tsoro da gaske.6Wannan daren kuma, dãma baƙin duhu ya rufe shi. Dãma kada ta yi farinciki a ranakun shekara; dãma kada a lissafa ta cikin kwanakin watanni.7Duba, dãma wannan dare ya zama wofi; kada muryar farinciki ta zo cikinsa.8Dãma su la'anci wannan rana, waɗanda suka san yadda a ke tashin Lebiyatan.9Dãma taurarin wayewar giri na wannan rana su yi duhu. Dãma wannan rana ta nemi haske, amma ta rasa; dãma kada ta ga ƙyallin wayewar gari,10saboda bata rufe ƙofofin cikin uwata ba, kuma domin bata ɓoye masifa daga idanuna ba.11Me yasa ban mutu sa'ad da na fito daga ciki ba? Me yasa ban saki ruhuna sa'ad da uwata ta haife ni ba?12Me yasa gwiwoyinta suka marabce ni? Me yasa nonanta suka yarda na shã su?13Gama da yanzu ina kwance shiru. Da ina barci ina hutawa14tare da sarakuna da mashawartan duniya, waɗanda suka gina wa kansu kaburbura kuma yanzu sun ruɓe.15Ko kuwa da yanzu ina kwance tare da sarakuna waɗanda dã suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.16Ko kuwa ƙila da an yi ɓari na, kamar jariran da basu taɓa ganin haske ba.17A can masu mugunta sun huta da masifa; a can masu gajjiya suna cikin hutu.18A can 'yan kurkuku sun sami saki tare; bãsu jin muryar masu kora bayi.19Manya da ƙananan mutane suna can; bawa yana da 'yanci daga wurin ubangijinsa a can.20Me yasa ake ba wanda ke cikin ƙunci haske? Me yasa a ke ba wanda ke da baƙin ciki rai,21wanda ya ƙagara yaga mutuwa bata zo ba, ga wanda yake neman mutuwa kamar ɓoyayyiyar dukiya?22Me yasa a ke bada haske ga wanda yake farinciki ƙwarai da murna idan ya sami kabari?23Me yasa a ke ba mutum wanda hanyarsa take a ɓoye haske, mutum wanda Allah ya kulle shi?24Gama ajjiyar zuciya nake yi maimakon cin abinci; an zubar da gurnanina kamar ruwa.25Gama abin da na ji tsoro ya zo kaina; abin dana tsorata yazo mani.26Ba sauƙi a gare ni, ban yi shuru ba, kuma ban huta ba; maimakon haka masifa ce take zuwa."
Wannan na nufin Ayuba ya fara magana.
Ayuba yayi maganar ranar da dare kamar dai mutane ne. AT: ''Da ma a ce ban taɓa haihuwa ba''
Wannan furcin yana ƙara faɗar maganar baƙin ciki na Ayuba ta hanyar ci gaba da komawa cikin lokaci tun daga haihuwarsa har zuwa ɗaukar cikirsa. AT: ''daren da ya ce 'an ɗauki cikin yaro' ya lalace.''
A nan ana maganar dare kamar wanda zai iya magana. Mai fassara na iya zaɓar, duk da haka, don fassara shi ta hanya mai ƙima. AT: ''daren da mutane suka ce game da shi''
Wannan na iya sanya shi cikin tsari mai aiki. AT: ''mahaifiyarsa ta ciki yaro namiji''
Kalmomin a cikin waɗannan ayoyin suna fatan cewa ranar hahuwar Ayuba ba za ta ƙara kasancewa ba. Wannan na iya nuna cewa ranar, ko da yake a baya, har yanzu ta kasance ko ta yaya.
Waɗannan kalmomin guda biyu sun bayyana duhun ranar da aka haifi Ayuba, don haka yana maimaita nadamar Ayuba da aka haifi shi.
A nan an yi duhu da inuwa mutuwa kamar dai su mutane ne da za su iya iƙirarin wani abu nasu. Kalmar ''ita'' na nufin ranar haihuwar Ayuba.
Anan ana magana girgije kamar dai mutum ne wanda zai iya rayuwa bisa ranar haihuwar Ayuba. AT: ''Dãma girgije ya rufe shi don kada wani ya gan shi''
Wannan na nufin abubuwan da ke toshe hasken rana ne da haifar da duhu. Anan ''baki'' na wakiltar duhu.
''tsorata wannan ranar.'' An yi maganar wannan ranar kamar wani mutum wanda zai iya ba shi tsoro da duhu.
Ana sake magana da wannan duhu kamar mutum ne wanda zai iya riƙe dare. AT: ''dãma baƙin duhu ya sa shi ya ɓace''
Kalmar ''ita'' na nufin ranar haihuwar Ayuba ko ɗaukar cikinsa. An yi magana akan ranar da aka yi cikin Ayuba kamar mutum da ba ya murna. AT: ''Bari wannan ranar ta ɓace daga kalanda''
Wannan daren ana maganarsa kamar dai mutum ne wanda zai iya tafiya. AT: ''kada wani ya ƙidaya shi cikin lamba"
Daren da aka haifi Ayuba ana maganar kamar mace ce. AT: ''dãma kada a haifi wani ɗa a wannan daren''
Anan cewa daren da aka haifi Ayuba ana magana kamar dai lokacin ne da har yanzu zai yiwu mutum ya yi farin ciki. AT: ''dãma kada wani ya ji muryar farin ciki cewa an haifi ɗa''
Anan muryar na nufin mutum mai farin ciki. AT: ''kada wani ya yi murna a cikin ta kuma har abada''
Wataƙila Ayuba yana magana ne game da matsafa da masu tsamo, waɗanda ya yarda zasu iya tashin Lebiyatan domin ya kawo balaƙi. Lebiyatan wani dabba ne sananne a cikin tarihin tsohuwar Bahaushe, wanda ake tunanin yana da alhakin kowane nau'i na lalacewa, cuta da hargitsi.
Wannan na nufin taurari waɗanda galibi ake iya ganinsu kafin wayewar gari. AT: "Dãma taurari da suka bayyana kafin hasken farko na wannan ranar su kasance duhu''
Ana maganar mahaifar mace kamar ganga ce wacce take da ƙofofi. AT: "domin wannan ranar ba ta rufe mahaifiyata ba''
An yi maganar ranar haihuwar Ayuba kamar dai mutum ne wanda zai iya ɓoye wani abu.
''Me ya sa ban mutu ba a sa'an haihuwa?'' Ayuba ya gabatar da wannan tambaya ne domin la'ana ranar haihuwarsa da kuma nuna baƙin cikin sa. AT: "Na so da na mutu ranar da aka haife ni''
Ayuba na nufin faɗi cewa bai kamata a haife shi da rai ba. AT: ''Na so da na mutu lokacin da na fito daga cikin uwata.''
Wannan na nufin mutuwa.
Wataƙila wannan na nufin cinikin mahaifiyar Ayuba ne. An yi maganar gwiwar uwarsa kamar dai mutane ne da za su iya maraba da sabon jariri. AT: ''Na so da a ce ba cinyar da zai karɓe ni.''
An yi maganar nunun mahaifiyar Ayuba kamar dai su ma mutane ne da za su iya maraba da jariri. AT: ''Na so a ce da ba nunun da zan sha.''
Ayuba na fara magana ne game da abin da zai kasance gaskiya ne idan ba a haife shi ba
Ayuba yayi amfani da jumla biyu yana tunani game da abin da zai zama idan bai taɓa haihuwa ba ko kuma ya mutu a lokacin haihuwa.
Ayuba yana tunanin wani abu da zai iya faruwa a da can amma wanda bai faru ba, kamar yadda muka gani a sama. AT: "Ya kamata in kwanta a natse''
''barci, hutawa cikin salama''
Anan kalmar ''hutu'' na nufin barci cikin salama, amma kuma cewa Ayuba bazai ɗanɗana jin zafin da yake yi ba.
''tare da sarakuna da mashawartansu''
Ayuba ya ci gaba da magana game da abin da zai kasance gaskiya ne idan ba a haife shi ba.
Wannan na bayyana wani abu da zai iya faruwa amma bai faru ba.
''Da ina hutawa da sarakuna.'' A cikin wannan kalmar, kalmomin ''kwance'' da ''hutawa'' wata hanya ce mai sauƙi na cewa ''ba da rai''
Ayuba yayi amfani da kalmomi masu hanun-riga domin ya nanata abin da yake fadi.
''Da na mutu a cikin mahaifiyata''
''kamar yara da ba su taɓa haihuwa ba''
''yara'' ko ''ƙananan yara''
Ayuba yayi amfani da jumla don ya nanata cewa ƙasƙantattu za su sami hutawa daga waɗanda ke damun su.
Ayuba yana zancen wurin da mutane suk e bayan daina rayuwa. AT: ''a wannan wurin, mugayen mutane sun daina haifar da matsala''
A nan, ''muryar'' na nuna ikon da masu koran bayi ke dashi akan bayi. AT: ''Ba su kuma ƙarkashin masu koran bayi''
Wannan adadin magana ne na nufin ''duk mutane, talakawa da masu arziki"
Ba dole ga bawa yayi wa maigidansa hidima
Tambayoyi biyu na Ayuba suna da ma'anar ɗaya ne. Ya na mamakin dalilin da yasa waɗanda suke fuskantar wahala suka ci gaba da rayuwa.
Anan Ayuba yana tunanin dalilin da yasa mutane dole su rayu kuma su wahala. AT: ''Ban fahimci abin da ya sa Allah ya ba da rai ga mutumin da yake wahala ba"'
Anan haske na wakiltar rai.
''me yasa Allah ya ba da wanda ke kunci rai?'' AT: ''Ban fahimci abin da ya sa Allah ya ba da rai ga mutumin da ba shi da farin ciki ... boyayyiyar dukiya''
Anan an yi maganar mutuwa kamar wani abu ne wanda yake zuwa ga wani. AT: ''ga mutumin da baya son rayuwa, amma yana raye''
Kalmar ''farin ciki kwarai'' na da ma'ana daya da ''murna''. Tare, jumlolin nan biyu na sun jaddada tnananin farin ciki. AT: "wanda ya yi farin ciki matuƙa"
Wannan ita ce kyakkyawar hanyar ishara zuwa ga mutu. AT: "lokacin da ya mutu kuma zai iya binne shi''
Anan kabari na wakiltar mutuwa.
Ayuba ya yi wannan tambayar ne domin ya ba da sanarwa. AT: ''Allah kada ya ba da rai ga mutum sa'an nan kuma ya kwashe makomarsa ya ɓoye shi."
Anan, haske na wakiltar rai. AT: "Me yasa Allah yake barin mutum da rai" (Duba: )
A nan Ayuba yana magana game da rayuwarsa, wanda bai sani a gaba, kamar dai Allah ya ɓoye shi.
Anan ana iya kasancewa da wahala da hatsarori kamar ana ancen kamar an ƙuntata mutum a cikin ƙunƙuntar wuri. (Figs_metaphor)
Anan Ayuba ya bayyana bacin rai a cikin hanyoyi biyu.
"A maimakon cin abinci, ina baƙin ciki''
Halaye na ɗabi'a da motsin rai irin su baƙin ciki yawan yin magana da su kamar ruwa ne.
Waɗannan jumla biyu suna ma'anar abu ɗaya ne. AT: "abin da na ji tsoro ya fi faruwa da ni'' ko "matsanancin tsoro na ya tabbata"
Ayuba ya bayyana bacin rai a cikin jumla guda uku. AT: "Ina makutar damuwa" ko "Ina cikin azanci da azaba ta jiki"
1Sai Elifaz Batemane ya amsa ya ce,2Idan wani yayi ƙoƙari ya yi magana da kai, baza ka yi haƙuri ba? Amma wa zai iya hana kansa yin magana?3Ka ga, ka koyawa mutane da yawa; ka ƙarfafa raunanan hannuwa.4Kalmominka sun tallafi wanda yake faɗuwa; ka sa raunanan gwiwoyi sun yi ƙarfi.5Amma yanzu masifa ta zo kanka, kuma ka gaji; ta taɓa ka, kuma ka kaɗu.6Tsoronka bai zama ƙarfi a gare ka ba, ammincinka bai ishe ka bege ba?7In ka yarda yi tunanin game da wannan: Wanda ba shi da laifi ya taɓa lalacewa? Ko a ina aka taɓa datse masu adalci?8Bisa ga abin da na gani, waɗanda suka huɗa mugunta suka shuka masifa su ke girbin ta.9Sukan lalace ta wurin numfashi Yahweh; zafin fushinsa ya kan cinye su.10Rurin zaki, muryar zaki mai ban tsoro, haƙoran 'yan zakuna --sukan karye.11Tsohon zaki yakan lalace idan ba abin da zai kama; 'ya'yan zakanya sukan warwatsu ko'ina.12An kawo mani wata matsala a asirce, kunnena ya karɓi raɗa game da ita.13Sa'annan tunanin ruya ya zo mani cikin dare, sa'adda barci mai nauyi ya zo kan mutane.14A cikin dare tsoro da fargaba suka zo mani, dukkan ƙasusuwana suka motsa.15Sai wani ruhu ya wuce a gaban fuskata, gashin jikina ya tashi tsaye.16Ruhun ya tsaya cik, amma ban iya gane baiyanuwarsa ba. Wani abu ya rufe idanuna; an yi shiru, sai na ji wata murya tace,17"Mutum mai mutuwa ya iya fin Allah adalci? Mutum zai iya fin mahallicinsa tsarki?18Ka gani, idan Yahweh bai amince da bayinsa ba; idan ya zargi mala'ikunsa da wawanci,19yaya ga waɗanda ke zama a cikin gidaje na yumɓu, waɗanda tushensu yana cikin ƙasa, waɗanda a kan mutsuke su nan da nan fiye da ƙwaro.20Tsakanin safiya zuwa yamma an hallaka su; sun lalace har abada ba abin da zai sa a tuna da su.21Ba a kan tsinke iggiyar ransu a jikinsu ba? Su mutu; su mutu ba tare da hikima ba.
Elifaz sunan mutum ne.
Batemane na wani daga kabilar Teman.
Elifaz yayi wannan tambayar domin yayi bayani. AT: "zaka yi rashin haƙuri"
Elifaz yayi wannan tambayar don ya ce duk wanda ya ga abokin da ke wahala yana iya yin shiru. AT: "Babu wanda zai iya hana kansa yin magana (ga abokin dake cikin wannan irin yanayi)" ko "Dole ne in yi magana da ku, (ganin kuna cikin halin baƙin ciki).''
Wannan ayar tana bayyana ra'ayi guda ɗaya ta hanyoyi biyu daban-daban.
Anan "raunanan hannuwa" na wakiltar mutane da ke neman taimako. AT: "ka taimaki wasu lokacin da suka neman taimako"
A cikin kowace ayoyin, marubucin ya faɗi ra'ayi guda ɗaya ta amfani da jumla daban-daban guda biyu don ƙarfafa: 1) goyon baya da Ayuba ya ba wasu baya, 2) tasirin abin da ya same shi na matsalolinsa na yanzu, da 3) taƙawarsa ga Allah.
Ana maganar wani wanda ya ƙarfafa shi kamar an hana shi faɗuwa.
Anan an yi maganar karya gwiwa kamar yana fadowa.
Anan an yi magana akan karya gwiwa kamar mutum wanda gwiwarsa bata da ƙarfin da zata tsayar da shi.
Anan ana magana masifa kamar dai abu ne wanda zai iya zuwa ga mutum. AT: "Amma yanzu kuna fama da bala'i"
"ka karaya"
"da yake kun girmama Allah"
Elifaz yayi waɗannan tambayayoyin don ya gaya wa Ayuba cewa zunubinsa ne yake shan wahala. AT: "Kowa yana tunanin kana tsoron Allah; kowa yana tunanin kai amintacce ne. Amma waɗannan abubuwab ba gaskiya bane, domin ba ku da dogara da Allah yanzu."
Anan "hanyoyinka" na wakiltar "halayenka" "yadda kake nuna rayuwa."
Elifaz yayi amfani da wannan tambayar don faɗakar da Ayuba don bincika ransa ko da zunubi
wannan tambayar na bayani ne, kuma domin a sa shi cikin aikatau. AT: "Ba wanda ya taba datse mai adalci"
Anan datse na nufin halakarwa
Anan aikin huɗa da shuka suna wakiltar haifar da matsala ga sauran mutane. Aikin girbi na wakiltar shan wahalar da mutum ya ƙirƙira.
Marubucin yayi bayanin ra'ayi guda ɗaya ta amfani da kalamai biyu daban-daban. Wannan wani irin wakoki ne na Ibraniyanci wanda aka yi amfani dashi don girmamawa, tsabta, koyarwa, ko kuma duka ukun.
Wannan na iya wakiltar aikin Allah yana ba da umarni.
Wannan na nufin da tsananin numfashi da mutum yake yi wasu lokuta ta hancinsa lokacin yana makutar fushi.
Na biyu na gini akan na farko. Suna yin magana iri ɗaya ta hanyar amfani da ma'anoni waɗanda ke ƙara sakamakon. ''Ta wurin ɓarna da bakin Allah su kan mutu; zafin fushinsa kan cinye su.''
Anan rurin zaki, muryarsa da kuma karya haƙoransa da aka karye ana amfani da su azaman hotunan yadda halakar da mugaye.
Wannan na iya sanya shi cikin tsari mai aiki. AT: "wani abu ya karyasu"
Elifaz yayi amfani da hoton tsohunwar zaki dake mutuwa saboda yunwa da kuma yadda ake warwasar da iyalin zaki a matsayin yadda halakar mugaye.
Ana yi bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "wani abu ya watsar da 'ya'yan zakin"
Waɗannan jumla suna yin bayyana ra'ayi iri ɗaya ta wata hanya daban. Sun kawo ra'ayin cewa Elifaz ya ji saƙo ya raɗa masa magana. Wannan irin nanatawa na nuna waƙoƙi na Ibraniyanci dake nuna nanatawa, koyarwa, ko fahimta.
''mafarkai"
"sa'ad da mutane suke barci mai zurfi"
Anan ana magana da tsoro da fargaba kamar dai abubuwa ne da zasu iya zuwa ga mutum. AT: "Na fara jin tsoroda rawar jiki"
Wannan na nuna tsoro sosai.
"kashin dake jikina
"Wani abu ya kasance a gaban idona," ko "Na ga wani abu"
Elifaz ya gabatar da wannan tamabyar domin in Ayuba yayi la'akari, "Zan ɗauki kaina mai adalci fiye da Allah?" ko "Ina barata a gaban Allah?" AT: "Dan Adam ba zai iya zama mafi adalci fiye da Allah ba" ko "Dan Adam ba zai iya zama adalci a gaban Allah."
Wannan tambaya na da manufa iri ɗaya da tambayar da ta gabata. AT: "Mutum ba zai iya zama tsarkakakke fiye da Mahalicinsa ba." ko "Mutum ba zai iya zama tsarkaka a gaban Mahalicinsa ba."
Wannan karin magana ne wata hanya ce ta kwatanta mutane, waɗanda aka halitta daga turɓayar ƙasa kuma jikinsu kamar gidaje ne, waɗanda aka yi su da yumɓu kuma suna da tushen ƙazanta.
Ma'anar mai yiwuwa ga wannan bayyanin ita ce 1) "wanda Allah ke halaka da sauƙi kamar yadda yake mutsuke ƙwaro" ko 2) waɗanda rayuwansu ƙalilanne kamar na ƙwaro."
Wannan na nufin ra'ayin wani abu ya faru nan da nan.
Hakanan zai iya sanya wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "sun mutu"
Wannan na iya sanya wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ba maƙiyansu sun tsinka iggiyar ransu daga cikinsu?"
Anan iggirar ransu na wakilta tanti. Wani lokacin ana ɗaukar hoto na gidan mutum da iyalinsa a kamar tantinsa, wanda kuma yana iya wakiltar duk mallakarsa.
1Ka yi kira yanzu; akwai wani mai ansa maka? Ga wanne cikin masu tsarkin zaka juya?2Gama fushi ya kan kashe wawan mutum; kishi yakan kashe dolo.3Na ga wawan mutum yana kahuwa, amma nan take na la'anci gidansa.4Zaman lafiya yana nesa da 'ya'yansa; an murƙushe su a ƙofar birni. Ba wanda zai kuɓutar da su.5Mayunwaci ya kan cinye anfaninsa dukka; sukan ma ɗauko shi daga cikin ƙayayuwa. Masu jin ƙishi suna hãki domin dukiyarsu.6Gama wahala bata fitowa daga cikin turɓaya; masifa kuma bata fitowa daga cikin ƙasa.7Maimakon haka an haifi mutum saboda masifa, kamar yadda tartsatsi yakan tashi sama.8Amma a gare ni, zan juya wajen Allah shi da kansa; a gare shi zan danƙa al'amurana--9shi wanda ke yin manyan al'amuran da ba a iya ganewa, abubuwan mamakin da basu lissaftuwa.10Yakan bada ruwa a kan ƙasa, yakan aika da ruwa bisa filaye.11Yakan yi haka ne domin ya tada ƙasƙantattu; yasa masu baƙin ciki su zauna lafiya.12Yakan lalata shirye--shiryen masu yaudara, domin kada su kai ga cika manufarsu.13Yakan kama mutane masu wayo cikin aikin yaudararsu; da sauri shirye--shiryen masu murɗiya sukan zo ƙarshe.14Dare kan same su da rana, sukan yi lalube da rana sai kace dare ne.15Amma ya kan ceci mutum matalauci da takobi cikin bakinsu mabukata kuma daga hannun ƙarfafan mutane.16Domin mutum matalauci ya sami bege, rashin adalci kuma ya rufe bakinsa.17Duba, mai albarka ne mutumin da Allah yakan hore shi; saboda haka kada ka rena horon Mai Iko Dukka.18Gama yakan sa a ji ciwo yayi magani, ya kan sa a ji rauni hannunsa kuma ya warkar.19Zai kuɓutar da kai daga masifu shida; hakika, a cikin masifu bakwai, babu muguntar da zata taɓa ka.20A cikin yunwa zai fanshe ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma daga hannun takobi.21Za a ɓoye ka daga la'anar harshe; ba zaka ji tsoron hallaka ba ko ta zo.22Zaka yi dariya a kan hallakar yunwa, ba zaka ji tsoron namun jeji na duniya ba.23Gama zaka yi alƙawari da duwatsu a gonarka, namun jeji na gona zasu yi zaman lafiya da kai.24Zaka sani rumfarka tana lafiya; zaka ziyarci garken tumakinka ba kuwa zaka rasa kome ba.25Zaka kuma sani irinka zai yi girma, tsatsonka zasu zama kamar ciyawa a kan ƙasa.26Zaka je kabari da tsufanka, kamar zangarkun damin hatsi da suke tafiya a lokacinsa.27Ka gani, mun yi binciken wannan lamari; ga kamanninsa, ka saurare shi, ka san shi kai da kanka."
Elifaz ya gabatar da wannan tambayar don ya nuna cewa babu wani Ayuba da zai iya juya baya don neman taimako. AT: ''Shin akwai wani mai tsarki wanda zaka juya gareshi?" ko "Babu wani mai tsarki wanda zaku nemi taimako wurinsa"
Wannan na nufin halittu na allahntaka na wasu irin, ko malaiku.
Anan an yi maganar mutum kamar shuka ne, wataƙila ya zama wawanci akan lokaci. AT: "wawa mutum kan ƙara dulmiya cikin wawancinsa"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da amfani da kalamai masu hanun riga, a nan suna nanatawa ta hanyoyi daban-daban ra'ayin cewa 'ya'yan wawaya ba su da wata matsala.
"Nesa" na nufin wawan mutu ko wawayen mutane a Ayuba 5:2. AT: "Ba salama ga 'ya'yansa"
"Babu wanda zai iya taimakon 'ya'yan wawaye a cikin wahalarsu"
A nan an yi maganar mutane masu haɗari kamar dai suna jin ƙishirwa, kuma arzikin wawaye kamar abin da za su iya sha.
A nan ana maganar game da wahala da masifa kamar suna tsirai.
Yana da dabi'a ga mutane, da zarar an haife su, don samun matsala kamar yadda ake don ƙyalƙyali su tashi daga wuta.
"abubuwa masu girma waɗanda ba za a fahimta ba, abubuwan al'ajabi da ba za a iya ƙidaya su ba"
Ana magana da mutane masu ƙasƙantar sa kai cikin wahala kamar suna cikin ƙasƙantar da kansu. Lokacin da Allah ya kuɓutar da su, suna karɓar girma. Lokacin da wannan ya faru, ana magana da su cewa ana tashe su kuma an saka su cikin babban matsayi. AT: "Allah yana yin hakan domin ya ceci kuma ya ɗaukaka masu tawali'u da ke wahala"
Anan ana sa masu hikima su wahala saboda muguntar da ake yi kamar ana kama su da tarko. Ayyukan da kansu suke yi suna magana kamar dai waɗancan tarko ne.
Anan ana amfani da mayaudara, mugayen mutane waɗanda Allah ya rikitar da su kamar suna tsammani suna cikin duhu da tsakar rana, lokacin da rana take a ƙarshen sararin samaniya. Ba za su iya yin wani abin da suke so su yi ba, domin ba za su iya gani ba. AT: "Waɗanda ke da dabara suna cikin duhu, ko da tsakar rana"
Anan maganganu na zagi da tozartarwa da mutane ke fada ana kamar dai da takobi a bakinsu. AT: "Amma ya ceci matalauta daga barazanar masu iko" ko "Amma ya ceci matalauta lokacin da mai girman ya yi masu barazanar ko yi musu zagi"
Mutanen da suke faɗi abubuwa marasa gaskiya ana maganarsu kamar dai su ne zalunci da kanta, waɗanda dole ne su daina magana. AT: "Kamar dai rashin adalci ne ke rufe bakinta"
An kwatanta Allah kamar yadda mahaifa yake gyara ko koyar da yaro.
"Domin yana jin rauni amma ya ɗaura shi; yana murƙushe amma hannunsa ya warkarwa"
Amfani da kara lambobi kamar "shida" da "bakwai" yana wakiltar ra'ayin da yawa, sau da yawa. AT: "Zai ƙuɓutar da kai daga masifu sau da sau; haƙiƙa, lokaci bayan lokaci, babu muguntar da zata taɓa ka"
Anan ana maganar fansa kamar sayen baya. AT: "A cikin yunwar, Allah zai ƙuɓutar da kai daga dukan wani hatsari"
Anan "hanu" tabbas na wakiltar mutanen da suke kai hari tare da makamai, game da takubba. AT: "mutane masu tashin hankali" ko "mutane da suka kai maka hari"
Anan "dariya" na wakiltar cewa mutumin baya jin tsoro. AT: "Ba za ku ji tsoron kowani irin hatsari mai hallakarwa ko yunwa ba"
Anan "rumfa" na wakiltar iyalin mutum, dangi da dukan mallakarsa. AT: "Za ku sani cewa iyalinka, bayinka, da duk abin da kuka mallaka naka na lafiya"
"Idan kun ziyarci garken tumakinka a dare, za ku sami duk suna nan"
Anan "tsatsonka" na wakiltar zuriyar mutum ne. AT: "zuriyanka za su yi yawa"
"Za ku mutu da tsufanku"
Kalmomin "mu"na nufin abokan Ayuba amma ba Ayuba ba. AT: "Duba, mun yi tunani game da wannan al'amarin. Ka saurari abin da nake faɗi ka kuma sani cewa gaskiya ne"
1Sa'an nan Ayuba ya amsa ya ce,2"Oh, da dai an auna nauyinbaƙin cikina; da dai an sa wahalata a ma'auni!3Gama yanzu za tafi yashin tekuna nauyi. Shi yasa nake magana barkatai.4Gama kibawun Mai Iko Dukka suna cikina, ruhuna yana shan dafin; razana daga Yahweh ta shiryo kanta gãba da ni.5Jakin jeji yakan yi hargowa inda yana da ciyawa? Sã yakan yi kuka ga abinci a gabansa?6Za a iya cin abin da ba shi da ɗanɗano ba tare da an sa masa gishiri ba? Ko akwai ɗanɗano ga farin ƙwai?7Na ƙi taɓa su; suna kama da abinci mai gundura a gare ni.8Oh, dãmã za a amsa mani roƙona; oh, dãma Yahweh zai yarda in sami abin da nake ta nema in samu:9dãma Yahweh zai yarda ya ruƙurƙushe ni kawai, dã zai saki hannunsa ya datse ni daga wannan rayuwa!10Bari wannan ya zama abin ƙarfafa ni--ko da ciwona ya ƙaru bai ragu ba: ban yi musun maganar mai tsarki ba.11Menene ƙarfina, da zan yi ƙoƙarin jira? mene ne ƙarshena, da zan ci gaba da rayuwa?12Ƙarfina kamar ƙarfin dutse yake? Ko an yi jikina da tagulla ne?13Ba gaskiya ba ne cewa ba ni da taimako a cikin kaina ba, kuma an kori hikima daga cikina?14Mutumin da ya kusa suma, ya kamata abokansa su ji tausayinsa; ko da ya watsar da jin tsoron Mai Iko Dukka.15Amma 'yan'uwana sun zama da aminci kamar hamadar da kan ƙafe, kamar magudanar ruwa marar anfani da ke wucewa a magudanai,16waɗanda sukan yi duhu saboda ƙanƙara ta rufe su, kuma saboda dusar ƙanƙara da ta ke a cikin su.17Idan su ka ji ɗumi sai su, sai su ɓace; idan zafi ya zo, sai su narke a inda suke.18Fataken da ke bi ta wurinsu sukan ruƙa neman ruwa; sukan yi garari a busasshiyar ƙasa su lalace.19Fatake daga Tema sun duba can, fatake daga Sheba sun sa bege a cikin su.20Sun kunyata saboda sun gaskata zasu sami ruwa. Sun je wurin, amma an ruɗe su.21Gama yanzu ku abokai baku da anfani a gare ni; kun ga takaicin da nake ciki kun ji tsoro.22Nace da ku, 'ku bani wani abu ne?' Ko ku bani wani abu daga dukiyarku?'23Ko ku cece ni daga hannun maƙiyina?' Ko ku fanshe ni daga hannun mai tsananta mani?'24Ku koya mani, ni kuwa zan yi shiru; ku ganar da ni inda ban yi dai-dai ba.25Gaskiya dai ɗaci gare ta! A ina gardandaminku suka ga laifina?26Kun yi shirin ku watsar da maganata, ku ɗauki maganar mutumin da yake cikin wahala kamar iska?27Tabbas, kun jefa ƙuri'a a kan ɗan da bashi da uba, kun mai da aboki abin samun riba.28To, yanzu, idan kun yarda ku dube ni, gama tabbas ba zan yi ƙarya a gaban kuba ba.29Ku dena magana haka, na roƙe ku; kada kuyi rashin gaskiya; hakika ne, ku dena yin haka, hakika ina da gaskiya a al'amarina.30Akwai mugunta a kan harshena ne? Bakina ba zai iya ganewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
Anan marubicin yayi amfani da magana iri biyu don isar da ra'ayi guda ɗaya, nauyin wahalar Ayuba. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "da a ce zan iya auna baƙin ciki na da kuma dukan matsalolina akan ma'auni"
Anan Ayuba ya kwada nauyin wahalarsa da da nauyin yashin rigar; duka suna iya murƙushe mutum. AT: "Domin baƙin cikina da matsalolina sun fi ƙasa na baƙin teku nauyi"
Wannan wata kalma don wahalar Ayuba. Ya kwatanta masa dimbin matsalolin sa da kiban da Allah ya buge jikinsa da shi. AT: "Kamar dai Mai Iko Dukka ya harba kibayoyi a cikin jikina"
Ayuba ya yi magana game da mummunan abin da ya same shi kamar dai sojojin da Allah ya shirya su kai masa hari gaba ɗaya. AT: "Allah ya sa dukan mugayen abubuwa da suke faruwa su faru da ni gaba ɗaya"
Ayuba ya gabatar waɗannan tambayoyi na magana don ya nanata cewa yana da dalilin yin gunaguni. Waɗannan tambayoyi ana iya rubuta su azaman kalamai. AT: "Kamar yadda jakin daji ba ya hargowa idan akwai ciyawa, kuma kamar yadda sa ba ya ƙoshin yunwar idan yana da abinci, ba zan yi gunaguni ba ni da dalili"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Zaka iya cin abin da bashi da ɗanɗano"
"Su" na nufin abinci mai ɗanɗano
Wannan na nufin Allah ya sa ya mutu. AT: "ya ragargaza ni ya bar ni in mutu"
Kalmonin "saki hannunsa" karin magana ne da take nufin a yi da sauri. Hakanan, kalmar "datse ni daga wannan rayuwa" wata hanyar tausasa magana ne dake nufin a kashe shi. AT: "cewa zai yi sauri kuma ya gaji da raina" ko "cewa zai yi sauri kuma ya kawo ƙarshen raina" (Duba: da figs euphemism)
"ban yi musun sanin Allah ba." Ana iya rubuta wannan cikin a tabbatacce hanya. AT: "A koyaushe na yi biyayya ga Mai Tsarki"
Ayuba ya gabatar da waɗannan tambayoyin don jaddada cewa ba shi da dalilin ci gaba da rayuwa. Waɗannan tambayayoyin suna da ma'anar iri ɗaya. Za a iya rubuta wannan a matsayin kalamai. AT: "Ba ni da isasshen ƙarfi don ci gaba rayuwa ba; ba ni da dalilin tsawanta rayuwata"
Ayuba ya bayyana raunin jikinsa da cewa ba shi da ƙarfi kamar dutsen da tagulla don ƙarfafa rashin ƙarfinsa. Wadannan tambayoyin anan iya rubuta su azaman kalamai. AT: "Ba ni da ƙarfi kamar duwatsu. Jikinsa ba shi da ƙarfi kamar ƙarfe."
Ayuba yayi amfani da wannan tambaya don ya nanata rashin hikimarsa da kuma rauninsa. Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. Hakanan, kalmar "ba taimako a cikin kaina" karin magana ne. AT: "Gaskiya ne cewa bani da sauran ƙarfin da ya rage ... ni"
Ana iya bayyana wannan acikin tsari mai aiki. AT: "Aboki ya kamata ya kasance mai aminci ne ga mutumin da ya ji cewa game da kusan suma"
Ayuba yayi maganar akana rashin amincin abokansa kamar "wadi" wanda rafin dake iya bushewa. Hakanan, Ayuba yana nufin abokansa a nan kamar "'yan uwansa." AT: "Amma abokaina marasa aminci a gare ni. Suna kama da bushe rafi a hamada"
Waɗannan jumla guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. Sun bayyana yadda rafi ke cike ƙanƙara da dusar ƙanƙara a cikin hunturu. AT: "waɗanda suke kama da duhu a cikin hunturu domin an rufe da ƙanƙara kuma suna cike da dusar ƙanƙara"
"Babban rukunin matafiya sun juya daga kan hanyoyinsu domin neman ruwa" ko " Babban rukunin matafiya sun canza hanya don neman ruwa"
Fatake ne babban rukuni na matafiya masu hawa raƙuma a cikin hamada.
Waɗannan sunayen wurare ne. Mutanen waɗannan wuraren suna amfani da fatake domin yin kasuwanci da mutane tare da wasu wurare.
Za iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "amma an karya masu gwiwa" ko "amma basu ƙoshi ba"
Ayuba yana amfani wannan kalmar don gabatar da babban ɓangaren abin da yake faɗi.
"ku abokai ba ku taimaka ni komai ba"
Ayuba yana amfani da waɗannan tambayoyin don jaddada cewa bai nemi abokansa su ba shi komai ko kuma su taimaka masu.
Wannan karin magana ne. AT: "Zan yi shiru"
Hakikanin ma'anar wannan jumla a cikin yaren asali ba ta tabbas. AT: "Idan mutum ya faɗi gaskiya, baya ji wa kowa."
Ayuba yana amfani da wannan tambayar don tsauta wa abokansa da kuma nanata cewa abin da suke faɗa ba shi da amfani a gare shi. An iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Dalilanku na tsawata mini ba su da amfani gare ni ko da yake kuna tsawata mini da ƙarfi" ko "Amma maganarku game da ni ba gaskiya ba ce, don haka ba sa tsawata mini!"
Ayuba yana amfani da wannan tambayar don tsauta wa abokansa. Ya kwatanta kalmominsa da iska don bayyana cewa abokansa suna yin kamar kalmominsa babu komai kuma marasa amfani. AT: "Kuna watsi da maganata! Ni mutum ne mai matsananciyar wahala, kuma kuna ɗaukar maganata kamar ba su da amfani kamar iska."
Anan "ka" da "na" na nufin mutum na biyu.
Wannan yana kwatanta yadda mutum zai siyar da abokinsa kamar yadda mutum yake sayar da kayan sayarwa.
Kalmar "ku" na nufin abokan Ayuba. A nan abokansa suna wakiltar fuskokinsu don jaddada cewa suna kallon sa. AT: "Ba zan yi muku ƙarya ba sa'ad da na ke duban ku"
"Ina roƙonku ku yi mani jinkai" ko "ku daina magana haka, ina roƙon ku"
Za a iya rubuta wannan azaman sunarwa tabbatacce. AT: "ku yi mani dai-dai"
"Shin ina faɗi mugayen abubuwa ne?" Ayuba yayi amfani wannan tambayar don tsauta wa abokansa kuma ya nanata cewa shi ba mugu ba ne. Za'a iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ba na faɗi mugayen abubuwa"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don tsauta wa abokinsa kuma ya nanata cewa zai iya faɗi bambanci tsakanin magarta da mugunta. Anan Ayuba yana nufin kansa ta bakin"bakinsa" don jaddada maganarsa, Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Na san abin da ke dai-dai in faɗi da abin da ba dai-dai ba faɗi."
1Ba wani mutum da ya taɓa yin aiki mai wuya ne a duniya?2Ashe kwanakinsa ba kamar na ɗan ƙwadago suke ba? Kamar bawan da ya ƙosa yamma ta yi, kamar ɗan ƙwadago mai neman haƙƙoƙinsa -3don haka an sa ni in jure da watannin wahala; An ba ni kwanaki cike da wahala.4Sa'ad da na kwanta, sai in ce da kaina, 'Yaushe zan tashi kuma yaushe gari zai waye? Ina ta juye-juye har sai gari ya waye.5Jikina yana cike da tsutsotsi da sanyin ƙasa; gyambunan jikina sukan bushe sai kuma su fashe su zama sababbi.6Kwanakina sun fi kibiya sauri; sukan wuce ba bege.7Allah ya tuna raina numfashi ne kawai; idona ba zai ƙara ganin alheri ba.8Idon Yahweh, da ke gani na, ba zai ƙara gani na ba; idanun Yahweh za su dube ni, amma ba zan kasance ba.9Kamar yadda girgije yakan ɓace, haka wanda ya je Lahira ba zai ƙara fitowa ba.10Ba zai ƙara dawowa gidansa ba.; wurinsa ba zai ƙara sanin sa ba.11Saboda haka ba zan kama bakina ba; zan yi magana cikin zafin rai a ruhuna; zan yi gunaguni cikin ɗacin raina.12Ni teku ce ko ni dorina ce da kuke tsaro na?13Idan nace, 'gadona zai yi mani ta'aziya, shimfiɗata zata sa in ji sauƙi,'14sai ka firgita ni da mafarkai ka sa in ji tsoro da wahayoyi,15har na kan so a maƙare ni in mutu da a raya ƙasusuwana.16Na rena rayuwata; bana marmarin in rayu koyaushe; ku ƙyale ni gama kwanakina basu da anfani.17Mene ne mutum har da zaka lura da shi, da zaka sa hankalinka a kan sa,18da zaka lura da shi kowacce safiya ka gwada shi kowanne lokaci?19Sai yaushe zaka dena dube na, kafin ka bar ni ni kaɗai in samu in haɗiyi yawuna?20Ko dana yi zunubi, me zaka yi da ni, kai da kake tsaron mutane? Me yasa ka sã mani ido, har da zan zama matsala a gare ka?21Me yasa ba zaka yafe laifofina ka ɗauke muguntata ba? Gama yanzu zan kwanta a cikin turɓaya; zaka neme ni a hankali, amma ba zan kasance ba."
Ayuba ya gabatar da wannan tambayar mara kyau don jaddada wayewar sa cewa mutane duka suna fuskantar aiki tuƙuru. Ana iya fassara shi azaman tabbataccen bayani. AT: "Akwai aikin tuƙuru ga kowane mutum a duniya."
Ayuba ya gabatar da wannan tambayar mara kyau don jaddada wayewar sa cewa duk mutane suna gwagwarmaya a rayuwa. AT: "Kwanakinsu kamar ran wani ma'aikaci ne"
"jiran a biya shi
Wannan za a iya fassara shi a cikin mai aiki. AT: "don haka na jure tsawon watanni na wahala; Ina samun dare cike da matsala"
Bayanin da aka nuna shi ne cewa lokacin da Ayuba zai yi barci da daddare. AT: "Lokacin da na kwanta barci"
Ayuba na nuna cewa yana shan tsani a lokacin da ya kamata yana barci. AT: "Na so a ce zan iya tashi amma gari ya ƙi wayewa."
"ina ta juyawa gaba da baya." Wannan yana nuna cewa Ayuba ya ta motsi a gadonsa dukan dare ba tare da hutawa ba.
an bada hoton tsutsotsi da sanyin kasa kamar riga da ya rufe Ayuba.AT: "An rufe jikina da tsutsotsi da ƙurar ƙasa kamar riga"
Wannan na nufin dukan jiki. AT: "Jikina"
Ma'anar mai yiyuwa ita ce 1) dunƙule ko datti ko 2) tabbai a jiki.
Ayuba ya gwada rayuwarsa da saurin allurar saƙa. AT: "Rayuwana na tafiya da sauri"
"tunawa." Wannan kalmomin "ya tuna" ba ya nufin Allah ya manta ba. Ayuba yana roƙon Allah ya duba ko tunani game da gajeriyar rayuwar Ayuba.
Ayuba ya gwada ƙarancin rayuwarsa kamar da gajeruwar numfashi. AT: "raina yana gajeru, kamar ɗaukar numfashi ɗaya"
Anan "idona" na wakiltar duk mutumin Ayuba ne da iyawarsa na gani ko fuskantar abubuwa. AT: "Ba zan sake fuskantar kyawawan abubuwa ba"
Anan Allah yana wakiltarsa da "idanunsa" don jaddada abin da yake kallo. AT: "Allah wanda ya dube ni ... Allah zai neme ni".
Za'a iya bayana wannan a kalmar aikatau. AT: "kamar yadda girgije yake wucewa"
Ayuba yana kwatanta mutuwa kamar girgije da suke wucewa.
"wanda ya mutu ba zai dawo ba"
Wannan kalman "wurinsa" na wakiltar wadanda suke zaune a wurinsa. AT: "mutane da ke zama a wurinsa" ko "iyalinsa"
Anan bakin yana wakiltar magana. AT: "Ba zan hana magana na ba"
"cikin damuwar ruhunana" ko "cikin azabar wahalata". Ana iya fassara wannan kalman "baƙin ciki" ta amfani da wannan "damuwa AT: "lokacin da ruhuna ya damu"
Anan ana maganar baƙin ciki kamar ya ɗanɗani danshi mai daci, kuma "kurwa" tana nufin mutum ne duka. AT: "da fushi da kiyayya"
Ayuba ya gabatar da wannan tambayar don nuna fushinsa ga Allah. A kwatanta kansa da bakin teku ko kuma dodon teku, Ayuba ya ba da shawara cewa Allah ya ɗauke shi wani abu ne mai ban tsoro. Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Ni ba teku bane ko dodon teku na wanda ke buƙatar mai tsaro don kallon shi"
"ka" anan na nufin Allah
Anan Ayuba yayi amfani da kalmar "ƙasusuwa" yana nufin jikinsa. AT: "Wannan jikina"
"ina ƙin raina"
"kwanakina ba su da ma'ana" ko "kwanakina raina sun zama wofi"
Ayuba ya yi wata tambaya mai magana don ya ce bai fahimci abin da ya sa Allah zai kula da mutane ba. Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Gaya mani wanene mutum da ... kowani lokaci."
Anan "lura" na wakiltar tunani da maida hankali. AT: "Maida hankali a kansa"
Anan Ayuba yayi isar da tunani guda daya ta amfani da tambayoyi biyu daban-daban don ƙarfafa begensa cewa Allah zai daina kallonsa. AT: "Ka nisantar da ni! Ka bar ni kyale ni na don ya ishe ni in hadiye miyau!"
Ayuba ya gabatar waɗannan tambayoyin don jayayya da Allah game da yi masa rashin adalci. AT: "Ko da na yi zunubi, hakan ba zai yi maka komai ba, yayin da kake lura da mutane."
Anan Ayuba yayi amfani da wasu kalamai biyu domin ya nanata nufinsa. Ma'anar mai yiyuwa ita ce: 1) Ayuba yana tambaya me yasa Allah bai yafe masa ba. AT: "Faɗa mini dalilin da ya sa ba ku yafe mini lamuran ku kuma ku kawar da zunubaina." ko 2) Ayuba yana roƙon Allah me yasa ba zai iya yin watsi da kuskurensa da ake zaton ya yi ba. AT: "Faɗi mini dalilin da ya sa ba ku ɗauka game da ƙetare iyaka da mugunta ba ba."
Wannan kalman "zauna cikin turɓaya" alama ce da ke nuna mutuwa ne. AT: "yanzu zan mutu"
"Ba zan kasance nan ba" ko "Zan tafi"
1Sa'an nan Bildad Bashune ya amsa ya ce,2"Har yaushe zaka yi ta faɗin waɗannan abubuwa? Har yaushe maganar bakinka zata zama iska mai ƙarfi?3Ko Allah yana ɓata shari'a ne? Ko Mai Iko Dukka yana ɓata adalci ne?4'Ya'yanka sun yi masa zunubi; mun san wannan, gama ya bashe su a hannun zunubansu.5Dama ace ka jure da neman Allah da miƙa roƙonka ga Mai iko dukka.6Idan da kana da tsarki da aminci, to da babu shakka da ya tashi da kansa a madadin ka ya dawo da kai inda ya kamace ka.7Ko da yake ka farkonka kaɗan ne, har yanzu matsayin ƙarshenka ya fishi girma ƙwarai.8Idan ka yarda ka tambayi mutanen dã, ka mai da hankali a kan abin da ubanninmu suka koya.9(Jiya a ka haife mu kuma bamu san kome ba saboda kwanankinmu a duniya inuwa ne).10Baza su gaya maka ko su koya maka ba? Baza su yi magana daga zuciyarsu ba?11Tsire-tsire kan iya yin girma inda ba laima? Iwa ta iya yin girma ba tare da ruwa ba?12Tun suna da korensu ba tare da an sare su ba, zasu riga kowacce shuka bushewa.13Haka kuma hanyoyin dukkan wanda ya mance da Allah; begen wanda bashi da halin kirki zai lalace.14Gabagaɗinsa zai lalace, bangaskiyarsa bata da ƙarfi kamar yanar gizo take.15Ya dogara ga gidansa, amma ba zai tallafe shi ba; ya riƙe shi, amma bai tsaya ba.16A ƙarƙashin rana kore ne shi, rassansa sukan rufe lambunsa dukka.17Tarin duwatsu sun rufe sauyoyinsa, sukan nemi wurare masu kyau cikin duwatsu.18Amma idan aka hallaka wannan mutum daga wurinsa, sa'an nan wannan wurin zai yi musun sa yace, 'Ban taɓa ganin ka ba.'19Duba, wannan ne "farinciki" na mutum mai irin wannan hali; waɗansu shuke--shuken zasu fito a wannan ƙasar a wurinsa.20Duba, Allah ba ya jefar da mutum marar laifi; kuma ba ya kama hannuwan masu aikin mugunta.21Zaya sake cika bakinka da dariya, leɓunanka kuma da sowa.22Kunya zata rufe maƙiyanka; rumfar masu mugunta zata lalace har abada."
A wannan surar, Bildad ya fara magana game da gunaguni da Ayuba ya yi.
"Bildad" sunan mutum ne wanda dan ƙabilar Shuah. (Duba: translate names)
Bildad yayi maganar kalmomin Ayuba kamar babu komai a cikin su kamar iska. Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Kalmomin bakinka ba su da mahimmanci kamar iska mai ƙarfi."
Anan "Allah" da "Mai Dukka Ikoi" su na nafin Yahweh. Ana iya fassara waɗannan tambayoyin azaman sanarwa. AT: "Allah baya ɓata sharia; Mai Dukka Iko baya ɓata adalci"
Anan "hannun" yana wakiltar iko ko sakamakon zunubi. Bildad ya nuna cewa Allah ya kashe 'ya'yan Ayuba ne saboda zunubansu. AT: "gama Allah ya sa sakamakon zunuban 'ya'yanka ya kashe su"
Waɗannan jumlolin guda biyu suna nufin Ayuba na roƙon Allah don neman taimako ko roƙon Allah don jinƙai.
"Da a ce kun kasance tsarkakakku, masu idalci" ko "Idan da za ku yi wa Allah biyayya kuma ku aikata abin da yake dai-dai"
Wannan na nufin a dawowa Ayuba abubuwan da ya rasa, har da iyalinsa, dukiyarsa da darajarsa.
A nan rashin wadata ana maganar rdashi da kasancewa "karamin farawa". AT: "Ko da kun kasance matalauta a farkon rayuwar ku, Allah zai mayar da ku wadata a cikin rayuwar ku"
"yi nazarin abin da ubanninmu suka gano" ko "yi la'akari da abubuwan da iyayenmu suka koya."
Ana manganar gajeriyar rayuwa kamar inuwa ce wacce take bacewa da sauri.
Bildad yayi amfani da waɗannan tambayoyi don tsauta wa Ayuba saboda rashin yarda da Bildad da magabatan. Ana iya fassara su azaman kalamai. AT: "Za su koya muku kuma su faɗa muku kuma su faɗi abin da suka yi imani da gaskiya"
Anan "zuciya" na wakiltar abin da suka yarda da shi. AT: "wanda suka yarda da shi ainun"
Bildad ya yi amfani da waɗannan tambayoyin masu haɗa kai don ƙarfafa aya guda ɗaya cewa mutane ba za su iya rayuwa ba tare da Allah ba. Anan tsire-tsire suna wakiltar mutane kuma ruwan yana wakiltar Allah. Ana iya fassara wannan tambayoyn azaman kalamai. AT: "Tsire-tsire na fafiirus ba zai iya yin ƙasa daga gurbar ruwa ba"
Ana nufin zasu bushe domin rashin ruwa. Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "Saboda rashin ruwa sukan yanƙwane su daina girma fiye da kowani irin tsiro, ko da ba wanda ya sare su"
"bushewa"
Anan "hanyoyin" na wakiltar makomar mutum da abin da zai same da shi. AT: "Abu ɗaya zai same dukan waɗanda suka manta da Allah"
"abubuwan da mutumin marasa ibada suke so ba zai faru ba"
Waɗannan kalmomin biyu suna ma'ana dai-dai kuma suna ƙarfafa cewa mutumin bautar yana dogara ga abin da ba zai iya cetonsa ba.
Anan Bildad ya kwatanta dogara mara tsoron Allah kamar yanar gizo take; yar turi sai ya ɓace. (Duba: figs:simile)
Wannan magana mai yi yiyuwa tana nufin mutumin da ya dogara ga dukiyarsa da arzikinsa ne don tsaro. Idan haka ne, to "gida" a nanyana wakiltar dukiyar da mallaka mai shi. AT: "Yana tunanin ba shi da wata matsala saboda yana da arziki, amma ba zai sami lafiya ba"
Anan Bildad yana kamata mutumin da mara tsoron Allah da skuka mai lafiya.
Ba a bayyana ma'anar wannan a cikin juyin Ibraniyanci. Ma'anar mai yiyuwa ita ce 1) yana da koshin lafiya da rana ko 2) ana shayar dashi kafin rana tayi.
Waɗannan kalmomin guda biyu na da ma'ana ɗaya, amma ma'anar bata fito ba. Ma'anar mai yiyuwa ita ce 1) ya kafu a cikin duwatsu, yana amfani da duk wata dama ko 2) tsauyoyinsa sun kasa samun ingantaccen ƙasa dole ya nemi sinadarai a cikin duwatsu.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "idan wani ya fitar da shi daga wurinsa" ko "idan manumi ya tumɓuke shi daga cikin gonar"
"wuri mai duwatsu" ko "gonar"
Ana maganar gonar kamar yana dai yana da ikon ɗan adam yayi magana. Nan da nan gonar kan manta cewa ya wanzu.
Bildad yana magana da bakin karfe don bayyana cewa babu wani farin ciki na gaske ga mutumin ba da tsoron Allah ba. AT: "wannan shi ne dukkan farin cikin da zasu samu yayin ayyukan su na marasa bin Allah"
Bildad ya ci gaba da magana daga Ayuba 8:6-17. Sauran mutane marasa tsoron Allah anan magana dasu kamar tsire-tsire waɗanda ke maye gurbin wanda bautar Allah na farko da ya mutu. AT: "lokacin da mugu ɗaya ya mutu, wani zai maye wurinsa"
Wannan za a iya bayyana azaman sanarwa tabbatacce AT: "Allah zai karɓi mara laifi"
Anan "kama hanu" yana nufin tamaiko ko tallafi. AT: "Allah ba zai taimaki mugayen mutane ba"
Waɗannan kalmomin guda biyu suna ma'ana dai-dai kuma suna nanata yadda Ayuba zai yi farin cikin idan ba shi da laifi. Kalmar "shi" tana nufin Allah kuma "ka" yana nufin Ayuba. AT: "Allah zai sake sa ku farin ciki idan kunkasance ba ku da laifi"
Ana ana cewa "kunya" kamar dai ita ce tufafin da Allah zai sa maƙiyan Ayuba su sa. Wannan yana nufin za su ji kunya sosai. AT: "Allah zai sa waɗanda suka ƙi ku su ji kunya sosai"
Anan "rumfa" tana nufin gidajen mugaye. AT: "za a lalata gidajen mugaye"
"ba zai dawama ba" ko "zai hallaka"
1Sa'an nan Ayuba ya amsa yace,2"Gaskiya ne haka yake na sani. Amma yaya mutum zai iya zama dai-dai wurin Allah?3Idan yana so yayi gardama da Allah, a cikin dubu ba zai iya amsawa ko sau ɗaya ba.4Allah mai hikima ne kuma mai ƙarfi ne; wane ne ya taɓa yin jayayya da shi yaci nasara5shi wanda yake cire duwatsu ba tare da gargaɗi ba yakan birkice kowannen su a cikin fushinsa--6shi wanda yake girgiza duniya daga wurinta yasa ginshiƙanta su raurawa.7Shi ne Allahn nan wanda yakan ce da rana kada ta fito, kuma ba ta fito ba, shi wanda ya kan lulluɓe taurari,8shi wanda yakan miƙar da sammai da kansa ya tattaka raƙuman ruwan teku,9shi wanda ƙungiyoyin taurari da zara da gamzaki da mafarauci da kare da zomo da kuma kaza da 'yayanta, gungun taurarin kudu.10Shi wanda ke yin manyan abubuwan da ba za a iya bincika su ba, da abubuwan mamaki da basu lissaftuwa.11Duba, yana tare da ni kuma bana ganin sa, kuma yakan wuce, amma bana ganin sa.12Idan ya ɗauke wani abu, wa zai iya hana shi? Wane ne zai iya cewa da shi, 'Me kake yi?'13Allah ba zai janye fushinsa ba; masu taimakon Rahab suna sunkuya wa a ƙarƙashinsa.14Yaya zan iya amsa masa, zan iya zaɓar kalmomin da zan iya yin nazari tare da shi?15Ko da ace ni mai adalci ne, ba zan iya amsa masa ba; sai dai in roƙi jinƙai kaɗai daga mai yi mani hukunci.16Ko dana yi kira ya amsa mani, ba zan gaskata cewa yana sauraren muryata ba.17Gama ya karairaya ni da iska mai ƙarfi ya ruɓanɓanya ciwukana ba dalili.18Ya hana ni in ja numfashi kuma; ya cika ni da baƙinciki.19Idan maganar ƙarfi ce, duba, shi mai iko ne! Idan maganar shari'a ce, wa zai iya sashi ya zo?20Ko da ina da gaskiya, bakina zai kãshe ni; koda ba ni da abin zargi, maganata zata nuna ni mai laifi ne.21Bani da abin zargi, amma ban damu da kaina ba ko kaɗan; na rena raina.22Bai bambanta da komai ba da nace yakan hallaka marar abin zargi tare da mai mugunta.23Idan bulala tayi kisa nan da nan, sai ya yi wa al'amuran marar laifi ba'a.24An bayar da duniya a hannun masu mugunta; Yahweh ya rufe fuskokin alƙalanta. Idan bashi ba ne, to, wane ne?25Kwanakina sun fi ɗan aike mai gudu sauri; kwanakina suna wucewa; basu ganin alheri a ko'ina.26Suna da sauri kamar jiragen ruwan iwa, yana sauri kamar gaggafar da ta kawo bãra a kan nama.27Idan nace zan mance da koke--kokena, zan dena baƙinciki in yi murna,28sai in ji tsoron dukkan wahalhaluna saboda na sani kai ba zaka dube ni a matsayin marar laifi ba.29Tun da za a kashe ni, me kenan, zan yi ƙoƙari a wofi?30Idan na yi wanka da ruwan ƙanƙara nasa hannuwana suka yi tsafta sosai,31Allah zai tura ni a kwari mai taɓo, tufafina zasu zama abin ƙyama tare da ni.32Gama Allah ba mutum ba ne, kamar yadda nake, balle in ba shi amsa, har da zamu zo kotu tare da shi.33Ba wani alƙali a tsakanin mu wanda zai sa mana hannu mu dukka biyu.34Ba wani alƙalin da zai iya ɗauke sandan Allah daga kaina, wanda ya hana tsoronsa ya firgitar da ni.35Sa'an nan ba zan yi magana in ji tsoronsa ba. Amma ga yadda abubuwa suke yanzu, ba zan iya yin haka ba.
"Na san cewa abin da ka faɗi gaskiya ne"
Anan kalmar "haka yake" na nufin abin da Bildad ya faɗa.
"ta yaya wani zai zama marar laifi a gaban Allah?
"Sau ɗaya cikin sau dubu" a nan kalmar kari tana nufin "sam-sam." Ma'anoni masu ma'ana su ne 1) "ba zai iya ba wata amsa ga Allah ba" ko 2) "Allah ba zai amsa masa ba sam-sam"
"sau dubu" ko "sau 1,000"
A nan zuciya tana wakiltar kasancewa ne ko tunani. AT: "mai hikima ga abin da ya yanke shawara"
Yin taurin kai yana nufin mutum ya zama mai rashin ji. AT: "tsayayyi da masa" ko "ba su yi biyayya da shi"
"Allah ya kawar tsauni"
Ana iya bayyana wannan kalma na "fushin" zuwa "fushi" AT: "saboda ya yi fushi"
"Allah ya girgiza duniya"
"wanda kan kare taurari domin ka da a gansu"
Anan an bayana Allah kamr halittar sammai ba tare da wani taimako ba, kamar dai sama masana'antu ne wanda yake shimfidawa.
Waɗannan sunayen taurari ne, wanda suke kama da suka samar da wani tsari a sama.
"abubuwan da ba za a fahimta ba"
"Kalla" ko "Ji" ko "Mai da hankali ga abun da zan faɗa maka."
Waɗannan tambayoyin ne da ke buƙatan amsa na "babu wani." Za a iya rubuta wannan tambayoyin a matsayin kalamai. AT: "idan ya ɗauke wani abu, ba wanda zai iya hana shi. Ba wanda zai iya tambayan shi, 'menene kake yi?"'
Anan "sunkuyawa a ƙarƙashinsa" miƙa wuya. AT: "ya kan ragargaza masu taimakon Rahab"
Kalmar "Rahab" anan tana nufin dodo na teku.
Ayuba ya gabatar da tambayoyin guda biyu don ƙarfafa jinkirin sa ya fuskanci Allah. Ana iya sake amfani dasu azaman bayani. AT: "Don haka ba zan iya amsa shi ba ko in zaɓi kalmomi don yin nazari da shi."
Ayuba yana kwatanta matsalolinsa kamar iska mai ƙarfi. AT: "Ya ji mani kamar da iska mai ƙarfi"
guguwa
"ya ba ni ciwuka" ko "raunin da ni kuma da sake"
"ko da shike ban ba shi wani hujja na yin haka" ko "duk da cewa ba ni da laifi"
Wannan ayar tana nuna Allah kamar yadda ya cika rayuwar Ayuba da abubuwan da zasu sa shi yin ɗaci. Ana iya bayyana sunan "haushi" a matsayin ma'anar "ɗaci" AT: "ya cika ni da abubuwa masu ɗaci"
"Idan ya kasance game ƙarfi ne"
"duba kuma za ku ga cewa shi mai iko ne" ko "kula da abin da zan gaya muku: yana da iko"
"shi ne mai ƙarfi ne"
Wannan tambaya na bukatar amsa na "babu wani" ya nuna cewa babu wanda ya isa ya gabatar da Allah kotu. Ana iya sake amfani da wannan tambaya azaman sanarwa. AT: "ba wanda zai iya kiransa."
Anan "ina hannun dama" yana nufin ni ne wanda ya aikata abubuwa na gaskiya. AT: "Ko da yake na aikata abubuwan da suka dace" ko "Ko da yake ban da laifi ba"
Anan, "baki" yana wakilta kalmomin Ayuba. AT: "maganata zata tuhume ni" ko "abin da na faɗi zai la'anta ni"
Anan "maganata" ana managa dasu kamar zasu iya ɗaukar mataki. AT: "Allah zai yi amfani da abin da na faɗi don tabbatar da ni mai laifi ne"
"bani da laifi"
"Duk iri ɗaya ne" ko "Ba abin damuwa ba ne"
Anan "mara abin zargi" da "mugu" nuna haɗi kai wanda ya haɗa duk abin da ke tsakanin. AT: "ya kawo kowa zuwa ƙarshen, ko mara abin zargi ne ko mugu ne"
AT: "mutane marasa laifi"
Anan "duniya" na nufin mutanen duniya. AT: "mutanen duniya sun"
Wannan ma'anar na nufin Allah ya tsare alƙalan ƙasa daga ikon yin hukunci banbanci tsakanin mai kyau da mugunta. AT: "Allah ya sa alƙalan ka da su yi sharia cikin gaskiya"
"Idan ba Allah bane yake yin waɗannan abubuwan, to wa zai yi su?"
Ayuba ya gwada yadda kwanakin sa ke wucewa zuwa ga mai gudu da sauri. AT: "Kwanaki na suna wucewa da sauri"
"ba wani abu mai kyau"
Ayuba ya gwada yadda kwanakin sa ke wucewa da saurin kamar kwale-kwale. AT: "Suna wucewa da sauri kamar kwall-kwalen na girke na fafirus"
"jirgin ruwan da aka yi daga girgi." Filin itacen fafirus ciyawa ce mai laushi wanda ke girma a gefen gabar koguna.
Ayuba ya gwada yadda kwanakinsa ke wucewa zuwa ga babban tsuntsu wanda ke sauka ƙasa don cin abincinta. AT: "kamar gaggafar da ke sauka ƙasa da sauri don kama abincinta"
AT: "Zan daina gunaguni" ko "Zan daina gunaguni ga Allah"
An yi maganar da baƙin cikin Ayuba kamar wani abu ne da zai iya cirewa. AT: "Zan daina nuna baƙin ciki in yi murna"
Ayoyi na 28 da 29 sun bayyana sakamakon idan Ayuba ya yi abin da ya faɗa a aya ta 27. Ana iya bayyana wannan ta ƙara kalmar "sai" AT: "Sai in ji tsoron dukkan wahalhalluna"
Za a iya canza kalmar "wahalhalluna". AT: "dukan abubuwan da suke bani wahala"
"Zan zama mai laifi kuma a hukunta ni." Za a iya fadin wannan a matsayin aikatau. AT: "Allah zai la'ane ni"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa shi baya tunanin wannan wani amfani ne don neman jawo hankalin Allah. Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "Ba shi da wata amfani a ƙoƙarin neman yardar Allah"
"Idan nayi wanka da ruwa mai tsarki, tsabta"
ruwan da yake fitowa daga ƙanƙarar da ya narke
"ya sanya hannuwa na su yi tsabta sosai." Wasu fassarorin Littafi Mai Tsarki sun fassara wannan da ma'anar "tsabtace hannuwa da sabulu mai ƙarfi"
"tura ni cikin rami"
An yi maganar da tufafin Ayuba kamar dai yana da mummunar amsa ga Ayuba bayan Allah ya jefa shi cikin rami. AT: "Zan kasance mai ƙazanta da tufafi na"
Ayuba ya nuna cewa Allah ya tuhume shi da aikata ba dai-dai ba, kuma yana son amsa waɗannan tuhumar. AT: "amsa tuhumar sa a gare ni" ko "in yi magana da shi a kan rashin laifi na"
"zamu zo tare domin sharia" Anan, "kotu" na nufin inda mutane kan je kuma alƙali sasanta rashin jituwan. "Zuwa tare kotu" na nufin gaba da juna a kotu sharia. AT: "tunkaran juna a kotu"
Wannan yana nufin babu wani alƙalin da ya fi Allah wanda zai iya yanke hukunci game da abin da ke dai-dai tsakaninsa da Ayuba.
Anan "sa mana hanu mu" na nufin samun iko akan sa. AT: "ike mu biyu" ko "a yi mana iko akanmu"
Waɗannan ayoyin na ci gaba da bayani cewa ba wani da ya fi Allah wanda zai iya tsayawa a matsayin alƙali tsakanin Allah da Ayuba.
Anan "sandar Allah" na nufin ma'anar Allah ne don hukunta ko gyara Ayuba. AT: "daina Allah daga horona"
Ana iya fassara ma'anar kalmar "firgitar" azaman ta "tsoro" AT: "hana shi tsorata ni da firgita ni"
"saboda haka ne yadda abubuwa suke yanzu"
1Na gaji da raina; zan yi maganar matsalata a fili; zan yi magana cikin ɗacin raina.2Zan ce da Allah, 'Kada ka kashe ni haka kawai; ka nuna mani abin da kake zargi na a kai.3Ya yi maka kyau ka wahalshe ni, ka rena aikin hannuwanka sa'ad da kake yin murmushi da shirye--shiryen masu mugunta.4Ko kana da idanu na jiki ne? Kokana gani kamar mutum ne?5Ko kwanakinka kamar na ɗan'adam ne ko shekarunka kamar na mutane ne,6da kake yin bincike a kan muguntata kana neman zunubina,7duk da ka san bani da laifi kuma ba wanda zai iya kuɓutar da ni daga hannunka?8Hannuwanka ne suka sifanta ni suka tsara kome nawa, amma kana hallaka ni.9Ina roƙon ka, ka tuna kai ne ka siffanta ni kamar yumɓu; zaka maishe ni cikin turɓaya ne kuma?10Baka zubar da ni kamar madara ka cakuɗe ni kamar abin taunawa ba?11Ka lulluɓe ni da fata da nama ka ɗinke ni da ƙasusuwa da guringuntsi.12Ka bani rai da jiyejiyenƙai; taimakonka ya tsare ruhuna.13Duk da haka ka ɓoye waɗannan abubuwaa zuciyarka--na san waɗannan abubuwan ne da kake tunaninsu:14idan na yi zunubi zaka kula da shi; ba zaka baratar da ni daga muguntata ba.15Idan na yi aikin mugunta, kaito na; ko da nayi aikin adalci, ba zan yi fahariya ba, da yake ina cike da kunya ka dubi wahalata!16Idan na ɗaukaka kaina zaka bi ni kamar zaki; kuma zaka nuna kanka da ayyukan na ban mamaki na iko a kaina.17Ka kawo mani sababbin shaidu ka ƙara fushinka a kaina; ka kawo mani hari da sababbin sojoji.18To, me yasa ka fito da ni daga cikin ciki? Dama na saki ruhuna ba idon da ya gan ni.19Dãma na zama kamar ban taɓa kasancewa ba; dama an ɗauke ni daga cikin ciki zuwa kabari.20Kwanakina ba 'yan kaɗan ba ne? Tsaya haka, ka rabu da ni, domin in ɗan sami hutu21kamin in kai inda ba zan iya dawowa ba, zuwa ƙasar duhu da inuwar mutuwa,22ƙasa mai duhu kamar tsakiyar dare, ƙasa ta inuwar mutuwa, babu wata ka'ida, inda haske kamar tsakar dare yake.'"
"Na gaji da rayuwa"
Ana iya fassara kalmar "maganata" da "matsalata" a "bayani" da "matsalar." AT: "Zan yi bayani akan matsalar" ko "Zan yi bayanin matsalar a fili"
Yadda aka ji Ayuba yana da ɗanɗano mai ɗaci. Ana iya fassara ma'anar "haushi" a matsayin kain magana "ɗaci." AT: "Zuciyata za ta yi magana cikin ɗaci" ko "zan yi magana da ɗacin raina"
Wannan tambayar tana tsammanin amsar "a'a" kuma za a iya canza shi zuwa cikin sanarwa. AT: "Ba shi da kyau cewa kada ku zalunce ni, ya kamata ku rena aikin hannuwanku, kuna murmushi kan da shirye-shiryen mugaye."
Anan ma'anar "murmushi akan" na wakiltar cewa yardar Allah. AT: "amince da shirye-shiryen mugaye"
Waɗannan tambayoyin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. Waɗannan tambayoyin suna tsammanin amsar da ba ta ɗace ba za ta nanata cewa Allah ba ya ganin ko fahimtar abubuwa kamar yadda mutum yake yi. Ana iya bayyana su azaman kalamai. AT: "Ba ku da idanu na jiki, kuma ba ka gani kamar yadda mutum yake gani"
Wannan tambayoyi na tsammanin amsar da na a'a domin ta nanata cewa Allah bai da karshe mutum kuma na da karshe."
Waɗannan kalmomin guda biyu na kusan ma'ana ɗaya.
Anan "hannuwaka" yana wakiltar Allah da aikinsa na hallita. AT: "Kai"
"sifanta ni da tsara ni". Kalmomin "fiɗa" da "kera" suna dai-dai da ma'ana.
"Tuna"
"sake mayar da ni cikin ƙura kuma"
Wannan tambaya ce da ke fatan amsa mai kyau. AT: "Kun zubar da ni kamar madara kuma ka cuɗa ni kamar cuku" ko "Ka halitta ni a cikin mahaifa kamar yadda madara aka zuba ya zama cuku."
Anan "kai" na nufin Allah.
Anan "ni" na nufin Ayuba.
Allah yana sanya fata da nama a jikin Ayuba ana magana ne kamar dai Allah yana sanye da tufafi ne. AT: "Kun sanya fata da nama a jikina"
wannan shi ne sassan jikin da ke haɗa tsokoki zuwa kasusuwa ko sauran sassan jikin mutum.
Za a iya wannan kalmar "rai" da "amincin" azaman "rayuwa" da "aminci." AT: "Kun kasance da aminci ga alkawarinku kuma kun yardar mini in rayu"
"kulawarka"
Anan Ayuba yana wakilta ta "ruhunsa." AT: "ta tsare ni" ko "a kiyaye ni a hankali" ko "kiyaye ni lafiya"
"idan na yi mugayen abubuwa"
zai zama abin tada hankali a gare ni"
Wannan ma'anar tana nufin zama da gabagaɗi. AT: "tsayawa da fahariya" ko "zama da gabagaɗi" ko "yarda da kai"
Wata ma'anar mai yiyuwa ce "Ina jin kunya gaba ɗaya kuma cike da wahalata."
Ma'anar mai yiyuwa sune 1) wannan yanayin halin da bai faru ba ne ko 2) wannan shi ne bayanin yanayin da ya faru akai-akai. AT: "Lokacin da aka daga kaina, kuna kama ni kamar zaki"
Wannan magana na nuna yadda Allah yake nuna ikonsa ta wajen aikata cutar da Ayuba.
Matsalar Ayuba daga Allah ana maganarta kamar su mutane ne waɗanda ke ba da shaida a kansa.
Allah yana aiko da masifa da Ayuba ana maganarsa kamar dai Allah yana aiko da sabbin rundunoni ne gaba da shi.
Anan fitar da mahaifar na wakiltar haihuwa a duniya. AT: "fito da shi daga cikin mahaifiyata" ko "kawo ni cikin duniya"
Wannan na wakiltar mutuwa. AT: "ta mutu"
Ayuba yana amfani da "ido" anan yana nufin dukan mutumin. Yana fatan zai mutu cikin haihuwa, kafin kowa ya gan shi. AT: "kafin wani ya taɓa ganina" ko "kafin a haife ni"
Anan "kwanakin raina" na wakiltar tsawon rayuwar Ayuba. Wannan tambayar na tsammanin amsa da kyau, don nanata cewa Ayuba kawai yana fatan ya yi kwanaki kaɗan. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Na rage sauran 'yan kwanaki in rayu" ko "Rayuwa na zata ƙare."
Anan wurin da ruhun matattu suke tafiya kamar ana ƙasa. AT: "wurin"
Wannan kalmar "inuwar mutuwa" na nuna girman "duhun." Suna nuna ida ruhun matattu suke tafiya.
Duhun wurin da matattu ke zuwa ya fi duhun dare duhu.
Wannan kalmomin mara kyau za a iya bayyana su da kyau. AT: "cike da ruɗani" ko "inda duk aka rikice"
Idan aka kwatanta hasken iwurin da ruhun matattu ke tafiya suke misalta da tsakar dare. AT: "inda babu haske"
1Sa'an nan Zofar Banamate ya amsa ya ce,2"Ba za a bada amsa a kan waɗanan maganganun masu yawa ba? A gaskata da wannan mutumin, mai yawan magana?3Fankamarka zata sa sauran mutane suyi shuru ne? Sa'ad da kayi ba'a, ba wanda zai sa ka ji kunya ne?4Gama kace da Allah, 'Bangaskiyata sahihiya ce, bani da laifi a idanunka.'5Amma, da Allah zai yi magana ya buɗe bakinsa gãba da kai;6da zai nuna maka asirin hikima! Gama shi yana da fahimta mai girma. Ka sani ba kamar yadda muguntarka take Allah yake nema ba.7Zaka iya ganewa da Allah ta wurin binciken sa? Zaka iya fahimtar Yahweh sarai?8Matsalar tayi tsawo kamar samaniya ne; me zaka iya yi? Ta fi Lahira zurfi; me zaka iya sani?9Ta fi duniya tsawo, kuma ta fi teku faɗi.10Idan ya wuce ya kulle wani, ko idan ya hukunta wani, wane ne zai iya hana shi?11Gama ya san maƙaryata; idan ya ga mugunta, baya lura da ita ne?12Amma wawayen mutane basu ganewa; zasu same ta sa'ad da jakin jeji ya haifi ɗan mutum.13Amma da ka tsayar da zuciyarka sosai ka miƙa hannuwanka zuwa ga Yahweh;14da akwai mugunta a hannunka, amma daka kasa ta nesa da kai, da baka bari rashin adalci ya zauna a rumfarka ba.15Da ka tada fuskarka ba tare da kunya ba; lallai da ka tsaya da ƙarfi ba tare da tsoro ba.16Da ka manta da damuwarka; sai dai ka tuna da ita kamar wucewar ruwa.17Da ranka yayi haske fiye da rana; ko da akwai duhu da ya zama kamar safiya.18Da zaka natsu saboda akwai bege; lallai da ka sami tsaro kewaye da kai da ka huta a tsanake. Kuma da ka kwanta ka huta,19Kuma ba wanda zai tsoratar da kai; lallai da mutane da yawa sun nemi tagomashi a wurin ka.20Amma idanun masu mugunta zasu kasa; ba zasu sami wurin ɓuya ba; begensu numfashin ƙarshe ne kaɗai"
Duba yadda kuka fassara sunan mutumin a cikin Ayuba 2:11. AT: "Zophar daga yankin Na'amat"
Zofar yana tambaya a cikin mara kyau don jaddada cewa dole ne a ƙalubalanci kalmomin Ayuba. AT: "Dole ne mu amsa dukkan waɗannan maganganu!" ko "Wani ya kamata ya amsa duk waɗannan maganganu!"
Zofar yayi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa bai kamata su yarda da abin da Ayuba yake faɗi ba. AT: "Wannan mutumin nan cike yake da magana, amma ya kamata mutane su yarda da shi!" ko "Maganganinku da yawa ba su kadai ba yana nufin kai marar laifi ne!"
Zofar ya yi amfani da wannan tambayar don tsauta wa Ayuba. AT: "Domin kawai kun faɗi maganganu da yawa, wannan ba ya nufin cewa dole ne wasu su yi shuru."
Zofar ya yi amfani da wannan tambayar don tsauta wa Ayuba. Wataƙila kuna buƙatar bayyana ainihin abin da Ayuba yake ba'a. AT: "Kun yi mana ba'a saboda abin da muka faɗi. Yanzu za mu baku kunya!"
"fahimta na dai-dai ne"
Idanu suna wakiltar gani, wanda yake game da kimar Allah ga Ayuba. Ma’anoni masu ma’ana sune 1) cewa Ayuba yana cewa Allah yana shar’ianta shi mara laifi ne. AT: "Kuna cewa bani da laifi" ko 2) da Ayuba ya yarda cewa bai zama marar aibu ba kuma ya kamata Allah ya yanke hukunci a matsayin mara aibi. AT: "Ya kamata ka sani cewa ni mai laifi ne"
Kalmomin "buɗe bakinsa" kalmomi ne na ma'ana suyi magana. Waɗannan jumla guda biyu suna ma'ana iri ɗaya ne kuma ana amfani dasu tare don ƙarfafa sha'awar Zophar cewa Allah zai yi magana da Ayuba da ƙarfi.
Abin da “asirin hikima” ake iya bayyaninsa a sarari. AT: "zai nuna muku cewa kuna shan wahala saboda zunubanku"
Neman daga Ayuba yana wakiltar azabtar da Ayuba. AT: "Allah ba zai azabta ku da abin da kuka cancanci"
Waɗannan tambayoyin guda biyu suna daidaita abu ɗaya. Marubucin yayi amfani da hanyar tambaya don ƙara girmamawa. AT: "Ba za ku iya fahimtar Allah da bincikansa ba, kuma ba za ku taɓa fahimtar Madaukaki sarai ba!"
Wannan yana nufin fahimtar Allah. AT: "Don fahimtar Allah"
Ba a yiwuwar fahimtar Allah ana magana da shi kamar ba shi yiwuwa a je waɗannan wurare masu nisa. AT: "ba a isa kamar yadda mafi girman wuraren da ke cikin sama ba ... ba a cikin mafi girman wurare fiye da zurfin cikin lahira"
Zofar yayi amfani da wannan tambayar don nuna cewa mutum ba zai iya yin komai don ya fahimci Allah sosai. AT: "Ba za ku iya yin komai ba." ko "baku fahimce shi cikakke ba."
An yi magana da girman Allah ko hikimarta kamar ana iya auna ta da nisa.
"Idan Allah ... ya rufe wani a kurkuku"
AT: "Idan Allah ya kira wani domin ya hukunta shi"
Wannan tambayar ta nanata cewa babu wanda zai iya hana Allah. AT: "babu wanda zai iya dakatar da shi!"
Wannan ya nanata cewa Allah yana lura da zunubi. AT: "lalle ya lura!"
Za a iya caza kalman "ganewa" zuwa "fahimta" AT: "amma wawaye basu fahimta"
Tun da jaki ba zai taɓa haihuwar mutum ba, wannan yana nuna cewa wawaye ba za su taɓa samun fahimta ba. AT: "kawai in jakin daji zai iya haihuwar mutum zai iya wawaye za su sami fahimta" ko "ba shi yiwuwa wawa ya sami fahimta kamar yadda jaki ya haifi mutum"
Zuciya tana wakiltar tunani da halaye. Kafa shi dai-dai yana wakiltar gyara shi. AT: "ko da kun gyara halayen ku"
Wannan na wakiltar roƙon Allah domin taimako. AT: "yayi roƙo da addu'a ga Allah"
Hannun yana wakiltar abin da mutum ya aikata. AT: "ko da kun aikata mugayen abubuwa a baya"
Sanya zunubi a baya yana wakiltar dakatar da zunubi. AT: "amma a lokacin ne kuka daina aikata mugunta"
Zaman rashin adalci na wakiltar mutane da suke yi rashin adalci. AT: "kuma ba ka bar mutanen gidanka su yi rashin adalci ba."
“dauke sama da fuskarka” tana wakiltar halayen mutumin da yake da ƙarfin zuciya kuma mai gabagaɗi.
Zofar yana kwatanta bala'i da ruwan da yake gangara ƙasa kuma ya tafi. AT: "Kuna iya tuna shi, amma masifa za ta tafi, kamar ruwan da ya gudana"
Haske na wakiltar wadata da farin ciki. AT: "Rayuwanka zata zama da wadata da farin ciki kamar hasken rana"
Duhu na wakiltar matsaloli da damuwa. AT: "Ko da akwai bakin wahala da damuwa"
Zofar ya sake maimaita irin ra'ayin don karfafawa. Safiya na wakiltar haske, wanda yake wakiltar wadata da farin ciki. AT: "zata zama da wadata da farin ciki kamar safiya"
Zofar ya mayar da wannan ra'ayin domin girmamawa da bayyana yiwuwar.
"Ku huta" a nan ne karin magana ce ta "hutawa." Ana iya bayyana kalmar "cikin aminci" tare da kalmar "a amince." AT: "za a huta lafiya"
Zofar ya mayar da wannan ra'ayin domin girmamawa da bayyana yiwuwar.
Idanunsu suna wakiltar fahimtar su. AT: “fahimtar mugaye ba zata yi nasara ba” ko kuma “mugaye ba za su iya fahimta ba”
1Sa'an nan Ayuba ya amsa ya ce,2"Ba shakka ku ne mutanen; hikima za ta mutu tare da ku.3Amma ni ma ina da fahimta kamar yadda kuma kuke da shi; ni ban gaza ku ba. Hakika, waye bai san irin abubuwa kamar waɗannan ba?4Ni wani abu ne da makwabcina zai yiwa dariya - Ni, da nake kira bisa sunan Allah wanda ya kuma amsa mani! Ni, mutum mai adalci marar aibu kuma - yanzu na zama wani abin dariya.5A tunanin wani wanda yake zaune lafiya, akwai reni game da masifa; yakan yi tunani irin na ƙara kawo masifa kan waɗanda ƙafafunsu ke zarmewa.6Rumfunan mafasa na azurta, waɗanda kuma ke cakunar Allah suna nan lafiya; hannunwansu ne allolinsu.7Amma yanzu ka tambayi dabbobi, kuma zasu koya maka; ka tambayi tsuntsayen sammai, zasu kuma gaya maka.8Ko kuma kayi wa ƙasa magana, zata kuma koya maka; kifayen teku zasu shaida maka.9Wace dabba ce cikin dukkan waɗannan da bata sani cewa hannun Yahweh ne yayi wannan ba?10A cikin hannunsa ran kowanne rayayyen abu yake da kuma numfashin dukkan 'yan adam.11Ashe kunne ba yakan gwada dukkan maganganu kamar yadda baki ke ɗanɗana abinci ba?12Hikima tana ga tsoffin mutane; a tsawon kwanaki kuma akwai fahimta.13Hikima da iko suna ga Allah; shi ke da shawara da fahimta.14Duba, yakan rushe, ba za a kuma iya ginawa ba, idan ya kulle mutum, ba sauran kuɓutarwa.15Duba, idan ya janye ruwaye, sai su bushe ƙurmus; kuma idan ya aika da su, sai su malale ƙasa.16A gunsa ƙarfi da hikima suke; mutanen da aka ruɗe su da mai ruɗin dukkansu biyu suna cikin ikonsa.17Yakan ɓad da mashawarta zuwa baƙinciki, ya mai da alƙalai wawaye.18Yakan tuɓe rawanin iko daga sarakuna; ya ɗaura ɗan ƙyalle a kwankwasonsu.19Yakan ɓad da firistoci su tafi ƙafa ba takalmi cikin baƙinciki ya kuma kaɓantar da manyan mutane.20Yakan ɗauke iya maganar mutanen da aka dogara gare su ya kuma ɗauke fahimtar dattawa.21Yakan zuba reni a kan hakimai ya kuma kwaɓe ɗamarar mutane masu ƙarfi.22Yakan bayyana zurfafan abubuwan duhu ya kuma kawo baƙin duhu cikin haske.23Yakan sa al'ummai suyi ƙarfi, yakan kuma hallakasu; yakan faɗaɗa al'ummai, ya kuma bi da su kamar 'yan kurkuku.24Yakan ɗauke fahimta daga shugabanin mutanen duniya; yasa su suyi ta yawo a jeji inda ba tafarki.25Suyi lalube cikin duhu babu haske; yakan sa suyi tangaɗi kamar bugaggen mutum.
Ayuba yana ba'a da yadda suke yi kuma yana nuna yadda suke ba'a. AT: "Lallai ku waɗannan mutane masu mahimmanci ne da hikimar ba za ta wanzu tare da ku ba" ko "Duk kuna yi kamar ku ne kawai masu hikima kuma idan kun mutu, hikima za ta shuɗe"
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don bayyana gaskiya wanda ya kamata ya bayyana ga masu sauraron sa. Ana iya bayyana shi azaman sanarwa. AT: "Tabbas babu wani wanda bai san irin waɗannan abubuwan ba." ko "Tabbas kowa ya san waɗannan abubuwan."
Dangantaka tsakanin waɗannan jumlolin za a iya bayyananniya tare da kalmomin "koda yake." AT: "Ni wani abu ne maƙwabcina don yin dariya - koda yake ni ne wanda ya kira Allah kuma ya amsa mini!"
Dangantaka tsakanin waɗannan jumlolin za a iya bayyananniya tare da kalmomin "koda yake." AT: "Koda yake ni mai adalci ne kuma mai laifi, amma yanzu mutane suna yi mini dariya" (Duba: writting_connectingwords)
Da kafar darje yana wakiltar kasancewa cikin haɗari ko matsala. AT: "ga waɗanda tuni ke cikin wahala"
Wannan na wakiltar mafasa na azurta a cikin rumfunansu. AT: "mafasa na rayuwa cikin wadata a cikin rumfunansu"
Anan "hannayensu" alama ce don ƙarfi, kuma "allolinsu" wani misali ne don girman kansu. AT: "suna alfahari da kwarewar su"
Wadannan maganganu guda hudu sun bayyana ra'ayin cewa dabbobin, tsuntsaye, kasa, da kifayen sun fahimci Allah fiye da abokan Ayuba.
Wannan tambaya ta jaddada zance cewa duk dabbobi sun sani Yahweh ya yi wannan. Ana iya yin wannan tambaya a matsayin bayani.AT: "Kowane dabba a cikin duk waɗannan sun san ... wannan."
Hannun Yahweh yana wakiltar sarrafawansa ko ikonsa. AT: "Allah ya yi wannan da ikonsa"
Hannun Yahweh yana wakiltar ikonsa. AT: "Allah yana tafiyar da kowane mai rai, yana kuma ba da numfashi ga dukkan 'yan adam"
Anan "numfashi" na wakiltar rai ko ikon iya rayuwa.
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa mutane suna sauraron abin da wasu ke faɗi kuma suna hukunci ko yana da kyau ko babu. Kunnuwa da kaunadodi kalmomi ne na ji da ɗanɗano. AT: "Mun ji abin da mutane suke faɗi kuma muna gwada shi kamar yadda muke ɗanɗano abinci da gwada shi."
"Mazazan tsufa suna da hikima." Ana iya bayyana sunan "hikima" da "mai hikima". Kalmar "maza" tana nufin mutane gaba ɗaya. AT: "Tsofaffin mutane suna da hikima"
Wannan yana wakiltar mutane su sami fahimta lokacin da suke rayuwa tsawon lokaci. Ana nuna kalmar "fahimta" tare da jimlar "fahimta sosai." AT: "mutane suna samun fahimta lokacin da suka daɗe" ko "mutanen da suka daɗe suna fahimtar abubuwa da yawa"
Aya ta 13 ta ce Allah na da hikima da iko. Sauran dukan wannan sura na nanata wannan ne ta wurin faɗar manya-manyar abubuwa da Yahweh yake yi.
Za a iya bayyana sunayen sunaye "hikima" da "ƙarfin" tare da ƙaddara "hikima" da "mai ƙarfi." AT: "Allah mai hikima ne mai iko"
"Kalla" ko "ji" ko "maida hankali ga abin da zan fada maka."
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "ba wanda zai iya sake gina ta"
Ana amfani da kalmar 'sakin fuska' tare da kalmar aikatawa "yanci." AT: "idan Allah ya rufe wani, ba wanda zai iya 'yantar da shi"
Ma’anoni masu ma’ana sune hana ruwa-ruwa wakiltar 1) hana ruwan sama faduwa. AT: "idan ya dakatar da ruwan sama daga faduwar ƙasa sai ya bushe" ko 2) hana ruwa gudu. AT: "idan ya hana ruwan ya gudano, ƙasa sai ya bushe"
Za a iya bayyana sunan suna "ƙarfi" da "hikima" tare da kalmomin "mai ƙarfi" da "mai hikima". AT: "Allah mai ƙarfi ne mai hikima"
Kasancewa cikin ikon Allah yana wakiltar Allah yake mulkinsu. AT: "mutanen da suka yi imani da karya da kuma mutanen da ke wa wasu karya kuma suna cikin ikonsa" ko "Allah yana sarauta bisa mutanen da suka yi imani da karya da kuma mutanen da ke yin karya ga wasu"
Wannan suna wakiltar kwashe hikimarsu da ikonsu.
"Yana sa alƙalai su zama wawaye"
Wannan suturar wataƙila abin da bawa yake sawa ne. Sanya wankin nan akan sarakuna yana wakiltar sanya bayin sarakuna ne. AT: "yana sa sarakuna su sa suturar bayi" ko "ya mai da su bayi"
Hana firistocin da ba su da kwatankwacin ƙafa na wakiltar kwashe ikonsu.
"yin nasara akan mutane masu iko"
Ana cire maganarsu yana wakiltar rashin iya maganarsu. AT: "Ya sanya waɗanda aka amince da su ba su iya yin magana" ko "Ya sa waɗanda aka yarda dasu su yi shuru"
Fice da fahimtar su yana wakiltar sanya su kasa fahimta ko yanke shawara mai kyau. AT: "yana sa dattawa su kasa fahimta" ko "ya sa dattawan suka kasa yanke shawara mai kyau"
Ma'anar mai yiwuwa ita ce (1) tsofaffi ko (2) shugabanni.
Wannan na nufin ya sa mutane su rena su. AT: "Ya sa mutane sun rena masu mulki ainun"
Damarar alama ce ta ƙarfi. Kwance damarar mai karfi na wakiltar cire karfinsa da zama rauni. AT: "yana sa mutane masu ƙarfi su zama marasa ƙarfi"
Bayyanar abubuwa suna wakiltar sanar dasu. “Abubuwa masu zurfi daga duhu” na wakiltar asirin da mutane ba su sani ba. AT: "Yana ba da sanannu asirin da mutane ba su sani ba"
Fitar da abubuwa zuwa ga haske yana wakiltar sanar dasu ne, kuma anan "inuwa" alama ce ta abubuwan da suke boye cikin inuwa, wanda hakan ma alamu ne ga gaskiyar da Allah ya tona wa mutane. AT: "ya bayyana abubuwan da babu wanda zai iya gani"
Allah yake jagorantar al'ummai yana wakiltar Allah yana sa kasashe maƙiyan su. Kalmar "su" na wakiltar al'ummai, wanda a nan ke wakiltar mutanen waɗannan ƙasashe. AT: "yana sa abokan gabansu su bishe su a matsayin mai kurkuku"
Yin yawo a cikin jeji inda babu wata hanya yana wakiltar kasancewa cikin mawuyacin hali ba tare da sanin abin da zan yi ba. AT: "rashin tabbas game da abin da za a yi kamar mutumin da yake yawo a jeji ba tare da wata hanya ba"
Kasancewa cikin duhu ba tare da haske ba yana wakiltar rashin ilimi. AT: "Suna gwagwarmayar yanke shawara ba tare da ilimi ba kamar yadda mutane ke gwagwarmaya yin tafiya cikin duhu ba tare da haske ba"
Yin yawo kamar mutum mai maye shine wakiltar yin rayuwa ba tare da wata manufa ba. AT: "yana sanya su rayuwa ba tare da wata ma'ana ba kamar mai maye kamar wanda yake yin zagi kamar yadda yake tafiya"
1Duba, idona ya ga duk wannan; kunnena yaji ya kuma fahimce shi.2Abin da kuka sani, ni ma ina sane da shi; ni ban gaza ku ba.3Duk da haka, na gwammace in yi magana da Mai Iko Dukka; ina so in tattauna da Allah.4Amma ku kuna lulluɓe gaskiya da ƙarereyi; ku dukka likitoci ne marasa amfani.5Kash, dama zaku yi shuru! Wannan zai zama maku hikima.6Ku saurari nawa hujjojin; ku kasa kunne ga ƙarar tawa leɓunan.7Za ku yi magana marar adalci domin Allah, zaku kuma yi maganar munafunci dominsa?8Zaku nuna masa bambanci? Zaku yi jayayya domin Allah?9Zai zama da kyau domin ku sa'ad da ya bincike ku? Zaku iya ruɗinsa kamar yadda zaku ruɗi mutane?10Hakika zai kwaɓe ku idan a ɓoye kuka nuna bambanci.11Darajarsa ba zata firgita ku ba, tsoronsa kuma ya faɗo a kanku?12Batutuwanku masu daɗin ji misalai ne da aka yi su da toka; hanzarinku hanzari ne da aka yi su da yumɓu.13Ku riƙe salamarku, ku kyale ni kawai, domin in yi magana, bari abin da zai auko kaina ya auko.14Zan sa namana a bakina; in ɗauki raina a hannuwana.15Bari mu gani, ko zai kashe ni, zan zama ba sauran bege; duk da haka, zan kare hanyoyina a gabansa.16Wannan zai zama dalilin cetona, gama ba wani mugun mutum da zai zo gabansa.17Allah, ka kasa kunne ga furcina; bari furcina ya zo kunnuwanka.18Duba yanzu, na shirya hanzarina sosai; na sani ba ni da aibu.19Wane ne wannan da zai yi jayayya gãba da ni a gaban sharia? Idan kun zo ne don ku yi, idan kun tabbatar da laifina, sai in yi shuru in saki raina.20Allah, kayi mani abu biyu kawai, sa'an nan bazan boye kaina daga fuskarka ba:21ka janye hannunka mai azaba daga gare ni, kuma kada ka bari razanarka ta tsorata ni.22Sa'an nan ka kira ni, zan kuma amsa; ko kuma ka bari in yi magana da kai, kai ka amsa mani.23Laifofina da zunubaina nawa ne? Bari in san kuskurena da zunubina.24Don me kake boye fuskarka daga gare ni ka maishe ni kamar maƙiyinka?25Zaka tsanantawa ganyen da iska ke kora? Zaka far wa tattaka?26Domin ka rubuta abubuwa masu ɗaci gãba da ni; kasa in gãji laifofin ƙuruciyata.27Ka kuma sa ƙafafuna a turu; kana duba dukkan tafarkuna kurkusa; kana bincike inda sawayen ƙafafuna suka taka,28ko da yake ni kamar ruɓaɓɓen abu ne da yake lalacewa, kamar rigar da asu suka cinye.
Ayuba ya ci gaba magana da abokansa.
"Kalla" ko "ji" ko "mai da hankali akan abin da zan faɗa maka"
Ayuba ya ambaci kansa a matsayin idanunsa tunda da idanunsa ne ya ga waɗannan abubuwan. AT: "Na ga duk waɗannan"
Ayuba ya ambaci kansa a matsayin kunne saboda yana da kunnuwansa ne ya ji waɗannan abubuwan. AT: "Na ji kuma na fahimta"
"Abin da kuka sani, ni ma na sani" ko "Na sani kamar yadda kuka sani"
Abokan Ayuba suna yi masa shari'a, amma ba sa faɗi gaskiya. Ayuba zai fi son yin jayayya da Allah kaɗai game da korafinsa.
Wannan na wakiltar yana nuna watsi da gaskiya. AT: "kun ɓoye gaskiya da ƙarya" ko "kun yi ƙarya kun ƙi gaskiya"
Kasancewa likita yana wakiltar kasancewa mutum mai ta'azantar da wasu. Kasancewa ba shi da mahimmanci yana nufin cewa ba su san yadda za su yi abin da ya kamata ba. AT: "duk kun kasance kamar likitoci waɗanda ba su san yadda za su warkar da mutane ba" ko kuma "ku duka sun ta'azantar da ni, amma ba ku sani yadda ba, kamar likitoci marasa ƙwarewa"
Wannan magana tana nufin "yi shuru" ko "daina magana."
Sun zaci suna faɗar abin da ke da hikima, amma Ayuba yana cewa ne za su kasance da hikima idan sun daina magana. Ana iya bayyana sunan "hikima" tare da kalmar "hikima". AT: "Da a ce za ka yi hakan, da a ce za ka sami hikima" ko "Idan aka daina magana, za ka zama mai hikima ne"
Anan "lebe" suna wakiltar mutumin da yake magana. AT: "ku saurari abin da ni da kaina nake roƙo"
Ayuba ya yi amfani da waɗannan tambayoyin biyu don tsauta wa abokansa don yin magana da rashin gaskiya. AT: "Kuna tsammani kuna magana ne don Allah, amma kuna magana ne ba da gaskiya ba. Kuna magana da ha'inci ne."
"ƙarya" ko "faɗin ƙarya"
Nuna alheri ga Allah yana wakiltar taimaka wa Allah ko kuma kare Allah daga gunaguni da Ayuba ya yi. Ayuba yana amfani da waɗannan tambayoyin guda biyu don tsauta wa abokansa don tunanin cewa za su iya kare Allah. AT: "Kuna tsammani Allah yana buƙatar ku don kare shi? Kuna tsammanin zaku iya jayayya ga Allah kamar lauyoyi a kotu."
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don gargaɗin abokansa cewa idan Allah zai bincika su, zai faɗi abin da suke yi ba dai-dai ba ne. AT: "Idan Allah ya bincike ku, ba zai zama muku da alheri ba."
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don gargaɗin abokansa cewa Allah ya san gaskiya game da su. AT: "Kuna iya yaudarar maza, amma ba zaku iya yaudarar Allah ba."
"tsauta maku"
Wannan na nufin fadar abin dake da kyau game da mutum domin alƙali yana da halin kirki. Yin wannan a ɓoye na nufin munafunci, halin nuna bambanci.
Ayuba ya yi amfani da waɗannan tambayoyin don tsauta wa abokansa. Ma'anar mai yiwuwa sune 1) Ayuba yana cewa ya kamata su ji tsoron Allah. AT: "Da girmansa ya kamata ya baka tsoro, tsoro ya kamata ya same ka." ko 2) Ayuba yana cewa za su ji tsoron Allah. AT: "Girmarsa zai baka tsoro, tsoro kuwa zai same ka!"
Jin tsoro kan mutane yana wakiltar su da fargaba sosai. AT: "kuma kada ku firgita sosai" ko "kuma kada ku firgita"
Toka yana wakiltar abubuwan da basu da amfani kuma basa dorewa. AT: "Kalamanku na yau da kullun ba su da amfani kamar toka" ko kuma "Za a manta da maganganunku kamar toka da ake watsewa"
Ayuba na magana akan abin da suke faɗa kamar bango ne aka yi da yumbu kewaye da birni; wannan ba zai iya kare mutane ba domin yumbu kan zaizaye da wuri. AT: "abin da kuke faɗa a matsayin kariya wofi ne kaman bangon yumɓu."
Ma'anar mai yiwuwa shine wannan yana nufin 1) abin da suke faɗi don kare kansu ko 2) abin da suke faɗi don kare Allah.
Wannan kalma ce da ke nufin "daina damuwa da ni" ko "daina hana ni" wannan na nufin "ku daina damuna" ko "ku daina hanani"
Abubuwan da ke zuwa ga mutum suna wakiltar abubuwan da ke faruwa ga mutum. Wannan furcin da ya fara da "bari" yana nufin cewa bai damu da abin da zai iya faruwa da shi ba. AT: "ka bar abin da zai faru da ni ya faru" ko "Ban damu da abin da zai iya faruwa da ni ba"
"Namana" a nan na nufin "rai". "Bakina" da "hannuwa" na nufin cikin ikonsa. Waɗannan kalamai na nunawa Ayuba kasada na ransa domin ya nuna hujjojinsa ga Allah. AT: "Ina shirye in yi kasadar raina"
AT: "Wannan shi ne dalilin da Allah zai cece ni" ko "Wannan shi ne dalilin da yasa Allah zai cece ni daga matsaloli na"
Ayuba ya fara gabatar da maganarsa kai tsaye ga Allah.
Waɗannan layin guda biyu suna ma'ana dai-dai da abu ɗaya kuma suna kara ɓukatar Ayuba ga Allah ya saurare shi.
Kunnuwa suna wakiltar sauraro. AT: "saurari furcina" ko "saurari abin da na furta"
Wannan na nanata akan abin da ke biye. "kasa kunne yanzu" ko "ina roƙonka ka mai da hankali"
Sanya tsaro a tsari yana wakiltar yanke shawarar abin da zai faɗa don ya kare kansa. AT: "Na yi tunani yadda zan kare kaina" ko "Na yanke shawara yadda zan bayyana kaina"
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don bayyana imaninsa cewa tunda yana da gaskiya, ba wanda zai yi jayayya da shi. AT: "Ban yi imani cewa kowa zai yi magana da ni a kotu ba"
"Idan kun zo kuna jayayya da ni"
“Kai” anan na nufin Allah da kansa.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "in da za ku tabbatar da ni mai laifi"
Wannan na nufin mutuwa. AT: "mutu"
"Fuska" na wakiltar mutumin. AT: "daga gareku"
Hannun azzalumi ma'anar yin abin da zai zalunta wani. Cire hannun yana wakiltar dakatar da yin waɗancan abubuwan. AT: "ka daina zaluntata"
Kalmar "razanarka" na nufin abin da ke sa mutane su ji tsoron Allah. AT: "kar ku firgita ni"
Ayuba ya ci gaba maganar ga Allah.
Ayuba yayi wannan tambayar don yin gunaguni game da yadda Allah yake bi da shi. Wataƙila yana tsammanin amsa.
Boye fuskokin mutum daga wani yana nuna kin yarda dashi ko watsi dashi. AT: "kun ƙi kalle ni" ko "kun yi watsi da ni"
Ayuba yana amfani da waɗannan tambayoyin don gaya wa Allah cewa tun da yake Ayuba yana da ƙarancin ƙarfi da rauni, ba shi da amfani a tsananta masa. “Ganya” da “ciyawa” alamu ne da ke bayyana raunin Ayuba, rashin cancanta da rashin ƙarfi. AT: "Kuna tsananta mini, amma ni mai rauni ne kamar ganye wanda iska take hurawa kuma mara ma'ana kamar ciyawar ciyawa."
"Abubuwa marasa kyau" suna wakiltar zargi. AT: "Kuna rubuta zargewata a kaina"
Samun zunuban ƙuruciyarsa karin magana ne. Ma'anar mai yiwuwa shine yana wakiltar 1) kasancewa mai laifi game da zunuban ƙuruciyarsa. AT: "kuna cewa har yanzu ina mai laifi game da zunuban ƙuruciyata" ko 2) azabtar da shi saboda zunuban ƙuruciyarsa. AT: "kuna azabtar da ni saboda zunuban ƙuruciyata"
AT: "laifin da na aikata tun ina ƙarami"
Yin wannan yana wakiltar hukunta Ayuba. Hakan ya nuna cewa Ayuba ya yi laifi kuma yanzu fursuna ne. AT: "kamar dai kun sanya ƙafafuna a cikin hannun jari ko sarƙa"
Ma’anoni masu ma’ana su ne 1) firam wanda yake riƙe ƙafafun fursunoni a wuri saboda ba zai iya motsawa kwata-kwata ko 2) sarƙoƙi a ƙafafun fursunonin waɗanda ke sa ya yi wuya a yi tafiya. Ana amfani da waɗannan azaman fasalin horo.
“Hanyoyi” suna wakiltar ayyukan da Ayuba yake yi. AT: "duk abin da nake yi"
Kadarorin ƙafafunsa suna wakiltar mutumin da yake tafiya. AT: "kuna bincika ƙasar da na tafiya"
Ayuba ya kamanta rayuwarsa da wani abu da ke lalacewa. A hankali ya ke mutuwa.
Ayuba ya kamanta kansa da tufafin da ke da ramuka a ciki saboda kwari sun ci sassan ta.
1Mutum, da mace ta haifa, ya kan rayu 'yan kwanaki kaɗan yana kuma cike da damuwa.2Ya kan tsiro daga ƙasa kamar fure sai kuma a datse shi; ya tsere kamar inuwa baya daɗewa.3Kana duba kowanne su? Kana gabatar da ni a gaban shari'a tare da kai?4Wane ne zai iya fitar da abu mai tsabta daga cikin marar tsabta? Babu ko ɗaya.5Kwanakin mutum a ƙayyade suke. Yawan watanninsa na tare da kai; ka ƙayyade masa iyaka da ba zai iya wucewa ba.6Ka ɗauke idonka daga gare shi domin ya huta, domin ya ji daɗin kwanansa kamar ɗan ƙwadago in ya iya.7Mai yiwuwa ne itace na da bege; idan an sare shi, zai iya toho kuma, 'yan sabbin rassansa ba sa ɓata.8Ko da yake saiwoyinsa sun tsufa a ƙasa, kututturensa kuma ya mutu a ƙasa,9amma da zarar ya ji ƙanshin ruwa, sai yayi toho ya kuma fid da rassa kamar tsiro.10Amma mutum yakan mutu; ya zama da rauni; hakika, mutum yakan bar yin numfashi, sa'an nan fa ina yake?11Kamar yadda ruwa ke ɓacewa a tafki, da yadda rafi ke rasa ruwa ya ƙone,12haka mutane ke kwantawa basa sake tashi. Sai ko in sammai sun ɓace, ba zasu farka ba ko kuma a tashe su daga barcinsu.13Kash, dama zaka ɓoye ni can Lahira nesa da wahalhalu, ka kuma a ajiye ni a ɓoye har sai fushinka ya wuce, sai kasa mani lokaci da zan kasance a can sa'an nan ka tuna da ni!14Idan mutum ya mutu, zai sake rayyuwa kuma? Idan haka ne, zan so in jira dukkan lokacin gajiyata a can har sai 'yantarwata ta zo.15Zaka kira, zan kuwa amsa maka. Zaka zama da marmarin aikin hannuwanka.16Zaka ƙididdige ka kuma lura da takawata; baza ka bi diddigin zunubina ba.17Za a ɗaure kurakuraina a jaka; zaka rufe laifofina.18Amma har tsaunuka ma sukan faɗi su zama ba komai ba, harma duwatsu akan kawar da su daga wurinsu;19ruwaye sukan zaizaye duwatsu; ambaliyarsu na kwashe ƙurar ƙasa. Haka nan ne, kake hallakar da begen mutum.20Kullum kana cin nasara a kansa, sai ya rasu; ka kan sauya fuskarsa ka aike shi ya mutu.21Idan an girmama 'ya'yansa maza, ba zai sani ba; ko kuma an wulaƙanta su, ba zai gani ba.22Yakan ji ciwon jikinsa ne kawai, yana kuma makokin domin kansa.
Wannan suran ya ci gaba da jawabin Ayuba, wanda ya fara a cikin Ayuba 12:1. Ayuba yana magana da Yahweh.
Wannan yana nufin dukkan mutane, maza da mata; duk an haife su cikin wannan duniya.
Wannan ƙari ne don ƙarfafawa cewa mutane suna rayuwa ne na ɗan kankanen lokaci. AT: "yana rayuwa na ɗan lokaci kaɗan"
Kasancewa "cike da matsala" yana wakiltar fuskantar matsala da yawa. AT: "yana da matsaloli da yawa" ko "yana wahala sosai"
Kamar rayuwar fure, rayuwar mutum takaice kuma tana cikin sauki kashe shi.
Idan aka kwatanta rayuwar mutum da takaitacciyar inuwa wacce take bacewa da sauri.
Ayuba ya nuna cewa baya son Allah ya saka masa da hankali sosai. AT: "Ba kwa kallon ɗayan waɗannan." ko "Ba ku mai da hankali sosai ga waɗannan ba. Ina roƙo kar ku mai da hankali gare ni sosai."
Anan, duba na nufin maida hankali akan mutum domin yin masa sharia. AT: "maida hankali" ko "neman laifi a"
Ayuba yayi wannan tambayar don ya nuna mamakinsa da Allah ke yin masa shari'a duk da cewa shi ba komai ba ne. AT: "Amma kana yin mani sharia"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don ya sa Allah ya yi amfani da abin da ya sani game da abubuwa marasa tsabta ga Ayuba. AT: "Ba wanda zai iya fitar da wani abu mai tsabta daga wani abu mara tsabta"
Wannan za a iya bayyana a cikin tsari mai aiki. AT: "Ka kayyade kwanakin ranakun mutum" ko "Ka shawarta tsawon lokacin da mutum zai rayu"
Wannan na nuna mana cewa Allah ne ke da ikon kayyade watannin da dan adam zai iya yi. AT: "Kai ka ke ƙayyade yawan watannin da zai yi"
Wucewa iyaka yana wakiltar yin rayuwar da Allah yayi wa mutum ya mutu. AT: "Ka sanya lokacin da zai mutu, kuma ba zai iya rayuwa fiye da wannan ba"
mutumin da aka ɗauke shi aiki don yin aiki kuma ya koma gidansa daga baya
An bayyana begen a cikin ayoyi 7-9. AT: "Muna iya fatan itace ta sake rayuwa"
"zai iya sake toho"
Bace na wakilta mutuwa. AT: "don kada rassansa su bac"
"ko da dai"
Wannan sahin itacen da ya rage bayan an sare yawancin bishiyar
Wannan siffantarwa kututture kamar zai iya shan warin ruwa yana wakiltar ruwa kusa da shi. AT: "ko da kuwa ruwa kadan ne kusa da shi"
Itacen da ke fitar rassa yana wakiltar rassan da ke girma a jikin bishiyar.
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa idan mutum ya mutu, ba ya kasancewa. AT: "ba wanda ya san inda yake." ko "ya tafi."
Ayuba ya fara amfani da hotuna na kalma don bayyana yadda hakan yake "mutum ya mutu; ya zama mai rauni" (aya 10).
Gaskiyar cewa mutuwan da ba za a iya juyawa ba aka kwatanta da ruwa wanda ya bushe, kuma ba zai sake komawa ba.
Ayuba ya gama kwatanta tsufa da mutuwa tare da bushewa da ruwa (aya 11).
Kwanciya yana wakiltar mutuwa. AT: "don haka mutane ke mutuwa"
Waɗannan kalmomin guda biyu suna wakiltar tunani iri ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa mutuwa ta ƙarshe ce.
Tashi yana wakiltar sake rayuwa. AT: "kada ku sake rayuwa"
Waɗannan kalmomin guda biyu suna wakiltar tunani iri ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa mutuwa ta ƙarshe ce.
Wannan furci ne mai nuna abin da Ayuba yake so amma ba ya tsammanin zai faru. AT: "Ina so da zaka ɓoye ni"
"ku kulle ni" ko "kulle ni"
Kira wani mutum don tunawa ma'anar kalma ce don yin tunani a kansa. AT: "yi tunani a kaina" ko "tuna da ni"
Amsar da aka nuna ita ce "a'a". AT: "idan mutum ya mutu ba zai sake rayuwa ba"
"in jira duk lokacina a can ko da zan kaji"
AT: "har sai an sake ni" ko kuma "sai kun sake ni"
Kalmar “marmari za a iya bayyana ta da kalmomin nan “so”. AT: "Kuna marmarin" ko "Kuna so"
Anan hannayen Allah suna wakiltar shi yana yin abubuwa. Ayuba yana nufin kansa aikin Allah ne. AT "A gare ni, wanda kuka yi"
Kafar kafa tana wakiltar rayuwarsa ko abin da yake yi. AT: "raina" ko "abubuwan da nake aikatawa"
Waɗannan jumla guda uku suna faɗi dai-dai tunani kuma ana amfani da su tare don ƙarfafa amincin Ayuba cewa Allah zai gafarta masa.
Kiyaye zunuban Ayuba yana wakiltar tunani game da zunubinsa. AT: "ba za ku kalli zunubina ba" ko kuma "ba za ku yi tunani game da zunubaina ba"
Rufe zunubin mutum ta yadda ba za a iya ganin hakan ba yana nuna kin yarda da shi. AT: “za ku ɓoye laifina” ko “za ku yi watsi da ɓata na”
"Rashin lalacewa" anan shine ma'anar ma'anar a rushe ta gaba daya. Wannan lafazin yana faɗaɗa akan kalmar "faɗuwa" kuma yana jaddada cikakken rushewa. AT: “tsaunuka suka fadi su warwatse”
Wannan za a iya bayyana a cikin tsari mai aiki. AT: "duwatsu sun fardado daga wurarensu"
Lalata bege yana wakiltar haifar da abubuwan da mutane suke fata ba abin da zai faru. AT: "Ka hana begen mutum kada ya faru"
AT: "Abubuwan da mutane suka sa bege akai"
Kalmar "shi" tana nufin kowane mutum. AT: "Kullum kuna kayar da mutum" ko "Kullum kuna kayar da mutane"
Wucewa yana wakiltar mutuwa. AT: "ya mutu"
Wannan na wakiltar sa shi ya mutu.
Kaskantar da kai yana nuna rashin kunya. AT fassarar: "idan an basu kunya" ko "idan mutane sun kunyata su"
1Sa'an nan Elifaz Batemane ya amsa ya ce,2"Ya kamata mutum mai hikima ya amsa da ilimin banza kuma cika kansa da iskar gabas?3Koya kamata ya kawo hujja da magana marar amfani ko kuma furce furce waɗanda baza su amfana ba?4Hakika, kana rushe bangirma ga Allah; kana hana sujada gare shi,5gama ƙuraƙuranka suna koya wa bakinka; ka zaɓa ka zama da harshen mutum mai wayo.6Bakinka da kansa ya kashe ka, ba nawa ba; hakika, leɓunanka suna shaida gãba da kai.7Kai ne mutum na fari da aka haifa? An kawo ka cikin rayyuwa kafin tuddai ne?8Ko ka taɓa jin asirin ilimin Allah? Ka ɗauka kai kaɗai ke da hikima?9Me ka sani da bamu sani ba? Me ka fahimta da baya cikinmu muma?10Tare da mu akwai masu furfura da tsoffi maza waɗanda suka girmi mahaifinka ainun.11Ta'aziyun Allah sun yi maka kaɗan ne, maganganu masu taushi zuwa gare ka?12Don me zuciyarka take yaudarar ka? Me yasa ka ke ruwan idanu,13har ka mai da ruhunka gãba da Allah kana fitar da maganganu irin waɗannan daga bakinka?14Wane ne mutum da zai zama da tsarki? Waye shi wanda mace ce ta haife shi da zai zama da tsarki?15Duba, Allah ba ya amincewa da tsarkakansa; hakika, sammai basu da tsarki a idanunsa;16ballantana wanda ya gaza a tsarki ƙazantacce lalatacce kuma, mutum wanda yake shan laifi kamar ruwa!17Zan nuna maka; ka kasa kunne gare ni; zan yi maka shelar abubuwan da na gani,18abubuwan da masu hikima suka gãda daga ubanninsu, abubuwan da kakannisu basu ̀ɓoye ba.19Waɗannan su ne kakanninsu, waɗanda su kaɗai aka ba ƙasar, wanda ba wani baƙo da ya taɓa ratsawa.20Mugun mutum yana murmurɗewa don zafin ciwo dukkan kwanakinsa, shekarun da aka aza wa azalumi yasha azaba.21Ƙarar firgitarwa na cikin kunnuwansa; sa'ad da yake cikin wadata, mai hallakarwa zai auka masa.22Baya tunani cewa zai komo daga cikin duhu; takobi na jiransa.23Sai ya tafi wurare da bam da ban domin abinci, yana cewa, 'Ina yake?' Ya sani ranar duhu ta gabato.24Ƙunci da raɗaɗi sukan tsoratar da shi; su ci nasara a kansa, kamar sarkin da ya shirya domin yaƙi.25Domin ya miƙa hannunsa gãba da Allah, ya kuma nuna girman kai gãba da Mai Iko Dukka,26wannan mugun mutum yana gudu zuwa ga Allah da taurararriyar zuciya, da garkuwa kakkaura.27Wannan gaskiya ne, ko da yake ya rufe fuskarsa da kitsensa ya kuma tara kitse a kwiɓinsa,28ya kuma zauna a rusassun birane; a gidajen da ba mazauna yanzu kuma suna shirye su zama tsibi.29Ba zai yi arzaki ba; arzaƙinsa ba zai daɗe ba kuma mallakarsa baza ta yaɗu a ƙasar ba.30Ba zai fita daga duhu ba; harshen wuta zai ƙona karmaminsa; numfashi daga bakin Allah zai kora shi ya tafi..31Kada ya dogara ga abubuwa marasa amfani, yana ruɗin kansa; gama abubuwa marasa amfani zasu zama ladansa.32Zai faru kafin lokacin mutuwarsa yazo; reshensa ba zai zama kore ba.33Zai kakkaɓe ɗanyun inabinsa kamar kuringar inabi; zai zubar da furanninta kamar itacen zaitun.34Gama tawagar marasa tsoron Allah ba zasu zama da zuriya ba; wuta zata cinye rumfar masu cin hanci.35Sukan ɗauki cikin ƙeta su haifi zunubi; mahaifarsu na ɗaukar cikin rikirkicewa.
Wannan sunan mutum ne. Ana kiran mutane daga Teman Batemane. Duba yadda aka fassara wannan a Ayuba 2:11.
Elifaz ya yi amfani da wannan tambayar don tsauta wa Ayuba. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Mai hikima yakamata ya ba da amsa tare da ilimin mara amfani kuma ya cika kansa da iskar gabas."
"iska mai zafi" ko "iskar hamada"
Elifaz ya yi amfani da wannan tambayar don tsauta wa Ayuba. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Bai kamata yayi iayayya ta amfani da magana mara amfani ba ko kuma yin maganganun cewa yi kome da kyau"
Ma’anoni masu ma’ana sune 1) “saboda abin da kuka fada da aikatawa, wasu mutane ba sa mutunta Allah” ko 2) “kun daina girmama Allah.”
yi karami
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) "ka sa ya zama da wahala wasu su ba da kansu ga Allah" ko 2) "ba ku keɓance kanku ga Allah ba."
toshe hanyar wani
"nazari a" ko "yin tunani a kai"
wannan ya bayyana "zunubi" kamar dai malami ne kuma an nuna bakin Ayuba kamar yana koyo.
Wannan ya yi maganar Ayuba, amma yana nufin “bakinsa” don nuna girmamawa ga abin da yake faɗi. AT: "ku yi magana" ko "ku faɗi abin da kuke faɗi"
Wannan yana nufin hanyar da mutum mai wayo ke magana da "harshensa". AT: "Yin magana a hanyar masu wayo"
mutumin da ke cutar da wasu ta hanyar yin musu karya
Wannan na nufin Ayuba da Elifaz ta "bakinsu" don jaddada abin da suke faɗi bakin ". AT: "An kashe ka ne ta wurin kalaman bakinka, ba ta wurin abin da na faɗa ba" ko "ka kashe kanka ta wurin abin da ka faɗa, ba nine na kashe ka ba."
Amsar a fili anan ita ce "a'a." Ana iya rubuta wannan tambayar a matsayin bayani. AT: "Ba ku ne mutumin farko da aka haife shi ba."
Amsar a fili anan ita ce "a'a." Ana iya rubuta wannan tambayar a matsayin bayani. AT: "Ba a samar da ku ba a gaban tsaunuka." ko "Allah bai halitta ku ba kafin ya halicci tuddai ya zama."
Amsar a fili anan ita ce "a'a." Ana iya rubuta wannan tambayar a matsayin bayani. AT: "Ba ku ji asirin sanin Allah ba."
Wannan tambayar ya nanata cewa ba zai iya taƙaita hikima ga kansa ba. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Ba za ku iya taƙaita hikima ga kanku ba." ko "Ba ku kaɗai ne ke da hikima ba."
Amsar a bayyane anan "ba komai bane." Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Babu wani abin da kuka sani wanda ba mu sani ba." ko "Duk abin da kuka sani, mu ma mun sani."
Wannan yana magana akan mazajen da suke da fahimta kamar dai wani abu ne "a ciki". AT: "Duk abin da kuka fahimta, mu ma mun fahimta." ko "Mun fahimci duk abin da kuka fahimta."
Elifaz ya yi magana game da shi da sauran mutanen da suka koya hikima daga tsofaffi da hikimar da aka bazu ta hanyar mutanen da suka gabata kamar dai waɗannan dattawan suna tare da su. AT: "Mun sami hikima daga tsofaffin masu launin toka, daga mutanen da aka haife kafin mahaifinka ya kasance"
Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ka dauki ta'aziya Yahweh kadan a gare ka, kalaman sa suaki suke da shi agare ka"
"ta'aziya" ko "juyayi"
Anan "zuciya" tana wakiltar motsin zuciyar mutum. AT: "Me yasa motsin zuciyar ku ya dauke ku?" ko "Me yasa kuke ba da damar motsin zuciyar ku ya jagoranci shawarar ku?" (Duba: ko figs idiom)
Wataƙila wannan yana nufin Ayuba ya nuna fushinsa ta yadda idanunsa suka yi. AT: "Me yasa idanun ka ke nuna fushi" ko "Me yasa ka yi fushi"
Ana ruhu na nufin dukan mutum. AT: "juya kanka"
Wannan ya nuna shi yana magana. AT: "don haka kuna faɗar maganganu masu zafi a kansa"
An yi wannan tambayar don ƙarfafawa cewa mutum ba zai iya zama cikakke "tsabta." Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Wani mutum, ba zai iya zama mai tsafta gaba ɗaya ba."
Wani abu da Allah ya yarda da shi a ruhaniya ana maganarsa kamar yana da tsabta ta jiki.
An yi wannan tambayar don jaddada cewa mutum ba zai iya zama cikakke "adali". Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Namijin da aka haifa daga mace ba shi da cikakken adadi."
"malaikunsa"
Anan gani yana wakiltar hukunci ko kimantawa. AT: "a cikin hukuncinsa"
Waɗannan kalmomin guda biyu suna nufin abu ɗaya ne kuma suna nanata yadda mugayen mutane suke.
Wannan yana bayyana zalunci kamar ruwa ne zaka sha. Ya kamanta yadda mugu yake sha'war zunubi da yadda yake sha'war shan ruwa.
Wannan karin magane ne. AT: "Zan yi muku bayani" ko "Zan bayyana maku a fili"
"zan sanar"
Elifaz ya nanata cewa kakanninsu sun koya musu waɗannan abubuwan. AT: "kakanninsu sun koyar da su a sarari"
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Waɗanda Allah ya ba ƙasar so kadai"
Wannan yana nufin cewa ba wani baƙon da ya zauna a cikinsu, takamaimai don kada su rinjayi addinin arna. AT: "Ba wani daga wata ƙasa da ya zo ya sa su yi tunani ba daidai ba game da Allah"
"shan wahala mai yawa." Wannan shi ne zafin jiki ko na rai.
Za a iya faɗin wannan a matsayin aikatau. AT: "Duk shekarun da Allah ya aza"
Wannan karin magana ne. AT: "waɗanda aka shirya" ko "waɗanda aka keɓe"
"Kullum yana jin sautuka waɗanda ke firgita shi"
Elifaz ya ci gaba da bayyanin mugun mutumin da ya fara a Ayuba 15:20.
Anan "duhu" ya na nufin matsala ko masifa. AT: "ɓarna don fitina"
A nan "takobi" ma'anar magana ce da ke nuni ga abokin gaba wanda ke jiran kashe miyagu. Ma'anar mai yiwuwa shine 1) yana cikin damuwa cewa wani zai kashe shi. AT: "yana damuwa cewa wani yana shirin kashe shi" ko 2) tabbas ne cewa za a kashe shi. AT: "wani yana jiran kashe shi"
Anan "burodi" yana nufin abinci gaba ɗaya. AT: "don abinci" "domin neman abinci"
Wannan karin magana ne. AT: "ranar masifa" ko "lokacin mutuwarsa"
Wannan karin magana ne. AT: "yana zuwa nan ba da jimawa ba"
Anan "ƙunci" da "raɗaɗi" suna nufin abu ɗaya ne kuma suna nuna zurfin yanayi ne. Anan an yi magana akan yanayoyin kamar makiyan mugu ne da suke tayar masa.
"fin karfin sa" ko "nasar"
Wannan na nuna yadda ƙunci da raɗaɗi sukan tasar wa mugu kamar yadda sarki yakan shirya domin yaƙi. AT: "kamar yadda sarki yake shiryawa domin yaki haka kuma suke ha kansa"
"ya girgiza fafin hannunsa ga Allah." Wannan alama ce ta tsokanar zalunci.
Wannan na nufin mai mugunta kamar yana gudu ne zuwa wurin Allah domin ya tayar masa. AT: "tayar wa Allah" ko "yin mugunta gaba da Allah"
"da garguwa mai karfi"
Wannan na nufin mugaye na gudu zuwa wurin Allah kamar yadda muka ga a aya ta baya.
An kwatanta wannan mutumin da mai kitse da rauni, yayin da ya gaskanta kansa ya yi ƙarfi don ya yi nasara da Allah. AT: "shi mai rauni ne a fuska mai ƙiba da tsattsarkan kitse"
"wanda aka watsar"
tsarin abubuwan mara amfani
Wadannan maganganu guda biyu sun bayyana cewa zai kasance akasin mai arziki, cewa zai kasance talaka. AT: "zai talauce; duk kuɗinsa zai ɓace"
Duhu anan yana wakiltar mutuwa. AT: "daga duhun mutuwa"
Anan harshen wuta na nufin shariar Allah kuma ƙona karmaminsa na wakiltar dukiyansa zasu bace, zai kuma mutu. AT: "Allah zai kwace dukkan abin da ya mallaka, kamar yadda wuta kan busar raba daga jikin itace"
Anan “numfashin” Allah yana wakiltar hukuncinsa. AT: "Numfashin Allah" ko "hukuncin Allah"
Wannan yana nuna yana mutuwa. AT: "zai mutu"
Wannan yana nuna cewa rashin amfani zai zama ladarsa idan ya dagora da abubuwa marasa amfani. AT: "idan ya dogara a gare su, rashin amfani zai zama ladarsa"
Wannan yana maganar mutumin kamar dai reshen itace ne mai bushe. AT: "zai yi kama da matatce, kamar rassan matatcen itace da baya iya zama kore"
Wannan yana magana game da mugu mutumin wanda ya zama mai rauni, ya mutu kamar kurangar inabin da saukad take danyun inabi. AT: "kamar yadda kurangar inabi da saukad take danyun inabinsa, haka zai kasance da mugu"
Wannan yana magana game da mugu mutumin wanda ya zama mai rauni kuma ya mutu kamar itace zaitun wanda yake furen furanin sa. AT: "kamar yadda itace zaitun kan zubar da furenta, haka mugu zai rasa karfinsa."
"kungiyar mutane marasa tsoron Allah"
Kalmomin “rumfar rashawa” na nufin cewa mugayen mutane sun sayi waɗannan rumfarsa da kuɗin da suka yi ta hanyar rashawa. AT: "rumfarsa da suka saya da cinikinsu za a ƙone su da wuta"
An maimaita irin wannan tunanin sau uku don jaddada irin mugunta da waɗannan mutane suke fitarwa. Wannan yana magana ne game da mutumin da yake shirin aikata mugayen abubuwa da aikata su kamar dai mutumin yana cikin juna biyu ne kuma yana haihuwar waɗannan abubuwan kamar yadda mace take juna biyu kuma ta haifi ɗa. AT: "Suna shirya ɓarna ne da aikata mugunta; koyaushe suna shirin yaudarar wasu ne"
Anan "mahaifar" ana amfani da ita ga mutumin da nufin a cikin cikine kowani irin shiri ke somawa. AT: "sun yi ciki"
1Sa'an nan Ayuba ya amsa yace,2"Na sha jin abubuwa da yawa kamar haka; ku dukka masu ta'aziyar ma abin ban tausai ne.3Maganganu marasa amfani basu da ƙarshe ne? Me ya dame ku da kuke amsawa haka?4Nima zan iya magana kamar yadda kuke yi, in da kuna gurbina; zan iya tattara maganganu in haɗa su tare gãba da ku kuma in girgiza kaina a gabanku don reni.5Zan ƙarfafa ku da bakina, ƙaɗawar leɓunana zasu kawo maku sauƙi.6Idan na yi magana wannan ba zai sauƙaƙe baƙincikina ba; idan na yi shiru, ƙaƙa wannan zai taimake ni?7Amma yanzu, Allah, ka sani na gaji; ka mai da dukkan iyali na wofi.8Ka sa na ƙeƙashe, wannan ma shaida ce gãba da ni; ƙeƙashewar jikina ya tashi gãba da ni, yana kuma shaida gãba da ni a fuskata.9Allah ya kekketa ni cikin hasalarsa ya kuma tsananta mani; Yana tauna haƙoransa cikin zafin fushi; magabcina ya kafa idanunsa a kaina sa'ad da ya kekketa ni.10Mutane sun buɗe bakinsu suna mani gwalo; sun buge ni ba dalili a kunci; sun taru gaba ɗaya gãba da ni.11Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefar da ni cikin hannun mugayen mutane.12Ina zaune lau, sai ya kakkarya ni. Hakika, ya kama ni a wuya ya jefar ya jefar da ni gutsu-gutsu; ya kuma tsai da ni daf a gabansa.13Maharbansa dukka sun kewaye ni; Allah ya sossoke ka'idojina bai yi mani rangwame ba; ya zubar da matsarmamata a ƙasa.14Yana bubbuga bangona akai akai; yana gudu a kaina kamar mayaƙi.15Na ɗaura tsumma a fatata; na soka ƙaho na cikin ƙasa.16Fuskata tayi jawur da kuka; a kan girata akwai inuwar mutuwa17ko da yake ba ta'addanci a hannuwana, addu'ata mai tsarki ce.18Ƙasa, kada ki rufe jinina; kada kukana ya sami wurin hutawa.19Ko yanzu ma, duba, shaidata tana cikin sama; wanda yake lamuni domina yana sama.20Abokaina suna yi mani ba'a, amma idona yana zubar da hawaye ga Allah.21Ina roƙo domin wannan mashaidi a cikin sama yayi muhauwara da Allah kamar yadda mutum zai yi da makwabcinsa!22Domin bayan 'yan shekaru sun wuce, zan tafi wurin da bazan komowa daga can ba.
"Maimakon ku ta'azantar da ni, duk kun sa ni baƙin ciki"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don nuna cewa yana fata za su daina magana da kalmomi marasa amfani. Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ina fatan kalmominku marasa amfani zasu ƙare!"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don tsauta wa Elifaz. Anan kalmar "kai" abu ne mufuradi kuma yana nufin Elifaz, wanda ya gama magana da Ayuba. Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Elifaz, ya kamata ka daina ba da amsa kamar haka!"
Wannan aiki ne da ke nuna rashin yarda.
A iya juya wannan kalman zuwa AT: "in rena ka"
Kalmomin “baki” da “lebe” alamu ne na kalmomin ko saƙonnin da mutum yake faɗi ta amfani da bakinsa da lebe. Anan Ayuba yana magana da ƙarfi yana nufin akasin abin da yake faɗi. AT: "Tabbas maganata ba zata ƙarfafa muku gwiwa ba! Tabbas ba za su sauƙaƙe baƙin cikinku ba" ko "Ta wurin magana da ku kamar yadda kuka yi mini magana ba da daɗewa ba, ba zan ƙarfafa ku ba ko kuma sauƙaƙe baƙin cikinku!"
Anan "bakin" Ayuba na nufin maganarsa. AT: "da abin da na faɗa"
wannan na nufin sako da yake bayarwa. AT: "kallamaina na karfafawa"
Anan an maganar damuwa kamar wata kaya ne mai nauyi da ake iya gani. AT: "ya rage maku damuwa" ko "zai taimake ko ya rage maku damuwa"
Ayuba ya ɗan yi rashin iyali da lafiyar jikinsa ta hanyar da ba za a iya fahinta ba, saboda haka ya na fama da "baƙin ciki mai girma da azaba"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don bayyana cewa yin shiru baya rage baƙin cikin da yake yi. Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "ba ya taimaka mini da komai."
Yanzu Ayuba ya koma gunaguni ga Allah.
"ya halaka dukkan iyalina"
Wannan yana nufin cewa jikin Ayuba ya bushe. AT: "Ka sa jikina ya bushe"
Ayuba yana bayyana ƙeƙashewansa a matsayin mai zarginsa. AT: "kuma mutane suna yin mani kallon mai zunubi ne ni"
Ayuba ya bayyana bakin cikin jikin sa kamar dai yana zargin shi. AT: "Sun ga yadda jikina ya yi zurfi, kuma suna tunanin hakan ya tabbatar da cewa ni mai laifi ne"
Anan an bayana Ayuba da "fuskansa" AT: "gaba da ni"
Wannan ya yi maganar Allah yana sa Ayuba zafi kamar Allah dabba dabba ce kuma Ayuba ce ganima da yake kashewa. AT: "Saboda Allah yana fushi da ni sosai, kamar dai dabbar dabba ce da ta tsage jikina da haƙoranta domin shi maƙiyi ne"
Ayuba yana ambaton Allah “magabcin” sa’ad da yake bayanin yadda ya jawo masa baƙin ciki mai girma.
Wannan karin magana ne. AT: "ya dube ni" ko "kallo a kaina"
Don "cikakke" na nufin kallon mutum da buɗe baki.
Wadannan layin guda biyu suna ma'ana abu daya ne. Tare suka jaddada tunanin Ayuba na Allah ya yaudare shi.
Wannan karin magana ne. AT: "ya sanya ni a ƙarƙashin ikon"
Anan "hannuwan" mutum na nufin "sarrafawa". AT: "ya bashe ni ga ikon"
Anan Ayuba na nunawa cewa wahalarsa kamar wani abu ne da za a iya kakkaryawa. AT: "amma dai na ji kamar ya kakkarya ni"
Ayuba ya yi maganar Allah yana sa shi baƙin ciki da fidda rai kamar dai shi wani abu ne da Allah ya ɗauka ya fashe. AT: "kamar dai ya kama ni da wuya ya ragargaje ni"
Ayuba yayi magana kansa da kansa shine harin da Allah zai kai kamar wanda Allah ya sa shi a matsayin wanda zai harba kibiya a kai. AT: "kamar dai ya sanya ni kamar niyya ne"
Ayuba yayi magana kansa da kansa shine harin da Allah zai kai kamar wanda Allah ya sa shi a matsayin abin hari kuma Allah ya sa maharba sun kewaye shi domin su kai masa hari. AT: "kaman dai maharba sun kewaye shi."
Ayuba yayi maganar zafin da yake ji ta hanyar kwatanta shi da Allah yana huda jikinsa da kibiyoyi. Anan "Allah" yana wakiltar kiban da yake harba. AT: "Ya kan ji kamar kibayan Allah sun soke kodan da hanta, suna zubar da jinina a kasa. Ba ya yafe min"
Ayuba yayi maganar zafin da yake ji ta wajen kwatanta kansa da bango da Allah ya huda.
Ayuba ya kwatanta Allah a matsayin sojan da ke kai masa hari. AT: "Yana kama da shi jarumi ne wanda yake gudu a wurina don ya yi karo da ni"
Ayuba yayi magana game da saka sutura da tsummoki kamar dai kayan yana a jikinsa. Sau da yawa mutane suna sanye da tsummoki don bayyana makoki ko baƙin ciki mai yawa. AT: "Saboda ina makoki na ɗinka summa ta zama tufafina" ko "na sa tufafi da nayi da tsumma, saboda ina makoki"
“Kakakin” Ayuba yana wakiltar ikon da yake da shi a yanzu amma yanzu babu. AT: "Na zauna anan cikin datti, mai cike da raɗaɗi"
Anan giran Ayuba na wakiltar idanunsa. Ayuba yayi maganar idanusa sun zama kamar na matatce. AT: "kewayen idanu na ta yi baki" ko "idanu na sunyi baƙi, kamar idanun matatce"
"Hannuwa" na nufin iyawarsa da ayyukansa. AT: "ban yi ta'addanci ba"
Ayuba yayi maganar kansa yana mutuwa kamar dai za'a kashe shi. Anan "jininsa" alama ce wanda yake magana akan rasuwarsa. AT: Da ma kada ƙasa ya tsotse jinina amma ya dauwama a bisanta domin nuna alamar yadda na mutu."
Ayuba yayi magana game da son kowa san abin da ya same shi kamar dai "kukansa" mutane ne da su gushe ba suna ba da shaidar abin da ya same shi kuma bai taba hutuwa ba. AT: "bari kowa ya ji abin da ya faru da ni"
Ayuba yayi amfani da wannan ne domin abin da zai faɗa a gaba. AT: "kasa kunne"
"na sheda ni mai adalci ne"
Wannan karin magana ne. AT: "a sama" ko "cikin ƙolin sama"
"ba'a" ko "maida abin dariya"
Ayuba na bayyana yadda ya ji baƙin cikin sa. Anan ya bita da yadda yake yawan kuka yayin da yake hawaye yana zubowa daga idanunsa. AT: "idanu na ya cika da hawaye lokacin da nake kuka"
"a gare ni" Anan Ayuba na nufin kansa a cikin mutum na uku.
"kamar yadda mutum yake yi wa makwabcinsa" Anan Ayuba na bayani akan yadda yake so mai sama yayi magana dominsa"
Anan Ayuba na maganar kansa yana mutuwa. AT: "Zan mutu in je wani wuri"
1An cinye ruhuna, kwanakina sun ƙare; kabari na shirye domina.2Lallai da akwai masu ba' a tare da ni; idona dole kullum ya ga cakunar su.3Ka bani shaida, kayi mani lamuni da kanka; wane ne kuma ke nan da zai taimake ni?4Domin kai, Allah, ka hana wa zuciyarsu fahimta; saboda haka, ba zaka ɗaukaka su a bisa na ba.5Wanda yaci amanar abokansa domin ya sami lada, idanun 'ya'yansa zasu dushe.6Amma ya maishe ni abin karin magana ga mutane; suna tofa mani miyau a fuska.7Idona ya sace saboda baƙin ciki; dukkan gaɓaɓuwan jikina sun ƙanjame kamar inuwa.8Mutane masu adalci zasu yi mamaki da wannan; mutum marar aibu zai husata kansa gãba da mugayen mutane.9Mutum mai adalci zai kiyaye hanyarsa; wanda ya ke da hannuwa mararsa laifi zai yi ta ƙaruwa da ƙarfi.10Amma game da dukkanku, kuzo yanzu; ba zan sami wani mai hikima a cikinku ba.11Shekaruna sun wuce; shirye shiryena sun watse, haka kuma marmarin zuciyata.12Waɗannan mutane, waɗannan masu reni, suna sauya dare zuwa rana; haske ya fi kusa da duhu.13Idan gidan da nake bege Lahira ne kaɗai; idan na baza shimfiɗata cikin duhu;14idan kuma na cewa rami, 'Kai ne mahaifina,' da kuma tsutsa, 'Ke ce mahaifiyata ko kuma 'yar'uwata,'15to ina begena ya ke? A game da begena, wa ya iya ganin ko da ɗan kaɗan?16Bege zai tafi tare da ni zuwa ƙofar Lahira ne sa'ad da zamu gangara cikin turɓaya?
Ayuba ya ci gaba magana
Ayuba yana nufin kansa ta “ruhunsa” don ƙarfafa motsin zuciyar sa. Yayi maganar rashin samun karfi kamar dai wani abu ne wanda aka amfani dashi. AT: "An ƙuraye ni" ko "Na ɓace duka ƙarfina"
"lokacina ya ƙare" ko "zan mutu nan bada jimawa ba"
Wannan kalmar ta bayyana “kabari” kamar dai ita ce mutumin da zai karɓi Ayuba a matsayin bako. AT: "na kusan mutuwa a kuma bisne ni."
"Waɗanda suke tare da ni na yin mani ba'a"
"Haƙiƙa" ko "Babu shakka"
Ayuba yana nufin kansa ne ta “idanun” shi don ya jaddada abin da yake gani. AT: "Dole ne in gani koyaushe" ko "Dole ne a koyaushe in ji"
"zagi na su." Kalmar "tsokani" ana iya bayyanata azaman fi'ili. AT: "su tsokane ni" ko "su, suna ƙoƙarin sa ni haushi"
Ayuba ya fara magana da Allah. Anan ya yi magana game da yanayin sa kamar dai yana cikin kurkuku. Yana roƙon Allah ya kawo mana mubaya'a domin a sake shi. AT: "Ya Allah, yanzu ka yi alƙawarin domin a sake ni daga wannan kurkuku" ko "biya bashin da aka sake ni daga kurkuku"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don a jaddada cewa babu wanda zai taimake shi. Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "ba wani kuma wanda zai taimake ni."
Kalmar "su" tana nufin abokansa. An ambace su ta hanyar "zukatansu" don jaddada motsin zuciyar su. AT: "sun kiyaye su" ko "sun kiyaye abokaina"
"ba za ku ba su damar cin nasara a kaina ba"
"duk wanda"
"ya zargi abokan sa da karya don su sami riba" ko kuma "ya bashe da abokansa domin samun lada"
'Ya'yan mutumin ana ambatarsu anan "idanunsu". Wannan magana tana bayanin yaran da ke wahala saboda abin da mahaifinsu ko mahaifiyarsu suka yi. AT: "'Ya'yansa za su wahala saboda shi"
Wannan na nufin mutane na magana akansa suna yin masa dariya kuma suna amfani da sunansa a matsayin zagi. AT: "saboda shi, mutane na amfani da sunana domin zagi" ko "saboda shi mutane na magana da sunana a matsayin karin magana"
"mutane suka tofa a fuskata." A cikin wannan al'adar fesawa wani babban zagi ne. Idan tofa yana da ma'ana dabam a cikin al'adun ku zaku iya rubuta wannan daban. AT: "mutane suna zage ni sosai, ta hanyar tofa mini a fuskata"
Ayuba yana maganar iya ganinsa a matsayin ido. AT: "Ba na iya gani sosai domin damuwana" ko "Na kusan makancewa saboda damuwa"
Inuwa ba su da kauri kuma suna da kauri sosai. Wannan magana ne game da yadda ƙananan sassan jikin Ayuba suke da bakin ciki. AT: "dukkan sassan jikina suna da fadi"
Wannan na nuna dukan jikinsa ya tsamure, musamman hannuwansa da ƙafafunsa. AT: "hannaye da kafafuna"
"zai gigice" ko "zai firgita"
"da abin da ya faru da ni"
Wannan karin magana ne. AT: "zama da damuwa saboda ni" ko "zai yi fushi sosai da"
Wannan karin magana ne. AT: "zai ci gaba da rayuwa ta hanyar adalci"
Wannan yana maganar mutumin da bashi da laifi kamar yana da hannayen tsabta. AT: "wanda ya yi abin da yake daidai" ko "wanda ba shi da laifi"
Wannan baya nufin karfin jiki kawai amma har da karfin zuciyar mutum da kuma motsin zuciyar sa.
Ayuba na magana ga Elifaz, Bildad, da Zofar.
Ayuba na tuhuman abokansa akan kalamansa domin su mai da martani. AT: "ko zo yanzu, domin gardama da ni"
Wannan karin magana ne. AT: "lokacina ya wuce" ko "Rayuwata ya ƙare"
Anan “zuciyar” Ayuba tana wakiltar kasancewarsa a ciki. AT: "shirye-shiryena ba zai taɓa faruwa ba, abubuwan da nake buƙata kuwa ba sosai ba"
Waɗannan jumlolin guda biyu suna magana ne game da Elifaz, Bildad, da Zofar, abokan Ayuba. Magana ta biyu tana karfafa halin da basu dace da juna ba.
Wannan na magana akan mutane da suke cewa dare rana ne, kamar sun canza su. AT: "suna ɗauka rana ne da dare" ko "suna fadar abin da ba gaskiya ba, kamar yadda dare yake dabam da rana."
Ana nufin masu renin na ɗauka da haske sa'ad da duhu ya gabato. AT: "sun dauka haske na kusa da duhu" ko "suna daukawa sa'ad da duhu ta gabato, wannan ne haske"
Maganar "idan" a nan suna da ma'anar "tunda"; Ayuba yana magana kamar dai duk waɗannan abubuwan gaskiya ne. "Tunda kawai gidan ... kuma tunda na yada"
Anan Ayuba yayi magana game da kasancewa cikin shiri ya mutu kamar yadda ya shimfiɗa gado a cikin duhu. AT: "na shirya kaina don tafiya in yi barci a cikin matattu"
"kabari"
Ayuba yayi magana game da kusancin da zai yi da kabarinsa ta hanyar kwatanta shi da kusancin da mutum yake da mahaifinsa. AT: "Kuna kusa da ni kamar mahaifina" ko "Lokacin da aka binne ni, zaku kasance kusa da ni kamar uba"
"da sifa". Tsutsotsi sune ƙananan halittun da ke cin gawawwakin.
Ayuba yayi magana game da kusancin da zai yi da tsutsotsi a cikin kabarinsa ta hanyar kwatanta shi da kusancin da mutum yake da uwarsa da 'yan'uwa mata. AT: "Kina kusa da ni kamar uwata ko 'yar uwata" ko "Za ku kasance kusa da ni kamar uwa ko' yar'uwa"
Amsar a bayyane “babu inda”, domin ba shi da bege. Ana iya rubuta wannan tambayar a matsayin bayani. AT: "Ba ni da fata."
1Sai Bildad Bashune ya amsa ya ce,2"Shin yaushe zaka dena maganarka? Kayi tunani, daga bayan haka zamu yi magana.3Don me za a ɗauke mu dabbobi, marasa wayo a ganinka?4Kai da ka ke yayyage kanka a cikin fushinka, ya kamata a kawar da duniya domin ka ko kuma ya kamata a tumbuƙe duwatsu daga wurarensu?5Hakika, za a ɓice hasken mugun mutum; tarwatsun wutarsa ba za ta haskaka ba.6Haske zai zama duhu a rumfarsa; fitilar da ke bisansa za a ɓice ta.7Takawar ƙarfinsa zata ragu; shirye shiryen kansa zasu kada shi.8Gama za a jefa shi cikin raga da ƙafarsa; zai yi tafiya zuwa cikin tarko.9Tarko zai kama diddigensa; ashibta zata riƙe shi.10An binne masa igiyar zarmewa a ƙasa a ɓoye; tarko ne dominsa akan hanya.11Banrazana zai sa shi tsoro a kowanne gefe; zasu fafari digadigansa.12Arzikinsa zai juya ya zama yunwa, kuma masifa na shirye a gefensa.13Gaɓaɓuwan jikinsa zasu mutu; hakika, ɗan farin mutuwa zai ci gaɓaɓuwansa.14Za a fizge shi daga rumfarsa da yake zaune lafiya a kora shi zuwa ga sarkin razanai.15Mutanen da ba nasa ba zasu zauna a rumfarsa bayan da suka ga wutar ƙibiritu ta bazu cikin gidansa.16Saiwowinsa zasu bushe daga ƙasa; a sama za a daddatse rassansa.17Ba sauran tunawa da shi a duniya; ba zai sami suna a titi ba.18Za a kora shi daga haske zuwa cikin duhu kuma za a kore shi daga wannan duniya.19Ba zai zama da ɗa namiji ko jikoki maza a cikin mutanensa ba, ko ragowar dangi inda dã ya zauna.20Waɗanda ke zaune a kudu zasu tsorata da abin da ya faru da shi wata rana; waɗanda ke zaune a gabas zasu firgita da wannan.21Tabbas haka gidan marasa adalci yake, wuraren waɗanda basu san Allah ba."
Bildad ɗan Shuwa yana magana da Ayuba.
Wannan tambayar tana nuna cewa Ayuba ya dade yana magana. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Dakatar da magana!"
"Ka kasance mai hankali, da" ko "Yi tunani game da waɗannan abubuwan, da"
Bildad yayi amfani da wannan tambayoyin don nuna wa Ayuba cewa kada ya ɗauki abokansa a matsayin dabbobi waɗanda ba za su iya yin tunani ko magana ba. Ana iya rubuta shi azaman bayani a cikin tsari mai aiki. AT: "Bai kamata a ɗauke mu kamar dabbobi ba, kamar wawaye a ganinku." ko "Kada ku ɗauki mu azaman dabbobi ko ku ɗauke mu a matsayin wawa."
Anan gani yana wakiltar hukunci ko kimantawa. AT: "a hukuncinku" ko "a cikin tunanin ku"
Anan Bildad yana nuna cewa saboda fushin Ayuba da rashin biyayya ne ya ji rauni, ba saboda fushin Allah ba kamar yadda Ayuba ya yi faɗi a baya. Kalmar "tsage" anan yana nufin "cuta". AT: "Ku da kuka haddasa rauninku saboda fushinku"
Wannan tambayar tana nuna cewa barin Ayuba, wanda suke ɗauka mai laifi ne, ya 'yantu kamar canza duniya dukka. Bildad yayi amfani da waɗannan ƙarin jita-jita a nan don ƙarfafa yadda yake ƙyamar tunanin wannan. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "roƙon Allah ya bar ka, mai laifi, 'yanci ya kasance kamar wauta kamar roƙon Allah ya bar duniya saboda ka ko kuma Allah ya kawar da duwatsun daga wurarensu don faranta maka!"
Bildad ya yi maganar mai mugunta yana mutuwa kamar ana kunna fitilarsa. AT: "Abin da zai faru shi ne rayukan miyagu kamar ku suna ƙare da sauri kamar yadda muke iya kashe wuta ko kashe wutar wata wuta"
Bildad ya ci gaba da magana game da muguwar mutuwa. Yayi maganar rayuwar miyagu kamar hasken wutar tantinsa. AT: "Zai zama kamar wutar cikin alfarwarsa ta koma duhu, kamar fitilar da ke samansa ta mutu "
Wannan yana magana game da mugu mutumin ba zato ba tsammani yana fuskantar bala'i kamar ba shi da ƙarfin yin tafiya. AT: "Zai zama kamar ba shi da ƙarfin yin tafiya"
"shawararsa ce ta sa shi fadi." Wannan yana maganar mugu yana fuskantar bala'i kamar wanda ya fadi. AT: "nasa shirye-shiryen za su kai shi ga bala'i"
"Kafafun shi za su kai shi cikin raga." Bildad yayi amfani da wannan hoton yana cewa hanyar da mugu yake rayuwarsa yana kai shi ga bala'i kwatsam. AT: "Zai zama kamar ya jagoranci kansa cikin raga, kamar dai yana tafiya kai tsaye ne cikin rami"
Waɗannan jumla hudun suna magana ne game da mugu da yake fuskantar bala'i kamar an kama shi cikin tarko. AT: "Zai zama kamar tarko ne zai kama shi ... tarko zai kama shi"
Anan "diddige" na nufin gaba ɗaya ƙafa. AT: "zai kama ƙafafunsa"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Wani ya ɓoye igiyar a cikin ƙasa don kama shi"
"Firgita ko'ina zai sa shi ji tsoro"
Wannan na maganar abubuwan da suke tsoratar da mugu kamar dai su abokan gaba ne masu bin sa. AT: "zai yi kama da idan 'yan ta'addar za su runtume shi"
Wannan yana magana game da mugu ya zama matalauci da yunwa kamar dai dukiyar sa wani abu ne wanda ya juya zuwa wani abu. AT: "Maimakon ya zama mai arziki, zai zama matalauta da mai fama da yunwa"
Kalmomin “na shirye a gefensa” karin magana ne nuna cewa a koyaushe wani abu yana nan. AT: "zai ci gaba da fuskantar bala'i" ko kuma "ba zai iya guje wa masifa ba"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. Hakanan, wannan yana magana game da wata cuta da ke lalata jikinsa kamar dabba ce wacce ta kai masa hari kuma tana cin sa. AT: "Cutar za ta cinye fatar ta" ko kuma "Cutar za ta lalata fatarsa"
Anan akwai cutar da ke kashe mutane da yawa ana kiranta "ɗan fari na mutuwa." Wannan yana maganar waccan cutar da ke lalata jikinta kamar dabba ce da ta kai hari kuma tana cin sa. AT: "wata cuta mai kisa za ta lalata sassa daban-daban na jikinta"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Bala'i ya kwance shi daga alfarwar sa, inda yake lafiya"
Wannan kwatanci ne game da "Sarki Mutuwa," allahn arna wanda aka yi imanin zai yi sarauta bisa mutuwa. AT: "wanda ke mulkin matattu" ko "sarkin mutuwa"
"Mutanen da ba danginsa bane"
Mutane sun yi amfani da wutar ƙibiritu don kawar da kowace cuta daga mai mutuwa. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "bayan sun bazuwar wutar ƙibiritu a duk faɗin gidansa"
Wannan na maganar mugaye mutumin yana mutuwa kuma baya da zuriya kamar shi itacen da tushensa ya bushe da rassa, ba ya ba da 'ya'ya. AT: "Zai mutu ba zai bar zuriyarsa ba, zai zama kamar itacen da tushensa ya bushe, kuma rassansa duk sun bushe"
Waɗannan jumla suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani da su tare don ƙarfafa gaskiyar cewa babu wanda zai tuna da shi bayan ya mutu.
Waɗannan jumla kalmomin tare sun nanata gaskiyar cewa za a aika miyagu zuwa lahira, wurin matattara.
Kalmar "haske" tana nufin rai, kuma kalmar "duhu" tana nufin mutuwa. AT: "daga hasken rai zuwa duhun mutuwa"
Gaba ɗaya waɗannan kalmomin guda biyu suna jaddada cewa ba zai sami iyali ko zuriya da suka ragu ba.
Kalmomin "a yamma" da "a gabas" sun kasance haɗin gwiwa wanda ke nufin duk mutanen da ke zaune ko'ina. Wannan ƙari ne kamar yadda ba kowa a duniya zai ji labarin abin da ya faru da takamaiman mugu. AT: "Kowane mutum a cikin duniya duka za su firgita da tsoro idan suka ga abin da ya faru da mugu" ko kuma "Mutane da yawa waɗanda ke zaune a gabas da yamma za su firgita da tsoro idan suka ga abin da zai faru da mugaye mutum "
Waɗannan jumlolin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna nufin mutane ɗaya ne. Anan an ambaci waɗannan mutanen ta wuraren da suke zaune. AT: "mutane marasa adalci, waɗanda ba su san Allah ba"
1Sai Ayuba ya amsa ya ce,2"Har yaushe zaku sa ni cikin wahala kuma ku daddatse ni gutsu gutsu da maganganu?3Sau goma ɗin nan kun zarge ni; baku ji kunya ba cewa kun wulaƙanta ni ainun.4Idan lallai gaskiya ne nayi kuskure, to kuskurena ya zama abin da ni kaina zan yi tunani sa.5Idan hakika zaku ɗaukaka kanku fiye da ni ku kuma yi amfani da ƙasƙancina gãba da ni,6sai ku sani Allah bai yi mani dai-dai ba ya kuma kama ni cikin ragarsa.7Duba, na ƙwala ihu, "Ta'adanci!" amma ban sami amsa ba. Na yi kira domin neman taimako, amma babu adalci.8Yasa katanga a hanyata domin kada in iya wucewa, ya kuma sa duhu a tafarkina.9Ya tuɓe mani darajata, ya kuma ɗauke kambi daga kaina.10Ya kakkarya ni ta kowanne gefe, na kuma ƙare; ya janye begena kamar itace.11Ya kuma kunna wutar hasalarsa gãba da ni; ya maishe ni ɗaya daga cikin abokan gabarsa.12Rundunarsa sun tashi gaba ɗaya; sun tula tsibin shara gãba da ni kuma sun kewaye rumfata.13Ya nisantar da 'yan'uwana maza daga gare ni; sanin idona an ware su gaba ɗaya daga gare ni.14Dangina sun yashe ni; aminaina na kurkusa sun manta da ni.15Waɗanda dã na saukar baƙi a gidana da barorina mata sun maishe ni kamar baƙo; ni bare ne a idanunnunsu.16Na kira barana, amma bai ba ni amsa ba ko da yake na roƙe shi da bakina.17Numfashina ya dunguri matata; har ta maishe ni abin watsi ga waɗanda mahaifiyarmu ɗaya.18Har ma 'yan yara ƙanana sun rena ni; idan na tashi zan yi magana, sai suyi magana gãba da ni.19Dukkan idon sani abokanaina sun kyamace ni; Waɗanda nake ƙauna suna gãba da ni.20Ƙasusuwana sun manne wa fatata da kuma naman jikina; ina raye da ƙyar.21Ku ji tausayina, ku ji tausayi na, abokaina, gama hannun Allah ya taɓa ni.22Me yasa kuke farautata kamar yadda Allah ke yi? Zaku taɓa ƙoshi da naman jikina?23Kash, da ma za a rubuta maganganuna! Aiya, dama za a rubuta su a cikin littafi!24Kash, dama da alƙalamin ƙarfe da tamã aka sassaƙa rubutun akan dutse har abada!25Amma a gare ni, na sani mai fansata yana raye, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya;26bayan fatata, watau, wannan jiki, an hallaka shi, sa'an nan a cikin jiki zan ga Allah.27Zan gan shi da idanuna-ni, ba kuma wani da bam ba. Zuciyata ta karai a cikina.28Idan kun ce, 'Yaya zamu tsananta masa! Tushen matsalarsa tana cikinsa,'29sai ku ji tsoron takobi, domin hasala na kawo hukuncin takobi, domin ku sani a kwai shari'a."
Ayuba ya yi magana da abokansa uku.
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don yin gunaguni game da yadda abokansa suke bi da shi. AT: "A daina hana ni wahala kuma a raba ni da kalmomi."
Ayuba ya yi amfani da wannan hoton ya ce kalmominsu suna sa shi baƙin ciki sosai da bege. AT: "Ku azabta ni da maganarku"
Kalmomin nan "Sau goma din" yana nufin hanyar da abokai suka tsauta wa Ayuba gabaki ɗaya. AT: "Ka raina ni gaba ɗaya" ko "Ka ɓata mini rai sau da yawa"
Ayuba yana tsauta musu ne saboda wannan. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa tabbatacce. AT: "Ya kamata kuji kunyar kun wulakanta ni"
Ayuba ya nuna cewa abokan sa ba su da alhakin ci gaba da tsawata masa tunda shi ne ya yi kuskuren. AT: "kuskurena alhakin kaina ne, saboda haka bai kamata ku ci gaba da tsawata mini ba" ko "kuskurena bai yi muku dadi ba, don haka bai kamata ku ci gaba da tsawata mini ba"
"zunubina" ko "kuskurena"
"Idan kuna ganin kun fi ni kyau" ko kuma "Tunda kuna yin kamar kun fi ni kyau"
Yadda abokansa za su yi wannan za a iya bayyana a sarari. AT: "da'awar wulakantata tabbatacciya ce a kaina" ko "yi amfani da wulakancin na a matsayin shaidar cewa ni mai laifi ne"
Ayuba yana magana kamar Allah mafaraucin da ya kama Ayuba ne a cikin ragarsa. Wannan kalmar yana wakiltar Allah yana shan iko da Ayuba da kuma tunanin Ayuba na rashin taimako. AT: "ya kama ni" ko "ya kame ni" ko "ya mallaki abin da ya same ni, don haka ni mai taimako ne"
"Ina ihu don taimako" ko "Ina kuka don taimako"
Ana iya fassara sunan "adalci" tare da jumla wanda ke tabbatar da ma'anar a sarari. AT: "amma ba wanda ya kare ni daga waɗanda ke yi mini rashin daidai"
Ayuba ya yi amfani da wa annan hotunan don ya bayyana yadda Allah ya sa ya ji kamar ba shi da taimako da kuma rashin bege.
Ayuba yana amfani da waɗannan hotunan yana faɗi cewa Allah ya ɗauke masa martabarsa, dukiyarsa, da mutuncinsa baya gareshi.
Ayuba ya yi maganar Allah yana rushe shi kamar dai yadda Ayuba yake gini da Allah yake rushewa. AT: "Ya lalatar da ni ta kowane hanya" ko "Ya yi karo da ni ta kowace hanya"
Kalmar "lalacewa" yana nuna an hallakar da shi gaba ɗaya. AT: "An lalata ni gaba ɗaya"
Ayuba yayi magana game da fushin Allah kamar wuta. AT: "Allah kuma ya yi fushi da ni" ko kuma Allah ya yi fushi da ni"
"Yana ganina a matsayina na makiyi"
Ayuba ya yi maganar Allah ya kawo masa hari kamar dai Ayuba birni ne kuma Allah yana aiko da sojoji su kawo mata hari. AT: "Allah yakan aiko da rundunarsa su yi karo da ni"
Kasancewa "nesa" da wani yana wakiltar rashin yarda ka danganta shi ko taimaka masa. AT: "Allah ya sa 'yan uwana su nisanta ni" ko "Allah ya sa' yan uwana suka ƙi su taimake ni"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "na sanni sun nisanta kaina daga gare ni" ko "abokaina sun ɗauke ni kamar wani baƙo"
"Yan uwa sun bar ni ba tare da taimako ba"
Ayuba ya bayyana yadda mutane suke ɗaukarsa a yanzu kamar dai shi ma ɗan waje ne. Anan gani yana wakiltar hukunci ko kimantawa. AT: "suna ɗauke da ni a matsayin baƙo"
"amma bai amsa mini ba" ko "amma bai zo wurina ba." Amsar ita ce amsa kiran Ayuba.
Kalmomin "bakina" ma'anar magana ce wadda ke nuni ga Ayuba yana magana. AT: "ko da shike na yi masa magana kuma na yi masa ƙara"
Anan "numfashi" yana wakiltar kamshin numfashinsa. Idan wani abu ya yiwa wani laifi, to hakan yana nuna cewa ya ƙi shi. AT: "Matata ba ta son ƙanshin numfashina"
Ayuba yana nufin 'yan'uwansa maza da mata wannan hanyar yana nuna cewa su mutane ne da ya kamata su ƙaunace shi. Ana iya bayyanar da cikakkiyar ma'anar wannan. AT: "an uwana da ya kamata su ƙaunace ni" ko "an uwana mata da ya kamata su ƙaunace ni"
"Duk abokaina na kusa" ko "Duk abokaina waɗanda na ba da asirinsu." Wannan yana nufin abokansa na kusa.
"Ni kawai fata ce da ƙasusuwa" ko "Fata na sandunansu zuwa a kan ƙasusuwana." Ayuba ya yi magana game da ƙasusuwa, fata, da namansa don bayyana kamanninsa. Ya kasance maras kauri sosai, kuma mutane iya ganin kamannin kasusuwarsa.
Wannan karin ma'ana yana nuna cewa ya ɗan tsira ne, kusan ba ya rayuwa. AT: "Ba ni da rai ko kaɗan" ko "Da ƙyar nake rayuwa"
Anan "ya taɓa ni" wani magani ne na "buga ni." Kuma, “hannu” yana wakiltar ikon Allah. Isar da Ayuba ya sha wahala ana magana kamar wanda Yahweh ya buge shi da hannunsa. AT: "domin Allah ya wahalshe ni"
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don yin gunaguni game da yadda abokansa suke bi da shi. AT: "Kada ku tsananta mani ... Allah ya yi!"
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don yin gunaguni game da yadda abokansa suke bi da shi. AT: "Kun cinye naman jikina sosai!" ko "A daina cin naman jikina!"
Wannan karin haske ya faɗi abin da Ayuba yake so. Ana iya bayyana shi a cikin tsari mai aiki. AT: "Ina fata wani ya rubuta maganata"
Wannan karin haske ya faɗi abin da Ayuba yake so. Ana iya bayyana shi a cikin tsari mai aiki. AT "Ina fata wani ya rubuta su a cikin wani littafi"
Wannan karin haske ya faɗi abin da Ayuba yake so. Ana iya bayyana shi a cikin tsari mai aiki. AT: "Da ma a ce wani ya yi amfani da alƙalami da baƙin ƙarfe ya kai su dutsen a cikin dutsen har abada"
"Mai kare ni." A nan "Mai Fansa" yana nufin mutumin da zai ceci Ayuba ta hanyar tabbatar da rashin laifin Ayuba, ya maido da darajarsa, ya kuma ba shi adalci.
Wannan yana nufin tsayawa yayi magana a kotu. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) Mai Fansa zai zama na ƙarshe da zai fara magana a kotu. AT: "zai yi hukunci ko ni mai laifi ne" ko 2) Mai Fansa zai tsaya a wannan kotun na ƙarshe don kare Ayuba. AT: "a ƙarshe zai kare ni a kotu"
Naman nashi yana wakiltar jikinsa, kuma “cikin jikina” yana wakiltar kasancewa a raye. AT: "yayin da nake zaune a cikin jikina, zan ga Allah"
Ma’anoni masu ma'ana sune 1) Ayuba yana jin bege sosai, da godiya, da farin ciki ko 2) Ayuba yana jin gajiya yana jiran Mai Fansarsa.
Wannan karin haske ne. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) lalle za su tsananta wa Ayuba ko 2) cewa za su tsananta masa sosai.
"Tushen" yana wakiltar asalin. AT: "Shi ne asalin dukkan matsalolinsa" ko "Yana da duk waɗannan matsalolin saboda abin da ya yi"
Ma'anar mai yiwuwa shine cewa takobi yana wakiltar 1) Allah yana hukunci dasu. AT: "sannan kuji tsoron cewa Allah zai shar'anta ku" ko 2) Allah ya kashe su. AT: "sai kuji tsoron Allah zai kashe ku"
Za a iya bayyana sunan suna da "fushin" da "horo" tare da ma'anar "fushi" da kuma kalmar "azaba". Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) fushin Allah yana haifar da horo. AT: "saboda Allah zai yi fushi da ku, ya yi muku horo" ko 2) fushin abokan Ayuba yana haifar da horo. AT: "domin idan kun yi fushi da ni, Allah zai yi muku horo"
Ana iya bayyana sunan "hukunci" tare da kalmar aikatau "alƙali." AT: "Allah yana hukunci da mutane"
1Sa'an nan Zofar Banamate ya amsa ya ce,2"Tunane tunanena suna sa ni in amsa da garaje saboda damuwar da ke cikina.3Ina jin zargi da ke kunyatar da ni, amma wani ruhu daga fahimtata yana amsa mani.4Baka san wannan abu tun daga zamanan dã ba, da Allah ya ajiye mutum a duniya:5cin nasarar mugun mutum na gajeren lokaci ne, kuma murnar marar tsoron Allah daɗewarta kamar ƙiftawar ido ne?6Ko da tsayinsa ya kai sammai, kuma kansa ya taɓa gizagizai,7duk da haka irin mutumin nan zai lalace tuttur kamar najasarsa; waɗanda suka gan shi zasu ce, 'Ina yake?'8Zai yi firiya ya ɓace kamar mafarki ba za a kuma same shi ba; hakika, za a fafare shi kamar wahayin dare.9Idon da ya ganshi ba zai ƙara ganin sa ba; mazauninsa ba zai ƙara ganinsa ba.10'Ya'yansa zasu roƙi gafarar matatalauta; hannuwansa zasu mayar da dukiyarsa.11Ƙasusuwansa suna cike da ƙarfin ƙuruciya, amma zai kwanta tare da shi cikin turɓaya.12Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa, ko da yake ya ɓoye shi ƙarƙashin harshensa,13ko da yake ya riƙe shi a can bai bari ya fita ba amma ya riƙe ya gama cikin bakinsa -14abincin da ke cikin hanjinsa zai juya ya zama da ɗaci; ya zama dafin maciji a cikinsa.15Yakan haɗiye arziki, amma sai ya haras da su kuma; Allah zai tutturo su waje daga cikinsa.16Zai sha dafin maciji; harshen kububuwa zai kashe shi.17Ba zai ji daɗin rafuffuka ba, yalwar zuma da madara.18Zai mayar da rabon wahalar aikinsa kuma ba zai iya ya cin sa ba; ba zai ji daɗin dukiyar da ya samu ta wurin cinikaiyarsa ba.19Gama ya wulaƙanta matalauta ya kuma yashe su; ya ƙwace gidajen da bai gina ba ƙarfi da yaji.20Domin bai san ƙoshi ba, ba zai iya tanada wani abin da yake marmari ba.21Ba wani abin da ya rage da bai cinye shi ba; saboda haka arzikinsa ba zai daɗe ba.22A cikin yalwar wadatarsa zai faɗa cikin wahala; hannun kowanne matalauci zai yi tsayayya da shi.23Sa'ad da yake gaf da cika cikinsa, Allah zai jeho masa fushinsa mai ƙuna a kansa; Allah zai kwararo masa shi sa'ad da yake cin abinci.24Ko da yake mutumin nan ya guje wa makamin ƙarfe, bakan tagulla zai harbe shi.25Idan ya cire shi a bayansa sai bakin mai tsini ya shiga hantarsa. Razana zata faɗo masa.26Duhu ne baƙi ƙirin ke ajiye domin kayansa masu daraja; wutar da ba a izawa zata cinye shi; zata cinye ragowar abin da ke rumfarsa.27Sammai zasu bayyana zunubansa, ƙasa kuma zata miƙe gãba da shi ta zama shaida.28Dukiyar gidansa zata ɓace; kayayyakinsa zasu gudu a ranar hasalar Allah.29Wannan shi ne rabon mugu daga Allah, gadon da Allah ya ajiye masa kenan."
Zofar ya ba Ayuba amsa.
Tunanin Zofar na sanya shi yin wani abu yana nuna tsananin sha'awar yin wani abu. AT: "Ina son in amsa muku da sauri"
Dalilin damuwar za a iya bayyana a sarari. AT: "saboda ina matukar damuwa da ku" ko "saboda ina matukar damuwa saboda abin da kuka faɗi"
AT: "Na ji kuna tsawata mini, kuma abin da kuke faɗi na ƙasƙantar da ni" ko "Kuna wulakanta ni ta yadda kuke kushe ni"
Anan "ruhu" mai yiwuwa yana nufin tunani ne ko ra'ayi. AT: "tunanina ya fahimce ni"
Zofar ya yi amfani wata tambayar don ya sa Ayuba ya yi tunani mai zurfi game da abin da zai faɗi a yanzu.
Zophar ya yi amfani da wata yar magana don sa Ayuba ya yi tunani mai zurfi game da abin da zai faɗi a yanzu. Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Tabbas kun san ... mutum a doron ƙasa, nasarar ... zuwa wani ɗan lokaci."
Ana iya bayyana sunan "nasara" tare da kalmomin nan "nasara" ko "bikin." AT: "mugu ya yi nasara a ɗan kankanin lokaci" ko kuma “mugu ya yi murna da ɗan lokaci kaɗan”
Kalmar nan ta "murna" za a iya bayyana ta da kalmar ''yi murna." Kalmar "lokaci" ƙari ne don ƙarfafawa cewa lokaci kaɗan ne sosai. AT: "marar tsoron Allah yakan yi farin ciki na ɗan lokaci kaɗan" ko kuma "marar tsoron Allah yakan yi farin ciki na ɗan ƙarancin lokaci"
Tsayin mugayen mutum yana wakiltar daraja ko girman kansa. Hakanan, a nan "ya kai har sama" yana wakiltar kasancewa mai girma. AT: "Ko da yake sunanshi yana da girma" ko "Ko da yake fahariyarsa tana da girma"
"kuma duk da cewa kansa yana da girma kamar girgije." Wannan kuma yana nuna martabarsa ko girmansa mai girma. Wannan yana nufin daidai da kalmar da ta gabata.
Najasa yana haɗuwa da ƙasa kuma ya ɓace. Bayani game da najasa yana iya nuna cewa mugu bai da daraja. AT: "zai shuɗe kamar najasarsa, wadda ta ɓace cikin ƙasa"
"Mai mugunta zai yi"
Anan "tashi daga nan" kuma "a kori shi" yana wakiltar ɓacewa. Hakanan suna iya nuna cewa an manta da su, tunda mafarki da wahayi sun ɓace lokacin da mutane suka manta da su. AT: "Zai ɓace kamar mafarki ... za a manta da shi kamar wahayin dare"
Ido yana wakiltar mutum. AT: "Duk wanda ya gan shi" ko "Mutanen da suka gan shi"
Kalmomin "wurinsa" yana wakiltar waɗanda suke zaune a wurinsa. AT: "mutanen da ke zama a wurinsa" ko "danginsa"
"Mugayen yaran"
Anan kalmar "hannaye" tana nufin 'ya'yan mugu. Idan ya mutu, 'ya'yansa dole ne su komar da duk abin da ya karɓa daga wasu.
Kalmar "ƙasusuwa" tana wakiltar jikinsa. Kasancewa "cike da ƙarfin ƙuruciya" wakiltar kasancewa mai ƙarfi kamar saurayi. AT: "Jikinsa yana da ƙarfi kamar jikin saurayi"
Kalmar "ita" tana nufin ƙarfin samartakarsa. Maganar "kwanciya ... cikin ƙura" tana wakiltar mutuwa. Karfin mutuwa alama ce ta bacewa. AT: "amma ƙarfin ƙuruciyarsa zai mutu tare da shi" ko "amma ƙarfin ƙuruciyarsa zai shuɗe lokacin da ya mutu"
A nan "mugunta tana da daɗi" tana wakiltar mutum yana jin daɗin yin mugayen abubuwa. AT: "Ko da yake yin munanan abubuwa abune mai daɗi kamar cin abinci mai daɗi a cikin bakin"
Lokacin da abinci ya zama mai daci a cikin ciki, yakan haifar da zafi da ɗanɗano mai ɗaci. Wannan kirin magana ne ga mutumin da yake fuskantar mummunan sakamakon aikata munanan ayyuka. AT: "waɗannan mugayen abubuwa sun zama kamar abinci wanda ya zama mai daɗi a cikin ciki" ko "sakamakon waɗannan mugayen abubuwa suna daɗaɗani kamar abinci wanda gubaya kan cika ciki"
Wannan hoton ya fi abinci ƙanƙanta a ciki. Wannan karin magana ne ga mutumin da yake fuskantar mummunan sakamakon aikata munanan ayyuka. AT: "Sakamakon aikata waɗannan mugayen abubuwa suna da laushi kamar gubar da ke jikin sa"
"guba" ko "macizai masu zafin dafi"
Zofar yayi magana akan samun da kuma asarar dukiya kamar dai abinci ne da mutum ya ci da ama. AT: "Mugu ya zama mai wadata, amma yana asarar dukiyarsa kamar mutumin da ya cinye abincinsa. Allah yana sa ya rasa shi dukka"
Anan "tsotse dafin maciji" yana wakiltar aikata mugunta. Duk suna da haɗari sosai. AT: "Yin mugunta yana kama da shan dafin maciji" ko "Zai aikata mugunta kuma ya sanya ransa cikin haɗari kamar mutumin da ke shan guba na asps"
Harshen macijin yana wakiltar gubarsa. AT: "ciwan maciji mai guba zai kashe shi" ko "maciji zai ciji shi kuma ya mutu"
“Koguna” da “rafuffuka” alamu ne da ke wakiltar yalwa. "Zuma" da "man shanu" alamu ne masu wakiltar kyawawan abubuwa da Allah yake ba mutane. AT: "yalwar kyawawan abubuwa waɗanda Allah ya bai wa mutanensa"
A yadda aka saba “rabon wahalar aikinsa” kawai yana nuni ne da sakamakon aikin sa. A wannan halin yana nufin abubuwan da mugu ya sata. AT: "abubuwan da ya yi aiki don samo" ko "abubuwan da ya sata"
Anan "mai cinye" yana wakiltar ɗaukar abubuwa don kansa. AT: "Babu wani abin da ya rage wanda bai karɓa wa kansa ba" ko "Ya ɗauki komai nasa, ba abin da ya rage"
Anan "hannun" yana wakiltar iko, kuma "hannu ... zai yi gāba da shi" yana wakiltar mutanen da ke kai masa hari. Ana iya bayyana sunan "talauci" tare da taken "matalauta." AT: "duk wanda yake cikin talauci zai kai masa hari" ko "duk wanda yake talaucin zai kai masa hari"
“Faushin fushinsa” yana wakiltar fushin Allah da horo. Saka azaba a kansa na nuna hukuncin azabtar dashi mai tsanani. AT: "Allah zai yi fushi kuma ya jefa azabarsa a kansa" ko "Allah zai yi fushi kuma ya azabtar da shi mai tsanani"
"Allah zai sa a yi ruwan sama a kansa." Anan "ruwan sama da shi" yana wakiltar haifar da azaba mai yawa ga mutumin. AT: "Allah zai azabta shi da tsanani"
Nan da nan zai ji tsoro sosai. AT: "ya firgita"
"Cikakken duhu" anan wani kalmomin ne na hallaka. AT: "An halakar da dukiyarsa saboda taskokinsa" ko kuma "za a lalata taskokinsa"
Kalmomin "ba a izawa" yana nuna cewa babu mutumin da zai fara barin wuta. Maimakon haka, Allah zai sa wutar. AT: "wutar da mutane bata fara ba za ta halaka shi" ko "Allah zai sa wuta ta rusa shi"
Anan "cinye" shine ma'anar lalata. AT: "wutar za ta lalace"
Ma'anar mai yiwuwa ita ce: 1) waɗanda suke rayuwa a cikin sammai da ƙasa ko 2) Zofar yana kwatanta sama da ƙasa kamar cewa su mutane ne waɗanda zasu ba da shaida a kotu game da mugu.
Anan "ya kwarara" yana wakiltar cire daga gare shi. AT: "za a karɓe kayansa daga gare shi, kamar kayayyaki waɗanda suke iyo ambaliyar ruwa, a kan"
"mallakarsa"
Anan "fushi" yana wakiltar horo. Ana iya bayyana kalmar "fushin" tare da kalmar aikatau. AT: "ranar da Allah zai yi wa mutane horo"
Anan “rabo daga wurin Allah” yana wakiltar abin da Allah ya yanke shawara ya kamata ya faru ga wani. Ana maganar kamar dai wani abu ne da Allah zai bashi. AT: "Abin da Allah ya yanke shawara ya faru da mugu kenan"
Wannan yana wakiltar abin da Allah ya yanke shawara ya kamata ya faru ga wani. Ana maganar kamar wani abu ne da Allah zai ba shi gado.AT: "abin da Allah ya yi niyya ya ba shi" ko "abin da Allah ya shirya ya faru da shi"
1Sai Ayuba ya amsa ya ce,2"Ku kasa kunne da kyau ga maganganuna, kuma bari wannan ya zama ta'aziyar da kuke yi mani.3Ku daure da ni, ni kuma zan yi magana; bayan nayi magana, sai ku cigaba da ba'a.4Ni dai kam, ƙarata ga mutum ne? Don mene ne bazan yi rashin haƙuri ba?5Ku duba ni kuyi mamaki, ku ɗibiya hannuku a kan bakinku.6Sa'ad da nayi tunani akan wahaluna, nakan tsorata, makyarkyata sai ta kama jikina.7Me yasa mugayen mutane suke a rayuwa, su tsufa, su girma su ƙasaita a iko?8Zuriyarsu ta kafu tare da su a kan idanunsu, kuma jikokinsu su da su a idanunsu.9Gidajensu lafiya ba tsoro; kuma babu hukuncin Allah a kansu.10Bijiminsu na barbara; baya fasa yi; shanunsu suna haifuwa basa yin ɓarin 'yan maruƙansu'11Sukan aika da 'yan maruƙansu kamar garke, 'ya'yansu suna rawa.12Suna waƙa da kuge da molo kuma suna farinciki da waƙar sarewa.13Suna zaman kwanakinsu cikin wadata, su gangara shuru zuwa Lahira.14Sai su cewa Allah, 'Ka rabu da mu domin ba ma son wani fahimta game da hanyoyinka.15Wanene Mai Iko Dukka, da zamu yi masa sujada? Wace riba ce zamu samu idan muka yi addu'a gare shi?'16Duba, arzikinsu ba a hannunsu yake ba? Ba ruwana da shawarar mugayen mutane.17Sau nawa fitilar mugayen mutane ana hure ta, ko kuma masifarsu ta auka masu? Sau nawa yakan faru sai Allah ya rarraba ma su baƙin ciki cikin fushinsa?18Sau nawa su ke zama kamar tattaka cikn iska ko kamar ƙaiƙai da iskar hadari ke kwashewa.19Kun ce, 'Allah yana tara alhakin mutum domin 'ya'yansa su biya.' Bari shi da kansa ya biya, domin ya san laifinsa.20Bari idanunsa su ga hallakarsa, kuma bari ya sha hasalar Mai Iko Dukka.21Gama me ya dame shi da iyalinsa da ya bari bayan an datse kwanakinsa?22Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da shima yana shari'anta har waɗanda suke sama?23Wani mutum yakan mutu cikin goshin ƙarfinsa, ya yi shuru a natse.24Jikinsa na cike da madara, kuma ɓargon ƙashinsa da danshi.25Wani mutum kuma ya mutu cikin ɓacin zuciya, wanda bai taɓa ɗanɗana wani abin kirki ba.26Dukkan su sukan kwanta a cikin turɓaya; tsutsotsi su mamayesu.27Duba, na san tunaninku, kuma da hanyoyin da ku ke so ku aibata ni.28Domin kun ce, 'Ina yanzu gidan ɗan sarki? Ina rumfar da mugun mutumin nan ya zauna a ciki?'29Baku taɓa tambayar mutane matafiya ba? Ko ba ku san shaidar da zasu iya faɗi ba,30cewa mugun mutum an keɓe shi daga ranar masifa, an kuma janye shi daga ranar hasala?31Wane ne zai zargi hanyoyin mugun mutum a fuskarsa? Wane ne zai sãka masa domin abin da ya yi?32Duk da haka za a kai shi kabari; mutane zasu yi ta kiyaye kushewarsa.33Ƙurar kabarinsa da aka tula a kansa zata zama masa da daɗi; dukkan mutane za su bi bayansa, kamar yadda mutanen ba su ƙidayuwa sun sha gabansa.34To ƙaƙa zaku ta'azantar da ni da rashin hankali, tun da cikin amsoshinku babu komai sai ƙarairayi?"
Ayuba ya fara amsa zarge-zargen Zofar.
"Ku kyale ni" ko "Kuyi hakuri da ni"
"Kuna iya ci gaba da ba'a ni." Ayuba yana amfani da zagi don nuna cewa abokansa za su yi watsi da abin da zai faɗi kuma su ci gaba da yi masa ba'a.
Ayuba yana amfani da tambayoyi don jaddada cewa yana tunanin cewa dai-dai ne a gare shi ya yi ƙara ga Allah. AT: "Ba na gunaguni ga mutum. Ina da 'yancin yin rashin haƙuri" (Duba: fig_rquestion)
"rufe bakinka da hannunka." Ma’anoni masu ma’ana sune 1) wannan amsa ce don nuna mamaki. AT: "rufe bakinka da hannunka" ko 2) wannan alama ce da mutumin ba zai yi magana ba. AT: "kada ku ce komai"
"tsoro yana sanya jikina ya yi rawar jiki" ko "Ina rawar jiki da tsoro"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don nuna cewa abokan sa ba dai-dai ba ne suyi tunanin mugayen mutane suna shan wahala koyaushe. AT: "Lallai mugayen mutane suna ci gaba da rayuwa, sun tsufa, kuma suna da ƙoshin lafiya."
Waɗannan lafazin biyu suna ma'ana daidai kuma sun jaddada cewa wannan gaskiyane.
Anan "gidaje" yana nufin dangin da ke zaune a cikinsu. AT: "Iyalansu"
Wannan yana nufin hukuncin Allah.
Ayuba ya gwada waɗannan yaran da raguna don ƙarfafa cewa suna gudu, wasa, kuma suna farin ciki.
Wannan itace kyakkyawar hanyar da suke cewa sun mutu. AT: "sun mutu cikin salama"
Wannan yana nufin yadda Allah yake son mutane suyi.
Mugayen mutane suna amfani da waɗannan tambayoyin suna yi wa Allah ba'a. AT: "Ba mu yi imani cewa wannan Allah Maɗaukaki ya cancanci bautarmu ba. Ba zai iya yi mana kome ba."
Anan "hannaye" suna nufin ikonsu ko sarrafawa. Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don ƙalubalantar abokansa. AT: "Duba, waɗannan mugayen mutane suna da'awar cewa suna wadatar da kansu!"
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don ƙarfafa cewa ga alama cewa Allah ba ya horon mugaye sau da yawa. AT: "Ba sau da yawa ... bala'o'insu ya same su."
Ayuba ya gwada rayuwar mugaye da fitila mai ci.
Ayuba yayi amfani da wannan tambaya ta biyu don nanata cewa ga alama cewa Allah baya azabta mugaye sau da yawa. AT: "Ba sau da yawa ... a cikin fushi."
Ayuba yayi amfani da wannan tambaya ta uku don nanata cewa ga alama cewa Allah baya azabta miyagu sau da yawa. AT: "Ba sau da yawa ... hadari yakan kwashe."
Ana magana da mutuwar mugaye kamar ba su da ƙoshin ƙaiƙayi da ciyawa waɗanda suke shuɗewa. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah yakan ɗauke su kamar yadda iska ke hura da ƙaiƙayi"
Ana ƙara waɗannan kalmomin da yawancin juzu'ai don ya bayyana sarai cewa Ayuba yana faɗar abokanansa a magana ta gaba.
Ana magana da laifi cikin wani abu wanda za'a iya adana shi don amfani na gaba. Anan "biya" yana nufin hukuncin zunubi. AT: "Allah yana kiyaye rikodin laifin mutum, sannan yakan azabtar da yaran mutumin saboda muguntar ayyukansa"
Yanzu Ayuba ya fara faɗi ra'ayin nasa. Zai iya taimaka a faɗi wannan a bayyane ta yin amfani da ambato ba kai tsaye. AT: "Amma ina cewa ya kamata ya biya shi da kansa, ... san laifinsa '"
Anan "idanu" yana nufin mutumin. AT: "Bari shi ya gani"
Anan ana maganar fushin Allah kamar wani abin sha ne wanda mutum zai iya ɗanɗana shi, kuma ɗanɗano wata alama ce ta fuskantar sha. Ayuba yana son mugu ya ɗanɗani azabar Allah.
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don nuna cewa hukunta 'ya'yan mugayen ba su da tasiri. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Gama miyagu ba ya kula da abin da zai faru da danginsa bayan ya mutu!"
Wannan ita ce hanyar nuna ladabi da ya ce ya mutu.
Ayuba ya yi wannan tambayar don ya jaddada cewa Allah ya san komai. AT: "Babu shakka, babu wanda zai iya koyar da Allah komai tunda yana yin hukunci da waɗanda ke cikin sama."
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) "waɗanda suke cikin sama" ko 2) "mutane masu iko."
Ayuba ya bambanta wannan mutumin da ya mutu cikin ƙoshin lafiya da salama ga mutumin da ya mutu cikin baƙin ciki da jin zafi a cikin Ayuba 21:25. Kuna iya bayyana wannan dalla-dalla. AT: "Idan mutane biyu suka kasance, mutum zai iya mutu da cikakken ƙarfinsa"
Ayuba ya bambanta wannan mutumin da mutumin da ya mutu cikin salama a cikin Ayuba 21:23.
Anan ana maganar baƙin ciki kamar ya ɗanɗani danshi mai ɗaci, kuma "kurwa" tana nufin mutum ne dukka. AT: "da fushi da fushi" ko "bayan rayuwa ta baƙin ciki"
Wannan ita ce hanya mai ladabi da za a ce sun mutu. AT: "Dukansu sun mutu mutane suna binne su"
Tsutsotsi suna da alaƙa da lalata gawawwakin mutane. AT: "tsutsotsi a cikin datti suna cin gawawwakinsu"
Ayuba ya yi imanin cewa abokansa za su yi wannan tambayoyin don su yi masa zargi. Tambayoyi guda biyu suna nufin abu ɗaya. AT: "Duba, gidan mugaye mai mulki ya ɓace. Rumfar ta mugu ta ɓace."
Ayuba ya yi amfani da waɗannan tambayoyin don tsauta wa abokansa don ba su koya daga mutanen da suke tafiya. AT: "Ya kamata ku saurari waɗanda suka yi tafiya zuwa wurare masu nisa." (Duba:
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don ya saɓa wa imanin abokansa cewa ana hukunta masu mugunta koyaushe. AT: "Babu wanda ke la'antar mugaye a fuskarsa."
Wannan yana nufin babu wanda zai je kai tsaye zuwa wurin mugaye ya hukunta shi da kansa.
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don ya saɓa wa imanin abokansa cewa ana hukunta masu mugunta koyaushe. AT: "Ba wanda zai saka masa da munanan ayyukan da ya yi."
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "mutane za su ɗauke shi"
Ayuba yana hasashe cewa mutum da ya mutu zai ma ji daɗin datti da aka ɗora masa. Wannan yana nufin cewa mugu zai iya samun mutu mai kyau da kuma binnewa mai kyau bayan rayuwa ta cika. ''Ƙurar'' na nufin duniya da ke rufe kabari. AT: "Zai ji daɗin rufe shi da datti na kwari" ko "Zai ji daɗin binne shi cikin datti na kwarin"
Ayuba ya nanata cewa babban taron mutane za su kasance cikin jana'izar wannan muguwar mutum don girmama shi. AT: "mutane da yawa suna zuwa wurin kabari"
Ayuba ya yi amfani da tambaya don tsawata wa abokansa. AT: "Ba za ku iya ta'azantar da ni da maganar banza ba. Duk amsoshin ku na ƙarya ne."
1Sai Elifaz Batemane ya amsa, yace,2"Mutum zai zama da amfani ga Allah? Mutum mai wayau zai zama da amfani ga gare shi?3Zai zama da jin daɗi ga Mai Iko idan ka zama mai adalci? Zai zama da wata riba gare shi idan hanyoyinsa marasa laifi ne?4Ai ba domin kana tsoronsa ba ne ya kwaɓe ka, ko kuma ka ɗauki shari'a?5Ba babbar muguntarka ba ce? Ashe babu ƙarshen muguntarka?6Domin ka bukaci a ba ka bashin da ke daga wurin ɗan'uwanka ba tare da wani dalili ba, ka kuma ƙwace tufafi daga wurin wanda ba shi da komai.7Ka hana ruwa ga mutane masu ƙishinruwa su sha; ka hana abinci ga mutane masu jin yunwa8ko da ya ke kai mutum ne mai iko, kana da kayan duniya, ko da ya ke kai, mutum ne mai girma, kana rayuw a cikinta.9Ka kori mata da mazajensu suka mutu ba tare da komai ba; hannuwan marayu sun karye.10Saboda haka, ramummuka a ko'ina kewaye da kai, sun kuma kawo maka tsoron damuwa.11Akwai duhu, saboda har baza ka iya gani ba; ruwaye masu yawa sun sha kanka.12Ashe Allah ba a saman sammai yake ba? Dubi taurare a sama, yaya nesan su a can!13Kace, 'Me Allah ya sani? Zai iya shari'a a cikin baƙin duhu?14Gizagizai masu duhu sune ke rufe shi, saboda haka ba ya ganin mu; yana tafiya a kan iyakar sararin sama.'15Kana bin tsohowar hanyar da mugayen mutane suke tafiya a kai--16waɗanda aka ƙwace kafin lokacinsu, waɗanda tuwasunsu suka shafe kamar rafi,17sune waɗanda suka ce da Allah, 'Tafi daga wurin mu,' su ne suka ce, 'Mene ne Mai Iko zai yi da mu?'18Duk da haka ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, shirye-shiryen mugayen mutane suna nesa daga gare ni.19Adalan mutane su na ganin kaddararsu suna murna; mutane marasa laifi kuma suna dariyarsu.20Sun ce, 'Babu shakka waɗanda suka taso gãba da mu an yanke su, wuta kuwa ta lashe mallakarsu.'21Yanzu ka yarda da Allah salama ta kasance tare da kai; ta wannan hanya, abu mai kyau zai zo gare ka.22Karɓi, ina rokon ka, ka koya daga bakinsa; ka riƙe kalmominsa a zuciyarka.23Idan zaka juyo ga Mai Iko, za a sake gina ka, idan za ka ajiye rashin adalci nesa daga gidanka.24Ka ajiye dukiyarka can cikin ƙura, zinariya daga ofir a cikin duwatsun rafuffuka,25Mai Iko zai zama dukiyarka, da azurfa mai daraja ga gare ka.26Sa'an nan zaka sami farin ciki a wurin Mai Iko, za ka tada fuskarka ga Allah.27Za ka yi addu'a gare shi, shi kuma zai ji ka; zaka kiyaye alkawaran da ka yi masa.28Za ka kuma hurta komai, za a kuma tabbatar maka, haske zai haskaka a hanyoyinka.29Allah yakan ƙasƙantar da mutum mai girmankai, yakan ceci mai tawali'u.30Zai ceci kowane mutum wanda ke da laifi; wanda za a ceta ta wurin abin da hannuwansa ke yi dai-dai."
Duk tambayoyin suna ma'ana dai-dai ne. Elifaz yana amfani da tambayoyi don ƙarfafa cewa ayyukan mutum da hikimarsa ba sa amfanar da Allah. AT: "Mutum ba zai iya amfanuwa da Allah ba. Mai hikima ba zai iya amfanuwa da shi ba."
Duk waɗannan kalmommin suna nufin abu ɗaya ne. Elifaz ya yi amfani da tambayoyi don ya nanata cewa abin da Ayuba ya yi bai taimaka wa Allah ba. AT: "Madaukaki ba ya jin daɗin komai idan kun kasance adali.
Elifaz ya yi amfani da tambayoyi don ya zargi Ayuba kuma ya zarge shi da yin mugayen zunubai. AT: "Tabbas ba saboda kun keɓe shi ga Allah ba, Allah yana tsauta muku kuma ya ɗauke ku zuwa hukunci!"
Elifaz ya yi amfani da tambayoyi don ya zargi Ayuba kuma ya zarge shi da yin mugayen zunubai. AT: "Kamar yadda kuka sani, yana yin hukunci a kanku saboda muguntarku mai girma ce kuma kuna ci gaba da yin zunubi!"
Wannan yana nufin mai ba da bashi wanda ke ɗaukar wani abu daga mai ba da bashi don tabbatar da cewa mai ba da bashi ya biya shi.
Elifaz yana zargi Ayuba da ɗaukar kayan takalawa kamar garantin abin da suka aro daga wurin Ayuba.
Anan "burodi" yana nufin abinci gaba ɗaya. AT: "an hana abinci"
Elifaz yana zargin Ayuba da ƙwace ƙasa daga hannun talakawa kuma bai ƙyale su su zauna a ciki ba. Yana nanata wannan magana ta hanyar maimaita shi sau biyu.
Elifaz yana ƙara yawan adadin abubuwan da Ayuba ya mallaka don ya nuna Ayuba mai haɗama ne. AT: "sun mallaki ƙasa mai yawa"
"Kun sa gwauraye suka tafi da komai ba"
Anan "makamai" suna nufin iko. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "har ma kun zalunci marayu"
Waɗannan kalmommin don matsala da haɗari. AT: "kullum kuna cikin hatsari ... kuna jin tsoro ba gaira ba dalili"
Kowace ɗayan waɗannan kalmommin na nufin matsaloli da haɗari suna kewaye da Ayuba saboda zunubinsa.
Elifaz ya yi amfani da wannan tambayar ya ce Allah yana ganin zunubin Ayuba kuma zai shar'anta shi. AT: "Allah yana cikin ɗaukakar sama kuma yana ganin duk abin da yake faruwa a duniya."
Elifaz ya nuna cewa Allah ya fi taurari girma. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "Duba yadda taurari suke. Allah ma ya fi taurari girma!"
Mutuwa tana kwatantawa da Allah yana kwace su. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "waɗanda suka mutu" ko "waɗanda Allah ya ɗauke su"
Mutuwar mugaye ana kwatanta ta da gine-ginen da ruwa ya share harsashin gininsu.
Elifaz ya faɗi tambayar da mugaye suke yi wa Allah. AT: "Madaukakin Sarki ba zai iya yin mana komai ba!"
"Duk da haka Allah ya cika"
Kalmomin "nesa da ni" yana nufin Elifaz ya ƙi yarda da su. AT: "amma ba zan kasa kunne ga munanan shirye shiryen su ba"
"san abin da zai faru da mugaye"
"Masu adalci sun ce"
Anan "waɗanda suka taso" suna nufin mugayen mutane. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Lallai Allah ya hallakar da mugayen mutanen da suka cutar da mu"
Anan "daga bakinsa" yana wakiltar abin da Allah ya faɗa. AT: "koyarwar da Allah ya faɗa"
Kalmomin Allah suna kwatankwacin dukiyar da Ayuba zai iya ajiyewa. AT: "a kiyaye dokokinsa"
Elifaz ya gwada maido da Ayuba da sake gina gidan da ya rushe. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "zai warkar da ku kuma ya sake inganta ku"
An nuna rashin adalci kamar mutumin da yake rayuwa a cikin rumfar Ayuba wanda dole ne a cire shi. AT: "idan kai da kowa a gidanka kuka daina yin zunubi"
Aora dukiyar a cikin ƙura ita ce ɗauka mara amfani. AT: "Lallai arzikin ka bashi da mahimmanci kamar ƙura"
Sanya zinariya a cikin rafi shine ayi ma shi mara amfani kamar duwatsu. AT: "zinariyar Ofir ba ta da amfani kamar dutse a cikin rafi"
Wannan sunan yankin da ya shahara wajen zinariyar.
Wannan yana nufin Allah zai zama mafi mahimmanci ga Ayuba fiye da duk wata taska.
Wannan yana nufin Ayuba ba zai ƙara jin kunya ba amma zai dogara ga Allah. AT: "zaku sami damar kusantar Allah da karfin gwiwa"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah zai sa ku yi nasara"
Albarkar Allah an kwatanta ta da haske a kan duk hanyoyin Ayuba. AT: "zai zama kamar haske yana haskaka hanya a gabanka"
Anan "idanun da aka runtse" yana nufin tawali'u. AT: "mai tawali'u"
An yi maganar Ayuba ba shi da laifi kamar dai hannayensa suna da tsabta ta zahiri. Ana iya bayyana kalmar "wanda za a ceci" a cikin tsari mai aiki. AT: "Yahweh zai ceci ko da wanda ba shi da laifi saboda kun yi abin da yake dai-dai"
1Sai Ayuba amsa ya ce,2"Har yau ƙarata nada zafi, hannuna yayi nauyi saboda gunagunina.3Oh, dama na san inda zan same shi! Oh, da sai in tafi wurinsa!4Da zan kai ƙarata a gabansa, da na cika bakina da muhawara.5Zan koyi kalmomi waɗanda zaya amsa mani, yadda zan san abin da zai ce da ni.6Zaya yi gardamar gãba da ni duk da ƙarfin ikonsa? A'a, zai saurare ni.7Akwai amintaccen mutum da zai yi gardama da shi. Ta wannan hanyar zan tabbatar da aminci har abada ta wurin shari'a ta.8Duba, na tafi gabashi, amma baya can, yammaci, amma ban same shi ba.9A arewa, a wurin yake aiki, duk da haka ban gan shi ba, a kudu, a wurin ya ɓoye kansa domin kada in gan shi.10Gama ya san hanyar da na ɗauka; ya jarraba ni, zan fito kamar zinariya.11Ƙafata tana bin sawun ƙafarsa; ina bin hanyarsa ban kuma kauce wani gefen ba.12Ban kuma koma da baya ba daga umarnin leɓunansa; na ajiye kalmomin baƙinsa sun zama abinci na.13Gama yana ɗaya daga cikin masu kirki, wa zai iya juyar da shi? Abin da yake so ya aikata.14Gama ya ɗauki ka'ida gãba da ni; akwai da yawa kamar su.15Saboda haka, ina rawar jiki a gabansa; duk lokacin da nake tunani a kansa.16Domin Allah ya sa zuciyata tayi sanyi; Mai Iko ya tsorata ni.17Amma duhu bai kawo ni ƙarshe ba, ko da yake baƙin duhu ya rufe mani fuskata.
Ayuba yayi magana game da gunaguni da ba a amsa ba game da Allah kamar yana ɗanɗano bakinsa. AT: "koke-koke da ba'a amsa na ya yi muni kamar abinci mai ɗaci a bakina"
Ma’anoni masu ma’ana sune 1) “Da kyar na iya daga hannuna saboda nishi na” ko 2) “Hannun Allah yana ci gaba da sa ni wahala duk da nishi na” inda “hannu” yana nufin ikon Allah na yin horo.
Waɗannan layin guda biyu suna ma'ana dai-dai kuma sun jaddada sha'awar Ayuba na saduwa da Allah.
"Zan iya nemo Allah"
Waɗannan layin guda biyu suna ma'ana iri ɗaya kuma suna jaddada sha'awar Ayuba don bayyana halin da ake ciki ga Allah.
Anan "cika bakina" yana nufin magana. AT: "Zan faɗi duk maganata"
"amsar da zai bani"
"Allah zai"
Wannan yana nufin wurin da Allah yake.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "alƙali na zai same ni har abada" ko "Allah, wanda yake alƙalaina, zai ce ba ni da laifi sau ɗaya"
Ayuba ya ci gaba da magana. Ya fara da cewa ya duba ko'ina.
Ta ambaci waɗannan fuskoki guda huɗu, Ayuba ya nanata cewa ya duba ko'ina.
Ayuba yayi maganar Allah kamar mutum ne wanda yake ɓoye.
An yi maganar ayyukan Ayuba kamar yana tafiya akan hanya. AT: "Allah ya san abin da nake yi"
Ayuba ya yi imanin cewa gwajin zai tabbatar da cewa shi mai kyau ne kamar zinariya. AT: "Zai ga cewa ni mai kyau kamar zinariya ne lokacin da duk abin da ba tsarkakke ba ya ƙone"
Anan "ƙafafuna" yana nufin Ayuba. AT: "Na bi hanyar da ya nuna mini"
An yi maganar biyayyar Ayuba kamar yana tafiya ne a hanyar da Allah ya nuna masa.AT: "Na yi abin da ya ce in yi"
Wannan za a iya bayyana shi da kyau. AT: "bi shi dai-dai"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa babu wani kamar Allah kuma babu wanda zai tilasta shi ya canza. AT: "Amma babu wani kamar shi, kuma ba wanda zai iya canza shi." ko "Amma shi kaɗai ne Allah, ba wanda zai iya rinjayar da shi."
"Yana yin duk abin da ya ga dama."
"yana yi mani abin da ya ce zai yi"
Waɗannan layin guda biyu suna ma'ana dai-dai da abu ɗaya kuma sun nanata cewa Ayuba yana tsoron Allah sosai.
Mutumin da zuciyarsa take rauni, mutum ne mai jin tsoro ko tsoro. AT: "ya ba ni tsoro"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) "Babban duhu a gabana bai sa ni yin shuru ba" ko 2) "Duhun bai hana ni ba" ko "Allah bai hana ni ba, ba duhu bane."
Anan Ayuba yana nufin kansa ta "fuskarsa". AT: "baƙin cikina"
1Meyasa Mai Iko bai tsaida lokatan shari'ar mugayen mutane ba? Meyasa bai tsayar wa waɗanda suke adalai ga Allah suga kwanakinsa na shari'a ya zo?2Akwai mugayen mutane da yawa da suke kawar da iyaka; akwai mugayen mutane waɗanda suke ɗaukan garke da tsiya su zuba cikin makiyayarsu.3Sukan saci jakin marayu; su kama takarkarin gwauruwa a matsayin jingina.4Sukan tilastawa mutane masu bukata su bar masu hanya; mutane matalauta na ƙasa dukka su ɓoye kansu daga gare su.5Duba, waɗannan mutane matalauta su fita daga wurin ayyukansu kamar jakunan daji a jeji, suna bi hankali su na neman abinci; me yiwuwa Arabah zai ba su abinci domin 'ya'yansu.6Matalautan mutane na girbi da dare a gonakin wasu mutanen, su na tattara 'ya'yan inabi daga gonakin waɗannan mugayen mutanen.7Su na kwance tsirara dukkan dare ba tare da tufa ba, basu da abin da zai hana su jin sanyi.8Suna jike sharkaf da ruwa da ke kwararowa daga kan duwatsu; suna kwance kusa da manyan duwatsu domin basu da mafaka.9Akwai mugayen mutane waɗanda suke figar marayu daga nonon iyayansu mata, mugayen mutane waɗanda suke ɗaukan yara a matsayin jingina daga matalautan mutane.10Amma matalautan mutane suna tafiya babu kaya a jikinsu; suna tafiya da yunwa, suna ɗauke da damunan hatsi na waɗansu mutane.11Matalautan mutane na matse mai a katangar mugayen mutane; suna kuma matsar ruwan inabin mugayen mutane, amma su da kansu suna fama da ƙishi.12Daga cikin birni ana jin nishin masu mutuwa, makogwaron masu rauni na kukan neman taimako. Amma Allah bai kula da masu laifin ba.13Wasu daga cikin waɗannan mugayen mutanen suna ƙin haske; basu san hanyarsa ba, ko su tsaya a hanyarsa.14Kafin hasken rana mai kisankai yakan fita ya kashe matalauci da mutane masu bukata; da dare kuma ya kan zama kamar ɓarawo.15Har yau, idon mazinaci yakan jira sai da magariba; ya faɗa, 'Babu idon da zai gan ni.' Yana ɓoye fuskarsa.16A cikin duhu mugayen mutane sukan kutsa kai cikin gidaje; amma suna ɓoye kansu da rana; basu damu da haske ba.17Gama dukkan su, mattsanancin duhu ne kamar duhun safiya; domin su abokan "yan ta'addar baƙin duhu ne.18Suna wucewa da sauri, duk da haka, kamar kumfa a kan fuskar ruwaye; ƙasar da suka mallaka an la'anta ta; babu wanda zai tafi yayi aiki a cikin gonar inabi.19Kamar dusar ƙanƙara take narkewa, iska mai laima cikin ruwaye, haka Lahira ke ɗaukan waɗanda suka yi zunubi.20Cikin da ya haife shi ba zai tuna da shi ba; macijin ciki zai ji daɗin ƙoshi a kansa; ba za a ƙara tunawa da shi ba; ta wannan hanya, miyagu zasu lalace kamar itace.21Mugun da ya lanƙwame matan da basu haifi yara ba; bai kuma nuna alheri ga matar da ke gwauruwa ba.22Duk da haka Allah yakan ja mutane masu iko ta wurin ikonsa; yakan ɗaga ya kuma hana su ƙarfi a rayuwarsu.23Allah ya kan bar su da tunanin sun tsira, suna murna a kan haka, amma idanuwansa na kan hanyoyinsu.24An ɗaukaka waɗannan mutane; a ɗan lokaci kaɗan, zasu ɓace; za a ƙasƙantar da su; za a tattara su wuri ɗaya kamar sauran; za a hallaka su kamar karan dawa da aka yanke.25Idan ba haka ba, wane ne ya tabbatar ni maƙaryaci ne; wa zai ce kalmomina ba gaskiya ba ne?"
Ayuba ya ci gaba da magana.
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don bayyana takaicin sa cewa Allah bai hukunta mugunta ba. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ban fahimci abin da ya sa Allah ba ya kafa lokacin da zai yi hukunci da mugayen mutane." ko kuma "Allah Maɗaukaki ya kafa lokacin da zai hukunta mugaye."
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don bayyana takaicin sa cewa masu adalci ba sa ganin Allah yana yin mugunta. AT: "Da alama cewa waɗanda suke yin biyayya da shi basu taɓa ganinshi suna yin hukunci da mugaye ba." ko "Allah zai nuna ranar da zai shar'anta mugaye ga waɗanda suka san shi."
Waɗannan duwatsun ne ko wasu abubuwa don alama kan iyaka tsakanin ƙasashen da mutane daban-daban suka mallaka.
"marayu" ko "yaran da iyayensu suka mutu"
Mai bada bashi zai dauki wani abu daga mai bashi don tabbatar da cewa mai karbar bashi ya biya shi.
Kalmar "dukka" ƙari ne don nuna cewa talakawa da yawa suna tsoron waɗannan mugayen.
"jakuna da ba wanda ya mallaka ko kula su"
Waɗannan layin guda biyu suna bayanin abu iri ɗaya kuma ana amfani da su tare don jaddada cewa mutanen nan suna fama da yunwa sosai da tilasta musu satar abinci da dare.
Waɗannan layin guda biyu suna bayanin abu ɗaya kuma ana amfani da su tare don ƙarfafa cewa waɗannan mutane ba su da isasshen suturar da za su yi ɗumi.
"Suna jika lokacin da ake ruwa a tsaunuka"
Anan "nono" yana nufin mahaifiyar. Wannan yana nuna cewa waɗannan marayu har yanzu suna kanana. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "matasa marayu daga cikin uwayensu" ko "jarirai marayu daga uwayensu"
"dauki yaran talakawa ka tabbatar cewa talakawa za su dawo da kudin da suka aro daga hannun mugayen mutane"
"je game da" ko "ci gaba"
Kalmomin "ba tare da sutura ba" suna ma'ana dai-dai da "tsirara." AT: "tsirara gaba ɗaya" ko "tsirara saboda ba su da suttura"
Wannan yana nufin aikinsu zai samar da abinci ga wasu amma ba don kansu ba.
Anan "ganuwar" tana nufin gidan gaba ɗaya. AT: "a cikin gidajen waɗannan mugayen"
Zai iya zama mai fa'ida a bayyana cewa sun yi wannan ne don samar da ruwan 'ya'yan itace don yin ruwan inabi. AT: "suna tattake inabi da ruwan 'ya'yan itace domin ruwan inabi"
"suna wahala daga ƙishirwa" ko "suna ƙishirwa"
Ma'anar ma'anar "haske" sune 1) haske bayyane ko 2) haske na ruhaniya, wanda ke nuni ga Allah ko rayuwa cikin adalci. AT: "ƙiyayya da hasken rana" ko "ba sa son yin abubuwa a bayyane" ko "yin tawaye ga Allah"
Waɗannan layin guda biyu suna bayanin abu ɗaya, kuma ana amfani dasu tare don ƙarfafa cewa basa son bin hanyoyin haske. AT: "ba su san yadda ake rayuwa mai kyau ba; sun yi nesa da rayuwa mai adalci"
Kalmomin "talakawa" da "mabukata" suna nufin rukuni guda na mutane da nanata cewa waɗannan mutanen da ba sa iya taimakon kansu.
Mai kisan kai yana kashewa a ɓoye kamar ɓarawo ya yi sata ba tare da wani ya ga abin da yake yi ba. AT: "yana kashe mutane a asirce, kamar ɓarawo yana sata a ɓoye"
Anan “ido” yana nufin mutum ne gaba ɗaya. AT: "mazinaciya"
"don faɗuwar rana"
Anan “ido” yana nufin mutum ne gaba ɗaya. AT: "Ba wanda zai gan ni"
"sun ɓoye a cikin"
Duffan duhu yana da nutsuwa ga mugaye kamar yadda hasken safiya yake ga mutane na al'ada.
"abubuwan ban tsoro da ke faruwa da dare"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah ya la'anci ɓangaren ƙasar da suka mallaka"
Ayuba ya ce masu zunubi za su shuɗe cikin Lahira dai-dai yadda dusar ƙanƙara ta narke kuma ta shuɗe lokacin da ta yi ɗumi.
Wannan yana nufin mahaifiyar. AT: "Mahaifiyar"
Wannan yana nuna cewa zai mutu kuma tsutsotsi zasu ci jikinsa. AT: "tsutsa za ta more jin dadin cin gawarsa" ko kuma "zai mutu sa'an nan kuma tsutsotsi su ci shi"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ba wanda zai ƙara tunawa da shi"
Halakar da Allah ya yi wa mugu ya kasance kamar an sare itace. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah zai hallakar da mugaye kamar dai itace"
Mutanen wannan ranar sun ɗauka cewa Allah ya la'anci wata mace bakarariya. Saboda haka, wannan yana wakiltar mata masu rashin tausayi.
Anan "baya karfafa su a rayuwa" yana nufin Allah baya kiyaye su da rai. AT: "Allah ya tashi kuma baya ba mugaye ikon da ikon rayuwa" ko "Allah ya tashi ya sa su mutu"
Anan “idanu” suna nufin Allah. AT: "amma a koyaushe yana lura da abin da suke aikatawa"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah zai ƙasƙantar da su" ko "Allah zai hallakar da su"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. Abin da "sauran" ake magana a kai za a iya bayyana a sarari. AT: "Allah zai tattara su kamar yadda ya tattara sauran mugayen mutane"
Waɗannan mugayen mutane za a yanke a cikin wannan hanyar da fi na hatsi an yanke a locakin girbi. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah zai sare su kamar yadda manomi zai sare ciyawar hatsi"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don bayyana tabbacin gardamar sa. Amsar a bayyane ita ce: "babu kowa." AT: "Wannan gaskiya ne, kuma ba wanda zai iya tabbatar da cewa ni maƙaryaci ne; ba wanda zai iya tabbatar da ni ba dai-dai ba."
1Sai Bildad Bashune ya amsa ya ce,2"Mulki da tsoro suna tare da shi, yayi samaniya wurarensa.3Akwai ƙarshen jimilar yawan sojojinsa? A kan wane ne haskensa yaƙi haskakawa?4Yaya mutum zai zama adali tare da Allah? Yaya shi wanda mace ta haifa zai zama da tsabta, ƙarɓaɓɓe gare shi?5Duba, ko da wata bashi da haske gare shi, taurari ma basu da tsarki a gabansa.6Yaya kuma mutum, wanda aka haifa--ɗan mutum, wanda aka haife shi!"
Anan "shi" yana nufin Allah. Za a iya bayyana sunan "mulki" da "tsoro" azaman fi'ili. AT: "Allah yana mulki bisa mutane kuma mutane suji tsoronsa kawai"
"Ya sa zaman lafiya a cikin samaniya mai tsayi"
Bildad yayi amfani da wannan tambayar don jaddada yadda Allah mai girma ne. Amsar a bayyane ita ce "a'a." Wannan yana nufin sojojin mala'ikun Allah. AT: "Babu ƙarshen adadin mala'iku a cikin sojojinsa." ko "Sojojinsa suna da girma sosai har babu wanda zai iya ƙidaya su."
Bildad yayi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa Allah yana ba kowane haske. AT: "Babu wani wanda haskensa ba ya haskakawa." ko "Allah yasa haske ya haskaka kan kowa."
Ana amfani da waɗannan tambayoyin biyun tare don ƙarfafa cewa ba shi yiwuwa mutum ya kasance da nagarta sosai a gaban Allah.
Wannan kalmar ta hada da kowa. AT: "duk wani mutum"
AT: "Wata bai zama mai haske ba ga Allah"
Anan "tsarkake" na nufin "cikkake". AT: "baya tunanin taurari cikakke ne"
Waɗannan layin guda biyu suna faɗi abu ɗaya kuma ana amfani dasu tare don ƙarfafa cewa mutum bai cikakke ba.
Wannan wata hanya ce ta mutum. AT: "mutum"
1Sai Ayuba ya amsa ya ce,2"Yaya ka taimakawa wanda bashi da ƙarfi! Ka cece hannun da bashi da ƙarfi!3Yaya kake ba wanda bashi da hikima shawara, kana sanar da amon ilimi!4Ta wurin wa ka sami taimako ka ke yin maganar waɗannan kalmomi? Wanne ruhu ne ya fito daga gare ka?5Matattu suna rawar jiki, su waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukkan waɗanda su ke zama da su.6Lahira ta na tsirara gaban Allah; hallakarwa da ke kanta ba rufe take ba a gare shi.7Ya shimfiɗa arewa a sarari a kan abin da ke fili, ya rataya duniya ba bisa kan kome ba.8Ya ɗaure ruwaye a gizagizai, amma gizagizan ba a ƙarƙashinsu suke ba.9Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa girgije a kanta.10Ya zana kewayanta a kan iyakar fuskar ruwaye kamar layi tsakanin haske da duhu.11Ginshiƙan samaniya sun girgiza, sun firgice sakamakon tsautawarsa.12Ta wurin ƙarfinsa ya kwantar da teku; ta wurin saninsa ya hallakar da Rahab.13Ta wurin numfashinsa yasa sararin sama yayi garau; da hannunsa ya sha zarar macijin nan mai gudu.14Duba, amma waɗannan su ne yatsun hanyoyinsa; yaya ƙanƙantar raɗa da muke ji a gare shi! Wane ne ya gane tsawar ikonsa?"
A cikin waɗannan bayanan, Ayuba yana zargin Bildad. Kalmar “wanda” tana nufin Ayuba. Kuma, kalmar "hannu" tana wakiltar mutum gaba ɗaya. AT: "Ba ni da ƙarfi, ba ni da ƙarfi, amma kun yi kamar kun taimaka mini; amma da gaskiya, ba ku taimake ni ba ko kaɗan"
Ayuba yana cewa Bildad bai samar masa da kyakkyawan shawara da ilimi ba. AT: "Kuna aiki kamar bani da wata hikima kuma kun shawarce ni, kun bani shawarwari masu kyau"
A cikin waɗannan tambayoyin Ayuba ya ci gaba da yi wa Bildad ba'a. Dukansu tambayoyi suna da ma'ana iri ɗaya. Ana amfani da su tare don ƙarfafa juna. AT: "Dole ku sami taimako wajen faɗi kalmomin. Wataƙila wasu ruhu sun taimake ku ku faɗi su."
Wannan yana nufin mutanen da suka mutu. AT: "Waɗanda suka mutu" ko "Ruhun matattu"
Suna rawar jiki domin suna tsoron Allah. Wannan za a iya bayyana a sarari. AT: "rawar jiki a cikin tsoro" ko "rawar jiki da tsoron Allah"
Ana maganar Lahiral kamar dai mutum ne. Wadannan jumla guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. Kasancewa “tsirara” ko kuma rashin “mayafi” shine fallasa gaba ɗaya kuma baya iya ɓoye komai. AT: "Kamar lahira tsirara ne a gaban Allah, don babu wani abu a cikin lahira, wurin ɓoyewa, ga Allah ɓoye yake"
Wannan kuma wani sunan ne na lahira. ATsarar: "wurin lalata"
Sararin sama arewa yana wakiltar sama, wurin da Allah yake zaune tare da halittun da ya halitta don zama a ciki.
Ana kwatanta girgije da babban bargo wanda Allah ya rufe ruwan sama. AT: "Ya lullube ruwan a cikin gizagizairsa"
Wannan bayanin ya faɗi yadda ya rufe saman wata. AT: "ta yada girgije a gabanta"
Mutane suna tunanin sama kamar yadda suke hutu akan ginshiƙi. Ayuba yana magana kamar dai gumakan mutane ne masu girgiza tsoro yayin da Allah yayi fushi. AT: "Ginshiƙan da suke riƙe sama suna rawar jiki lokacin da Allah ya tsauta su" ko "Abubuwan da ke riƙe sama suna girgiza kamar mutanen da suke jin tsoro lokacin da Allah ya tsauta musu"
Wannan shi ne sunan dodo mai tsoratarwa wanda ya rayu a cikin teku. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Ayuba 9:13.
Wannan hoton yana wakiltar Allah ne yake sa iska ta busa girgije. AT: "Allah ya hura girgije domin sararin sama ya bayyana"
An ɗauka cewa Allah yana riƙe da takobi, a nan kuma “hannunsa” yana wakiltar wannan takobi. Hakanan, "soke" yana wakiltar kisa. AT: "Da takobinsa ya soki maciji mai gudu"
"Macijin kamar yadda yake ƙoƙarin tserewa daga gare shi." Wannan yana nufin Rahab, dodo a cikin teku. Duba Ayuba 26:12.
Anan "gefuna" yana wakiltar karamin sashi wanda zamu iya ganin wani abu wanda yafi girma girma. AT: "Duba, waɗannan abubuwan da Allah ya yi suna nuna kaɗan ne kawai na ikonsa mai ƙarfi"
Wannan karin magana ce da ke nuna irin mamakin da Ayuba ya yi na duk manyan abubuwan da Allah yayi wanda ba mu san shi ba. Ana ganin abin da Allah yake yi ana maganar jin muryar Allah. AT: "kamar yadda dai mun ji kawai ya rada!"
“Tsawar ikonsa” tana wakiltar girman Allah. Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa ikon Allah yana da girma sosai har ba wanda zai iya fahimtarsa. AT: "Aradu yana nuna girman ikonsa wanda ba wanda zai iya fahimta!"
1Ayuba ya fara magana, ya ce,2"Yadda Allah na raye, wanda ya ɗauke mani adalci, Mai Iko, wanda yasa rayuwata ɗaci,3har yanzu raina baya tare da ni, numfashi daga Allah ya cika hancina, wannan shi ne abin da zan yi.4Leɓena ba zai faɗi mugunta ba, ko harshena ya hurta maganganun yaudara;5ba zan taɓa yarda cewa ku ukun kun yi dai-dai ba; har in mutu ba zan daina tsare mutuncina ba.6Ina rike da adalcina ba kuwa zan sake shi ba ya tafi; tunanina ba zai zarge ni ba idan dai ina raye.7Bari maƙiyina ya zama kamar mugun mutum; bari wanda ya ke gãba da ni ya zama kamar mutum marar adalci.8Gama wacce sa zuciya ke ga mutum marar tsoron Allah sa'ad da Allah ya datse shi, sa'ad da Allah ya ɗauke ransa?9Allah kuwa zai ji kukansa a lokacin da wahala ta same shi?10Zai yi farinciki da kansa a wurin Mai Iko, zai yi kira ga Allah a dukkan lokatai?11Zan koya maka game da hannun Allah; ba zan ɓoye tunanin Mai Iko ba.12Duba, dukkan ku kun ga wannan da kanku; me yasa kuke yin wannan magana ta wawanci?13Wannan shi ne rabon mugun mutum a wurin Allah, gãdo ne kuma wanda azzalumi zai karɓa daga wurin Mai Iko:14Idan 'ya'yansa sun riɓamɓanya, zasu zama rabon takobi; zuriyarsa kuwa ba zata sami isasshen abinci ba.15Duk wanda ya tsira za a bizne shi da annoba, gwaurayensu ba zasu yi makoki domin su ba.16Ko da yake mugun mutum ya tsibe azurfa kamar turɓaya, tarin tufafi kamar laka,17zai iya tara tufafi, amma adalan mutane zasu zuba a kai, mutanen kirki zasu raba azurfar a tsakaninsu.18Ya gina gidansa kamar saƙar gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.19Ya kwanta a gadon mai arzaki, amma ba zai ci gaba da yin haka ba, zai buɗe idanunsa, yaga komai ya tafi.20Razana zata auko masa kamar ruwaye; iska zata tafi da shi da dare.21Iskar gabas zata fyauce shi, zai tashi; zata share shi daga wurinsa.22Zata jefar da kanta a kansa, babu tsayawa; zai yi ƙoƙari ya tsere daga hannunsa.23Zata tafa hannuwanta a kansa domin ba'a; zata yi masa ƙara daga wurinsa.
Wannan magana tana nuna cewa Ayuba yana rantsuwa ne. Ayuba ya gwada tabbacin cewa Allah yana da rai da tabbacin abin da yake faɗi. Wannan wata hanya ce ta cika alkawari. AT: "Na rantse da Allah"
Ana magana da adalci kamar dai abu ne wanda za'a iya cire shi ko kuma a bayar dashi. Dauke shi yana nuna rashin yarda a yi wa Ayuba da adalci. AT: "ya ƙi yi da ni da adalci"
“Rayuwar” Ayuba yana da zafin rai yana wakiltar Ayuba yana jin haushin Allah. AT: "ya sa ni yin fushi" ko "ya ba ni haushi saboda yadda bai bi da ni ba"
Wannan yana nufin tsawon rayuwarsa. AT: "a duk tsawon lokacin da raina yake cikina" ko "muddin raina yana cikina"
"Numfashi ... a cikin hanci na" yana wakiltar samun damar numfashi. “Numfashi daga wurin Allah” yana wakiltar Allah ne ya sa Ayuba sami ikon numfashi. AT: "Allah ya sa na numfasa"
Wadannan jumla guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani da su tare don ƙarfafa cewa ba zai yi magana a cikin waɗannan hanyoyi ba. Kalmomin "leɓunana" da "harshena" suna wakiltar Ayuba ne da kansa. AT: "Ba zan faɗi mugunta ba ko yaudara"
"Ba zan taɓa yarda da ku ba kuma ba zan ce ku uku dai-dai ne"
"Ba zan taɓa faɗi mara laifi ba" ko "zan fada koyaushe cewa ni marar laifi ne"
Anan "riƙe" magana ne na wakiltar cewa an ƙuduri niyyar ci gaba da faɗi wani abu. AT: "Na yanke shawarar ci gaba da faɗi cewa ni mai adalci ne"
Anan "bazai kyale shi ba" karin magane ne wanda ke wakiltar bai daina faɗar wani abu ba. AT: "ba zai daina faɗi cewa ni mai adalci bane" ko "ba zai daina faɗi haka ba"
Anan kalmar "tunanina" tana wakiltar Ayuba. AT: "har ma a tunanina, ba zan zargi kaina ba"
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "Bari a azabtar da makiyina kamar mugayen mutum" ko "Bari Allah ya azabtar da makiyina kamar yadda yake azabtar da mugayen mutane"
Za a iya bayyana cikakkiyar ma'anar wannan bayani. AT: "Bari a hukunta wanda ya tashe ni a matsayin mutumin azzalumi"
Anan "ya tashe ni" magane ne kalma ce "yana hamayya da ni." Gaba ɗayan magana tana nufin abokin gaban Ayuba. AT: "wanda ke hamayya da ni" ko "maƙiyina"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar yana cewa irin wannan mutumin bashi da bege. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Babu wani bege ga marassa Allah yayin da Allah ... ya karbi ransa."
Wadannan jumla guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. AT: "lokacin da Allah ya yanke shi, ya tafi da ransa" ko "lokacin da Allah ya sa shi mutu"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar ya ce Allah ba zai taimaki mutumin ba. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwai. AT: "Allah ba zai ji kukansa ba lokacin da masifa ta same shi." ko "Idan wahala ta same shi kuma ya yi kuka don neman taimako, Allah ba zai ji shi ba."
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar yana cewa mugayen mutumin da bashi da iko ba zai aikata waɗannan abubuwan ba. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Ba zai ji daɗinsa da Madaukaki ba, ya yi kira ga Allah koyaushe." ko "ba zai yi farin ciki da abin da Madaukaki yake yi ba kuma ba zai yi addu'a ga Allah ba sau da yawa."
“Hannun” Allah yana wakiltar ikonsa. AT: "ikon Allah"
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don tsauta wa abokansa saboda faɗar irin waɗannan wauta. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Bai kamata kuyi magana da wauta ba!"
"Wannan shi ne abin da Allah ya shirya wa mugayen mutum"
Anan "gãdo na azzalumi" wani magane ne wanda zai wakiltar abin da zai faru da azzalumi. Abin da Allah zai yi da shi ana maganarsa kamar dai shi gãdo ne da Allah zai ba shi. AT: "abin da Mai Iko Dukka zai yi wa azzalumi"
Anan "takobi" yana wakiltar mutuƙar yaƙi. AT: "za su mutu a yaƙi"
Wannan yana nufin 'ya'yan mugaye. Wannan za a iya bayyana a sarari. AT: "Waɗanda suka ci gaba da rayuwa bayan mahaifinsu mugu ya mutu"
Anan "binne" yana wakiltar mutuwa. AT: "zai mutu da annoba"
Kalmomin "nasu" da "su" suna nufin "Waɗanda suka tsira daga gare shi," wato, 'ya'yan mugaye.
Anan "tsibi" shine ma'anar na nufin "tara abubuwa da yawa." Ayuba yana magana kamar dai azurfa tana da sauƙin samu kamar ƙura. AT: "yana tara babban tarin azurfa" ko "ya tara azurfa da sauƙi kamar yana iya tara ƙura"
Anan "tsibi" shine ma'anar na nufin "tara abubuwa da yawa." Ayuba yayi magana kamar yadda tufafi suke da sauƙin samu kamar yumɓu. AT: "a tara manyan tarin tufafi" ko kuma “a tara kayan a saukake kamar yadda zai iya tara yumɓu”
Yanar gizo-gizo take ba mai rauni kuma sauƙin halaka. AT: "Ya gina gidansa ba kamar yadda gizo-gizo yake gina gidan yanar gizo ba" ko "Ya gina gidansa kamar mai rauni kamar gizo-gizo gizo-gizo"
"Yana da wadatar arziki lokacin da ya kwanta a gãdo." Wannan yana nufin kwanciyarsa a gãdo da daddare.
"amma ba zai ci gaba da kwanciya a gãdo mai arziki ba" ko kuma "amma ba zai ci gaba da zama mai arziki lokacin da ya kwanta a gãdo ba"
Buɗe idanunsa yana wakiltar farkawa da safe. AT: "ya farka"
"Duk dukiyarsa sun tafi" ko "komai ya lalace"
Anan "auko masa" yana wakiltar faruwa kwatsam. Ma'anar mai yiwuwa ita ce "ta'addanci" alama ce don 1) abubuwan da ke haifar da tsoro ga mutane. AT: "Abubuwa masu ban tsoro suna faruwa ba zato ba tsammani" ko 2) tsoro. AT: "Ba zato ba tsammani sai ya firgita"
"iska mai karfi ta buge shi"
Ayuba yayi maganar iska tana busa mugaye mutum daga cikin gidansa kamar wanda iska takeyi tana share ƙura daga gida tare da tsintsiya. AT: "iska tana kwashe shi daga matsayin sa kamar mace wacce take share datti daga gida" ko "iska tana bugo masa daga wurin sa"
"gidansa"
A cikin ayoyi 22-23 Ayuba yayi magana game da iska kamar dai mutumin da ke kai wa mutumin mugu.
1Babu shakka akwai ma'adani na azurfa, a wurin da ake tace zinarya.2Ana samun ƙarfe daga cikin ƙasa; a kuma narkar da tagulla daga dutse.3Mutum ya kan kawar da duhu, ya kuma bincike zuzzurfar iyaka, ya haƙo duwatsun a lunguna masu sulɓi da ke cikin duhu baƙi ƙirin.4Ya kan buɗe ƙyaure daga wurin da mutane ke zama, wuraren da ƙafar wani ba zata manta ba. Yakan kafa abin lilo nesa da mutane; yayi ta lilo zuwa da komawa.5Daga cikin ƙasa ake samun abinci, takan juyo ƙarƙashinta kamar ta wurin wuta.6Duwatsu ne wurin da ke samun shudin yakutu, zinariya ɗauke da ƙurarta.7Tsuntsu mai cin nama bai san hanyarta ba, shaho ma da idanuwansa bai ganta ba.8Namomi masu fahariya basu taɓa bin irin hanyar ba, ko zaki mai zafi ma bai taɓa wucewa can ba.9Mutum yasa hannunsa a kan ƙanƙarar dutse, yana kuma iya tunɓuke tushen duwatsun daga saiwoyinsu.10Yana kuma iya sarar magudanar ruwa cikin duwatsu; idannunsa kan ga kowanne abu mai daraja a can.11Yana iya datse rafuffuka ya hana su gudu; ya binciko abin da ke ɓoye a can ya kawo shi a sarari.12Daga ina za a samo hikima? Ina ne wurin haziƙanci?13Mutum bai san darajarta ba; ko a samo ta a ƙasar masu rai.14Zurfafan ruwaye a ƙarƙashin ƙasa sun ce, 'Bata cikina,' teku ta faɗa, 'Bata tare da ni.'15Ba zata iya samuwa daga zinariya ba; ko azurfa bata yi nauyi kamar tamaninta ba.16Ba zata yi kimanin zinariyar Ofir, tare da darajar baƙin dutse mai daraja ba ko saffir.17Zinariya da madubi ba zasu yi dai-dai da tamaninta ba; ko kuma a musanyata da murjanin da aka yi da zinariya mai kyau.18Kada ma a ambaci darajar murjani ko dutse mai walkiya; lallai tamanin hikima yafi shi.19Duwatsu masu darajar Kush ba za a dai-dai su da tamaninta ba; ko kuma darajar tamaninta yafi na zinariya tsantsa.20Daga ina hikima take fitowa? A wanne wuri kuma hazaƙa take?21Hikima a ɓoye take daga idon dukkan abubuwa masu rayuwa, haka nan yake a ɓoye ga tsuntsaye da ke tashi a sammai.22Hallaka da mutuwa sun ce, 'Mun ji ƙishin-ƙishin a kanta a kunnuwanmu.'23Allah ya fahimci hanyar zuwa gare ta; ya san wurinta.24Saboda yana ganin ƙarshen duniya, yana duban ƙarƙashin dukkan sammai.25Yasa iska mai ƙarfi da ƙunshi daga ciki ta wurin auna ruwaye.26Yayi ka'ida domin ruwan sama da hanya domin tsawa.27Sai ya ga hikima, ya sanar da ita; ya tabbatar da ita; ya gwada ta.28Ga mutane yace, 'Duba, tsoron Ubangiji -- shi ne hikima; rabuwa daga mugunta kuma ita ce hazaƙa.'"
Wannan shine wurin da mutane suke tono duwatsu. Waɗannan duwatsun suna da karfe a cikinsu.
Wannan shine aikin dumama karfe don cire duk ƙazamar abubuwan dake ciki.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Mutane suna ɗaukar baƙin ƙarfe daga ƙasa"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "mutane suna fasa jan karfe daga dutse" ko "mutane suna hura dutse domin narke jan ƙarfe daga ciki"
Anan "ya kawo ƙarshen duhu" yana wakiltar haske ne a cikin duhu. Mutane sun yi amfani da fitila ko wutan don haske. AT: "Wani mutum yana ɗaukar haske zuwa wurare masu duhu"
rami mai zurfi da aka tono a ƙasa ko dutse. Mutane na gangarawa cikin rami don nikar ta. Wata mashingar wurin ma'addini.
Ana magana da ƙafar kamar mutum ne wanda zai iya tunawa. AT: "wuraren da mutane ba sa tafiya" ko "inda ba wanda ke tafiya"
Anan "burodi" yana wakiltar abinci gaba ɗaya. Abincin da ke fitowa daga ƙasa magana ne ga abinci da yake fitowa daga ƙasa. AT: "ƙasa, inda abinci ke tsiro"
Ma'anar mai yiwuwa ita ce: 1) mutane sun kunna wuta a ƙasa daga bangon dutsen. AT: "Wata gobara da masu hakar gwal ta yi" ko 2) "juya" alama ce don canji. AT: "ya faskara ƙasa da sosai har ya bayyana cewa an lalata shi da wuta"
da muhimmanci dutse mai daraja
tsuntsu wanda ke cin sauran dabbobi
Wannan yana nufin dabbobi masu ƙarfi sosai.
Wannan yana wakiltar rushe dutse. AT: "tono a cikin dutsen mai ƙaura"
"dutse mai wuya"
Narkar da tsaunuka da ƙasa a ƙarƙashinsu magana ne ta tono ciyayi ko bishiyoyi, ƙari ne wanda ke nuna ma'anar tono ma'adinai daga ƙasa. AT: "yakan jujjuya duwatsun ta hanyar kawar da asalinsu"
Anan "idanunsa" suna wakiltar shi. AT: "yana gani"
Anan "ɗaure kogunan" yana nufin lalata ko toshe ƙofofin. AT: "Yana toshe ƙofofin don kada su gudu"
Wannan yana nufin abubuwan da mutane ba sa ganinsu saboda suna cikin ƙasa ko cikin ruwa.
A cikin Ayuba 28: 12-28, ana magana da hikima da haziƙanci kamar dai su abubuwa ne masu tamani waɗanda suke wani wuri kuma mutane suna son neme su. Neman hikima da haziƙanci yana wakiltar zama mai hikima da koyon fahimtar abubuwa da kyau.
Waɗannan tambayoyin suna ma'ana dai-dai kuma suna amfani dasu don nuna cewa yana da matukar wahala a sami hikima da haziƙanci. AT: "Yana da matukar wahala a sami hikima da haziƙanci."
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) ana magana da hikima kamar dai wani abu ne da mutane zasu iya siye. AT: "Mutane ba su san abin da ya dace ba" ko 2) kalmar da aka fassara da "farashi" ma'ana "wuri." AT: "Mutane ba su san inda yake ba"
"kuma ba a samo shi a ƙasar masu rai ba." “a ƙasar masu rai” tana nufin wannan duniyar da mutane suke zama. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "kuma ba wanda zai iya samun hikima a duniyar nan"
An gabatar da ruwa mai zurfi da teku kamar dai mutane ne da zasu iya magana. AT: "Hikima ba ta cikin zurfafa cikin ruwa a karkashin ƙasa, ba kuma cikin teku"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. Wannan yana nuna cewa hikima ta fi zinariya girma. AT: "Mutane ba za su iya biyan hikima da zinariya ba"
Wannan yana nuna cewa hikima ta fi ta azurfa nesa. Ana iya bayyana shi a cikin tsari mai aiki. AT: "kuma mutane ba za su iya ƙima yawan kuɗin da za su biya don hikima ba"
Wannan yana nuna cewa hikimar ta fi zinariyar Ofir, daraja onyx da safiya.
"ba za a iya musayar ta da kayan adon zinariya ba." Wannan yana nuna cewa hikimar tana da ƙima fiye da kayan adon zinariya.
"ciniki"
"Bai da kyau a ambaci murjani da kuma yasfar." Wannan yana nuna cewa hikima ta fi ta murjani da yasfar da ba a bukatar Ayuba don ya faɗi komai game da su. AT: "Ba zan damu da ambatar murjani ba ko yasfar ba" ko "Murjani da yasfar ba su da amfani idan aka kwatanta da hikima"
Ayuba yana amfani da waɗannan tambayoyin don gabatar da yadda mutane suke samun hikima da haziƙanci. AT: "Zan faɗa muku inda hikima ta zo da kuma inda haziƙanci take." ko "Zan faɗi yadda zan zama mai hikima da yadda ake koyon fahimtar abubuwa."
Wannan yana nufin cewa abubuwa masu rai basa iya ganin hikima. Ana iya bayyana shi a cikin tsari mai aiki. AT: "Babu wani abu mai rai da zai iya ganin hikima"
Wannan yana nufin cewa tsuntsaye sun kasa ganin hikima. Wannan za a iya bayyana a cikin tsari mai aiki. AT: "har ma tsuntsayen da ke tashi a sararin sama basa iya ganin hikima"
Ana magana da hikima kamar dai a wani wuri yake. AT: "Allah ya san yadda ake neman hikima. Ya san inda yake"
"wurare mafi nisa a duniya"
Wannan ya bayyana Allah yana yanke shawarar yadda yawan ruwa ya zama a kowane wuri. Ma'anar mai yiwuwa shine wannan yana nufin yanke hukunci 1) yawan ruwan sama da yakamata ya kasance a cikin kowane girgije ko 2) nawa ruwa yakamata ya kasance a cikin kowane teku. AT: "yanke shawarar nawa ne ruwa ya kamata a kowane wuri"
"Ya yanke shawarar yadda za a iya jin tsawa" ko "ya yanke shawarar hanyar tsawa"
Ana iya bayyana sunan "tsoro" tare da kalmomin nan "tsoro" ko "girmamawa." Ana iya bayyana sunan "hikima" tare da kalmar "hikima" AT: "Saurara, idan kun ji tsoron Ubangiji, za ku sami hikima"
Anan “rabu da mugunta” yana nufin ƙin aikata mugunta. Ana iya bayyana sunan "haziƙanci" tare da kalmar aikatau "fahimta." AT: "idan kun ƙi aikata mugunta, to zaku fahimci abubuwa da yawa"
1Ayuba yaci gaba da magana yace,2"Oh, dama ina ma yadda nake a watanin da suka wuce ne? lokacin da Allah yake lura da ni,3sa'ad da fitilarsa take haska mani kai, da kuma lokacin da nake tafiya cikin duhu ta wurin haskensa.4Kash, dãma na tsaya yadda nake cikakke a kwanakina, sa'ad da abokantaka da Allah ke kan gidana,5lokacin da Mai Iko ke tare da ni, 'ya'yana ke kewaye ni,6sa'ad da aka rufe hanyata da madara, duwatsu kuma na fito mani da rafuffukan mai!7A lokacin da nakan fito ƙofar birni, sa'ad da na zauna a wurin zamana a dandali,8da samari sukan gan ni, sai su kawar da kansu daga gare ni don girmamawa, tsofaffi mutane kuma su miƙe tsaye domi na.9Sarakuna na yin shiru da magana sa'ad da nazo; sai su ɗora hannuwansu a kan bakinsu.10Muryoyin manyan mutane sun yi tsit, harshensu ya liƙe a dasashin bakunansu.11Gama bayan da kunnuwansu suka ji ni, sai su albarkace ni; bayan da idanuwansu suka gan ni, sai su ba da shaida a kaina su kuma amince da ni12domin nakan ceci duk matalauci sa'ad da yayi kuka, da kuma wanda bashi da uba kuma bashi da wanda zai taimake shi.13Albarka ga wanda yake bakin mutuwa idan yazo gare ni; nakan sa zuciyar gwauraye ta yi waƙar murna.14Na sa sutura ta adalci, ta rufe ni; gaskiyata ita ce kamar suturata da rawanina.15Ni ne idon makafin mutane; ni ne ƙafaffun guragun mutane.16Ni mahaifi ne ga mutane masu bukata; nakan yi bincike don in warware al'amari harma wanda ban san shi ba.17Nakan karya muƙamuƙan mutum marar adalci; in fisge wanda aka zalunta daga cikin tsakanin haƙoransa.18Sa'an nan nace, 'Zan mutu cikin gidana; zan riɓaɓɓanya kwanakina kamar tsabar yashi.19Saiwoyina suna shimfiɗe cikin ruwaye, raɓa na sauka a dukkan dare a rassana.20Daraja a gare ni kullum garau take, baka shi ne ƙarfina kullum sabo yake a hannuna.21A gare ni mutane ke saurare; suna jira na, sun tsaya shiru su ji shawarata.22Bayan na gama magana ba wanda ya sake wata magana kuma; maganata tana sauka kamar ruwa a kansu.23Suna jira na kullum kamar yadda ake jiran ruwan sama; sun buɗe bakinsu sosai don su sha daga kalmomina, kamar yadda suke jiranruwan bazara.24Na yi masu murmushi sa'ad da basu sa tsammaninsaba; ba su yi watsi da fara'ar fuskata ba.25Nakan zaɓar masu hanya, in zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin sojojinsa, kamar wanda yake ta'azantar da masu makoki.
Ayuba yayi amfani da wannan mamaki don bayyana bege. AT: "Da ma ace na kasance kamar yadda na kasance a watannin da suka gabata"
Fitilar Allah da ke haskakawa a kan Ayuba tana wakiltar Allah ya albarkaci Ayuba. AT: "lokacin da albarkar Allah ta zama kamar fitila da ke haskaka haske a kaina"
Yin tafiya cikin duhu yana wakiltar fuskantar yanayi mai wahala.
Ayuba ya yi magana game da lokacin da yake saurayi da ƙarfi kamar dai kwanakinsa ne lokacin girbi ya girma. AT: "lokacin da nake saurayi da karfi"
Ana iya bayyana sunan "abokantaka" tare da sunan "aboki". Kalmar nan “rumfar” tana wakiltar gidan Ayuba. AT: "lokacin da Allah ya kasance abokina kuma ya kiyaye gidana"
Wannan alama ce ta girmamawa. Ana iya bayyana hakan a sarari. AT: "ya tashi ya tsaya bisa ga girmamawa gare ni"
Wannan alama ce ta girmamawa.
Sun yi wannan ne domin nuna cewa ba zasuyi magana ba. Wannan alama ce ta girmamawarsu ga Ayuba.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Manyan jami'ai sun rufe bakinsu" ko kuma "Manyan jami'ai sun daina magana"
Wannan yana wakiltar su da daraja sosai ga Ayuba har suka rasa abin da za su ce. AT: "sun ji cewa ba sa iya magana" ko kuma "ba su da abin faɗi '
Kunnuwa suna wakiltar waɗanda suka ji shi, idanun kuma suna wakiltar waɗanda suka gan shi. AT: "bayan sun ji abin da na gaya masu ... bayan sun ganni"
A nan "wanda yake matalauci" yana nufin kowane matalauci. AT: "Na kasance ina tserar da matalauta waɗanda suka yi ihu"
Albarkar da wani zaiyi akan wani yana wakiltar wannan mutumin yana yiwa wani albarka. AT: "Wanda ya kusa lalacewa zai sa mini albarka"
Wannan yana wakiltar duk wanda ya kusan mutuwa. AT: "waɗanda suka kusan mutu"
Anan “zuciyar gwauraye” tana wakiltar kowace gwauruwa. AT: "Na sa gwauruwa suka raira waƙa da farin ciki"
Mutane sau da yawa suna maganar adalci kamar dai sutura ne. AT: "Na aikata abin da yake mai adalci, kuma kamar tufa ne wanda na sa"
Mutane kan yi maganar adalci kamar dai sutura ne. AT: "Na yi abin da ke dai-dai, kuma ya zama kamar riguna da rawani a kaina"
Wannan yana wakiltar taimakawa makafin mutane. AT: "Na kasance kamar idda makafin mutane" ko "Na jagora makafin mutane"
Wannan yana wakiltar taimakawa guragun mutane. AT: "Na kasance ƙafafu ne ga guragun mutane" ko "Na tallafa wa guragun mutane"
Anan "Ni uba ne" yana wakiltar wadatar mutane. AT: "Na yi tanadi ga mabukata kamar yadda uba yake ciyar da 'ya'yansa"
A cikin ayoyi 18-20 Ayuba ya faɗi labarin abubuwan da ya saba faɗi tun kafin munana ta same shi.
Anan “wanda aka zubo kamar ruwa a kansu” yana wakiltar wartsakar da mutanen da suka ji shi. Ana iya fassara kalmar "magana" tare da kalmar aikatawa "yi magana" ko "faɗi." AT: "maganata ta wartsake wa zuciyoyinsu kamar saukakkun ruwanda ke wartsatsin jikin mutane" ko kuma "abin da na fada masu na wartsake su kamar saukowar ruwa"
Mutane sun jira Ayuba cikin haƙuri kuma suna tsammanin su ji abubuwa masu kyau.
Wannan yana wakiltar jira ne don Ayuba ya yi magana don ya amfana daga abin da aka faɗa. AT: "sun jira ni in yi magana don in amfana daga abin da na faɗi"
"Kamar yadda manoma ke jira don ruwan sama na karshe"
Wannan yana nufin yawan ruwan sama wanda zai fadi kafin lokacin damina.
Za a iya bayyana a sarari cewa dalilin murmushi shine karfafa su. AT: "Na yi murmushi a kansu don in ƙarfafa su"
Wannan yana wakiltar kirkirar da suka gani a fuskar Ayuba.
Anan "zabi hanyar su" yana wakiltar yanke shawarar abin da ya kamata suyi.
Ayuba ya yi magana game da yadda ya jagoranci mutane da kuma yadda suke yi masa biyayya kamar shi sarki ne kuma su sojojinsa ne.
Wannan kalmar tana nufin cewa Ayuba a zahiri shine wanda ya ta'azantar da mutane. AT: "Na ta'azantar da su lokacin da suke makoki"
1Yanzu waɗanda na girme su, sai ba'a kaɗai suke yi mani -- waɗannan matasa maza waɗanda iyayensu ban ma yarda in bar su suyi aiki tare da karnukan da suke kiwon garke tumakina ba.2Lallai, ƙarfin hannuwan iyayensu maza, ba zasu iya taimako na ba--mutanen waɗanda ƙarfin balagarsu yake lalacewa?3Sun rame daga talauci da yunwa; sai gaigayar ƙasa suke yi da duhu, cikin jeji da kufai.4Sukan tsinki ganyaye masu ɗaci na jeji su ci, doyar jeji ita ce abincinsu.5Aka kore su daga cikin mutane ana bin su da ihu kamar yadda ake yi wa ɓarawo ihu.6Sai a kwazazzaban rafi suke zama, ramummukan ƙasa da kogwannin duwatsu.7A cikin jeji suke ta kuka kamar jakai, sukan taru tare a ƙarƙashin sarƙaƙiya.8Su 'ya'yan wawaye ne, lallai, 'ya'ya maza marasa suna a mutane! Aka kore su daga ƙasar tare da tsumagu.9Amma yanzu na zama abin yiwa zambo, na zama abin magana a gare su.10Suna ƙyamata ta, sun tsaya da nisa daga gare ni; basu daina tofa mani yawu a fuskata ba.11Domin Allah ya katse lakata, ya ƙasƙantar da ni, waɗanda suka yi mani ba'a sun hana ni sakewa in yi wani abu.12A hannun damana 'yan iska sun taso mani; sun kore ni suna gãba da ni sun tura ni hanyarsu ta hallaka.13Sun lalata hanyata, sun jawo bala'i domi na, ba wanda ya hana su.14Sun zo suna gãba da ni kamar soja wanda yabi ta babbar kafar bangon birni; a tsakiyar hallaka sun naɗa kansu a kaina.15Babban tsoro ya faɗo mani; an kore darajata kamar iska; wadatata kuma ta shuɗe kamar girgije.16Yanzu raina yana kwararowa daga gare ni; kwanakin wahala sun same ni.17A cikin dare ƙasusuwana na karkaɗawa; azaba tana gaigaya ta ba hutawa.18Ƙarfin girman Allah yaci wuyan rigata; ya kuma kewaye ni kamar ƙarfin taguwata.19Ya jefar da ni cikin laka; na zama kamar ƙura da toka.20Na yi kuka a gare ka, Allah, amma ba ka amsa mani ba; na tashi tsaye, ka dai kalle ni kawai.21Ka canja sai ka zama mara tausayi a gare ni; da ƙarfin hannunka ka tsananta mani.22Ka jefa ni cikin guguwa, ka sa ta kora ni; ka jefa ni baya da gaba a cikin hadari.23Gama na sani zaka kai ni ga mutuwa, a gidan da aka ƙaddara wa kowanne mai rai.24Duk da haka, ba wanda ya isa ya miƙa hannunsa ya roƙi taimako idan ya faɗi? Babu wani da zai nemi taimako idan ya shiga cikin wahala?25Ashe ban yi kuka saboda shi wanda yake cikin wahala ba? Ashe ban yi ɓacin rai saboda mutum mai bukata ba?26Sa'ad da nasa bege don abin kirki, sai ga mugunta ta zo; sa'ad da nake jiran haske, sai duhu ya zo.27Zuciyata tana cikin damuwa, bata huta ba; kwanakin wahala ya zo a kaina.28Na tafi kamar wanda ke rayuwa cikin duhu, amma ba domin rana ba, na tsaya a gaban taron jama'a ina kukan neman taimako.29Na zama ɗan'uwan dila, aminin jiminai.30Fatata baƙa ce, ta faɗi daga gare ni; ƙasusuwana suna ƙuna da zafi.31Saboda haka garayata ta juya ga waƙar makoki, sarewata kuma ta zama waƙoƙi ga waɗanda ke kuka.
Wannan ya nuna yadda ya raina wadancan ubannin. Basu ma isa ya kasance tare da karnukansa ba. AT: "wanda na raina ubansa kuma ba zai ba shi damar yin aiki kusa da karnukan garken ba"
Ayuba ya yi amfani da wannan tambayar don yin ba'a da rauni na waɗannan mutanen. AT: "Ƙarfin hannayen kakaninsu ba zai iya taimaka min ba ... lalacewa."
Kalmar "Su" tana nufin ubannin matasa masu ba'a.
Ma’anoni masu ma’ana su ne 1) “busasshiyar ƙasa” alama ce don bushewar da ke girma a ƙasa. AT: "sun tauna a bushe asalinsu da suka samo a cikin ƙasa" ko 2) "an toya a busasshiyar ƙasa" kalmomi ne na cin duk abin da zasu samu a busasshiyar ƙasa.
Ayuba ya ci gaba da magana game da ubannin masu ba'a.
Waɗannan tsire-tsire ne waɗanda mutane za su ci kawai idan ba su sami komai mafi kyau ba.
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) mutanen sun ci tushen itacen tsintsiya ko 2) mutanen suna yin ɗumi da wuta ta wurin ƙona Tushen itacen tsintsiya.
Kalmomin "an fitar da su" yana nufin "an tilasta musu su tafi." Waɗannan jumla za a iya sake jujjuya su kuma a bayyana su ta hanyar aiki. AT: "Mutanen sun yi ihu a bayansu kamar ... ɓarawo da tilasta musu barin"
Ayuba ya yi magana a kan mutanen da ke kuka da yunwa kamar dai jakai ne na daji suna hayaniya. AT: "suka yi kururuwa kamar jakunan jeji saboda suna fama da yunwa"
Wannan shi ne daji tare da kaifi ƙaya. Wannan yana nuna cewa ba su da gida.
Anan "sune 'ya'yan wawaye" yana wakiltar samun halayen wawaye. AT: "Sun kasance kamar wawaye" ko "sun kasance wawaye ne"
Kalmar "lallai" tana nuna cewa abin da ke biyo baya yana ƙarfafa tunanin da ya gabata. Anan "'ya'yan mutane marasa suna" suna wakiltar samun halayen mutane marasa suna. AT: "hakika, mutane ba su da suna" ko "hakika, ba su da wani amfani"
Anan kasancewa "mara suna" yana nuna rashin daraja ko girmamawa. Yana nufin cewa ba su da amfani. AT: "mutane marasa amfani"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. Ma'anan iya ma'ana sune 1) tunanin bulala yana nuna cewa an kula dasu kamar masu laifi. AT: "Mutane sun wulaƙanta su kamar masu laifi kuma suka tilasta su barin ƙasar" ko 2) mutane da gaske suna amfani da bulala don tilasta su. AT: "Mutane sun matse su kuma suka tilasta musu barin ƙasar"
Ana iya bayyana sunan "waƙa" da kalmomin nan "yin waƙa." AT: "Amma yanzu suna raira waƙoƙi game da ni don su ba'a ni"
Anan "abin magana" kalma ce ga mutumin da mutane suke yiwa ba'a ba'a. AT: "Ni ne wanda suke yiwa mummunan izgili game da shi" ko "Suna dariya kuma suna faɗi maganganu game da ni"
Wannan za a iya fada da gaskiya. AT: "har ila yau sun fesa a fuskata"
Mai kamewa yana hana mutum yin motsi ba tare da bin komai ba. Anan "kamewa" yana wakiltar nisantar yin wani abu, kuma "nunin hanawa" wakilcin baya hana yin wani abu. A wannan yanayin ma ba'a yi watsi da zalunci ga Ayuba ba. AT: "kar ku guji zaluntar ni" ko "aikata duk wani zalunci da suke so su yi min"
Ayuba ya yi magana game da masu yi masa ba'a suna yi masa azaba kamar dai su mahara ne kuma sojoji suna kai masa hari.
Wannan na nufin a taron matasa mutane suka wargaje. Ma’anoni masu ma’ana sune 1) tashi kan daman Ayuba yana wakiltar kai hare hare. AT: “taron matasa suna kai hari a ƙarfina” ko 2) tashi sama a hannun dama na Ayuba yana wakiltar kai tsaye ga ɗaukakarsa. AT: "taron mutane sun kai hari ga girmata"
"Suna tilasta ni in gudu"
Wannan yana nuna hana Ayuba tserewa daga harin. AT: "Sun hana ni tserewa daga gare su"
Anan "tura gaba da bala'i" yana nuna ƙoƙarin yin bala'i ne. AT: "suna ƙoƙarin cutar da ni" ko "suna ƙoƙari su lalata ni"
Anan "a hana su" yana wakiltar dakatar da su daga aikata wani aiki. AT: "mutanen da ba su da wanda zai hana su kai min hari"
Wannan yana wakiltar mutane da yawa suna zuwa su kai masa hari yanzu, kamar manyan raƙuman ruwan teku masu yawo a kan shi.
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) Ayuba ya firgita ko 2) abubuwa suna faruwa ga Ayuba wanda ya ba shi tsoro.
Ayuba yayi maganar ba zato ba tsammani bashi da wata daraja kamar dai iska tana hura masa iska. AT: "Ba wanda ya girmama ni" ko "Ni yanzu ni mutum ne da mutane ba sa mutuntawa"
Ayuba yayi magana game da wadatar sa wanda ya ƙare kamar girgije ne wanda aka hura. Anan "wadatar arziki" na iya nufin kyautatawa ko aminci. AT: "Ba na iya cin nasara ko kaɗan" ko "Ba ni da tsaro"
Ayuba yayi magana kamar ransa kamar ruwa ne kuma jikinsa kwantena ne. Yana jin ya kusa mutu. AT: "Yanzu na mutu"
Ayuba yayi maganar ci gaba da shan wahala kamar dai kwanakin wahala sun kama shi. AT: "Na sha wahala kwanaki da yawa, wahala kuma ba ta ƙare"
Ayuba yayi maganar zafin cikin kasusuwarsa kamar ana soke ƙasusuwansa. AT: "ƙasusuwana suna jin ciwo sosai" ko "Ina jin raɗa a cikin ƙasusuwana"
Ayuba ya yi magana game da azabarsa koyaushe kamar yana raye kuma ciji shi ya ƙi hutawa. AT: "raɗaɗin da ke sa ni wahala ba su daina" ko "Ina cikin azaba koyaushe"
Hoton ikon Allah na kama Ayuba misali ne. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) tana wakiltar zafin Ayuba. AT: "Jin daɗina yana kama da Allah ya kama rigata ya tafi" ko 2) yana wakiltar Allah ne ya sa matsalolin Ayuba da yawa. AT: "Kamar dai Allah ne ya yi nasara bisa tufafina" (Duba: metonymy)
Hoton ikon Allah a rufe yake game da Ayuba kwatanci ne. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) tana wakiltar zafin Ayuba. AT: “ya lullube rigar mayafina a kaina” ko 2) yana wakiltar Allah ne ya haddasa matsaloli da yawa na Ayuba. AT: "Kamar dai yana kama ni da abin wuya na nemo"
Ayuba ya ce Allah ya kunyata shi. AT: "Kamar dai ya jefa ni ikin laka ne" ko "Ya ƙasƙantar da ni, kamar mutumin da aka jefa cikin laka"
Wannan yana wakiltar jin daɗin Ayuba na rashin amfani. AT: "Na zama kamar ƙura da toka"
Wannan kalma tana nufin rashin tausayi.
Ayuba ya yi maganar duniyar matattu kamar ya ce gidan da Allah ya sanya duk abubuwa masu rai su tafi. AT: "duniyar matattu, wanda duk abin da ya rayu ya kasance"
Ayuba yana amfani da waɗannan tambayoyin don tabbatar da kansa saboda kuka ga Allah na neman taimako. AT: "Kowa ya ɗaga hannu da hannu don roƙon taimako lokacin da ya faɗi. Duk wanda ke cikin matsala yana kira da taimako." ko "Na fadi, don haka Allah bai kamata na yi laifi ba yayin da na nemi taimakonsa. Ina cikin wahala, don haka na yi kira don neman taimako!"
Anan “haske” yana wakiltar albarkar Allah da falalarsa kuma “duhu” yana wakiltar matsala da wahala. AT: "Na jira hasken albarkar Allah, amma a maimakon haka na ɗanɗano duhun wahala"
Ayuba yana maganar zuciyarsa kamar dai mutum ne. AT: "Na shiga uku a cikin zuciyata kuma jin da nake yi ba ya ƙare"
Zamanin wahala da ke zuwa kan Ayuba yana wakiltar Ayuba yana fuskantar wahala na kwanaki da yawa. AT: "Ina fuskantar wahala kwanaki da yawa" ko "Ina wahala kowace rana"
Kasancewa dan uwan wadannan dabbobin wata magana ne ta kasancewarsu. AT: "Ni kamar diloli ne da kuza mu fashe da kuka a jeji"
A nan "kasusuwa" yana nufin jiki dukka, wanda ke fama da zazzabi.
Anan "garayata" tana wakiltar Ayuba da kansa, kuma yana wakiltar sha'awar sa ta raira waƙoƙin makoki kawai. AT: "Ina kawai waƙoƙin makoki a kan garayata"
Yin makoki shi ne babban kuka saboda tsananin bakin ciki ko azaba.
1Na yi alƙawari da idanuna; me zai sa in dubi budurwa har in yi sha'awa?2Gama wanne irin rabo zan samu daga wurin Alla a sama, gãdon me kuma zan samu daga wurin Mai Iko a samaniya?3Na kan yi tunanin masifa daga wurin mutane mara sa adalci, bala'i na masu aikata mugunta ne.4Ko Allah ba ya ganin hanyoyina da dukkan matakallaina?5Idan ina tafiya da rashin gaskiya, idan kafata tana hanzarin aikata yaudara,6bari a auna ni da ma'aunin yadda Allah zai san halayena na kwarai.7Idan ƙafata ta kauce daga hanya, idan kuwa zuciyata ta bi sha'awar idanuna, idan akwai wani aibi ya wuce ta hanuwana,8to bari na shuka, bari wani yaci, bari kuma amfanina ya tumɓuke.9Idan zuciyata tayi sha'awar wata mace, idan har naje na laɓe a ƙofar maƙwabcina,10to bari matata tayi niƙan hatsi domin wani, bari waɗansu su kwanta a kanta.11Gama wannan mugun laifi ne ƙwarai; lallai, alƙalai ne zasu hukunta.12Domin wuta mai ci zata hallaka, zata cinye har zuwa Abaddon, zata kone dukkan girbina har saiwa.13Idan naƙi kulawa da roƙo domin adalci daga barorina maza da mata sa'ad da suka kawo koke-kokensu a kaina,14to me zan yi lokacin da Allah ya tashi don ya hukuntar da ni? Sa'ad da yazo yi mani shari'a, ya ya zan amsa masa?15Ai shi wanda yayi ni a mahaifa shi ne ya yi su kuma? Ba shi ne dai ya siffata mu dukka a cikin mahaifa ba?16Idan na taɓa hana matalautan mutane daga sha'awarsu, ko idan nasa gwauruwar da mijinta ya mutu idanunta su dushe da kuka,17ko kuwa naci ɗan abincina ni kaɗai ban bar waɗanda basu da iyaye maza suma su ci abincina ba--18gama tun daga yarintaka marayu suka yi girma tare da ni kamar mahaifi, na lura da mahaifiyarsa, gwauruwa, daga cikin mahaifiyata.19Idan na ga wani yana lalacewa saboda rashin sutura; ko idan naga wani mutum da bukata na rashin sutura;20idan zuciyarsa bata albarkace ni ba domin bai ji dumi da ulun tumakina ba,21idan na daga hannuna gãba da marayun mutane, don naga taimakona a ƙofar birni, sai a kawo ƙara a kaina!22Idan na yi waɗannan abubuwa, bari kafaɗata ta ɓaɓɓalle daga in da su ke, bari hannuna ya karye daga mahadarsa.23Gama firgici da bala'i daga wurin Allah; saboda ɗaukakarsa, ba zan iya yin kome a kan waɗannan abubuwa ba.24Idan nasa zinariya abin fatana, idan nace ina da zinariya mai kyau, 'Kana nan yadda na ke da aminci;25idan ina murna saboda dukiyata ta na da girma, ko saboda abin da na mallaka ne, sai su kawo s̀̀̀u a kaina!26Idan na ga rana tana haske, ko wata yana tafiya da haskensa,27idan zuciyata jarabtu a asirce, yadda bakina zai sumbace hannun a sujadarsu--28wannan ma zai zama laifi wanda shari'a zata hukunta, gama na musanta Allah wanda ke sama.29Idan ina murna saboda hallaka ta sami wanda ya ke maƙiyina, ko zan yiwa kaina barka ne, idan wahala ta same shi, zai kawo ƙarata!30Lallai, ban ma yarda in bar bakina ya yi zunubi ta wurin tambaya don ransa tare da la'ana.31Idan a rumfata akwai mutanen da suka ce, 'Wane ne zai sami wanda bai ƙoshi da abincin Ayuba ba?"32(ko da baƙon da baya zama a dandalin birni, domin kullum ina buɗe ƙofufina ga mai tafiya), idan ba haka ba ne, sai a kawo ƙarata!33Idan, kamar 'yan adam, na ɓoye zunubai na ta wurin ɓoye laifi a cikina34(saboda ina jin tsoron babban taron jama'a, domin tsoron rainin iyalai gare ni, na yi shuru, ban ma iya fita waje ba), sai a kawo ƙarata!35Oh, idan za a sami wani shi kaɗai ya ji ni! Duba a nan ga sa hannuna; bari Mai Iko ya amsa mani! Idan ni kaɗai na yi ƙarar maƙiyana a rubuce!36Babu shakka zan ɗauke ta a buɗe a kan kafaɗata; zan sa ta kamar rawani.37Zan furta a kansa lissafin takawa ta; a matsayin asirin sarki zan tafi wurinsa.38Idan ƙasata tana kuka da ni, tare da ƙungiyoyinta,39idan na ci amfaninta ba tare da biya ba, ko na yi sanaɗin mutuwar masu ita,40bari ƙayayuwa su tsiro maimakon alkama, tsire tsire marasa amfani kuma maimakon bali." Maganganun Ayuba sun kare.
Ayuba ya ci gaba da magana.
Abin da aiki ya yi alkawarin za a iya bayyana a sarari. AT: "Na yi alƙawarin ba zan yi kallon budurwa ba" ko kuma "Na yi alƙawarin ba zan kalli budurwa da sha'awar aure ba”
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa ba zai taɓa cika alkawarinsa ba. AT: "Saboda haka ba zan duba da sha'awar budurwa ba."
Ma'anar mai yiwuwa shine Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don ƙarfafa 1) cewa Allah ba zai albarkaci mummunan hali ba. AT: "Gama idan na yi sha'awar mace, Allah Mai Iko Dukka ba zai albarkace ni ba." ko 2) cewa Allah zai azabtar da munanan halaye. AT: "Gama idan na kalli mace da sha'awar, hakika Allah Maɗaukaki a sama zai hukunta ni."
Anan "hanyoyi na" da "matakai na" magana ne na halayen Ayuba. Anan "ga hanyata" da "ƙidaya dukkan matakai na" na sanin duk abin da Ayuba yake yi. Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa Allah ya san duk abin da yake yi. AT: "Tabbas Allah yana dubana kuma ya san duk abin da nake yi."
A cikin Ayuba 31: 5-40 Ayuba ya bayyana yanayi daban-daban inda zai cancanci azabar Allah. Amma, ya sani cewa ba su da gaskiya kuma ba shi da laifi.
Anan "tafiya" da "sauri" magana ne waɗanda ke wakiltar yadda Ayuba ya rayu. AT: "aikata wani abu na karya ko da gangan aka ruɗi kowa"
Mutane sunyi amfani da ma'auni don auna abubuwa da ƙayyade ƙimar su. Wannan hoton yana wakiltar yin hukunci da gaskiya. Ana iya bayyana shi a cikin tsari mai aiki. AT: "bari a yi mini shari'a da gaskiya" ko "bari Allah ya yi mini hukunci da gaskiya"
Anan "mataki na" wani magana ne ga halayen Ayuba, kuma "an bi shi daga madaidaiciyar hanya" magana ne don canji daga rayuwa ta gari. AT: "Idan na canza daga rayuwa ta dama" ko "Idan na daina yin abin da ke daidai"
Anan “zuciyata” da “idona” suna game da abin da Ayuba yake so da gani. Zuciyar da ke bin idanu wani kwatanci ne na son aikata abin da ya gani. Yana nuna cewa wannan yana nufin abubuwan zunubi da Ayuba yake gani. AT: "Idan na so yin kowane irin zunubi da na gani"
Ayuba yana cewa idan ya yi zunubi da gaske, to wannan mummunan abin da ya kamata ya same shi. Zai yi aiki tuƙuru wajen shuka gonakinsa, amma ba zai iya ci ba.
Anan “zuciyata” tana wakiltar Ayuba. Anan kalmar "yaudare" tana bayyana ra'ayin "yaudarar". Kalmar "mace" tana bayyana ra'ayin "matar wani." Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Idan matar wani ta ruɗe ni" ko "Idan na buƙaci matar wani"
Za a iya bayyana a sarari abin da ya sa ya jira a ƙofar maƙwabcinsa. AT: "Idan na jira a ƙofar maƙwabta don ni ma in kwana da matarsa"
Ma’anoni masu ma’ana su ne 1) wannan lafazin mugunta ne wanda yake nufin Ayuba yana cewa wataƙila matarsa ta kwana da wani mutum ko 2) wannan na nuna cewa za ta zama bawa ta yi aiki ga wani mutum.
Ayuba ya ci gaba da bayanin yanayi inda ya cancanci hukuncin Allah, amma ya san ba gaskiya bane.
Kalmar "wannan" tana nufin Ayuba yana bacci tare da wata mace.
Ayuba yayi magana game da lahanin bacci da wata mace yana haifarda kamar wutar da take lalata komai. Kalmomin "wannan" da "shi" suna nufin yin barci tare da matar wani. AT: "Gama zina kamar wutar da take ƙone komai daga nan zuwa Abaddon kuma hakan zai ƙone dukkan girkina"
Kalmar "shi" a nan tana nufin aikin bacci tare da matar wani. Wannan matakin magana ne tana hukuncin da Ayuba zai sha sakamakon aikin. Wutar da ke ƙona girbin sa, magana ne tana rasa duk abin da ya yi aiki da ita. AT: "waɗanda suka hukunta ni za su kwashe duk abin da na yi aiki da su"
Ayuba ya yi amfani da waɗannan tambayoyin don jaddada cewa idan Allah zai shar'anta shi, Ayuba ba zai iya nuna kansa ya zama mai kyau ba. AT: "to babu abin da zan ce don kare kaina lokacin da Allah ya zo ya yi mini hukunci."
Ayuba ya yi amfani da waɗannan tambayoyin don nuna cewa bai bambanta da bayinsa ba. Yana nuna cewa Allah zai yi fushi idan Ayuba zai ɗauki barorinsa kamar marasa ƙima da kansa. AT: "Wanda ya sa ni cikin mahaifa shi ne ya yi su. Shi ya maishe mu duka cikin mahaifa."
"Idan na kiyaye talakawa daga samun abin da suke so"
Anan "don yayi girma" yana nufin gwauruwar da ke da mummunan gani daga yawan kuka. AT: "idan na sa gwauruwa ta yi kuka cikin baƙin ciki mai ƙarfi"
Anan "maraya" yana wakiltar marayu gaba ɗaya. Ayuba yana bayyana yadda ya kula da marayu da gaske. AT: "domin ko da ina saurayi na kula da marayu kamar uba"
Ayuba yana bayanin yadda ya bi da mata gwauraye da gaske. Tare da furcin “daga mahaifar mahaifiyata” ya yi amfani da ƙari wajen ƙarfafa cewa ya yi wannan duk rayuwarsa. AT: "Duk rayuwata na jagoranci mahaifiyar marayu, gwauruwa" ko "a dukkan rayuwata na jagoranci gwauraye"
Kalmomin "zuciyarsa" tana wakiltar talakawa wanda ke buƙatar sutura. AT: "idan bai yi mini albarka ba"
Anan “ulu na tumakinna” suna wakiltar bargo ko sutturar da aka yi da ulu na tumakin Ayuba. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "saboda ulu tumakin ba su yi masa zafi ba" ko "saboda ban ba shi tufafin da aka yi da ulu ba"
Dagawar sama da hannu kan wani yana wakiltar barazanar cutar da shi. AT: "Idan na yi barazanar cutar da marayu"
Anan "gani" wani magana ne na "san," "tallafi" wani magana ne na "amincewa," "ƙofar birni" ma'ana ce ga shugabannin da suka zauna a ƙofar garin. AT: "Na san cewa shugabannin a ƙofar garin za su amince da ni"
Wannan shi ne inda manyan mutanen garin za su hallara su yanke shawara.
Wannan shine dalilin da Ayuba baiyi wani mummunan aikin da yayi magana akai a ayoyi 7 zuwa 21 ba.
Ana iya fassara kalmar nan "bege" tare da kalmomin nan “dogara” ko “bege.” AT: "Idan na dogara da zinariya" ko "Idan na yi fatan samun zinariya da yawa zai sa na sami tsaro"
Anan "hannuna" yana wakiltar ikon Ayuba na yin abubuwa. AT: "Na sami dukiya da yawa ta ikon kaina"
Anan "tafiya" yana wakiltar motsi a hankali. AT: "wata zai yi gaba zuwa sama"
Ana iya bayyana kalmar ta "haske" tare da kalmar "mai haske". AT: "wata mai haske yana motsawa sama" ko "waton yana tafiya mai haske a sararin sama"
Anan “zuciyata” tana wakiltar Ayuba. Wannan kalma za a iya bayyana ta a cikin tsari mai aiki. AT: "idan na ruɗe su a asirce" ko "idan na yi niyyar bauta musu a asirce"
Anan “bakina” yana wakiltar Ayuba. Wannan alama ce ta kauna da takawa. AT: "don haka da na sumbace hannuna"
"Zan kasance marar aminci ga Allah wanda ke sama"
"lokacin da ya sami bala'i"
Anan "bakina" yana wakiltar magana Ayuba. AT: "Gaskiya ban bar kaina nayi zunubi ba" ko "Gaskiya ban yi zunubi ba"
Anan "neman ransa tare da la'ana" yana nuna la'anar rayuwar wani ne domin ya mutu. AT: "ta la'ane shi domin ya mutu" ko "ta zagi rayuwarsa"
Rumfa tana wakiltar gidan Ayuba. Mazajen rumfata nasa sun hada da danginsa da kuma barorinsa. Duk waɗannan sun san Ayuba da kyau. AT: "mutanen gida na" ko "membobina da barori na"
Mutanen Ayuba za su yi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa Ayuba mai karimci ne ga kowa. AT: "Kowa ya cika da abincin Ayuba!" ko kuma "Duk wanda muka san shi ya ci yawancin abincin Ayuba kamar yadda yake so!"
Ayuba yana bayanin yadda ya bi da baƙi da gaske. Anan "zauna a cikin filin gari" yana wakiltar bacci na dare a farfajiyar birni. AT: "Baƙi ba su taɓa yin bacci a dandalin birni ba" ko kuma "baƙi ba su taɓa yin barci a waje ba"
Anan "na buɗe ƙofofina ga matafiyi" yana wakiltar maraba matafiya zuwa gidansa. AT: "Na yi marhabin da matafiyi a cikin gidana"
Anan “sun ɓoye zunubaina” suna wakiltar ƙoƙarin hana mutane sanin cewa ya yi zunubi. AT: "Idan ... Na yi ƙoƙarin ɓoye zunubaina na sirri"
Wannan yana wakiltar kokarin hana mutane sanin cewa shi mai laifi ne. AT: "ta hanyar ɓoye shaidar laifina a cikin rigata" ko "kamar wanda ke ɓoye shaidar laifin sa cikin suturar sa"
Wannan zai zama dalilin ɓoye zunubansa. Waɗannan suna nufin abu ɗaya ne. Sun jaddada cewa mutum na iya ɓoye zunubinsa saboda yana tsoron abin da wasu mutane za su yi tunani game da shi.
Wannan karin haske ya nuna burin Ayuba. AT: "Da a ce ina da wani ya saurare ni" ko "Ina fata wani ya saurare ni"
Anan "sa hannuna" yana wakiltar alkawarin Ayuba ne cewa duk abin da yake faɗi gaskiya ne. Yana maganar korafinsa kamar ya rubuta takamaiman doka. AT: "Na yi alkawari sosai cewa duk abin da na faɗi gaskiya ne"
Anan amsar wataƙila tana nufin gaya wa Ayuba ne kuskuren da ya zargi Ayuba da aikatawa. AT: "Maɗaukaki ya faɗi abin da na yi ba daidai ba" ko "Ina fata Madaukaki ya faɗi abin da na yi ba dai-dai ba"
Wannan yana nuna nufin Ayuba. Ayuba yayi magana kamar dai matsalolin sa shaida ce cewa wani ya rubuta abin da ake zargin sa da mummunan zunubi. AT: "Ina so in sami la'anar da abokin gaba na ya rubuta" ko "Idan zan karanta karar abokan adawar na game da ni"
Ma'anar mai yiwuwa sune 1) wannan yana nufin Allah ko 2) wannan yana nufin wani.
Wannan yana nuna sanya shi inda kowa zai iya karanta shi.
Anan “matakai na” suna wakiltar ayyukan Ayuba. AT: "Zan sanar da shi lissafin duk abin da na yi" ko "Zan gaya masa duk abin da na yi"
Wannan yana nufin Ayuba zai kusanci Allah ba tare da tsoro ba. Ayuba ya nuna cewa zai iya yin hakan domin bai yi laifi ba. AT: "Zan kusanci shi da ƙarfin hali"
Wannan ya kammala bayanin Ayuba game da yanayin da ya cancanci hukuncin Allah, amma ya san ba gaskiya bane.
Ayuba ya yi maganar yin laifi kamar dai ƙasar sa ta kasance mutumin da ke yin kuka ne da Ayuba saboda laifin da Ayuba ya yi wa ƙasar. AT "Idan na yi kuskure game da ƙasata" ko "Idan na saci ƙasarmu daga wani"
Wannan yana wakiltar mutuwa. AT: "a mutu"
Kalmar "bari" da "girma" an fahimta daga sashin da ya gabata. Wani zaɓi: "Bari ciyayi su yi tsiro a maimakon sha'ir"
1Sai mutanen uku suka daina ba Ayuba amsa saboda yana ganin kansa shi adali ne.2Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz daga iyalin Arama, ya husata da fushi a kan Ayuba saboda ya baratar da kansa maimakon Allah ya baratar da shi.3Elihu ya fusata da fushi a kan abokansa uku saboda sun rasa amsawa Ayuba, duk da haka sun gani Ayuba ne ke da laifi.4Yanzu Elihu ya jira ya yi magana da Ayuba, don sauran mutanen uku sun girme shi da shekaru.5Sa'ad da Elihu ya ga babu wata amsa a bakunan waɗannan mutanen uku, har fushinsa ya yi ƙuna.6Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya yi magana ya ce, "Ni yaro ne, ku manya ne sosai. Wannan ya sa na yi shuru, ban iya faɗa maku ra'ayina ba.7Na ce, "Yawan kwana su yi magana; yawan shekaru kuma su koyar da hikima.8Amma akwai ruhu a cikin mutum; numfashin Mai Iko ya ke ba da sani da basira.9Ba manyan mutane ne kaɗai waɗanda suke da wayo da hankali ba, ko tsofaffin mutane kaɗai suke da sanin adalci da gaskiya.10Don haka nace da ku, 'Ku saurare ni; zan kuma faɗa maku ta wa fahintar.'11Duba, na jira domin inji maganarku; na kasa kunne da jin muhawararku, tun kuna tunani a kan abin da za ku faɗa.12Lallai, na saurare ku, amma duba, babu wanda ya kada Ayuba ko wanda ya bashi amsar maganganunsa.13Ku yi hankali kada wani ya ce, "Mun sami hikima! Allah ne zai ci nasara a kan Ayuba; mutum mai mutuntaka ba zai iya ba.14Gama Ayuba ba da ni ya ke magana ba, saboda haka ba zan amsa da irin amsarku ba.15Waɗannan mutane uku abin ya cika masu ciki, ba su ƙara amsawa Ayuba ba; ba su da sauran abin da za su ce kuma.16Ni kuma zan tsaya don su basu ce kome ba, don sun tsaya a wurin shiru, basu da wata amsa kuma?17A'a, ni kuma zan ba da ta wa amsa; zan kuma faɗa masu na wa sanin.18Gama ina cike da magana, ruhu da ke ciki na ya iza ni.19Duba, kirjina ya na kama da ruwan inabin da ba shi da mafitar iska. kamar sabuwar salkar ruwan inabi wadda ya ke shirin ya fashe.20Zan yi magana saboda in huce, zan buɗe lebuna na in ba da amsa.21Ba zan nuna san zuciya ba, ko kuma in yi wa wani mutum fadanci.22Gama ni ban san yadda zan iya yi fadanci ba; idan nayi haka kuwa Mahaliccina zai ɗauke ni nan da nan.
Idanu suna wakiltar gani, da gani suna wakiltar tunani ne ko hukunci. AT: "ya ɗauke shi mai adalci ne"
Wannan ya kwatanta fushin Elihu da wani wanda ya fara wuta. Hakanan, za a iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz, daga zuriyar Ram, ya yi fushi da Ayuba"
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan shi ne sunan mai mutane kungiyar.
Wannan yana nuna cewa ya ɗauki kansa mara laifi ne kuma ya yi imani cewa Allah bai yi kuskure ya hukunta shi ba. AT: "ya baratar da kansa kuma ya faɗi cewa Allah bai yi kuskure ya azabta shi ba"
Wannan ya kwatanta fushin Elihu da wani wanda ya fara wuta. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Elihu kuma ya yi fushi sosai da abokansa guda uku"
Ana amfani da wannan kalmar wajen dakatar da wani sashin asalin labari. Wannan ya nuna bayanin karin haske game da Elihu.
Wannan yana nufin cewa mutanen an gama magana da Ayuba. Wannan yana magana game da mutanen da wataƙila suna da amsar kamar dai amsar wani abu ne da zai kasance a cikin bakinsu. AT: "cewa waɗannan mutane ukun ba su da sauran abin da za su faɗa" ko "cewa waɗannan mutanen uku ba su da amsar da za su ba Ayuba"
Wannan ya kwatanta fushin Elihu da wani wanda ya fara wuta. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "ya yi fushi sosai"
Anan "ku" yana nufin Ayuba da abokansa uku.
Waɗannan layin guda biyu suna ma'ana iri ɗaya ne. Elihu ya nanata cewa tunda tsofaffi sun fi saurayi ƙarfi, ya kamata su zama na farko da za su faɗi abin da suka sani. AT: "Wanda ya rayu shekaru da yawa ya kamata ya yi magana; wanda zai tsufa yakamata ya koyar da hikima"
Elihu ya ci gaba da magana da Ayuba da abokansa.
Dukansu jumla suna nufin abu ɗaya ne. Elihu yana ƙarfafa cewa hikimar mutum ta Allah ce. AT: "akwai wani ruhu a cikin mutum, wato, numfashin Mai Iko Dukka wanda yake"
Anan ruhun yana wakilta ta "numfashi." AT: "ruhun Mai Iko Dukka"
"Na jira naji abinda zaku ce." Kalmar "naku" tana nufin abokan Ayuba.
Wannan yana nufin cewa sun yi imani cewa sun gano abin da ke da kyau. AT: "Mun gano abin da ke da hikima"
Wannan yana magana game da Allah yana amsawa ga Ayuba kuma yana gyara shi kamar dai yana cin nasara da shi a yaƙi. AT: "don ɓata wa Ayuba laifi" ko "don ba da amsa ga Ayuba"
"ta hanyar faɗin abin da kuka fada"
mamaki, ya kasa magana
Elihu ya yi amfani da tambaya don ƙarfafa cewa ba zai jira wani lokacin yin magana ba. Elihu ya amsa wannan tambayar da kansa a aya ta gaba. AT: "Amma saboda ba ku yin magana, ba zan ƙara jira ba; Ka kawai tsaya a nan ba kwa amsawa"
"Yanzu zan dauki lokaci na don amsa"
Elihu yayi maganar samun abubuwa da yawa da zai faɗi kamar yana cike da magana. AT: "Ina da abubuwa da yawa da zan faɗi"
"ruhuna ya tilasta ni in faɗi shi"
Yayin da ruwan inabin yake motsa shi, iska yana tarawa a cikin akwati. Idan ba a barin iska ɗin sai kwandon ya fashe. Elihu yana nufin yana da abubuwa da yawa da zai faɗi cewa idan bai yi magana ba yana jin kamar zai fashe. Hakanan, waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. AT: "Ina jin kamar kirjina kusa fashewa, kamar tukunyar ruwan inabin da ba ta da iska"
Wannan yana wakiltar Elihu, musamman ruhunsa. AT: "ruhuna ne" ko "Ni ne"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Zan iya jin daɗi"
Anan "lebe" suna wakiltar bakin. AT: "buɗe bakina"
"ba zan yabe wani mutum ba ko kuma sanya masa taken girmamawa"
Wannan suna ne wanda yake nufin Allah. AT: "Allah wanda ya yi ni"
Wannan yana nuna cewa zai hallaka shi. AT: "halaka ni"
1Amma yanzu, kai Ayuba, ina roƙon ka, ka saurari abin da zan ce, ka saurari dukkan maganganuna.2Duba yanzu, na buɗe bakina; harshena ya yi magana da bakina.3Kalmomina sun zo da gaskiyar zuciyata; leɓuna suna faɗar ilimi tsantsa.4Ruhun Allah ne yayi ni; numfashin Mai Iko ne ya bani rai.5Idan za ka iya ka amsa mani; ka shirya kalmominka dai-dai a gabana, kayi tsaye a kansu.6Duba, ni kamar ka mu ke a wajen Allah; ni kuma daga yumɓu aka siffanta ni.7Duba, razanata ba zata sa ka ji tsoro ba, ko matsawata ta zama da nauyi a kanka.8Babu shakka maganar da ka yi na ji ta; na kuwa ji amon maganganunka,9ni tsabtattace ne, ba wani laifi, bani da laifi, kuma ba wani zunubi a gare ni.10Duba, Allah ya sami damar zargi na, ya ɗauke ni tankar maƙiyinsa.11Ya sa ƙafaffuna a turu, ya na lura da dukkan hanyoyina.'12Duba, a wannan kayi kuskure--zan baka amsa, gama Allah ya fi kowane mutum girma.13Me yasa kake yi masa gunaguni? Baya lissafin kowanne abu da yayi.14Gama Allah yakan yi magana sau ɗaya ne--i, har sau biyu, duk da haka mutum baya kula da ita.15Cikin mafarki, ko cikin wahayi da dare, a sa'ad da dogon barci ya faɗo wa mutane, ana barci a kan gado--16sai Allah ya buɗe kunnuwan mutane, ya tsorata su da faɗakarwarsa,17don ya kawar da mutum daga zunubinsa da yayi nufi, ya kuma kawar da girmankai daga gare shi.18Allah yakan hana ran mutum daga faɗawa rami, rayuwarsa daga haurawa zuwa mutuwa.19A kan hori mutum kuma da cuta mai zafi a gadonsa, yayi ta fama da azaba a cikin ƙasusuwansa,20saboda da ransa ya kyamaci abinci, kurwarsa ta ƙyamaci daɗinsa.21Tsokar jikinsa ta rame ƙangayau yadda ba za a iya ganinta ba, ƙasusuwansa baza a iya gani ba, yanzu sun zama waje.22Lallai, ranna yasa gab da shiga rami, ransa yana wurin waɗanda suke so su hallaka shi.23Amma idan a ce akwai wani mala'ika wanda zai yi sulhu dominsa, mai sulhu, ɗaya daga cikin duban mala'iku, zai nuna masa abin da ke dai-dai da zai yi,24idan mala'ikan da zai yi masa alheri ya faɗa wa Allah, 'Cece wannan mutum daga gangarawa zuwa cikin ramin; dana sami abin da zai fansa domin sa,'25Naman jikinsa zai koma fiye da na yaro, zai komo irin kwanakin ƙarfin ƙuruciyarsa.26Zai yi addu'a ga Allah, Allah kuma zai yi masa alheri, saboda ya ga fuskar Allah da murna. Allah zai ba mutumin nasararsa.27Sai wannan mutum ya raira waƙa a gaban sauran mutane yace, 'Na yi zunubi, ban yi dai-dai ba, amma zunubi bai sa a hore ni ba.28Allah ya fanshi raina daga tafiya can cikin rami, raina zai cigaba da ganin haske.29Duba, Allah yayi dukkan waɗannan abubuwa ga mutum harma sau biyu, i, harma lokatai uku,30ya komo da ransa daga rami, don a haskaka shi da hasken rai.31Ka yi lura Ayuba, ka saurare ni, kayi shiru, zan yi magana.32Idan kana da wani abu da zaka ce, ka amsa mani, yi magana, don in tabbatar maka kana dai-dai.33Idan ba haka ba, sai kayi shiru ka ji ni, ka zauna shiru, zan kuwa koya maka hikima."
Elihu ya ci gaba da magana
Waɗannan suna nufin dai-dai da wancan. Elihu yana jaddada cewa a shirye yake ya yi magana. "Harshen" maganarsa yana wakiltar kansa yake magana. AT: "Na buɗe bakina kuma na fara magana"
Anan Elihu ya ambaci kansa da kansa ta hanyar "zuciyarsa" yayin da yake magana game da kasancewa dai-dai. AT: "Zan yi magana da gaskiya" ko "Zan yi magana da gaskiya"
Anan Elihu yana magana game da kansa ta "leɓunsa" don ƙarfafa maganarsa. AT: "Zan yi muku magana da gaskiyan abin da na sani"
Waɗannan layin guda biyu suna ma'ana iri daya ne. Elihu yana nanata cewa Allah ne ya yi shi kuma haka ya ba da iko ga abin da yake faɗi.
Wannan yana maganar Ayuba yana shirya abin da zai faɗi kamar yana kafa da kuma shirya abubuwa na zahiri. AT: "shirya abin da za ku faɗi, ku miƙe tsaye ku amsa mini"
Anan gani yana wakiltar hukunci ko kimantawa. Watau fassarar: "Ni dai kamar yadda kake a hukuncin Allah" ko "Allah yana shar'anta ni kamar yadda yake yi maka hukunci"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah kuma ya yi ni" ko "Allah ya sanya mu biyun"
"baka bukatar jin tsoron ni"
Wannan yana nufin cewa ba zai hana Ayuba aiki ko kuma wahalar da shi ba. Yayi Magana game da nauyin rai na nan kamar dai wani nauyi ne na jiki. AT: "ba zan kallafa muku ba" ko "ba zan zalunce ku da abin da na faɗi ba"
"Na ji kuna cewa"
"Ban yi zunubi ba"
Elihu ya ci gaba da faɗo abin da ya ji Ayuba yana faɗi.
"Hannun jari" sune shinge na katako wanda mai tsaron kurkuku ya sanya ƙafafun fursunoni don taƙaita motsi. Ayuba yayi maganar jin kamar yana fursuna ta hanyar cewa yana cikin hannun jari. AT: "Na ji ya mai da ni fursuna"
Elihu yayi amfani da wannan tambayar don jaddada cewa bai kamata Ayuba ya yi faɗa da Allah ba. Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Kada kuyi gwagwarmaya da Allah." ko "Kada ku gwada yin jayayya da Allah."
"Ba lallai ne ya bayyana mana komai da yake yi ba"
Wannan karin magana ne. AT: "Allah yana maimaita magana sau da yawa ta hanyoyi dabam-dabam"
Wannan yana maganar mutane suna cikin barci mai zurfi kamar dai bacci ya same su ko ya rinjaye su. AT: "lokacin da mutane ke yin cikakken barci akan gado"
Wannan yana maganar Allah yana sanar da mutane abubuwan da kamar yana buɗe kunnuwansu ne don su ji. AT: "sai Allah ya bayyana wa mutane wani abu"
Wannan yana maganar Allah yana hana mutum yin wani abu kamar yana jan jiki da lalacewa daga cutarwa. AT: "domin a nisantar dashi"
Duk waɗannan maganganun suna nufin abu ɗaya ne. AT: "Allah yana ceton mutane daga kabari da mutuwa"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah kuma yana azabtar da mutum"
Wannan yana nuna cewa mutumin yana fuskantar wannan azaba wanda dole ne ya kwanta a gado. AT: "tare da raɗaɗi domin dole ne ya kwanta a gado"
Waɗannan jumla guda biyu suna nufin ma'ana dai-dai ne, cewa mutumin yana cikin tsananin wahala har ya kasa cin abinci. Mutumin da “ransa” da “kurwarsa” suke wakiltar mutumin. AT: "sakamakon shi ne baya son kowane irin abinci, har ma da abinci na musamman"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. “Namansa” yana nufin kitsensa da ƙashin kansa, baya ga fatar jikinsa. AT: "Cutar tana sanya jikinsa rauni da bakin ciki har mutum ya iya ganin kasusuwarsa"
Anan mutum yana wakiltar "kurwarsa". AT: "yana gab da shiga cikin kabari"
Anan mutumin yana wakiltar "ransa". Kalmomin "waɗanda suke son halaka ta" yana nufin wurin da mutane suke bayan sun mutu. AT: "kuma yana gab da zuwa wurin da mutanen da suka mutu suke tafiya" ko kuma "da sannu zai je wurin mamaci"
Wannan baya nufin takamaiman mutum. Elihu ya ci gaba da magana game da kowane mutum gaba ɗaya.
A cikin wasu yaruka na iya zama mafi dabi'un halitta a koma zuwa "adadi mai yawa" maimakon "dubu." AT: "ɗaya daga yawan mala'iku"
Wannan yana nufin cewa mala'ika ya sami wata hanya ta biyan zunuban mutumin don kada ya mutu. AT: "Gama na sami wata hanya don ku kange shi daga mutuwa"
Ana amfani da wannan kalmar "sa'an nan" don alamar abin da zai faru idan Allah ya amsa roƙon mala'ikan. AT: "to a sakamakon" ko "sakamakon roƙon mala'ika ga Allah"
Wannan na maganar mutumin da aka warkar kuma jikinsa ya sake karfi kamar jikinsa ya zama sabo kamar jikin yarinyar. AT: "jikin marar lafiya zai sake zama kamar jikin saurayi"
Wannan na maganar jikin mutumin yana da ƙarfi kamar yadda yake lokacin da yake saurayi. AT: "zai sake ƙarfi kamar yadda yake saurayi"
Wannan karin magana ne. AT: "yana murna da bauta wa Allah"
Anan Allah yana wakiltar "fuskarsa". AT: "Allah"
"Allah zai ceci mutumin" ko kuma "Allah zai sake wasu abubuwa domin mutumin kuma"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "amma Allah bai yi mini horo na aikata zunubi ba"
Anan mutumin yana wakiltar "ransa". Hakanan, ana maganar rayuwa kamar ganin haske. AT: "Zan ci gaba da rayuwa in ga wayewar gari" ko "Zan ci gaba da rayuwa"
Wannan karin magana ne. AT: "kuma da sake"
Wannan karin magana ne kuma ana iya bayyana ta a yanayin aiki. AT: "zai yi farin ciki har yanzu yana da rai"
Waɗannan jumla suna nufin abu ɗaya. AT: "Ya Ayuba, ka saurare ni sosai"
Wannan karin magana ne. AT: "ba ku da laifi" (Duba: figa_idiom)
1Hakanan, Elihu ya ci gaba da magana:2"Ku saurari kalmomina, ku masu hikima; ku ji ni, ku masu ilimi.3Domin kunnuwa na gwada kalmomi kamar yadda faranti ke ɗanɗana abinci.4Bari mu zaɓar wa kanmu abin da ke na adalci, mu kuma yiwa kanmu abin da ke mai kyau.5Domin Ayuba yace ni adali ne, amma Allah ya ɗauke abin da ke dai-dai.6Ba a ma la'akari da adalcina, sai aka ɗauke ni maƙaryaci, raunukana kuma basu warkuwa duk da yake bani da zunubi.7Wanne irin mutum ne Ayuba wanda ke shan ba'a kamar ruwa,8wanda ke tafiya da ma su yin mugunta, wanda kuma ke rayuwa tare da miyagu.9Domin ya ce ba amfani mutum yayi abin da ke mai kyau a gaban Allah10Ku saurare ni ku mutane masu fahimta Allah ya sauƙaƙe ace Allah yayi aikin mugunta, kuma Allah ya sha ƙarfin ace yayi zunubi,11Domin yana sakawa kowanne mutum gwargwadon aikinsa, kowanne mutum kuma gwargwadon abin da ya aikata.12Hakika Allah ba ya aikata mugunta, kuma mai iko dukka bai taɓa watsi da adalci ba13Wane ne ya ɗora shi bisa duniya? Wane ne kuma ya ɗora duniya a ƙarƙashinsa?14Shi kaɗai ne yasan abin da yake so ya aikata, in har ya taɓa tattaro ruhunsa da numfashinsa,15daga nan sai dukkan talikai su lalace mutum kuma ya koma ƙura.16I kuna da fahimta yanzu sai ku saurari wannan ku saurari ƙarar kalmomina.17Ko wanda yaƙi adalci zai iya yin shugabanci? Ko zaku iya shari'anta Allah? Wanda ke da adalci da kuma girma?18Allah wanda ke cewa da sarki kai ɗan tawaye ne? ko kuma ya ce da masu daraja ku miyagu ne'?19Allah wanda baya nuna tara ga shugabanni kuma baya la'akari da mawadata fiye da matalauta, domin dukkansu aikin hannunsa ne.20A cikin ɗan lokaci sukan mutu; da tsakar dare za a girgiza mutane zasu kuwa shuɗe; za a kwashe ƙarfafan mutane, amma ba ta hannuwan mutum ba.21Domin idanun Allah suna bisa hanyoyin mutum; yana ganin dukkan sawayensa.22Babu duhu, ko dishi-dishi inda ƙofofin laifofi zasu ɓoye kansu,23Domin Allah baya bukatar ya sake yiwa mutum ƙwanƙwanto; babu bukatar kowanne mutum yaje gabansa domin alƙalanci.24Ya kakkarya mutane masu girma gunduwa-gunduwa domin tafarkinsu da ke bukatar ƙarin bincike; ya ɗora waɗansu a madadinsu.25Ta wannan fannin yasan abin da suke yi; ya kaɓantar da waɗannan mutane da dare an kuma hallakar da su.26A idon sauran, ya karkashe su saboda miyagun ayyukansu kamar masu aikata miyagun laifofi,27saboda sun juya masa baya sun kuma ƙi yin la'akari da dukkan tafarkunsa.28Ta wannan hanya, suka sa kukan mutane matalauta yazo gare shi; yaji kukan waɗanda ake zalunta.29In ya yi shiru wane ne zai bashi laifi? in ya ɓoye fuskarsa, wane ne zai ji shi? Yana mulkin al'uma haka kuma kowa,30domin kada mutum marar tsoron Allah ya yi mulki, domin kada a sami wanda zai jefa mutane cikin tarko.31A misali in a ce wani zai ce da Allah, ' Hakika nayi laifi, amma bazan ƙara yin laifi ba,32koya mani abin da bazan gani ba; Nayi zunubi, amma bazan ƙara yinsa ba.'33Kana tunanin cewa Allah zai hori zunubin na wancan mutum, tun da yake kun ƙi abin da Allah ke yi? Dole ne kuyi zaɓi, ba ni ba. To sai ku faɗi abin nan da kuka sani.34Mutane masu fahimta zasu ce da ni-hakika, duk mutum mai fahimta da ya ji ni zai ce,35Ayuba na yin magana ba tare da sani ba; kalmominsa kuma basu da hikima.'36In da za a sa Ayuba a ma'auni na ɗan lokaci saboda maganarsa kamar ta miyagun mutane.37Domin ya ƙara tawaye a kan zunubinsa; ya tafa hannuwansa cikin zagi a tsakiyarmu; ya jera kalmomi gãba da Allah."
"Sa'an nan, Elihu"
Elihu yana kushe Ayuba da abokansa. Ba ya tunanin cewa suna da hikima a zahiri.
Elihu yana nufin mutane suna saurara da kyau don sanin abin da ke da-dai ko ba dai-dai ba kamar yadda muke ɗanɗano abinci don sanin idan yana da kyau ko mara kyau. Anan ana ambaton mutane ta hanyar "kunnen" da kuma "faranti" don jaddada cewa suna dandanawa da ji. AT: "Domin mun saurari kalmomi don sanin abu mai kyau da mara kyau, kamar yadda muke ɗanɗana abinci don sanin abin da ke da kyau a ci"
A nan "mu" yana nufin Elihu, Ayuba, da abokansa uku.
"ya ki ba ni adalci"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah yana ɗaukar ni maƙaryaci ne"
Anan ana maganar rashin lafiyar Ayuba da wahala kamar "rauni". AT: "Ba ni da lafiya kuma ba wanda zai iya warkar da ni"
Elihu yayi amfani da wannan tambayar don tsawata wa Ayuba. Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Babu wani kamar Ayuba"
Elihu yana zargin Ayuba da yi wa wasu ba'a duk lokacin da mutum ya sha ruwa. AT: "wanda ke yin ba'a ga wasu mutane duk lokacin da yake shan ruwa"
Anan "tafiya" kalma ne na yadda mutum yake aikatawa. AT: "wanda ke yin mugunta kamar mugaye"
Waɗannan jumla guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani da su tare don ƙarfafa cewa Allah ba zai taɓa yin abin da ba dai-dai ba. Kalmomin "nesa da ita daga" karin magana ne. AT: "Allah Maɗaukaki ba zai taɓa yin wani abin da yake mugu ko mara daidai ba"
Wannan yana nuna cewa yana bawa mutum abinda ya cancanci aikin da yayi. Anan "aiki" wani magana ne ga abin da mutum yake yi. AT: "Gama yakan ba mutum abin da ya cancanci sakamakon don abin da ya yi"
Kalmomin "nasa hanyoyin" karin magana ne ga yadda mutum yake rayuwarsa. Elihu ya nanata cewa Allah yana ba mutane abin da suka cancanta. AT: "yana sa kowane mutum ya sami ladar da ya cancanci yadda yake rayuwa"
Duk waɗannan tambayoyin suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna nanata cewa babu wanda ya isa ya ba Allah izini domin tuni nasa ne. Waɗannan tambayoyin ana iya rubuta su azaman kalamai. AT: "Babu wanda ya isa ya ba da izinin Allah don ya ɗauki nauyin duniya. Shi ne ya cancanci ya yi mulkin duniya."
Elihu yana kwatanta halin da bai yi imani ba zai taɓa faruwa.
“Ruhun” da “numfashin” Allah sune suke sa dukkan abubuwa masu rai su rayu. AT: "ruhunsa da numfashin da suke ba mu rai"
Anan dukkan abubuwa masu rai suna wakiltar su da "nama". AT: "dukkan abubuwa masu rai"
Wannan yana nufin cewa duk mutane zasu mutu kuma jikinsu zai lalace kuma su zama ƙasa. A cikin farko Allah ya halicci mutum daga turɓaya. AT: "jikin mutane nan da nan za su sake zama ƙasa"
Elihu yayi amfani da wannan tambayar don tsauta wa Ayuba saboda yana nuna cewa Allah ba ya son adalci. AT: "Wanda ba ya son adalci, ba za a tsammaci ya yi mulkin mutane ba. Don haka ba za ku iya yin Allah wadai da adalci, mai iko, kuma ba ku iya cewa abin da ya yi ba daidai ba ne."
An yi amfani da wannan tambayar don tabbatar da cewa Ayuba bashi da iko ko dalilin da zai hukunta Allah. AT: "Ba za ku iya kuɓutar da Allah wanda yake adali da ƙarfi ba!" (Duba: rquestion)
Wannan ya ci gaba da tambayar daga ayar da ta gabata, ta nanata wa Ayuba cewa ba zai iya hukunta Allah ba. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Yana gaya wa wasu sarakuna, 'Kuna da miyagu,' sai ya ce wa wasu manyan mutane, 'Ku miyagu ne.' "
"mugunta" ko "marasa amfani"
Anan "hannaye" suna nufin iko. AT: "Gama Allah ya yi su duka"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. Kalmomin "za a girgiza" kalma ce mai ma'ana da za a buge ta. AT "Allah yakan buge su har su mutu"
Wannan yana nuna cewa Allah ne yake jawo mutane su mutu, ba mutane ba. Hakanan, za'a iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah ba mutum bane ke haddasa mutuwar manyan mutane"
“Allah” yana wakiltar gabansa. Kalmomin "hanyoyin mutum" karin magana ne ga abin da yake yi da yadda yake rayuwa. AT: "Gama Allah yana duban duk abin da mutum yake yi"
"saboda haka ya iya yanke hukunci" ko "a yi masa hukunci"
Wannan yana maganar Allah yana lalata waɗannan mutanen kamar ya fashe jikinsu da gaske. AT: "Yana rushe manyan mutane" ko "Yana halakar da manyan mutane"
Ba ya buƙatar bincika abin da suka yi domin ya riga ya san komai game da su. AT: "ba tare da buƙatar yin ƙarin bincike ba, domin ya riga ya san hanyoyinsu"
Wannan yana nuna cewa ya nada wasu mutane ne don su yi mulki a matsayinsu. AT: "kuma ya zaɓi wasu mutane don yin mulki a wuraren su"
Wannan magana tana kwatanta hanyar da waɗannan mutane suke mutu akan yadda masu laifi ke mutuwa. AT: "Yana kashe su saboda mugayen ayyukansu, a gaban sauran mutane kamar dai su masu laifi ne"
Wannan karin magana ne. AT: "A wani wuri da kowa zai iya gani"
Wannan yana magana ne game da Allah yana kashe waɗannan mutanen, ko da yake bai kashe su da takobi kansa ba. Yana iya sa wani ya kashe su ko wata masifa ta same su. AT: "yana sa su mutu"
Wannan yana nufin umarnin Allah ne game da yadda mutane yakamata suyi.
Ana iya bayyana kalmar "kuka" azaman fi'ili. Wannan yana magana game da Allah yana jin kukansu kamar dai kukan wani mutum ne da ya zo gareshi. AT: "sun sa talakawa suna kuka, Allah kuma ya ji su"
Elihu yayi amfani da wannan tambayar don koyar da Ayuba. Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Babu wanda zai iya kushe Allah idan ya yanke hukuncin yin shuru"
Elihu yayi amfani da wannan tambayar don koyar da Ayuba. Ana iya rubuta wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ba wanda zai iya zuwa ya gan shi idan ya yanke shawarar ɓoye fuskarsa"
Anan don "gani" yana nufin sani. AT: "koya mani abin da na yi kuskure wanda ban sani ba"
"Tunda baka son abin da Allah yayi, shin kana tunanin cewa Allah zai hore hukuncin wannan mutumin?" Elihu yayi amfani da wannan tambayar don a jaddada cewa bai kamata ya yi tunanin cewa Allah ba zai azabtar da wannan mutumin ba. Ana iya rubuta wannan azaman sanarwa. AT: "Duk da cewa ba ku son abin da Allah yake yi, tabbas ba ma tsammanin cewa Allah zai azabtar da wannan mutumin"
Wane ne ya ji ni
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Idan da za mu shigar da Ayuba a gaban shari'a"
Wannan karin magana ne. AT: "ku saurari karar shi sosai" ko "don jin cikakkun bayanai game da shari'ar sa"
"yadda ya yi magana kamar mugu"
Wannan yana nufin yin tawaye ga Allah. AT: "yana ƙara tawaye ga Allah"
A cikin wannan zargi, wannan yana nuna cewa Ayuba ya ɗora hannuwansa don ƙarfafa ba'a da Allah. AT: "ya tafa hannuwansa yayin da yake yi wa Allah ba'a tsakaninmu" ko "yana yi wa Allah ba'a gabanmu"
Elihu ya yi maganar “kalmomi” kamar dai su kayayyaki ne, da kuma faɗin kalmomi da yawa kamar dai suna ɗaukar waɗannan abubuwan ne a ɗayan ɗayan. AT: "yana magana da yawa kalmomi a kan Allah"
1Bugu da ƙari Elihu ya ƙara cewa,2"Kana tunanin hakan dai-dai ne a lokacin da kayi magana, 'Hakina a gaban Allah'?3Domin kayi tambaya, cewa wanne amfani yake da shi a gare ni?' kuma 'Ashe bai fi ba in da a ce nayi zunubi?'4Zan amsa maka kai da abokanka.5Ka dubi rana a sama, ka gan ta; ka dubi sararin sama wanda ya fi ka tsayi.6In ka yi zunubi a ina ka sa Allah ya ji zafi? In laifofinka su jeru zuwa sama, me zaka yi masa?7In kana da adalci me zaka iya bashi? Me zai karɓa daga hanunka?8Aikin muguntarka na iya cutar da mutum, kamar yadda kake mutum, aikin adalcinka kuma na iya amfanar wani ɗan mutum.9Sabo da ayyukana na tsanantawa, mutane suka yi kuka; suka nemi taimako daga damatsan ƙarfafan mutane.10Amma ba wanda yace ina Allah mahallicina, wanda ke bada waƙoƙi da dare,11wanda ke koyar damu fiye da yadda yake koyar da dabbobin duniya, wanda kuma yasa muka fi tsuntsayen sararin sama hikima?'12Suka yi kuka a can amma Allah bai amsa ba saboda girman kan miyagun mutane.13Hakika Allah ba zai ji kuka na wawanci ba, maɗaukaki ba zai saurare shi ba.14Yaya kuma zai ƙi amsa maka in ka ce baka ganinsa, cewa kuma ƙararka na gabansa, da kuma cewa kana jiransa!15Yanzu kuma kuka ce fushinsa baya yin hukunci, kuma baya ko ɗan kula da laifofi.16To Ayuba ya buɗe bakinsa domin kawai ya faɗi maganar; ya jera kalmomi ba tare kuma da sani ba."
"Kana ganin ya dace ka ce"
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) Ayuba yana da'awar mara laifi ne a gaban Allah ko 2) Ayuba yana da'awar cewa shi, maimakon Allah, dai-dai ne.
Elihu ya kwaso Ayuba yana faɗi waɗannan tambayoyin guda biyu. AT: "Gama kuna cewa, 'Ba ya amfanar da ni' da kuma, 'Ba ni da mafificiya fiye da idan na yi zunubi.' "
Elihu ya ci gaba da magana
Elihu ya yi wannan tambayar don ƙarfafa cewa zunuban Ayuba ba za su iya yin wani abu ga Allah ba. AT: "Idan kun yi zunubi, ba ku yi wa Allah wani lahani ba."
Elihu ya yi maganar “keta haddi” kamar dai su abubuwa ne, da kuma yin laifofin da yawa kamar dai suna ɗaukar waɗancan abubuwan ne a saman ɗayan. Ya yi wannan tambayar ne domin ya jaddada cewa Ayuba bai yi wa Allah komai ta wurin laifofinsa ba. AT: "Idan kun yi laifi mai yawa, har yanzu ba ku yi masa komai ba.
Tambayoyin guda biyu suna magana iri ɗaya daidai ne, cewa adalcin Ayuba bai ƙara komai ga Allah ba. AT: "Idan kai adali ne, wannan ba ya ba ka damar ba shi komai, kuma babu wani abin da zai karɓa daga hannunka."
"wani mutum"
Anan "makamai" yana nufin ƙarfi. AT: "Suna kira wani ya cece su daga ikon jarumawa"
Elihu yayi magana akan Allah na baiwa mutane damar samun bege a cikin mawuyacin hali, kamar dai yana basu wasu wakoki ne wadanda zasu iya raira daren.
"Mutanen da ake zalunta suna kuka"
Tun da Allah ba zai ji addu'ar masu girman kai ba, mugayen mutane, wataƙila ma zai iya sauraron Ayuba, wanda yake gunaguni a kansa. AT: "Don haka lalle shi ba zai amsa muku ba ... cewa kuna jiransa!"
"kuna jiran shi ya amsa"
Elihu ya yi maganar “kalmomi” kamar dai su kayayyaki ne, da kuma faɗin kalmomi da yawa kamar dai suna ɗaukar waɗannan abubuwan ne a ɗayan ɗayan. AT: "yana magana da kalmomi da yawa ba tare da sanin abin da yake faɗi ba"
1Elihu yaci gaba ya ce,2Bani dama in yi magana 'yar kaɗan, zan kuma nuna maka wani abu domin ina da ɗan sauran abin faɗi domin in kare Allah.3Zan sami fahimtata daga can nesa; Zan yi la'akari da adalcin da ke na Mahallicina.4Domin hakika kalmomina baza su zama ƙarya ba; wani wanda yayi girma cikin sanina tare da kai.5Duba Allah mai iko ne, kuma baya rena kowa; yana da ƙarfi cikin ikon fahimta.6Baya kiyaye rayukan miyagun mutane, amma a memakon haka ya kan yi abin da ke dai-dai ga waɗanda ke shan wahala.7Baya kawar da idanunsa daga adalan mutane amma yakan ɗora su a kursayi kamar sarakuna har abada, kuma sun ɗaukaka sosai.8In an ɗaure su da sarƙoƙi da karkiya ta wahala,9to sai ya baiyana musu abin da suka yi, da laifofinsu da girman kansu.10Hakannan ya buɗe kunnuwansu ga umarnansa, da dokokinsa ya kuma gargaɗe su da su juyo daga aikata laifofi.11In sun saurare shi sun kuma yi masa sujada, zasu yi kwanakinsu cikin wadata, shekarunsu kuma cikin wadar zuci.12Duk da haka, in basu saurare shi ba, zasu hallaka ta wurin takobi; zasu mutu saboda basu da sani.13Marasa tsoron Allah a zuciya na ajiye wa kansu fushi; basu yi kukan neman temako ba koma da a lokacin da Allah ya ɗaure su.14Sun mutu cikin ƙuruciyarsu; rayukansu sun kai ga ƙarshe a cikin ɗabi'ar karuwanci.15Allah na kuɓutar da waɗanda ake tsananta wa, ya buɗe kunnuwansu ta wurin tsananinsu.16Hakika zai so ya jawo ka daga cikin tsanani zuwa wuri inda ba ƙunci, kuma inda za a shirya teburinka da abinci mai cike da kitse.17Amma ka cika da hukunci ga miyagun mutane; hukuncisu ne ke riƙe ka.18Kar ka yarda fushinka ya ruɗe ka ga yin zagi, ko kuwa girman fansa yasa ka ka kauce.19Ko wadatarka zata amfane ka, domin kada ka shiga damuwa, ko kuwa ƙarfinka zai taimake ka?20Kada kayi marmarin da zaka yi zunubi ga waɗansu, lokacin da a ka kama mutane a cikin wurarensu.21Ka lura domin kada ka koma ga yin zunubi saboda an gwada ka da tsanani domin kada kayi zunubi.22Duba Allah ya sami ɗaukaka cikin ikonsa, wane ne mai koyarwa kamarsa?23Wa ya taɓa bashi umarni game da tafarkinsa? Wane ne zai iya cewa da shi, ka aikata rashin adalci?24Tuna ka yabi ayyukansa, wanda mutane suka rera waƙarsu.25Dukkan mutane sun duba waɗannan ayyukan, amma daga nesa ne kawai suke ganin su.26Duba Allah nada girma, amma bamu fahimce shi sosai ba; yawan shekarunsa basu ƙidayuwa.27Domin ya jawo ɗigon ruwa wanda yasa ya zama ruwan sama daga taskarsa,28wanda giza-gizai ke sheƙowa daga sama cikin wadatuwar mutum.29Hakika ko akwai wanda zai iya fahimtar yawan faɗin yadda giza-gizai suke da kuma yadda tsawa take daga gare shi?30Duba ya shimfiɗa walƙiyarsa a kewaye da shi ya rufe sauyoyin teku.31A wannan hanya ya hukunta mutane kuma yana bada abinci a yalwace.32Ya cika hannuwansa da walƙiya har sai da ya umarce ta takai iyakarta.33Tsawarta takan gargaɗi hadari, dabbobima kan ji tana zuwa.
Elihu yayi magana game da bayyana wa Ayuba abubuwa kamar zai nuna wa Ayuba waɗannan abubuwan. AT: "Zan bayyana muku wasu abubuwa"
Elihu yayi maganar samun ilimi game da fannoni daban-daban kamar ana samun ilimin sa daga wurare masu nesa. AT: "Zan nuna muku babban ilimin na"
Anan ana iya fassara kalmar "adalci" tare da ma'ana. AT: "Mahaliccina mai adalci ne"
Kalmar "wani" tana nufin Elihu da kansa. Yayi maganar kasancewarsa mai ilimi kamar dai yadda ake zurfafa da ilimi ne. AT: "Ni, wanda nake tare da ku, ni masani ne sosai"
Kalmar "mai ƙarfi da ƙarfi" tana da sau biyu wanda ke nufin "da ƙarfi sosai." Elihu yayi magana da Allah game da fahimtar komai daidai kamar dai fahimin sa na da ƙarfi. AT: "yana da ƙarfi sosai a cikin fahimta" ko "yana fahimtar komai gaba ɗaya"
Elihu ya yi maganar Allah yana kiyaye mutanen kirki kamar dai Allah yana kallonsu da idanunsa, kuma Allah yana daina kare su kamar yana kawar da idanunsa daga gare su. AT: "Ba ya daina kare adalai"
Elihu ya yi maganar Allah yana ɗaukaka mutane masu adalci kamar dai Allah yana sa su hau kujerar mulki kamar yadda sarakuna suke yi.
Elihu yayi magana game da Allah yana girmama mutanen kirki kamar ya ɗaga su a kan tudu. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "ya kan daukaka su" ko "ya girmama su"
Anan kalmar "su" tana nufin mutanen kirki waɗanda Allah zai hore su idan suka yi zunubi. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Idan wani ya ɗaure su cikin sarƙoƙi" ko "Idan wani ya sanya su a ɗaurin kurkuku"
Elihu ya yi maganar mutumin da ya yi wahala kamar dai an tsinci mutumin da igiyoyin da ke jawo wahala. AT: "wani yana cutar da su"
Elihu yayi magana game da sa mutum ya saurara kamar wanda yake buɗe kunnen mutumin. AT: "Ya kan sa su saurare"
Elihu yayi maganar dakatar da aiki kamar dai yana juya baya ne. AT: "dakatar da aikata mugunta"
Kalmomin "kwanaki" da "shekaru" duka suna nufin rayuwar mutumin. AT: "za su yi rayuwarsu cikin wadata da wadatar zuci"
Elihu ya yi maganar mutum yana mutuwa da ƙarfi kamar wanda ya kashe su da takobi. AT: "za su mutu da mutuƙar tashin hankali"
Anan kalmar "zuciya" tana nufin tunani da motsin zuciyarmu. Kalmomin suna iya nuna cewa mutumin ya taurin kansa ya ƙi dogara da Allah. AT: "waɗanda suka ƙi dogara da Allah"
Anan "karuwai masu bautar gumaka" na nufin samarin da suka yi aiki a cikin bautar arna waɗanda suke yin fasikanci azaman ɓangarorin al'adunsu. Ma'anar mai yiwuwa ga wannan kalmar ita ce 1) marasa ibada ta mutu saboda halayensu marasa kyau ko 2) marasa ibada sun mutu cikin kunya da kunya.
Elihu yayi magana game da rayuwa ba tare da matsala ba kamar ana cikin sarari ne sosai inda babu wahala.
Nama da ke da kitse a ciki alama ce ta wadatar saboda dabbobi suna da lafiya da ƙoshinsu. AT: "mafi kyawun abincin"
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) "Allah yana yi maku horo kamar yadda zai hori miyagu" ko 2) "kun damu da hukuncin da mugu ya cancanci."
Wasu juyin Littafi Mai Tsarki suna fassara wannan da cewa "ku mai da hankali da cewa dukiyarku ba ta ruɗe ku."
Elihu ya yi waɗannan tambayoyin don bayyana cewa kuɗi da iko ba za su iya taimaka wa Ayuba ba idan ya yi rashin gaskiya. AT: "Dukiyarka ba za ta iya sa ka daina kasancewa cikin wahala ba, kuma duk ƙarfin da kake da shi ba zai iya taimaka maka ba."
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) cewa "mutane" suna nufin mutane gaba ɗaya kuma "yankewa a wurarensu" wani magana ne na zaluntar wasu ta hanyar fitar da su daga gidajensu. AT: "lokacin da mutane suka jawo wasu daga gidajensu" ko 2) cewa "mutane" wakilci al'ummai ne kuma "yankewa a wurinsu" wani misali ne ga halakar al'umma. AT: "lokacin da al'ummai za su lalace"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah na jarraba ku ta hanyar wahalar da ku"
Ma’anoni masu ma'ana sune 1) “Allah mai iko ne sosai” ko 2) “mutane suna ɗaukaka Allah saboda yana da iko”
Elihu ya yi wannan tambayar don jaddada cewa babu wanda yake malami kamar Allah. AT: "Babu wanda yake malami kamar sa." ko kuma “babu wanda ya koyar da kamarsa.”
Elihu ya yi wannan tambayar don jaddada cewa babu wanda ya taɓa koya wa Allah abin da zai yi. AT: "Babu wanda ya koya masa abin da ya kamata ya yi."
Elihu ya yi wannan tambayar don ƙarfafawa cewa babu wanda zai iya zargin Allah da laifin rashin adalci. AT: "Ba wanda zai ce masa, 'Kun yi rashin adalci.'"
Wannan yana nufin tsawon lokacin da Allah ya kasance. AT: "mutane ba za su iya sanin tsawon lokacin da ya rayu ba" ko kuma "mutane ba za su iya sanin shekarun sa ba"
Kalmar "jawo" na iya ma'ana "tsaftace" ko "tace". Elihu ya bayyana yadda Allah ya mai da maɓuɓɓugar ruwa, ko tururi, wanda ya zana ya zama ruwan sama. AT: "sai ya zama ruwan sama"
Ana iya fassara jumlar "yaduwar yadu" tare da jimlar magana. AT: "yadda giza-gizai suka watsa a sararin sama"
Elihu yayi magana game da sama kamar "bukka" wanda Allah yake zaune. AT: "daga sama, inda Allah yake zaune"
"Duba da kyau ka ga yadda yake shimfiɗawa"
Elihu ya yi magana game da zurfin zurfin teku kamar teku ne tsirrai, zurfinsa kuma tushen sa ne. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) koda yake walƙiya tana haifar da haske a sararin sama, ɓangarorin teku suna duhu. AT: "amma zurfin teku ya kasance duhu" ko
Elihu ya yi magana game da walƙiyar da hadari ke haddasawa kamar Allah yana riƙe walƙiya a hannunsa kuma yana jagorantar ta buge ta inda ya ga dama. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) cewa Allah yana riƙe da walƙiyar walƙiya a hannunsa don jefa su, ko 2) cewa Allah yana ɓoye ƙofofin walƙiya a cikin hannayensa har sai ya yi shirin amfani da su.
"ji cewa hadari yana zuwa"
1Hakika zuciyata ta firgita a kan wanan; an cire shi daga wurinsa.2Ku saurara, i ku saurari ƙarar muryarsa, ƙarar da ke fita daga bakinsa.3Ya fitar da ita waje a ƙarƙashin dukkan sararin sama, ya kuma aika da walƙiyarsa zuwa iyakokin duniya.4Sai wata murya tayi ruri a bayansa, yayi tsawa da muryar darajarsa; bai hana mariƙin walƙiya ba a lokacin da aka ji muryarsa.5Allah yayi tsawa mai ban mamaki da muryarsa; yayi manyan abubuwa da ba zamu iya bada da bayaninsu ba.6Domin yace da ƙanƙara, 'faɗo a duniya', haka nan ruwan sama shima ya sheƙo, 'Ya zama babbar mafitar ruwa.'7Ya dakatar da hanun kowa daga aiki, domin dukkan mutanen daya hallitta suga ayyukansa.8Sai dabbobi su gudu zuwa maɓoya su kuma zauna a kogonninsu.9Hadari yakan zo daga mazauninsa a kudu kuma sanyi ya tattaru daga iskar da ta warwatsu a arewa.10Ta wurin numfashin Allah a ka bayar da ƙanƙara; sai ruwa ya daskare kamar ƙarfe.11Hakika ya kan tarwatsa baƙin girgije da ikonsa; ya warwatsa walƙiyarsa a cikin giza-gizai.12Yakan sarrafa giza-gizai ta wurin bishewarsa, domin su yi duk abin da ya umarce su a sararin duniya.13Yasa duk wannan ya faru; waɗansu lokutan yana faruwa domin gyara, waɗansu lokutan domin ƙasarsa, waɗansu lokutan su zama ayyukan amintaccen alkawari.14Ayuba ka saurari wannan; ka dena kayi tunani kan al'amuran Allah masu girma.15Ko ka san yadda Allah ya shimfiɗa giza-gizai ya kuma sa walƙiya ta haskaka a cikin su16Ko ka fahimci tashin giza-gizai, da ayyukan ban mamaki na Allah, wanda ke da cikakken sani?17Ko ka fahimci yadda tufafinka suka zama da zafi lokacin da ƙasar ta tsaya saboda iska ta taso daga kudu?18Zaka iya shimfiɗa rana kamar yadda zai yi, wadda keda ƙarfi kamar madubi an kuma zuba shi kamar ƙarfe?19Koya mana abin da za mu ce da shi, domin ba zamu iya shimfiɗa gardamarmu bisa tsari ba saboda duhun tunaninmu.20Ko za a faɗa masa abin da naso yi masa magana? Ko mutum zai so a haɗiye shi?21Yanzu kuma mutane baza su iya duban rana ba lokacin da tayi zafi a sararin sama ba bayan iska ta wuce ta share giza-gizanta.22Daga cikin arewa ake samun wadatar zinariya-a sama Allah ya isa aji tsoronsa cikin daraja.23Ga mai iko dukka, ba zamu iya samunsa ba! Yana da girma cikin iko; baya ƙuntatawa adalci da cikakakken adalci.24Saboda haka mutane ke tsoronsa. Baya sauraron waɗanda ke da hikima a cikin tunaninsu."
Waɗannan kalmomin guda biyu suna ma'ana dai-dai da abu ɗaya kuma suna jaddada tsananin tsoron sa.
Elihu yayi magana game da zuciyarsa tana bugawa da ƙarfi kamar zai tsalle daga kirjinsa. AT: "yana motsawa daga inda yake" ko "ya buge da ƙarfi"
Waɗannan jumla guda biyu suna ma'ana daidai ne. Elihu yayi magana game da tsawar kamar dai muryar Allah ce.
Elihu yayi magana game da wurare masu nisa a duniya kamar dai iyakokin ƙasa ne. AT: "ko'ina a cikin duniya"
"yana ruri bayan walƙiya"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "lokacin da mutane suka ji muryarsa"
Anan kalmar "hannu" tana wakiltar mutum gaba ɗaya. AT: "Ya dakatar da kowane mutum"
Elihu yayi magana game da guguwar dake tahowa daga kudu kamar dai hadari yana da wurin da zai sauka har sai ya zo.
Elihu yayi magana game da iskar arewa mai sanyi kamar numfashin Allah. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Allah yana sa kankara"
Elihu ya gwada taurin kankara da taurin karfe. AT: "mai sanyi, mai ƙarfi kamar ƙarfe"
Elihu ya yi maganar Allah ya sa girgije mai ƙarfi ta cika da ruwa kamar dai danshi yana yin nauyi a cikin girgije. AT: "yana sa farin gizagizai cike da danshi"
Abinda ya “gyara” mutane ne. AT: "wani lokacin tana faruwa ne don gyara mutanensa"
Wannan yana nufin cewa ruwan sama ke kwararar ƙasa kuma yana sa ciyayi su yi girma. AT: "wani lokacin don shayar da ƙasa"
Ana nuna kalmar 'amincin' a matsayin "mai aminci" ko "da aminci". AT: "wani lokacin don aminci da alkawarinsa" ko kuma wani lokacin ya kasance da aminci ga mutanen sa "
Elihu ya yi wannan tambayar don ƙarfafa cewa Ayuba ba zai iya sanin wannan ba. AT: "Ba za ku iya fahimtar yadda Allah yake kafa giza-gizai ba, kuma ya sanya walƙiya walƙiyar a cikin su." (Duba: fig_rquestion)
"Yana iko da girgije" ko "yana sa girgije sun yi masa biyayya"
Elihu ya yi wannan tambayar don ƙarfafa cewa Ayuba bai san waɗannan abubuwan ba. AT: "Ba kwa fahimtar yadda girgije ya ke, abubuwan al'ajibi na Allah, wanda ya kasance cikakken sani."
"yadda kuke zama kuke zafi a tufafinku" ko "yadda kuke shaƙa cikin tufafinku"
AT: "saboda iska mai ƙarfi, busasshiyar iska da ke shigowa daga kudu"
Elihu ya yi wannan tambayar don ƙarfafa cewa Ayuba ba zai iya yin wannan ba. AT: "Ba za ku iya shimfiɗa sama ba ... madubi na ƙarfe." (Duba: rquestion)
A cikin zamanin Littafi Mai Tsarki, an yi madubai da karfe. Elihu ya yi maganar sararin sama ba da ruwan sama kamar da bakin karfe mai ƙarfi.
Anan kalmomin "mu" da "mu" suna nufin Elihu, Elifaz, Bildad, da Zofar, amma ba Ayuba ba.
Elihu yayi magana game da rashin fahimta kamar dai yana da duhu a cikin zuciyar mutum. AT: "saboda ba mu fahimta"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Shin in sami wani ne ya gaya masa"
Elihu yayi magana akan mutum ya lalace kamar wanda aka haɗiye shi. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "domin Allah ya hallaka shi"
Kalmar "mai firgita" yana nufin cewa yana haifar da tsoro. Elihu yayi magana game da ɗaukakar Allah kamar dai abin da ya dogara ne ga Allah. AT: "Daukakar Allah tana sa mutane su ji tsoro"
Ma’anoni masu ma’ana su ne 1) “ba za mu iya kusanta shi ba” ko 2) wannan magana ne da Elihu ya yi maganar mutum bai iya fahimtar Allah cikakke kamar ba zai iya samun Allah ba. AT: "ba za mu iya fahimta da shi ba"
Anan "zukatan" suna wakiltar tunanin mutumin. AT: "waɗanda ke da hikima a cikin tunaninsu" ko "waɗanda ke ɗaukar kansu masu hikima" (Duba:
1Sai Yahweh ya kira Ayuba ta cikin gawurtacciyar guguwa yace,2"Wane ne wannan da ke kawo duhu domin shirye shirye ta wurin kalmomin da ba ilimi?3Yanzu sai ka yi ɗammara kamar namiji domin zan tambaye ka, kuma dole ne ka ba ni amsa.4Ina ka ke sa'ad da na shimfiɗa ginshiƙan duniya? Faɗa mini, in kana da isarshiyar ganewa.5Wane ne ke aiyana inda iyakokinta? Faɗa mini, in ka sani. Wane ne ya miƙa fitaccen layi a kan ta?6A kan me a ka kafa ginshiƙanta? wane ne ya ɗora dutsen kan kusurwarta?7lokacin da taurarin asubahi suka rera waƙa tare kuma dukkan 'ya'yan Allah suka yi sowa domin farinciki?8Wane ne ya kulle tekuna da ƙofofi lokacin da suka tumbatsa, inda ta zama kamar tazo daga mahaifa-9lokacin da nayi giza-gizai su zama suturarta, kuma baƙin duhu ya zama babbar iyakokinta?10Cewa lokacin da nasa alamomi a kan tekuna da kuma iyakokina,11da kuma lokacin dana sa kuryoyin ƙofofinta, lokacin kuma da nace da ita, 'Zaki iya zuwa daga wannan nisan, amma ba ci gaba; nan ne zan sa iyakoki ga wannan fahariyar ta raƙuman ruwanki.'12Ka taɓa ba da umarni ga safiya, ko ka sa faɗuwar rana ta san wurinta,13domin ta jira iyakokin duniya ta kuma kakkaɓe miyagu daga cikin ta?14An canja fasalin duniya kamar yadda yunɓu ke canjawa a ƙarƙashin hatimi; dukkan abubuwa sukan tsaya a kanta a sarari kamar gezar sutura.15Daga miyagu sai aka ɗauke haskensu; dantsensu da ya ɗaukaka sai aka kakkarya shi.16Ka taɓa zuwa maɓɓuɓɓugan ruwan tekuna? ka taɓa yin tafiya a wuri mafi zurfi?17Ko an taɓa nuna maka ƙofofin mutuwa, ka taɓa ganin ƙofofin inuwar mutuwa?18Ko ka fahimci duniya da duk cikarta? faɗa mini in ka san ta dukka.19Ina hanyar da haske ke bi domin hutawa-game da dare kuma ina nasa wurin?20Zaka iya yi wa haske da dare jagora zuwa wuraren aikinsu? Zaka iya samun hanya domin su bi su koma gidajensu!21Babu shakka ka sani, domin an haife ka a lokacin; shekarunka kuma suna da yawa!22Ka taɓa zuwa ma'ajiyar sino, ko ka taɓa ganin ma'ajiyar ƙanƙara,23waɗannan abubuwan da na adana na tsawon lokaci saboda masifa, domin ranar hargitsi da yaƙe-yaƙe?24Ina ne sashen da walƙiya ke warwatsuwa ko kuma inda ake warwatsa iska daga gabas akan duniya?25Wane ne ya yi kwazazzaban da ruwan damina ke bi, ko kuma wane ne ya yi wa aradu hanya,26yasa tayi ruwa a bisa ƙasa inda ba wani mutum da ke wurin, da kuma jeji, inda ba kowa,27don ƙosar da yasassun wurare ya kuma sa ciyayi su firfito?28Ko ruwan sama yana da uba, ko kuma wane ne ya zama uba ga raɓa?29Daga mahaifar wa ƙanƙara ke zuwa? Wane ne ya kafa daɓen hasken sararin sama?30Ruwaye kan ɓoye kansu su zama kamar dutse; cikin zurfafa kuma ya zama daskararru31Zaka iya kafa sarƙoƙi kan taurari na musamman ko ka datse sarƙar Oriyon?32Za ka iya yiwa dandazon taurari jagora su baiyana a lokutan da suka dace? Zaka iya yi wa damisa da 'ya'yanta jagora?33Ko ka san sharruɗan sararin sama? Zaka iya saita wurin da sararin sama ke mulki a kan duniya?34Zaka iya tada murya har zuwa cikin giza-gizai, domin ruwa mai yawa ya rufe ka?35Zaka iya aika cincirindon walƙiya domin su fita, domin suce da kai, ga mu nan'?36Wane ne ya bayar da hikima a cikin giza-gizai ko kuma ya bada fahimta ga masu tatsuniya?37Wane ne zai iya ƙirga giza-gizai ta wurin fasaharsa? Wane ne zai iya kwararo ruwan sararin sama,38lokacin da ƙura ta murtuke ƙasa kuma ta murtuke tare?39Zaka iya kamo abin da zakanya zata ci? ko kuma ka iya ƙosar da marmarin 'ya'yan zaki,40lokacin da suke kuyakuyai a cikin kogonninsu suke kuma cikin inuwa a ɓoye suna fako?41Wake bada kamammu ga hankaki lokacin da ƙananansu suka yi kuka ga Allah suka kuma yi yako saboda ƙarancin abinci?
"ya amsa Ayuba" ko "ya amsa wa Ayuba"
"daga guguwa mai karfi"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya ƙarfafa cewa Ayuba yayi magana akan abubuwan da bai sani ba. Ana iya fassara shi azaman wata sanarwa. AT: "Kuna kawo duhu ga shirye-shiryena ta hanyar kalmomi ba tare da ilimi ba."
"Wane ne ku kawo"
"ta hanyar faɗi abin da ba ku sani ba"
"ɗaure mayafinka kamar yadda mutum." Maza suna ɗaure rigunansu a ɗamararmu don ƙafafunsu su iya motsawa da yardar kaina yayin da suke yin babban aiki. Karin magana kalmar ''ɗaure ɗamararku kamar mutum" na nufin samun shirye don yin wani abu wanda ya haɗa da aiki kamar aiki, gasa, ko yaƙi. Ayuba ya shirya don wahalar amsa Allah. AT: "shirya kanka don yin aiki tuƙuru"
Yahweh ya fara ƙalubalanci Ayuba da jerin tambayoyin da suka nanata cewa ya halicci duniya kuma Ayuba bai yi ba.
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Ku faɗi inda kuka kasance lokacin da na sa harsashin ƙasa, idan kuna da fahimta sosai"
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Ku gaya mani wanda ya ƙididdige girmansa, in kun sani"
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Ku gaya mini wanda ya shimfiɗa layin muni."
igiya ko igiya da mutane ke amfani da ita don yin wani abu daidai girman da siffar
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "A kan me aka kafa tushenta?" ko "Ku gaya mani abin da aka sa harsashin ginin."
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Ku gaya mini wanda ya sa dutsen gini"
An yi magana da taurari na asuba suna waka kamar mutane. Ma'anar mai yiwuwa ita ce: 1) “taurarin asuba” iri ɗaya ne da '''ya'yan Allah” a layin gaba ko 2) “taurari na safe” suna nufin taurari a sararin sama.
"taurari masu haske waɗanda suke hasala da safe"
Wannan yana nufin mala'iku, halittu na sama. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Ayuba 1: 6.
Yahweh ya kamanta hanyar da ya hana teku ta rufe duk duniya har ta rufe shi da ƙofofin. AT: "ya hana ruwa ya cika ambaliyar ƙasar"
Yahweh ya kamanta halittar ruwan teku da haihuwa.
Ana iya fassara wannan azaman umarni. AT: "Ku gaya mini wanda ya rufe ... lokacin da na yi giza-gizai ... da kuma duhu duhu gaɓoɓinsa mara nauyi."
dogayen kayan wanki da mutane ke amfani da shi don sanyawa yaro bayan ta haihu
"Na yi iyaka ga teku"
"lokacin da na ce ga teku." Yahweh yana magana da teku kamar mutum.
Kalmomin "wannan har zuwa" yana nufin kawai har zuwa iyakar da Yahweh ya kafa. AT: "Za ku iya zuwa iyakar wannan iyaka, amma ba wani nisan da ke nesa"
Yahweh ya bayyana safe da ikon karɓar umarni da sanin abubuwa kamar mutum.
"sanya alfijir ya san inda yake"
hasken rana da ke bayyana a sararin samaniya kafin rana ta fito
Ana maganar hasken alfijir kamar yana kama da cikar duniya. AT: "ku fahimci iyakar duniya"
An nuna hoton hasken rana kamar yana haifar da mugayen mutane barin kamar girgiza wani abu don cire abubuwan da ba'a so. AT: "ka kori mugayen mutane daga duniya"
A cikin dare, mutane ba za su iya gani a sarari ba, amma da safe haske yana bayyana bambancin kowane abu, kamar hatimi na keɓance launuka dabandaban a cikin yumbu.
Anan "shi" yana nufin duniya. Wannan magana tana da ma'ana iri ɗaya ga jumlar farko a cikin wannan ayar.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Washegari tana dauke da 'hasken' mugayen mutane"
Mugaye suna ɗaukar duhu kamar haskensu, Domin suna aikata mugayen ayyukansu a cikin duhu, kuma sun san duhu sosai.
Hannun mugu ya tashe shi, yana nuna ikonsu da niyyar aikata mugunta, amma mugaye sukan daina aikata mugayen lokacin da hasken safiya ya zo.
Yahweh yayi amfani da tambayoyi guda biyar ya jaddada cewa ya fahimci duniya da tekuna kuma Ayuba bai fahimta ba.
Ana iya bayyana wannan azaman sanarwa. AT: "Ba ku taɓa zuwa hanyoyin ruwan teku ba."
Ana iya bayyana wannan azaman sanarwa. AT: "Ba ku taɓa tafiya a ƙasan mafi ƙasƙanci ba."
"marmaro"
Wannan yana nufin teku inda ruwan yake zurfi. AT: "zurfin teku" ko "zurfin teku" ko "zurfin ruwa"
Ana maganar mutuwa kamar dai birni ne wanda yake da ƙofofin da mutane suke shiga ciki. Wannan za a iya bayyana a cikin tsari mai aiki. AT: "Shin wani ya nuna maku ƙofofin mutuwa"
Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Ayuba 3: 5.
Ana iya bayyana wannan azaman sanarwa. AT: "Ba kwa fahimtar duniya a sararin samaniyarta."
"manyan wurare a duniya"
"idan kun san duk waɗannan abubuwan"
Yahweh yana amfani da tambayoyi uku don ƙarfafa cewa ya fahimci haske da duhu kuma Ayuba bai fahimta ba.
Ana iya bayyana wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Ba ku san hanyar zuwa wurin hutuwar haske ko wurin duhu ba."
"mazaunin haske." Ana maganar haske kamar samun wurin hutawa inda yake fitowa kowace rana.
"hasken rana"
Waɗannan tambayoyin suna tsammanin amsawa mara kyau ce. Ana iya bayyana su azaman sanarwa. AT: "Ba za ku iya jagoranci haske da duhu zuwa wuraren aikinsu ba, ko kuma neman hanyar komawa gidajensu saboda su."
"Zuwa yankinsu." Ana maganar haske da duhu kamar yadda ake fitar da su gaba da baya kowace rana don cim ma nufin Allah.
Yahweh yana amfani da ba'a ne don ya ƙarfafa cewa Ayuba bai fahimci haske da duhu ba. AT: "A bayyane yake cewa ba ku sani ba, domin ba a haife ku ba lokacin da na halicce su, kuma baku tsufa ba"
"domin kun riga kun kasance a lokacin." Kalmar "to" tana nufin lokacin da aka kirkira haske da rabuwa da duhu. AT: "don an haife ku lokacin dana ƙirƙira su"
"kun rayu shekaru da yawa"
Yahweh yayi amfani da tambaya don jaddada cewa yana mulkin duniyar zahiri kuma Ayuba bai yi ba.
Ana nuna hoton sino da ƙanƙara kamar yadda Yahweh ya tanada don yin nufinsa.
kwallayen kankara (galibi karami) waɗanda wani lokacin kan fado daga sama yayin hadari
Tambayar wacce ta fara da kalmomin "Kun shiga" a aya ta 22 ya ƙare anan. "Ba ku taɓa shiga cikin ɗakunan ajiya na dusar ƙanƙara ba, kuma ba ku taɓa ganin wuraren adana kayan ƙanƙara ba, waɗannan abubuwan da na kiyaye ... da yaƙi."
Kalmomin "waɗannan abubuwan" suna nufin sino da ƙanƙara (aya 22).
Ana iya bayyana waɗannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Ta wace hanya zuwa ina rarraba makarar walƙiya ko kuma zuwa inda na watsa iska daga gabas akan duniya?"
"iskokin suna hurawa"
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Na ƙirƙiri tashoshi don ambaliyar ruwan sama"
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "kuma ni ne kawai nayi hanyar tsawa"
"inda babu mutane"
"ɓata da ɓata." Waɗannan kalmomin guda biyu suna da kusan ma'ana iri ɗaya kuma suna jaddada yanayin lalacewa da wofin waɗannan yankuna.
"a gyara kasa sabon ciyawa"
Yahweh ya fara jerin tambayoyi huɗu don nuna wa Ayuba cewa ya yi ruwan sama, raɓa, kankara, da sanyi kuma Ayuba bai yi ba. Ana maganar ruwan sama, raɓa, kankara, da sanyi kamar ana iya haifan su kamar mutane.
Waɗannan ana iya fassara su azaman sanarwa. AT: "Ku gaya mani waye mahaifin ruwan sama, kuma ku faɗa mani wanda ya zama mahaifin saukowar raɓa."
Waɗannan ana iya fassara su azaman sanarwa. AT: "Ku gaya mani wanda mahaifin kankara ya fito? Gaya mani wanda ya haifi farin dusar daga sama."
An yi magana da taurin kankara kamar dutse. AT: "ku yi ƙarfi kamar dutse"
Yahweh yana amfani da tambayoyi guda biyar don ƙarfafa wa Ayuba cewa yana mulkin sama kuma Ayuba bai yi ba.
Wadannan ana iya fassara su azaman sanarwa. AT: "Ba za ku iya ɗaure sarƙoƙi ba a cikin Pleiades, kuma ba ku iya kwance igiyoyin Oriyon ba."
Waɗannan sune sunayen taurari. Duba yadda zaka fassara su a cikin Ayuba 9: 9.
Za a iya fassara su azaman kalamai. AT: "Ba za ku iya jagorancin taurari ba ... lokacin da ya dace. Ba za ku iya jagorar ... yara ba."
kungiyoyin na taurari waɗanda suke yi kama da suna da nau'i ɗaya a sararin sama
Yahweh yana amfani da tambayoyi guda biyu don ƙarfafa wa Ayuba cewa yana mulkin girgije da ruwa, kuma Ayuba bai yi ba.
Wadannan ana iya fassara su azaman kalamai. AT: "Ba za ku iya tashe ... mai yiwuwa ya rufe ku ba."
Wadannan ana iya fassara su azaman kalamai. AT: "Ba za ku iya aiko muku, 'Ga mu nan!' "
Ana magana da walƙiyar walƙiya kamar yadda bayin suka ce suna shirye don bin umarni.
Yahweh yana amfani da tambayoyi uku don jaddada wa Ayuba cewa yana mulkin girgije da ruwan sama kuma Ayuba bai yi ba.
Wadannan tambayoyin ana iya fassara su azaman kalamai. AT: "Ni ne wanda ya ba da hikima a cikin gajimare kuma ya ba da fahimta ga ma'anar."
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Ni ne wanda zai iya fitar da fatun sama."
Ruwan sama yana sa datti mai datti ya kasance tare kamar yanki guda ɗaya. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "lokacin da ruwan sama ya sanya datti ta zama mawuyacin hali"
Yahweh yana amfani da wata tambaya don ƙarfafa cewa ya san yadda ake ciyar da zakuna kuma Ayuba bai yi ba.
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Ka sani cewa ba zaku iya farautar wanda aka azabtar da shi ba don zaki ko gamsar da ƙoshin 'ya'yan sa"
Tambayar wacce ta fara da kalmomin "Shin kuna iya farauta" a cikin aya ta 39 ta kare anan. Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Kun san cewa ba zaku iya farauta ba ... lokacin da suke makara ... don yin kwanto."
A "kogo" shi ne wurin da zakuna ke zaune.
Zakuna sun ɓuya a cikin ciyayi lokacin farauta.
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Ku gaya mini wanda ke ba da waɗanda ke fama ... saboda ƙarancin abinci."
"yana samar da abinci." Wannan yana nufin dabbobin da hankaka suke nema kuma zasu iya ci.
manyan tsuntsaye masu fuka-fukai baƙaƙƙen fata waɗanda ke ciyar da dabbobi da suka mutu
1Ko ka san lokacin da awakin jeji ke renon ƙananansu a cikin duwatsu? Zaka iya jira lokacin da kishimai ke maza?2Zaka iya ƙirga watannin da suke kammala ɗaukan ciki? Ka san lokacin da suke renon 'ya'yansu?3Sukan durƙusa su haifi 'ya'yansu, daga nan su gama zafin naƙudarsu.4'Ya'yansu kan yi ƙarfi su yi girma a cikin saura, sai su tafi ba su kuma ƙara dawowa.5Wane ne ke 'yantar da jakin jeji? wane ne ke kwance dabaibayin jaki,6gidan wa na yi a Arabah, gidansa a ƙasa mai gishiri.7Sai ya yi dariyar reni ga hayaniyar cikin birni; ba ya jin tsawar mai tuƙi.8Ya yi ta gararanba a kan duwatsu a matsayin makiyayarsa; a can ya yi ta neman koren tsiron da zai ci.9Ko takarkarin jeji zai yi murna ya bauta maka? Ko zai so ya tsaya a wurin kwaminka?10Za ka iya riƙe jakin jeji da igiya lokacin da ya fusata? Za ka iya baje kwarurruka a lokacin da ya rarake ka?11Ka iya amincewa da shi domin yana da ƙarfi sosai? Zaka iya bar masa aikinka yayi maka?12Zaka iya dogara gare shi domin ya kawo maka hatsinka gida, ya tattara hatsi domin masussukarka?13Fukafukan jimina na da faɗi sosai, to amma ko dogayen gashin fuka-fukan da kuma ƙananan gasusuwan zasu iya kare ta?14Domin ta kan bar ƙwaiƙwayenta a ƙasa, ta kan barsu su sha ɗumi a cikin ƙura,15takan manta cewa sawaye zasu iya farfasa su ko kuma dabbobin jeji su tattake su.16Takan azabtar da 'ya'yanta kamar ba ita ta haife su ba; bata jin tsoro kada naƙudarta ta zama a banza,17domin Allah bai bata hikima ba kuma bai bata wani fahimta ba.18Lokacin da take gudu takan yi dariyar wulaƙanci ga doki da kuma mahayin dokin.19Ka ba doki ƙarfinsa ne? kai ne ka yiwa wuyansa ado da dogon gashi mai sheƙi?20Ka taɓa sa shi ya yi tsalle kamar bãbe? Girman haniniyarsa abin tsoro ne.21Yana haniniya da ƙarfi, yana kuma murna da ƙarfinsa; yakan fita domin ya tunkari makamai.22Ya kan rena tsoro kuma baya alhini; baya kafcewa takobi.23Kwari da bãka na hararsa, tare da sheƙin mãshi da dogon ƙarfe mai tsini.24Yana haɗiye ƙasa cikin ƙarfi ya murtuke ta a lokacin da ya ji ƙarar ƙaho, baya tsayuwa wuri ɗaya.25Duk lokacin da ya ji ƙarar ƙaho, yakan ce, Aha! Ya kan sunsini yaƙi daga nesa-ƙara mai ƙarfi da ihun kwamandoji da hayaniyarsu.26Ta wurin hikimarka ne shaho ke miƙar da fuka-fukansa ya fuskanci kudu da su?27Ko ta wurin umarninka ne gaggafa ke yin sheƙarta a can ƙonƙoli?28Yakan zauna a can ƙonƙolin itace yakan yi sheƙarsa a reɗimar rassa, ya zama mafakarsa.29Daga can yake duban abincinsa idanunsa na hangen su daga can nesa, hakanan30'Ya'yanta kan sha jini a inda aka karkashe mutane, a can yake.
Yahweh yana amfani da tambayoyi guda huɗu don nuna cewa ya fi Ayuba girma domin Yahweh yana lura da awaki da dabbar daji da Ayuba ba ya kula da su.
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Lallai ba ku san lokacin da ... ɗiyansu ba."
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Ba ku da ikon sa ido don tabbatar da cewa komai ya tafi dai-dai lokacin da barewar ta haihuwar 'yayansu!" (Duba:
"haifi 'yayansu"
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Ba za ku iya kirga watannin da suke ciki ba."
Kalmar "su" tana nufin awaki da barewa.
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Gaskiya ba ku san lokacin da za su haihu ba."
Ma’anoni masu ma’ana su ne 1) azabar na su ya ƙare idan an gama haihuwa ko 2) “azabar naƙuda” wata magana ce da ke nuni ga zuriyar awaki da barewa domin su ne sakamakon aikin uwa da azaba. AT: "aika da zuriyarsu daga mahaifar su"
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Ni ne na saki jakin daji kyauta."
Waɗannan sunaye daban-daban don jaki ɗaya.
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Ni ne na buɗe ɗayan jakin sauri"
igiya, sarƙoƙi, ko madauri waɗanda suke riƙe dabba da kiyaye ta daga gudu
Yahweh ya bayyana jakin kamar dai shi mutum ne wanda yake da gida. "Na ba shi Arabah a matsayin wurin zama"
ƙasar kusa da Tekun Gishirin da ke da gishiri da yawa a ciki
Kalmar "Sai" tana nufin jakin jeji.
Yahweh ya bayyana jakin kamar dai shi mutum ne. Jakar ta yi dariya domin waɗanda ke cikin birni dole ne su ji amo, amma yana zaune a inda babu kowa.
Anan Yahweh yana amfani da tambayoyi guda huɗu don ƙarfafawa cewa Ayuba ba kamar Yahweh ba ne domin Ayuba ba zai iya sarrafa bijimin ba.
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin bayani. AT: "The sa dabbar ba za ta yi farin cikin bauta maka ba."
Ma'anar mai yiwuwa sune 1) wani nau'in sa da yake zaune a cikin daji ko 2) wani irin salo da yayi kama da shanu.
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin bayani. AT: "Ba zai yarda a zauna a cikin gidan dabbobi ba."
"zauna kusa da komin dabbobi cikin dare"
wani abu wanda yake riƙe abinci domin dabbobi su iya ci
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin bayani. AT: "Ba za ku iya sarrafa bijimi tare da igiya ba don yin huɗa a gonakinku."
Manoma zasu daure igiyoyi a kawunan dabbobi ko kuma wuyan wuyan dabbobi don su jagorance su.
Waɗannan tashoshi ne masu tsayi da yawa da aka yi cikin datti yayin huɗar ruwa. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Ayuba 31:38.
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin bayani. AT: "Ba zai taɓar kwarin kwarin kwabo kamar yadda ya biyo baya ba."
don santsi da rushe ƙasa
Anan Yahweh ya yi amfani da tambayoyi guda uku don ci gaba da gardamarsa cewa Ayuba ba kamar Yahweh ba ne domin Ayuba ba zai iya sarrafa bijimin ba.
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin bayani. AT: "Ba za ku iya amincewa da shi ba domin ƙarfinsa yana da yawa."
Kalmar "shi" tana nufin "takarkarin jeji."
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin bayani. AT: "Ba za ku iya sa shi ya yi muku aikinku ba."
"Ku sa shi ya yi muku aiki mai wahala"
Waɗannan kalmonin biyu suna ma'ana dai-dai ne. Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ba za ku iya dogaro da shi ba ... hatsi don masussukarku."
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya jaddada cewa Ayuba ba zai iya yin bayani game da dalilin ous ɗin yakan nuna yadda suke yi ba. AT: "Ba ku sani ba ko ɓarin da itacen jimina suna wakiltar ƙauna yayin da suke jujjuya fikafikansu."
babban tsuntsu wanda ke iya gudu da sauri amma ba zai iya tashi ba
dogon gashin tsuntsaye a fuka-fukan tsuntsaye
da kananan gashin fuka-fukai waɗanda suke rufe jikin tsuntsu
Kalmar Ibraniyanci ba shi da tabbas. Ma’anoni masu ma’ana sune 1) “amincin” ko 2) “mai kunshe. Sunan muryar yana ma'anar "mai aminci" ko "ƙaunataccen" saboda mutane sun san cewa storks suna kula da kajin nasu sosai.
Kalmar "ta" tana nufin mace jimina.
aikin da take yi yayin da ta ɗora ƙwai
Idan kajin suka mutu, duk aikinta ba shi da amfani. AT: "da ba shi da amfani idan kajin sun mutu"
Yahweh yana amfani da tambayoyi uku don jaddada cewa Ayuba ba kamar Yahweh ba ne domin Ayuba ba zai iya iko da dokin daji ba.
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ba ku taɓa ba dokin ƙarfinsa ba."
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ba za ku iya suturta da wuyan sa ba."
dogon gashi a saman wuyan doki
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ba ku da ikon sa shi ya yi tsalle kamar bãbe."
babban ciyawar ciyawa wacce zata iya tsalle sosai da sauri
Kalmar "Ya" yana nufin doki. Doki yana kashe kasa domin yana matukar farin cikin fara yaƙin. Watau fassarar: "Yana nainiya da farin ciki da"
"Ya tono a ƙasa tare da kofato"
Anan "makamai" suna wakiltar yakin da ake amfani dasu. AT: "don shiga yaƙi"
"Ba ya tsoron komai"
kwandon shara da ke riƙe da kibiyoyi
ya girgiza kuma ya yi amo
gefen doki
dogon sanda tare da kaifi mai kyau wanda mutane suke jefa abokan gabansu
Doki yana gudana a kasa da sauri har ƙasa ta wuce kamar ruwan da mutum ya sha. AT: "yana gudana da sauri sosai a kan ƙasa"
Doki yana da matukar farin ciki, saboda haka yana motsawa da sauri da ƙarfi.
Ana iya bayyana cewa wani ya busa ƙaho. AT: "idan mutum ya busa kakaki don sanarwa cewa an fara yaƙin"
"ya yi matukar farin ciki har ya tsaya"
Kalmar “Aha” sauti ne da mutane suke yi lokacin da suka gano wani abu. Doki yayi sauti saboda ya gano yakin.
Yahweh yana amfani da wannan tambayar don tabbatar da cewa Ayuba bai yi girma sosai kamar Yahweh ba. Amsar a bayyane ga wannan tambayar ita ce "a'a." AT: "Ba don hikimarku ba ne ... don kudu."
Anan shimfidar fikafikan sa yana nufin tashiwa. AT: "kwari zuwa kudu"
Yahweh yana amfani da wannan tambayar don tabbatar da cewa Ayuba ba shi da iko ya umurce gaggafa. Amsar a bayyane ga wannan tambayar ita ce "a'a." AT: "Ba ku da ikon umurce gaggafa don hawa sama da kuma gina mazauninsa a manyan wurarensa."
Ana iya bayyana sunan "umarni" a matsayin fili. AT: "saboda kuna faɗi haka ne"
Babban dutsen tsafin ƙauyuwa ne na gaggafa saboda dabbobin da za su so su ci ba zai iya kaiwa gare su ba.
Anan kalmar "ya" tana nufin gaggafa.
"ga dabbobi da zai iya kashe ya ci"
Anan "idanunsa" suna nufin gaggafa. AT: "yana ganinsu"
"Jariri gaggafa." Zai iya zama da taimako a faɗi cewa hakan na faruwa bayan gaggafa ya kashe da dabba. AT: "Bayan gaggafa ta kashe dabba, sai jariri gaggafa"
"sha jinin dabbar da ya kashe"
"inda akwai mutane da suka mutu." Wannan kalmar tana nufin gawawwakin da suke kwance a fili, ba gawarwakin da aka binne a ƙasa ba.
Ana iya bayyaninsa a fili cewa ya zo ya ci gawar. AT: "yana nan don cinye su"
1Yahweh yaci gaba da yiwa Ayuba magana cewa,2"Ko duk wani da ke ƙoƙarin ganin laifi zai iya ƙoƙarin yi wa Mafi iko dukka gyara? Shi wanda ke gardama da Allah sai ya amsa."3Sai Ayuba ya amsawa Yahweh cewa,4"'Duba ni da ban can-canta ba; yaya zan amsa maka? Na sa hanunna a kan bakina.5Sau ɗaya na yi magana, kuma ba zan amsa ba; hakika sau biyu ne, amma ba zan ci gaba da yi ba."6Sai Yahweh ya amsawa Ayuba daga cikin hadari yace,7"Yanzu sai ka yi wa kanka ɗammara kamar jarumi, domin zan tambaye ka tambayoyi, kuma dole ne ka amsa mini.8Ko hakika za ka ce ba ni da adalci, ko za ka hukunta ni domin ka nuna mini cewa ka yi dai-dai?9Ko kana da damatsa kamar na Allah? Ko za ka iya yin tsawa da murya kamar sa?10To ka yi wa kanka sutura cikin ɗaukaka da ƙima, ka yi wa kanka kwalliya da daraja.11Ka baje kewaye da fushinka, ka dubi kowanne mai fahariya ka ƙasƙantar da shi.12Ka duba duk mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake miyagu a inda suke tsayiwa.13Ka bisne su tare a ƙasa, ka kulle su a ɓoyayyen wuri,14Daga nan zan yi la'akari da kai da kuma sanin cewa hannunka na dama zai cece ka.15Yanzu ka duba dodon ruwa, lokacin da nayi a lokacin da na halice ka, yana cin ciyawa kamar takarkari,16Yanzu duba, ka ga yadda ƙarfinsa ke ƙirjinsa, ikonsa kuma yana cikin tumbinsa.17Ya mayar da bindinsa kamar sidar, haƙoransa a haɗe suke.18Ƙasusuwansa kamar cikin ƙarfe suke, ƙafafunsa kuma kamar makaran ƙarfe suke.19Shi ne sarki a cikin hallitar Allah. Allahn da ya yi shi ne kawai ke iya kayar da shi,20Domin tuddai ne ke ba shi abinci, sauran dabbobi kuma na kusa da wurin suna wasa a kusa.21Yana kwance can cikin lollokin ganyaye.22Ganyaye masu toho sun rufe shi da inuwarsu duhuwar itatuwa ta shinge shi. Duba23Idan rafi yayi ambaliya ba ya fIrgita, yana da ƙarfin hali ko da ruwan Yodan zai kawo masa iya bakinsa.24Ko wani zai iya kama shi da ashifta, ko ya iya huda hancinsa ta wurin yaudara?
Yahweh ya ci gaba da kalubalantar Ayuba.
Yahweh yana tsauta wa Ayuba. Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Babu wanda yake so ya zarge ni da ya yi ƙoƙarin yin jayayya da ni, gama ni Allah Maɗaukaki ne." ko "Kai, mutum, kana so ka soki ni, Allah Maɗaukaki, amma bai kamata ka yi ƙoƙarin gyara ni ba."
Yahweh yayi magana akan Ayuba da kanshi kamar wasu mutane biyu ne domin su tunatar da Ayuba cewa babu wani mutum a ko'ina da zaiyi jayayya da Allah. AT: "Kuna son jayayya da ni, saboda haka ku amsa mini"
Ayuba yayi amfani da wannan tambayar don neman afuwa don tambayar Allah. AT: "Ba zan iya amsa muku ba."
Mutumin da ya suturta mayafinsa a ƙarƙashin rigarsa ko abin ɗamara yana shirya don aiki mai wahala, kuma Ayuba ya shirya don wahalar amsa Allah. Duba yadda zaka fassara wannan a cikin Ayuba 38: 3.
Kalmar "a zahiri" tana nuna cewa Yahweh ya yi mamakin cewa Ayuba zai faɗi cewa Yahweh ba shi da gaskiya kuma Ayuba ya kamata ya tabbata cewa yana son ya faɗi hakan. Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Na yi mamakin cewa kuna faɗi cewa ni marar adalci ne." ko "Ya kamata ku tabbata kuna son faɗi cewa ni marar adalci ne, saboda abin da kuke faɗi kenan."
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Kuna la'anar ni saboda ku iya da'awar cewa ba ku da laifi."
Hannun magana ne don ƙarfin cikin hannu. AT: "ƙarfi kamar ƙarfin Allah"
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Tabbas ba za ku iya sa tsawa da muryar ku kamar yadda Allah yake yi da nasa ba."
"murya kamar yadda ya yi" ko "murya kamar muryarsa"
Kalmomin “ɗaukaka,” “daraja,” “girma”, da “girma” ana maganarsu kamar dai tufafi ne da mutum zai saka. AT: "ka ɗaukaka kanka; ka yi wani abu mai girma don mutane su girmama ka su girmama ka; sa mutane su ɗauka cewa kai sarki ne mai girma"
Kalmar "fushi" ana magana dashi kamar wani abu ne wanda yawanci za'a iya riƙe shi a cikin akwati, amma a wannan yanayin akwai abubuwa da yawa daga ciki wanda abin da bai dace ba yana buƙatar yadawa. Hakanan ishara ne ga ayyukan da mutum yakeyi idan yana fushi. Kuna iya buƙatar bayyana takamaiman dalilin da yasa mutumin yayi fushi. AT: "Yi fushi saboda mutane suna alfahari, kuma suna azabtar da su"
"dauke dukan abubuwan fahariyansa"
“Fuska” tana wakiltar mutum gaba ɗaya. AT: "su"
karin magana don wurin da ruhun mutane ke tafiya idan sun mutu
babban dabbar ruwa, wataƙila dorinan ruwa
dodon ruwa na ci
da dodon ruwan da takarkari na cin ciyawa
Waɗannan suna nufin akan jiki ne
Sidar wani itace ne mai karfi sosai
Anan, ƙasusuwansa suna kwatanta su da bututu da aka yi da tagulla don nuna yadda wannan dabba take.
Wannan kwatancen na ƙarshe ya bayyana ƙarfin wannan babban dabba.
"mafi mahimmancin halittu" ko "mafiya ƙarfi daga halittu"
Yahweh yana magana kamar wani mutum. AT: "na halittu. Ni kaɗai, Allah ne"
Ana maganar tuddai kamar suna mutanen da zasu iya ba shi abinci. AT: "abinci yana tsiro akan tuddai"
ciyawar tsire-tsire masu fure da ke iyo akan ruwa a cikin yankunan da ke dawamba
ciyayi masu tsayi da aka samo a cikin fadama
Wanna itatuwa sune manyan bishiyoyi waɗanda suke girma a cikin ƙasa mai bushe. Idan ba a san su ba a cikin al'adun ku, zaku iya amfani da janar na gaba ɗaya ga itatuwan da ke girma kusa da ruwa.
bangarorin kogin
"Ko da ambaliyar Kogin Yodan zata iya zuwa bakinsa"
Ana iya fassara wannan azaman sanarwa. AT: "Babu wanda zai iya kama shi da ƙugiya ko kuma ya tona hancinsa da mari."
1Ko za ka iya jawo Lebiyatan da ƙugiyar kamun kifi? za ka iya ɗaure wuyanta da sarƙa?2Za ka iya sa igiya a hancinta? ko ka iya huda cikin bakinta da ƙugiya? lokacin da ta ke yi maka gurnani3Ko za ta ji daɗinka? Ko za ta yi maka magana mai lumana?4Kuna da yarjejeniya da ita kan cewa ba za ka mai da ita baiwarka ba har abada?5ko za ka iya wasa da ita kamar yadda zaka yi da tsuntsu? Za ka iya ɗaure ta kamar bayinka mata?6Ko masunta zasu iya ƙulla wata yarjejeniya dominta? Ko zasu iya yin fataucinta a cikin fatake?7Za ka cika maɓoyarsa da ƙayayuwa, Ko kansa da mãsun kamun kifi?8Ka ɗora hanunka bisansa sau ɗaya tak daga nan za ka san yaƙi ba kuma za ka ƙara yinsa ba.9Duba duk mai begen yin hakan ƙarya yake yi; ba wanda za a jefa masa a gabansa da ba zai tattake ba.10Ba wanda zai iya tarar dorinar ruwa ba tare da ya furgita ba?11Wane ne ya fara ba ni wani abu domin in biya shi? Duk abin da ke ƙarƙashin sararin sama nawa ne.12Ba zan yi shiru ba game da ƙafafun dorinar ruwa, da kuma game da al'amarin ƙarfinta ba, ba kuma game da tagomashin hallitar da take da ita ba.13Wane ne zai iya yaye masa wannan lulluɓin na samansa? Wane ne zai iya ratsa garkuwoyinsa masu ninki biyu?14Wane ne zai iya buɗe ƙofofin fuskarsa-zagaye da haƙoransa masu banrazana?15bayansa an yi shi ne da garkuwoyi aka harhaɗa su wuri ɗaya, kamar da wata rufarfiyar alama.16Suna marmatse da juna domin kada iska ta iya ratsa su, suna harhaɗe da juna.17Suna manne da juna, domin kada a ɓamɓare su.18Haske na walƙatawa daga gurnaninsa; haskensa kamar na hasken fitowar rana.19Daga cikin bakinsa tartsatsin wuta na fita.20Daga cikin hancinsa kuma hayaƙi na fita kamar na matoyar tukunya da ta toyu ta yi zafi sosai.21Numfashinsa ne ke samar da gawayin wutar; wuta na fita daga bakinsa.22Wuyansa na da ƙarfi, masifa na rawa a gabansa.23Maɗaukan jikinsa a harhaɗe suke tare, suna kafe a jikinsa; baza su iya ciruwa ba.24Zuciyarsa na da ƙarfi kamar dutse, hakika tana da tauri kamar dutsen niƙa.25Sa'ad da ya miƙar da kansa tsaye alloli ma kan firgita saboda tsoro, sukan ja baya.26In takobi ya sare shi, ba ya yi masa komai- hakama mãsu da sauran makamai duk ba su yi masa komai.27Ya na ganin kibiya kamar rauga ce kawai, namijin ƙarfe kuma kamar abin da tsatsa ta riga ta cinye.28Kibiya ba ta sa shi gudu; a gare shi duwatsu masu sulɓi kamar ƙaiƙai suke.29Rundunoni kuma kamar tattakar ciyawa; ya kan yiwa walƙiyar kibiya dariya.30Ƙananan sassansa kamar rusarshiyar masana'antar tukwane ce, yakan bar wuri a damalmale kamar wurin da a ka yi kwaɓar fitar da zinariya da azurfa.31Ya kan haƙa wuri ya yi zurfi ya zama kamar tukunyar dafa ruwa; ya kan mayar da teku ta zama kamar tukunyar mai.32Ya kan sa haske ya haskaka bayansa; wani zai yi tunanin yadda zurfin suma mai furfura take.33A cikin duniya babu wanda ke dai-dai da shi, wanda aka yi shi ya zama da rashin tsoro.34Yana ganin duk wani abu da ke taƙama; shi sarki ne a kan dukan 'ya'yan masu taƙama.
Allah ya yi amfani da wannan tambayar don tunatar da Ayuba cewa Ayuba ba shi da iko kamar Lebiyatan. Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Kun san cewa ba za ku iya fitar da Lebiyatan tare da kamun kifi ba."
ja daga ruwan
Kalmar "za ka iya" an fahimta daga tambayar da ta gabata. Ana iya maimaita su anan. Allah ya yi amfani da wannan tambayar don tunatar da Ayuba cewa Ayuba ba shi da iko kamar Lebiyatan. Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ko za ku iya ɗaure muƙamuƙi da igiya?" ko "Kuma kun sani cewa ba zaku iya ɗaura mukamai da igiya ba."
Allah ya yi amfani da wannan tambayar don tunatar da Ayuba cewa Ayuba ba shi da iko kamar Lebiyatan. Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Kun san cewa ba za ku iya sanya igiya ba a cikin hancin Lebiyatan ... tare da ƙugiya."
Allah ya yi amfani da wannan tambayar don tunatar da Ayuba cewa Ayuba ba shi da iko kamar Lebiyatan. Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Kun dai san cewa ba zai yi muku afuwa ba."
Lebiyatan
Allah ya yi amfani da wannan tambayar don tunatar da Ayuba cewa Ayuba ba shi da iko kamar Lebiyatan. Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Kun san cewa ba zai yi muku magana mai laushi ba."
Yahweh ya ci gaba da tsawata wa Ayuba. Yayi amfani da tambayoyi don tunatar da Ayuba cewa Ayuba bashi da iko kamar Lebiyatan.
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ka sani cewa ba zai yi muku wani alkawari ba, ya kamata ku ɗauke shi ya zama bawa har abada."
Kalmomin "ku" da "ka" suna nufin Lebiyatan.
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Kun san cewa ba za ku iya wasa tare da shi kamar yadda za ku yi wasa da tsuntsu ba."
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ka sani ba za ku iya ɗaura shi a kan barorinku mata ba."
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ka sani cewa kungiyoyin masunta ba za su yi ciniki da shi ba."
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Kun san cewa ba za su raba shi har zuwa kasuwanci tsakanin masu ciniki ba."
"Kungiyoyin masunta za su rarrabu"
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin sanarwa. AT: "Ba zaku iya soki fatarsa da makaman farauta ba, kuma ba zaku iya soki kansa da mãsun kamun kifi ba."
Wannan fassarar za a iya fassara ta azaman bayani a cikin tsari mai aiki. AT: "Duk wanda ya dube shi zai firgita sosai har ya jefa kansa ƙasa."
"ta dubansa" ko "ta ganinsa"
Zai fi sauƙi a zuga Lebiyatan da tsayawa a gaban Yahweh. Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin wata sanarwa. AT: "Tun da kuka san cewa babu mutumin da ke da muni da ya isa ya tayar da Lebiyatan, tabbas ya kamata ku san cewa babu wanda zai iya tsayawa a gabana."
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin wata sanarwa. AT: "Kun san cewa babu wanda ya fara ba ni wani abu, don haka babu wani wanda nake buƙata in biya."
Wannan za a iya fassara azaman sanarwa tabbatacce. AT: "Tabbas zan yi magana game da ... da game ... da kuma game da"
Waɗannan abubuwa uku ne waɗanda Allah ba zai yi shuru ba.
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin wata sanarwa. AT: "Ba wanda zai iya suturta da mayafinsa."
Kalmar "makamai" wani magana ne na sikelin mai wuya ko ɓoye a bayansa. Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin wata sanarwa. AT: "Ba wanda zai iya shiga ainihin ɓoyewar ɓoyayyen nasa."
Ana iya fassara wannan tambaya a matsayin wata sanarwa. AT: "Babu wanda zai iya tsinkayar ja da baya ... tsoro."
Kalmar "garkuwa" magane ne na harhaɗa Lebiyatan. Dukansu garkuwa da garken Lebiyatan suna kiyaye lafiya kuma suna kare kibiyoyi da sauran makamai.
Wannan yana nufin "garkuwar" suna da kusanci da juna kuma babu abin da zai samu tsakanin su.
Wannan za a iya fassara shi a cikin aiki mai aiki. AT: "ba wanda zai iya raba su"
Wannan yana nuna cewa idanun sa sunyi ja kamar sanyin safiya yayi ja.
Allah ya faɗi irin wannan ra'ayin a cikin hanyoyi biyu mabambanta don ya jaddada bayyanar firgita na Lebiyatan. Kuna iya bayyana wannan ta ƙara kalmomin da aka tsallake. AT: "Daga bakinsa suna ci da ƙuna masu ƙuna, harshen wuta yana fitowa daga bakinsa"
Duk hayaki da tukunyar tafasa suna da zafi sosai.
Ana iya fassara kalmar "ta'addanci" azaman kalmar ar "ku ji tsoro". AT: "lokacin da mutane suka gan shi yana zuwa, suna tsoro sosai"
Wannan za a iya fassara shi a cikin aiki mai aiki. AT: "ba wanda zai iya motsa su"
Dutse ko dutse baya canzawa ya zama mai laushi. Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) Kirji na Lebiyatan da gabobin da ke ciki suna da rauni a jiki ko 2) Lebiyatan ba ya jin tsoron komai ko 3) Ana maganar Lebiyatan a matsayin mutumin da yake kashewa ba tare da yin nadama ba.
"mafi wuya daga kankara." Wannan dutsen shi ne mafi girma da wuya na dutsen guda biyu da ake amfani da nika hatsi. Zai iya zama dutsen mafi wuya mutane su samu.
Ma'anar mai yiwuwa ita ce 1) "mayaƙan mutane" ko 2) "mutane masu ƙarfi".
ya sare Lebiyatan
"Yana tunanin makaman da aka yi da baƙin ƙarfe kamar dai su ƙera ne da bambaro." Bishiyoyi ba za su shiga cikin harhadar sa ba, kuma makaman ƙarfe ba za su samu ta harhadar sa ba.
Kuna iya bayyana wannan ta ƙara kalmomin da aka tsallake. AT: "yana tunanin makaman da aka yi da tagulla kamar dai sune waɗanda keɓaɓɓun itace ne"
Ciyawa ba zai iya cutar da Lebiyatan ba, kuma duwatsu masu sulɓi ba ta da amfani kamar ciyawa.
Kulki da aka yi da ciyawa bazai cutar dashi ba, kuma kulki da aka yi da katako ba zai cutar dashi ba. Wannan za a iya fassara shi a cikin aiki mai aiki. AT: "Yana tunanin kulake kamar dai bambaro ne"
Mutumin da yake jefa mashin yana fatan cewa mashin zai kashe Lebiyatan, amma marubucin yayi magana kamar dai Lebiyatan ya san mashin ba zai kashe shi ba don haka ya bushe da dariya.
"Yayin da yake wucewa ta cikin ruwa, sai ya bar sahun kumfa a bayansa, kamar yadda ake fashewa da tafasasshen ruwa a cikin tukunya"
Man shafawa a cikin tukunya yana da hadari idan wani ya girgiza shi, kuma tekun ya cika da laima yayin da Lebiyatan zai iyo.
"Babu wani mai kama da Lebiyatan"
"Shi mai matukar girman kai ne"
Ana magana da Lebiyatan kamar mutum ne wanda zai iya zama sarki kuma ya yi fahariya. AT: "Lebiyatan yana da ƙarin dalilin yin fahariya fiye da kowa a duniya"
1Daga nan sai Ayuba ya amsawa Yahweh ya ce,2"Na sani zaka iya yin komai, kuma ba wani nufi naka da ba zai cika ba.3Wane ne wannan da ke ɓata shiri ba tare da ilimi ba? Hakika, na faɗi abubuwan da ban fahimta ba, abubuwan da ke da wahalar fahimta a gare ni, waɗanda ban sani ba.4Ka ce da ni, 'Yanzu ka saurara, zan yi magana; zan tambaye ka abubuwan da za ka faɗa mini'.5Na ji labarinka da jin kunnuwana, amma yanzu na ganka.6Domin haka na rena kaina ina hurwa cikin toka da ƙura.7Sai ya zamana bayan ya faɗi waɗannan maganganu ga Ayuba, sai Yahweh yace da Elifhas Batishmine, fushina yayi ƙuna a kanka da kai da abokanka guda biyu, domin ba ku yi mani maganar da ta dace ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi ba.8To yanzu sai ku tanada wa kanku shanu bakwai da raguna bakwai, ku je wurin bawana Ayuba ku miƙa baiko na ƙonawa domin kanku. Ayuba zai yi muku addu'a, zan kuma amsa addu'arsa, domin kada in yi fushi da ku saboda wawancinku, domin ba ku faɗi abin da ya dace game da ni kamar yadda Ayuba bawana ya yi ba."9Sai Elifas da Bildad Bashune, da Zofar Bana'ame suka je suka yi kamar yadda Yahweh ya umarce su, Yahweh kuma ya karɓi Ayuba.10Bayan Ayuba ya yi addu'a domin abokansa, Yahweh ya komo masa da wadatarsa. Yahweh ya ninka wa Ayuba wadatarsa fiye da ta dã.11Daga nan 'yan'uwan Ayuba mata, da duk waɗanda suka san shi a dã suka zo suka ci abinci tare da shi a gidansa. Suka nuna tausayinsu da kuma ta'aziya a gare shi kan duk asarar da Yahweh ya aukar masa, kowanen su kuma ya ba shi zoben zinariya da kuma azurfa.12Yahweh ya albarkaci ƙarshen rayuwar Ayuba fiye da lokacin farko, yana da tumaki dubu goma sha huɗu, raƙuma dubu shida, bijimai dubu ɗaya, da matan jakuna ɗari.13Haka nan ya sake samun 'ya'ya bakwai maza da 'ya'ya mata uku.14Ya raɗa wa ta fari suna Yemima ta biyun kuma Keziya, ta ukun kuma Keren-Haffuk.15A cikin dukkan ƙasar babu matan da aka samu kyawawa da suka kai su kyau, mahaifinsu ya ba su gãdo tare da 'yan'uwansu maza.16Bayan wannan Ayuba ya rayu shekaru 140; ya ga 'ya'yansa da kuma jikokinsa. Har zuwa tsara ta huɗu.17Bayan nan Ayuba ya mutu cikin tsufa da kuma cikakkun kwanaki.
Kuna iya son maimaita kalmomin "Na sani." AT: "Na sani cewa zaku iya komai duka. Na san cewa ba wani dalilin nufin ku da za a iya tsayar da shi"
Wannan za a iya fassara shi a cikin aiki mai aiki. AT: "ba wanda zai iya dakatar da duk shirye-shiryenku"
ULB da mafi yawan juyi zamani sun yarda da cewa Ayuba yana faɗar kalmomin Allah kansa kawai daga Ayuba 38: 2. Kuna iya yanke shawara, kamar yadda ULB, ya bayyana sarai cewa Allah ya yi wannan tambayar na Ayuba kuma yanzu Ayuba yana tunawa da shi. AT: "Kun ce mini, 'Wanene wannan"
Wato, ɓoye ko ɓoye shirin Allah.
Idanun suna wakiltar gani, gani yana wakiltar fahimta. AT: "amma yanzu na fahimce ku da gaske"
Ayuba kai yana nufin abinda ya fada. AT: "Na rena abubuwan da na faɗi"
mai tsananin ƙiyayya ko kiyayya mai karfi
Zama cikin turbaya da toka alama da ke nuna mutumin ya yi nadama.
Wannan kalmar ana amfani da ita anan don nuna alama mai mahimmanci a cikin labarin. Idan harshenku yana da hanyar yin wannan, zaku iya tunanin amfani da shi anan.
Wuta magana ne na fushi, fara wuta wata alama ce ta yin fushi. AT: "Na yi fushi da ku sosai"
"bijimai 7"
AT: "Ko da yake kun kasance wawaye sosai, ba zan hukunta ku kamar yadda kuka cancanci ba"
Mutumin magana ne ma'anar addu'ar da yake yi. AT: "Allah ya karɓi addu'ar Ayuba don abokansa guda uku"
"Yahweh ya maido da dukiyar sa" ko kuma "Yahweh ya maido masa da wadatarsa"
"duk mutanen da ya sansu a baya"
Anan, a iya fahimtar waɗannan kalmomin "ya albarkaci" da "rayuwar Ayuba" saád da aka la'akari bayani na baya. Za a iya fasar shi kaman haka AT: "fiye da yadda ya sa masa albarka a farko"
tumaki 14, 000
raƙuma 6,000
bijimai 1,000
7 yaya maza da 3 mata
Waɗannan sunayen mata ne
"'Ya'yan Ayuba sun fi kyau fiye da sauran matan dukka"
"yayi rayuwa shekaru 140"
Kalmomin "cike da kwanaki" na ma'ana dai-dai ne dai-dai da abu ɗaya "kasancewa da tsufa." Kalmomin nan guda biyu suna da salon magana iri ɗaya. AT: "wani dattijo ne"
1Albarka ga mutum wanda ba ya tafiya a cikin shawarar miyagu ko ya tsaya a hanyar masu zunubi ko ya zauna tare da masu ba'a.2Amma yana jin daɗin shari'ar Yahweh, yana nazarinta dare da rana.3Zai zama kamar itacen da aka dasa a gefen ƙorama wanda ya ke bada 'ya'yansa a kan kari, ganyayensa ba sa yin yaushi, ya kan yi nasara a dukkan abin da ya ke yi.4Mugaye ba haka suke ba, amma suna kamar yayi wanda iska ke kwashewa.5Saboda haka mugaye ba zasu tsaya a shari'a ba, ko masu zunubi su taru a wurin adalai ba.6Gama Yahweh yana lura da hanyar adalai, Amma hanyar mugaye za ta lalace.
Ana maganar "shawarar mugaye" kamar wata hanya ce da za a bi. AT: "wanda baya bin shawarar miyagu" ko "wanda baya yin abin da miyagu ke ba shi shawara"
Anan kalmar "hanya" tana wakiltar yadda mutane suke rayuwa. Kalmar "tsayawa" tana nan a layi daya da "tafiya." AT: "ku kwaikwayi halayen mutane masu zunubi"
Zama tare da mutanen da suke yi wa Allah ba'a yana wakiltar haɗuwa da mutanen da suke yi wa Allah ba'a. AT: "ko shiga waɗanda suke yi wa Allah izgili" ko "ko yi wa Allah ba'a tare da wasu waɗanda suke yi masa ba'a"
Wannan sunan Allah ne wanda ya bayyana wa mutanensa a Tsohon Alƙawari. Duba translationWord shafi game da Yahweh game da yadda za a fassara wannan.
Wannan nassi yana gabatar da wani hoto mai fasali wanda ake tunanin mai adalci game da bishiyar itaciya.
A cikin Littafi Mai Tsarki, ana yawan magana da mutane kamar bishiyoyi. Mutanen da ke jin daɗin shari’ar Yahweh za su iya yin duk abin da Allah yake so su yi kamar yadda itacen da aka dasa ta ruwa yake ba da ’ya’ya masu kyau. AT: "Zai kasance mai wadata kamar bishiya ... 'ya'yan itace a lokacinta"
Lafiyayyun bishiyoyi suna ba da 'ya'yansa a kirki a lokacin da suka dace.
"Zai yi nasara a duk abin da ya yi"
Yadda ba sa haka ana iya bayyana su a sarari. "Mugayen mutane ba su da wadata" ko "Miyagu ba sa cin nasara"
Yadda suke kamar ƙaiƙayi za a iya bayyana a sarari. AT: "amma a maimakon haka ba su da daraja kamar ƙaiƙayi"
Abubuwan da ke yiwuwa ma'anar su ne 1) tsayawa a cikin shari'a alama ce ta yanke hukunci ta wurin Allah da kuma barin gabansa. AT: "ba zai ci gaba da kasancewa a gaban Allah lokacin da yake hukunta su ba" ko "dole ne ya bar gaban Allah lokacin da yake yanke musu hukunci a matsayin masu laifi" ko kuma 2) rashin tsayawa a cikin hukuncin kwatanci ne na la'antar hukuncin." AT: "za a yanke masa hukunci a hukuncin" ko "za a yanke masa hukunci lokacin da Allah ya hukunta su"
Kasancewa da Allah a matsayin adali ana magana akan tsayawa tare da ƙungiyar mutanen kirki. AT: "kuma Allah ba zai karɓi masu zunubi ba tare da mutanen kirki"
Yadda mutane suke rayuwa ana maganarsu kamar wata "hanya" ko "hanya" da suke tafiya a kanta. AT: "yadda masu adalci ke rayuwa"
Yadda mutane suke rayuwa da abin da suke aikatawa ana maganarsu kamar wata "hanya" ko "hanya" da suke tafiya a kanta. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) hanyar halakar tana wakiltar miyagu da halakarwa saboda yadda suke rayuwa. AT: "Mugayen mutane zasu mutu saboda yadda suke rayuwa" ko kuma 2) hanyar lalacewa kwatanci ne na rashin iya rayuwa yadda suke yi. AT: "miyagu ba za su iya rayuwa yadda suke rayuwa ba"
1Meyasa al'ummai suke shirin tayarwa, kuma don me mutane ke ƙulla shawarwarin banza?2Sarakunan duniya ke ɗaukar matsayi tare, masu mulki kuma suna shirya maƙarƙshiya tare su yi gãba da Yahweh da kuma zaɓaɓɓensa Almasihu, cewa,3"Bari mu tsaga karkiyar da suka ɗora a kanmu, kuma mu jefar da sarƙoƙinsu."4Shi wanda ke zaune a sammai zai yi masu dariya; Ubangiji yana yi masu ba'a.5Ya yi masu magana cikin fushinsa da razanar dasu da kuma hasalarsa, cewa,6"Ni da kaina na naɗa sarkina a Sihiyona, tsattsarkan dutsena."7Zan yi shelar abin da Yahweh ya furta. Ya ce da ni, "Kai ɗana ne! Wannan rana na zama mahaifinka.8Ka roƙe ni, zan kuma ba ka al'ummai don gãdonka da yankunan duniya domin su zama mallakarka.9Za ka mallake su da sandar ƙarfe; za ka farfashe su kamar tukunyar yumɓu, za ka ragargaza su su farfashe."10To yanzu, ku sarakuna, ku ji gargaɗi; ku mai da hankali, ku sarakunan duniya.11Ku bauta wa Yahweh da tsoro da kuma murna tare da rawar jiki.12Sumbaci ɗan ko ya yi fushi da ku, zaku mutu ta hanyar fushinsa na ɗan lokaci. Albarka ta tabbata ga dukkan waɗanda ke zuwa gare shi neman mafaka.
Wannan yana iya nufin cewa al'ummai suna ta hayaniya da hayaniya.
Wadannan kila makirci ne ga Allah da kuma mutanensa.
Mutanen wasu ƙasashe suna magana game da Yahweh da mulkin Almasihu a kansu kamar dai ƙuƙumma da sarƙoƙi ne. AT: "Ya kamata mu 'yantar da kanmu daga ikonsu; kada mu sake su sake mulkarmu"
Anan zama wakiltar hukunci. Abin da ya zauna a kansa ana iya bayyana shi a sarari. AT: "yana mulki a cikin sammai" ko "yana zaune akan kursiyinsa a sama"
"Ubangiji yana izgili da mutanen." Dalilin da ya sa yake musu ba'a za a iya bayyana a sarari. AT: "Ubangiji yana izgili da su saboda dabarun wautarsu"
Bayyanar sunan "fushi" za'a iya bayyana shi a matsayin "mai tsananin fushi." AT: "zai yi fushi ya firgita su"
Yahweh yana jaddada cewa shi, ba waninsa ba, ya naɗa sarkinsa.
Mutumin da yake faɗin haka sarki ne. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Sarki ya ce, 'Zan sanar da hukuncin Yahweh shi'"
Daga cikin mutane da yawa a wannan sashin na duniya a lokacin, maza na iya yanke shawarar ɗaukar yara bisa doka, waɗanda za su zama magada. Anan Yahweh ya ɗauki mutum ya naɗa shi Sarkin Isra'ila. AT: "Na mai da ku ɗa na. Yau na zama mahaifin ku" ko "Yanzu ku ɗana ne kuma nine mahaifin ku"
Yahweh yana ci gaba da magana da sabon sarkin Isra'ila.
"ƙasashen da suke da nisa sosai"
An yi magana akan cin al'ummai kamar ya fasa su, kuma ana maganar ƙarfinsa kamar sandar ƙarfe. AT: "Za ku kayar da su kwata-kwata da ƙarfinku"
An yi maganar al'umman da ke hallakarwa kamar za a farfashe su kamar tukunyar yumɓu. AT: za ku hallakar da su kwata-kwata kamar tukunyar yumɓu "
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya. AT: "Don haka yanzu, ku sarakuna da shuwagabanin duniya, a gargaɗe ku kuma a gyara ku"
Wannan na iya nufin mutuwa a can, kafin mutum ya sami damar tafiya. AT: "zaku mutu nan take"
Ana maganar fushin sarki kamar wuta ce da zata iya ci. AT: "lokacin da ya fusata ba zato ba tsammani"
1Yahweh, nawa ne maƙiyana! Nawa ne suka tashi suna gãba da ni.2Da yawa suna magana a kaina, "Babu taimako dominsa daga Allah." Selah3Amma kai, Yahweh, kai ne garkuwa a gare ni, darajata, kuma wanda ke tallafar kaina.4Na yi kira da muryata ga Yahweh, ya kuma amsa mani daga tsattsarkan dutsensa. Selah5Na kwanta na kuma yi barci; na farka, gama Yahweh ya tsare ni.6Ba zan ji tsoron taron mutane waɗanda suka kewaye ni ta kowanne gefe.7Tashi, Yahweh! Ka cece ni, Allahna! Gama zaka buga dukkan abokan gãba har ƙasa; zaka kakkarye haƙuran mugaye.8Ceto zai zo daga wurin Yahweh. Bari ya sa wa jama'arsa albarka. Selah
Wannan tsawa ya nuna cewa Dauda yana tsoron maƙiyansa. AT: "Oh Yahweh, Ina da makiya da yawa!"
Yin magana da wani yana magana ne kamar tashi da shi. AT: "zo da ni"
Garkuwa tana kare soja. Dauda yayi magana kamar Allah garkuwa ne yana kare shi. AT: "kai, Yahweh, ka kiyaye ni kamar garkuwa"
"kai ne wanda ya daga min kai." Bai wa wani ƙarfin hali ana maganarsa kamar ɗaga kansa. AT: "wanda ya karfafa ni"
"sun kewaye ni don su hallaka ni"
Dauda yayi maganar fara yin wani abu kamar tashi. AT: "actionauki mataki" ko "Yi wani abu"
Wannan hanya ce ta zagin mutane. Dauda yayi magana kamar dai Yahweh zai zo ya bugi abokan gabansa. AT: "Gama za ku zagi duk abokan gābana kamar wanda ya buge su a muƙamuƙi"
Ana iya bayyana kalmar 'tsira' ta ƙuruciya da kalmar aikatau. AT: "Yahweh yana ceton mutanensa"
1Ka amsa mani sa'ad da cikin matsuwa nayi kira, Allahna mai adalci; ba ni hutu a lokacin da nake cikin matsuwa. Ka ji tausayina ka kuma saurari addu'ata.2Ku mutanen nan, sai yaushe zaku daina juya ɗaukakata zuwa kunya? Har yaushe zaku yi ta ƙaunar abubuwan banza kuna kuma cigaba da neman abin da ya ke na ƙarairayi? Selah3Amma kun sani Yahweh ne ya keɓe mai tsoronsa don kansa. Yahweh zai ji idan na yi kira a gare shi.4Ku ji tsoro, domin ku daina zunubi! Ku yi nazari a cikin zukatanku a kan gadajenku, kuma ku yi shuru. Selah5Ku miƙa hadayun adalci kuna kuma dogara ga Yahweh.6Da yawa sun ce, "Wane ne zai nuna mana wani abu mai kyau? Yahweh, ka ɗaga hasken fuskarka a kanmu.7Ka ba zuciyata farinciki fiye da na waɗanda ke da wadatar hatsi da sabon ruwa inabi.8A cikin salama zan kwanta har barci ya kwashe ni, domin kai kaɗai ne, Yahweh, ka kiyaye ni cikin lafiya sosai.
"Amsa mani idan na kira" ko "Ka taimake ni idan na kira"
"Allah, wanda ya nuna ni mai adalci ne"
Ana magana akan kasancewa cikin haɗari kamar kasancewa a cikin kunkuntar sarari. AT: "ku cece ni lokacin da nake cikin haɗari"
Dauda ya raira wannan waƙar kamar yana magana da abokan gaba.
Dauda yayi amfani da wannan tambayar don tsauta wa abokan gaba. AT: "Ku a koyaushe ku mai da mutuncina kunya!"
"Yahweh ya zaɓi mutanen da suke masu ibada"
Zuciya tana wakiltar tunanin mutum. Yin magana da kyau ana magana da shi azaman yin bimbini a cikin zuciyar mutum. AT: "Yi tunani a hankali"
"Hadaya mai kyau"
Anan ana maganar "amana" kamar abu ne wanda za'a iya sanya shi a wani wuri. Ana iya bayyana kalmar 'amana' ta ƙuruciya azaman aiki. AT: "dogara ga Yahweh" ko "amince da Yahweh"
Mai yiwuwa ma'anoni sune 1) nuna wani abu mai kyau yana wakiltar kawo abubuwa masu kyau. AT: "Wanene zai kawo mana abubuwa masu kyau?" ko 2) nuna wani abu mai kyau yana wakiltar faɗi cewa abubuwa masu kyau sun faru. AT: "Wanene zai ce wani abu mai kyau ya faru?"
Zuciya tana wakiltar mutum. AT: "Kun ba ni ƙarin farin ciki"
Ana maganar zaman lafiya kamar dai wuri ne. Ana iya sake bayyana wannan don cire sunan nan na yau da kullun "zaman lafiya." AT: "Zan kasance cikin lumana lokacin da na kwanta da bacci" ko "Ba zan ji tsoron haɗari ba lokacin da na kwanta da barci"
1Ka saurari kira na zuwa gare ka, Yahweh; kayi tunani a kan nishe-nishena.2Ka saurari muryar kirana, sarkina da Allahna, gama a gare ka nake yin wannan addu'ar.3Yahweh, da safe kaji kukana; da safe zan kawo rokona gare ka in kuma jira ka.4Gaskiya ne kai ba Allahn dake yarda da mugunta ba ne; ko mugayen mutane su zama bãƙinka.5Masu fahariya ba zasu tsaya a gabanka ba; kana ƙin dukkan mugaye.6Ka kan hallakar da maƙaryata; Yahweh yakan rena masu ta da hankali da mayaudaran mutane.7Amma ni, saboda babban alƙawarin ƙaunarka, zan zo cikin gidanka; in kuma rusuna maka da bangirma a tsattsarkan haikalinka.8Ya Ubangiji, ka bida ni in aikata adalcinka domin abokan gãbana; ka kuma fayyace mani hanyarka a gabana.9Gama babu gaskiya a cikin bakinsu; abubuwansu mugunta ne; harshensu kamar buɗaɗɗen kabari ya ke; suna yaudara da harshensu.10Ka furta su masu laifi ne, Allah; bari shirye-shiryensu su zama dalilin faɗuwarsu! Ka kore su sabili da yawan zunubansu, da kuma tayarwar da suke yi maka.11Amma bari dukkan waɗanda suka fake gare ka su yi farinciki; bari kullum su yi ta murna don kana kiyaye waɗanda ke ƙaunar sunanka.12Gama ka sawa masu adalci albarka, Yahweh; zaka kewaye su da alheri kamar garkuwa.
Wannan kira ne na neman taimako. AT: "Ku saurare ni kamar yadda nake kiranku don neman taimako"
ƙananan sauti waɗanda mutane suke yi da murya lokacin da suke wahala
"Zan yi roƙo" ko "zan tambaye ku abin da nake buƙata"
Tunda Dauda yana magana da Allah a cikin wannan zabura, ana iya bayyana wannan jumla da kalmar "kai." AT: "Yahweh, kuna raina masu tashin hankali da mayaudara" ko "Yahweh, kuna ƙin mutanen da ke aikata mugunta da yaudarar wasu"
Dauda yayi magana game da adalci kamar dai hanya ce kuma koyarwa tana jagoranci. Kalmomin "adalcinku" yana nufin cewa Allah mai adalci ne. AT: "ku koya mani in aikata abin da yake daidai kamar yadda kuke yi"
Dauda yayi maganar adalci kamar wata hanya. Hanya madaidaiciya tana da sauƙin gani ko tafiya a kanta. AT: "nuna mani a fili yadda zan rayu a hanyar da ta dace" ko "sauƙaƙa min sauƙi in yi abin da ke daidai"
Gaskiya kasancewa a baki wakiltar magana da gaskiya. AT: "Ba za su taɓa faɗin gaskiya ba"
Halin cikin yana wakiltar tunanin mutane da sha'awar su. AT: "tunaninsu da sha'awar su mugaye ne"
"ƙila makircinsu ya haifar musu da masifa" ko kuma "ƙila su zama ba su da muhimmanci saboda makircinsu"
Ana maganar Allah kamar yana mafaka ne, wurin da za'a kiyaye mutane. AT: "Bari duk waɗanda suka je wurinku don kariya su yi murna"
Sunan Allah yana wakiltar shi. AT: "waɗanda suke ƙaunarku"
1Yahweh, kada ka tsauta mani a lokacin fushinka ko ka hukunta ni da fushinka.2Ka yi mani jinƙai, Yahweh, gama na tafke sarai, ka warkar da ni, Yahweh, domin ƙasusuwana na makyarkyata.3Raina yana damuwa ƙwarai. Amma kai, Yahweh - har sai yaushe wannan zai ci gaba?4Ka zo, Yahweh! ka kuɓutar da ni. Ka cece ni domin alƙawarin amincinka!5Gama a cikin mutuwa ba a tunawa da kai. Don wane ne zai yi maka godiya a lahira?6Na gaji tilis saboda baƙinciki. Dukkan dare gadona ya kan jiƙe da hawayena; Na jiƙa matashin kaina da hawayena.7Idanuna sun yi kumburi saboda kuka; sun zama marasa ƙarfi saboda dukkan abokan gãbana.8Ku tafi daga wuri na, dukkan ku masu aikin mugunta; Gama Yahweh ya ji kukana. Yahweh ya ji rokona don jinƙai;9Yahweh ya amsa mani addu'ata.10Dukkan abokan gãbana zasu sha kunya da babbar damuwa. Zasu juya baya tare da babban ƙasƙanci.
Kasusuwan suna wakiltar dukkan jiki. Jikinsa na iya rawa saboda rashin lafiya ko tsananin gajiya. AT: "dukkan jikina yana rawa"
Dauda yayi amfani da wannan tambayar don ya nuna cewa baya son ci gaba da jin rauni da damuwa. AT: don Allah, kada ku bar wannan ya ci gaba!"
Cikakken sunan "ambaton" yana wakiltar yabo. AT: "Gama lokacin da mutane suka mutu, ba za su ƙara yabon ku ba"
Dauda ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa babu wani a cikin Lahira da zai gode wa Allah. AT: "Babu wanda ke cikin Lahira da zai ba ku godiya!" ko "Matattu ba za su iya yabonka ba!"
Nishinsa yana wakiltar zafi ko damuwa da yake ji. AT: "Na gaji sosai saboda azaba ta"
"Ina jika gado na a jike da hawaye na" ko "Gina na jike sosai saboda hawaye na"
Ana magana game da ikon gani dangane da idanu. AT: "Gani na ya yi duhu" ko "Ba na iya gani sosai"
Kasancewa da yardar rai don yin abin da Dauda ya roƙa ana maganarsa azaman karɓar addu'arsa. AT: "Yahweh zai amsa addu'ata"
1Yahweh Allahna, na sami mafaka a wurinka! Ka cece ni daga dukkan masu nema na, ka ƙwace ni.2Idan ba haka ba kuwa zasu ɗauke ni kamar zaki, su yayyaga ni har babu wani da zai kawo mani ceto.3Yahweh Allahna, ban aikata abin da maƙiya suka ce nayi ba; babu rashin adalci a cikin hannuwana.4Ban yi wani abu da ba dai-dai ga kowa ba wanda muke zaman salama dani, ko da ga wani mai gãba da ni.5Idan ba gaskiya nake faɗa ba bari maƙiya su nemi raina har su kama shi; bari ya taka rayayyen jikina a ƙasa ya bar ni da kunyata a ƙura. Selah6Ka tashi, Yahweh, cikin fushinka; tashi kayi gãba da hasalar abokan gãbana; ka tashi domina ka aiwatar da alƙawarin amincinka da aka sanka da shi.7Dukkan kabilu sun taru a gabanka; ka sake ɗaukar wurinka a bisan su.8Yahweh, kai ne alƙalin dukkan alummai; ka 'yantar da ni, Yahweh, gama ni adali ne bani da laifi, Maɗaukaki.9Bari mugun abu na masu aikata mugunta ya zo ƙarshe, amma ka tabbatar da adalan mutane, Allah mai adalci, kai kake gwada zukata da tunane-tunane.10Kariyata tana zuwa daga Allah, wanda ya ke ceton masu yin adalci a zuciya.11Allah ne alƙali mai adalci, Allah wanda ya ke jin haushi a kowacce rana.12Idan mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa ya kuma shirya bakansa don yaƙi.13Zai shirya kayayyakin faɗa gãba da shi; zai auna kibansa masu wuta.14Ka yi tunani akan wanda ya ɗauki ciki da mugunta, wanda ya shirya aiwatar da mugunta, wanda ya haifi cutar ƙarairayi.15Yana haƙa rami mai zurfi har kuma ya faɗa ramin da ya gina.16Mugun shirin da yayi ya koma a kansa kenan, don rikicin ya sauka a kansa kenan.17Zan gode wa Yahweh saboda adalcinsa; zan raira yabo ga Yahweh Maɗaukaki.
Maganar zuwa ga Yahweh don kariya ana magana ne da neman mafaka a gare shi. AT: "tafi zuwa gare ku don kariya!"
Dauda yayi maganar magabtansa sun kawo masa hari kamar zasu yaga jikinshi su yaga shi kamar zaki yayi. AT: "za su kashe ni da karfi kamar zaki yana tsattsage jikin wanda aka azabtar da shi ya kuma farfashe shi" ko "za su kashe ni da karfi"
"kuma ba wanda zai iya cetona"
Hannaye suna wakiltar abin da mutum yake yi. AT: "Ban yi wa kowa rashin adalci ba"
Anan "rayuwata" tana wakiltar marubuci. AT: "barshi ya halakar dani"
Tashi yana wakiltar yin wani abu ko ɗaukar mataki. AT: "Yi wani abu a cikin fushinku" ko "Yi fushi da maƙiyana kuma ku ɗauki mataki"
Ana maganar fada da mutane a matsayin tsayayya da su. AT: "yaƙi da fushin magabtana" ko "auka wa magabtana da suke fushi da ni"
Ana magana da mutane masu mulki a matsayin wanda ke kan su. Wurin da ya dace na Yahweh yana nufin ko sama ko kuma yin mulki gaba ɗaya. AT: "Ku yi mulkin su daga sama" ko "Ku yi mulkin su"
"nuna musu cewa banyi laifi ba"
"sa mutanen kirki su zama masu ƙarfi" ko "sa mutanen kirki su sami ci gaba"
Zukata da tunani suna wakiltar sha'awar mutane da tunaninsu. AT: "ku da kuka san tunaninmu na ciki"
Kalmar nan “garkuwa” tana wakiltar kariyar Allah.
Wanda Allah yake fushi da shi za a iya bayyana shi a sarari. AT: "Allah wanda yake fushi da mugaye kowace rana"
A cikin ayoyin ta 12 da 13, Dauda yayi magana game da Allah yana yanke hukuncin hukunta miyagu kamar Allah mayaƙa ne wanda ke shirin yaƙi da su da makamai. AT: "Allah zai ɗauki mataki a kansa kamar jarumin da ya kaifi takobinsa ya shirya bakansa don yaƙi"
Ana magana game da halakarwa da tashin hankali kamar sun buga kan mutum ko sun faɗi a kansa. AT: "Shirye-shiryen nasa masu halakarwa sun lalata shi, saboda tashin hankalinsa ya afka masa" ko "Lokacin da yake shirin halakar da wasu, wasu sukan hallaka shi; yayin da ya far wa wasu, wasu sukan kai masa hari"
1Yahweh Ubangijinmu, yaya girman sunanka ya ke a dukkan duniya, ka bayyana ɗaukakarka a cikin sammai.2Daga cikin bakin yara da jarirai ka shirya yabo domin maƙiyanka, domin ka tsai da abokan gãbarka da ramako.3Sa'ad da na duba sararin sammai, wanda yatsunka suka yi, wata da taurari, waɗanda kasa a wuraren zamansu.4Mene ne mahimmancin 'yan adam har da kake tunawa da su, ko mutune har da kake lura da su?5Duk da haka ka maida su ƙasa kaɗan da halittun dake sama ka kuma naɗa su da ɗaukaka da daraja.6Ka sa shi yayi mulkin dukkan abin da kayi da hannuwanka; ka ɗora dukkan abubuwa a ƙarƙashin ƙafafuwansa:7dukkan tumaki da shanu har ma da namomin jeji,8tsuntsayen sammai da kifayen teku da dukkan halittun dake cikin tekuna.9Yahweh Ubangijinmu yaya girman sunanka ya ke a cikin dukkan duniya!
“Sunan” Allah yana wakiltar dukan zatinsa. AT: "mutane a duk duniya sun san cewa ku manya ne"
Abubuwan da za a iya fahimta su ne 1) ana magana game da yabo a matsayin abu mai ƙarfi wanda Allah yake ɗauke da shi daga jarirai bakuna kuma ya zama bango na kariya ko 2) Allah ya halicci duniya don yabo ta gaskiya ta zo masa daga jarirai. AT: "Kun ba jarirai da jarirai ikon yabe ku" ko "Jarirai ne da jarirai waɗanda ke yabon ku da gaske"
Yatsun Allah suna wakiltarsa. AT: "sammai waɗanda kuka yi"
An bayyana waɗannan maganganun a cikin hanyar tambaya don ƙara ƙarfafawa. AT: "Abin mamaki ne cewa kuna tunanin mutane kuma kuna damuwa da su!"
Hannaye suna wakiltar abin da Allah yayi. AT: "abubuwan da kuka yi"
Samun ikon mallakan wasu ko sarrafa abubuwa ana maganarsu da kasancewa ƙarƙashin su ƙarƙashin ƙafafun mutum. Wannan yana nufin Allah ya ba mutane iko akan duk abin da ya halitta. AT: "kun bashi iko akan komai"
Da wannan furcin, Dauda ya nuna farincikin sa da kuma tsoron sa game da girman Allah. AT: "sunanka abin birgewa ne a duk duniya" ko "mutane a duk duniya sun san girman ku"
1Zan yi maka goɗiya Yahweh da dukkan zuciyata; zan furta dukkan abubuwa masu ban mamaki da ka yi.2Zan yi murna da farinciki da kai; zan raira waƙar yabo ga sunanka Maɗaukaki!3Lokacin da magabtana suka ja da baya, sun faɗi sun mutu a gabanka.4Gama kai ka tsare ni; ka zauna a kan kursiyinka, mai shari'ar adalci!5Ka kwaɓi al'ummai, ka kuma hallakar da mugaye; ka kawar da sunayensu har abada abadin.6An rugurguje abokan gãba kamar kangaye a lokacin da aka lalata biranensu. Dukkan tunawa dasu ya ƙare.7Amma Yahweh ka kasance har abada; ka kafa kursiyinka domin yin shari'a.8Zan yi mulkin dukkan duniya da adalci, kuma zai yi wa mutane shari'a da gaskiya.9Yahweh kuma zai zama mafaka ga waɗanda ake zalunta, wurin ɓuya a lokatan wahala.10Waɗanda suka san sunanka zasu dogara gare ka, domin kai ne, Yahweh, ba za ka yi watsi da duk wanda ya neme ka ba.11Ku yi waƙar yabo ga Yahweh, wanda ke mulki a Sihiyona; ku faɗa wa al'ummai abin da ya yi.12Gama Allah wanda ke ramakon jinin da aka zubar na tunawa; baya mantawa da kukan waɗanda ake cutar su.13Ka yi mani jinƙai, Yahweh; dubi yadda waɗanda ke gãba da ni suka wulaƙanta ni, kaine wanda zai kuɓutar da ni daga ƙofofin mutuwa.14Dãma inyi shelar dukkan yabonka. A ƙofofin budurwar Sihiyona zan yi farincikin cetonka!15Al'ummai sun faɗa cikin ramin da suka haƙa; tarkon da suka kafa don su buya ya kama ƙafafuwansu.16Yahweh ya bayyana kansa; ya gudanar da shari'a; mugu ya kama kansa da abubuwan da ya aikata. Selah17An maida miyagu makomarsu a Lahira, rabon dukkan waɗanda suka manta da Allah.18Gama ba kullum ne ake mantawa da masu buƙata ba ko masu bege waɗanda ake zalunta zasu ɓace har abada.19Ka tashi, Yahweh; kada ka bar mutum yayi nasara da kai; bari a yiwa al'ummai hukunci a gabanka.20Tsoratar da su, Yahweh; bari al'ummai su sani su mutane ne kawai.
Tunda ana magana da wannan waƙar ga Yahweh, ana iya kiran Yahweh da "ku." AT: "Yahweh, zan yi muku godiya da dukan zuciyata"
Za a iya nuna kalmar "ayyukan" da kalmar aikatau ta aikata. AT: "duk abubuwan mamakin da kuka aikata" ko "duk abubuwan ban mamaki da kuka aikata"
Anan sunan Allah yana wakiltar Allah. AT: "Zan raira yabo gare ku"
Sarakuna suna da iko su shar'anta mutane, kuma su kan zauna a kan karagarsu lokacin da suke hukunci. Dauda yayi magana kamar Allah sarki ne na duniya. AT: "kuna yin hukunci kamar sarki wanda yake zaune a kan karagarsa, kuma ku masu adalci ne"
Ana maganar sa mutane a manta da su kamar share sunan su. AT: "Kun sa an manta da su kamar an goge sunansu" ko "ba wanda zai sake tuna su"
Ana maganar makiya kamar birni ne cike da gine-ginen da suka rushe. AT: "An hallaka maƙiyanmu"
Ana iya bayyana kalmar 'ambaton' ta ƙananan kalmomin tare da kalmar "tuna". AT: "Babu wanda ya tuna su kwata-kwata"
"Kasance" mai yiwuwa wakiltar zama akan kursiyin a matsayin sarki. AT: "Yahweh yana zaune akan kursiyinsa har abada" ko "Yahweh yana mulki har abada"
Furcin "kursiyinsa" yana wakiltar sarautar Allah. Abubuwan da ke yiwuwa ma'anar su ne 1) "Yana hukunci ne domin ya shar'anta mutane" ko 2) "Yana mulkin mutane bisa adalci"
Anan “duniya” tana nufin dukkan mutanen duniya. AT: "Zai yi hukunci ga dukkan mutanen duniya da adalci"
Ana magana akan Allah kamar yana wurin da mutane zasu iya zuwa don aminci. AT: "Yahweh kuma zai kare waɗanda aka zalunta" ko "Yahweh zai kuma ba da kariya ga waɗanda ake zalunta"
Anan kalmomin "sunanka" suna wakiltar Allah. AT: "Waɗanda suka san ku"
"wanda ke zaune a Yerusalem"
Abin da ya tuna ana iya bayyana shi a sarari. AT: "Domin Allah mai rama zubar da jini yana tunawa da wadanda aka kashe" ko "Domin Allah yana tunawa da wadanda aka kashe kuma yana azabtar da masu kisan"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ku ga yadda waɗanda suka ƙi ni suke zaluntata" ko "ku ga yadda maƙiyana suka cutar da ni"
Ana maganar mutuwa kamar birni ne wanda yake da kofofin da mutane suke shiga ta ciki. Idan wani yana kusa da ƙofofin mutuwa, yana nufin cewa zai mutu nan ba da daɗewa ba. Ana maganar hana wani daga mutuwa kamar ɗauke shi daga ƙofar garin. AT: "ku wanda zai iya tsamo ni daga mutuwa" ko "ku da ke iya hana ni mutuwa"
Mutane suna haƙa rami don su kama dabbobin da suka faɗa cikinsu. Anan haƙa rami yana wakiltar yin shirye-shirye don halakar da mutane. AT: "Al'ummai suna kama da mutanen da suke haƙa rami ga wasu sannan su faɗa ciki"
Mutane suna ɓoye taru don su kama dabbobin da aka kama a cikinsu. A nan ɓoye raga yana wakiltar yin shirye-shirye don halakar da mutane. AT: "suna kama da mutanen da ke ɓoye raga kuma suna kamawa a ciki"
Wannan yana nufin "mugaye."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ba zai taɓa mantawa da mabukata ba" ko "Allah zai tuna da mabukata"
Ana magana da fata kamar abubuwa ne da za a iya fasa su ko lalata su. Fatan da ake lalatawa yana wakiltar abubuwan da mutane ke fata ba zai taɓa faruwa ba. AT: "kuma waɗanda ake zalunta ba za su yi fata har abada ba tare da sakamako ba" ko "kuma wata rana abin da ake zalunta ke fata zai faru"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ku yanke hukunci tsakanin al'ummomi a gabanku" ko "ku ɗauki al'ummomin a gabanku kuma ku hukunta su"
1Yahweh don me kake tsaye, a can nesa? Me ya sa ka ɓoye kanka a lokatan wahala?2Domin fahariyarsu, mugayen mutane na tsananta wa matalauta; amma bari tarkon da mugaye suka ɗana ya kama su.3Gama mugun mutum yana fahariya da manufofinsa; yana albarkatar haɗamarsa har yakan zagi Yahweh.4Mugun mutum yana ɗaga fuska; ba ya neman Allah. Ba ya tunani a kan Allah domin bai damu ya kula da dukkan al'amura a kansa ba.5Ya kan yi nasara a dukkan lokatai, domin adalcin dokokinka sun yi masa tsada; yana furci a kan abokan gãbansa.6Ya ce a cikin zuciyarsa, "Ba zan taba faɗuwa ba; a cikin dukkan tsararraki ba zan sadu da wahala ba."7Maganganunsa suna cike da zage-zage da yaudara, da mugayen kalmomi; harshensa kuma mai hatsari ne da hallakar wa.8Yana kwanto kusa da ƙauyuka; a ɓoyayyun wurare har ya kashe marasa laifi; idanuwansa kuma suna duban waɗanda baza su iya yin komai ba.9Yana jira a inda ya ɓuya kamar zaki a cikin kurmi; ya kan kwanta yana fakon wanda zai kama lokacin da yasa tarkonsa.10Kamammunsa kuma an buga su har ƙasa; suka faɗa cikin ƙaƙƙarfan ragarsa.11Ya ce a cikin zuciyarsa, "Allah ya manta; ya rufe fuskarsa; ba zai damu ya duba ba."12Tashi, Yahweh! Ɗaga hannunka, Allah! Kada ka manta da waɗanda ake tsanantawa.13Me yasa mugun mutum zai ƙi Allah har ya ce a cikin zuciyarsa, "Ba zai kama ni da wani alhaki ba"?14Kana kula da komai, don kullum kana ganin wanda ake sa masa damuwa da baƙinciki. Kana sa mai bukata yasa dogararsa a gare ka; kana kuɓutar da marasa iyaye.15Ka karya hannun mugu da mai aikata mugunta. Kasa ya ɗauki laifin mugun aikinsa, kada ya yi tunanin ba za a taba ganewa ba.16Yahweh Sarki na har abada abadin; al'ummai kuma za a kore su daga ƙasarsa.17Yahweh, ka ji buƙatun wanda ake tsanantawa; ka karfafa zukatansu, ka saurari addu'arsu.18Zaka kãre marasa iyaye da waɗanda ake ƙuntata masu saboda babu wani mutum a wannan duniya da zai sake jawo razana.
Mai jawabin yana amfani da waɗannan tambayoyin don bayyana damuwarsa cewa Allah bai taimake shi ba. AT: "Yahweh, kamar dai kuna nesa da ni kuma kuna ɓoye mini a duk lokacin da nake cikin matsala"
Fuskar da aka daga tana wakiltar girman kai ko girman kai. AT: "yana da halin girman kai" ko "yana da girman kai"
Neman Allah yana wakiltar 1) neman taimakon Allah ko 2) yin tunani game da Allah da kuma yi masa biyayya. AT: "baya neman taimakon Allah" ko "baya tunanin Allah"
"Yana cikin aminci a kowane lokaci." Ba shi da lafiya sosai, amma yana tunanin cewa yana da lafiya.
Ana magana da wani abu mai wahalar fahimta kamar yayi sama da isa. AT: "ba zai iya fahimtar dokokinka na adalci ba"
Ana magana game da fuskantar masifa kamar saduwa da ita. AT: "Ba zan sami matsala ba"
Abin da mutane ke faɗi ana maganarsa kamar kasancewa a bakinsu. AT: "A koyaushe yana zagin mutane, yana faɗar ƙarairayi, kuma yana barazanar cutar da mutane"
Anan harshe yake wakiltar magana. AT: ko "abin da yake fada na cutar da lalata mutane" ko "yana magana da kalmomin da ke barazana da cutar da mutane"
Kalmar "ya" tana nufin mugaye.
Wannan yana magana ne game da mugu kamar yana zaki. AT: "Yana ɓoyewa yayin da yake jiran marasa ƙarfi su yi tafiya kusa da shi, kamar yadda zaki yakan yi shuru a cikin daji don dabbar da yake so ya kai wa hari"
Marubucin yayi maganar mugaye yana kama mutane kamar shi maharbi ne yana amfani da taru don kama dabbobi. AT: "Yana kama waɗanda ake zalunta kamar mafarauci wanda ya kama dabba a cikin raga ya jawo ta"
Ƙi kula da abin da mutane ke yi ana magana da shi kamar mantawa. AT: "Allah baya kulawa" ko "Allah baya kula da abin da nake yi"
Ƙi kula da abin da wani ya yi ana maganarsa kamar rufe fuska. AT: "Allah ya ƙi ganin abin da ke faruwa"
"Ba za ku buƙaci na gaya muku dalilin da ya sa nake yin abin da nake yi ba." Tsayar da wani a nan yana wakiltar hukunta shi. AT: "Ba za ku hukunta ni ba"
Anan "hannu" yana wakiltar iko. AT: "Rushe ikon mugaye da mugu mutum" ko "Sanya mugaye da mugu mutum ya zama mai rauni"
Sanya wani hisabi kan munanan ayyukansa yana wakiltar hukunta shi. AT: "Ku hukunta shi saboda mugayen abubuwan da ya aikata"
Ana nuna cewa mutanen da ake zalunta sun yi kuka ga Allah. AT: "lokacin da mutanen da ake zalunta suka yi kuka gare ku, sai ku saurari abin da suke gaya muku abin da suke buƙata"
Zuciya mai ƙarfi tana wakiltar ƙarfin zuciya, kuma ƙarfafa zuciyar mutane yana wakiltar ƙarfafa su. AT: "kuna ƙarfafa su" ko "kuna ƙarfafa su"
1Na sami mafaka a wurin Yahweh; yaya zaka ce da ni, "Ka tashi kamar tsuntsu akan tsauni"?2Amma duba! miyagu sun shirya ƙibansu a kan tsarkiya don su harba cikin duhu a zuciyar adali.3Gama idan ginshiƙai suka lalace, mene ne adali zai iya yi?4Yahweh yana cikin tsatsarkan haikalinsa; idanuwansa suna kallo, idanuwansa suna gwada 'ya'yan 'yan adam.5Yahweh yana gwada masu kirki da miyagu dukka, amma yana ƙin waɗanda ke ƙaunar tashin hankali.6Yana ruwan garwashin wuta da ƙibiritu a kan mugaye; iska zata kone rabonsu daga finjilinsa!7Gama Yahweh mai adalci ne, yana kuma ƙaunar masu gaskiya; adalai kuma zasu ga fuskarsa.
Maganar zuwa ga Yahweh don kariya ana magana ne da neman mafaka a gare shi. AT: "je wurin Yahweh don kariya"
An yi wannan tambayar don bayar da girmamawa. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Don haka kar ku ce in gudu!"
Anan "dai-daitacciyar zuciya" tana nufin mutane masu ibada ko adalai.
Anan "tushe" ť na iya nufin doka da oda. Ana tambayar wannan tambaya ta lafazi don ƙara ƙarfafawa. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Mutanen kirki ba za su iya yin komai ba yayin da ba a hukunta mugaye lokacin da suka ƙi bin dokoki!"
"mutuntaka"
"cutar da wasu"
An bayyana azabar Allah kamar tana ƙone garwashin wuta da kibiritu daga dutsen mai fitad da wuta. AT: "Yana azabtar da mugaye; ba za a sami sauƙi a kansu ba!"
1Ka yi taimako, Yahweh, saboda mutanen kirki sun ɓace; aminitattu ma sun ɓace.2Kowanne mutum yana maganar banza ga maƙwabcinsa; kowanne yana maganar yaudara da leɓuna da zuciya biyu.3Yahweh, ka datsa dukkan leɓunan yaudara, kowanne harshe ya riƙa faɗin manyan abubuwa.4Waɗannan sune waɗanda suka ce, "Ta wurin harshenmu zamu rinjaya. Sa'ad da leɓunanmu suka yi magana, wane ne zai zama gwani a bisanmu?"5"Saboda tashin hankali akan matalauta, domin nishin masu buƙata, zan tashi," inji Yahweh. "Zan basu tsaron da suka yi marmari."6Kalmomin Yahweh kalmomi ne zalla, kamar azurfar da aka narkar a tanderun wuta, aka tace har sau bakwai.7Kai ne Yahweh! Ka kiyaye su. Ka tsare mutanen kirki daga muguwar tsara har abada.8Mugaye suna tafiya ko'ina a lokacin da mugunta ke ɗaukaka a cikin 'yan adam.
"Ya Yahweh, ka taimake ni"
"mutane masu aminci duk sun ɓace"
Anan "lebe mai daɗin kai" a alama ce ta mutanen da suke fadan wasu. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "yankewa" a ishara ce ga kisa. AT: "kashe duk wanda ya fadanta wasu" ko (2) "yankewa" a ishara ce ta dakatar da wani abu. AT: "dakatar da duk waɗanda ke fadan wasu" (Duba:
Anan "kowane harshe" yana wakiltar duk mutumin da yake shelar manyan abubuwa. AT: "duk mutumin da yake alfahari"
An yi wannan tambayar ta lafazin ne don jaddada cewa sun yi imani babu wanda zai iya mulkar su. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "babu wanda zai iya mulkin mu!"
Wannan yana nufin Yahweh zai yi wani abu don taimaka wa mutane.
An kwatanta kalmomin Yahweh da azurfa da aka tsarkake. AT: "ba su da wani ajizanci"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da mutane a ko'ina suke yabon mugunta"
1Yahweh, har sai yaushe, za ka ci gaba da mantawa da ni? Har yaushe ne zaka ɓoye mani fuskarka daga gare ni?2Har yaushe ne zan daina damuwa da baƙinciki a zuciyata dukkan yini? Har yaushe ne maƙiyana zasu rika cin nasara a kaina?3Ka dube ni ka kuma amsa mani, Yahweh Allahna! Ka bani haske ga idanuwana, ko in yi barcin mutuwa.4Kada ka bar maƙiyina ya ce, "Na ce nasara a kansa," don kada maƙiyina ya sami abin cewa, "Na yi rinjaye akan abokin gãbana;" idan ba haka ba, maƙiyina zai yi murna saboda faɗuwata.5Amma na dogara ga amintaccen alƙawarinka; zuciyata zata yi murna da cetonka.6Zan yi waƙa ga Yahweh domin ya yi mani abin kirki ƙwarai.
An yi wannan tambayar ne don jawo hankalin mai karatu da ƙara ƙarfafawa. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Yahweh, da alama kun manta da ni!"
Ana tambayar wannan tambaya don ƙara ƙarfafawa. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Tabbas abokan gaba na ba koyaushe za su ci ni ba!"
"Ka ba ni hankalin ka ka saurare ni"
Wannan hanya ce ta neman ƙarfi. AT: "Ka sake ƙarfafa ni"
Yin “barci cikin mutuwa” na nufin mutuwa.
Cikakken sunan "aminci"ana iya fassara shi azaman sifa. AT: "Na aminta da cewa kun kasance masu aminci ga alkawarinku" ko "Na amince da ku saboda kun kasance masu aminci ga alkawarinku"
Anan "zuciyata" tana wakiltar mutum duka. AT: "Zan yi murna saboda kun cece ni"
1Wawa yace a cikin zuciyarsa, "Ba Allah." Sun lalace sun kuma aikata laifin ban ƙyama; babu wani wanda ya aikata nagarta.2Yahweh ya duba ƙasa daga sama a kan 'yan adam ya gani idan ko akwai wani mai fahimta, wanda ke neman sa.3Dukkansu sun koma baya. Ga baki ɗayansu sun zama marasa kirki. Ba wanda ya ke aikata abin da ya ke dai-dai, babu ko ɗaya.4Sun san wani abu, waɗanda suka aikata laifi, waɗanda suke cin mutanena kamar yadda suke cin gurasa, amma wane ne ba ya kiran Yahweh?5Sun razana tare da fargaba, gama Allah yana tare da taruwar adalai!6Kuna so ku ci mutuncin matalaucin mutum koda ya ke Yahweh ne mafakarsa.7Oh, dama ceton Isra'ila zai zo daga Sihiyona! Sa'ad da Yahweh ya dawo da mutanensa daga bauta, Yakubu zai yi murna, Isra'ila ma zata yi farinciki!
Wannan karin magana ne da ke nufin mutum ya ce wa kansa ko tunanin kansa. AT: "Wawa ya ce wa kansa"
Kalmar "su" tana nufin duk wawayen mutane da suka ce babu Allah.
Wannan yana bayyana waɗanda suke son su san Allah kamar suna bin sa a kan hanya. AT: "waɗanda suke son su san shi"
Wannan yana bayanin mutanen da suka ƙi Allah kamar sun daina tafiya akan madaidaiciyar hanya kuma sun tafi wata hanyar. AT: "Dukkansu sun juya baya ga Yahweh"
Abubuwan da ke bayyane suna "mugunta" ana iya bayyana su da "munanan ayyuka." AT: "waɗanda suke aikata mugunta"
Wannan yana nufin waɗanda suke aikata mugunta kuma suna ɓata bayin Allah kamar suna cin abinci.
Kalmar "su" ť tana nufin waɗanda suke aikata mugunta.
Faɗi cewa "Allah yana tare da" waɗanda suke masu adalci yana nufin yana taimaka musu. Ana iya bayyana wannan a sarari cikin fassarar. AT: "Allah yana taimakon waɗanda suke yin adalci" ko "Allah yana taimakon waɗanda suke yin abin da ya dace"
Wannan yana magana ne game da kariyar da Yahweh ke bayarwa kamar yana da matsuguni wanda mutum zai iya nema a cikin hadari. AT: "Yahweh kamar masauki ne na kariya"
Wannan kirari ne. Marubucin yana fadar abin da yake so ko kuma fatan Allah ya yi. AT: "Ina fatan dai ceton Isra'ila ya zo daga Sihiyona!"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya. Anan dukka "Yakubu" da "Isra'ila" suna wakiltar mutanen Isra'ila. Za a iya haɗa jimloli biyu a cikin fassarar. AT: "to duk jama'ar Isra'ila za su yi murna ƙwarai"
1Yahweh, wane ne zai iya tsaya wa a rumfar sujadarka? Wa zai iya zama a tudun ka mai tsarki?2Duk wanda ba shi da laifi, wanda ke aikata abin dake dai-dai wanda kuma ya ke faɗar gaskiya daga zuciyarsa.3Wanda baya ɓatanci da harshensa, baya cin mutuncin wasu, baya ɓatanci ga maƙwabcinsa.4Mutumin wofi abin reni ne a idanunsa, amma yana girmama waɗanda ke tsoron Yahweh. Yana rantsuwa ba don kansa ba, kuma yana cika alƙawaran da yayi.5Baya karɓar ruwa a kuɗin da ya bayar bashi. Baya karɓar cin hanci don ya yi shaidar zur a kan marar laifi. Duk wanda ya ke yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa girgiza ba.
"Tsattsarkan tudun" na Allah yana wakiltar haikalin Allah, wanda yake a Tsaunin Sihiyona. AT: "Wanene zai iya zama a tsattsarkan wurinku?"
"yayi magana da gaskiya"
A nan "harshe" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. Kalmar "ya"tana nufin "mutum mai tsaurin kai"
"Mugu ne" ko "Mutumin da ya ƙi Yahweh"
Anan "don a girgiza" ť yana wakiltar rashin rayuwa lafiya. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "zai rayu cikin aminci"
1Ka tsare ni, Allah, gama na zo neman mafaka a gare ka.2Na ce da Yahweh, "Kai ne Ubangijina; nagarta ta a banza take idan bana tare da kai.3Kamar yadda tsarkakakkun mutane waɗanda ke a duniya, su mutane masu kirki; dukkan murnata a gare su take.4Wahalolinsu zasu ƙaru, waɗanda ke neman waɗansu gumaka. Ba zan zubo masu da baye-baye na shan jinin allolinsu ba ko in furta sunayensu da leɓuna na ba.5Yahweh, kaine kaɗai na zaɓa da ƙoƙona. Kai ne kake riƙe da rabona.6An ajiye ma'aunan layi domina a wuraren jin daɗi; babu shakka gãdon dake kawo jin daɗi nawa ne.7Zan albarkaci Yahweh, wanda ke bani shawara; ko da dare ma ina tunanin umarninsa.8Na sa kaina a wurin Yahweh a dukkan lokuta, saboda kada in girgiza daga hannun damarsa!9Don haka cike nake da murna; ɗaukakata na farinciki. Babu shakka zan zauna a cikin tsaro.10Saboda baza ka bar raina a Lahira ba. Ba zaka bar amintaccenka ya ga rami ba.11Ka koya mani hanyar rai; yalwataccen farinciki na kasancewarka; murna zata zauna a hannun damarka har abada!"
Maganar zuwa ga Yahweh don kariya ana magana ne da neman mafaka a gare shi. AT: "tafi zuwa gare ka don kariya"
Anan "tsarkakakkun mutane" na isharar da mutanen Allah wadanda suka dogara gare shi. AT: "mutanenku da ke rayuwa a wannan ƙasar"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki.AT: "Matsalar waɗanda ke neman wasu alloli za su ƙaru"
Laga sunayensu kwatanci ne na yabon su, kuma “leɓɓa” alama ce ta abin da mutum ya faɗa. AT: "ko ku yaba musu da maganata" ko "kuma ba zan yabi gumakansu ba"
Anan Dauda yayi magana game da Yahweh kamar yana cikin yankin ƙasa da aka ba shi.
"Kuna ƙaddara makomata" ko "Kuna sarrafa abin da zai faru da ni"
Anan Dauda yayi maganar albarkar Yahweh kamar dai gadon da ya samu ne. AT: "Ina murna da duk abubuwan da ya ba ni"
"Kullum ina tuna cewa Yahweh yana tare da ni"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "babu abin da zai dauke ni daga gefensa"
Anan "zuciya" tana wakiltar tunanin mai magana da motsin ranshi. AT: "Saboda haka na yi murna"
Marubucin yayi maganar “murna” kamar dai mutum ne.
1Ka kasa kunne ga roƙona don adalci, Yahweh; ka saurari kirana na neman taimako! Ka kasa kunne ga addu'ata daga leɓuna marasa yaudara.2Bari baratarwata ta zo daga wurinka; bari idanuwanka su ga abin dake dai-dai!3Idan zaka gwada zuciyata, idan zaka zo gare ni da dare, zaka tsarkakeni ba kuma za a sami wata mugunta a shirye-shiryena ba; bakina ba zai yi saɓo ba.4Game kuma da ayyukan mutane; sune a cikin maganar leɓunanka waɗanda na tsare kaina daga hanyoyi na marasa bin doka.5Na yi tafiya a kan tafarkinka sosai; sawayena basu kauce ba.6Na yi kira a gare ka, domin ka amsa mani, ya Allah; ka juyo da kunnenka gare ni ka kuma saurara a lokacin da na yi magana.7Ka nuna mani amintaccen alƙawarinka ta hanya mai banmamaki, kai da ke yin ceto ta hannun damarka ga waɗanda ke neman mafaka a gare ka daga maƙiyansu!8Ka tsare ni kamar ƙwayar idanunka; ka ɓoye ni a ƙarƙashin inuwar fukafukanka9daga fuskar miyagu waɗanda ke zargi na, maƙiyana da suka kewaye ni.10Basa jin tausayin kowa; bakunansu na magana da fahariya.11Sun kewaye sawayena. Sun sa idanuwansu don su fyaɗa ni ƙasa.12Su kamar zakoki ne sun ƙosa su ga abin da zasu hallaka, kamar 'ya'yan zakoki suna laɓe a ɓoyayyun wurare.13Ka tashi, Yahweh! Ka hare su! Ka jefar da su a ƙasa a kan fuskokinsu! Ka cece raina daga takobin mugaye!14Yahweh, ka cece ni daga gare su da hannun ka, daga mutanen wannan duniya waɗanda arziƙinsu a cikin wannan rayuwa ne kaɗai! Za ka cike wuraren ajiyar mutanenka da arziki; zasu zama da 'ya'ya dayawa kuma zasu bar wadatarsu ga 'ya'yansu.15Amma ni, zan ga fuskarka a cikin adalci; zan gamsu, sa'ad da na farka, da ganin ka.
Maganar "ba da kunne" kwatanci ne na sauraro, kuma "leɓunan da ba yaudara" wani magana ne ga mutumin da ba ya yin ƙarya. AT: "Ku saurari addu'ata domin na yi magana ba tare da yaudara ba"
Tabbatarwa daga Allah yana wakiltar Allah yana hukunta wani kuma ya ayyana shi mara laifi. 'Kasancewar' Allah met alama ce ta Allah kansa. AT: "Bari hujjata ta zo daga gare ku" ko "Bayyana ni mara laifi ne"
Anan "idanunku" ť sunaye ne don Allah kansa, kuma "gani" kwatanci ne na kulawa da ƙudurin yanke shawara yin wani abu. AT: "don Allah a ga abin da yake dai-dai" ť ko "a yi abin da yake dai-dai"
Anan "gwada zuciyata" yana nufin bincika tunanina da muradi na. AT: "Idan kun bincika tunanina cikin dare"
Anan ana magana bakin kamar yana iya yin aiki da kansa. Hakanan yana wakiltar kalmomin da mutum yake magana. AT: "Ba zan yi ƙarya ko yin zunubi da maganata ba"
Anan "maganar leɓunanku" na nuna koyarwar Allah, kuma "hanyoyin marasa bin doka" wani magana ga abubuwan da marasa bin doka suke aikatawa. AT: "ta hanyar bin umarninku ne yasa na kiyaye kaina daga aikata abubuwan da mutane masu aikata laifi ke aikatawa" ko "koyarwar ku ta sa na guji aikata miyagun abubuwa"
Duk waɗannan maganganun suna nufin abu ɗaya. Maimaitawa yana ƙara ƙarfafawa.
Marubucin yayi maganar biyayyarsa ga Allah kamar yana tafiya akan hanya. AT: "Na ƙuduri aniyar bin hanyoyinku"
"Hannun dama" ť na nufin ikon Allah. AT: "ƙarfin ku mai ƙarfi"
Maganar zuwa ga Yahweh don kariya ana magana ne da neman mafaka a gare shi. AT: "tafi zuwa gare ka don kariya" ť
'' Idon idonka '' yana nufin wani abu mai mahimmanci. AT: "Kare ni kamar yadda zaku kiyaye wani abu mafi daraja da daraja"
Dauda yayi maganar kariyar Allah kamar shi tsuntsu yana kare ga itsanta a ƙarƙashin fikafikanta. AT: "Kiyaye ni kamar yadda uwa tsuntsu ke kare ta hanyar tara su a ƙarƙashin reshenta"
Anan "an kewaye takunkuna na" yana wakiltar yadda magabtan Dauda suka bi shi duk inda ya tafi domin su kama shi. AT: "Makiyana sun kewaye ni"
Wadannan kalmomin guda biyu suna bayyana ra'ayoyi masu kama da juna. Maimaitawa yana ƙara ƙarfi.
Wadannan kalmomin guda biyu suna bayyana ra'ayoyi masu kama da juna. Maimaitawa yana ƙara ƙarfi.
Tsohon rubutu yana da wuyar fahimta. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "taskace" kwatanci ne na ƙaunatacce, kuma "wadatattunku" yana nufin mutanen da Allah yake ƙauna. AT: "zaku cika cikunnin mutanen da kuke so da wadata" ko 2) "wadatattunku" yana nufin dukiyar da Allah yake baiwa mutane, "mutanen wannan duniyar" AT: "ku za su cika cikinsu da dukiya mai tarin yawa"
Anan "fuska" yana wakiltar Yahweh a cikin dukkan yanayin rayuwarsa. Dauda yana da tabbaci cewa zai ga Yahweh. AT: "saboda nayi daidai yadda ya dace, zan kasance tare da ku wata rana"
1Ina ƙaunarka, Yahweh, ƙarfina.2Yahweh ne dutsena, hasumiya ta, wanda ke kawo mani tsaro; shi ne Allahna, dutsena; zan ɓoye a cikinsa. Shi ne garkuwata, ƙahon cetona, shi ne kuma ƙarfina.3Zan yi kira ga Yahweh wanda ya cancanci a yabe shi, za a kuma cece ni daga maƙiyana.4Sarƙoƙin mutuwa sun kewaye ni, hargowar ruwaye marasa daraja sun sha kaina.5Sarƙoƙin Lahira sun kewaye ni; tarkon mutuwa kuwa ya kama ni.6A cikin ƙuncina na yi kira ga Yahweh; na yi kiran neman taimako ga Allahna. Ya ji muryata daga haikalinsa; kirana na neman taimako ya kai gare shi; ya shiga har cikin kunnuwansa.7Sai duniya ta raurawa ta girgiza; ginshiƙan duwatsu kuwa suka jijjigu suka kuma yi rawar jiki saboda Allah ya husata.8Hayaƙi kuwa ya yi ta tuƙaƙowa daga kafofin hancinsa, harshen wuta ya fito daga bakinsa. Gawayin garwashi suka fita ta wurinsa.9Ya buɗe sammai ya sauko ƙasa, duhu kuma baƙiƙƙirin na ƙarƙashin ƙafafunsa.10Ya hau kan kerub ya tashi; ya yi tafiya a kan fikafikan iska.11Ya maida duhu rumfa a kewaye da shi, gizagizan ruwan sama masu nauyi a sararin sama.12Ƙanƙara da garwashin wuta sun faɗo daga walƙiya dake gabansa.13Yahweh ya yi tsawa a cikin sammai! Muryar Maɗaukaki ta yi tsawa.14Ya harba kibansa, ya warwatsar da magabtansa; walƙatawar walƙiyoyi ta warwatsar da su.15Daga nan hanyoyin ruwa suka bayyana; ginshiƙan duniya dukka aka bayyana su a cikin kukan yaƙinka, Yahweh- a cikin hurawa mai ƙarfi ta numfashin kafofin hancinka.16Ya miƙo hannunsa ƙasa daga samaniya; ya riƙe ni! Ya tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi.17Ya kuɓutar da ni daga ƙaƙƙarfan abokin gãbata, daga waɗanda ke ƙi na, domin sun fi ni ƙarfi sosai.18Sun tasar mani a ranar shan ƙuncina amma Yahweh ne mai taimako na!19Ya fitar da ni daga hatsari a buɗaɗɗen wuri; ya cece ni domin yana farinciki dani.20Yahweh ya sãka mani saboda adalcina; ya dawo da ni saboda hannuwana na da tsarki.21Domin na kiyaye tafarkun Yahweh ban kuma juya ga mugunta daga Allahna ba.22Gama dukkan ka'idodinsa na adalci suna gaba na; game kuma da fariilansa, ban kauce daga gare su ba.23Na kuma zama marar laifi a gabansa, na kiyaye kaina daga zunubi.24Domin haka Yahweh ya dawo dani saboda adalcina, domin hannuwana masu tsafta ne a idanunsa.25Ga kowanne mai aminci, kana nuna kanka mai aminci; ga mutum marar laifi, ka nuna kanka marar laifi.26Ga duk wani mai tsarki, ka nuna kanka mai tsarki; amma kana da dabara ga duk mai aikin mugunta.27Gama kana ceton mutane daga wahala, amma ka kan ƙasƙantar da masu girmankai da suka ɗaga idanunsu!28Domin ka bada haske ga fitilata; Yahweh Allahna ka haskaka duhuna.29Gama ta wurinka zan iya tserewa maƙiyana; ta wurin Allahna zan iya tsallake saman katanga.30Kamar yadda Allah ya ke, hanyarsa dai-dai take. Maganar Yahweh tsartsarka ce! Shi garkuwane ga duk wanda yake neman mafaka a wurinsa.31Gama wane ne Allah sai Yahweh? Wane ne dutse in ba Allahnmu ba?32Shi ne Allahn dake ƙarfafa ni kamar ɗammara, wanda ya ke sa mutanen da basu da aibu a kan hanyarsa.33Yana tabbatar da lafiyar ƙafafuna kamar barewa ya kuma sa ni a bisa!34Yakan koyar da hannuwana don yaƙi makamaina kuma za su tankware bakan tagulla.35Kai ka bani garguwar cetona. Hannunka na dama yana ƙarfafa ni, tagomashinka kuma ya maida ni babba.36Kayi mani buɗaɗɗen wuri don ƙafafuwana suna ƙarƙashina saboda kada santsi ya ɗauke ƙafafuwana.37Na kori maƙiyana har na kama su; ban juya ba har sai da na lalata su dukka.38Na buga su har ba wanda zai iya tashi; sun faɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.39Gama ka sa ƙarfi a kaina kamar ɗamara don yaƙi; ka sa waɗanda ke gãba da ni a ƙarƙashina.40Ka bani nasara akan maƙiyana; zan hallaka waɗanda ke gãba da ni.41Suna kira don taimako, amma babu wani da ya cece su; sun yi kira ga Yahweh, amma bai amsa masu ba.42Na buge su har sun zama gutsu-gutsu kamar ƙura a fuskar iska; na jefar da su waje kamar laka a tituna.43Ka cece ni daga mutane masu husuma. Ka maida ni shugaba a kan al'ummai. Mutanen da ban san su ba, ban ma yi masu aiki ba.44Yayin da suka ji ni, zasu yi mani biyayya; bãƙi zasu rusuna mani dole.45Bãƙin zasu zo da rawar jiki daga kagarunsu.46Yahweh mai rai ne; dutsena abin yabo. Allah mai cetona a gimama shi.47Shi ne Allah wanda ya ke ɗaukar fansa domina, yana sawa a rinjaye al'ummai a ƙarƙashina.48Ni 'yantacce ne daga maƙiyana! Lalle, ka ɗaukaka ni sama da waɗanda suka taso suna gãba da ni! Ka cece ni daga mutane masu tawaye.49Saboda haka zan yi yabo a gare ka, Yahweh, a cikin al'ummai; zan raira maka waƙar yabon sunanka!50Allah yana bada babbar nasara ga sarkinsa, ya kan nuna amintaccen alƙawarinsa ga wanda ya zaɓa, ga Dauda da zuriyarsa har abada.
"ya rera wannan waƙar ga Yahweh"
"bayan da Yahweh ya cece shi"
Anan "hannu" yana nufin ikon Saul. AT: "daga ikon Saul"
Dauda yayi maganar Yahweh kamar dutse. Kalmar "dutse" hoton wuri ne mai aminci.
Anan kalmomin "dutse" da "sansanin soja" suna raba ma'anoni iri ɗaya kuma suna jaddada cewa Yahweh yana ba da kariya daga abokan gaba.
Dauda yayi magana game da Yahweh kamar shi "garkuwa," "ƙahon" cetonsa, da "dagararsa. "Yahweh shi ne yake kiyaye shi daga cutarwa. Anan irin wannan ra'ayin an maimaita shi ta hanyoyi uku don girmamawa.
Dauda yayi maganar mutuwa kamar mutum ne zai iya kama shi ya ɗaure shi da igiyoyi. AT: "An kusa kashe ni"
Dauda kamar bashi da karfi kamar wanda ruwa mai gudu ya kwashe shi. AT: "Na ji ba ni da komai gaba ɗaya"
"A cikin babban buƙata ta" ko "A cikin yanke kauna"
Anan Dauda yayi magana game da "kiran taimako" kamar dai mutum ne wanda zai iya zuwa gaban Yahweh. AT: "Na yi masa addu'a"
Anan Dauda yayi magana game da yadda Yahweh ya ji kukansa na neman taimako. An maimaita ra'ayin don girmamawa. AT: "ya ji roko na"
Kalmomin "girgiza" da "rawar jiki" suna da ma'ana abu ɗaya kuma suna ƙarfafa yadda ƙasa ta girgiza. AT: "ƙasar ta yi gaba da gaba" ko "ƙasa ta yi sama da ƙasa" ko "an sami girgizar ƙasa mai ƙarfi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "harsashin duwatsu kuma ya girgiza ya girgiza"
Dauda yayi maganar Yahweh kamar yana hura wuta. Wannan hoton yadda Allah yayi fushi ne.
Kalmar "ya" tana nufin Yahweh.
Kodayake Yahweh bashi da ƙafa a zahiri, Mai Zabura ya bashi halayen mutane. AT: "duhu mai kauri yana ƙarƙashinsa"
Anan mai Zabura yayi maganar iska kamar tana da fikafikai kamar mala'ika.
Anan ana maganar duhu kamar alfarwa ce. AT: "Ya sanya duhu sutura" ko "Ya sanya duhu wuri ne ɓoye"
"gizagizai masu nauyi tare da ruwan sama" ko "lokacin farin ciki, duhu mai duhu"
Muryar Yahweh ta yi kama da tsawa.
Duk waɗannan sassan suna da ma'ana iri ɗaya.
"ka aike su ta hanyoyi daban-daban"
Waɗannan jimloli guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sannan hanyoyin ruwa suka bayyana kuma kasan tekun ya bayyana; kun fallasa tushen duniya"
Kodayake Allah ba shi da halayen mutum kamar yadda aka bayyana a nan, wannan yana nuna ƙarfinsa mai girma. Ana magana game da iska a nan kamar tana zuwa kamar babbar iska daga hancin Allah.
Kalmar "ya" a cikin waɗannan ayoyin tana nufin Yahweh.
Anan mai Zabura yayi magana game da haɗarin abokan gabansa kamar babbar igiyar ruwa ko ruwa mai ƙarfi, wanda Yahweh ya cece shi daga gare su.
Anan "Su" yana nufin abokan gaba masu ƙarfi a cikin aya ta 17.
Cikakken sunan "damuwa" za a iya bayyana shi azaman sifa ne. Cikakken sunan "tallafi" ana iya bayyana shi a matsayin "mai kariya." AT: "Makiya masu ƙarfi sun kawo mani hari a ranar da na wahala, amma Yahweh ya kiyaye ni"
Anan samun hannaye masu tsabta yana nuna rashin laifi daga aikata ba daidai ba. AT: "Ban kasance mara laifi ba" ko "ayyukana sun yi daidai"
Ana magana akan dokokin Yahweh kamar dai sune hanyoyin da mutum zai bi. AT: "Na yi biyayya ga dokokin Yahweh"
Anan ana magana da mugunta kamar mutum ya bar hanya madaidaiciya kuma ya ɗauki hanyar da ba daidai ba. AT: "ba ku aikata mugunta ba da juya baya ga Allahna"
"sun shiryar da ni" ko "Na tuna"
"mara laifi a cewarsa"
"Ban yi zunubi ba"
Anan "aminci" ť na nufin aikata abin da Allah ya umurce mutum yayi. Kuna iya bayyana wannan a sarari. AT: "ga waɗanda suke biyayya da dokokinka da aminci" ko "ga waɗanda suka cika alkawarinku da aminci"
"kun yaudare duk wanda baya gaskiya"
Wannan salon magana yana nufin waɗanda ke da girman kai. AT: "waɗanda ke alfahari"
Marubucin yayi maganar kasancewar Yahweh kamar haske ne. Wadannan jimlolin suna da ma'ana iri daya.
"Domin da taimakonku zan iya tsallake kowace matsala"
Garkuwa tana kare soja. Dauda yayi magana kamar Allah garkuwa ne yana kare shi. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Zabura 3: 3. AT: "Kai, Ya Yahweh, ka kiyaye kamar garkuwar duk wanda ya nemi mafaka a gare ka"
Amsar da aka bayar ba kowa bane. AT: "Yahweh ne kawai Allah! Allahnmu kaɗai ne dutse!"
Anan Dauda yayi magana game da rayuwar da ke faranta wa Allah rai kamar ana ɗora shi a kan madaidaiciyar hanya. AT: "yana sa marar laifi ya yi rayuwa ta adalci"
Wannan yana nufin bawa mutum damar yin sauri. AT: "yana sa ni gudu da sauri sosai"
A barewa ne musamman sauri da kuma barga a cikin duwatsu.
Anan "hannayena" yana nufin mutum. AT: "Yana horar dani" ť
Anan marubucin yayi maganar kariyar Allah kamar garkuwa ce. Cikakken sunan "ceto" ana iya bayyana shi da kalmar "ajiye." AT: "kariyarka kuma ka cece ni"
Marubucin yayi magana game da amincin da Allah ya tanadar masa kamar wani wuri ne mai fadi da zai tsaya. Anan "ƙafafuna" suna wakiltar mutumin. AT: "wuri ne mai aminci gareni"
Anan "ƙafafuna" yana nufin mutum. Marubucin ya yi maganar amincin kariyar Allah kamar yana tsaye ne a wurin da ba zai zame ba ko ya faɗi. AT: "Ban zame ba" ko "Ina cikin aiki sosai"
"Na murkushe su" ko "Na farfasa su gunduwa gunduwa"
Wannan karin magana yana nufin mai Zabura ya ci abokan gabansa. AT: "Na ci su duka"
Anan mai Zabura yayi maganar kayen abokan gaba kamar yana tsaye akansu. AT: "kun kayar dani saboda ni"
Wannan yana wakiltar Allah ya ba Dauda nasara akan abokan gaba. AT: "Kun ba ni nasara a kan maƙiyana"
Wannan yana nufin Yahweh bai ba da wani taimako ba. AT: "amma bai taimaka musu ba"
An kwatanta makiya masu zabura da ƙura don nuna yadda aka ci su.
Anan "kai" yana wakiltar mai mulki. AT: "ya nada ni in zama mai mulkin kan al'ummomi da yawa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ya tilasta wa baƙi su durƙusa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "shi dutse na ne kuma ya kamata a yaba masa" ko "mutane su yabi dutsen na"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari mutane su daukaka Allah na cetona"
"Ramawa" na nufin hukunta mutane saboda mugayen ayyukansu. Wannan za a iya sake maimaita shi don cire sunan mara abu "ramuwar gayya." AT: "Allah wanda yake azabtar da mutane saboda munanan abubuwan da suka yi mini"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ya 'yanta ni"
Ana magana game da kariyar Yahweh ga marubuci kamar ya ɗaga marubucin sama don haka maƙiyansa ba za su iya zuwa gare shi don cutar da shi ba. AT: "kun sanya ni a cikin aminci wuri sama"
"wanene ya kawo min hari" ko "wanene ya yi min tawaye"
Ta amfani da kalmomin "sarkinsa," Dauda yana nufin kansa a matsayin sarki.
1Sammai na bayyana ɗaukakar Allah, sararin sama kuma na bayyana ayyukan hannunsa!2A kowacce rana ana fitar da magana; dare bisa dare na bayyana ilimi.3Babu magana ko kalma da aka furta; ba a ji amonsu ba.4Duk da haka maganarsu ta tafi dukkan duniya, jawabinsu kuma har ƙarshen duniya. Ya kafa rumfa domin rana a cikinsu.5Rana kamar ango na taƙama daga kagararsa, kuma kamar ƙaƙƙarfan mutum wanda ke farinciki idan ya ƙosa ya yi tsere.6Rana tana fitowa daga ɗaya gefen zuwa ɗaya tsallaken; ba abin da zai tsere daga zafinta.7Dokar Yahweh cikakkiya ce, tana wartsakar da rai; shaidar Yahweh kuwa abar dogara ce, tana ba da hikima ga masu buƙata.8Ka'idodin Yahweh dai-dai suke, tana sa zuciya ta ji daɗi; umarnin Yahweh na da kyau, yana kawo haske ga idanuwa.9Tsoron Yahweh tsabbatacce ne, tabbatacce ne har abada; dokokin Yahweh gaskiya ne dukkansu dai-dai suke!10Suna da girma da daraja fiye da zinariya, fiye ma da zinariyar da aka tace; sun fi zuma zaƙi, zuman dake ɗigowa daga saƙarsa.11I, ta wurinsu bawanka ya sami gargaɗi; akwai lada mai girma idan an yi biyayya dasu.12Wane ne zai iya rarrrabe kuskuren kansa? Ka tsabtacce ni daga ɓoyayyun laifuffuka.13Ka tsare bawanka kuma daga zunubai marasa kangado; kada ka bari su yi mulki a kaina. Sa'an nan ne zan zama kamili, zan kuma zama mara laifi daga laifuffukana masu yawa.14Ka sa maganar baƙina da tunanin zuciyata su zama abin karɓa a wurinka, Yahweh, dutsena da fansata.
An bayyana sammai kamar mutane ne. AT: "Sammai suna nuna" ko "Sammai suna kama da yadda suke ayyanawa"
An bayyana sararin samaniya kamar dai su malami ne. AT: "Sammai suna nuna mana aikin Allah"
Wadannan kalmomin suna bayyana a fili cewa ayoyi biyun farko kwatanci ne. AT: "Babu ainihin magana ko kalmomin magana; babu wanda ya ji ainihin murya da kunnuwansa"
Za a iya haɗa kalmomin da aka ambata cikin fassarar. AT: "maganganunsu suna zuwa ƙarshen duniya"
Marubucin yayi maganar fitowar rana kamar ango. AT: "Rana kamar angon da ke tafiya cikin farin ciki zuwa wurin amaryarsa"
Wannan yana gwama rana da dan wasa don jaddada karfi da hasken rana.
"waɗanda ba su da ƙwarewa" ko "waɗanda ba su koya ba"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "kawowa mutum fahimta" ko 2) "sa mutum ya zama cikin ƙoshin lafiya"
Dokokin Yahweh ana maganarsu kamar ana saya da ɗanɗana. AT: "Idan da za ku iya siyan su, da sun fi zinariya daraja ... idan kun dandana su, za su fi zuma zaƙi"
An fahimci kalmar "mai mahimmanci" from daga jumlar da ta gabata kuma ana iya maimaita ta. AT: "har ma fiye da tamani mai yawa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "sun gargadi bawan ka" ť ko "su gargadi ne ga bawan ka"
Kalmar "su" tana nufin ƙa'idodin adalci na Yahweh.
Wannan karin magana yana nuna bawa kamar ana cire shi daga zunuban da ba ya son aikatawa. AT: "Hakanan, kare bawanka daga yin" ko "Kuma, Ka tabbata cewa ban aikata ba"
An kwatanta zunubai kamar sune sarki wanda zai iya mulkin wani. AT: "Kada ku bari zunubaina su zama kamar sarki wanda yake mulkina"
Waɗannan maganganun da aka ɗauka tare suna bayyana duk abin da mutum ya faɗa da tunani. AT: "abubuwan da na fada da kuma abubuwan da nake tunani game da su"
"karɓi yarda a gabanka" ko "a faranta maka"
1Bari Yahweh ya taimake ka a ranar wahala; bari sunan Allah na Yakubu ya tsare ka,2ya kuma aika taimako daga wuri mai tsarki ya kawo maka tallafi daga Sihiyona.3Bari ya tuna da dukkanbaye-bayenka ya kuma karɓi hadayun ƙonawarka. Selah4Ya biya maka buƙatar zuciyarka, ya kuma cika maka dukkan shirye-shiryenka.5Sai mu yi sowa ta farinciki saboda ka ci nasara, a cikin sunan Allahnmu, zamu ɗaga tutoci. Yahweh zai biya dukkan roƙe-roƙenmu.6Yanzu dai na sani Yahweh zai ceci zaɓaɓɓensa; zai amsa masa daga wurinsa mai tsarki a sama da iko a hannun damarsa wanda ya cece shi.7Waɗansu sun dogara ga karusansu wasu kuma ga dawakansu, amma mu muna kira ga Yahweh Allahnmu.8Su zasu yi tuntuɓe har su faɗi ƙasa, amma mu zamu tashi mu tsaya daram!9Yahweh, ka ceci sarki; ka taimake mu sa'ad da muka yi kira.
"a lokutan wahala" ko "lokacin da kuke cikin matsala"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) a nan "suna" a nufin ta ƙarfin Allah. AT: "mayarfin Allah na Yakubu ya kiyaye ku" ko "Allah na Yakubu ya kiyaye ku da ikonsa" ko 2) a nan "suna" a nufin ta Allah kansa. AT: "Allah na Yakubu ya kiyaye ku"
Ana magana akan taimakon Allah daga tsarkakakken wuri kamar Allah yana aiko da taimako. AT: "bari Yahweh ya taimake ku daga tsattsarkan wurinsa"
Jumlar "kira zuwa zuciya" a hanya ce ta faɗar "tuna." Baya nufin Allah ya manta. Yana nufin la'akari ko tunani. AT: "Bari ya tuna"
Anan "zuciya" tana nufin mutum duka. Cikakken sunan "so" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "abin da kuke so" ko "abin da kuke so"
Cikakken sunan "tsare-tsaren" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "zai iya taimaka muku don cim ma duk abin da kuka shirya yi"
Anan "mu" yana nufin mutane. Za su yi murna da nasarar sarki.
Anan "suna" yana wakiltar girma ko suna. AT: "don girmama Allahnmu" ko "don darajar Allahnmu"
"ya baku duk abin da kuka nema daga gareshi"
Anan "karusai" da "dawakai" suna wakiltar sojojin sarki.
Anan "mu" yana nufin sarki da mutanensa.
Waɗannan jumlolin guda biyu ma'anarsu ɗaya ce. Duk waɗannan suna tsaye don nasara a yaƙi.
Zai yiwu fassarorin su ne 1) mutane suna roƙon Allah ya kare sarki ko 2) sarki ya ci gaba da magana game da kansa a cikin mutum na uku.
1Sarki na yi farinciki cikin ƙarfinka, Yahweh! Babu iyaka ga farincikinsa daga cikin ceton da ka tanada!2Ka biya masa buƙatar zuciyarsa baka kuma hana masa roƙon leɓunansa ba. Selah.3Gama ka kawo masa albarku masu wadata; ka sanya bisa kansa kambi na tsabar zinariya.4Ya nemi rai daga gare ka; ka bashi; ka bashi tsawon kwanaki har abada abadin.5Darajarsa na da girma sabili da nasarar ka; ka ɗibiya masa daraja da ɗaukaka.6Gama ka bashi madawwaman albarku; ka sashi jin daɗi da farinciki da ke a gabanka.7Gama sarki yana dogara ga Yahweh; ta wurin alƙawarin amincin Maɗaukaki ba zaya jijjigu ba.8Hannunka zaya kama dukkan maƙiyanka; Hannunka na dama zaya kama waɗanda suka ƙi ka.9A lokacin hasalarka; zaka ƙona su sarai kamar daga cikin tanderu mai ƙuna. Yahweh zai haɗiye su cikin hasalarsa, kuma wutar za ta cinye su.10Zaka hallakar da zuriyarsu daga ƙasar kuma zuriyarsu daga cikin 'yan adam.11Gama sun shirya yi maka mugunta; sun tsiro da shiri wanda ba za su iya yin nasara ba!12Gama za ka sa su koma da baya; zaka jã kwarinka a fuskarsu.13Ka ɗaukaka, Yahweh, cikin ƙarfin ka; zamu raira waƙa mu kuma yaɓi ikonka.
Ana nuna cewa Allah ya ceci sarki daga abokan gaba. Cikakken sunan "ceto" za'a iya bayyana shi azaman kalma. AT: "saboda kun cece shi daga abokan gabansa"
"burin zuciyarsa." Anan “zuciya” tana nufin mutum dukka. AT: "burinsa" ko "abin da yake fata"
"ba su ƙi shi ba." Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "kun ba shi"
Cikakken sunan "albarka" ana iya bayyana shi azaman "albarka" ko "kyawawan abubuwa." AT: "kun albarkace shi ƙwarai" ko "kuna ba shi kyawawan abubuwa da yawa"
Sanya kambi a kan mutum alama ce ta sanya shi sarki.
Cikakken sunan "rai" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "Ya nemi ku sa shi ya rayu na dogon lokaci; ku kuka sa hakan ya faru"
"Ka sanya masa ɗaukaka da ɗaukaka." Ana faɗar da sarki ya zama mai wadata da iko kamar ana maganar ɗaukaka da ɗaukaka abubuwa ne da aka ɗora masa. AT: "kun sanya shi mai wadata da iko"
"murnar kasancewa a gabanka" ko "farin cikin da ke zuwa daga gareka kasancewa kusa da kai"
Cikakken sunan "aminci" za a iya fassara shi azaman sifa. AT: "saboda Maɗaukaki mai aminci ne ga alƙawarinsa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba wanda zai cire shi a matsayin sarki"
Wannan yana nufin abu ɗaya dai-dai da ɓangaren farko na jumlar. Ya jaddada cewa Allah zai ba sarki iko ya tsayar da maƙiyansa. (Duba: figa_parallelism)
"Lokacin da kayi fushi ka fara aiki"
Duk sassan jumlar suna nufin abu guda. Ana maganar Yahweh gaba ɗaya da hallaka maƙiyansa kamar hasalarsa wuta ce da ta ƙone maƙiyansa gaba ɗaya.
"in yi maka sharri"
Wannan hanya ce ta faɗar cewa Allah da sarki zasu ci abokan gaba a yaƙi.
Wannan yana nuna cewa a zahiri yana harba kibiyar da ke cikin abokan gaba.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Yahweh, nuna mana cewa kai kana da ƙarfi sosai" ko 2) "Yahweh, saboda kana da ƙarfi za mu ɗaukaka ka"
Kalmomin "raira" da "yabo" suna da ma'anoni iri ɗaya. Anan kalmar “iko” tana wakiltar Allah da ikonsa. AT: "tare da rera waka za mu yabe ku saboda kuna da iko"
1Allahna, Allahna, me yasa ka yashe ni? Me yasa ka yi nisa daga ƙubutar da ni kuma kayi nisa daga muryata ta azaba?2Allahna, na yi kuka da tsakar rana, amma baka amsa mani ba, da dare kuma ban yi shuru ba!3Amma kai mai tsarki ne; kana zaman sarki tare da yabon Isra'ila.4Iyayenmu sun dogara gare ka; sun dogara gare ka, ka kuma ƙubutar da su. Sun yi kira gare ka an kuma ƙuɓutar da su.5Sun dogara gare ka basu kuma kunyata ba.6Amma ni tsutsa ne ba mutum ba, abin kunya ga "yan adam da kuma abin raini ga mutane.7Dukkan waɗanda suka ganni suka cakune ni; suka yi mani haibaici; suka kaɗa mani kai.8Suka ce, "Ya dogara ga Yahweh; bari Yahweh ya kuɓutar da shi. Bari ya kuɓutar da shi, gama yana fahariya da shi."9Gama ka fito dani daga mahaifa; ka sa in dogara gare ka a sa'ad da nake shan nono wurin mahaifiyata.10Tun daga mahaifa aka jefo ni gare ka; kai Allahna ne tun daga mahaifar mahaifiyata!11Kada ka yi nisa dani, gama damuwa na kusa; babu wani mai taimako.12Bajimai masu yawa sun kewaye ni; Bajimai masu ƙarfi na Bashan suna zagaye dani.13Sun buɗe bakinsu da girma gãba dani kamar zaki mai ruri yana yagar abin da ya kama.14An kwararo ni kamar ruwa, kuma dukkan ƙasusuwana sun goce. Zuciyata kamar kitse; ta narke daga cikin cikina.15Ƙarfina ya bushe kaf kamar fasasshiyar tukunya; harshena ya manne sama a bakina. Ka kwantar da ni a cikin ƙurar mutuwa.16Gama karnuka suka zagaye ni; taron masu aikata mugunta suka kewaye ni; suka huda hannuwana da ƙafafuna.17Zan iya ƙirga ƙasusuwana. Suka duba suka kuma zura mani ido.18Suka rarraba tufafina a tsakaninsu, suka jefa ƙuri'a a bisa kayana.19Kada ka yi nisa, Yahweh; ina roƙon ka kayi sauri domin ka taimake ni, ƙarfina!20Ka kuɓutar da raina daga takobi, raina ɗaya daga hannuwan karnukan daji.21Ka cece ni daga bakin zaki; ka kuɓutar dani daga ƙahonni na shanun daji.22Zan furta sunanka ga 'yan'uwana; a tsakiyar taruwar jama'a zan yabe ka.23Ku da kuke tsoron Yahweh, yabe shi! Dukkan ku zuriyar Yakubu, girmama shi! Ku tsaya cik cikin tsoronsa, dukkan ku zuriyar Isra'ila!24Gama baya rena ko yayi banza da wahalar ƙuntattu ba; Yahweh baya ɓoye fuskarsa daga gare shi ba; a lokacin da ƙuntacce yayi kira gare shi, ya ji.25Yabona zai zama sabili da kai a cikin babban taron jama'a; Zan cika wa'adina a gaban waɗanda ke tsoron sa.26Tsanantattu za su ci su ƙoshi; Waɗanda suka nemi Yahweh zasu yabe shi. Bari zukatanku su rayu har abada.27Dukkan mazamnan duniya zasu tuna su kuma juyo ga Yahweh; dukkan iyalan al'ummai zasu durƙusa a gabanka.28Gama mulki na Yahweh ne; shi yake mulki bisa al'ummai.29Dukkan mawadatan mutanen duniya za su yi buki su kuma yi sujada; dukkan su masu gangarawa zuwa turɓaya zasu durƙusa a gabansa, su waɗanda baza su iya adana rayyukansu ba.30Tsara mai zuwa zata yi masa hidima; zasu gaya wa tsara ta gaba game da Ubangiji.31Zasu zo su kuma yi magana game da adalcinsa; zasu faɗi abin da yayi ga mutanen da ba a haife su ba.
Marubucin yayi amfani da tambaya don jaddada cewa yana ji kamar Allah ya yashe shi. Zai iya zama mafi kyau a bar wannan azaman tambaya. Hakanan za'a iya fassara shi azaman bayani. AT: "Allahna, Ina jin kamar ka yashe ni!"
Har ila yau marubucin ya yi amfani da tambaya don jaddada cewa yana jin kamar Allah ya yi nesa da shi. Zai iya zama mafi kyau a bar wannan azaman tambaya. Hakanan za'a iya fassara shi azaman bayani. AT: "Kun yi nesa da cetona kuma ba ku da nisa daga kalmomin baƙin cikina!"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Har yanzu ina magana"
"yabon Isra'ila sune kursiyin da kake zaune a matsayin sarki." An bayyana yabon Isra’ila kamar suna kursiyi ne wanda Allah zai zauna ya yi mulki a kansa, ko kuma gidan da Allah zai zauna a ciki. AT: "kai sarki ne kuma mutanen Isra'ila sun yaba maka"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "kun cece su" ko "kun yi musu abin da suke buƙatar ku yi"
Marubucin yayi magana kansa kamar yayi tsutsa. Wannan ya nanata cewa yana ganin ba shi da daraja ko kuma mutane suna ɗaukarsa kamar ba shi da daraja. AT: "Amma dai kamar ni tsutsa ne ba mutum ba"
Duk waɗannan kalmomin suna nufin abu ɗaya ne. Za'a iya bayyana kalmar "mutane suka raina" a cikin tsari mai aiki. AT: "kowa yana ganin ni ba komai bane kuma mutane suna ƙina"
Mutanen suna faɗin wannan ne don su yi wa marubucin ba'a. Ba su gaskanta da gaske cewa Yahweh zai cece shi ba.
Wannan wata hanya ce ta faɗi "kun sa aka haife ni."
Kalmar "an jefa" hanya ce ta faɗi cewa Yahweh ya kula da shi kamar dai Yahweh ya ɗauke shi a matsayin ɗansa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ya zama kamar kun karɓe ni daidai lokacin da aka haife ni"
"tun kafin a haifeni"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Ku zo kusa da ni"
Marubucin yayi magana ne game da makiyansa kamar bijimai. Wannan yana jaddada yadda maƙiyansa suke da haɗari da ƙarfi. AT: "Ina da makiya da yawa kuma suna kama da bijimai waɗanda ke kewaye da ni; sun zama kamar bijimai masu ƙarfi daga Bashan da suka kewaye ni"
Marubucin yayi magana game da abokan gabansa kamar zakuna wadanda bakuna a shirye suke su cinye shi. Makiyansa na iya yin karya don bata masa suna. Ko kuma suna iya yi masa barazana da farmaki.
Marubucin yayi magana game da jin kasalar gaba ɗaya da rauni kamar ana zubo ruwa daga tulun.
Marubucin yayi magana game da jin rauni kamar dai ƙarfinsa kamar busassun tukwane ne wanda zai iya karyewa cikin sauƙi.
Mai yiwuwa ga "ƙurar mutuwa" su ne 1) yana nufin mutum ya juya zuwa ƙura bayan sun mutu. AT: "Kuna gab da barin ni in mutu kuma in zama turbaya" ko kuma 2) hanya ce ta magana game da kabari, wanda ke nufin Allah ne ke sa marubucin ya mutu. AT: "Kun sanya ni a kabarina"
Marubucin yayi magana akan abokan gaba kamar karnuka. Makiyansa suna zuwa kusa da shi kamar yadda karnukan daji suke yi wa dabba mai mutuwa. AT: "Maƙiyana kamar karnukan da suka kewaye ni"
"gungun masu aikata mugunta" ko "gungun masu aikata mugunta"
Wannan yaci gaba da kwatancin kare. Marubucin yana magana ne game da abokan gaba kamar karnuka ne masu cizon hannu da kafafunsa da haƙoransu.
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Kasance kusa sosai" (Duba: fig_litotes)
Anan "ƙarfi" yana wakiltar Yahweh wanda ya ba shi ƙarfi. AT: "ku da kuke ba ni ƙarfi"
Anan “kurwa” tana nufin mutum duka. AT: "Ka cece ni"
"rayuwata mai tamani" ko "rai daya tilo da nake da shi"
"Zan sanar da kai sunan ka." Anan “suna” yana nufin halayen Allah ko kuma suna. AT: "Zan yi magana game da halayenku"
"lokacin da ni da 'yan uwana Isra'ilawa muka taru" ko "lokacin da' yan'uwana masu bautar Yahweh suka kewaye ni"
Duk waɗannan suna nufin rukuni ɗaya ne na mutane.
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) bai raina masu wahala ba saboda yana wahala ko 2) bai raina wahalar mai wahala ba
Ɓoye fuskokin mutum ga wani yana wakiltar watsi da shi. AT: "bai juya hankalinsa daga gare shi ba" ko "bai yi biris da shi ba"
Wannan yana nufin sadaukarwa da marubucin ya yi alkawarin miƙa wa Allah.
Wannan yana nufin abincin zumunci wanda ke faruwa bayan marubucin ya miƙa wa Allah hadayu waɗanda ya alkawarta. Zai gayyaci waɗanda suke wahala su ci naman hadayarsa.
Anan “zukata” suna wakiltar mutum duka. AT: "Za ku rayu har abada"
Farawa don yin biyayya da Yahweh ana magana ne kamar mutane suna juyawa zuwa ga Yahweh a zahiri. AT: "zan tuna da Yahweh kuma mu yi masa biyayya"
"Gama mulki na Yahweh ne." Anan “mulki” yana wakiltar sarautar Allah a matsayin sarki. AT: "Gama Yahweh sarki ne"
Anan “al’ummai” suna wakiltar mutanen ƙasashe. AT: "yana mulkin mutanen al'ummai"
Dukkansu jimlolin suna nufin rukuni ɗaya. Dukkansu suna nufin dukkan mutane saboda dukka mutane zasu mutu.
Anan "Zamani" yana wakiltar mutanen tsara ne. Kalmomin "mai zuwa" yana magana ne game da wani lokaci mai zuwa kamar wani abu ne wanda yake tafiya kuma ya iso wani wuri. AT: "Mutane a cikin al'ummomi masu zuwa"
"game da Yahweh" ko "game da abin da Yahweh ya yi"
1Yahweh makiyayina ne; ba zan rasa komai ba.2Yana sa ni in kwanta a cikin korayen makiyayu; yana bi da ni kurkusa da kwantaccen ruwa.3Ya maido da raina; yana bishe ni ta tafarku madaidaita domin sunansa.4Ko da ina tafiya ta cikin kwari na inuwa mafi duhu, ba zan ji tsoron cutarwa ba tun da kana tare da ni; sandarka da kerenka na ta'azantar da ni.5Ka shirya teburi a gabana a fuskar maƙiyana; ka shafe kaina da mai; ƙoƙona ya cika har yana zuba.6Tabbas nagarta da amintaccen alƙawari zasu bi ni dukkan kwanakin raina; zan kuma zauna a cikin gidan Yahweh na lokaci mai tsawo sosai!
Marubucin yayi magana game da Yahweh kamar makiyayi. Wannan ya nanata yadda Allah yake kulawa da mutane kamar yadda makiyayi yake kulawa da tumakinsa. AT: "Yahweh kamar makiyayi ne a gareni" ko "Yahweh yana kula da ni kamar yadda makiyayi ke kula da tumakinsa"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Ina da duk abin da nake buƙata"
Marubucin yana magana ne game da kansa kamar tunkiya, kuma yana magana game da Yahweh kamar makiyayi. AT: "Yana ba ni hutawa kamar makiyayi wanda ke jagorantar tumakinsa don hutawa a cikin makiyaya masu ciyayi"
Marubucin yana magana ne game da kansa kamar tunkiya, kuma yana magana game da Yahweh kamar makiyayi. AT: "yana tanadar min da abin da nake buƙata kamar makiyayi wanda ke jagorantar tumakinsa a gefen ruwa mai nutsuwa"
Wannan yana nufin Allah yana sanya mutum mai rauni da gajiya ya zama mai ƙarfi ya sake hutawa.
Nuna wa mutum yadda zai rayu a hanyar da za ta faranta wa Allah rai ana maganarsa kamar makiyayi ne da ke nuna tunkiya madaidaiciyar hanyar da za ta bi. AT: "Ya nuna min yadda ake rayuwa dai-dai"
Marubucin ya bayyana mutumin da yake fuskantar mummunar matsala kamar tunkiya da ke tafiya cikin kwari mai haɗari da haɗari. A can tumaki na iya ɓacewa ko dabbar daji ta kai musu hari. AT: "Duk da cewa raina kamar tafiya yake cikin duhu mai haɗari"
Cikakken sunan "cutarwa" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "Ba zan ji tsoron wani abu ya cutar da ni ba"
Sanda da sandar suna wakiltar kariya ne saboda makiyaya suna amfani da su don kare tumakinsu daga haɗari. AT: "Ba na jin tsoro saboda kuna kiyaye ni kamar makiyayi wanda ke kiyaye tumakinsa da sandarsa da sandarsa"
Teburi yana wakiltar biki saboda mutane zasu sanya duk abincin akan teburi.
Ma'ana anan shine marubuci baya damuwa da makiyansa domin shi babban baƙon Ubangiji ne sabili da haka kariya daga cutarwa. AT: "duk da kasancewar magabtana"
A nan kopin giya wanda yake malala yana wakiltar albarkatu masu yawa. AT: "Kun cika ƙoƙona sosai har ya malalo" ko "Kuna ba ni albarkoki da yawa"
Ana magana da cewa Yahweh mai kyau da aminci ga mutum kamar nagarta da amincin alkawari abubuwa ne da suke bin mutum. Sunayen "nagarta" da "aminci" za a iya fassara su azaman sifofi. AT: "Tabbas za ku zama nagari kuma masu aminci a gare ni"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan yana nufin gidan Yahweh na har abada, ko 2) wannan yana nufin haikalin Yahweh a Yerusalem. Idan za ta yiwu, fassara shi don a fahimci duka ma'anonin biyu.
1Ƙasa ta Yahweh ce, da dukkan cikarta, duniyar, da dukkan mazauna cikinta.2Gama ya gina ta a bisa tekuna ya kuma ƙafa ta a bisa koguna.3Wane ne zai haura tudun Yahweh? Wane ne zai tsaya a cikin wurinsa mai tsarki?4Shi wanda ke da hannuwa masu tsarki da kuma zuciya mai tsabta; wanda baya faɗar ƙarya, ba ya kuma yin rantsuwa domin yayi yaudara.5Zai karɓi albarka daga wurin Yahweh da kuma adalci daga Allah na cetonsa.6Haka ya ke ga tsarar masu neman sa, masu neman fuskar Allah na Yakubu. Selah7Tãda kanku, ku ƙyamare; ku tashi, madawwaman ƙofofi, domin Sarkin daraja ya shigo ciki!8Wane ne wannan Sarkin daraja? Yahweh, mai ƙarfi da girma; Yahweh, mai girma cikin yaƙi.9Tãda kanku, ku ƙyamare; ku tashi, madawaman ƙofofi, domin Sarki na daraja ya shigo ciki!10Wane ne wannan Sarkin daraja? Yahweh mai runduna, shi ne Sarkin daraja. Selah
Cikakken sunan "cika" ana iya bayyana shi da kalmar aikatau "cika." AT: "duk abin da ya cika shi"
Anan "kafa shi akan tekun" da kuma "kafa shi akan rafuka" ma'ana abu ɗaya dai-dai. Ibraniyawa na lokacin sun yi imanin cewa ƙasarsu tana da goyan bayan ruwaye da zurfafan koguna. AT: Gama ya kafa harsashin gininsa a kan tekuna kuma ya gina shi a kan zurfin ruwa "
Duk waɗannan tambayoyin suna nufin abu ɗaya ne. Mai magana yana tambaya game da wanda aka yarda ya je ya bauta wa Yahweh.
Wannan yana nufin Tsaunn Sihiyona a Yerusalem.
Kalmar nan “hannu” tana wakiltar abin da mutum yake yi. Don “hannayensa” su zama masu tsabta yana nufin ya yi abin da yake dai-dai. AT: "wanda ya aikata abin da yake dai-dai"
Kalmar "ya" ba tana nufin wani takamaiman mutum ba. Yana nufin wadanda suke da tsarkakakkiyar zuciya da aka ambata a ayar da ta gabata. Ana iya bayyana sunan 'albarka' a matsayin fi'ili. AT: "Yahweh zai albarkace su"
Kalmar "adalci" za a iya bayyana a matsayin "mai adalci." Kuma, "ceto" za'a iya bayyana azaman "ajiyewa." AT: "Allah zai yi masa adalci kuma ya cece shi"
Anan “fuska” tana nufin mutum duka. AT: "Allah na Yakubu"
Hanyoyi guda biyu suna da kamanceceniya da ma'ana. Kalmomin "ƙofofi" da "ƙofofi" suna nuni ga ƙofar haikalin. Marubucin yana magana ne da ƙofofin kamar suna mutum. Mai tsaron ƙofar ne zai buɗe ƙofofin. AT: "Ku buɗe, ku ƙofofin dā" ko "Buɗe waɗannan tsoffin ƙofofin"
Marubucin yayi magana game da Yahweh kamar jarumi ne mai ƙarfin yaƙi.
Hanyoyi guda biyu suna da kamanceceniya da ma'ana. Kalmomin "ƙofofi" da "ƙofofi" suna nuni ga ƙofar haikalin. Marubucin yana magana ne da ƙofofin kamar suna mutum. Mai tsaron ƙofar ne zai buɗe ƙofofin. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Zabura 24: 7. AT: "Ku buɗe, ku ƙofofin dā" ko "Buɗe waɗannan tsoffin ƙofofin"
1A gare ka, Yahweh, na miƙa raina!2Allahna, Na dogara gare ka. Kar ka bari a wulaƙanta ni; kar ka bari maƙiyana suyi farincikin nasara a kaina.3Duk wanda yasa begensa a kan kada shi kunyata bari waɗanda suke aikata makirci babu dalili su ji kunya!4Ka bayyana mani hanyarka, Yahweh; koya mani tafarkinka.5Bishe ni cikin gaskiyarka ka kuma koyar dani, gama kai ne Allah na cetona; na sa begena bisan ka a koda yaushe.6Ka tuna, Yahweh, ayyukanka na tausayi da kuma amintaccen alƙawari; gama sun kasance tun tuni.7Kada kayi tunanin zunubaina na ƙuruciyata ko tayarwata; ka tuna da ni game da amintaccen alƙawarinka sabili da alherinka, Yahweh!8Yahweh yana da nagarta kuma yana da alheri saboda haka yana koyawa masu zunubi tafarki.9Yana bi da kamili ga abin da ke dai-dai kuma yana koya masu hanyarsa.10Dukkan tafarkun Yahweh na dawwamammiyar ƙauna ne da kuma aminci ga waɗanda ke kiyaye alƙawarinsa da kuma umarnansa tabbatattu.11Sabili da sunanka, Yahweh, ka gafarta zunubina, gama yana da girma sosai.12Wane ne mutumin dake tsoron Yahweh? Ubangiji zaya umarce shi a hanyar da zaya zaɓa.13Rayuwarsa zata bi ta hanya mai kyau; kuma zuriyarsa zasu gaji ƙasar.14Abokantakar Yahweh na ga waɗanda ke girmama shi, kuma yana sanar da alƙawarinsa gare su.15Idanuna suna bisa Yahweh koda yaushe, gama zaya ƙuɓutar da sawayena daga tarko.16Ka juyo gare ni kayi mani jinƙai; gama ni kaɗai ne kuma cikin ƙunci.17Damuwoyin zuciyata sun yawaita; ka tsamo ni daga nawayata!18Ka dubi wahalata da kuma matsalolina; ka gafarta zunubaina.19Ka dubi maƙiyana, gama suna da yawa; suna ƙina da ƙiyayya mai zafi.20Ka kare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari a wulaƙanta ni, gama ina samun mafaka a wurinka!21Bari nagarta da aminci su kiyaye ni, gama begena a cikinka ya ke.22Ka kuɓutar da Isra'ila, Allah, daga dukkan wahalolinsa!
Jimlar "ɗaga rayuwata" kwatanci ne. Zai yiwu ma'anoni su ne 1) marubuci ya ba da kansa ga Yahweh, wanda ke nufin ya dogara gaba ɗaya ga Yahweh. AT: "Na ba da kaina gare ku" ko 2) yana yin addu'a da sujada ga Yahweh. AT: "Ina yi muku sujada ina kuma kaunar ku"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kada ku bar magabtana su wulakanta ni"
"Kada ka bari wadanda suke fatan ka su wulakanta." Wulakanci na iya zuwa idan an kayar da abokan gaba. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kada ku bar makiya su ci galaba kan wadanda suke fatan ku"
Duk maganganun guda biyu ma'anarsu daya. An yi maganar Allah yana koya wa mutum yadda ya kamata su nuna kamar yana nuna wa mutum hanyar da mutum zai bi ne.
Jagora da koyarwa ma'anarsu daya, bada umarni. AT: "Ku umarce ni da in gudanar da rayuwata ta hanyar bin gaskiyarku"
Sunayen "tausayi" da "aminci" za a iya bayyana su a matsayin sifofi. AT: "yadda kuka kasance mai tausayi da aminci ga alkawarinku"
Anan "suka" keɓance tausayi da amincin Allah. AT: "domin haka kuke koyaushe"
Cikakken sunan "zunubai" ana iya bayyana shi a matsayin "zunubi." AT: "Kada ku yi tunanin yadda na yi muku laifi tun ina ƙarami"
Ana iya bayyana wannan sifa ɗin mara suna a matsayin sifa. AT: "mutane masu tawali'u" ko "waɗanda ke da tawali'u"
Kalmar "hanyoyi" ishara ce ga hanyoyi. AT: "Yahweh yana ƙaunace mu koyaushe saboda alƙawarinsa kuma amintacce ne koyaushe"
AT: "don Allah ku gafarce ni, don na yi zunubi da yawa"
Wannan tambaya ta gabatar da "mutumin da ke tsoron Yahweh" a matsayin sabon batun. AT: "Zan ba ku labarin mutumin da ke tsoron Yahweh."
Yakan koya wa mutane yadda ya kamata su kasance ana maganarsu kamar Yahweh yana koya wa mutane hanya ko hanyar da za su bi.
"Allah zai sa ya ci gaba" ko "Allah zai sa su ci gaba"
"Yahweh aboki ne ga waɗancan." Wasu suna fassara shi kamar yadda "Yahweh ya yarda da su." Amincewar da ya yi musu ya nuna irin abokantakar da yake da su.
Anan "idanu" suna wakiltar kallo. Ana nuna cewa yana neman taimakon Yahweh. AT: "A koyaushe ina neman Yahweh don ya taimake ni" ko "Kullum na dogara ga Yahweh don ya taimake ni"
Raga tarko ne. Ana maganar mutumin da ke cikin haɗari kamar ana sa ƙafafunsu cikin taru. AT: Zai cece ni daga haɗari "
Anan “zuciya” tana wakiltar motsin mutum. AT: "Na kara shiga damuwa"
"Ka fitar da ni daga wahalata." Wannan yana magana ne game da damuwa kamar dai wuri ne da za'a fito da mutum daga ciki. AT: "Ka cece ni daga wahalata" ko "sauƙaƙa min wahalata"
"sun ƙi ni da ƙiyayya" ko "sun ƙi ni sosai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kada ku bar magabtana su wulakanta ni"
Wannan yana magana ne game da "mutunci" da "daidaito" kamar dai su mutane ne waɗanda zasu iya kiyaye wani mutum lafiya. Wadannan sunaye marasa ma'ana za a iya bayyana su azaman sifofi. AT: "Iya kasancewa mai gaskiya da yin abin da ke daidai ya kiyaye ni" ko "Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, saboda ni mai gaskiya ne kuma ina yin abin da ke dai-dai"
"Ka ceci Isra'ila" ko "Ka fanshi Isra'ila"
1Yi mani shari'a, Yahweh, gama nayi tafiya da aminci; na dogara ga Yahweh babu ja da baya.2Ka gwada ni, Yahweh, ka kuma jaraba ni; jaraba tsabtar cikin raina da zuciyata!3Gama amintaccen alƙawarinka na gaban idanuna, kuma ina tafiya cikin amincinka.4Ban yi hurɗa da mutane marasa gaskiya ba, ko in yi cuɗanya da mutane macuta ba.5Na ƙi jinin taruwar masu aikata mugunta, ban kuma zauna da mugaye ba.6Na wanke hannuna cikin rashin laifi, ina kuma zagaya bagadinka, Yahweh,7domin in raira waƙar yabo da ƙarfi in kuma shaida dukkan ayyukanka masu ban girma.8Yahweh, ina ƙaunar gidan da kake zama, inda ɗaukakarka take!9Kada ka kawar dani tare da masu zunubi, ko raina tare da mutane masu marmarin shan jini,10waɗanda a cikin hannuwansu akwai mugun shiri, kuma hanunsa na dama ke cike da rashawa.11Amma ni, zan yi tafiya cikin aminci; ka fanshe ni ka kuma yi mani jinƙai.12Sawayena suna tsaye a shimfiɗarɗiyar ƙasa; a cikin taruwa zan albarkaci Yahweh!
Kalmar "tafiya" kwatanci ne na hali. AT: "Na nuna hali"
Anan "sassan ciki" da "zuciya" suna nufin dalilai. AT: "gwada ko dalilai na masu kyau ne"
Kalmar "tafiya" kwatanci ne na hali. Cikakken sunan "aminci" za a iya fassara shi da sifa. AT: "Ina gudanar da rayuwata gwargwadon amincinku" ko "Na yi yadda nake yi saboda kun kasance masu aminci"
"tare da waɗanda suka yaudari wasu"
Wannan yana nufin dai-dai yake da sashin farko na jumlar. AT: "kuma bana shiga tare da mutane marasa gaskiya"
"waɗanda suka taru don aikata mugunta"
Wannan yana nuni ga al'adar wankan hannu cikin ruwa don nuna alamar 'yanci daga zunubi da laifi.
Anan “ɗaukaka” yana wakiltar bayyanuwa da ikon Allah, wanda yake kama da haske mai haske sosai. AT: "wurin da mutane zasu iya ganin ɗaukakar hasken kasancewar ku"
"Shafe kai" a nan kwatanci ne na hallaka. AT: "Kada ku halakar da ni tare da masu zunubi"
Kalmar "zubar jini" tana wakiltar son kashe mutane. AT: "mutanen da ke ɗokin zubar da wasu jini" ko "masu kisan kai"
"Tafiya" anan kwatanci ne na hali. AT: "Zan nuna hali mai kyau"
"idan na tara tare da Isra'ilawa zan yabe ka"
1Yahweh ne haske na da cetona; wane ne zan ji tsoro? Yahweh ne mafakar raina; wane ne zai razana ni?2Lokacin da masu aikata mugunta suka taso mani domin su cinye namana, magabtana da maƙiyana suka yi tuntuɓe suka kuma faɗi.3Koda runduna zasu zagaye ni da gãba, zuciyata baza ta ji tsoro ba; koda yaƙi zai taso gãba dani, duk da haka zan kasance da ƙarfin hali.4Abu guda ɗaya nayi roƙo ga Yahweh, zan kuma biɗi wannan; shi ne in zauna a cikin gidan Yahweh dukkan kwanakin raina, in dubi kyawun Yahweh in kuma yi bimbini a cikin haikalinsa.5Gama a ranar wahala zaya ɓoye ni a cikin fukafukansa; a ƙarƙashin inuwar rumfarsa zaya suturce ni. Zaya ɗaukaka ni a bisa dutse mai tsawo!6Sa'an nan za a ɗaukaka kaina fiye da maƙiyana dake kewaye dani, zan kuma miƙa hadayu na farinciki a cikin rumfarsa! Zan raira waƙa in kuma yi waƙoƙi ga Yahweh!7Yahweh ka ji, muryata a lokacin da nayi kuka! Kayi mani jinƙai, ka kuma amsa mani!8Zuciyata na ce da kai, "Nemi fuskarsa!" Na nemi fuskarka, Yahweh!9Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni; kada ka juyar da bawanka daga gare ka cikin fushi! Tun dama kaine mai taimakona; kada ka yashe ni ko kayi banza dani, Allah na cetona!10Koda mahaifina ko mahaifiyata sun yashe ni, Yahweh zaya karɓeni.11Ka koya mani tafarkinka, Yahweh! Ka bishe ni a daidaitacciyar hanya saboda maƙiyana.12Kada ka bayar da ni ga nufin maƙiyana, gama shaidun ƙarya sun tashi gãba dani, suna kuma huro da ta'addanci!13Da mene ne zai faru dani da ba domin na yarda cewa zan ga alherin Yahweh a cikin ƙasar masu rai ba?14Ka jira ga Yahweh; yi ƙarfi, bari zuciyarka ta ƙarfafa! Saurari Yahweh!
Anan “haske” yana wakiltar rai. AT: "Yahweh shine tushen raina"
Wannan tambayar ta nanata cewa babu wanda ya kamata Dauda ya ji tsoro. AT: "Ba zan ji tsoron kowa ba"
Wannan yana magana ne game da Yahweh kamar dai shi ne wurin da mutane zasu iya zuwa don aminci. AT: "Yahweh shine ya tsare ni lafiya"
Wadannan kalmomin ma'anarsu daya. Waɗannan mugaye ne suka kusace shi.
"kodayake sojoji sun kewaye ni" ko "ko da yake sojoji sun kafa alfarwansu kewaye da ni"
Anan “zuciya” tana wakiltar mutum dukka. AT: "Ba zan ji tsoro ba"
"Zan ci gaba da dogaro ga Allah ya taimake ni"
"Na roki Yahweh ya bar ni in yi"
Ana magana game da halayen Allah mai ban al'ajabi kamar yana da kyau na zahiri. AT: "don ganin irin ban mamaki na Yahweh"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "tambayar Allah abin da yake so na yi" ko 2) "Yi tunani sosai game da Allah a cikin haikalinsa."
"a lokacin wahala" ko "lokacin da nake cikin matsala"
Ana maganar Allah mai tsare marubuci daga makiyansa kamar Allah yana sanya shi a kan wani dutse mai tsayi inda makiyansa ba za su iya zuwa gare shi ba.
Wannan yana wakiltar marubucin da ke samun girman kai ko girmamawa lokacin da ya kayar da abokan gabansa. Ana iya bayyana shi cikin tsari mai aiki. AT: "mutane za su girmama ni lokacin da na ci nasara a kan magabtana" ko "Allah zai girmama ni ta hanyar ba ni damar cin nasara kan magabtana"
“Muryar” galibi tana wakiltar mutumin da ya yi magana ko ya yi kira. AT: "Yahweh, ji ni"
Mutumin da ke zuwa haikalin don yin addu'a ga Yahweh ana maganarsa kamar mutum yana neman neman Yahweh. Anan “fuska” tana wakiltar duk na Allah ne. AT: "Zan zo haikalinku in yi addu'a gare ku"
Fuskar a nan tana wakiltar hankalin Yahweh, kuma ɓoye fuska yana wakiltar ƙin wani. AT: "Kada ku ƙi ni" ko "Kada ku daina kula da ni"
"Ko da mahaifina da mahaifiyata za su bar ni." Ba yana cewa da gaske sun yi wannan ba ko kuwa za su aikata shi. Maganarsa ita ce, ko da sun yi haka, Allah ba zai rabu da shi ba.
"Yahweh zai kiyaye ni" ko kuma "Yahweh zai kula da ni"
Yadda mutum ya kamata ya yi magana ana maganarsa kamar wata hanya ce ko hanyar da mutum ya kamata ya bi. AT: "Ku koya mani yadda kuke so in rayu" ko "Koyar da ni in yi abin da kuke so in yi"
Ana magana akan Yahweh mai kiyaye marubuci daga abokan gabansa kamar dai Yahweh yana jagorantar marubuci kan turba madaidaiciya inda ba zai yi tuntuɓe ya faɗi ba. AT: "Kiyaye ni lafiya"
Cikakken sunan "sha'awa" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "Kada ku bar magabtana su yi min abin da suke so"
Ana iya bayyana wannan tambayar ta magana mai ma'ana. AT: "Wani mummunan abu zai faru da ni"
Ana iya bayyana sunan '' kyautatawa '' azaman sifa. AT: "kyawawan abubuwan da Yahweh ke aikatawa"
Anan “zuciya” tana wakiltar mutum duka. AT: "ku zama masu ƙarfin zuciya"
1A gare ka, Yahweh, nayi kuka; dutsena, kada kayi banza da ni. Idan baka amsa mani ba, zan harɗe da waɗanda ke gangarawa zuwa kabari.2Kaji ƙarar roƙona a lokacin da nayi kira domin taimako daga gare ka, a lokacin da na tãda hannuwa na zuwa wurinka mai tsarki!3Kada ka kawar dani tare da masu aikata mugunta, su masu aikata laifuffuka, su dake faɗin alheri da maƙwabtansu da baki amma zuciyarsu cike take da mugunta.4Ka basu dai-dai abin da ayyukansu ya dace dasu da kuma abin da muguntarsu ta wajaba, ka biya su bisa ga aikin hannuwansu ka kuma mayar masu bisa ga ladarsu.5Domin basu gane da ayyukan Yahweh ba ko ayyukan hannuwansa, zaya buga su ƙasa baza a ƙara gina su ba.6Albarka ga Yahweh domin ya ji muryar kukana!7Yahweh ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta dogara gare shi, na kuma sami taimako. Saboda haka zuciyata tayi farinciki ƙwarai, zan kuma yabe shi da raira waƙoƙi.8Yahweh ne karfin mutanensa, kuma shi ne maɓoyar ceto na shafaffensa.9Ka ceci mutanenka ka kuma albarkaci gãdonka. Ka zama makiyayinsu ka kuma ɗauke su har abada.
Ana maganar mutanen da suka mutu kamar suna gangarawa zuwa kabari. AT: "Zan mutu kamar waɗanda suke cikin kabari"
Anan "sauti" yana nufin abubuwan da ya nema. AT: "Ku ji roƙona mai ƙarfi"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) idan Dauda ya rubuta wannan, to wannan yana nufin alfarwar da Allah ya gaya wa mutanensa su kafa don su bauta masa a can, ko kuma 2) idan mutum ya rubuta wannan bayan zamanin Dauda, to marubuci yana magana ne game da haikalin da ke Yerusalem.
Ana magana game da azabtar da mutane kamar Allah yana jan su. A cikin wannan kwatancin Yahweh na iya jan su zuwa kurkuku, ƙaura, ko mutuwa. AT: "Kada ku cire ni"
Anan "hannaye" suna wakiltar abin da mutum yayi. AT: "abubuwan da suka aikata"
"ka basu abinda suka cancanta"
Anan “hannaye” suna wakiltar abin da Yahweh ya yi ko ya halitta. AT: "abin da ya halitta"
Anan "sauti" yana wakiltar abin da marubucin ya faɗi. AT: "ya ji abin da na fada lokacin da na roke shi"
Bayyanar sunan "ƙarfi" ana iya bayyana shi da "ƙarfi." AT: "Yahweh yana ƙarfafa
Bayyanar sunan "ƙarfi" ana iya bayyana shi da "ƙarfi." AT: "Yahweh yana sa mutanensa su yi ƙarfi"
Wannan yana magana ne game da mutanen Allah kamar suna wani abu da Allah ya gada. AT: "mallakinku" ko "waɗanda ke nasa"
Marubucin yayi magana game da Yahweh kamar dai shi makiyayi ne kuma mutanen tumakinsa ne. Makiyayi zai iya ɗaukar tunkiya idan tana bukatar taimako ko kariya. AT: "Ku zama kamar makiyayinsu kuma ku kiyaye su har abada"
1Bada yabo ga Yahweh, ku 'ya'yan Allah! Bada yabo ga Yahweh domin ɗaukakarsa da ƙarfinsa.2Ba Yahweh ɗaukakar da ta cancanci sunansa. Durƙusa ƙasa ga Yahweh cikin jamalin tsarkinsa.3An ji muryar Yahweh har bisa ruwaye; Allah maɗaukaki ya yi tsawa, Yahweh na tsawa bisa ruwaye masu yawa.4Muryar Yahweh na da cikakken iko; Muryar Yahweh mai daraja ne.5Muryar Yahweh na fasa itatuwan sida; Yahweh na fasa gutsu-gutsu itatuwan sida na Lebanon.6Yana sa Lebanon tayi tsalle kamar ɗan maraki da kuma Dutsen Hamon kamar ɗan shanu.7Muryar Yahweh na aikar da harshen wuta.8Muryar Yahweh na girgiza hamada; Yahweh na girgiza hamadar Kadesh.9Muryar Yahweh nasa rimaye su tanƙware tana kuma kware daji a fili. Kowanne a cikin haikali na cewa, "Daukaka!"10Yahweh na zaman sarki a bisa ruwa mai ambaliya; Yahweh na zaman sarki har abada.11Yahweh yana bada karfi ga mutanensa; Yahweh yana albarkatar mutanensa da salama.
Sunayen "ɗaukakar" da "ƙarfi" ana iya bayyana su azaman sifofi. AT: "ku yabi Yahweh saboda yana da ɗaukaka da ƙarfi"
Cikakken sunan "ɗaukakar" za a iya bayyana shi azaman aiki ko sifa. AT: "Ku girmama Yahweh kamar yadda sunansa ya cancanci" ko "Yi shelar cewa Yahweh ɗaukaka ne kamar yadda sunansa ya cancanci"
Muryar Allah ta fi duk sauran sautuka da kara. Ana iya jin sautin akan wasu manyan sautuka kamar sautin ruwaye. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Lokacin da Yahweh yayi magana muryarsa ta fi ta bakin teku ƙarfi" ko kuma "Yahweh ya fi ƙarfi fiye da sautin ruwa"
Wannan yana magana ne game da Allah yana magana kamar sauti na tsawa. Kamar dai sautin aradu, ana iya jin muryar Yahweh a manyan wurare. AT: "Muryar Allah mai ɗaukaka tana da ƙarfi kamar tsawa" ko "Idan Allah mai ɗaukaka ya yi magana sai ya yi ta daka kamar tsawa"
Ana maganar ƙasar Lebanon tana girgiza kamar ana kiran ɗan maraƙi tsalle. Wannan yana nanata cewa lokacin da Yahweh yayi magana, ƙarfin sautinsa yana girgiza ƙasa. AT: "Ya sa ƙasar Lebanon ta girgiza kamar ɗan maraƙi yana tsalle"
Kalmomin "ya sanya" da "tsallake" ana fahimtar su daga jimlar farko. Za a iya maimaita su a nan. Ana maganar kasan Siriyon girgiza kamar wani saurayi ne da ke tsalle. Wannan yana nanata cewa lokacin da Yahweh yayi magana, ƙarfin sautinsa yana girgiza ƙasa. AT: "yana sanya Sirion tsallake kamar ɗan ƙaramin shanu"
Duk faruwar “murya” anan suna wakiltar Yahweh yana magana. AT: "Idan Yahweh yayi magana sai ya sa walƙiya ta haskaka a sama"
Wannan yana nufin cewa Yahweh yana mulki. AT: "Yahweh yana mulki" ko "Yahweh sarki ne"
A nan “ambaliya” tana nufin ruwan da ya rufe duniya.
AT: "Yahweh ya albarkaci mutanensa ta hanyar sanya su ci gaba da zama lafiya"
1Zan girmama ka, Yahweh, gama ka tã dani sama kuma baka bari maƙiyana sun yi farinciki bisa na ba.2Yahweh Allahna, nayi kuka gare ka domin taimako, ka kuma warkar dani.3Yahweh, ka tsamo raina daga Lahira; ka adana ni da rai kada in gangara ƙasa zuwa kabari.4Raira yabbai ga Yahweh, ku amintattunsa! Ku bada godiya a lokacin da kuka tuna da tsarkinsa.5Gama fushin sa na lokaci kaɗan ne; amma tagomashinsa na har abada ne. Kuka na zuwa da dare ne, amma farinciki na zuwa da safe.6Da ƙarfin hali nace. "Ba zan jijjigu ba."7Yahweh, da tagomashinka ka kafa ni kamar ƙaƙƙarfan tsauni; amma daka ɓoye fuskarka, na shiga damuwa.8Nayi kira gare ka, na kuma nemi tagomashi daga wurin Ubangijina!9Wacce riba ce ke cikin mutuwata, idan na gangara cikin kabari? Ko turɓaya zata yabe ka? Zata furta tabbatattun amincinka?10Ka saurara, Yahweh, kayi mani jinƙai! Yahweh, ka zama mai taimakona.11Ka juyar da makokina zuwa rawa; ka cire mani tsumma ka kuma sanya mani rigar farinciki.12Yanzu ɗaukakata zata yi maka waƙar yabo kuma ba zata yi shuru ba; Yahweh Allahna, zan yi maka godiya har abada!
Marubucin yayi maganar Allah ne ya tseratar dashi ya kuma tsare shi daga mutuwa kamar Allah ne ya tsamo shi daga rijiya mai zurfi. AT: "kun cece ni"
“Kabari” yana wakiltar mutuwa. AT: "daga mutuwa"
Ana iya bayyana sunayen "godiya" da "tsarki" azaman "godiya" da "tsarki." AT: "Ku tuna cewa Allah mai tsarki ne kuma ku gode masa" ko "Ku tuna da abin da Allah ya yi saboda shi mai tsarki ne kuma ku gode masa"
Ana iya bayyana sunan "ni'ima" wanda ba a fahimta ba azaman sifa ce "kyakkyawa." AT: "amma ya kyautata mana a rayuwarmu dukka"
Kalmar "girgiza" kwatanci ne na shan kashi. AT: "Ba wanda zai ci ni"
Ana maganar tsaron marubuci kamar shi tsauni mai ƙarfi. AT: "kun sanya ni amintacce kamar babban tsauni"
Marubucin yayi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa ba zai da kima a wurin Allah ba idan ya mutu. AT: "Babu fa'ida idan na mutu na gangara zuwa kabari."
Marubucin yayi amfani da waɗannan tambayoyin don ya nanata cewa gawarsa da lalatacciyar jikinsa ba za su iya yabon Allah ba. AT: "Tabbas ƙurar ba za ta yabe ku ba ko ta gaya wa wasu game da amincinku ba."
Al’ada ce Yahudawa suna rawa lokacin da suke farin ciki sosai. Ana iya bayyana sunayen suna "makoki" da "rawa" azaman kalmomin aiki. AT: "Kun sa ni na daina makoki kuma na yi rawa da murna maimakon"
Marubucin yayi maganar farin ciki kamar dai tufa ce da zai iya sanyawa. AT: "ya sa ni farin ciki"
1A cikin ka, Yahweh, na sami mafaka; kada ka barni in wulaƙanta. Ka kuɓutar dani cikin adalcinka.2Ka saurare ni; Ka kuɓutar dani da sauri; ka zama dutsen mafakata, ƙaƙƙarfar maɓoya domin cetona.3Gama kai ne dutsena da kuma mafakata; Saboda haka sabili da sunanka, ka shugabance ni ka kuma bishe ni.4Ka ƙwato ni daga cikin tãrun da suka ɓoye domi na, gama kai ne maɓuyata.5A cikin hannuwanka nake bada ruhuna; zaka fanshe ni, Yahweh, Allah madogarata.6Na ƙi jinin waɗandɑ suke bautawa gumakan banza, amma na dogara ga Yahweh.7Zan yi murna da kuma farinciki cikin amintaccen alƙawarinka, gama ka ga ƙuncina; ka san matsalar raina.8Baka miƙa ni a cikin hannuwan maƙiyana ba. Ka kafa ƙafafuwana a buɗaɗɗen wuri mai faɗi.9Kayi mani jinƙai, Yahweh, gama ina cikin ƙunci; idanuna sun yi nauyi da azaba tare da raina da jikina.10Gama raina yayi nauyi da makoki kuma shekaruna na cike da nishe-nishe. Ƙarfina ya gaza sabili da zunubina, ƙasusuwana suna lalacewa sarai.11Sabili da maƙiyana, mutane sun yi banza dani; maƙwabtana suka gaji da yanayina, kuma waɗanda suka san ni suka tsorata. Waɗanda suka gamu dani a hanya suka gudu daga gare ni.12An manta da ni kamar mataccen mutum wanda babu wanda ke tunaninsa. Ina kama da fasasshiyar tukunya.13Gama na ji raɗe-raɗe masu yawa, labarai masu ban tsoro daga kowanne sashe sa'ad da suke shiri gãba da ni. Sun yi shiri domin su ɗauke raina.14Amma na dogara gare ka, Yahweh; Na ce, "Kai ne Allahna."15Ƙaddarata na cikin hannuwanka. Ka kuɓutar dani daga hannuwan magabtana daga kuma waɗanda suke fafarata.16Bari fuskarka ta haskaka bisa bawanka; ka cece ni cikin amintaccen alƙawarinka.17Kada ka bar ni in wulaƙantu, Yahweh; gama na yi kira gare ka! Bari mugu ya wulaƙanta! Bari suyi shuru a cikin Lahira.18Bari harsuna masu ƙarya suyi shuru su dake magana gãba da mai adalci da renin girma da kuma tozartarwa.19girman alherinka da ka shirya wa masu girmama ka, abin da kake aiwatar wa domin waɗanda suka yi mafaka a cikinka a gaban dukkan 'ya'yan talikai!20A cikin mahallin bayyanuwarka, ka ɓoye su daga makircin mutane. Ka ɓoye su a cikin mahalli daga ta'addancin harsuna.21Mai albarka ne Yahweh, gama ya nuna mani amintaccen alƙawarinsa mai ban mamaki a lokacin da nake a cikin birnin kwanto.22Ko da ya ke na faɗa cikin gaggawata, "An datse ni daga fuskarka," duk da haka ka ji roƙona domin taimako lokacin da nayi kuka gare ka.23Oh, ƙaunaci Yahweh, dukkan ku amintattun mabiya. Yahweh yana tsare amintattu, amma yana sãka wa masu girman kai.24Ku ƙarfafa kuyi ƙarfi, dukkan ku dake dogara cikin Yahweh domin taimako.
Maganar zuwa ga Yahweh don kariya ana magana ne da neman mafaka a gare shi. AT: "Na je gare ka, Ya Yahweh, don kariya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kar ku bari wasu su wulakanta ni"
Jimlar "zama dutsen mafaka na" neman neman kariya ne. Jumla ta biyu ta jaddada magana ta farko.
Kalmomin "jagoranci" da "jagora" ma'anarsu abu ɗaya ne kuma suna ƙarfafa roƙon da Yahweh ya bishe shi. AT: "kai ni inda kake so in je"
Ana maganar marubuci kamar tsuntsu ne da aka kama a cikin ragar da aka ɓoye, kuma yana jiran Yahweh ya 'yantar da shi daga tarkon.
Anan "ruhuna" yana nufin marubuci. AT: "Na sanya kaina"
"kai Allah ne zan iya dogaro"
Duk waɗannan kalmomin suna bayyana ra'ayin cewa Allah ya san matsalolin marubuci.
Anan "ƙafafuna" na nufin marubuci. AT: "Kun saita ni"
Ibraniyawa suna tunanin sararin buɗe sarari a matsayin kwatanci na aminci da yanci. AT: "wurin da nake 'yanci"
Ana amfani da kalmomin “raina” da “jiki” don kwatanta cikakken mutum.
Yankin "ya gaji" ya ɓace, amma ana nuna shi. AT: "shekaruna sun gaji da nishi"
Anan "ƙarfina" yana nufin marubuci. Madadin fassara: "Na zama mai rauni"
Anan "ƙashina" yana nufin lafiyar jikin marubuci. AT: "lafiyata tana ta rauni"
Mutane ba sa tunanin matattu. Marubucin baya tunanin mutane suyi tunanin sa.
"ban tsoro rahotanni daga kafofin da yawa"
Anan “hannunka” yana nufin ikon Yahweh. AT: "Kuna da ikon yanke hukunci kan makomata"
Marubucin yayi magana game da Yahweh yana nuna masa alheri kamar fuskar Yahweh ta haskaka shi. AT: "Ka yi aiki nagari ga bawanka"
"Inã fatan Allah Ya wulãkanta azzãlumai!"
Anan “cikin Lahira” yana wakiltar mutuwa. AT: "Bari su mutu don kada su iya magana"
"waɗanda suka girmama ka ƙwarai"
Maganar zuwa ga Yahweh don kariya ana magana ne da neman mafaka a gare shi. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Zabura 31: 1. AT: "waɗanda suka je wurinku don kariya"
Anan "matsuguni" yana wakiltar wuri mai aminci. AT: "Kuna tanada musu amintaccen wuri"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kun cire ni daga wurinku"
Anan ana iya bayyana "roƙo" tare da fi'ili. AT: "kun ji na nemi taimako"
Anan "biya" wani karin magana ne wanda yake nuni ga horo. AT: "yana baiwa mutanen da ke alfahari duk hukuncin da ya kamace su"
1Mai albarka ne taliki wanda an gafarta masa kurakuransa, wanda aka rufe zunubinsa.2Mai albarka ne mutum wanda Yahweh ba ya lisafta laifi bisansa kuma wanda babu algus cikin ruhunsa.3Da na yi shuru, ƙasusuwana suna lalacewa sa'ad da nake nishe-nishe dukkan yini.4Gama rana da dare hannunka na da nauyi bisana. ƙarfina ya gaza kamar lokacin fãrin kaka.5Sa'an nan na furta zunubi na gare ka, ban kuma ƙara ɓoye laifi na ba. Na ce, "Zan furta kurakuraina ga Yahweh," ka kuma gafarta mani ladar zunubina.6Saboda wannan, dukkan waɗanda ke na allahntaka suna adu'a a gare ka a lokacin gwagwarmaya mai girma. Sa'an nan lokacin da ruwaye masu hauka suka taso, baza su cimma waɗannan mutane ba.7Kai ne maɓuyata; zaka tsare ni daga wahala. Zaka zagaye ni da waƙoƙin nasara.8Zan umarce ka in koya maka hanyar da zaka bi. Zan umarce ka da idanuna a bisanka.9Kada ka zama kamar doki ko kamar alfadari, wanda ba shi da fahimta; sai tare da linzami da ragama domin a bi da su inda ake so su tafi.10Mugu yana da baƙinciki mai yawa, amma amintaccen alƙawarin Yahweh zai zagaye wanda ya dogara gare shi.11Yi murna cikin Yahweh, da farinciki, ku adalai; yi sowa ta farinciki, dukkan ku masu tsabta cikin zuciya.
Waɗannan jimlolin suna da ma'anoni iri ɗaya. Ana iya bayyana su a cikin tsari mai aiki. AT: "wanda Allah ya gafarta masa laifinsa kuma ya rufe zunubinsa"
Anan ana maganar zunubin da aka gafarta kamar wanda aka lulluɓe shi don kada a gani. AT: "wanda aka yi watsi da zunubinsa" ko "wanda aka manta zunubinsa da gangan"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda Yahweh yake ganin ba shi da laifi" ko "wanda ba shi da laifi a bisa ga Yahweh"
Anan “hannu” yana nufin Yahweh. Dukkanin jimlar kain magana ne na nufin "kun wahalar dani." AT: "kun wahalar da ni matuka"
An gwada ƙarfin Dauda da ƙaramin tsire-tsire mai ɗanɗano wanda ya zama ruwan kasa da keɓewa a lokacin rani.
"lokacin da suke cikin babbar matsala."
Ana magana da matsaloli kamar suna ambaliyar ruwa. AT: "To idan matsaloli suka zo kamar ambaliyar ruwa, waɗancan mutane za su sami aminci"
Ana magana da Yahweh kamar dai shi amintaccen wuri ne daga harin abokan gaban marubuci. AT: "Kun kasance kamar wurin da zan iya ɓoye kaina daga maƙiyana"
Wannan magana a bayyane yana nufin cewa kariyar Yahweh ga marubuci shine sanadin waƙoƙin cin nasara. AT: "Saboda ku zan raira waƙoƙin nasara"
Yin magana akan madaidaiciyar hanya ana maganarsa kamar wata hanya ce da ya kamata marubuci ya bi. AT: "yadda ya kamata ku rayu"
Anan “ido na” yana nuni ga hankalin Yahweh. AT: "kuma in ja da hankalina zuwa gare ku" ko "kuma in kula da ku"
Marubucin ya kwatanta mutane da rashin fahimta ga dawakai da alfadarai. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) marubucin yana faɗar kalmomin Yahweh ga masu karatunsa, "Dukku kada ku zama kamar doki ... babu fahimta" ko 2) Yahweh yana magana da marubucin kamar yana magana da gungun mutane ne. (Duba: fig_simile)
Anan "a cikin Yahweh" yana nufin abin da Yahweh ya yi musu. "Ku yi murna saboda abin da Yahweh ya yi"
Anan “zuciya” tana nufin mutum. AT: "mutanen da ke tsaye" (Duba: idiom)
1Yi farinciki cikin Yahweh, ku adalai; Yin yabo ya dace ga adalai.2Kuyi godiya ga Yahweh da molo; yi waƙoƙin yabo gare shi da molo mai tsarkiya goma.3Raira sabuwar waƙa gare shi; ku yi kiɗa da ƙwarewarku kuna raira waƙa tare da farinciki.4Gama maganar Yahweh mai adalci ce, kuma dukkan abin da ya aikata dai-dai ne.5Yana ƙaunar adalci da shari'a. Duniya na cike da amintaccen alƙawarinsa.6Da maganar Yahweh aka hallici sammai, kuma dukkan taurari sun kasance ne ta numfashin bakinsa.7Yana tara ruwayen teku wuri ɗaya kamar tudu; ya ajiye tekuna cikin ɗakunan ajiya.8Bari dukkan ƙasar taji tsoron Yahweh; Bari dukkan mazaunan duniya su tsaya cik a gabansa.9Gama ya yi magana, aka kuma aikata; ya umarta, ya kuma tabbata.10Yahweh yana lalatar da ƙawancen al'ummai; yana mulki akan shirye-shiryen mutane.11Shirin Yahweh ya tsaya har abada, shirye-shiryen zuciyarsa ga dukkan tsararraki.12Mai albarka ce al'ummar da Yahweh ne Allahnta, mutanen da ya zaɓa abin gãdonsa.13Yahweh yana gani daga sama; yana ganin dukkan mutane.14Daga wurin da ya ke zama, yana duban dukkan masu zama cikin ƙasar.15Shi wanda ya ke shirya zuciyarsu dukka yana la'akari da ayyukansu.16Babu sarkin da zai tsira sabili da yawan runduna; jarumi baya tsira ta dalilin ƙarfinsa.17Doki tsaro ne na banza domin nasara; duk da ƙarfinsa, ba zai iya ƙubutarwa ba.18Duba, idanun Yahweh na bisan waɗanda ke tsoronsa, a bisa waɗanda suka dangana bisa amintaccen alƙawarinsa19domin ya kuɓutar da rayukansu daga mutuwa ya kuma kiyaye su da rai a lokacin yunwa.20Muna jiran Yahweh; shi ne taimakonmu da kuma garkuwarmu.21Zuciyarmu tayi farinciki cikinsa, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.22Bari amintaccen alƙawarinka, Yahweh, ya kasance da mu a lokacin da muka kafa begenmu cikinka.
Anan "a cikin Yahweh" yana nufin abin da Yahweh ya yi musu. "Ku yi murna saboda abin da Yahweh ya yi"
"yabon Yahweh ya dace da mutanen kirki"
Anan ana amfani da "madaidaiciya" a matsayin kwatanci don abin da yake gaskiya ne. AT: "Yahweh yana aikata abin da ya ce zai yi koyaushe"
Waɗannan sunayen na ƙila za a iya bayyana su azaman ayyuka. AT: "Yana son yin abin da ke daidai da adalci" ko "Yana son waɗanda suke yin abin da ke daidai da adalci"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ta amfani da maganarsa, Yahweh ya halicci sammai"
Marubucin ya bayyana yadda aka halicci tekuna kamar Allah ne ya sa su a ɗakin ajiya. AT: "yana sanya tekuna a wurinsu, kamar yadda mutum yake sanya hatsi a cikin ma'ajiya" (Duba: figa_metaphor)
A nan "tsaya cikin tsoro" wani karin magana ne da ke nufin "ku firgita." AT: "girmama shi"
Yahweh yana halakarwa" ko "Yahweh na karya"
Kalmar bacewa "tsayawa" ana nuna ta. AT: "tsare-tsaren zuciyarsa suna tsaye ga tsararraki duka"
A nan "al'umma" tana nufin mutanen ƙasar. AT: "Masu albarka ne mutanen ƙasar"
"waɗanda ke bauta wa Yahweh kamar Allah"
A nan "zukata" suna nufin tunanin waɗannan mutane. Marubucin yayi magana game da Yahweh yana shiryar da tunanin mutane kamar shi maginin tukwane ne wanda yake tsara kwano. AT: "yana jagorantar tunaninsu kamar yadda maginin tukwane yake tsara kwano"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Babban runduna ba abin da ke ceton sarki"
Anan "doki" yana wakiltar mafi ƙarfi daga rundunar. AT: "Samun sojoji da dawakai masu ƙarfi ba ya samar da tsaro"
Anan “ido” yana nufin hankalin Yahweh. AT: "Hankalin Yahweh"
A nan “jira” wani karin magana ne da ke nufin amana. AT: "Mun dogara ga Yahweh" ko "Muna fatan Yahweh"
Anan ana magana da Yahweh kamar garkuwa ne wanda ke kare sojoji a yaƙi. AT: "shi ne mataimakinmu kuma yana kiyaye mu kamar garkuwa"
"kamar yadda muke fatan taimakonku"
1Zan yabi Yahweh a dukkan lokaci, Yabonsa zai kasance a bakina koda yaushe.2Zan yabi Yahweh! Bari ƙuntattu su ji su kuma yi farinciki.3Ku yabi Yahweh tare da ni, bari mu ɗaukaka sunansa tare.4Na nemi Yahweh kuma ya amsa mani, ya kuma ba ni nasara bisa dukkan tsorona.5Waɗanda ke duban sa suna haskakawa, kuma fuskarsu ba ta ji kunya ba.6Wannan matsattsen mutum yayi kuka Yahweh kuma ya ji ya kuma cece shi daga dukkan matsalolinsa.7Mala'ikan Yahweh na zagaye waɗanda ke tsoronsa ya kuma ƙubutar da su.8Ku ɗanɗana ku kuma gani cewa Yahweh na da kyau. Mai albarka ne mutum wanda ke ɓuya cikinsa.9Ku ji tsoron Yahweh, ku mutanensa masu tsarki. Babu rashi ga waɗanda ke tsoronsa.10'Ya'yan zakuna wasu lokuttan suna rasa abinci su kuma ji yunwa, amma waɗanda suka nemi Yahweh baza su rasa kowanne abu mai kyau ba.11Ku zo, 'ya'ya maza, ku saurare ni. Zan koya maku jin tsoron Yahweh.12Wanne mutum ne mai biɗar rai ya ke kuma ƙaunar ranaku masu yawa, domin ya ga alheri?13To, sai ka tsare harshenka daga faɗin mugunta leɓunanka kuma daga faɗin ƙarya.14Ka juyo daga barin mugunta ka kuma aikata nagarta. Nemi salama ka kuma bi ta.15Idanun Yahweh suna bisa masu adalci kuma kunnuwansa suna karkatawa zuwa ga kukansu.16Fuskar Yahweh na gãba da waɗanda ke aikata mugunta, domin a datse tunawa da su daga duniya.17Masu adalci sun yi kira Yahweh kuma yana kuɓutar da su daga dukkan matsalolinsu.18Yahweh yana kurkusa da masu karyayyar zuciya, kuma yana ceton waɗanda aka ƙuntatawa a cikin ruhu.19Da yawa suke matsalolin masu adalci, amma Yahweh yana ƙubutar da su daga dukkan su.20Ya kare dukkan ƙasusuwansa, babu ko ɗaya daga cikinsu da za a karya.21Mugunta zata kashe mai mugunta. Waɗanda suka ƙi masu adalci za a hallakar da su.22Yahweh yana ƙubutar da rayukan bayinsa. Babu ɗaya daga cikin waɗanda ke neman mafaka wurinsa da za a kayar.
Anan "a bakina" yana nufin Dauda yana magana game da Yahweh. AT: "Zan yabe shi da ƙarfi"
Fi'ili "yabo" umarni ne ga rukuni. AT: "Kowa ya yabi Yahweh tare da ni"
Anan “dagawa” wani karin magana ne wanda ke nufin ɗaukaka Yahweh. AT: "ku gaya wa mutane girman sa"
Anan "ya nemi Yahweh" yana nufin Dauda yana neman taimakon Yahweh. AT: "Na yi addu'a ga Yahweh" ko "Na nemi Yahweh don taimako"
Anan "fuskokinsu" na nuni ga mutanen da suka dogara ga Yahweh. Hakanan za'a iya bayyana shi a cikin tsari mai kyau. AT: "ba sa jin kunya" ko "suna alfahari"
An yi magana game da nagartar Yahweh a matsayin abin da za a ɗanɗana kuma a gani. AT: "Gwada kuma ku gani cewa Yahweh nagari ne"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Waɗanda ke tsoron sa koyaushe suna da abin da suke buƙata"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "koyaushe suna samun kyawawan abubuwan da suke buƙata"
Amsar a bayyane ga wannan tambayar ita ce "kowane mutum." Ana iya fassara wannan tambayar ta lafazi a matsayin sanarwa. AT: "Kowane mutum yana son rayuwa kuma yana son rayuwa tsawon kwanaki kuma ya sami rayuwa mai kyau"
A nan "harshe" yana nufin mutum dukka. AT: "Saboda haka, kada ku faɗi mugunta"
A nan “leɓɓa” na nufin mutumin da yake magana. AT: "kar kuyi magana da karya"
Anan “idanun Yahweh” suna nuni ne ga lura mai kyau. "Masu adalci" na nufin ga mutanen kirki. AT: "Yahweh yana lura da mutanen kirki"
Anan Yahweh yana wakiltar “kunnuwansa”. Don fuskantarwa zuwa wani abu yana nufin kula da shi. AT: "yana kula da kukansu" ko "yana amsa kukansu"
Wannan sanannen sifa ne wanda ke nufin mutanen da suka karai. Ana magana da baƙin ciki mai zurfi kamar zuciyar mutum ta karye. AT: "mutanen da suke cikin bakin ciki sosai"
Mutanen da suka yi sanyin gwiwa ana maganarsu kamar ana murkushe ruhunsu. AT: "mutanen da suka karai a zuciya"
A nan "duk ƙasusuwansa" na zahiri ne, amma kuma yana nuna cewa Yahweh yana kula da duka mutumin. AT: "Ya tanada masa cikakkiyar kariya, ba zai cutar da shi ta kowace hanya ba"
An bayyana mugunta kamar mutum ne wanda zai iya kashe mutane. AT: "Mugayen ayyukan mugaye zasu kashe su"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai la'ane waɗanda suka ƙi adalai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Hakanan za'a iya bayyana shi a cikin tsari mai kyau. AT: "Yahweh zai gafarta wa duk wanda ya dogara gare shi"
1Yahweh, ka yi gãba da waɗanda ke aiki gãba da ni; ka yaƙi waɗanda ke yaƙi da ni.2Ka ɗauki garkuwarka ƙarama da babba; tashi ka taimake ni.3Yi amfani da mashi da gatarin yaƙin ka gãba da waɗanda ke runtuma ta; ka ce da raina, "Ni ne cetonka."4Bari su waɗanda ke neman raina su ji kunya su kuma faɗi. Bari waɗanda ke shirin cuta na a juyar da su a kuma hargitsa su.5Bari su zama kamar ƙaiƙayi a fuskar isaka, a sa'ad da mala'ikan Yahweh ke korar su.6Bari hanyar su ta duhunta tana kuma zamewa, a sa'ad da mala'ikan Yahweh ke runtumar su.7Babu dalili suka shirya mani tarkonsu; Babu dalili suka haƙa rami domin raina.8Bari halakarwa ta auko masu ba zato. Bari tarkon da suka ɗana ya kama su. Bari su faɗa ciki, ga hallakarsu.9Amma zan yi farinciki cikin Yahweh in kuma yi murna cikin cetonsa.10Dukkan ƙasusuwana za su ce, "Yahweh, wane ne kamar ka, wanda ke ƙuɓutar da ƙuntattu daga waɗanda suka fi ƙarfinsu da kuma matalauta da kuma mabuƙata daga waɗanda ke ƙoƙarin yi masu fashi?"11Shaidu marasa adalci sun tashi; sun yi mani zargin ƙarya.12Sun sãka mani nagarta da mugunta. Ina cike da ɓacin rai.13Amma a lokacin da suke ciwo, na sanya tsummokara; na yi azumi a madadinsu da kaina sunkuye ga ƙirjina.14Na yi tafiya cikin ƙunci domin ɗan'uwana; Na durƙusa cikin makoki domin mahaifiyata.15Amma da nayi tuntuɓe, suka yi murna suka taru wuri ɗaya; suka taru wuri ɗaya gãba da ni, kuma suka bani mamaki. Suka kawo mani farmaƙi babu fasawa.16Da rashin girmamawa samsam suka yi mani ba'a; suka tauna mani haƙoransu.17Ubangiji, har yaushe zaka duba? Ka ƙuɓutar da raina daga farmaƙinsu mai hallakarwa, raina daga zakuna.18Sa'an nan zan gode maka a babban taro mai girma; Zan yabe ka a cikin mutane masu yawa.19Kada ka bar maƙiyana masu ƙarya su yi murna a kaina; kada ka barsu su aiwatar da mugun shirinsu.20Gama basu maganar salama, amma suka shirya maganganun ƙarya gãba da waɗanda ke zaman salama cikin ƙasar.21Sun buɗe bakunansu da girma gãba da ni; suka ce, "Aha, Aha, idanunmu sun gan shi."22Ka gan shi, Yahweh, kada ka yi shuru; Ubangiji, kada kayi nisa dani.23Ka tãda kanka ka kuma farka domin ka kare ni; Allahna da Ubangijina, ka kare bukatata.24Ka kãre ni, Yahweh Allahna, sabili da adalcinka; kada ka bar su suyi murna a kaina.25Kada ka bari su faɗa a cikin zuciyarsu, Aha, mun sami abin da muke nema." Kada ka bar su su ce, "Mun haɗiye shi."26Ka basu kunya ka kuma ruɗar da waɗanda ke niyyar cutar da ni. Bari waɗanda ke cakuna ta a rufe su da kunya da ƙasƙanci.27Bari su dake marmarin kuɓutata suyi sowa ta murna su kuma ji daɗi; bari koyaushe su ce, "Bari Yahweh ya ɗaukaka, shi da ya ke jin daɗi cikin wadatar bawansa."28Sa'an nan zan faɗi game da shari'arka in kuma yabe ka dukkan yini.
Marubucin ya bayyana Allah a matsayin jarumi wanda ke shirya kansa don yaƙi.
Wannan yana nufin marubuci. AT: "ku ce mini"
Ana iya bayyana wannan ba tare da jimla ba. AT: "Ni ne mai cetonka" ko "Zan cece ku"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari Yahweh ya kunyata kuma ya tozarta waɗanda suke neman raina"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki.AT: "Bari Yahweh ya juya ya kunyata waɗanda ke shirin cutar da ni"
Ana maganar hallaka kamar wata dabba ce mai haɗari da za ta auka musu ba zato ba tsammani. AT: "Bari a hallaka su kwatsam" ko "Ka ba su mamaki saboda ka halakar da su kwatsam"
Wannan kwatancen iri ɗaya ne kamar yadda yake a aya ta 7. Yanar gizo an yi niyyar kama marubuci. AT: "Bari su faɗa cikin ramin da suka tono mini"
Amsar a bayyane ga wannan tambaya ita ce, babu wanda yake kama da Yahweh. AT: "Yahweh, babu wani kamarku ... waɗanda ke ƙoƙarin ɓata su."
Wannan magana ne wanda ke nufin sun mayar da mugunta a madadin kyawawan abubuwan da suka samu. AT: "Saboda kyawawan abubuwan da na yi musu, suna aikata min abubuwa marasa kyau"
"Na nuna cewa ina bakin ciki"
Marubucin ya yi baƙin ciki kamar mahaifiyarsa ta mutu. AT: "Na yi baƙin ciki kamar mahaifiyata ta mutu"
AT: "Tare da mutanen banza sun yi min ba'a" ko "Ba tare da girmamawa ba sai suka yi min ba'a"
Wannan tambayar tana nuna cewa marubucin yana son Allah ya daina duban sa kawai kuma ya fara taimaka masa. AT: "har yaushe za ku kalle su kawai suna yin wannan?" ko "yaushe zaka taimake ni?"
"Kada ka bari magabtana, wadanda suke yin karya a kaina,"
"wadanda suke zaune lafiya a kasarmu"
Dalilin da yasa suke buda bakinsu shine su tuhumi marubucin. AT: "Suna yi min ihu don su zarge ni"
Wannan baya nufin Allah yana bacci. Marubucin yana son Allah ya shiga tsakani. Duk kalmomin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna jaddada gaggawar wannan buƙatar. AT: "Ina jin kamar kuna barci! Ku farka"
"kar ka bari su yi murna saboda ina wahala"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari ku sa sutura da kunya ku wulakanta waɗanda ke fifita kansu a kaina"
Anan "tabbatarwa" yana nufin Yahweh na shela ko hukunta mai zabura mara laifi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari mu yabi Yahweh"
1Mugun mutum yana zancen kurakuransa daga cikin zuciyarsa, babu tsoron Allah a idanunsa.2Gama yana yiwa kansa ta'aziya, da tunanin cewar zunubansa ba zasu tonu ba ko kuma a ƙi su.3Maganganunsa na zunubi ne da yaudara; ba ya son ya zama mai hikima ya kuma aikata nagarta.4A lokacin da ya ke kwance a gado, yana shirya yadda zai yi zunubi; ba ya ƙin mugunta.5Amintaccen alƙawarinka, Yahweh, na kaiwa har zuwa sammai; amincinka na kaiwa zuwa cikin giza-gizai.6Adalcinka na kama da duwatsun Allah; shari'unka na kama da manyan zurfafa. Yahweh, ka kare talikai da dabbobi.7Yaya darajar amintaccen alƙawarinka ya ke, Allah! Bil'adama na fakewa a ƙarƙashin inuwar fukafukanka.8Zasu ƙoshi daga yalwar abincin gidanka; zaka sa su sha daga cikin koginka mai manyan albarku.9Domin a gare ka akwai maɓulɓular rai; cikin haskenka zamu ga haske.10Ka kawo gare ni amintaccen alƙawarinka cikakke ga waɗanda suka san ka, kariyarka zuwa ga kamilai a zuci.11Ka da ka bar ƙafafun mai girman kai shi zo kusa dani. Ka da ka bar hannun mugaye su kore ni da nisa.12A can mugaye suka faɗi; aka buga su ƙasa basu kuma iya tashi ba.
Anan "zuciya" tana nufin yanayin cikin mutum. AT: "daga cikin zuciyarsa"
"ya fi son yin imani" ko "yana son yin tunani"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ba zai gano ya ƙi jinin zunubinsa ba"
Ana ambaton ayyukan zunubin mutum kamar yana tafiya a kan hanyar da ke mugunta. AT: "yana fara aikata mugunta"
Anan "mugunta" za'a iya bayyana ta wani nau'i. AT: "baya ƙin mugunta"
Ana maganar girman alkawarin Allah mai aminci kamar ana magana ne da shi kamar abu ne wanda ya kai sama. Cikakken sunan "aminci" za a iya fassara shi azaman sifa. AT: "amincin alkawarinku ... yana da girma ƙwarai" ko "Ku ... ku masu aminci ne ga alkawarinku kamar yadda sammai suke sama da ƙasa"
Kalmar nan "mai daraja" tana nufin yadda marubuci yake daraja amincin alkawarin Yahweh sosai. Cikakken sunan "aminci" za a iya fassara shi azaman sifa. AT: "Ina matukar girmama yadda kuke aminci ga alkawarinku"
Cin abinci da yawa a matsayin baƙi a cikin gida kwatanci ne na Allah wanda yake biyan duk mutanensa da suke buƙata. AT: "Za su sami duk abin da suke buƙata saboda za ku ba su" ko "Kuna da yawa da za ku bayar, kuma za ku wadata su da duk abin da suke buƙata"
Akwai maganganu biyu a nan. Ana magana akan yawan ni'imomin Allah kamar ruwa ne a cikin kogi mai gudana. Hakanan, waɗanda suka sami waɗancan albarkatu ana maganarsu kamar suna shan su kamar ruwa. AT: "ni'imominku masu daraja kamar kogi ne wanda zaku bar su su sha daga ciki"
Cikakken sunan "tsaro" za'a iya bayyana shi azaman kalma. "A ci gaba" an nuna daga jumlar da ta gabata. AT: "Ci gaba da kare masu karkatacciyar zuciya"
Anan "ƙafa" da "hannu" suna nufin mutane mugaye. Wadannan ba takamaiman maza bane. Wannan yana nufin mugayen mutane gaba ɗaya. AT: "mutane masu girman kai ... mugayen mutane"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kun rusa su" ko "kun hallakar da su"
1Kada ka damu da masu mugunta; kada ka ji ƙyashin waɗanda ke ayyukan rashin adalci.2Gama zasu bushe da wuri kamar ciyawa, su kuma yanƙwane kamar korayen tsire-tsire.3Ka dogara ga Yahweh kuma ka yi abin da ke nagari; ka zauna a ƙasar ka yi kiwo cikin aminci.4Sa'an nan ka yi murna da al'amuran Yahweh, kuma zai biya maka buƙatun zuciyarka.5Ka miƙa hanyoyinka ga Yahweh; ka dagara gare shi, kuma zai yi abu a madadinka.6Zai nuna aɗalcinka kamar hasken rana da rashin laifinka kamar rana tsaka.7Ka natsu a gaban Yahweh kuma kayi jira da haƙuri domin sa. Kada ka ji haushi idan wani ya yi nasara da abin da ya ke yi, ko sa'ad da ya ke ƙulla mugunta.8Kada ka ji haushi da takaici. Kada ka damu. Wannan na bada damuwa ne kawai.9Za a datse miyagu, amma waɗanda ke jiran Yahweh zasu gãji ƙasar.10A ɗan lokaci ƙaɗan mugun mutum zai ɓace; zaka dubi wurinsa, amma ba zai kasance ba.11Amma masu tawali'u zasu gãji ƙasar kuma zasu yi murna da gagarumar wadata.12Mugun mutum yana shirya maƙarƙashiya gãba da adali yana kuma cizon haƙora gãba da shi.13Ubangiji yana yi masa dariya, gama yana ganin zuwan ranarsa.14Mugaye sun zare takubbansu suka kuma tanƙware bakkunansu don su kãda waɗanda ake masu danniya da masu buƙata, su kashe waɗanda ke da nagarta.15Takkubansu zasu soke zukatansu, kuma bakkunansu zasu kakkarye.16Gara ƙanƙanen abin da mutumin kirki ya ke da shi da yawan abubuwan mugayen mutane.17Gama za a ƙarɓe ƙarfin mugayen mutane, amma Yahweh zai taimaki adalai18Yahweh yana lura da marasa abin zargi a kowacce rana, kuma gãdonsu zai kasance har abada.19Ba za su ji kunya a lokacin masifa ba. Sa'ad da Yunwa tazo, zasu samu isasshen abinci.20Amma mugaye zasu lalace. Maƙiyan Yahweh za su zama kamar darajar ciyawa; za a cinye su su ɓace kamar hayaƙi.21Mugu yakan ci bashi amma ba ya biya, amma adali yana bayarwa hannu sake.22Waɗanda Allah ya sawa albarka zasu gãji ƙasar; waɗanda ya la'anta zasu zama korarru.23Ta wurin Yahweh ne hanyoyin mutum ke kafuwa, mutumin da hanyarsa amintacciya ce a fuskar Allah.24Ko da ya ke yana tuntuɓe, ba zai faɗi ba, gama Yahweh na riƙe shi da hannunsa.25Dã ni yaro ne kuma yanzu na tsufa; ban taɓa ganin an yashe da adali ba ko kuma 'ya'yansa na roƙon abinci.26Dukkan yini yana yin alheri yana ba da rance, kuma 'ya'yansa sun zama albarka.27Ka bar mugunta kayi abin da ke dai-dai; zaka cetu har abada.28Gama Yahweh yana ƙaunar adalci kuma baya rabuwa da amintattun masu binsa. Yana kiyaye su har abada, amma zuriyar mugaye zasu zama korarru.29Adalai zasu gãji ƙasar su zauna ciki har abada.30Bakin adali yana maganar hikima da kuma ƙara adalci.31Shari'ar Allahnsa na zuciyarsa; ƙafafunsa ba za su yi santsi ba.32Mugu yakan yi fakon adali ya nemi hanyar kashe shi.33Yahweh ba zai bar shi a hannun mugun ba ko kuwa ya yanke masa hukunci sa'ad da ya ke masa shari'a.34Ka jira Yahweh ka kuma kiyaye hanyoyinsa, zaya kuma ɗaga ka sama ka mallaki ƙasar. Za ka gani sa'ad da ake korar mugaye.35Na ga mugu da azzalumin taliki ya baje kamar koren itace a ƙasarsa ta asali.36Amma sa'ad da na sãke wucewa kuma, bai kasance a wurin ba. Na neme shi, amma ba ya samuwa.37Dubi mutumin kirki, ka kuma lura da adali; gaba zai zama da kyau ga mutumin salama,38Masu zunubi kuwa za a hallaka su ƙaƙaf; za a kuma share zuriyar mugun mutum.39Ceton adalai yakan zo daga Yahweh ne; yakan kiyaye su a lokatan damuwa.40Yahwe ya taimake su ya kuɓutar da su, Ya kuɓutar dasu daga mugaye ya cece su saboda sun sami garkuwa a cikinsa.
"Kada ku bari mugayen mutane su bata muku rai" ko kuma "Kada ku damu da abin da mugayen mutane suke yi"
Ana magana game da masu aikata mugunta kamar ciyawa ne da tsire-tsire waɗanda suka bushe suka mutu a lokacin zafi. Wadannan kwatancen biyu duk suna nufin zasu mutu. AT: "mutu" ko "zo ƙarshe"
Ana magana da aminci kamar dabba ce da za a ƙarfafa ta ta ciyarwa a makiyaya mai kyau. AT: "ciyar da aminci" ko "ƙara aminci"
Anan “zuciya” tana wakiltar yanayin mutum da tunanin sa. AT: "zurfin sha'awarku, cikinku" ko "abubuwan da kuka fi so"
Anan "bada hanyoyinku" wani karin magana ne wanda yake nufin roƙon Yahwehya mallaki rayuwarku. AT: "Nemi Yahweh ya jagoranci ayyukanku a rayuwa"
Wannan don wakiltar wani a cikin lamuran shari'a. Anan, lokacin da mutum ya dogara ga Yahweh, zai kare mutumin kuma ya ba da adalci ga mutumin.
"Yi shuru"
"amma waɗanda suka dogara ga Yahweh"
Ana maganar mallakar ƙasar kamar ana karɓa azaman gado. AT: "za su karɓi ƙasar a matsayin mallakarsu" ko "za su zauna lafiya a ƙasar"
Mugu yakan ƙi adali, har ya fara haƙora don nuna fushinsa.
Ana nuna cewa "ranar tasa" za ta zama ranar shari'a. AT: "rana tana zuwa da Yahweh zai hukunta shi kuma ya hukunta shi" ko "ranar tana zuwa da Yahweh zai hukunta kuma ya hukunta mugaye"
Waɗannan kalmomin duka suna nufin mutanen da ba su da ikon kare kansu. AT: "mutanen da ba za su iya tsayayya da su ba"
Takobi misalai ne na makamai kuma “zukata” suna wakiltar mutane. Don "huda zuciya" magana ce da ke nufin "kisa." AT: "Za a juya makamansu a kansu kuma za su kashe kansu"
"Ya fi kyau mu zama matalauta kuma adalai da zama mugaye tare da dukiya mai yawa"
Anan “makami” suna wakiltar ƙarfin mugaye. Karya hannayensu yana wakiltar karɓar ikonsu. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Gama Yahweh zai cire ƙarfin azzaluman mutane"
'Kula' yana nufin kare wani. Anan "marasa laifi" yana nufin mutane marasa aibu. AT: "yana kare mutane marasa aibu"
Wannan jumlar tana nufin masifu, kamar su yunwa. AT: "idan masifa ta faru"
Marubucin ya kamanta magabtan Yahweh da furannin da ke fure a filayen.
Marubucin yayi maganar halakar miyagu kamar sune ciyawa ko furannin furanni a filin da aka ƙone bayan girbi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai hallaka su kamar yadda wuta ta juya ciyawar filin ta zama hayaƙi"
Wannan nau'ikan daidaituwa ne na daidaici. Wadanda Allah yabasu akasin wadanda Allah ya tsine musu.
Ana iya bayyana wannan azaman mai aiki. AT: "Waɗanda Allah ya yi wa albarka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh shine ya taimaka wa mutum ya sami nasara"
Anan “tuntuɓe” da “faɗuwa” suna nuni ne ga yadda mutumin ya aikata a mawuyacin lokaci. AT: "Duk da cewa yana da mawuyacin lokaci, ba zai gaza ba gaba ɗaya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya rabu da mai adalci"
"'ya'yansa sun girma don albarkar wasu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai kiyaye su har abada"
Anan “baki” yana wakiltar duk mutumin da yake magana. AT: "Mutumin kirki"
Anan "a cikin zuciyarsa" yana nufin mafi zurfin cikinsa. AT: "Yana daraja umarnin Allahnsa a cikin cikinsa"
Anan kallon yana nuna kiyaye masu adalci don cutar dasu. AT: "yana jiran kwanto don mutumin kirki"
Waɗannan kalmomin suna nufin hannun kowane mugaye, ba na wani takamaiman mutum ba. Anan "hannu" yana wakiltar ƙarfi ko iko. AT: "hannayen mugaye" ko "ikon mugaye"
Anan “tayar da ku” yana nufin ba da girma ga waɗanda suke jiran sa. AT: "zai girmama ku ta hanyar ba ku ƙasar"
Wannan baya nufin wani takamaiman mutum ba. Magana ce ta gama gari.
Anan ana maganar wadatar mugu kamar mutumin lafiyayye ne wanda yake girma a ƙasa mai kyau.
Wannan baya nufin wani takamaiman mutum ba. Magana ce ta gama gari.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah zai kawo ƙarshen layin gidansa" ko "ba zai sami zuriya ba"
Ana iya bayyana kalmar 'Ceto' a matsayin aiki. AT: "Yahweh yana tserar da mutanen kirki"
Maganar zuwa ga Yahweh don kariya ana magana ne da neman mafaka a gare shi. AT: "sun tafi wurinsa don kariya"
1Yahweh, kada ka tsauta mani a cikin fushinka; kada ka hukunta ni a cikin hasalarka.2Gama kibiyoyinka suna sukana, kuma hannunka na matse ni har ƙasa.3Dukkan jikina na ciwo saboda hasalarka; babu lafiya a ƙasusuwana saboda laifina.4Gama zunubaina sun fi ƙarfina; sun zamar mani kaya mai nauyi da yawa.5Raunukana sun harbu suna wari saboda wawancin zunubaina.6Ana dakatar dani ana wulaƙanta ni kowacce rana; Ina ta makoki dukkan tsawon rana.7Gama daga ciki, ina cike da zafin ciwo; babu lafiya a jikina.8An sandare ni an ragargaza ni; ina gunaguni saboda fushin zuciyata.9Ubangiji kana sane da buƙatar zuciyata, kuma gunagunina basa ɓoyu ba daga gare ka.10Zuciyata na bugawa, ƙarfina na ƙarewa, bana kuma gani sosai.11Abokaina da aminai sun ƙaurace mani saboda yanayina; maƙwabtana na tsaye daga nesa.12Waɗanda ke so su kashe ni sun ƙafa mani tarko. Su waɗanda ke neman yi mani rauni suna maganar hallakarwa da faɗin kalmomin ruɗu dukkan tsawon rana.13Amma ni, ina kamar kurman mutum kuma bana jin komai; ina kamar beben da ba ya iya faɗin komai.14Ina kamar mutumin da ba ya ji kuma ba shi da amsa.15Tabbas ina jiranka, Yahweh; zaka amsa, Ubangiji, Allahna.16Na faɗi haka saboda maƙiyana ba zasu yi murna a kan damuwata ba. Idan tafin ƙafata ya zame, zasu yi mani mugayen abubuwa.17Gama ina gab da mutuwa, kuma ina cikin wahala kowacce sa'a.18Na furta laifofina; na kuma damu da zunubina.19Amma maƙiyana na da yawa; waɗanda suka ƙi ni cikin kuskure na da yawa.20Suna rama mani nagarta da mugunta; suna ta tuhuma ta koda ya ke ina neman abin da ke nagari.21Kada ka yashe ni, Yahweh; Allahna, kada ka tsaya nesa dani.22Ka zo da sauri ka taimakeni, Ubangiji, cetona.
An yi magana game da tsananin azabar Yahweh ga marubuci kamar dai Yahweh ya harba kibiyoyi a cikin marubucin. AT: "Hukuncinku yana da zafi kamar kun harba kibiya a wurina"
An yi magana akan horon Yahweh akan marubuci kamar dai Yahweh na fasa marubucin da hannunsa. Anan, "hannu" yana nufin ikon Yahweh. AT: "ikonka ya buge ni"
Anan "ƙasusuwana" suna wakiltar jikin marubuci. AT: "Jikina duka yana da cuta saboda zunubina"
Ana maganar laifofin marubuci kamar ambaliyar ruwa ce da ta rufe shi. AT: "Laifofin na sun rufe ni kamar ambaliyar ruwa"
Anan "wari" yana nuni ga ciwon nasa wanda yake da ƙamshi mai haɗari wanda yake da ruɓaɓɓen nama. AT: "Raunin na ciwo ne kuma suna wari yayin da suka ruɓe"
Na marubucin yana fama da zazzaɓi sosai kamar dai yana ƙone ciki. AT: "Jiki na yana kuna da zazzaɓi"
Anan “namana” yana nufin marubuci. AT: "Ba ni da lafiya kwata-kwata"
Anan "zuciyata" tana nufin marubuci. Zai iya zama taimako a bayyana cewa marubucin yana son ƙoshin lafiya. AT: "Babban burina" ko kuma "Ina so ku warkar da ni"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kuna iya ganin duk nishin da nake yi na baƙin ciki"
Waɗannan jimlolin guda biyu ma'anar abu ɗaya ne kuma suna jaddada yanayin cutarwar abin da waɗannan mutane ke faɗi.
Marubuci baya jin abinda makiyan sa suke fada.
Marubuci ba ya faɗan mugayen maganganu ga maƙiyansa ba.
"ba zan yi murna da wahalata ba"
Zai yiwu ma'anonin wannan kalmonin su ne 1) "Ba ni da lafiya har na kusan mutuwa" ko 2) "Da sannu zan lalace." Zai iya zama mafi kyau kada a fassara fassarar a cikin rubutun.
"kullum ina cikin raɗaɗi"
Ayyukan abokan gaban marubucin suna magana ne azaman ma'amala ta kuɗi inda suka ba shi mugayen abubuwa don musanya abubuwa masu kyau. Ana iya bayyana sunayen suna "mugunta" da "kyakkyawa" azaman siffofi. AT: "Suna yi min mummunan abu bayan na kyautata musu"
Yadda magabtan marubucin suke zarginsa ana maganarsu kamar suna jifansa da zargi kamar duwatsu.
Tunda har yanzu Yahweh bai amsa roƙon marubucin ba, ya yi magana game da Yahweh kamar Yahweh yana tsaye nesa da marubucin.
Ana maganar Allah kamar yana gudu zuwa wurin marubuci don ya taimake shi.
1Na yi shiri, "Zan lura da furcin da zan yi saboda kada in yi zunubi da harshe na. Zan sa wa bakina takunkumi a lokacin da nake wurin da mugu ya kasance."2Na yi shiru; Na riƙe maganganuna daga faɗin wani abu koda nagari ne, shanwuta kuma ta ƙaru.3Zuciyata ta yi zafi; sa'ad da nayi tunani a kan abubuwan nan, yana ci kamar wuta. Sa'an nan a ƙarshe nayi magana.4"Yahweh, kasa in san yaushe ne ƙarshen rayuwata da tsawon kwanakina. Ka nuna mani ina kurkusa da matuwa.5Duba, kã maida kwanakina kamar tsawon hannuna, kuma rayuwata kamar ba komai take ba a wurinka. Hakika kowanne mutum lumfashi ɗaya ne. Selah6Hakika kowanne mutum yana tafiya kamar inuwa. Hakika dukkan kowa yana hanzari ya tattara arziki ko da yake basu san wanda zai karbe su ba.7Yanzu, Ubangiji, domin me nake jira? Kai ƙaɗai ne begena.8Ka cece ni daga zunubaina; kada ka bari in zama abin ba'a ga wawaye.9Na yi shiru kuma bazan iya buɗe bakina ba, saboda kai ne kayi haka.10Ka daina yi mani rauni; na karaya ta wurin bugun hannunka.11Sa'ad da kake horar da mutane don zunubi, kakan cinye abubuwan da suke marmari kamar asu; hakika dukkan mutane ba komai bane banda tururi kawai. Seleh12Ka ji addu'ata, Yahweh, ka saurare ni; ka saurari kukana! Kada ka zama kurma a gare ni, gama ni kamar baƙo ne tare da kai, ɗan gudun hijira kamar yadda dukkan kakannina suke.13Ka juyar da harararka daga gare ni domin in sake yin murmushi kafin in mutu,"
A nan "lura ko kallo" wani karin magana ne da ke nufin "kula da hankali." AT: "Zan mai da hankali ga abubuwan da zan faɗi"
A nan "harshe" yana nufin jawabin marubuci. AT: "don kada in yi magana game da abin da ya saɓa wa Yahweh"
"Ban yi magana ba"
Anan “zuciya” tana wakiltar mutum dukka. Maganganun damuwa na marubuci ana maganarsu kamar wuta ce tana ci a cikinsa. AT: "Na kasance cikin damuwa lokacin da na yi tunani game da waɗannan abubuwa"
"Nuna min yadda rayuwata ta taƙaice" ko "Nuna min yadda kwanan nan zan mutu"
Marubucin yayi maganar rayuwarsa idan za'a iya auna shi da fadin hannunsa. AT: "kawai a ɗan gajeren lokaci"
Rayuwa takaitacciya ce, kuma mai zabura yayi magana akanta anan kamar dai tsawon lokacin da mutum zai ɗauka yana numfashi ɗaya. AT: "Lokacin da mutane suke rayuwa gajere ne kamar numfashin mutum ɗaya"
Ana maganar rayuwar mutane kamar ba su da muhimmanci kamar inuwa. AT: "Kowa ya ɓace kamar yadda inuwa ke yi"
Marubucin yayi wannan tambayar don ya nanata cewa mutane ba za su iya taimaka masa ba. Ana iya fassara wannan tambayar ta lafazi a matsayin sanarwa. AT: "Don haka yanzu, Yahweh, ba zan iya samun komai daga kowa ba."
"saboda azaba ta daga gare ka take"
"An kayar da ni gaba daya"
An yi maganar azabar Allah ga marubuci kamar Allah yana buge shi da dunƙulen hannu. Anan “hannu” yana wakiltar hukuncin Allah. AT: "hukuncin ku a kaina"
Allah zai ɗauke musu abubuwan da suke ɗauka daidai kamar yadda asu ke cinye ƙyallen mayaƙi. AT: "cinye abubuwan da suke so kamar kwari yakan cinye kayan sawa"
Marubucin yayi magana game da rashin amsawar Yahweh a gare shi kamar dai Yahweh kurma ne. AT: "Kada ku yi watsi da ni kamar ba za ku iya ji na ba"
Marubucin yayi magana game da rashin amsawar Yahweh kamar dai Yahweh na ɗauka shi bako ne gareshi. AT: "Ni kamar cikakken baƙo ne a gare ku"
Anan "murmushi" yana haɗuwa da farin ciki. AT: "domin in sake yin farin ciki"
1Na jira Yahweh da haƙuri; ya saurare ni ya ji kukana.2Ya fitar dani daga rami mai furgitarwa, daga taɓo, ya sa ƙafafuna a kan dutse ya tsare takawata.3Ya sa sabuwar waƙa a bakina, yabo ga Allahnmu. Da yawa zasu gani su kuma girmama shi su dogara ga Yahweh.4Mai albarka ne mutumin da ya maida Yahweh madogararsa kuma baya girmama masu fahariya ko waɗanda suka juya daga gare shi zuwa ƙarairayi.5Da yawa suke, Yahweh Allahna, ayyukan al'ajiban da ka yi, kuma babu wanda zai iya ƙirga abubuwan da kake tunani gme da mu; Idan na yanke shawara in yi magana a kan su, za su fi abin da za a iya ƙirgawa.6Ba ka buƙatar hadaya ko baiko, amma ka buɗe kunnuwana; ba ka buƙatar baye-baye na ƙonawa ko baye-baye na zunubi.7Sa'an nan na ce, "Duba, Na zo; a rubuce ya ke a game dani cikin littafin Yahweh.8Ina jin daɗin yin nufinka, Allahna, shari'unka na cikin zuciyata."9Na yi shelar nagartattun labaran ayyukanka na adalci a babban taron jama'a; Yahweh, ka san leɓunana basu dena yin wannan ba.10Ban ɓoye ayyukan adalcinka a zuciyata kaɗai ba; Na furta amincinka da cetonka; Ban ɓoye amintaccen alƙawarinka ko madawwamiyar ƙaunarka daga babban taron jama'a ba.11Kada ka yi jinkirin yi mani ayyukan jinƙai; ka bar amintaccen alƙawarinka da madawwamiyar ƙaunarka su kiyaye ni.12Damuwoyin da basu ƙidayuwa sun kewaye ni; alhakin zunubaina ya tarar da ni har yasa bana iya ganin wani abu; Sun fi gashin kaina yawa, kuma zuciyata ta karaya.13In ka yarda, Yahweh, ka cece ni; ka yi hanzari ka taimake ni, Yahweh.14Ka sa waɗanda suke son kashe ni su sha kunya da yawa. Kasa su koma baya a ci nasara a kansu, ka kawo waɗanda ke murna saboda wahalar da nake sha, cikin ƙasƙanci.15Kasa su razana saboda kunya, su waɗanda ke yi mani ba'a, "16Amma bari dukkan waɗanda ke neman ka su yi farinciki da murna a cikinka; ka sa duk mai ƙaunar cetonka ya ci gaba da cewa, "A yabi Yahweh."17Na talauce na zama mabuƙaci; duk da haka Ubangiji yana tunani a kai na. Kai ne mai taimako na kuma ka zo domin ka cece ni; kada ka yi jinkiri, Allahna.
Wannan yana nufin marubucin yana jiran Yahweh ya taimake shi.
Waɗannan suna nufin abu ɗaya, kuma ana iya haɗa su zuwa bayani ɗaya. AT: "ya saurare ni lokacin da na kira shi"
Wadannan kalmomin biyu suna nufin abu daya ne. Ana maganar hatsarin marubucin kamar wani rami ne mai mutuƙar cika da laka. Wannan yana jaddada haɗarin. AT: "daga shiga cikin mummunan rami mai cike da laka mai laushi"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Ya koya mani kalmomin zuwa wata sabuwar waƙa" ko 2) "Ya ba ni sabon dalilin rera waka."
"Mai albarka ne mutumin da ya dogara ga Yahweh" ko "Waɗanda suka dogara ga Yahweh suna da albarka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "babu wanda zai iya kirga duk abubuwan da kuke tunani akan mu"
Wannan karin gishiri ne don bayyana cewa wasu abubuwan sun fi muhimmanci ga Allah. AT: "Hadaya da sauran abubuwan sadaukarwa ba su ne abubuwan da ke faranta muku rai ba"
Anan "zuciyata" tana nufin yanayin cikin marubuci. AT: "Kullum ina tunanin dokokinku ne a cikina"
"Na yiwa babban taron mutane busharar adalcinku."
Anan "leɓunana" suna wakiltar marubucin, suna ƙarfafa jawabinsa. AT: "Ban hana kaina shelar waɗannan abubuwa ba"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Na fadawa duk wanda yake cikin babban taron game da amincin alkawarinku ko amincinku"
A nan ana magana da matsaloli kamar abubuwa ne da ke kewaye da tarko mai magana. AT: "akwai matsaloli da yawa a wurina fiye da yadda zan iya ƙidaya" ko "ƙarin matsaloli sun same ni fiye da yadda zan iya ƙidaya"
Fassarori sun banbanta ta yadda za a fahimci wannan wurin mai wahala. Yana iya nufin cewa mai magana yana kuka sosai har ya kasa ganin komai saboda hawayensa.
Ana iya sake dawo da wannan kuma a bayyana ta cikin aiki. AT: "Bari waɗanda ke bin rayuwata su ɗauke shi abin kunya su ji kunya kuma su ɓata rai gaba ɗaya"
Bari waɗanda suka ce da ni, "Aha, aha!" su firgita saboda kunyarsu"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna ƙarfafa tsananin farin ciki. AT: "ku yi murna ƙwarai"
"Ubangiji yana kulawa da ni"
"Kai ne wanda ya taimake ni"
1Mai albarka ne wanda ke kulawa da marasa ƙarfi; a ranar masifa, Yahweh zai 'yantar da shi.2Yahweh zai kiyaye shi ya kare shi, kuma zai zama da albarka a duniya; Yahweh ba zai bar shi ga nufin maƙiyansa ba.3Yahweh zai yi masa gudummawa a gadon wahalarsa; zaka maida gadonsa na ciwo zuwa gadonsa na warkarwa.4Na ce, "Yahweh, ka yi mani jinƙai! Ka warkar dani, gama na yi maka laifi."5Maƙiyana suna muguwar magana gãba da ni, cewa, 'Yaushe ne zai mutu kuma sunansa ya lalace?'6Idan maƙiyina ya zo gani na, ya furta maganganun banza; zuciyarsa na ƙoƙarin sanin dukkan matsalolina; sa'ad da ya tafi daga gare ni, sai ya gaya wa kowa game da su.7Dukkan waɗanda ke ƙi na na raɗa da juna gãba da ni; gãba da ni suna fatan shan wahalata.8Suna cewa, "Mugun ciwo ya make shi; yanzu da ya ke kwance ƙasa, ba zai ƙara tashi ba."9Lallai, ko abokina na ƙut da ƙut, da na yarda da shi, wanda ya ci gurasata, ya juya mani baya.10Amma kai, Yahweh, ka yi mani jinƙai ka ɗaga ni sama saboda in mai da martani.11Ta wannan na san kana farinciki dani, gama maƙiyina bai yi murna a kaina ba.12Amma ni, ka tallefe ni cikin aminncina kuma zaka kiyaye ni a fuskarka har abada.13Bari Yahweh, Allah na Isra'ila a yabe shi daga dawwama zuwa dawwama. Amin da Amin. Littafi Biyu
Maganar "gadon wahala" tana nufin lokacin da mutum yake kwance a gado saboda rashin lafiya. AT: "Lokacin da bashi da lafiya kuma yana kan gado, Yahweh zai taimake shi"
Maganar "gadon warkewa" tana nufin lokacin da mutum yake hutawa a gado kuma ya warke daga rashin lafiyarsa. AT: "kai, Yahweh, za ku warkar da shi daga cutar sa"
Kalmomin "makiyina" na nufin duk wani makiyi gaba daya, kuma ba ga wani makiyi na musamman ba.
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) "ya faɗi abubuwa marasa ma'ana" ko 2) makiyansa su faɗi abin don ya sa ya yi tunanin cewa su abokansa ne alhalin ba su ba. AT: "yana faɗin abubuwan yaudara" ko "suna nuna kamar sun damu da ni"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "suna fatan cewa mummunan abubuwa zasu same ni" ko kuma 2) "suna shirin cutar da ni."
Anan kalmomin "kwanciya" na nuni ga kwanciya kan gado saboda rashin lafiya. Cewa ba zai “tashi ba” yana nufin zai ci gaba da kwanciya, wannan maƙarƙancin mutuwa ne. AT: "yanzu tunda bashi da lafiya a gado, zai mutu a can"
Wannan buƙata ce. AT: "Ina roƙon ka, Yahweh, ka yi mani jinƙai ka tashe ni"
Hakanan za'a iya fassara wannan a cikin yanayi na gaba, tunda Yahweh bai riga ya warkar da shi ba. AT: "Idan kun ba ni damar yin hakan, sakamakon cewa magabtana ba su ci ni ba, zan san kun yarda da ni"
Wannan ayar ta fi ƙarshen wannan zaburar. Magana ce ta ƙarshe ga duka Littafin 1 na Zabura, wanda ya fara daga Zabura ta 1 kuma ya ƙare da Zabura ta 41.
Wannan yana nufin matattakala biyu da ma'ana koyaushe. AT: "har abada abadin"
1Kamar yadda mariri ke marmarin rafukan ruwa, haka nake ƙishinka, Allah.2Ina ƙishin Allah, Allah mai rai, yaushe zan zo in bayyana a gaban Allah?3Hawayena sun zama abincina dare da rana, lokacin da maƙiyana kullum suna cewa dani, "Ina Allahnka?"4Waɗannan abubuwan nake tunawa da su yayin da nake zubo raina: yadda na tafi tare da taron mutane na jagorance su zuwa gidan Allah tare da muryar jin daɗi da yabo, babban taro na shagalin buki.5Me yasa ka rusuna ƙasa, raina? Me yasa kake damuwa daga can ciki? Yi bege ga Allah, gama zan ƙara yabonsa wanda shi ne cetona.6Allahna, raina ya rusuna ƙasa a can ciki, don haka na tuna da kai daga ƙasar Yordan, daga ƙololuwar Dutsen Hamon, kuma daga tudun Miza.7Zurfi na kira ga zurfi da jin ƙarar kwararowar ruwanka; dukkan raƙuman ruwanka da matsirgan ruwanka sun mamaye ni.8Duk da haka Yahweh zai umarci amintaccen alƙawarinsa da rana; da dare waƙarsa zata kasance tare da ni, addu'a ce ga Allah na rayuwata.9Zan yi magana ga Allah, dutsena, "Me yasa ka mance da ni" Me yasa nake makoki saboda danniyar maƙiyina?"10Kamar da takobi a ƙasusuwana, maƙiyana ke yi mani zargi, yayin da kullum suke cewa dani, "Ina Allahnka?"11Me yasa kake rusuna a ƙasa, raina? Me yasa kake damuwa can ciki? Yi bege cikin Allah, gama kuma zan yabe shi wanda shi ne cetona da Allahna.
Marubucin ya kwatanta son da yake yi wa Allah da muradin barewar ƙishirwa ga ruwa.
Marubucin ba ya yin wannan tambayar don ya sami amsa sai dai don ya nuna tsananin sha'awar kasancewa a gaban Allah.
Marubucin yayi nuni da hawayensa kamar abinci ne da yake ci. Wannan yana nufin cewa yana baƙin ciki ƙwarai har ya kasa cin abinci. AT: "Hawayena kamar abincina ne kuma bana cin komai"
Makiyan marubucin suna amfani da wannan tambayar don su yi masa ba'a kuma su nuna cewa ba sa ganin Allahnsa ya taimake shi. AT: "Allahnku ba ya nan ya taimake ku"
Anan kalmar "raina" tana nufin motsin rai. Marubucin yayi maganar ruhinsa kamar wani ruwa ne yake zubawa. Yankin yana nufin yana bayyana baƙin cikin da yake ji. AT: "Na nuna baƙin cikina"
Marubucin ya ambaci yanayinsa kamar “ruhunsa,” wanda yake wakiltar kansa. Yana yin waɗannan tambayoyin don tsawata wa kansa. AT: "Bai kamata a sunkuyar da ni ƙasa ba. Ba zan damu ba"
Marubucin ya ci gaba da magana da ransa kuma ya umurce ta da dogaro ga Allah.
Wannan jimlar na nufin tuna ko tunani game da wani abu. AT: "Ina tunanin ku"
Marubucin yayi magana game da babban rashin sa'a da bakin ciki kamar suna cikin zurfin zurfafawa waɗanda suka nutsar dashi tare da kala-kala bayan ɗaya.
Marubucin yayi magana game da amincin alkawarin Yahweh kamar mutum ne wanda ya ba da umarnin kasancewa tare da shi. Cikakken sunan "aminci" za a iya fassara shi azaman sifa. AT: "Yahweh zai nuna min amincin alkawarinsa da rana" ko "Yahweh zai nuna min da rana irin amincin da yake yi da alkawarinsa"
"Allah wanda ya bani rai"
Marubucin yayi maganar Allah kamar wani babban dutse ne wanda zai bada kariya daga harin makiya.
Yin "makoki" shine aiwatar da al'adun da suka danganci baƙin ciki.
Marubucin ya ambaci yanayinsa kamar “ruhunsa,” wanda yake wakiltar kansa. Yana yin waɗannan tambayoyin don tsawata wa kansa. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Zabura 42: 5. AT: "Bai kamata a sunkuyar da ni ƙasa ba, Ba zan damu ba"
1Kawo mani adalci, Allah, kayi mani taimakon kãriya a kan al'umma marasa tsoron ka.2Gama kai ne Allah na ƙarfina. Meyasa ka yashe ni? Me yasa nake tafiya cikin makoki saboda muzgunawar maƙiya?3Oh, ka aiko da haskenka da gaskiyarka, su jagorance ni. su kawo ni ga tudunka mai tsarki da wurin zamanka.4Sa'an nan zan yi tafya zuwa ga bagadin Allah, ga Allah matuƙar jin daɗina. Zan yabeka da garaya, Allah, Allahna.5Me yasa ka rusuna ƙasa, raina? Me ya sa kake damuwa can ciki? Yi bege cikin Allah, gama zan ƙara yabonsa wanda shi ne cetona da Allahna.
Marubucin ya yi waɗannan tambayoyin ne don yin gunaguni ga Allah da kuma bayyana yadda yake ji, ba don ya sami amsa ba.
Marubucin yayi magana game da ceton Allah kamar haske ne wanda yake nuna masa hanya da gaskiyar da ke koya masa yadda ake rayuwa. AT "ku shiryar da ni da haskenku da gaskiyarku"
"Allah wanda shine babban farin cikina" ko "Allah wanda yake bani matukar farin ciki"
Marubucin ya ambaci yanayinsa kamar “ruhunsa,” wanda yake wakiltar kansa. Yana yin waɗannan tambayoyin don tsawata wa kansa. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Zabura 42: 5. AT: "Bai kamata a sunkuyar da ni ƙasa ba. Ba zan damu ba"
Marubucin ya ci gaba da magana da ransa kuma ya umurce ta da dogaro ga Allah. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Zabura 42: 5.
1Mun ji da kunnuwanmu, Allah, Kakanninmu suka faɗa mana irin aikin da ka yi a kwanakinsu, a kwanakin dã.2Ka kore al'ummai da hannunka, amma ka dasa mutanenmu; ka azabci mutane, amma ka baza mutanenmu cikin ƙasar.3Gama basu samu mallakar ƙasar ta takobin kansu ba, ba kuma ƙarfin kansu ba ne ya cece su; amma hannun damanka da ƙarfinka da hasken fuskarka ne, saboda yi tagomashi gare su.4Allah, kai ne sarkina; ka umarta nasara domin Yakubu.5Da taimakonka zamu tura maƙiyanmu; da sunanka za mu tattakesu, waɗanda suka tashi gãba da mu.6Gama ba zan dogara ga bakana ba, takobina kuma ba zai cece ni ba.7Amma ka cece mu daga maƙiyanmu, ka ba masu ƙinmu kunya.8A cikin Allah muke fahariya a kullum, kuma za mu yi godiya ga sunanka har abada. Selah9Amma yanzu ka ƙi mu ka kawo mu ga kunya, kuma baka yi tafiya tare da mayaƙanmu ba.10Ka sa muka juya baya daga maƙiyin; kuma waɗanda suka ƙi mu suna ɗibi ganima domin kansu.11Ka maida mu kamar tumakin da aka ƙaddara don abinci ka warwatsar da mu cikin al'ummai.12Ba a bakin komai ka sayar da mutanenka ba; ba ka ƙara wadatarka ta yin haka ba.13Ka maida mu abin zargi ga maƙwabtanmu, waɗanda ke kewaye da mu suna yi mana reni da ba'a.14Ka sa mun zama abin zãgi cikin al'ummai, abin girgiza kai cikin tarrukan mutane.15A dukkan tsawon rana ƙasƙancina na gabana, kuma kunyar fuskata ta rufe ni16saboda muryar wanda ke tsautarwa da zage-zage, saboda maƙiyi da mai ɗaukar fansa.17Dukkan waɗannan sun zo a kanmu; duk da haka ba mu mance da kai ba ko kuwa mu yi aiki cikin rahin gaskiya da alƙawaranka.18Zuciyarmu bata juya ba; ƙafafunmu ba su yi nisa daga hanyarka ba.19Duk da haka ka kakkarya mu a wurin diloli ka rufe mu da inuwar mutuwa.20Idan mun mance da sunan Allahnmu ko kuwa muka buɗe hannuwanmu ga wani bãƙon allah,21Allah ba zai bincika haka ba? Gama ya san asiran zuciya.22Hakika, ta dalilinka ake karkashe mu dukkan rana; ana yi mana kallon tumaki domin yanka.23Farka, me yasa kake barci, Ubangiji? Tashi, kada ka jefar da mu da daɗewa.24Me yasa ka ɓoye fuskarka ka mance da matsananciyar azabarmu da wahalarmu?25Gama mun narke mun zama ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.26Tashi tsaye domin taimakonmu ka 'yantar da mu ta dalilin amintaccen alƙawarinka.
Kalmar "kunnuwa" tana ƙara girmamawa ga maganar da suka ji kuma suka fahimci abubuwan da marubucin yake shirin bayyanawa. Marubucin yayi wannan bayani ga Allah. AT: "Allah, mun ji sarai"
"Kun tilasta wa mutane daga wasu al'ummomin ficewa"
Marubucin yayi maganar Allah yasa Isra’ilawa su zauna a cikin ƙasa kamar yana dasa su ne a cikin ƙasa kamar itaciya. AT: "kun sa mutanenmu suka zauna a can"
A nan kalmar “hannu” na nufin ikon Allah. A hade, suna nanata girman ikon Allah. AT: "ƙarfin ku mai girma"
Kuna iya samar da fi'ili don wannan jumlar. AT: "hasken fuskarka ya sami ƙasar don mallakarsu"
Ana kiran jama'ar Isra'ila da sunan kakansu "Yakubu."
Marubucin yayi maganar abokan gabansa shan kashi kamar suna "ƙasa" kuma suna shirin yaƙi kamar suna "sama."
Anan kalmar “suna” tana nufin ikon Allah da ikonsa. AT: "da ikonka"
"tattaka su ƙarƙashin ƙafafunmu" ko "tafiya a saman su"
Ana iya fassara kalmar "alfahari" tare da fi'ili. AT: "mun yi alfahari"
Anan kalmar "suna" tana nufin Allah, kansa. AT: "za mu yi muku godiya"
Marubucin ya kwatanta Isra’ilawa da tumakin da mutane ke yanka kuma suke ci. Kamar yadda tumaki ba su da ƙarfi a gaban waɗanda suka kashe su, haka Isra'ilawa ba su da ƙarfi a gaban maƙiyansu. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Kun ba wa magabtanmu damar su kashe mu kamar yadda za su yanka tunkiya su cinye ta"
"ya sa muka zauna a kasashe da yawa"
Ana iya fassara kalmar "tsawata" a matsayin fi'ili. AT: "Kuna sanya mana abin da maƙwabta suke tsawata"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "waɗanda suke kewaye da mu suna yi mana ba'a kuma suna yi mana ba'a"
Ana iya fassara kalmar "zagi" azaman aiki. AT: "Kuna sanya al'umman da ke kusa da mu su zage mu"
Marubucin yayi maganar kunyarsa kamar wani abu ne ya lullubeshi kamar bargo zai lullubeshi. AT: "Kunyar fuskata ta mamaye ni" (Duba: metaphor)
A nan kalmomin "muryar" suna wakiltar mutumin da yake zaginsa. AT: "saboda abin da mutumin ya fada wanda ya tsawata min kuma ya zageni"
Anan kalmar "zuciya" tana nufin motsin rai, kuma musamman don aminci da ibada. AT: "Ba mu daina yi muku biyayya ba"
Anan kalmar "suna" tana nufin Allah, kansa. Manta da Allah shine a daina bauta masa. Wannan wani abu ne da bai faru ba. AT: "Idan da mun manta da Allahnmu" ko "Da mun daina bautar Allahnmu"
Mika hannaye wata alama ce da mutane suka saba bauta wa da kuma addu'a ga allah. AT: "ya bauta wa baƙon allah" ko "ya yi addu'a ga baƙon allah"
Marubucin yayi amfani da wannan tambayar don bayyana cewa Allah zai san idan zasu bautawa wani allah. AT: "Tabbas Allah zai sani"
Wannan baya nufin Allah yana bacci. Marubucin yayi magana game da rashin aiki kamar Allah yana barci. Ya yi tambayar don tsauta wa Allah don ya nuna bai damu da matsalolin su ba. AT: "Ku farka! Ina jin kamar kuna barci, Ya Ubangiji!"
Marubucin yayi amfani da wannan tambayar don yin gunaguni cewa Allah yana bayyana yana watsi da su. AT: "Kada ku ɓoye fuskarku ... zaluncinmu."
Marubucin yayi maganar wulakantasu kamar dai jikunansu abubuwa ne, kamar kankara, da ke narkewa kuma suke jika cikin datti.
Marubucin yayi maganar wulakancin su kamar dai jikinsu ya makale a kasa kuma ba zasu iya daga kansu ba.
1Zuciyata na jin daɗi da nagartaccen zance; Zan karanta kalmomin da na harhaɗo a kan sarki da ƙarfi; harshena shi ne al'ƙalamin shiryayyen marubuci.2Ka fi 'ya'yan ɗan Adam kyau; an zuba alheri a leɓunanka; saboda haka mun san Allah ya albarkaceka har abada.3Kasa takobinka a gefenka, mai girma, cikin ɗaukakarka da martabarka.4Cikin darajarka ka hau dokinka cikin murna saboda yarda da tawali'u da ayyukan adalci; hannun damanka zai koya maka abubuwan bantsoro.5Kibawunka na da ƙaifi; mutane sun faɗa ƙarƙashinka; kibawunka na cikin zukatan maƙiyan sarki.6Kursiyinka, Allah, yana nan har abada, sandar adalci shi ne sandar mulkinka.7Kana ƙaunar ayyukan adalci kuma kana ƙin mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya shafe ka da mai na murna fiye da abokan taraiyarka.8Dukkan tufafinka na ƙamshin turaren mur da aloyes da ƙahonnin da aka samo; daga kowacce fadar hauren giwa kayyakin busa da kiɗe-kiɗe sun saka murna.9'Ya'ya mata na sarakuna na cikin matayenka masu martaba; sarauniya na tsaye da tufafin zinariya da Ofir a hannun damanka,10Saurara, ɗiya, ki maida hankali ki buɗe kunne, ki mance da mutanenki da gidan mahaifinki.11Ta haka sarkin zai yi marmarin kyanki; shi shugabanki ne; ki girmama shi.12Ɗiyar Taya zata kasance a wurin da kyauta; masu arziki cikin mutanen za su nemi alfarmarku.13Ɗiya gimbiya a fãda tana cikin dukkan ɗaukaka; an yi aikin tufafinta da zinariya.14Za a kaita wurin sarki cikin kyawawan tufafi masu ado kala-kala; budurwai, ƙawayenta dake binta, za a kawo maka.15Za a jagorance su da murna da farinciki; za su shiga cikin fadar sarki.16A fãdar ubanninka 'ya'yanka zasu kasance, waɗanda zaka maida su yarimai a dukkan duniya.17Zan sa sunanka ya dawwama a dukkan tsararraki; saboda haka mutanen zasu yi maka godiya har abada abadin.
Marubucin yayi maganar zuciyarsa kamar wani akwati ne wanda yake malala da ruwa. Kalmar "zuciya" tana wakiltar motsin zuciyar sa, wanda ke daɗaɗa da waƙar da ya rera. AT: "Murmushina yana tausaya game da maudu'i mai kyau"
Marubucin yayi maganar harshensa kamar alkalami. Yana magana da kalmomin da gwaninta kamar yadda gogaggen marubuci yake rubuta kalmomi. AT: "harshena kamar alkalami ne na mutumin da ya yi rubutu mai kyau" ko "Ina magana da kalmomi kamar yadda gwanintar marubuci ke iya rubuta kalmomi"
Wannan jumlar wuce gona da iri ce wacce ke jaddada cewa sarki yafi kowa kyau. Kalmomin "'ya'yan' yan adam" karin magana ne kuma yana nufin dukkan mutane. AT: "Kun fi kowane mutum kyan gani"
Marubucin yayi maganar alheri kamar dai mai ne wanda wani yayi amfani da shi ya shafa leɓunan sarki. Kalmar "lebe" tana nufin jawabin sarki. Jumlar tana nufin sarki yana magana da iya magana. AT: "kamar dai wani ya shafe leɓunku da mai" ko "kuna magana da kyau"
Jarumawa sun ɗauki takubansu a cikin ɗamara wanda aka rataye a ɗamara a kugu. Takobin zai tsaya a gefen su. Wannan jimlar ta bayyana aikin wani da ke shirin yaƙi. AT: "Shirya kanku don yaƙi"
Abubuwan suna na "amintacce," "tawali'u," da "adalci" za'a iya bayyana su a matsayin sifofi. Mai yiwuwa ma'anoni sune 1) waɗannan halayen halayen mai girma ne. AT: "saboda kai amintacce ne, mai tawali'u ne, mai adalci" ko kuma 2) waɗannan halayen kirki ne da yake yaƙi da su don mutanen da yake mulka. AT: "don yin yaƙi don abin da yake amintacce, mai tawali'u, da kuma daidai"
Yawancin sojoji suna riƙe takubbansu da hannun dama lokacin da suke yaƙi. A nan, kalmar "hannun dama" tana nufin ikonsa na yaƙi, wanda marubucin ke magana kansa kamar mutum ne wanda zai iya koyar da sarki ta hanyar kwarewar da ya samu a yaƙi.AT: "Za ku koyi cika manyan ayyukan soja ta hanyar faɗa a yaƙe-yaƙe da yawa"
Wannan jimlar tana nufin sarki yana cin abokan gabansa. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "mutane sun faɗi a ƙafafunku don miƙa wuya" ko 2) "mutane sun faɗi matattu a ƙafafunku."
Kalmar "kursiyi" tana wakiltar masarauta da mulkin sarki. AT: "Mulkinka ... har abada abadin ne" ko "Za ka yi sarauta ... har abada abadin"
Kalmar "sandar sarauta" tana wakiltar ikon sarki na mulkin masarautarsa. AT: "kuna mulkin masarautarku da adalci"
Marubucin yayi maganar murna kamar dai mai ne wanda Allah ya shafe shi da sarki. Cewa Allah ya shafe shi aiki ne na alama wanda yake wakiltar zaɓen da Allah ya zaɓe shi ya zama sarki. AT: "lokacin da Allah ya naɗa ku sarki, sai ya faranta muku rai"
Waɗannan matan matan sarki ne waɗanda suka sami amincewarsa.
Wannan ishara ne ga matar da za ta zama sarauniya. AT: "amaryarka, sarauniyar" ko "amaryarka, wacce za ta zama sarauniya"
Marubucin yayi magana game da sarauniyar da baya bin imani da al'adun mutanen garinsu kamar tana manta su. AT: "kada ku bi al'adun mutanenku"
Anan kalmar "gida" tana nufin dangi. AT: "danginku"
Wannan hanya ce mai ladabi da za a ce sarki zai so ya kwana da sarauniya a matsayin matarsa.
Marubucin ya yi maganar mutanen da ke zaune a Taya kamar su 'ya'yan Taya ne. AT: "Mutanen Taya"
An yi mata ado ko ado da zinariya. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "tana sanya suturar da wani ya zana da zaren zinariya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT "Mutane za su jagorance ta zuwa ga sarki yayin da take sanye da rigar ado"
Wannan jimlar ta bayyana "farin ciki da murna" a matsayin mutumin da ke jagorantar wasu don yin biki. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Murna da murna za su jagorance su" ko "Za su ci gaba da farin ciki da farin ciki"
'Ya'yan sarki za su naɗa shi sarki, kamar yadda ya maye gurbin kakanninsa.
Kalmomin “a cikin dukan duniya” ƙari ne kawai don a nanata cewa za su mallaki al’ummai da yawa. AT: "zaku sanya masu mulki akan al'ummomi da yawa"
1Allah shi ne mafakarmu da ƙarfinmu, Mai matuƙar taimako a lokacin wahala.2Domin haka ba za mu ji tsoro ba, ko duniya zata canza, ko an girgiza duwatsu har cikin tekuna,3ko ruwayenta sun yi ruri da tangaɗi, duwatsu kuma suna motsi saboda kumburinsu. Selah4Akwai kogi, da ƙoramu waɗanda ke sa birnin Allah farinciki, wuri mai tsarki na shirayi na Maɗaukaki.5Allah yana cikin tsakiyarta; ba zata kawu ba; Allah zai taimake ta, kuma zai yi haka da sassafen safiya.6Al'ummai suka fusata kuma mulkoki suka girgiza; ya tayar da muryarsa, kuma duniya ta narke.7Yahweh mai runduna na tare da mu; Allah na Yakubu shi ne mafakarmu. Selah8Zo, dubi ayyukan Yahweh, hallakar da ya kawo wa duniya.9Ya sa yaƙe-yaƙe su ƙare har zuwa iyakar duniya; ya kakkarya baka ya daddatsa mãsu gutsu--gutsu; ya ƙone garkuwoyi.10Ku yi shiru ku sani Ni ne Allah; Zan sami ɗaukaka a cikin al'ummai; Za a ɗaukaka ni a duniya.11Yahweh mai runduna na tare da mu; Allah na Yakubu ne mafakarmu. Saleh
Marubucin yayi magana game da Allah kamar dai shine wurin da mutane zasu iya zuwa don aminci. AT: "Allah ya bamu lafiya da karfi"
Marubucin yayi magana akan zurfin zurfin teku kamar dai zuciyar zuciyar teku ce. A nan ya kwatanta girgizar ƙasa da ta sa duwatsu su narke su faɗa cikin teku. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "duwatsu su girgiza da ƙarfi har su faɗo cikin zurfin teku"
"duk da cewa ruwan teku yana ruri da fushi." Kalmomin "ruri" da "fushi" suna bayyana motsin tashin hankali na tekun yayin hadari mai ƙarfi.
Hoton kogi mai gudana yana nuna zaman lafiya da ci gaba ga garin Allah.
Wannan jumla tana bayanin "garin Allah." AT: "tsattsarkan wuri inda Maɗaukaki yake zaune"
Kalmomin "ita" da "ita" suna nufin "garin Allah."
A nan, kalmar "motsa" ita ce kalmar da aka fassara da "girgiza" a cikin Zabura 46:1. Marubucin ya yi maganar halakar Urushalima da sojoji kamar girgizar ƙasa za ta hallaka shi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "babu abin da zai iya hallaka ta"
Anan, kalmar "girgiza" ita ce kalmar da marubucin yayi amfani da ita a Zabura 46:1 don bayyana tasirin girgizar ƙasa a kan duwatsu. Marubucin yayi maganar kifar da mulkoki da dakaru kamar girgizar kasa zata hallaka su. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "rundunoni sun kifar da masarautu"
"Allah ya daga murya." Marubucin yayi magana akan "murya" a matsayin abun da mutum zai iya ɗauka ya ɗaga sama. Wannan yana nufin cewa muryar ta ƙara ƙarfi. AT: "Allah ya yi ihu"
Marubucin yayi magana game da Allah kamar dai shine wurin da mutane zasu iya zuwa don aminci. AT: "Allah na Yakubu yana bamu aminci"
"Ya sa al'ummai su daina yaƙe-yaƙe"
Anan, Allah ya fara magana.
Waɗannan jimlolin guda biyu ma'anarsu ɗaya ce kuma suna jaddada cewa mutanen kowace al'umma a duniya za su ɗaukaka Allah. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane daga kowace al'umma za su girmama ni; mutane a duk faɗin duniya za su ɗaukaka ni"
Marubucin yayi magana game da Allah kamar dai shine wurin da mutane zasu iya zuwa don aminci. Duba yadda kuka fassara waɗannan layukan a cikin Zabura 46: 6.
1Ku tafa hannuwanku, ku dukkan mutane; ku yi sowa ga Allah da muryar nasara.2Gama Yahweh Maɗaukaki abin tsoro ne; shi Sarki ne mai girma bisa dukkan duniya.3Ya mayar da mutane ƙarƙashinmu, ya sa al'ummai a ƙarƙƙashin ƙafafunmu.4Ya zaɓi gãdonmu dominmu, ɗaukakar Yakubu wanda ya ke ƙauna. Selah5Allah ya tafi sama da sowa, Yahweh da ƙarar kakaki.6Raira waƙoƙin yabo ga Allah. raira waƙoƙin yabo; raira waƙoƙin yabo ga Sarkinmu, raira waƙoƙin yabo.7Gama Allah Sarki ne a kan dukkan duniya; raira woƙoƙin yabo da ganewa.8Allah yana mulki a kan al'ummai; Allah na zaune a tsattsarkan kursiyinsa.9'Ya'yan sarakuna sun tattaru wurin mutanen Allah na Ibrahim; gama garkuwoyin duniya na Allah ne; yana da ɗaukaka mai girma.
Tafada hannu yana hade da biki. AT "Tafada hannuwanku cikin murna"
"ku yi ihu ga Allah da muryoyi masu daɗi." Anan kalmar "nasara" na nuni ga farincikin da ke tattare da cin nasara.
Waɗannan jumlolin guda biyu suna a layi ɗaya kuma suna nufin cewa Allah ne ya ba Isra’ilawa damar cin abokan gaba.
Marubucin yayi magana game da ƙasar Isra'ila kamar dai gadon da Allah ya ba mutane a matsayin mallaka ta har abada. AT: "Ya zaɓi wannan ƙasar ta zama gado a gare mu"
Wannan jimlar ta yi daidai da jimlar da ta gabata. Ana iya samar da fi'ilin don tsabta. AT: "Yahweh ya hau yayin da mutane suke busa ƙahoni"
An maimaita kalmar "raira yabo" don girmamawa. Kuna iya barin maimaitawa idan ya kasance mara kyau a yarenku. Madadin fassara: "Ku raira waƙa, ku raira yabo ga Allah; ku raira waƙa, ku raira yabo ga Sarkinmu"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne cewa "garkuwa" 1) tana nufin kayan yaƙi. AT: "Allah yana da iko fiye da makaman dukkan sarakuna a duniya" ko 2) yana nufin shuwagabannin al'ummomin da ake magana akansu kamar garkuwa masu kare al'ummominsu. AT: "Sarakunan duniya suna ƙarƙashin Allah"
1Yahweh mai girma ne kuma a yabe shi da girma, cikin birnin Allahnmu a tsauni mai tsarki.2Mai kyakkyawan tsawo, farincikin duk duniya, shi ne Tsaunin Sihiyona, a kusurwoyin arewa, birnin sarki mai girma.3Allah ya maida kansa sananne a cikin fadodinta a matsayin mafaka.4Gama, duba, sarakuna sun tattaro kansu; suna wucewa tare.5Suka gan ta, sa'an nan suka yi mamaki; suka damu ƙwarai, sai suka wuce da sauri.6Firgici ya mamaye su a wurin, da azaba kamar ta mace mai naƙuda.7Da iskar gabas ka karya jiragen ruwan Tarshish.8Kamar yadda muka ji haka muka gani a birnin Yahweh mai runduna, a birnin Allahnmu; Allah zai kafa shi har abada. Selah9Mun yi tunanin amintaccen alƙawarinka, Allah. a tsakiyar haikalinka.10Kamar yadda sunanka ya ke, Allah, haka yabonka har ga iyakar duniya; hannun damanka na cike da ayyukan adalci.11Tsaunin Sihiyona yi murna, bari 'ya'ya mata na Yahuda su yi farinciki saboda shari'unka masu adalci.12Yi tafiya a kewayen Dutsen Sihiyona, je ka kewaya ta, harabarta da hasumiyarta,13lura da bangayenta sosai kuma ka duba fãdodinta da kyau, don ka faɗa wa tsara mai zuwa.14Gama wannan Allahn shi ne Allahnmu har abada abadin; shi zai bi damu har mutuwa.
Wannan ishara ne ga Yerusalem, wanda aka gina akan Tsaunin Sihiyona.
"Kyakkyawa kuma babba." Kalmar "daukaka" tana nufin yadda Tsaunin Sihiyona yake.
Anan kalmar "ƙasa" tana nufin duk wanda ke rayuwa a duniya. Ana iya fassara kalmar "farin ciki" azaman aiki. AT: "Tsaunin Sihiyona yana ba da farin ciki ga kowa a duniya" ko "kowa a duniya yana farin ciki saboda Tsaunin Sihiyona"
Marubucin yana magana ne game da sarakuna tsoro kamar dai mutum ne ya sa sarakuna da rundunoninsu suka yi rawar jiki. AT: "A can suka yi rawar jiki da tsoro"
Marubucin yayi magana game da sarakuna tsoro kamar dai azabar da mace ke fuskanta yayin haihuwa kuma yana magana game da wannan zafi kamar mutum ne. Ana iya samar da fi'ilin daga sashin da ya gabata. AT: "zafi ya kama daga cikinsu, kamar lokacin da mace take nakuda" ko "sun firgita, kamar mace tana tsoron fuskantar azaba"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan kwatanci ne wanda marubucin ya bayyana sarakuna suna jin tsoro kamar jiragen ruwa ne da ke girgiza saboda Allah yana halakar da su da iska mai ƙarfi. AT: "Sun girgiza da tsoro, kamar yadda jiragen ruwan Tarshish suke girgiza lokacin da kuka farfasa su da iskar gabas" ko 2) wannan tawaye ne wanda marubucin ya bayyana ikon Allah mai girma.
Duk waɗannan kalmomin suna nufin Yerusalem. AT: "a cikin garin Allahnmu, Yahweh Mai Runduna"
"kamar yadda muke a haikalinku"
Wannan karin magana ne wanda yake nufin ko'ina a cikin kalmar. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Zabura 46:8.
Marubucin yayi maganar adalci kamar wani abu ne da Allah zai iya riƙewa a hannunsa. Anan kalmar "hannu" tana nufin ikon Allah da ikon yin sarauta. AT: "kuna mulki da adalci" ko "ku masu adalci ne kamar yadda kuke mulki"
Marubucin yayi magana akan Tsaunin Sihiyona kamar dai mutum ne wanda zai iya murna. Yankin yana nufin mutanen da ke zaune a Yerusalem. AT: "Bari waɗanda ke zaune a Tsaunin Sihiyona su yi murna"
Marubucin ya yi maganar biranen Yahuda kamar ’ya’yan Yahuda ne. Jumlar tana nufin mutanen da suke zaune a waɗancan garuruwan. AT: "bari mutanen da ke zaune a cikin biranen Yahuda su yi murna"
Waɗannan jumlolin biyu daidai suke. AT: "Ku yi tafiya a ko'ina cikin Tsaunin Sihiyona"
Ana iya fassara kalmar "jagora" azaman aiki. AT: "zai shiryar da mu"
1Ku ji wannan, dukkanku mutane; ku kasa kunne, dukkanku mazaunan duniya, ƙanana da manya,2masu arziki da matalauta dukka.3Bakina zai yi maganar hikima kuma nazarin zuciyata zai zama na ganewa.4Zan sa kunnena ga misali; zan fara misalina da molo.5Me zai sa in ji tsoron kwanakin mugunta, sa'ad da zunuban maƙiyana suka kewaye ni.6Me zai sa in ji tsoron waɗanda suka dogara ga wadatarsu suke kuma yin fahariya game da arzikinsu?7Tabbas babu wanda zai iya fansar ɗan'uwansa ko ya ba Allah fansa dominsa,8Gama 'yantar da ran wani na da tsada, kuma ba wanda zai iya biyan bashinmu.9Babu wanda zai dawwama da har jikinsa ba zai ruɓe ba.10Gama zai ga ruɓa. Masu hikima na mutuwa; wawaye da sakarkaru ma na lalacewa su kuma bar wadatarsu ga waɗansu.11Tunaninsu na can ciki shi ne iyalansu zasu cigaba har abada, wuraren da suke zama kuma, su cigaba har dukkan tsararraki; suna kiran gonakinsu da sunayensu.12Amma mutum, mai arziki ba shi rayuwa har abada; yana kamar dabbobi dake mutuwa.13Wannan, hanyarsu, ita ce wautarsu; duk da haka bayansu, mutane suna amincewa da maganganunsu.14Kamar tumaki an ƙaddara su ga Lahira, kuma mutuwa zata zama mai kiwon su. Adalai zasu yi mulki a kansu da safe, kuma jikunansu zasu hallaka a Lahira, tare da rashin wurin zama dominsu.15Amma Allah zai 'yantar da rai na daga ikon lahira; zai karɓe ni. Selah16Kada ka ji tsoro sa'ad da wani ya yi arziki, kuma darajar gidansa ta ƙaru.17Gama sa'ad da ya mutu ba zai tafi da komai ba; darajarsa ba zata tafi tare da shi ba sa'ad da ya mutu.18Ko da mutum yana farinciki da nasararsa saboda arzikinsa yayin da ya ke raye- kuma mutane na yabonka sa'ad da kake rayuwa don kanka-19zai tafi zuwa tsarar ubanninsa kuma ba za su ƙara ganin haske kuma ba.20Mai wadata amma ba shi da ganewa yana kamar dabbobi, dake lalacewa.
Waɗannan jumlolin biyu dai-dai suke. Tare suna ƙarfafa umarnin ga dukkan mutane su saurara.
Anan kalmar "baki" tana nufin gaba daya mutumin da yake magana. AT: "Zan yi magana da kalmomin hikima"
Anan kalmar "zuciya" tana wakiltar hankali da tunani. Ana iya fassara sunayen suna "zuzzurfan tunani" da "fahimta" azaman kalmomi. AT: "tunanin da nake yin bimbini a kansa zai taimaka muku fahimtar"
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) marubucin ya yi magana game da muguwar sha'awar abokan gabansa kamar dai shi mai farauta ne da ke shirin riske shi. AT: "lokacin da muguntar mutane masu zunubi ke shirin yin nasara da ni" ko 2) abokan gaba na marubucin sun kewaye shi yayin da suke aikata muguntarsu. AT: "lokacin da maƙiyana suka kewaye ni"
Waɗannan mutane sun amince da dukiyoyinsu za su hana su shan wahala.
Duk waɗannan kalmomin suna bayyana cewa mutum ba zai iya ba Allah isasshen kuɗi don ya iya guje wa mutuwa ba. AT: "babu wanda zai iya biyan kuɗi ga Allah don ɗan'uwansa ba zai mutu ba"
Wannan yana nufin jikin da ke ruɓewa a cikin kabari.
Marubucin yana magana ne akan dukkan mutane ta hanyar yin nuni ga waɗanda suke da mafi ƙarancin hikima.
Ana iya samar da kalmar daga jimlar da ta gabata. AT: "wuraren da suke zaune zasu ci gaba har zuwa tsararraki duka"
"suna sanya wa ƙasashensu sunayensu." Wannan jimlar tana nuna mallaka.AT: "suna da nasu ƙasashen"
Marubucin yayi maganar makomar wawaye kamar dai shine makoma a ƙarshen hanyar da suke tafiya a kanta. AT: "Wannan shi ne makomar waɗanda ke yin wauta"
Marubucin yayi magana game da maza suna mutuwa ta hanyar siffanta mutuwa a matsayin makiyayi wanda ke jagorantar su zuwa kabari. AT: "mutuwa za ta tafi da su kamar yadda makiyayi ke jagorantar tumaki don yanka"
Marubucin yana maganar Lahira, wurin matattu, kamar dai mutum ne ko dabba. Ya yi maganar ruɓewar gawawwaki kamar Lahira yana cinsu. AT: "jikinsu zai bazu a cikin kabari"
Marubucin yayi maganar Lahira kamar mutum ne wanda yake da iko akan waɗanda suka mutu. Daga mahallin, ana nuna cewa wannan ikon yana nufin cinye jikin matattu.
Kalmar nan “daukaka” a nan tana nufin wadata ko arziki. Abubuwan da ke yiwuwa ma'anar su ne 1) "lokacin da ya kara samun dukiya a gidansa" ko 2) "lokacin da danginsa suka yi arziki."
Jimlar "sauka" tana nufin lokacin da mutumin ya mutu. AT: "ɗaukakarsa ba za ta tafi tare da shi ba lokacin da ya mutu" ko "ba zai riƙe sunansa ba lokacin da ya mutu"
Anan kalmar “kurwa” na nufin mutum dukka. Wannan jumlar tana nufin cewa ya ɗauki kansa mai farin ciki da nasara saboda wadatar sa. AT: "Ya taya kansa murna"
Kalmar "su" tana nufin mawadacin da kakanninsa. Kalmar "haske" na iya nufin rana ko kuma abin kwatance ne na rayuwa. AT: "ba za su sake ganin rana ba" ko "ba za su sake rayuwa ba"
1Maɗaukaki, Allah, Yahweh, ya yi magana yana kiran duniya daga fitar rana zuwa faɗuwarta.2Daga Sihiyona, wuri mafi kyau, Allah yana haskakawa.3Allahnmu ya zo kuma ba ya tsaye shiru; wuta na ci a gabansa, kuma babban hadari na kewaye da shi.4Ya kira sammai da duniya domin ya shar'anta mutanensa.5Tattaro mani amintattuna dukka gare ni, waɗanda suka yi alƙawari dani ta miƙa hadaya."6Sammai zasu yi shelar ayyukan adalcinsa, gama Allah da kansa alƙali ne. Selah7Ku ji, mutanena, kuma zan yi magana; Ni ne Allah, Allahnku.8Ba zan kwaɓe ku domin hadayunku ba; hadayunku na ƙonawa na gabana kullum.9Ba zan ƙarɓi bijimi daga gidanku ba, ko kuwa bunsurai daga garkenku ba.10Gama kowanne naman jeji nawa ne da shanun kan tuddai dubu.11Na san dukkan tsuntsayen duwatsu, kuma namomin jeji na fili nawa ne.12Idan ina jin yunwa, ba zan faɗa maku ba; gama duniya tawa ce, da dukkan abin da ke cikinta.13Ko zan ci naman bijimai ko in sha jinin awakai?14Ku miƙa wa Allah hadayar godiya, kuma ku bada alƙawaranku ta rantsuwa ga Mai iko dukka.15Ku yi kira gare ni a ranar damuwa; Zan cece ku, kuma zaku girmama ni."16Amma ga mugaye Allah yace, "Me zaku yi da furtawar farillaina, har da zaku ɗauki alƙawarina a bakinku,17tunda kun ƙi umarnina kuma kun jefar da maganganuna?18Sa'ad da kuka ga barawo, kuka yarda da shi; kuna ayyuka tare da waɗanda ke yin zina.19Kun bada bakinku ga mugunta, kuma harshenku na fitar da ruɗu.20Ka zauna kana magana gãba da ɗan'uwanka; ka na saran ɗan mahaifiyarka.21Kun aikata waɗannan abubuwan, amma na yi shiru, sai kuka zata cewa Ni kamarku nake. Amma zan kwaɓe ku in kawo a gaban idanuwanku, dukkan abubuwan da kuka yi.22Ku lura da wannan da kulawa, ku da kuka mance da Allah, ko kuma zan yayyaga ku gutsu-gutsu, kuma babu wanda zai zo ya taimake ku!23Wanda ya ke miƙa hadayar godiya yana yabona ne, kuma ga duk wanda ya ke rayuwarsa a hanyar da ta dace zan nuna masa ceton Allah."
Marubucin yayi amfani da sunaye daban-daban guda uku yayi maganar Allah.
Wannan jumlar tana nufin kwatance a gabas, inda rana take fitowa, da yamma, inda rana take fadi. Marubucin yayi amfani da waɗannan tsauraran matakan biyu don wakiltar ko'ina a duniya. AT: "ko'ina a duniya"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Sihiyona, wanda kyawunsa cikakke ne" ko 2) "Sihiyona, mafi birni mafi kyau."
Marubucin yayi amfani da wannan kalami mara kyau don jaddada mai kyau. AT: "yayi magana ta yadda kowa zai iya jin sa"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Allah yana kiran duk waɗanda ke sama da ƙasa su zama shaidu kamar yadda yake hukunta mutanensa ko 2) Allah yana magana da sama da ƙasa kamar dai su mutane ne, kuma yana kiransu su zama shaidu yayin da yake hukunta mutanensa.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) marubucin ya yi amfani da kalmar "sammai" don yin nuni ga mala'ikun da ke zaune a wurin ko kuma 2) marubucin ya yi maganar "sammai" kamar dai su mutane ne da suka yi shaidar adalcin Allah.
"Zan tsawatar muku, amma ba don sadaukarwar ku ba." Allah ya bayyana cewa sadaukarwarsu ba shine dalilin yake tsawatar musu ba.
Wannan yana bayanin dalilin da yasa Allah baya tsawatar musu game da hadayunsu. Kalmomin "koyaushe suna gabana" yana nufin kasancewa a gaban Allah kuma yana nufin cewa mutanensa koyaushe suna miƙa masa hadayu na ƙonawa. AT: "koyaushe kuna miƙa hadayu na ƙonawa gareni"
Jumlar "a kan duwatsu dubu" ba ta wakiltar adadin shanun da Allah ya mallaka. Lambar wuce gona da iri ce da ke jaddada cewa Allah ya mallaki dukkan shanu a duniya. Ana iya samar da kalmar daga jimlar da ta gabata. AT: "duk shanun da ke duniya nawa ne"
Allah ya yi wannan tambaya ta zance don ya nanata cewa ba ya yin waɗannan abubuwa don haka ba shi da bukatar sadaukarwa. AT: "Bana cin naman bijimai ko shan jinin awaki."
Marubucin yayi magana akan "alwashi" kamar suna kudin da mutum yake biya ga Allah. AT: "ku cika alwashin da kuka yi wa Maɗaukaki" ko "ku yi abin da kuka alkawarta wa Maɗaukaki ya yi"
Anan kalmar "yini" tana nufin kowane lokaci. AT: "duk lokacin da kuka sami matsala"
Anan Allah yana magana har yanzu kuma yana magana kansa game da mutum na uku. AT: "Amma ga miyagu na ce"
Allah yayi magana akan mugayen mutane suna karanta kalmomin alkawarinsa kamar suna sanya alkawarin a bakinsu. AT: "magana game da alkawarina"
Allah yana magana akan mutumin da yake faɗar mugayen abubuwa kamar dai bakin mutumin saƙo ne wanda mutumin yake aikawa don aikata mugunta. AT: "Kullum kuna faɗin mugunta"
Kalmar "harshe" tana wakiltar mutumin da yake magana. AT: "Kullum kuna yin ƙarya"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya amma suna amfani da kalmomi daban-daban. Allah ya zarge su da yin ƙarya game da danginsu.
Tunda Allah yayi shuru kuma bai tsawata wa mugayen mutane ba saboda ayyukansu, suna ganin cewa Allah ya yarda da abin da sukayi. AT: "kun yi zato cewa ni wani ne mai aikata abin da kuke yi"
Allah yana maganar mugaye sun ƙi shi kamar sun manta shi. Yana maganar kansa a mutum na uku. AT: "ku da kuka ƙi ni"
Allah yayi magana akan hanyar da mutum yake rayuwa kamar wata hanya ce da mutum yake tafiya. AT: "yana rayuwarsa yadda ya dace"
Bayyanar sunan "ceto" ana iya bayyana shi azaman "ajiye". Allah yana nufin kansa a cikin mutum na uku. AT: "Zan cece shi"
1Ka yi mani jinƙai, Allah, saboda amintaccen alƙawarinka; saboda kana yin ayyukan jinƙai masu yawa, ka tsige kurakuraina.2Ka wanke ni sosai daga zunubina ka share mani laifina.3Gama na san kurakuraina, kuma laifina yana gabana kullum.4Gãba da kai, kai kaɗai, na yiwa laifi kuma na yi abin mugunta a fuskarka; ka yi dai-dai sa'ad da kayi magana; baka yi kuskure ba sa'ad da ka shar'anta.5Duba, An haife ni a cikin zunubi; tun daga cikin mahaifiyata, ina cikin zunubi.6Duba, kana so in yi marmarin aminci cikin zuciyata; a cikin zuciyata zaka sa in san hikima.7Ka tsarkake ni da abin tsarkakewa, zan kuwa tsarkaka; ka wanke ni, zan kuwa fi auduga fari.8Ka sa in ji daɗin rai da murna saboda ƙasusuwan da ka karya suyi farinciki.9Ka ɓoye fuskarka daga laifofina ka hure dukkan zunubaina.10Ka sa in so yi maka biyayya kullum, Allah, ka sa kullum in so yin abin da ke dai-dai.11Kada ka kore ni daga gare ka, kar kuma ka ɗauke mani Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.12Ka maido mani da farincikin cetonka, ka riƙe ni da ruhun yin biyayya.13Sa'an nan zan koya wa masu zunubi hanyoyinka, masu laifi kuma zasu komo gare ka14Ka gafarce ni domin zub da jini, Allahn cetona, sai in yi sowa domin farincikin ayyukan adalcinka.15Ubangiji, ka buɗe leɓunana, sai bakina ya furta yabonka.16Gama baka murna da sadaka, da zan bada ita; Baka jin daɗin baye-bayen ƙonawa.17Hadayu na Allah sune karyayyen ruhu. Kai, Allah, baza ka ƙi zuciya mai tuba da kuma tawali'u ba.18Kayi nagarta cikin managarcin jin daɗinka ga Sihiyona; ka sake gina garun Yerusalem.19Sa'an nan zaka yi murna da sadakokin ayyukan aɗalci da baye-bayen ƙonawa da ainihin baye-yen ƙonawa; sa'an nan mutanenmu zasu miƙa bijimai a bagadinka.
"saboda kuna yawan jinkai"
Ana magana game da gafarta zunubai kamar 1) share su ko 2) share rubutaccen zunuban. AT: "gafarta zunubaina kamar wanda ya goge wani abu" ko "manta da zunubaina kamar wanda ya goge bayanan zunubai"
Ana magana game da yarda da Allah a matsayin mai tsabta. Allah yana sa mutane su zama karɓaɓɓu ta wurin gafarta zunubansu. AT: "Ka wanke dukkan zunubina" ko "Ka gafarta min zunubaina duka ta yadda zan yarda da ku"
Ana magana game da yarda da Allah a matsayin mai tsabta. Allah yana sa mutane su zama karɓaɓɓu ta wurin gafarta zunubansu. AT: "Ku tsarkake ni daga zunubina" ko "ku gafarce ni don zunubina don in kasance mai tsabta"
Rashin iya mantawa da zunubansa ana maganarsa kamar koyaushe suna gabansa inda zai gansu. AT: "A koyaushe ina sane da zunubaina" ko "Ba zan iya mantawa da zunubaina ba"
Kalmar nan “gani” a nan tana wakiltar hukunci. Yahweh ya ga ayyukan Dauda, bai kuma yarda da su ba.AT: "abin da kuke ganin mugunta ne" ko "abin da kuke ganin mugunta ne"
Kasancewa mai zunubi ana magana akan kasancewa cikin mugunta. AT: "Na kasance mai zunubi ne lokacin da aka haife ni"
Kasancewa mai zunubi ana magana akan kasancewa cikin zunubi. AT: "ko da mahaifiyata ta ɗauki cikina, ni mai zunubi ne"
“Zuciyar cikin” tana wakiltar 1) sha'awar mutum ko 2) dukan mutumin. AT: "kuna son in so amintacce" ko "kuna so na zama amintacce"
Marubucin yayi magana game da Allah kamar Allah firist ne wanda zai yayyafa masa ruwa don ya sami karɓaɓɓe ga Allah. AT: "Ka sanya ni karɓa ta wurin yayyafa mini ruwa a ɗaɗɗoya" ko "Ka gafarta mini zunubaina don in zama karɓaɓɓe a gare ku"
Jin bakin ciki da yawa ana maganarsa kamar kashinsa ya karye. AT: "don kun jawo min baƙin ciki a cikina. Bari in sake yin farin ciki"
Tunani game da zunuban wani ana maganarsa kamar ganin su. Ana yin afuwa ko ƙin yin tunani game da zunubai kamar zaɓaɓɓen ganin su. AT: "Kada ku kalli zunubaina" ko "Kada ku tuna zunubaina"
Anan “zuciya” tana wakiltar yadda ake ji da sha’awa. Ana magana game da keɓewa gaba ɗaya da yin biyayya ga Allah azaman tsarkakakkiyar zuciya. AT: "Ka sanya ni cikakkiyar sadaukar da kai gare ka" ko "Ka sa ni so in yi maka biyayya koyaushe"
Anan “ruhu” yana wakiltar halaye da sha'awar Dauda. AT: "sa halina ya zama dai-dai" ko "sa ni koyaushe in yi abin da ke dai-dai"
"Kar ka tilasta min na rabu da kai." Ana magana game da ƙiwar Allah kamar ana tilasta shi barin shi. AT: "Kada ku ƙi ni ɗaya daga mutanenku"
"riƙe ni" ko "taimake ni"
Wannan jumlar tana nufin kashe wani mutum.
"Hadayu da ke faranta wa Allah rai"
Kasancewa da tawali'u da nadama ga zunubin mutum ana magana ne akan samun karyayyar zuciya da nadama. Zuciya tana wakiltar motsin rai da so. AT: "baƙin ciki da tawali'u" ko "mutumin da ya yi nadama don zunubinsa da tawali'unsa"
Bangon birni yana kiyaye birni da mutanen da ke ciki. Mai iya yiwuwa su ne 1) "ba mu damar sake gina ganuwar Yerusalem" ko 2) "kare Yerusalem da ƙarfafa ta"
1Meyasa kuke taƙama da tada fitina, ku manyan mutane? Alƙawarin Allah mai aminci yana zuwa kullum.2Harshenku yana shirya hallakarwa kamar reza mai kaifi, kuna aikata yaudara.3Kuna ƙaunar mugunta fiye da nagarta ƙarya kuma fiye da maganar adalci. Selah4Ka na ƙaunar maganar da zata hallaka waɗansu, kai harshe mai yaudara.5Haka Allah zai hallaka ka har abada, zai ɗauke ka daga rumfarka ya tumɓuke ka daga ƙasar masu rai. Selah.6Masu adalci zasu gani su ji tsoro; su yi masa dariya su ce,7"Ku dubi mutumin da bai mayar da Allah wurin fakewarsa ba, amma ya dogara ga dukiya da yawa, kuma yana da ƙarfi sa'ad da ya hallaka waɗansu."8Amma ni, ina kama da itacen inabi mai sheƙi a cikin gidan Allah; zan dogara ga alƙawarin Allah mai aminci har abada.9Zan yi godiya gare ka har abada saboda abin da kayi. Zan jira ga sunanka, saboda yana da kyau a cikin taron jama'arka masu tsoron ka.
Wannan tambayar ta nuna irin fushin da Dauda ya yi da wanda ya kawo matsala. AT: "Bai kamata ku yi alfahari da yin matsala ba, ya mai girma."
Dauda yayi maganar amincin alkawarin Allah kamar wani abu ne da zai iya zuwa. Wataƙila Dauda yana magana ne game da alkawuran Allah na kāre mutanensa daga mugayen mutane. Cikakken sunan "aminci" za a iya fassara shi azaman sifa ko karin magana. AT: "Kowace rana, Allah mai aminci ne ga cika alkawaran alkawarinsa" ko "Kowace rana, Allah da aminci yana kiyaye mutanensa daga mugayen mutane kamar ku"
Anan ana kwatanta harshe da kaifin reza wanda ke iya haifar da lahani mai yawa. AT: "Harshenku yana cutar da mutane kamar kaifin reza, idan kun shirya lalata kuma kuna yaudarar wasu"
"kuna son ƙarya fiye da fadan abinda yake dai-dai"
A nan ana magana da kalmomin da ke cutar da wasu kamar dabbobi ne da ke cinye mutane. AT: "kalmomin da ke cutar da wasu"
Ana maganar rayuwa a duniya kamar mutane suna da shuke-shuke masu tushe a cikin ƙasa. Ana maganar Allah kashe wani kamar tono tushen tsire-tsire da fitar da shi daga cikin ƙasa. AT: "zai fitar da ku daga ƙasar masu rai" ko "Zai kashe ku don haka ba za ku ƙara kasancewa tare da masu rai a duniya ba"
"Masu adalci kuma zasu ga Allah ya cire shi kuma zasu ji tsoro"
Ana maganar kasancewa cikin aminci da kwanciyar hankali kamar itace mai ƙarfi. AT: "Ina da ƙarfi a cikin gidan Allah, kamar itacen zaitun ɗan kore" ko "Saboda ina yin sujada a cikin gidan Allah, na sami kwanciyar hankali kamar itacen zaitun ɗan kore"
Sunan Allah yana wakiltar Allah da kansa. Jiran Allah wakiltar jiran Allah ya taimake shi. AT: "Zan jira ku, saboda kuna da kyau" ko "Zan jira ku don ku taimake ni, domin kuna da kyau"
1Wawa a zuciyarsa yace, "Babu wani Allah." Dukkan su sun gurɓace sun yi aikin mugunta; babu ko ɗaya dake aikata abin kirki.2Allah ya dubo 'yan Adam daga sama, ya gani ko akwai wani mai fahimta, wanda ke neman sa.3Dukkan su sun fanɗare. Gabaɗayan su sun gurɓace. Ba wani mai aikata abin kirki, babu ko guda ɗaya.4Waɗanda ke aikata mugunta basu da fahimta ne--waɗanda ke cin naman mutanena kamar suna cin gurasa kuma ba su kira ga Allah ba?5Suna cikin tsoro mai yawa ko da ya ke ba wani abin tsoratarwa; gama Allah zai tarwatsa duk wanda ya yi maku kwanto; irin waɗannan mutane zasu sha kunya gama Allah ya ƙi su.6Oh, dama ceton Isra'ila ya zo daga Sihiyona! Sa'ad da Allah ya dawo da mutanensa daga bauta, Yakubu zai yi farinciki, Isra'ila kuma zai yi murna!
Wannan yana nufin dukkan mutane.
Ana magana game da ƙin Allah da abin da yake daidai kamar juya baya. AT: "Dukkansu sun juya baya ga aikata abin da yake daidai" ko "Duk sun ƙi Allah"
Ana maganar halakar mutane kamar cinsu. Yin shi kamar suna cin burodi yana nuna cewa sun yi shi da sauƙi ko kuma ba tare da jin laifi game da shi ba. AT: "waɗanda ke halakar da mutanena kamar yadda suke cin burodi"
Fasa kasusuwan mutane yana nuna kashe su da kuma barin ƙashinsu ya kasance a duk inda suka mutu kuma ba za a binne su da kyau ba. "Allah zai hallakar da duk wanda zai yi yaƙi da kai, kuma ƙasusuwansu za su warwatse a ƙasa"
Ceto yana wakiltar Allah, mai ceto, wanda haikalin yake a Sihiyona. AT: "Mai ceton Isra'ila zai zo daga Sihiyona" ko "Allah zai zo daga Sihiyona ya ceci Isra'ila"
"Idan Allah ya tseratar da mutanensa da ke tsare"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya.
1Ka cece ni ya Allah, ta wurin sunanka, ka yi mani shari'a cikin ƙarfin ikonka.2Allah, ka ji addu'ata, ka saurari kalmomin bakina.3Gama bãƙi sun afko mani, lalatattun mutane na neman raina, basu sa Allah a gabansu ba. Selah.4Duba, Allah shi ne mai taimako na, Ubangiji shi ne mai tallafa ta.5Zai saka wa maƙiyana da mugunta; cikin amincinka, ka hallaka su!6Zan baka hadaya ta yardar rai, zan yi godiya ga sunanka, Yahweh gama haka na da kyau.7Gama ya kuɓutar dani daga kowacce damuwa; idona na duban nasara a kan maƙiyana.
Anan sunan Allah yana wakiltar halayensa. Yana iya wakiltar musamman ikonsa ko adalcinsa. AT: "Ka cece ni, ya Allah, da ikonka"
"mutanen da basu da rahama"
Kafa Allah a gabansu yana wakiltar mai da hankali ga Allah. AT: "ba sa mai da hankali ga Allah" ko "sun yi watsi da Allah"
Ana yin hukunci kamar ana biya. AT: "Zai aikata mugunta ga magabtana kamar yadda suka yi mini" ko "Zai sa muguntar da magabtana suka yi mini a yi musu"
Anan Dauda ya canza daga magana game da Allah zuwa magana da Allah. AT: "Allah, ka hallaka su saboda ka kasance da aminci a gare ni"
Sunan Yahweh yana wakiltar shi. AT: "Zan yi maka godiya, ya Yahweh, don kana da kirki"
Ido yana wakiltar mutum. AT: "Na duba"
1Allah, ka ji addu'ata, kada ka ɓoye kanka daga roƙona.2Ka saurare ni ka amsa mani, gama bani da hutu cikin wahaluna,3saboda muryar maƙiyana, saboda matsin masu mugunta, gama suna tsananta mani cikin fushi.4Zuciyata tana kiɗima a cikina, tsoron mutuwa ya faɗo kaina.5Firgita da razana sun zo kaina, kuma fargaba ya sha kaina.6Na ce, "Oh, dãma ina da fukafukai kamar kurciya! Da na tashi in je in huta.7Da zan tafi can nesa in zauna a cikin jeji. Selah8Da zan yi hanzari in sami mafaka daga hadari mai iska da guguwa.9Ka haɗiye su, Ubangiji, kasa ruɗami cikin harsunansu! Gama na ga ta'addanci da hargitsi a cikin birnin.10Suna ta yawo a kan ganuwarsa dare da rana. Mugunta da lalata suna cikin tsakiyarsa.11Aikin mugunta na cikin tsakiyarsu; Tsanani da zamba ba su bar hanyoyinsu ba.12Gama da maƙiyi ne ke tsauta mani, da na iya jurewa; ba kuma wanda ya ke gaba dani ne ya tada kansa gaba dani ba, da na ɓoye kaina daga wurin sa.13Amma kai ne mutum kamar ni, abokina, da aminina kuma.14Mun yi zumunci mai kyau tare, mun je gidan Yahweh tare da ƙarfafa.15Bari mutuwa ta afko masu, bara su gangara lahira, gama mugunta ce kaɗai rayuwarsu, haka suke.16Ni kuwa zan kira ga Allah, Yahweh zai cece ni.17Ko da yamma ko da rana ko da safe, idan na yi ƙara da nishi zai ji muryata.18Zai kuɓutar da raina daga masu kawo mani hari, gama waɗanda ke faɗa dani suna da yawa.19Yahweh, wanda ya ke mulki tun daga farko, zai ji su ya ƙasƙantar dasu. Ba zasu taɓa canzawa ba, kuma ba sa tsoron Yahweh.20Abokina ya tada hannuwansa gaba da waɗanda ke zaman salama dani. Bai cika alƙawarin da ya yi ba.21Bakinsa yana da taushi kamar mai, amma zuciyarsa tana da hasala; kalmominsa suna da taushi kamar mai, amma a gaskiya takubba ne zararru.22Ka ɗora wa Yahweh matsalolinka, shi zai riƙe ka, ba zai bari adalai su lalace ba.23Amma kai Allah, za ka kawo miyagu cikin ramin hallakarwa. Masu shan jini da mayaudaran mutane ba za su rayu koda kamar na rabin sauran mutane ba, amma zan dogara gare ka.
Barin kunne yana wakiltar sauraro. AT: "Ku saurari addu'ata"
Ƙi kula da roƙonsa ana maganarsa azaman ɓoye kansa daga gare ta. AT: "kar ku yi watsi da roƙo na"
Anan “murya” tana wakiltar abin da suke faɗa. AT: "saboda abin da maƙiyana ke faɗi"
Anan, "zuciya ta girgiza" tana nufin zafin rai da wahala. Wannan wahala saboda tsoro ne. AT: "Ina wahala saboda tsoro da fargaba"
Ana maganar jin tsoro da rawar jiki kamar ana jin tsoro da rawar jiki abubuwa ne da suke zuwa wa mutum. AT: "Na tsorata sosai kuma na yi rawar jiki"
Wannan motsin rai yana bayyana wani abu da marubuci yake so sosai. AT: "Ina fata sosai da ina da fukafukai kamar kurciya"
"Da ina da fikafikai, da sai in tashi"
"Harshe" a nan yana wakiltar abin da mutane ke gaya wa juna, kuma mai yiwuwa yana nufin musamman su ne suna magana game da shirye-shiryen aikata mugunta. Rikita shi yana wakiltar sanya mutane su kasa fahimtar junan su. AT: "dame su yayin da suke magana da juna" ko "rikita shirinsu"
Ana maganar mugunta da matsala kamar dai mutane. Ana iya bayyana wannan ta hanyar gayawa game da mutanen da suke aikata mugunta da matsala. AT: "mutane suna aikata mugunta suna haifar da matsala a tsakiyar gari" ko "mutane suna aikata abubuwan zunubi kuma suna haifar da matsala a ciki"
Ana magana da zalunci da yaudara kamar suna mutane. Ana iya bayyana wannan ta hanyar faɗi game da mutanen da ke zaluntar wasu kuma suna yaudarar su. AT: "Mutane suna zaluntar wasu kuma suna yaudarar su a titunan birni, kuma basa barin" ko kuma "Mutane koyaushe suna zalunci da yaudarar wasu a titunan birni"
Yin magana da girman kai da zagin wani ana maganarsa kamar ɗaga kansa akan wani. AT: "cin mutunci na" ko "raina ni"
Ana iya raba wannan kuma a fara sabon jumla. AT: "kaina. Kun kasance abokina kuma babban abokina"
Ana maganar mutuwa kamar mutum ne da zai iya afkawa mutane. AT: "Bari maƙiyana su mutu farat ɗaya"
Ana maganar mugunta kamar abu ne wanda zai iya kasancewa a wani wuri. Maganar muguntar da magabtansa suka saba magana ana maganarsu kamar mugunta tana tare da su ko kuma kusa da su. AT: "koyaushe suna aikata mugunta a inda suke zaune"
"don mutane da yawa sun yi yaƙi da ni"
Yadda Allah zai wulakanta su za a iya bayyana a sarari. AT: "zai kayar da su kuma zai wulakanta su"
Kiwon hannu a kan mutane yana wakiltar kai musu hari. Wannan na iya zama ishara ga faɗin abin da ke jefa mutane cikin haɗari ko haifar musu da matsala. AT: "ya afka wa waɗancan" ko "ya ci amanar waɗancan"
Jawabin da yake da daɗi ko kyau a ji shi ana maganarsa kamar tana da sassauƙa da sauƙi a haɗiye ta. AT: "Abin da ya faɗa mai daɗi ne kamar santsi mai laushi" ko "Ya faɗi kyawawan abubuwa"
Mutane suna sanya mai a fatarsu don jin daɗinsu, kuma suna sanya shi a kan raunuka don taimaka musu warkewa. Ana magana wacce take da kirki ko taimako kamar tana da taushi ko kwantar da hankali. AT: "abin da ya faɗa mai daɗi ne kuma mai kwantar da hankali kamar mai" ko "ya faɗi alheri"
Jawabin da yake jawowa mutane matsala ana maganarsa kamar takuba ce da ke cutar da mutane. AT: "abin da ya ce mutanen da suka ji rauni kamar yadda takubba masu jan hankali suke yi" ko "abin da ya faɗa ya jawo wa mutane matsala"
Anan ana maganar matsaloli kamar suna da nauyi da mutane zasu ɗauka. Dogaro da Allah ya taimake mu lokacin da muke cikin matsala ana magana ne game da ɗora mana nauyi a kanmu domin ya iya ɗaukar mana su. AT: "Ka ba Yahweh matsalolinka" ko "Dogara ga Allah ya taimake ka game da duk damuwarka kamar wanda ya amince da mutum mafi ƙarfi don ɗaukar kayansa"
Ana magana game da mutumin da wani irin bala'i zai cutar da shi sosai kamar yana girgiza ko girgiza kuma yana gab da faɗuwa. AT: "ba zai bar mai adalci ya ruɗe ya fado ba" ko "ba zai bar a halaka mai adalci ba"
Wannan yana wakiltar haifar da mutane su mutu. AT: "zai sa mugaye su mutu" ko "zai sa miyagu su mutu kuma su tafi inda matattun suke"
1Ka ji ƙaina ya Allah, gama mutane na kawo mani hari! Dukkan yini suna tsananta ɓatancin da suke yi mani.2Maƙiyana na musguna mani dukkan yini, gama waɗanda ke yin faɗa dani cikin wauta suna da yawa.3Sa'anda na ji tsoro, zan dogara gare ka.4Ina jin daɗin maganar Allah, ga Allah zan dogara; ba zan ji tsoro ba; me mutum kawai zai iya yi ma ni?5Juya maganata suke yi dukkan yini, dukkan tunaninsu a kaina na mugunta ne.6Sun tattara kansu, sun yi kwanto, suna bin sawuna, suna neman raina.7Kada ka bari su dena yin mugunta. Ya Allah, ka kayar da su a cikin fushinka.8Ka lissafa yawace-yawacena ka kuma sa hawayena cikin kwalba; ko ba a cikin littafinka suke ba?9Sa'ad da na kira ka, maƙiyana zasu koma da baya, abin da na sani kenan, Allah yana tare da ni.10A cikin Allah --wanda maganarsa nake yabo, a cikin Yahweh--11a cikin Allah na dogara, bazan ji tsoro ba. Me wani zai iya yi mani?12Aikina shi ne in cika wa'adina gare ka, Yahweh. Zan miƙa baye-baye na godiya a gare ka.13Gama ka kuɓutar da raina daga mutuwa, ka tsare ƙafafuna daga faɗuwa, domin in yi tafiya a gaban Allah a cikin masu rai.
Makiyan mummunan hari ana magana da su kamar suna murkushe jikinsa ta hanyar tafiya a kanta. AT: "Makiyana sun kawo min hari mai tsanani"
Anan ana amfani da tambaya don nuna cewa mai zabura baya jin tsoron mutane, domin ba zasu iya cutar da shi da gaske ba. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "mutum kawai ba zai iya yi min komai ba!" ko "mutum kawai ba zai iya cutar da ni da kyau ba!"
"koyaushe suna da mummunan tunani a kaina" ko "koyaushe suna tunanin miyagun abubuwa da zasu yi mani"
Ana maganar kallon abin da mutum yayi domin ganin yadda za a haifar masa da matsala kamar kallon matakansa, kamar yadda wanda yake son kama mutum yake kallon inda mutumin yake tafiya. AT: "suna kallon duk abin da nake yi"
Ana maganar jiran kashe wani ana maganar ransa. AT: "yayin da suke jira su kashe ni"
Damuwar Allah ga mai zabura ana maganarsa kamar Allah yana lissafa kowane lokaci da mai zabura yayi tafiya cikin baƙin ciki kuma ba shi da wurin zuwa ta'aziyya. AT: "Kun damu da dukkan lokutan da nake yawo ni kad'ai"
Ana magana da damuwar Allah ga mai zabura kamar Allah ya ceci hawayen mai zabura a cikin kwalba. Hawaye na wakiltar kuka. AT: "Kun san yawan kuka na kuma kun damu da ni"
Ana maganar damuwar Allah ga mai zabura kamar ya rubuta adadin hawayen mai zabura a littafinsa. An yi amfani da wannan tambayar don tunatar da Allah game da yadda yake kula da mai zabura sosai. AT: "kun yi rubutu game da su a littafinku!" ko "ka tuna da kukana!"
Wannan yana nufin cewa Allah ya yi masa ni'ima. A cikin wannan mahallin yana nuna cewa Allah yana yaƙi da magabcin mai zabura don ya kāre shi. AT: "Allah yana yaƙi domin ni"
Yin magana a kan wajabta aikata wani abu ana maganarsa kamar idan aikin aikata wani abu ya hau kan mutum. AT: "Dole ne in cika alkawuran da na yi muku" ko "Dole ne in cika abin da na yi muku alkawari zan yi"
Ƙafafun nan suna wakiltar mutum. Faduwa a nan yana iya wakiltar kashewar makiyansa. AT: "ka hana ni faɗuwa" ko "ka hana ni kashewa daga maƙiyana"
Rayuwa da ganin Allah ana magana ne game da tafiya a gaban Allah. AT: "domin in rayu a gaban Allah"
1Ka yi mani jinƙai, Yahweh, ka yi mani jinƙai, gama na fake wurin ka har sai waɗannan wahalu sun wuce. Na tsaya a ƙarƙashin inuwar fukafukanka har sai wannan hallaka ta ƙare.2Zan yi kuka ga Allah Maɗaukaki, ga Allah, wanda ya ke yi mani komai.3Zai aiko da taimako daga sama ya cece ni, yana jin haushin waɗanda ke ƙuje ni. Allah zai aiko mani da jinƙansa da amincinsa.4Raina yana cikin zakuna, ina cikin waɗanda suke a shirye su cinye ni. Ina cikin mutanen da haƙoransu mãsu ne da kibau, haƙoransu kuma kamar takubba masu kaifi.5Ya Yahweh, ka ɗaukaka a bisa sammai, bari ɗaukakarka ta zama a bisa duniya.6Sun baza taru saboda ƙafafuna; Na shiga cikin ƙunci. Sun gina rami a gabana. Amma su da kansu ne suka faɗa a cikin tsakiyarsa! Selah7Zuciyata ta kafu, Allah, zuciyata a kafe take; Zan raira, I, zan raira yabbai.8Tashi, ke zuciyata mai daraja, tashi, ke sarewa da molo, nima tun da asuba zan tashi.9A cikin jama'a zan yi maka godiya, ya Ubangiji; zan raira yabo gare ka a cikin al'ummai.10Gama ƙaunarka tana da girma ƙwarai, ta kai har sama, amincika kuma ya kai gizagizai.11Ka ɗaukaka ya Allah, sama da sammai, darajarka ta ɗaukaka bisa dukkan duniya.
Maganar zuwa ga Yahweh don kariya ana magana ne da neman mafaka a gare shi. AT: "Ina zuwa gare ku don kariya"
Mai zabura yayi magana game da Allah kamar mahaifiya mai tsuntsu wacce take kare itsa itsanta ta hanyar ɗaura su a ƙarƙashin fikafikanta. AT: "Na aminta da ku kare ni"
Wannan ya bayyana dalilin da yasa zai yi kuka ga Allah. Ana iya fassara shi da "saboda." AT: "saboda yana yi min komai"
Kasancewar Allah mai alheri da aminci ana maganarsa kamar yana aiko da alheri da aminci. Nau'in suna "alheri" da "aminci" za a iya bayyana a matsayin "mai alheri" da "amintacce." AT: "Allah zai kasance mai alheri gare ni kuma amintacce"
Makiyan mashi da kibau ana maganarsu kamar na zakoki hakora. Mai zabura yaci gaba da maganar magabtansa kamar zakoki. AT: "mutanen da ke kashe wasu da mashi da kibau kamar yadda zaki ke kashewa da haƙoransu masu kaifi"
Harshen yana wakiltar abin da wani ya faɗi, kuma magabta ana maganarsu da munanan maganganu kamar takuba. AT: "wanda kalmominsa na kama da takuba masu kaifi" ko "waɗanda ke haifar min da masifa ta hanyar abin da suka faɗa"
Mai zabura yana roƙon Allah ya nuna cewa ya ɗaukaka. Daukaka shi sama yana nuna girma. AT: "Allah, ka nuna cewa an ɗaukaka ka sama da sammai" ko "Allah, ya nuna cewa kai mai girma ne a cikin sammai"
Ana magana game da cutarwar da makiyansa suka yi lokacin da suke ƙoƙarin kama shi kamar sun faɗa cikin tarkon da suka yi masa. AT: "Su da kansu sun faɗa cikin ramin da suka haƙa mini" ko "Amma su kansu sun ji ciwo saboda abin da suka shirya yi mini"
Kasancewa mai karfin gwiwa ana magana ne azaman zuciyar mutum tabbatacciya maimakon girgiza ko sauƙin motsawa. An maimaita kalmar don nuna cewa yana da cikakken tabbaci ga Allah kuma ba zai canza ba. AT: "Ina da cikakken yakini da ku, Ya Allah"
Ana iya bayyana a sarari cewa dalilin farkawa shi ne don raira yabo ga Allah. Tashi na iya zama kwatanci don farawa ko shirya yin wani abu. Zuciya tana wakiltar mai zabura ko motsin zuciyar sa. AT: "Ku farka, zuciyata mai daraja, don raira waƙar yabo ga Allah" ko "Zan shirya zuciyata mai daraja don raira waƙar yabo ga Allah" ko "Ina girmamawa in farka in raira yabo ga Allah"
Ana maganar girman ƙaunar Allah mara yankewa kamar ana iya auna ta daga nesa. AT: "ƙaunarka mara mutuƙar girma kamar tazara daga duniya zuwa sama"
Kalmomin "babba naka ne" da "isa" ana fahimtarsu daga jumlar da ta gabata. AT: "amincinka mai girma ne, ya kai gizagizai" ko "amincinku ya kai nisan duniya da gajimare"
Mai zabura yana roƙon Allah ya nuna cewa ya ɗaukaka. Daukaka shi sama yana nuna girma. AT: "Allah, ka nuna cewa an ɗaukaka ka sama da sammai" ko "Allah, ya nuna cewa kai mai girma ne a cikin sammai"
1Ku shugabanni kuna faɗin gaskiya? Ku jama'a kuna yin shari'ar gaskiya?2Babu, kun yi aikin mugunta cikin zuciyarku; kun baza tashin hankali da hannuwanku a cikin ƙasar dukka.3Tun daga cikin ciki, masu mugunta ke fanɗarewa, tun daga haihuwarsu suke ratsewa, suna faɗin ƙarya.4Dafinsu kamar dafin maciji ya ke, suna kama da kurmar ƙasa wadda take toshe kunnuwanta,5wadda bata jin muryar masu layu, komai gwanintarsu.6Ka karairaya haƙoransu a cikin bakunansu, ya Allah; ka ciccire manyan haƙoran 'yan zakuna, ya Yahweh.7Bari su narke kamar ruwan dake gangarewa; idan suka harba kibansu, bari su zama kamar basu yi saiti ba.8Bari su zama kamar dodon koɗi wanda ke narkewa ya lalace, kamar jaririn da mace ta haifa kafin lokacinsa yayi wanda bai taɓa ganin hasken rana ba.9Kafin tukunyarka ta ji zafin wuta, zai kwashe su da guguwa, da ɗanye da wanda a ke ƙonawa dukka.10Mai adalci zai yi farinciki sa'ad da ya ga ramako daga Allah, zai wanke ƙafafunsa da jinin masu mugunta,11domin mutane su ce, "Gaskiya ne akwai lada ga mutum mai adalci, gaskiya ne akwai Allah wanda ke shar'anta duniya.
Marubucin yayi amfani da wannan tambayar don tsawata wa masu mulki saboda basa magana da adalci. AT: "Ku masu mulki ba ku faɗi abin da yake dai-dai ba!"
Marubucin yayi amfani da wannan tambayar don tsawata wa alƙalai waɗanda ba sa yin hukunci dai-dai. AT: "Ba ku taɓa yanke hukunci ga mutane daidai!"
Zuciya tana nufin tunani ko shirin mutane. AT: "kuna aikata mugunta a cikin tunaninku" ko "kuna tunanin aikata mugunta"
Miyagun maganganun mutane ana maganarsu kamar dafi. AT: "Mummunan kalaman nasu suna haifar da matsala kamar yadda gubar maciji ke cutar mutane"
Ana magana da leda da ba ta amsa waƙar mai fara'a ba kamar za ta iya sa wani abu a kunnuwan ta don kada ta ji. AT: "kurmar da ba ya saurara"
Marubucin ya lissafa abubuwan da zai so Allah ya yi wa miyagu.
Ana magana da mugayen mutane kamar suna kankara ko ruwa. Ba a magana game da wanzuwar kasancewa narkewa ko malalawa cikin busasshiyar ƙasa. AT: "Ka sa su ɓace kamar ruwan da yake gudu" ko kuma "Ka sa su ɓace kamar kankara da ke narkewa da malalawa a cikin ƙasa"
"bari kibiyoyin su su zama kamar basu da saiti"
Babu wanzu ana magana akan zama kamar jaririn da aka haifa mutu. AT: "kamar jaririn da aka haifa da wuri shi ma ya rayu kuma ya ga hasken rana" ko "kamar jaririn da aka haifa ya mutu"
Kalmomin "masu adalci" yana nufin mutanen kirki ne gaba ɗaya. AT: "Mutane masu adalci za su yi murna idan suka gani"
Ana magana game da sanya ƙafafun mutum ta yin tafiya akan jini kamar wanke ƙafafun cikin jini. AT: "masu adalci za su jike ƙafafunsu cikin jinin mugaye" ko "masu adalci za su yi tafiya a kan jinin mugaye"
1Ka kuɓutar dani daga maƙiyana, ya Allahna; ka ɗora ni can sama nesa daga waɗanda suke taso mani.2Ka tsare ni daga waɗanda suke aikata mugunta, ka cece ni daga mutane waɗanda suke zubar da jini.3Gama, duba, sun yi kwanto domin su ɗauki raina. Manya manyan masu aika mugunta sun tattara kansu gãba dani, amma ba saboda nayi kuskure ko zunubi ba, Yahweh.4Sun shirya domin su tattake ni ba tare da laifina ba, duba, tashi ka taimake ni.5Kai Yahweh, Allah Mai Runduna, Allah na Isra'ila, tashi ka hori dukkan al'ummai. Kada ka ji tausan wani mai laifin aika mugunta ko ɗaya.6Sukan dawo da yamma, su zagaya birnin suna haushi kamar karnuka.7Duba suna yin gyatsa da bakunansu, takubba suna kan leɓunansu, suna cewa, "Wane ne ya ke sauraren mu?"8Amma kai, Yahweh, kana yi masu dariya, dukkan al'ummai ba a bakin komai suke a gare ka ba.9Allah, ƙarfina, zan kasa kunne gare ka, kaine hasumiyata mai tsawo.10Allahna zai same ni da alƙawarin amincinsa, Yahweh, zai biya muradina a kan maƙiyana.11Kada ka kashe su domin kada jama'ata su mance. Yahweh, garkuwarmu, ka warwatsa su, ka sa su faɗi.12Saboda kalmomin bakinsa, da maganar leɓunansu, ka bari a kwashe su cikin girman kansu, kuma saboda la'ana da ƙarairayin da suka bayyana.13Ka hallaka su cikin hasalarka, ka hallaka su domin kada su ƙara kasancewa. Bari su sani, Allah ne ke mulki cikin Yakubu kuma har iyakar duniya. Selah14Sukan dawo da yamma, su zagaya birnin suna haushi kamar karnuka.15Sukan yi yawo suna neman abinci, sukan yi gurnani idan ba su ƙoshi ba.16Amma zan yi rairawa game da ƙarfinka, da safe kuma zan yi rairawa saboda ƙaunarka madawwamiya! Gama ka zama hasumiyata mai tsawo, mafaka a lokacin dani ke cikin matsala.17A gare ka ƙarfina zan raira yabo, gama Yahweh ne hasumiyata mai tsawo, Allah mai amincin alƙawari.
Babban wuri yana wakiltar wuri mai aminci inda maƙiyansa ba za su iya zuwa wurinsa ba. AT: "sanya ni a cikin amintaccen wuri"
Kalmar "mai zubar da jini" ta ƙunshi "jini," wanda ke nufin kisan kai da "ƙishi," wanda ke nufin sha'awa. AT: "mutanen da suke son kashewa" ko "mutanen da suke son kashe mutane"
Maƙiyan Dauda suna ɓoyewa suna jira shuru don lokacin da za su iya kawo masa hari.
Kalmar nan “al’ummai” a nan tana wakiltar mutanen ƙasashen da ba sa girmama Allah. AT: "mutanen duk al'ummomi"
Mai zabura yayi maganar abokan gabansa suna barazanar afkawa mutane kamar karnuka ne sukeyi, kuwwa, ko kuma haushi ga mutane. AT: "suna barazanar afkawa mutane"
Fadin mummunan abubuwa ana magana ne da kirari. Waɗannan munanan abubuwa na iya zama zagi ko barazana. AT: "suna faɗar mummunan abu" ko "suna ihu da mummunan kalmomi"
Ana amfani da wannan tambayar don a nuna cewa sun yi imani cewa Allah ba zai ji su ba kuma zai hukunta su. AT: "Ba wanda zai iya jinmu!" ko "Allahnku baya jinmu!"
"yi musu dariya rainin wayo" ko "yi musu ba'a." Allah zai yi musu dariya domin ba su da daraja da ƙarfi.
Babban hasumiya wuri ne da mutane za su iya zuwa don fakewa daga abokan gabansu. Mai zabura yayi maganar Allah yana kare shi kamar dai Allah mai karfi ne, mai kariya. AT: "kuna kiyaye ni kamar doguwar hasumiya"
Wannan jimlar tana nuna cewa Allah zai zo wurinsa domin ya cece shi. Cikakken sunan "aminci" za a iya fassara shi da sifa. AT: "Allahna, wanda ya cika alkawarinsa, zai zo ya cece ni" ko "Allahna zai zo ya cece ni saboda yana da aminci ga alkawarinsa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "bari mutane su kamasu saboda girman kansu"
Lalata su gaba daya ana magana ne game da ƙona su ko cin su. AT: "Ku yi fushi da su ku hallaka su kwata-kwata saboda haka ba za a sami su ba"
Mai zabura yayi maganar abokan gabansa suna barazanar afkawa mutane kamar karnuka ne sukeyi, kuwwa, ko kuma haushi ga mutane. AT: "barazanar afka mana" ko "barazanar afka mana kamar karnukan daji"
“Zuwa gare ku, ƙarfina” za a iya haɗuwa azaman magana ɗaya. AT: "Ku ne ƙarfina, don haka zan raira muku waƙar yabo"
Manyan hasumiyoyi wurare ne da mutane zasu iya zuwa don neman tsari daga abokan gaba. Mai zabura yayi maganar Allah yana kare shi kamar dai Allah mai karfi ne, mai kariya. AT: "kun kiyaye ni kamar babbar hasumiya"
1Yahweh, ka yashe mu, ka kutsa cikin matsararmu, ka yi fushi, ka dawo da mu.2Kasa ƙasar ta girgiza, ka ɓarke ta; tana girgiza, ka warkar da ɓarakarta.3Kasa mutanenka su ga abubuwa masu wuya, kasa mun sha ruwan inabin tangaɗi.4Saboda waɗanda ke darjantaka, kasa an tada tuta gãba da masu ɗaukar baka.5Saboda waɗanda kake ƙauna su kuɓuta, ka amsa mani ka kuɓutar da mu da hannun damanka.6Allah ya yi magana cikin tsarkinsa, "Zan yi farinciki, zan raba Shekem, zan karkasa Kwarin Sukot.7Giliyad tawa ce Manasse ma tawa ce, Ifraim kuma hular kwanona ce, Yahuda kuma sandar girmana ce.8Mowab bangajin wankina ne, zan ajiye takalmina a kan Idom, zan yi sowa ta murna saboda Filistiya."9Wa zai kawo ni birni mai ƙarfi? Wa zai kai ni Idom?10Amma kai Yahweh, ba ka yashe mu ba? Gama ba ka tafi yaƙi tare da sojojinmu ba.11Ka taimake mu gãba da maƙiyanmu gama taimakon mutum banza ne.12Da taimakon Allah za mu yi nasara; shi zai tattake maƙiyanmu.
An yi magana game da mutanen da suka ƙi Allah kamar ya jefa su. AT: "kun ƙi mu"
An ba da izinin Allah ya ba magabtan Isra’ilawa keta kariyarsu ana magana kamar yadda Allah da kansa ya aikata hakan. AT: "kun ba wa magabtanmu damar kutsawa ta hanyar kariyarmu"
Mai zabura yayi maganar bala'i a kasarsa kamar girgizar kasa ce.
Anan "gani" yana wakiltar "ƙwarewa" ko "wahala."
An yi magana game da jagorancin Allah ga mutanensa yayin yaƙi kamar Allah sarki ne na mutane ko kwamanda wanda ya kafa tuta ga rundunar. AT: "kuna kamar sarki ne wanda ya kafa tuta" ko "kuna umartar mu a yaƙi kamar sarki wanda ya ɗaga tuta"
Kalmar "waɗanda ke ɗaukan baka" na nufin sojojin abokan gaba a yaƙi. AT: "don nunawa lokacin da ya dauki rundunarsa zuwa yaƙi da makiyanku"
Allah yayi magana game da kabilar Ifraim kamar sojojinsa ne. Hular kwalba tana nuna kayan aiki don yaƙi. AT: "Ifraim kamar kwalkwalin da na zaɓa ne" ko "kabilar Ifraim ita ce runduna ta"
Allah ya zaɓi mutane daga ƙabilar Yahuda don su zama sarakunan mutanensa, kuma yana magana game da wannan ƙabilar kamar sandar sarautarsa ce. AT: "Kabilar Yahuda kamar sandata ce" ko "Yahuda ita ce kabilar da nake mulkin mutanena"
Allah yayi magana akan Mowab bashi da mahimmanci kamar Mowab kwandon wanka ne ko ƙaramin bawa. AT: "Mowab kamar kwanon da nake amfani da shi don wanki"
Wataƙila Allah yana magana ne game da mallakar mallakar Idom kamar dai a alamance yana jefa takalminsa a waccan ƙasar don ya nuna cewa ya mallake ta. Koyaya wasu sifofin suna da wasu fassarar. AT: "Na mallaki ƙasar Idom" ko "Na jefa takalmina a kan ƙasar Idom don in nuna cewa nawa ne"
Mai zabura yayi amfani da wannan tambayar don ya nuna baƙin cikin sa da alama Allah ya ƙi su. AT: "Amma Allah, da alama kun ƙi mu." ko "Allah, da alama kun watsar da mu."
Mai zabura yayi maganar Allah yana taimakon rundunarsu kamar Allah zai tafi ya yi yaƙi dasu. AT: "baku taimaki sojojinmu ba idan muka tafi yaƙi"
1Ka ji kukana Yahweh, ka amsa addu'ata.2Daga iyakar duniya zan kira gare ka lokacin da zuciyata ta ruɗe, ka kai ni wurin dutsen da ya fi ni tsawo.3Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi daga maƙiyana.4Ka bar ni in zauna a shirayinka har abada! Ka bar ni in ɓoye cikin inuwar fukafukanka. Selah5Gama kai Allah, ka ji wa'adina, ka bani gãdon waɗanda suke darjanta sunanka.6Za ka sa ran sarki ya yi tsawo, shekarunsa kuma kamar tsararraki da yawa.7Zai kasance a gaban Yahweh har abada.8Zan raira yabo ga sunanka har abada, domin in cika wa'dina gare ka kowacce rana.
Waɗannan jimlolin suna da ma'ana iri ɗaya. AT: "Ya Allah, ka ji ni ka amsa addu'ata"
Anan marubucin yayi maganar Allah kamar wani babban dutse ne da zai hau domin kariya.
Maganar zuwa ga Yahweh don kariya ana magana ne da neman mafaka a gare shi. Anan akwai kwatanci na biyu wanda yayi magana game da kariyar Yahweh kamar dai shi kaza ce da ke kare hera 'ya'yanta a ƙarƙashin fikafikanta. AT: "tafi zuwa gare ka don kariya kamar yadda kajin ke da aminci a ƙarƙashin fikafikan mahaifiyarsa"
Marubucin yayi maganar albarkar Allah kamar dai gadon da ya samu ne. AT: "kun ba ni albarkar"
"Za ku tsawaita ran sarki" ko "Za ku sa ran sarki ya daɗe"
Anan "shekaru" yana nufin tsawon lokacin da sarki zai yi rayuwa. AT: "zai rayu tsawon ƙarnuka da yawa"
Anan “suna” yana nufin Allah ne da kansa. AT: "Zan raira muku yabo koyaushe"
1Na yi shiru a gaban Yahweh kaɗai, daga wurin sa cetona ya ke zuwa.2Shi kaɗai ne cetona, shi ne hasumiyata mai tsawo, ba zan girgiza ba sosai.3Har yaushe ku dukka, zaku kai hari ga mutum ɗaya? Domin ku rufe shi kamar bangon da a ke jigina da shi, shinge mai rawa?4Suna shawara da shi ne domin su ture shi daga matsayinsa mai daraja kaɗai; su na ƙaunar faɗin ƙarya, suna sa masa albarka da bakinsu, amma cikin zuciyarsu suna la'antar sa. Selah5Ga Allah kaɗai nake saurare, gama shi ne begena.6Shi kaɗai ne dutsena da cetona, shi ne hasumiyata mai tsawo ba zan jijjigu ba.7Allah ne cetona da ɗaukakata, dutsen ƙarfina da mafakata a cikin Allah suke.8Ku dogara gare shi kowanne lokaci, ku mutane, ku kafa zuciyarku a gaban sa, Allah shi ne mafakarmu. Selah9Ba shakka mutanen da basu da matsayi ba komai bane, waɗanda ke da matsayin kuma ƙarya ne. Idan a ka auna su a ma'auni ba su da nauyi, inda za a haɗa su a auna ba su da nauyin komai.10Kada ku dogara ga aikin zalunci ko ƙwace, kada ku sa begenku ga dukiyar wofi, gama ba su da amfanin komai, kada ku sa zuciya gare su.11Allah ya yi magana sau ɗaya, sau biyu kuwa na ji wannan: iko na Allah ne.12Kuma Ubangiji, a gare ka alƙawarin gaskiya yake. Gama kana ramawa kowanne mutum bisa ga abin da ya yi.
"shi ne wanda ya kubutar da ni" ko "shi ne wanda ya cece ni"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "babu abin da zai iya motsa ni"
A cikin waɗannan ayoyin, Dauda yana nufin kansa ta wurin "shi."
Wannan yana nufin tunaninsu.
"gama ina sa zuciyata a gareshi"
Marubucin yayi maganar Allah kamar yana dutsen da yake kiyaye mutum daga maƙiyansa. Yana kuma magana game da Allah kamar dai shi mafaka ne wanda ke ba da kariya. AT: "Allah koyaushe yana bani ƙarfi da kariya"
Idan ka hada duk wadannan nau'ikan mazaje a sikeli, da basuda nauyi. Wannan yana nufin cewa basu da wata ƙima a gare ku.
A nan "sa zuciyarka" wani karin magana ne da ke nufin sha'awar abu ƙwarai. AT: "kar ku so su"
Wannan yana nufin cewa Allah Ya faɗi wannan fiye da sau ɗaya.
Ana magana game da ikon Allah da iko kamar ikon nasa ne. Cikakken sunan "iko" ana iya fassara shi da sifa. AT: "Allah mai iko ne"
Marubucin yayi maganar ladan Allah kamar yana biyan ladan aiki.
1Allah, kai ne Allahna, da gaske raina ya ke neman ka, raina yana ƙishin ka, jikina ya ƙagara ya gan ka, a cikin ƙasa da turɓaya in da babu ruwa.2Na dubo zuwa gare ka a cikin mutane masu tsarki domin in ga ikonka da ɗaukakarka.3Saboda alƙawarin ka mai aminci yafi rai, leɓunana zasu yabe ka.4Zan albarkace ka sa'ad da nake da rai, a cikin sunanka zan tada hannuwana.5Zai zama kamar na ci abinci mai ɓargo da kitse, zan yabe ka da leɓuna masu farinciki,6sa'ad da ni ke tunaninka a kan gadona, sa'ad da nake nazarin ka a cikin dare.7Gama kai ne taimakona, a ƙarƙashin inuwar fukafukanka nake yin farinciki.8Na manne maka hannun damanka yana tallafa ta.9Amma waɗanda ke nema su hallaka raina, zasu faɗa cikin wuri mai zurfi na duniya;10za a bashe su ga hannun masu aiki da takobi, zasu zama abicin diloli.11Amma sarki zai yi farinciki cikin Allah, dukkan wanda ya rantse da shi, zai yi fahariya da shi kuma, amma bakin masu faɗin ƙarya za a kwaɓe shi.
Waɗannan kalmomin biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani dasu tare don ƙarfafa yadda marubuci yake sha'awar kasancewa tare da Allah. AT: "Dukan halittata na matukar son kasancewa tare da ku"
"zafi, busasshiyar hamada"
A nan “leɓunana” suna wakiltar dukkan mutumin. AT: "Zan yabe ku"
Anan "da sunanka" yana nufin "a gare ku." AT: "Zan yi muku sujada kuma zan yi addu'a gare ku"
A nan “da bakina na farin ciki” bakina yana wakiltar dukan mutumin da zai yabi Allah da farin ciki. AT: "Zan yabe ku da farin ciki"
Waɗannan jimloli biyu suna da ma'ana iri ɗaya. Ana maimaita ra'ayoyin don jaddada yadda marubuci yake tunani game da Allah.
"Ina bukatan ku" ko "na dogara da ku"
Anan, ana amfani da hannun dama a matsayin alama ta ƙarfi da ƙarfi. AT: "kun goyi bayan ni" ko "kun ɗauke ni"
Anan “takobi” yana wakiltar mutuwa a yaƙi, kuma “waɗanda hannuwansu suka yi amfani da takobi” yana nufin maƙiyan da suka kashe su a yaƙi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah zai sa su mutu a yaƙi"
Anan "su" suna nufin gawawwakin waɗanda suka mutu a yaƙi. AT: "jackal za su ci mushen su"
Kalmar "shi" tana nufin "Allah."
1Ka ji muryata, Allah, ka saurari ƙarata; ka tsare raina daga tsoron maƙiyana.2Ka ɓoye ni daga shirin miyagu, daga hargowar masu aika mugunta.3Sun wasa harsunansu kamar takubba, sun haro kibansu, wato maganganu masu ɗaci,4domin su harbi wanda ba shi da laifi daga wurin da suke ɓoye, nan da nan suka harbe shi ba tare da sun ji tsoro ba.5Suna ƙarfafa kansu cikin shirya mugunta, suna shawara a asirce domin su ɗana tarkuna, suna cewa, "Wa zai gan mu?"6Suna ƙulla mugunta; "Mun gama" suka ce, "Natsastsen shiri" Tunanin ciki da zuciyar mutum suna da zurfi.7Amma Yahweh, zai harbe su, nan da nan kibau zasu ji masu ciwo.8Zasu yi tuntuɓe tun da ya ke harshensu yana gãba da su; dukkan waɗanda suka gan su zasu kaɗa kansu.9Dukkan mutane zasu ji tsoro su bayyana ayyukan Allah. Cikin hikima zasu yi tunani a kan abin da ya yi.10Masu adalci zasu yi murna da Yahweh, zasu sami mafaka a wurinsa. Dukkan waɗanda ke tafiya dai-dai zasu yi fahariya a cikin sa.
Anan "ɓoye" yana wakiltar karewa, kuma "makircin ɓoye na masu aikata mugunta yana wakiltar" yana wakiltar cutarwar da miyagu ke shirin ɓoye wa Dauda. AT: "Kare ni daga cutarwar da miyagu ke shirin ɓoye ni a ɓoye"
An fahimci kalmomin "ɓoye ni" daga jumlar da ta gabata kuma ana iya maimaita su a nan. AT: "ku ɓoye ni daga hargitsi" ko "kare ni daga tashin hankali"
Marubucin yana magana ne game da makiyansa harsuna kamar suna kaifi kamar takubba. Anan "harsuna" suna wakiltar munanan kalmomin da abokan gaba ke magana da su. AT: "Mummunan maganganun da suke fada sun cutar da ni kamar kaifin takobi"
Marubucin yayi magana game da "tunanin mutum" da "zukatan mutane" kamar suna cikin zurfin ruwa wanda babu wanda zai iya bincika har zuwa ƙasan.
Marubucin yayi maganar azabar Allah akan masu aikata mugunta kamar Allah yana harba musu kibiyoyi.
Marubucin yayi magana ne game da sa Allah ya sa masu aikata mugunta shirin su kasa kamar dai Allah yana sa su tuntuɓe a hanyoyin su. Ana iya bayyana wannan a cikin aiki. AT: "Allah zai sa su tuntuɓe" ko "Allah zai sa shirin su ya kasa"
Anan “madaidaiciyar zuciya” karin magana ne da ke nufin ibada ko adalci. AT: "duk mutanen da ke da ibada za su yabe shi"
1Domin kai Allah a Sihiyona ne, yabonmu; da wa'adodinmu, za a kawo maka su a cikin Sihiyona.2Kai da kake jin addu'a, a gare ka dukkan mutane za su zo.3Laifofi sun yi mana tsayayya, amma za ka gafarta zunubanmu, za ka kuma gafarta su.4Mai albarka ne mutumin daka zaɓa ya zo ya zauna a kusa da kai a cikin harabarka. Za mu gamsu da kyawawan abubuwan dake a gidanka, haikalinka mai tsarki.5Cikin adalci za ka amsa mana ka yi abubuwan mamaki, kai Allah na cetonmu, Kai wanda dukkan mutane ke dagara gake ka har da waɗanda ke a can hayin teku.6Gama kai ne ka kafa duwatsu suka yi ƙarfi, kai wanda ka yi ɗamara da iko.7Kai ne ka kwantar da rurin tekuna da balalloƙansu da hargowar mutane8Su waɗanda ke zama a can ƙarshen duniya suna jin tsoron alamun ayyukanka, kasa gabas da yamma suna farinciki.9Ka zo domin ka taimaki duniya; ka yi mata banruwa, kasa ta yi arziki, kogin Allah na cike da ruwa; tun da ka hallicci duniya ka tanadawa ɗan Adam hatsi.10Ka jiƙe kwarin kunyai a wadace, ka dai-daita kwarin kunyai sosai, kakan sa su yi taushi, kasa albarka a kan yabanyarsu.11Ka yi wa shekara dajiyar alherai, sawayen karusanka suka zubo da kitse a kan duniya.12Wuraren kiwo a jeji sun jiƙe da raɓa, ka sa tsire--tsire suyi farinciki.13Wuraren kiwo sun cika da garkuna, kwarurruka sun cika da hatsi, suna shewa ta farinciki, suna rairawa.
Wannan yana magana game da yabo kamar dai mutum ne wanda zai iya yin aiki da kansa. AT: "A gare ku kai kaɗai, Allah a Sihiyona, za mu yabe mu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "za mu yi abin da muka alkawarta muku cewa za mu yi"
Kalmar "su" tana nufin "laifofinmu."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kyakkyawan gidanka, tsattsarkan haikalinka, zai gamsar da mu"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya. AT: "na duk mutanen da ke rayuwa a cikin duniya da kuma ketare teku"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani dasu tare don ƙirƙirar kyakkyawan ra'ayi akan mai sauraro ko karatu. AT: "ci gaba da rurin teku"
Jumlar "gabas da yamma" tana nuni ne ga mutanen da ke rayuwa a ko'ina cikin duniya. AT: "kuna sa mutane ko'ina su yi ihu da murna"
Wannan yana nuni ga samar da ruwa a sama wanda Allah ya aiko ya shayar da duniya ya kuma cika rafuka. AT: "kun cika rafuka da ruwa"
Anan an ba da "shekara" ta ɗan adam ta sanya kambi. AT: "Kun girmama shekara ta girbi mai kyau"
Marubucin yayi maganar kyawawan tuddai kamar mutanen farin ciki, kuma farin ciki kamar sutura. AT: "tuddai kamar mutane suke sa farin ciki" ko "tuddai kamar mutane ne masu farin ciki"
Marubucin yayi magana game da wuraren kiwo kamar an rufe su da garken tumaki har ta zama kamar makiyayan suna sanye da tufafi.
Makiyaya, tuddai da kwaruruka suna da yawan gaske, da alama suna ihu suna raira waƙa don farin ciki. AT: "sun kasance kamar mutane masu raha da farin ciki"
1Ku yi sowa ta farinciki ga Yahweh, ku duniya dukka.2Ku raira ɗaukakar sunansa, ku sa yabonsa ya zama ɗaukakakke.3Ku ce da Allah, "Ayyukanka suna da ban tsoro! Da girman ikonka kasa maƙiyanka su yi ladabi a gabanka.4Dukkan duniya zasu bauta maka su raira yabo gare ka, zasu yi rairawa ga sunanka." Selah5Ku zo ku ga ayyukan Yahweh, ayyukansa na da ban mamaki ga 'yan Adam.6Ya mayar da teku busasshiyar ƙasa; sun bi ta cikin teku da ƙafa; can muka yi farinciki a cikin sa.7Da ikonsa ya ke mulki har abada, idanunsa suna lura da al'ummai; kada masu tawaye su ɗaukaka kansu. Selah8Ku albarkaci Allah, ku mutane, bari a ji amon yabonsa.9Ya bar mu cikin masu rai, bai bari ƙafafunmu suka yi tuntuɓe ba.10Gama kai Yahweh ka gwada mu, ka gwada mu kamar yadda a ke gwada azurfa.11Ka kawo mu cikin taru, ka ɗora mana kaya mai nauyi a kanmu.12Ka bari mutane su tattaka mu, mun shiga cikin wuta da ruwa, amma ka kawo mu cikin wuri mai faɗi.13Zan zo cikin gidanka da baiko na ƙonawa, zan cika wa'adodina gare ka,14waɗanda leɓunana suka yi alƙawarin su, bakina kuma ya furta, sa'ad da nake cikin wahala.15Zan kawo maka baiko na ƙonawa da dabbobi masu ƙiba da ƙamshin raguna; zan miƙa bijjimai da awaki.16Ku zo ku saurara, dukkan ku dake tsoron Allah, zan bayyana abin da ya yi domin raina.17Na yi kuka gare shi da bakina, harshena kuma ya yabe shi.18Idan dana dubi zunubi a cikin zuciyata, da Ubangiji bai saurare ni ba.19Amma da gaske Allah ya ji; ya kula da muryar addu'ata.20Albarka ta tabbata ga Allah, wanda bai yi watsi da addu'ata ba ko ya ɗauke alƙawarinsa mai aminci daga gare ni ba.
“Murya mai daɗi ga Allah” tana wakiltar rera waƙoƙi da yabon Allah. AT: "Bari dukkan duniya su raira waƙa da farin ciki ga Allah"
Waɗannan jimlolin suna da ma'anoni iri ɗaya kuma ana amfani dasu tare don ƙarfafa yadda Allah yake da ban mamaki. AT: "Ku raira waƙa game da yadda sunan Allah mai ban mamaki; raira yabo mai ban mamaki game da girman Allah"
Ayyukan Allah suna sa mu firgita da firgita saboda mun san cewa yana da iko da tsarki.
"Saboda kuna da babban iko"
Wannan yana nufin dukkan mutanen da suke rayuwa a duniya. AT: "Duk mutanen duniya zasu yi muku sujada"
Wannan yana nufin ƙetare Bahar Maliya.
"kada mutane masu tawaye su daukaka kansu" ko "kada masu tawaye su yi alfahari"
Waɗannan jimloli guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya. An maimaita wannan ra'ayi don a nanata muhimmancin yabon Allah.
Wannan hoto ne na cin nasara ƙwarai a yaƙi. AT: "Kamar dai makiyanmu sun ci mu a yaƙi sannan suka kori karusansu a kan jikkunanmu da suka faɗo"
Allah ya jarabce su da masifu irin na gobara da ambaliyar ruwa. AT: "mun sha wahala kamar mutanen da ke fama da gobara da ambaliyar ruwa"
Anan "lebe" da "bakin" suna nuni ga kalmomin alƙawarin da aka faɗi. AT: "wanda nayi alƙawari"
Kalmar nan “kurwa” tana wakiltar dukan mutumin. AT: "Zan gaya muku abin da ya yi mini"
Anan "harshe" yana wakiltar kalmomi ko magana. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Na yaba masa da harshena" ko "Na yaba masa"
Waɗannan jumloli biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani da su tare don ƙarfafawa cewa Allah ya ji addu'arsa. AT: "Amma hakika Allah ya ji addu'ata"
1Bari Allah ya yi mana jinƙai, yasa fuskarsa ta haskaka wajenmu. Selah2domin a san hanyoyinka a duniya, cetonka kuma cikin al'ummai dukka.3Bari mutane su yabi Allah, dukkan mutane su yabe ka.4Oh, bari al'ummai suyi murna su raira domin farinciki, gama za ka hukunta mutane cikin adalci, ka shugabanci mutanen duniya. Selah5Bari mutane su yabe ka Allah, bari dukkan mutane su yabe ka.6Ƙasa ta ba da amfaninta kuma Allah, Allahnmu ya albarkace mu.7Allah ya albarkace mu kuma dukkan ƙarshen duniya na darjanta shi.
Marubucin yayi magana game da Yahweh yana nuna musu alheri kamar fuskar Yahweh ta haskaka musu. AT: "ku aikata mana yadda ya kamata"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane na iya sanin hanyoyinku a bayan ƙasa"
Magana ta biyu ta ƙarfafa ma'anar farkon don ta nanata muhimmancin yabon Allah.
Anan marubucin yayi magana ne game da "ƙasa" kamar dai ta zaɓi ne don samar da girbi ga mutane. AT: "Mun girbe alfanu mai yawa daga albarkatunmu"
Wannan yana nufin cewa mutane a ko'ina su girmama Allah saboda ni'imominsa. AT: "Ina son dukkan mutane ko'ina a duniya su girmama shi ƙwarai"
1Bari Allah ya tashi, bari maƙiyansa su warwatse, bari kuma waɗanda ke ƙin sa su gudu daga gabansa.2Ka kore su kamar yadda hayaƙi ke watsewa, kamar yadda saƙar zuma kan narke a gaban wuta, haka masu mugunta zasu lalace a gaban Allah.3Amma bari masu adalci suyi murna, su ɗaukaka a gaban Allah; bari su yi farinciki su kuma ji daɗi.4Ku raira ga Allah! Ku raira yabbai ga sunansa! Ku yabe shi wanda ke ratsawa ta filin kwarin Kogin Yodan! Yahweh ne sunansa! Ku yi farinciki a gabansa!5Uban marar uba, alƙali saboda gwauraye, shi ne Allah daga wurin zamansa mai tsarki.6Allah yakan sa masu kaɗaici cikin iyali, ya kan fito da 'yan kurkuku cikin waƙa, amma 'yan tawaye suna zama a faƙo.7Allah idan da kayi tafiya a gaban mutanenka, idan ka bi ta cikin jeji, Selah8Ƙasa takan girgiza, sama kan zubo da ruwa a gaban Allah, a gaban Allah sa'ad da ya zo Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra'ila.9Kai, Allah, ka aiko da ruwa isasshe, ka ƙarfafa abin gãdonka sa'ad da suka gaji.10Mutanenka suka zauna a ciki; kai, Allah, daga cikin alherinka ka bayar ga matalauta.11Ubangiji ya bada umarnai, waɗanda suka sanar da su kuwa manyan sojoji ne.12Sarakunan sojoji sun gudu, suka gudu, matayen dake zama a gida kuwa suka raba ganima.13Kurciyoyi rufe da azurfa, da fukafukan zinariya rawaya. Sa'ad da waɗansu ku mutane kuka tsaya a garkunan tumaki, me ya sa kuka yi haka?14Mai iko dukka ya tarwatsa sarakuna a wurin, sai ya zama kamar dusar ƙanƙara a Dutsen Zalmon.15Babban dutse shi ne tudun ƙasar Bashan, dutse mai tsawo shi ne tudun ƙasar Bashan.16Me yasa ki ke ƙyashi ke ƙasar kan tudu, a kan dutsen da Allah ya zaɓi ya zauna a wurin? Tabbas, Yahweh zai zauna a cikinta har abada.17Karusan Allah dubu ashirin ne, dubbai bisa dubbai; Ubangiji na cikinsu a wuri mai tsarki, kamar a Sinai.18Ka haye sama, ka kwashi 'yan bauta, ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga waɗanda suka yi faɗa da kai, domin kai Yahweh Allah, ka zauna a can.19Albarka ga Ubangiji, wanda kullum ya ke kula da mu, Allah wanda shi ne cetonmu.20Allahnmu, Allah ne wanda ke yin ceto. Yahweh, Ubangiji, shi ne kaɗai wanda zai iya kuɓutar da mu daga mutuwa.21Amma Allah zai rotsa kan maƙiyansa, ta wurin fatar kai mai gashi ta waɗanda ke tafiya cikin yi masa laifi.22Ubangiji yace, "Zan dawo da maƙiyana daga Bashan, zan dawo da su daga cikin zurfin teku23domin ka ragargaza maƙiyanka, kana tsoma ƙafarka cikin jini, domin harsunan karnukanka su sami rabo daga cikin maƙiyanka."24Sun ga shigowar ka, Allah, shigowar Allahna, Sarkina cikin wuri mai tsarki.25Mawaƙa suka fara yin gaba, masu busa na bin baya, a tsakiya kuwa 'yammata na kaɗa molo.26Ku albarkaci Allah a cikin taro, ku yabi Yahweh, ku zuriyar Isra'ila na gaskiya.27Da fari akwai Benyamin, kabila mafi ƙanƙanta, sai kuma shugabannin Yahuda da jama'arsu, shugabannin Zebulun da shugannin Naftali.28Allahnka, ya Isra'ila ya umarta ƙarfinka, ka nuna ikonka, Allah, kamar yadda ka nuna shi a lokacin dã.29Ka nuna mana ikonka daga Yerusalem inda sarakuna ke kawo maka kyautai.30Yi ruri cikin yaƙi gãba da namomin jejin dake zama cikin iwa, a kan mutane, da bijimai masu yawa da 'yan maruƙa. Kunyatar dasu kasa su kawo maka kyautai, ka tarwatsa mutanen dake ƙaunar yin yaƙi.31Sarakuna zasu fito daga Masar; Itofiya zata yi sauri ta kawo hannuwanta ga Allah.32Ku raira yabbai ga Allah ku mulkokin duniya; Selah ku raira yabbai ga Yahweh.33Gare shi wanda ke sukuwa kan saman sammai, shi wanda ya kasance tun zamanin dã; duba, ya tada muryarsa da iko.34Ku furta ƙarfi ga Allah, darajarsa tana kan Isra'ila, ikonsa na cikin sararin sama.35Allah, kai abin tsoro ne a cikin wurinka mai tsarki, Allah na Isra'la yana ba da ƙarfi da iko ga mutanensa. Albarka ga Allah.
An fara magana Allah yana farawa kamar yana tsaye. AT: "Bari Allah ya fara aiki"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "bari Allah ya kori maƙiyansa"
Ana magana akan magabtan Allah kamar hayaƙi ne wanda iska ke kaɗawa cikin sauƙi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Korar su kamar yadda iska ke kaura hayaƙi"
Ana magana akan Allah a matsayin Allah mai jinƙai wanda yake aiki kamar uba ga marayu. AT: "Wanda ya zama kamar uba ga yaran da basu da iyaye"
An ambaci Allah a matsayin Allah mai jinƙai wanda yake kiyaye gwauraye. AT: "mai kariya ga zawarawa"
Ana magana akan Allah kamar yana sanya mutane masu kadaici cikin dangi. "Allah yana samar da iyalai ga waɗanda ba su da wanda za su zauna tare da su"
"ka jagoranci mutanenka"
Ana magana akan Allah kamar soja ne wanda zaiyi gaba da jama'ar Isra'ila.
Wannan karin magana anan yana nufin bayyanuwar Allah a gaban Isra'ilawa. AT: "lokacin da Allah ya bayyana ga Isra'ilawa"
Ana maganar ƙasar Isra'ila kamar dai mutum ne wanda zai iya gajiya, ko kuma ya sami ƙarfi. AT: "kun sa ƙasar ta samar da kyawawan amfanin gona"
Wannan yana nufin cewa wasu daga cikin ganimar tana da tamani sosai saboda an lulluɓe ta da ƙarfe masu tamani.
Ana amfani da wannan tambayar don tsawata wa mutanen da ba su halarci yaƙi ba.AT: "Waɗanda suka tsaya a tsakanin garken tumakin bai kamata su tsaya ba; ya kamata su tafi yaƙi."
Wadannan kalmomin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma ana amfani dasu tare don ƙarfafa juna. AT: "dutse mai tsayi kuma mai tsayi shine ƙasar Bashan"
Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Babban tsaunin Bashan bai kamata ya yi hassadar dutsen da Allah yake so ba don wurin da zai zauna."
Wannan wataƙila ba ana nufin ya zama lambar dai-dai ba, amma don nuna adadi mai yawa. AT: "dubbai da yawa"
"yana ɗauke da kayanmu masu nauyi a kowace rana." Maganar Ubangiji ga mutanensa ana maganarsa kamar yana ɗauke da matsalolinsu kamar nauyi.
An ambaci Allah a matsayin jarumi wanda zai kashe maƙiyansa ta hanyar buge su a kawunansu don ya kashe su. AT: "zai kashe makiyansa ta hanyar buge su a kai"
Ana maganar hallaka maƙiyan Isra’ila gabaki ɗaya kamar Isra’ilawa sun murƙushe su a ƙarƙashin ƙafafunsu. AT: "kayar da makiyanka gaba daya"
Rikicin daga halakar abokan gaba ana maganarsa cikin tsari sosai, kamar dai Isra'ilawa zasu tsaya cikin jinin abokan gabansu da suka mutu. AT: "shiga cikin jininsu"
Jerin jerin gwano rukuni ne na mutanen da ke tafiya tare cikin tsari a matsayin ɓangare na bikin.
Yana iya zama da taimako canza tsarin waɗannan jumlolin. AT: "Ku da kuka fito daga maɓuɓɓugar Isra'ila, ku yabi Yahweh ku yabi Allah a cikin taron"
Wasu sifofin sun fahimci rubutun Ibraniyanci daban: "Ku tara ƙarfinku, Allah" ko "Yi amfani da ƙarfinku, ya Allah"
"Idan kun kasance a haikalin da ke Yerusalem, nuna mana ikonka"
Masana da yawa sun gaskata cewa waɗannan dabbobin daji kwatanci ne wanda ke nufin mutanen Masar. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "mutanen Masar waɗanda suke kamar namun daji a cikin iwa"
Ana maganar al'umman sauran al'ummu kamar wasu manyan shanu ne. AT: "kasashe masu karfi, wadanda suke kamar garkunan bijimai"
An nuna cewa waɗannan yariman sun fito ne daga Masar don ba da kyauta ga Allah a Yerusalem. Madadin fassara: "To shugabannin Masar za su kawo maku kyaututtuka"
Anan "masarautu" na nufin 'yan ƙasa na masarautun. AT: "ku mutanen ƙasa ne na masarautu a duk duniya"
Kalmar "raira waƙa" ana nuna ta farkon wannan aya. Anan an siffanta Allah kamar yana tafiya a cikin karusar cikin sama. AT: "Ku raira waƙa ga Allah wanda yake hawan sama a cikin karusarsa"
"Bayyana" yana nufin ba da daraja ga wani. AT: "ƙarfi na Allah ne"
Anan marubucin yayi magana kai tsaye da Allah.
1Ka cece ni Allah, gama ruwaye sun sa raina cikin hatsari.2Na nutse cikin laka, mai zurfi inda ba wurin tsayawa; na zo cikin ruwa mai zurfi, rigyawa ta sha kaina.3Na gaji da kuka, maƙogwarona ya bushe, idanuna sun dishe sa'ad da nake jiran Allahna.4Waɗanda ke ƙi jinina ba dalili sun fi gashin kaina yawa, su waɗanda zasu datse ni saboda dalilan da ba dai-dai ba, suna da ƙarfi, abin da ban sata ba, sai na mayar.5Allah, ka san wawancina, zunubaina kuma ba ɓoye suke a gare ka ba.6Kada waɗanda ke jiran ka su ji kunya saboda ni, Ubangiji Yahweh Mai Runduna, kada masu neman ka su ƙasƙanta saboda ni, Allah na Isra'ila.7Saboda kai na jure da tsautawa; kunya ta rufe fuskata.8Na zama bãƙo ga 'ya'uwana, bare kuma ga 'ya'yan mahaifiyata.9Gama niyyar zuwa gidanka ta ɗauke hankalina, tsautawar waɗanda ke tsauta maka ta faɗo kaina.10Idan na yi kuka na ƙi cin abinci, sai su zage ni.11Idan kayan makoki suka zama kayan sawata, sai in zama abin misali gare su.12Waɗanda ke zama a ƙofar birni magana suke yi a kaina, mashaya waƙa su ke yi a kaina.13Amma ni addu'ata gare ka take, Yahweh, sa'ad da ka ga yayi dai-dai, ka amsa mani cikin aminci cetonka.14Ka tsamo ni daga cikin laka, kada ka bari ni nutse; bari a ɗauke ni daga waɗanda ke ƙina, a kuma tsamo ni daga cikin ruwaye masu zurfi.15Kada ka bari rigyawa ta sha kai na, kada ka bari zurfi ya haɗiye ni. Kada ka bari rami ya rufe bakinsa a kaina.16Ka amsa mani Yahweh, gama alƙawarin amincinka yana da kyau; domin jiye-jiyen ƙanka suna da yawa zuwa gare ni, ka juyo wajena.17Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka, gama ina cikin wahala, ka amsa mani da sauri.18Ka zo wuri na ka cece ni, saboda maƙiyana ka fanshe ni.19Ka san tsautawar da a ke yi mani, ka san kunyata, ka san ƙasƙancin da nake sha; dukkan magabtana a gabana suke.20Tsautawa ta karya zuciyata; cike nake da nauyi; na duba ko wani zai ji tausayi na, amma ban samu ba.21Sun ba ni dafi shi ne abincina, cikin ƙishina kuma sai suka ba ni ruwan tsami domin in sha.22Bari teburin gabansu ya zama tarko, sa'ad da suke tsammanin suna lafiya bari ya zama tarko a gare su.23Bari idanunsu su dishe yadda ba zasu iya gani ba; bari kwankwasonsu su riƙa yin rawa.24Ka zuba masu hasalarka, bari zafin fushinka ya yi ƙuna a kan su.25Bari wurin zamansu ya zama kufai; kada kowa ya zauna a rumfunansu.26Gama sun tsanantawa wanda ka fyaɗe ƙasa. Sun ƙarawa waɗanda suka ji rauni zafin ciwo.27Ka zarge su a kan aikata mugunta a kan mugunta; kada ka bari su zo cikin nasararka mai adalci.28Bari a shafe su daga cikin lattafin rai, kada a rubutasu tare da tsarkaka.29Amma ni matalauci ne mai baƙinciki, bari cetonka; Allah, ya sanya ni can sama.30Zan yabi sunan Allah da waƙa, zan ɗaukaka shi da shaidar godiya.31Wannan zai gamshi Yahweh fiye da sã da bijimi mai ƙahonni da kofatai.32Masu taushin zuciya za su gani suyi murna, ku da kuke neman Yahweh, zukatanku zasu rayu.33Gama Yahweh na sauraron mabuƙata, ba ya kuma raina 'yan sarƙarsa.34Bari sama da ƙasa su yabe shi da tekuna da dukkan abubuwan dake iyo a cikinsu.35Gama Allah zai ceci Sihiyona, zai sake gina biranen Yahuda; mutane zasu zauna a can ya zama nasu.36Zuriyar bayinsa zasu gaje shi, waɗanda ke ƙaunar sunansa zasu zauna a can.
Marubucin ya bayyana matsaloli a rayuwarsa kamar yana nitse cikin ambaliyar ruwa. AT: "don yana jin kamar na nitse cikin ruwa ne"
Marubucin ya bayyana matsalolinsa kamar yana nitsewa cikin rami mai zurfin gaske. AT: "ina jin kamar ina cikin ruwa mai zurfi, kuma ruwan ambaliyar ya mamaye ni"
Wannan karin gishiri ne don bayyana yawan makiyin da marubucin yake da su. AT: "fiye da yadda zan iya kirgawa, kamar gashin kai na"
Ana iya bayyana wannan azaman sanarwa mai kyau. AT: "Kun san dukkan zunubaina"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Don Allah kar a ba kowa damar ya kunyata waɗanda suke jiran ku saboda ni"
Maganganun abokan gaba na marubuci ana maganarsu kamar suna da nauyi mai nauyi da ya kamata ya ɗauka. AT: "Na jimre zagin magabtana"
Marubucin yayi maganar kansa kamar baya cikin danginsa. AT: "'Yan'uwana ba su san ni ba ko kuma karɓe ni kwata-kwata"
Marubucin yayi magana game da himmarsa ga haikalin Allah kamar dabba ce ta cinye marubucin. AT: "himmar da nake da ita a gidanka ta cinye ni"
Gaskiyar cewa marubucin yana azumi yana nuna cewa yana baƙin ciki game da yadda mutane suka bi da haikalin Allah.
Sanya tufafi masu tsada, araha alama ce ta makoki kan zunubi.
Anan "ƙofar gari" yana da alaƙa da jagorancin gari. AT: "Muhimman mutanen birni"
Marubucin yayi maganar kansa kamar shi mutumin da mashaya giya suke rera waƙoƙin ba'a. AT: "mashaya birni suna raira waƙoƙi masu banƙyama game da ni"
"a cikin karbuwar lokacinku" ko "lokacin da kuka yarda"
Anan "ɗauke" yana nufin cirewa daga haɗari. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ku dauke ni" ko "ku cece ni"
Marubucin yayi magana game da haɗarinsa daga abokan gaba kamar ruwan tsufana yana rufe shi gaba ɗaya.
Anan ana maganar "rami" kamar yana da baki kamar mutum kuma yana iya cin marubucin. AT: "Kada ku bari ramin ya cinye ni" ko "Kada ramin mutuwa ya rufe ni"
"ka tausaya min sosai"
Ɓoye mutum yana nufin ƙin ji ko taimaka wa wani. AT: "Da fatan za a taimaki bawanka" ko "Da fatan za a taimake ni"
Waɗannan sunayen na ƙila za a iya bayyana su azaman ayyuka. AT: "yadda mutane suka tsawata min, suka kunyata ni, suka tozarta ni"
Anan “gabaninka” yana nufin cewa Allah yana gani kuma ya san dukkan su. AT: "kun san su waye duk abokan gaba na"
Babban marubucin ana maganarsa kamar wanda yake cike da nauyi. AT: "Na yi nauyi da baƙin ciki"
Abincin da mutane suka ba marubucin ya munana sosai har ya ɗanɗana kamar dafi. AT: "Sun ba ni abincin da ya ɗanɗana kamar guba"
Marubucin yayi magana akan idanun da basa iya gani da kyau kamar sunyi duhu. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Da fatan za a basu damar ganin komai"
Ana maganar baya masu rauni kamar suna girgiza cikin rauni. AT: "sa bayansu ya yi rauni da ba za su iya yin komai ba"
Bayyanar fushin Allah an bayyana shi kamar ya zubo a kan magabtansa kamar ruwa.
"fushinka mai zafi" ko "fushinka mai karfi"
"sun tsananta wa mutumin"
"Ci gaba da rubuta dukkan zunubansu"
"zunubai da yawa"
Shiga cikin nasarar Allah magana ce da ke nufin karɓar lada daga gare shi. AT: "kar ku yarda su sami ladanku na adalci"
Anan "su" yana nufin sunayen makiya. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Shafe sunayensu a cikin"
Ana iya bayyana kalmar "ceto'' ta ainihi tare da kalmar aikatau "cece". Anan "a sama" yana nufin wurin aminci. AT: "Allah, ka cece ni ka sanya ni a cikin amintaccen wuri"
Anan “suna” yana nufin Allah da kansa. AT: "Allah"
Wannan jimlar ta banbance cikakkun bijimai da sauran kananan shanu. AT: "bijimin da ya cika girma da ƙaho da kofato"
Neman Allah yana wakiltar 1) neman taimakon Allah ko 2) yin tunani game da Allah da kuma yi masa biyayya. AT: "ku da kuke roƙon Allah taimako" ko "ku da kuke tunani game da Allah"
Anan "zukata" suna nufin mutane. Anan "rayu" wani karin magana ne wanda ke nufin a karfafa. AT: "a ba ku kwarin gwiwa"
Anan "ji" na nufin amsawa. AT: "Yahweh ya amsa"
Anan ana maganar sama da ƙasa da tekuna kamar mutane ne masu iya yabon Allah.
An nuna cewa "Bari ... yabe shi" ya kamata a fahimta anan. AT: "ya bar shi tekuna kuma duk abin da ya motsa a cikinsu ya yabe shi"
Anan "Sihiyona" tana nufin mutanen da suke Sihiyona. AT: "Allah zai ceci mutanen Sihiyona"
1Ka cece ni ya Allah, Yahweh, ka zo da sauri ka taimake ni.2Bari waɗanda ke so su ɗauki raina su ji kunya su ƙasƙanta; bari su koma baya a wulaƙance, su waɗanda ke murna da raɗaɗina.3Bari su koma baya cikin kunya, su waɗanda ke cewa, "Aha, aha."4Bari dukkan waɗanda ke neman ka suyi farinciki, suyi murna a cikin ka, bari waɗanda ke ƙaunar cetonka koyaushe su ce, "A yabi Allah."5Amma ni matalauci ne mai bukata, ka yiwo sauri wurina Allah, kai ne taimakona ka kuɓutar dani, Yahweh, kada ka yi jinkiri.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ya juyar da su kuma ya basu kunya saboda abin da suka aikata"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari kowa ya yabi Allah"
Anan jimlar "ka cece ni" ta bayyana yadda Allah shine "taimako" nasa. AT: "kun taimake ni ta hanyar cetona"
1Yahweh, a gare ka nake samun mafaka, kada ka taɓa bari in ji kunya.2Ka kuɓutar da ni ka sa in zauna lafiya cikin adalcinka.3Ka zama dutsen fakewa a gare ni inda zan zo ko yaushe, ka bada umarni a cece ni, gama kai ne dutsena da kagarata.4Ka cece ni, Allahna daga hannun miyagu, daga masu shirya mugunta.5Gama kai ne begena, Ubangiji Yahweh. Na dogara gare ka tun ina yaro.6Kai ne kake ta taimako na tun daga cikin ciki; kai ne ka fito dani daga cikin mahaifiyata; yabona a gare ka ya ke koyaushe.7Na zama misali ga mutane da yawa, kai ne mafakata mai ƙarfi.8Bakina zai cika da yabonka, da ɗaukakarka dukkan yini.9Kada ka yashe ni a lokacin dana tsufa, kada ka manta dani lokacin da ƙarfina ya ƙare.10Gama maƙiyana maganata, waɗanda ke neman raina suna shiri tare.11Sun ce, "Allah ya yashe shi, ku bi ku ɗauko shi, gama ba wanda zai cece shi."12Allah, kada ka yi nisa dani, Allahna, ka yi sauri ka taimake ni.13Bari su sha kunya su hallaka su waɗanda suka hasalar da raina; su ji kunya su hallaka. bari zarga da raini su rufe su, su waɗanda ke so su lahanta ni.14Amma zan sa begena a gare ka, zan yabe ka gaba-gaba.15Bakina zai yi maganar adalcinka da cetonka dukkan yini, koda yake ba zan iya gane shi ba.16Zan zo da manyan ayyukan Ubangiji Yahweh, zan faɗi adalcinka, naka kaɗai.17Allah, ka koya mani tun ina saurayi, har yanzu ina shelar ayyukanka na ban mamaki.18I, ko lokacin da kaina ya yi furfura, Allah, kada ka yashe ni, ina ta shelar ƙarfinka ga tsara mai zuwa, ikonka kuma ga kowanne mai zuwa.19Adalcinka kuma, ya Allah yana da tsawo ƙwarai, kai da ka yi manyan abubuwa, Allah, wane ne kamar ka?20Kai da ka nuna mana wahalhalu da yawa masu tsanani, za ka farfaɗo damu, ka fito damu daga ƙarƙashin ƙasa.21Ka ƙara mani martaba, ka juyo ka ƙarfafa ni.22Zan kuma yi maka godiya da molo saboda amincinka, Allahna; gare ka zan yi yabo da molo, mai tsarki na Isra'ila.23Leɓunana zasu yi sowa ta farinciki, sa'ad da nake raira yabo a gare ka-har da raina, wanda ka fanso.24Harshena kuma zai yi maganar adalcinka dukkan yini; gama sun ji kunya sun rikice, su waɗanda ke nema su lahanta ni.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Duba yadda "kada ka bari a wulakanta ni" an fassara a cikin Zabura 25:1. AT: "ka da ku bari magabtana su sa ni kunya"
Mai iya yiwuwa su ne 1) "sanya ni lafiya saboda koyaushe kuna yin abin da ke daidai" ko 2) "ku ba ni lafiya kamar yadda nake aikata abin da kuke so in yi"
Mai zabura ya yi amannar cewa Yahweh zai kāre shi kuma ya ba shi lafiya kamar yana ɓuya a saman wani babban dutse ko kuma a cikin sansanin soja da mutum ya ƙera.
Mai zabura ya yi amannar cewa Yahweh zai kāre shi kuma ya ba shi lafiya kamar yana ɓuya a saman wani babban dutse ko kuma a cikin sansanin soja da mutum ya ƙera.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) kalmar "hannu" alama ce don ƙarfi. AT: "daga ikon mugaye, daga ikon azzalumai" ko 2) "hannu" yana nufin mutumin da kansa. AT: "daga mugaye, daga marasa adalci ... mutane" ko "don mugaye da marasa adalci ... mutane ba za su iya cutar da ni ba"
Anan “bege” ishara ce ga wanda mai zabura ke fatan sa. AT: "kai ne wanda nake da tabbacin zan taimake ni"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kun tallafa min tun daga mahaifar" ko "Kun kula da ni tun lokacin da na fito daga mahaifar mahaifiyata"
"Mutane da yawa suna ganin yadda nake rayuwa kuma suna so in yi rayuwa kamar yadda nake yi"
"Kar ka tilasta min na rabu da kai." Don Allah ya ƙi shi ana magana ne kamar Allah ne ke tilasta shi ya tafi. Duba yadda aka fassara wannan a cikin Zabura 51:10. AT: "kar ku ƙi ni"
"kar ka bar ni har abada"
Ana nuna cewa suna kallon dama don ɗaukar ransa. Kalmomin "ɗaukar rai" na nufin kisa. AT: "kula da wata dama don ɗaukar raina" ko "jira wata dama don kashe ni"
Tunda har yanzu Yahweh bai amsa roƙon marubucin ba, ya yi magana game da Yahweh kamar Yahweh yana tsaye nesa da marubucin.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ka basu kunya ka kuma hallakar dasu"
Bakin bakin ne ga mutum dukka. AT: "Zan fada" ko "Zan yi magana da bakina in fada"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Zan ba su labarin manyan ayyukan da Ubangiji Yahweh ya yi" ko kuma 2) "domin Ubangiji Allah Ya ba ni ƙarfi don yin manyan ayyuka."
Ana iya bayyana bayanin a sarari. "ya koya mani abubuwa da yawa"
Bayanin da aka bari za'a iya bayyana a sarari. AT: "kuma kamar yadda na shelanta ikonku ga duk wanda zai zo"
Mai zabura yayi maganar kyawawan abubuwa da Allah yayi kamar an haɗa su kamar babban gini ko dutse.
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "babu irin ku!"
Wannan yana bayyana aiki ɗaya ta hanyar jimloli biyu. AT: "sake yi mani ta'aziya"
"A gare ka, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, zan raira waƙoƙin yabo lokacin da nake kaɗa molaye"
"Lebe" yana wakiltar mutum duka. AT: "Zan yi ihu don murna"
A nan "harshe" yana nufin mutum dukka. AT: "Zan kuma yi magana"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Gama Allah ya kunyata su kuma ya rikitar da su"
1Ka ba sarki dokokinka masu adalci, Allah, adalcinka kuma ga ɗan sarkin.2Dãma ya hukunta jama'arka da adalci, matalautanka kuma da adalci.3Dãma duwatsu su fito da salama saboda mutanenka; dãma tuddai kuma su fito da adalci.4Dãma ya hukunta mutane matalauta; dãma ya ceci 'ya'yan mabuƙata, ya ragargaza azzalumi.5Dãma su ba ka daraja muddin rana tana haskakawa, wata kuma yana nan har zuwa tsararraki dukka.6Dãma ya sauko kamar ruwan sama a kan ciyawar da a ka tattake, kamar zubowar ruwan sama a kan ƙasa.7Dãma masu adalci su yalwata a kwanakinsa, dãma kuma a sami salama a yalwace har sai wata ya shuɗe.8Dãma ya yi mulki daga teku zuwa teku, daga kogi har zuwa ƙarshen duniya.9Dãma waɗanda ke zama a jeji su rusuna a gabansa; dãma maƙiyansa kuma su lashi turɓaya.10Dãma sarkunan Tarshish da na tsibirai su kawo gaisuwa a gare shi, dãma sarakunan Sheba da Seba su ba shi kyautai.11I, dãma dukkan sarakuna su rusuna a gabansa, dãma kuma dukkan al'ummai su bauta masa.12Gama ya kan taimaki mabuƙacin da yayi kuka da matalaucin da ba shi da mai taimako.13Ya ji tausayin mabuƙata da matalauta, ya kuma ceci ran mabuƙata.14Ya fanshi rayukansu daga wahala da kuma wulaƙanci, jininsu kuma yana da daraja a idanunsa.15Dãma ya rayu! Dãma a ba da zinariyar Sheba a gare shi. Bari mutane su yi masa addu'a koyaushe; dãma Yahweh ya albarkace shi dukkan yini.16Dãma a sami hatsi a yalwace a cikin ƙasa, na kan tudu kuma amfaninsu ya yi yabanya. Dãma kawunan hatsinsu ya zama kamar Lebanon, dãma jama'a su sami albarka kamar ciyawa ta saura.17Dãma sunansa ya kasance har abada, dãma sunansa ya ci gaba muddin rana ta nan; dãma jama'a su sami albarka ta wurinsa; dãma dukkan al'ummai su kira shi mai albarka.18Dãma Allah Yahweh, Allah na Isra'ila, ya zama mai albarka; wanda shi kaɗai ne ke yin abubuwan ban mamaki.19Dãma sunansa mai daraja ya zama mai albarka har abada, dãma kuma dukkan duniya ta cika da ɗaukakarsa. Amin -- Amin.20Dauda ɗan Yesse ya gama yin addu'o'insa. Littafi na Uku.
"Taimaka wa sarki hukunci dai-dai"
Ana iya samar da kalmar daga jimlar da ta gabata. Anan kalmar "adalci" tana nufin yanke hukunci na adalci. AT: "ku ba ɗan sarki adalcinku" ko "bawa ɗan sarki damar yin mulki da adalci"
Mai zabura yayi magana game da mutanen Isra’ila kamar dai su ne duwatsu da tuddai da suke rayuwa a kansu. Yana maganar duwatsu da tuddai kamar su duk ƙasar Isra’ila ne, kamar wannan ƙasar lambu ne mai ba da ’ya’ya, da salama da adalci kamar su’ ya’yan ne. AT: "Bari mutanen ƙasar su zauna cikin salama ... su yi komai a kan hanya madaidaiciya"
Marubucin yayi magana game da sarki wanda ya kayar ko azabtar da mutanen da ke zaluntar wasu kamar dai waɗancan mutane abubuwa ne waɗanda sarki zai farfashe. AT: "azabtar da mutumin da ya zalunci wasu"
Rana da wata wata ma'ana ce ta yini da dare, waɗanda suke tare da juna abune mai ma'ana har abada. AT: "har abada, ba tare da ƙarewa ba"
Sarki zai yi kyau, zai yi wa jama'arsa abubuwa masu kyau kamar ana ruwan sama yana mai daɗi ga ciyawar da aka yankinta.
"Ko ya sauko kamar saukar ruwan." Sarki zai yi kyau, kuma zai yi wa mutanensa abubuwa masu kyau kamar dai ana ruwan sama ne yana yi wa ƙasa alheri. (Duba: da
Mai zabura yayi magana kamar dai zaman lafiya abu ne na zahiri kamar abinci. "Yawan" shine lokacin da akwai wani abu mai yawa. Ana iya sake bayyana wannan don cire sunayen suna "yawa" da "salama". AT: "na iya mutanen kirki su zauna lafiya"
"muddin wata ya haskaka" ko "har abada"
"Bari sarki ya yi sarauta"
Duk waɗannan maganganun abubuwa ne masu rai kuma suna nufin duniya duka.
Wannan kwatanci ne na tsananin wulakanci. AT: "kuyi duk abin da zasu iya don ya basu damar rayuwa"
"ku rusuna a gabansa" ko "girmama shi a matsayin sarkinsu"
"Yana so ya hana matalauta da mabukata wahala"
Anan “rayuwa” tana nufin mutum duka. AT: "ya fanshe su" ko "ya cece su" ko "ya cece su"
Anan "jininsu" shine wani magana don ƙoshin lafiyarsu. Ganin Yahweh yana wakiltar hukuncinsa ko kimantawarsa. AT: "zaman lafiyarsu yana da matukar muhimmanci a gare shi" ko "yana son su rayu da kyau"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari su ba shi zinaren Sheba" ko "Bari ya karɓi zinariyar Sheba"
"Yawan" shine lokacin da akwai wani abu mai yawa. Ana iya bayyana wannan suna mara amfani a matsayin "yawa" ko "yalwa" Madadin fassara: "hatsi da yawa" ko "hatsi mai yawa"
Ana maganar ci gaban mutane a cikin birane kamar ciyawa ce da ke yalwata a cikin filayen.
Ana amfani da wannan maganar don girmama Allah ta hanyar bayyana sha'awar mutane su tuna shi koyaushe. AT: "Bari mutane koyaushe su san shi" ko "Kada mutane su taɓa mantawa da wanene shi" (Duba: fgs_idiom)
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ya sa shi ya aikata abubuwa masu kyau ga mutane"
Waɗannan ayoyin sun fi ƙarshen wannan zaburar. Magana ce ta ƙarshe ga duka Littafin 2 na Zabura, wanda ya fara daga Zabura ta 42 kuma ya ƙare da Zabura ta 72.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari mutane su yabi Yahweh Allah, Allah na Isra'ila"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari mutane su albarkaci sunansa mai ɗaukaka har abada" ko kuma, ɗaukar "sunan" a matsayin ƙaren sunan Yahweh da kansa, "Bari mutane su san har abada yadda ɗaukakarsa take"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Dauda, ɗan Jesse ya gama addu'arsa" ko "Wannan ita ce addu'ar ƙarshe ta Dauda ɗan Jesse"
1Hakika Allah mai alheri ne ga Isra'ila, gare su da suke da tsabtar zuciya.2Amma a gare ni kafafuna sun kusa su zame; kafafuna sun kusa su zame waje daga karkashina.3saboda na ji kishin masu girmankai sa'ad da na ga wadatar masu mugunta.4Gama basu da raɗaɗi har ranar mutuwarsu, amma suna da ƙarfi kuma suna ci da kyau. Basu da nawayar sauran mutane;5Basu da masifu kamar na sauran mutane.6Girmankai na rataye a wuyansu kamar sarƙa; tashin hankali ya rufe su kamar riga.7Daga irin wannan makantar zunubi ke zuwa; mugayen tunani sun ratsa zukatansu8Suna ba'a kuma suna magana cikin mugunta; cikin fankamarsu suna yin kurarin zalunci.9Suna magana gãba da sammai, harsunan su kuma na tattaki a ƙasa.10Domin haka mutanensa sun juya gare su isassun ruwaye sun cika kwararo.11Suka ce, "Ta yaya Allah ya sani? Akwai wani sani a wurin maɗaukaki?"12Kula: waɗannan mutane mugayene; a koyaushe a huce suke, sai ƙara zama mawadata suke yi.13Lallai a banza na kiyaye zuciyata kuma na wanke hannuwana cikin rashin laifi.14Kowacce rana ina shan azaba da horo kowacce safiya.15Idan nace, "Zan faɗi waɗannan abubuwa," da naci amanar wannan tsarar ta 'ya'yanka.16Ko da shike na yi ƙoƙarin fahimtar waɗannan abubuwa, ya zama da wahala a gare ni.17Daga nan sai na tafi cikin wuri mai tsarki na Allah daga nan na fahimci makomarsu.18Hakika ka sanya su a wurare masu santsi; ka kawo su ƙasa ga hallaka.19Yadda suka zama jeji farat ɗaya! ƙarshensu yazo sun ƙarasa cikin babban tsoro.20Sun zama kamar mafarki bayan da mutum ya farka; Ya Ubangiji, sa'ad da ka tashi, ba zaka yi tunanin komai game da waɗannan mafarkan ba.21Gama zuciyata ta damu, a cikina nayi rauni. Na zama jahili na kuma rasa basira;22Na zama kamar dabba marar tunani a gabanka.23Duk da haka kullum ina tare da kai; Ka riƙe hannuna na dama.24Zaka bishe ni da shawarar ka bayan wannan ka karɓe ni zuwa ɗaukaka.25Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba wani a duniya da nake marmari in ba kai ba.26Jikina da zuciyata sun yi sanyi, amma Allah shi ne ƙarfin zuciyata har abada.27Waɗanda suke nesa da kai zasu lalace; zaka hallaka dukkan marasa aminci gare ka.28Amma ni, abin da nake bukata shi ne in kusanci Allah. Na mai da Ubangiji Yahweh mafakata. Zan bayyana dukkan ayyukanka.
Mai zabura yayi maganar rashin iya dogaro da Allah da kuma son yin zunubi kamar ya kusan faɗuwa yayin da yake tafiya a kan wata hanya mai santsi. AT: "Na kusan daina dogaro ga Allah; Na kusan aikata laifin aikata babban zunubi a kansa"
Nayi kishi “mai girman kai” za a iya fassara shi azaman jumlar suna. AT: "mutane masu girman kai"
Ana iya fassara kalmar "wadata" azaman aiki. AT: "yadda miyagu ke da kyawawan abubuwa da yawa"
Kalmomin "nauyaya" wani magana ta gwagwarmayar rayuwar yau da kullun (buƙatar abinci, mafaka, sutura, da lafiya).
"ba sa shan wahala kamar yadda sauran mutane ke sha"
Wannan yana nufin miyagu suna nunawa kowa girman kai da tashin hankali kamar suna sanye da abin wuya ko kyakkyawan tufafi.
Domin suna kama da makafi waɗanda ba sa ganin inda za su, suna yin zunubi ba tare da sun sani ba. Kasancewa makaho kwatanci ne ga mutum ya kasa ganin muguntarsa.
A nan “bakinsu” misalai ne ga maganarsu, kuma “sammai” alama ce ta Allah, wanda ke zaune a cikin sammai. AT: "Suna magana game da Allah, wanda ke cikin sama"
Kalmar "harsuna" tana wakiltar mutane da kansu. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "suna tafiya a cikin duniya suna faɗar abubuwa marasa kyau game da Allah" ko 2) "suna zuwa ko'ina suna alfahari da kansu."
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Mutanen Allah suna sauraro da kyau ga maganganun mugayen mutane" ko 2) "miyagu suna da yalwar abinci da za su ci da ruwan inabin da za su sha"
Wadannan tambayoyin na zance shine nuna raini ga Allah. Wadannan tambayoyin ana iya fassara su azaman maganganu. AT: "Tabbas Allah bai san abin da muke yi ba. Maɗaukaki ba shi da masaniya game da shi."
Asaf yayi maganar kare zuciyarsa kamar yana tsare birni ko gini daga makiya. AT: "Na kiyaye tunanina tsarkakakku"
Marubucin yayi maganar tsarkakakken kansa kamar ya wanke hannayensa da rashin laifi maimakon ruwa. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Zabura 26: 6. AT: "ayyukana sun kasance tsarkakakku" ko "Na wanke hannuwana don nuna ba ni da laifi"
"Kin wahalar dani." Duba yadda "ba a azabtar da su ba" an fassara a cikin Zabura 73: 4.
"An hukunta ni"
"abin da ke faruwa da mugaye lokacin da suka mutu" ko "yadda mugaye suke mutuwa"
Kalmar "jeji" wani magana ne ga mutumin da ya rasa komai mai kyau. AT: "Da sauri aka hallakar da su"
Miyagu ba za su daɗe kamar abin da mutum ya gani a mafarki ba. Yana bacewa da zarar mutum ya farka.
Kalmar nan "zuciya" tana wakiltar mutum yana mai jaddada tunaninsu da yadda suke ji. AT: "Na yi bakin ciki ƙwarai"
Waɗannan jimlolin guda biyu ma'anar abu ɗaya ne kuma suna jaddada ƙaramin saninsa. AT: "jahili sosai"
Kalmar "Ni" a nan tana wakiltar Asaf. Kalmar "ku" anan tana wakiltar Allah.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "sanya ni inda mutane za su girmama ni" ko 2) "girmama ni ta hanyar kai ni inda kake." Duba yadda ake karɓar "karɓe ni" a cikin Zabura 49:14.
Kuna iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Babu wani a wurina a sama sai ku!" ko "Kai kadai nake da shi a sama"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya. Tare suna wakiltar mutum dukka. AT: "Jikina da hankalina"
A nan an kwatanta ra'ayin nisantar Allah da rashin son yi masa biyayya. AT: "Waɗanda ba sa son yi muku biyayya"
1Ya Allah, don me ka yashe mu har abada? Don me fushin ka yayi ƙuna a kan tumakin makiyayarka?2Ka da tuna mutanenka, waɗanda ka saya a zamanin dã, kabila wadda ka fãnsa su zama abin gãdonka, da Tsaunin Sihiyona, inda kake zama.3Kazo ka dubi dukkan hallakarwa, dukkan ɓarnar da maƙiyi yayi a cikin wuri mai tsarki.4Abokan gãbar ka sun yi ruri a tsakiyar zaɓaɓɓen wurinka; sun kafa tutocin yaƙinsu.5Sun sassare ruƙuƙin kurmi da gatura.6Sun ragargaza sun kuma sassake su dukka; sun karya su da gatura da gudumai.7Sun kunna wa wurinka mai tsarki wuta; sun tozarta wurin zaman ka, sun buga shi har ƙasa.8A cikin zuciyarsu suka ce, "Zamu hallakar dasu dukka," Sun ƙone dukkan wuraren taruwarka cikin ƙasar.9Bamu ga wasu alamu ba; ba sauran wani annabi, ba wani a cikin mu da yasan har yaushe wannan zai ƙare.10Ya Allah, har yaushe maƙiyi zai yi ta cin mutuncin ka? Maƙiyi zai yi ta saɓon sunanka har abada?11Donme ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fito da hannunka na dama daga cikin rigarka ka hallaka su.12Duk da haka Allah sarkina ne tun zamanun dã, mai kawo ceto a duniya.13Ka raba teku da ƙarfinka; ka farfasa kawunan dodannin teku cikin ruwaye.14Ka murƙushe kan Lebiyatan; ka ciyar da waɗanda suke zama cikin jeji da shi.15Ka karya buɗaɗɗun maɓuɓɓulai da ƙoramai; kasa koguna masu gudu su ƙafe.16Yini naka ne, dare kuma naka ne; kaine ka sanya rana da wata.17Kaine ka sanya dukkan iyakokin duniya; kayi damina da rani.18Yahweh, Ka tuna yadda maƙiyi yayi ta jefa maganganun banza a kanka, wawayen mutanen nan sun yi saɓon sunanka.19Kada ka miƙa ran kurciyarka ga naman jeji. Kada ka manta da ran mutanenka da ake zalunta har abada.20Katuna da alƙawarinka, gama wurare masu duhu na ƙasa suna cike da tashin hankali.21Kada ka bari waɗanda ake zalunta su dawo cikin kunya; bari talakawa da waɗanda ake zalunta su yabi sunanka.22Ka tashi, ya Allah; ka kãre mutuncinka; ka tuna yadda wawaye suke zaginka dukkan yini.23Kada ka manta da muryar magabtanka ko hargowar waɗannan da suke ci gaba da adawa da kai.
Ana iya fassara wannan azaman bayani. "naku har abada" AT: "Allah, ba mu yi wani laifi ba, amma ka ƙi mu har abada!" (Duba: figa_rquestion)
Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Mu ne waɗanda kuka yi alƙawarin kulawa da su, kuma ba mu yi laifin komai ba, amma yanzu kuna fushi da mu!"
Asaf yayi magana game da mutanen Isra'ila kamar tumaki. AT: "akan Isra'ila, waɗancan kamar tumakin da kuka ke kiwon su a wurin kiwo"
"naku har abada"
Waɗannan ayoyin suna bayanin ainihin abin da ya faru, hari na zahiri a kan haikalin Isra'ila a Yerusalem.
Abokan hamayyar suna ihu da ƙarfi da babbar nasara.
Wannan karin magana ne. AT: "Sun ce wa kansu" ko "Sun yi tunani a kansu"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Ba mu ga wasu alamu na banmamaki daga Allah ba" ko 2) "Duk alamominmu masu alfarma sun tafi" ko kuma 3) "alamomin" su ne tutoci da alamomin rundunar da ke wakiltar rundunar kanta. . AT: "Sun lalata sojojinmu kwata-kwata"
Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Allah, makiya sun dade suna zaginka a kan ka!"
Mai zabura yayi maganar Allah kamar yana da jiki. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Dakatar da riƙe hannunka, hannunka na dama!"
Asaf yana maganar Allah kamar Allah yana da jiki na zahiri. "Kuna da ƙarfi sosai kun sami ikon yin busasshiyar ƙasa a tsakiyar teku."
Asaf tabbas yana magana ne game da Fir'auna da rundunarsa kamar dodo. Idan za ta yiwu, fassara waɗannan kalmomin a zahiri. AT: "lokacin da kuka kashe sojojin Fir'auna, sai kace kun fasa kawunan dodannin ruwa a cikin ruwa"
Lebiyatan wani dodo ne na teku. Yana wakiltar azzalumin makiyi.
Yahweh yana sa maɓuɓɓugai da rafuffuka suna gudana daga ƙasa kamar dai ya buɗe ƙasa domin su gudana. AT: "Kun sa maɓuɓɓugai da ƙoramu suka malalo daga ƙasa"
"iyakokin ƙasa da teku"
Asaf yayi magana akan kalmomin zagi kamar abubuwa ne na zahiri, kamar duwatsu, wanda abokan gaba ke jefawa Yahweh. AT: "makiyi ya zage ku sau da dama"
Asaf yayi magana kansa kamar kurciya, tsuntsu mara kariya. Wannan jumlar na iya zama ishara ga mutanen Isra'ila. AT: "ni, kurciyar ku"
"Kada ku ci gaba har abada ba abin da zai taimaki mutanenku da ake zalunta." Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Ku zo nan kusa don taimaka wa mutanenku da ake zalunta"
Kalmar "duhu" wataƙila kwatanci ne na wurin da abubuwa marasa kyau ke faruwa ko kuma ga filayen da aka tura Isra'ilawa zuwa bauta, amma ya kamata a fassara waɗannan kalmomin a zahiri idan zai yiwu.
"Kada ka bari azzaluman mutane su ci nasara a kan wadanda aka zalunta su kunyata su"
"Nuna wa kowa cewa kana da gaskiya"
Kalmar "murya" ishara ce ga kalmomin da mutane suke amfani da su lokacin da suke magana. AT: "abin da abokan adawar ku ke fada"
1Muna yi maka godiya, ya Allah; muna godiya, domin ka bayyana kasancewarka; mutane suna faɗin ayyukanka na al'ajabi.2A ƙayyadajjen lokaci zanyi hukunci da dai-daita.3Koda ya ke duniya da mazauna cikinta sun girgiza cikin tsoro, na kafa wa duniya ginshiƙai. Selah4Nace wa masu girmankai, "Kada kuyi girmankai," ga masu mugunta kuma, "Kada ku ɗaga ƙaho;5kada ku ɗaga ƙahonku ga sammai; kada kuyi magana da ɗaga wuya na rashin mutuntawa."6Ba daga gabas bane ko daga yamma, kuma ba daga jeji bane ɗaukaka take fitowa ba.7Amma Allah ne mai shari'a; yakan ƙasƙantar yakan kuma ɗaukaka sama.8Gama Yahweh ya riƙe ƙoƙon inabi cikin hannunsa mai sa buguwa, wanda yake gauraye da kayan yaji, yana tsiyayar da shi. Hakika dukkan miyagun duniya zasu shanye shi dukka.9Amma zan ci gaba da faɗin abin da kayi; Zan raira yabbai ga Allah na Yakubu.10Yace, zan datse dukkan ƙahonnin miyagu, amma ƙahonnin masu adalci zasu ɗaukaka."
"duk mutanen da suke rayuwa a kanta"
"kiyaye ƙasa daga halakarwa" ko AT: "kiyaye mutanena lafiya"
Asaf yayi magana game da mugayen mutane kamar dabbobi masu ƙaho a kawunansu, yana miƙa wuyansu yana riƙe da kawunansu sama yadda zasu iya tsoratar da sauran dabbobi. AT: "Tabbas musamman kada ku yi alfahari da cewa kun fi Allah"
Asaf yayi magana game da mugayen mutane wadanda suka nuna bijirewa ko kalubalantar Allah kamar dabbobi masu ƙaho a kawunansu, suna miƙa wuyansu suna ɗaga kai sama don tsoratar da wasu dabbobi. AT: "da girman kai" (Duba:
Asaf yayi magana game da wanda ya daga sama kamar dai shi ne aikin dagawa. Ya kuma yi maganar Allah yana ba mutum ƙarfi da ɗaukaka kamar dai Allah yana ɗaga mutumin a sama. AT: "Wanda zai daga ku ba zai zama wanda ya zo daga gabas ba" ko "Wanda zai karfafa ku kuma ya sa mutane su girmama ku ba zai kasance daga gabas ba"
An yi kalmomin suna iya bayyana a sarari: "ya saukar da wasu mutane ya kuma ɗauke wasu mutane sama." Kalmomin "ya saukar da ƙasa" da "tayar da su" kwatanci ne na Allah yana sa mutane su zama masu iko kuma ya karɓe ikonsu. AT: "ya naɗa mutum ɗaya sarki a maimakon wani mutum" ko "ya ƙwace ikon mutum ɗaya ya ba wani mutum iko"
Kumfa kwatanci ne na ikon giya don sa mutane su bugu, AT: "ruwan inabi mai ƙarfi"
Ƙahonin dabba kwatanci ne na ƙarfin mutum. Ana iya fassara wannan azaman sanarwa a cikin tsari mai aiki. AT: "Zan ɗaga ƙahonin adalai" ko "Zan sa masu adalci su zama masu ƙarfi"
1Allah ya sanar da kansa cikin Yahuda; sunansa mai girma ne cikin Isra'ila.2Rumfarsa cikin Salem take; wurin zaman sa cikin Sihiyona ya ke.3A can ya kakkarya kibawu na baka, garkuwa da takobi da sauran kayan yaƙi. Selah4Ka haskaka da sheƙi kuma ka bayyana ɗaukakarka, daka sauka daga duwatsu, wurin daka kashe masu azabtar da kai.5Masu ƙarfin zuciya an washe su; an kashe su. Dukkan jarumawa sun rasa mai taimako.6Bisa ga tsautawarka, Allah na Yakubu, doki da mahayinsa sun faɗi sun mutu.7Kai, I kaine za a ji tsoro; wa zai tsaya gabanka lokacin da kayi fushi?8Daga sama kasa aji hukuncinka; duniya ta ji tsoro tayi shiru9lokacin da kai, Allah, ka tashi don tabbatar da hukunci kuma ka ceci dukkan waɗanda ake zalunta na duniya. Selah10Hakika fushin hukuncin ka akan ɗan adam zai kawo maka yabo; ka yiwa kanka ɗamara da sauran abin da ya ragu na fushinka.11Kayi alƙawura ga Yahweh Allahnka ka kumaa cika su. Bari duk waɗanda suke kewaye da shi su kawo kyautai gare shi wanda ya isa a ji tsoronsa.12Ya datse ruhun 'ya'yan sarakai; sarakunan duniya sun ji tsoron sa.
"ya sa mutanen Yahuda su san shi wane ne" ko "ya zama sananne a cikin Yahuda"
Kalmomin "sunansa" magana ne don sunansa. AT: "mutanen Isra'ila sun dauke shi mai kyau da iko"
Waɗannan kalmomin wataƙila kwatanci ne na Allah don ya sa mutanen Yahuda su zauna lafiya ba tare da jin tsoron maƙiyan da za su yaƙi su ba, amma ya kamata a fassara kalmomin a zahiri.
Jumla ta biyu tana ƙarfafa jimla ta farko a cikin cewa ɗaukakar Yahweh tana da alaƙa da Yahweh yana haske.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutanenku sun kashe jaruman sojoji na abokan gaba sannan kuma suka kwashe dukiyoyinsu"
Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Ba wanda zai iya tsayawa a gabanku lokacin da kuka yi fushi." ko "Kuna iya halakar da duk wanda kuka yi fushi da shi."
"ka yanke hukunci" ko "ka sanar da yadda zaka hukunta mugaye"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "mutane za su yabe ka saboda ka yi fushi da mugaye kuma ka hukunta su" ko 2) "mutanen da suke fushi da kai za su yi abubuwan da za su sa mutane su yabe ka."
"Yahweh, wanda za su ji tsoronsa"
Jimlar "Ya yanke ruhu" karin magana ne wanda ke nufin Ya karya ruhun ko Ya kaskantar da kai. AT: "Ya ƙasƙantar da sarakuna"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "sarakunan duniya suna tsoronsa"
1Da muryata zan yi kira ga Allah; Zan yi kira da muryata ga Allah, Allah zai ji ni.2A cikin ranar masifata na biɗi Ubangiji; da dare na miƙar da hannuwana waje, ba kuwa zasu gaji ba. Raina yaƙi ta'azantuwa.3Na tuna da Allah yayin da nayi nishi; Nayi tunaninsa yayin dana sụma. Selah4Ka riƙe idanuna a buɗe; na damu ƙwarai na kasa magana.5Na tuna da kwanakin dã, game da lokuttan da suka wuce tun-tuni.6A cikin dare na tuna da waƙar dana taɓa rairawa. Nayi tunani a hankali kuma nayi ƙoƙarin fahimtar abin da ya faru.7Ko Ubangiji zai ƙini har abada? Ba zai ƙara nuna cewa ya ji ɗaɗi na ba?8Amintaccen alƙawarinsa ya tafi har abada? Ko alƙawarinsa ya tsinke har abada?9Ko Allah ya manta zama mai alheri? Ko fushinsa ya kulle jinƙansa ne? Selah10Nace, "Wannan baƙinciki na ne: Canjin hannun dama na Maɗaukaki a kanmu."11Amma zan tuna da ayyukanka; Zan yi tunani game da ayyukanka na al'ajabi na dã.12Zan yi bin-binin dukkan ayyukanka kuma in yi tunani a kansu.13Hanyarka, ya Allah, mai tsarki ce, ba wani allah da za a kwatanta shi da Allahnmu babba?14Kaine Allah wanda kake aikata al'ajibai; ka bayyana ƙarfinka tsakanin dangogi.15Ka ba mutanenka nasara ta wurin girman ikonka - zuriyar Yakubu da Yosef. Selah16Ruwaye sun ganka, ya Allah; ruwaye sun ganka, kuma sunji tsoro; zurfafa sun raurawa.17Giza-gizai sun zubo da ruwa ƙasa; hadarin sammai sun yi tsawa; hasken walƙiyarka sun tashi kamar kibau.18Muryar tsawarka an ji ta cikin guguwa; hasken ya ɗaga duniya; duniya ta raurawa ta girgiza kuma.19Hanyarka tabi ta teku tafarkin ka kuma ta manyan ruwaye, amma ba a ga sawayenka ba.20Ka bi da mutanenka kamar garken tumaki ta hannun Musa da Haruna.
"Na yi addu'a tare da mika hannuna"
“Raina” na wakiltar mutumin. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba zan yarda kowa ya yi ƙoƙarin ta'azantar da ni ba"
"Na ce da Allah, 'Ka buɗe idanuna.'"
Idan ya cancanta, ana iya haɗa “zamanin da” da “lokutan da suka wuce”. AT: "game da abubuwan da suka faru tuntuni mai tsawo"
Wata ma'ana mai yiwuwa ita ce "abin da ke faruwa."
Waɗannan jimlolin biyu suna nuna ƙin yarda daga Ubangiji.
Asaf yayi magana game da Yahweh ba ya ƙara yin aminci ga alkawarinsa kamar dai amincin Yahweh ya tafi. Cikakken sunan "aminci" za a iya fassara shi da sifa. AT: "Shin ya daina kasancewa da aminci ga alkawarinsa ne har abada?"
"Hannun dama" sigar metonym don ƙarfi, iko ko ƙarfi. AT: "Maɗaukaki baya amfani da ikonsa don taimaka mana"
"abubuwan ban al'ajabi da ka aikata tuntuni"
Waɗannan kalmomin guda biyu suna bayyana ma'anar yin bimbini a kan abin da Yahweh ya yi.
Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "babu wani allah da zai kwatanta shi da Allahnmu mai girma."
Cikakken sunan "ƙarfi" ana iya fassara shi da sifa. AT: "an nuna wa mutane daga ƙungiyoyin mutane da yawa yadda ƙarfin ku yake"
Cikakken sunan "nasara" ana iya fassara shi da sifa. AT: "ya sa mutanenku su yi nasara"
"ruwa" da "zurfin" na nufin manyan ruwaye kamar teku.
Asaf yayi maganar gajimare kamar mutane ne wadanda suke zubo ruwa daga kwantena. AT: "Ruwan sama mai yawa ya faɗi" ko "An yi ruwan sama sosai"
Wannan karin gishiri ne don jaddada cewa walƙiya ta haskaka duk abin da marubuci zai iya gani. AT: "walƙiya ta haskaka komai gwargwadon yadda kuke iya gani"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "babu wanda ya ga sawun sawunku"
Wannan kalmomin yana kwatanta mutanen Allah da garken dabbobi.
1Ku ji koyarwata, ya mutanena, ku saurari maganar bakina.2Zan buɗe bakina cikin misalai; Zan raira game da ɓoyayyun abubuwa na dã.3Waɗannan sune abubuwan da muka ji muka kuma koya, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana. Ba zamu ɓoye su daga zuriyarsu ba.4Zamu sanar da tsara mai zuwa game da yabban ayyukan Yahweh, ƙarfinsa, da al'ajiban da ya aikata.5Gama ya tabbatadda shaidar alƙawari cikin Yakubu ya sanya shari'a cikin Isra'ila. Ya umarci kakanninmu cewa su koyar dasu ga 'ya'yansu.6Ya umarta wannan domin tsara mai zuwa ta iya sanin umarnansa, 'ya'yan da ba a haifa ba, su kuma su faɗi wa 'ya'yansu.7Daga nan sai su sa zuciyarsu ga Allah kada su manta da ayyukansa amma su kiyaye dokokinsa.8Daga nan ba zasu zama kamar kakanninsu ba, da suka zama da taurin kai da tsara mai tayarwa, tsarar da zukatansu ba dai-dai suke ba, waɗanda ruhohinsu basu tsaya sun yi aminci ga Allah ba.9'Ya'yan Ifraim sun riƙe makamai tare da bakukkuna, amma suka juya baya a ranar yaƙi.10Basu kiyaye alƙawari da Allah ba, suka ƙi yin biyayya da dokarsa.11Suka manta da ayyukansa, ayyukan al'ajiban daya nuna masu.12Sun manta da ayyukan mamaki da yayi a idanun kakanninsu a cikin ƙasar masar, cikin ƙasar Zowan.13Ya raba teku ya ƙetaradda su; ya sa ruwa ya tsaya kamar bangaye.14Da rana ya bishe su da girgije dukkan dare kuma da hasken wuta.15Ya tsaga duwatsu cikin jeji, ya basu ruwa a yalwace, isasshe dake iya cika zurfafan teku.16Yasa rafuffuka su malala daga cikin dutse ya kuma sa ruwan ya gudana kamar koguna.17Duk da haka suka ci gaba da yi masa zunubi, suna tayar wa Maɗaukaki cikin ƙasa busasshiya.18Suka ƙalubalanci Allah cikin zukatansu ta wurin tambayar abinci domin ƙosar da marmarinsu.19Sun yi wa Allah baƙar magana; suka ce, "Zai yiwu Allah ya shirya teburi a cikin jeji?20Duba, lokacin da ya bugi dutsen, ruwaye suka ɓullo rafuffuka suka yi ambaliya. Amma zai yiwu ya bada gurasa kuma? Zai iya tanada nama domin mutanensa?"21Lokacin da Yahweh ya ji wannan, yayi fushi; wutarsa tayi ƙuna akan Yakubu, fushinsa kuma ya hari Isra'ila,22saboda basu gaskata Allah ba basu kuma dogara ga cetonsa ba.23Duk da haka ya umarci sammai a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sararin sama.24Ya zuba masu manna su ci, ya kuma basu hatsi daga sama.25Mutane suka ci abincin mala'iku. Ya aika masu da abinci isasshe.26Yasa iskar gabas ta hura cikin sama, ta wurin ikonsa kuma ya jagoranci iskar kudu.27Ya zuba masu nama kamar ƙura, tsuntsaye da yawa kamar yashin teku.28Suka faɗo a tsakiyar sansaninsu, ko'ina kewaye da rumfunansu.29Suka ci suka ƙoshi sosai. Ya basu abin da suke marmari.30Amma duk da haka basu cika ba; tun abincinsu na cikin bakinsu.31Daga nan fushin Allah ya buge su ya kashe mafi ƙarfin su. Majiya ƙarfin Isra'ila ya buga su ƙasa.32Duk da wannan, sun ci gaba da yin zunubi kuma basu gaskata ayyukan al'ajabansa ba.33Domin haka Allah ya taƙaita kwanakin su; shekarunsu suna cike da razana.34Duk sa'ad da Allah ya buge su, sai su fara neman sa, za su juyo su neme shi da gaske.35Zasu tuna cewa Allah ne dutsensu Allah maɗaukaki kuma shi ne mai fansarsu.36Amma suka yi masa daɗin baki suka kuma yi masa ƙarya da maganganunsu.37Gama zukatansu basu dogara gare shi ba, basu yi aminci ga alƙawarinsa ba.38Amma shi, mai tausayi ne, ya gafarta laifofinsu bai hallaka su ba. I, lokuta da yawa yakan janye fushinsa bai tayar da dukkan hasalarsa ba.39Ya tuna cikin jiki aka yi su, iska mai wucewa da bata dawowa.40Sau nawa suka yi ta tayar masa cikin jeji suka ɓata masa rai cikin hamada!41Akai akai suka tuhunci Allah suka cakuni Mai tsarki na Isra'ila.42Ba su tuna da ikonsa ba, yadda ya fanso su daga abokin gaba.43Lokacin da ya aikata alamominsa masu tsoratarwa cikin Masar da al'ajabansa cikin yankin Zowan.44Ya juyarda kogunan Masarawa su zama jini don kada su sha daga rafuffukansu.45Ya aika da cincirindon ƙudaje da suka cinye su da kwaɗi da suka mamaye ƙasar.46Ya bada amfaninsu ga fãra aikin hannun su kuma ga babe.47Ya lalata inabinsu da ƙanƙara itatuwansu masu bada 'ya'ya ga jaura.48Ya saukar da ƙanƙara ga garkunansu aradu kuma ta fãɗa akan dabbobinsu.49Ya zuba masu zafin fushinsa. Ya aika da fushi, hasala, da wahala kamar wakili mai kawo masifa.50Ya baje wa fushinsa hanya; bai barsu su rayu ba amma ya ba she su ga annoba.51Ya kashe dukkan 'ya'yan fari cikin Masar, ɗan farin ƙarfinsu cikin rumfunan Ham.52Ya fitar da mutanensa waje kamar tumaki ya bishe su cikin jeji kamar garke.53Ya kare su kuma ba su ji tsoro ba, amma teku ya dulmiyadda abokan gabarsu.54Daga nan ya kawo su kan iyakar ƙasarsa mai tsarki, zuwa tsaunin nan da hannun damansa ya saya.55Ya kori al'ummai daga gaban su ya raba masu gadonsu. Ya sa kabilun Isra'ila suka zauna cikin rumfunansu.56Duk da haka suka ƙalubalanci da tozartar da Allah Maɗaukaki kuma ba su kiyaye umarnansa ba.57Sun yi rashin aminci suka yi yaudara kamar ubanninsu; suka zama marasa abin dogaro kamar tanƙwararren baka.58Gama sun sa shi fushi da masujadansu kuma suka harzuƙa shi ga yin kishi da gumakansu.59Sa'ad da Allah ya ji wannan, ya hasala ya ƙi Isra'ila gaba ɗaya.60Ya yashe da wuri mai tsarki na Shilo, rumfar in da ya zauna a tsakiyar mutane.61Ya bari a ƙwace ƙarfinsa ya bada ɗaukakarsa a cikin hannun abokan gãba.62Ya miƙa mutanensa ga takobi, yayi fushi da abin gãdonsa.63Wuta ta cinye majiya ƙarfinsu, "yanmatansu kuma ba su sami waƙar aure ba.64Firistocinsu sun faɗi ta kaifin takobi, gwaurayensu kuma suka kasa yin kuka.65Sa'an nan sai Ubangiji ya farka sai ka ce mai tashi daga barci, kamar jarumi wanda ya fasa kuwwa saboda buguwa da ruwan inabi.66Ya kori magabtansa baya; ya sa su cikin kunya ta har abada.67Ya ƙi rumfar Yosef, bai kuma zaɓi kabilar Ifraim ba.68Ya zaɓi kabilar Yahuda da Tsaunin Sihiyona wanda yake ƙauna.69Ya gina tsatsarkan wurinsa kamar sammai, kamar duniya wadda ya kafa ta har abada.70Ya zaɓi Dauda, bawansa, ya ɗauke shi daga wurin tsaron tumaki.71Ya ɗauke shi daga bin tumaki da ƙananan su, ya kawo shi ya zama makiyayin Yakubu, mutanensa, da Isra'ila, abin gãdonsa.72Dauda yayi kiwonsu da mutuncin zuciyarsa, ya bishe su da gwanintar hannuwansa.
Kalmar "bakin" tana wakiltar mutumin. AT: "maganata"
Karin maganar "bude bakina" na nufin magana. AT: "yi magana da misalai"
Ana iya rubuta wannan ta hanya mai kyau. AT: "Lallai za mu gaya wa zuriyarmu game da su"
Sauran ma'anoni masu yiwuwa su ne "shaidu" ko "dokoki."
Sojojin ma suna da kibiyoyi. AT: "yana da bakuna da kibiyoyi don makamai"
Wannan yana nufin yankin da ke kusa da garin Zowan, wanda yake a Masar.
AT: "karin ruwa fiye da yadda za su iya sha"
Suna son Allah ya tabbatar da cewa zai iya yin abin da ya ce zai yi kafin su gaskata da shi.
"don haka za su iya ci yadda suka ga dama"
Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Ba mu yi imani cewa Allah da gaske zai iya shimfida mana tebur a jeji ba!" ko "Allah, ka gwada mana cewa da gaske kana iya shimfida mana tebur a cikin jeji!"
Mutane suna yi wa Allah dariya don ya wulakanta shi da waɗannan tambayoyin. AT: "Amma ba za mu yarda cewa zai iya ba mu burodi ba ko kuma ya samar da nama ga mutanensa har sai mun ga yana yi."
Marubucin yayi maganar Yahweh yana azabtar da Isra'ila lokacin da ya fusata kamar dai fushinsa mutumin da ya auka wa Isra'ila ne. AT: "saboda ya fusata, sai ya auka wa Isra'ila"
Asaf yayi magana akan sararin samaniya kamar mutane ne masu ji da biyayya da umarnin Allah. AT: "ya yi magana da sama"
"Ya sa manna ta faɗo daga sama kamar ruwan sama"
Cikakken sunan "yawa" za a iya fassara shi da sifa. AT: "wadataccen abinci" ko "adadi mai yawa na abinci"
Marubucin yayi magana ne game da Yahweh yana sa tsuntsaye su faɗo daga sama kamar tsuntsayen suna ruwan sama wanda Yahweh ya sa su fadi. Ya kamanta yawan tsuntsayen da ƙura. AT: "Ya sa nama ya faɗo daga sama kamar ruwan sama, kuma akwai da yawa daga ciki har ya rufe ƙasa kamar ƙura"
karfi ake so
"Allah ya yi fushi ya auka musu." Duba yadda "fushinsa ya auka wa Isra'ila" an fassara shi a cikin Zabura 78:21.
AT: "ya kashe su tun suna ƙuruciya"
Asaf yayi maganar shekaru kamar suna kwantena. AT: "kowace shekara suna tsoran kowane lokaci"
Marubucin yayi magana game da Allah kamar yana kan tudu ko tsauni inda mutane zasu je su sami lafiya daga abokan gaba. AT: "Allah ne ya kare su"
Anan "zukata" shine meton don tunanin su. Ana magana ne don kasancewa da aminci a gare shi a matsayin haɗe da shi. AT: "tunaninsu bai karkata zuwa gareshi ba" ko "ba su kasance masu aminci a gare shi ba"
Asaf yayi magana game da fushin Allah kamar dai mutum ne mai fushi wanda Allah ya riƙe shi don ya hana shi afkawa wanda ya fusata shi. AT: "bai hukunta su ba duk da cewa ya yi fushi da su"
Asaf yayi magana game da fushin Allah kamar wanda yake bacci wanda Allah ya bashi damar bacci bai farka ba. AT: "bai bar kansa ya fusata sosai da su ba"
"wuraren da babu abinda ke tsiro"
Suna son Allah ya tabbatar da cewa zai iya yin abin da ya ce zai yi kafin su gaskata da shi. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Zabura 78:17.
Asaf yayi magana akan amfanin gona kyauta ce da Allah yayi wa ciyawa. AT: "Ya bar ciyawar ta ci ciyawar su"
"ya ba da kwarkwata ga ɓarna." Asaph yayi magana akan aikin mutane kamar wata baiwa ce da Allah yayi wa ciyawa. Kalmar "aiki" wani magana ne ta amfanin gona da aikinsu ya samar. AT: "ya bar fara ga fara cin amfanin gonar da suka yi aiki tuƙuru don samarwa"
Asaf yayi magana game da zafin fushin Allah kamar dai mutum ne wanda zai iya kaiwa wani hari. AT: "Ya yi fushi da su, don haka sai ya auka musu da ƙarfi ba zato ba tsammani"
Asaf yayi magana game da fushi, hasala, da matsala kamar dai su mutane ne da Allah zai iya aikowa suyi masa aikin sa. AT: "Ya fusata sosai har yana son cutar da Masarawa, don haka ya sanya musu matsala kuma ya kawo su cikin masifa"
"bai hana Masarawa su mutu ba" ko "bai yarda Masarawa su rayu ba"
Asaf yayi magana game da annobar kamar dai mutum ne wanda zai cutar da Masarawa. AT: "ya sanya su duka suna fama da rashin lafiya"
Marubucin yayi magana game da Isra'ilawa kamar tumaki. Wannan yana nufin Allah ya kula kuma ya kiyaye mutane kamar yadda makiyayi yake kiwon tumakinsa.
Kalmomin "hannun dama" na nufin iko. AT: "ya yi nasara da kansa ta amfani da nasa ikon"
Mai yiwuwa ma'anonin su ne 1) Allah ya sanya wa Isra'ilawa gadonsu a cikin ƙasar da sauran al'ummu suka taɓa rayuwa a ciki ko kuma 2) Allah ya sanya wa al'umman da ya kori waɗansu gādo a wani wuri dabam. "Ya ba su ƙasar da koyaushe zata zama tasu"
Wadannan kalmomin kusan abu daya suke nufi. Marubucin ya yi amfani da su biyun don ya nanata cewa Isra’ilawa ba su yi wa Allah abin da suka ce za su yi ba.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna cikin layi ɗaya kuma suna da ma'anoni iri ɗaya.
Asaf yayi magana akan ƙarfi da ɗaukakar Allah kamar wasu abubuwa ne na zahiri da mutane zasu iya kamawa su riƙe. Kalmomin "ƙarfi" da "ɗaukaka" wataƙila sunaye ne na akwatin alkawarin. Kalmar "hannu" magana ne ce ta ƙarfin abokan gaba. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ya ba wa magabtansa damar kama akwatin alkawarinsa na ɗaukaka; kawai ya ba su ne don su yi duk abin da suke so da shi"
"ya yi fushi da mutanen da ya ce zai zama nasa har abada"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Makiyan sun yi amfani da wuta don kashe samarinsu duka" ko 2) "Samarinsu sun mutu da sauri a yaƙi kamar wuta tana ƙone busasshiyar ciyawa." Kada kuyi magana cewa wadannan mutane sunyi amfani da bindiga.
Anan kalmar "takobi" tana wakiltar sojojin da suka yi yaƙi da takuba. Jimlar "faɗuwa da takobi" kalma ce da ke nufin mutu a yaƙi. AT: "Firistocinsu sun mutu a yaƙi" ko "Makiya sun kashe firistansu da takuba"
Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) wani ya tilasta gwauraye kada su yi kuka ko 2) firistoci da yawa sun mutu cewa babu lokacin jana'izar da ta dace.
Ubangiji ba ya aiki na wani lokaci ana maganarsa kamar yana barci, kuma farkon maganarsa ana magana da shi kamar ya farka. AT: "Ubangiji ya fara aiki kamar wanda ya farka daga barci"
Anan kalmar "rumfar" na nufin iyali. A cikin wannan magana yana nufin zuriyar Yosef. AT: "zuriyar Yosef"
Zai yiwu ma'anonin wannan misalin su ne 1) Yahweh ya daukaka tsattsarkan wurinsa sama. AT: "Ya gina tsattsarkan wurinsa sama, kamar sama" ko 2) Yahweh ya sanya tsattsarkan wurin ya dawwama kamar sammai. AT: "Ya gina tsattsarkan wurinsa domin ya dawwama, kamar yadda sammai suke har abada"
Kalmar "makiyayi" wani magana ne na jagoranci da kariya. AT: "Dauda ya bishe su kuma ya kiyaye su"
1Ya Allah bãƙin alummai sun zo cikin gãdonka; sun kazantar da haikalinka maitsarki; sun maida Yerusalem ta zama tsibin kangaye.2Sun bada gawawwakin bayinka a matsayin abinci ga tsuntsayen sararin sama, jikkunan amintattun mutanenka ga dabbobin duniya.3Sun zubar da jininsu kamar ruwa kewaye da Yerusalem, ba wanda zai yi jana'izar su.4Mun zama abin ba'a ga makwabtanmu, ba'a da reni ga waɗanda ke kewaye damu. Har yaushe, Yahweh? Zaka yi ta fushi har abada?5Har yaushe kishin fushinka zai yi ta ci har abada?6Ka zubo da fushinka kan al'umman da basu san ka ba da bisa mulkokin da basu kira bisa sunanka ba.7Gama sun cinye Yakubu sun hallaka ƙauyukansa.8Kada kayi ta tunawa da zunubin kakanninmu har su shafe mu; bari ayyukan jinƙanka su zo kanmu, gama mun yi sanyi ƙwarai.9Ka taimake mu, ya Allah na cetonmu, domin ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka yafe zunubanmu sabili da sunanka.10Don me al'ummai zasu ce, "Ina Allahn su?" Bari jinin bayinka da aka zubar yayi ramako akan al'ummai a idanunmu.11Bari nishin ɗaurarru ya zo gabanka; da girman ikonka ka tsare 'ya'yan waɗanda aka yanke wa mutuwa da rai.12Ya Ubangiji. Ka maida zagin da ƙasashe maƙwabtanmu suka zazzageka ka sau bakwai bisa cinyoyinsu.13Don haka mu mutanenka da tumakin makiyayarka zamu yi maka godiya har abada. Za mu faɗi yabbanka ga dukkan tsararraki.
Kalmar “jini” na nufin ta rayuwa marar laifi. Zubar da jini yana nufin kashe marasa laifi. Yawancin mutane suna ganin ruwa kowace rana, don haka don jini ya zama ruwan dare kamar ruwa, mutane da yawa marasa laifi zasu mutu. AT: "Sun kashe mutane da yawa marasa laifi har jinin yana ko'ina, kamar ruwa bayan an yi ruwa"
Kalmomin "zargi" da "izgili" sunaye ne ga waɗanda wasu suka zagi, ba'a, da izgili. AT: "Mun zama mutanen da maƙwabta suke zargi; waɗanda ke kewaye da mu suna yi mana ba'a da ba'a"
Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Kamar dai fushinku na hassada ba zai gushe yana ci kamar wuta ba."
Asaf yayi maganar fushin Allah kamar mai ruwa. AT: "Tunda kuna cikin fushi, hukunta al'ummomi"
"Kada ka ci gaba da tuna zunuban magabatanmu ka hukunta mu saboda su" ko "Ka gafarta mana zunuban kakanninmu"
Kalmar "suna" na nuna ta sunansa, don abin da mutane suka sani game da shi. AT: "domin mutane su san ɗaukakarku"
Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Bai kamata al'ummomi su iya cewa 'Ina Allahnsu yake ba?'"
Zubar da jini wata na nuna ta kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Ka ɗaukar fansar bayinka marasa laifi waɗanda al'ummomi suka kashe a inda za mu ga ka yi ta"
Kalmar "tumaki" kwatanci ne na mutanen da basu da karfi wanda makiyayi yake kiyayewa kuma yake jagoranta. AT: "mu da muke mutanenku, waɗanda kuke kiyayewa da jagorantar su, za mu gode muku"
"ku tabbatar cewa tsararraki masu zuwa duk abubuwan alherin da kuka aikata"
1Ka kasa kunne, Ya Makiyayi na Isra'ila, kai mai bida Yosef kamar tumaki; kai mai zama bisan Kerubim, ka haskaka a bisanmu!2A idon Ifraim da Benyamin da Manasse, ka motsa ikon ka; zo ka cece mu.3Ya Allah, ka maishe mu; ka sa fuskarka ta haskaka a bisanmu, mu kuwa zamu tsira.4Ya Yahweh Allah mai runduna, har yaushe zaka yi fushi da addu'ar mutanenka?5Ka ciyar dasu da gurasar hawaye ka basu hawaye mai yawa su sha.6Kasa mana wani abin da zamuyi jayayya da maƙwabtanmu a kansa, maƙiyanmu kuma suna yi mana dariya tsakaninsu.7Ya Allah mai runduna; ka dawo damu; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu tsira.8Ka fito da kuringa daga Masar; Ka kori al'ummai ka dasa ta.9Ka gyara kasa domin ta; ta kafa saiwa ta cika ƙasa.10Duwatsu sun rufe ta da inuwarta, Rassanta suna kama da itacen sida na Allah.11Ta miƙa rassanta har bakin teku tohonta kuma har bakin Kogin Yuferitis.12Don me ka rushe garunta har dukkan masu wucewa ta hanyar zasu tsinki 'ya'yanta.13Aladun kurmi sun batata, namomin jeji kuma suna kiwo cikin ta.14Ya Allah mai runduna; ka juyo, ka duba daga sama kayi la'akari ka kula da wannan kuringar.15Wannan itace sauyar daka dasa da hannunka na dama, reshen da kasa ya girma.16An ƙone shi da wuta an sare shi ƙasa; sun hallaka saboda tsautawarka.17Bari hannunka ya kasance bisa mutumin hannunka na dama, bisa ɗan mutum wanda kasa ya zama da karfi domin kanka.18Daga nan ba zamu juya daga gare ka ba; ka farkar da mu, mu kuwa zamu kira bisa sunanka.19Ya Yahweh, Allah mai runduna, ka dawo damu; kasa fuskarka ta haskaka a kanmu, ta haka zamu tsira.
Kuna iya bayyanawa a sarari cewa kerubobin sune waɗanda suke kan murfin akwatin alkawari. Marubutan Littafi Mai Tsarki sau da yawa suna magana game da akwatin alkawari kamar dai matashin sawun Yahweh ne wanda ya dogara da ƙafafunsa yayin da yake zaune a kan kursiyinsa a sama. AT: "ku da kuke zaune a kan kursiyinku a saman kerubobi a kan akwatin alkawari"
Kalmomin "motsa" na nufin "a aiwatar da shi."
Marubucin yayi magana game da Yahweh yana nuna musu alheri kamar fuskar Yahweh ta haskaka musu. AT: "ku aikata mana yadda ya kamata"
Kalmomin "gurasar hawaye" da "hawaye don sha" magane ne na ci gaba da baƙin ciki. AT: "Kun tabbatar da cewa suna bakin ciki a koyaushe"
Asaf ya kwatanta al'ummar Isra'ila da itacen inabi da aka shirya don dasawa. AT: "Kun fito da mu, kamar itacen inabi, daga Masar"
Mai Zabura yayi magana game da mutanensa kamar dai tsiron da Yahweh ya dasa. AT: "kun kori al'ummu daga ƙasarsu kuma kuka ba mu ita, itacen inabi, kuka dasa mu a can"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Inuwarta ta rufe duwatsu, rassanta kuma itacen al'ul na Allah ne"
bangon dutse, ba na itace ko katako ba
Hannun dama yana wakiltar ikon Yahweh. AT: "Wannan shine tushen da ku, Yahweh, kuka dasa"
Wannan kalmomin na nufin jama'ar Isra'ila, waɗanda Yahweh ya zaɓa domin mutanensa.
Anan "juya baya" kwatanci ne na ƙin wani. Hakanan za'a iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "ba za mu daina yin maka biyayya da yi maka biyayya ba" ko "koyaushe za mu yi maka sujada kuma mu yi maka biyayya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "za ku cece mu"
1Ku raira da ƙarfi ga Allah karfinmu; ku tada muryar farinciki ga Allah na Yakubu.2Ku raira waƙa ku kaɗa ganga, garaya mai daɗi da molo.3Ku busa ƙahon rago a ranar tsayawar sabon wata, a ranar cikar wata, ranar da bukukuwanmu ke farawa.4Gama farilla ce ga Isra'ila, sharia da Allah na Yakubu ya bayar.5Ya bada ita a matsayin doka cikin Yosef lokacin da ya tafi gãba da kasar Masar, in da naji muryar da ban fahimta ba.6Na kawar da nauyin daga kafaɗarsa; an raba hannunsa daga ɗaukar kwando.7A cikin masifa ka yi kira, na taimake ka; Na amsa maka daga duhun tsawar girgije. Na gwada ka a bakin ruwayen Meriba. Selah8Ku saurara, mutanena, gama zan gargaɗe ku, zan so da kun saurare ni!9Kada wani bãƙon allah ya kasance a cikinku; baza kuyi sujada ga wani bãƙon allah ba.10Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito da ku daga kasar Masar. Ku wage bakinku, ni ma in cika shi.11Amma mutanena basu saurara ga maganata ba; Isra'ila bata yi mani biyayya ba.12Domin haka na bar su da taurinkansu domin suyi abin da suka ga dama.13Ina ma, mutanena zasu saurare ni; ina ma, mutanena zasu yi tafiya cikin tafarkuna.14Dana hanzarta mamaye abokan gabarsu in kuma juya hannuna akan masu zaluntar su.15Dama waɗanda suka ƙi Yahweh su faɗi cikin tsoro gabansa! Dama su ƙasƙanta har abada. Zan ciyar da Isra'ila da alkama mai kyau;16Zan ƙosarda ku da zuma daga cikin dutse."
Bayyanar sunan "ƙarfi" ana iya bayyana shi da "mai ƙarfi." AT: "Allah wanda ya sa mu zama masu ƙarfi"
Anan "Yakubu" yana wakiltar dukkan zuriyarsa. AT: "Allah na Isra'ila, al'ummar zuriyar Yakubu"
Wannan tsakiyar watan ne.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah na Yakubu ya hukunta shi" ko "Allah na Yakubu ya umurce shi"
"ya ba shi a matsayin doka"
Wannan yana nufin abubuwanda suka faru na tarihi a Masar lokacin da mutanen Isra’ila suka zama bayi kuma Allah ya cece su.
Anan “kaya daga kafaɗarsa” yana wakiltar bautar da Isra'ilawa suka yi na bautar a ƙasar Masar.
"A cikin tsananin wahalar ku"
Lokacin da Allah ya zo wurin Isra'ilawa, ya ɓoye cikar kasancewarsa da ɗaukakarsa a cikin duhu mai duhu da barazanar.
"yaya zan so ku saurare ni" ko "amma dole ne ku fara saurare na!"
Ana maganar Allah yana kulawa da dukkan bukatun mutane kamar shi mahaifiya ce wacce take ciyar da 'ya'yanta tsuntsaye.
An yi magana game da barin Allah su ci gaba da taurin kai kamar Allah yana ba da su ga maƙiyi don ya bar abokan gaba su cutar da su. AT: "Saboda haka, na bar su da taurin kai"
Ana magana akan Allah yana son mutane suyi masa biyayya kamar yana son mutane suyi tafiya akan hanyoyinsa ko hanyoyin sa. AT: "Ina fatan da su kiyaye dokokina"
Yahweh yana magana akan kansa a cikin mutum na uku. AT: "wanda ya ƙi ni ... a gabana"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan wulakanta su har abada" ko "Zan hukunta su har abada"
Wannan yana nufin zumar daji. Ƙudan zuma na yin amya a cikin ramuka a cikin duwatsu kuma su sa zumar a wurin.
1Allah yana tsaye cikin taron jama'ar Allah; cikin tsakiyar alloli yana zartar da hukunci.2Har yaushe zaka yi hukuncin rashin gaskiya ka nuna kana goyon bayan masu mugunta? Selah3Ka kare talakawa da marasa mahaifa; ka kare hakkin masu shan azaba da marasa galihu.4Ka ceci fakirai da mabukata; ka fisshe su daga hannun mugu.5Basu da sani basu kuwa da fahimta; suna kai da komowa cikin duhu; dukkan harsasun duniya sun rugurguje.6Na ce, ku alloline, dukkan ku kuma 'ya'yan Maɗaukaki ne.7Duk da haka za ku mutu kamar mutane kuma ku faɗi kamar ɗaya daga cikin sarakuna."8Ya Allah, ka tashi, ka shar'anta duniya, gama kana da gãdo cikin dukkan al'ummai.
"yana bada hukunci." Cikakken sunan "hukunci" za'a iya bayyana shi azaman aiki. AT: "yana hukunci"
Yahweh yana amfani da tambaya don tsauta wa allolin don bai hukunta mutane da adalci ba.
Waɗannan duk maganganun suna ne. Ana iya bayyana su azaman sifofi. AT: "waɗanda suke fakirai ... waɗanda suke mabukata ... waɗanda suke fasiƙai"
Anan kalmar "hannu" tana wakiltar ƙarfi ko iko. AT: "a hana miyagu cutar su"
Ana magana game da aikata mugunta kamar suna tafiya a cikin wuri mai duhu.
Ana magana game da gumakan da suke lalata tsarin ɗabi'a da Yahweh ya kafa kamar alloli suna girgiza duniya kuma suna sa ta wargajewa.
Anan "alloli" suna nufin rukuni ɗaya kamar yadda yake a cikin Zabura 82: 1. Ko wannan yana magana ne game da mutane na ruhaniya ko mutane, su ba alloli bane kamar Yahweh shine Allah, kuma ba zahiri bane 'ya'yansa maza. Ta wurin kiransu "alloli" da "'ya'yan Maɗaukaki," Yahweh yana sane cewa ya ba su iko da ƙarfi.
Anan "ƙasa" tana wakiltar mutane. AT: "ku yanke hukunci ga mutanen duniya"
"gama dukkan al'umman gadonka ne." Yahweh yana ɗaukar dukkan mutane a matsayin nasa kuma yana mulkin su ana magana kamar al'ummai mallaki ne wanda ya gada. AT: "domin ku kuke mulkin duk mutanen kowace al'umma"
1Ya Allah, kada kayi shiru! Kada ka manta damu kada kuma kaƙi taimakon mu, ya Allah.2Duba, abokan gabarka suna tada hankali, su da suka ƙi ka sun tada kansu.3Sun shirya wa mutanenka makirci suna ƙulli gaba da waɗanda ka kãre.4Suka ce, "Ku zo mu hallaka su a matsayin al'umma. Daga nan ba za'a ƙara tunawa da sunan Yahweh ba.5"Sun ƙulla Makirci tare dabararsu ɗaya ce; don suyi gãba dakai suka yi ƙawance.6Wannan ya haɗa da rumfunan Idom da na Ishma'ilawa, da mutanen Mowab da Hagarawa, waɗanda suka ƙulla tare da7Gebal, Ammon, Amalek; ya kuma haɗa da Filistiya da mazaunan Taya.8Assuriya kuma ta hada kai dasu; suna taimakon zuriyar Lot. Selah9Kayi masu kamar yadda kayi wa Midiyan kamar yadda kayi da Sisera da Yabin a Kogin Kishon.10Suka hallaka a Endo suka zama kamar taki domin ƙasa.11Ka sa shugabanninsu sun zama kamar Oreb da Zib, da dukkan sarakunansu kamar Ziba da Zalmunna.12Suka ce, "Bari mu ɗaukar wa kanmu makiyayar Allah."13Ya Allahna, ka maishe su kamar ƙurar guguwa, kamar ƙaiƙai gaban iska,14kamar wuta mai cin kurmi, kamar harshen wuta mai kama duwatsu.15Ka koresu da iskarka mai ƙarfi, ka razanar dasu da guguwar hadari.16Ka cika fuskokinsu da kunya domin su nemi sunanka, Ya Yahweh,17bari su sha kunya su firgita har abada; dama su lalace cikin kunya.18Daga nan zasu sani kai kaɗai ne, Yahweh, kai ne Maɗaukaki bisa dukkan duniya.
Anan "yin hayaniya" yana nufin suna tayar da hankali da tawaye. AT: "Duba, maƙiyanku suna tawaye a kanku"
Jumlar "ɗaga kawunansu" hanya ce ta faɗar cewa suna yiwa Allah tawaye. AT: "waɗanda suka ƙi ku suna ƙin ku"
Anan "suna" yana wakiltar suna ko ƙwaƙwalwar wani. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "babu wanda zai taɓa tuna Isra'ilawa sun wanzu"
"makiyanku sun yarda tare da tsari daya"
Wannan shi ne sunan ƙungiyar mutanen da suke gabashin Kogin Yodan.
Duk waɗannan suna wakiltar mutanen kowane yanki ko kabila. AT: "mutanen Gebal da Ammon da Amalek da Filistiyawa"
Anan "Midiyawa" suna wakiltar mutanen Midiyan. AT: "aka yi wa Midiyawa"
Wannan yana nufin gawawwakin Sisera da Yabin ba a binne ba amma an bar su suna ruɓewa.
Wannan yana magana ne game da kasar Isra'ila kamar dai kasar ta tumaki ne da zasu yi kiwo kuma Allah ne makiyayin da ke lura da ita.
Duk maganganun biyu suna magana ne game da Allah yana halakar da magabtansa kamar yana iska mai ƙarfi da ke saurin kaɗa su.
Duk maganganun guda biyu suna rokon Allah ya ruguza makiya da hadari.
Anan "fuskoki" suna wakiltar mutum dukka. AT: "Ka sa su kunya sosai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ka sanya su kunya da firgita har abada"
Ana maganar Allah mai mulki akan komai na duniya kamar ana daukaka shi sama da komai. AT: "su ne maɗaukaki, kuma ku ke mulkin komai a duniya"
1Ina misalin ƙaunar wurin da kake zaune, Yahweh mai runduna!2Ina marmarin harabun Yahweh, marmarin da nake da shi dominsa yasa na suƙe. Zuciyata da dukkan kome nawa ya kira ga Allah mai rai.3Har tsaddu ta samar wa kanta gida mashillira ta yi wa kanta sheka inda zata ajiye 'ya'yanta kusa da bagadanka, Yahweh mai runduna, sarkina, Allahna kuma.4Masu albarkane waɗanda suka zauna cikin gidanka, zasu yita ci gaba da yabonka. Selah5Mai albarkane mutumin da ƙarfinsa yana cikinka, wanda zuciyarsa ke marmarin zuwa Sihiyona.6Cikin ratsawa zuwa kwarin Hawaye, sun iske maɓulɓulan ruwa domin sha. Ruwan farko ya rufe shi da albarku.7Suna tafiya daga karfi zuwa karfi; kowanne ɗayan su ya bayyana gaban Allah cikin Sihiyona.8Yahweh Allah mai runduna, kaji addu'ata; Allahn Yakubu, ka saurari abin da nake cewa! Selah9Ya Allah, ka duba garkuwarmu; ka nuna damuwarka ga shafaffenka.10Gama yini ɗaya cikin harabunka ya fi dubu a wani wuri. Na gwammace in zama mai tsaron ƙofa cikin gidan Allahna, da in zauna tsakanin rumfuna na masu mugunta.11Gama Yahweh Allah shi ne ranar mu da garkuwa;12Yahweh zai bada alheri da ɗaukaka; ba ya hana wani abu mai kyau ga waɗanda suke tafiya cikin gaskiya. Yahweh mai runduna, mai albarkane mutumin da ya ke dogara gare ka.
"Ina matukar son kasancewa a kotunan Yahweh"
"burina ya gaji da ni" ko "na gaji saboda ina son sa sosai"
Anan “zuciya” tana wakiltar mutum dukka. AT: "Ina kira da dukkan halina"
"inda zata sa ƙwai kuma ta kula da jariranta"
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) "su" suna nufin firistocin da suke aiki na dindindin a cikin haikalin ko 2) "su" suna nufin mutane gaba ɗaya waɗanda suka zo suka yi sujada a haikalin.
Haikalin yana cikin Yerusalem a saman dutsen da ake kira Dutsen Sihiyona.
Wannan yana nufin bushe, busassun wuri. Wasu juyi na Baibul suna da "Kwarin Baca." Kalmar "Baca" na nufin "kuka."
Ana maganar sarkin da yake kare mutanensa kamar shi garkuwa ne. AT: "Allah, ka lura da sarkinmu"
Ana iya bayyana wannan tare da bayanan da aka fahimta. AT: "Na fi so in kasance a kotunanku na kwana ɗaya da in kasance a wani wuri na tsawon kwanaki dubu"
Ana iya bayyana sunayen 'alheri' da 'ɗaukaka' azaman kalmomin aiki. AT: "Yahweh zai yi mana alheri kuma ya girmama mu"
Ana maganar yadda mutum yake gudanar da rayuwarsa ko kuma halinsa kamar mutum yana tafiya. AT: "waɗanda ke rayuwa da gaskiya" ko "masu gaskiya"
1Yahweh ka nuna wa ƙasarka tagomashi; ka dawo da lafiya da arzikin Yakubu.2Ka yafe zunubin mutanenka; ka rufe dukkan zunubinsu.3Ka janye dukkan fushinka; ka juya baya daga zafin fushinka.4Ka dawo damu, Allahn cetonmu, kasa rashin jindaɗinka tare da mu ya wuce.5Zaka yi ta fushi da mu har abada? Zaka yi ta yin fushi har ga tsararraki masu zuwa?6Ba zaka sake falkar damu ba? Daga nan mutanenka za suyi murna a cikin ka.7Ka nuna ma na amincin alƙawarinka ya Yahweh, ka bamu cetonka.8Zan saurari abin da Yahweh Allah zai ce, gama zai kawo salama ga mutanensa, amintattun mabiyansa. duk da haka ba zasu koma ga bin hanyoyinsu na wauta ba.9Hakika cetonsa yana kusa da masu tsoronsa; daga nan ɗaukaka zata zauna cikin ƙasarmu.10Alƙawarin aminci da gaskiya sun haɗu tare; adalci da salama sun yi wa juna sumba.11Gaskiya tana tsirowa daga ƙasa, adalci yana kallo daga sama.12I, Yahweh zai ba da albarku masu kyau, ƙasarmu zata bada amfaninta.13Adalci zai tafi gabansa kuma zai yi hanya domin sawayensa.
Anan “ƙasa” tana wakiltar ƙasar da kuma mutanen Isra’ila.
Anan ana maganar zunubin da aka gafarta kamar wanda aka lulluɓe shi don kada a gani. AT: "da gangan kuka manta zunubinsu"
Ba a sake magana game da azabtar da Isra'ilawa kamar Israila abu ne da Yahweh zai iya ɗauka daga Isra'ilawa.
Allah baya yin fushi da Isra'ilawa ana maganarsa kamar fushi wuta ne wanda Allah ya juya baya daga gare shi.
Neman Allah ya daina yin fushi da Isra'ilawa ana magana ne kamar rashin jin daɗi wani abu ne da marubucin yake so Allah ya bar shi.
Marubucin yayi amfani da wata tambaya don jaddada buƙatarsa ga Allah ya sa mutanen Isra’ila su sami ci gaba kuma su sake farin ciki. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Da fatan za mu sake samun ci gaba."
Wannan shine yadda marubucin yake son Allah ya nuna amincin sa ga mutanen sa. Idan aka sake tsara jumla, ra'ayoyin da ke cikin sunan "ceto" za'a iya bayyana su da kalmar aikatau. AT: "kuma ka cece mu" ko "ta hanyar ceton mu" (Duba: da abstractnouns)
"zama da dangantaka ta lumana da mutanensa" ko "kawo zaman lafiya ga mutanensa"
Ana magana da mutumin da ke canza yadda yake nuna halinsa kamar yana juyawa zuwa wata hanyar daban. AT: "Duk da haka ba za su sake fara aikata abubuwan wauta ba"
A nan “ɗaukaka” tana wakiltar bayyanuwar Allah. AT: "to kuwa kasancewar sa mai ɗaukaka zai kasance a ƙasarmu"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) mutane za su yi abin da ke daidai kuma Allah zai sa mutane su zauna lafiya ko 2) Allah zai yi abin da yake daidai kuma zai sa mutane su zauna lafiya. Ko ta yaya adalci da salama sunaye ne na gama gari kuma ana maganarsu kamar mutane ne da ke sumbatar juna.
Mutanen da ke duniya masu aminci ga Allah ana magana akan su kamar amintaccen tsiro ne da ke tsirowa daga ƙasa. Cikakken sunan "amintacce" ana iya bayyana shi a matsayin "mai aminci." AT: "A nan duniya, za mu kasance masu aminci ga Allah"
Kalmar "adalci" baƙon abu ne, kuma ana magana akan shi kamar mutum yana kallon ƙasa kamar yadda Allah yake yi. AT: "Allah zai dube mu daga sama kuma zai yi mana adalci"
Ana yin Allah yana yin abin da yake daidai a duk inda ya tafi ana magana ne kamar dai adalci na mutum ne wanda ke gaba da Allah kuma yana shirya wa Allah hanya don tafiya.
1Ka saurara, Yahweh, ka kuma amsa mani, domin ni matalauci ne, wanda aka tsanantawa.2Ka kare ni domin ina biyayya, ya Allahna, ka ceci bawanka wanda ya ke dogara a gare ka.3Ka yi mani jinƙai, ya Ubangiji, don a gare ka nake kuka dukkan yini.4Kasa bawanka yayi murna domin a gare ka nayi addu'a ya Ubangiji.5Ubangiji, kai nagari ne, kuma kana shirye kayi gafara. Kana kuma nuna jinƙai ga duk waɗanda suka yi kuka gare ka.6Yahweh, ka ji addu'ata, ka kuma ji muryar roƙona.7A ranar masifata nayi kira gare ka, domin zaka amsa mani.8Ya Ubangiji ba wanda za a kwatanta shi da kai a cikin alloli, ba ayyukan da za a kwatanta su da naka.9Dukkan al, umman da kayi zasu zo su rusuna maka. Za su girmama sunanka.10Domin kana da girma kana kuma yin abubuwan al'ajabi, kai kaɗai ne Allah.11Ka koya mani tafarkinka Yahweh. Sa'an nan zan yi tafiya cikin gaskiyarka. Ka haɗa zuciyata ta girmamaka.12Ubangiji Allahna zan yabe ka da dukkan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.13Domin alƙawarinka mai aminci yana da girma a gare ni, domin ka ceto raina daga zurfafan Lahira.14Ya Allah marasa hankali sun tasar mani. Ƙungiyar masu husuma sun tasar mani suna neman raina, ba su kula da kai ba.15Amma kai, Ubangiji, Allah ne mai jinƙai da alheri, mai jinkirin fushi, mai mayalwacin alƙawari mai aminci da kuma madogara.16Ka juyo wurina kayi mani jinƙai; ka bada ƙarfinka ga bawanka; ka ceci ɗan baiwarka.17Ka nuna mani alamar jinƙanka. Sa'an nan waɗanda ke ƙi na zasu gani su kunyata saboda kai, Yahweh, ka taimake ni ka kuma ta'azantar dani.
"rauni da matalauta"
Dauda ya kira kansa "bawanka," wato bawan Allah. AT: "Ka sanya ni, bawanka" ko "Ka sanya ni"
"A lokacinda nake cikin wahala"
Anan “suna” yana wakiltar mutum dukka. AT: "Za su girmama ku"
Mutumin da yake yin biyayya ga abin da Allah yake so, ana maganarsa kamar yana tafiya a kan hanyar Allah ko kuma hanyar sa. AT: "Ka koya mani gaskiyar ka, ya Yahweh. To zan yi biyayya da abin da ka fada"
Anan “zuciya” tana wakiltar tunanin mutum, motsin rai, da kuma muradin mutum. Ana roƙon Allah ya sa mutum ya girmama shi kwata-kwata ana magana ne kamar zuciyar zuciyar ta kasance a dunƙule da yawa kuma Allah yana haɗa su tare. AT: "Ka sa in girmama ka da gaske da dukkan zuciyata" ko "Ka sa in girmama ka da gaske"
Anan “zuciya” tana wakiltar tunanin mutum, motsin rai, da kuma muradin mutum. AT: "Zan yabe ku gaba ɗaya kuma da gaske"
Wannan baya nufin Allah ya tashe shi bayan ya mutu. Yana nufin Allah ya cece shi lokacin da yake gab da mutuwa.
"suna taruwa don cutar da ni"
Neman Allah ya ɗauke shi magana yake kamar yana son Allah ya juyo ya dube shi.
AT: "ƙarfafa bawanka" ko "ƙarfafa bawanka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "za su ji kunya"
1Akan dutse mai tsarki birninsa da ya samo ya tsaya;2Yahweh yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da rumfuna na Yakubu.3An faɗi maɗaukakan abubuwa game da kai birnin Allah. Selah.4Na ambaci Rahab da Babila ga masu bi na. Duba, akwai Filistiya, da Taya, tare da Itofiya- kuma zasu ce, 'Wannan an haife shi a can.'"5Ga Sihiyona za'a ce, "Dukkan wɗannan an haife su a cikinta, kuma Mafi Girma dukka da kansa zai kafa ta."6Yahweh ya rubuta a cikin littafin ƙidaya na al'ummai, "Wannan an haife shi a can." Selah7Haka kuma mawaƙa da masu rawa suka faɗa tare, "Dukkan maɓulɓulaina suna cikinka."
Mutanen sun zauna cikin tanti yayin da suke yawo a cikin hamada. Anan marubucin yayi amfani da "tanti na Yaƙub" don wakiltar inda Isra'ilawa suke zaune yanzu. AT: "kowane ɗayan wuraren zama na Isra'ilawa"
Marubucin yana magana da birnin Kudus kamar yana sauraron sa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ku mutane a Yerusalem, wasu mutane suna faɗin abubuwan ban mamaki game da garinku"
Anan "Rahab" hanya ce ta waƙa ta nufin Masar. Dukkansu "Rahab" da "Babila" suna wakiltar mutane. AT: "mutanen Masar da Babila"
"zuwa ga waɗanda suke bauta mini"
Ana magana akan mutane daga wasu al'umman da ke bautar Yahweh kamar suna haifaffen Yerusalem. AT: "Kamar dai duk waɗannan mutanen an haife su ne a Yerusalem"
"zai sa Yerusalem ta zama mai ƙarfi"
Yahweh yana sane da cewa mutane daga wasu al'ummai suna cikin nasa ana maganarsa kamar sarki ne wanda yake rubuta sunayen mutanen da ke zaune a garin sa.
Ana magana akan Yerusalem inda mutane suke karɓar duk albarkun su ana magana kamar Yerusalem maɓuɓɓugar ruwa ce da ke ba mutane ruwa.
1Yahweh, Allah na cetona, Na yi kuka a gabanka dare da rana.2Ka ji addu'ata, ka saurari kukana.3Domin na cika da damuwoyi, raina kuma ya kai Lahira.4Mutane sun ɗauke ni kamar waɗanda suka faɗa rami; Mutumin da ba shi da ƙarfi.5An yi watsi da ni a cikin matattu; Ina kama da matacce dake kwance a kabari, game da wanda ka daina kula da shi saboda an datse su daga ikonka.6Ka ajiye ni a wuri mafi ƙasƙanci na cikin rami, a wuri mai zurfi da kuma duhu.7Fushinka yayi nauyi a kaina, kuma dukkan rigyawarka tabi ta kaina. Selah8Saboda kai, abokan tarayyata suka yashe ni. Ka maishe ni abin rawar jiki a gare su. An shinge ni a ciki ba kuma zan tsira ba.9Idanuna sun gaji da damuwa; Dukkan yini ina kira gare ka, Yahweh; na buɗe hannuwana gare ka.10Ko zaka yi mu'ujuzai ga matattu? Ko waɗanda suka mutu zasu tashi su yabe ka? Selah11Ko za'a yi shelar alƙawarin amincinka a kabari, amincinka kuma a wurin matattu?12Ko za'a san ayyukanka na al'ajibai a cikin duhu, ko kuma adalcinka a wurare na mantuwa?13Amma nayi kuka gare ka, Yahweh; da safe addu'ata tana zuwa gare ka.14Yahweh me yasa ka ƙi ni? Me yasa ka ɓoye fuskarka daga gare ni?15Har kullum an tsananta mani kamar a hallaka ni tun daga ƙuruciyata. Na sha hukuncin horonka ina cikin fargaba.16Ayyukanka na fushi sun bi ta kaina, kuma ayyukanka masu ban razana sun kawar da ni.17Sun kewaye ni kamar ruwa a dukkan yini; dukkan su sun kewaye ni.18Ka kawar da abokaina da duk waɗanda suka shaƙu dani daga gare ni. Wanda ya shaƙu dani duhu ne kaɗai.
Cikakken sunan "ceto" za'a iya bayyana shi azaman kalma. AT: "kai ne wanda ya cece ni"
Marubucin yayi amfani da waɗannan kalmomin tare da ma'anoni masu ma'ana don cewa yana ci gaba da kuka.
Marubucin yayi magana kansa kamar yana akwati kuma matsaloli sune abubuwan da ke cike akwatin. AT: "Gama na damu ƙwarai"
Anan “rayuwa” tana wakiltar marubuci. Kuma “Lahira” yana wakiltar mutuwa. Marubucin yayi magana game da kansa mai yiwuwa ya mutu nan da nan kamar Lahira yana wuri kuma ya isa wurin. AT: "Na kusan mutuwa"
Mutanen da ke ɗaukar marubuci kamar ya riga ya mutu ana magana da su kamar dai gawa ce da suka bari ba a binne ta ba. AT: "An bar ni ni kaɗai kamar na mutu"
Marubucin yana jin kamar mutane kuma Allah ya yashe shi yana magana ne game da kansa kamar ya riga ya mutu ne yana kwance a kabari.
Marubucin yana jin kamar Allah ya rabu da shi yana magana ne game da kansa kamar Allah ne ya sanya shi a cikin zurfin da duhu mafi duhu.
Wannan yana magana ne game da fushin Allah ƙwarai da marubucin kamar dai fushin Allah abu ne mai nauyi wanda yake kwance akan marubucin. AT: "Ina jin fushinku mai girma" ko "Ina jin irin fushin da kuke yi da ni"
"Kun sanya ni abin ƙyama a wurinsu" ko "Saboda ku, suna kaduwa lokacin da suka gan ni"
Ana magana game da yanayin marubucin wanda ya sa ya zama abin ƙyama ga abokansa kamar ana cikin rufewa a cikin wani sarari. AT: "Kamar dai ina cikin kurkuku ne" ko "Ina cikin tarko"
Anan “idanu” suna wakiltar ikon mutum na gani. Gama idanunsa sun gaji da damuwa daga matsala wata hanya ce ta cewa shi damuwar sa ta sa shi kuka sosai wanda da wuya ya iya gani.
Marubucin ya yi amfani da wata tambaya don ya nanata cewa idan Allah ya bar shi ya mutu to Allah ba zai iya sake yi masa abubuwan al'ajabi ba. AT: "Ba kwa yin abubuwan al'ajabi ga mutanen da suka mutu."
Marubucin yayi amfani da wata tambaya domin ya nanata cewa idan Allah ya barshi ya mutu to ba zai iya kara godewa Allah ba. AT: "Ka sani cewa waɗanda suka mutu ba za su tashi tsaye su yaba maka ba."
Duk tambayoyin guda biyu suke. Marubucin yayi amfani da tambayoyi don ya nanata cewa waɗanda suka mutu ba za su iya dandana ko shelar manyan abubuwan da Allah yake yi ba. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane ba za su yi magana game da ayyukanku masu ban al'ajabi da adalcinku a cikin duhun mataccen da aka manta da shi ba."
Ana iya fassara wannan azaman jumla daban. AT: "Shin za a san adalcinku a wurin mantuwa?" ko "Waɗanda suke wurin mantawa ba za su san abubuwan kirki da kuke aikatawa ba."
Ana maganar marubucin da ke addu’a ga Yahweh kamar addu’ar da kanta za ta yi magana da Yahweh.
Wannan karin gishirin yana magana ne game da yadda Allah yake azabtar da marubuci kamar dai Allah ya halaka marubucin kwata-kwata. AT: "abubuwan ban tsoro da kuka aikata sun hallaka ni" ko "abubuwan ban tsoro da kuke aikatawa sun kusan hallaka ni"
Marubucin ya kamanta “ayyukan fushin” Allah da “ayyukan ban tsoro” da ambaliyar ruwa. AT: "Duk tsawon yini suna barazanar hallaka ni kamar ambaliya"
Marubucin yayi magana game da "ayyukan fushin Allah" da "ayyukan ban tsoro" kamar dai abokan gaba ne waɗanda ke ƙoƙarin kama shi su kashe shi. AT: "sun kewaye ni kamar sojojin abokan gaba"
Wannan yana magana ne game da duhu kamar dai mutum ne wanda zai iya abokantaka da wani. Marubucin yana jaddada cewa yana jin shi kaɗai. AT: "Duk inda na je sai duhu ne"
1Zan raira yabon ayyukan alƙawarin amincin Yahweh na har abada, Zan yi shelar gaskiyarka ga tsararraki masu zuwa.2Domin na ce "Anyi amintaccen alƙawari na har abada; ka kuma kafa gaskiyarka a cikin sammai."3Na yi alƙawari da zaɓaɓɓena, nayi alƙawari ga Dauda bawana.4Zan kafa zuriyarka har abada, kuma zan kafa kursiyinka a dukkan tsararraki." Selah5Sammai na yabon al'ajibanka, Yahweh; a na yabon gaskiyarka a taron tsarkaka.6Domin da wane ne za a kwatanta shi da Yahweh a sammai? Wane ne za a kwatanta shi da Yahweh?7Shi Allah ne dake da girmamawa a taron tsarkaka yana kuma da kwarjini ga dukkan waɗanda suka kewaye shi.8Yahweh Allah mai runduna, wa keda ƙarfi kamar ka? amincinka ya kewaye ka.9Kana mulkin haukan teku; lokacin da ambaliyoyi su ka tashi ka kwantar da su.10Ka buge Rahab kamar wadda aka kashe. Ka warwatsa maƙiyanka da ƙarfin damtsenka.11Sammai naka ne, haka kuma duniya. Ka hallici duniya da dukkan abin da ke cikin ta.12Ka hallici arewa da kudu. Tabor da Harmon na murna a cikin sunanka.13Kana da damtse mai iko da kuma hannu mai ƙarfi, hannunka na dama kuma yana da tsayi.14Aikin adalci da adalci su ne ginshiƙan mulkinka. Alƙawari mai aminci da kuma dogara daga gare ka suke zuwa.15Masu albarka ne waɗanda ke yi maka sujada! Yahweh, suna tafiya a cikin hasken fuskarka,16Suna murna da sunanka dukkan yini. Ayyukan adalcinka kuma sun ɗaukaka ka.17Kai ne ƙarfin ikonsu, ta wurin jinƙanka kuma mun yi nasara.18Domin garkuwoyinmu na Yahweh ne; sarkinmu kuma na Mai tsarki na Isra'ila ne.19Tun da daɗewa kayi magana da tsarkakanka ta wurin wahayi; kace "Na sa kambi bisa mai iko; Na tayar da wani da aka zaɓa daga cikin mutane.20Na zaɓi Dauda bawana, da maina na keɓe shi.21Hannuna zai taimake shi. Damtsena kuma zai ƙarfafa shi.22Ba maƙiyin da zai yaudare shi; ba kuma ɗan magabcin da zai ƙuntata masa.23Zan buge maƙiyansa a gabansa, masu ƙin sa kuma zan hallaka su.24Gaskiyata da alƙawarin amincina zai kasance tare da shi, ta wurin sunana zai yi nasara.25Zan ɗora hannunsa a kan teku, hannunsa na dama kuma bisa koguna.26Zai yi kira gare ni yace kai ne ubana, 'Kai ne Ubana kuma Allahna, da kuma dutsen cetona.'27Zan ɗora shi a matsayin ɗan farina, mafi ɗaukaka a cikin sarakunan duniya.28Zan tsawaita alƙawarin amincina a gare shi har abada; zan kuma riƙe alƙawarina da shi.29Zan kafa zuriyarsa har abada, mulkinsa kuma zai kai har sammai.30Idan 'ya'yansa suka yi watsi da shari'una suka kuma yi rashin biyayya ga sharuɗɗana,31idan kuma sun karya dokokina basu kuma kiyaye umarnaina ba,32to sai in hori rashin biyayyarsu da sandar ƙarfe laifofinsu kuma da nushe-nushe.33Amma ba zan janye madawammiyar ƙaunata ba daga gare shi ko kuma in yi rashin aminci a kan alƙawarina ba,34Ba zan karya alƙawarina ba ko kuma in canza maganganun leɓuna na ba.35Sau ɗaya tak na rantse da tsarkina-Ba zan yiwa Dauda ƙarya ba:36zuriyarsa zata ɗore har abada mulkinsa kuma zai zama kamar rana a gabana.37Za a kafa shi har abada kamar wata, amintaccen mashaidi a sararin sama." Selah38Amma ka ƙi ka kuma yi watsi; kana kuma fushi da shafaffen sarki.39Ka kuma musunta alƙawarin bawanka. Ka ƙazamtar da rawaninsa a ƙasa.40Ka kuma rushe katangunsa dukka. Ka kuma mayar da ƙarfafan kagarunsa kufai.41Duk masu wucewa suka yi masa ƙwace. Ya zama abin ƙyama a cikin maƙwabta.42Ka tayar da hannun damar maƙiyansa; ka kuma sa dukkan maƙiyansa suyi farinciki.43Ka juya takobinsa ka kuma hana shi ya tsaya a lokacin yaƙi.44Ka kawo ƙarshen martabarsa; ka kuma karya mulkinsa45Ka gajarta kwanakin ƙuruciyarsa. Ka kuma rufe shi da kunya. Selah46Yahweh har yaushe? Ko zaka ɓoye kanka, har abada? Har yaushe zaka bar fushinka yayi ta ƙuna kamar wuta?47Oh, ka yi tunanin yadda gajartar lokacina ya ke, da kuma rashin amfanin yadda ka hallici dukkan mutane!48Wane ne zai rayu ba zai mutu ba, ko kuma ya iya kuɓutar da ransa daga Lahira? Selah49Ya Ubangiji, ina ayyukanka na dã a kan alƙawarin amincinka da ka rantsewa Dauda a cikin gaskiyarka?50Ka tuna ya Ubangiji da rainin da aka yi wa bayinka da kuma yadda na ji a zuciyata ire-iren cin mutunci daga al'ummai.51Maƙiyanka suna nuna wulaƙanci, Yahweh; suna wulaƙanta sawayen keɓaɓɓenka.52Albarka ta tabbata ga Yahweh har abada. Amin da Amin. Littafi na Huɗu
Allah yana yin abin da ya alkawarta koyaushe ana maganarsa kamar amincinsa gini ne da Allah ya gina kuma ya tabbatar dashi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Za ku kasance da aminci koyaushe saboda alkawarin da kuka yi da mu"
Allah yana yin abin da ya alkawarta koyaushe ana maganarsa kamar amincinsa gini ne da Allah ya gina kuma ya tabbatar dashi.
Mai yiwuwa ma'anoni sune 1) wannan yana nufin mazaunin Allah. Wannan yana nufin Allah yana mulki daga sama kuma koyaushe yana yin abin da yayi alƙawari ko 2) wannan yana nufin sama. Wannan yana nufin cewa alkawuran Allah tabbatattu ne kamar sararin sama.
Kuna iya bayyane cewa "zaɓaɓɓen" yana nufin Dauda. AT: "Na yi wa Dauda alkawari, wanda na zaɓa"
Ana magana akan Yahweh koyaushe ɗayan zuriyar Dauda ya zama sarki kamar zuriya Dauda sune gini da Yahweh zai gina kuma ya tabbatar dashi.
"yabonka, ya Yahweh, saboda kyawawan al'amuran da kake aikatawa"
Wannan yana nufin mala'iku a sama.
Duk tambayoyin guda biyu suke. Marubucin yana amfani da tambaya don nanata cewa babu wani a sama kamar Yahweh.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Majalisar tsarkaka tana girmama Allah ƙwarai"
Marubucin yayi tambayar don ya jaddada babu mai ƙarfi kamar Yahweh.
Yahweh koyaushe baya yin abin da yayi alƙawarin yi ana maganarsa kamar gaskiyarsa mayafi ce ko sutura da ke kewaye da shi.
"Kai ne ke kula da teku mai haushi"
Kalmar "Rahab" anan tana nufin dodo ne na teku.
Marubucin yayi amfani da kalmomin "arewa" da "kudu" tare don ma'anar cewa Allah ya halicci komai a ko'ina. (Duba: fig_merism)
Tabor dutse ne da ke kudu maso yammacin Tekun Galili kuma Hermon dutse ne da ke arewa maso gabashin Tekun Galili. Marubucin ya bayyana waɗannan duwatsu kamar mutane ne da zasu iya yin farin ciki. AT: "Kamar dai Tsaunin Tabor da Tsaunin Hermon suna murna da sunanka"
Kalmomin “ƙarfin hannu,” “hannu mai ƙarfi,” da “hannun dama” duk suna wakiltar ikon Allah.
Allah yana mulki kamar sarki kuma yana aikata abin da ke daidai da adalci ana maganarsa kamar kursiyin Allah gini ne, kuma adalci da gaskiya sune tushenta.
Allah yana kasancewa mai aminci koyaushe kuma yana aikata abin da yayi alƙawarin aikatawa ana maganarsa kamar amintaccen alkawari da aminci sun zo saduwa da Allah. Ana iya fassara sunayen mara amfani azaman sifofi. AT: "Kullum kuna da aminci ga alƙawarinku kuma kun cancanci mutane su amince da ku"
Marubucin yayi magana game da Yahweh yana nuna musu alheri kamar fuskar Yahweh ta haskaka musu. AT: "da sanin cewa kuna yi musu alheri"
Anan “suna” yana wakiltar mutumin. AT: "a cikin ku"
Cikakken sunan "adalci" za'a iya bayyana shi azaman sifa ne. AT: "Suna daukaka ku saboda koyaushe kuna yin abin da ke daidai"
Cikakken sunan "ƙarfi" za a iya bayyana shi azaman sifa ne. AT: "Kuna sanya su ƙarfi masu ban mamaki"
Anan "mu" yana nufin marubuci da Isra'ilawa amma ba ga Yahweh ba, wanda yake magana da shi.
Ana magana da sarkin da ke kāre mutanensa kuma wanda Yahweh ya zaɓa kamar garkuwa ce ta Yahweh.
Sanya kambi a kan mutum alama ce ta sanya shi sarki. AT: "Na yi ƙaƙƙarfan sarki sarki"
Anan "ɗaga" yana nufin naɗa. Ana nuna cewa Allah ya zaɓi wannan mutumin ya zama sarki. AT: "Na zaɓi ɗaya daga cikin mutane ya zama sarki"
A nan zuba mai a kan mutum alama ce ta cewa Allah yana naɗa mutumin ya zama sarki. (Duba:
Anan “hannu” da “hannu” dukka suna nufin ƙarfi da ikon Yahweh. AT: "Zan tallafa masa kuma in ƙarfafa shi"
Anan "suna" yana wakiltar ikon Allah. AT: "Ni, Allah, zan sa shi ya zama mai nasara"
Anan "hannu" da "hannun dama" suna wakiltar ƙarfi da iko. A nan “teku” kamar tana nufin Tekun Bahar Rum da ke yamma da Isra’ila, kuma “koguna” suna nufin Kogin Yufiretis a gabas. Wannan yana nufin Dauda zai mallaki komai tun daga teku har zuwa kogin. AT: "Zan ba shi iko a kan komai tun daga Tekun Bahar zuwa Kogin Yufiretis"
Wannan yana da zance a cikin ambato. Ana iya bayyana shi azaman zance na kai tsaye. AT: "Zai ce ni Ubansa ne, Allahnsa, da dutsen cetonsa." (Duba: da rquestion)
An yi magana da Yahweh don ba Dauda matsayi na musamman da fifiko a kan sauran mutane kamar Dauda zai zama ɗan farin Yahweh.
Wani daga dangin Dawud yana mulki koyaushe ana maganarsa kamar kursiyinsa zai dawwama muddin sama zai dawwama.
An yi maganar Allah mai hukunta zuriyar Dauda kamar zai buge su da sanda. Cikakken sunan "tawaye" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "azabtar da su saboda tawaye da ni"
Ana magana game da azabtar da zuriyar Dauda kamar Allah zai buge su a zahiri. Ana iya bayyana wannan azaman cikakkiyar jimla. AT: "Zan hukunta su saboda sun yi min laifi"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Zan kasance ina son David koyaushe, kuma zan yi abin da na yi masa alkawari"
An fahimci kalmomin "za su ci gaba". Madadin fassara: "kursiyinsa zai ci gaba muddin rana ta gabana"
Allah ya misalta mulkin Dauda a matsayin sarki da rana don ya nuna cewa wani daga zuriyar Dauda zai yi sarauta koyaushe.
Allah ya kwatanta mulkin Dauda a matsayin sarki ga wata don ya nanata cewa wani daga zuriyar Dauda zai yi sarauta koyaushe.
Kalmomin "sarki" an fahimta. AT: "kun ƙi kuma kun ƙi sarki"
"Kun ƙi alkawarin"
Wannan yana nuna cewa Allah ya yale maƙiya su halakar da kariya a Yerusalem. AT: "Kun bar abokan gaba su ruguza ganuwar sa kuma su lalata kagararsa a Yerusalem"
Anan "hannun dama" yana wakiltar iko. “don daga hannun dama” yana nufin cewa Yahweh ya ba magabtansa ƙarfi su kayar da zaɓaɓɓen sarkin Allah.
Anan “takobi” yana wakiltar ikon sarki a yaƙi. Mayar da takobi baya yana sa sarki ya kasa yin nasara a yaƙi.
Anan "tsayawa" yana wakiltar kasancewa mai nasara a yaƙi. AT: "Ba ku taimaka masa ya ci nasara a yaƙi ba"
Anan “kursiyi” yana wakiltar ikon yin sarauta kamar sarki. AT: "kai, Yahweh, kun ƙare mulkinsa a matsayin sarki"
Wannan hanya ce ta faɗar cewa Allah ya sanya sarki yayi kamar tsoho duk da yana saurayi. AT: "Duk da cewa yana saurayi kun sanya shi rauni kamar dattijo"
Cikakken sunan "rashin amfani" ana iya bayyana shi a matsayin "mara amfani." AT: "da ka halicci dukkan mutane don su mutu ba tare da amfani ba"
Marubucin yayi amfani da waɗannan tambayoyin don jaddada cewa duk mutane zasu mutu. AT: "Ba wanda zai iya rayuwa har abada ko ya dawo da kansa bayan ya mutu"
Anan "hannu" yana nufin iko. Marubucin yayi maganar Lahira kamar mutum ne wanda yake da iko akan waɗanda suka mutu. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) mutum ba zai iya dawo da kansa cikin rai ba bayan ya mutu ko 2) mutum ba zai iya kiyaye kansa daga mutuwa ba.
Anan "bayinka" na nufin mutanen Isra'ila. AT: "yadda suke yi mana ba'a, bayinku"
Anan “zuciya” tana wakiltar motsin mutum. AT: "Na jimre zagi da yawa daga mutanen al'ummomi" ko "Na wahala saboda mutane daga al'ummomi suna zagina"
Maganganu suna ihu da zagi ga sarki ana maganarsu kamar zagi wani abu ne da makiya suka jefawa sarki da karfi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT "Bari mutane su yabi Yahweh har abada"
1Ubangiji kai ne mafakarmu a dukkan tsararraki.2Kafin a kafa duwatsu, ko kuma ka hallici duniya da abin dake cikinta, har abada abadin, kai Allah ne.3Ka kan komar da mutum ƙura, ka ce "ku koma ku zuriyar ɗan adam."4Domin shekaru dubu a gare ka kamar jiya ne data wuce, kamar kuma sa'ar tsaro ce ta dare.5Ka share su kamar da rigyawa sun kuma yi barci; da safe suna kama da ciyayi da suka yi girma.6Da safe sukan yi yabanya suyi girma; da yamma kuma su kan yanƙwane su bushe.7Hakika, an cinye mu a cikin fushinka, a cikin fushinka kuma mun gigice.8Ka jejjera zunubanmu a gabanka, laifofinmu na ɓoye kuma kasa su a hasken gabanka.9Ran mu yana shuɗewa a ƙarƙashin fushinka;10shekarunmu kuma sun wuce da sauri kamar ajiyar zuciya. Shekarunmu saba'in ne, ko kuma tamanin in muna da lafiya; amma koma da shekarunmu mafiya kyau suna cike da damuwa da baƙinciki. Hakika, sukan wuce da sauri sai kuma mu ɓace.11Wa ya san ƙarfin fushinka, da kuma fushinka da ke dai-dai da tsoronka?12ka koya mana yadda zamu yi la'akari da rayuwarmu domin mu yi rayuwa cikin hikima.13Juya, Yahweh! Har yaushe zai zama? Ka ji tausayin bayinka.14Ka ƙosar da mu da alƙawarin amincinka da safe domin muyi farinciki a cikin dukkan kwanakinmu.15Ka samu muyi murna gwargwadon kwanakin daka azabtar damu da kuma shekarun da muka fuskanci matsala.16Ka bar bayinka suga aikinka, kuma ka bar 'ya'yanmu suga darajarka.17Da ma jinƙan Ubangiji Allahnmu ya zama namu; ka wadata aikin hannuwanmu; hakika, ka wadata aikin hannuwanmu.
Ana yawan samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
"Wannan shine addu'a da Musa ya rubuto"... Allah yana kare mutanensa faɗaɗɗece ne sai ka ce Allah shine dama mafaka ko rumfa. AT: "Ubangiji kai ne kamar mafakar gare mu"
Wannan za a iya bayanata cikin kafa aiki. AT: "Kafin ka kafa duwatsu"
Wannan na wakiltar dukan abubuwan da ke a duniya.
Wannan na nufi cewa daidai kamar da mutum na fari, Adamu, daga kasa, Allah zai sa jikuna mutane su juya baya zuwa cikin kasa bayn da sun mutu. AT: "Ka kan komar da mutane ƙura sa'adda suka utu" .
Wannan shine hanyar ce da ta taɓi 'yan adam dukka. AT: "ku 'yan adam" ko "ku mutane"
Marubuci yana nufi cewa tsawo ƙayadadden lokacin a gani kamar kajeruwan ƙayadadden lokaci ne ga Allah. AT: "Ka duba shekaru dubu daidai ne da gwana guda da ta wuce, ko kamar 'yan kaddan sa'a cikin dare" ko "Daidai yawan shekaru dubu ba shi da tsawo lokaci gare ka"
A nan "gani" na wakiltar tunani ko ra'ayi. AT: "ga kai"
Allah yana sa mutane su mutu ba zato ba tsammani faɗaɗɗe sai ka ce ya share su daga nan da tsintsiya. Wannan sharewa an kuma faɗa sai kace ita ce ambaliya da ta ɗauko mutane daga nan. AT: "Ubangiji, ka hallaƙar da mutane kamar da ambaliya kuma sun mutu"
Mutanen an kwatanta su da ciyayi domin a jaddada cewa mutane ba su yin rayuwa tsawon lokaci sosai. ... Dukkan waddan nan magana na nufi ta yaya ciyayi ta ke girma. AT: "ta kan fara da girma kuma ta ci gaba" ... Dukkan waddan nan magana na nufi ta yaya ciyayi ta ke mutuwa. AT: "ta kan yi yaushi ta bushe"
Allah cikin fushinsa na hallaƙawa mutane faɗaɗɗece sai ka ce fushin Allah wutane wanda ke ƙona mutane gaba daya. Wannan na iya bayana ta a cikin fom aiki. AT: "Ka hallaƙa mu cikin fushinka" ... "kuma sa'adda ka ke fushi muna cike da tsoro ƙwarai"
Allah na la'akari da zunuban mutane faɗaɗɗece sai ka ce zunuban kamar abu ne da zai iya ajiye a gabansa da kansa kuma ya dubi su. AT: "Ka Gani dukkan al'amarin mai zunubi da muka yi, ko da al'amaren zunubi da muka yi a ɓoye"
Kalman nan "saboda" iya zama da amfani domin a bayyana cewa fushin Allah na haddasawa rayuwan mutum ga ƙarshe. AT: "Rayuwan mu ta kan zo ne ga ƙarshe saboda fushinka" ... Marubuci ya kwantanta rayuwa mutum da ajiyar zuciya domin ya jaddada cewa rayuwa gajerewa ce sosai.
Wannan ana iya bayyana ta a cikin fom aiki. AT: "Koda cikin shekarunmu mafiya kyau mun kware da damuwa da baƙinciki" ... Wannan hanyar ce mai ladabi na mai da yanda mutane na mutuwa. AT: "mun mutu"
Marubuci ya yi amfani da tembaya da ya jaddada cewa ba wanda yana da cikake sani fushin Allah. Saboda haka ba wanda da gaske na girmama Allah kuma na ji tsoron fushinsa sa'adda mutane sun yi zunubi. AT: "Ba wanda ya san tsamani fushinka. Saboda haka ba wanda ya ke tsoron fushinka sa'adda sun yi zunubi."
Rokon Yahweh don kada ya ci gaba da fushi faɗaɗɗe ce sai ka ce marubuci ya na son Allah ya juya irin ta jiki daga nan daga fushinsa. AT: "Yahweh, in ka yarda kada ka kara jin fushi kuma"
A nan "bayinka" yana nufi mutane Isra'ila. AT: "Yi mana jinkai, mu bayinka"
Suna mai zuzzu'rfar ma'ana "amincin" ana iya bayyanata kamar siffa. AT: "da kasancewa aminci saboda alƙawarinka da mu"
Dukkan wadda nan magana su na nufi abu daya. Marubuci yana rokon Yahweh domin ya sa su murna bisa ga yawan lokaci da ya hora su. AT: "Daidai jimila lokaci da ka azabtar damu kuma ka yi shan wahalanmu"
A nan "bayinka" na nufi mutane Isra'ila. AT: Bar mu, bayinka" ko "Bar mu" ... Anan "'ya'yan" na nufi 'ya'yan da zuriyar ... Wannan suna mai zuzzu'rfar ma'ana "zati" ana iya bayyana ta kamar "abubuwa masu girma." AT: "Gani abubuwa masu girma da ka yi"
Wannan suna mai zuzzu'rfar ma'ana "jinƙa" ana iya bayyana ta kamar "yin kirki." AT: Da ma Ubangiji Allahnmu ya yi mana kirki"
A nan "hannayen" na wakiltar dukkan mutum. AT: "ka sa mu mu zama da nasara" .
1Wanda ya ke rayuwa a bukkar Mafi Ɗaukaka zai zauna a inuwar Mai Iko Dukka.2Zan ce da Yahweh, "Shi ne mafakata da kagarata, Allahna, wanda na dogara a gare shi."3Domin zai kuɓutar da kai daga wayon tarkon maharbi kuma daga annoba mai hallakarwa.4Zai rufe ka da fukafukansa, kuma a ƙarƙashin fukafukansa zaka sami mafaka. Madogararsa garkuwa ce da kuma kariya.5Ba za ka ji tsoron masifa ba da dare, ko kuma kibiyoyin dake shawagi da rana.6Ko kuma annobar dake aukowa da dare ba.7Ko cutar dake samuwa da tsakar rana ba. Dubu zasu faɗi a gefenka dubu goma kuma a hannunka na dama, amma ba zasu iso wurinka ba.8Zaka duba ne kawai kaga hukuncin da za'a yiwa miyagu,9Domin Yahweh ne mafakata! Kuma ka maida Maɗaukaki mafakarka.10Ba mugun abin da zai same ka; ba wani abu mai cutarwa da zai kusanci gidanka.11Domin zai umarci mala'ikunsa su kare ka, su kuma yi tsaronka a cikin dukkan hanyoyinka.12Zasu tayar da kai tsaye da hannunsu domin kada kayi tuntuɓe a kan dutse.13Zaka hamɓare zãkuna da damisoshi a ƙarƙashin ƙafafunka; zaka tattake 'yan zãkoki da kuma macizai.14Saboda ya sadaukar da kansa gare ni, zan cece shi. Zan kare shi saboda yana yi mani biyayya.15Sa'ad da yayi kira gare ni zan amsa masa. Zan kasance tare da shi a cikin masifa; Zan ba shi nasara zan kuma girmama shi.16Zan ƙosar da shi da tsawon rai in kuma nuna masa cetona.
Ana yawan samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Don "rayuwa" da "zauna" na nufi kusan abu daya, kamar yadda "bukkar" da "inuwar," wadda nan dukka musilai ne domin kariya, za ka iya bukata gamma kai layin biyu zuwa ciki daya. AT: Mafi Ɗaukaka, Mai Iko Dukka, zai kula da dukka waɗanca wanda da na rayuwa inda ya iya kare su"
Kalmomin "Mafi Ɗaukaka" na nufi Yahweh. Gani yadda aka juya wannan a 18:13. ... wanda yake da iko da mulki akan kome da kome. Dubi yadda aka juya wannan a 68:14 ... "mafaka" shine kowane mazauna mutum na iya je kuma na da wani mutum ko wani abu ya kare shi. "Kagara" wani abu ne da mutane su yi domin su iya kare kansu da kuma dukiyar su. Asaph ya yi amfani da su anan kamar musilai domin kariya. AT: "wanda zan iya je gare shi kuma zai kare ni"
Kalmomi da a ka bari an iya sa su a ciki. AT: "Domin Allah zai kuɓutar da kai daga tarkon maharbi kuma zai kuɓutar daga annoban da zai iya kisa"
Kariyan Allah shine a ke nufi anan kamar "fukafukan" wanda sunsu ke amfani ta rufe 'ya'yan ta daga hadari. "Rufeka da fukafukansa" da kuma "ƙarƙashin fukafukansa" na nufi na asalin ta abu daya. AT: "Zaya rike ka lafiya kuma ya kare ka"
Madogarar Allah na nufi anan kamar "garkuwa" wanda ke iya kare mutane waɗanɗa sun dangana bisa kan sa. AT: "Ka na iya dogara a gare shi domin ya kare ka"
Ba wanda ya san tabataceyar mene ne wannan kalma ke nufi. Mai yiwu ma'anan su ne 1) karami garkuwa ɗaure a hannu da dantse wanda sojoji ke amfani su kare kansu akan kibiyoyi da takuba ko 2) ganuwan duwasu ajiye cikin da'irar inda sojoji zasu iya ɓoye da kuma harba kibiyoyi.
Marubucin zabura ya yi magana game da masifa sai ka ce ruhu ne ko wata dabba mai ban tsoro wanda ke iya kai farmaki da dare kuma haka ke razana mutane. AT: "abubuwa da ke kai maka farmaki da dare" ... kibiya shine metonym (wata kalma) domin mutane wanda ya harba kibiyoyi. AT: "mutane na kai maka farmaki da kibiyoyi da rana"
Marubucin zabura yayi magana game da ciwo sai ka ce mutum ne wanda ya tafi misalin da dare yana kisa saura mutane. AT: "Ba za ka ji tsoron mutuwa daga daga ciwo ba" ... ke duk inda ya na son ya tafi a kowane lokaci ... ciwo da kan sa mutane dayawa rashin lafiya a lokaci guda
"Mutane da yawa za su faɗi duka kewaye da kai." Indan aka juya ta daidai lambobin na iya birkitar da masu karatu, ka na iya ƙetare su.
"Kai da kanka ba zaka sha wahala ba, amma za ka kalla ka mai da hankali, kuma za ka gani" ... "yadda Allah ke hukunta miyagu"
"Yahweh shine wanda na kan je sa'ad da ina bukata wani da zai kare ni"
"Ya kamata ka maida Maɗaukaki mafakarka kuma." Marubucin zabura ya tsaya da magana da Allah kuma yana magana da mai karatu.
"Ba abu mugun da zai faru da kai" ... Marubucin zabura yayi magana game da mutane waɗanɗa ke wahal da wasu ko da ya ke kamar su ne cutar su ne sanadin. AT: "ba wani da zai iya cutar da iyalinka"
"Yahweh zai umurta" ... Marubucin zabura yayi magana game da hanya da mutum ke rayuwar ransa sai ka ce hanya ce kasa wanda mutum ke yi tafiya. AT: "cikin dukkan abu da ka yi" ko " dukkan lokaci"
"Malaikun Yahweh zasu tayar da kai" ... Malaikun ba zasu kare kafan mai karatu kawai ba amma duk da dukkan sauran jikinsa. AT: "ba za ka ko buga kafanka a kan dutse" ko "ba abu mugu da zai faru da kai"
Inda "buga kafanka a kan dutse" qananan matsalar ce, zakuna da macizai misalai hatsarori ne mai girma. Marubucin zabura ya yi magana game da zakuna da macizai sai ka ce su karami isasshe da za a rugurguje a karkashin kafan mutum. AT: "Za ka iya kashe zakuna da kasa sai ka ce su karami dabbobi ne wanda za ka iya rugurguje a karkashin kafafunka"
irin maciji mai guba. ... rugurguje tawurin yi tafiya mai nauyi a kan.
"Saboda ya na kauna ta" ... Wannan a na iya mai da a bayyane. AT: "Zan kasance da shi sa'ad da ya na cikin masifa"
Marubucin zabura ya yi magana game da rai sai ka ce wani abu ne da wani zai iya ci. AT: "Zan bar shi ya rayu da tsawon kuma da rai mai farin ciki"
"kuma zan nuna masa cetona." Marubucin zabura ya yi magana game da aikin da Allah ke yi don ceto mutane sai ka ce abu ce ta jiki. AT: "Zan cece shi domin ya san ni ne wanda na cece shi"
1Abu mai kyau ne a yi godiya ga Yahweh, a kuma yi waƙar yabo ga sunanka, Maɗaukaki,2a kuma yi shelar alƙawarin amincinka da safe gaskiyarka kuma kowanne dare,3da garaya mai tsarkiya goma da kuma kayan kaɗe-kaɗe masu daɗi.4Domin kai, Yahweh, kasa ni murna ta wurin ayyukanka. Zanyi waƙar farinciki saboda ayyukan hannuwanka.5Ina misalin girman ayyukanka, Yahweh! Tunane-tunanenka suna da zurfi.6Daƙiƙin mutun bai sani ba, haka ma wawa bai fahimci wannan ba:7Lokacin da miyagu suka firfito kamar ciyawa, ko ma a lokacin da miyagu suka taru, duk da haka an miƙa su ga hallaka ta har abada.8Amma kai Yahweh zaka yi mulki har abada.9Hakika ka duba maƙiyanka, Yahweh! Hakika ka duba maƙiyanka. Hakika zasu hallaka! Duk masu aikin mugunta za'a warwatsa su.10Ka tada ƙahona kamar na bijimin sã; An keɓe ni da sabon mai.11Idanuna sun ga faɗuwar maƙiyana; kunnuwana kuma sun ji hallakar miyagun maƙiyana.12Masu adalci zasu yi yaɗo kamar gazarin dabino; zasu yi girma kamar itacen sida na Lebonon.13An dasa sune a gidan Yahweh; Suna sheƙi a harabar Allahnmu.14Suna ba da 'ya'ya har ma a kwanakin tsufansu; suna nan kore shar,15Don ayi shela cewa Yahweh mai adalci ne. Shi ne dutsena, ba kuma rashin adalci a cikinsa.
Ana yawan samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Kalaman nan "sunanka" wata kalma don "kai." AT: "a rerar yabo gare ka"
Shi suna mai zuzzurfar ma'ana "amincin" ana iya bayana ta da siffa "amintacce." AT: "gaya wa mutane cewa kai amintacce ne don rikon alƙawarinka" ... Shi suna mai zuzzurfar ma'ana "gaskiyar" ana iya bayana ta da siffa "gaskiya ne." AT: "cewa duk abin da ka ce gaskiya ne"
Shi suna mai zuzzurfar ma'ana "ayyukanka" za a iya bayana ta da sharaɗin dangi "abin da ka yi." AT: "da mene ne ka yi"
Shi suna mai zuzzurfar ma'ana "ayyukan hannuwanka" za iya bayana ta da sharaɗin dangi "abin da hannuwanka ya yi." Kalman nan "hannuwan"
"Ba zamu iya fahinta abin da ka shirya ka yi sai ka yi shi"
Shi suna mai zuzzurfar ma'ana kalma " tunane-tunanenka" za a iya bayana ta da sharaɗin dangi. AT: "Abin da ka yi tunani" ko "Abin da ka shirya"
mai tashin hankali da wawa
Wannan yana kwantanta mungaye mutane da ciyawa, wanda ya ke tsiro da sauri kuma cikin wurare masu yawa. AT: "Lokacin da mungaye mutane na ɓullo da sauri kuma da alama na ko'ina, kamar ciyawa"
Wannan za a iya juya ta cikin fom na aiki. AT: "Allah ya yanke shawarar cewa zai hallaƙa su gaba daya"
Matanai masu yawa ba su da waɗannan kalomin.
"Zasu mutu" ko "Zai kashe su"
Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "zaka watsad da dukan waɗɗanɗa suna yin mugunta"
"kori daga nan"
Marubucin Zabura yana yin magana Allah sai ka ce Allah ya yi shi kamar daban daji mai ƙarfi. AT: "Ka yi ni kamar bijimin sã mai ƙarfi"
"sa ni in yi ƙarfi" Dubi yadda "tada...ƙaho" an juya ta cikin 75:4.
Mai yiwuwa yake ma'ana cewa main da Allah ya sanya akan marubucin zabura musili wa Allah 1) yana sa shi farin ciki "ka sa ni farin ciki sosai" ko 2) yana sa shi ƙarfi, "ka sa ni in yi ƙarfi" ko 3) ba shi daman cin nassara akan maƙiyansa, "ka ba ni dama cin nassara akan maƙiyana."
Kalman nan "idanu" da "kunnuwa" wata kalma ne
Mai yiwuwa ma'anan shine cewa mutane masu adalci zasu zama kamar gazarin dabino mai lafiya domin zasu 1) zama da ƙarfi ko 2) yi zama na tsawon lokaci.
Mai yiwuwa ma'anan shine cewa mutane masu adalci zasu zama kamar itacen sida na Lebonon mai lafiya da ke girma cikin kasar Lebonon domin 1) zasu zama da ƙarfi ko 2) mutane zasu girmamasu.
Za'a iya bayyana wannan cikin fom aiki. AT: "Yahweh ya dasa su" ko "Yahweh yana lura da su sai ka ce su itatuwa ne wanda ya dasa"
Marubucin zabura na magana game da mutane masu adalci sai ka ce su itatuwa ne masu lafiya. AT: "suna girma da kyau" ko "suna da ƙarfi sosai"
Marubucin zabura na magana game da mutane masu adalci sai ka ce su itatuwa ne masu haifar da abinci. AT: "Allah ya ji daɗi su"
Marubucin zabura na magana game da mutane masu adalci sai ka ce su itatuwa ne. AT: "sun zama da ƙarfi kuma da lafiya" ko "kullum suna yi abinda Allah na jin daɗi"
Mai yiwuwa tana ma'ana 1) "kore, don su iya shela" ko 2) "kore, Wannan na nuna cewa"
Yahweh ne wanda yana kare ni." MArubucin zabura na magana game da Yahweh sai ka ce shi dutse ne da zai kare shi. Dubi yadda an juya wannan cikin 18:2.
1Yahweh yana mulki; Yana saye da daraja; Yahweh yasa sutura ya kuma yiwa kansa ɗammara da ƙarfi. An kafa duniya daram; kuma ba zata gusa ba.2Kursiyinka ya kafu tun zamanin dã can; kana nan tun fil azal.3Tekuna suka tashe, Yahweh; sun ta da muryarsu; raƙuman tekuna sunyi tumbotso sunyi ruri.4Sun fi dukkan sauran ambaliyoyi masu ikon karya teku, Yahweh na sama maigirma ne.5Manyan umarnanka abin dogara ne na hakika; Yahweh, tsarki ya ƙayata gidanka, har abada.
Ana yawan samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa. (Dubi:|Poetry and|Parallelism)
Marubucin zabura ya yi magana game da ƙarfin Yahweh da darajan sai ka ce abubuwa ne da Yahweh ke sa. AT: "ya nuna kowa da kowa ceewa shine sarki mai iko duka" ko "darajansa na nan don duka su gani, kamar tufafi da sarki ke sa; kome game da Yahweh na nuna cewa na da ƙarfi kuma ya na shirye ya yi aiki mai girma" (Dubi:|Metaphor and|Simile)
da iko na sarki da kuma yadda sarki ke yi
saka bel--madauri ne na fata ko wani kaya da mutum ke sa kewaye da ƙugunsa--ya shirya shi domin aiki ko yaki
wadansu juyi kan ce "ambaliya ... ambaliya." Kalma nan sau da yawa na nufi rafikogi (dubi "kogin," 72:8), amma tekuna ... tekuna" an zabe shi ana saboda tekuna,, ba kogi, samun "rakuman ruwa" da "haɗari da ruri."
yin dogo, ƙara mai ƙarfi.
Kalma nan "masu ikon karya teku" na nufi asalin abu daya kamar "sauran ambaliyoyi" kuma na jaddada yadda girman wadda nan ambaliyoyi suke. AT: "Fiye the da faduwa na dukan wadda nan ambaliyoyin teku masu girma sosai"
Marubucin zabura ya yi magana game da inda Allah na zama sai ka ce tana sama bisan duniya ne. AT: "cikin sama"
mai isan tunani sosai ... "kullum tana nan daidai" ko " ba ta chenjawa faufau (UDB)
Marubucin zabura ya yi magana game da gidan Yahweh sai ka ce mece ne da take sa tufafi mai kyau gani ko kayan ado na zinare kuma game da tsarkin Yahweh kamar tufafi mai kyaun gani ko kayan ado zinare. AT: "gidanka yana da kyau gani domin kai mai tsarki ne" ko "tsarkinka na sa gidanka kyau yadda tufafi masu kyau kuma yadda kayan ado na kara wa mece kyau"
haikalin cikin Yerusalem
tasa kyaun gani
1Yahweh, Allah mai sakayya, Allah mai sakayya ka haskaka a bisan mu.2Ka tashi tsaye mai shari'ar duniya ka ba masu girman kai abin da ya kamance su.3Har yaushe miyagu, Yahweh har yaushe miyagu za suyi farinciki4Dukkan masu aikin mugunta suna ta yin maganganunsu na wauta; Duk masu mugunta suna fahariya.5Yahweh; sun buge mutanenka, Sun ƙuntata wa al'ummarka.6Sun kashe gwauruwa da bãƙon dake zaune a ƙasarsu, sun kuma kashe marayu.7Suka ce, "Allah ba zai gani ba, Yahweh na Yakubu bai kula da abin ba."8Ku lura mutane marasa hankali! Ku wawaye, har sai yaushe zaku koyi darasi?9Shi wanda yayi kunne ashe ba zai ji ba? Shi wanda yayi ido ba ya gani ne?10Shi dake horon al'ummai, ashe ba zai tsautar ba? Shi ne mai ba da ilimi ga mutum.11Yahweh ya san tunanin mutane, cewa turiri ne kawai.12Mai albarka ne wanda ka yiwa gargaɗi, Yahweh wanda ka koyar daga cikin shari'arka13Ka bashi hutu a lokutan damuwa har sai da aka gina rami domin miyagu.14Domin Yahweh ba zai yashe da mutanensa ba ko kuma yayi watsi da abin gãdonsa ba.15Domin hukunci zai sake zama da adalci; kuma dukkan masu tsarkin rai zasu bi shi.16Wa zai tashi ya kuɓutar dani daga masu mugunta?17In da ba domin Yahweh ya taimake ni ba da yanzu ina can kwance a lahira.18Lokacin dana ce ƙafafuna na barci," Yahweh alƙawarin amincinka ya ɗaga ni sama.19Lokacin da fargaba ya cika ni ta'aziyarka ta kan sani in cika da murna.20Ko akwai hurɗa tsakaninka da mulkin hallakarwa da ya kafa rashin adalci?21Sun shirya maƙarƙashiya tare domin su kashe mai adalci sun kuma hukuntawa marar laifi mutuwa.22Amma Yahweh ne babbar hasumiyata, Allahna kuma shi ne dutsen fakewa ta.23Zai saukar masu da laifofinsu zai kuma daddatsa su a cikin aikin muguntarsu. Yahweh Allahnmu zai daddatse su.
Ana yawan samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
"nuna kanka" ko "bayyana ãdalcinka"
"Zo, mai shari'ar duniya, kuma ka hori masu girman kai"
Marubucin zabura ya yi magana game da farko yin wani abu kamar tashiwa ne. Indan yarenka yana da kalma na farko a aikata, yi amfani da ita a nan. AT: "Ɗauki mataki" ko "yi wani abu"
Marubucin zabura ya yi ta maimata tambayan don nuna cewa bai jidadi ba da yadda Yahweh ya yarda miyagu su yi farinciki. Wannan tambayar da ba ta damu da amsa ba. ana iya jjuya ta kamar wata kalma. AT: "Ka jira na sawon lokaci Yahweh; ka jira na sawon lokaci da ka tsayad da miyagu daga farinciki."
Don mene ne miyagu suke farinciki za'a iya bayyana ta a fili. AT: miyagu za suyi farinciki saboda ba ka taba horansu domin mugu ayyuka da sun yi"
Marubucin zabura ya rubuta game da miyagu suna magana sai ka ce kalmominsu ruwa ce da ke kasancewa an zubar waje.
"Dukan waɗanɗa suna yin alfahari da mugunta game da mugu ayyukansu da halinsu"
Anan kalman
Marubuci zabura ya yi magana game da mutane masu iko suna mugun zalunta mutane marasa iko sai ka ce suna hudamah su ko karya su gutsuri-gutsuri. AT: "Sun cũtar dasu kwarai." Dubi yadda "karya gutsuri-gutsuri" an fassara ta a 72:4.
"mata wanda mazan sun mutu" ... "yara da babu ubanninsu"
"Allah na Isra'ila ba ya gani abinda muna yi"
Marubuci yanzu ya umurce miyagu mutane.
Wannan tambayar da ba damu da amsa ba na jaddada fushin marubucin da miyagun mutane da yake magana. Wannan tambaya za'a iya fassara ta kamar bayani. AT: "daina wauta hanyoyinka!" ko "kowa daga kuskurenka!"
Wannan tambayar da ba damu da amsa ba za'a iya fassara ta kamar bayanai ko dokokin. AT: "Allah ya yi kunnuwa, don haka ya iya ji. Allah ya yi idanu, don haka ya iya gani." ko "Allah ya yi kunnuwa, don haka daina aiki sai ka ce ba ya ji. Allah ya yi idanu, don haka daina aiki sai ka ce ba ya gani."
Marubuci ya ci gaba da umurta miyagun mutane.
Wannan tambaya za'a iya fassara ta kamar bayani. Tana nuna cewa Yahweh na gyara mutanensa. AT: "Ka sani cewa Yahweh na gyara al'ummai, don ka iya tabbata cewa yana gyara mutanensa" ko "zai horon mutanensa"
A nan an kwatanta tunani mutane da tururi wanda ke ɓace wa cinkin iska. Wannan musili ya nuna yadda suke da rashin muhimminci kuma da mara amfani.
"tururi." Dubi wannan kalma an fassara ta cikin 39:10
Yanzu kuma marubuci yana magana da Yahweh.
Marubucin zabura na magana game da horon Yahweh akan miyagu sai ka ce Yahweh yana tarkon naman daji a cikin rami. Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "har sai ka tauna rami domin miyagu" ko "har sai ka hallaka miyagu"
Marubucin zabura ya yi magana game da waɗanɗa suna hukunci sai ka ce shawara da sun yanka kenan. Suna mai zuzzurfar ma'ana "hukunci" ana iya fassara ta da fi'ili "hukunta." AT: "mahukunta zasu hukunta da adalci" ko "mahukunta zasu yanke shawara da adalci"
Siffa kalma nan "masu zuciya nagari" ana iya fassara ta kamar maganan suna. AT: "waɗanɗa zuciyar su na nan daidai da Allah"
Wannan ana iya fassara ta kamar bayani. AT: "Ba wanda zai kuɓutar dani daga masu mugunta. Ba wanda zai taimaki ni fada da mugaye."
Siffan "mugaye" ana iya fassara ta kamar kalma suna. AT: "mugaye mutane"
Wannan misali ne na halin da ake ciki. Yahweh ya taimake shi, don haka ba ya kwance a wuri da ke nan shiru.
Sunan mai zuzzurfar ma'ana "taimako" ana iya faɗi shi kamar fi'ili. AT: "Idan Yahweh da bai taimaki ni ba."
Anan "da ina kwance" na nufi "mutuwa" kuma "a wuri shiru" na nufi " zuwan kabari." AT: " a cikin gajeren lokaci, da na mutu, kwance shiru cikin kabari"
Marubucin zabura ya yi magana game da kula sai ka ce zai iya lissafta kulan na rabe. Sunan mai zuzzurfar ma'ana "abun da zai kawo maka sassauci lokacin da kai fushi" ana iya fassara ta da fi'ili "kwantarma da wani hankali a lokacin da ya yi fushi" ko "ta'aziya." AT: Lokacin da ina damuwa game da abubuwa dayawa, ka ta'azantar da ni kuma ka sa ni murna"
Wannan tambaya da ba ta damu da amsa ba na yin amfani don ba da ma'ana. Ana iya fassara ta kamar bayani. AT: "Mugun sarki wanda ya ba da azzãlumai dokokin ba abokinka bane"
A nan wata kalma nan
shiriya wani abu mai cutarwa tare da mutum ko na ketare doka
Wannan kari ne wadda ke nufi a yi kisan wani.
A nan "hasumiya" karin magana domin kariya. AT: "Yahweh ya kare ni daga abokan gaba na"
Marubucin zabura ya yi magana game da yadda Allah ya kare shi sai ka ce Allah ne wurin inda marubucin zabura zai iya je ya samu lafiya. Dubi yadda "dutse" da "mafaka" an fassara ta cikin 62:7. AT: "Na roki Allah ya kare ni, kuma ya rike ni lafiya da ikonsa"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1)"zai yi masu mugun abubuwa da suka yi wa wasu" ko 2) "zai huƙunta su domin dukan mugun abubuwa da ya yi wa wasu."
Wannan shine kari wanda ke ma'ana "kashe su."
1Ku zo mu raira yabo ga Yahweh, Sai mu raira waƙar farinciki ga dutsen cetonmu.2Sai mu zo gabansa da godiya, sai mu raira masa yabo da waƙoƙin zabura.3Domin Yahweh Allah ne mai girma, sarki ne mai girma da yafi dukkan alloli.4Zurfafan duniya dukka a hannunsa suke; Duwatsu masu tsawo kuma nasa ne.5Teku tasa ce, shi ne yayi ta. Hannuwansa kuma suka yi busasshiyar ƙasa.6Ku zo muyi sujada mu durƙusa ƙasa, sai mu durƙusa a gaban Yahweh mahallicinmu;7Domin shi ne Allahnmu, mu mutanen makiyayarsa ne, tumakin hannunsa kuma. Yau ace dai za ku ji muryarsa!8Kada ku taurare zuciyarku, kamar a Meriba, ko kuma kamar ranar Massa a cikin jeji,9inda ubanninku suka gwada ni suka kuma jaraba ni, koda ya ke sun ga aikina.10Shekaru arba'in ina fushi da waccan tsarar na ce, "Waɗannan mutane ne da zuciyarsu ta karkace; basu san hanyoyina ba.11'Domin haka cikn fushina na rantse cewa ba zasu taɓa shiga wurin hutu na ba
Ana yawan samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Marubucin zabura ya yi magana game da Yahweh sai ka cr Yahweh wani babban tsauni ne da mutane za su hau don su zama sa lafiya. AT: "dutsen inda muna iya je kuma Allah zai cece mu." Dubi yadda "dutse" da "cetona" an fassara su cikin 18:46.
Marubucin zabura ya yi magana sai ka ce yana gaya wa masu karatu su tafi zuwa cikin ɗakin kursiyi na sarki. AT: "tafi zuwa inda ya ke"
Mai yiwuwa ma'ana suna nan cewa Yahweh shine mai girma sarki 1) "wanda ke mulki a kan dukan sauran alloli."
Wannan kari ne wanda yake ma'ana "a karkashin kulansa" ko "yana da alhakin."
wuri mai zurfi ... dogon wuri
Kalma nan "hannuwan" shine wata kalma
sa duka gwiwoyi biyu a kasa, sau da yawa na nuna biyayya
Kalma nan "makiyaya" wata kalma ce
wuri inda dabbobi sukan samu ciyawa su ci ... Kalma nan "hannu" ana na nufi yadda Yahweh na kare mutanensa kamar yadda makiyayin tumaki ke kare tumakinsa. AT: "mutanen wanda yake kare kamar yadda makiyayin tumaki na kare tumakinsa"
A nan "muryarsa" yana nufn mai da hankali akan kalmomin Allah. AT: "saurare shi da kyau"
Yanzu marubuci ya rubuto kalmomin da Yahweh ya fadi.
"kassance da taurin kai"
Wanda nan wurare cikin hamada da Musa ya sar mai suna domin Isra'ilawa sun yi wa Allah tawaye.
Waɗannan kalmomi biyun duka musilai ne domin mutanen ganin irin mugunta da zasu iya yi kafin Yahweh ya hukunta su. Wannan kalmomin mafin muhimminci na faɗi abu daya ne kuma ana iya haɗa su. AT: "gwada ni" ko "neman a gani ko zasu yi mugu abubuwa ba tare da na hukunta su ba... gwada ko zan ci gaba da yin hakuri da su"
Yahweh ci gaba da magana kai tsaye da mutanensa.
"dukan waɗancan mutane" ko "waccan dukan tsarar mutanen"
Allah ya yi magana game da mutane sai ka ce su tumaki ne, wanda zai iya ji ko ina da suke so su ji kuma ba su tsaya kusa da makiyayar tumakin. AT: "je can nesa da ni" ko "su je hanyar su"
"wurin wanda zan yarda masu su huta"
1Ku raira sabuwar waƙa ga Yahweh; ku raira waƙa ga Yahweh, dukkan duniya.2Ku raira waƙa ga Yahweh, ku albarkaci sunansa; kuyi shelar cetonsa a kowacce rana.3Ku furta ɗaukakarsa a cikin al'ummai, ayyukansa na ban mamaki a cikin al'ummai.4Domin Yahweh yana da girma ya kuma isa yabo sosai. A ji tsoron sa fiye da dukkan sauran alloli.5Saboda allolin al'ummai gumaka ne, amma Yahweh ne ya hallici sammai, martaba da wadata suna gabansa.6Jamali da ƙarfi suna cikin wurinsa mai tsarki.7Kuyi yabo ga yahweh ku dukkan kabilu na mutane, ku yabi Yahweh sabili da ɗaukakarsa da ƙarfinsa.8Ku ba yahweh ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo baiko a haikalinsa.9Ku durƙusa a gaban Yahweh saye da tufafin dake girmama tsarkinsa. Yi rawar jiki a gabansa, dukkan duniya.10Ku faɗa a cikin al'ummai cewa,"Yahweh ne ke mulki." Hakannan kuma aka kafa duniya; ba kuma zata jijjigu ba. Yana yiwa mutane shari'ar dake dai-dai.11Sai sammai suyi murna, sai duniya kuma ta yi farinciki; sai teku yayi ruri abin da ke cikinsa kuma su cika da murna.12Filaye suyi murna da duk abin da ke cikin su. Sa'an nan kuma dukkan bishiyoyin duniya su ɓarke da yabo13a gaban Yahweh, domin yana tafe. Yana zuwa domin ya shar'anta duniya. Zai shar'anta duniya da adalci da mutane kuma cikin amincinsa.
Ana ywan samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Wannan yana nufi mutanen duniya. AT: "dukkan ku mutane waɗanda ke zaune a duniya"
Kalma "suna" wata kalma ce (a turance ake ce da ita metonym) don Yahweh da kansa. AT: "bless Yahweh" ko "yi abun da zai sa Yahweh murna." Dubi yadda "bari sunansa mai daraja ya zama da albarka" an fassara ta cikin 72:18.
Sunan ra'ayi na gamayya "ceto" ana iya fassara ta wurin yin amfani da fi'ilin "ceta". AT: "sanad da cewa ya cece mu" ko "faɗa wa mutane cewa shine wanda yana ceto"
"Ku gaya wa dukkan mutane cikin kowane al'umma game da girma darajansa"
Wannan za'a iya fassara ta cikin fom na aiki. AT: "Yahweh yana da girma. Yi yabonsa matuƙa" ko "Yahweh yana da girma, kuma ya kamata mutane su yi matuƙan yabonsa"
Za'a iya fassara wannan cikin fom na aiki. AT: "Ji tsoron sa fiye da dukkan saura aloli"
"Inda ya na nan"
Marubucin zabura yana magana sai ka ce martaba da wadata mutane ne wanda zai iya tsaya a gaban sarki. AT: "Kowa da kowa ya san martabansa da zatinsa"
Kalma "ƙarfi" da "kyawu" metonyms ne domin umurnin akwatin alkawarin, wanda ake samu cikin guri mai tsarki. AT: "haikalinsa ne da ya kunshi umurnin akwatin alkawarin"
Sunan ra'ayi na gamayya "ɗaukaka" da "ƙarfi" ana iya bayyana ta kamar siffa. AT: "Ku Yabi Yahweh ... ku yabi Yahweh saboda ɗaukakarsa da ƙarfinsa." Dubi yadda an fassara waɗannan kalmomin cikin 29:1.
Ku ba yahweh ɗaukakar da ta dace da sunansa Sunan ra'ayi na gamayya "ɗaukaka" ana iya bayyana ta kamar fi'ili ko siffa. AT: Girmama Yahweh daidai kamar da ta dace da sunansa" ko "Yi shelar cewa Yahweh yana da daraja daidai kamar da ta dace da sunansa." Dubi yadda an fassara waɗannan kalmomin cikin 29:1.
"suna" na nufi anan mutumtakar na Allah. AT: "shi" ... haikalin tsakar gida inda firistoci suna hadayan dabobi ga Yahweh
Mutum zai sa tufafin da ke nuna cewa yana gane cewa Yahweh yana da tsarki. "Yahweh, kuma da sa tufafin wanda ya dace domin yana yana da tsarki." Dubi yadda an fassara waɗannan kalmomin cikin 29:1.
yi rawa saboda tsoro ... "dukkan mutanen duniya"
Wannan za'a iya fassara ta a fom na aiki. AT: "Hakannan ya kafa duniya kuma"
Wannan za'a iya fassara ta a fom na aiki. AT: "ba abun da zai jijiga ta"
Mai yiwuwa ma'anan sune 1) cewa marubucin zaburan yana magana sai ka ce :sammai" da "duniya" suna da motsin zuciyar kamar mutane. "Bari ya zama sai ka ce sammai suna murna duniya kuma su yi farinciki" ko kuwa 2) "Bari waɗanda sun zauna cikin sammai suyi murna sai waɗanda suke zaune a duniya kuma ta yi farinciki"
"Bari filaye da duk abin da ke cikin su suyi farinciki." Marubucin zabura yana magana sai ka ce "filaye" da dabobin da ke zaune cikin su na da motsin zuciyar kamar mutane. AT: "Bari ta zama sai ka ce filayen da kansu da dukkan dabobin da ke zaune cikin su suyi farinciki"
Mai yiwuwa wani ma'ana kuma shine "ya yi mulki" ... "zai yi mulki."
Anan "duniya" metonym ne domin dukkan mutane cikin duniya. AT: "Za ya shar'anta dukkan mutanen duniya da adalci." Dubi yadda waɗannan kalmomin an fassara su cikin 9:7.
1Yahweh na mulki sai duniya ta yi murna, sai dukkan ƙasashe masu nisa suyi murna.2Gizagizai da duhu na kewaye da shi. Adalci da gaskiya ne harsashen kursiyinsa.3Wuta na tafe a gabansa tana cinye magafta ko ina4Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta furgita.5Duwatsu kuma sun narke kamar tufa a gaban Yahweh Ubangijin dukkan duniya.6Sararin sama na shaida adalcinsa, dukkan al'ummai kuma sun ga ɗaukakarsa.7Duk waɗanda ke bauta wa abin da hannu ya sassaƙa zasu kunyata, masu taƙama da gumaka marasa amfani- ku rusuna masa da dukkan allolinku!8Sihiyona taji sai tayi farinciki, biranen Yahuda kuma suka yi murna saboda dokokinka na adalci, Yahweh.9Domin kai, Yahweh, kafi kowa ɗaukaka a cikin dukkan duniya. An ɗaukaka ka fiye da dukkan alloli.10Ku dake ƙaunar Yahweh ku ƙi mugunta! Yana kare ran tsarkakansa, ya karɓo su daga hannun mugun.11An shuka haske domin adalai farinciki kuma domin masu zukata masu aminci.12Kuyi murna cikin Yahweh ku adalai; ku kuma yi masa godiya lokacin da kuka tuna da tsarkinsa.
Ana yawan samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Duniyan da ƙasashe gaɓar teku an ce da su na da motsin zuciyar kamar mutane. AT: " Yi farinciki da murna kowane mutum a duniya kuma da wanda ke kusa da tekuna
Kalman "kursiyi" metonym ne domin ayyukan da kalmomin na wanda ke zaune a bisan ta. Marubucin zabura yana magana sai ka ce adlaci da gaskiya ns hslitatun abubuwa ne da ke kumshe rike kursiyin da kyau. AT: "Ya na da adalci da gaskiya cikin dukkan abun da ya ke yi" ko kuwa "Ya iya yin mulki domin ya na mulki da adalci da gaskiya"
A nan "harsashen kursiyinsa" yana nufin yadda Yahweh ke mulki masarautansa.
Marubucin zabura yana magana ne sai ka ce wuta mutum ne da ke yin tafiya a gaban Yahweh Sarki kuma na gayawa mutane cewa sarkin na zuwa.
"duniya" na nufin mutane wanda ke zaune a duniya. AT: mutane da ke duniya sun gani kuma suka yi rawar jiki"
"ya girgiza da tsoro"
Duwatsun sun kasa su saya sa'ad da Yahweh ya zo kusa" ko kuwa "Duwatsun na marmashe a gaban Yahweh"
Mai yiwuwa ma'anan sunne 1) maruburucin zabura yana magana sai ka ce sararin masinja Yahweh ne wanda ke bayyana cewa Yahweh na da adalci. AT: "Kowa da kowa na iya gani cewa Allah na da adalci, haka nan kowa da kowa na iya gani sararin" ko kuwa 2) sararin ya nufa rai da ke zama cikin sammai. AT: "Duk waɗanda suna zaune cikin samma na bayyana cewa Yahweh na da adalci"
Wannan ana iy fassara ta cikin fom na aiki. AT: "Allah zai kunyatar da duk waɗanda suna taƙama da gumakai marasa amfani kuma masu bauta wa abin da hannu ya sassaƙa"
Wannan na nufi da mutane wanda ke zaune cikin waɗannan kasashe. AT: "Mutanen Sihiyona taji ... mutanee Yahuda"
Marubucin zabura yana magana sai ka ce waɗanda suna da isasshen karfi su yi mulki sune mafi girma ta jiki fiye da waɗansu. AT: "yi mulki bisan dukkan mutane mazaunanta"
Waɗannan kalmomin biyu na da ma'ana mai kama kuma an yi amfani da su tare domin girmamawa. AT: "Yahweh ya shuka haske domin waɗanda ke yi abin da ke daidai, kuma ya shuka murna domin masu zukata masu aminci"
Kalma nan "shuka" musili ne domin mataki da sakamako nan gaba. "haske" musili ne domin abubuwa masu kyau. AT: "Yahweh yana shirye domin abubuwa masu kyau ya faru da sãlihai a nan gaba"
"murna kuma an shuka ta domin masu zukata masu gaskiya." Kalma nan "shuka" musili domin mataki da sakamako nan gaba. AT: "Yahweh yana shirye domin mutane masu zukata masu gaskiya su yi farinciki a nan gaba"
Wannan aya yana da umurnin biye da dalilin domin umurnin. Idan harshenka na bukatar dalilin ya riga umurnin: "Saboda abin da Yahweh yana yin domin ku, ku mutane masu adalci, yi murna kuma da yin godiya. sa'ad da kun tuna tsarkinsa."
"Ku yi murna saboda abin da Yahweh yana yin domin ku"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "lokacin da kuka tuna da yadda ya ke da tsarki" ko kuwa 2) "ga sunansa mai tsarki," metonym domin "gare shi."
1Oh, ku raira sabuwar waƙa ga Yahweh domin yayi ayyuka masu ban mamaki; hannunsa na dama da damtsensa sun ba shi nasara.2Yahweh ya sa cetonsa ya sanu; ya nuna adalcinsa a fili ga dukkan al'ummai.3Ya tuna da alƙawarinsa mai aminci da gaskiya ga gidan Isra'ila; dukkan iyakokin duniya zasu ga nasarar Allahnmu.4Ku raira waƙar farinciki ga Yahweh, dukkan duniya ku ɓarke da waƙa, kuyi waƙa domin murna, kuyi waƙoƙin yabo.5Ku raira yabo ga Yahweh da garaya, tare da garaya haɗe da waƙoƙi masu daɗi.6Tare da kakaki da ƙarar ƙaho, ku tada muryoyi masu daɗi a gaban Sarki, Yahweh.7Sai teku yayi ihu da dukkan abin dake cikinsa!8Sai rafuffuka su tafa hannuwansu, sai duwatsu kuma su raira waƙar yabo.9Yahweh yana zuwa domin ya yi wa duniya shari'a da adalci da kuma al'ummai tare da gaskiya.
Ana yawan samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Kalma "hannun dama" da "damtse mai tsarki" na nufi ƙarfin Yahweh. Tare sun jaddada yadda girman ƙarfinsa yake. AT: "girman ikonsa kwarai yana da"
Mafin yawa iko da gwanin hannu ... Anan "damtse" metonym ne domin iko. AT: "iko da ke na shi ne kadai"
Suna mai zuzzu'rfar ma'ana "adalci" ana iya fassara ta ta yin amfani da siffa "adali." Kalma "al'ummai" metonym ne domin "mutanen da zasu rayu cikiin dukkan al'ummai." AT: "nuna mutanen da suna rayuwa cikin dukkan al'ummai cewa shi adali ne"
"tuna da." Dubi yadda "tuna da" an fassara ta cikin 20:3.
Wannan metonyms ne domin mutanen duniya. AT:m"mutane daga dukkan iyakokin duniya ... dukkan mutanen duniya"
Suna mai zuzzu'rfar ma'ana "nasara" ana iya fassara ta ta yin amfani da fi'ili "cin galaban wani ko wasu." AT: "zasu ga Allahmu ya ci galaban abokan gabansa"
"ba zato ba tsammani ya fara yin waƙa da farinciki" ... yi waƙa domin kana da farinciki" ... yi waƙa ga Allah"
mai ban murna ko ƙaran kiɗi mai gamsarwa
ƙahon dabba na yin amfani kamar kayan kide kide
"tada ihu." Dubi yadda an fassara "ihu" cikin 47:1.
Marubucin zabura ya yi magana sai ka ce teku mutum ne wanda zai iya ihu ga Allah. AT: "Bari ta zama sai ka ce tekun da dukkan abin dake cikinta su yi ihu"
Marubucin zabura ya yi magana sai ka ce duniya mutum ne. AT: "kuma bari duniya da waɗanda ke zaune a cikinta su yi ihu"
Marubucin zabura ya yi magana sai ka ce rafuffukan da duwatsun mutane ne wanda zasu tafa da kuma ihu. AT: "Bari ta zama kamar yadda ko da yake rafuffuka suna tafa hannuwansu kuma duwatsun suna ihu domin murna"
"gaskiya" ko "yin amfani da ma'auni daya domin kowa da kowa"
1Yahweh na mulki; bari al'ummai suyi rawar jiki, yana zaune kan kursiyi sama da Kerubim, duniya ta girgiza,2Yahweh yana da girma a Sihiyona yana da ɗaukaka fiye da dukkan al'ummai.3Sai a yabi sunanka mai jamali da girma; yana da tsarki.4Sarki yana da ƙarfi, yana kuma ƙaunar adalci. ka kafa gaskiya; ka aikata adalci akwai adalci kuma a cikin Yakubu.5A yabi Yahweh Allahnmu a kuma yi sujada a digadigansa. Ya na da tsarki.6Musa da Haruna na cikin firistocinsa, Sama'ila kuma na cikin waɗanda suka yi addu'a gare shi. Sun yi addu'a ga Yahweh, ya kuma amsa masu.7Ya yi masu magana daga ginshinƙin girgije. Sun kiyaye tsattsarkan umarninsa da farillan da ya basu.8Ka amsa masu, Yahweh Allahnmu. Kai Allah ne mai gafara a gare su, amma kuma kana horon ayyukansu na zunubi.9Ku yabi Yahweh Allahnmu, ku kuma yi sujada akan tudunsa mai tsarki, gama Yahweh Allahnmu yana da tsarki.
Ana yawan samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Marubucin zabura yana magana sai ka ce kursiyin wanda Yahweh yana zaune sama da kerubim a kan murfin na akwatin alkawarin na umurnin cikin haikalin.
"Ba wai Yahweh na da girma a Sihiyona kawai ba, yana da ɗaukaka fiye da dukkan al'ummai" ko "Ba wai Yahweh na mulkin cikin Sihiyona kawai ba, yana yin mulki bisan dukkan al'ummai"
A nan mawallafi ya canja daga yin magana game da Allah, zuwa ga yin magana da Allah. bayan wannan magana ko da yake, ya na canjawa a baya ga yin magana game da Allah.
Suna mai zuzzu'rfar ma'ana "adalci" za'a iya fassara da yin amfani da magana "abin da ke daidai." AT: "yana ƙaunar yin abin da ke daidai."
Suna mai zuzzu'rfar ma'ana "gaskiya" metonym ne domin dokokin da suke da gaskiya. "Dokokin da ka kafa suna nan gaskiya"
"gaban kursiyinsa"
"tsarki"
"ka amsa mutanenka"
"Dutsen Sihiyona"
1Kuyi ihu da farinciki ga Yahweh ku dukkan duniya,2Ku bautawa yahweh da farar zuciya, kuzo gabansa da waƙoƙin farinciki.3Ku sani Yahweh Allah ne; yayi mu, mu kuma nasa ne. Tumakin makiyayarsa kuma.4Ku shiga ƙofofinsa da godiya cikin gidansa da yabo. Kuyi masa godiya ku albarkaci sunansa.5Domin Yahweh nagari ne; alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada gaskiyarsa kuma har dukkan tsararraki ne.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
"Ku ta da ihu ga Yahweh." Dubi yadda an fassara "ihu" cikin 47:1.
Wanna yana nufi dukkan mutane duniya. AT: "kowa da kowa a duniya"
Marubucin zabura yana magana sai ka ce yana gaya wa masu karatu su je cikin dakin kursiyin na sarki. AT: "ku je inda ya ke da waƙoƙin farinciki" ko "yana iya jin ka, don haka ku rera waƙar don farincikn"
Mutanen Allah suna nan kamar tumaki. AT: mutanen Allah yana yin masu tanadi da kariya"
wurin da yake rufe da ciyawa domin ciyar da dabobi
"yayin da yana godiyansa" ko "yayin da yana ba da godiya gare shi"
Kalman "suna" metonym ne domin Yahweh da kansa. AT: "albarkaci Yahweh" ko "yi abin da yana sa Yahweh farinciki." Dubi yadda "bari sunansa mai daraja ya zama da albarka" an fassara ta cikin 72:18.
"gaskiyarsa yana dawwama har dukkan tsararraki "
"ƙarni bayan ƙarni." Dubi yadda an fassara wannan cikin 89:3.
1Zan raira alƙawarin aminci da gaskiya; a gare ka, Yahweh, zan raira yabbai.2Zan yi tafiya cikin aminci. Oh, yaushe zaka zo wurina ne? Ni da gidana za muyi tafiya cikin nagarta.3Ba zan ƙyale mugunta a idanuna ba; Na ƙi mugun aiki marar cancanta; ba zai manne mani ba.4Ɓatattun mutane zasu rabu dani; bana yin biyayya ga mugunta.5Zan hallaka duk wanda ya yiwa maƙwabcinsa yanke a asirce. Ba zan ƙyale duk wani mai fankama da rashin hankali ba.6Zan nemi masu aminci na ƙasar su zauna a gefena. Masu tafiya cikin gaskiya da riƙon amana ne zasu bauta mani.7Mayaudara ba zasu kasance a gidana ba; maƙaryata bazan marabce su a idona ba.8Duk safiya zan hallakar da miyagu dukka daga ƙasar; Zan kawar da dukkan miyagu daga birnin Yahweh.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Anan Dauda ya yi magana game da "mai rai" sai ka ce tana "tafiya." AT: "Zan yi tafiya cikin hanyar mai gaskiya da kuma daidai" ko "Zan yi rayuwa dake cike da aminci"
A nan Dauda ya yi magana game da "yanda mutum ke rayuwa" sai ka ce tana "tafiya." Kuma, Dauda ya yi magana game da sa ido akan gidansa da aminci, sai ka ce aminci abu ne wanda za'a iya tabawa da ke zaune a cikin gidansa. AT: "Zan sa ido a gidana da nagarta"
azzãlumai" suna ne mai zuzzurfa ma'ana da ana iya rubuta ts kamar jimla. Karin magana, "sa mugunta kafin idannuna," ma'ana a amince da ita. AT: "Ba zan amince da duk wani abun da an aikata da ba daidai ba a gabanna"
Dauda ya bayyana "mugunta" sai ka ce wani abu ne da ya kasa sa a manne masa. Wannan ya ma'ana cewa zaya kauce wa mugaye abubuwa da mutane masu aikata mugayen abubuwa. AT: "Zan kauce wa mugaye abubuwa gaba daya"
Wannan jimla biyu na ma'ana yana na asalinta abu daya `kuma na jadada yadda girman kai mutanen nan yake.
Wannan yana ma'ana cewa Dauda zai kyale waɗannan mutane su zama kusa da shi kuma su yi zama da shi. AT: "Zan kyale masu aminci a kasar su zauna da ni"
Wannan yana nufa mutane wanda suna da aminci ga Allah. AT: "mutane masu aminci"
A nan Dauda yana magana game da "rayuwa" sai ka ce suna "tafiya." AT: "yin zama cikin a hanyar ta gaskiya kums da daidai" ko "yin zama rayuwa da aminci"
Waɗannan jimla biyu suna da ra'ayi daya kuma ana amfani da su tare a jadada yadda Dauda ba zaya yi hakuri da mutane masu yaudara ba.
A nan "idannuna" yana nufi na shi Dauda da kansa. AT: "a gabana" ko "cikin kasancewarna"
"Yau da kullum"
Dauda yana magana da birnin da yana ciki kamar da "birnin Yahweh." Wannan ana iya bayyana ta. AT: "daga wannan birnin, wanda shine birnin Yahweh"
1Yahweh ka ji addu'ata, Yahweh ka ji kukana dana keyi gare ka.2Kada ka ɓoye mani fuskarka a lokacin da nake damuwa. Ka ji ni. A lokacin da nayi kira gare ka, ka amsa mani da sauri.3Gama kwanakina sun wuce kamar hayaƙi, ƙasusuwana kuma na ƙuna kamar wuta.4An buge zuciyata na zama kamar ciyawar data bushe. Na manta in ci wani abinci.5Da nishe-nishena na kullum, na rame.6Na zama kamar zalɓe a hamada; na zama kamar mujiya a kufai.7Na kwanta ba tare da yin barci ba, kamar tsuntsun dake kaɗaici, shi kaɗai a bisa kan gida.8Maƙiyana nayi mani ba'a; masu yi mani habaici na la'anta sunana.9Toka ce abincina kuma gurasa abin shana ya gauraye da hawaye na.10Saboda fargaban fushinka ka ɗaga ni sama domin ka fyaɗa ni ƙasa.11Kwanakina sun zama kamar inuwar data gushe, na kuma yanƙwane kamar ciyawa.12Amma kai Yahweh, kana raye har abada, kuma shahararka ta dukkan tsararraki ce.13Zaka tashi kayi jinƙai ga Sihiyona. Yanzu ne lokacin nuna mata jinƙai; lokacinta da kasa yayi.14Domin bayinka sun riƙe duwatsunta ƙaunatacce ka ji tausayi saboda ƙurar kufanta.15Al'ummai zasu girmama sunanka, Yahweh, kuma dukkan sarakunan duniya zasu girmama ɗaukakarka.16Yahweh zai sake gina Sihiyona ya kuma bayyana a cikin ɗaukakarsa.17A wancan lokacin, zai amsa addu'ar wulaƙantattu; ba zai ƙi addu'arsu ba.18Za a rubuta wannan saboda tsararraki masu zuwa, da mutanen da ba'a haifa ba tukuna zasu yabi Yahweh.19Domin ya dubo ƙasa daga can sammai; Daga samaniya Yahweh ya dubi duniya,20domin ya ji nishe-nishen 'yan sarƙa, ya kuɓutar da waɗanda aka hukuntawa mutuwa.21Mutane zasu yi shelar sunan Yahweh a Sihiyona da kuma yabonsa a Yerusalem22lokacin da mutane da mulkoki suka tattaru tare su bauta wa yahweh.23Ya ɗauke ƙarfina a tsakiyar rayuwata. Ya gajarta kwanakina.24Na ce Allahna kada ka kawar dani a tsakiyar rayuwa; kana nan a dukkan tsararraki.25A can lokacin dã ka kafa duniya a wurinta; sammai kuma aikin hannuwanka ne.26Zasu lalace amma kai zaka dawwama; duk zasu tsufa kamar sutura; kamar tufafi, zaka cire su, zasu kuma ɓace.27Amma kai kana nan yadda kake, shekarunka kuma basu da iyaka.28'Ya'yan bayinka zasu rayu, zuriyarsu kuma zasu rayu a gabanka."
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Wannan yana nufin da mutu wanda ya ke cikin kunci. AT: "mutum wanda ya ke cikin kunci"
"suma" ko "ƙumama"
Yadda marubuci ya bayyana makokinsa aka kwatanta shi da zuban ruwa. AT: "da yardan kai ya bayyana bakin cikinsa ga Yahweh"
A nan "kwanakina" na nufin da rai marubuci kuma da ra'ayi na "hayaƙi" wani abu ne da yake ɓace wa da sauri. AT: "raina yana wucewa da sauri"
A nan marubuci yana nufin da "jikinsa" kamar yadda "ƙasusuwansa." AT: "jikina yana ji kamar tana ƙunawa" '
A nan marubucin yana nufin da kansa kamar yadda "zuciyarsa." Wannan na iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "I na cikin fid da zuciya"
Wannan wani hanyar ce na bayyana fid da zuciyarsa. AT: "Ina jin kamar ina bushewa kamar ciyawa da ke yanƙwane wa"
Ya kwatanta kaɗaicinsa da na zalɓe, wanda sau da yawa na ba da alama zaman kadai maimakon zaman da sauran tsuntsaye. AT: "Ina nan mai kadaici da kas kantattu kamar da zalɓe cikin hamada"
babban tsuntsu mai cin kifi
Mawallafi ya ci gaba da bayyana kaɗaici ta wuri kwatanta kansa da mujiya cikin kango da akayi watsi dashi. AT: "Na zama kaɗai kamar mujiya cikin kango da akayi watsi dashi"
Wannan tsuntsu ne da yake a farke da dare. AT: "tsuntsun dare"
Marubuci ya kwatanta kanasa da tsuntsu don ya jadada kaɗaici da yake ji.
Da Dauda zaya zauna cikin toka kamar yadda akan yi bakin ciki, saboda haka toka da zaya fadi cikin abincisa. AT: "Ina cin toka kamar ina cin gurasa" ko "Kamar yadda ina bakinciki, toka na faɗi akan gurasa da ina ci"
Dauda bai yi shi da niyya ya gauraye abin shansa da hawaye ba; ko dai hawayensa da ya faɗi a cikin kofinsa yayin da yana bakinciki da kuma kuka. AT: "hawaye na kuma ya faɗi a cikin kofin da ina sha"
A zahiri Allah bai ɗaga sama kuma don ya jefar da jikin Dauda ƙasa ba; ko dai Dauda yana ce haka ya kwatanta yadda yake jin da kuma fuskantar. AT: "ta na nan kamar ka ɗaga ni sama domin ka jefar da ni ƙasa"
Dauda ya kwatanta lokacinsa da ta rege masa a duniya da inuwa mai koɗewa. AT: "Lokaci na na kasancewa da rai gajerewa ce kamar inuwa na maraiceda ba dadewa ba zaya tafi"
Sa'ad da jikin Dauda ya zama kumama kuma yana kusa da karshen rayuwansa, ya kwatanta kansa da ciyawar mai yankwanewa. AT: "jiki na ya zama kumaman kamar yadda ciyawa ke yankwanewa"
"zaka zama da shaida domin dukkan tsararraki masu zuwa"
kasancewa da sani daga mutane masu yawa
A nan "Sihiyona" na nufi mutane waɗanda ke zama cikin Sihiyona. AT: "kayi jinkai ga mutane Sihiyona" (Dubi: Metonymy)
"Duwatsun" na nufi duwatsun da suna sashi ganuwar birnin kafin an rushe su. AT: "har yanzu ana kauna duwatsun da suke cikin ganuwar birnin da"
Mutanen zasu girmama Yahweh saboda ɗaukakarsa. Anan an kira Yahweh da ɗaukakarsa. AT: "zaya girmamaka saboda kana da daraja"
za'a ganinka da daraja" ko "mutane zasu gani ɗaukaka"
Wannan na nufi da wulaƙantattu mutane.
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom mai yaƙini. AT: "Yahweh zaya amsa addu'ar su"
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Zan rubuta wannan domin tsararraki masu zuwa"
Wadanan jimla biyu suna da ma'ana kama da kuma suna da amfani tare domin jadada yadda Allah yana duba ƙasa daga sama.
"wurinsa mai tsarki can bisa duniya"
Ana iya bayyana wannan cikin fom na aiki. AT: "waɗanda hukumomin suka yanke masu hukumcin mutuwa"
Wadannan jimla biyu suna da ma'ana daya kuma suna jadada ra'ayi na yin yabo ga sunan Yahweh.
Ana iya kara kalmomin da sun ɓace. AT: "kuma yi shelar yabonsa"
Dauda ya bayyan Allah ne sanadi ya zama kumama sai ka ce ƙarfinsa wani abu wanda za'a iya gani wanda za'a iya ɗauke shi daga nan. AT: "ya yi sanadin in zama kumama"
Kalman "kwanaki" ana na nufi da rayuwansa. AT: "rayuwana"
Dauda yana rokon Allah kada ya bar shi ya mutu. AT: "kada ka ɗauke ni daga nan duniya" (UDB) ko "kada ka bar ni in mutu"
"kana kasancewa a dukkan tsararraki"
Kalman "su" na nufi "da duniya" da "sammai"
Anan Dauda ya bayyana tsawon lokaci da Allah na da rai kamar yadda "shekarunsa." Ana iya rubuta wannan a fom na aiki. AT: "zaka rayu har abada"
"zasu ci gaba da rayuwa"
Anan Dauda ya bayyana zuriyar na kasancewa da kariya da Yahweh kamar yadda suna kasancewa a gabansa. AT: "zama da kariya kamar yadda suna rayuwa a gabanka"
1Ina godiya ga Yahweh da dukkan raina, da dukkan abin da ke cikina, Ina yabon sunansa mai tsarki.2Ina godiya ga Yahweh da dukkan raina, na kuma tuna da dukkan ayyukansa nagari.3Ya gafarta dukkan zunubanka, ya kuma warkar da dukkan cututtukanka.4Ya ceci ranka daga hallaka yayi maka rawani da alƙawarin aminci da ayyukan jinƙai.5Ya ƙosar da ranka da abubuwa masu kyau domin haka ƙuruciyarka ta sabunta kamar gaggafa.6Yahweh yakan yi abin dake dai-dai da adalci ga duk waɗanda aka tsanantawa.7ya sanar da hanyoyinsa ga Musa, ayyukansa kuma ga zuriyar Isra'ila.8Yahweh mai jinƙai ne da alheri; yana da haƙuri; yana da matuƙar amincin alƙawari.9Ba kullum ya kanyi horo ba; ba kullum kuma ya kanyi fushi ba.10Baya yi mana bisa ga gwargwadon zunubanmu ko ya saka mana kan hukuncin zunubanmu ba.11Domin kamar yadda sammai ke nesa da duniya, to haka girman alƙawarinsa ya ke ga masu girmama shi.12Kamar yadda gabas tayi nisa da yamma hakannan ya kawar da laifofin zunubanmu daga gare mu.13Kamar yadda mahaifi ke tausayin 'ya'yansa, haka Yahweh ke tausayin masu girmama shi.14Domin yasan yadda aka yi mu; ya sani cewa mu ƙura ne.15mutum kwanakinsa kamar ciyawa ce yakan yi yabanya kamar furen saura.16Iska ta kan hura ta kansa, sai kuma ya ɓace kuma ba wanda zai san yadda yayi girma.17Amma alƙawarin Yahweh mai aminci har abada abadin ne ga masu girmama shi. Adalcinsa ya kai har ga zuriyar su.18Sun kiyaye alƙawarinsa sun kuma tuna su yi biyayya da dokokinsa.19Yahweh ya kafa kursiyinsa a sammai, masarautarsa kuma na mulkin kowa.20A yi yabo ga Yahweh, ku mala'ikunsa, ku masu iko dukka dake yin biyayya da maganarsa.21Ku yabi Yahweh, dukkan rundunoninsa, ku bayinsa ne dake yin nufinsa.22A yabi Yahweh, dukkan halittunsa, a dukkan wuraren da ya ke mulki. Zan yabi Yahweh da dukkan raina.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Zai yiwu ma'ana sune 1) Dauda ne ya rubuta Zabura ko 2) zabura game da Dauda ne ko 3) zabura yana cikin salo na zaburan Dauda.
Wadannan jimla biyu na ma'ana abu daya ne kuma na jadada yadda zaya yi wa Yahweh yabo kwarai. AT: " Zan yi wa Yahweh yabo da dukkan abin da ke ni"
"dukkan ni" ko "dukkan abin da ke ni." Dauda ya yi amfani da wannan jimla na nufin kansa kuma don jadada dukufansa ga Yahweh.
Wannan na nufi cewa Yahweh ya rike shi da rai. AT: "Ya ceci ni daga mutuwa"
Jimla "ranka" na nufi "kai," amma tana jadada cewa Yahweh ne bayar da albarku cikin rayuwa. AT: "Ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau ta rayuwanka"
Ka zama da "sabuntuwan ƙuruciyar" na nufi ka ji matasa kuma. Anan Dauda ya kwatanta yadda yake jin samartaka da hanzari da ƙarfi na gaggafa. AT: "ka ji matashi kua kana da ƙarfi kamar gaggafa"
"ƙuruciya" yana nufi ƙarfi da wani yake da shi kamar matashi.
"yin sanadin abin da ke daidai ya faru"
Wanda yake yin zalunta ana iya bayyana ta baro-baro. AT: "duk wanda an zalunta daga mutane"
Zai yiwu a kara kalmomin da sun ɓace. AT: "ya sa ayyukansa sannane ga zuriyar"
"yana cike da amince da kauna"
Wadannan jimla biyu suna da ma'ana masu kama da. Abun na biyu na ƙarfafa tunani na farko.
Waɗannan jimla biyu daidaici ne kuma yana jadada cewa Allah ba ya huronmu kamar yadda ya cancanci mu. AT: "Ba ya saka mana da hukuncin da ya cancanci mu domin zunubanmu ba"
"horonmu"
Tamka yana kwatanta nisan mai girma sakani sama da duniya da yawan kauna Allah zuwa ga mutanensa.
Nisan da ke sakani gabas da yamma ta na da nisa sosai da ba za a iya aunawa ba. Cikin wannan tamka, cewa nisa na kasancewa kwatanci da yadda nisan da Allah yana motsa laifofin mu daga gare mu.
Anan mawallafi ya kwatanta tausayin mahaifi ga 'ya'yansa da tausayin Yahweh ga masu girmama shi.
Sa'ad da Yahweh ya yi halitan Adamu mutum na farko ya yi halita shi ne daga ƙura. AT: "yana tuna cewa yayi halitan mu daga ƙura"
Cikin wannan tamka, tsawon rayuwan mutum na kasancewa an kwatanta ta da gajerewan tsawon lokacin da ciyawa ke girma kafin ta mutu.AT: "Tsawon rayuwan mutum gajerewa ne kamar na ciyawa"
Cikin wannan tamka, yadda mutum yana yi girma bisan lokaci an kwatanta da yadda fure ke yin girma.
Wadannan jimla na ci gaba da magana game da furen da kuma ciyawa. Sun kwatanta yadda furen da kuma ciyawa su kan mutu da yadda mutu ya kan mutu. AT: "Iska ta kan hura ta kan furen da ciyawa kuma su ɓace, kuma ba wanda zai san yadda tayi girma--haka nan mutum yake"
Wannan yana nufi da cewa kauna Yahweh yana cin gaba har abada. AT: "zai ci gaba har abada"
Wadannan jimla biyu suna da ma'ana mai kamar da.
A nan mulkin Yahweh amasayi sarki na nufi da kamar yadda "kursiyinsa." AT: "Yahweh ya dauka kujeransa a cikin sammai inda yana mulki kamar sarki"
Anan na nufan Yahweh da "mulkinsa" don ya jadada ƙarfin ikonsa amasayi sarki. AT: "yana mulki"
Wannan karin magana ce mai ma'ana "yi nufinsa." AT: "yi nufinsa"
"yi yabonsa cikin dukkan wuraren da ya ke mulki"
"da dukkan kaina"mko "da dukkan rai na." Wannan jimla na nufi cewa zaya yabi Yahweh da zuciya xaya kuma an yi amfani do jadada dukufansa a gare shi.
1Na bada yabo ga Yahweh da dukkan raina, Yahweh Allahna, kai mai girma ne da ƙawa; Kayi sutura da martaba da daraja.2Ka rufe kanka da haske kamar da sutura; ka shimfiɗa sammai kamar yadda ake simfiɗa labulen rumfa.3Ka shimfiɗa katakan fadodinka a kan gajimarai; ka mai da gajimarai karusanka; kana tafiya akan fika-fikan iska.4Ya mai da iskoki manzanninsa, harsunan wuta kuma bayinsa.5Ya kafa tushen duniya ba kuma zata jijjigu ba.6Ka rufe duniya da ruwa kamar sutura; ruwa ya rufe duwatsu.7Tsautawarka nasa ruwaye su janye; da jin ƙarar tsawarka sai suka gudu.8Duwatsu sun tashi, kwarurruka kuma suka bazu zuwa wuraren da ka shirya masu.9Ka yi masu iyakar da ba zasu tsallake ba; ba zasu ƙara rufe duniya ba.10Yasa maɓuɓɓugan ruwa su gudana zuwa kwarurruka; maɓulɓulan sun kwarara tsakanin duwatsu.11Suna bayar da ruwa ga dukkan dabbobin saura; jakunan jeji a wurin ne suke kashe ƙishinsu.12A bakin kogunan ruwa tsuntsaye suka yi sheƙunansu; suna raira waƙa a cikin rassa.13Ya shayar da duwatsu daga ruwansa ya kafa kursiyinsa a sammai. Duniya ta cika da 'ya'yan aikinsa.14Yasa ciyawa ta fito domin dabbobi da kuma tsire-tsire domin mutum ya nome ya sami abinci daga ƙasa.15Yayi inabi domin mutum yayi murna, mai kuma domin fuskarsa tayi haske, abinci kuma domin rayuwarsa.16Itatuwan Yahweh suna samun ruwa; Sidar Lebanon da ya dasa17Acan tsuntsaye ke yin sheƙunansu. Shamuwa ta mai da itacen sifurus gidanta.18Awakin jeji kuma suna zama a kan duwatsu; rimaye kuma sun mayar da ƙonƙolin duwatsu mafakarsu.19Yasa wata ya nuna lokuta; rana kuma ta san lokacin faɗuwarta.20Ka yi duhun dare lokacin da duk daji ke fitowa waje.21Sagarun zakuna kan yi gurnani domin neman abincinsu daga wurin Allah.22Lokacin da rana ta fito sai su koma suyi barci a kogunansu.23Hakanan mutane kan je waje wurin aikinsu suyi ta aiki har yamma.24Yahweh ayyukanka iri-iri guda nawa ne! Da hikima kayi su dukka; duniya ta cika maƙil da ayyukanka.25A can kuma sai teku, mai zurfi da faɗi cike da manya da ƙananan hallitu marasa ƙidayuwa,26Jiragen ruwa sukan je can, Lebiyatan kuma a can ya ke, wanda ka yi domin yayi wasa a cikin teku.27Duk waɗannan gare ka suke zuba ido domin samun abinci a kan lokaci28Lokacin da ka basu, su kan tara; lokacin daka buɗe hannunka, sukan ƙoshi.29Lokacin da ka ɓoye fuskarka, sukan shiga damuwa; in ka ɗauke numfashinsu sukan mutu su koma ƙura.30Lokacin da ka aiko Ruhunka, aka hallice su, ka kuma sabunta gefen ƙasarsu.31Dãma ɗaukakar Yahweh ta dawwama har abada; dãma Yahweh ya ji daɗin hallitarsa.32Ya dubi duniya, sai ta girgiza; yakan taɓa duwatsu suyi hayaƙi.33Zan raira yabo ga Yahweh a dukkan kwanakin raina; zan raira waƙar yabo ga Allah muddin ina raye.34Dãma tunane-tunanena su zama da zaƙi a gare shi; Zan yi murna cikin Yahweh.35Dãma masu zunubi su hallaka daga duniya, dãma miyagu su ɓace daga duniya. Ina yabon Yahweh dukkan kwanakin raina. A yabi Yahweh.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Kalma nan "mastaba " da "daraja" suna da ma'ana mai kama kuma suna jadada girman ɗaukaka Yahweh. Suna kwatanta kamar yadda Yahweh na yi sutura kamar tufafi. AT: "kana da martaba da daraja duk kewaye da kai"
An kwatanta Yahweh kamar yadda kasancewa ya rufu da haske sai ka ce hasken wani sutura ne kewaye da shi. AT: "Kana rufe cikin haske" ... Anan an kwatanta Allah kamar yadda ake shimfiɗa sammai kamar da wani yakan shimfiɗa alfarwa sa'ad da ana kafa ta. AT: "ka shimfiɗa sammai kamar wani ya kafa alfarwa"
"Ka gina babba dakunanka a cikin sammai." Wannan yana nufi da gidansa na da tsayi sosai da ke daɓe na sama shimfiɗe cikin girgije.
Zai yiwu ma'ana sune 1) ya sa iska ya iya kawo sako kamar manzo, "Ya mai da iskoki su zama kamar manzanninsa" ko 2) "Ya mai da Manzanninsa masu sauri kamar iska"
Zai yiwu ma'ana sune 1) "yana sa harsunan wuta su zama kamar bayinsa." Yana sa wuta su yi masa hidima kamar yadda bawa zai yi" ko 2) "yana mai da bayinsa su zama kamar harsunan wuta " kuma
Ana iya bayyana wannan ta wurin nuna bayyani daga layi wanda ya rigaya. AT: " Ya yi harsunan wuta kuma bayinsa"
A nan jimla "kafa tushen" na nufi "halita." AT: "Ya halita dukkan duniya."
A nan an kwatanta ruwa da rufe duniya yadda babban sutura na iya rufe wani abu gabaki daya. AT: "Ka rufe duniya da ruwa gabaki daya"
Waɗannan jimla biyu na da ma'ana kuma na amfanu tarento jadada yadda Allah yana magana da ruwaye tafi daga nan.
"ritaya" ko "koma baya"
A nan marubucin zabura yana magana game da ruwaye da ke janye sai ka ce suna gudu ne kamar daba bayan jin muryan Yahweh. Kalma "gudu" na nufi a yi gudu daga nan da sauri. AT: "ruga daga nan"
Anan marubucin zabura na magana da Allah na haddasa duwatsu da kwarurruka su gusar da kuma su canza sai ka ce suna zabi gusar da kansu. An kwatanta su ne domin a jadada ikon Allah.
A nan marubucin zabura na magana na haddasa iyakar ruwaye da ba zasu tsalleke ba wanda ya halita domin su sai ka ce ruwaye da kansu sun zaba da ba zasu tsalleke ta ba. An kwatanta su haka don a jadada iznin Allah bisan su. AT: "iyakar domin su da ba su iya tsalleke ba"
"layi" ko "mararraba"
Kalma "su" na nufi da ruwaye.
karamin kogi
Ana iya bayyana a fili cewa sun kashe ƙishinsu ta wurin shan ruwa. AT: "jakunan jeji suna shan ruwan domin su kashe ƙishinsu"
ƙasan da ke baki kogi
A nan Dauda ya kwatanta chirping tsuntsaye sai ka ce suna waka ne. AT: "suna shirp a cikin rasan itace"
Wannan na nufi cewa Allah yana sa ta ta yi ruwan sama. An kwatanta ruwayen kamar suna zaune cikin shirayin a cikin sama. AT: "Ya shayar da duwatsu ta wurin sa ruwan sama ta faɗi daga sama"
"kyau abubuwa masu yawa da ya halita" (UDB)
Kalmomin wanda aka rasa zai yiwu a kara su. AT: "kuma ya yi tsire=tsire domin mutum ya nome"
Ana iya bayyana wannan a cikinfom na aiki. AT: "Yahweh na yin yalwa tanadi na ruwan sama domin itatuwansa"
Suna yi sheƙunansu cikin itatuwan sidar. Ana iya bayyana wannan sarai. AT: "Tsuntsaye sun yi sheƙunansu cikin itatuwan sidar"
Wannan iri tsuntsu ce. AT: "tsuntsu" ... Rimaya ƙarami dabba ne da ke kamar da dabba mai gurgurawa. AT: "wata irin dabba ta su ta Turai na dutse"
Wannan kalma na nufi yanayin iska dabam dabam da ke canje-canje a cikin shekara. waɗansu wurare na damina kuma da rani, yayin da wasu na lokacin bazara, zafi, faɗuwa ko ruwa, da sanyi.
A nan Dauda ya bayyana rana sai ka ce ta san lokacin rana ta yau. AT: "ya yi rana ta faɗi a lokacin ta"
"Yahweh, ka yi." Anan mawallafa sun canza daga yin magana game da Yahweh da yin magana da shi.
Wannan shine daba da ke abinni ne ga wani daba.
"amma su kan dogara ga Allah domin tanadi abinsu"
"koma baya" ko "tafi daga nan"
gidajen na waɗansu dabbobi masu shayarwa
A nan Dauda ya bayyana adadin abubuwan da Yahweh ya halita sai ka ce su dã ruwa ne da ta cika maƙil daga ganga. AT: "an cika ta da aikinka!"
"ta cika maƙil"
"Abin da ba za a iya kirgawa ba"
Wannan na nufi halitun dukkan girma dabam.
"Jiragen ruwa sukan yi tafiya a kan tẽku"
"Duk waɗannan halitu" ... "ba su abincisu sa'ad da suke bukatan ta"
Zai zama da taimako a bayyana ta cewa abinci ne a ba da. AT: "Lokacin da ka basu abinci, sun tara ta"
Wannan ya bayyana Yahweh kamar yadda buɗe hannunsa domin ba da abinci zuwa ga halitu. AT: "sa'ad da ka buɗe hannunka domin ciyad da su"
Wannan na nufi cewa Yahweh ba ya duba su ko mai da hankali akan su. AT: "sa'ad da ba ka duba su ba" ko "sa'ad da ka yi watsi da su"
Wannan na nufi cewa jikinsu ya rube sun kuma sake zama kasa. AT: "jikinsu ya rube sun kuma koma kasa"
Wannan yana nufin da Ruhunsa da ke kasancewa an aika ya ba da rai ga halittu.
"ka sa kasan ta zama cike da sabon rai"
Yana kwatanta tunane-tunanensa da wani abu da ke da dandano zaƙi. AT: "tunane-tunanena su zama da jin daɗi
"ɓacewa" ... Jimlan "miyagu" yana nufin da miyagun mutane. AT: "zai yiwu miyagu mutane su ɓace"
1Ku bada godiya ga Yahweh, ku kira bisa sunansa; ku sanar da ayyukansa cikin al'ummai.2Ku raira gare shi, ku raira yabbai gare shi; kuyi maganar dukkan ayyukansa na ban mamaki.3Kuyi taƙama cikin sunan sa mai tsarki; bari zuciyar waɗanda ke biɗar Yahweh ta yi farinciki.4Ku biɗi Yahweh da ƙarfinsa kuma; ku biɗi bayyanuwarsa ba fasawa.5Ku tuna da abubuwan ban mamaki da yayi, al'ajibansa da kuma dokoki daga bakinsa,6ku zuriyar Ibrahim bawansa, ku mutanen Yakubu, zaɓaɓɓunsa.7Shi ne Yahweh, Allahnmu. Dokokin sa suna bisan dukkan duniya.8Cikin ransa yana ajiye alƙawarinsa har abada, maganarsa da ya umarta domin dubun tsararraki.9Yana tunawa a cikin ransa alƙawarin da yayi da Ibrahim da kuma rantsuwarsa ga Ishaku.10Wannan ne abin da ya tabbatar wa Yakubu a matsayin farilla da Isra'ila a matsayin madawwamin alƙawari.11Ya ce, "Zan baku ƙasar kan'ana a matsayin kasonku na gãdonku."12Ya faɗi wannan sa'ad da suke kaɗan a lissafi, 'yan kima sosai, kuma suna baƙi a ƙasar.13Suka tafi daga al'umma zuwa al'umma kuma daga masarauta zuwa wata.14Bai bar wani ya tsananta masu ba; ya tsautawa sarakuna sabili da su.15Ya ce, "Kada ku taɓa shafaffuna, kada kuma ku yi lahani ga annabawana."16Yayi kira domin yunwa bisa ƙasar; ya yanke dukkan biyan buƙatar gurasa.17Ya aika da mutum gaba da su; Yosef a ka sayar da shi a matsayin bawa.18Aka ɗaure ƙafafunsa da sarƙoƙi; a bisa wuyansa aka sa maɗaurin ƙarfe,19har sai lokacin da maganganun sa suka zama gaskiya, kuma maganar Yahweh ta gwada shi.20Sarki ya aika da bayi su sake shi; shugaban mutanen ya 'yantar da shi.21Ya sanya shi lura da gidansa a matsayin shugaban dukkan mallakarsa22ya bayar da umarni ga shugabanninsa yadda ya so ya kuma koyar da dattawansa hikima.23Daga nan Isra'ila ya zo cikin Masar, Yakubu kuma ya zauna na wani lokaci a cikin ƙasar Ham.24Yahweh yasa mutanen sa suka yi 'ya'ya, ya kuma sa suka yi ƙarfi fiye da maƙiyansu.25Ya kuma sa maƙiyansa suka ƙi Jinin mutanensa, suka muzguna wa bayinsa.26Ya aika da Musa, bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.27Suka aikata alamunsa a tsakiyar masarawa, al'ajibansa a ƙasar Ham.28Ya aika da duhu ya maida ƙasar duhu, amma mutanen ta basu yi biyayya da umarninsa ba.29Ya maida ruwansu ya zama jini ya kuma kashe kifinsu.30Ƙasar ta cika da gungun kwaɗi, har ma cikin ɗakunan shugabanninsu.31Yayi magana, kuma gungun ƙudaje da ƙwari suka zo cikin dukkan ƙasar.32Ya maida ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da wuta mai ci balbal bisa ƙasarsu.33Ya lalata kuringun inabinsu da itatuwan ɓaurensu; ya karya itatuwan ƙasarsu.34Yayi magana, fãri suka zo, fãri masu yawan gaske.35Fãrin suka cinye dukkan ganyayyaki a ƙasar; suka cinye dukkan amfanin gona.36Ya kashe kowanne ɗan fãri a cikin ƙasar, 'ya'yan fãrin dukkan ƙarfinsu.37Ya fito da Isra'ilawa tare da azurfa da zinariya; babu wani cikin kabilunsa da yayi tuntuɓe a hanya.38Masar ta yi farinciki da suka tafi, domin masarawa sunji tsoronsu.39Ya shimfiɗa girgije a matsayin abin rufa ya kuma yi wuta ta haskaka dare.40Isra'ilawa suka yi roƙon abinci, ya kuma kawo makwarwa ya kuma ƙosar da su da gurasa daga sama.41Ya fasa dutse ruwa kuma ya ɓulɓulo daga gare shi; ya malala cikin jeji kamar kogi.42Domin ya tuna a ransa da alƙawarin sa mai tsarki wanda yayi wa Ibrahim bawansa.43Ya bida mutanen sa suka fita da farinciki, zaɓaɓɓunsa da sowace-sowace fiye da gaban masu nasara.44Ya basu ƙasashen al'ummai; suka ɗauki mallakar dukiyar mutanen45domin su kiyaye farillansa su kuma yi biyayya da shari'unsa. A yabi Yahweh.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Hebraniyawa.
A nan "suna" na wakilcin Yahweh. AT: "ku kira gare shi ... Kuyi taƙama cikin Yahweh"
Wannan na nufi da mutane da ke cikin al'ummai. AT: "mutane cikin al'ummai"
A nan "zuciyar" na wakilcin mutum wanda ke neman Yahweh. AT: "bari mutane da ke neman Yahweh su yi farinciki"
A "neman ƙarfin Yahweh" na nufi a roki shi ya ƙarfafa shi. AT: "
Zai zama da taimako a kara da kalmomin wanda aka rasa. AT: "tuna da al'ajibansa da kuma"
A nan "baki" na nufi da abubuwan da ya yi magana. AT: "dokoki da ya riga ya yi magana"
Mawallafi ya yi magana da Isra'ilawa, na kiran su da waɗannan sunaye.
Waɗannan jimka biyu sun yi kama a ma'ana kuma ana amfani da su tare domin jadadawa. Kalma "magana" na nufi da alƙawari. AT: "Yana ajiye a ransa alƙawarinsa har abada, alƙawari da yi"
Wannan na nufi a tuna da kuma a yi tunani game da wani abu. AT: "tuna da"
1,000 tsararraki"
Jimla nan "tunawa a cikin ransa" na nufi a tuna da wani abu. AT: "yana tuna da"
Waɗannan jimla dukka biyun su "alƙawarin" da "rantsuwar" suna nufi alƙawari ɗaya da Yahweh ya yi ga mutanensa.
Tana iya zama da taimako a kara kalmomi da aka rasa. AT: "rantsuwarsa da ya ba wa Ishaku"
Marubucin zabura na rubutawa game da Isra'ila.
Tana nuna cewa "kasan" na nufi da Kan'ana. AT: "kuma suna baƙi a cikin ƙasar Kan'ana"
"Sun cigaba da yin yawo"
Waɗannan jimla biyu suna da ma'ana masu kama kuma suna amfani tare domin jadadawa.
Marubucin zabura na rubutawa game da Isra'ila.
"sabili da kan su." Wannan na nufi da Isra'ila.
A nan "taɓa" na nufin lahani, tana nan karin azama ce Yahweh ya yi amfani ya kara ƙarfafa gargaɗinsa da ba zai yi wa mutanensa lahani ba. AT: "Kada ku yi wa mutane da na shafe lahani ba"
"Ya aika." Wannan na nufi da sa yunwan ta faru cikin kasar.
A nan "gurasa" na nufin da abinci cikin na duka. AT: "dukkan biyan buƙatar abinci"
Zai zama da taimako a bayyana ta cewa ya aike shi gaban da su zuwa Masar.AT: "Ya aika da mutum gaban da su zuwa Masar; ya aika da Yosef wanda"
Ana iya bayyana wannan a cikin fom na aiki. AT: "'Yan'uwa Yosef sun sayar da shi a matsayin bawa"
ƙarfe na hani da ake amfani don daure wuyar hannu na fursunoni ko idanun sãwu biyu tare
Waɗannan kalamai za a iya sake bayyani kamar mai yi. AT: "Masarawa sun ɗaure ƙafafunsa da sarƙoƙi; sun sa maɗaurin ƙarfe a bisan wuyansa.
A nan "maganar" na nufi da sakon Yahweh. AT: "sakon Yahweh ta gwada shi"
Waɗannan jimla biyu na da ma'ana daya mafi muhimmanci kuma suna yi amfani tare don jadada cewa tsarkin ya sake Yosef.
A nan "Isra'ila" na nufi da Yakubu. Yakubu har ila yau ya kawo iyalinsa tare da shi. AT: " Daga nan Isra'ila kuma da iyalinsa sun zo cikin Masar"
Marubuci yana magana game da karuwan Isra'ila sai ka ce su tsiro da su kan ba da 'ya'ya itace masu yawa. "Allah na kara lambar mutanensa kwarai"
"suka ƙi mutanensa kuma suka muzguna wa bayinsa"
Waɗannan jimla biyu na da ma'ana daya mafin muhimmanci kuma suna yi amfani tare domin jadadawa. AT: "Musa da Haruna suka aikata mu'ujizai na Allah cikin Masar atsakanin zuriyar Ham"
Za a iya kara kalmomin da aka rasa. AT: "kuma suka aikata al'ajibansa"
"ya maida sararin sama duhu"
karami halitan mai rarrafe mai yin tsalle
"suna nan har ma cikin ɗakunan shugabanninsu"
Marubucin zabura ya cigaba da bayyana hukuncin Yahweh a bisan Masar.
babban kungiyoyin masu tashiwa sama ... kanana kwari masu tashiwa sama kamar ƙudaje amma karami ... kankara da ke faɗi daga tsararrin sama kamar ruwan sama
Allah ya sa kankara, ruwan sama, da walkiya su lalata kuringun inabinsu da itatuwan. AT: "Ya sa ta hallaka ... kuma ta karye"
"akwai fãri masu yawan gaske"
Waɗannan jimla biyu suna da ma'ana daya mafin muhimmanci kuma suna yi amfani tare domin jadadawa. AT: "Kwarin sun cinye dukkan tsire-tsire da kuma dukkan amfanin gona kasar"
A nan jimla na biyu game da "'ya'yan farin" an yi amfani a bayyana "ɗan fari" a cikin jimla na farko. AT: "Ya kashe kowanne ɗan fari a cikin kasar, wanda sune 'ya'yan farin na dukkan ƙarfinsu" ko "Sa'an nan Yahweh babban yaro a cikin kowanne gida na mutane Masar"
A lokacin da Isra'ilawa suka bar Masar sun ɗauki azurfa da zinariyan tare da su. AT: "Ya fito da Isra'ilawa daga Masar tare da azurfa da zinariya cikin mallakansu"
Ba wanda aka bari a baya. Ana iya bayyana wannan gaskiya ma AT: "dukkan kabilunsa son iya yin tafiya"
A nan marubucin zabura yana bayyana Yahweh na ajiye girgije cikin tsararrin sama sai ka ce yana shimfiɗa tufa a waje. Girgijen "abin rufa" ne don ta kare su daga rana. AT: "Ya ajiye girgije cikin tsararrin sama ta kare su daga zafin rana"
Yahweh ya ajiye ginshikin wuta a cikin tsararrin sama ta bayar da haske cikin dare. AT: "Ya ajiye wuta a tsararrin sama ta kaskaka dare"
Zai zama da taimako a yi bayyana cewa makwarwa kanana tsuntsaye ne da Yahweh ya aika domin su ci. AT: "kuma Yahweh ya aika da kanana tsuntsaye su ci"
Yahweh ya sa manna, irin gurasa, da ta faɗi daga tsararrin sama. AT: "da gurasa da ta faɗi daga tsararrin sama"
"ruwan ya malala
Wannan na nufi tuna da. AT: "tuna"
Waɗannan jimla biyu suna da ma'ana daya mafin muhimmanci kuma suna da amfani tare don jadada cewa mutanen Allah suna da farinciki sa'ad da ya bida su daga Masar. Mutanen suna ta ihu na farinciki. AT: "Ya bida zaɓaɓɓun mutanensa da ihun farinciki da nasara"
A nan "zaɓaɓɓe" na nufin da zaɓaɓɓen Yahweh. AT: "zaɓaɓɓe mutanensa" ... "biki" ko "farinciki"
Waɗannan jimla biyu suna da ma'ana daya mafin muhimmanci kuma suna da amfani tare domin jadadawa. "Ajiyewa" farillansa na nufi a yi biyaya da su. AT: "yi biyaya da umurnensa da farilansa"
1A yabi Yahweh. A bada girma ga Yahweh, domin shi nagari ne, domin alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.2Wa zai lissafa manyan ayyukan Yahweh ko yayi cikakken shelar dukkan ayyukansa da suka cancanci yabo?3Masu albarka ne waɗanda suke yin abin dake dai-dai, waɗanda kuma a koyaushe ayyukansu baratattu ne.4Ka tuna dani a rai, Yahweh, sa'ad da ka nuna tagomashi ga mutanenka; ka taimake ni sa'ad da ka cece su.5Daga nan zan ga wadatar zaɓaɓɓun ka, in yi farinciki cikin murnar ƙasarka, da ɗaukaka tare da gãdonka.6Mun yi zunubi kamar Kakanninmu; mun yi laifi, mun kuma aikata mugunta.7Ubanninmu basu yaba wa ayyukanka masu ban mamaki ba a Masar; suka yi banza da ayyukanka masu yawa na alƙawarin aminci; suka yi tawaye a bakin teku, Tekun Iwa.8Duk da haka, ya cece su domin sunansa saboda ya bayyana ikonsa.9Ya tsautawa Tekun Iwa, ya kuwa bushe. Daga nan ya bida su ta cikin zurfafan, kamar ta cikin jeji.10Ya cece su daga hannun waɗanda suka ƙi su, ya kuma ƙwato su daga hannun maƙiyansu.11Amma ruwayen suka rufe magaftansu; babu wanin su da ya tsira.12Daga nan suka gaskata maganganunsa, kuma suka raira yabonsa.13Amma nan da nan suka manta da abin da yayi; ba su jira umarninsa ba.14Suka yi kwaɗayi marar ƙosarwa a jeji, kuma suka ƙalubalanci Allah a cikin hamada.15Ya basu abin da suka roƙa, amma ya aika da cuta wadda ta cinye jikkunansu.16A sansanin suka zama masu kishin Musa da Haruna, firist mai tsarki na Yahweh.17Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta kuma rufe mabiyan Abiram.18Wuta ta ɓarke a tsakaninsu; wutar ta cinye mãsu mugunta.19Suka yi maraƙi a Horeb suka kuma yi sujada ga sarrafaffar siffar ƙarfe.20Suka musanya ɗaukakar Allah domin siffar maraƙi mai cin ciyawa.21Suka manta da Allah Maicetonsu, wanda yayi manyan ayyuka a Masar.22Yayi abubuwan ban mamaki a ƙasar Ham ya kuma yi ayyuka masu iko a Tekun Iwa.23Da ya zartar da dokar hallakar dasu, inda ba domin Musa, zaɓaɓɓensa, ya shiga tsakaninsu da shi ba ya juya fushinsa daga hallakar dasu.24Daga nan suka raina ƙasa mai bayar da amfani; ba su gaskata da alƙawarinsa ba,25amma suka yi gunaguni a rumfunansu, ba su kuma yi biyayya da Yahweh ba.26Saboda haka ya ɗaga hannunsa kuma ya rantse masu cewa zai barsu su mutu a hamada,27ya warwatsa zuriyarsu cikin al'ummai, ya kuma warwatsa su cikin bãƙin ƙasashe.28Suka yi sujada ga Ba'al na fowa suka kuma ci hadayun da a ke miƙawa ga matattu.29Suka cakune shi ya yi fushi da ayyukansu, annoba kuwa ta faso a tsakaninsu.30Daga nan Fenihas ya tashi ya kai ɗauki, annobar kuwa ta tsagaita.31Aka lissafa masa shi a matsayin aikin adalci ga dukkan tsara har abada.32Suka kuma ba Yahweh haushi a ruwayen Meriba, Musa kuma ya sha wahala saboda su.33Suka sa Musa ya ji haushi, ya kuma yi magana da fushi.34Basu hallakar da al'ummai ba kamar yadda Yahweh ya dokace su,35amma suka gauraye da al'ummai suka kuma koyi hanyoyinsu36kuma suka yi sujada ga gumakansu, waɗanda suka zamar masu tarko.37Suka yi hadayar 'ya'yansu maza da 'ya'yansu mata ga aljanu.38Suka zubar da jini marar laifi, jinin 'ya'yansu maza da 'ya'yansu mata, waɗanda suka yi hadaya dasu ga gumakan Kan'ana, suka ƙazantar da ƙasar da jini.39Suka ɓãci da ayyukansu; cikin ayyukansu suka zama kamar karuwai.40Saboda haka Yahweh ya yi fushi da mutanensa, ya kuma rena nasa mutanen.41Ya bayar dasu cikin hannun al'ummai, waɗanda kuma suka ƙi su suka yi mulki a kansu.42Maƙiyan su suka tsananta masu, aka kuma kawo su ƙarƙashin hukuncinsu.43Lokutta da yawa yazo ya taimake su, amma suka ci gaba da yin tawaye aka kuma kawo su ƙasa ta wurin zunubinsu.44Duk da haka, ya lura da ƙuncin su sa'ad da ya ji kukansu domin taimako.45Ya tuna a ransa da alƙawarin sa tare dasu ya kuma yi jinkiri saboda matuƙar ƙaunarsa.46Ya sa dukkan waɗanda suka yi nasara dasu suka ji tausayin su.47Ka cece mu, Yahweh, Allahnmu. Ka tattaro mu daga cikin al'ummai domin mu ba da godiya ga sunan ka mai tsarki mu kuma yi ɗaukaka cikin yabban ka.48Bari Yahweh, Allah na Isra'ila, ya sami yabo daga matuƙa zuwa matuƙa. Dukkan mutane sukace, "Amin." A yabi Yahweh. Littafi na Biyar
Ana samun daidaici waƙoƙin Ibraniyawa.
Mawallafi ya yi wannan tambaya don yabon Allah kuma baya jiran amsar. AT: "Ba wanda zai iya lissafa manyan ayyukan Yahweh ... ayyukansa."
"ayyukkansa da suka cancanci yabo"
Jimla nan "tunawa" na nufi a tuna da wani abu. AT: "tuna da ni"
Kalman "zaɓaɓɓe" na nufin da zaɓaɓɓun mutanen Yahweh" AT: "zaɓaɓɓun mutanenka"
Waɗannan abubuwa da Dauda ya fada zaya yi, tare da "ganin wadata na zaɓaɓɓunka." Za a iya kara kalmomin da aka rasa. AT: "Zan yi farinciki cikin murnar ... kuma zan yi ɗaukaka"
A nan jimla "gãdonka" na nufin Isra'ilawa, waɗanda suke zaɓaɓɓun mutanen Yahweh. Anan "ɗaukaka" na nufi "a yi alfahari game da" wani abu; a cikin wannan hali suna yin alfahari game da Yahweh. AT: "yi alfahari da girman ka da mutanenka"
"basu gõde ba domin ayyukanka masu ban mamaki da da ka yi"
Waɗannan jimla biyu suna nufin da teku daya. Na biyun suna tekun ne.
"Tukuna" ko "ko da don haka"
A nan "sunansa" na nufi da Yahweh. AT: "saboda sunan mallakarsa"
A nan Dauda ya kwatanta yadda Yahweh na bida Isra'ilawa ta cikin tekun iwa da yadda za a iya bida mutane ketare busasshen ƙasa na jeji. "Zurfafan" na nufin da kogin da yake bayyana bayan da Yahweh raba ruwayen. AT: "a cikin tekuna iwa da akan busasshen ƙasa"
Waɗannan jimla biyu na nufi abu daya mafi muhimminci kuma suna da amfani tare don jadada cewa Yahweh ya cece su daga maƙiyansu.
A nan "hanu" na nufin iko ko kula da. AT: "Ikon waɗanda suka ƙi su"
Wannan shine hanyar magana da ladabi game da suke nitsewa a cikin ruwa. AT: "nutsad da abokan gabansu"
A nan kalma "su" na nufin da magabatansu" kuma kalman "sa" na nufin da "Yahweh".
Tana nuna cewa sun yi abubuwa ba tare da jiran su gani abin da Yahweh ya so su yi. AT: "sun yi abubuwa da ba tare da jiran umurnin Yahweh da farko ba"
"kwaɗayi da ba za a iya gamsuwa ba"
"Suka yi tawaye ga Allah"
A nan Dauda yana magana game da Yahweh ya sa mutane cikin bala'i ta cuta sai ka ce Yahweh aikar da cuta gare su ta hanya daya da wani yana aika da mutu ko manzo. AT: "amma ya sa cuta ta cinye jikkunansu"
A nan yadda ƙasa ta duɗe kuma ta binne mutanen an kwatanta ta ce da yadda halita ya kan haɗiye wani abu. AT: "Duniya ta buɗe kuma ta binne"
Waɗannan sune ma'aikacin waɗanda sun yi tawaye da Musa.
Mabiyan Abiram su ma an binne su sa'ad da duniya ta buɗe kuma ta binne Datan. AT: "ta kuma rufe mabiyan Abiram" ko "ta kuma binne mabiyan Abiram"
Waɗannan jimla biyu suna nufin abu daya kuma an rubuta su tare don a jadada yadda miyagun mutane da an kashe ta wurin wuta.
Wannan bayyani za'a iya canji don sake shiryawa domin ta zama da saukin ganewa cewa maraƙi sarrafaffar siffar ƙarfe ne. AT: "A Horeb, suka yi sarrafaffar siffar ƙarfe na ɗan maraƙi suka kuma yi mata sujada"
Wannan na nufi cewa maimakon yi wa Allah sujada suka yi sujada ga siffar maraƙi mai cin ciyawa. AT: "Suka musanya yin sujada ga ɗaukakar Allah da yin sujada ga siffar maramai cin ciyawa"
A nan Allah yana nufin da ɗaukakarsa. AT: "daraja Allahnsu" ko "Allah wanda yana daraja"
Wannan na nufin da ƙasar inda zuriyar Ham suka zauna. AT: "a ƙasar inda zuriyar Ham ke zama"
"abubuwan madalla"
A nan Dauda ya yi magana game da Musa lallashe Yahweh ka da ya hallakar da Isra'ilawa kamar yadda ya shiga tsakaninsu da shi. AT: "tsaya tsakanin Yahweh da Isra'ilawa kuma ya roki Yahweh don ka da ya hallaka su"
"yi kuka"
Wannan na nufin da alƙawarin Yahweh cewa zaya bar su su ɗauka ƙasar Kan'anaan kamar mallakarsu.
Kalman "sa" na nufin da Yahweh. Har ila yau, ta na al'ada ne a ɗaga hannu sa'ad da za'a yi rantsuwa.
Waɗannan jimla biyu suna da ma'ana daya mafin muhimminci kuma suna amfani tare domin jadadawa. AT: "kuma cewa zaya sa zuriyar su su zauna cikin bãƙin ƙasashe"
Wannan na nufin da a watsa ko a baza wani abu a waje.
Ana iya bayyana wannan cikin fom na aiki. AT: "hadayun wanda suke miƙawa ga matattu"
"Matattun" na nufin da gumaka da allolin da Isra'ilawa suka yi sujada. AT: "ga allolin wanda suke matattu" ko "ga alloli marasa rai"
"annoba da ta bazu"
"fusatar da shi"
Fenihas ya sa baki a tsakanin mutane, hukunta su domin zunubinsu. Ana iya mai da wannan da sauƙin ganewa. AT: "Daga nan Fenihas ya tashi ya sa baki a tsakanin mutanen saboda zunubinsu"
Ana iya bayyana wannan cikin fom na aiki. AT: "Mutane suka sanya masa shi a matsayin aikin adalci"
Wannan wuri ce.
Musa ya sha wahala saboda zunubin mutanen. Anan kalma "su" wakilin suna ne domin mutane da kuma metonym ne dake magana game da zunubinsu. AT: "sha wahala saboda ayyukansu"
A nan Dauda yana magana game da mutane da ke aurayya da mataye daga sauran al'ummai kamar yadda gauraye da su. AT: "amma suka gauraya cikin aure da sauran al'ummai"
Gumakan suka zamar masu tarko.
Jimlan "zubar da jini" siffatawa kalma kamar "euphemism"
Ana iya bayyana wannan cikin fom na aiki. AT: "Ayyukan ta kazantar su"
A nan Dauda ya kwatanta rashin bangaskiyar su ga Yahweh da rashin bangaskiyar na karuwai. AT: "suna da rashin imani ga Yahweh kamar karuwai"
"Saboda haka Yahweh ya yi fushi da mutanensa kuma ya tsanansu
A nan "hannu" na nufin iko ko mulki. AT: "Allah ya bar al'ummai su ɗauki mulki a kan su"
"mutane wanda suka ƙi su"
Ana iya bayyana wannan cikin fom na aiki. AT: "maƙiyan su kuma suka sa su ƙarƙashin hukuncinsu"
A nan jimlan "kawo ƙasa" na nufi da hallaka. Har ila yau, wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "zunubinsu ta halakani su"
"Tukuna" ko "ko da don haka." Dubi yadda ka fassara wannan a 106:8. ... "masifansu" ko "wahalarsu"
Jimlan "tuna a ransa" na nufi da tunawa da wani abu. AT: "tuna da"
"ya kuma ji tausayin su"
"waɗanda suka kama su." Wannan na nufin da abokan gaba Isra'ilawa waɗanda suka dauka su fursuna. ... "an zama da tausayi a kan su"
A nan 106:48 ya fi karshen wannan zabura. Ta zama rufen bayyani domin dukkan litafin 4 na Zaburan, wanda tana farawa dafa Zabura 90 ta kuma kare da Zabura 106.
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Bari mutane su yabi Yahweh Allahn Isra'ila"
A nan an kira Yahweh da "tsarki sunansa." AT: "gare ka"
Wannan na nufin matuka biyu da kuma ma'ana domin dukkan lokaci. Dubi yadda ka fassara wannan a 41:13. AT: "domin dukkan abada abadin"
1Ku ba da godiya ga Yahweh, domin shi nagari ne, kuma alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.2Bari fansassun Yahweh suyi magana, waɗanda ya cafko daga hannun maƙiyi.3Ya tattaro su daga bãƙin ƙasashe, daga gabas daga kuma yamma, daga arewa daga kuma kudu.4Suka yi yawo a jeji bisa hanyar hamada ba su kuma sami birnin da zasu zauna ba.5Saboda sunji yunwa da ƙishi, suka some cikin gajiya.6Daga nan suka yi kira ga Yahweh cikin damuwarsu, ya kuma ceto su daga ƙuncinsu.7Ya bida su ta miƙaƙƙen tafarki saboda su tafi cikin birnin da zasu zauna.8Da ma mutane su yabi Yahweh domin alƙawarin amincinsa domin kuma abubuwan ban mamaki da yayi domin 'yan adam!9Domin ya biya buƙatun begen masu jin ƙishi, da marmarin masu jin yunwa ya cika da abubuwa masu kyau.10Waɗansu suka zauna cikin duhu da ɓoyewa, 'yan kurkuku cikin ƙunci da sarƙoƙi.11Wannan kuwa saboda sun yi tawaye gãba da maganar Yahweh suka kuma yi watsi da umarnin Maɗaukaki.12Ya ƙasƙantar da zukatansu ta wurin shan wuya; suka yi tuntuɓe kuma babu wanda zai taimake su ya ɗaga su.13Daga nan suka yi kira ga Yahweh a cikin damuwarsu, ya kuma fito dasu daga cikin ƙuncinsu.14Ya fito dasu daga cikin duhu da ɓoyewa ya kuma karya karkiyarsu.15Dãma mutane su yabi Yahweh domin alƙawarin amincinsa domin kuma abubuwan ban mamaki da ya yi domin 'yan adam!16Domin ya karya ƙofofin tagulla ya kuma datse ginshiƙan ƙarfe.17Sun yi wawanci a cikin hanyoyinsu na tawaye suka kuma ƙuntata saboda zunubansu.18Marmarinsu na cin abinci ya ɓace, suka kuma zo kusa da ƙofofin mutuwa.19Daga nan suka yi kira ga Yahweh a cikin damuwarsu, ya kuma fito dasu daga cikin ƙuncin su.20Ya aika da maganarsa ya warkar da su, ya kuma ceto su daga hallakarsu.21Dãma mutane su yabi Yahweh domin alƙawarin amincinsa domin kuma abubuwan ban mamaki da yayi domin 'yan adam!22Bari su miƙa hadayun godiya su kuma yi shelar ayyukansa cikin waƙa.23Waɗansu suka yi tafiya bisa teku cikin jiragen ruwa suka kuma yi sana'o'i bisa tekuna.24Waɗannan sun ga ayyukan Yahweh da al'ajibansa bisa tekuna.25Domin ya bada umarni ya kuma zuga iskar guguwa dake motsa tekuna.26Suna kaiwa ga sararin sama; su tafi ƙasa cikin zurfafa. Rayuwar suna narkewa cikin ƙunci.27Suna gushewa suyi tangaɗi kamar bugaggu waɗanda kuma suka kawo ga ƙarshen iyawarsu.28Daga nan suka yi kira ga Yahweh cikin damuwarsu, ya kuma fito dasu daga cikin ƙuncinsu.29Ya tausar da guguwar, kuma raƙuman suka yi tsit.30Daga nan suka yi farinciki saboda tekun ya tausu, ya kuma kawo su in da suke so su sauka.31Dãma mutane su yabi Yahweh domin alƙawarin amincinsa domin kuma abubuwan ban mamaki da ya yi domin 'yan adam!32Bari su ɗaukaka shi a cikin taron mutane su kuma yabe shi a majalisar dattawa.33Ya maida koguna suka koma jeji, maɓulɓulan ruwa suka koma busasshiyar ƙasa,34da ƙasa mai bada 'ya'ya zuwa bakararen wuri saboda muguntar mutanenta.35Ya maida jeji kuma ya zama tafkin ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulan ruwa.36Ya wadatar da masu jin yunwa a wurin, suka kuma gina birni su zauna a ciki.37Suka gina birni su dasa gonaki a ciki, su dasa garkunan inabi, su kuma kawo yalwar kaka.38Ya albarkace su suka zama fiye da lissafi sosai. Bai bar garken dabbobinsu ba su ragu a lissafi.39Suka ragu aka kuma ƙasƙantar dasu ta wurin ƙunci mai zafi da wahala.40Ya zubo raini bisa shugabanninsu yasa kuma suka yi yawo cikin jeji, in da babu hanyoyi.41Amma ya kiyaye mabuƙata daga ƙunci ya kuma lura da iyalinsa kamar garken tumaki.42Masu adalci zasu dubi wannan suyi farinciki, dukkan mugunta kuma ta rufe bakinta.43Duk mai hikima ya yi la'akari da waɗannan abubuwa ya kuma yi tunani bisa ayyukan Yahweh na alƙawarin aminci.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
"Fansassun" na nufin da mutane wanda Yahweh ya ceta. AT: "waɗanda Yahweh ya ceta"
A nan "hannu" na nufin da iko. AT: "daga ikon maƙiyi"
A nan umarnai hudu nan an bayar da su ne don a jadadacewa ya tara su ne daga ko'ina. AT: "daga kowane umurni" ko "daga kowane sashi na duniya"
"Wasu mutane suka yi yawo" ... "bisa kan hanyar da ke cikin hamada" ... "da zasu iya zauna a cikin"
Tana nuna cewa suna yin addu'a ga Yahweh domin zaya taimaki su. AT: "Sa'an nan suka yi addu'a ga Yahweh don ya taimake su cikin damuwarsu"
"matsaloli" ko "bala'i"
"Bari mutane su yabi Yahweh domin ya kaunace su da aminci" ko "Ya kammata mutane su yabi Yahweh domin amincin kaunansa." Anan kalman "Ma" an yi amfani da shi a sad da da marmari mai karfi domin mutane su yabe shi.
"Domin yana bada ruwa ga masu marmarin ta--ga masu ƙishi"
"kuma ga masu jin yunwa sosai da kuma marmarin abinci, ya ba su abubuwan masu kyau su ci"
Duka biyu "duhu" da "ɓoyewa" suna da ma'ana daya mafin muhimmanci kuma ana yin amfani don a jadada yadda duha da kurkuku yake. AT: "cikin cikaken duhu"
Waɗannan jimla suna da ma'ana mai kama da kuma suna jadada yadda suka yi tawaye da Allah, wanda shine abin da ya sa aka ɗaure su cikin kurkuku.
A nan zuciyan tana wakiltar mutum, amma musamman son ransa. AT: "Ya ƙasƙantar da su ta wurin barin su su sha wuyan wahala"
Kalman "tuntuɓe" na nufin da lokacin sa'ad da mutane samu kan su cikin yanayi mai wuya. AT: "suka shiga cikin damuwa kuma babu wanda zai taimake su fita cikin ta"
Tana nuna cewa suna yi addu'a ga Yahweh don zaya taimake su. Dubi yadda ka fassara wannan a 107:4. AT: "Sa'an nan suka yi addu'a ga Yahweh don ya taimake su a cikin damuwarsu"
"Yahweh ya fito da waɗanda ke cikin kurkuku" ... Duka "duhu" da "ɓoyewa" suna da ma'ana daya mafin muhimmanci kuma suna amfani don jadada yadda kurkuku yake da duhu. Dubi yadda ka fassara wannan a 107:8. AT: "cikaken duhu"
"Bari mutane su yabi Yahweh domin ya kaunace su da aminci" ko "Yakamata mutane su yabi Yahweh domin aminci kaunansa." Anan kalma "ma" an yi amfani da shi don sad dar da marmari mai karfi domin mutane su yabi shi. Dubi yadda ka fassara wannan a 107:8.
Duka waɗannan jimla na bayyana Yahweh yana yantacce mutanensa daga kurkuku kuma na da amfani don jadada cewa Yahweh da gaske ya yantacce. AT: "Ya yantacce mutanensa daga kurkuku"
"Sun yi wawanci a cikin hanyoyi da suka yi wa Yahweh tawaye"
"kuma suka sha wahala." Musamman an ƙuntata su ta zama da ciwo. AT: "kuma sun zama da ciwo"
A nan yanayin "mutuwa" an bayyana shi kamar yadda wuri yake, "ƙofofin mutuwa" AT: "kusa su mutu"
Tana nuna cewa suna yin addu'a ga Yahweh don zaya taimake su. Dubi yadda ka fassara wannan a 107:4. AT: "Sa'an nan suka yi addu'a ga Yahweh don ya taimake su a cikin damuwarsu"
A nan Dauda ya bayyana Yahweh na magana kaar yadda ya aika da kalmansa sai ka ce sune manzosa. Zai yiwu ma'ana sune 1) "Ya ba da umurni don su warke kuma suka warke" ko 2) "Ya karfafa su kuma sun warke"
"Bari mutane su yabi Yahweh domin ya kaunace su da aminci" ko "Yakamata mutane su yabi Yahweh domin aminci kaunansa." Anan kalma "Ma" an yi amfani da shi don sad dar da marmari mai karfi domin mutane su yabi shi. Dubi yadda ka fassara wannan a 107:8.
"wanda na nuna cewa suna da godiya"
"ta yin waƙa game da su"
Zasu tashi zuwa wurare kuma su saya su kuma sayar da abubuwa da mutane a can. AT: "sayar da abubuwa cikin birane masu nesa"
"ya umurce iska kuma ya sa ta zama babban iskar guguwa dake motsa tekun"
A nan Dauda yana bayana iska na sa taguwar ruwa su zama da tsawo sai ka ce iska shine abun dake nacewa akan motsa wani abu. AT: "dake sa taguwar ruwan teku su zama da tsawo sosai"
Wannan yana bayyana tashiwan jirage da fadowan tare da taguwar ruwa. Matukan tashiwa zuwa ga sararin da fadowa zuwa ga zurfafa ƙara azama ne don bayyana yadda mai razanawa iskar guguwa yake. AT: "jiragensu zasu tashi da tsawo sosai bisan taguwar ruwa kuma sa'an na zasu faɗi ƙasa-ƙasa sosai sakani taguwar ruwa" .
Jimla "kawo ga ƙarshen iyawarsu" na nufi cewa ba su san abin da zasu yi ba. AT: "kuma ba su san abin da zasu yi ba" ko "ba su da wani dabara abin yi"
Tana nuna cewa suna yi addu'a ga Yahweh domin zaya taimake su. Dubi yadda ka fassara wannan a 107:4. AT: "Sa'an nan suka yi addu'a ga Yahweh don ya taimake su a cikin damuwarsu"
"Ya yi iskar ta tsaya"
Wannan ana iya bayyana cikin fom na aiki. AT: "ya yi raƙuman ruwa su yi tsit"
"ya jagorace su" ... "zuwa ga tashar jiragen ruwa inda suke so su tafi"
"Bari mutane su yabi Yahweh domin ya kaunace su da aminci" ko "Yakamata mutane su yabi Yahweh domin aminci kaunarsa." Anan kalma "Ma" an yi amfani da shi don sad dar da marmari mai karfi domin mutane su yabi shi. Dubi yadda ka fassara wannan a 107:8.
"sa'ad da dattawa suka zauna tare." Dattawan sun zauna tare don su tattaunawa al'amurran da suka shafi cikin jama'a kuma domin yanke shawara domin jama'a.
"Yahweh ya yi" ... "saboda mutane da suke a can suna da mugunta"
dukan waɗannan jimla suna da ma'ana irin daya kuma na jadada yadda Yahweh ya yi ruwa ta ɓullo a cikin busasshiyar ƙasa. AT: "Ya yi maɓulɓulan kuma tafkinan ruwa cikin ƙasa dake amfani su zama hamada"
Kalma "wurin" na nufin da wurare inda Yahweh ya yi muɓulɓula da kuma tafkina su ɓullo. Har ila yau, jimla "masu jin yunwa" na nufin da mutane wanda suna yunwa. AT: "Yahweh ya sa mutane wanda suna jin yunwa su zauna a wurin"
"shuka gonakin inabi a ciki" ... domin su iya fito da yalwar kaka" ... "don mutane su zama fiye da lissafi sosai"
Wannan ana iya bayyana ta a fom na aiki. AT: "Ya na ajiya dabobinsu fiye da lissafi sosai"
Kalma "Su" na nufin da mutane wanda suna jin yunwa wanda Yahweh ya zaunar a cikin ƙasar. Wannan magana na bayyana yadda suna nan kafin Yahweh ya zaunar da su cikin ƙasar.
"ya zama 'yan kaɗan cikin lamba" ... Wannan na nufi suwa ga zama ci mutumci. AT: "ci mutuci"
A nan Dauda ya yi magana da Yahweh yana nuna raini don shugabanni sai ka ce raini ruwa ne da ya zubo bisansu. AT: "na nuna raini domin"
"masu girma." Wannan na nufin da shugabanni wanda suke ƙuntata mutane. AT: "shugabannin wanda ke ƙuntata su"
Anan Dauda ya kwatanta yadda Yahweh yake lura da mutanensa da yadda makiyayi yake lura da garken tumakinsa. Zai yiwu ma'ana sune 1) ya sa lamba mutane cikin iyalai su ƙaru kamar garken tumaki" ko 2) daukan lura da su kamar makiyayi na lura da tumakinsa"
Wannan na nufin da mutane wanda ke zaune cikin hanyar adalci. AT: "mutane masu adalci" ko "Mutane wanda ke yi abin da ke daidai"
A nan mugaye mutane suna mai da kamar "mugunta." AT: "dukkan mugaye mutane"
Wannan ke nufi da ba a ce wani abu ba a ba da amsa. AT: "babu abin da zai ce ga Yahweh a ba da amsa"
1Zuciyata ta kafu, Allah; zan raira, I, zan raira yabbai kuma tare da zuciyata ta girmamawa.2Ku tashi, sarewa da garaya; zan tashi da asuba.3Zan bada godiya gare ka, Yahweh, a tsakanin mutane; zan raira yabbai gareka a tsakanin al'ummai.4Domin alƙawarin amincinka mai girma ne sama da sammai; amincin ka kuma ya kai sararin sama.5Ka ɗaukaka, Allah, sama da sammai, bari kuma darajarka ta ɗaukaka sama da dukkan duniya.6Domin waɗanda kake ƙauna su sami ceto, ka ceto mu da hannunka na dama ka kuma amsa mani.7Allah yayi magana cikin tsarkinsa; "Zan yi farinciki; zan raba Shekem in kuma yi kason kwarin Sukkot.8Giliyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Ifraim ma ƙwalƙwali nane; Yahuda kuma sandar sarautana ne.9Mowab kwanon wankina ne; bisa Idom zan jefa takalmina; Zanyi sowa cikin nasara saboda Filitiya.10Wa zai kawo ni ckin birni mai karfi? Wa zai bida ni zuwa Idom?"11Allah, baka watsar damu ba? Baka tafi cikin yaƙi tare da mayaƙanmu ba.12Ka ba mu taimako gãba da maƙiyinmu, domin taimakon mutum wofi ne.13Zamu yi nasara da taimakon Allah; zaya tattake maƙiyanmu.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Anan Dauda ya na magana da kan sa daga zuciyar sa. Har ila yau, kalman "kafu" na nufi a dõgara gaba daya. AT: "Zuciyata ta kafu a kan ka, Allah" ko "Ina dõgara gaba daya a cikin ka, Allah"
A nan Dauda na nufin da kansa kamar yadda yana da girma na yabon Allah. AT: "Ka girmama ni ta wurin kyale ni in raira yabonka"
Anan Dauda ya bayyana yin wasa da kayan kide kide kamar tashinsu daga barci. AT: "Zan yabe ka da yin wasa da sarewa da garaya"
Waɗannan jimla biyu suna da ma'ana iri daya. Suna kwatanta girman alƙawarin amincin da gaskiyan Yahweh da grman sawo yadda sammai suna bisan duniya. AT: "alƙawarin amincinka da gaskiyanka suna da girma fiye da nisa sakanin sama da duniya"
Marubucin zabura yana rokon Allah don nuna cewa yana da ɗaukaka. Kasancewa da ɗaukaka bisan sammai na wakiltar kasancewa da girma. AT: "Allah, nuna cewa kana da ɗaukaka bisan sammai" ko "Allah, nuna cewa kana da girma a cikin sammai"
A nan Yahweh ya na mai da shi da "ɗaukakarsa." AT: "bari ka zama da ɗaukaka"
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Domin waɗanda kake ƙauna na bukata ceto" ko "ceton waɗanda kana ƙauna"
A nan "hannun dama" Yahweh na nufin da ikonsa. AT: "da ikonka"
Anan Dauda yana bayyana Allah na magana wani abu saboda yana da tsarki kamar yadda magana "a cikin tsarkinsa," sai ka ce tsarkinsa wani abu ne wanda yana daga ciki.AT: "Allah, domin yana da tsarki, ya ce"
A nan Allah na magana game da raba ƙasa Shekem da kwarin Sukkot.
Allah na magana game da kabilar Ifraim sai ka ce sojojinsa ne. Ƙwalƙwalin alama ce ta kayan aiki ne domin yaki. AT: "Ifraim yana kamar ƙwalƙwali da na zaba" ko "Kabilar Ifraim rundunar sojoji na ne"
Allah ya zaba mutane daga kabilar Yahuda su zama sarakuna mutanensa, kuma na magana game da kabilar sai ka ce sandar sarautan sa ne. AT: "Kabilar Yahuda na kamar da sandar sarautana" ko "Yahuda ita ce kabilar ta hanyar wanda ina mulki mutanena"
Allah na magana game da Mowab ta kasance mara muhimmanci sai ka ce Mowab kwanon wanki ne ko kuwa kaskantattu bawan. AT: "Mowab tana kamar kwano da ina amfani domin yin wanki"
Zai yiwu Allah yana magana game da daukin mallakan Idom sai ka ce yana kwatanci jefawa takalminsa zuwa ga ƙasar don a nuna cewa yana mallakan ta. Duk da haka wani irin ra'ayi na sauran fassarori. AT: "Na dauka mallaka na ƙasar Idom" ko "Na jefa takalmina zuwa ƙasar Idom don nuna cewa nawa ne"
Marubucin zabura na amfani da wanna tambaya ya bayyana bakincikinsa wanda ke da alama cewa Allah ya ƙi su. AT: "Tana da alama kamar ka ƙi mu" ko "Allah, da alama ka yi watsi da mu"
Marubucin zabura na magana game da Allah yana taimakon sojojinsu sai ka ce da Allah ya tafi ya kuma yi yaki tare da su. AT: "ba ka taimaki sojojinmu ba sa'ad da muka tafi cikin yaƙi"
Marubucin zabura ya yi magana game da Allah ya taimake sojojinsu ba wa maƙiyansu kashi sai ka ce da Allah ya tattake maƙiyan. AT: "zaya ba mu dama tattake maƙiyanmu" ko "zaya sa mu iya ba wa maƙiyanmu kashi."
1Allah wanda nake yabo, kada ka yi shiru,2Domin miyagu da macuta sun kawo mani hari; sun faɗi ƙarairayi game dani.3Sun kewaye ni kuma sun faɗi abubuwan ƙiyayya, kuma sun kawo mani hari babu dalili.4A ramuwar ƙaunata sun kawo mani sãra, amma nayi addu'a domin su.5Sun biya nagarta ta da mugunta, kuma sun ƙi ƙauna ta.6Ka naɗa mugun mutum bisa irin waɗannan maƙiya kamar waɗannan mutanen; ka naɗa mai sãra ya tsaya a hannun damansa.7Idan aka shar'anta shi, bari a same shi mai laifi; bari addu'arsa a ɗauke ta zunubi.8Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani ya ɗauki gurbinsa.9Bari 'ya'yansa su zama marasa mahaifi, matar sa kuma gwauruwa.10Bari 'ya'yan sa su tafi gantali da bara. Suna roƙon abin da aka rage yayin da suka bar rusassun gidajensu.11Bari mai bin bashi ya ɗauke dukkan abin da ya mallaka; bari bãƙi su washe abin da ya ke samu.12Kada wani ya miƙa wani halin kirki gare shi; kada wani ya ji tausayin 'ya'yansa marasa mahaifi.13Bari a datse 'ya'yan sa; bari a share sunansu daga tsara ta gaba.14Bari a faɗi zunuban kakanninsa ga Yahweh; bari kuma kada a manta da zunubin mahaifiyarsa.15Bari laifinsu a koyaushe ya kasance a gaban Yahweh; Bari Yahweh ya datse tunawa dasu daga duniya.16Bari Yahweh yayi haka saboda mutumin nan bai kula daya nuna wani alƙawarin aminci ba, amma a maimako ya firgitar da masu shan tsanani, masu buƙata, da masu ɓacin zuciya har ga mutuwa.17Yana ƙaunar la'ana; bari ta dawo kansa. Yaƙi albarka; bari kada albarka ta zo gareshi.18Ya lulluɓe kansa da la'ana kamar tufafi, kuma la'anarsa ta shiga cikin sa kamar ruwa, kamar mai cikin ƙasusuwansa.19Bari la'anoninsa su zame masa kamar suturar da ya ke sanyawa ya rufe kansa, kamar ɗamarar da ya ke sanyawa koyaushe.20Bari wannan ya zama rabon masu zargina daga Yahweh, ga waɗanda ke faɗin miyagun abubuwa game dani.21Yahweh Ubangijina, ka yi mani alheri sabili da sunanka. Saboda alƙawarin amincinka nagari ne, ka cece ni.22Domin ni mai shan tsanani ne mai buƙata kuma, zuciya ta kuma taji ciwo a cikina.23Ina ƙarewa kamar inuwar maraice; Ina kakkaɓewa kamar fãra.24Gwiwowina sun rasa ƙarfi daga azumi; Ina komawa fata da ƙasusuwa.25Na zama wulaƙantacce wurin masu zargina; idan suka ganni, suna girgiza kawunansu.26Ka taimake ni, Yahweh Allahna; ka cece ni ta wurin alƙawarin amincin ka.27Bari su san cewa wannan yinka ne, cewa kai, Yahweh, ka yi wannan.28Koda ya ke sun la'ance ni, ina roƙon ka ka albarkace ni; Idan suka kawo hari, bari su sha kunya, amma bari bawanka yayi farinciki.29Bari magafta na suyi sutura da kunya; bari su sanya kunyar su kamar alkyabba.30Da bakina na bada babbar godiya ga Yahweh; Zan yabe shi a tsakiyar taro.31Domin zai tsaya a hannun daman wanda keda buƙata; ya cece shi daga waɗanda ke shar'ianta shi.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
"Wannan shine domin darektan waka da kiɗa don amfani cikin sujada."
Zai yiwu ma'ana sune 1) Dauda ya rubuta zaburan ko 2) zaburan game da Dauda ne ko 3) zaburan yana cikin salon zaburan Dauda.
Kalman "miyagu" da "macuta" na nufi da mutane. Suna da ma'ana daya kuma suna jadada yadda waɗannan mutane na da mugu. AT: "Doin miyagu da macuta mutane"
"Ko da yake ina ƙauna su, sun dora mani laifi" ... "ƙauna ta domin su" ... Kalman "sun" na nufi da mutane wanda suke miyagu da macuta.
Waɗannan jimlan biyu layi daya ne kuma jimlan "mugun mutum" da "mai sãra" na nufin mutum daya.
"a hannun daman maƙiyana"
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Lokacin da yana aka shari'a, bari mahukunta ya same shi mai laifi"
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "ɗauke addu'arsa zunubi"
Jimla "kwanakinsa" na nufin da tsawon rayuwansa. AT: "Bari kada ya rayu da dogo lokaci"
"matsayinsa na iko" ... abinci ko kuɗi da a ke ba wa masu bara ... "gidajensu da aka rushe"
Wani wanda yake ara kuɗi ga wani mutum amma na jira cewa mutumin zai biya kuɗin
Waɗannan jimla biyu suna da ma'ana mai kama da kuma na jadada 'ya'yan sa kasancewa hallaka.
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Sa a datse 'ya'yan sa" ko "Sa 'ya'yan sa su mutu"
A nan ra'ayin can kasancewa ba wanda zai ci gaba da sunan iyalin an yi magana ta kamar yadda "sunansu ya kasance an share." AT: "bari a samu ba wanda zai ci gaba da sunansa"
A nan Dauda yana magana game da Yahweh yana tunani game da laifinsu sai ka ce laifinsu wani abu ne dake kasancewa a gabansa. AT: "Bari Yahweh ya ci gaba da tunani game da laifinsu"
Dauda ya yi amfani da kalma "duniya" don ta'allaka da dukkan mutane da ke zama a duniya. Har ila yau, jimlan "tunawa dasu" na nufin da mutane da ke tuna da su bayan da sun mutu. AT: "bari Yahweh ys yi ta domin kada a tuna da su a duniya"
Wannan na nufin da shi yana nuna alƙawarin aminci ga mutane. AT: "mutumin nan bai taba kula ba ya nuna wani alƙawarin aminci ga mutane"
Wannan na nufin da mutane wanda suna da ɓacin zuciya. AT: "mutane masu ɓacin zuciya" ko "mutane wanda suka rasa sa zuciya"
Dauda ya yi magana game da hali mugu mutum sai ka ce ita tufafi ne. AT: "Ya la'anta sauran mutane kamar yadda sau da yawa kamar yadda ya sa tufafi" ko "Ya la'anta mutane dukan lokaci"
Zai yiwu ma'ana sune 1) Ya yi magana la'ana haka sau da yawa cewa sun zama sashin ainihinsa. "la'anar da ya yi magana su ne sashi wanda yana" ko 2) la'anar da ya yi magana ya faru da shi. "dukan kasancewansa shine la'ana daga la'ana da ya yi magana"
Wannan na nufin da yadda mutum ke shan ruwa. aT: "kamar ruwan da mutum ke sha"
Wannan na nufin da yadda mai jike cikin ƙasusuwa sa'ad da aka goga ta akan fata. AT: "kamar mai zaitun jike cikin ƙasusuwan mutum sa'ad da aka goga ta akan fatansa"
mutane suna sa tufafinsu kowace rana. Dauda ya yi magana game da shi kulluyaumin na kasancewa a rufe da la'anoninsa kamar yana rufe da tufafinsa. AT: "Bari la'anoninsa su zama a kan sa kowace rana kamar da tufafin da yake sa"
Za'a iya kara wannan kalmomin da a ka rasa. AT: "kuma bari la'anoninsa koyaushe su zama akan sa kamar ɗamarar da ya ke sanyawa koyaushe"
"Bari waɗannan la'ana su zama rabon"
Wannan rokon ne domin Yahweh ya bi da shi da alheri. AT: "bi da ni da alheri" ... "sabili da shahararka"
Waɗannan jimla biyu suna da ma'ana masu kama da kuma suna jadada cewa bai iya taimaki kansa ba.
A nan Dauda yana magana game kasancewa cikin babban fid da zuciya kamar yadda zuciyarsa na kasancewa da rauni. AT: "Ina cike da bakinciki da fid da zuciya"
Dauda yana ji kamar zaya mutu ba dadewa ba kuma ya bayyana wannan abun da yake ji a zuciyarsa ta wuri kwatanta kansa da koɗewar inuwa da kuma yadda iska na busa fãra daga nan. AT: "Ina ji kamar ina kusan mutuwa, kamar wani inuwar maraice da ba da dadewa ba zai ɓace, kamar fãra da ke da sauri busa daga nan ta iska"
Wannan na nufi cewa yana da rashi ƙarfi kuma tana da wuya domin ya tsaya. AT: "ina da wahala tsayawa" ko "Jikina yana da kumame" ... "saboda ban cin wani abinci"
Wannan na nufi cewa ya rasa nauyi mai yawa. AT: "Jikina ya zama siriri"
Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Masu zargina suna yi mani ba'a"
Wannan wani harka ne na kin yarda.
Kalman "su" na nufin da masu zargin Dauda da kuma mutane wanda suna faɗa mugun abu game da shi.
"ka cece ni"
"amma ko ni, bawanka, in yi farinciki" ko "Ni ne bawanka, bari in yi farinciki." Dauda ya yi amfani da jimla "bawanka" na da ta'allaka da kansa.
Waɗannan jimla biyu suna da ma'ana ɗaya kuma suna amfani tare domin jadada yadda kwarai yana yi masu fata su zama da kunya.
A nan Dauda ya yi magana game da su kasancewa da jin kunya sai ka ce su ne sutura da sun sanya. AT: "su ji kunya sosai"
Dauda ya yi magana game da kasancewa su da jin kunya sai ka ce wata alkyabba da su sa. AT: "bari kunyar su ta rufe su kawai kamar alkyabbansu na nannade kewaye da su"
Wannan na nufi cewa zai yi magana. AT: "Zan yi magana kuma zan bayar"
Wannan na nufi cewa zaya taimake kuma tsare mutum mai buƙata. AT: "zai tsare mutum wanda ke da buƙata"
1Yahweh ya cewa ubangijina, "Ka zauna hannun damana har sai na maida maƙiyanka abin takawar ka."2Yahweh zai riƙe sandar mulkin ƙarfin ka daga Sihiyona; kayi mulki a tsakiyar maƙiyanka.3Mutanenka zasu bi ka cikin tsarkakan tufafi da nufin kansu ranar ikonka; daga mahaifar asubahi ƙuruciyar ka zata zame maka a kamar raɓa.4Yahweh yayi rantsuwa, kuma ba zai canza ba: "Kai firist ne na har abada, bisa ga ɗabi'ar Melkizadek."5Ubangiji yana hannun damanka. Zai kashe sarakuna a ranar fushinsa.6Zai shar'anta al'ummai; zai cika filin yaƙi da gawarwaki; zai kashe shugabanni a ƙasashe masu yawa.7Zai sha daga rafin bakin hanya, daga nan kuma zai ɗaga kansa sama bayan nasara.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Zai yiwu ma'ana sune 1) Dauda ne ya rubuta zabura ko 2) zaburan game da Dauda ko 3) zabura ta na cikin salo zaburan Dauda.
Jimla "hannun damana" na nufin da wurin ɗaukaka. AT: "Ka zauna a wurin ɗaukaka wanda ina da shi domin ka"
A nan Dauda na bayyana Yahweh yana sakawa abokan gaba maigidansa a karkashin ikonsa da mulki kamar sa su a karkashin kafansa kamar da karkashin sawaye. AT: "sa maƙiyanka a karkashin ikonka"
Muhimmin Bayyani: Dauda ya cigaba da magana ga sarkin.
A nan Dauda na magana game da Yahweh na shimfiɗa wuri cewa sarkin yana mulki kamar yadda yana riƙe da sandar mulkinsa. AT: "Yahweh zai shimfiɗa wurin a kan wanda ka ke mulki da iko"
Dauda na bayyana raɓa kamar yadda jariri ga wanda asubahi ya bada haihuwa. AT: "a cikin safiya ... kamar da raɓa"
Dauda yana gaya wa sarki cewa zaya zama da ƙarfin ƙuruciyar kowace safiya ta wuri kwatanta ta da yadda raɓa ke bayyana da farkon kowace safiya. AT: "kowace safiya za ka cika da ƙarfin ƙuruciyar ya raya ka dadai kamar da kowace safiya raɓa takan bayyan da ruwa kuma ta rayar da duniya"
Yahweh yana magana da ubangiji
Wannan na nufi da cewa ba zai canja abin da ya ce. AT: "ba zai canja tunaninsa ba" ko "ba zai canja abin da ya ce ba"
Za'a iya kara kalma da ta ɓace. AT: "bayan ɗabi'ar Melkizadek ya ke firist" ko "cikin hanyar ɗaya da Melkizadek ya ke firist"
Sa'ad da Ubangiji ya tafi yaƙi, Yahweh ya kan tsaya a hannu damansa domin ya taimake shi. AT: "Ubangiji yana taiakon ka a cikin yaƙi"
Kalman "Ya" na nufin da Yahweh. Zai sa sarakuna a ci su da yaƙi kuma su mutu, amma zai kyale rundunar sojojin sarkin su kashe maƙiyan sarakuna. AT: "Zai sa sarakunan ssu mutu, ko "zai kyale rundunar sojojin ka su kashe sarakuna"
A nan Dauda ya yi magana game da ranar sa'ad da Yahweh zai zama da fushi kuma ya ci nasarra da sarakuna kamar "a ranar fushinsa." AT: "a ranar hukunci sa'ad da hakurinsaya juya da fushi"
Wannan na nufi da cewa Yahweh zai sa wannan ya faru, ba cewa da kansa zaya kashe dukan mutane wanda da sun mutu a filin yaƙi. AT: "zai sa filin yaƙi ta zama a cike da gawarwaki"
Sarkin ya tsaya a taikace kawai domin ya sha kuma sa'an nan ya cigaba da bi maƙiyansa. AT: "Kamar yadda yana bi maƙiyansa, zai tsaya kawai don ya sha da sauri daga rafin"
Wannan na nufi da zai sha ruwa daga rafin. Rafin ƙarami korama ne. AT: "zai sha ruwa daga rafin"
Zai yiwu ma'ana su ne 1) sarkin ya ɗaga kansa a sama ko 2) Yahweh ya ɗaga kan sarkin da sama.
Mutane su kan su sa'ad da suna nasara, amincewa, da kuma farinciki. AT: "zai da amincewa ɗaga kansa bayan nasara" ko "zai zama da nasara"
1Ku yabi Yahweh. Zan bada godiya ga Yahweh da dukkan zuciyata a cikin taron masu adalci, a cikin tattaruwarsu.2Ayyukan Yahweh masu girma ne, ana jira da ɗoki ga dukkan waɗanda ke marmarin su.3Aikin sa mai daraja ne cike da ɗaukaka, adalcinsa kuma ya dawwama har abada.4Yana yin abubuwan ban mamaki daza a tuna; Yahweh cike da alheri ya ke cike kuma da jinƙai.5Yana bayar da abinci ga amintattun mabiyansa. Za ya tuna a ransa koyaushe da alƙawarinsa.6Ya nuna ayyukansa a cike da iko ga mutanensa inda ya basu gãdon al'ummai.7Ayyukan hannuwansa sun isa amincewa da hukunci; dukkan umarninsa abin dogara ne.8An kafa su har abada, domin a kiyaye su da aminci a dai-dai kuma.9Ya bada nasara ga mutanensa; ya naɗa alƙawarinsa har abada; tsarki da ban mamaki ne sunansa.10Girmama Yahweh shi ne farkon hikima; waɗanda suke aikata umarninsa suna da fahimta mai kyau. Yabonsa ya dawwama har abada.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
A nan kalman "zuciya" na wakiltar dukan kasancewa na cikin mutum da motsin zuciyarsa. AT: "da dukan abin da na ke"
Waɗannan jimla biyu na nufi cewa abu daya kuma za'a iya hada su in wajibi ce. AT: "a cikin taron mutane masu adalci"
Kalma nan "su" na nufin da ayyukan Yahweh." Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "dukan waɗanda ke marmarin ayyukan Yahweh na jiran su da ɗoki"
Zai yiwu ma'ana sune 1) "biɗa daga bisani" ko 2) "naxarin."
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "cewa mutane zasu tuna kulluyaumin"
Wannan shi ne karin maganan cewa na nufi da a tuna. AT: "tuna da"
"ayyukansa da ke nuna ikonsa"
Marubucin yana magana game da ƙasa wanda mallakar al'ummai Kananaan sai ka ce tana gãdonsu ne. AT: "ƙasar wanda mallakar sauran al'ummai"
Anan kalman "hannuwa" na nufin da Yahweh, kansa. AT: "Aikin da yana yi"
Wannan na nufi da umarnin Yahweh ba su canzawa ba kuma zai daɗe har abada. Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Ya kafa su har abada" ko "Zasu daɗe har abada"
Zai yiwu ma'ana sune 1) Yahweh ya bada umarninsa cikin aminci da kuma dacen yanayi ko 2) mutanensa su lura da umarnin Yahweh cikin aminci da kuma dacen yanayi. Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "domin mutanensa sun lura da su da amincin da kuma dacen yanayi"
A nan kalman "suna" na nufin da Yahweh, da kansa. AT: "Yahweh yana da tsarki da ban mamaki"
Kalman "hikima" ana iya fassara ta kamar da fi'ili. AT: "mataki na farko don a zama da hikima" ko "abu mafin muhimminci don zama da hikima"
"waɗanda suke biyaya da umarninsa"
Kalman nan "yabo" za a iya fassara ta kamar fi'ili. AT: "Mutane zasu yi yabonsa har abada"
1A yabi Yahweh. Mai albarka ne mutumin dake biyayya da Yahweh, wanda ya ke jin daɗin dokokinsa sosai.2Zuriyarsa zasu zama cike da iko a duniya; zuriyar mutum mai tsoron Allah masu albarka ne.3Dukiya da arziki suna cikin gidansa; adalcinsa zai dawwama har abada.4Haske yana haskaka wa cikin duhu domin taliki mai tsoron Allah; yana cike da alheri, cike da jinƙai, da hukunci.5Yana tafiya lafiya ga mutumin dake aikata alheri da bayar da rancen kuɗi, wanda ke tafiyar da al'amuransa tare da gaskiya.6Domin ba zai taɓa gusawa ba; mai adalci za a tuna da shi har abada.7Baya jin tsoron mugun labari; yana da ƙarfin hali, dogara ga Yahweh.8Zuciyar sa lif, ba tare da tsoro ba, har sai ya duba cikin nasara bisa magabtansa.9A yalwace ya ke bayar wa ga talakawa; adalcinsa ya dawwama har abada; za a ɗaukaka shi da girmamawa.10Wanda ke mugu zai duba wannan kuma ya ji haushi; zai ciza haƙoransa ya kuma narke; marmarin miyagun mutane zaya lalace.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
"ɗauka jin daɗin mai girma"
Wannan ana iya fassara ta cikin fom na aiki. AT: "Yahweh zai albarkace zuriyar mutum mai tsoronsa"
Mutum da ya rera wannan waka ya cigaba sa bayyana mutum wanda yana girmama Yahweh.
A nan kalma "gida" na nuna da iyali. Kalmomin "dukiya" da "arziki" mafi muhimmin ci na nufi abu daya kuma na nuna yalwan dukiya. AT: "Iyalinsa masu arziki ne sosai"
Marubuci na magana game da albarkar Allah ga mutum mai tsoron Allall cikin lokaci mai wuya sai ka ce shi ne hasken da ke haskakawa cikin duhu. AT: "Albarkun da mutum da ke tsoron Allah na karba daga Allah kamar haske wanda ke haskakawa cikin duhu"
Fahimcin bayyani nan za a iya yi ta da saukin ganewa. AT: "bayar da rancen kuɗinsa ga sauran mutane."
Mutum da ya rera wannan waka ya cigaba sa bayyana mutum wanda yana girmama Yahweh.
ba zai zama da damuwa ba ko yanayi ta sha karfi domin dogaransa a cikin Yahweh? Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Domin ba abun da zai taɓa gusad da shi"
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "mutane zasu tuna da mutun mai adalci har abada
Mutum da ya rera wannan waka ya cigaba sa bayyana mutum wanda yana girmama Yahweh.
"Zuciyarsa an yi goyon baya." Anan kalman "zuciya" na nufin da mutum. Zai yiwu ma;anan su ne 1) "Ya na nan da salama" ko 2) Ya na da tabbaci"
"ayyukansa na adalci zai dawama har abada." Dubi yadda ka fassara wannan cikin 112:3.
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Yahweh zai ɗaukaka shi ta wuri ba shi girma"
"zai duba cewa abubuwa suna tafi da kyau domin mutum mai tsoron Allah." Kalman "wannan" na nufin da kome da kome da kyau wanda marubucin ya bayyana ta cikin ayoyin baya game da mutum mai tsoron Allah.
Cizan haƙoran wani motsin jiki ne mai nuna raini. Duba yadda ka fassara jimla mai kamar da ta a 35:15.
Marubucin ya yi magana game da rasuwa mugu mutum daga baya sai ka ce mutum nan wani abu ne, irin kamar ƙanƙara, wanda na iya narke wa. AT: "rasuwa daga baya"
Mai yiwuwa ma'ana game da "marmarin" su ne 1) marmarin wani tunani da mugaye mutane na da shi. AT: "abubuwa da mugaye mutane ke son yi ba zai taɓa faru ba" ko 2) shine a turance
1Ku yabi Yahweh. Ku yabe shi ku bayin Yahweh; ku yabi sunan Yahweh.2Albarka ta tabbata ga sunan Yahweh, duk da yanzu da har abada abadin.3Daga tasowar rana har zuwa faɗuwarta, sunan Yahweh ya sami yabo.4Yahweh ya ɗaukaka sama da dukkan al'ummai, darajarsa kuma ta wuce gaban sararin sammai.5Wane ne kamar Yahweh Allahnmu, wanda keda mazauninsa a sama,6wanda ke duba sararin sama da duniya?7Yana taso da talaka daga datti kuma ya ɗaga mabuƙaci daga tarin toka,8domin ya zaunar da shi tare da shugabanni, tare da shugabannin mutanensa.9Yana bayar da gida ga bakarariyar macen gidan, yana mayar da ita uwar 'ya'ya cike da farinciki. A yabi Yahweh!
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
A nan kalman "suna" na misalin da Yahweh, da kansa. AT: "Yahweh"
Wannan jimla na nufin da gabatad da gabas, inda rana ke tasowa, da yamma, inda rana ke faɗuwa. Marubucin ya yi amfani da waɗannan matuka biyu don gabatad da ko'ina a duniya. Duba yadda ka fassara wannan a 50:1. AT: "ko'ina a duniya"
A nan kalman "suna" na wakiltar Yahweh, da kansa. Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "ya kamata mutane su yi yabon Yahweh"
Darajar Allah a ke magana game da ita sai ka ce tana da tsawo sosai. AT: "darajarsa shine mafi girma fiye da sararin sammai" ko "darajarsa ya na samu girma"
Marubucin ya yi roko wannan tambaya don jadada cewa babu wani kamar Yahweh. Wannan tambaya da ba ta damu da amsa ba za'a iya fassara ta kamar yadda ke a bayyani. AT: "Babu wani kamar da Yahweh Allahnmu ... da duniya."
"wanda ke zaune a samma" ko "wanda ke mulki cikin mafin matsayi wurin"
Waɗannan jimla biyu na nan da layi daya. Marubuci ya yi magana game da Yahweh na taimako da kuma girmama mutane wanda talaka ne sai ka ce Yahweh ya sa su su tashi daga zama cikin datti da kuma toka.
Zaune cikin datti da toka na wakiltar ko dai talauci ko fid da zuciya.
A nan jimla na biyu na bayyana cewa jimla na farko na nufin da shugabanni mutanen Yahweh. Waɗannan bayyanai biyu ana iya haɗawa. AT: "domin Yahweh zai zaunar da shi kusa da shugabanni na mutanensa"
A nan "gida" na nufin da 'ya'ya da ke zaune a cikin gidan. AT: "Ya na bayar da 'ya'ya ga macen wanda babu shi"
1Da Isra'ila suka bar Masar, gidan Yakubu daga waɗannan bãƙin mutane,2Yahuda ya zama wurinsa mai tsarki, Isar'ila masarautarsa.3Teku ya duba kuma ya gudu; Yodan ya juya baya.4Duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai suka yi tsalle kamar 'yan raguna.5Me yasa ka gudu, teku? Yodan, me yasa ka juya baya?6Duwatsu, me yasa kuka yi tsalle kamar raguna? Ku ƙananan tuddai, me yasa kuka yi tsalle kamar 'yan raguna?7Yi rawar jiki, duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allahn Yakubu.8Ya juya dutse ya zama tafkin ruwa, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓular ruwa.
Ana samun daidaici a gama gari waƙoƙin Ibraniyawa.
Waɗannan layin biyu layi daya ne, da "Isra'ila" da "gidan Yakubu" na ma'ana abu daya ne kuma "Masar" da "waɗannan bãƙin mutane" na nufin da mutane daya.
Kalma nan "gida" anan na wakiltar iyali ko zuriya. Fi'ilin watakila kawota ne ma wannan jimla. AT: "zuriyar Yakubu sun tashi daga waɗannan bãƙin mutane"
Zai yiwu ma'ana domin "Yahuda" da "Isra'ila" su ne 1) suna nufi da ƙasar. AT: "Ƙasar Yahuda ta zama wuri mai tsarki na Yahweh, ƙasar Isra'ila ta zama masarautarsa" ko 2) su ne (metonym) wato kalma da ake amfani a madadin wata kalma kamar anan domin mutanen Yahuda da Isra'ila. AT: "Mutane Yahuda sun zama waɗanda suke tsakanin wanda Yahweh ya zauna, mutanen Isra'ila su zama waɗanda a kan wanda ya yi mulki"
Marubucin ya yi magana game da iwan teku sai ka ce ita mutum ne wanda ya gudu daga nan kamar yadda Yahweh ya jagorance mutane Isra'ila ta kan busashen ƙasa. AT: "Ta na kamar ko da yake tekun ta duba kuma ta gudu"
Marubucin ya yi magana game da rafin Yodan sai ka ce ita mutum ne wanda ya ja da baya kamar yadda Yahweh ya jagorance mutane Isra'ila ta kan busashen ƙasa. AT: "tana kamar ko da yake Yodan ya ja da baya"
Marubucin ya yi magana game da duwatsu da tuddai sai ka ce su na a raye. Ya na yin magana mai yiwuwa game da girgizar kasa ne sa'ad da ya bayyana tsoron su a gaban Yahweh sai ka ce su na yin tsalle kamar raguna da 'yan raguna. AT: "tana nan sai ka ce duwatsu sun girgiza kamar da yin tsallen raguna kuma tuddai sun girgiza kamar da yin tsallen 'yan raguna"
Ayoyin 5-6 na ɗauka tambaya da ba ta damu da amsa ba hudu. Amsa da a ke sa ran ga kowane tambaya ana samu ta cikin aya 7, "saboda kasancewa ubsngiji."
Marubucin ya yi magana game da duwatsu da tuddai sai ka ce suna nan a raye. Mai yiwuwa yana magana game da girgizar kasa sa'ad da ya bayyana tsoronsu a gaban Yahweh sai ka ce su na yin tsalle kamar raguna da 'yan raguna. Dubi yadda ka fassara jimla mai kamar da ita a 114:3. AT: "girgiza kamar yin tsalle raguna ... girgiza kamar yin tsalle 'yan raguna"
Jimla biyu na karshe su layi daya ne. Fi'ilin mai yiwuwa ana iya kawota a layi na biyu. AT: "Yi rawar jiki, duniya, a gaban Allahn Yakubu"
Zai yiwu ma'ana su ne 1) marubucin yana yin magana da duniya sai ka ce ita mutum ne da kuma dokokin ta da yi rawar jiki da tsoro gaban Allah ko 2) kalman "duniya"
Waɗannan jimla biyu suna nan a layi daya. Marubuci yana bayyana Yahweh yana sa ruwa ta gudu daga dutse sai ka ce ya juya dutse zuwa ruwa.
Fi'ilin mai yiwuwa ana iya kawota daga jimla da ta rigaya. AT: "Ya uya dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓular ruwa"
1Ba gare mu ba, Yahweh, ba gare mu ba, amma ga sunanka ka kawo daraja, domin alƙawarin amincinka domin kuma isar amincewarka.2Me yasa al'ummai zasu ce, "Ina Allahnsu?"3Allahnmu yana sama; yana yin abin daya so.4Gumakan al'ummai azurfa ne da zinariya, aikin hannuwan mutane.5Waɗannan gumakai suna da baki, amma ba su magana; suna da idanu, amma basu gani;6suna da kunnuwa, amma basu ji; suna da hanci, amma basu sunsuna wa.7Waɗannan gumakai suna da hannuwa, amma basu taɓa wa; suna da tafin ƙafafu, amma basu tafiya; ko kuwa suyi magana daga bakunansu.8Waɗanda suka yi su kamar su suke, haka ma duk wanda ya dogara gare su.9Isra'ila, ku dogara ga Yahweh; shi ne taimakonku da garkuwarku.10Gidan Haruna, ku dogara ga Yahweh; shi ne taimakonku da garkuwarku.11Ku waɗanda ke girmama Yahweh, ku dogara gare shi; shi ne taimakonku da garkuwarku.12Yahweh yana la'akari damu kuma zai albarkace mu; zai albarkaci iyalin Isra'ila; zai albarkaci iyalin Haruna.13Zai albarkaci waɗanda ke girmama shi, yara da tsofaffi.14Bari Yahweh ya ƙara lissafin ku ƙari da ƙari, naku dana zuriyarku.15Bari ku yi albarka ta wurin Yahweh, wanda yayi sama da duniya.16Sammai na Yahweh ne; amma duniya ya bayar ga 'yan adam.17Matattu basu yabon Yahweh, ko kuwa wani wanda ya gangara cikin shiru;18Amma zamu albarkaci Yahweh yanzu da har abada abadin. A Yabi Yahweh.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Marubucin ya maimaita jimla "Ba gare mu ba" domin ya jadada cewa ba su cancanci su karba daraja da ya dace wa Yahweh kadai ba. Idan wajibi ne, jimla na fi'ili ana iya kawota anan. AT: "Kada ka kawo daraja gare mu, Yahweh"
A nan kalman "suna" na wakiltar Yahweh, kansa. AT: "amma ka kawo daraja ga kanka"
Wannan tambaya da ba ta damu da amsa ba na jadada cewa kada a samu wani dalili domin al'ummai su ce abin da suka ce. Wannan tambaya ana iya fassara ta kamar yadda a bayyani. AT: "Mutanen al'ummai bai kammata su iya ce, 'Ina Allahnsu?'"
Mutane sauran al'ummai na amfani wanna tambaya don su yi wa mutane Isra'ila ba'a kuma don bayyana cewa ba su gani taimakon da Yahweh yana yin masu ba. Wannan tambaya ana iya fassara ta kamar yadda a bayyani. AT: "Allahnka baya a nan don ya taimake ka."
A nan kalman "hannuwa" na hotn mutane wanda suka yi gumakan. AT: "abubuwa wanda mutane suka yi"
Gumakan ba su da ainihi baki, idanu, kunnuwa, ko hanci. Maimakon haka, mutane na yin su da kamani baki, idanu, kunnuwa, da hanci. Marubuci yana jadadawa cewa waɗannan gumakan ba su da rai bisa gaskiya. Ka na iya bayyana bayyani da aka nuna. AT: "Mutane sun ba da baki ga waɗannan gumakan"
Gumakan ba su da hannayen, tafin kafafu, ko bakuna na hakika. Ko dai, mutane sun yi su da kamanin hannayen, tafin kafafu, da bakuna. Marubucin ya na jadadawa cewa waɗannan gumakan ba su da rai bisa gaskiya. Ka na iya sa wannan bayyani da ke a fakaice da sauƙin ganewa. AT: "Mutane sun ba da hannayen ga waɗancan gumakai"
"amma waɗancan hannayen basu taɓa wa"
Waɗanda suka yi kuma suna bautawa gumakai sun zama matace da mara ƙarfi, daidai kamar waɗamca gumakai. Cikake ma'ana na wannan bayyani ana iya bayyana ta. AT: "Waɗanda suka yi su sun zama matace kamar da suke, kamar yadda kowa da kowa da ya dogara cikin su ke yi"
Kalma nan "Isra'ila" na gabatad da mutane na Isra'ila. AT: "Mutane Isra'ila, ku dogara ga Yahweh"
Marubucin yana magana game da Yahweh sai ka ce shi garkuwar ne saboda ya tsare mutanensa kamar yadda garkuwar zai tsare su daga cũta. AT: "wanda ya taimake ka da tsare ka"
A nan kalman "gida" na gabatad da iyali ko zuriya. Wannan jimla na nufin da firistocin wanda sune zuriyar Haruna. AT: "Zuriyar Haruna" ko "firistoci"
Wannan na nufin da mutane Isra'ila, wanda sune zuriyar Yakubu, wato wanda da ake kira Isra'ila. AT: "mutane Isra'ila"
Wannan na nufin da firistocin, wanda sune zuriyar Haruna. AT: "Zuriyar Haruna" ko "firistocin"
"duka karami da mai girma." Zai yiwu ma'ana sune cewa wannan na nufin 1) zuwa ga matsayin na zaman jama'a ko 2) zuwa ga shekaru. ko dai cikin hali, matuka biyu na gabatad da kowane mutum, ko da kuwa da shekaru ko matsayi na zaman jama'a.
Marubucin yana magana game da lambar na 'ya'ya da mutane Isra'ila zasu samu. AT: "Bari Yahweh ya daɗa lambar 'ya'yanku ƙari akan ƙari"
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Bari Yahweh, wanda ya yi samma da duniya, albarkaceka"
Wannan bai nuna cewa duniya ba na Yahweh ba, amma cewa ya ba duniya wa 'yan adam a bakin wurin mazauni.
Siffa "Matattu" mai yiwuwa a fassara ta da jimlar suna. AT: "Mutane wanda suka mutu"
Wannan jimla layi daya na da ma'ana mai kama da jimla kafin ita. Fi'ilin mai yiwuwa a kawota daga jimla wanda ya rigaya don samu ma'ana a bayyane. AT: "ko kuwa wani wanda ya gangara cikin shiru ya yabe Yahweh"
Marubucin na magana game da kabari ko wurin matattu kamar wurin da ke shiru inda babu wani da zai iya magana. Wannan shine kalma da ake anfani da ita domin gudun kunyatarwa domin mutuwa. AT: "ko kuwa wani wanda ya tafi zuwa wurin matattu"
Kalmar "mu" na nufin da mutane Isra'ila wanda suna da rai har yanzu.
1Ina ƙaunar Yahweh saboda yana jin murya ta da kuma roƙe-roƙe na domin jinƙai.2Saboda yana saurare na, zan yi kira a gare shi muddan ina da rai.3Sarƙoƙin mutuwa sun kewaye ni, tarkon Lahira kuma ya fuskance ni; naji ƙunci da baƙinciki.4Daga nan nayi kira ga sunan Yahweh: "Ina roƙon ka Yahweh, ka ceto rai na."5Yahweh yana cike da jinƙai da adalci; Allahnmu mai tausayi ne.6Yahweh yana kiyaye marasa sani; an kawo ni ƙasa, kuma ya cece ni.7Raina zai koma wurin hutawarsa, domin Yahweh yana yi mani da kyau.8Domin ka ceto raina daga mutuwa, idanu na daga hawaye, tafin ƙafafuna kuma daga tuntuɓe.9Zan bauta wa Yahweh a ƙasar masu rai.10Na bada gaskiya a gare shi, ko sa'ad da nace, "Ina cikin babban ƙunci."11Nayi garejen cewa, "Dukkan mutane maƙaryata ne."12Yaya zan biya Yahweh domin dukkan jiyejiyenƙansa zuwa gare ni?13Zan ɗaga ƙoƙon ceto, in kuma yi kira ga sunan Yahweh.14Zan cika alƙawaraina ga Yahweh a gaban dukkan mutanensa.15Abu mai daraja a gaban Yahweh shi ne mutuwar tsarkakansa.16Yahweh, tabbas, ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka ɗauke tsarƙoƙina.17Zan miƙa maka hadayar godiya in kuma yi kira ga sunan Yahweh.18Zan cika alƙawaraina ga Yahweh a gaban dukkan mutanensa,19cikin harabun gidan Yahweh, a tsakiyarki, Yerusalem. A yabi Yahweh.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
A nan kalman "murya" yana gabatad da mutum wanda yana magana. Jimlar "roke-roke na domin jinkai" na bayyana abin da ya ke magana kuma ana iya fassara ta tare da jimla fi'ili. AT: "yana jin na sa'ad da na roka shi domin jinkai"
Mutum wanda ya hada wannan zabura yana cigaba da magana.
Marubucin yana magana game da mutuwa sai ka ce ita ne mutum wanda zai kama shi kuma ya daura shi da igiyoyi. Dubi yadda ka fassara wannan a 18:4. AT: "Ina ji kamar na yi kusa in mutu"
Marubucin yana magana game da "Lahira," wurin matattu, sai ka ce ita ne mutum wanda zai yi masa maƙarƙashiya da tarkon. AT: "Na ji kamar ina shirye in shiga kabari"
A nan kalman "suna" na gabatad da Yahweh da kansa. AT: "kira ga Yahweh"
A nan kalma "rai" na gabatad da mutum. AT: "ceci ni" ko "kiyaye ni daga mutuwa"
Mutum wanda ya yi wannan waƙa ya cigaba da yi magana.
Wannan na nufin da mutane wanda suna da rashin basira ko wanda basu iya lura da kansu. Siffa ana iya fassara kamar jimla suna. AT: "waɗanda marasa sani ne" ko "waɗanda ba su samu masu taimako ba"
Marubuci ya yi magana game da kasancewa kamar da kasancewa cikin ƙasƙantaciyar matsayi. AT: "Ina nan wanda bai samu mai taimakon ba"
Mutum wanda ya hada wannan zabura ya cigaba da magana.
Marubucin yana magana game da salama da amincewa da yana da shi sai ka ce ita ne wuri inda ransa ke samu hutawa. Kalma "rai" na gabatad da mutum. AT: "Ina iya huta cikin salama kuma"
A nan kalmar "ka" na nufin da Yahweh. Kalmar "rayuwa" na gabatad da mutum. AT: "ka cece ni daga mutuwa" ko "ka kiyaye ni daga mutuwa"
Jimlar na fi'ili mai yiwuwa ana iya kawota daga jimla na baya don a bayyana ma'ana. AT: "ka cece idanu na daga hawaye" ko "ka kiyaye ni daga kuka"
Jimlar na fi'ili mai yiwuwa ana iya kawota daga jimla na baya don a bayyana ma'ana. Tafin kafafun anan na gabatad da mutum. Tuntuɓe anan mai yiwuwa na gabatad da kasancewa kisa daga maƙiyansa. AT: "ka cece ni daga tuntuɓe" ko "ka kiyaye ni daga kisa daga maƙiyansa"
Mutum wanda ya hada wannan zabura ya cigaba da magana.
"a cikin wannan duniya inda mutane suke da rai." Wannan shi ne bambanci da wurin matattu.
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Na sha wuya kwarai" ko "Mutane sun raunanar da ni kwarai sosai"
"Na yi saurin ce" ko "Na ce ba tare da la'akari ba"
"Kowane mutum maƙaryata ne" ko "Dukkan mutane maƙaryata ne"
Mutum wanda ya yi wannan waka ya cigaba da magana.
Marubucin ya roka wannan manya tambaya don gabatar da yadda zaya amsa abin da Yahweh ya yi domin na. Wannan tambaya ana iya fassara ta kamar yadda a bayyani. AT: "Wannan shi ne yadda zan biya Yahweh ... gare ni."
Wannan mai yiwuwa zance ne game da hadayar sha, wanda an sadaukar da ya kunshi zubawa ruwan inabi akan bagade, kuma wanda marubucin zai bayar cikin amsa wa Yahweh cetonsa. Cikake ma'ana wannan bayyani ana iya yin ta a bayyane. AT: "Zan bayar da hadayar sha ga Yahweh domin ya cece ni"
Anan kalmar "suna" na gabatad da Yahweh da kansa. AT: "kira bisa ga Yahweh"
Kalmar "mai daraja" anan baya nufi cewa Yahweh na daraja mutuwa tsarkakansa ba, amma cewa mutuwa tsarkakansa mai tsada ne a gare shi kuma na sa shi bakinciki. Jimlar "a gaban" na gabatad da yanayin Yahweh zuwa ga abin da yake gani. Cikaken ma'ana wannan bayyani ana iya yin ta a bayyane. AT: "Yahweh ya ɗauki mutuwa tsarkakansa abu ne mai tsada"
Mutum wanda ya wallafa wannan zabura ya cigaba da magana.
Wata kila wannan batun game da uwar marubucin ne kuma yana nuna cewa ta bautawa Yahweh da aminci. Cikake ma'ana wannan za'a iya bayyana ta. AT: "kamar yadda mama na take"
Marubucin ya yi magana game da kasancewa cikin hatsarin mutuwa sai ka ce ya kasance cikin sarkar kurkuku. AT: "ka cece ni daga mutuwa"
"hadaya don bayyana godiyar na"
A nan kalmar "suna" na gabatad da Yahweh da kansa. AT: "zan yi kira ga Yahweh"
Mutum wanda yi wannan waƙa na cigaba da yi magana.
Fassara wannan aya daidai yadda ka fassara 116:12.
Kalmar "gida" na nufin da haikali Yahweh. AT: "cikin tsakar gida haikalin Yahweh"
Marubucin na magana da Yerusalem kamar ko da yake ita mutum ne. AT: "cikin Yerusalem"
1Ku yabi Yahweh, dukkan ku al'ummai; ku ɗaukaka shi, dukkan ku mutane.2Domin alƙawarin amincinsa mai girma ne zuwa gare mu, isar amincin Yahweh kuma ya dawwama har abada. A yabi Yahweh.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
"Saboda shi"
"alƙawarin amincinsa zuwa gare mumai girma ne"
"na jimawa har abada"
1Ku bada godiya ga Yahweh, domin shi nagari ne, domin alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.2Bari Isra'ila su ce, "Alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada."3Bari gidan Haruna su ce, "Alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada."4Bari amintattun masu bin Yahweh su ce, "Alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada."5A cikin ƙuncina nayi kira ga Yahweh; Yahweh ya amsa mani ya kuma 'yantar dani.6Yahweh yana tare dani; ba zan ji tsoro ba; me mutum zai yi mani?7Yahweh yana gefe na a matsayin mai taimako na; zan duba cikin nasara bisa waɗanda suka ƙi ni.8Ya fi kyau a ɗauki mahalli cikin Yahweh da a sa dogara cikin mutum.9Gwamma a ɗauki mafaka cikin Yahweh da wani yasa dogararsa cikin sarakuna.10Dukkan al'ummai sun kewaye ni; a cikin sunan Yahweh na datse su.11Sun kewaye ni; I, sun kewaye ni; a cikin sunan Yahweh na datse su.12Sun kewaye ni kamar zuma; sun ɓace da sauri kamar wuta a tsakiyar sarƙaƙiya; a cikin sunan Yahweh na datse su.13Sun kawo mani hari saboda su mãke ni ƙasa, amma Yahweh ya taimake ni.14Yahweh ne ƙarfina da farincikina, shi ne kuma ya ceto ni.15Sowar farinciki ta nasara aka ji a cikin rumfunan adalai; hannun dama na Yahweh ya ci nasara.16Hannun dama na Yahweh ya ɗaukaka; hannun dama na Yahweh yaci nasara.17Ba zan mutu ba, amma zan rayu kuma inyi shelar ayyukan Yahweh.18Yahweh ya horar da ni da zafi; amma bai miƙa ni ga mutuwa ba.19Ka buɗe mani ƙofofin adalci; zan shige su kuma zan bada godiya ga Yahweh.20Wannan ce ƙofar Yahweh; adali yana bi ta ciki.21Zan bada godiya a gare ka, domin ka amsa mani, kuma ka zama cetona.22Dutsen da magina suka watsar ya zama dutsen kusurwa.23Wannan yin Yahweh ne; mai ban mamaki ne a idanunmu.24Wannan ce ranar da Yahweh ya yi aiki; za muyi farinciki da murna a cikin ta.25Ina roƙon ka, Yahweh, ka bamu nasara! Ina roƙon ka, Yahweh, ka bamu ci gaba!26Mai albarka ne wanda ya zo cikin sunan Yahweh; mun albarkace ka daga gidan Yahweh.27Yahweh Allahn ne, ya kuma bamu haske; ku ɗaure hadaya da igiyoyi a ƙahonnin bagadi.28Kai Allahna ne, kuma zan bada godiya a gare ka; kai Allahna ne; zan ɗaukaka ka.29Oh, ku bada gadiya ga Yahweh; domin shi nagari ne; domin alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.
An samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
"Gode wa Yahweh saboda na gari abubuwa da ya yi"
"Ya kaunace mu da aminci har abada"
Kalmar "Isra'ila" na gabatad da mutane Isra'ila. AT: "Bari mutane Isra'ila su ce"
A nan kalma "gida" na gabatad da iyali da zuriyar mutum. Wannan jimla na nufin da firistoci, wanda sune zuriyar Haruna. AT: "Bari zuriyar Haruna su ce" ko "Bari firistocin su ce"
"Ya kaunace mu da aminci har abada." Dubi yadda ka fassara wannan a 118:1.
"masu tsoron Yahweh" ko "masu bautan Yahweh"
Marubucin na magana game da Yahweh yana cetonsa daga wahala sai ka ce Yahweh ya dauke shi daga wurin daurin kurkuku zuwa sararin mai fadi a buɗe inda zai iya tafi da yardar kaina.
Marubucin ya roka wannan tambaya da ba ta damu da amsa don jadada cewa babu abin da mutum zai yi don ya yi masa rauni tun da Yahweh yana tare da shi. Wannan tambaya ana iya fassara ta kamar a bayyani. AT: "mutane ba zasu iya yin kowani abu don su yi mani lahani ba."
Zaman a gafe daya wani karin magana da ke nuna cewa wanda mutum yana amince da ita kuma zai taimake wani. AT: "Yahweh ya amince da ni kuma zai taimake ni"
Tana nuna cewa Yahweh shine wanda zai sha kashi da maƙiyan marubucin, yayin da marubucin duba samma. Cikakke ma'ana wannan za'a iya bayyana ta. AT: "Zan duba Yahweh yana ba da kashi dukkan masu ki na"
Allah ya yi magana game da sai ka ce shi ne mahalli, wuri inda mutane zasu samu kariya. AT: "a nema kariya daga Yahweh"
Fil'ilin layi daya ne da wanda ya riga ta. Allah ya yi magana sai ka ce shi mafaka ne, wurin inda mutane zasu samu kariya. AT: "a nema kariya daga Yahweh"
A nan kalmar "al'ummai" na gabatad da rudunar sojojin waɗancan al'ummai. Marubucin ya amfani da kalma da ke ƙara azama don jadada girman lambar rudunar sojojin da ke kewawe da shi. AT: "Rudunar sojojin na al'ummai da yawa"
A nan kalmar "suna" na gabatad da ikon Yahweh. AT: "da ikon Yahweh"
Marubucin ya yi magana game da ba da kashi wa rudunar sojojin makiyi sai ka ce yana datse su kamar da mutum zai datse reshe na tsiro. AT: "Na ba su kashi"
Marubucin ya kwatanta rundunar sojoji maƙiyi da taron zuma. AT: "Sun kewaye ni kamar taro zuma zai kewawe mutum"
Daidai kamar busashe kaya da ke kona da sauri, kai hari da rundunar sojojin maƙiyi shine da sauri a kan. AT: "hari da suka kai ya dade na karami lokaci kawai, kamar da wuta da ke cinye kaya da ya mutu da sauri"
Marubucin ya yi magana game da rundunar sojojin maƙiyin na yin kokari su ba shi kashi sai ka ce suna kokari su tura shi a kasa zuwa ƙasa. AT: "domin ya ba ni kashi"
"Yahweh yana ba ni ƙarfi da farinciki"
Wannan ana iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Mutane sun ji sowar farinciki ta nasara a cikin rumfunan adalai" ko "Adalai sun yi sowar da farinciki domin nasara a cikin rumfunan su"
A nan kalmar "hannu" na gabatad da ikon Yahweh. AT: "Yahweh ya ci nasara ta wurin girman ƙarfinsa"
Anan, a daga hannun wani karimci ne na nasara. Wannan anan iya bayyana ta cikin fom na aiki. AT: "Yahweh ya ɗaukaka hannun damansa" ko "Yahweh ya daga hannun damansa cikin nasara"
Marubucin yana bayyana irin ra'ayi duka barnatar da gaskiya ma don jadada cewa zai rayu lalle.
"Yahweh ya ladabtar da ni"
Marubucin ya yi magana game da mutuwa sai ka ce ita mutum a karkashin iko wanda Yahweh zai ajiye marubucin. AT: "bai bar ni in mutu ba" ko "bai bar maƙiyana su kashe ni"
"Buɗe mani ƙofofin ta hanyar wanda mutane masu adalci sukan shiga." Wannan shine zance game da ƙofofin haikalin, kuma marubucin yana magance batu masu tsaron. Cikake ma'ana wannan za'a iya bayyana ta. AT: "Buɗe mani ƙofofin haikalin"
"ƙofofin da ke kai zuwa gaban Yahweh" ko "ƙofofin Yahweh"
A nan marubucin ta fara da yin magana da Yahweh.
Kalmar "ceto" za'a iya fassara ta tare da jimla na fi'ili. AT: "ka cece ni"
Wannan watakila karin magana ne cewa marubucin ya yi amfani don bayyana ko dai sarkin ko al'umman Isra'ila. Wancan wanda wasu su dauke shi na banza, Yahweh ya sa ta zama mafin muhimmanci.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "abu mai ban mamaki don mu gani" ko 2) "mun dauke shi ta zama abun mamaki."
Waɗannan jimla biyu na nufi abu daya ne mafin muhimmanci kuma na jadada tsanani farin ciki. AT: "yi murna sosai"
A nan kalmar "suna" na gabatad da ikon Yahweh. AT: "wanda ya zo cikin ikon Yahweh"
Kalmar "gida" na nufin da haikali. AT: "Haikali Yahweh"
Marubucin ya yi magana game da Yahweh yana albarkace mutanensa sai ka ce Yahweh yana haskaka haske akan su. AT: "ya albarkace mu"
"ɗaure hadaya da igiya"
A nan marubucin ya fara da magana kuma da adreshin Yahweh kai tsaye.
Wannan maganar motsin rai ne da ya kammata a fassara ta tare da duk abin da maganar motsin rai ke girmamawar ka na da shi a harshenka don sa ta yi amo na hallita.
"gode wa Yahweh saboda abubuwan na gari da ya yi." Duba yadda ka fassara wannan a 118:1.
"Ya kaunace mu da aminci har abada." Duba yadda ka fassara wannan a 118:1.
1Masu albarka ne waɗanda hanyoyinsu basu da laifi, waɗanda ke tafiya cikin shari'ar Yahweh.2Masu albarka ne waɗanda suka kiyaye umarnansa masu tsarki masu neman sa da dukkan zuciyarsu.3Sun yi abin da ke dai-dai; suna tafiya cikin hanyoyinsa.4Ka umarce mu mu kiyaye dokokinka, domin muyi lura mu kiyaye su,5Kash, ina ma zan ɗore a cikin lura da farillanka!6To da ba za a kunyata ni ba a lokacin da nayi tunanin dukkan dokokinka.7Zan yi maka godiya da zuciya mai tsarki a lokacin dana koyi sharuɗɗanka.8Zan kiyaye farillanka; kar ka barni ni kaɗai.
9Yaya matashi zai tsare tafarkinsa da tsabta? Ta wurin kiyaye maganarka.10Da dukkan zuciyata na neme ka; Kar ka barni in kauce wa umarnanka.11Na adana maganarka a cikin zuciyata domin kada in yi maka zunubi.12Yahweh kai mai albarka ne, ka koya mani farillanka.13Da bakina na furta dukkan ayyukanka na jinƙai da ka bayyana mani.14Ina murna da umarnanka fiye da dukkan wadata.15Zan yi ta nazarin dokokinka in kuma saurari sharuɗɗanka.16Ina jin daɗin farillanka; ba kuma zan manta da maganarka ba.
17Yiwa bawanka kirki domin in rayu in kiyaye maganarka.18Buɗe idanuna domin in ga ayyukan al'ajibi a cikin shari'arka.19Ni bãƙo ne a cikin ƙasar; kada ka ɓoye umarnanka daga gare ni.20An rushe marmarina ta wurin jimirin sanin umarnanka masu adalci a kowanne lokaci.21Ka tsauta wa masu fahariya, waɗanda aka la'anta, Waɗanda suka bauɗe wa dokokinka.22Kãre ni daga wulaƙanci da cin mutunci, domin na kiyaye sharuɗɗan alƙawarinka.23Koda ya ke shugabanni sun ƙudurta suka yi mani maƙarƙashiya, ni bawanka ina binbinin farillanka.24Alƙawaran farillanka sune nake jin daɗi, sune kuma ke yi mini jagora.
25Raina yana birgima a ƙura! Ka bani rai ta wurin maganarka.26Na faɗa maka hanyoyina, ka kuma amsa mani; ka koya mani farillanka.27Ka sani in fahimci tafarkin umarninka, domin in yi ta nazarin koyarwarka mai al'ajibi.28Baƙinciki ya cika ni! Ka ƙarfafa ni ta wurin maganarka.29Ka jutar daga gare ni hanyar yaudara; ta wurin alheri ka koya mani shari'arka.30Na zaɓi hanyar aminci; Har kullum na kiyaye farillanka masu adalci daka sa a gabana.31Na manne wa umarnin alƙawarinka; Yahweh kada ka bar ni in ji kunya.32Zan bi hanyoyin dokokinka da gudu, gama ka faɗaɗa zuciyata tayi haka.
33Ka koya mani, Yahweh, hanyar umarnanka, kuma zan kiyaye su har ga ƙarshe.34Ka bani ganewa, kuma zan kiyaye shari'arka; Zan lura da ita da dukkan zuciyata.35Ka bishe ni ta tafarkin dokokinka, gama ina fahariya in yi tafiya cikinta.36Ka jagoranci zuciyata ga alƙawarin umarnanka da kaucewa daga ƙazamar riba.37Ka juya idanuwana daga duban wofintattun abubuwa; ka rayar da ni cikin hanyoyinka.38Ka cika wa bawanka alƙawarin da kayi ga waɗanda ke girmama ka.39Ka ɗauke zage-zagen da nake tsoro, gama hukuncin adalcinka na da kyau.40Duba, na jira umarnanka; ka farkar dani cikin sanin gaskiyarka.
41Yahweh, ka ba ni madawwamiyar ƙaunarka- cetonka bisa ga alƙawarinka;42sa'an nan zan sami amsa domin duk mai yi mani ba'a, gama na amince da maganarka.43Kada ka ɗauke maganar gaskiya daga bakina, gama Na yi jira domin umarnan sanin gaskiyarka.44Zan kiyaye dokarka babu fasawa, har abada abadin.45Zan yi tafiya cikin kwanciyar hankali, gama ina neman ka'idodinka.46Zan yi magana a kan hakikanin umarninka a gaban sarakuna kuma ba zan ji kunya ba.47Ina murna da dokokinka, waɗanda nake ƙauna sosai.48Zan ɗaga hannuwana ga dokokinka, waɗanda nake ƙauna; Zan yi nazari a kan farillanka.
49Ka tuna da alƙawarinka zuwa ga bawanka domin ka ba ni bege.50Wannan itace ta'aziyata a cikin ƙuncina: cewa alƙawarinka ya kiyaye ni da rai.51Mai girman kai ya yi mani gwalo, duk da haka ban juya daga dokarka ba.52Nayi tunanin umarnanka masu adalci dake tun zamanun dã, Yahweh, kuma sai na yi wa kaina ta'aziya.53Fushi mai ƙuna ya riƙe ni sabili da mugu da ya ƙi dokarka.54Farillannka sun zama waƙoƙina a cikin gidan da nake zama na ɗan lokaci.55Na yi tunanin sunanka a cikin dare, Yahweh, na kuma riƙe dokarka.56Wannan ya zama abin da na ke yi domin na kula da umarnanka.
57Yahweh ne rabona; nayi ƙudirin kula da maganganunka.58Nayi matuƙar neman tagomashinka da dukkan zuciyata; ka yi mani jinƙai, kamar yadda maganarka tayi alƙawari.59Nayi la'akari da tafarkina na kuma juyar da ƙafafuna zuwa ga umarnan alƙawarinka.60Nayi sauri ban kuma ɓata lokaci ba domin in kiyaye dokokin ka.61Igiyoyin mai mugunta suka nannaɗe ni; Ban manta da shari'arka ba.62Cikin dare na tashi domin inyi maka godiya sabili da dokokinka masu adalci.63Ni abokin dukkan waɗanda ke girmamaka ne, da dukkan waɗanda ke kula da umarnanka.64ƙasar, Yahweh, tana cike da amintaccen alƙawarinka; ka koya mani farillanka.
65Kayi abin alheri ga bawanka, Yahweh, ta wurin maganarka.66Ka koya mani sasancewa da fahimta, gama na gaskata da dokokinka.'67Kamin a wahalshe ni sai da na bijire, amma yanzu ina kula da maganarka.68Kana da kyau, kuma kai ne mai aikata abu mai kyau; ka koya mani farillanka.69Mai girman kai ya rufe ni da ƙarairayi, amma na adana umarninka da dukkan zuciyata.70Zuciyarsu ta taurare, amma ina fahariya da shari'arka.71Ya dace dani dana sha wahala domin in koyi farillanka.72Umarni daga bakinka ya fiye mani daraja fiye da dubban zinariya da azurfa.
73Hannayenka sunyi ni ka ƙera ni; ka ba ni fahimta domin in koyi dokokinka.74Waɗanda suke yi maka biyayya za suyi murna idan suka ganni saboda na sami bege cikin maganarka.75Yahweh, Na sani, dokokinka masu adalci ne, cikin amincinka kuma ka hukunta ni.76Bari alƙawarin amincinka ya ta'azantar dani, kamar yadda ka alƙawarta wa bawanka.77Ka nuna mani jinƙai domin in rayu, gama shari'arka ita ce jin daɗina.78Bari masu girmankai su sha kunya, gama sun ɓata sunana; amma zan yi nazarin umarnanka.79Bari masu darjanta ka su juyo gare ni, su da suka san alƙawaran dokokinka.80Bari zuciyata ta zama da rashin laifi da darjanta farillanka domin kada in sha kunya.
81Na suma domin sauraron cetonka! Na sa zuciya cikin maganarka.82Idanuna na jiran ganin alƙawarinka; yaushe za ka ta'azantar dani?83Gama na zama kamar salka cikin hayaƙi; Ban manta da farillanka ba.84Har yaushe bawanka zai jiure da wannan; yaushe zaka hukunta waɗanda suke tsananta mani?85Masu girmankai sun haƙa ramuka domina, suna rena shari'arka.86Dukkan dokokinka abin dogaro ne; waɗannan mutanen suna tsananta mani cikin kuskure; ka taimake ni.87Saura kaɗan su kawo ƙarshena a duniya, amma ban ƙi umarnanka ba.88Ta wurin tsayayyar ƙaunarka, ka kiyaye ni a raye, domin inyi biyayya da umarnanka.
89Yahweh, maganarka ta tsaya har abada; maganarka ta kahu da ƙarfi a cikin sama.90Amincinka ya dawwama ga dukkan tsararraki; ka kafa duniya, ta kuwa tsaya.91Dukkan abubuwa sun ci gaba har yau, kamar yadda ka faɗi cikin amintattun umarnanka, gama dukkan abubuwa bayinka ne.92Da shari'arka ba jin daɗina ba ce, da na hallaka a cikin ƙuncina.93Ba zan taɓa mantawa da umarnanka ba, gama ta wurinsu ka kiyaye ni da rai.94Ni naka ne; ka cece ni, gama na nemi umarnanka.95Masu mugunta sunyi shirin hallakar dani, amma zan nemi in san alƙawarin umarnanka.96Naga cewa dukkan abu yana da iyakarsa, amma dokokinka suna da fãɗi, basu da iyaka.
97Oh ina ƙaunar shari'arka! ita ce abin bin-binina dukkan yini.98Dokokinka sun sani na zama da hikima fiye da maƙiyana, gama dokokinka kullum suna tare dani.99Ina da sani fiye da dukkan malamaina, gama ina tunani akan alƙawaran umarnanka.100Ina da sani fiye da waɗanda suka girmeni; wannan ya faru domin na kiyaye umarnanka.101Na kiyaye sawayena daga hanyar mugaye saboda in lura da maganarka.102Ban juya daga dokokin adalcinka ba, saboda kai ne ka bani umarni.103Ya ya zaƙin maganarka ga ɗanɗanona, I, tafi zuma zaƙi a bakina!104Ta wurin umarninka na ƙaru da basira; saboda haka ina ƙin kowacce hanyar ƙarya.
105Maganarka fitila ce ga sawayena, haske ne kuma ga hanyata.106Na rantse na kuma tabbatar da ita, saboda haka zan kula da adalcin dokokinka.107Ina shan azaba; ka bar ni a raye, Yahweh, kamar yadda ka alƙawarta a cikin maganarka.108Yahweh, idan ka yarda karɓi shaidar godiyar bakina, ka koya mani adalcin dokokinka.109Raina kullum yana hannuna, duk da haka ban manta da shari'arka ba.110Mugaye sun ɗana tarko domina, amma ban ratse daga umarninka ba.111Na nemi alƙawaran dokokinka a matsayin gãdona har abada, gama su ne murnar zuciyata.112Zuciyata a shirye take don biyayya da farillanka har abada, har kuma zuwa ƙarshe.
113Ina ƙin waɗanda ba sa son yi maka biyayya, amma ina ƙaunar shari'arka.114Kai ne kake tsare ni da garkuwarka; ina jiran maganarka.115Ku tafi daga gare ni, ku masu aikata mugunta, domin in kiyaye dokokin Allahna.116Ka ƙarfafa ni ta wurin maganarka saboda in rayu ba domin inji kunyar sa begena ba.117Ka ƙarfafa ni, zan kuma tsira. Zan yi ta nazari a kan umarninka.118Ka ƙi dukkan waɗanda suka ratse daga umarninka, domin waɗancan mutanen masu yaudara ne kuma ba abin dogara ba ne.119Ka cire dukkan mugayen duniya kamar dattin maƙera; saboda haka ina ƙaunar mahimman umarninka.120Na cika da tsoronka, kuma ina jin tsoron adalcin ka'idodinka.
121Na yi abin da ke na gaskiya da adalci, kada ka bashe ni a wurin masu yi mani tsanani.122Ka tsare lafiyar bawanka, kada ka bari masu girman kai su wahallar da shi.123Idanuna sun gaji sa'ad da nake jiran cetonka da maganarka mai adalci.124Ka nuna wa bawanka amincin alƙawarinka, ka koya mani farillanka.125Ni bawanka ne, ka bani fahimta domin in sa alƙawarin farillanka.126Lokaci ya yi da Yahweh zai yi aiki, domin mutane sun karya shari'arka.127Gaskiya ne ina ƙaunar dokokinka fiye da zinariya, fiye da zinariya mai kyau.128Saboda haka na bi umarninka a hankali, na tsani kowacce hanya ta ƙarya.
129Ka'idojinka suna da ban mamaki, shi yasa nake yin biyayya dasu.130Buɗewar maganarka tana bada haske, tana bada ganewa ga wanda ba koyayye ba.131Na buɗe bakina ina haki, saboda na ƙagara domin maganarka.132Ka juyo wajena ka yi mani jinƙai kamar yadda ka ke yiwa waɗanda ke ƙaunar sunanka.133Ka bida ƙafafuna da maganarka, kada ka bari wani zunubi yayi mulki a kaina.134Ka fanshe ni daga hannun masu zalunci domin in lura da umarninka.135Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka, ka koya mani farillanka.136Ƙoramun ruwaye suna gudu daga idanuna saboda mutane ba sa lura da shari'arka ba.
137Mai adalci ne kai, Yahweh, dokokinka kuma dai-dai suke.138Ka bada dokokinka na alƙawari masu adalci kuma amintattu.139Fushi ya hallaka ni saboda maƙiyana sun manta da maganganunka.140An jaraba maganarka sau da yawa, bawanka kuma yana ƙaunar su.141Ni ba komai bane an kuma rena ni, duk da haka ban manta da umarninka ba.142Adalcinka dai-dai ya ke har abada, shari'arka madogara ce.143Koda ya ke wahala da azaba sun afko mani, duk da haka dokokinka suna faranta mani rai.144dokokinka na alƙawari masu adalci ne har abada.; ka bani fahimta domin in rayu.
145Nayi kuka da dukkan zuciyata, "Ka amsa mani, Yahweh, zan yi biyayya da farillanka.146Na kira ka; ka cece ni, zan kuwa aikata dokokinka na alƙawari.147Da asussuba nake tashi in yi kukan neman taimako. Na sa begena a cikin maganarka.148Na kan farka kafin masu gadin dare suyi sauyi domin in yi bin-binin maganarka.149Ka saurari muryata a cikin alƙawarin amincinka; ka barni da rai, Yahweh, kamar yadda ka alƙawarta a cikin dokokinka na adalci.150Su waɗanda suke tsananta mani suna matsowa kusa dani, amma suna nesa da shari'arka.151Kana kusa, Yahweh, kuma duk umarnanka amintattu ne.152Tun dã can na koya daga dokokin alƙawaranka cewa ka tsaida su har abada.
153Ka dubi ƙunci na kayi mani taimako, gama ban manta da shari'arka ba.154Ka tsaya mani ka kuma fanshe ni; ka riƙe ni, kamar yadda ka alƙawarta a maganarka.155Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa ƙaunar farillanka.156Ayyukanka na jinƙai masu girma ne, Yahweh; ka kiyaye ni da rai, kamar yadda ka saba yi.157Masu zaluntata da maƙiyana suna da yawa, duk da haka ban bar bin dokokinka na alƙawari ba.158Ina duban maciya amana a ƙyamace domin ba sa biyayya da maganarka.159Dubi yadda nake ƙaunar umarninka; ka kiyaye ni da rai, Yahweh, kamar yadda ka alƙawarta ta wurin alƙawarinka mai aminci.160Cibiyar maganarka ita ce gaskiya; kowanne ɗaya daga cikin dokokinka na adalci ne sun tabbata har abada.
161Sarakuna suna tsananta mani ba dalili; zuciya ta ta karai, gama ina jin tsoron karya maganarka.162Ina farinciki da maganarka kamar wanda ya sami ɗumbin ganima.163Ina ƙin ƙarairayi ina kuma wofintar dasu, amma ina ƙaunar shari'arka.164Ina yabon ka sau bakwai a rana sabili da dokokinka na adalci.165Masu ƙaunar shari'arka, suna da babbar salama; ba abin da zai sasu suyi tuntuɓe.166Ina jiran cetonka, Yahweh, ina kuma biyayya da dokokinka.167Ina aikata dokokinka tabbatattu, ina kuma ƙaunarsu ƙwarai.168Ina biyayya da umarninka da kuma dokokinka tabbatattu, gama kana sane da duk abin da nake yi.
169Ka saurari kukana na neman taimako, Yahweh; ka bani fahimtar maganarka.170Bari roƙona ya zo gaba gare ka; ka taimake ni, kamar yadda ka alƙawarta a maganarka.171Bari leɓunana su cika da yabo, gama kana koya mani farillanka.172Bari harshena yayi waƙa akan maganarka, gama dukkan dokokinka dai-dai suke.173Bari hannunka ya taimake ni, gama na zaɓi umarnanka.174Ina marmarin cetonka, Yahweh, shari'arka ce farincikina.175Ka rayar dani don in yabe ka, bari dokokinka na adalci su taimake ni.176Nayi makuwa kamar ɓatacciyar tunkiya; ka nemi bawanka, gama ban manta da dokokinka ba.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Wannan shine sunan baki na farko na haruffan Hebraniyawa.
Yadda mutum yake nuna hali an yi magana game da ita kamar "hanyoyi" ko "tafarkai." AT: "waɗanda halinsu basu da laifi" ko "waɗanda babu wanda zai iya sa laifi domin yin abin da ba daidai ba"
Hanyar da mutum ke rayuwa ko nuna hali an yi magana game da ita kamar tafiya. AT: "wanda rayuwa bisa ga shari'ar Yahweh" ko "wanda yake biyaya da shari'ar Yahweh." Wannan jimla na bayyana ma'ana "waɗanda hanyoyinsu basu da laifi."
Wannan shine karin magana wanda ka nufi mai zafi ko da gaske. AT: "da dukkan ransu" ko "da kowane abu da ke cikin su" ko "da gaske"
Mafin wannan zabura ya yi jawabi game da Allah, kuma kalmomin "ka" da "naku" kusan kulluyaumin na nufi da shi.
Ba su yi wa Yahweh rashin biyayya.
"suna yin tafiya cikin hanyoyin Yahweh." Anan an yi magana game da halayen su kamar yadda ake yi "tafiya," kuma yadda Allah ya so su su nuna halin an yi magana game da ita ka,ar "hanyarsa." AT: "sun nuna halin kamar yadda Yahweh yake son su su yi" (UDB)
"biyayya da dukkan abubuwa da ya yi shella cewa zai yi"
Wannan shine yin hankali a sani kuma a fahimta dokokin kuma don biyayya da waɗannan dokokin.
Marubuci ya yi magana game da kasancewa kafu cikin dokokin sai ka ce ba wanda zai sa shi ya motsawa ta jiki.
"cikin yin biyayya da farillanka"
Marubucin bai so ya kunyata ba sa'ad da yana a gaban Allah.
"dukkan abin da ka umarce mu"
"da sahihiyar zuciya." Mutum wanda sahili ne zai yi abin da ke daidai. Zuciya na nufin da motsin zuciya da ke cikin mutum. Duba yadda ka fassara "gaskiya" a 25:20. )
"farillai" na nufin da shari;ar ko dokokin Allah.
Wannan shine sunan baki na biyu na haruffan Hebraniyawa. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na aya 9 - 16 ta fara da wannan harafi.
Wannan tambaya ana amfani don gabatar da sabon daraja ga kalma Allah. Wannan tambaya da ba ta damu da amsa ba za'a iya fassara ta kamar yadda a bayyani. AT: "Wannan shine yadda matashi zai tsare tafarkinsa da tsabta"
Marubucin ya kwatanta rayuwa bisa shari'ar Allah kamar da tafarki da ke ajiye a share daga toshewa.
Wannan shine salon zance. Zuciyaa na nufin da dukkan motsin zuciya, jin, sha'awa, da son rai na mutum. AT: "da dukkan rai na" ko :da duk abin da ke ciki na" ko "da gaske"
A nan rashin biyayya ga dokokin Allah an bayyana ta kamar yadda batar daga tafarki. AT: "Kada ka bar ni in yi rashin biyayya da dokokinka"
"Na sa maganarka a cikin zuciyata." Wannan shine musili wanda ke nufi "na hadace kalmar ka." Zuciyar an yi hoton ta kamar bokiti da za'a rike abin da ,utne ke tunani.
"fiye da dukkan wadata"
Zan yi ta nazarin ... in kuma saurari Waɗannan sune faralel tunani da ke da ma'ana mai kama da, wanda sun maimaita domin girmamawa.
"yi tunani a hankali game da abin da ka umarce mu"
Wannan salon zancen na nufin da yi tunani a fili game da abin da ke kasancewa a tattauna. AT: "Ba da hankali a tunani"
ina ɗauka jin daɗin
Wannan shine sunan baki na uku na haruffan Hebraniyawa. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 17 - 24 ta fara da wannan harafi.
Marubucin ya kira kansa "bawanka" don nuna tawali'unsa.
Mawallafa ya yi magana samun fahimta, ilmi da hikima kamar kasancewa a iya gani. AT: "Taimaki ni in fahimta"
Mawallafa ya yi magana game da basira cikin shari'ar abu mamaki.
"cikin umarninka" ko "cikin dokokinka"
bãƙo ne wanda ba zai daɗe sosai a cikin ƙasar ba. AT: "Ina nan kamar bãƙo da ke zama a gajerewar lokaci cikin ƙasar" ko 2) rashin sani shari'ar Allah marubucin sai ka ce yana nan bãƙo wanda bai sani shari'ar ƙasar ba. AT: "Ina da rashin sani kamar bãƙo cikin ƙasar"
Marubuci na magana game da marmarinsa kasancewa da karfi sosai sai ka ce suna cikin zafi. AT: "Cikin rai na na matukan marmarin ya sani" ko "Rai na na ciwo saboda ina son in sani sosai"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) Allah zai la'anta su ko 2) sun cancanci horon Allah. AT: "wanda ya cancanci horonka"
arubucin ya yi magana game da yin rashin biyayya ga dokokin Allah sai ka ce sune tafarki da zasu iya yin yawo daga. AT: "wanda ya tafi daga tafarki dokokinka" ko "wanda ya yi rashin biyayya ga dokokinka"
"rike ni daga" ko "cece ni daga"
"kuma jin kunya da wauta"
"Koda ya shugabanni sun yi shiri don cuta na kuma suka ce mugu abubuwa game da ne"
Alƙawaran farillanka na sa ni farincikin sosai."
Farillan Allah sune an yi magana game da sai ka ce su mutane ne. AT: "sune kuma kamar mashawarata hikima gare ni" ko "kuma suna ba ni shawara mai hikima"
Wannan shine sunan baki na hudu haruffan Hebraniyawa. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 25-32 ta fara da wannan harafi.
Wannan shine salon zance. Mai yiwuwa ma'ana sune cewa 1) ya yi tunani cewa zai mutu ba da dadewa ba, ko 2) ya kwantawa cikin ƙura saboda yana da bakin ciki, 3) ya gane cewa yana son abubuwa na banza na duniya.
Wannan shine salon zance. Anan "rai" na nufin da manufa da muhimmancin, ba na nazarin hallitun masu rai kawai.
"Maganar" Allah na gabatad da abin da ya ce. Anan ta na nufin da abin da ya alkawarta. AT: "bisa ga alkawarinka"
Abin da mutum ke yi ko yadda ya ke nuna hali an yi magana sai ka ce ita hanya ce ko. AT: "abin da na yi"
"koyarwar mai ban mamaki"
"domin ina da bakin ciki"
"Sa ni in yi ƙarfi." Wannan zai yiwu na nufi da ƙarfi na jiki ko na ruhu.
Kalma "hanyar" anan na nufin da hanya na nuna hali. AT: "Ka rike ni daga bin hanyar yaudara" ko "Ka hana ni daga kasancewa yaudarar mutum"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "yin karya" ko 2) "gaskantawa da karya" ko "bin karya."
Yadda mutum ke nuna hali ko ayyukan an yi magana sai ka ce ita ce hanyar ko hanya. AT: zaman amintacce a gare ka"
Rike tam da su na nufin da kasancewa ɗaure don bin umurnin su. AT: "Na rike tam umurnin alƙawarinka" ko "Ina yin biyayya da umurnin alƙawarinka"
Wannan na nufin da dokokin Musa.
Marubucin ya yi magana mayar da hankali ko ɗaure don bin umurrnin dokokin Allah sai ka ce wani yana guduwa aka hanyar. AT: "Zan ɗaure don biyayya da dokokinka"
Wannan shine salon zance. Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Ka taimaki ni samun fahimta mai girma game da dokokinka" ko 2) ka ba ni marmarin mai girma don biyayya da dokokinka"
Wannan shine sunan baki na biyar haruffan Hebraniyawa. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 33-40 ta fara da wannan harafi.
Wannan shine atat hanya da ke bayyna Doka Musa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "gaba daya" ko 2) "ƙarshe rayuwar ta" ko 3) "zuwa ga ƙarshen lokaci."
"Yin biyayya da shari'ar ka"
"Zan yi biyayya da shari'arka lalle" ko "Ina ɗaure gaba daya da yin abin da ta na faɗa"
"Ka bishe ni bisa fa dokokinka" ko "Ka koya mani yin biyayya da dokokinka." An kwatanta dokokin Allah da hanyar da mutum ke tafiya cikin biyayya da Allah.
Wannan shine salon zance. "Zuciya" anan na nufin da son rai, muraɗin da zaɓi shugabanta rayuwan wani. AT: "Sa ni in so"
"don yi biyayya da alƙawarin umarnanka". Wannan shine na magana game da biyayya da Shari'ar Musa.
"sha'awar domin arziki." Wannan na magana game da dũkiyanda ake samu ta wurin ketare doka hanyar yin abubuwa ko azzãlumai zuwa ga wasu.
Wannan musili ne da ke nufin da wani da ke marmarin abubuwan da ba ta da dawwamammen daraja.
"ka sa in iya zama kamar yadda ka so in zama"
"ka sa rai na ƙarfi" ko "ka ba ni ƙarfin"
Ka yi wa bawanka abin da ka alƙawarta ka yi wa waɗanda ke girmama ka"
Marubucin na magana game da kansa a masayi bawan Allah ya nuna tawali'un sa. AT: "ni, bawanka"
"Ina jin tsoro da sosai"
Allah na hukuncin gaskiya kuma yanke shawararsa na da kyau. AT: " hukuncinka na ƙwarai ne kuma na da kyau"
Wannan salon zance ne. Anan "duba" na nufin da kasancewa da sani halin da ake ciki. Mayar da hankalin akan ilmi ko fahimta, fiye da wajen lura kawai.
Kalmar "gaskiyar" suna mai zuzzurfar ma'ana ne kuma na nufin da kasancewa mai adalci. AT: "ka farkar dani saboda kai mai adalci ne"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na shida. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 41-48 ta fara da wannan harafi.
Wannan roko ne. AT: "don Allah ka ba ni madawwamiyar ƙaunarka"
Ka na iya bayyana wannan bayyani da an fahimta. AT: "ka ba ni cetonka" ko "cece ni"
"wani amsar" ko "amsa"
"bakina" na nufin da yin magana game da kalmar Allah. AT: "Ba mai yiwuwaba ka hana ni daga yin maganar gaskiyar ka"
"jira" ya na da ra'ayi na dogara, da amincewa cewa Allah ba zai yi kamar yadda ya umurta.
"Zan yi biyayya"
Yin tafiya cikin kwanciyar hankali shine zaman rayuwar wani cikin kwanciyar hankali. AT: "Zan zauna cikin kwanciyar hankali a cikin Allah"
"Neman" shine a fahimtar, ko samun fahimtagame da ka'idodin Allah sai ka ce wani na iya gani su.
"Muhimmin umurnin ga sarakuna" ko "Umarnin ga sarakuna"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Ina samun murna cikin yin bincike dokokinka" 2) "Ina da murna cewa ina da zarafi bincike dokokinka."
Wannan shine salon zance wanda na nufi da daraja, so kwarai ko girmaawa dokokin Allah.
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na bakwai. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 49-56 ta fara da wannan harafi.
"Tuna da alƙawarinka." Duba yadda ka fassara wannan a 20:3
Wannan sharaɗin za'a iya canza ta. AT: "Dalilin ta'aziyata ita ce alƙawaarinka ya ajiye ni da rai cikin bakincikina"
Wannan siffa mara muhimmanci za'a iya bayyana ta kamar sifffa. AT: "Mutane masu girman kai"
Yi wa wani ko wani abu ba'a wanda an raina, shakkar ko ba girmamawa
Wannan shine zance da lokaci umurnin, shari'ar, da an ba wa Musa shekaru masu yawa a dã.
Wannan shine salon zance. An bayyana fushi sai ka ce ita mutum da zai damƙe wani mutum. AT: "Na zama da fushi sosai"
"Na yi amfani da farillanka kamar yadda kalmomin dake cikin waƙa na" ko "Na ƙirƙiro waƙoƙi daga farillanka"
A nan kalmar "suna" na gabatad da Yahweh kansa. AT: "Na yi tunani game da kai, Yahweh"
Wannan salon zance ne wanda na nufi da biyayya da doka. AT: "Na yi biyayya da dokanka"
"hali na"
Wannan salon zance wanda na nufi da bin ko yin biyayya da waɗancan umarnan"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na takwas. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 57-64 ta fara da wannan harafi.
Wannan na nufi Yahweh shine duk abin da ya ke so. Dadai kamar yadda Lawiyawa da ba su karba ƙato yankunan ƙasa ba domin Ubangiji shine rabon su haka marubucin ya yi da'awar Yahweh kamar wanda ke ƙosad da bukatun sa.
A nan "kafafu" na gabatad da dukkan mutum. Don a tuba kuma a zaba yin biyayya da dokokin Allah na kamar da juyawa kafafun wani a kan hanyar da ya yi ta wani waje. AT: "canza adireshi na"
Marubucin ya bayyana ra'ayi irin daya duka abu mai muhimmanci ko mara muhimmanci sosai domin jadada gaggawa wanda zaya yi biyayya ga dokokin Yahweh.
Cikin wannan musili, mugaye ko mutane masu mugunta sun yi kokari su sa marubuci ya yi zunubi kamar da mafarauci ke neman ya kama daba da tarko. AT: "Abokan gaba na sun yi kokari su kama ni"
"Ni abokin dukkan wanda ke girmamaka"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na tara. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 65-72 ta fara da wannan harafi.
Marubucin na nufin da kansa kamar "bawanka." AT: "ga ni, bawanka" ko "zuwa ga ni"
Wannan salon zance ne. "maganarka" na nufin da alƙawaren Yahweh wanda ya yi wa marubuci. AT: "kamar yadda ka alƙawarta"
Wannan za'a iya bayyyana ta cikin fom na aiki. AT: "Kamin ka wahalshe ni" ko "Kamin ka hukunta ni" Kamin a wahalshe ni"
Rashin biyayyan ga Allah an magana game da ita sai ka ce mutum ne da ya yi tafiya akan hanyar da ba dadai ba. AT: "na yi maka rashin biyayya"
A nan "magana" na gabatad da dokokin. AT: "Ina biyayya da dokokinka"
Wannan siffa mara muhimmanci ana iya bayyana ta kamar ita siffa ne. AT: "Mutane masu girman kai"
Mutane na faɗin ƙarairayi masu yawa game da mutum an yi magana game da sai ka ce sun sa mutum mai dati ta wurin yada ƙarairayi bisan sa.
A nan "zuciya" na gabatad da son rai mutum. AT: "da dukan alkawari" ko "gaba daya"
A nan "zuciyar" na gabatad da mutane masu son rai. Mutum mai taurin kai an yi magana sai ka ce zuciyarsu ko son ransu suna da tauri kamar dutse. AT: "Suna da taurin kai"
A nan "baki" na gabatad da abin da Allah ya ce. AT: "Umarnin da ka yi magana sune" ko "umarninka sune"
Wannan za'a iya bayyana ta mafi yawa gabaki daya. AT: "fiye da babban iyan yawa kudi" ko "fiye da dũkiya mai girma"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na goma. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 73-80 ta fara da wannan harafi.
Allah yana halita mutum an yi magana game da sai ka ce Allah ya yi amfani da hannayensa don siffar da mutum kamar yadda wani mai yiwu siffar da yumbu zuwa cikin abu.
A nan "Hannayen" na gabatad da ikon Allah ko yin wani abu. AT: "ka"
A nan "magana" na gabatad da abin da Allah ya ce. AT: "saboda na dogara ga abin da ka ce" ko "Ina amincewa gaskanta da abin da ka ce"
"ka horar da ni saboda kana da aminci." Allah ya yi alkawuran ba wa mai adalci lada kuma ya azabta azzãlumai, don haka yana da aminci ya yi abin da ya ce zai yi.
Marubuci na nufin da kansa kamar "bawanka." AT: "ni, bawanka" ko "ni"
Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai kuzari. AT: "Ka sa masu girmankai su kunyata" ko "Sa masu girmankai su sha kunya"
Wannan siffa mara muhimmanci ana iya bayyana ta kamar ita siffa ne. AT: "mutane masu girmankai" ko "waɗanda suna da girmankai"
Mutane na dawo da abokantaka ga marubuci an yi magana game da sai ka ce sun juyo zuwa gare shi. AT: "zo gare ni" ko "yi taraya da ni"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) Wannan ƙari ya bayyana waɗanda suka darjanta Allah ko 2) Wannan na nuna manufan waɗanda suna darjanta Allah su juyo ga marubuci. Kalmar "domin" za'a iya hada ta don nuna wannan. AT: "domin mai yiwuwa su koyi abin da ka ba da umurni"
A nan "zuciya" na gabatad da tunanin mutum da kuma muradi. AT: "Bari in zama da rashin laifi"
Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai kuzari. AT: "domin kada in ji kunya"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na goma sha ɗaya. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 81-88 ta fara da wannan harafi.
A nan "magana" na gabatad da abin da Allah ya ce. AT: "Ina amincewa dõgara da abin da ya ce"
A nan "idanu" na gabatad da cikakke mutum. AT: "Na jira sosai domin ka yi abin da ka alƙawarta zaka yi"
Salka na halakani sa'ad da tana rataya na sawon lokaci a cikin wurin da ke cike da hayaƙi. Marubuci ya kwatanta kansa da salkan wanda ya kasance halakani ta wuri hayaƙi don jadada cewa yana ji mara amfani.
Marubucin ya yi amfani da tambaya don rokon Allah ya hore waɗanda suna tsananta masa. Wannan tambaya da ba ta damu da amsa ba za'a iya fassara ta kamar yadda bayyani. AT: "Don Allah kada ka jira wani sawo ba. Ka hore waɗanda suna tsananta mani."
Marubucin na mai da kansa kamar "bawanka." AT: "tilas ni, bawanka" ko "tilas ni"
Masu girmankai suna neman su kama marubuci ko su sa shi ya yi abin da ba dadai ba. Wannan an yi magana game da ita sai ka ce su mafarauci ne da suke tona ramuka don su kama marubucin kamar yadda wani dabba.
Wannan siffa mara muhimmanci ana iya bayyana ta kamar siffa. AT: "mutane masu girmankai" ko "waɗanda suna da girmankai"
Wannan hanyar mai ladabi ne na yin magana game da wani yana kashe wani dabam. AT: "Saura kaɗan su kashe ni"
"Bisa ga tsayayyar ƙaunarka." Jimlan "tsayayyar ƙaunar" ko "amincin" ana iya bayyana ta kamar yar bab. AT: "saboda cikin aminci kana ƙauna ta"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na goma sha biyu. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 89-96 ta fara da wannan harafi.
A nan "magana" na gabatad da wani abu da Allah ya yi magana da mutane. AT: "Abin da ka ce zai zama gaskiya har abada"
A nan "magana" na gabatad da wani abu da Allah ya yi magana da mutane. Wannan na magana game da abin da Allah ya ce sai ka ce wani abu ne da ke tsaye a mike da tabbaci. AT: "abin da ka ce zai zama gaskiya a cikin sama har abada"
"ga dukkan tsararraki na gaba." Wannan shine salon zance wanda ke nufi "har abada."
Dukkan halitattu abubuwa an yi magana game da su saimka ce su mutane wanda suna iya yi hidima ga Allah. AT: "dukkan abubuwa suna yi maka hidima" ko "dukkan abubuwa sun yi biyayya da dokokinka"
Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai yaƙini. AT: "Zan tuna da kulluyaumin"
Tana nuna cewa marubuci yana yin biyayya da umarnan Allah. Cikakke ma'ana wannan bayyani ana iya sa ta bayyane. AT: "gama ka ajiye ni da rai saboda ina biyayya da su"
Kokari kwarai don biyayya da umarnan Allah an yi magana game da sai ka ce umarnan wani abu ne wanda tilas mutum ya bincika.
"zan yi matukan kokari in fahimta"
"dukkan abubuwa suna da karshe"
Dokokin Allah na kasancewa gaskiya a koyaushe da kuma cikakke an yi magana game da sai ka ce dokokin Allah wani abu ne wanda ta na da faɗi da ba ta ta da iyakar faufau. AT: "amma dokokinka basu da karshe" ko "amma dokokinka suna nan har abada"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na goma sha uku. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 97-104 ta fara da wannan harafi.
Kullum tunani game da dokokin Allah an yi magana game da sai ka ce dokokin wasu abu ne da marubuci ke ajiye tare da shi a kulluyaumi.
Guje wa yin abin da ke mugu an yi magana game da ita sai ka ce tana guje wa yin tafiya akan hanyar da take ta mugunta. AT: "Na guje wa yin abin da ke mugu"
Anan "sawaye" na gabatad da dukkan mutum. AT: "kiyaye kaina"
"biyayya da maganarka"
A nan "magana" na gabatad da dokokin Allah.
Cigaba wa da biyayya da dokokin adalcin Allah an yi magana game da ita sai ka ce marubucin ba ta jiki ne ba ya juya daga dokokin adalcin. Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai yaƙini. AT: "Ina biyayya da dokokin adalcinka kulluyaumi"
Marubusci yana jin daɗi cikin abin da Allah ya ce an yi magana game da sai ka ce kalmomin Allah abinci ne wanda an ɗanɗanar zaki zuwa ga marubuci. AT: "Kalmominka suna da kyau kuma mai farantawa!"
Wannan suna mai zuzzurfar ma'ana "basira" za'a a iya bayyana ta kamar da fi'ili. AT: "Na koya in gane abin da ke daidai"
Mugu hali an yi magana game da ita sai ka ce sune hanyar ko hanya ƙarya.
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na goma sha hudu. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 105-112 ta fara da wannan harafi.
Waɗannan jimla biyu na da ma'ana sun yi kama. Suna magana game da Allah yana gaya wa mutum yadda zasu zauna sai ka ce mutum suna yin tafiya akan hanya da maganar Allah shine haske da ke taimakon mutum ya gani inda zasu je. AT: "Maganarka na gaya mani yadda zan yi rayuwa"
A nan "magana" na gabatad da dukkan wanda Allah ya na magana ga mutane.
A nan "magana" na gabatad da abin da Allah ya na magana da mutane. AT: "kamar yadda ka alƙawarta zaka yi"
Marubuci ya yi magana game da addu'arsa sai ka ce sune hadaya wanda yana bayarwa ga Allah. AT: "Addu'a na kamar hadaya ne gare ka"
A nan "baki" na gabatad da dukkan Mutum.
Wannan shine salon zance da ke nufi da rayuwan marubuci na cikin haɗari kullum. AT: "Abokan gaba na suna kokari sau da yawa don su kashe ni"
Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai yaƙini. AT: "Kullum ina tuna da shari'arka"
Mugaye mutane na yin kokari don su kama kuma su kashe marubuci an yi magana game da sai ka ce su mafarauci ne da ke sa tarko don kama wani dabba.
Wannan siffa maras muhimmanci za'a iya bayyana ta kamar wani siffa. AT: "Mugaye mutane"
Bana yi wa umarnin Allah rashin buyayya an yi magana game da sai ka ce marubuci baya yin tafiya daga umarnin Allah. Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai yaƙini. AT: "Ina biyayya da umarninka"
Marubuci kullum yana son ƙwarai kuma na yi biyayya da dokokin Allah an yi magana game da ita sai ka ce dokokin su ƙasa ne ko mallaka da marubuci zai gãda. AT: "Shari'arka zai zama nawa har abada" ko "Alƙawarin umarninka suna kamar da gãdo da zan rike har abada"
A nan "zuciya" na gabatad da dukkan mutum. AT: "suna sa ni farinciki" ko "Ina jin daɗin su"
A nan "zuciya" na gabatad da son rai marubuci. Jimla "zuciya a shirye" salon zance ne. Hanyar ce na faɗin marubuci yana ƙuduri. AT: "Ina ƙuduri yi biyayya"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "kowanen su" (UDB) 2) "zuwa ƙarshen rayuwa ta" ko 3) "zuwa ƙarshen lokaci"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na goma sha biyar. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 113-120 ta fara da wannan harafi.
Mutum wanda ba shi da hali na gari kuma ba ya cikakke yi wa Allah biyayya an yi magana game da shi sai ka ce mutumin na da zuciyar biyu. AT: "waɗanda ba su yi maka biyayya gaba daya" ko "waɗanda suna da rashin kirki"
Allah yana hadawa marubuci lafiya an yi magana game da sai ka ce Allah shine wurin inda marubuci zai ji kuma ya ɓoye.
Allah yana kare marubuci an yi magana game da sai ka ce Allah shine garkuwar marubuci.
A nan "jira" na nufi da jiran da zaman sa rai. Wannan yana da ra'ayin bege da dogara. AT: "Ina dogara da maganarka"
Ka tallafe ni ta wurin maganarka." Anan "magana" na gabatad da abin da Allah ya na magana da mutane. AT: "Ba ni ƙarfi kamar yadda ka ce zaka yi" ko "Ba ni dama in zama da ƙarfi kamar yadda ka alƙawarta"
A nan "begena" na gabatad da dogarar marubuci a cikin Allah da alƙawarinsa. Wannan za'a iya bayyana ta kamar yadda a cikakke jumla. AT: "Kada ka yanke mani buri." (UDB) ko "Kada ka sa in jii kunya ta wurin rashi yin abin da ka alƙawarta ka yi."
"Ka taimake ni" ko "Ka ƙarfafa ni"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "waɗancan mutane suna da karya kuma babu wanda zai dogara da su" ko 2) "waɗancan mutane suna yin shiri yaudara amma zasu gaza"
Dattin maƙera ɓarɓashi ne ko kuwa raguwar da ba a so cikin tsari tata zinariya ko wasu karafa. Yahweh ya kawar da mugaye mutane sai ka ce su sharan ne.
Wannan siffa maras muhimmanci za'a iya bayyana ta kamar wani siffa. AT: "Mugaye mutane"
"kamar shara" ko "kamar ɓarɓashi"
A nan "jiki" na gabatad da dukkan mutum. AT: "Na girgiza saboda da tsoron ka"
Tana nuna cewa marubuci ya na tsoron adalcin ka'idodin Allah saboda marubuci ya sani cewa Allah na horon masu yi dokokinsa rashin biyayya. Ka na iya ba da cikakke ma'ana wannan bayyani a bayyane.
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na goma sha shida. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 121-128 ta fara da wannan harafi.
"kada ka bar mutane su tsananta mani"
Marubuci ya yi magana game da kansa kamar "bawanka." AT: "Ka tabbatar da lafiya na" ko "Ka taimaka kuma ka kare ni, bawanka"
Wannan siffa maras muhimmanci za'a iya bayyana ta kamar wani siffa. AT: "waɗanda suna da girman kai" ko "mutane masu girman kai"
A nan "idanu" na gabatad da dukkan mutum. AT: "Na gaji saboda na yi ta jira sosai"
Suna mai zuzzurfar ma'ana "ceto" za'a iya bayyana ta kamar yadda a fi'ili. AT: "gama ka cece ni kamar yadda ka alƙawarta ka yi"
A nan "magana" na gabatad da abin Allah ke sanad da mutane. AT: "alƙawarin adalcinka"
Marubuci na magana game da kansa kamar "bawanka." AT: "Ka nuna mani" ko "Ka nuna mani, bawanka"
Suna mai zuzzurfar ma'ana "amincin" za'a iya bayyana ta kamar yar bab ko siffa. AT: "cewa kana kaunar na da amincin" ko "cewa kana da aminci gare ni saboda alƙawarinka"
Suna mai zuzzurfar ma'ana "fahimta" za'a iya bayyana ta kamar yadda a fi'ili. AT: "ka ba ni dama in fahimta abin da kake so da ni in sani"
Marubuci yana magana da Yahweh kamar da mutumin da ake yin magana a kansa. Wannan za'a iya bayyana ta a mutumin na biyu. AT: "Lokaci ya yi ka yi aiki, Yahweh"
Wannan salon zance ne. Anan "sun karya" na nufi "rashin biyayya." Wannan shine hanyar cewa mutane suna rashin biyayya da shari'ar Allah.
Mutum yana biyayya da dukkan umarnin Allah a hankali an yi magana game da sai ka ce umarnin suna bida mutum kuma cewa zai bi daga baya. AT: "Na yi biyayya da dukkan umarninka a hankali"
Mutane masu yi abin da ke mugu an yi magana game da sai ka ce suna tafiya akan hanya da ba daidai ba. AT: "dukkan hanyoyin marasa kyau da wasu mutane ke zama"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na goma sha bakwai. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 129-136 ta fara da wannan harafi.
Marubuci ya yi magana game da maganar Yahweh sai ka ce waɗannan maganar masana'anta ne wanda an naɗe, kuma gae da mutum wamda ke bayyana maganar Yahweh sai ka ce suna buɗe wancan masana'anta. AT "Bayyani maganarka suna bada haske" ko "Sa'ad da wani ya bayyana maganarka, sun bada haske"
Marubuci ya yi magana game da maganar Yahweh yana bada hikimar ga mutum sai ka ce maganarsa suna bada haske akan su. AT: "Bayyani maganarka na ba mutane hikima"
Marubuci ya yi magana game da marmarinsa domin dokokin Yahweh sai ka ce shi Kare tana haki domin ruwa. AT: "Na yi marmari da naciya domin dokokinka"
A juya zuwa ga wani na nufi da sa hankali da wancan mutum. AT: "Sa hankali a kan na"
A nan kalma "suna" na gabatad da Yahweh da kansa. AT: "ƙaunarka"
A nan kalma "ƙafafu" na gabatad da marubuci sai ka ce yana yin tafiya. Ya yi magana game da hanyar da yake zama, ko gudanarwarsa, sai ka ce yana yin tafiya akan hanya. AT: "Bida ni" ko "Koya mani yadda zan zauna"
Marubuci na magana game da zunubi sai ka ce ita mutum ne wanda yana da izni a kan sa. Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "kada ka bar wani zunubi ya zama jiki gare ni" ko 2) kada ka bar mutane masu zunubi su yi mulki a kaina"
Kalmar "zalunci" za'a iya fassara ta kamar yadda a fi'ili. AT: "Ka cece ni daga mutane wanda suke zalunta wasu"
Marubuci na magana game da Yahweh yana addashin abun alfarma zuwa gare shi sai ka ce fuskan Yahweh ya haskaka akan sa. AT: "Yin abun alfarma zuwa ga bawanka"
Marubuci ya yi magana game da hawayensa masu yawa sai ka ce sune ƙoramun ruwaye. AT: "hawaye masu yawa"
"biyayya da shari'arka"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na goma sha takwas. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 137-144 ta fara da wannan harafi.
Sauran mai yiwuwa ma'ana sune "shaidar" ko "dokokin." Duba yadda ka fassara wannan a 78:5.
Wannan shine salon zance. Jimla ita ce ƙara azama kuma shine adadin jawabi wanda ke nuna ƙara azama na "Ina fushi mai tsanani."
Wannan za'a iya bayyana ta cikin fo mai ƙuzari. AT: "Na jaraba maganarka sau da yawa"
Marubuci ya yi magana game da kanasa sai ka ce wani mutum dabam ne. AT: "Ni, bawanka, ina ƙauna" ko "Ina ƙauna"
Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai ƙuzari. AT: "Mutane suna rena ni"
Marubucin zabura ya yi magana game da wahala da azaba sai ka ce su mutane ne. AT: "Na zama wanda an wahalar da wanda an ɓakantar rai" ko "jikina da zuciyana na shan wahala"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na goma sha tara. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 145-152 ta fara da wannan harafi.
Marubucin zabura ya yi magana game da dukkan kasancewarsa sai ka ce ita ne zuciyarsa kadai. AT: "gaba daya"
Sauran mai yiwuwa ma'ana sune "shaidar" ko "dokokin." Duba yadda ka fassara wannan a 78:5.
"Kafin rana ya bayyana da farko"
Wannan shine salon zance. Cikin al'adun Hebraniyawa, yawanci an raba dare cikin uku "lura da" ko kayadadden lokaci. AT: "Ina farke dukkan dare"
Marubucin zabura ya yi magana game da abin da ya na ce sai ka ce ita ne murya da ya na yin amfani don magana. AT: "ka saurari abin da na ce saboda alƙawarin amincinka" (Dubi:|Metonymy)
"sun bata daga shari'arka" ko "ba su sa wani hankali ga shari'arka ba" (UDB)
Suna mai zuzzurfar ma'ana "amintacce" za'a iya fassara ta ta yin amfani da fi'ili "amince da." AT: "Ina iya amince da umarnanka"
Sauran mai yiwuwa ma'ana sune "shaidar" ko "dokokin." Duba yadda ka fassara wannan a 78:5.
Marubucin zabura ya yi magana game da dokokin Yahweh sai ka ce an ƙafa sune tari cikin ƙasa. AT: "bayar da su don mutane su yi biyayya"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na ashirin. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 153-160 ta fara da wannan harafi.
Marubucin zabura ya yi magana game da ƙunci sai ka ce ita wani abu ne da mutane zasu iya gani. AT: "Ka dubi yadda ina shan wahala"
"Ka kare ni daga masu dora mani laifi"
"Ka kare rai na" ko "ka ba ni rai"
Marubucin zabura ya yi magana game da ceto sai ka ce ita abun jiki ne. Suna mai zuzzurfar ma'ana "ceto" za'a iya fassara ta ta amfani da fi'ili "ceta." AT: "Lalle ba zaka cece mugaye ba"
A nan "girma" na nufi "da yawa." "Ka nuna jinkai ga mutane sau da yawa" ko "Ka yi abubuwa na jinkai masu yawa"
Wani mai yiwuwa ma'ana shine "saboda ka yi abin da ke daidai."
Suna mai zuzzurfar ma'ana "masu zaluntata" za'a iya fassara ta ta amfani da fi'ili "zalunta." AT: "Waɗanda suna zalunta na"
Wannan shine salon zance. "Ban tsaya da yin biyayyan ba" ko Ban tsaya da gaskantawa ba"
Sauran mai yiwuwa ma'ana sune "shaidar" ko "dokokin." Duba yadda ka fassara wannan a 78:5.
Siffan "maciya amana" za'a iya fassara ta kamar yadda a jimlar suna. AT: "mutane maciya amana" ko "waɗanda sun ci amana na" ko "abokan gaba na"
"ba sa biyayya da"
"Sanarwa" ko "Duba ni don haka zaka iya gani"
"Maganarka gaskiya ne gaba daya" ko "Za'a iya amince da maganarka"
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na ashirin da daya. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 161-168 ta fara da wannan harafi.
Marubucin zabura ya yi magana game da zuciya sai ka ce tana iya rawar jiki da zaman tsoro. Zuciya kalma ne
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) abubuwa da sojoji da yan fashi sukan ɗauka daga waɗănda sun ci su cikin yaki ko 2) abubuwa masu girman daraja ko "dukiya mai yawa."
Waɗannan kalmomin biyu na nufin kusan abu daya. AT: "ƙin kwarai da karfi"
Mai yiwuwa ma'ana sune wannan kalma ne da ake amfani a madadin suna wani martaba, don 1) "mutane masu karya" ko 2) "kalmomin karya wanda mutane sun ce."
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "ba abin da zai sa su yi ba daidai ba" ko 2) "ba abin da sa su tuntuɓe."
"Ina yin biyayya da dokokinka tabbatattu"
Sauran mai yiwuwa ma'ana sune "shaidar" ko "dokokin." Duba yadda ka fassara wannan a 119:1.
"Ina biyayya da umarninka
Wannan shine sunan baki haruffan Hebraniyawa na ashirin da biyu. Cikin harshe Hebraniyawa, kowane layi na ayoyin 169-176 ta fara da wannan harafi.
Marubucin zabura ya yi magana game da ƙwazo don fahimta sai ka ce tana nan ne abu mai kauri. AT: "Ka taimake ni in fahimta maganarka"
Marubucin zabura ya yi magana game da kalmomin da ya ce cikin addu'a sai ka ce sune mutane wanda sun so magana da sarki. AT: "Bari ka ji addu'ar na"
Marubucin zabura ya yi magana game da leɓunansa sai ka ce sune ganga kuma yabonsa ruwa ne da za'a iya zubawa. Anan kalman "leɓuna" kalma ne da aka yi amfani da ita a madadin dukkan mutum. AT: "Ina marmarin yabonka kwarai"
Marubucin zabura ya yi magana game da harshensa ko dai 1) Sai ka ce ita mutum ne ko 2) kamar yadda a sydecdoche domin dukkan kasancewansa. AT: "ni in yi waka"
Hannun synecdoche wato ita kalma nan da ke a turance da an yi amfani da ita a madadin dukkan mutum. AT: "Don Allah ka taimake ni"
"na zaɓi in yi biyayya"
Suna mai zuzzurfar ma'ana "ceto" za'a iya bayyana ta kamar yadda a fi'ili. AT: "kai don cetona"
Suna mai zuzzurfar ma'ana "farinciki" za'a iya bayyana ta kamar yadda a fi'ili. "Ina matukan jin daɗi yin biyayya da shari'arka"
Marubucin zabura yayi magana game da dokokin Yahweh sai ka ce su mutum ne wand za'a iya taimake shi. AT: "bari in kasa kunne akan dokokinkana adalci don haka kuma in zama da hikima da ƙarfi"
"Na bar hanyarka kamar tunkiya da ta bar garkenta"
"domin ni bawanka ne, zo kuma domin ka bincike ni"
1A cikin ƙuncina nayi kira ga Yahweh, ya kuma amsa mani.2Ka ƙwato raina, Yahweh, daga waɗanda ke ƙarya da leɓunansu da ruɗi da harsunansu.3Ta yaya zai hore ka, mene ne kuma zai ƙara yi maka, kai wanda ke da harshe na ƙarya?4Zai hore ka da kibiyoyin mayaƙi da aka wãsa bisa garwashin wutar ƙiraren itace.5Kaito na saboda ina zaune jim kaɗan cikin Meshek; Dã na zauna a rumfunan Keda.6Har dogon lokaci na zauna tare da waɗanda suka ƙi salama.7Ni domin salama nake, amma idan na yi magana, domin yaƙi suke.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin su ne kamar matakai."
"Cikin damuwarna" ko "Sa'ada ina cikin damuwa"
A nan kalmar "rayuwa" na gabatad da mutum. AT: "Ka cece ni"
A nan jimlar "leɓunansu" da "harsunansu" na gabatad da mutum wanda yana maganar karya da yaudara. AT: "masu yi mani ƙarya da kokari su ruɗe ni"
Marubuci ya roki wannan kamar tambaya mai jagora ne don bayyana abin da Allah zai yi da makaryata. Wannan tambaya za'a iya fassara ta kamar yadda a bayyani. AT: "Wannan shine yadda Allah zai horar da kai, kai wanda ka ke da harshen karya"
A nan "harshe na ƙarya" na gabatad da mutum wanda yana maganar karya. AT: "Kai wanda ke faɗin karya"
Marubuci ya yi magana game da Allah na horo mai tsanani makaryata sai ka ce Allah yana harbin su da kibiyoyi. AT: "Zai hore ka mai tsanani, sai ka ce yana harbin ka da kibiyoyin mayaƙi"
Wannan na nufin da yadda mutane kan kirkira bakin marshi a cikin wuta. Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai kuzari. AT: "cewa ya wãsa bisa garwashin wutar ƙiraren itace"
Waɗannan wuraren biyu suna nisa daga nan kowace sauran. Marubuci wata kila ne na yin amfani da sunaye musili don gabatad da zama a tsakanin azzalumai da jahilai mutane. AT: "tana sai ka ce ina zaune cikin Meshek ko a tsakanin rumfunan Keda"
Wannan jimla na gabatad da mutane Keda wanda suna zaune cikin waɗancan rumfunan. AT: "Mutanen da ke zaune cikin Keda"
"Ina son salama"
"suna son yaƙi"
1Zan ɗaga idanu na ga duwatsu. Daga ina taimakona zai zo?2Taimakona na zuwa daga Yahweh, wanda yayi sama da duniya.3Ba zai bar sawunka ya zãme ba; shi wanda ya ke kiyaye ka ba zai yi gyangyaɗi ba.4Duba, mai lura da Isra'ila ba zai taɓa gyangyaɗi ba ko barci.5Yahweh shi ne mai lura da kai; Yahweh shi ne inuwa a hannun damanka.6Rana ba zata cutar da kai ba da rana, ko kuma wata da daddare.7Yahweh zai kiyaye ka daga dukkan cutarwa, kuma zai kiyaye ranka.8Yahweh zai kiyaye ka cikin dukkan abin da kake yi yanzu da har abada abadin.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin su ne kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
Wannan magana na nufi "Dubi" ko "mayar da hankali na a kan."
Marubuci ya yi amfani da wannan tambaya don ya mayar da hankali akan tushin taimakonsa. Wannan tambaya da ba ta damu da amsa ba za'a iya fassara ta kamar yadda yake a bayyani. AT: "Zan gaya maka daga ina taimakona za ya zo."
Wannan shine amsar na tambaya baya.
Akwai motsi anan zuwa ga mutum na biyu. Wanna mai yiwuwa na nufi 1) marubucin ya fara yin magana zuwa ga mutanen Isra'ila ko 2) marubucin yana ɗauko fadar wani mutum yana magana zuwa ga marubucin.
Zãmewa sawun a hade yake da fadowa. AT: "kai ka faɗi"
Waɗannan jimla biyu na nufi da abu daya, kuma na jadada matsayin Allah kamar wani mai tsaro.
A nan wa "gyangyaɗi" na nufi zai daina yin tsaro. Fom mara muhimminci na qarfafa bayyanin. AT: "Allah ba zai faɗi barci ba kuma ba zai daina tsaron ka ba" ko "Allah zai tsare ka ko da yaushe"
A nan "inuwa" na nufin da kariya. AT: "Allah yana a gefena don ya kare ni daga abubuwa da zai raunata ka"
A nan wannan bayyani na nufi da zama a gefen ko kusa da marubucin.
Sharuddan mai banbancewa "rana" da "dare" na nufi da waɗannan matuka da kowane abu a tsakanin. AT: "Allah yana kare ka daga abubuwa dukkan lokatai"
Tana nuna cewa "ba zai cuce ka ba" an nuna ta anan. Cikakkeyar ma'ana wannan bayyani mai yiwuwa a mai da ita mai sauƙin ganewa. AT: "ko kuma wata da zai cuce ka da dare"
Waɗannan jimla dukka suna da ma'ana mai kama. Maimaitawan ta kara karfafa ra'ayoyin.
Wannan tana nufin zuwa ga marubucin. AT: "kai"
1Nayi farinciki da suka ce mani, "Bari mu tafi gidan Yahweh."2Yerusalem, sawayenmu na tsaye cikin ƙofofinki!3Yerusalem, an gina ki birnin da aka yiwa shiri a hankali!4Kabilun suna tafiya Yerusalem - kabilun Yahweh - a matsayin shaida ga Isra'ila, su bada godiya ga sunan Yahweh.5An kafa kursiyoyin hukuncinsu, kursiyoyin gidan Dauda.6Kuyi addu'a domin salamar Yerusalem! "Bari masu ƙaunar ki su sami salama.7Bari salama ta kasance cikin katangogin dake kãre ki, bari kuma su sami salama cikin ƙarfafan wurin tsaronki."8Domin albarkacin 'yan'uwana da abokaina zan ce, "Bari salama ta kasance a cikin ki."9Domin albarkacin gidan Yahweh Allahnmu, zan biɗi alheri game dake.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
Marubuci a takaice ya tsayad da yin magana da masu sauraronsa kuma yana magana kai tsaye zuwa ga birnin Yerusalem. Yerusalem ita ce an yi magana ga sai ka ce ita mutum ne wanda zai ji marubucin.
A nan "sawaye" na nufin da dukkan mutum. AT: "muna tsaye"
A nan "ƙofofin" na nufin da birnin. AT: "cikinka, Yerusalem"
A nan "suna" na nufin da Yahweh da kansa. AT: "Yahweh"
A nan "gida" na nufin da zuriyar Dauda. AT: "zuriyar Dauda"
Wannan sashi na bayyana wadatacce addu'a wanda marubucin yana son masu sauraronsa su yi addu'a. Ya na rokon su su yi magana kai tsaye zuwa ga birnin Yerusalem, sai ka ce birnin mutum ne wanda zai ji su.
Waɗannan jimla biyu suna da ma'ana daya kuma sune an yi amfani tare don karfafa juna"
A nan Yerusalem an mai da ita da sansani ƙatangogi da ke kãre ta. Kalman "ƙatangogi" da "sansani" na nufin abu daya. AT: "cikin Yerusalem"
Cikin wannan sashi, marubuci ya yi magana kai tsaye zuwa ga birnin Yerusalem, sai ka ce birnin mutum ne wanda zai ji mu.
"Domin ƙyau-kasancewa"
"Na yi addu'a cewa mutane cikinka zasu zauna cikin salama"
Suna mai zuzzurffar ma'ana "alheri" za'a iya bayyana ta kamar yadda a wani mataki. AT: "armarin cewa mutane suna bi da kai da ƙyau"
1A gare ka na ɗaga idanuna, kai wanda kake bisa kursiyi a sammai.2Duba, kamar yadda idanun bãyi ke duban hannun ubangijinsu, kamar yadda idanun baiwa ke duban hannun uwargijiyarta, haka idanunmu ke duban Yahweh Allahnmu har sai ya nuna mana jinƙai.3Kayi mana jinƙai, Yahweh, kayi mana jinƙai, domin cike muke da wulaƙanci.4Mun ma fi cike da ba'ar masu ba'a da kuma renin masu fahariya.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
A nan mawallafi na nufin da idanunsa saboda cewa gabban jiki ne da a ke amfani domin gani. AT: "Na duba gare ka"
Waɗannan jimla biyu na da ma'ana mai kama. Jimlar na uku, game da Isra'ilawa ne, an kwatanta ta yadda bãyi da baiwa na duba ubangijinsu da uwargijiyarsu domin taimako. A cikin kowace harka "idanu" na nufin da dukkan mutum.
A nan "hannun" na nufin da tanadi don bukatun. AT: "tanadi ubangijinsu ... tanadi uwargijinsu"
Suna mai zuzzurffar ma'ana "jinƙai" za'a iya bayyana ta kamar yadda a wani mataki. Dubi yadda ka fassara jimlar mai kama da ita cikin 123:1. AT: "yi mana jinkai"
Waɗannan jimla biyu na da ma'ana mai kama, tare da na biyu yana kara tsanani na farkon
A nan wulaƙanci an yi magana ne game da sai ka ce wani abu ne da zai zama cike a mutum. "an ci mana mutuncin"
Wannan salon zancen na nufi da cewa adadin ya wuce kima, irin ta masu 'ba'. AT: "Mun dandana fiye da"
Akwai jimla biyu da ke da ma'ana masu kama kuma an yi amfani da su tare don a jadada yawan yadda sun kasace da ba'a daga mutane.
1"Idan da ba don Yahweh yana gefenmu ba," bari Isra'ila suce yanzu,2"Idan da ba don Yahweh yana gefenmu ba sa'ad da mutane suka taso gãba da mu,3daga nan da sun haɗiye mu ɗungum da rai sa'ad da fushin su ya wo hauka gãba da mu.4Da ruwa ya share mu; igiyoyin da sun sha ƙarfinmu.5Daga nan haukan ruwayen da ya shanye mu."6Albarka ta tabbata ga Yahweh, wanda bai bari haƙoran sa suka yayyage mu ba.7Mun kucce kamar tsuntsu daga tarkon mafarauta; tarkon ya karye, mun kuma kucce.8Taimakonmu yana cikin Yahweh, wanda ya yi sama da ƙasa.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
Wannan misali Bayyani ne da ke bayyana wani sakamakon wanda bai faru ba, domin hakika Yahweh yana gefensu. AT: "Yahweh yana gefenmu ... don haka ba su iya haɗiye mu ɗungum da rai"
Waɗannan jimla biyu na nufin abu daya. AT: "Da ba tare da taimakon Yahweh ba ... da ba tare da taimakon Yahweh"
Wannan karin magan yana bayyana yadda Isra'ilawa da zai mutu da yadda dabba mai ban tsoro zai kai hari wa wani karami dabba domin ya cinye. AT: "kashe mu"
Cikin Waɗannan ayoyi biyu mawallafi yana kwatanta abokan gaba na Isra'ila da ambaliyan ruwa.
Wannan yana ci gaba da misali bayyani ne daga aya na baya. Tana bayyana sakamakon da bai faru ba, domin Yahweh hakika yana gefenmu. AT: "Ruwan bai share mu ba ... bai haɗiye mu ba"
Waɗannan jimla na nufin abu daya.
Waɗannan jimlar na nufin da abu daya.
A nan abokan gaba marubucin an yi magana game da sai ka ce su ambaliya ruwa ne. AT: "Abokan gaban mu zasu ci nassara akan mu da sauri"
Abokan gaban au ne an yi magana game da su sai ka ce su dabobin daji ne da zai hallakar da Isra'ilawa ta wuri cin su. AT: "hallakar sai ka ce sun cinye mu ta wuri dabobin daji"
Marubucin ya bayyana kuɓucewansa daga abokan gaba sai ka ce shi tsuntsu ne wanda ya kuɓuce daga tarkon mafarauta. AT: kuɓuce daga abokan gaban mu kamar wani tsuntsu da ta kuɓuce daga tarkon da mafarauta sun sa" (UDB)
wani karami tarko na igiya ko waya da an yi domin a kama kanana dabobi ko tsuntsaye
Mãkircin abokan gaba don su kama marubuci ya kasa sai ka ce ita wani tarko ne da an karye.
1Waɗanda suka sa dogararsu ga Yahweh suna kama da Tsaunin Sihiyona, marar jijjiguwa, mai dawwama har abada.2Kamar yadda duwatsu suka kewaye Yerusalem, haka Yahweh ya kewaye mutanensa yanzu da har abada.3Sandar mulkin mugunta ba za tayi mulki ba a ƙasar mai adalci. Idan ba haka ba mai adalci zai iya yin abin da ba dai-dai ba.4Kayi da kyau, Yahweh, ga waɗanda suke yi da kyau waɗanda kuma suke masu adalci a zukatansu.5Amma ga waɗanda suka kauce gefe ga karkatattun hanyoyinsu, Yahweh zai kawar dasu tare da masu aikata mugunta. Bari salama ta kasance a Isra'ila.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
Mutane wanda suna dogara cikin Yahweh an yi magana anan sai ka ce sune Tsaunin Sihiyona. Tsaunika basu iya jijiguwa.
Kariyan Yahweh shine an yi magana a kai sai ka ce shine tsaunikan da ke kewaye Yerusalem. Yerusalem na kewaye da tsaunika da yawa, wanda ta kare ta daga hari. AT: "Kamar yadda duwatsu ke kewaye da Yerusalem tana kare ta, haka ne Yahweh yana kare mutanensa" (UDB)
A nan sandar mulkin mugunta na gabatada da mulkin miyagun mutane. AT: "miyagun mutane" ko "miyagun sgugabanni"
Wannan roko ne. Suna mai zuzzurfar ma'ana "kyau" za'a iya bayyana ta kamar yadda wani mataki, AT: "Yahweh, don Allah kayi abubuwa masu kyau" ko "Yahweh, na roke ka don kayi abubuwa masu kyau"
A nan, "zukata" na nufin da marmarinsu. AT: "marmari don yin gaskiya"
Kin yi wa Yahweh biyayya an yi magana kamar yadda juyawa daga hanya mai kyau. AT: "bar kyau kuma tafi"
A nan mugu hanyoyi sune an yi magana a kan sai ka ce su hanya ne da ba ta da maidaidaiciya. AT: :"mugaye hanyoyinsu"
An kawar da mutane domin horon su. Cikakke ma'ana wannan bayyani za'a iya sa ta a bayyane. AT: "kawar dasu tare don horon su"
1Sa'ad da Yahweh ya maido da kadarorin Sihiyona, mun zama kamar masu mafarki.2Daga nan bakunanmu suka cika da dariya harsunanmu kuma da waƙa. Daga nan suka ce a tsakanin al'ummai, "Yahweh ya yi masu manyan abubuwa."3Yahweh ya yi mana manyan abubuwa; mun kuwa yi murna!4Ka maido da kadarorinmu, Yahweh, kamar rafuffukan Negeb.5Su waɗanda suka yi shuka cikin hawaye zasu yi girbi tare da sowace-sowacen farinciki.6Shi wanda ya fita da kuka, yana ɗauke da irin shuka, zai sake dawowa da sowace-sowacen farinciki, yana kawo dammunansa tare da shi.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
"sa Sihiyona ya sami arziki kuma"
Yin dariya an yi maganan ta sai ka ce bakunansu shine gangan kuma dariyarsu ya ke cikin ta. za'a iya bayyana cewa wannan dariyan amsa ne zuwa ga murnarsu. AT: "mun yi dariya don murna"
Fi'ilin "suna cika" za'a iya bayyana ta a bayyane. Rera waka an yi magana ta anan sai ka ce harsunansu su ne ganga da kuma rera waka na cikin su. AT: "harsunanmu sun cika rerawar waka" ko "mun rera waƙoƙin murna"
"mutanen al'ummai sun ce a tsakani kansu." An yi amfani da wakilin suna kafin an gabatar da abin da tana nassoshin. Wannan sabon abu ne sosai.
"Mun kuwa yi murna, domin Yahweh ya yi waɗannan abubuwan masu girma domin mu!"
Waɗannan ayoyin biyu na farallel da kowace sauran. Jumla na biyu yana da ma'ana daya kamar yadda a jumla na farkon, amma tana bayar mafin yawa bayyanin filla-filla.
"Su waɗanda suka shuka tare da hawaye"
1Sai idan Yahweh ne ya gina gida, sun yi aikin banza, su waɗanda ke ginin. Sai idan Yahweh ne yayi tsaron birni, masu tsaron suna tsayawa tsaro a banza.2Aikin banza ne a gare ka ka tashi da wuri, ka dawo gida da latti, ko ka ci gurasar aiki tuƙuru, domin Yahweh yana biyan buƙatun masu ƙaunarsa yayin da suke barci.3Duba, 'ya'ya gãdo ne daga Yahweh, kuma ɗiyan mahaifa lada ne daga gare shi.4Kamar kibiyoyi a hannun mayaƙi, haka nan 'ya'yan ƙuruciyar mutum.5Yaya albarkar mutumin da yake da kwarinsa cike da su. Ba zai sha kunya ba sa'ad da ya fuskanci maƙiyansa a ƙofa.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
Mutum wanda yake aikin ƙwarai sau da yawa ya kan tashi da wuri da safe kuma ya koma gida da latti da dare.
Wannan shine salon zance. Gurasar sau da yawa na gabatad da abinci da mutum ke bukata kowace rana domin ya rayu. AT: "yi alki tuƙuru domin bukatun ka na yau da kullum"
"kyauta" ko "mallaka mai daraja". 'Ya'ya kullum suna karɓa gãdo daga iyayensu. Gãdo yake tafi daga iyaye zuwa ga 'ya'ya. Wannan maganar da aka tsinto daga littafi na nufi da 'ya'ya kamar gãdon iyayensu.
Kibiyoyi suna da muhimmanci sosai zuwa ga mayaƙi sadoda suna kare shi a cikin yaƙi. 'Ya'ya haka aka yi magana game da su sai ka ce su ne kibiyoyin mayaƙi. AT: "Samun 'ya'ya zai taimaka don kare ka"
Kwarin shine abun da ake ajiye kibiyoyin. Samun 'ya'ya aka yi magana game da su sai ka ce 'ya'ya sune kibiyoyin cikin kwarin. AT: "gida da ke cike da 'ya'ya" ko "'ya'ya masu yawa"
1Mai albarka ne duk wanda ya girmama Yahweh, wanda ya ke tafiya cikin hanyoyinsa.2Abin da hannuwanka suka wadatar, zaka ji daɗin sa; zaka yi albarka da wadata.3Matarka zata zama kamar inabi mai bada 'ya'ya a cikin gidanka; 'ya'yanka zasu zama kamar itatuwan zaitun yayin da suka zauna kewaye da teburinka.4I, tabbas, mutumin zai zama mai albarka wanda ya ke girmama Yahweh.5Bari Yahweh ya albarkace ka daga Sihiyona; bari kaga wadatar Yerusalem dukkan kwanakin rayuwarka.6Bari ka rayu ka ga 'ya'yan 'ya'yanka. Bari salama ta kasance bisa Isra'ila.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
Wannan jimla ya auku cikin murya mai goyan baya don kauce wa da yana nufa cewa wajibi ne Yahweh ya albarkace waɗanda ke darajanta shi. Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai ƙuzari. AT: "Yahweh zai albarkace kowa da kowa wanda ke darajanta shi"
Za'a iya kiran mutum ta wurin hannuwansa saboda cewa gabban jiki ne da ya ke ayyuka da shi. AT: "Abin da ka tanada" ko "Abin da ka yi aiki don"
Kalman "yi albarka" da "wadata" na raba ma'ana mai kama kuma tana jadada Alherin Allah. AT: "Yahweh zai albarkace ka ya kuma wadata ka" ko "Yahweh zai sa ka zama mai albarka da kuma mai arziki"
Matar ne an yi magana game da ita kamar inabi mai ba da 'ya'ya masu yawa. Wannan na nuna cewa 'ya'ya suna kamar 'ya'yan itace kuma matar aure zai zama da 'ya'ya masu yawa. AT: "ba da 'ya'ya sosai kuma ba ka yara masu yawa"
An kwatanta 'ya'ya da itatuwan zaitun saboda yadda su kan yi girma su kewaye wani abu. 'Ya'yan zasu kewaye tebur kuma su sa ta cika. AT: "zaka zama da 'ya'ya masu yawa wanda zasu yi girma kuma su ɓunkasa"
Wannan na nufin da wuri inda iyali na taru su ci abinci. Sau da yawa, dukkan waɗanda ke cin abinci a teburin mutum suna karkashin ikon ko mulkinsa
Wannan za'a iya bayyana ta kamar yadda wani fi'ili mai ƙuzari. "Yahweh zai albarkace mutumin wanda yana girmama shi"
"cikin rayuwarka"
1"Sau da yawa tun ƙuruciya ta suke kawo mani hari," bari Isra'ila yace.2"Sau da yawa tun ƙuruciya ta suke kawo mani hari, duk da haka ba su kayar dani ba.3Masu huɗa suna huɗa bisa bayana; sunyi kuyyoyinsu da tsawo.4Yahweh mai adalci ne; ya datse igiyoyin mai mugunta."5Bari dukkan su su sha kunya su kuma koma baya, su waɗanda suka ƙi jinin Sihiyona.6Bari su zama kamar ciyawar dake bisa rufin gida wadda ke yaushi kafin ta girma,7wadda ba zata cika hannun mai girbi ba ko ƙirjin mai ɗaure dammuna.8Bari waɗanda ke ratsawa su wuce kada su ce, "Bari albarkar Yahweh ta kasance a kan ka; mun albarkace ka a cikin sunan Yahweh."
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
Sara daga bulala da suke magana game da ita kamar yadda garma na mutum mai garma. Manomi ya huɗa mai zurfi layi cikin sauran. AT: "Abokan gaba na sun yanka ni da zurfin kwarai bisa bayana"
Wannan shine ci gaba na yin huɗa karin magana. "Kuyyoyin" layi ne da manomi ya ke huɗa. AT: "sunyi yanka da tsawo"
An yi magana game da Isra'ila kamar kasancewa iyaka da miyagu mutane. AT: "ya yantas da mu daga abokan gaban mu"
Yahweh bai ambata baro-baro kamar yadda wani wanda ya yi waɗannan abubuwa ba. Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai ƙuzari. AT: "Bari Yahweh ya kunyatar da su kuma ya ba su kashi"
Marubuci zabura yana magana game da abokan gabansa na mutuwa kuma na kasance kankanci a lamba. Suka kwatanta su da karami ragama ciyawa da ke girma bisan jinkan gida da ya yi yaushi kuma bai isa don yanka ko a daura ba. AT: " Bari su mutu kuma bari ya zama akwai kadan daga cikin su da zasu zama kamar da ciyawa ... dammuna"
"Yahweh ya albarkace ka"
1Daga zurfafa nayi kuka gare ka, Yahweh.2Ubangiji, ka ji murya ta; bari kunnuwanka su saurari roƙe-roƙe na domin jinƙai.3Idan kai, Yahweh, zaka kula da kurakurai, Ubangiji, wane ne zai iya tsayawa?4Amma akwai gafartawa tare da kai, saboda a girmama ka.5Nayi jira domin ka Yahweh, raina yana jira, kuma a cikin maganarsa nake da bege.6Raina yana jira domin Ubangiji fiye da yadda masu tsaro ke jira domin safiya.7Isra'ila, kuyi bege cikin Yahweh. Yahweh yana cike da jinƙai, kuma yana da nufin gafartawa sosai.8Shi ne wanda zai fanshi Isra'ila daga dukkan zunubansa.
Ana samun daidaici a wakokin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
An yi magana game da bakinciki mawallafin sai ka ce ita wani ganga ne. Bakincikinsa ya kan zo ne daga kasan gangan. Sau da yawa a kan yi magana game da bakinciki kamar kasance wani ganga da ke cike daga bisan zuwa kasa. AT: "Domin ina da bakinciki,"
Kunnuwa na gabatad da Yahweh, amma saboda marubucin ya sani cewa Yahweh yana jin kowane abu, yana tambayar da gaske don Yahweh ya amsa. AT: "don Allah kasa kunne" ko "don Allah amsa"
"Jinkai" ba wani abu ba ne da za'a ta jiki ba wa kowa. Mawallafi ya yi tabayar domin Yahweh ya zama mai jinkai zuwa gare shi. AT: "zuwa ga roke-roke na da kuma zama mai jinkai zuwa gare ni"
Mai magana ya yi amfani da wannan tambaya don bayyana banza tunani cewa kowa zai iya tsayawa cikin wannan hali da ake ciki. Wannan tambaya da ba ta damu da amsa ba za'a iya fassara ta kamar yadda wani bayyani. AT: "ba wani da zai iya tsayawa."
"Tsayawa" sau da yawa na gabatad da gudu ko tsira sa'ad da wani zai kai farmaki. A wannan hali, za ta zama gudun daga kasancewa azabtar. AT: "ba wani da zai iya gudun daga horonka" ko "ba wani da zai iya tsira daga horonka"
"Raina" na gabatad da marubucin zaburan. AT: "ni"
Marubuci zabura an yi magana game da shi sai ka ce yana jiran wani abu ne tare da fata. AT: "Ina ɓege" ko "Ina dogara" ko "Ina marmarin domin wani abu"
Marubucin zabura yana magana game da marmarinsa domin Ubangiji ya taimake shi kamar yadda ya kasance da girma fiye da marmarin waɗanda suke aiki dukkan dare suna dashi domin safiya ta zo. (Dubi: [[rc://*/ta//man/translate/figs-simile]])
Waɗannan sune mutane wanda suke tsare garuruwa ko sauran daga abokan gaba ko yan fashi. Anan tana nufin da mutane wanda sukan tsaya a faɗake da dare suna yin wannan.
Mutanen Isra'ila an yi magana game da su sai ka ce su wani mutum ne. AT: "mutanen Isra'ila ... su" ko "mu mutane Isra'ila ... mu"
1Yahweh, zuciyata ba tayi fahariya ba ko idanuna suyi tsauri. Bani da manyan bege domin kaina ko in dami kaina da abubuwan da suka sha kaina.2Tabbas na tsaida kuma na tausar da raina; kamar ɗan da aka yaye tare da mahaifiyarsa, raina a ciki na kamar ɗan yaye ya ke.3Isra'ila, kasa bege cikin Yahweh yanzu da har abada.
An samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
Zuciyan da idanun na gabatad da mutum. AT: "Ba na yi fahariya ko girman kai"
Mai yiwuwa ma'ana sune "Bani da fata yi abubuwa masu girma" ko "bani da tunani ina da girma."
Abubuwan da suka sha kan mutum ya fahimta an yi magana game da ita sai ka ce sun sha kan mutum ko fiye da yadda nisa daga nan daga mutum don ya iya kai su. AT: "abubuwan da suke da wuya kuwa fahimta"
Rai na gabatad da mutum ko motsin zuciyarsa. Kasancewa kwantad da hankali da kuma zaman lafiya an yi magana game da yana sa rai wani har yanzu da shiru. AT: "Ina kwantad da hankali da zaman lafiya"
Rai na gabatad da mutum ko motsin zuciyarsa. AT: "Ni"
Marubucin zabura yana magana game da kansa kasancewa wadatacce da yin hutu sai ka ce yana nan karami yaro ba ya bukatar nono daga mahaifiyarsa. AT: "wadatacce kamar karami yaro da ba ya kuka domin nono amma yana hutu cikin hannu mahaifiyarsa" ko "wadatacce da yin hutu"
1Yahweh, albarkacin Dauda ka tuna da dukkan ƙuncinsa.2Ka tuna da yadda ya rantse wa Yahweh, yadda yayi wa'adi ga Mai Iko Dukka na Yakubu.3Yace, "Ba zan shiga gidana ba ko in kwanta a kan gadona ba,4ba zan ba idanuna barci ba ko kuma in rintsa5sai na samawa Yahweh wuri, rumfar sujada domin Maɗaukaki na Yakubu."6Duba, munji haka a Ifrata; mun same shi a jejin Yayir.7Zamu shiga rumfar sujada ta Allah; zamu yi sujada a ƙafafunsa.8Tashi, Yahweh, zuwa wurin hutawarka, kai da akwatin alƙawarinka mai nuna ƙarfinka!9Bari firistocinka su suturta da adalci; bari amintattunka suyi ihu don murna.10Saboda bawanka Dauda, kada ka juya wa zaɓaɓɓen sarkinka baya.11Yahweh ya rantse da tabbatacciyen wa'adi ga Dauda, tabbataccen wa'adi da ba zai janye ba: "Zan naɗa ɗaya daga cikin zuriyarka in sa shi bisa gadon sarautarka.12Idan 'ya'yanka sun yi biyayya da umarnina da kuma dokokin da zan koya masu, 'ya'yansu zasu zauna a gadon sarautarka har abada."13Hakika Yahweh ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa.14"Nan ne wurin hutawana har abada. Zan zauna a nan, gama ina marmarinta.15Zan albarkaceta da yalwar abin da take buƙata, zan ƙosar da matalautanta da abinci.16Zan suturta firistocinta da ceto, amintattunta zasu yi sowa da ƙarfi don murna.17Can zan sa ƙaho ya toho domin Dauda zan kuma kafa fitila domin zaɓaɓɓena.18Zan suturta maƙiyansa da kunya, amma a kansa kambinsa zai yi walƙiya."
Ana samun daidaici na gama gari ne a wallafa waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
"saboda abin da ya faru da Dauda"
"tuna da" ko "yi tunsni akan"
Wannan na nufin da Allah.
"Sarkin Dauda ya ce"
Barci da hutu an yi magana game da ita sai ka ce sune abubuwan da za'a iya bayar. Anan idanun da rintsa na gabatad da dukkan mutum. AT: "ba zan bari idanun tayi barci ko rintsa ta huta ba"
An yi magana game da gina wuri domin Yahweh kamar samun wuri domin sa. AT: "sai na gina wuri domin Yahweh"
Wannan na nufin da Allah.
Kalma "ita" mai yiwuwa na nufin da inda akwati Allah mai tsarki yake. Jimla "a Ifrata" mai yiwuwa na nufin da inda suke lokacin da suka ji game da ita. Wannan za'a iya bayyana ta a fili. AT: "mu da muke a Ifrata mun ji game da inda akwati mai tsarki yake" ko "mu a Ifrata mun ji cewa akwatin mai tsarki yana a Yayir"
Yayir mai yiwuwa wani suna domin birni dake Kiriath Jearim. Wannan mai yiwuwa na nufin da filayen kewaye da birnin.
An yi magana game da yin sujada ga Allah a gaba akwatin alkawari kamar durkusa a kafa sarki wanda yana zaune bisa kursiyensa. Wannan na magana tawali'u da biyayya ga Allah. AT: "zamu je gaban akwati alkawarin Allah kuma mu yi masa sujada kamar sarki"
Wurin da Allah ya zaba domin mutane su yi masa sujada ake magana sai ka ce wuri ne da ya ke hutu ko yahe zaune har abada. AT: "Wurin inda ka tsaya" ko "alfarwarka"
An yi magana game da adalci sai ka ce ita tufafi ne. AT: "Bari mutane su gane cewa firistocinka suna da adalci" ko "Ina son mutane su dubi yadda firistocinka kullum suna yi abin da ke daidai"
"Saboda abin da ya faru da bawanka Dauda." Duba yadda ka fassara jimla mai kama a 132:1.
A nan "juya wa" na nufi da kin wani. AT: "kada ka bari sarkin da ka shafe"
An yi magana game da sa zuriyar sarkin ya zama sarki a wurin sa kamar naɗi shi bisa gadon sarautar sarkin. AT: "Zan sa daya daga zuriyarka ya yi mulki Isra'ila a wurinka"
An yi magana game da yin mulki kamar sarki kamar zama bisa gadon sarautar. AT: "mulki kamar sarki"
A nan "'ya'yanka" na gabatad da zuriyar Dauda cewa zai zama sarki. AT: "zuriyarka"
"Shi", "na" da "ina" na nufin da Yahweh kuma "ta" na nufin da Sihiyona.
Mawallafi yana rubuta kamar yadda ko da yake birni Sihiyona wata mace ne.
Anan "mazaunin na gabatad ko dai 1) kursiyinsa inda zaya yi mulki, ko 2) wurin inda zaya tsaya.
"Yahweh ya yi marmarinta domin mazauninsa." Wannan ya nuna ainihin mahalarta.
Wurin da Allah ya zaba domin mutane su yi masa sujada an yi game da ita sai ka ce tana wurin ne inda yana hutawa ko yana zaune har abada. AT: "wurin inda na tsaya" ko "alfarwarka"
Allah ya ci gaba da yin magana game da birni Sihiyona sai ka ce Sihiyona wata mace ne.
A nan "matalautan" na nufin da matalautan mutane Sihiyona. Anan "gurasa" mai yiwuwa na gabatad da abinci na duka. AT: "zai ƙosar da matalautan mutane cikin Sihiyona da abinci"
"zai yiwa Sihiyona yalwar albarka"
An yi magana game da ceto sai ka ce ita tufafi ne. Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Zan sa firistocin su nuna hali cikin hanya da ta cancanci waɗanda na ceta"
Allah ya yi magana game da ikon zuriyar Dauda sai ka ce ikon ƙaho na wani dabba ne. AT: "Zan sa wani a zuriyar Dauda ta zama sarki bayn shi" ko "Zan sa Dauda ya samu wani a zuriyar wanda zai zama sa ikon sarki"
Allah yana maganar saka zuriyar Dauda ta ci gaba da mulki a masayin sarki sai ka ce sune wani fitila da zai ci gaba da haske. AT: "Zan sa zuriyar zaɓaɓɓena ta ci gaba da mulki a masayi sarki"
"zaɓaɓɓen sarkina" ko "sarkin da na zaɓa"
An yi magana game da kunya sai ka ce ita tufafi ne. Wannan kunya zai zama sakamakon daga rasa nasara a yaƙi. AT: "Zan sa maƙiyansa su zama da kunya" ko "Zan sa maƙiyansa su zama an ci su kuma da sha kunya"
Kambin na gabatad da mulkinsa, da girma aka yi magana game da kamar haske ne. AT: "Zai zama babba sarki" ko "girmansa zai yi haske"
1Duba, yadda ya ke da kyau da kuma daɗi idan 'yan'uwa suka zauna tare!2Wannan yana kama da mai mai kyau a kai dake gangarowa zuwa gemu - gemun Haruna, yana kuma gangarowa har kan wuyar rigarsa.3Kamar raɓar Hermon da take fadowa bisa duwatsun Sihiyona. Gama a nan ne Yahweh ya umarta albarka - rai na har abada.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
Wannan kalma ana yi amfani da shi ne don a ba da karfi akan muhimminci bayyani da yana bi.
Dangantaka a tsakanin 'yan'uwan mutane Allah an yi magana game da ita sai ka ce su 'yan'uwan ne. AT: "idan mutane Allah sun zauna tare cikin salama kamar 'yan'uwan"
An yi magana game da alherin hadin kai a tsakanin mutane Allah sai ka ce tana kama da mai mai kyau da aka zuba a kai Haruna. AT: "Wannan hadin kai tana da daraja kamar da mai mai kyau dake zuba a kai Haruna"
An yi magana game da alherin hadin kai a tsakanin mutane Allah sai ka ce tana kama da raɓar mai wartsake. AT: "wartsakewa kamar da raɓar Hermon"
Wannan shine dutse cikin Isra'ila dake da garin kankara bisa ganiyarta kewayon - shekara.
1Ku zo, ku albarkaci Yahweh, dukkanku bayin Yahweh, ku da kuke wa Yahweh hidima da dare a haikalinsa.2Ku ɗaga hannunwanku zuwa wuri mai tsarki ku albarkaci Yahweh.3Bari Yahweh ya albarkace ku daga Sihiyona, Shi da yayi sama da ƙasa.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya zuwa Yerusalem domin biki" ko 2) "Waƙar mutane sun rera yayin da suna tafiya a sama da matakai cikin haikalin" ko 3) Waƙar wanda kalmomin suna nan kamar matakai." Duba yadda ka fassara wannan cikin 120:1.
"Dukkanku wanda suke yi wa Yahweh hidima"
Wannan shine yadda mutane ke yin addu'a ko yabon Allah.
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "zuwa haikalin" ko 2) "wurin mai tsarki cikin haikalin."
Jimla "sama da ƙasa" anan na gabatad da dukkan abubuwa. AT: "duk abin da ke cikin sama da ƙasa"
1Ku yabi Yahweh. Ku yabi sunan Yahweh. Ku yabe shi, ku barorin Yahweh,2ku da kuke tsayawa a cikin haikalinsa, cikin harabun gidan Allahnmu.3Ku yabi Yahweh, gama shi nagari ne; ku raira waƙoƙin yabo ga sunansa, gama yana da ƙyau a yi haka.4Gama Yahweh ya zaɓi Yakubu domin kansa, Isra'ila abin mallakarsa.5Na sani Yahweh mai girma ne, kuma Ubangijinmu yafi dukkan alloli.6Ko mene ne Yahweh ya ke marmari, yakan yi shi a cikin sama, da ƙasa, a cikin ruwaye da dukkan zurfafan tekuna.7Yakan kawo gizagizai daga nesa, yakan sa walƙiya da ruwan sama su taho tare, ya kuma fito da iska daga rumbunsa.8Ya kashe ɗan farin Masar, na mutum dana dabbobi.9Ya aika da alamu da al'ajibai a tsakiyarsu, Masar, gãba da Fir'auna da dukkan barorinsa.10Ya hari al'ummai da yawa ya kuma kashe manyan sarkuna,11Sihon sarkin Amoriyawa da Og sakin Bashan da dukkan mulkokin Kan'ana.12Ya ba mu ƙasarsu abin gãdo, gãdo ga Isra'ila mutanensa.13Sunanka, Yahweh, ya dawwama har abada; ka shahara, Yahweh, dawwamamme har tsararraki dukka.14Gama Yahweh zai kare mutanensa, yana juyayin barorinsa.15Allolin al'ummai azurfa ne da zinariya, aikin hannuwan mutane.16Waɗannan allolin suna da bakuna, amma ba su yin magana; suna da idanu, amma ba sa gani;17suna da kunnuwa, amma ba sa ji, babu kuma numfashi a bakunansu.18Waɗanda suka siffanta su kamar su suke, haka kuma wanda ya dogara gare su.19Zuriyar Isra'ila, ku albarkaci Yahweh; ku zuriyar Haruna, ku albarkaci Yahweh.20Ku zuriyar Lebi, ku albarkaci Yahweh; ku da kuke girmama Yahweh, ku albarci Yahweh.21Mai albarka ne Yahweh a cikin Sihiyona, shi wanda da ya ke zaune cikin Yerusalem. Ku yabi Yahweh.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Sunan Yahweh na gabatad da shi. "Ku yabi Yahweh" ko "Ku yabi shi"
Wannan na gabatad da yi wa Yahweh hidima cikin haikalinsa.
Ka tabbata cewa mutane na iya fahimta cewa jimla "Allahnmu" na nufin da Yahweh.
"saboda mun samu daɗi daga yi yabon sunansa"
"Yakubu" anan na nufin da zuriyarsa, mutanen Isra'ila. AT: "Yahweh ya zaɓi zuriyar Yakubu"
Farkon jumla za'a iya bayyana ta a fili. AT: "ya zaɓi Isra'ila su zama mallakarsa"
"Na sani cewa Ubangijinmu yafi dukkan alloli." Kasancewa girma fiye da wani abu an yi magana ne kamar kasancewa bisan ta. AT: "kuma Ubangijinmu yana da girma fiye da dukkan alloli"
Rumbun wuri ne inda ana ajiye abubuwa domin amfani nan gaba. Wannan hasashe na nuna ikon Allah don kula da iska. AT: "Haddasa iska ta hura ta wurin ikonsa"
Waɗannan kalmomi biyu na mafin muhimmanci nufin abu daya kuma na ta'allaka da matsaloli mai mu'ujiza da Allah ya sa a cikin Masar.
Marubucin zabura ya yi magana sai ka ce mutane Masar suna sauraron sa. AT: "a tsakaninku mutanen Masar" ko "a tsakanin mutane Masar"
"don hukuntar Fir'auna"
Waɗannan sune sunaye game da mutane biyu.
Kyautar Allah na ƙasa zuwa ga Isra'ilawa an yi magana akan sai ka ce sune gãdo daga baba zuwa ga ɗa. AT: "Ya ba mu ƙasarsu don mallaka har abada" ko "Ya ba mu ƙasar su ta zama namu har abada"
Sunansa anan na gabatad da shahararsa ko yin suna. AT: "Sunanka" ko "Yin sunanka"
An yi magana game da Allah sai ka ce yana zaune cikin Yerusalem saboda haikalin inda Isra'ilawa suke yin masa sujada a can. AT: "shi wanda haikalin sa na cikin Yerusalem"
1Oh, kuyi godiya ga Yahweh; gama nagari ne, gama alƙawarin amincisa ya dawwama har abada.2Oh, kuyi godiya ga Allahn alloli, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.3Oh, ku yi godiya ga Ubangiji iyayengiji, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.4Kuyi godiya ga wanda shi ƙaɗai ya ke manyan mu'ujizai, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -5ga shi wanda ta wurin hikima yayi sammai, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.6Ku yi godiya ga shi wanda ya shinfiɗa ƙasa da sama da ruwaye, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -7ga shi wanda yayi manyan haske, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.8Kuyi godiya ga wanda ya bada rana yayi mulkin yini, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -9wata da taurari suyi mulki da dare, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.10Kuyi godiya ga wanda ya karkashe 'ya'yan fari na Masar, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -11ya fitar da Isra'ila daga tsakiyarsu, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -12da ƙarfin hannunsa ba janyewa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.13Ku yi godiya ga wanda ya tsaga Tekun Iwa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -14yasa Isra'ila suka wuce ta tsakiyarsa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -15amma ya dulmayar da Fir'auna da rundunarsa cikin Tekun Iwa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.16Kuyi godiya ga wanda ya bida mutanensa cikin jeji, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -17ga shi wanda ya kashe manyan sarakuna, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.18Kuyi godiya ga wanda ya kashe shahararrun sarakuna, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -19Sihon sarkin Amoriyawa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -20da Og sarkin Bashan, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.21Kuyi godiya ga shi wanda ya bada ƙasarsu abin gado, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -22abin gado ga Isra'ila bawansa, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -23ga wanda ya tuna damu ya kuma taimake mu cikin ƙasƙancinmu, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.24Kuyi godiya ga shi wanda ya bamu nasara bisa maƙiyanmu, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada -25ga wanda ke bada abinci ga dukkan masu rai, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.26Oh, sai ku yi godiya ga Allah na sama, gama alƙawarin amincinsa ya dawwama har abada.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Wannan shine motsin rai cewa za'a iya fassara ta tare duk abin da motsin rai na jadada ka samu cikin harshenka don sa ta yi amon halitta.
Allahn wanda yana da girma fiye da alloli wanda wasu mutane suke bautawa
Wancan shine, saboda yana da hikima.
Isra'ilawan zamanin da na tsammani cewa busashen ƙasar duniya na bisan kai teku ne. AT: "sanya duniya bisan ruwaye"
Wannan shine zancen masomin haske domin duniya, musamman rana da wata. AT: "Rana da wata kuma da tauraro"
Ranan, watan, kuma da tauraro an yi magana akan sai ka ce su sarakuna ne. AT: "don alama lokacin yini ... don alama lokacin dare"
"daga tsakiyar mutanen Masar"
A nan "hannu" da "hannu" na gabatad da iko. AT: "tare da iko mai girma"
Sojojin Fir'auna nutsar cikin Tekun Iwa.
A nan ci nassara an yi magana akan sai ka ce ita karsheb abu n e da wani bisan. AT: "cin nassara da Fir'auna" ko cin nassara da sarkin Masar"
Wanda shine, rundunar sojan Fir'auna.
Waɗannan sarakuna sune biyu kawai daga yawan sarakunan da Allah ya ba Isra'ilawa dama su ci nasara akan su.
"Yin tunani game da mu"
Yanayin da jin kunya an yi magana akan sai ka ce ita wani wurin ne wanda Isra'ilawa sun kasance a ciki. Wannan shine zance game da lokatai da dama sa'ad da maƙiyen Isra'ilawa na cin nasara da su cikin yaƙi kuma an kumyatar da su. AT: "kula sa'ad da muna kumyata"
Haddasa mutane su zama da nasara da kuma cin galaban akan maƙiyansu an yi magana akan kamar ba su nasara, sai ka ce nasara wani abu ne wanda za'a iya ba da. AT: "ya yi mana nasara a kan maƙiyanmu" ko "ya ba mu iya cin galaban maƙiyanmu"
"Allah wanda yana zaune cikin sama" ko "Allah wanda halittun na sama ke yi wa sujada"
1Muka zauna a bakin kogunan Babila muka yi ta kuka da muka tuna da Sihiyona.2Muka rataye garayunmu akan itatuwa.3A can waɗanda suka bautar damu suka roƙa muyi masu waƙoƙi, kuma waɗanda suka yi mana ba'a suka matsa mana muyi farinciki, suna cewa, "Ku raira mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona."4Ƙaƙa zamu raira waƙa kan Yahweh a baƙuwar ƙasa?5Idan na ƙyale tunawa dake, Yerusalem, bari hannun damana ya manta da iya kaɗa garaya.6Bari harshena ya manne a rufin bakina, idan na dena tunaninki, idan ban fi son Yerusalem da abin da nafi jin daɗi ba.7Ka tuna, Yahweh, abin da Idomawa suka yi a ranar da Yerusalem ta faɗi. Suka ce, "A ragargazata, a ragargazata har harsashenta."8Ɗiyar Babila, an kusa hallaka ki - bari mutumin nan ya zama da albarka, ko ma wane ne wanda ya sãka maki domin abin da kika yi mana.9Bari mutumin nan ya sami albarka, duk wanda ya kwashe 'ya'yanki ƙanana ya fyaɗa su kan duwatsu.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
"Gaba ga daya daga cikin kogunan dake kusa da Babila"
Marubucin bai haɗa da masu karatu ba.
Itatuwan ba ta yin girma cikin Isra'ila. "Itatuwa" zai yiwu anan ta tsaya domin dukkan itatuwa cikin Babila. AT: "Akan itatuwa cikin Babila"
A nan "waƙoƙi" na gabatad da ayyukan na yin waƙa. AT: "waɗanda suka bautar damu suka roka mu raira masu"
"sun sa mu yi da'awa muna yi farinciki"
Wannan mai yiwuwa na nufin da waƙoƙi wanda Isra'ilawa suka yi amfani cikin sujada a haikalin cikin Yerusalem.
Marubuci yana magana sai ka ce Yerusalem yana jin sa. AT: "Idan na yi sai ka ce bana tunawa da kai Yerusalem" ko "Idan na yi kokarin in manta da kai, Yerusalem"
hannun da mafin yawa mutane na amfani mafin sau da yawa
"Tuna da" ko "yi tunani game da"
A nan tunawa da abin da Idomawa suka yi na gabatad da horon su domin abin da suka yi. AT: "Horon Idomawa, Yahweh, domin abin da suka yi"
Yerusalem ta kasance an kama ta wurin rundunar soja maƙiyan an yi magana game akan sai ka ce ta faɗi. Wanda ya kama Yerusalem zai iya bayyana ta a fili. AT: "ranar da a kama Yerusalem" ko "ranar da rundunar soja Babilawa suka shiga cikin Yerusalem"
Marubucin zabura yana adireshin mutane Babila sai ka ce suna sauraron sa.
Wannan na gabatad da birnin Babila kuma da mutanensa.
Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai kuzari. AT: "bari Allah ya albarkaci mutumin"
Marubucin yana magana game da wani zai yi wa wasu abin suka yi sai ka ce sune biya. AT: "yi maka abin da suka yi mana"
"Fashe ragargaje kai jariran kan duwatsu"
1Zan yi maka godiya da dukkan zuciyata; a gaban alloli zan raira yabbai gare ka.2Zan rusuna ina fuskantar haikalinka mai tsarki in kuma bada godiya ga sunanka sabili da amincinka na alƙawarinka domin kuma amincewarka. Ka fifita maganarka da sunanka da muhimmanci fiye da komai.3A ranar dana kira ka, ka amsa mani; ka ƙarfafa ni ka bani karfin zuciya.4Dukkan sarakunan duniya zasu yi maka godiya, Yahweh, gama zasu ji maganganun bakinka.5Hakika, zasu raira waƙoƙi akan abubuwan da Yahweh yayi, gama ɗaukakar Yahweh mai girma ce.6Gama ko da ya ke Yahweh mafifici ne, duk da haka yana kula da masu kaɗaici, amma ya san masu girman kai tun daga nesa.7Koda ya ke ina tafiya a tsakiyar hatsari, zaka tsare raina; zaka miƙa hannunka gãba da hushin maƙiyana, hannun damanka zai cece ni.8Yahweh yana tare da ni har ƙarshe; alƙawarin amincinka, Yahweh, dawwamamme ne har abada. Kada ka yasar da waɗanda hannuwanka suka yi.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Zuciya anan na gabatad da motsin zuciyarmu. Yin wani abu da gaske ko gaba daya an yi magana akan kamar yin ta tare da dukkan zuciyar mutum. AT: "Zan yi godiya gare ka da gaske"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Duk da haka daga gumakan karya da sun wanzu" ko 2) "gaban taron na sama," wanda yana nufi "cikin sani malaikun cikin sama."
rusunawa a ƙasa alamar ce na aiki wanda ke gabatad da sujada da ban girma. AT: "Zan yi maka sujada"
Wannan na nufin da abin da Allah ya faɗa. AT: "Abin da ka faɗa" ko "dokokinka da alkawuranka"
"Dukkan shugabannin cikin duniya"
Wannan magana na tsaye domin Allah da kansa. AT: "ka"
Yahweh shine bisa dukkan halitta cikin iko, matsayi, da ƙarfin iko. Duk da haka amfaninsa na cikin waɗanda suna da tawali'u cikin ruhu, bayin ga dukkan. Wannan shine sauki nuna bambanci.
Wannan magana mai yiwuwa na ma'ana cewa Allah ba shi da amminci ga masu girman kai.
rayuwa, zama
Kasancewa cikin hatsari ana magana ne kamar kasancewa cikin wuri da za'a iya gani.
An yi magana game da Allah sai ka ce zaya buga maƙiyan da hannunsa.
An yi magana game da fushi sai ka ce ita wani abu ne a maimakon motsin zuciya. AT: "maƙiyana, wanda suke fushi"
An yi magana game da Allah sai ka ce yana yin amfani ta jiki da hannuwan don halitta. AT: "kai ka halitta"
1Yahweh, ka jaraba ni, ka kuma sanni.2Ka san lokacin da zan zauna da lokacin da zan tashi; ka san tunanina tun daga nesa.3Kana lura da tafarkina da kwanciyata; hanyoyina sanannu ne dukka a gareka.4Gama kafin magana ta kasance a kan harshena, ka sani sarai.5Ka kewaye ni gaba da baya kuma ka ɗibiya hannunka a kaina.6Wannan sani ya fi ƙarfina ƙwarai; yayi mani zurfi, ba zan iya fahimtar sa ba.7Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan guje wa fuskarka?8Idan na hau cikin sammai, kana can; Idan na tafi na zauna cikin Lahira, to duba, kana can.9Idan nayi asubanci na tashi sama akan fukafukai na tafi na zauna can nesa a ƙurewar teku,10ko can ma hannunka zai bishe ni, hannun damanka zai riƙe ni.11Idan nace, "Hakika duhu zai rufe ni, haske kuma ya zama dare kewaye dani,"12ko duhunma ba zai zama duhu a gare ka ba. Daren zai haskaka kamar rana, gama da duhu da haske duk ɗaya suke a gare ka.13Kai ka yi gaɓaɓuwan cikin cikina; kai ka siffanta ni a cikin mahaifiyata.14Zan yabe ka, gama an yini da ƙyan gaske. Raina ya tabbatar da wannan sosai.15Ƙasusuwana ba a ɓoye suke ba gare ka sa'ad da aka siffanta ni a ɓoye, sa'ad da aka hallita ni a can cikin zurfin ƙasa.16Ka ganni a cikin mahaifa; dukkan kwanakin da an ƙaddara mani suna rubuce cikin littafinka tun kafin na farkon ya faru.17Tunaninka yana da daraja a guna, Allah! Tarinsu da yawa basu lisaftuwa.18Idan na yi ƙoƙarin ƙididdiga su, zasu fi yashi yawa. Sa'ad da na farka, ina tare da kai.19Dãma zaka kashe mugaye, ya Allah; ku rabu dani, ku 'yan ta'adda.20Suna yi maka tawaye suna aikata munafunci, maƙiyanka suna faɗar ƙarairayi.21Ba na ƙi waɗanda suka ƙi ka ba, Yahweh? Ba ina rena waɗanda suka tashi gãba da kai ba?22Na ƙi su fau-fau; sun zama maƙiyana.23Ka jaraba ni, ya Allah, ka san zuciyata; ka gwada ni ka san tunanina.24Ka duba ko akwai muguwar hanya a cikina, ka kuma bishe ni a madawwamiyar hanya.
Daidaici na gama gari ne a wallafa wakokin Hebraniyawa.
"Wannan shine darektan mawaƙa don amfani cikin sujada."
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) Dauda ne ya rubuta zaburan ko 2) zaburan game da Dauda ne ko 3) zaburan yana cikin salon na zaburan Dauda.
"gwada"
Marubucin zabura ya yi afani da waɗannan matakai biyu na gabatad da duk abin da yana yi. AT: "duk abin da ina yi" ko "duk abin da ke game da ni"
Anan "tafarki" na tsaye doin halin wani. "Tafarkinada kwanciyata" tare na gabatad da duk abin da ke game da marubucin zabura.
A nan "magana akan harshena" na gabatad da jawabin. AT: "kafin in ce wani abu"
Wannan magana na nufin da kasancewar Allah a ko'ina.
Wannan magana na nufin da jagora da taimako. AT: "kai ne jagora da taimako na"
Kasancewa da tsawo kuma baya kusa magana ne, a wannan halin, game wasu sani da 'yan Adam ba zasu samu ba. AT: "tana da wuya sosai in fahimta"
Waɗannan tambiyoyi suna nan faralel. Marubucin zabura yana faɗa cewa baza ya iya tafi daga gaban Allah ba. AT: "Ba zan iya kuɓuce daga Ruhunka ba.
"Shirian gadon wani" na nufin da zama a wani wuri. AT: "Ko da idan na zauna cikin lahira"
Mawallafan yana bayyana cewa duk inda yake, Allah yana can ma.
A dã kusa da gabas, akan kwatanta rana sau da yawa sai ka ce tana da fukafukai wanda ke ba ta dama yin shawagi a dukan faɗin sama. AT: "Idan rana zai kawo ni tare da kanta a dukan faɗin sama"
"da nisa sosai dagan nan zuwa ga yamma"
"zai taimaki ni"
Marubucin zabura ya yi magana game da dare sai ka ce ita wani bargo ne da zai rufe shi.
Daren, wanda yake da duhu, an yi magana ta sai ka ce tana mai walkiya da haske.
"Cikin cikina" na nufin da gabobin ciki na wani mutum, amma anan maganan mai yiwuwa na tsaye domin dukan jiki. AT: "Kai ka yi dukan jikina"
A nan "rai" mai yiwuwa na nufin da sadarin iyawa na Marubucin zabura don a tabbata da kauna da jagoranci Allah. Mai fassara watakila, ko da yaya, yi wa "rai" anan kamar yadda ke yi madadi domin hankali da zuciyar marubucin zabura. AT: "Na san wannan da zuciyar na"
"hallita tare da babban hadaddun"
Wannan shine mai yiwuwa wata hanyar yin magana game da mahaifar uwar
Wannan magana na nuna cewa Isra'ilawa dã na yin tunani cewa Allah ya rubuta wannan shirinsa cikin wani littafi.
"muhimmanci" ko "daraja"
"Tunaninka suna da yawa."
"suna fiye gaba a kidaya"
Marubucin zabura yana yi da'awa ne kawai da magana kai tsaye zuwa ga mutane 'yan ta'adda waɗanda yana da su a zuciya. Masu fassara ai yiwuwa su yanke don bayyana wannan doka kamar yadda wani ya so
"sun yi tawaye akan karfin ikonka, Allah"
"maƙiyanka na ƙarya game da kai"
Waɗannan jumla biyu na da ma'ana masu kama. Daya daga biyun kara karfafa tunani da ke cikin na farko. Dukka biyu daga waɗannan tamboyoyi na yin zahirin kalamai.
yin tawaye
Wannan roko doin Allah ya fada wa marubucin zabura game da wani tunani mai zunubi wanda shi ya yi. AT: "Don Allah ka bincike ni" ko "na roka ka bincike ni"
Waɗannan jumla biyu na da ma'ana masu kama. Daya daga biyun kara karfafa tunani da ke cikin na farko.
A nan "hanyar" na tsaya ne domin hali.
Anan "hanyar" na nufin da a dogara da yin biyayya cikin Allah. Duk wanda ke yin "tafiya" wannan hanyar zai samu rai madawwami.
1Yahweh, ka cece ni daga mugaye; ka kiyaye ni daga mutane masu zafin rai.2Sukan shirya mugunta a zuciyarsu; sukan sa yaƙi kowacce rana.3Harsunansu suna sara kamar maciji; dafin kububuwa na leɓunansu. Selah4Ka tsare ni daga hannuwan mugaye, Yahweh; ka tsare ni daga mutane masu zafin rai waɗanda suka shirya su kada ni ƙasa.5Masu fariya sun ɗana mani tarko; sun baza taru; sun shirya mani tarko. Selah6Na cewa Yahweh, "Kai ne Allahna; ka kasa kunne ga koke-kokena na neman jinƙai.7Yahweh, Ubangijina, kai mai iko ne ka iya ceto na; kana kare kaina a lokacin yaƙi.8Yahweh, kada ka biya buƙatun mugaye; kada ka bari shirye-shiryensu yayi nasara. Selah9Waɗanda suka ɗaga kansu sun kewaye ni; bari makircin leɓunansu ya rufe su.10Bari garwashin wuta su afko masu; ka jefa su cikin wuta, cikin rami marar matuƙa, kada su ƙara tashi.11Kada mutane masu mugun harshe su sami kwanciyar rai a duniya; bari bala'i ya farauci ɗan ta'adda ya buge shi ya mutu.12Na sani Yahweh zai kyautata wa mai shan ƙunci a shari'a kuma zai yi adalci ga matalauci.13Hakika mutane masu adalci zasu bada godiya ga sunanka; mutanen dake yin gaskiya zasu kasance a gabanka.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Wannan shine domin darekta na waka don amfani cikin sujada."
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) Dauda ne ya rubuta zaburan ko 2) zaburan game da Dauda ne ko 3) zaburan yana cikin salon na zabura Dauda.
A nan "yaƙi" mai yiwuwa na nufin da rikici na wani iri, har da faɗa.
Mutane wanda ke sa rikici ta wurin abin da suka ce suna magana sai ka ce suna da harsunan maciji. Hakika, macizai ba su yi lalacewar tare da harsunansu, amma tare da cizonsu kuma musamman tare da guba. Ba ko mutum da zai iya sa harshensa kaifi. Maimako, anan ra'ayin game da kaifin harshen na tsaye domin yin magana cikin hanyar da ta jawo matsala. Kuma ra'ayin na macizai da harsunan masu kaifi ke tsaye domin al'amari cewa da yawan su na da guba.
Haka, ikon mugaye
Irin na ainihi game da tarkuna suna mafin kankanta muhimmanci fiye da ra'ayi cewa "mugaye ... 'yan ta'adda" suna shiryawa sa matsala domin marubucin zaburan. Idan masu karatunka basu sani sau da yawa game da kamawa ba, zaka bukaci rage wannan kasa zuwa layi daya, kamar yadda UDB na rage layin biyu daga ULB ga daya cikin 140:1.
Wannan shine kira domin taimako. AT: "kasa kunne gare ni kamar yadda ina kira gare ka yanzu domin taimako"
Kan mutum yana cikin babba haɗari a lokacin yaƙi. AT: "ka kare ni sa'ad da na tafi yaƙi"
A nan "yaƙi" mai yiwuwa na tsaye domin wqni iri game da matsala mai tsanani
"don Allah kada ka bari mugaye su samu abin da suna buƙata"
Wannan shine alama kasance da girman kai. AT: "suna da girman kai"
Wannan shine addu'a cewa Allah zai sa azzãlumai su sha wuya daga matsala cewa su jawo ta wuri abubuwa da suka ce.
Kamannin wuta na tsaye domin hukunci mai tsanani domin mugaye.
Wannan yana yiwuwa zance game da lahira, duniyan matattu.
masu yin mugun magana game da wasu ba tare da dalili
A nan an yi magana game da adalci sai ka ce ita wani abu ne da za'a iya ba wani. AT: "Zan aikata ta hanya adalci don taimako matalauci"
ga kai
1Yahweh, ina kuka gare ka; ka zo wurina da sauri. Ka saurare ni sa'ad da na kira ka.2Bari addu'ata ta zama kamar turare a gaban ka; bari tãda hannuwana sama ya zama kamar hadayar maraice.3Yahweh, kasa mai tsaro a bakina; ka kiyaye ƙofar leɓunana,4Kada ka bari zuciyata ta yi marmarin wani mugun abu ko in haɗa kai cikin ayyukan zunubi tare da mutanen dake aikata mugunta. Kada ma in ci wani kayan lashe-lashensu.5Bari adilin mutum ya buge ni; zai zamar mani alheri. Bari ya tsauta mani; zai zama kamar mai a kaina; bari kada in ƙi karɓar wannan. Amma addu'ata kullum gãba take da ayyukan muguntarsu.6Za a jefar da shugabanninsu daga kan duwatsu; zasu ji cewa maganganuna masu daɗi ne.7Tilas zasu ce, "Kamar yadda mutum yakan yi huɗa ya rugurguza ƙasa, haka suka warwatsar da ƙasusuwanmu a ƙofar Lahira."8Hakika idanuna suna kanka, Yahweh, Ubangiji; a cikinka zan fake; kar ka bar raina ba tsaro.9Ka tsare ni daga tarkunan da suka ɗana mani, daga tarkunan masu mugun aiki.10Bari mugaye su faɗa cikin tarkonsu ni kuwa in kubce.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Marubucin zabura yana magana sai ka ce Yahweh mutum ne wanda ke da bukata ya zo daga wani wuri don ya taimaki shi. Abin da marubucin zabura ya so Yahweh ya yi za'a iya bayyana ta a fili. AT: "zo da sauri don ka taimaki ni"
Marubucin zabura yana son Yahweh ya ji daɖin da shi saboda yana yin addu'a kuma saboda kalmomi addu'arsa.
"hannuwa da na tãda sama." Tãda hannuwa wata kalma ce a madaɗin addu'a. Mutane sun tãda hannuwansu sa'ad da suka yi addu'a ko yi yabon Yahweh. Duba yadda ka fassara ta "tãda hannuwan ka sama" cikin 134:1.
zama kamar da dabba da za'a kona akan bagade cikin maraice. Marubucin zabura yana magana sai ka ce yana so Yahweh ya zama kamar da jin daɗin da shi kamar yadda yana tare da masu kawo dabbobi don hadaya. Ya so Yahweh ya zama da jin daɗin saboda marubucin zabura yana yin addu'a ko saboda kalmomin addu'arsa.
Marubucin zabura ya yi magana sai ka ce mugu kalmomi sune fursunoni suna kokari su kuɓucce daga bakinsa. AT: "sai ka taimake ni kada in faɗa abubuwa da suke mugu"
"gaya wa wani ya yi tsaro"
Marubucin zabura ya yi magana sai ka ce mugu kalmomi sune fursunoni suna kokari su kuɓucce daga bakinsa. "sai ka taimake ni kada in faɗa abubuwa a lokaci da bai kamata ba"
"yin ayyukan zunubi"
"abinci na musamman"
Marubucin zabura ya yi magana sai ka ce ba da wani tsauta wa jiki da ke buga wani. AT: "tsauta mani"
Mai yiwuwa ma'ana sune wanda marubucin zabura ya yi magana sai ka ce wani mutum da yana gyara shi ta saka mai a kansa 1) a darajanta shi. AT: "lokacin da yana gyara ni, zan sani cewa wanda yana gyara ni yana yin aiki mai kyau gare ni ko 2) ya sa kansa ji mafin kyau.
Kai kalma ce yana musanya domin mutum. Rashin fahimta tambayar da ba ta damu da amsa sakamako ba za'a iya fassara ta kamar yadda wani bayyani mai yaƙini. AT: "bari in karɓa ta da murna"
Kalmar "ayyukan muguntar" wani kalma ne
Idanun sune wani kalma da yana musanya domin dukkan mutum. AT: "Ina neman in gani abin da zaka yi" ko "Na sa ran zaka taimake ni"
"Ina rokonka don ka kare ni" dubi yadda "zan fake" an fassara ta cikin 118:8.
Rai wani kalma ne
Marubucin zabura ya yi magana game da yaudara wani mutumin nagari don haka mutumin zai yi zunubi domin mugayen mutane su iya cin nasara da shi sai ka ce tana sa tarko ne domin dabba. Kalma "tarkuna" kalma ne
1Da muryata nayi kuka domin neman taimako daga Yahweh; da muryata na roƙi Yahweh tagomashi.2Na zuba masa koke-kokena a gabansa; na gaya masa wahaluna.3Sa'ad da ruhuna ya raunana a cikina, ka san tafarkina. Sun ɗana ɓoyayyen tarko domina a hanyar da nake bi.4Na duba hannun damana sai na ga babu wanda ya kula dani. Ba mafita domina, ba wanda ya kula da rayuwata.5Na kira gare ka, Yahweh; nace, "Kai ne mafakata, rabona kuma a ƙasar rayayyu.6Ka kasa kunne ga kirana, gama an ƙasƙantar dani; ka cece ni daga masu tsananta mani, gama sun fi ƙarfi na,7Ka fitar da raina daga kurkuku domin in yi godiya ga sunanka. Masu adalci zasu tattaru kewaye dani domin ka yi mani alheri."
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Wannan watakila na nufin da salon waƙa. Dubi yadda ka fassara wannan cikin 32:1.
buɗaɗɗen wuri karkashin duniya isasshe ne babba domin mutane su yi tafiya kewaye da cikin
Idan waɗannan layin biyu suna kwarai hakanan daya wanda mai karatu zai samu ma'ana da ba daidai ba, kana iya fassara su kamar layi daya.
Idan waɗannan layin biyu suna kwarai hakanan daya wanda mai karatu zai samu ma'ana da ba daidai ba, kana iya fassara su kamar layi daya.
"Na raunana" ko "Na musamman karya karfin gwiywa"
"ka sani tafarki da zan kama." Marubucin zabura yana magana sai ka ce abin da mutum ya yi sune tafarki wanda wancan mutum ya yi tafiya tare. AT: "ka san hanyar da ya kammata in yi rayuwa"
Marubucin zabura yana magana game da mutane suna son cutan sa sai ka ce suna kokari kama wani dabba da tarko. AT: "Suna shirya domin duk abin da ina yi su iya mani lahani"
Wannan shine kira domin taimako. AT: "kira gare ka yanzo domin taimako"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "duk abin da ina so" ko 2) "duk abin da nake bukata" ko 3) "duk abin da ina da shi."
Wannan shine kira domin taimako. Duba yadda ka fassara wannan cikin 5:1. AT: "Ka kasa kunne gare ni kamar yadda na yi kira gare ka yanzo domin taimako"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "Ina bukata sosai" kuma 2) "Na raunana sosai." Duba yadda "mun kaskantu sosai" an fassara ta cikin 78:7.
Wannan wani roko ne. AT: "ka fitar da ni daga kurkuku"
Kalma "suna" wani kalma ne (da yake kwatanta wani abu amma na nufin wani dangantak abu) domin mutum. Duba yadda ka fassara wannan cikin 5:11. AT: "yi godiya gare ka"
1Ka ji addu'ata, Yahweh; ka ji roƙona. Saboda amincinka da adalcinka, ka amsa mani!2Kada ka gabatar da bawanka a gaban shari'a gama a gabanka babu mai adalci ko ɗaya.3Maƙiyina ya hari raina; ya ture ni ƙasa; ya sãni in zauna cikin duhu kamar waɗanda suka mutu tun-tuni.4Ruhuna ya karaya a cikina; babu sauran bege a raina.5Idan na tuna kwanakin dã; na kan yi bin-bini akan ayyukanka; ina tunani akan nasararka.6Na tada hannuwana zuwa gare ka cikin addu'a; raina yana da ƙishinka cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa. Selah7Ka amsa mani da wuri, Yahweh, saboda ruhuna ya some. Kada ka ɓoye mani fuskarka, domin kada in zama kamar masu gangarawa cikin rami.8Bari inji alƙawarinka na aminci da safe, gama na dogara gare ka. Ka nuna mani tafarkin da zan bi, gama nasa zuciyata a gare ka.9Ka cece ni daga maƙiyana, Yahweh; ina gudu gare ka domin in ɓoye.10Ka koya mani in aikata nufinka, gama kai ne Allahna. Bari Ruhunka mai kyau ya bishe ni cikin ƙasar da ake adalci.11Yahweh, sabili da sunanka, ka barni da rai; cikin adalcinka ka fitar da raina daga wahala.12Cikin alƙawarin amincinka ka datse maƙiyana kuma ka hallaka dukkan maƙiyan rayuwata, gama ni baranka ne.
Ana samun daidaici aa gama gari ne a wallafa waƙoƙin Ibraniyawa.
Kalmomin "addu'arta" su wani kalma ne
"In ka yarda kada ka sharanta" ko "Ina rokonka kada ka sharanta"
Marubucin zabura yana magana game da kansa sai ka ce yana yin magana game da wani mutum. AT: "ni"
"ba ka da tunani wani na da adalci"
"bi na don kokari kama ni"
"ya ci nasara a kaina gaba daya" (Dubi UDB)
"Na raunana" ko "Na musamman karya karfin gwiywa"
"ba ni da wani sauran bege"
Suna mai zuzzufar ma'ana "nasarar" za'a iya fassara ta yin amfani da fi'ili "gama yin." AT: "duk abin da ka gama yin" ko "dukkan abubuwa masu girma da ka yi"
"yi addu'a gare ka da hannuwana tada a sama a gefena"
Marubucin zabura yana magana game da so ya zama tare da Allah sai ka ce yana cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa kuma har ila yau yana kusan ya mutu da ƙishi. AT: "Ina son in zauna tare da kai yadda wani mutum cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa wanda yana jin kishinrwa sosai."
Marubucin zabura yana marmarin sani Yahweh. Tsananin marmarinsa don ya san Yahweh yana kamar wani wanda ya na jin kishinrwa sosai. AT: "Ina marmarinka"
"Na raunana" ko "Na musamman karya karfin gwiywa"
Marubucin zabura yana magana game da Yahweh yana kin ya yi abin da marubucin zabura yana roka sai ka ce Yahweh na kin ya ko da ya duba marubucin zaburan. Wannan Rashin fahimta tambayar da ba ta damu da amsa sakamako ba za'a iya bayyana ta kamar yadda wani mai yaƙini. AT: "Kada ka ki kasa kunne gare ni" ko "Sai ka kasa kunne gare ni"
"Zan zama daidai kamar wani matacce mutum"
"Ka sa ni in ji alƙawarinka na aminci" ko "Ka da gaya mani game da alƙawarinka na aminci"
Marubucin zabura yana magana game da hanyar mutane na rayuwa sai ka ce su wani tafarki ne wanda suke tafiya a kan. AT: "yadda kana son in yi zama"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "ina gudu gare ka domin in iya ɓoye" da 2) "ina gudu gare ka domin zaka ɓoye kuma ka kare ni."
"in yi abin ka ke son in yi"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) "taimake ni in zama na kwarai" ko 2) "bari rayuwa na ta zama babu damuwa"
Mai yiwuwa ma'ana sune 1) wannan shi wani musili domin zama mai adalci ko 2) "wani ƙasa da ya ke na daidai," wani musili domin rayuwa da babu damuwa.
"maƙiyan waɗanda na son su dauki raina"
"Ka nuna alƙawarinka na aminci ta wuri datse maƙiyana"
"maƙiyan rai na" ko, dauka "rayuwata" kamar yadda wani kalman
1Mai albarka ne Yahweh, dutsena, wanda ya ke horar da hannuwana domin yaƙi da yatsuna domin faɗa.2Kai nawane mai amintaccen alƙawari da mafakata, kaine hasumiyata mai tsawo wanda ya ke ceto na, garkuwata wanda a cikinsa nake fakewa, shi ya ke sarayar da al'ummai ƙarƙashina.3Yahweh, wane ne mutum har da kake kula shi ko ɗan mutum da kake tunani a kansa?4Mutum kamar huci ya ke; kwanakinsa kamar inuwa mai wucewa ne.5Ka sa sararin sama ya tsage ka sabko ƙasa, Yahweh; ka taɓa duwatsu ka sa suyi hayaƙi.6Ka aika walƙiyar tsawa ka warwatsar da maƙiyana; ka harba kibanka ka kore su su sheƙa a ruɗe.7Ka miƙo hannunka daga sama; ka cece ni daga ɗumbin ruwaye; daga hannun baƙi.8Bakunansu suna faɗar ƙarairayi, komai kuma dake hannunsu sun samu ne daga rashin gaskiya.9Zan raira maka sabuwar waƙa, ya Allah; akan garaya mai igiya goma zan raira maka yabo,10kai wanda ke bada ceto ga sarakai, wanda ya tsirar da Dauda bawanka daga mugun takobi.11Ka cece ni ka 'yantar dani daga hannun baƙi. Bakunansu suna faɗar ƙarairayi, a hannun damansu kuma akwai rashin gaskiya.12Bari 'ya'yanmu maza su zama kamar dashe-dashen da suka yi girma suka ƙosa a samartakarsu 'ya'yanmu mata kuma kamar sassaƙaƙƙun ginshiƙan fãda masu kyan fasali.13Bari rumbunanmu su cika da kowanne irin amfani, bari kuma tumakinmu su hayayyafa dubbai kan dubbai har sau goma a saura.14Sa'an nan shanunmu zasu haifi 'yan maruƙa da yawa. Ba wanda zai hudo ta katangunmu; baza a tafi bautar talala ba ko a ji koke-koke a tituna.15Masu albarka ne mutanen dake da waɗannan albarku; masu farinciki ne mutanen da Allahnsu shi ne Yahweh.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Kalmomi "hannuwa" da "yatsuna" su ne wani kalma da yana musanya domin "ni." Idan "yaƙi" da "faɗa" suna da kalma daya cikin harshenka, kana iya fassara wannan kamar daya layi. AT: "wanda yake horad da ni domin yaƙi kuma yake horad da ni domin faɗa" ko "wanda yake horad da ni domin yaƙi"
Marubucin zabura yana amfani da musilai masu yawa don jadada cewa Yahweh zai kare shi.
Dauda yana magana game da Yahweh sai ka ce shine mafaka da ke kare shi daga hari. Yahweh shine wanda yana kare Dauda daga hari.
Dauda yana magana game da Yahweh sai ka ce shi wani garkuwa ne da ke kare wani soja. Yahweh shi ne wanda ya ke kare Dauda daga hari. Duba yadda wannan an fassara ta cikin 18:2.
Waɗannan tambayoyi za'a iya fassara su kamar yadda a bayyane. AT: "utum karami ne a kwatanta cikin dukkan abu kuma da ka yi wanda ina ji mamaki cewa kake kula da mutum kuma cewa kake tunani game da ɗan mutum"
kalmomi biyu domin 'yan'yan Adam.
Marubuci yana kwatanta mutane da waɗannan abu don jadada yadda gajere rayuwansu yake.
Waɗannan mai yiwuwa ya kammata kasantuwa fassara ta kamar yin rokon, ba umarnin ba, tun da maburucin zabura ya dauki Allah da girma fiye da shi.
Zai yiwuwa ma'ana su ne 1) tsaga sararin a ɓude ko 2) lankwasa sammai kamar wani rashe itace dake lankwasawa sa'ad da wani yana tafiya akan ta ko kamar yadda wani ya lankwasa baka kafin ya yi harbi kibiyoyi.
"ashe basu sani abin da sun yi tunani akan ba ko abin da zasu yi ba"
Dauda yana magana sai ka ce Allah yana a ƙasan bisa ambaliya kuma yana da hannuwa da wanda zaya ja Dauda daga ambaliya. Ambaliyan wani musili ne domin matsaloli da ke jawo ta wuri "baƙi6." AT: "Kai wanda ka iya yi, taimake ni shawo kan matsaloli na"
A nan "hannu" na nufin da iko. AT: "daga ikon baƙi"
"Suna fadar ƙarairayi"
Zai yiwuwa ma'ana sune 1) Dauda yana magana game da al'ada na daga hanun dama ya rantse cewa abin da wani yana so ya fada cikin kotu gaskiya ne, "suna karya ko da lokacin suna rantsuwa gaya gaskiya," ko 2) "hannun dama" musili domin iko, "duk abin da suka samu, sun samu ne ta wuri gaya karairayi."
Zai yiwuwa ma'ana sune 1) "waƙa da ba wanda ya taba rerarwa gabanin" ko 2) "waƙa da ban taba rerawa ba."
Dauda yana magana game kansa sai ka ce shi wani ne dabam. "ni, Dauda, bawanka"
Dauda yana magana game da mugu mutane sai ka ce su takuba ne suke amfani kamar makamai. AT: "daga mugun mutane wanda suna kokari su kashe shi"
A nan "hannu" na nufin da iko. Fassara waɗannan kalmomi kamar yadda ka fassara su a 144:7. AT: "daga ikon baƙi"
Zai yiwuwa ma'ana sune 1) Dauda yana magana game da al'ada na daga hanun dama ya rantse cewa abin da wani yana so ya fada cikin kotu gaskiya ne, "suna karya ko da lokacin suna rantsuwa gaya gaskiya," ko 2) "hannun dama" musili domin iko, "duk abin da suka samu, sun samu ne ta wuri gaya karairayi." Fassara waɗannan kalmomi kamar yadda ka fassara su a 144:7.
lafiya da karfi
lokacin da sa'ad da mutane ke yi girman
kyau itace da ke rike da sasannin na babban gida"
ginshiƙan wanda suke sassaƙaƙƙun domin yin wani fãda masu kyan fasali"
"dubbai--ko da dubbai har sau goma!--kuma cike sama da sauranmu"
"Ba wanda zai iya memaye birninmu"
"ba wanda ke yi kuka cikin zafi" ko "ba wanda ke yi roko domin abinci" ko "ba wanda ke kira domin ãdalci"
1Zan ɗaukaka ka, ya Allah, Sarki; zan albarkaci sunanka har abada abadin.2Kowace rana zan albarkace ka; zan albarkaci sunanka har abada abadin.3Yahweh Mai Girma ne, ƙasaitarsa ta cancanci yabo; Girmansa ba ya bincikuwa.4Daga wata tsara zuwa wata tsara za a yabi ayyukanka kuma za a labarta manyan ayyukanka.5Zan yi bin-bini akan martabar ɗaukakarka da kuma ayyukanka masu ban mamaki.6Zasu yi magana akan ikon manya-manyan ayyukanka, ni kuwa zan yi shelar girmanka.7Zasu yi shelar ayyukanka nagari masu yawa, kuma zasu raira yabo akan adalcinka.8Yahweh mai alheri ne kuma mai jinƙai ne, mai jinkirin fushi amincinsa kuma cikin alƙawari ba iyaka.9Yahweh yana yi wa kowa kirki; jinƙansa na bisa dukkan aikin hannunsa.10Dukkan abubuwan da kayi zasu yi maka godiya, Yahweh; amintattunka zasu sa maka albarka.11Amintattunka zasu yi magana akan darajar mulkinka, zasu faɗi ikonka.12Zasu sanar da 'yan adam ayyukan Allah masu girma da kuma ɗaukakar darajar mulkinka.13Mulkinka, dawwamammen mulki ne, masarautarka ta dawwama har tsararraki dukka.14Yahweh yakan tallafa wa dukkan waɗanda suke faɗuwa ya kuma tãda dukkan waɗanda ke a wulaƙance.15Idanun kowa na jiranka; ka kan basu abincinsu a madai-daicin lokaci.16Ka kan buɗe hannuwanka ka biya buƙatun kowanne abu mai rai.17Yahweh mai adalci ne a dukkan tafarkunsa mai alheri ne a dukkan abin da ya ke yi.18Yahweh na kusa da dukkan waɗanda suke kira gareshi, ga dukkan waɗanda suke kiransa da amincewa.19Yana biyan buƙatun waɗanda suke girmama shi; yana jin kukansu sai kuma ya cece su.20Yahweh yana lura da dukkan waɗanda ke ƙaunarsa, amma zai hallaka duk mugaye.21Bakina zai furta yabon Yahweh; bari duk 'yan adam su albarkaci sunansa mai tsarki har abada abadin.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
"Wannan shine zabura ta yabo wanda Dauda ya rubuta."
"gaya wa mutane yadda da ban mamaki ka ke"
Kalma "suna" wani kalman
Kalma "suna" wani kalman
"abubuwa da za ka iya yi saboda ka na da karfi"
"gaya wasu yadda kwarai nagari ka ke"
Marubucin zabura yana magana game da amincin alkawari sai ka ce ita wani abu wanda wani zai iya mallaka da babban adadin. AT: "gabaki daya da aminci ga alkawarinka"
"mutane na iya gan shi ya nuna jinkai cikin duk abin da yana yi"
"Dukkan mutane da ka yi zasu yi godiya" ko "Zata zama sai ka ce duk abin da ka yi zasu ba ka godiya"
"kasance har abada"
Marubucin zabura yana magana game da Yahweh yana karfafawa mutane sai ka ce yana taimakon mutane wanda suna da rauni a jiki. Kana yiwuwa bukata don fassara dukka layi ta yin amfani da layi daya kawai. AT: karfafa waɗanda sun kusan fid da zuciya"
"kowa da kowa na jira"
"Ka yi kariminci tanadin"
"ka ba kowa da kowa fiye da bukatansu kuma iyakar son su"
"Mutane na iya gani daga duk abin da Yahweh yana yi cewa yana da adalci"
"kuma shi mai alheri ne cikin dukkan abin da ya ke yi" ko "mutane na iya gani daga duk abin da Yahweh ya ke yi cewa shi mai alheri ne"
"ya yi da sauri don ya taimake waɗanda ke yi addu'a"
"ga dukkan waɗanda ke faɗa gaskiya kawai sa'ad da suke addu'a" ko "ga dukkan wanda ya ke dogara sa'ad da suke addu'a"
"Zan yi"
"gaya wa kowa da kowa yadda nagari Yahweh ya ke"
Kalma "suna" wani kalman
1Ka yabi Yahweh, Yabi Yahweh, ya raina.2Ina ba da yabo ga Yahweh a dukkan rayuwata; Zan raira yabo ga Allahna muddin ina raye.3Kada ka dogara ga sarakuna ko ga ɗan adam, waɗanda babu ceto gare su.4Sa'ad da ran mutum ya dena numfashi, sai ya koma turɓaya; a ranan nan shawarwarinsa zasu watse.5Mai albarka ne wanda mataimakinsa Allahn Yakubu ne, wanda begensa na cikin Yahweh Allahnsa.6Yahweh ne yayi sama da ƙasa, da teku, da dukkan abubuwan dake cikinsu; yana kiyaye gaskiya har abada.7Yana zartar da hukunci domin dukkan waɗanda ake zalumta kuma yana bada abinci ga mayunwata. Yahweh yakan 'yantar da ɗaurarru;8Yahweh yana ba makafi ganin gari; Yahweh yana tãda waɗanda an tanƙwaresu; Yahweh yana ƙaunar mutane masu aikata adalci.9Yahweh yana kãre bãƙin dake cikin ƙasa; yana agajin marayu da gwauraye, amma yana tsayayya da mugaye.10Yahweh zai yi mulki har abada, Allahnki, Sihiyona, domin dukkan tsararraki. Mu yabi Yahweh.
Ana samun daidaici a gama gari ne a wallafa waƙoƙin Ibraniyawa.
A nan "rai" na gabatad da mutum na cikin marubuci. Marubuci na ba da umurni na cikin sa ya yabe Yahweh. Wannan za'a iya fassara ta kamar yadda ke wani bayyani. AT: "Zan yabe Yahweh tare dukkan raina" ko "Na ba da yabo ga Yahwe tare da dukkan rayuwata"
"har sai na mutu" ko "yayin da ina raye"
A nan "sarakuna" na gabatad da dukkan shugabanin 'yan Adam.
Suna mai zuzzurfar ma'ana "ceto" za'a iya bayyana ta kamar "tsirad da." AT: "ga kowane mutum saboda ba su iya tsirad da kai"
"ga yan Adam" ko "ga mutane"
Wannan shine hanyar da'a don ta'allaka da wani na mutuwa"
Wannan na nufi cewa daidai kamar yadda Allah ya yi mutum na farko, Adamu, daga turɓaya ƙasa, haka nan jiki mutum zai rube kuma ya zama ƙasa kuma sa'ad da ya mutu.
Kalmomin "sama" da "ƙasa" na gabatad duk abin da ke wanzu cikin duniya.
Suna mai zuzzurfar ma'ana "gaskiya" za'a iya bayyana ta kamar yadda a wani siffa. AT: "kasance amintacce" ko "kasance da aminci"
"Yana yanke shawarar al'amura cikin gaskiya" (UDB)
Wannan siffa maras muhimmanci za'a iya bayyana ta kamar manufofi. AT: "domin dukkan mutane da ake zalumta" ko "domin dukkan waɗanda wasu mutane suke zalunta"
Wannan siffa maras muhimmanci za'a iya bayyana ta kamar manufofi. AT: "ga mutane da ke fama da yunwa" ko "ga waɗanda suke fama da yunwa"
Yana sa mutum makaho ya gani an yi magana akan sai ka ce Yahweh yana ɓude Idannun mutum. AT: "ya sa makafi su gani"
Yahweh yana taimakon wani mutum an yi magana akan sai ka ce yana taimakon wani mutum ya tashi tsaye. AT: "Yahweh na taimakon waɗanda suna kusad fid da zuciya" ko "Yahweh ya taimakon waɗanda sun raunana"
Allah yana taimakon wani mutum ya yi magana sai ka ce yana ɗaga su sama.
A nan "Sihiyona" na gabatad da dukkan mutane Isra'ila. Marubucin ya yi magana da mutane Isra'ila sai ka ce suna can suna kasa kunne gare shi. AT: "Allahnki, mutane Isra'ila"
Kalmomi "zai yi mulki" an fahimci su. AT: "zai yi mulki domin dukkan tsararraki" ko "zai yi mulki har abada"
1Ku yabi Yahweh gama yana da kyau a raira yabo ga Allahnmu, yana da daɗi, ya dace a yi yabo.2Yahweh zai sake gina Yerusalem, zai sake tattaro warwatsatsun mutanen Isra'ila.3Yana warkar da masu karyayyar zuciya ya ɗaure raunukansu.4Yana ƙididdiga taurari, ya ba dukkansu sunaye.5Mai girma ne Ubangijinmu mai daraja a iko, saninsa ya zarce gaban aunawa.6Yahweh yana tãda waɗanda aka wulaƙantasu, yakan jawo miyagu ƙasa.7Ku raira waƙa ga Yahweh tare da godiya, mu raira yabbai ga Allahnmu da garaya.8Yakan rufe sammai da gizagizai ya shirya ruwan sama domin ƙasa, ya sa ciyayi su tsiro bisa duwatsu.9Yana ba dabbobi abincinsu da kuma 'ya'yan hankaki lokacinda suka yi kuka.10Ba ya jin daɗin ƙarfin doki, ba ya dogara ga ƙarfin mutum.11Yahweh yana jin daɗin waɗanda suke girmama shi, waɗanda suka kafa begensu akan amintaccen alƙawarinsa.12Ku yabi Yahweh, Yerusalem, ki yabi Allahnki, Sihiyona.13Gama yana ƙarfafa ƙarafun ƙofofinki, yana albarkatar 'ya'yanki a cikinku.14Yana kawo wadata cikin iyakar ƙasarki, yana ƙosar dake da kyakkyawar alkama.15Yana aika dokokinsa cikin duniya, dokokinsa yakan sheƙa da gudu.16Yakan yin ƙanƙara kamar ulu, ya baza dusarta kamar toka.17Yakan aiko da ƙanƙara kamar 'yan gutsittsire, wa zai iya jure sanyin da ya ke aikowa?18Ya aika dokokinsa ya narkar dasu, yakan sa iska ta buga su sai ruwan ya kwarara.19Ya yi shelar maganarsa ga Yakubu, farillansa da dokokinsa masu adalci ga Isra'ila.20Bai taɓa yin haka ba da wata al'umma, game da dokokinsa ma, basu san su ba. Mu yabi Yahweh.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Maƙasudin watakila a kawota daga jimlan baya. AT: yana da daɗi a raira yabo"
"yabo ya kamata" ko "yabo mai dacewa"
Marubuci yana magana game bakincikin da kashe jikin mutane sai ka ce suna da raunuka, kuma Yahweh yana karfafa su sai ka ce yana warkad da waɗancan raunuka. AT: "Yana karfafa waɗanda suna bakincikin kuma ya taimake su warke daga raunukansu da ake ji"
Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai ƙuzari. AT: "ba wanda ya iya aunawa fahimtarsa" ko "fahimtarsa babu iyaka"
Marubuci yana magana game Yahweh yana girmama waɗanda suna wulaƙanta sai ka ce Yahweh yana tãda su sama daga ƙasa. AT: "Yahweh ya girmama waɗanda ke danne"
Marubuci yana magana game da Yahweh yana wulãkantãwa mugaye sai ka ce Yahweh yana tilasta su kwanta akan ƙasa. AT: "yana wulãkantã mugaye"
"yayin da a ke yin wasa da garaya"
Jimla na fi'ili za'a iya kawota daga layi na baya. AT: "kuma yana ba da abinci ga 'ya'yan hankaki lokacin da suka yi kuka"
lokacin da suka yi kuka chirp" ko "lokacin da suka yi kira"
"Karfin dawakai ba ya ba shi jin daɗin"
Zai yiwuwa ma'ana sune 1) "karfin kafafun" wani kalma ne
Marubuci yana magana da Yerusalem, wanda yana ko da yaushe kira Sihiyona, sai ka ce ita wani mutum. Sunaye birni sune kalma
Jimla "ƙarafun ƙofofinki" na gabatad da birni kamar wani dukka. Yahweh zai sa Yerusalem a daure daga mamayewa abokan gaba. AT: "domin yana kare Yerusalem"
Marubuci yana magana game da wanda suna zaune a Yerusalem sai ka ce su 'ya'yan Yerusalem ne. AT: "yana albarkace waɗanda suna zaune cikin Yerusalem"
"Yana kawo salama." Zai yiwuwa ma'ana sune 1) Yahweh yana sandin mutane wanda ke zama cikin Yerusalem don ya wadata ta kaya da kuma na kudi ko 2) kalma da an fassara kamar "wadata" na nufi "salama" kuma Yahweh yana rike Yerusalem tsira daga harin abokan gaba.
Marubuci ya bayyana dokokin Allah sai ka ce tana wani masinja ne ada ke hanzarta yin ƙaura domin itsar da sakon Allah.
Waɗannan na jadada yadda da sauki ta ke domin shi ya yi waɗannan abubuwa. Yana rufe ƙasa da ƙanƙara da sauki kamar yadda mutum ya rufe wani abu tare da bargo ulu. And, ya kau da sanyi da sauki kamar yadda iska tana baza toka.
Yahweh yana baza ƙanƙara da sauki kamar yadda mutum zai baza yan gutsittsire gurasa. AT: "Yana wasad da ƙanƙara da sauki, sai ka ce ita yan gutsittsire ne"
yan kanana gutsittsire ƙanƙara wanda ke faɗi daga sararin sama kamar rana
arubuci yana amfani da wannan tambaya don ya jadada cewa yana da wuya a jure wa yannayi sanyiida Yahweh ya yi sanadin. AT: "babu wanda da zai iya zama cikin sanyi da ya aika."
Marubuci yana magana game da dokokin Yahweh sai ka ce ita masinja ne. Kalma "dokokin" za'a iya fassara ta da wani fi'ili. AT: "Yana ba da umurni ƙanƙara ta narke"
Waɗannan layi biyu na nufi abu daya kuma na jadada cewa Yahweh ya bayarda dokansa ga Isra'ila kawai.
Jimlan na fi'ili za'a iya kawota daga layi na baya. AT: "Ya yi shella farillansa da dokokinsa masu adalci ga Isra'ila"
Kalmomin "farillan" da "dokokin adalci," tare da "kalma" cikin layi na baya, dukkan na nufi da dokokin Musa. Idan harshen ka babu kalmomi da bambanta don waɗannan sharuddan, kana iya hada layin biyu zuwa cikin daya, yi amfani ko dai "Yakubu" ko "Isra'ila" don mutane da sun karbe su.
Sauran al'ummai basu san dokokin Yahweh ba.
1Ku yabi Yahweh. Ku yabi Yahweh, ku dake cikin sammai; ku yabe shi, ku dake can tuddan sama.2Ku yabe shi, dukkanku mala'ikunsa; ku yabe shi, dukkan rundunarsa.3Ku yabe shi, rana da wata; ku yabe shi, dukkanku taurari masu ƙyalli.4Ku yabe shi, ku sammai mafi tsayi daku ruwayen dake sama da sarari.5Bari su yabi sunan Yahweh, gama ya bada umarnj, sai aka hallicesu.6Ya kuma kafasu har abada abadin; ya zartar da doka da bazata taɓa canzawa ba.7Ku yabe shi daga duniya, ku dodannin ruwa, da dukkan zurfafan teku,8wuta da ƙanƙara, dusar ƙanƙara da giza-gizai, iskar hadari masu biyayya da maganarsa.9Ku yabe shi, duwatsu, da dukkan tuddai, itatuwa masu bada 'ya'ya, da duk itatuwan sida,10namun jeji da na gida, hallitu masu rarrafe da tsuntsaye.11Ku yabi Yahweh, sarakunan duniya da dukkan al'ummai, hakimai da dukkan masu mulki a duniya,12samari da 'yan mata, dattawa da yara.13Bari dukkansu su yabi sunan Yahweh, gama sunansa kaɗai aka fiffita, ɗaukakarsa kuma ta mamaye duniya da sammai.14Ya ɗaga ƙahon mutanensa domin yabo daga dukkan amintattunsa Isra'ilawa. Mutanen dake kurkusa da shi. Ku yabi Yahweh.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
"Ku yabi Yahweh, ku dake cikin sammai ... ku dake can sararin sama." Waɗannan layi biyu suna nan faralel, da jimla "tuddan sama" na ma'ana abu daya ne kamar "sammai" a cikin layi na baya.
Marubuci yana magana da rana da wata sai ka ce su mutane ne kuma na umurtansu su yabe Yahweh. AT: "Ku yabe Yahweh, rana da wata, kamar yadda mutane ke yi"
Marubuci yana magana da taurari masu ƙyalli sai ka ce su mutane ne kuma suna umurtansu su yabe Yahweh. AT: "ku yabe Yahweh, dukkanku taurari masu ƙyalli, kamar yadda mutane ke yi"
Jimla "ku sammai mafi tsayi" wani salom zance da ke nufin da sama da kansa. Marubuci yana magana da sama sai ka ce ita mutum ne da dokokinta su yabe Yahweh. AT: "Ku yabe Yahweh, ku sammai mafi tsayi, kamar yadda mutane ke yi"
Marubuci yana magana game da wuri bisa da sararin sama inda ake adana ruwa kuma daga wace ruwan sama ke zo.
A nan kalma "suna" na gabatad da Yahweh da kansa. AT: "Bari su yabe Yahweh"
Wannan za'a iya bayyana ta cikin fom mai ƙuzari. AT: "ya hallicesu"
Zai yiwuwa ma'ana sune 1) "ya ba da doka wanda dauwamamme ne" ko 2) "ya ba da doka wanda ba zasu yi rashin biyayya ba."
"ya ba," kamar wani sarki bayarwa"
Wannan jimla na gabatad da kowane hallita da ke zaune cikin zurfafan tekuna. AT: "dukkan hallitu cikin zurfafan teku"
Marubuci yana magana da waɗannan abin aukuwa bisa ga ikon Allah sai ka ce su mutane ne da kuma dokokinsu su yabe Yahweh.
Jimla "maganarsa" na gabatad da abin da Yahweh ya umurta. AT: "iskar hadari da ke yin abin da Yahweh ya umurta"
Marubucin yana cin gaba da magana da abubuwa da ba mutum ba ne sai ka ce su mutane ne da dokokinsu don yabon Yahweh.
Kalmomin "jeji" da "gida" sun sha bam-bam. Tare sun lissafa dukkan dabbobi. AT: "dukkan dabbobi"
Marubucin ya umurce dukkan mutane su yabe Yahweh.
Kalma "al'ummai" na gabatad da mutane wanda ke zaune cikin waɗancan al'ummai. AT: "mutane na kowane al'umma"
Marubucin ya yi amfani cikin kashi biyu, daya na labarta da jinsi kuma dayan na labarta da shekaru, don gabatad da kowane mutum.
A nan kalma "suna" na gabatad da Yahweh da kansa. AT: "Yahweh, gama shi kaɗai"
Marubucin yana magana game girmaYahweh kamar yadda ɗaukakarsa kasancewa da tsawo bisa duniya da sama.
Marubucin yana magana game da karfi sai ka ce ita ƙaho ne na dabba. Dagawa sama wani ƙahon dabba wani kwatanci aiki ne da ke gabatad da nasarar soja. AT: "Ya sa mutanensa karfi" ko "Ya ba wa mutanensa nasara"
"domin dukkan amintattunsa wadanda sun yabe shi"
Marubucin yana magana game da Yahweh yana kauna mutanensa sai ka ce mutanensa suke kurkusa da shi. AT: "mutane da yana kauna"
1Ku yabi Yahweh. Ku raira wa Yahweh sabuwar waƙa; ku raira yabonsa cikin taron amintattunsa.2Bari Isra'ila su yi murna cikin wannan daya yi su; bari mutanen Sihiyona su yi murna da sarkin sarkinsu.3Bari su yabi sunansa suna rawa; bari su raira masa yabo da bandiri da molo.4Gama Yahweh yana jin daɗin mutanensa; yana ɗaukaka masu tawali'u da cetonsa.5Bari masu tsoronsa su yi murna cikin nasara; bari su yi waƙa don murna bisa gadajensu.6Bari yabon Allah ya kasance a bakinsu da takkuba masu kaifi biyu a hannunsu7domin su maida martani kan al'ummai da ayyukan hukunci akan mutane.8Zasu ɗaure sarakunansu da sarƙoƙi shugabanninsu kuma da baƙin ƙarfe.9Zasu aiwata hukunci da aka rubuta. Wannan ne zai zama ɗaukaka domin dukkan amintattunsa. Ku yabi Yahweh.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Marubucin zabura yana magana ga dukkan mutanen Allah don ka kammata ka yi amfani da siffa jam'i doka idan harshen ka yana da daya.
Zai yiwuwa ma'ana sune 1) "wani waƙa kana da shi da ba ka taba rerawa ba" ko 2) wani waƙa da ba wanda ya taba rerawa ba.
"ku yabe shi da waƙoƙi"
Zai yiwuwa ma'ana sune 1) "yi murna domin ya yi su" ko 2) "yi murna saboda wanda ya yi su nagari."
Kalmomin "sarkinsu" watakila zance da Allah. Zai yiwuwa ma'ana sune 1) "yi murna domin shi ne sarkinsu" ko 2) "yi murna domin sarkinsu nagari."
Kalman "suna"
kaya na kidi da waƙa da ke da kai kamar kalangu wanda za'a iya buga da gutanye karfe kewaye da gefe wanda ke kara sa'ad da kayan kide kide ake girgiza su
"ya bada ɗaukaka ga masu tawali;u ta wurin cetonsu daga maƙiyansu"
"ko da kamar yadda sun kwanta su yi barci da dare"
Bakin wani kalma ne
takkuba masu kaifi biyu a hannunsu - Idan takkuba ba a san su ba, yi amfani da makamin gida. Kalmar "takobi" wani kalma ne
Jimla "al'ummai" wani kalma ne
Waɗannan an yi su da karfe mai nauyi kuma na kuntata motsi na fursunoni.
sarƙoƙin biyu ko a ɗaure da sarƙa sakani wanda ke iyaka motsi na dukkan hannuwan da kafafun mutum.
yi abin da Yahweh ya sa Musa ya rubuta wanda mutane sun kammata su yi da waɗancan wanda suke da laifi
1Ku yabi Yahweh. Ku yabi Allah cikin wurinsa mai tsarki; ku yabi ƙarfinsa cikin sammai.2Ku yabe shi saboda manyan ayyukansa; ku yabe shi saboda fiffikon girmansa.3Ku yabe shi da ƙarar ƙaho; ku yabe shi da garayu da molaye.4Ku yabe shi da bandiri da rawa; ku yabe shi da garayu da sarewa.5Ku yabe shi da kuge masu ƙara; ku yabe shi da kuge masu amo.6Bari dukkan abin dake da numfashi su yabi Yahweh. Ku yabi Yahweh.
Ana samun daidaici a waƙoƙin Ibraniyawa.
Wannan yana mayar da hankali akan yabo ko sujada shi ne mafi fiye yunkurin cikin haikalin.
Haikalin Allah na sau da yawa ta'allaƙa kamar tsarkin wurinsa. Wannan shine mafin sananne wuri a tafi don sujada ga Allah.
"girman abubuwa da yana yi." "Manyan ayyukan" Allah za'a iya yiwu na nufi 1) hallita kamar hadiri da girgizar ƙasa ko 2) mu'ujjiza kamar warkasuwa da babban nasara cikni yaƙi.
Wannan bantara yana mayar da hankali akan yin yabo ko yin sujada ga Allah da kayan kide-kide da rawa.
Bandiri wata kaya na kidi da waƙa da ke da kai kamar kalangu wanda za'a iya buga da gutanye karfe kewaye da gefe wanda ke kara sa'ad da kayan kide kide ake girgiza su
siriri abu biyu, mulmulalle faranti karfe wanda ana buga su tare don ta yi amo mai karfi
Wannan aya ya fi karshen wannan zabura. Bayyani ne na rufewa domin dukkan Littafi na 5 na Zaburan, wanda ra fara a Zabura 107 kuma ta na karshe da Zabura 150.
Zai yiwuwa ma'ana sune 1) dukkan mutane wanda suna da rai su yabe Allah ko 2) dukkan halitta da yake da rai ya yabe Allah.
1Misalai na Suleman ɗan Dauda, sarkin Isra'ila.2Waɗannan misalai zasu koyar da hikima da koyarwa, zasu koyar da maganganun fasaha,3domin ka sami koyarwa domin ka rayu ta wurin yin abin da ke dai-dai, gaskiya da adalci.4Waɗannan misalai kuma zasu bada hikima ga marar sani, su kuma bada ilimi da fahimta ga matasa.5Bari mutane masu hikima su saurara su ƙaru a koyonsu, bari mutane masu ganewa su sami bishewa,6su kuma fahimci misalai, karin magana, da maganganun mutane masu hikima da kacici-kacicinsu.7Tsoron Yahweh shi ne mafarin ilimi - wawaye sukan rena hikima da koyarwa.8Ɗana, ka kasa kunne ga koyarwar mahaifinka, kada kuma ka watsar da dokokin mahaifiyarka;9zasu zamar maka rawani cike da alheri a kanka da abubuwan ratayawa masu kyau a wuyanka.10Ɗana, idan masu zunubi suka jarabce ka zuwa cikin zunubinsu, kada ka bi su.11Idan suka ce, "Ka zo tare da mu, bari mu yi fakon jinin, bari mu yi kwanto mu kai farmaƙi ga mutane marasa laifi ba tare da dalili ba.12Bari mu haɗiye su da rai, kamar yadda Lahira take ɗauke waɗanda ke lafiyayyu, ta maishe su kamar waɗanda suka faɗa cikin rami.13Zamu sami abubuwa iri iri masu daraja; zamu cika gidajenmu da ganimar da muka sato gun waɗansu.14Ka haɗa kai da mu; zamu kasance dukka da ma'aji guda tare."15Ɗana, kada ka bi wannan hanyar tare da su; kada ka yarda ƙafarka ta bi wajen da suke tafiya;16ƙafafunsu suna gudu garin yin mugunta suna hanzari su zubda jini.17Gama ba amfani a kafa wa tsuntsu tarko a idanunsa.18Waɗannan mutane jininsu ne suke kafa wa tarko - suna kwanto ne su kama rayukansu.19Haka kuma duk hanyoyin wanda ya sami arziƙi ta rashin adalci; ƙazamar riba takan ɗauke rayukan waɗanda suka riƙe ta kam-kam.20Hikima tana kuka da ƙarfi a tituna, tana ɗaga murya a dandali;21a karafku da ake hayaniya tana kururuwa, a ƙofofin birane tana magana,22"Har yaushe, ku mutane marasa ganewa, zaku ƙaunaci rashin ganewa? Har yaushe, ku masu ba'a, zaku ci gaba da jin daɗin ba'a, kuma har yaushe, ku wawaye zaku ƙi ilimi?23Ku kasa kunne ga tsautawa ta; zan faɗa maku tunanina; Zan sanar maku da maganganuna.24Na yi kira, amma kuka ƙi ku saurara; na miƙa maku hannuna, amma ba wanda ya kula.25Amma duk kun yi watsi da koyarwata ba ku saurara da gyaran da na yi maku ba.26Zan yi dariya sa'ad da masifa ta zo maku, zan yi maku ba'a sa'ad da razana ta zo -27lokacin da abin da kuke jin tsoro ya zo kamar hadari kuma bala'i ya auko kanku kamar guguwa, lokacin da azaba da damuwa suka sauko bisa kanku.28Sa'an nan zasu kira ni, ba zan kuma amsa ba; zasu kira ni da himma, amma ba zasu same ni ba.29Domin sun ƙi ilimi, kuma ba su zaɓi tsoron Yahweh ba,30ba zasu bi koyarwata ba, kuma suka rena dukkan gyaran kuskurensu da na yi masu.31Zasu ci 'ya'yan hanyoyinsu, da kuma 'ya'yan shirye shiryensu zasu ƙoshi.32Domin a kan kashe dolaye lokacin da suka bar tafarki, wautar wawaye ta rashin kulawa zata hallaka su.33Amma dukkan wanda ya kasa kunne gare ni zai zauna lafiya, zai huta a tsare babu tsoron masifa."
Ayoyi na 2-33 waka ce.
Ana iya sake amfani da wannan don sake bayyana sunayen "hikima" da "umarni" azaman siffofi ko kalmomin aiki. AT: "don koya muku yadda ake hikima da kuma koya muku yadda ake rayuwa mai ɗabi'a"
"don taimaka muku fahimtar koyarwar hikima"
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda bayyananniyar suna “wa’azi” ya zama kalmar aiki. AT: "ana iya umurtar yadda ake rayuwa"
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda za'a iya bayyana kalmar "hikima" a matsayin kalmar sihiri "mai hikima." Hakanan za'a iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kuma koya wa waɗanda basu da hankali yadda ake hikima"
"rashin kwarewa ko rashin haihuwa"
Ana iya bayyana sunayen suna "ilimi" da "hankali" azaman kalmomin aiki. AT: "da kuma koya wa matasa abin da ya kamata su sani da kuma yadda za su fahimci abin da ya dace su yi"
"Bari masu hankali su maida hankali su kara koya"
"bari masu hankali su koya daga waɗannan karin magana yadda ake yanke shawara mai kyau"
maganganun da mutum zai iya fahimta sai bayan tunanin su
Uba yana koyar da ɗansa.
AT: "Dole ne ku fara jin tsoron Yahweh domin fara sanin abin da ke da hikima"
Wannan sunan Allah ne wanda ya bayyana wa mutanensa a Tsohon Alkawari. Duba shafin tranlationWord game da Yahweh game da yadda za a fassara wannan.
"waɗanda ba su daraja abin da yake da hikima da kuma koyarwa su wawaye ne"
Dokoki da umarni da iyaye ke koya wa yaransu suna da mahimmanci da mahimmanci don ana magana da su kamar suna da kyakkyawan fure ko abin al'ajabi da mutum ke sanyawa. AT: "za su ba ka hikima kamar yadda sanya hular wuya a kanka ko abin wuya a wuyanka ya ba ka kyau"
"kokarin lallashe ka ka yi zunubi kamar yadda suke yi"
"ƙi su" ko "kar ku saurare su"
Anan mai maganar yana bada misalin abin da masu zunubi zasu iya ƙoƙarin yaudarar wani yayi"
Ayoyi 12-14 sun ƙare bayanin tunanin masu zunubi waɗanda suke ƙoƙarin yaudarar wasu suyi zunubi.
Masu zunubi suna maganar kisan marasa laifi kamar suna Lahira kuma zasu ɗauki mai rai da lafiya zuwa inda matattu suke.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan na nufin matafiya ne da suka faɗa cikin rami mai zurfi inda ba wanda zai same su ko 2) a nan "rami" wata kalma ce da ke nufin Lahira ko wurin da matattu suke.
Wannan karin magana ne. AT: "Kasance tare da mu"
Don kauce wa yin abu kamar yadda masu zunubi suke yi ana magana ne kamar ɗa zai guji yin tafiya a kan ko ma taɓa hanyoyin da masu zunubi suke bi. AT: "kada ku tafi tare da masu zunubi ko ku aikata abin da suke yi"
Anan “jini” yana wakiltar rayuwar mutum. 'Zub da jini' na nufin kisan wani.
Wannan kwatancen yana kwatanta hikimar tsuntsayen da ke guje wa tarkunan da suke gani da wautar masu zunubi da suka faɗa cikin tarkunan da suka yiwa kansu.
Wannan ya gama kwatancen da aka fara a cikin Misalai 1:15. Mutanen da ke halakar da kansu ta aikata abubuwan zunubi suna magana ne kamar suna kafa tarko kuma su kashe kansu. AT: "Amma waɗannan mutanen sun fi tsuntsaye wauta. Suna kashe kansu da tarkon kansu"
Ana maganar makomar mutum ko kaddararsa kamar wata hanya ce da mutum yake bi. AT: "Wannan shine abin da ke faruwa ga kowa da kowa"
Mutumin da yake lalata kansa ta hanyar ƙoƙarin neman arziki ta hanyar tashin hankali, sata, da yaudara ana maganarsa kamar dai rashin adalci zai kashe waɗanda suka ɗauka. AT: "kamar riba ce mara kyau za ta halakar da waɗanda suka riƙe ta"
A cikin Misalai 1: 20-1: 33 ana magana da hikima kamar mace ce ke magana da mutane.
Idan yarenku bai baku damar daukar hikima ba kamar yadda mace take yiwa mutane kirari a cikin gari, kuna iya gwada wani abu kamar "Kaka Hikima tana kuka da ƙarfi" ko "Mai Girma Hikima tana kuka da ƙarfi" ko "Hikima kamar mace ce da ke ihu da ƙarfi "
Hikima tana amfani da wannan tambayar don tsawata wa waɗanda ba su da hikima. AT: "Ku da kuke butulci dole ne ku daina ƙaunaci butulci."
Hikima tana amfani da wannan tambayar don tsawata wa masu izgili da wawaye. AT: "Ku da kuke ba'a dole ne ku daina jin daɗin ba'a, ku kuma wawaye dole ku daina ƙin ilimi."
Hikima ta cigaba da magana.
"A yi saurara sosai"
Hikimar gaya wa mutane duk abin da take tunani game da su ana magana da ita kamar tunaninta ruwa ne da za ta zubo.
"Zan fada muku abin da nake tunani"
Wannan jumlar wani karin magana ne da ke nufin yiwa mutum alama ko kuma gayyatar mutum ya zo. AT: "Na gayyace ku ku zo wurina"
Hikima na ci gaba da magana, tana bayanin abin da ke faruwa ga waɗanda suka yi biris da ita.
Ana iya bayyana wannan tare da kalmar "saboda haka" don nuna cewa mace hikima tana musu dariya saboda sun yi biris da ita. AT: "Saboda haka zan yi dariya"
"idan sharri ya same ka"
An kwatanta munanan abubuwa da ke faruwa ga mutane da guguwar da ta auka masu kuma haifar da tsoro da wahala.
Hikima ta ci gaba da magana.
"Sa'an nan wadanda suka yi biris da ni za su nemi taimako na"
Ana iya bayyana kalmar 'ilimin' wacce ba a sani ba azaman kalmar "koya". AT: "Saboda sun ƙi koyon hikima"
AT: "bai ji tsoron Yahweh ba" ko "bai girmama kuma girmama Yahweh ba"
"ba zai karɓi umarni na ba" ko "ya ƙi shawarata"
Aya ta 33 ta ƙare da bayanin hikima wanda ya fara a Misalai 1:20.
Anan ana maganar halayen mutum kamar wata hanya ce ko hanya. Hakanan, mutum yana karɓar sakamakon halayensu ana magana ne kamar mutum yana cin ɗanɗanar halayensu. AT: "dandana sakamakon ayyukansu"
"Za su ci amfanin makircinsu har sai sun koshi." Ana magana da mutumin da ke karɓar sakamakon sakamakon mugayen dabarunsu kamar ya ci amfanin dabarunsu. AT: "za su sha wahala sakamakon makircinsu na mugunta"
Mutumin da ya ƙi hikima ana maganarsa kamar mutum ya juya baya ga hikima. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "sun mutu saboda sun ƙi koyo"
1Ɗana, idan ka karɓi zantattukana kuma ka ajiye dokokina tare da kai kamar abu mai tamani,2ka sa kunnenka ya maida hankali ga hikima kuma ka bada zuciyarka ga fahimta.3Idan ka ƙwala kira domin fahimta ka ɗaga murya dominta,4idan ka nemeta kamar yadda zaka nemi azurfa ka kuma biɗi fahimta kamar yadda zaka biɗi ɓoyayyiyar dukiya,5sa'an nan zaka san tsoron Yahweh zaka kuma sami sanin Allah.6domin Yahweh yana bada hikima, daga bakinsa ilimi da fahimta ke fitowa.7Yana tanada sahihiyar hikima domin waɗanda suka gamshe shi, kuma garkuwa ne ga waɗanda suke da aminci,8yana tsaron tafarkun adalci zai kuma kiyaye hanyoyin waɗanda suke bin sa da aminci.9Sa'an nan ne zaka fahimci abin da ke da adalci, da, gaskiya, da kowanne tafarki mai kyau.10Gama hikima zata shiga cikin zuciyarka, ilimi kuma zai ji wa ranka daɗi.11Hankali zai lura da kai, fahimta kuma zata kiyaye ka.12Zasu cece ka daga hanyar mugunta, daga kuma masu faɗar abubuwan saɓo,13waɗanda suka yi watsi da tafarkun gaskiya suna tafiya a hanyoyin duhu.14Suna farinciki sa'ad da suke yin mugunta, suna jin daɗi cikin aikata mugunta iri-iri.15Suna bin karkatattun tafarku, suna amfani da ruɗu sun ɓoye manufarsu.16Hikima da sanin dai-dai zasu cece ka daga mace mazinaciya, daga mace mai ƙazantar rayuwa daga maganganunta na zaƙin baki.17Takan yashe da abokinta na ƙuruciya ta manta da alƙawarin Allahnta.18Gama gidanta na bishewa zuwa mutuwa hanyoyinta zasu bishe ka zuwa gun waɗanda ke cikin kabari.19Duk masu tafiya wurinta ba zasu sake dawowa ba kuma ba zasu sami tafarkun rai ba.20Saboda haka zaka yi tafiya a hanyar mutanen kirki ka kuma bi tafarkun adalan mutane.21Domin adalai zasu kafa mazauni a ƙasar, amintattu kuma za a barsu a cikinta.22Amma za a datse mugaye daga ƙasar, marasa bangaskiya kuma za a datse su daga ita.
Uba yana koya wa ɗansa amfani da waƙa.
"idan kun saurari abinda nake koya muku"
Amincewa da abin da aka umurta ana maganarsa kamar dokokin sun kasance taska ce kuma mutum ya kasance amintaccen wuri don adana taskar. AT: "ku yi la'akari da dokokina da ƙima kamar taska"
Anan “zuciya” tana wakiltar tunanin mutum. Kalmomin "karkatar da zuciyar ka" karin magana ne da ke nufin aikata ko cika ba da hankalin mutum ga aiki. AT: "yi ƙoƙari ka fahimci abin da yake mai hikima" ko "ka sadaukar da kanka sosai don fahimtar koyarwa mai hikima"
Duk waɗannan jimlolin suna da ma'ana iri ɗaya. An nuna cewa mutumin yana roƙon Yahweh da ƙarfi don fahimta. AT: "Idan kuka roƙi Allah da gaggawa kuma kuka roƙe ku don fahimta"
Dukansu jimlolin suna da ma'ana iri ɗaya. Waɗannan kamannin suna nuna babban ƙoƙarin da ya kamata mutum ya yi don fahimtar abin da yake da hikima. AT: "idan kuna neman fahimta da kwazo kamar yadda kuke neman abu mai mahimmanci"
Yin nasara cikin sanin Allah ana maganarsa kamar ilimin Allah abu ne da mutum ya samu bayan ya bincika.
Anan “baki” yana wakiltar Yahweh ne da kansa ko abin da yake faɗa. AT: "daga Yahweh ne ilimi da fahimta suke zuwa" ko kuma "Yahweh yana gaya mana abin da muke buƙatar sani da fahimta"
Yahweh yana koyar da hikima ga mutane ana maganarsa kamar hikima wani abu ne wanda Yahweh yake ajiyewa kuma yake bawa mutane. AT: "Yana koyar da ainihin hikima ga waɗanda suka faranta masa rai"
Mai yiwuwa ma'anoni sune 1) adalci kansa ana maganarsa kamar yana hanya. AT: "Allah yana tabbatar da cewa mutane sunyi adalci" ko 2) ana maganar rayuwar mutum kamar dai hanya ce. AT: "Allah yana kiyaye waɗanda ke yin adalci"
Halin da ke da hikima da kuma faranta wa Yahweh rai ana maganarsa kamar hanya ce mai kyau. AT: "hanyoyin rayuwa wadanda suke yardar da Allah"
Anan “zuciya” tana wakiltar yanayin mutum. Ana magana da mutumin da ya zama mai hikima kamar hikima za ta shiga zuciyar mutum. AT: "zaku sami hikima da yawa" ko "za ku koyi yadda ake samun hikima da gaske"
Anan “kurwa” tana wakiltar mutum duka. AT: "yana faranta maka" ko "yana maka daɗi"
Wannan yana magana ne akan "hankali" da "fahimta" kamar dai su mutane ne da zasu iya kula da wani. Duk maganganun guda biyu suna nufin abu guda ne. AT: "Saboda kun yi tunani mai kyau kuma kun fahimci abin da ke daidai da kuskure za ku sami lafiya"
"Su" suna nufin hankali da fahimta, waɗanda ake maganarsu kamar mutane ne da zasu iya ceton wani. AT: "Za ku san ka nisanci mugunta"
Mutum baya yin abin da yake daidai amma yana yanke shawarar aikata mugunta ana maganarsa kamar mutum ya daina tafiya akan madaidaiciyar hanya kuma ya zaɓi ya bi ta hanyar da ke cikin duhu.
"Su" yana nufin mutane iri ɗaya kamar yadda a cikin Misalai 2:1.
Wannan yana nufin abu ɗaya daidai da ɓangaren farko na jumlar. AT: "jin daɗin aikata abin da suka san mugunta ne"
Mutanen da suke yi wa wasu ƙarya ana maganarsu kamar suna tafiya a kan karkatattun hanyoyi. AT: "Suna yaudarar wasu mutane"
Ana yin magana da mutane don kada wasu su gano abin da suka aikata ana maganarsu kamar sun rufe hanyoyin akan hanyar saboda babu wanda zai iya bin su. AT: "suna yin karya don kada wani ya san abin da suka aikata"
Uba yana ci gaba da koya wa ɗansa yadda hikima za ta kāre shi.
Marubucin yayi maganar hikima da hankali kamar mutane ne masu ceton wanda yake dasu. AT: "Idan kuna da hikima da hankali, zaku ceci kanku"
Wannan yana nufin mijinta, wanda ta aura tun tana ƙarama.
Wataƙila wannan yana nufin alkawarin aure da ta yi da mijinta a gaban Allah.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "zuwa gidanta yana kaiwa ga mutuwa" ko 2) "hanyar gidanta hanyar mutuwa ce."
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "ba za su koma ƙasar masu rai ba" ko 2) "ba za su sake rayuwa cikin farin ciki ba."
Marubucin ya faɗi sakamakon samun fahimta da hankali.
Ana magana akan halayen mutum kamar yana tafiya akan hanya. AT: "zaku rayu ta hanyar ... bi misali"
Marubucin yayi maganar Yahweh yana cire mutane daga ƙasar kamar yana yanke mutane, kamar yadda mutum zai iya yanke reshe daga itace. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai cire mugaye daga ƙasar"
1Ɗana kada ka manta da umarnaina ka riƙe koyarwata a cikin zuciyarka,2domin za su ƙara maka tsawon kwanaki da shekarun rayuwa za su kuma ƙara maka salama.3Kada ka bari alƙawarin aminci da dogara su taɓa barinka, ka ɗaura su tare a wuyanka, rubuta su a allon zuciyarka.4Sa'an nan zaka sami tagomashi da suna mai kyau a gaban Allah da mutum.5Ka dogara ga Yahweh da dukkan zuciyarka kada ka jingina ga taka fahimta;6cikin dukkan hanyoyinka ka san da shi, shi kuwa zai maida tafarkunka miƙaƙƙu.7Kada ka zama da hikima a naka idanu; ka ji tsoron Yahweh ka guji mugunta.8Za ta zamar maka warkaswa ga naman jikinka da wartsakewa ga jikinka.9Ka girmama Yahweh da dukiyarka da nunar fari na dukkan aikinka,10sai rumbunanka su cika kuma matatsar ruwan 'ya'yan inabinka zasu yi ambaliya, su cika da ruwan inabi.11Ɗana, kada ka rena koyarwar Yahweh kuma kada ka ƙi kwaɓarsa,12gama Yahweh yana horon wanda ya ke ƙauna, kamar yadda mahaifi ya ke tarbiyantar da ɗansa wanda ya ke gamsarsa.13Mai albarka ne wanda ya sami hikima; ya kuma sami fahimta.14Ribar da ka samu daga hikima ta fi abin da azurfa zata bayar a bisani kuma ribarta tafi zinariya.15Hikima tafi duwatsu masu ƙawa daraja kuma dukkan abin da kake marmari ba za a gwada su da ita ba a tamani.16Tana da tsawon kwanaki cikin hannun damarta a cikin hannun hagunta akwai arziki da ɗaukaka.17Hanyoyinta hanyoyin alheri ne kuma dukkan tafarkunta na salama ne.18Itacen rai ce ga waɗanda suka kamata, waɗanda suka riƙe ta suna da farinciki.19Ta wurin hikima Yahweh ya kafa duniya, ta wurin fahimta ya shimfiɗa sammai.20Ta wurin iliminsa zurfafa suka buɗe kuma giza-gizai suka zubo da raɓarsu.21Ɗana, ka riƙe hukuncin gaskiya da sanin dai-dai kada ka ɗauke ido daga gare su.22Za su zama rai a rayuwarka da kayan ado na alheri da zaka rataya zagaye da wuyanka.23Sa'an nan zaka yi tafiya a hanyarka lafiya ƙafarka ba zata yi tuntuɓe ba;24sa'ad da ka kwanta, ba zaka ji tsoro ba; lokacin da ka kwanta, zaka yi barci mai daɗi.25Kada ka ji tsoron masifar da zata zo farat ɗaya ko hallakarwar da mugaye suka haddasa, sa'ad da ta zo,26domin Yahweh za ya kasance tare da kai ya tsare kafafunka daga faɗawa cikin tarko.27Kada ka janye daga yin alheri ga waɗanda suka cancanta, yayin da kake da ikon aikatawa.28Kada ka cewa maƙwabcinka, "Tafi ka sake dawowa, gobe zan baka," alhali kuwa da kuɗin tare da kai.29Kada ka shirya cutar da maƙwabcinka - wanda ya ke kusa da kai ya kuma amince da kai.30Kada ka yi jayayya da mutum ba dalili, sa'an nan bai yi komai ba don ya cuce ka.31Kada ka ji ƙyashin ɗan ta'addar mutum ko ka zaɓi hanyoyinsa.32Domin masu aikata mugunta abin ƙyama ne ga Yahweh, amma yana karɓar mutum mai adalci ya amince da shi.33La'anar Yahweh tana kan gidan mugun mutum, amma yana sa albarka a gidan adalan mutane.34Yakan yi wa masu ba'a ba'a, amma yakan bada jinƙansa ga mutane masu tawali'u.35Mutane masu hikima sukan gãji girmamawa, amma za a ɗauke wawaye cikin kunyarsu.
Marubucin yana magana ne a matsayin uba yana koya wa ɗansa amfani da waka.
Ana iya fassara kalmar "umarni" azaman aiki. AT: "kar ku manta da abin da na umurce ku"
Wannan jumlar ta faɗi ta ƙa'idodi masu ma'anar abin da kalmar da ta gabata ta faɗa a cikin mummunan ra'ayi. Anan kalmar "zuciya" tana wakiltar hankali. Kalmar "koyarwa" ana iya fassara ta azaman aiki. AT: "koyaushe ku tuna da abin da na koya muku"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna nufin tsawon rayuwar mutum. AT: "duk rayuwar ku" ko "muddin kuna raye"
Marubucin yayi maganar "amincin alkawari" da "amana" kamar dai su mutane ne da zasu iya barin wani. Sunayen "aminci" da "amana" za'a iya bayyana su da "aminci" da "amintacce." AT: "Koyaushe ku kasance amintattu kuma ku kasance masu aminci ga alkawarin"
Marubucin yayi maganar aminci da rikon amana kamar dai su abubuwa ne da mutum zai iya ɗaurawa a wuya kamar abin wuya. Hoton ya nuna cewa waɗannan abubuwa ne masu ƙima waɗanda mutum yake nunawa a zahiri. AT: "a nuna su da alfahari kamar wanda zai sa abun wuya"
Anan zuciya tana wakiltar tunanin mutum. Ana magana da hankali kamar dai kwamfutar hannu ce wanda wani zai iya rubuta sakonni da umarni a kansa. Madadin fassara: "koyaushe ku tuna da su, kamar dai kun rubuta su dindindin a kan kwamfutar hannu"
Anan kalmar "zuciya" tana wakiltar mutum ne na ciki. Madadin fassara: "dukkan ku"
Marubucin yayi maganar dogaro ga fahimtar mutum kamar cewa "fahimta" abu ne da mutum zai dogara da shi. AT: "kada ku dogara da fahimtarku"
Marubucin yayi maganar ayyukan mutum kamar dai hanyoyi ne da mutum yake tafiya akansu. AT: "a cikin duk abin da kuke yi"
Marubucin yayi magana game da Yahweh yana sa ayyukan mutum su zama masu ci gaba kamar dai ayyukan mutumin hanyoyi ne da yake tafiya akan su kuma wanda Yahweh ke sanyawa ba tare da matsaloli ba. AT: "zai baku nasara"
Marubucin yayi maganar ra'ayin mutum kamar mutumin yana ganin wani abu da idanunsa. AT: "Kada ku zama masu hikima a ra'ayinku"
Marubucin yayi maganar rashin aikata mugunta kamar tana nisantar mugunta. AT: "kada ku aikata mugunta"
Kalmar "ta" tana nufin umarnin da marubuci ya bayar a ayar da ta gabata. Cikakkiyar ma’anar wannan ana iya bayyana ta a sarari. Kalmar nan “nama” tana wakiltar jiki duka. AT: "Idan kunyi haka, zai zama waraka ga jikinku"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Madadin fassara: "rumbunanku za su cika"
kwandunan ajiyar ku zasu cika sosai, kamar dai a shirye suke su buɗe.
Marubucin ya yi rubutu a matsayin uba yana koyar da ɗansa.
"ɗa wanda yake faranta masa rai." Wannan yana nuni ne ga soyayyar uba ga ɗa, kuma ba don yardar uba ga halayen ɗansu ba. AT: "ɗa wanda yake ƙauna"
Marubucin yayi maganar “hikima” kamar abu ne wanda mutum ya samu. AT: "Wanda ya sami hikima"
Wannan yana nufin ribar da mutum zai iya samu daga ciniki ko saka azurfa.
Marubucin yayi maganar hikima kamar mace.
Marubucin yayi maganar fa'idodi da mutum yake samu daga samun hikima kamar hikima itace mace wacce ta riƙe waɗannan halayen a hannunta ta miƙa su ga mutane. AT: "Hikima tana ba mutum tsawon kwanaki da wadata da girma"
Marubucin yayi magana game da hikima kamar mace kuma game da fa'idodin da hikima ke ba mutum kamar hikima tana jagorantar mutumin a kan hanya. AT: "Hikima koyaushe za ta yi muku alheri kuma ta ba ku zaman lafiya"
Marubucin yayi maganar hikima kamar itace da take bada 'ya'yan itacen mai ba da rai da kuma mutumin da ke cin gajiyar hikima kamar mutumin ya ci 'ya'yan itacen. AT: "Hikima kamar itaciya ce wacce ke rayar da rayuwar waɗanda suka ci 'ya'yanta"
Marubucin yayi maganar Yahweh ne wanda ya halicci duniya da sammai kamar yana aza harsashin gini ne. AT: "Yahweh ya halicci duniya ... ya yi sammai"
Marubucin yayi maganar rashin manta abu kamar koyaushe yana iya ganin sa. AT: "kar ku manta da su"
Anan kalmar “kurwa” tana wakiltar mutumin. AT: "Za su zama muku rai"
Marubucin yayi magana game da "ingantaccen hukunci" da "fahimta" kamar dai abubuwa ne da mutum zai iya ɗaurawa a wuyansa kamar abun wuya. Hoton ya nuna cewa waɗannan abubuwa ne masu ƙima waɗanda mutum yake nunawa a zahiri. AT: "nuni na alheri kamar wanda zai yi wa kansu ado da abin wuya"
Marubucin yayi maganar rayuwar mutum kamar mutum yana tafiya akan hanya. AT: "zaku rayu a cikin aminci"
Kalmar "ƙafa" tana wakiltar mutum duka. Marubucin yayi maganar yin ba dai-dai ba kamar mutum yayi tuntuɓe akan abu a cikin hanyar sa. AT: "ba za ku aikata abubuwan da ba daidai ba"
Marubucin yayi maganar bacci mai nutsuwa da sanyaya rai kamar yana ɗanɗana wa mutumin da yake bacci. Ana iya fassara kalmar "bacci" azaman fi'ili. AT: "barcinku zai kasance mai daɗi" ko "za ku yi barci cikin kwanciyar hankali"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da mugaye ke haddasa barna"
"Yahweh zai kasance tare da kai." Mutumin da yake tsaye kusa da wani mutum karin magana ce ta nufin cewa ɗayan zai taimaka kuma ya goyi bayan ɗayan. AT: "Yahweh zai goyi bayan ku kuma ya kare ku"
Marubucin yayi magana akan mutumin da yake fuskantar cutarwa daga "ta'addanci" da "lalacewa" kamar dai an kama mutumin ne cikin tarko. Kalmar "ƙafa" tana wakiltar mutum duka. AT: "zai kare ku daga waɗanda suke son cutar ku"
"Kada ku hana abubuwa masu kyau" ko "Kada ku hana kyawawan ayyuka"
"lokacin da kuka sami damar taimakawa"
Ana nuna cewa ba zai zaɓi ya kwaikwayi ayyukan mutumin tashin hankali ba. AT: "Kada ku" zabi don kwaikwayon kowace hanyar sa "
"Yahweh yana ƙyamar mai ha'inci"
Yahweh yana faɗar tunaninsa ga waɗanda suke aikata dai-dai kamar yadda yake tare da amini, amintacce. AT: "Yahweh babban aboki ne ga masu karkata"
Marubucin yayi maganar la'anar Yahweh kamar wani abu ne wanda ya sanya shi a saman gidan mugu. Kalmar "gida" magana ne ga iyali. AT: "Yahweh ya la'anci dangin mugaye"
Kalmar "gida" tana wakiltar iyali. AT: "ya albarkaci dangin mutanen kirki"
Marubucin yayi magana akan yardar Yahweh kamar wani abu ne da yake baiwa mutane. AT: "yana nuna falalarsa ga mutane masu tawali'u" ko "yana da karimci ga masu tawali'u"
Marubucin yayi maganar mutane masu hikima da suka sami suna na girmamawa kamar sun gaji girmamawa azaman mallaka ta din-din-din. AT: "Masu hikima za su sami daraja" ko "Masu hikima za su sami suna mai daraja"
Marubucin yayi magana ne game da Yahweh yana mai bayyana rashin hankalin wawaye ga kowa kamar dai Yahweh yana ɗaga wawaye ne domin kowa ya gansu. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai sa kowa ya ga abin kunya na wawaye"
1Ku kasa kunne, 'ya'ya maza, ga koyarwar mahaifinku, ku maida hankali, domin ku san ko mene ne fahimta.2Ina baku koyarwa mai kyau; kada ku yi banza da koyarwata.3Sa'ad da nake ɗan yaron mahaifina, ina cikin ƙuruciya kuma ni kaɗai ne a gun mahaifiyata,4ya koyar da ni ya ce mani, "Bari zuciyarka ta riƙe maganganuna da kirki; ka kiyaye dokokina ka rayu.5Ka sami hikima da fahimta; kada ka manta kuma kada kuma ka ƙi maganganun bakina;6kada ka ƙyale hikima zata tsare ka; ka ƙaunaceta zata kiyaye lafiyarka.7Hikima ita ce mafificin abu, saboda haka ka sami hikima ka sayar da duk mallaƙarka don ka sami fahimta.8Ka ƙaunaci hikima za ta girmamaka; zata girmama ka sa'ad da ka rungume ta.9Zata ɗaura maka rawanin girmamawa a kanka; zata ba ka kambi mai kyau."10Ka kasa kunne, ɗana, ka maida hankali ga maganganuna, zaka kuma sami shekaru da yawa a cikin rayuwarka.11Ina nuna maka hanyoyin hikima; ina bishe ka a miƙaƙƙun tafarku.12Sa'ad da kake tafiya, ba wanda zai tsaya a hanyarka in kana gudu, ba zaka yi tuntuɓe ba.13Ka riƙe koyarwa, kada ka barta ta kubce; ka tsare ta, gama ita ce ranka.14Kada ka bi tafarkin mugaye kuma kada ka bi hanyoyin masu aikata mugunta.15Ka kauce mata, kada ka bi ta kanta; juya daga gare ta ka bi wata hanyar.16Domin ba sa iya barci sai sun aikata mugunta kuma sukan rasa barci sai sun sa wani ya yi tuntuɓe.17Domin sukan ci abincin mugunta su sha ruwan inabin ta'addanci.18Amma tafarkin adalan mutane kamar fitowar rana ne da ke ta ƙara haskakawa; hasken yana ta ƙara girma har tsakiyar rana ta zo.19Hanyar mugu kamar duhu take - ba su san yadda take ba suke tuntuɓe a kai.20Ɗana, ka maida hankali ga maganganuna; ka bada kunnuwanka ga faɗata.21Kada ka bari su guje wa idanunka; ka ajiye su a zuciyarka.22Gama maganata rai ne ga waɗanda suka same ta lafiya ce kuma ga dukkan jikinsu.23Ka kiyaye lafiyar zuciyarka ka tsare ta da himma, domin daga cikinta maɓuɓɓugar rai ke zubowa.24Ka kawar da alfasha nesa daga gare ka ka kuma kawar da ruɓaɓɓar magana nesa daga gare ka.25Bari idanunka su dubi gaba sosai ka kuma kafa ƙurawarka miƙe a gaban ka.26Ka yi wa ƙafarka tafarkin da ke dai-dai; sa'an nan ne dukkan hanyoyinka zasu zama lafiyayyu.27Kada ka juya zuwa dama ko hagu; ka juyar da ƙafafunka daga mugunta.
Marubucin yayi magana kamar uba yana koyarda yaransa.
"a saurara lafiya"
"zaku san yadda zaku fahimta" ko "zaku sami fahimta"
"Abin da nake koya muku mai kyau ne"
Wannan yana nufin lokacin da marubucin ya kasance yaro har yanzu yana rayuwa ƙarƙashin kulawar mahaifinsa. AT: "Lokacin da nake saurayi koya daga mahaifina"
Anan kalmar "taushi" tana nufin ƙaramin yaro wanda har yanzu yaron ba shi da ƙarfi. Yana ƙirƙirar magana tare da kalmar "kawai." AT: "ɗa mai taushi"
Anan kalmar “zuciya” tana wakiltar tunanin mutum. Marubucin yayi maganar tuno kalmomi kamar zuciya tana makale dasu sosai. AT: "Kullum ku tuna da abin da nake koya muku"
Uba yana ci gaba da koya wa yaransa abin da mahaifinsa ya koya masa.
"Yi aiki tuƙuru don neman wa kanka hikima" ko "Samu hikima"
Anan kalmar "baki" tana wakiltar mutumin da yayi magana. AT: "abin da nake fada"
Marubucin yayi maganar hikima kamar mace ce ke kare mutumin da ke aminta da ita.
Uba ya gama koyawa yaransa abinda mahaifinsa ya koya masa.
"darajar fahimta fiye da duk abinda ka mallaka"
Marubucin yayi magana game da hikima kamar mace ce kuma ta hikima tana ba mutum girma girma kamar hikima ce ta ɗaga wannan mutumin zuwa wani babban matsayi. AT: "Idan kuna girmama hikima, za ta ba ku girma mai girma"
Marubucin yayi magana game da girmamawar da mutum zai samu daga samun hikima kamar dai hikima ta sanya fure a kan mutumin. AT: "Hikima za ta zama kamar hure a kanka wanda ke nuna girman darajarka"
Marubucin yayi maganar girmamawar da mutum zai samu daga samun hikima kamar hikima ta sanya rawanin kan mutumin. AT: "hikima za ta zama kamar kyakkyawar kambi a kanka"
"zaka rayu tsawon shekaru"
Marubucin yayi maganar koyawa ɗansa rayuwa mai hikima kamar yana jagorantar ɗansa akan hanyoyin da mutum zai sami hikima. AT: "Ina koya muku yadda ake rayuwa cikin hikima; Ina bayanin yadda ya dace a rayu"
Wadannan layi guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. Marubucin yayi magana akan yanke shawara da ayyukan da mutum yakeyi kamar dai mutumin yana tafiya ne ko kuma yana tafiya akan hanya kuma mutumin yana cin nasara kamar dai hanyar bata da matsaloli da zasu iya sa mutumin yayi tuntuɓe. AT: "Lokacin da kuka shirya wani abu, zaku sami nasarar aikata shi"
Marubucin yayi maganar mutum yana tuna abin da ya koya kamar "umarni" abu ne da mutum zai iya riƙewa sosai. AT: "Ku ci gaba da yin biyayya ga abin da na koya muku kuma kada ku manta da shi"
Marubucin yayi maganar ayyukan mutum kamar mutumin yana tafiya akan hanya. AT: "Kada ku aikata abin da mugayen mutane suke yi kuma kada ku shiga ayyukan mutanen da suke aikata mugunta"
Wataƙila suna iya yin barci a zahiri, amma marubucin ya yi amfani da ƙari magana don bayyana yadda suke son aikata mugunta.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan magana ne wanda marubuci yake magana game da waɗannan mutane koyaushe suna aikata mugunta da tashin hankali kamar suna ci suna sha kamar wanda zai sha gurasar da ruwan inabin. AT: "mugunta kamar gurasar da suke ci ne kuma tashin hankali kamar ruwan inabin da suke sha" ko 2) waɗannan mutanen suna samun abincinsu da abin shan su ta hanyar aikata mugunta da tashin hankali. AT: "suna cin gurasar da suke samu ta hanyar aikata mugunta kuma suna shan ruwan inabin da suka samu ta hanyar tashin hankali"
Marubucin ya kwatanta hanyar mutanen kirki da fitowar rana, ma'ana suna cikin aminci saboda suna da haske don ganin inda suke tafiya. AT: "mutanen kirki suna tafiya akan hanyarsu lafiya domin rana ta wayewa a kanta kuma tana haskakawa"
Marubucin ya kwatanta hanyar mugaye da duhu, ma'ana koyaushe suna cikin haɗari saboda basu da hasken ganin inda suke tafiya. AT: "Miyagu suna tafiya cikin haɗari a kan hanyar su saboda ba su da hasken da za su iya gani"
Anan kalmar "kunne" tana wakiltar mutumin da yake sauraro. Marubucin yayi maganar saurarawa da kyau ga wani kamar yana jingina ne don kunne ya kusanci wanda yake magana. Ana iya fassara kalmar "maganganun" azaman aiki. AT: "saurara da kyau ga abubuwan da nake fada"
Marubucin yayi maganar koyaushe tunanin wani abu kamar yana ajiye shi inda mutum zai iya ganin sa. AT: "Kada ku daina tunanin su"
Marubucin yayi maganar kalmominsa suna kiyaye rayuwar mutum kamar suna rayuwar mutumin. AT: "kalmomina suna ba da rai" ko "abubuwan da na faɗi suna ba da rai"
Anan kalmar "zuciya" tana wakiltar tunanin mutum da tunanin sa. AT: "Ka kiyaye zuciyarka kuma ka kiyaye tunaninka"
Kalmar "ta" tana nufin zuciya, wanda ke wakiltar ma'anar hankali da tunani. Marubucin yayi maganar rayuwar mutum kamar wani marmaro ne mai gudana daga zuciya. AT: "daga tunaninku ne duk abin da kuka faɗa kuma kuka aikata" ko "tunaninku yake ƙayyade yanayin rayuwar ku"
Marubucin yayi maganar karya ko yaudara kamar wacce take karkace kuma mutum baya amfani da irin wannan lafazin kamar yana cire shi nesa da kansa. AT: "Kada ku yi ƙarya kuma kada ku yi magana da yaudara"
Anan kalmar "idanu" tana wakiltar mutumin da yake kallo. Marubucin yayi magana akan mutum mai jajircewa wajan yin abu dai-dai kamar dai wannan mutumin yana ci gaba da sa ido ba tare da ya juya kansa ya kalli wata hanya ba. AT: "Kullum ka kalli gabanka kai tsaye ka gyara idanunka gabanka"
Anan kalmar "ƙafa" tana wakiltar mutumin da yake tafiya. Marubucin yayi magana akan ayyukan mutum kamar yana tafiya akan hanya, kuma yana tsara waɗancan ayyukan a hankali kamar yana yin wannan matakin ne. AT: "Yi hanya madaidaiciya don tafiya a kan" ko "Shirya abin da kuke son yi da kyau"
Marubucin yayi magana akan ayyukan mutum kamar mutum yana tafiya akan hanya kuma waɗancan ayyukan suna cin nasara kamar dai hanyar aminci ce kuma amintacciya. AT: "to duk abin da kuka yi zai zama daidai"
Hanyoyin "dama" da "hagu" suna haifar da haɗuwa, ma'ana cewa mutumin ba zai bar matakin matakin ba ta kowace hanya. AT: "Yi tafiya kai tsaye gaba kuma kada ka bar madaidaiciyar hanyar"
1Ɗana, ka maida hankali ga hikimata; ka kasa kunne ga fahimtata,2domin ka koyi sanin abin da ke dai-dai leɓunanka zasu tsare ilimi.3Domin leɓunan mace mazinaciya suna ɗiga da zuma kuma bakinta yafi mai tabshi,4amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar shuwaka, tana yanka kamar takobi mai kaifi.5Kafafunta suna gangarawa zuwa mutuwa sawunta yana tafiya har Lahira.6Ba ta tunani game da hanyar rayuwa. Sawayenta sun ratse daga hanya; ba ta san inda zata ba.7Yanzu dai, 'ya'yana maza, ku saurare ni; kada ku juya baya ga barin jin maganganun bakina.8Bari tafarkinku ya yi nesa da ita kuma kada ku je kusa da ƙofar gidanta.9Da haka ba zaka bada girmamawarka ga waɗansu ba ko shekarun rayuwarka ga mugun mutum ba;10bãƙi ba zasu cinye dukiyarka ba; abin da ka yi wahala ka samu ba zai tafi gidan bãƙi ba.11A ƙarshen rayuwarka zaka yi nishi sa'ad da jikinka zai lalace.12Zaka ce, "Ai kuwa na ƙi jinin umarni kuma zuciyata ta wofintar da kwaɓa!13Na ƙi yin biyayya da malamaina na kuma ƙi in saurari umarnansu.14Na kusa lalacewa gaba ɗaya a tsakiyar taro, a cikin tattaruwar mutane."15Ka sha ruwa a cikin randar da ke taka ka kuma sha ruwa mai gudana daga taka rijiyar.16Ko ya kamata maɓuɓɓugarka ta yi ambaliya ko'ina kuma rafuffukan ruwanka su kwarara a bainar jama'a?17Bari su zama naka kaɗai ba kuma domin bãƙin da ke tare da kai ba.18Bari maɓuɓɓugarka ta zama da albarka kuma bari ka yi farinciki da matar kuruciyarka,19gama ita ƙaunatacciyar barewa ce kuma kurciya cike da alheri. Bari nonnanta su ƙosar da kai koyaushe; bari ka bugu da ƙaunarta kowanne lokaci.20Don mene ne, ɗana, zaka shaƙu da mazinaciya; donme za ka rungumi nonnan karuwar mace?21Yahweh yana ganin dukkan abin da mutum ke yi yana kuma lura da dukkan tafarkun da ya ɗauka.22Zunuban mugun mutum zasu cafke shi; igiyoyin zunubinsa zasu riƙe shi kam-kam.23Zai mutu domin ya rasa umarni; an ɓadda shi ta wurin wautarsa mai girma.
Marubucin yayi magana kamar uba yana koyarda yaransa.
Anan kalmar "lebe" tana wakiltar mutumin da yayi magana. Marubucin yayi maganar mutum yayi taka tsantsan kawai ya faɗi gaskiya kamar idan leben mutum suna kare ilimi. AT: "za ku yi magana ne kawai da abin da yake gaskiya"
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) kalmar "lebe" tana wakiltar kalmomin mazinaciya kuma marubucin ya tana magana game da jan hankalin kalmomin nata kamar dai leɓun nata sun zubo da zuma. AT: "kalmomin mazinaciya suna da daɗi, kamar ana ɗiɗowa da zuma" ko 2) marubucin ya yi magana game da sha'awar sumbatar mazinaciyar kamar leɓɓanta sun zubo da zuma. AT: "sumbancin mazinaciya mai daɗi ne, kamar dai leɓanta sun zubo da zuma"
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) kalmar “baki” tana wakiltar maganar mazinaciya kuma marubucin ya tana maganar lallashin maganganunta kamar bakinta ya fiye mai laushi. AT: "maganarta tana da shawo da mai santsi fiye da man zaitun" ko 2) marubucin ya tana maganar jin daɗin sumbatar mazinaciyar kamar bakinta ya mai santsi fiye mai laushi. AT: "sumbanta sun mai santsi fiye mai laushi"
Marubucin ya yi magana game da cutarwar da ke zuwa daga haɗuwa da mazinaciya kamar tana ɗanɗana ɗaci kamar ɗaci. AT: "amma a ƙarshe, ta zama kamar itaciyar ɗanɗano mai ɗaci kuma za ta cutar da ku"
tsiro mai ɗanɗano
Anan "ƙafafunta" suna wakiltar mazinaciya yayin da take tafiya. Marubucin yayi maganar halayenta kamar tana tafiya akan hanya. AT: "Tana tafiya a kan hanyar da zata kai ga mutuwa" ko "salon rayuwarta yana kaiwa ga mutuwa"
Marubucin yayi maganar halaye wadanda suke baiwa mutum tsawon rai kamar wata hanya ce wacce take kaiwa ga rayuwa. AT: "Ba ta tunanin yin tafiya a kan hanyar da take kaiwa zuwa rai" ko "Ba ta damu da halin da zai kai ga rai ba"
Anan malamin ya sauya daga gargaɗi game da mazinaciya zuwa bada shawara.
Anan kalmar “hanya” tana wakiltar halin mutum da yanayinsa na yau da kullun. AT: "Kiyaye kanka nesa da ita" ko "Nisantar ta"
Anan "ƙofar gidanta" yana wakiltar gidan da kansa. Zai iya zama mafi dacewa a yi amfani da kalmar "tafi" maimakon "zo" tunda na biyun yana iya nuna cewa mai maganar tana ƙofar gidanta. AT: "kada ku kusanci ƙofar gidanta" ko "ko kusa da gidanta"
"Idan kayi haka." Wannan jumlar tana nufin abin da ya faɗa a cikin ayoyin da suka gabata.
Mai yiwuwa ma'anonin kalmar "girmamawa" su ne 1) yana nufin mutuncin mutum. AT: "Ba za ku rasa kyawawan halayenku a tsakanin sauran mutane ba" ko 2) tana nufin dukiyar mutum da kuma dukiyarsa. AT: "Ba zaku ba da dukiyar ku ga wasu mutane ba" ko 3) yana nufin ƙarfi kuma yana wakiltar shekarun farkon rayuwar mutum. AT: "Ba za ku ba da mafi kyawun lokutan rayuwar ku ga wasu mutane ba"
Marubucin yayi magana game da mutum yana mutuwa da wuri, wataƙila ta hanyar kisan kai, kamar shekarun shekarun rayuwarsa abubuwa ne da ya ba wani mutum. AT: "ko kuma ba da ranka ga mutumin azzalumi" ko "ko kuma sa azzalumi ya kashe ka tun kana saurayi"
Anan kalmar "gida" tana wakiltar dangin mutum. AT: "abubuwan da kuka samo ba zai ƙare da mallakar dangin baƙi ba"
Kalmomin “nama” da “jiki” ma’anarsu abu ɗaya ne kuma suna wakiltar mutum duka. AT: "jikinku ya lalace" ko "ku ɓata"
Waɗannan jumlolin guda biyu suna bayyana ra'ayi ɗaya kuma suna ƙarfafa yadda wannan mutumin ba ya son abin da malamin ya faɗa.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna nufin jama'ar mutumin da suka taru ko dai 1) don sujada ga Allah ko 2) su yanke masa hukunci game da laifin da ya yi.
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya dai-dai. Marubucin yayi maganar mutum yana kwanciya da matarsa kawai kamar yana shan ruwa kawai daga rijiyar kansa ko rijiyar.
A nan kalmomin "maɓuɓɓugai" da "rafuka na ruwa" wataƙila kalmomi ne don magudanar haihuwar namiji. Mai iya yiwuwa ga waɗannan jimlolin jimla su ne 1) kwanciya da matan da ba matar mutum ba ana maganarsu kamar tana barin ruwan mutum ya gudana a cikin titunan jama'a ko 2) ana maganar haihuwa da matan da ba matar mutum ba kamar yana barin mutum ya kwarara a titunan jama'a.
Marubucin yayi magana game da matar ɗa kamar dai ita ce maɓuɓɓugar ruwa. A nan kalmar "mai albarka" tana nufin ma'anar farin cikin da namiji yake da shi a cikin matarsa. AT: "Ko da yaushe za ku sami farin ciki tare da matar ku"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "matar da ka aura tun kana saurayi" ko 2) "matarka matashiya."
Ana magana da tsananin tashin hankali da farin ciki daga soyayyar matar mutum kamar wanda ya sha maye daga wannan soyayyar. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "bari ƙaunarta ta mallake ku kamar yadda giya ke sarrafa wani maye"
Marubucin ya yi waɗannan tambayoyin don jaddada cewa ɗansa dole ne ya ƙi yin waɗannan abubuwa. AT: "ɗana, kada mazinaci ya birge ka! Kada ka rungumi ƙirjin mace mai lalata!"
Marubucin yayi magana game da mugu wanda ya kasa kauce wa sakamakon laifinsa kamar dai waɗannan laifofin mutane ne da ke kama mai mugunta. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Laifukan mugaye za su kama shi" ko "Mugu zai iya guje wa sakamakon laifinsa"
Marubucin yayi magana game da mugu wanda ya kasa kauce wa sakamakon zunubinsa kamar dai wannan zunubi tarko ne da aka yi da igiya wanda aka kama mutumin. AT: "saboda zunubinsa, zai zama kamar dabba da aka kama a cikin tarko"
1Ɗana, idan ka ɗauki lamunin bashin da makwabcinka ya ci, idan ka yi alƙawari domin bashin wani da baka san shi ba,2to ka kafa wa kanka tarko ta wurin alƙawarin da ka yi an kuma kama ka da maganganun bakinka.3Sa'ad da an kama ka ta wurin maganganunka, ka yi wannan ka ceci kanka, tunda ka faɗa hannun makwabcinka; ka tafi ka ƙasƙantar da kanka ka faɗi wa makwabcinka abin da ya faru.4Kada ka ba idonka barci ko gyangyaɗi.5Ka tsirar da ranka kamar barewa daga hannun mafarauci, kamar tsuntsuwa daga hannun maharbi.6Dubi tururuwa, kai ragon mutum, ka yi la'akari da hanyoyinta, ka yi hikima.7Ba ta da hafsa, shugaba, ko mai mulki,8duk da haka tana shirya abincinta da kaka kuma a lokacin girbi ta kan tanada abin da za ta ci.9Har yaushe zaka yi ta barci, kai ragon mutum? Yaushe zaka tashi daga barcinka?10"Ɗan barci kaɗan, ɗan gyangyaɗi kaɗan, ɗan naɗe hannuwa don a huta" -11sai talaucinka ya zo maka kamar ɗanfashi buƙatunka kuma kamar jarumi mai makami.12Wofin taliki - mugun mutum - yana rayuwa ne ta wuri karkata maganarsa,13yana ƙifci da idanunsa, yana nuni da tafin ƙafarsa yana nuni da yatsunsa.14Yana shirya mugunta da ruɗi a ransa; kullum yana haddasa rashin jituwa,15Saboda haka masifarsa zata auko masa farat ɗaya; ba zato za a karairaye shi ba damar warkewa.16Akwai abu shida da Yahweh yaƙi, har ma bakwai da ya ke ƙyamar su.17Idanun taliki mai girman kai, harshe mai faɗar ƙarairayi, hannaye masu zub da jinin mutane marasa laifi,18zuciya mai ƙago mugayen shirye-shirye, ƙafafu masu saurin gudu su je su yi mugunta,19mashaidi mai furta ƙarairayi yana shuka husuma a tsakanin 'yan'uwa.20Ɗana, ka yi biyayya da umarnin mahaifinka kada kuma ka watsar da koyarwar mahaifiyarka.21Kullum ka ajiye su a zuciyarka; ka ɗaura su zagaye da wuyanka22Sa'ad da kake tafiya zasu bishe ka; sa'ad da kake barci, zasu tsare ka; sa'ad da ka farka, zasu koyar da kai.23Gama umarnai fitila ce, koyarwa kuma haske ne; tsautawa da ke zuwa daga koyarwa hanyoyin rai ne.24Zata kiyaye ka daga muguwar mace, daga lallausar maganganun muguwar mace.25Kada ka yi sha'awar kyanta a zuciyarka kuma kada ka bari ta cafke ka da girar idanunta.26Kwana da karuwa tsadarsa kamar na kuɗin ɗan curin gurasa ne, amma matar wani zaka biya diyya da ranka.27Mutum zai iya ɗaukar wuta a ƙirjinsa har da ba zata ƙona masa kayan jikinsa ba?28Ashe mutum zai iya tafiya bisa garwashin wuta mai zafi ba tare da ya ƙona ƙafafunsa ba?29To haka ya ke da mutumin da ya kwana da matar maƙwabcinsa; wanda ya kwana da ita ba zai kuɓuta daga hukunci ba.30Mutane ba zasu rena ɓarawo ba idan ya yi sata domin biyan buƙatar yunwar cikinsa.31Amma idan an kama shi, zai biya riɓi bakwai na abin da ya sata; dole ya sadaukar da dukkan abubuwa masu daraja da ke cikin gidansa.32Wanda ya yi zina ba shi da hankali; wanda ya yi ta yana hallakar da kansa.33Raunuka da kunya su ne sakaiyarsa kuma ƙasƙancinsa ba za a iya sharesu ba.34Gama kishi yakan sa mutum ya husata; ba zai nuna jinƙai ba; sa'ad da zai ɗauki fansarsa.35Ba zai karɓi wata fansa ba, kuma ba za iya ba da toshiya ba ko da an bashi kyautai da yawa.
Abinda aka ambata anan shine alƙawarin ka da yanayin sun tilasta maka ka tara kuɗin ka. AT: "ya zama dole ya adana wasu daga cikin ku"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) maƙwabcinka na iya zuwa wurinka don neman rance ko 2) maƙwabcinka yana son karɓar rance daga wani, amma ka yi alkawarin za ka biya mai rance idan maƙwabcinka ba zai iya ba.
Wannan karin magana ne yana cewa zaku kama kanku. AT: "kun sanya tarko wanda aka kama kanku da shi"
Wannan karin magana ne ta amfani da kalmar "hannu" don ma'anar "cutarwa." AT: "maƙwabcinku na iya kawo muku cutarwa idan yana so" ko "maƙwabcinku yana da iko a kanku" (Duba: fig_idiom)
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma ana maimaita su don ƙarfafa yadda mahimmancin ba kasala ba. Hakanan an bayyana shi mara kyau don ƙarin ƙarfafawa. AT: "Ku kasance a farke, kuma ku yi abin da za ku iya"
"Ku tsere daga maƙwabcinku kamar barewa da ke gudu daga mafarauci"
"kuma ku tsere kamar tsuntsu wanda yake tashi daga wurin mai farauta"
"Yi nazari ... kuyi tunani game da" ko "ku kiyaye"
Wadannan jimlolin guda biyu ma'anarsu abu daya kuma ana maimaita su don nuna yadda alhakin tururuwa yake.
Malamin yayi amfani da waɗannan tambayoyin don tsawata wa rago saboda yawan bacci. AT: "Ka farka, kai malalaci! Fita daga gadonka!"
Hanya farat ta rago ta zama matalauciya kamar ba zato ba tsammani ɗan fashi yakan zo ya saci abubuwa. AT: "ba zato ba tsammani za ku talauce, kamar dai yadda ɗan fashi ya zo ya saci duk abin da kuke da shi"
Kwatsam yadda malalaci yake bukatar abubuwa kamar hanyar kwatsam da sojoji masu ɗauke da makamai suka karɓi abu daga hannun mutum. Ana iya bayyana wannan azaman cikakkiyar jimla. AT: "kuma bukatunku zasu zo muku kamar sojan da ke dauke da makamai" ko "kuma za ku zama mabukata kamar dai sojan da yake dauke da makami ya saci duk abubuwanku"
Waɗannan kalmomin guda biyu suna da ma'ana ɗaya kuma suna ƙarfafa yadda muguntar wannan mutumin take. AT: "Mutumin da bashi da daraja" "mugu ne"
Duk waɗannan jimlolin guda uku suna bayyana hanyar da mugu yake magana cikin ɓoye don yaudarar wasu mutane.
"Yana shirya mugunta" ko "Yana shirya don aikata mugunta"
"koyaushe yana haifar da fitina" ko "koyaushe yana neman rikici kuma yana haɓaka shi"
Wannan yana nuna cewa bala'in yana bin sa kamar mutum ko dabba, kuma hakan zata same shi ba da daɗewa ba. AT: "masifarsa za ta kama shi"
Duk wannan ayar jaddada cewa Allah yana ƙin abubuwa da yawa ba ɗaya kawai ba. AT: "abubuwa shida da Yahwah ya ƙi; abubuwa bakwai da"
"wannan yana sa shi ya ji ƙyama" ko "wannan yana sa ku zama abin ƙyama a cewarsa"
Wannan shine jerin abubuwan da Yahweh ya ƙi waɗanda aka gabatar a cikin Misalai 6:16.
Duk waɗannan sassan jiki suna nufin mutum duka. Kuna iya fassara kowane ɗayan waɗannan tare da "mutane."
Waɗannan jimloli guda biyu a bangare guda ma'anarsu daya. A gefe guda kuma, maimaitawar girmamawa akan "uba" da "mahaifiya" a bayyane ya haɗa da mata cikin ɗaukacin tsarin koyarwar koyarwa.
Wannan karin magana yana amfani da mummunan "watsi" don ma'anar tabbatacce "yi biyayya." AT: "ku yi biyayya ga koyarwar mahaifiyarku"
Ana amfani da waɗannan jimlolin guda uku tare don jaddada cewa darussan suna da amfani koyaushe.
Maimaita waɗannan jimlolin shine don nuna cewa darussan suna da mahimmanci ga kowane irin abu. Hakanan yana magana akan waɗancan darussan kamar suna mutane.
Anan kalmar "shi" tana nufin darussan da uba da uwa suke koyarwa a cikin Misalai 6:20. AT: "Yana cece ka daga" ko "Yana kiyaye ka daga"
Waɗannan kalmomin guda biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Duba yadda kuka fassara kalmar "mazinaciya" a cikin Misalai 5: 3.
Wannan yana magana ne game da tsadar kuɗi, ba tsadar ruhaniya ko halin ɗabi'a ba. AT: "kaɗan"
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) matar wani mutum ta halakar da rayuwar ku saboda a koda yaushe tana son karin ko 2) mijin wata matar zai farautar ku ya kashe ku.
Wannan aikin zai kasance da haɗari sosai kuma zai haifar da cutarwa. Amsar a bayyane ga tambayar ita ce "a'a." AT: "Duk mutumin da ya ɗauki wuta a kirji zai ƙona tufafinsa."
Yin tafiya a kan garwashin wuta zai ƙone ƙafafun mutum, don haka amsar da ake bayarwa ita ce "a'a." AT: "Duk mutumin da ke tafiya a kan garwashin wuta zai sami ƙafafun ƙafafunsa."
"kada ku dauki barawo da raini" ko "kada kuyi tunanin barawo mugu ne"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "idan wani ya kama shi"
"Mutumin"
Wannan karin magana yana amfani da kalmar "wulakanci" don nuni ga yadda yake jin kunya. ATr: "ƙwaƙwalwar ajikin abin kunyar sa"
fushi sosai
"Shi" makwabcin ne wanda matarsa ta yi zina da wani mutum. AT: "ba zai iyakance azabar da zai jawo muku ba" ko "zai cutar da ku gwargwadon iko"
"a lokacin da yake ɗaukar fansa" ko "lokacin da lokacin ya isa lokacin da zai iya ɗaukar fansarsa"
1Ɗana, ka adana maganganuna ka kuma ajiye dokokina a cikinka.2Ka kiyaye dokokina ka rayu ka kiyaye koyarwata kamar ƙwayar idonka.3Ka ɗaura su a yatsun hannunka; ka rubata su a allon zuciyarka.4Ka ce da hikima, "Ke 'yar'uwata ce," kuma ka kira fahimi danginka,5domin ka kiyaye kanka daga mace mazinaciya, daga karuwar mace da maganganunta masu zaƙi.6Ta tagar ɗakina ina leƙe ta labule.7Sai na duba wasu dolayen mutane, sai na lura cikin samari wani matashi wanda bashi da hankali.8Saurayin ya gangara wani titi kusa da saƙonta, ya nufi wajen gidanta.9Da maraice, wajen yammaci a ranar nan, a lokacin dare da duhu.10A can wata mata ta gamu da shi, ta yi shigar karuwa, mai zuciyar wayo.11Tana magana da ƙarfi da iskanci; ƙafafunta basu zauna a gida ba.12Yanzu tana titi, an jima tana kasuwa, a kowanne saƙo takan jira ta yi kwanto.13Sai ta kama shi kuma ta sumbace shi, da fuska mai yaudara ta ce masa,14"Na yi baikona da salama yau, na cika wa'adina,15shi yasa na fito in sadu da kai, da himma in biɗi fuskarka, na kuma same ka.16Na baza shimfiɗu a kan gadona, lilin masu launuka daga Masar.17Na fesawa gadona miyor da alos da kirfa.18Ka zo, mu sha ƙaunarmu mu ƙoshi har safiya; bari mu ji daɗi sosai cikin ayyukan ƙauna.19Gama mijina ba ya cikin gidansa; ya yi tafiya mai nisa.20Ya ɗauki jakkar kuɗi tare da shi; zai dawo in wata ya raba."21Da maganganu masu yawa ta sa shi ya ratso; da daɗin bakinta tasa shi ya karkace.22Nan da nan ya bi ta kamar san da ake kai shi wurin yanka, kamar barewar da aka kama a tarko,23har sai da kibiya ta tsire shi har zuwa hantarsa. Yana kama da tsuntsun da ya ke gaggautawa ya faɗa tarko. Bai san cewa zai sadaukar da ransa ba ne.24Yanzu dai, ɗana, ka kasa kunne gare ni; ka maida hankali ga maganganun bakina.25Kada zuciyarka ta kauce zuwa tafarkunta; kada ka bari a ɓadda kai zuwa tafarkunta.26Ta sa mutane da yawa sun faɗi sokakku; kasassunta da suka mutu na da yawan gaske.27Gidanta yana kan tafarkun Lahira; suna gangarawa ne zuwa ɗakunan kwanan mutuwa mai baƙin duhu.
Anan kiyaye wakiltar yin biyayya ne. AT: "ku bi maganata"
Anan ana maganar umarnin Allah kamar abubuwa ne da wani zai iya sanyawa cikin ma'aji. AT: "haddace dokokina"
Anan kiyayewa yana wakiltar biyayya. AT: "ku bi umarnina"
Tambarin ido shine ɗalibin cikin ido, wanda mutane ke kiyayewa cikin ɗabi'a idan abu ya tashi akan fuskarsu. Anan "kwayar idanun" tana wakiltar duk abin da mutum ya daraja da kariya sosai. AT: "a matsayin mallakarku mafi daraja"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) cewa marubucin ya so ɗansa ya sassaka wasu umarni daga Allah a kan zobe kuma ya sanya, ko kuma 2) marubucin yana son ɗansa ya riƙa tuna dokokin Allah koyaushe, kamar dai koyaushe yana sanye da wani zobe.
Anan ana magana da hikima kamar mutum ne. AT: "Darajar hikima kamar yadda za ku ƙaunaci 'yar'uwar ku"
Anan ana maganar ingancin fahimta kamar dangi ne. AT: "ku bi da hankali kamar yadda za ku yi wa danginku"
murfi a kan taga da aka yi da siririn sassan itace waɗanda ke gicciye juna ta hanyar laulayi wanda ya samar da buɗaɗɗen murabba'i mai fasali a tsarin
Anan "ta" tana nufin duk wata baƙon mace, kamar yadda ake magana a cikin Misalai 7: 4. Tana tsaye a wani kusurwa, tana jiran wani mutumin da ya dace ya wuce. AT: "kusurwar da baƙon mace ke tsaye"
Anan “zuciya” tana wakiltar niyya ko shiri. AT: "ta shirya yaudarar wani"
"Ta yi magana da ƙarfi kuma ta aikata yadda ta so"
"Ta" na nufin matar da aka gabatar a cikin Misalai 7:10.
Anan “alwashi” yana wakiltar abin da mutumin ya yi alkawarin miƙa wa Allah. AT: "Na yi sadaukarwa da na yi wa Allah alƙawari"
"warwatse akan gadona"
Anan ana maganar jin daɗin soyayyar soyayya kamar wani abu mai kyau ne a sha.AT: "bari muyi soyayya da junanmu yadda muke so"
"baya gida"
"ta lallashe shi ya aikata mugunta" AT: "ta shawo kansa ya yi zunubi tare da ita"
Wannan yana nuna cewa saurayin ya ɗauki ɗan lokaci kaɗan don yin tunani game da abin da ya kamata ya yi. AT: "Da sauri ya yanke shawarar bin ta"
Halin rashin hankali da saurayin ke bi wa mazinaciyar idan aka kwatanta shi da yadda dabbobi basu san hatsarin da suke ciki ba.
Wannan kalmonin yana nuna cewa mafarauci ya kama barewa don harba shi da kibiyoyi. AT: "har sai lokacin da maharbi ya harbe shi a mafi mahimmancin sashi"
Wannan shi ne sanya hankalin thea thean mai magana akan ƙarshen wannan darasin.
Anan "hanyoyi" na nufin hanyoyin da mutum ya zaɓi ya bi. Yana wakiltar halayen mutum, abubuwan da ya yanke shawarar aikatawa a rayuwa. AT: "Ka sa zuciyarka ta yi nesa da hanyoyin matar mazinaciya" ko "Kada zuciyarka ta so yin abubuwan da matar da ke yin zina ke yi"
Samun mashi ko kibiya yana wakiltar kashewa. AT: "Ta yi sanadiyyar mutuwar mutane da yawa"
Anan "hanyoyi" suna wakiltar nau'in ɗabi'a da wawaye ke shiga ciki. Lahira shi ne sunan duniyar matattu.
1Ba hikima na ƙwala kira ba? Ba fahimta na ɗaga muryarta ba?2A kan tsaunukan dutse a gefen hanya, a mararrabar hanya, Hikima ta ɗauki matsayinta.3A gaban ƙofofi, inda ake shiga cikin birni, a ƙofofin shiga cikin birni, tana ƙwala kira.4A gare ku, ku mutane, nake kira; muryata domin 'yan adam.5Ku marasa azanci, ku koyi hikima; ku kuma da kuke wauta, dole ku sami zuciya mai fahimta.6Ku saurara, domin zan yi magana a kan mafifitan al'amura, kuma sa'ad da bakina ya buɗe zan faɗi madaidaitan al'amura.7Gama bakina yana faɗin gaskiya, mugunta kuma abin ƙyama ce ga leɓunana.8Dukkan maganganun bakina na adalci ne; a cikinsu ba murɗiya ko karkatarwa.9Dukkansu miƙaƙƙu ne ga mutum mai fahimta; maganganuna dai-dai ne ga wanda ya sami ilimi.10Ka sami koyarwata maimakon azurfa; ka sami ilimi maimakon zinariya tsantsa.11Domin hikima tafi duwatsu masu ƙawa, ba wata dukiya da ta kai ta daraja.12Ni Hikima ina zaune da Hankali; Na kuma mallaki ilimi da sansancewa.13Tsoron Yahweh shi ne ƙin jinin mugunta. Na ƙi girman kai da alfarma, da muguwar hanya, da gamtsin baki, ina ƙinsu.14Ina da shawara mai kyau; da sahihiyar hikima; ni mai gani ce; ƙarfi nawa ne.15Ta wuri na sarakai suke sarauta, kuma masu mulki suke tsara dokoki masu adalci.16Ta wurina mahukunta ke mulki, hakimai, da dukkan masu mulki da adalci.17Ina ƙaunar masu ƙauna ta, kuma dukkan masu biɗata da himma, suna samu na.18A guna akwai wadata da daraja, dawwamammar dukiya da adalci.19'Ya'yana sun fi zinariya, koma sahihiyar zinariya ce; amfanina ya fi azurfa da aka tãce.20Ina tafiya a hanyar adalci, cikin tsakiyar tafarkun adalci.21Sakamakon wannan, nakan sa masu ƙaunata su gaji wadata; nakan cika rumbunansu taf.22"Yahweh ya hallice ni tun farko, ayyukansa na farko a lokacin.23Tun zamanun dãdã da suka wuce aka yini - daga farko, tun farkon duniya.24Kafin tekuna su kasance, aka haife ni - kafin maɓuɓɓugai masu yawan ruwa.25Kafin kafawar duwatsu kuma kafin tuddai, aka haife ni.26An haife ni kafin Yahweh ya hallici duniya ko jeji, kafin ma ƙura ta farko a duniya.27Ina nan sa'ad da ya kafa sammai, sa'ad da ya zana alamar zobe a sararin zurfi.28Ina nan sa'ad da ya kafa giza-gizai a sama da sa'ad da maɓuɓɓugai cikin zurfi suka kafu.29Ina nan sa'ad da ya sa wa teku iyaka, domin kada ruwaye su yi ambaliya su ƙetare umarninsa, da sa'ad da aka dasa iyakar harsashin busasshiyar ƙasa.30Ina gefensa, kamar gwanin masassaƙi, ni abin farincikinsa ne rana bayan rana, ina farinciki a gabansa koyaushe.31Ina ta murna da dukkan duniyarsa, kuma farincikina game da 'yan adam ne.32Yanzu dai, 'ya'yana, ku kasa kunne gare ni, domin waɗanda suka kiyaye tafarkuna za a albarkace su.33Ku kasa kunne ga koyarwata ku zama da hikima; kada ku ƙi ta.34Wanda ya saurareni za a albarka ce shi. Zai yi ta tsaro a ƙofofina kowacce rana, yana ta jira a dogaran ƙofofina.35Gama duk wanda ya same ni, ya sami rai, zai kuma sami tagomashin Yahweh.36Amma wanda ya kãsa, yana cutar ransa ne; dukkan masu ƙina mutawa suke ƙauna."
A cikin sura ta 8 an yi maganar hikima a matsayin matar da ke koya wa mutane yadda za su zama masu hikima.
Ana amfani da wannan tambayar don tunatar da masu karatu wani abu da ya kamata su sani. AT: "Hikima tana kira"
Anan "Fahimta" na nufin dai-dai da "Hikima."
Hikima tana magana da mutane a cikin ayoyi 4-36.
Anan "murya" tana wakiltar kalmomin da ake faɗa. AT: "maganata tana ga ɗan mutane"
"dole ne ku fara fahimtar abubuwa da hankalinku"
A nan “leɓɓa” na wakiltar bakin mutum, da abin da yake magana da shi. AT: "lokacin da na buɗe bakina don yin magana"
A nan “baki” yana wakiltar mutumin da yake magana. AT: "Na yi magana"
A nan “leɓɓa” na wakiltar mutumin da yake magana. AT: "mugunta abin ƙyama ne a gare ni" ko "faɗin mugayen abubuwa zai zama abin ƙyama a gare ni"
“Bakin” yana wakiltar mutumin da yake magana. AT: "Abubuwan da nake koyarwa"
Wannan yana iya nufin cewa waɗanda suka sami ilimi za su iya fahimtar cewa kalmomin mai magana a tsaye suke. Anan "kalmomi" suna wakiltar saƙo ko koyarwa. AT: "waɗanda suka san abin da ke daidai da abin da ba daidai ba sun ɗauki abin da na koyar dai-dai ne"
"Ya kamata ka yi ƙoƙari sosai ka fahimci umarnaina fiye da neman azurfa"
Anan Hikima, wanda aka siffanta ta da mace, ba ya magana. Koyaya, yana yiwuwa a sanya Hikima mai magana a nan kuma. AT: "Gama Ni, Hikima, na fi lu'ulu'u; babu wata dukiya da ta yi daidai da ni"
An kuma wakilci Kankali a nan a matsayin mutum.
Ra'ayoyin da ba a fahimta "ilimi" da "mai hankali" ana iya bayyana su ta wasu hanyoyi. AT: "Ni mai ilimi ne kuma mai hankali" ko "Na san abubuwa da yawa, kuma ina taka tsantsan"
"shawarwari masu hikima"
Anan ana magana da Hikima kamar tana da hankali. AT: "Ina da hankali"
"Ina da wadata da girma"
Wannan ya bayyana abin da ake nufi da "wadata da girma." Ana iya bayyana wannan tare da bayanin haɗin "saboda haka." AT: "saboda haka, zan ba da wadataccen dukiya da adalci ga waɗanda suka same ni"
abin da hikima ke haifarwa ko yake haifarwa
Ana magana akan rayuwa madaidaiciya kamar tafiya akan hanya madaidaiciya. AT: "Ina rayuwa dai-dai" ko "Na yi abin da ke dai-dai"
Wannan ya faɗi ƙarin abin da ake nufi da "tafarkin adalci." AT: "Ina yin abin da ya dace kawai" ko "Abin da kawai nake yi kawai"
"Ni ne farkon abubuwan da ya halitta sannan"
"Da dadewa"
AT: "daga lokacin da Allah ya halicci duniya"
"Kafin a kafa tushen duwatsun." Hakanan za'a iya sanya wannan cikin tsari mai aiki. AT: "Kafin Allah ya yi harsashin ginin duwatsu kuma ya sanya su a wuraren da suka dace"
Wannan hikima ce game da kanta.
Wannan yana nufin sanya iyaka ga yadda wani a cikin jirgi a teku zai iya ganin kewaye kansa. AT: "lokacin da ya yi alama a saman teku yadda mutum a teku zai iya gani ta kowane bangare"
Hikima ta cigaba da magana.
"lokacin da ya halicci gabar teku don tekuna." Iyakancin teku "ya raba tekuna daga busasshiyar kasa"
Ana iya sanya wannan cikin tsari mai aiki. AT: "lokacin da Allah ya sanya iyaka ga kafuwar duniya"
Wannan har yanzu hikima ce. Hikima yanzu ta ce tana kusa da Yahweh, yana nuna cewa ta kasance mataimakiyarsa a cikin halittar duniya.
"Ni ne abin da ya faranta masa rai." Kalmar "ni'ima" kalma ce wacce ba za'a iya bayyana a matsayin fi'ili ba. AT: "ya yi murna saboda ni"
Wannan shine sanya hankalin yara zuwa ƙarshen wannan darasin.
Anan "hanyoyi na" suna wakiltar halayen hikima. AT: "waɗanda suke yin abin da na koyar" ko "mutanen da suke bin misalina"
Waɗannan jimlolin guda biyu ma'anarsu ɗaya ce. An bayyana hikima da samun gida; yuwuwar ma'anonin "kallo" su ne 1) mai hankali yana jira a kofar gidan hikima da safe domin yayi mata hidima, ko kuma 2) mai hankali yana jiran gidan hikima domin ta zo ta koya masa.
Wannan har yanzu hikima ce game da kanta. (Duba: personification)
1Hikima ta gina gidanta; ta sassaƙa ginshiƙai bakwai daga duwatsu.2Ta yanka dabbobinta; ta gauraya ruwan inabinta; kuma ta shimfiɗa teburinta.3Ta aiki barorinta; tana kira daga wurare masu tsayi na birni,4"Wane ne dolo? Bari ya ratso nan!" Tana magana da wanda ba shi da hankali.5Kazo, ka ci abincina, kuma ka sha ruwan inabi da na gauraya.6Ka bar ayyukan dolonci ka rayu; ka bi tafarkin fahimta.7Duk wanda ya hori mai reni za a zage shi, kuma duk wanda ya kwaɓi mugun mutum zai sami zargi.8Kada ka tsauta wa mai renako, domin zai ƙi jininka; ka tsauta wa mutum mai hikima, zai ƙaunace ka.9Ka bada hikima ga mutum mai hikima, zai ƙara hikima sosai. Ka koya wa adalin mutum, zai ƙaru cikin koyonsa.10Tsoron Yahweh shi ne mafarin hikima, kuma sanin Mai Tsarkin nan shi ne fahimta.11Ta wurina za a tsawanta kwanakinka, shekarun rayuwa za a ƙara maka su.12Idan kana da hikima, domin kanka kake da hikimar, idan ka yi renako, zaka ɗauka kai kaɗai."13Wawuyar mace mai jahilci ce; ba a iya koyar da ita kuma bata san komai ba.14Takan zauna a bakin ƙofarta, a wurare mafi tsayi a gari.15Tana kiran masu wucewa a tituna, ga waɗanda ke tafiya a miƙe a hanyarsu.16"Bari wani dolo ya ratso wurin," takan cewa dolaye.17"Ruwan da aka sata ya fi daɗi, kuma abincin sirri yana da daɗi.18Amma bai sani ba matattu na wajen, cewa gayyatattunta suna cikin zurfin Lahira.
Waɗannan ayoyin sun fara wani misali wanda a ciki ake tunanin hikima mace ce da ke ba da kyakkyawar shawara ga mutane.
Marubucin yayi magana game da hikima kamar mace ce ta gina gidanta.
Wannan yana nufin dabbobi waɗanda za a ci naman su a abincin abincin dare da Hikimar za ta bayar. AT: "Ta kashe dabbobin don nama a abincin dare"
"ta shirya teburin ta"
Wadannan ayoyin sun fara bada sakon Hikima, wanda aka siffanta shi da mace.
Waɗannan baronin sun fita sun gayyaci mutane don su zo idi ɗin da Hikima ta shirya.
Gayyatar ana ihu daga manyan wurare domin jama'a su ji sosai.
Wadannan kalmomin guda biyu suna bayanin rukuni guda na mutane, waɗanda suke buƙatar ƙarin hikima a rayuwarsu. A nan ana ba da tambaya ga duk irin waɗannan mutane. AT: "Duk wanda bai da hankali, bari ... kowa ya rasa mai hankali"
Anan ana maganar ayyukan butulci kamar suna wani wuri da mutum zai iya barinsa. AT: "Dakatar da halayenku na butulci"
Anan ana maganar aiwatar da fahimtar hikima kamar wata hanya ce da mutum zai iya bi. AT: "yadda rayuwar mai hankali take rayuwa"
Wadannan kalmomin guda biyu suna faɗin abu ɗaya.
Waɗannan dokokin guda biyu suna wakiltar bayanan sharaɗi ne. AT: "Idan ka ba wayayye, to ... in dai za ka koyar da mutumin kirki, shi"
Duba yadda kuka fassara wannan jumlar a cikin Misalai 1: 7.
Ana iya sanya wannan cikin tsari mai aiki. AT: "Zan ninka muku kwanakinku" ko "Zan sa ku daɗe da yawa"
Hikima tana magana ne game da rayuwar shekaru kamar dai abubuwa ne na zahiri. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan kara muku shekaru na rayuwa" ko "Zan kara shekaru a rayuwarku" ko "Zan ba ku damar yin tsawon rai"
Wadannan ayoyin sun fara bayanin wauta, wanda kuma aka siffanta shi da mace.
Zai yiwu a fassara "wauta" azaman bayanin kamar "Mace marar hankali." Koyaya, idan harshe ya ba da izinin hikima ta mutum, kamar yadda ya gabata a farkon wannan babin, hakan na iya ba da izinin wauta wajan mutum. AT: "Matar Wauta"
Wadannan maganganun guda biyu suna da ma'ana iri daya, wanda aka maimaita shi don nuna irin rashin amfanin matar wauta. AT: "ba ta san komai ba kwata-kwata"
Mace marar hankali tana maganar jin daɗin ruwan da aka sata da kuma burodi na sirri don gaya wa maza cewa idan sun kwana da ita, za su ji daɗi. Ana iya bayyana wannan a fili cikin kamance. AT: "Kuna iya jin daɗina kamar yadda kuke jin daɗin ruwan da kuka sata ko burodi a ɓoye"
1Misalai na Suleman. Ɗa mai hikima yakan sa mahaifinsa ya yi farinciki amma wawan ɗa yana kawo wa mahaifiyarsa baƙinciki.2Dukiyar da aka tara da mugunta bata da amfani, amma aikata abu nagari zai tsare ka daga mutuwa.3Yahweh ba ya barin ran mutum mai adalci ya yunwata, amma yana kaɓar da kwaɗayin mugaye.4Hannun da ke da ƙiyuwa sa mutum ya talauce, amma hannun ma'aikacin mutum yakan ribato arziƙi.5Ɗa mai hikima yakan tattara amfani da kaka, amma abin kunya ne ya yi barci da kaka.6Alheran Allah suna kan mutum mai adalci, amma bakin mugu yana cike da ta'addanci.7Mutum mai adalci ya kan sa masu tunawa da shi su ji daɗi, amma sunayen mugaye zasu lalace.8Mutane masu hankali suna karɓar umarni, amma wawa mai surutai zai lalace.9Mai rayuwa cikin adalci zai yi tafiya lafiya, amma wanda ya maida tafarkunsa na maguɗi, za a kama shi.10Mai ƙibce da ido yana kawo baƙinciki, amma wawa mai surutai za a kã da shi.11Bakin mutum mai adalci maɓuɓɓugar ruwan rai ne, amma bakin mugu yana rufe da ta'addanci.12̀Ƙiyayya tana haddasa tashin hankali, amma ƙauna tana rufe dukkan laifofi.13Hikima tana kan leɓen mutum mai basira, amma bulala domin bayan wanda ba shi da hankali ne.14Mutane masu hikima suna tara ilimi, amma bakin wawa yana kawo hallakarwa kusa.15Wadatar mutum attajiri shi ne tsararren birninsa; talaucin matsiyaci shi ne hallakarsa.16Ladan mutum mai adalci yana kai ga rai; ribar mugaye takan kai su ga zunubi.17Akwai tafarkin rai domin wanda ya ke bin tarbiya, amma wanda ya ƙi kwaɓa ya bijire ne.18Kowanne ya ɓoye ƙiyayya yana da leɓunan ƙarya, wanda ya baza tsegumi wawa ne.19Sa'ad da akwai maganganu dayawa, ba a rasa zunubi, amma wanda ya ke lura da abin da ya ke faɗa mai hikima ne.20Harshen mutum mai adalci azurfa ne tsantsa; babu wani abin amfani a zuciyar mugu.21Leɓunan mutum mai adalci sukan amfani mutane da yawa, amma wawaye sukan mutu saboda da rashin hankalinsu.22Alheran Yahweh masu kyau sukan kawo wadata kuma ba ya sa cutarwa a ciki.23Mugunta abu ne da wawa ya ke jin daɗi yana kuma wasa da ita, amma hikima abu ne na jin daɗi ga mutum mai fahimi.24Abin da mugu ke jin tsoro zai auka masa, amma za a biya muraɗin adilai.25Mugaye kamar hadari mai wargajewa ne, sai kawai ka ga basu kuma, amma adalai ginshiƙi ne da ya dawwama har abada.26Kamar abu mai tsami a hakori koma kamar hayaƙi a idanu, haka ma rago ya ke ga waɗanda suka aike shi.27Tsoron Yahweh ya kan tsawonta rai, amma shekarun mugaye za a gajarta su.28Begen mutane adilai shi ne murnarsu, amma shekarun mutane mugaye zasu gajarce.29Hanyar Yahweh ta kan tsare aminci, amma hallaka ce domin mugaye.30Ba za a taɓa kawar da mutum mai adalci ba, amma mugu ba zai zauna a ƙasar ba.31Daga bakin adilin mutum 'ya'yan hikima suke fitowa, amma za a sare harshe mai gatse.32Leɓunan mutum mai adalci sun san karɓaɓɓiyar magana, amma bakin mugu, sun san abin cutarwa kawai.
Bayan gabatarwar Misalai Sura na 1-9, Sura na 10 ya fara tattara karin magana; gajerun maganganu wadanda ke koyar da hikima.
Anan “kurwa” na nufin mutum. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Yahweh yana tabbatar waɗanda suka yi abin da ke dai-dai suna da abincin da za su ci"
Hannu" yana wakiltar ƙarfi da iyawar mutum. AT: "Mutumin da ba ya son yin aiki"
"Hannu" yana wakiltar ƙarfi da iyawar mutum. AT: "mutumin da ke aiki tuƙuru"
“kan” yana wakiltar dukan mutumin. AT: "an ba su"
“bakin” yana wakiltar abin da mutum yake faɗi. AT: "kalmomin da miyagu ke faɗi"
"a hallaka" ko "a mai da kai mara amfani"
ba madaidaiciya ba; mara kyau; rashin gaskiya; mayaudari
"Karkatar da ido" na wakiltar alama ce ta sirri don zaluntar wani. AT: "Wanda ya yi sigina da ishara"
A nan “baki” yana wakiltar abin da mutane suke faɗi. AT: "Jawabin mutumin kirki"
Ana magana da maganar wannan mutum kamar tana kiyaye dabbobi masu rai ko mutane, kamar yadda maɓuɓɓugar ruwa ke yi a cikin sandararriyar ƙasa.
ƙauna tana aiki ne kamar mutum mai huce rikici tsakanin mutane maimakon tayar da hankali.
"Lebe" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "a cikin abin da mai hankali ke faɗi"
"Baki" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "kalmomin daga wawan mutum"
Wannan yana wakiltar dukiya azaman wurin aminci. AT: "lafiyarsa"
"Mutumin da ya yi biyayya da hikima zai sami tsawon rai da farin ciki"
"amma wanda bai yi biyayya da umarni mai hikima ba ba zai sami rayuwa mai kyau ba"
"Lebe" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "yana faɗar ƙarairayi"
"akwai zunubi da yawa"
"Harshe" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "Duk abin da mai adalci ya faɗi"
"Azurfa" tana wakiltar maganganu masu mahimmanci. AT: "yana da matukar daraja"
Wasa wani aiki ne da mutane suke yi don jin daɗi. AT: "Wawaye suna samun farin ciki a cikin mugunta"
Kamar yadda hadari ya zo ya kwashe komai sai mugaye za su shuɗe.
"Gidauniya" tana wakiltar tushe ko farkon wani abu da mutane zasu gina. AT: "farawa ne don wani abu wanda zai dawwama har abada"
"Mai tsami" da "hayaki" suna wakiltar abubuwan da ke cutar haƙoran mutum da idanunsa. AT: "Aika malalaci don cim ma wani aiki abin haushi ne kuma mara daɗi"
Anan “shekaru” suna wakiltar lokacin da mutum yake rayuwa. AT: "rayuwar mai mugunta"
Ana iya bayyana wannan azaman mai aiki da tabbatacce: AT: "zai kasance amintacce"
"Harshe" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "Allah zai rufe bakin mutanen da ke faɗar ƙarya"
"Lebe" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "mutumin kirki ya san yadda ake magana da yarda"
1Yahweh yana ƙin ma'aunai da ba na gaskiya ba, amma yana murna da madaidaicin nauyi.2Sa'ad da girmankai yazo, daga nan ƙasƙanci ke zuwa, amma tare da tawali'u hikima ke zuwa.3Mutanen kirki mutuncinsu ke bishe su, amma hanyoyin zamba kan hallaka maciya amana.4Dukiya ba komai ba ce a ranar hukunci, amma yin abin da ke dai-dai zai hana ka mutuwa.5Halin kirkin amintaccen mutum kansa hanyarsa ta zama a sawwaƙe, amma mugu zai faɗi saboda muguntarsu.6Halin kirki na waɗanda suke gamsar Allah kan kiyaye su lafiya, amma marasa aminci haɗamarsu ce takan zamar masu tarko.7Sa'ad da mugun mutum ya mutu, sa zuciyarsa takan lalace sa zuciyar kuma da ke kan ƙarfinsa takan ɓace.8Akan kiyaye adalin mutum daga wahala kuma takan aukawa mugu a maimako.9Marar tsoron Allah da bakinsa yakan hallaka maƙwabcinsa, amma ta wurin hikima adalai sukan sami tsaro.10Sa'ad da adalan mutane suka azurta, birni yakan yi farinciki; sa'ad da mugu ya lalace, akwai sowa ta murna.11Ta wurin kyautai masu kyau na waɗanda ke farantawa Allah rai, birni yakan ƙasaita; amma ta wurin maganganun mugaye, birni yakan ɓarke ƙasa.12Mutumin da ke rena abokinsa bashi da tunani, amma mutum mai fahimta yakan yi shiru.13Duk mai yawon yin tsegumi yakan bayyana asirai, amma amintaccen mutum yakan rufe al'amarin.14Wurin da babu jagoranci cikin hikima al'umma takan faɗi, amma nasara takan zo ta wurin tuntuɓar mashawarta masu yawa.15Duk wanda ya ɗaukar wa bãƙo lamuni lallai shi zai cutu, amma wanda ya ƙi bayarwa ta wurin ɗaukar alƙawari ya kuɓuta.16Mace cike da alheri takan sami girmamawa, amma azzalumai na haɗamar dukiya.17Mutum mai taimako yakan amfanawa kansa, amma macuci kansa ya ke cuta.18Mugun mutum yakan kwanta ya sami ladansa, amma wanda ya shuka abin da ke dai-dai yakan girbi sakamakon gaskiya.19Mutum mai gaskiya wanda ya yi abin da ke dai-dai zai rayu, amma wanda ke bin mugunta zai mutu.20Yahweh yana ƙin waɗanda tunaninsu mugaye ne, amma yana murna ga waɗanda hanyoyinsu marasa aibu ne.21Ku tabbatar da wannan - mugun mutum ba zai tafi ba tare da hukunci ba, amma zuriyar mutane masu adalci zasu zauna lafiya.22Kome kyaun mace idan bata da tunani tana kama da zoben zinariya a hancin alade.23Abin da adalan mutane suke so yakan jawo abu mai kyau, amma mugayen mutane zasu sa begensu ga hukunci kaɗai.24Akwai mai warwatsawa - zai samu ma da yawa; wani kuma yakan riƙe abin da zai bayar - yakan talauce.25Mutum mai bayarwa zai azurta kuma wanda ya ke bada ruwa ga waɗansu zai sami ruwa domin kansa.26Mutane sukan la'anta mutumin da yaƙi sayar da hatsi, amma kyaututtuka masu kyau sukan zama kambi akan mutumin daya sayar da nasa.27Mai la'akarin neman abu mai kyau yana neman tagomashi, amma mai neman mugunta zai same ta.28Masu dogara ga dukiyarsu zasu faɗi, amma kamar ganye, haka adalan mutane zasu azurta.29Wanda ya jawo wa iyalin gidansa wahala zai gãji iska wawa kuma zai zama bawan mai hikima a zuciya.30Adalin mutum zai zama kamar itacen rai, amma tashin hankali ya kan ɗauke rayuka.31Duba! Adalin mutum yana karɓar abin da ya dace da shi; balle ma mugu da mai zunubi!
"Sikeli ko Ma'auni" yana wakiltar aunawa dai-dai gwargwado a tattaunawar. AT: "Allah yana ƙin ma'aunin yaudara" ko "Allah yana ƙin sa yayin da mutane suke yaudara"
"Matsakaicin nauyi" yana wakiltar daidaito a tattaunawar. AT: "amma yana jin daɗin gaskiya" ko "amma yana farin ciki idan mutane suka faɗi gaskiya"
AT: "mutane mayaudara" ko "waɗanda suke mayaudara"
"Ranar fushi" tana wakiltar takamaiman abin da ya faru, kamar "ranar Yahweh" ko "ranar shari'a" ko "kwanaki na ƙarshe." AT: "Dukiyar mutum ba za ta amfani shi ba idan Allah ya zo ya yi hukunci"
"yana da bayyanannun kwatance"
"waɗanda suke aikata mugunta shaƙuwa ta wurin sha'awar su"
"amincewar da yake da ita a nasa karfin"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah yana nisantar da matsala daga wanda ya aikata abin da yake dai-dai"
"Baki" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "Kalmomin marasa tsoron Allah"
"Birni" yana wakiltar al'umma ko ƙungiyar mutane. AT: "ƙungiyar mutane suna samun ci gaba" ko "al'umma sun sami ci gaba"
"Rufe" yana wakiltar ɓoye abubuwa yadda ya kamata. AT: "baya fada" ko "baya magana game da lamarin"
waɗanda ke ba da shawarwari a matsayin jagora zuwa aiki; masu ba da shawara
"wanda ya ƙi bayarwa"
mutane ba tare da tausayi ko tausayi ba; azzaluman mutane
Yin "shuka" yana wakiltar yadawa don samun karin. AT: "yana shimfida abin da yake da-idai"
Don "girbe" yana wakiltar samun ko tarawa a cikin" AT: "tabbas za a sami lada"
"bi mugunta" ko "neman yin mugunta"
"Zuciya" tana wakiltar yadda mutum yake ji, halaye da kuma motsa shi. AT: "waɗanda ke da mummunan tunani"
Wannan jumlar tana amfani da mara kyau don ƙarfafa ra'ayi mai kyau. AT: "tabbas za a hukunta shi"
Kyakkyawar mace ba tare da hankali ba ana kwatanta ta da zoben zinare mara amfani da mara kyau a hancin alade.
Wannan kwatanci ne ga mutumin da ya zama mai wadata ta hanyar karimci. AT: "Wasu mutane suna ba da kyauta ga wasu kuma duk da haka sun zama mawadata"
"zai sami riba har ma"
Wannan yana bayanin mutumin da yake tara dukiyar sa maimakon taimakawa masu bukata.
"Kambi" yana wakiltar lada ne ko lambar yabo ga mutumin da yake son sayar da hatsi. AT: "ana ba da kyaututtuka masu kyau a matsayin rawanin girmamawa ga wanda ya sayar da shi" ko "mutumin da ya sayar da ita ana girmama shi da albarkatu masu yawa"
wanda yake nema da hankali da ci gaba da ƙoƙari
"Ganye" yana wakiltar girma da ci gaba. AT: "mutanen kirki za su ci gaba kamar yadda lafiyayyen ganye ke tsirowa"
"Iska" kwatanci ne na wani abu da ba za'a iya fahimtarsa ba ko kuma bashi da wata daraja ba. AT: "kada ku gaji komai"
Ana kwatanta mutumin da ke yin abin da yake daidai da bishiyar da take ba da rayuwa a matsayin itsa itsan ta. AT: "Waɗanda suka yi daidai za su kawo rayuwa ga kansu da kuma wasu"
1Duk mai son horo yana son ilimi, amma wanda ya ke ƙin yarda da gyara wawa ne.2Mutumin kirki yakan sami tagomashi a wurin Yahweh, amma yakan hukunta mutum mai shirya miyagun dabaru.3Mutum ba zai kafu ta wurin mugunta ba, amma ba za a tuge adalan mutane ba.4Mace mai tsabtar rai kambi ce ga mijinta, amma ita mai kawo kunya tana kama da cuta mai ruɓar da ƙasusuwansa.5Shirye-shiryen adali adalci ne, amma shawarar mugu yaudara ce.6Maganganun miyagun mutane su ne ayi kwanto a jira domin a sami zarafin yin kisa, amma maganganun adalai sukan cece su.7Miyagun mutane ana kaɓantar da su kuma sun tafi, amma gidan adalin mutum zai tsaya.8Akan yabi mutum bisa ga yawan hikimar da ya ke da ita, amma za a rena wanda ya ke tunanin mugunta.9Gara baka da wani muƙami mai muhimmanci - kawai kana matsayin bawa - da kayi fankamar kai wani ne amma baka da abinci.10Adalin mutum yakan kula da buƙatun dabbobinsa, amma ko tausayin mugu zalunci ne.11Wanda ya yi aiki a gonarsa zai sami isasshen abinci, amma duk mai bin ayyuka marasa ma'ana ba shi da tunani.12Mugun mutum yana marmarin abin da mugayen mutane suka sato daga wurin waɗansu, amma ribar adalai sukan zo daga gare su ne.13Maganar mugun mutum takan zamar masa tarko, amma adalin mutum yakan kuɓuta daga wahala.14Mutum zai ƙoshi da abubuwa masu kyau ta wurin amfanin maganganunsa, kamar yadda aikin hannuwansa zai sãka masa.15Hanyar wawa a ganinsa dai-dai ce, amma mutum mai hikima yakan saurari shawara.16Wawa yakan nuna fushinsa nan da nan, amma mai yin watsi da zagi yana da hikima.17Wanda ke faɗin gaskiya yana faɗin abin da ke dai-dai, amma mai shaidar zur na faɗin ƙarairayi.18Maganganun mai faɗin magana cikin garaje na kama da saran takobi, amma harshen mai hikima kan kawo warkarwa.19Leɓuna masu faɗin gaskiya sukan tabbata har abada, amma harshe mai yin ƙarya na ɗan lokaci ne.20Akwai yaudara cikin zukatan masu shirin aikata mugunta, amma murna takan zo wa masu shawarar salama.21Ba cutar da zata sami adalin mutum, amma mugayen mutane suna cike da wahaloli.22Yahweh yana ƙin leɓunan masu faɗar ƙarya, amma masu zama cikin aminci abin murnarsa ne.23Mutum mai hikima yakan ɓoye abin da ya sani, amma zuciyar wawaye takan yi shelar wauta.24Hannun mai ƙwazo zai yi mulki, amma ragayen mutane za a sa su aikin dole.25Damuwa cikin zuciyar mutum takan nawaita masa, amma maganganu masu kyau sukan sa shi ya yi murna.26Adalin mutum jagora ne ga abokinsa, amma hanyar miyagu takan bauɗar da su.27Ragayen mutane ba zasu iya gasa naman farautarsu ba, amma mutum mai ƙwazo zai sami dukiya mai tamani.28Waɗanda suka yi tafiya a hanyar da ke dai-dai sukan sami rai a cikin tafarkinsa babu mutuwa.
Ayoyi 1-15 sun bambanta hikima da wauta.
"mutumin da baya son a fada masa abin da zai yi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Babu wanda zai iya zama mai aminci da aminci ta hanyar aikata mugunta"
Kambi yana wakiltar mafi girman darajar da mutum zai samu. AT: "Mace ta gari alama ce ta girmamawa ga mijinta"
Wata cuta da ke lalata ƙasusuwa na wakiltar ɓata rayuwar mutum. AT: "Abubuwan kunya na mata suna lalata tasirin mijinta da farincikinsa"
Maganganun yaudara da mugayen mutane ke fada don cutar da wasu mutane ana maganarsu kamar maganarsu tana jiran kashe wani ba zata. AT: "Abubuwan yaudara da mugayen mutane ke furtawa suna kama da mutumin da ya jira ya kashe wani ba zato ba tsammani"
"shawara daga mutum mai adalci tana kiyaye mutane lafiya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane za su kifar da azzaluman mutane" ko "Mutane za su cire mugaye daga mulki"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane za su yaba wa waɗanda ke da hikima"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane za su ƙi wanda yake tunanin mummunan tunani koyaushe" ko kuma "mutane za su ƙi wanda ya ɗauki kyawawan abubuwa kuma ya murɗe su cikin mummunan"
"Gara mutum ya zama talaka"
"yana haifar da wahala"
"shirin banza" ko "ayyuka marasa amfani"
"Tarkon" yana wakiltar kamawa cikin tarko ko yaudara. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Miyagun abubuwa da mugu ya faɗi za su kama shi"
Kalmomin, "aikin hannuwansa" yana wakiltar aikin da aka samu ta hanyar aiki na zahiri. AT: "kamar yadda kyakkyawan aikin da yake yi ya saka masa"
Wannan jimlar tana wakiltar ra'ayin da yake da shi daga hangen nesan sa, tunanin sa ko ƙwaƙwalwar sa. AT: "a nasa ra'ayin"
Kalmomin, "matsi na takobi" yana wakiltar kalmomin mugunta waɗanda suka cutar da wani. AT: "Abin da mutum ya faɗa ba tare da tunani ba na iya cutar kamar ya soki takobi"
"Harshe" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "abin da masu hikima ke faɗi"
"Lebe" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "Mai gaskiya zai dawwama har abada"
"Harshe" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "wanda ya yi ƙarya yana ɗauka ne na ɗan lokaci"
Maganar, "A'a" ya soke ra'ayin "rashin lafiya"
"Lebe" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "Yahweh ya ƙi waɗanda suke faɗar ƙarya"
"baya fada duk abinda ya sani"
"Hannu" yana wakiltar abin da mutum yayi - ayyukansa. AT: "Mutane masu himma"
"Aikin karfi" yana bayanin abin da dole ne mutum ya yi wanda ba shi da 'yancin yin abin da yake so. AT: "zai zama bawa"
rashin jin tsoro na tsoro ko tsoro, damuwa
"Yin nauyi" yana wakiltar tunanin ɗora wa mutum nauyi sosai don haka ba zai iya motsawa ba cikin walwala. Wannan jimlar tana nufin sa mutum baƙin ciki. AT: "yana sa shi baƙin ciki"
AT: "amma idan wasu suka yi masa magana mai kyau, sai ya sake yin fara'a"
"Naman farautarsu" na nufin dabbobi da aka kama yayin da suke farauta. Kuma "soyayyen" hanya ce ta dafa abinci.
"dukiya mai daraja"
1Ɗa mai hikima yakan saurari koyarwar mahaifinsa, amma shaƙiyi ba zai saurari tsautawa ba.2Mutum zai ci moriyar abubuwa masu kyau ta wurin amfanin bakinsa, amma marmarin mayaudara ta'addanci ne.3Mai tsaron bakinsa yana kare ransa, amma wanda ya wage bakinsa zai hallaka kansa.4Raggayen mutane na marmarin samu, amma ba sa samun komai, amma begen mutane masu ƙwazo zai sami ƙosarwa.5Mutum mai adalci ya kan ƙi ƙarairayi, amma mugun mutum yakan maida kansa abin ƙyama, kuma yakan yi abin kunya.6Adalci yakan tsare kamilai a cikin tafarkinsu, amma mugunta ta kan juyar da waɗanda suka aikata zunubi.7Akwai wani mai azurta kansa, amma ba shi da komai sam, kuma akwai wanda ba ya ba kansa komai, duk da haka yana da wadata da gaske.8Fãnsar ran mai arzaki dukiyarsa ce, amma matalauci baya jin razanarwa.9Hasken adalan mutane yakan yi murna, amma fitilar miyagun mutane za a ɓice ta.10Girmankai husuma kaɗai ya ke kawowa, amma akwai hikima ga waɗanda ke karɓar shawara.11Wadata zata ragu idan hanyar samunta ta banza ce, amma wanda ya sami kuɗi ta wurin yin aiki da hannunsa zai sa kuɗinsa su ƙaru.12Sa'ad da aka dakatar da bege, zuciya takan karaya, amma samun abin da aka sa zuciya itacen rai ne.13Duk wanda ya rena umarni yana jawowa kansa hallaka, amma mai mutunta doka za a sãka masa.14Koyarwar mai hikima maɓulɓular rai ce, da zasu juyar da kai daga tarkunan mutuwa.15Tunani mai kyau kan jawo tagomashi, amma hanyar mai cin amana bata da iyaka.16Mutane masu hikima sukan yi aikinsu bisa ga ilimi a cikin kowacce shawara, amma wawa yakan bayyana wawancinsa.17Mugun ɗan saƙo yakan faɗa cikin damuwa, amma amintaccen wakili yakan kawo sasanci.18Wanda ya ƙi koyarwa zai sami talauci da kunya, amma girmamawa zata zo ga wanda ya koya ta wurin gyara.19Samun abin da aka daɗe ana sauraro da daɗi ya ke ga rai, amma wawaye na ƙin juyawa daga mugunta.20Ka yi tafiya da masu hikima zaka zama mai hikima, amma abokin tafiyar wawaye zai hallaka21Bala'i na bin masu zunubi, amma adalan mutane za a saka masu da abu mai kyau.22Nagarin mutum yakan bar gãdo domin 'ya'yan 'ya'yansa, amma a kan ajiye dukiyar mai zunubi domin adalin mutum.23Gonar talaka da ba'a nomawa akwai abinci da yawa, amma rashin adalci yakan kawar da shi.24Wanda baya horon ɗansa yana ƙinsa, amma mai ƙaunar ɗansa yana kula ya hore shi.25Adalin mutum yakan ci har sai ya ƙosadda marmarinsa, amma cikin mugu koyaushe yunwa ya ke ji.
Anan "ji" yana wakiltar sauraro domin yinshi. AT: "Ɗa mai hikima yana biyayya"
Anan "saurara" yana wakiltar bada hankali domin aikata shi. AT: "ba zai koya daga tsautawa ba" ko "ba zai yi biyayya ba, duk da tsautawa"
Anan “’ya’yan itace” suna wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "Daga kalmomin bakinsa" ko "Daga abin da yake faɗa"
Bude lebe yana wakiltar magana, kuma bude su a sarari yana wakiltar magana sau da yawa. AT: "yayi magana da yawa" ko "yayi magana da yawa"
"yake so da karfi amma bai samu komai ba"
Anan "begen" yana wakiltar sha'awa.AT: "mutane masu himma za su sami wadatacciyar rayuwa" ko "zama mai ƙwazo zai sa mutane su gamsu sosai"
haifar da mummunan ji na ƙyama
"Adalci" yana wakiltar hanyar rayuwa da Yahweh ya amince da ita. Wannan halayen yana aiki kamar mutumin da yake kiyayewa. AT: "Hanyar rayuwa wacce Yahweh ya yarda da ita tana kiyayewa"
Anan "hanya" tana wakiltar yadda mutum yake tafiyar da rayuwarsa. AT: "waɗanda ba su da aibi a hanyar rayuwarsu" ko "waɗanda ke rayuwa ta aminci"
Anan "mugunta" tana wakiltar mummunan halin rayuwa. Wannan halin yana yin kama da wanda ya juya wa waɗanda suka yi zunubi baya. AT: "mugunta tana kawar da masu zunubi daga hanyar nasara" ko "mugunta tana lalata masu zunubi" ™ rayuka "
"wa ya maida kansa mai arziki"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) babu wanda zai yi barazanar sata daga gare shi saboda ba shi da wani abin da kowa zai so ya sata ko 2) ba zai saurara ba yayin da mutane suka yi masa gyara domin ba shi da abin da zai rasa idan sun hukunta shi. AT: "baya jin tsawatarwa"
Anan haske yana wakiltar rayuwar mai adalci ko ɗabi'a mai kyau, murna kuwa tana nuna farin ciki ga mutane. AT: "Rayuwar mutumin kirki kamar haske ne wanda yake farantawa mutane rai"
Anan fitilar tana wakiltar rayuwa ko halayen mugaye, kuma “a kashe” wani karin magana ne wanda ke nufin an dakatar da wuta. Fitilar da take kashewa tana wakiltar mutum ne zai mutu ko kuma rayuwar mutumin ba ta da wani farin ciki. AT: "rayuwar mugaye kamar fitila ce wacce za'a dakatar da wutarta"
"Girman kai koyaushe yana haifar da rikici"
"Arziki yana raguwa" ko "Dukiya a hankali ta ɓace"
Kalmomin "aiki tare da hannunsa" na nufin aiki na zahiri maimakon na tunani ko wasu nau'ikan aiki kawai. Mutane da yawa suna ba da aikin jiki ƙaramin ƙima. AT: "aiki da ƙarfin jiki"
Anan "bege" yana wakiltar abinda mutum yake fata. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Idan mutum ya yi fatan wani abu amma bai karɓe shi ba na dogon lokaci"
Ana magana da wanda yake karbar abin da suke fata kuma ya zama mai farin ciki sosai kamar cika begensu itace mai ba da rai. AT: "dogon buri da ya cika kamar bishiyar rayuwa ce"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "za su saka wa wanda ya girmama umarni"
Maɓuɓɓugar ruwa kyakkyawa ce tushen ruwa kuma a nan tana wakiltar tushen rai. AT: "tushen rayuwa mai falala"
Anan "tarko" suna wakiltar haɗarin da zasu kashe. AT: "tarkunan da ke haifar da mutuwa"
Anan ana magana ne game da halayyar mutum ko halinsa kamar wata hanya ce ko hanyar da mutum yake bi. Mutumin da ya lalace ta hanyar yaudararsa ana maganarsa kamar suna kan hanya ko hanyar da ba ta ƙarewa.AT: "amma halayen masu ha'inci zai haifar da halakar kansu"
''zuwa farati '' na nufin nunawa a gaban kowa. AT: "wawa ya nuna wautarsa ga kowa"
"ba abin dogaro bane" ko "yayi mummunan abu"
Cikakken sunan "gyara" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "ya koya yayin da wani ya gyara shi"
"abin murna ne" ko "yana kawo farin ciki"
An ba da "Bala'i" halaye na mutane kamar ikon gudu. AT: "Masu zunubi suna da matsala duk inda suka tafi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah yana saka wa mutanen kirki da alheri"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda ya yi dai-dai zai karɓi dukiyar da mai zunubi ya tara"
"Filin da ba a shirya shi don noman abinci ba" ko "Filin fanko ba shiri don dasawa"
"Shafe" yana wakiltar cire abu gaba ɗaya. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "amma rashin adalci yana ƙwace abincin" ko "amma mutane marasa adalci suna karɓar abincin"
"ya gamsar da kansa" ko "yana cika burinsa"
Anan "ciki" yana wakiltar sha'awar mutum. AT: "azzalumin mutum koyaushe yana neman ƙarin"
1Mace mai hikima takan gina gidanta, amma wawar mace takan rushe shi da hannuwanta.2Wanda ya ke tafiya cikin gaskiya yana tsoron Yahweh, amma wanda ba shi da gaskiya yana rena shi.3Daga bakin wawa tsiron girman kansa ke fitowa, amma leɓunan masu hikima zasu tsare su.4Wurin da babu dabbobi kwamin ciyar da dabbobi yakan zama da tsabta, amma isasshen abinci yakan zo ta wurin ƙarfin bajimi.5Amintaccen mashaidi ba yayin ƙarya, amma mai shaidar zur ƙarairayi ya ke furtawa.6Mai ba'a yakan nemi hikima amma ba zai samu ba, amma ilimi yakan zo a sauƙaƙe ga wanda ya ke da fahimta.7Ka guje wa wawan mutum, domin ba zaka sami ilimi daga maganganunsa ba.8Hikimar mutum mai fahimta shi ne ya gane hanyarsa, amma wautar wawaye itace yaudara.9Wawaye sukan yi ba'a sa'ad da aka miƙa hadayar laifi, amma a kan raba tagomashi tsakanin kamilai.10Zuciya tasan ɓacin ranta bata raba murnarta da bãƙo.11Za a hallaka gidan mugayen mutane, amma rumfar masu adalci zata yi albarka.12Akwai hanya wadda take dai-dai ga ganin mutum, amma ƙarshenta takan kai ga mutuwa kaɗai.13Zuciya na iya dariya amma ta kuma kasance cikin damuwa murna kuma kan iya zama baƙinciki.14Marar aminci zai sami abin da ya dace da hanyoyinsa, amma nagarin mutum zai sami abin da ke nasa.15Marar wayo yakan gaskanta kowanne abu, amma mutum mai himma yakan yi tunani game da takawarsa.16Mutum mai hikima yakan ji tsoro kuma ya rabu da mugunta, amma wawa da gangan yakan yi banza da gargaɗi.17Mai saurin fushi yakan yi abubuwan wauta, kuma mutum mai tsara mugayen dabaru a na ƙinsa.18Marasa wayo sukan gãji wauta, amma mutane masu himma a na masu kambi da ilimi.19Mugayen mutane zasu russuna a gaban waɗanda ke nagari masu mugunta kuma zasu russuna a ƙofofin masu adalci.20Matalauci har abokan hurɗansa ƙinsa suke, amma masu arziki suna da abokai da yawa.21Wanda ya rena maƙwabcinsa zunubi ya ke yi, amma wanda ke taimakon matalauci mai albarka ne.22Masu shirin mugunta ba ratse hanya suke yi ba? Amma masu shirin yin alheri zasu karɓi rabon amintacciyen alƙawari da karɓuwa.23Ta wurin aiki tuƙuru a kan sami riba, amma wurin da taɗi ne kawai, talauci yakan zo.24Rawanin masu hikima dukiyarsu ce, amma wautar wawaye takan ƙara kawo masu wawanci.25Mashaidi mai gaskiya yakan ceci rayuka, amma mai shaidar zur yakan furta ƙarairayi.26Sa'ad da wani yaji tsoron Yahweh, shi ma yana da gabagaɗi a cikinsa; waɗannan abubuwa zasu zama kamar wurin fakewa mai ƙarfi domin 'ya'yan wannan mutumin.27Tsoron Yahweh maɓulɓula ne na rai, domin mutum ya iya juyawa daga tarkunan mutuwa.28Ɗaukakar sarki na cikin yawan mutanensa, amma rashin mutane ke hallaka yarima.29Mutum mai jinkirin fushi na da ganewa mai yawa, amma mutum mai garaje na ɗaukaka wauta.30Natsattsiyar zuciya rai ce ga jiki, amma kishi yakan ruɓar da ƙasusuwa.31Wanda ya zalunci matalauta yana la'anta Mahaliccinsa, amma wanda ya nuna tagomashi ga mabuƙata yana girmama shi.32Akan kãda mugun mutum ƙasa ta wurin mugayen ayyukansa, amma mai adalci na da mafaka ko a cikin mutuwa.33Hikima takan zauna cikin zuciyar mai fahimta, amma ko cikin wawaye takan bayyana kanta.34Aikata adalci na ɗaukaka al'umma, amma zunubi abin kunya ne ga kowacce jama'a.35Tagomashin sarki na tare da baran da ke aiki da himma, amma fushinsa na kan wanda ke aikata abin kunya.
"gina gidanta" ko "inganta gidanta"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan na iya nufin gidanta na ainihi, wato ginin da take zaune a ciki ko 2) wannan na iya nufin danginta.
Matar tana wakiltar “hannayen” ta. AT: "da kanta" ko "ta hanyar halinta"
Baki da lebe duk suna nufin abin da mutum yake faɗa.
Sanda da mutane zasu azabtar da wawa ta hanyar doke shi a bayansa saboda kalmominsa na wauta wata magana ce ta kalmomin da ke fitowa daga bakinsa. AT: "kalmomin da zasu sa mutane su hukunta shi"
"zai kiyaye su daga cutarwa" ko "zai kiyaye su da aminci"
Wannan karin magana yana amfani da "numfashi" don magana akan karya koyaushe. AT: "karya kullum"
"wanda yake da hikima" ko "mutumin da yake da hankali"
Wawancin wawaye shi ne yasa suke tunanin suna da hikima, alhalin basuda hankali.
"a laifi" ko "a hadayar laifi." Ma'anar wannan jumlar ita ce, wawaye ba sa neman gafara ga Allah ko mutane game da abubuwan da suka yi ba dai-dai ba.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "amma masu karkata suna jin daɗin ni'ima tare" ko "amma ni'imar Allah tana tare tare a tsakanin masu karkata"
Kalmar "hanya" tana wakiltar yanayin rayuwar da mutum yake bi. AT: "Mutane suna tunanin cewa hanyar da suke rayuwa ita ce hanya adaidaiciya"
Kalmar "zuciya" tana wakiltar yadda mutum yake ji, halaye da kuma motsa shi. AT: "Jin ra'ayin mutum na iya nuna dariya"
Kalmar "hanyoyi" tana wakiltar halin rayuwar mutum. AT: "abin da ya cancanta, dangane da yadda ya rayu"
Anan ana maganar mugunta kamar wani wuri. AT: "ya guji aikata mugunta"
"da gaba gaɗi watsi"
"yayi fushi da sauri"
Anan "gado" yana wakiltar samun abu na dindindin.
Anan ana magana da ilimi kamar yana da ado mai kyau wanda ake sawa a kai, kamar rawani da lu'ulu'u. AT: "sanya ilimi azaman rawani" (Duba: fig_metaphor)
Kalmar "ƙofofi" tana wakiltar ƙofar saduwa da wata. Wannan yana nufin cewa mugaye zasu jira mutumin kirki kuma suyi roƙo don shiga gabansa. AT: "don saduwa da mutumin kirki"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kowa ya ƙi talaka ko da maƙwabtansa ne"
Amsar da aka ɗauka ga wannan tambayar ita ce "eh." AT: "Waɗanda ke ƙulla muguwar cuta za su ɓace."
"amma idan kuna magana ne kawai" ko "amma lokacin da duk abin da mutum yake yi yana magana"
Kalmar "kambi" tana wakiltar babbar nasara ce da ake iya samu kuma ga kowa. AT: "Ladan masu hikima"
Wannan karin magana yana amfani da "numfashi" don magana akan karya koyaushe. Duba yadda kuka fassara wannan jumlar a cikin Misalai 6:17. AT: "karya kullum"
"Maɓuɓɓugar ruwa" maɓuɓɓugar ruwa ce mai kyau kuma tana wakiltar tushen rai.AT: "tushen rayuwa"
"Tarko" wani irin tarko ne da ake amfani dashi don farautar dabbobi kuma yana wakiltar wani abu mai wayo da haɗari wanda zai kashe. AT: "daga tarkon da zai kashe"
"mutane nawa yake mulki"
"yarima bashi da komai kuma masarautarsa zata fadi"
"Tunani mai lumana" ko "Halin da ke zaman lafiya"
"mai alheri ne ga" ko "taimaka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mugayen ayyuka sun gusa" ko "mugayen ayyuka sun lalace"
Kalmar nan "zuciya" tana wakiltar yadda mutum yake ji, halaye da kuma motsa shi. AT: "Hikima tana cikin halayyar"
"yana kawo kunya ga wasu mutane" ko "ya kamata sa wasu mutane su ji kunya"
1Mayar da magana da taushi kan juyar da hasala, amma magana mai zafi na tada fushi.2Harshen mutane masu hikima na yabon ilimi, amma bakin wawaye yana zuba wauta.3Idanun Yahweh suna ko'ina, suna lura da mugaye da nagari.4Harshe mai warkarwa Itacen rai ne, amma harshe mai yaudara na karya ruhu.5Wawa yakan ƙi kulawa da umarnin mahaifinsa, amma wanda ke koya ta wurin gyara mai himma ne.6A cikin gidan adalin mutum akwai dukiya mai yawa, amma dukiyar mugun mutum na ba shi damuwa.7Leɓunan mutane masu hikima sukan baza ilimi, amma ba haka zukatan wawaye suke ba.8Yahweh yana ƙin hadayun mugayen mutane, amma yana murna da addu'ar adalai.9Yahweh ya ƙi hanyar mugayen mutane, amma yana ƙaunar wanda ke bin abin da ke dai-dai.10Horo mai zafi na jiran duk wanda yabar hanyar da ke dai-dai shi kuma wanda yaƙi tsautawa zai mutu.11Lahira da hallakarwa a buɗe suke a gaban Yahweh; to balle zukatan "yan adam?12Mai ba'a baya son gyara; ba zai je wurin mai hikima ba.13Zuciya mai murna takan sa fuska tayi murmushi, amma ciwon zuciya yakan karyar da ruhu.14Zuciya mai basira takan nemi ilimi, amma bakin wawa naci daga wawanci.15Mutanen da ke shan tsanani suna cikin takaici dukkan kwanakin ransu, amma zuciya mai farinciki zata yi buki marar matuƙa.16Gwamma a samu kaɗan tare da tsoron Yahweh da samun dukiya da yawa cikin ruɗami.17Cin abinci tare da 'ya'yan itatuwa a wurin da akwai ƙauna ya fi cin ɗan maraƙi mai ƙiba tare da ƙiyayya.18Mutum mai zafin rai yakan tãda husuma, amma mai jinkirin fushi na kwantar da rigima.19Hanyar rago na kama da wurin da aka shinge ta da ƙayayuwa, amma hanyar adali lafiyayya ce.20Ɗa mai hikima na kawo farinciki ga mahaifinsa, amma wawa yana rena mahaifiyarsa.21Daƙiƙai na murna da mutumin da ba shi da tunani, amma mai fahimta na tafiya a hanyar da ke dai-dai.22Wurin da babu shawara shirye-shirye kan tafi ba dai-dai ba, amma zasu yi nasara inda akwai mashawarta da yawa.23Mutum yakan sami farinciki sa'ad da ya bada amsar da ta dace; magana a lokacin da ya dace abu mai kyau ne!24Tafarkin rai na kaiwa sama-sama ga mutane masu himma, domin su tsere daga Lahira ta ƙarƙashi.25Yahweh yana rushe gidan mai girmankai, amma yana kiyaye dukiyar gwauruwa.26Yahweh yana ƙin tunanin mugayen mutane, amma kalmomi masu daɗi tsabtatattu ne.27Ɗan fashi na kawo masifa cikin iyalinsa, amma mai ƙin cin hanci zai rayu.28Zuciyar adalin mutum takan yi tunani kafin ta bada amsa, amma bakin mugayen mutane na zuba dukkan muguntarsa.29Yahweh na nesa da mugayen mutane, amma yana jin addu'ar adalan mutane.30Fuska mai fara'a takan kawo murna ga zuciya kuma labari mai daɗi lafiya ce ga jiki.31Idan ka maida hankali sa'ad da wani ke maka gyara yadda zaka yi rayuwa, zaka zauna cikin mutane masu hikima.32Wanda yaƙi horo rena kansa ya ke yi, amma mai sauraron gyara zai sami fahimta.33Tsoron Yahweh na koyar da hikima kuma tawali'u kuma na zuwa kafin girmamawa.
Sanadin mutum ya daina yin fushi ana magana ne kamar yana juya fushin mutumin ne. AT: "Amsawa mutum a hankali zai huce fushin mutumin"
Sanadin sa mutum ya kara yin fushi ana magana ne kamar yana tayar da hankali ko tada fushi. AT: "amma magana mai tsauri tana sa mutumin ya ƙara yin fushi"
Anan kalmar "harshe" tana nufin mutumin da yake magana. AT: "Mutane masu hikima suna yabawa da ilimi yayin da suke magana" (Duba: fig_synecdoche)
Marubucin yana magana ne game da wawayen bakinsu kamar kwantena kuma wauta kamar ruwa ne ya cika su. Idan wawaye suka yi magana, bakunansu suna zubda ruwan. Kalmar "baki" tana wakiltar waɗanda ke magana. "wawaye koyaushe suna magana da wauta"
Anan kalmar "idanu" tana wakiltar Yahweh kuma tana nanata ikonsa na ganin komai. AT: "Yahweh yana ganin komai"
Kalmomin "mugunta" da "mai kyau" suna nufin mutane. AT: "mugaye da mutanen kirki"
Kalmar "harshe" tana nufin magana. Marubucin yayi maganar kalmomin mutumin da ke faɗar abubuwan da ke taimakawa da ƙarfafa wasu kamar bishiya ce da ke ba da abinci mai ba da rai. AT: "Kyakkyawan kalmomi kamar itaciya ce mai ba da rai"
Kalmomin "harshe mai ruɗi" yana nufin magana mai yaudara ko cuta. Marubucin yayi magana ne game da cutar da wani mutum ko kuma ya yanke ƙauna kamar dai ruhun mutumin wani abu ne da kalmomi suka murƙushe shi. AT: "Kalaman yaudara na sa mutum ya yanke kauna"
Ana iya fassara kalmar "gyara" a matsayin fi'ili. AT: "wanda ya koya yayin da wani ya gyara shi"
AT: "dukiyar da mugaye suka samu tana bayarwa"
Kalmar nan “lebe” tana wakiltar abin da masu hikima suka faɗa. Marubucin yayi maganar ilimi kamar dai tsaba ce wacce mutane masu hikima ke watsuwa lokacin da suke magana. AT: "Jawabin mutane masu hikima yana yada ilimi"
Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) kalmar "zukata" yana nuna ga wawaye da kansu kuma tana nufin ba sa watsa ilimi kamar yadda masu hikima ke yi. AT: "wawaye ba sa watsar da ilimi game da" ko 2) wawaye ba su da ilimi a cikin zukatansu, tare da "zukatan" kasancewa meton don tunani. AT: "wawaye basa fahimtar ilimi"
Ana maganar salon rayuwar miyagu kamar suna hanyoyi ne da wadancan mutanen suke tafiya akansu. AT: "Yahweh ya ƙi jinin yadda mugaye suke rayuwa"
Yin himma don rayuwa dai-dai ana maganarsa kamar tana bin abubuwa masu kyau. AT: "mutumin da ya yi ƙoƙari ya rayu da gaskiya"
Anan "hanya" tana nufin hanyar adalci. Ana magana da mutumin da ya daina yin abin da yake dai-dai kamar ya daina tafiya a kan madaidaiciyar hanya. AT: "duk wanda ya daina rayuwa dai-dai"
Kalmomin “Lahira da halaka” duk suna nufin wurin da matattu suke. Yahweh yana san komai game da matattu ana magana akan shi kamar a buɗe yake a gaban Yahweh. AT: "Yahweh ya san komai game da wurin da matattu suke"
Wannan tambayar tana nanata cewa tunda Yahweh ya san komai game da matattu, to a bayyane yake cewa ya san komai game da zukatan mutane.AT: "saboda haka tabbas ya san zukatan 'yan adam!"
Anan kalmar "zuciya" tana wakiltar mutum. AT: "Idan mutum ya yi murna, fuskarsa tana da fara'a"
Anan kalmar "zuciya" tana wakiltar hankali da tunani. AT: "Zuciyar mai hankali" ko "Mai hankali"
"Mutanen da ake zalunta suna cikin wahala duk tsawon kwanakinsu"
Anan kalmar "zuciya" tana wakiltar mutum. Marubucin yayi maganar mutum mai fara'a da jin daɗin rayuwa kamar dai mutumin yana yin biki ne wanda ba ya ƙarewa. AT: "mai farinciki yana jin daɗin rayuwa, kamar yana yin biki ne mara ƙarewa"
Kayan lambu suna wakiltar ƙaramin abinci tare da abinci kaɗan. AT: "ƙaramin abinci" ko "abinci kaɗan"
Ana iya fassara kalmar "kauna" tare da jimlar magana. AT: "inda mutane suke son junan su"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "ɗan maraƙin da aka yi kiba da shi wanda yake aiki da ƙiyayya"
Marubucin ya kwatanta salon rayuwar malalaci da ƙoƙarin yin tafiya ta cikin shingen ƙaya. Dukansu suna sa mutum ya sha wahala. AT: "Rayuwar malalaci kamar mutum yake ƙoƙarin tafiya ta cikin shingen ƙaya"
Marubucin yayi magana akan ni'imar da adalai ke samu a rayuwa kamar suna tafiya akan hanya mai santsi.
Marubucin yayi magana game da mutum yana aikata abin da yake daidai kamar yana tafiya kai tsaye a kan hanya. Madadin fassara: "mutumin da yake da fahimta ya aikata abin da yake daidai" (Duba:
"Shirye-shirye sun kasa a lokacin da babu mai ba da shawara"
"amsa mai dacewa" ko "amsar da ta dace"
Wannan kirari yana jaddada cewa kalma da aka faɗa a lokacin da ya dace tana da kyau ƙwarai. AT: "kalmar da mutum ya yi magana a lokacin da ya dace tana da kyau"
Wannan tsarin zinare ne na gidan mutum, dukiyarsa, da dukiyarsa. (Duba:
"kalmomin kirki tsarkakakku ne" ko "kalmomi masu daɗi tsarkakakku ne"
Anan kalmar "zuciya" magana ne don hankali da tunani. Wannan yana wakiltar mutumin da yake tunani. AT: "Mutumin da ya yi daidai yana tunanin abin da zai faɗa kafin ya ba da amsa"
Marubucin yayi maganar bakin mugayen mutane kamar suna cikin kwantena kuma yayi magana akan mugunta kamar dai shine ruwan da ya cika su. Lokacin da mugaye suke magana, bakinsu yakan zubar da ruwa. Kalmar "bakin" tana wakiltar waɗanda suke magana. AT: "mugayen mutane koyaushe suna faɗar mugu"
Marubucin yayi maganar Yahweh baya sauraron mugaye kamar yana nesa da su a zahiri. AT: "Yahweh baya jin tsoron mugaye" ko kuma "Yahweh baya amsawa ga miyagu"
Marubucin yayi maganar farin ciki a fuskar mutum kamar idanun mutum suna fitar da haske. AT: "Maganar fara'a"
Kalmar nan “zuciya” tana wakiltar mutumin. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) mutumin da yake da fara'a ya zama mai farin ciki ko 2) wasu mutane suna yin farin ciki idan suka ga wani da furcin farin ciki. AT: "yana sa mutum ya kasance cikin farin ciki"
Anan kalmar “jiki” tana wakiltar mutum. AT: "karɓar labari mai daɗi yana sa mutum ya ji daɗi"
Mai yiwuwa su ne 1) mutane za su ci gaba da ɗaukan ka a matsayin mutum mai hikima ko 2) za ka ci gaba da jin daɗin tarayya da masu hikima.
AT: "Idan mutum ya ji tsoron Yahweh, zai koyi hikima"
Wannan yana nufin cewa dole ne mutum ya fara koyan tawali'u kafin Yahweh ya girmama shi.
1Shirye-shiryen zuciya na mutum ne, amma daga harshen Yahweh amsa ke fitowa.2Dukkan hanyoyin mutum suna da tsarki a ganinsa, amma Yahweh ke auna ruhohi.3Ka miƙa ayyukanka ga Yahweh shirye-shiryenka kuma zasu yi nasara.4Yahweh ya yi kowanne abu da dalili, har da mugu domin ranar wahala.5Yahweh na ƙin kowanne mutum mai zuciya mai fahariya, amma ku tabbatar da wannan, ba zasu kuɓuta daga hukunci ba.6Ɗa amintaccen alƙawari da gaskatawa akan gafarta zunubi ta wurin tsoron Yahweh mutane suke juyawa daga mugunta.7Lokacin da hanyoyin mutum suka gamshi Yahweh, zai sa maƙiyan mutumin su zauna lafiya da shi.8Gwamma kaɗan da abin da ke na adalci, da dukiya mai yawa da ke ta rashin adalci.9A cikin zuciya mutum ke shirya hanyarsa, amma Yahweh ke bida sawayensa.10Ƙudurori masu zurfi na a leɓunan sarki, kada bakinsa ya munafunci adalci.11Ma'aunai na gaskiya na zuwa ne daga Yahweh; dukkan ma'aunai cikin jakka ayyukansa ne.12Sa'ad da sarakuna suka yi mugayen abubuwa, wannan abin ƙi ne, gama kursiyi na kafuwa ne ta wurin yin abin da ke dai-dai.13Sarki na murna da leɓunan da ke faɗin abin da ke dai-dai kuma yana ƙaunar mai magana kaitsaye.14Fushin sarki saƙon mutuwa ne amma mutum mai hikima zai yi ƙoƙarin kwantar da fushinsa.15A cikin fara'ar sarki rai ne kuma tagomashinsa na kama da hadari mai kawo ruwan sama a lokacin bazara.16Yafi kyau a sami hikima fiye da zinariya. A sami fahimta yafi neman azurfa.17Babbar hanyar adalan mutane na kauce wa mugunta; wanda ke kãre ransa na kula da hanyarsa.18Girmankai na zuwa kafin hallaka kuma ruhun fahariya kafin fãɗuwa.19Ya fi kyau ka zama mai tawali'u cikin matalauta da ka zama mai raba ganima tare da masu girmankai.20Duk wanda ke tunani a kan abin da aka koya masa zai sami abin da ke mai kyau, waɗanda kuma suka dogara ga Yahweh zasu yi albarka.21Mai hikima cikin zuciya za a ce da shi mai sansancewa kuma zaƙin maganarsa na inganta iya koyarwa.22Fahimta maɓuɓɓugar rai ce ga wanda ya ke da ita, amma umarnin wawaye wawancinsu ne.23Zuciyar mutum mai hikima na bada basira ga bakinsa ta kuma ƙara ikon rinjaya ga leɓunansa.24Kalmomi masu daɗi saƙar zuma ce - abin daɗi ga rai warkarwar kuma ga ƙasusuwa.25Akwai hanyar da ke dai-dai ga mutum, amma ƙarshenta hanyar zuwa ga mutuwa ce.26Marmarin ma'aikaci na yi masa aiki; yunwarsa na tura shi gaba.27Mutum marar amfani na haƙo da damuwa maganarsa kuma na kama da wuta mai ƙuna.28Mugun mutum na tãda tashin hankali magulmaci kuma na raba abokanai na kurkusa.29Mutum mai ta'addanci na yin ƙarya ga maƙwabcinsa ya kuma gangara dashi ga tafarki da ba dai-dai ba.30Mutum mai kaɗa ido abubuwan mugunta ya ke ƙullawa; waɗanda ke tsayar da leɓuna zasu kawo mugunta.31Furfura kambin daraja ce; a na samunta ne ta yin rayuwar data dace.32Ya fi kyau ka zama mai jinkirin fushi da ka zama jarumi kuma wanda ke mulkin ruhunsa ya fi wanda ke mamaye birni.33Akan jefa ƙuri'a a cikin cinya, amma yanke shawara daga wurin Yahweh ne.
Anan kalmar "zuciya" tana wakiltar tunanin mutum da tunanin sa. AT: "Mutum yana yin shiri a cikin zuciyarsa"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Yahweh yayi magana akan amsar sa ga shirin mutum, wanda ma'ana kwatanci ne da cewa Yahweh yana yanke hukuncin sakamakon shirin mutumin ko 2) Yahweh yana bawa mutum damar yin magana game da shirin da yayi.
Idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. Marubucin yayi maganar abin da mutum yakeyi kamar mutumin yana tafiya akan hanya. AT: "Mutum yana tunanin cewa duk abin da yake yi mai tsarki ne" ko "Mutum yana yanke hukunci a kan duk abin da ya aikata da tsarkakakke"
Anan kalmar "ruhohi" tana wakiltar sha'awar mutane da kuma muradinsu. Marubucin yayi magana game da Yahweh yayin fahimta da hukunta sha'awar mutum da muradinsa kamar yana auna ruhun mutumin. AT: "Yahweh yana hukunta dalilan mutum"
Ana iya samar da jimlar ta magana daga jumlar da ta gabata. AT: "ya sanya har ma da mugaye don ranar wahala"
Anan kalmar "zuciya" tana wakiltar mutum. AT: "duk mai girman kai"
Sunayen "aminci" da "amana" za'a iya bayyana su da "aminci" da "amintacce." Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) AT: "Saboda Yahweh mai aminci ne ga alƙawarinsa kuma amintacce ne yana gafarta zunuban mutane" ko 2) AT: "Yahweh zai gafarta zunuban waɗanda suka yi aminci ga alkawarin kuma amintattu"
"tare da zalunci"
A nan kalmar "lebe" magana ne ga abin da sarki ya ce. AT: "Abin da sarki ya ce shawara ce mai hankali"
Kalmar "bakin" tana wakiltar sarki da kansa. AT: "bai kamata yayi magana da yaudara ba yayin da yake yanke hukunci"
Yahweh yana buƙatar adalci da gaskiya yayin kasuwanci. Mutane marasa gaskiya suna amfani da nauyi mai nauyi ko nauyi a cikin ma'auninsu don samun ƙarin lokacin saye ko sayarwa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wannan wani abu ne da mutane suka raina" ko "wannan wani abu ne da Yahweh ya ƙi"
Anan kalmar "kursiyi" tana wakiltar mulkin sarki. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "don sarki ya kafa mulkinsa ta hanyar yin abin da yake dai-dai"
Marubucin yayi magana game da sarki mai fushi wanda ya sa wani ya mutu kamar fushin sarki manzo ne wanda ya aiko don ya kashe wani. AT: "Sarki mai fushi zai iya kashe mutane"
Marubucin yayi magana game da nuna farin ciki a fuskar sarki kamar fuskarsa tana annuri. AT: "Lokacin da sarki ya kasance da fara'a, mutane suna rayuwa"
Marubucin ya kwatanta sarki yana nuna fifiko ga wani tare da gajimare wanda ke kawo ruwan sama don sa albarkatu su yi girma. Dukansu sunyi alƙawarin albarkatu ga waɗanda suka karbe su.
Marubucin yana magana ne game da salon rayuwar mutanen kirki kamar dai hanya ce ingantacciya, babu cikas. AT: "Hanya madaidaiciya wacce adalai ke rayuwa"
Marubucin yayi maganar kaucewa ko daina aikata mugunta kamar yana nisantar mugunta. AT: "yana hana su aikata mugunta"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "abin da wani ya koya musu" ko "abin da suka koya"
Anan zuciya tana wakiltar tunani. AT: "Wanda yake da hikima" ko "Wanda yake da hikima a cikin tunaninsa"
Marubucin yayi maganar alheri ko magana mai daɗi kamar dai wani abu ne mai ɗanɗano mai daɗi. AT: "kyakkyawar magana" ko "magana mai daɗi"
Anan kalmar "baki" na nuna ta magana. AT: "yana sa maganarsa ta zama mai hikima"
Mai yiwuwa ma'anar kalmar "kurwa" ita ce 1) tana wakiltar sha'awar mutum da jin daɗinsa. AT: "mai daɗin daɗi don faranta wa mutum rai" ko 2) yana iya nufin "maƙogwaro" kuma yana da kyan gani ga harshen mutum da ikon ɗanɗano. AT: "mai daɗin ɗanɗanar mutum"
Marubucin yayi magana game da sha'awar kamar dai mutum ne mai aiki a madadin ma'aikata. Wannan yana nufin cewa mutumin da yake yin kwadago shine sha'awar sa ta ci. AT: "Ma'aikacin na aiki ne don biyan bukatar sa"
Marubucin yayi magana akan "yunwa" kamar dai mutum ne wanda ya kwadaitar da lebura ya ci gaba da aiki. AT: "ya ci gaba da aiki saboda yana jin yunwa"
Marubucin yana magana ne game da mutumin da yake ƙoƙarin neman hanyoyin cutar da wasu mutane kamar dai wannan mutumin yana haƙa ƙasa don neman wani abu da aka binne. AT: "Mutum marar amfani yana neman ɓarna kamar yana haƙa wani abu a ƙasa"
Marubucin ya kwatanta yadda maganar wannan mutumin take cutar da wasu da yadda wuta take kona abubuwa. AT: "yana cutar mutane da kalamansa, kamar wuta tana cin abinda ta taba"
An nuna cewa wannan mutumin yana yiwa maƙwabcin sa ƙarya don ya sa maƙwabcin ya kasance tare da shi cikin ayyukan tashin hankali. AT: "Mutum mai yawan tashin hankali ya yaudari maƙwabcinsa"
Marubucin yayi maganar ayyukan mutum kamar dai hanya ce da mutum yake tafiya akanta. AT: "sa shi ya aikata abubuwan da ba su da kyau"
Marubucin yayi maganar furfura kamar tana da kambi. "Furfura" magana ne na tsufa. AT: "Mutumin da ya daɗe da samun furfura kamar wanda ya sa kambi mai daraja a kansa"
Marubucin yayi magana ne game da mutum yana iya kame fushinsa da motsin ransa kamar yana mulkin ruhunsa kamar yadda sarki yake mulkin jama'arsa. AT: "wanda ya kame fushinsa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutum ya jefa kuri'a a cinyarsa"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Yahweh ne ya yanke shawarar yadda kuri'a za ta fadi ko 2) ba kuri'a ba ce, amma Yahweh ne yake ƙaddara abin da zai faru.
1Ya fi a ci busasshiyar gurasa rai kwance da gida cike da shagali tare da tashin hankali.2Bawa mai hikima zai yi mulki bisa ɗan da ke aikata abin kunya zai kuma sami rabon gãdo kamar ɗaya daga cikin 'yan'uwa.3Maƙera da tanderun wuta domin tãce azurfa da zinariya ne; amma Yahweh ke tace zukata.4Mai aikata mugunta na kasa kunne ga mugayen leɓuna; maƙaryaci na sauraren harshe mai hallakarwa.5Duk wanda ya yi wa matalauci ba'a Mahallicinsa ya ke zagi kuma wanda ke farinciki da hasara ba zai tsira ba tare da hukunci ba.6Jikoki kambin tsofaffi ne iyaye kuma suna kawo daraja ga 'ya'yansu.7Yin magana da ƙwarewa bata da daɗi ga wawa; balle leɓuna masu faɗin ƙarya ba dai-dai bane da masu mulki.8Cin hanci na kama da dutsen dabo ga wanda ya bada shi; duk inda ya juya, nasara ya ke yi.9Duk wanda ke yafe laifi yana neman ƙauna, amma wanda ke maimaita batu yana raba abokai na kurkusa.10Tsautawa kan shiga da zurfi cikin mutumin da ke da fahimta fiye da naushe-naushe ɗari ga jikin wawa.11Mugun mutum tawaye kaɗai ya ke nema, don haka za a aika masa da mugun manzo ya yi gãba da shi.12Ya fi kyau ka gamu da kerkeci wadda aka kwashe mata 'ya'yanta da ka gamu da wawa cikin wawancinsa.13Idan wani ya maida mugunta maimakon alheri, mugunta ba zata taɓa rabuwa da gidansa ba.14Mafarin jayayya na kama da wanda ya saki ruwa ko'ina, don haka ka kaucewa jayayya kafin ta ɓarke ko'ina.15Mutumin da ya baratar da mugun mutum da mutumin da ya kãda adalin mutum - dukkansu abin ƙi ne ga Yahweh.16Donme wawa zai biya kuɗi ya koyi hikima, ganin cewa ba shi da iyawar koyon ta?17A koyaushe aboki yana nuna ƙaunarsa ɗan'uwa kuma an haife shi ne domin kwanakin damuwa.18Sai mutum marar hankali ke ɗaukar zaunannun alƙawarai domin basusuwan maƙwabcinsa.19Duk wanda ke ƙaunar rikici yana ƙaunar zunubi; wanda ya sa bakin ƙofarsa tayi yawan tsayi zai haifar da karyewar ƙashi.20Mutumin da ke da gurɓatacciyar zuciya ba ya ganin abin da ke dai-dai; wanda ke da mugun harshe na faɗawa cikin bala'i.21Mahaifin da ɗansa wawa ne yakan jawowa kansa ɓacin rai; mahaifin wawa kuma ba shi da farinciki.22Zuciya mai farinciki magani ne mai kyau, amma karyayyen ruhu kan busar da ƙasusuwa.23Mugun mutum yakan karɓi cin hanci a ɓoye domin ya karkatar da hanyoyin adalci.24Mai fahimta yakan sa fuskarsa wajen hikima, amma idanun wawa a kafe suke har ga ƙarshen duniya.25Wawan ɗa abin baƙinciki ne ga mahaifinsa abin haushi ne kuma ga matar da ta haife shi.26Haka kuma, ba dai-dai ba ne a hukunta mutum mai adalci; kuma ba shi da kyau a bulali mutane masu daraja masu mutunci.27Wanda ke da ilimi yakan yi amfani da kalmomi kaɗan wanda kuma ke da fahimta yana da natsuwa.28Har wawa idan ya yi shiru za a zaci shi mai hikima ne; sa'ad da bai yi magana ba, ana masa kallon mai basira.
Anan "shiru" yana nufin "salama." AT: "don samun salama"
Kalmomin "a sami" an fahimta daga jumlar da ta gabata. Za a iya maimaita su. AT: "fiye da kasancewa da gida cike da idi tare da jayayya" ko "fiye da zama a cikin gida cike da liyafa a inda ake rikici"
Wannan yana nufin yadda ake tace zinariya da azurfa. Ana yin ƙarfe da ƙarfe ta hanyar dumama shi zuwa zazzabi mai ƙarfi don ya narke kuma ana iya cire ƙazantar. AT: "Ana amfani da dusar ƙanƙan don tace azurfa kuma ana amfani da tanda wajen tace zinariya"
Wannan yana maganar Yahweh yana gwada mutane don ya taimake su su daina mugunta da wauta kamar dai zukatansu ƙarfe ne da Yahweh yake gyarawa don cire duk abin da ba shi da tsabta. AT: "Yahweh yana gwada mutane zukata"
Wannan suna ne da ke nufin Yahweh. Wannan ma suna ne wanda ba a fahimta wanda za a iya rubuta shi azaman aiki. AT: "wanda ya yi shi"
Wannan yana magana ne game da tsofaffin mutanen jikoki kasancewa alama ce ta girmamawa a gare su kamar dai jikokin su kambi ne. AT: "kawo girmamawa ga"
"Kyakkyawan magana" ko "Kyakkyawan magana"
Wannan yana bayyana mutane suna yin ƙarya kamar dai ainihin leɓunansu ne suke yin ƙarya. AT: "har ma fiye da haka bai dace da sarauta ta yi ƙarya ba"
Wannan yana magana ne game da cin hanci na mutum yana aiki ta hanyar kwatanta shi da dutse mai sihiri ko abin layya. AT: "Cin hanci yana aiki kamar dutse mai sihiri ga wanda ya bayar da shi" ko "Cin hanci yana aiki kamar sihiri ne ga wanda yake bayar da cin hanci"
Wannan yana nufin kawo yanayin da ya gabata wanda aboki ya ɓata ko ɓata rai. AT: "wanda ya maimaita laifin da ya gabata"
Wannan yana kwatanta yadda tsautawa ke tasiri ga mutum mai hankali da yadda duka yake shafan wawa. Wannan yana magana ne akan tasirin waɗannan mutane kamar dai za'a iya auna su da zurfin abin da yake shiga cikinsu. AT: "Tsautawa tana da tasiri a kan mutum ... kamar busa dari da aka yiwa wawa"
Kalmar "tawaye" ana iya bayyana ta azaman aiki. AT: "yana neman tawaye"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wani mummunan manzo zai zo akansa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kerkeci wacce ta rasa 'ya'yanta kawai"
Anan ana maganar "mugunta" kamar dai mutum ne wanda ba zai bar gidan mutumin ba. Anan ana iya ɗauka kalmar "gida" a zahiri, amma kuma yana nuna kyan gani ga danginsa. AT: "munanan abubuwa za su ci gaba da faruwa da shi da danginsa" ko "mummunan abubuwa ba za su daina faruwa da shi da danginsa ba"
Wannan yana kwatankwacin yadda rikici ke yaduwa cikin sauki da yadda malalar ruwa ke kwarara ko'ina. AT: "Fara rikici kamar ɗora ruwa ne da barin shi ya gudana ko'ina"
ya bayyana wani ba laifi
Wannan tambayar tana jaddada cewa bai kamata wawa ya aikata wannan ba. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Wawa bai kamata ya biya kuɗi don koyo game da hikima ba saboda ba shi da ikon koyon sa."
Ɗaya daga cikin dalilan ɗan’uwa shi ne kasancewa can don taimaka wa ɗan’uwansa ko ’yar’uwansa a lokacin wahala. AT: "ɗan'uwa yana wurin don lokutan wahala"
Wannan yana nufin cewa wani zai yi tuntuɓe a bakin ƙofar kuma ya fasa ƙasusuwa, wataƙila a ƙafarsu. AT: "tabbas zai sa wani ya yi tuntuɓe kuma ya fasa ƙasusuwan ƙafarsu" ko "tabbas zai sa wani ya yi tuntuɓe har ya ji wa kansa rauni"
“Zuciya” tana wakiltar yadda mutum yake ji, halaye da kuma motsa shi. AT: "wanene ke yaudara" ko "wanene ba shi da gaskiya"
“Harshen” yana wakiltar jawabin mutum. AT: "yayi magana mugu" ko "yayi magana mugunta"
Wannan yana magana ne game da zuciya mai farin ciki kamar kyakkyawan magani domin yana sa ku ji daɗi. AT: "Zuciya mai fara'a kamar magani ce da ke sa ku ji daɗi"
Anan “ruhu” yana wakiltar yadda mutum yake ji da yanayin motsin rai. Karyayyen ruhu yana nufin yanayin motsin rai mara kyau. AT: "bakin ciki"
"don hana zartar da adalci" ko "don karkatar da adalci"
Wannan yana magana ne game da hankalin mutum akan aikata hikima kamar yana duban hikima. AT: "yana mai da hankali kan aiki da hikima"
Wannan yana magana ne game da ɗa da ya haifar wa mahaifinsa baƙin ciki kamar dai ɗan da kansa “baƙin ciki” ne. AT: "Aan wawa ya kawo baƙin ciki ga mahaifinsa"
"wa ya haife shi"
Wannan yana nufin yadda yake magana. AT: "yayi magana da 'yan kalmomi"
Ana iya rubuta wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane ma suna ganin wawa mai hikima ne"
Wannan yana nufin ba ya magana. AT: "baya magana"
1Wanda ya ware kansa muradin kansa ya ke nema yana kuma jayayya da dukkan hukunci mai kyau.2Wawa bai da mu da ya fahimta ba, amma ya da mu kaɗai ya bayyana abin da ke cikin zuciyarsa.3Sa'ad da mugun mutum yazo, reni yakan zo tare da shi - tare da kunya da ƙasƙanci.4Maganganun bakin mutum ruwaye ne masu zurfi; maɓulɓular hikima rafi ne mai gudãna.5Ba dai-dai ba ne a nuna son kai ga mugun mutum, ko a hana adalci ga mutum mai adalci.6Maganar wawa takan jawo masa tsatsaguwa bakinsa kuma na gayyatar dũka.7Bakin wawa ke lalatar da shi da leɓunansa kuma ya ke ɗana wa kansa tarko.8Maganganun magulmaci na kãma da loma mai daɗi sukan kuma gangara zuwa can cikin ciki.9Haka kuma, wanda ya yi sanyi cikin aikinsa ɗan'uwa ne da wanda ke lalatarwa sosai.10Sunan Yahweh ƙaƙƙarfar hasumiya ne; adalan mutum yakan ruga cikinsa ya kuma tsira.11Attajiri na zaton dukiyarsa ce zata kare shi kamar garu mai tsayi da ke kewaye da birni.12Kafin faɗuwarsa zuciyar mutum takan kumbura, amma tawali'u yakan zo kafin girmamawa.13Wanda ya amsa kafin ya saurara - wauta ce a gare shi da kunya.14Ruhun mutum zai jure rashin lafiya, amma wa zai daure da karyayyen ruhu?15Zuciyar mai ƙwazo takan sami ilimi kunnen mai hikima yana biɗarsa.16Kyautar mutum zata bude masa hanya ta kuma kai shi gaban mutum mai muhimmanci.17Wanda ya fara gabatar da damuwarsa za a ga shi ne da gaskiya har sai abokin ƙara ya zo ya ƙalubalance shi.18Jefa ƙuri'a takan dai-daita jayayya ta raba tsakanin masu iko da ke jayayya.19Ɗan'uwan da aka ɓata da shi ya fi birni mai ƙarfi wuyar shiryawa, tantankawa kuma na kama da makaran kagara.20Cikin mutum zai ƙoshi da amfanin bakinsa; zai gamsu da amfanin leɓunansa.21Mutuwa da rai harshe ne ke sarrafasu, waɗanda ke ƙaunar harshe zasu ci amfaninsa.22Wanda ya sami mata abin kirki ya samu yana kuwa samun tagomashi daga wurin Yahweh.23Fakirin mutum yakan roƙi jinƙai, amma mawadaci na amsa magana da kaushi.24Wanda ke taƙamar yana da abokai da yawa, sukan yashe shi ta wurinsu, amma akwai abokin da ke zuwa kusa fiye da ɗan'uwa.
Wannan yana magana ne game da mutumin da yake rashin jituwa da hukunci mai kyau kamar dai "ingantaccen hukunci" mutum ne da yayi yaƙi da shi. AT: "bai yarda da duk hukuncin da ya dace ba"
"Wawa bai damu da fahimta ba, sai dai kawai" Wannan yana nufin wawa yayi la'akari da "fahimtar" akasin jin daɗi. AT: "Wawa yana kyamar fahimta kuma yana samun farin ciki ne kawai"
A nan ana maganar "raini," "kunya," da "zargi" kamar dai su mutane ne da ke tare da mugu. Zai yiwu ma'anonin su ne 1) mutane suna raina mugaye kuma suna sa shi jin kunya da zargi. AT: "mutane suna jin wulakanta shi tare da kunya da zargi" ko kuma 2) mugu ya nuna raini ga wasu kuma ya sa su jin kunya da zargi. AT: "yana nuna raini ga wasu mutane kuma yana sa su jin kunya da zargi"
Wadannan layin biyu suna nuna cewa mutumin da ke layin farko mutum ne mai hikima. AT: "Maganar bakin mai hikima ruwa ne mai zurfin gaske; ... maɓuɓɓugar hikima rafi ne mai gudana"
Wadannan kalmomin za a iya rubuta su cikin kyakkyawar siga. AT: "Yana da kyau a bi da mugaye kamar yadda ya cancanta, kuma a yi adalci ga mutumin kirki"
Wannan yana magana ne akan wawa yana fadin abubuwan da suke sa mutane su so su doke shi kamar yana kiran su ne su doke shi. AT: "bakinsa yana sa mutane su so su doke shi"
Duk waɗannan jimlolin suna nufin abin da wawa yake faɗa. AT: "Abin da wawa ya ce ... ta abin da ya faɗa "
Wannan yana maganar kalmomin gulma abin so ne a saurare su kamar abinci mai daɗin ci ne. AT: "Kalmomin tsegumi kyawawa ne don saurare" ko
Wannan yana magana ne da kalmomin gulma da ke shiga zuciyar mutum kuma yana shafar tunaninsa kamar abinci ne da ke shiga cikinsa. AT: "kuma suna shigar da tunanin mutum kuma suna shafar tunaninsa"
Wannan yana magana ne game da wanda sanyi cikin aikinsa yayi kama da wanda yake halakarwa kamar dai alaƙar su ce. AT: "yana da kusanci da" ko "yana da kamanceceniya da"
Wannan yana magana ne game da Yahweh yana kiyaye mutanensa kamar dai hasumiya ce mai ƙarfi da za su iya fakewa a ciki. AT: "Yahweh yana kiyayewa kamar hasumiya mai ƙarfi" ko "Yahweh yana kiyaye mutanensa kamar hasumiya mai ƙarfi"
Wannan yana magana ne game da mutanen da ke neman aminci daga Yahweh da Yahweh yana kiyaye su kamar dai hasumiya ce mai ƙarfi da suka ruga ciki don aminci. AT: "ku gudu zuwa gare shi kuma suna cikin aminci" ko "ku neme shi kuma suna cikin aminci"
Wannan yana magana ne game da mawadaci dangane da dukiyar sa kamar dai dukiyar sa katanga ce wacce ta kāre shi. AT: "Mawadaci ya dogara da dukiyarsa kamar yadda birni ya dogara da ganuwar ganuwarta"
Wannan yana magana ne game da mawadaci ya gaskanta da dukiyarsa zai kiyaye shi kamar babban bango yana kiyaye waɗanda suke cikin birni lafiya. AT: "yana tsammanin zai kiyaye shi da kuma babban bango"
"Da farko zuciyar mutum takan yi alfahari, amma sai ga faduwarsa"
Anan ana ambaton mutum da ruhunsa don jaddada halinsa. AT: "Mutumin da ke da bege zai tsira daga rashin lafiya" ko "Idan mutum yana cike da fata a cikin cikinsa, zai tsira daga rashin lafiya"
Wannan tambaya tana jiran amsar da 'yan kaɗan za su iya ɗauka. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "amma yana da matukar wuya a ɗauki karyayyen ruhu."
Anan ana nufin mai hankali da zuciyarsa don jaddada sha'awar sa. AT: "Burin hankali don neman"
Anan ana ambaton mai hikima ta hanyar jinsa don jaddada abin da yake son saurarawa. AT: "masu hikima suna neman koyo game da shi"
Wannan yana nufin mutanen da suke yaƙi mai zafi game da wani rikici. Lokacin da suka rabu, ba sa yin faɗa game da rikicinsu. AT: "yana sa abokan hamayya su daina yin faɗa game da rikicinsu"
Wannan yana magana ne game da wahalar yin sulhu da ɗan'uwan da kuka ɓata wa rai idan kuka gwada shi da wahalar cin nasara a yaƙi da birni mai ƙarfi. AT: "Idan kun cuci ɗan'uwanku, neman hanyar sasantawa da shi zai iya zama mafi wuya fiye da yin yaƙi don cin birni"
Wannan yana magana ne game da wahalar warware sabani ta hanyar kwatanta shi da wahalar fasa sandunan gidan sarauta. AT: "sasanta rikici yana da wahala kamar rushe sandunan gidan sarki"
Wadannan layin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani dasu tare don ƙarfafa abin da aka faɗa. Ana iya haɗuwa da su. AT: "Mutum ya gamsu da sakamakon kyawawan abubuwan da ya faɗi"
Ana iya rubuta wannan ta hanyar aiki. AT: "Harshe na iya haifar da rayuwa ko mutuwa" ko "Abin da mutane ke faɗi na iya haifar da rai ko mutuwa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "abokai da yawa - za su kawo shi ga lalacewa" ko "abokai da yawa - abokansa za su hallaka shi"
1Gara matalaucin mutum mai tafiya cikin mutuncinsa da mai maganar mugunta gashi kuwa wawa.2Kuma, ba shi da kyau a kasance da marmari ba tare da sani ba kuma wanda ke gudu da sauri yakan ɓata hanya.3Wautar mutum takan ɓata ransa zuciyarsa kuma tana fushi gãba da Yahweh.4Arziki na ƙara abokai da yawa, amma matalauci a ware ya ke da abokansa.5Mai shaidar zur ba zai tserewa hukunci ba mai furta ƙarairayi ba zai kuɓuta ba.6Mutane da yawa zasu roƙi tagomashi daga wurin mutum mai kyauta kuma kowanne mutum aboki ne ga mai bada kyautai.7Dukkan 'yan'uwan matalauci na ƙinsa; balle ma abokansa waɗanda suka yi nisa da shi! Ya kira su, amma sun tafi.8Wanda ya sami hikima yana ƙaunar ransa; wanda ya kiyaye fahimta zai sami abin da ya ke da kyau.9Mai shaidar zur ba zai tsere wa hukunci ba, amma mai furta ƙarairayi zai hallaka.10Bai dace da wawa ya zauna cikin daula ba - balle bawa ya yi mulki bisa 'ya'yan sarakuna.11Mutum mai sanin ya kamata yakan yi jinkirin fushi kuma daraja ce a gare shi ya ƙyale laifi.12Hasalar sarki na kama da rurin ɗan zaki, amma alherinsa na kama da raɓa a bisan ciyawa.13Wawan ɗa masifa ce ga mahaifinsa mace mai tankiya ɗiɗɗigar ruwa ne koyaushe.14Gida da dukiya ana gãdonsu daga iyaye, amma mace mai hankali daga wurin Yahweh take.15Ragonci kan jefa mutum cikin barci mai zurfi, amma wanda bai son aiki zai sha yunwa.16Wanda ya kiyaye doka ransa ya ke kiyayewa, amma mutumin da baya tunani game da al'amuransa zai mutu.17Duk mai jin tausayin fakirai yana bada rance ga Yahweh kuma zai sãke biyansa da abin da ya yi.18Ka hori ɗanka tun da sauran bege kuma kada ka ƙallafa ranka ga kashe shi.19Mutum mai zafin rai za ya ɗauki alhaki; idan ka cece shi, sai ka sake yi karo na biyu.20Ka saurari shawara ka karɓi koyarwa, domin ka iya zama mai hikima a ƙarshen rayuwarka.21Shirye-shirye masu yawa ke a cikin zuciyar mutum, amma manufar Yahweh ce zata tabbata.22Biyayya ce ya kamata mutum ya yi marmari kuma gara matalauci da maƙaryaci.23Girmama Yahweh yakan jagoranci mutane ga rai; wanda ke da shi zai gamsu ba abin da zai cutar da shi.24Rago yakan tsoma hannunsa cikin kwano; ba zai ko iya dawo da shi bakinsa ba.25Ka bugi mai ba'a, mutum marar wayau zai zama mai tattali; ka hori mai fahimta, zai kuma ƙaru da ilimi.26Wanda ya yi wa mahaifinsa fashi ya kuma kori mahaifiyarsa ɗa ne mai kawo kunya da zargi.27Idan ka daina jin koyarwa, ɗana, zaka ratse daga zantattukan ilimi.28Gurɓataccen mashaidi ya kan yi wa adalci ba'a bakin mugu yakan haɗiye laifi.29A kan shirya hallakarwa domin masu ba'a bulala kuma domin bayan wawaye.
"Zai fi kyau ka zama talaka"
Wannan yana nufin mutane suna ƙoƙari suyi wani abu ba tare da ilimin yadda ake yin sa dai-dai ba. AT: "don yin aiki tuƙuru ba tare da sanin abin da kuke yi ba"
Wannan yana magana ne game da mutum yana yin abu da sauri da yin kuskure kamar yana gudu da sauri da ɓacewa hanya. AT: "wanda yayi aiki da sauri yayi kuskure" ko "wanda yayi aiki da sauri yayi mummunan zaɓi"
Wannan yana nufin cewa mutumin da yake da wadata zai kasance yana da abokai da yawa domin dukiya tana jawo mutane. Cikakkiyar ma’anar wannan ana iya bayyana ta a sarari. AT: "Waɗanda ke da wadata a sauƙaƙe suna samun abokai da yawa"
Ana iya rubuta wannan ta ingantacciyar hanya. AT: "Lallai za su hukunta mai shaidar zur"
Wannan yana nufin cewa za a kama shi. AT: "za su kamo wanda ya fitar da k'arya"
Wannan jumlar ihun ce don nuna cewa wannan ya fi magana a baya. AT: "sabili da haka abokansa tabbas za su ƙi shi kuma su tafi nesa da shi!"
"Ba dai-dai bane"
yanayin wadata da jin daɗi
"Mutumin da yake da hankali yana jinkirin yin fushi"
Anan rurin zaki yana nufin kai hari. An kwatanta fushin sarki da rashin tabbas da haɗari na ƙaramin zaki. AT: "Fushin sarki yana da haɗari kamar harin ɗan zaki"
An kwatanta tagomashin sarki da ruwa mai wartsakewa wanda yake bayyana akan ciyawa da safe. AT: "amma alherinsa yana wartsakarwa kamar raɓa akan ciyawa" ko "amma ni'imarsa tana wartsakarwa kamar raɓa a ƙasa da safe"
Wannan yana magana ne game da matar da ke ba ta haushi kamar dai ita ce ɗimbin ruwa. AT: "matar da ke rikici tana da damuwa da rikicewa kamar diga ruwa a kai a kai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "'Ya'ya sun gaji gida da dukiya daga iyayensu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh yana ba mace mai hankali"
Wannan yana magana ne kan yadda lalaci ke sa mutum yin bacci mai yawa kamar lalaci da karfi ke jefa mutum cikin bacci. AT: "Kasala kan sa mutum bacci mai yawa" ko "Malalaci yana yawan bacci"
Yahweh ya ɗauki alherin da aka nuna wa talakawa a matsayin alheri da aka nuna masa. Daya daga cikin hanyoyin da mutane suke kyautatawa talaka shine ta hanyar bayarwa. AT: "Mutumin da ya ba matalauta yana bayarwa ga Yahweh"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan jimlar tana bayanin ladabtar da ɗanka. AT: "amma kada ku azabtar da shi da tsanani har ya mutu" ko 2) wannan jumlar tana bayanin yadda take idan ba ku hukunta ɗanku ba. AT: "domin idan ba ku hukunta shi ba kuna taimaka masa ya hallaka kansa"
Wannan karin magana yana nufin mutum mai saurin fusata. AT: "Mutumin da ba ya kame fushinsa" ko "Mutumin da ya yi saurin fushi"
Waɗannan jimlolin guda biyu ma'anarsu ɗaya ce kuma ana maimaita su don jaddada muhimmancin su.
"shirye-shiryen Yahweh"
Wannan yana nufin cewa zasu rayu tsawon lokaci idan suka girmama Yahweh. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "Waɗanda suka girmama Yahweh za su daɗe; duk wanda ya girmama Yahweh zai sami gamsuwa"
"idan ka ladabtar da mai hankali,"
Anan ana maganar "sauraro da biyayya" kamar "ji" ne. AT: "Idan kuka daina kula da umarni" ko "Idan kuka daina bin umarnin"
"za ku yi watsi da" ko "za ku juya baya"
Wannan yana magana ne akan yadda mugaye suke jin daɗin aikata mugunta ta hanyar cewa suna haɗiye mugunta cikin sauƙi kamar yadda suke haɗiye abinci. AT: "miyagu suna jin daɗin aikata mugunta kamar yadda suke jin daɗin cin abinci"
Kalmomin "la'anta" da "bulala" ana iya bayyana su azaman magana. AT: "Yahweh a shirye yake ya la'anci masu ba'a da bulala"
1Ruwan inabi mai ba'a ne barasa kuma mai tankiya ce; duk wanda ya kauce ta wurin sha marar hikima ne.2Tsoron sarki kamar tsoron ɗan zaki ne mai ruri; wanda yasa shi ya yi fushi zai rasa ransa.3Abin darajantawane ga kowanne mutum da ya kauce wa husuma, amma kowanne wawa yakan yi tsalle cikin jayayya.4Ragon mutum baya huɗa lokacin bazara; yakan nemi hatsi a lokacin girbi amma ba zai sami komai ba.5Shawara cikin zuciyar mutum tana kama da ruwa mai zurfi, amma mutum mai fahimta zai jawo ta waje.6Mutane da yawa suna shelar nasu alheri, amma mutum mai aminci wa ya iya samunsa?7Mutum mai aminci wanda ke tafiya cikin mutuncinsa, 'ya'yansa da suka bishi zasu zama masu albarka.8Sarkin da ya zauna a kan dakalin shari'a ya ke aikin alƙali da idanunsa ya ke sheƙar da dukkan muguntar da ke gabansa.9Wane ne zai ce, "Na tsabtace zuciyata; Ni tsarkakakke ne daga zunubina"?10Ma'auni daban-daban da mudun da ba dai-dai ba - Yahweh yaƙi su dukka.11Ko matashi a kan sanshi ta wurin ayyukansa, ko aikinsa mai tsabta ne ko dai-dai kuma.12Kunne mai ji da ido mai gani - Yahweh ne ya yi su dukka biyun.13Kada kaso barci domin kada ka talauce; ka buɗe idanunka da haka zaka sami isasshen abinci ka ci.14"Ba kyau! Ba kyau!" inji mai saye, amma sa'ad da ya tafi sai fahariya ya ke yi.15Akwai zinariya da duwatsu masu tsada, amma leɓuna masu sani duwatsu ne masu tamani.16Wanda ya tsayawa bãƙo ka karɓi rigarsa, ka karɓi jingina kuma daga hannun wanda ya tsayawa mace marar kintsuwa.17Gurasar da aka samu ta wurin yaudarar ɗanɗano mai daɗi ce, amma daga baya bakinsa zai cika da tsakuwa.18Shirye-shirye sukan kahu ta wurin shawara da jagorancin mai hikima kaɗai zaka yi yaƙi.19Mai tsegumi yakan bayyana asirai domin haka kada kayi hurɗa tare da mutane masu yawan magana.20Idan mutum ya la'anta mahaifinsa ko mahaifiyarsa, za a ɓice fitilarsa a cikin tsakiyar duhu.21Gãdon da aka samu cikin gaggawa da farko amma a ƙarshe ba zai zama da kyau ba.22Kada ka ce, "Zan rama wannan muguntar!" Ka jira Yahweh zai kuɓutar da kai.23Yahweh yana ƙin ma'aunin algus mizanan rashin gaskiya basu da kyau.24Al'amuran mutum Yahweh ke shugabantarsu; ta yaya zai fahimci tafarkinsa?25Tarko ne ga mutum ya yi magana cikin sauri, "Wannan abu mai tsarki," daga nan ya fara tunanin ma'anar bayan ya yi wa'adinsa.26Sarki mai hikima yakan sheƙe miyagu ya juyar da turmin chasa a kansu.27Ruhun mutum fitilar Yahweh ce, tana bincike dukkan sassan ciki.28Alƙawarin aminci da gaskiya suna tsare sarki; kursiyinsa an kintsa shi da ƙauna.29Ɗaukakar samari ƙarfinsu ne darajar tsofaffin mutane kuma furfurarsu ce.30Buge buge waɗanda ke sa rauni sukan tsarkake mugunta dũka kuma yakan sa sassan cikin jiki su tsarkaka.
Anan “ruwan inabi” na nufin mutumin da aka bugu da ruwan inabi. AT: "Mutumin da ya bugu da ruwan inabi"
Anan "abin sha mai ƙarfi" yana nufin mutumin da aka bugu da ruwan inabi mai ƙarfi. AT: "mutumin da ya bugu da ruwan inabi mai karfi ya fara faɗa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "duk wanda ya sha har sai sun kasa yin tunani mai kyau"
Wannan yana nufin kashewa. "Rayuwa" anan tana nufin rayuwar jiki. AT: "zai mutu"
"Abin girmamawa ne." Wannan yana nufin cewa za a girmama mutum.
Wannan yana magana ne game da shigar da gardama da sauri kamar dai gardamar wani abu ne da wawa ya tsallake ciki. AT: "kowane wawa da sauri ya shiga cikin jayayya" ko "kowane wawa yana saurin shiga cikin jayayya"
Wannan yana magana ne game da yadda yake da wahalar fahimtar dalilan ayyukan mutum ta hanyar kwatanta shi da wahalar kai wa ruwa a cikin rijiya mai zurfi. AT: "Yana da wuyar fahimtar manufa a cikin zuciyar ɗan adam kamar yadda yake isa ga ruwa a cikin rijiya mai zurfi" ko "Manufar da ke zuciyar mutum tana da wuyar fahimta"
Amsar a fakaice ita ce "'yan kaɗan ne za su iya samun irin wannan." Za a iya rubuta wannan tambayar ta magana a matsayin sanarwa. AT: "amma maza kalilan za su iya samun mutum mai aminci!" ko "amma yana da wuya a sami mutumin da gaske yake mai aminci!"
Anan tafiya tana nufin zama. Duba yadda kuka fassara wannan jumlar a cikin Misalai 19: 1. AT: "yana rayuwa ta mutuncinsa" ko "yana rayuwa mai gaskiya"
Wannan yana magana ne game da sarki yana hukunci tsakanin nau'ikan mugunta kamar yana raba su kamar yadda mutum yake busar hatsi. AT: "yana gani kuma yana rarrabe nau'ikan mugayen abubuwa da aka kawo gabansa"
Amsar a bayyane ga wannan tambayar ita ce, "Ba wanda zai iya faɗi haka." Za a iya rubuta wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Ba wanda zai iya cewa zuciyarsa tana da tsabta kuma ba shi da zunubi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane sun san saurayi ta hanyar ayyukansa"
"ko halayensa masu tsarki ne kuma masu gaskiya ko a'a"
Maganar "ku zo" a nan na nufin canzawa zuwa wani sabon yanayi; zama. AT: "zama talaka"
Anan mai siye yana sukar abin da wani ke siyarwa don samun ƙima daga gare shi. Bayan ya saya sai ya yi alfahari da kyakkyawan farashin da ya bi mai sayarwa don ya ba shi. Cikakkiyar ma’anar wannan ana iya bayyana ta a sarari. AT: "Ba kyau! Ba kyau!" in ji mai siye yana sukar kayan mai sayarwa, amma bayan ya siya sai ya tafi yana alfahari da ƙaramar farashin da ya biya"
Wannan yana magana ne akan darajar leɓunan ilimi ta hanyar kwatanta su da lu'ulu'u mai daraja. AT: "leɓunan ilimi suna da daraja kamar tsada mai tsada"
Lokacin bada lamuni, mai bada rancen zai dauki wani abu daga wanda ya karba, kamar tufa, a matsayin garanti na sake biya. Zai mayar dashi bayan an biya kudin. Idan mai karɓar bashi ya talauce sosai, wani zai iya ba wa mai rance wani abu a matsayin garanti a gare shi. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "Dauki tufa a matsayin tsaro daga wanda ya ba da tabbacin abin da baƙon ya ranta za a biya shi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Gurasar da wani ya samu ta hanyar yaudara"
Wannan yana magana ne game da dandano abinci mara dadi kamar dai bakinsa a zahiri cike yake da tsakuwa maimakon abinci. AT: "amma daga baya sai yaji kamar tsakuwa a bakinsa" ko "amma nan da nan sai yaji kamar yashi a bakinsa"
"bai kamata ka zama abokai da"
Wannan yana maganar mutum ya mutu kwatsam kuma ba zato ba tsammani kamar ransa fitila ce da aka kashe a cikin duhu. AT: "rayuwarsa zata ƙare kwatsam kamar hasken fitilar da aka kashe a cikin duhu" ko "zai mutu ba zato ba tsammani"
Wannan yana nufin aikata ba daidai ba ga wani saboda sun yi maka laifi. AT: "Zan hore ku"
Wannan yana nufin samun imani cewa Yahweh zai magance halin da ake ciki. AT: "Kuyi imani da Yahweh" ko "Bege ga Yahweh"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh yana jagorantar matakan mutum"
Amsar a fakaice ita ce ba zai iya fahimtarsa ba. Ana iya rubuta wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "saboda haka, mutum ba zai iya fahimtar hanyarsa ba"
Wannan yana magana ne game da sarki yana hukunta miyagu kamar yana tuƙa mashin ƙasa a kansu. AT: "yana azabtar da su sosai"
Wannan yana maganar ruhun mutum kamar fitila ce. Ruhun mutum yana taimaka masa ya fahimci abin da yake ciki. AT: "Yahweh ya ba mu ruhi don fahimtar zurfin kanmu, kamar yadda fitila ke sa ku gani a cikin duhu"
Za'a iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sarki yana kiyaye kansa ta hanyar kasancewa mai aminci da aminci ga alkawarin"
Anan “kursiyi” yana wakiltar ikon sarki na sarauta. Cikakken sunan "kauna" za a iya bayyana shi azaman magana. Hakanan, ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "sarki yana tabbatar da cewa zai yi mulki na dogon lokaci ta hanyar kaunar wasu"
Duk maganganun guda biyu suna da ma'ana ɗaya kuma ana maimaita su don ƙarfafawa. Amfani da ukubar jiki don gyara mutum ana maganarsa kamar mugayen ƙazanta ne kuma duka ya tsabtace shi. AT: "Bugun mutumin da ya yi ba daidai ba zai gyara shi kuma ya sa ya zama mutumin kirki"
1Zuciyar sarki kamar tafki ce mai gudanowa a cikin hannun Yahweh kuma yana juya shi a duk inda ya ga dama.2Kowanne mutum na ganin hanyarsa dai-dai ne a idanunsa, amma Yahweh ke auna zukata.3Aikata abin da ke dai-dai da gaskiya abin karɓa ne ga Yahweh fiye da hadaya;4Idanun masu fahariya da zuciya mai girman kai - fitilar mugaye - zunubi ne.5Shirye-shiryen mai himma na kai wa ne kaɗai ga wadata, amma duk mai yawan sauri zai kai ga talauci.6Tãra dukiya da harshe na ƙarya kamar tururi ne mai wucewa kuma tarko ne mai kashewa.7Ta'addancin masu mugunta zai kwashe su ya tafi, domin sun ƙi aikata abin da ke dai-dai.8Hanyar marar gaskiya karkatacciya ce, amma mai gaskiya na aikata abin da ke dai-dai.9Ya fiye a zauna laɓe a lungun ɗaki da a zauna ɗaki ɗaya da mace mai yawan faɗace-faɗace.10Ƙishin mugu na marmarin aikata mugunta; maƙwabtansa baya samun tagomashi a idanunsa.11Lokacin da aka yiwa mai ba'a horo, marar wayau na samun hikima, kuma idan aka bai wa hikima umarni, yana tara ilimi.12Mutum mai adalci na lura da gidan mutum mai mugunta; yana kawo masu mugunta zuwa ga bala'i.13Duk wanda ya hana wa kunnensa jin kukan matalauta, haka zai yi kuka, amma ba za a amsa masa ba.14Kyauta a ɓoye na kwantar da fushi kuma asirtacciyar kyauta na kauda hasala mai girma.15Lokacin da aka shar'anta gaskiya, tana kawo farincikin ga mutum mai adalci, amma tana kawo fargaba ga masu aikata mugunta.16Wanda ya kauce daga hanyar fahimta, za shi zauna a cikin taron matattu.17Duk wanda ke ƙaunar annashuwa za shi talauce; wanda ke ƙaunar ruwan inabi da mai ba zai wadata ba.18Mugun mutum abin fansa ne domin mai adalci, maci amana kuma abin fansa ne domin nagargarun mutane.19Ya fiye a zauna cikin hamada da a zauna tare da mata mai yawan faɗace-faɗace da fushi.20Zaɓaɓɓun dukiya da mai an ajiye su a mazaunin masu hikima, amma mutum marar wayo yana haɗiye su dukka.21Wanda ke aikata adalci yana kuma kyautatawa - wannan mutum ya sami rai, da adalci, da kuma ɗaukaka.22Mutum mai hikima na tsallake birnin masu iko, kuma yana rusar da ƙaƙƙarfan wurin da suka dogara da shi.23Duk wanda ya kiyaye bakinsa da harshensa yana tsare kansa ne daga wahala.24Mai girman kai da mutum mai fahariya - "Mai ba'a" ne sunansa - yana ayyukansa da girmankai na kumburi.25Sha'awar rago tana kashe shi, gama hannunsa na ƙin yin aiki.26Dukkan yini yana marmari yana ƙara marmari, amma mutum mai adalci yana bayarwa kuma baya hanawa.27Hadayar mugaye ƙazanta ce; ƙazantar na yawaita idan ya kawo su da miyagun manufofi.28Mai shaidar ƙarya zai hallaka, amma wanda ya yi sauraro za ya yi magana a dukkan lokaci.29Mugun mutum na mai da fuskarsa da tauri, amma mai adalci na dai-daita tafarkunsa.30Babu hikima, babu fahimta, kuma babu shawara da ke iya gãba da Yahweh.31Ana shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara ta Yahweh ce.
Marubucin yayi magana game da zuciyar sarki kamar dai itace ramin ban ruwa a cikin busasshen yanki wanda mutane ke jagorantar ruwa zuwa shuke-shuke da suke buƙata. AT: "Yahweh yana sarrafa zuciyar sarki kamar yadda mutum ke jagorantar ruwa don ban ruwa"
Idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. Marubucin yayi magana game da abin da mutum yake yi kamar dai mutumin yana tafiya ne a kan hanya. AT: "Kowane mutum yana tunanin cewa abin da ya yi mai kyau ne" ko "Kowane mutum yana yanke hukuncin abin da ya aikata a matsayin mai kyau"
"Yin mu'amala da mutane kamar yadda Yahweh yake so mutane suyi ma wasu mutane"
Kalmomin "idanu" da "zuciya" magana ne na mutum wanda ya ɗauki kansa mafi kyau fiye da sauran mutane kuma yana son sauran mutane su san shi. AT: "Mutanen da suke son wasu su yi tunanin sun fi wasu mutane"
Abubuwan da ke taimaka wa miyagu ana maganarsu a matsayin fitila. AT: "abubuwan da ke taimakon mugaye kamar fitila suna taimakawa wurin gani a cikin duhu"
Cikakken sunan “talauci” ana iya fassara shi azaman sifa. AT: "sai kawai ya zama talaka"
Harshen magana ne ga kalmomin da mutum ke amfani da harshe don magana. AT: "yin magana da ƙarairayi"
Marubucin ya kwatanta dukiyar da mutum yake samu ta hanyar yin ƙarya da hazo da ke saurin wucewa da safe. AT: "hazo mai ɓacewa"
Marubucin yayi magana kamar tashin hankali mutum ne wanda zai iya jan wasu mutane. Allah zai hukunta mugaye waɗanda suka cutar da maƙwabtansu marasa laifi.
Wannan yana kwatanta yadda mutum yake rayuwa zuwa karkatacciyar hanya wanda zai iya tafiya. Wannan karin magana ne. AT: "Yadda mai laifi yake rayuwa yana karkatacce"
Gidaje a wancan lokacin suna da rufin kwano. Isra'ilawa na dã suna amfani da lokaci mai yawa a saman rufinsu, inda sau da yawa yakan fi sanyi a cikin gida, kuma wani lokacin mutane sukan gina masauki da zai isa mutum ya kwana a ɗaya kusurwar rufin.
Marubucin yayi magana game da sha'awar mutum, sha'awar jiki don abinci da abin sha, kamar dai mutum ne mai iya sha'awar abu. Kalmar "mugaye" sifa ce ta zahiri wacce take nufin mutane mugaye, kuma kalmar "mugunta" kalma ce ta mara ma'ana wacce take nuni zuwa ga munanan ayyuka. AT: "Mugayen mutane suna son aikata mugunta kamar yadda suke son ci da sha"
Kalmomin idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunanin mutum da halayensa ga wani mutum. AT: "maƙwabcinsa ba ya karɓar alheri daga gare shi" ko "ba ya yin alheri ga maƙwabcinsa"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Idan wani ya hukunta mai izgili"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "yayin da wani ya umarci mai hikima"
A nan ana magana da ilimi kamar abu ne wanda wani zai iya riƙewa ya kiyaye wa kansa.
Wannan karin magana ne. AT: "Wanda ba zai saurara ba yayin da matalauta suka nemi taimako"
"yana sa mutum mai fushi ya ji daɗi don haka ya daina yin fushi"
Cikakken sunan "adalci" ana iya fassara shi azaman jimlar suna. Waɗannan kalmomin ana iya fassara su cikin aiki. AT: "Lokacin da masu mulki ke yin abin da yake dai-dai"
Wannan karin magana ne. AT: "baya rayuwa da hikima"
"zai kasance cikin taron matattun ruhohi"
mutumin da yake cutar da waɗanda suka aminta da shi ta hanyar ƙarya da kuma bautar ƙarya
"yana amfani da shi duka ba don kyakkyawar manufa ba" ko "ɓata shi"
"garin da jarumawa ke zaune a ciki" ko "garin manyan jarumawa"
"ganuwar da hasumiyoyin da ke kewaye da garin da ba su yi tsammanin wani zai iya wucewa cikin garin ba, don haka suka ji lafiya"
Duk “bakin” da “harshen” suna nuni ga abin da mutum yake faɗi. AT: "Duk wanda ya mai da hankali game da abin da yake faɗi"
"Kuna iya tsammanin mutane masu girman kai da girman kai suyi aiki da girman kai"
Marubucin yayi maganar abin da mutum yake so kamar mutum ne wanda zai iya kashe malalaci. A nan malalacin mutum yana so ya zama rago kuma ba ya aiki. AT: "Malalaci kawai yana son zama mara aiki, kuma saboda wannan zai mutu" ko "Malalaci zai mutu saboda baya son aiki"
Za'a iya bayyana jumlar "baya riƙewa" tabbatacce, kuma za'a iya bayyana abin da ya bayar bayyane. Madadin fassara: "yana ba da duk abin da ya kamata" ko "yana bayarwa da karimci"
Marubucin bai ambaci Yahweh a nan ba, kamar yadda yake a Misalai 15: 8, amma ya kamata mai karatu ya fahimci cewa Yahweh ne yake ƙin hadayar miyagu.
Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) "yi kamar ya nuna ƙarfin hali" ko 2) "ba zai saurari gyara ba."
Ana magana akan ayyukan mutum kamar wata hanya ce da mutum yake tafiya akanta. AT: "ya tabbata game da abin da ya aikata" ko "yana da kwarin gwiwa game da abin da ya aikata"
Kalmomin "akwai" an maimaita su ne don jaddada sunayen suna "hikima," "fahimta," da "shawara." Yahweh ya fi duk abin da kowa zai iya sani ko tunani ko faɗi. Yarenku na iya buƙatar kada ku maimaita "babu babu." Ana iya fassara sunayen mara amfani a matsayin sifa ko kalmomin aiki. AT: "Babu wani mai hikima, babu wanda ya fahimci komai, kuma babu wanda zai gaya wa wasu abin da za su yi wanda" ko "Babu hikima, fahimta, ko shawara cewa"
"kayar da Yahweh" ko "aiki ga abin da Yahweh yake so ya yi" ko "nuna cewa yana da gaskiya kuma Yahweh ba daidai ba ne"
Waɗannan kalmomin ana iya fassara su cikin aiki. AT: "Sojoji suna shirya dawakai don ranar yaƙi"
1Zaɓen suna mai kyau ya fi wadata mai yawa kuma tagomashi ya fi azurfa da zinariya.2Wannan na faruwa da masu arziƙi da matalauta - Yahweh ne mahallicinsu dukka.3Mutum mai ƙwazo na hangen wahala ya kuma ɓoye kansa, amma marasa cikakkiyar kula na wucewa har ga wahala.4Ladan tawali'u da tsoron Yahweh arziƙi ne, da ɗaukaka, da kuma rai.5Ƙayayuwa da tarkuna suna kan hanyar bijirarru; duk wanda ya kiyaye ransa zai yi nisa da su.6Ka koya wa yaro hanyar da zai bi kuma idan ya manyanta ba zai kauce daga wannan umarnin ba.7Masu arziki ne ke mulkin matalauta kuma mai cin bashi bawa ne ga mai bada bashi.8Shi wanda ya shuka rashin adalci za shi girbi masifa kuma sandar hasalarsa zata ƙare.9Shi wanda ke da ido na hannu sake za shi yi albarka, gama yana raba gurasarsa da talakawa.10Ka kori mai ba'a, husuma zata fita; faɗace-faɗace da zage-zage zasu ƙare.11Shi wanda ke ƙaunar tsabtacciyar zuciya wanda kuma kalamansa masu alheri ne, za shi zama abokin sarki.12Idanun Yahweh na bisa ilimi, amma yana rusar da maganganun maci amana.13Ragon mutum ya ce, "Akwai zaki a kan hanya! Za a kashe ni a buɗaɗɗun filaye."14Bakin karuwa rami ne mai zurfi; Fushin Yahweh na gãba da duk wanda ya faɗi cikinta.15Ana samun wawanci a zuciyar ɗan yaro, amma sandar horo na korarsa da nisa.16Wanda ke zaluntar matalauta don ya tara dukiyarsa, ko ya baiwa mutane masu arziki, zai talauce.17Ka kusanto da kunnuwanka ga maganganun masu hikima ka kuma miƙa zuciyarka ga ilimina,18gama zata zamar maka abin daɗi, idan ka adana su cikinka, idan dukkansu suna shirye cikin leɓunanka.19Domin dogararka ta kasance cikin Yahweh, na koyar da su gare ka yau - lallai a gare ka.20Bana rubuta maka talatin maganganun na umarni da ilimi bane,21domin na koyar da kai waɗannan amintattun maganganu, dominn ka bayar da amintattun amsoshi ga waɗanda suka aike ka ba?22Kada ka cuci matalauci wai don shi matalauci ne, ko ka murƙushe mabuƙaci a bakin ƙofa,23gama Yahweh zai yi magana a madadin su, kuma zai ƙwace ran wadda ya cuce su.24Kada ka yi abokantaka da wanda fushi ke mulkinsa kuma kada ka yi tafiya da wanda ke hucin fushi,25in ba haka ba zaka koyi halayensa da haka zaka ɗana wa ranka tarko.26Kada ka zama wanda ke buga hannu don ɗaukar alƙawari, ko mai tsayawa a madadi na basussuka.27Idan ka rasa hanyar biya, me zai hana wani ya ɗauke gadonka daga gare ka?28Kada ka matsar da dutsen iyaka na dã wanda ubanninka suka sa.29Ko ka ga mutum ƙwararre ga aikinsa? Zai tsaya a gaban sarakuna; ba zai tsaya a gaban mutane marasa daraja ba.
Waɗannan kalmomin ana iya fassara su cikin aiki. AT: "Ya kamata mutum ya zaɓi suna mai kyau maimakon wadata mai yawa"
"Samun wasu suyi tunanin daya mutumin kirki ne"
"Mutum mai hikima". Duba yadda aka fassara "mai hankali" a cikin Misalai 12:15.
Marubucin yayi magana akan yadda mutane karkatattu suke rayuwa kamar dai hanya ce da masu karkacewa zasu sami matsala akan "ƙaya" da kuma "tarko" da mutum yayi.
Ana magana da mutumin da yake yin abin da ya kamata don ya rayu tsawon lokaci kamar wannan mutumin yana hana ɓarayi nesa da wani abu na zahiri. AT: "mutanen da suke son rayuwa na dogon lokaci"
Marubucin yayi maganar mai mulki ko wani mutum mai iko yana zaluntar waɗanda basu da ƙarfi sosai kamar yana shuka iri wanda zai haifar da shuke-shuke da zai kawo matsala. AT: "Idan mutum ya bi da waɗanda ba su da ƙarfi fiye da shi ba da adalci, za su jawo masa matsala daga baya"
Kalmar "sanda" magana ne ta iko akan sauran mutane. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) azzalumin mai mulki zai rasa ikon da yake da shi wanda ya ba shi damar mu'amala da wasu mutane ba daidai ba ko 2) lokacin da mutane suka amsa zaluncin da ya yi ta cutar da shi, ba shi da ikon hana su. AT: "ba zai sake samun ikon da yake amfani da shi ba don cutar mutane"
Waɗannan kalmomin ana iya fassara su cikin aiki. AT: "Allah zai albarkaci wanda yake da ido mai karimci"
Ido wani magana ne da ake amfani da shi don ganin abin da sauran mutane ke buƙata, kuma "idaka mai karimci" ba wai kawai tana gani ba amma yana ba da abin da sauran mutane suke buƙata. Ido ma magana ne ga dukkan mutum. AT: "mai karimci" ko "mutumin da ke shirye ya bayar da abubuwa ga wasu mutane"
Zuciyarsa ce mutum yake so ya zama mai tsabta. Zuciya magana ne ga mutum. AT: "yana son samun tsarkakakkiyar zuciya" ko "yana son zama mai tsabta"
Idanun na nufin mutum. Marubucin yayi magana kamar dai Yahweh yana da idanu na zahiri kamar mutum. AT: "Yahweh yana sa ido" ko "Yahweh yana kiyaye ilimi"
Maganganun da ke biye ƙarya da uzuri ne na rashin aiki. Idan yarenku yana gabatar da bayanan karya ta hanya ta musamman, zaku iya amfani da hakan anan.
Kalmar "baki" magana ne ga kalmomin da ke fitowa daga bakin. Marubucin yayi maganar mutum ya kasa tserewa yayin da mutane suka hukunta shi saboda ayyukan mugunta kamar dai mutumin ya faɗa cikin ramin da wani ya haƙa a cikin ƙasa wanda ba zai iya tserewa ba. AT: "Kalmomin da mazinaciya ke faɗi za su jawo ku ciki, kuma zai zama kamar kun faɗa cikin rami mai zurfi da haɗari"
Anan "zuga" yana nufin cewa fushinsa ya ƙaru. AT: "Yahweh yana fushi"
"Zuciyar yaro cike take da wauta"
Marubucin yayi magana game da iyaye ta amfani da kowane irin horo kamar dai wannan iyayen suna doke yaro da sandar katako.
Marubucin yayi magana kamar wauta mutum ce wanda wani mutum zai iya amfani da sandar jiki ya kore shi. AT: "zai sa yaro ya zama mai hikima"
Aya ta 17 ta fara gabatarwa zuwa wani sabon sashi na Littafin Misalai.
Anan kalmar "kunne" tana wakiltar mutumin da yake sauraro. Marubucin yayi maganar saurarawa da kyau ga wani kamar yana jingina ne don kunne ya kusanci wanda yake magana. Duba yadda ka fassara "karkata kunnenka" a cikin Misalai 4:20. AT: "Kula da saurara" ko "Saurara sosai"
"me mutane masu hikima ke faɗi"
Ana magana da mutumin da yake shirin magana kamar dai kalmomin ne da suke a shirye. AT: "kuna iya magana game da su a kowane lokaci"
Wadannan ayoyin suna ci gaba da kawo karshen gabatarwar da ta fara a Misalai 22:17.
Wannan tambaya ya fara da kalmomin "Shin ban rubuta ba" a cikin Misalai 22:20. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Ya kamata ku sani cewa na rubuta ... don koya muku ... wanda ya aiko ku." (Duba:
Wasu fassarorin sun karanta, "kyawawan maganganu."
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Idan yarenku yana da hanyar nuna cewa wannan ita ce hanyar da wani zai yi magana mai karfi ga wani, ya bambanta da dokar gama gari da ya kamata mutane su bi, ya kamata ku yi amfani da ita a nan.
Kalmomin na lauyan da ke kare mabukata ne a gaban alkali. AT: "Yahweh zai kare mabukata daga wadanda ke zaluntar su" ko "Yahweh zai ga cewa mabukata sun sami adalci"
Yahweh ba ɓarawo bane, amma kamar ɓarawo zai karɓi rai daga waɗanda ba su zaɓi su ba ta ba. AT: "zai hallaka waɗanda ke zaluntar talakawa"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
wani wanda ba zai iya kame fushinsa ba
Mutumin da yake so ya zama kamar mai fushi kamar dabba ne yake kama tarko a cikin tarko. AT: "za ku zama kamar dabbar da ta cinye tarko wanda ya rufe tarko kuma ya kasa tserewa"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Mutum zai bugi hannunsa a hannun wani don ya ɗaure kansa don yin abin da ya yarda ya yi. Anan mai maganar yana faɗakar da mai sauraro kada ya ɗora hannu a matsayin wata hanya ta alkawarin biyan bashin wani.
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Wannan tambayar umarni ce. AT: "Kuyi tunanin wani wanda kuka sani wanda ya kware a aikinsa"
1A lokacin da ka zauna cin abinci da mai mulki, ka kula da kyau abin da a ka ajiye a gaban ka,2ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka idan fa kai wani ne mai yawan son cin abinci mai yawa.3Kada ka yi marmarin kayan kwaɗayinsa, gama abincin ƙarya ne.4Kada ka wahalar da kanka garin neman arziki; ka sami hikimar sanin lokacin da ya kamata ka huta.5Ko zaka bar idanuwanka bisa arziki? Zai watse, gama lallai za shi ɗauki fuka-fukai kamar gaggafa ya tashi sama.6Kada ka ci abincin wanda ke da mugun ido - kuma kada ka yi marmarin kayan kwaɗayinsa,7gama shi irin mutum ne da ke ƙirgen farashin abincin. "Ka ci ka sha!" yana ce maka, amma zuciyarsa bata tare da kai.8Za ka yi aman abin da ka ci kuma kalaman abokancin ka su tafi a banza.9Kada ka yi magana a gaban wawa, gama zai rena hikimar maganganunka.10Kada ka matsar da daɗaɗɗen dutsen iyaka ko ka shige gonar marayu,11gama mai Fansarsu na da ƙarfi kuma zai yi magana a madadin su gãba da kai.12Ka kafa zuciyar ka ga umarni kuma kunnuwanka ga maganganu na ilimi.13Kada ka ƙi yiwa yaro umarni, gama idan ka yi masa horo, ba zai mutu ba.14Kai ne ya zama dole ka doke shi da sanda ka kuma ceci ransa daga Lahira.15Ya ɗa na, idan zuciyarka na da hikima, da haka kuma zuciyata za ta yi murna;16can cikin zuciyata za ta yi farinciki lokacin da leɓunan ka suka furta abin da ke dai-dai.17Kada ka bar zuciyarka ta yi kishin masu zunubi, amma ka ci gaba da tsoron Yahweh dukkan rana.18Tabbas akwai gobe kuma ba za a datse begen ka ba.19Ka ji - kai! - ɗa na, ka sami hikima ka kuma bida zuciyarka a hanyar.20Kada ka yi abokantaka da mashaya, ko masu cin abinci fiye da kima,21gama da mashayi da marar horo ga ci suna zama matalauta kuma gyangyadi za shi suturce su da tsummokara.22Ka saurari mahaifin ka wanda ya haife ka kuma kada ka rena mahaifiyar ka sa'ad da ta tsufa.23Ka sayi gaskiya, amma kada ka sayar da ita; sayi hikima, da umarni, da kuma fahimta.24Mahaifin mutum mai adalci za shi yi farinciki, kuma duk wanda ya haifi yaro mai hikima za shi yi murna dominsa.25Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna kuma bari ita da ta haife ka ta yi farinciki.26Ɗana, ka ba ni zuciyarka kuma bari idanuwanka su kula da hanyoyi na.27Gama karuwa rami ne mai zurfi, kuma mace mai gurɓataccen hali rijiya ce ƙuntacciya.28Tana kwanciya kamar ɗan fashi tana kuma barbaza yawan munafunci cikin 'yan adam.29Wa keda waiyo? Wa ke da kaito? Wa keda faɗace-faɗace? Wa ke ƙorafi? Wa keda raunuka babu dalili? Wa keda jajayen idanuwa?30Waɗanda suka daɗe da ruwan inabi, waɗanda suka gwada gaurayayyen ruwan inabi.31Kada ka dubi ruwan inabi sa'ad da ya yi ja, lokacin da ya ke kumfa a cikin moda yana kuma kwararowa ƙasa a hankali.32A ƙarshe zai yi sãra kamar maciji ya kuma yi harbi kamar kãsa.33Idanunka zasu ga baƙon abubuwa kuma zuciyarka za ta furta gurɓatattun abubuwa.34Za ka zama kamar wanda ke kwanciya bisa tekuna ko kwantawa bisa rufin jirgi.35"Sun buge ni," za ka ce. "amma ban ji ciwo ba. Sun buge ni, amma ban ji zafi ba. Har yaushe zan farka? Zan nemi wani abin shan."
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Mai yiwuwa wannan kalmomin su ne 1) "yi hankali sosai kada ku ci da yawa" ko 2) "kada ku ci komai"
Wannan karin magana ne. AT: "yana baku shi ne don ya yaudare ku"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
"Kada ku yi aiki da yawa har ku gaji kullum"
Ana maganar mutumin da ya rasa dukiyarsa kamar arzikin tsuntsu ne. AT: "wadatar zata gushe da sauri kamar gaggafa zata iya tashi"
Wannan karin magana ne. AT: "da gaske ba ya son ku more abincin"
Wannan karin gishiri ne don fatan mutum bai ci komai ba. AT: "Za ku yi fatan da ba ku ci komai ba"
Ana maganar yabo kamar suna abubuwa masu mahimmanci. Cikakken sunan "yabo" ana iya fassara shi azaman aiki. AT: "ba zai yi farin ciki ba ko da kuwa kun faɗi kyawawan abubuwa game da shi da abincin"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Cikakken sunan "ji" ana iya fassara shi azaman aiki. AT: "inda wawa zai ji ku"
Kalmomin na lauyan da ke kare mabukata ne a gaban alkali. AT: "zai kare marayu a kanku" ko "zai ga cewa marayu sun sami adalci kuma sun hukunta ku"
Wannan karin magana ne. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Misalai 22:17. AT: "Yi iyakar ƙoƙarinku don fahimta da tunawa"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Cikakken sunan "wa'azi" ana iya fassara shi azaman aiki. AT: "Kada ku yi watsi da koyar da yaro" ko "Kada ku ƙi koya wa yaro"
Babu wani da zai yi hakan. Mai sauraro ne ke da alhakin ceton ran yaron daga Lahira, kuma hanyar da za a cece shi ita ce ta doke shi.
"Leɓunan ka" na nufin mutum dukka. AT: "lokacin da kuke magana"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Kalmar "zuciya" magana ne ga dukka mutum. AT: "Kada ku yarda ku hassada ga masu zunubi" ko "Tabbatar da cewa ba ku kishin masu zunubi"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ba zai bar kowa ya yanke begenku ba" ko "Allah zai cika alkawuran da ya yi muku"
Yanke shawarar yin abin da ke daidai ana magana ne kamar mutum ɗaya yana nuna wa wani hanyar da ta dace ya bi. AT: "ku tabbata kun yi abin da ya dace"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "mutanen da suka ci nama fiye da yadda suke buƙata" ko 2) "nama" yana wakiltar abinci ne gaba ɗaya. AT: "mutanen da suka ci abinci fiye da yadda suke buƙata"
Kalmar "barci" karin gishiri ne ga mutum yana ciyar da lokaci mai yawa yana jin daɗin abinci da abin sha har ba ya yin aikin da ya dace. Ana magana akan wannan aikin kamar iyaye ne da ke sanya sutura a kan yaro. AT: "saboda sun bata lokaci mai yawa suna ci da sha, ba zasu yi wani aiki ba don haka zasu zama matalauta"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Wata ma'ana mai yiwuwa ita ce "Sayi gaskiya, kuma kada ku sayar da hikima, wa'azi, ko fahimta." Kalmomin "gaskiya," "hikima," "wa'azi," da "fahimta" sunaye ne waɗanda ba a cika magana ba waɗanda ake maganarsu kamar abubuwa ne na zahiri da mutum zai iya saya ya sayar a kasuwa. Ana iya fassara su azaman kalmomin aiki. AT: "Yi abin da ya kamata ka yi don ka san abin da ke gaskiya, don haka ka zama mai hikima, don ka iya koyon yadda ake aiki, don haka za ka iya faɗin abu mai kyau da mara kyau; kada ka taɓa tunanin wani abu da ya fi muhimmanci wadannan abubuwan "
Wata ma'ana mai yuwuwa ita ce kalmomin "wanda ya haifi ɗa mai hikima" ya bayyana wane ne "mahaifin mai adalci". AT: "Mahaifin adali, wanda ya haifi ɗa mai hikima, zai yi farin ciki matuƙa kuma ya yi farin ciki da shi."
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Kalmar "zuciya" magana ne ta abin da mutum yake tunani da yanke shawarar aikatawa. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "a kula sosai" ko 2) "a amince da ni gaba ɗaya."
Idanun ido ne na mutum gaba ɗaya. AT: "ku kiyaye" ko "duba a hankali"
Yin magana game da aikata mugunta wanda za a azabtar da shi ana magana da shi kamar faɗawa cikin kunkuntar wuri wanda ba zai iya tserewa ba. AT: "Kwanciya da matar wani mutum kamar fadowa ne cikin kunkuntar rijiya"
Marubucin yayi amfani da waɗannan tambayoyin don shirya mai karatu ga batun da yake shirin yi game da wani nau'in mutum. Ba ya fatan amsa ga kowace tambaya. Yarenku na iya samun wata hanyar daban ta gabatar da darasi. AT: "Ku saurare ni yayin da nake gaya muku wane irin mutum ne yake da kaito, baƙin ciki, faɗa, gunaguni, raunuka ba tare da dalili ba, da zubda jini."
Waɗannan kalmomin suna amsa tambayoyin da ke a aya ta 29 kuma suna bayyana mutanen da ke shan ruwan inabi da yawa.
Kalmar "shi" tana nufin "ruwan inabin lokacin da yake ja." "Cizon" da "harbi" kwatanci ne na yadda yawan shan ruwan inabi ke sa mutane su ji. AT: "yana sa ka baƙin ciki kamar maciji ya sare ka ko kuma wani adder ya sakar maka"
“Zuciya” tana wakiltar mutumin kuma tana nanata abin da yake tunani da kuma shawarar da zai yanke. AT: "zaku yi tunani kuma ku yanke shawarar yin abubuwa masu karkatattu"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20). Cigaban bayanin mai shaye shaye ne.
Za'a iya bayyana wurin a kan rufin jirgi din da mutum yake kwance. AT: "yana kwance cikin kwandon a kusa da saman rufin jirgi"
Saboda mai maye baya tunani sosai, yana tunanin mutane suna dukanshi da duka, duk da haka baya jin zafi kuma baya iya tuna komai.
Mai shaye shaye yana tunanin yaushe zai sake nutsuwa; lokacin da tasirin giya zai daina.
1Kada ka yi ƙyashin masu aikata mugunta, ko ka yi marmarin yin abokantaka da su,2domin zuciyarsu na ƙirƙiro da ta'addanci kuma leɓunansu na zancen rigima.3Ta wurin hikima a ke gina gida ta wurin fahimta a ke kafa shi.4Ta wurin ilimi a ke cika ɗakunan da dukkan dukiya masu tamani da daraja.5Jarumi mai hikima na da ƙarfi, kuma mutum mai ilimi na ƙara ƙarfinsa;6domin ta wurin shawara na hikima zaka yi yaƙi kuma cikin shawarwari masu yawa akwai nasara.7Hikima na da tsawo ga wawa; a bakin ƙofa ba ya buɗe bakinsa.8Akwai wani wanda ke shirin aikata mugunta - mutane na kiransa shugaban dabaru.9Wawan shiri zunubi ne kuma mutane na ƙyamar mai ba'a.10Idan ka yi sanyi sabili da tsoro a ranar wahala, to ƙarfinka ƙalilan ne.11Ka ƙwaci waɗanda aka ɗauke ga mutuwa ka kuma hana waɗanda ke gangarawa zuwa yanka.12Idan ka ce, "Duba, ba mu san da komai game da wannan ba," shi wanda ke auna zuciya ba ya fahimci abin da kake faɗa ba? Wanda ke tsaron ranka, ba yana sane da haka ba? Allah ba zai saka wa kowanne abin da ya cancance shi ba?13Ya ɗana, ka ci zuma domin yana da kyau, domin ɗigo-ɗigon sakar zuma na da zaƙi a bakin ka.14Haka hikima take ga ranka - Idan ka same ta, gobe tabbas ne kuma begen ka baza a katse shi ba.15Kada ka yi kwanto kamar mugun mutum wanda ke kai farmaki ga gidan mutum mai adalci. Kada ka lalatar da gidansa!16Gama mutum mai adalci na faɗuwa ƙasa sau bakwai ya tashi kuma, amma ana kãda mugayen mutane ƙasa da bala'i.17Kada ka yi farinciki sa'ad da maƙiyin ka ya faɗi kuma kada zuciyarka ta ji daɗi sa'ad da ya yi tuntuɓe,18domin Yahweh zai gani ya kuma bayyana rashin yardarsa ya kuma juyar da hasalarsa daga gare shi.19Kada ka da mu saboda masu aikata mugunta, kuma kada ka yi ƙyashin mugayen mutane,20gama mugun mutum ba shi da tabbaccin gobe kuma fitilar mugaye za ta ɓice.21Ka ji tsoron Yahweh, ka kuma ji tsoron sarki, ya ɗana; kada ka yi abokantaka da waɗanda suka tayar masu,22gama ba zato azaba zata auko kuma wa ya sani girman lalatar da zata zo daga dukkan su biyun?23Haka ma waɗannan maganganu ne na masu hikima. Nuna bambanci cikin shari'a ba abu ne mai kyau ba.24Duk wanda ya cewa mugun mutum, "Kai mutum mai adalci ne," mutane zasu la'anta shi al'ummai kuma zasu ƙi shi.25Amma waɗanda suka hori mai mugunta zasu sami jin daɗi kuma kyautai na alheri zasu zo gare su.26Wanda ya ba da amsa mai kyau yana bada sumba ga leɓuna.27Ka shirya aikinka na waje, ka kuma shirya wa kanka komai cikin fili; bayan haka, sai ka gina gidanka.28Kada ka zama shaida gãba da maƙwabcinka babu dalili kuma kada ka ruɗar da leɓunanka.29Kada ka ce, "Zan yi masa abin da ya yi mani; Zan sãka masa abin da ya yi."30na ratsa ta cikin filin rãgo, ta gonar inabi na mutumin da ba shi da hankali.31Duk ƙayayuwa sun rufe ko'ina, ƙasar ta cika da sarƙaƙiya, kuma ganuwarta ta dutse ta rushe.32Sai na gani na kuma yi lura da ita; na duba na kuma karɓi umarni.33Yin barci kaɗan, da ɗan gyangyaɗi, da ɗan naɗe-naɗen hannuwa domin hutu -34da haka talauci za shi saukar maka, kuma buƙatarka kamar soja mai makami.
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Kalmomin "zukatansu" suna nuni ne ga mutum duka. AT: "su"
Cikakken sunan 'hikima' ana iya fassara shi azaman sifa. Waɗannan kalmomin ana iya fassara su cikin aiki. AT: "Mutane suna bukatar hikima idan zasu gina gida mai kyau"
Cikakken sunan "fahimta" ana iya fassara shi azaman aiki. Waɗannan kalmomin ana iya fassara su cikin aiki. AT: "Mutane suna buƙatar fahimtar abin da ke da kyau a ɗabi'a da kuma abin da ke muguwar ɗabi'a idan za su kafa gida"
Cikakken sunan "ilimi" ana iya fassara shi azaman aiki. Waɗannan kalmomin ana iya fassara su cikin aiki. AT: "Mutane suna bukatar sanin abin da ke da tamani da kuma daɗi idan za su cika dakunan su"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Cikakken sunan "hikima" ana iya fassara shi da "mai hikima." AT: "mai hikima jarumi"
Ana iya fassara sunayen suna "ilimi" da "ƙarfi" azaman kalmar aikatau "sani" da kuma ma'anar "ƙarfi." AT: "mutumin da ya san abubuwa da yawa ya fi ƙarfi saboda ya san waɗannan abubuwa"
Wannan karin magana ne. AT: "mawuyaci ne ga wawa ya fahimta"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
wanda ya kware wajan shirya mugunta. AT: "maƙerin mutum" ko "mai kawo matsala"
Wannan karin magana ne. AT: "kuna da ƙarancin ƙarfi" ko "lallai ku masu rauni ne"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Waɗannan kalmomin ana iya fassara su da yanayi ta aiki ta amfani da kalmar "su" wanda zai iya zama kowa, amma tabbas jami'an gwamnati ne. AT: "waɗanda suke ɗauka"
Marubucin yana ɗaukar masu karatu sun san amsar kuma sun nemi wannan don ƙarfafawa. AT: "wanda ya auna zuciya ya fahimci abin da kuke fada."
Marubucin yana ɗaukar masu karatu sun san amsar kuma sun nemi wannan don ƙarfafawa. AT: "Wanda ya kiyaye rayuwarku ya san shi."
Marubucin yana ɗaukar masu karatu sun san amsar kuma sun nemi wannan don ƙarfafawa. AT: "Allah zai ba kowane ɗayan abin da ya cancanta."
Mai yiwuwa ma'anoni sune 1) za'a iya fassara ta azaman aiki. AT: "babu wanda zai cire begenku" ko 2) za'a iya fassara su da kyakkyawar siga. AT: "Tabbas fatan ku zai ci gaba"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Kalmomin "kwanto cikin jira" karin magana ne. Fassara "kwanto kwanto" kamar yadda yake a cikin Misalai 1:11. AT: "Kada ku ɓoye ku jira lokacin da ya dace"
Marubucin yayi magana kamar "bala'i" mutum ne wanda zai iya aikata mummunan abu ga wasu mutane. Waɗannan kalmomin ana iya fassara su cikin aiki. AT: "Allah zai yi amfani da masifa don saukar da azzaluman mutane"
"wani mummunan abu ya faru ga makiyinka"
Wannan umarni ne mai ƙarfi. Kalmar nan “zuciya” tana wakiltar mutumin. AT: "kar ka yarda ka yi farin ciki" ko "ka hana kanka farin ciki"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da "maganganu talatin" (Misalai 22:20).
Ana amfani da fitilar a matsayin kwatancin rayuwa. Rayuwar mugaye zata ƙare kamar yadda fitila ke kashewa.
Marubucin yayi wannan tambayar don jaddada bala'i. AT: "babu wanda ya san irin ɓarnar da za ta zo daga su biyun."
Wannan jumla ta fara sabon tarin misalai.
Kalmar "al'ummai" magana ne na nufin mutanen da ke zaune a cikin al'ummai. Waɗannan kalmomin ana iya fassara su cikin aiki. AT: "Mutane za su la'anta duk wanda ya ce wa mugu, ..., kuma mutanen wasu ƙasashe za su ƙi shi "
Ana magana akan kyautai kamar mutane ne da zasu iya motsawa da kansu. Cikakken sunan "kyautatawa" za a iya fassara shi azaman sifa. AT: "mutane zasu basu kyautuka masu kyau"
Sumba alama ce ta girmamawa da sadaukarwa a cikin wannan al'adar. AT: "yana nuna abokantaka ta gaskiya"
Lebe alama ce ta kalmomin da mutum zai yi magana da su. AT: "ta abin da kuka ce"
Wannan karin magana ne. "yi masa fansa"
tsire-tsire waɗanda aka rufe su da ganyayen harbawa da gashi
"ya faɗi ƙasa"
"koyi darasi"
Wasu fassarorin sun karanta, "talauci ya same ku kamar ɗan fashi." Ana maganar talauci kamar mutum ne ko dabba da za su iya faɗa wa rago.
Ana magana akan buƙatu kamar mutane ne waɗanda zasu iya kai hari ga malalacin. AT: "bukatunku zasu zo muku kamar sojan da ke dauke da makamai"
1Waɗannan ƙarin karin magana na Suleman ne, wanda mutanen Hezekiya, sarkin Yahuda suka kwafa.2Ɗaukaka ta Allah ce ya ɓoye zance, amma ɗaukakar sarakuna su bincike shi.3Kamar yadda sammai suke da tsayi duniya kuma tana da zurfi, haka zuciyar sarakuna sun wuce gaban ganuwa.4Ka sheƙe azurfa gwani kuma za shi yi amfani da azurfar ga aikinsa.5Haka ma, ka cire mugayen mutane daga gaban sarki kursiyinsa kuma zai kafu ta wurin aikata adalci.6Kada ka ɗaukaka kanka a gaban sarki kada kuma ka zauna a mazaunin da aka shirya wa mutane masu daraja.7Ya fi kyau shi da kansa ya ce maka, "Hauro zuwa nan," da shi ya kunyatar da kai a gaban mutum mai daraja. Abin da ka yi shaidar sa,8kada ka yi saurin kawo shi ga shari'a. Gama me zaka yi a ƙarshe idan maƙwabcinka yasa ka cikin kunya?9Ka yi jayayya bisa matsala tsakaninka da maƙwabcinka da kansa kada kuma ka fallasa wani asirin,10domin kada wanda ya ji ka yasa ka ji kunya kuma mugun rohota a kanka da ba za a iya tsayarwa ba.11'Ya'yan itacen aful na zinariya da aka yi masu jerin azurfa kamar magana ce da aka yi ta dai-dai.12Zobe na zinariya ko sarƙar da aka yi ta da zinariya mai kyau horo ne na hikima ga kunnuwan mai sauraro.13Kamar yadda sanyin ƙanƙara ya ke lokacin girbi haka ɗan aike mai aminci ke ga waɗanda suka aike shi; yana dawo da ran shugabanninsa.14Giza-gizai da iska amma babu ruwan sama ne wanda ke fahariya da kyautar da bai bayar ba.15Cikin hakuri ake rinjayar mai mulki kuma harshe mai taushi na iya karya ƙashi.16Idan ka sami zuma, kada kayi masa shan fitar hankali - in ba haka ba, idan ka sha dayawa, za ka amayas.17Kada ka cika zuwa gidan maƙwabcinka, yana iya gajiya da kai ya kuma ƙi ka.18Mutumin da ya yi shaidar ƙarya bisa maƙwabcinsa na kama da kulkin da aka yi amfani da shi a yaƙi, ko takobi, ko wani mãshi mai tsini.19Mutum marar amincin daka amince da shi a lokacin wahala na kama da ruɓaɓɓen haƙora ko tafiya da gurguwar ƙafa.20Kamar mutumin da ya kwaɓe rigarsa a yanayi mai tsananin sanyi, ko zuba inabi bisa ainihin gawayi na soda, haka wanda ke yin waƙoƙi ga zuciya mai nauyi.21Idan makiyinka na jin yunwa, ba shi abinci ya ci, idan kuma yana jin ƙishi, ba shi ruwa ya sha,22gama zaka tula masa tarin garwashin wuta a bisa kansa Yahweh kuma zai baka lada.23Kamar yadda iskar arewa ke kawo ruwan sama, haka take da harshen da ke faɗin asirai yana hadasar da fuskoki masu fushi.24Gara a zauna a saƙon rufin ɗaki da a zauna gida ɗaya tare da mace mai yawan faɗace-faɗace.25Kamar yadda ruwan sanyi ke ga wanda ke ƙishi, haka ya ke ga labari mai daɗi da ke zuwa daga ƙasa mai nisa.26Kamar ƙazantacciyar maɓuɓɓuga ko gurɓatacciyar rijiya haka ya ke da mutum adali da ya yi sanyi a gaban mugayen mutane.27Ba shi da kyau a sha zuma da yawa; wannan kamar neman yabo ne bisa yabo.28Mutumin da bashi da kamun kai na kama da birnin da ke a buɗe kuma bashi da ganuwa.
"a ɓoye wasu abubuwa"
An kwatanta zukatan sarakuna da girman sammai da ƙasa. AT: "Kamar yadda babu wanda zai iya auna tsayin sammai ko zurfin duniya, har ma ba wanda zai iya fahimtar zuciyar sarakuna"
Kursiyin wakilci ne na ikon yin mulki. Waɗannan kalmomin ana iya fassara su cikin aiki. AT: "sarki zai kafa kursiyinsa ta hanyar yin" ko "zai sami ikon yin mulki saboda yana yi"
Anan "sama" yana nufin matsawa zuwa wani wuri a tebur wanda yake kusa da sarki. Babban abin alfahari ne mutum ya zauna kusa da sarki. AT: "Zai fi kyau wani ya gayyace ku ku zauna kusa da sarki fiye da"
An yi wannan tambayar ne don sanya mai karatu la'akari da yiwuwar cewa zai iya fahimtar halin da ake ciki. Ana iya bayyana hanyar da maƙwabta zai iya kunyata mai karatu a bayyane. AT: "Gama ba za ku san abin da za ku yi ba a ƙarshen lokacin da maƙwabcinku ya ba ku kunya." ko "Gama idan maƙwabcinku yana da bayani, zai kunyata ku, kuma ba za ku sami abin da za ku ce don kare kanku ba."
"kada ka raba sirrin makwabcinka ga wasu mutane"
Anan "mummunan rahoto" yana nufin abubuwan cutarwa waɗanda mutumin zai gaya ma wasu. Ana iya bayyana jumlar "ba za a iya yin shuru" ba a cikin yanayi mai aiki. AT: "ba za ku iya hana shi gaya wa wasu abubuwa masu cutarwa game da ku ba" ko "zai gaya wa mutane mummunan abubuwa game da ku kuma ba za ku sake samun suna mai kyau ba"
Kyakkyawan "kalma da aka faɗa a lokacin da ya dace" ana maganarsa kamar dai kyakkyawa ce ta zahiri ta "aful na zinariya a cikin saitunan azurfa." Yawancin fassara suna fassara wannan kwatancen a matsayin misali kuma suna sauya tsarin jimloli. AT: "Kalmar da aka faɗi a dai-dai lokacin tana da kyau kamar aful na zinariya a cikin saitunan azurfa"
Ana magana akan ƙima da mahimmancin "tsautawa mai hikima" kamar tana da kyau da darajar zinariya. Yawancin fassara suna fassara wannan kwatancen a matsayin misali kuma suna sauya tsarin jimloli. AT: "Tsawatarwa mai hikima ga kunne mai sauraro yana da kyau kuma mai daraja kamar zoben zinare ko kayan adon zinariya"
A nan ana kwatanta manzo mai aminci da sanyin dusar ƙanƙara, saboda dukka suna da daɗi.
Yawancin fassara suna fassara wannan kwatancen a matsayin misali kuma suna sauya tsarin jimloli. Ruwa yana da mahimmanci ga Isra’ilawa saboda ƙarancin ruwa ne ya faɗo, don haka gajimare ba ruwan sama ba shi da amfani kuma ya kawo baƙin ciki ga Isra’ilawa. AT: "Wanda ya yi alfahari ... bai bayar ba kamar gajimare ne da iska ba tare da ruwan sama ba" ko "Wanda ya yi alfahari ... kar ya bayar bashi da wani amfani kuma abin takaici ne, kamar girgije da iska ba ruwan sama"
Kalmar "harshe" wata kalma ce don kalmomin da mutum yake magana da su ta hanyar amfani da harshen. Kalmar "kashi" wata kalma ce ga adawa mai karfi. AT: "magana mai taushi na iya shawo kan adawa mai ƙarfi"
Aya ta 16 ta faɗi wata ƙa'ida ta gaba ɗaya, kuma aya ta 17 ta ba da takamaiman misali. Maganar cin zuma da yawa sannan kuma amai shi abin wata kalmomin ne domin shan abu mai kyau da nadama daga baya.
Ana kwatanta shaidar zur da makamai uku waɗanda zasu iya cutar ko kashe mutane.
Mutum marar amincin idan aka kwatanta shi da wani sashi na jiki wanda yake haifar da matsala ga mutum. AT: "Dogara ga mutumin da ba ya da aminci a lokacin wahala zai kawo muku ciwo kamar mummunan haƙori ko ƙafa wanda ya zame"
Zuciya na wakiltar dukkan mutum. AT: "mutum mai bakin ciki"
Wannan karin magana ne. AT: "sa shi ya zama lamiri mai laifi kuma ya ji kunyar abin da ya aikata"
Fuska na wakiltar mutum. AT: "yana sa wasu mutane fusata sosai zaka gansu a fuskokinsu"
An gwada ruwan sanyi da bisharar mai daɗaɗawa.
Tushewa wata kalma ne na ko dai 1) ƙi yaƙi da mugaye ko 2) shiga cikin muguntarsu. AT: "wanda ya bar mugaye su aikata mugunta" ko "wanda ya fara aikata abin da mugaye suke aikatawa"
Duk son mutane su girmama ka da kuma cin zuma suna da kyau, amma zaka iya cin zuma da yawa, kuma zaka yi ƙoƙari sosai don mutane su girmama ka.
"wanda sojoji suka rusa bangonsa suka rusa"
1Kamar garin ƙanƙara a lokacin zafi ko ruwan sama a lokacin girbi, haka ma yabo bai dace ga wawa ba.2Kamar tsuntsayen da ke shawagi a sama basu sauka ba, haka la'annar da ba a cancance ta ba baza ta sauka ba.3Tsumagiya domin doki ne, linzami domin jaki sanda kuwa domin bayan wawaye.4Kada ka bada amsa ga wawa bisa ga wawancinsa, in ba haka ba za ka zama kamar sa.5Ka bada amsa ga wawa sai ka ƙara masa wawancinsa, domin kada ya ɗauki kansa wani mai hikima ne.6Duk wanda ya aika da saƙo ta hannun mai wauta na datse ƙafafunsa ne yana kuma shan ta'addanci.7Kamar ƙafafuwa shanyayyu da ke rataye da ƙasa haka karin magana ya ke a bakin wawaye.8Kamar a gwada harba dutse a majajjawa haka ya ke a bada yabo ga wawa.9Kamar ƙaya data shiga hannun mashayin giya haka karin magana a bakin wawaye.10Kamar maharbin da yaji wa dukkan waɗanda ke kewaye da shi raunuka haka wanda ya yi hayar wawa ko hayar duk mai wucewa kan hanya.11Kamar yadda kare ke komawa ga abin da ya amayas, haka wawan da ke maimaita wawancinsa.12Ko ka ga wani wanda ke ganin kansa mai hikima ne? Ko wawa na da bege fiye da shi.13Ragon mutum ya ce, "Akwai zaki a kan hanya! Akwai zaki a tsakanin buɗaɗɗun wurare!"14Kamar yadda ƙofa ke juyawa a ƙyaurenta, haka ragon mutum bisa gadonsa.15Ragon mutum na sa hannunsa cikin abinci duk da haka ba shi da ƙarfin ɗaga shi zuwa bakinsa.16Ragon mutum a ganin sa mai hikima ne shi fiye da mazaje bakwai da suka bada dalilai masu kyau.17Kamar wadda ya riƙe kunnuwan kare, haka mai wucewa kan hanya da ya yi fushi ga shawarwarin da basu shafe shi ba.18Kamar mahaukacin da ke harba kibiya mai wuta,19haka wanda ya ruɗi maƙwabcinsa yana cewa, "Ba wasa kawai nake yi ba?"20Don rashin itace, wuta ke mutuwa; kuma duk inda babu magulmaci faɗace-faɗace na ɗaukewa.21Kamar yadda gawayi ke ga wuta maici itace kuma ga wuta, haka ya ke da mutum mai faɗace-faɗace wurin kunna husuma.22Maganganun magulmaci suna kama da abinci mai daɗi; suna shigewa can cikin jiki.23Kamar kaskon da aka dalaye da azurfa haka baki mai zafi da kuma zuciya mai mugunta.24Shi da ke ƙin mutane yana ɓoye yadda ya ke ji da leɓunansa kuma yana ajiyar munafunci cikinsa.25Zai yi maganar alheri, amma kada ka yarda da shi, Gama akwai ƙazanta guda bakwai cikin zuciyarsa.26Ko da ya ke rashin gaskiya ya ɓoye ƙiyayyarsa, za a bayyana muguntarsa a cikin taro.27Duk wanda ya haƙa rami zai faɗa cikinsa kuma dutsen zai gangaro wa wanda ya turo shi.28Maƙaryacin harshe na ƙin mutanen da ya ke murƙushewa kuma baki mai fahariya na kawo hasara.
Ana iya bayyana wannan tare da nau'i mai aiki. AT: "la'ana ga mutumin da bai cancanci hakan ba"
Bulala, birki, da sanda abubuwa ne da mutane suke amfani da shi don yin doki, jaki, da wawa suyi abin da suke so.
Ana yin amarya da madauri. Mutane sun ɗora a kan jaki suna riƙe ɗaya daga cikin madaurin don jakar ta tafi yadda suke so.
Shiga cikin wautar wauta yayin amsa masa yana wakiltar amsa masa ta hanyar wauta. AT: "Amsa wawa bisa ga wautinsa" ko "Amsa wawa wawa"
Anan hannu yana wakiltar nauyin wawa ne na isar da saƙo. AT: "Duk wanda ya aika wawa don isar da saƙo"
Za a iya sake sanya jumla. AT: "Misali a bakin wawaye kamar kafafun mai larurar shan inna ne wanda ke ratayewa" ko "Misali a bakin wawa bashi da amfani kamar kafafun mai ciwon inna da suka rataya"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) idan mashayi ya bugu da ƙugiya, ƙaya za ta buga masa hannu, ko kuma 2) idan maye ya bugu, zai ɗauki ƙaya kuma ya yi ta yi wa mutane magana. Don ma'ana ta biyu, kalmar "ƙaya" tana wakiltar ƙaya.
"Kamar yadda kare yake cin nasa amai"
Ana amfani da wannan tambayar don sa mai karatu yayi tunani game da wani wanda yake da wayo a gaban kansa. Kalmomin "mai hikima ne a ganinsa" yana nufin "yana ganin shi mai hikima ne," kuma a nan yana nuna cewa mutumin ba shi da hikima da gaske. AT: "Ka yi la’akari da mutumin da yake zaton shi mai hikima ne amma ba shi da hikima.”
Malalaci ya yi ƙarya ya ce ba zai iya fita waje ya yi aiki ba saboda akwai zaki a hanya ko tsakanin buɗaɗɗun wurare.
Kofa da malalaci suna tafiya, amma ba sa zuwa ko'ina.
Kalmomin "idanunsa" suna wakiltar tunaninsa. AT: "Malalaci yana zaton ya fi maza bakwai hikima"
Bayanin da aka gabatar shine cewa kare zai fusata kuma ya ciji mutumin. AT: "Kamar mutumin da ya fusata kare ta hanyar kame kunnuwansa" ko "Kamar mutumin da ya kame kunnen kare kuma kare ya cije shi"
Bayanin da aka gabatar shine cewa mai wucewa zai fara jayayya, kuma mutanen da ke yaƙin za su yi fushi da shi kuma su cutar da shi.
Duk mahaukacin da wanda ke yaudarar mutane sun cutar da mutane amma basu dauki alhakin hakan ba.
Abin da gawayi yake yi wa gawayi da abin da itace yake yi wa wuta ana iya bayyana shi sarai. AT: "Kamar yadda gawayi yake taimaka wa garwashin konewa haka kuma itace yake taimakawa wajen kona wuta"
Wannan yana magana ne game da tsegumi abin kyawawa ne don saurare kamar yana da abinci mai daɗin ci. AT: "Kalmomin tsegumi kyawawa ne don saurare" ko
Wannan kalmomin yana nufin cewa mutumin da yake faɗar abubuwa don ɓoye mugunta a cikin zuciyarsu kamar jirgin ruwa ne wanda aka lulluɓe shi da kyalli don ya yi kyau. Waɗannan kalmomin za a iya sake yin oda. AT: "Mutanen da ke da lebe mai ƙuna da muguwar zuciya kamar jirgin ruwa ne da aka rufe da gilashi"
Sanya yanayin sa yana wakiltar hana mutane sanin menene jin sa. Kalmomin "leɓunansa" alama ce ta abin da yake faɗi. AT: "ɓoye abubuwan da yake ji game da abin da ya faɗa" ko "yana magana ta yadda mutane ba za su iya sanin ainihin abin da yake ji ba"
Maganar hana mutane sanin cewa yana ƙin su ana magana ne game da rufe kiyayyarsa. AT: "Duk da cewa karya yake yi don ya hana mutane sanin cewa ya ƙi su" ko "Ko da yake yana yin ƙarya ne don kada mutane su san cewa ya ƙi su"
Kasancewa a bayyane yana wakiltar ganowa ko zama sananne. AT: "za a san muguntarsa a cikin taron" ko "taron zai gano muguntarsa"
Ana nuna cewa mutum ya haƙa ramin azaman tarko ne don wani ya faɗa cikin ta. AT: "Duk wanda ya haƙa rami don faɗawa wani zai faɗa ciki" ko "Idan wani ya tono rami don ya kama wani, to wanda ya haƙa shi zai faɗa ciki"
An nuna cewa mutumin ya tura babban dutse don ya mirgina zuwa ƙasa kuma ya murƙushe wani can. AT: "idan wani ya tura dutse don ya yi kasa ya murkushe wani, dutsen zai sake juya shi a maimakon" ko "idan wani ya yi mirgina dutse don ya cutar da wani, dutse zai murkushe shi maimakon"
Kalmomin "harshe mai ƙarya" yana wakiltar mutumin da ya faɗi ƙarya. Murkushe mutane yana wakiltar haifar musu da matsala. AT: "Maƙaryaci yana ƙin waɗanda ya cutar da su ta hanyar ƙaryar sa"
1Kada ka yi alfahari game da gobe, domin baka san me ranar ke iya kawo wa ba.2Bari wani ne ya yabe ka amma ba naka bakin ba; baƙo amma ba naka leɓunan ba.3Ka yi la'akari da yadda dutse ke da nauyi da kuma nauyin yashi - cakuna ta wawa tafi dukkansu biyu nauyi.4Akwai rashin imanin hasala da kuma ambaliyar fushi, amma wa zai iya tsayawa a gaban kishi?5Tsautawa a fili ta fi nuna ƙauna a ɓoye.6Har yanzu akwai aminci a cutar da tazo daga aboki, amma maƙiyi na iya sumbatarka babu iyaka.7Mutumin da ya ci abinci ya ƙoshi zai ƙi ko da ma saƙar zuma ne, amma ga mutum mai yunwa, kowanne abu mai ɗaci na da zaƙi.8Kamar tsuntsun da ke yawo daga sheƙarsa haka mutumin da ya kauce daga inda ya ke zama.9Kayan ƙamshi da turare suna sa zuciya ta yi farinciki, amma daɗin aboki na zuwa ne daga amintacciyar shawararsa.10Kada ka yi banza da abokinka da kuma abokin mahaifinka, kuma kada ka tafi gidan ɗan'uwanka a ranar wahalar ka. Maƙwabcin da ke kusa da kai ya fiye maka da ɗan'uwanka mai nisa da kai.11Ka zama mai hikima, ya ɗana, ka sa zuciyata ta yi farinciki; sa'an nan zan bada amsa ga wanda ke yi mani ba'a.12Mutum mai cikakken hankali na ɓoyewa ne idan ya ga wahala, amma mutane masu halin baƙunci na tafiya kai-tsaye har su kuma shiga wahala.13Ka karɓe mayafin wanda ya tsaya wa baƙo, ka kuma riƙe shi a matsayin alƙawari sa'ad da ya tsayawa karuwar mace.14Duk wanda yasa wa maƙwabcinsa albarka da babbar murya da sassafe, wannan albarkar za a ganta kamar la'ana ce!15Mace mai yawan faɗace-faɗace na kama da yayyafi a ranar ruwan sama marar tsayawa;16hana ta na kama da hana iska ne, ko kuma yin ƙoƙarin riƙe mai cikin hannun damanka.17Ƙarfe ke wãsa ƙarfe; haka nan kuma, mutum ke wãsa abokinsa.18Wanda ya yi noman zaitun zai ci 'ya'yan itacensa, kuma wanda ya tsare ubangidansa za a yabe shi.19Kamar yadda ruwa ke nuna fuskar mutum, haka zuciyar mutum ke bayyana mutumin.20Kamar yadda Lahira da Abaddon basu ƙoshi, haka idanun mutum basu taɓa ƙoshi.21Maƙera domin gwada azurfa ne tanderun wuta kuwa domin zinariya ne; mutum kuma ana gwada shi ne sa'ad da aka yabe shi.22Ko da zaka daka wawa da taɓarya - harɗe da hatsi - duk da haka wawancinsa ba zai bar shi ba.23Ka tabbatar ka san lafiyar tumakinka ka kuma nuna damuwarka ga garkenka,24gama dukiya ba ta har abada ba ce. Ko masarauta tana dawwama dukkan tsararraki?25Ka san lokacin da busasshiyar ciyawa ta ɗauke sabuwa kuma ta fito, da kuma lokacin da ciyawa daga bisa tuddai ke taruwa ciki.26Waɗannan tumakai zasu yi maka tanadin tufafin sawa haka kuma ragunan zasu yi tanadin kuɗi domin filin.27Za a sami madarar awaki domin abincinka - abinci domin iyalinka - kuma wartsakarwa domin 'yan matanka bayi.
Wannan gargadi ne kar kuyi alfahari da abin da kuke tsammanin zai faru gobe. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Kada ku yi magana cikin alfahari game da shirinku na gobe"
Wahalar yin haƙuri da wawa wanda ya tsokane ku ana magana ne kamar wannan wahalar tana da nauyi. AT: "tsokanar wawa ya fi kowane ɗayansu haƙuri" ko "Ya fi wuya a yi haƙuri lokacin da wawa ya tsokane ku fiye da yadda za a yi haƙuri yayin ɗaukar su"
Sunayen "fushin", "fushi" da "kishi" ana iya fassara su azaman sifofi. AT: "Mutum mai yawan fushi yana da zalunci kuma mai fushi yana da ƙarfi, amma wa zai iya tsayawa a gaban mai kishi?"
Ana iya bayyana kalmar 'tsawatarwa' ta kalmomin aiki tare da kalmar aikatawa. AT: "Zai fi kyau a tsawata muku a bayyane"
"fiye da soyayyar da ba a bayyane ba." Cikakken sunan “kauna” za a iya fassara shi azaman kalmar magana. AT: "fiye da a ƙaunace ku a asirce"
"Raunin da aboki ya haifar amintacce ne." Kalmar nan “raunuka” a nan tana wakiltar zafi da baƙin ciki da mutum yake ji sa’ad da abokinsa ya tsawata masa ko ya yi masa gyara.
"Mutumin da ya koshi" ko "Mutumin da ya ci abinci ya koshi"
Kalmomin "yawo" da "ɓata" suna da abu ɗaya a cikin wannan ayar.
Anan “zuciya” tana wakiltar yadda mutum yake ji. AT: "sa mutum ya ji daɗi" ko "faranta wa mutum rai"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "zaƙi" yana wakiltar kirki. AT: "muna gane alherin abokinmu ta hanyar nasiharsa" ko 2) "zaƙi" yana wakiltar abin da muke yaba wa game da mutum. AT: "abin da muke yabawa game da aboki shi ne shawararsa"
Anan "amsa" baya nufin amsa tambaya. Yana nufin amsa ko amsa ga wanda yake izgili. Ta yaya wannan yake da alaƙa da zancen kafin a bayyana shi a sarari. AT: "sa'annan zan amsa wa wanda ya yi mini ba'a ta hanyar gaya masa labarinku"
Dubi yadda kuka fassara wani magana makamancin wannan a cikin Misalai 22: 3.
Lokacin bada bashi, mai bada bashi zai dauki wani abu daga wanda ya bashi, kamar tufa, a matsayin garanti na sake biya. Zai mayar dashi bayan an biya kudin. Idan mai karɓar bashi ya talauce sosai, wani zai iya ba wa mai rance wani abu a matsayin garanti a gare shi. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Misalai 20:15. AT: "dauki tufa a matsayin tsaro daga wanda ya ba da tabbacin abin da baƙon ya ranta za a biya shi"
"Duk wanda ya ba maƙwabcinsa albarka"
Bayanin da aka kawo shine cewa yana da wahala ko mara amfani a gwada a hana ta kamar yadda ake kokarin hana iska ko kama mai a hannunka
Wadannan jimlolin guda biyu suna kwatanta yadda za'a iya inganta ƙarfe da namiji. AT: "Kamar yadda baƙin ƙarfe ke iya kaifafa wani ƙarfe, haka ma halayen mutum ya inganta ta hanyar hulɗa da abokinsa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "maigida zai girmama wanda ya kiyaye shi"
Anan wannan yana nufin tunanin mutum. AT: "abin da mutum yake tunani"
Wannan suna ne da ke nufin "mai halakarwa." AT: "Mai hallakarwa"
Wannan yana nufin yadda ake tace zinariya da azurfa. Ana yin ƙarfe da ƙarfe ta hanyar dumama shi zuwa zazzabi mai ƙarfi don ya narke kuma ana iya cire ƙazantar. Duba yadda kuka fassara magana makamancin wannan a cikin Misalai 17: 3. AT: "Ana amfani da murtsen dutse don tace azurfa kuma ana amfani da tanda wajen tace zinariya"
Wannan yana nufin cewa ko da wawa ya sami wahala ko zafi (murkushe shi sau da yawa wani magana ne na wahala a Ibraniyanci), zai kasance wawa.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani dasu tare don girmamawa.
Wannan tambayar tana tsammanin amsar mara kyau don nuna batun cewa sarakunan masu mulkin duniya ba zai dawwama har abada. Ana iya bayyana wannan azaman bayani. AT: "Kambi ba ya ɗorewa har zuwa tsararraki dukka"
Aya ta 26 da 27 suna tafiya tare da ayoyi 23 zuwa 25 a matsayin misali.
Bayanin da aka bayar shine cewa ana iya amfani da ulu
Bayanin da aka gabatar shine cewa kudin da aka karba ta hanyar siyar da awakin zasu isa sayen filin. AT: "siyar da awakinku zai samar da farashin filin"
1Mugayen mutane na gudu babu wani mai korar su, amma masu adalci basu da tsoro kamar ɗan zaƙi.2Saboda kurakuran ƙasa, ta sami shugabanni da yawa, amma ga mutum mai fahimta da ilimi, zata dawwama na lokaci mai tsawo.3Matalaucin da ke zaluntar wasu matalautan mutane na kama da ruwan sama da baya bada abinci.4Waɗanda suka yi banza da shari'a na koma wa ga yabon mugayen mutane, amma waɗanda ke bin shari'a na gãba da su.5Mugayen mutane basu fahimtar hukunci, amma masu neman Yahweh na fahimtar komai.6Ya fiye wa matalaucin mutum mai tafiya cikin aminci, da mai arziƙi wanda ke tafiya cikin hanyoyinsa na rashin aminci.7Shi wanda ya kula da shari'a ɗa ne mai fahimta, amma abokin mashaya abin kunya ne ga mahaifinsa.8Duk wanda ya tara dukiyarsa ta hanyar zamba dukiyarsa zata tafi wurin wani wanda zai tausaya wa matalauta.9Idan wani ya juyar da kunnuwarsa daga sauraren shari'a, ko addu'arsa ma abin ƙyama ce.10Duk wanda ya ɓatas da mai gaskiya domin aikata mugunta zai faɗa cikin ramin da ya haƙa, amma mai gaskiya zai sami gãdo mai kyau.11Mai arziki na yi wa kansa kallon shi mai hikima ne, amma mai fahimta wanda ke matalauci zai tona masa asiri.12Lokacin da masu adalci ke mulki, akwai babbar ɗaukaka; amma sa'ad da mugaye suka tashi, ana tone asirin mutane.13Wanda ya ɓoye zunubansa ba za shi yi albarka ba, amma shi wanda ya furtasu ya kuma rabu da su za a yi masa jinƙai.14Shi wanda ke rayuwa cikin girmamawa mai albarka ne, amma wanda ya taurare zuciyarsa zai abka cikin wahala.15Kamar zaki mai ruri ko kamar dabbar kerkeci mai huci haka mugun shugaba a bisa mutane matalauta.16Shugaban da ba shi da fahimta azzalumi ne, amma wanda ya tsani zalunci zai daɗe da kwanakinsa.17Idan mutum ya yi laifi domin ya zubda jinin wani, zai zama mai gudun hijira har sai ya mutu kuma ba wanda zai taimake shi.18Duk wanda ya yi rayuwa cikin gaskiya zai zauna lafiya lau, amma wanda tafarkinsa karkataccc ne zai faɗi ba zato.19Shi wanda ya yi aiki cikin gonarsa zai sami abinci mai yawa, amma wanda ya bi wofi zai sami talauci mai yawa.20Mutum mai aminci zai sami albarka mai girma, amma wanda ya sami wadata cikin hanzari ba zai tsira daga hukunci ba.21Bai kamata a nuna sonkai ba, amma akan 'yar gurasa mutum kan iya aikata ba dai-dai ba.22Mutum mai rowa na hanzarin neman arziki, amma bai san da cewar talauci na zuwa bisansa ba.23Duk wanda ya yi ma wani horo, daga baya zai sami tagomashi daga gare shi fiye da wanda daga shi aka yi masa zaƙin baki.24Duk wanda ya zambanci mahaifinsa da mahaifiyarsa ya kuma ce, "Wannan ba zunubi bane," shi abokin wanda ke hallakarwa ne.25Mutum mai yawan son kansa na haddasar da rigima, amma wanda ya dangana da Yahweh zai yi albarka.26Shi wanda ya dangana ga tasa zuciya wawa ne, amma duk wanda ya yi tafiya cikin hikima zai yi nisa daga hatsari.27Wanda ya bayar ga matalauta ba za shi rasa komai ba, amma wanda ya rufe idanunsa gare su zai sami la'ana.28Lokacin da miyagu suka tashi, mutane na ɓoye kansu; amma idan suka lalace, masu adalci na ƙaruwa.
Cikakken sunan "ƙetare iyaka" za a iya fassara shi azaman aiki. AT: "Saboda yadda ƙasa take ketare iyaka"
Wannan wani magana ne na zunuban mutanen da ke zaune a ƙasa. AT: "laifin mutane na wata ƙasa"
Bayanin da aka gabatar shine cewa wannan mutumin mai mulki ne ko shugaba. Ana iya fassara sunayen kalmomin "fahimta" da "ilimi" azaman kalmomi. AT: "tare da mutumin da ya fahimta kuma ya san yadda ake sarauta"
Talakawan da ke zaluntar sauran talakawa ana gwama shi da ruwan sama mai ƙarfi wanda ba ya barin amfanin gona ya girbe.
"Kiyaye doka" na nufin yin abin da dokar Allah ta buƙata. AT: "waɗanda ke yin biyayya ga dokar Allah"
Cikakken sunan "adalci" za a iya bayyana shi a matsayin sifa. AT: "ba ku fahimci abin da ke daidai ba"
"Zai fi kyau ka zama talaka ... hansai dai ka zama mai arziki "
Cikakken sunan "fahimta" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "ɗan da ya fahimta"
"sanya mahaifinsa kunya" ko "tozarta mahaifinsa"
Wannan yana wakiltar duk mutumin da ya juya baya ya ƙi dokar Allah. AT: "ya kau da kai daga jin doka da yin biyayya"
Wannan wani maganai ne na jagorantar mutanen kirki zuwa ga mummunar hanya. AT: "Duk wanda ya sa karkata zuwa ga tafarkin mugunta"
"zai gaji abu mai kyau"
"Idan adalai suka yi nasara"
Wannan karin magana ne wanda ke nufin lokacin da mugaye suka sami iko ko fara mulki. AT: "lokacin da miyagu suka hau kan mulki"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah zai nuna jinƙai ga wanda ya furta kuma ya yashe su"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah zai albarkaci wanda yake rayuwa koyaushe tare da girmamawa"
Wannan karin magana ne da ke nufin taurin kai ko rashin son yin biyayya ga Allah. AT: "ya ƙi yin biyayya ga Allah"
Talakawan da ba su da ƙarfi a kan mugu sarki ana kwatanta su da mutanen da zaki yana ruri a kansu ko beyar da ke kawo musu hari.
Cikakken sunan "fahimta" ana iya fassara shi azaman aiki. AT: "Mai mulkin da bai fahimta ba"
Anan “jini” yana wakiltar rayuwar mutum. 'Zub da jini' na nufin kisan wani. AT: "ya kashe wani" ko "ya kashe wani"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah zai kiyaye duk wanda ya yi tafiya cikin aminci"
"bi bayan ayyuka marasa amfani." Ana ambaton mutumin da yake shagaltar da yin abubuwa waɗanda ba su haifar da komai ba kamar neman abubuwan banza.
Mugu biyu "ba zai tafi da hukunci ba" ana amfani dashi don ƙarfafawa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Tabbas Allah zai hukunta wanda ya yi arziki nan da nan"
"Gurasar burodi" a nan ƙari ne don ƙaramar cin hanci ko lada. AT: "mutum zai yi zunubi don ɗan riba kaɗan"
Ana maganar sakamakon rowa kamar talauci yana riskar mai rowa. Cikakken sunan “talauci” ana iya fassara shi azaman sifa. AT: "ba zato ba tsammani zai talauce"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki, tare da bayyananniyar suna "ni'ima" kamar yadda ake nunawa a matsayin kalma. AT: "Mutum zai fifita wanda ya hore shi fiye da yadda yake fifita mutumin da ya faranta masa rai da harshensa"
Dogaro da kan mutum ana maganarsa kamar amintacce a cikin zuciyar kansa. AT: "Mutumin da ya dogara da kansa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) za su sami la'ana da yawa daga matalauta. AT: "talakawa zasu bada la'anoni da yawa ga duk wandaya rufe idanuwansu zuwa garesu" ko kuma 2) zasu sami la'anoni da yawa daga mutane gaba ɗaya. AT: "mutane zasu bada la'ana da yawa ga duk wanda ya rufe idanunsa ga talakawa" ko kuma 3) zasu sami la'ana da yawa daga Allah. AT: "Allah zai ba da la'ana da yawa ga duk wanda ya rufe idanunsa ga matalauta"
1Mutumin da ya karɓi horo dayawa amma ya taurare wuyansa za a karya shi cikin ƙanƙanen lokaci da ba za shi warke ba.2Lokacin da masu adalci suka ƙaru, mutane na farinciki, amma lokacin da mugu ke shugabanci, mutane na ajiyar zuciya.3Duk wanda ya ƙaunaci hikima nasa mahaifinsa ya yi farinciki, amma wanda ya yi abokantaka da karuwai na lalatar da dukiyarsa.4Sarki na kafa ƙasar da adalci, amma wanda ya nemi cin hanci yana yayyaga ta dukka.5Mutumin da ya yi wa maƙwabcinsa daɗin yana shinfiɗa wa sawayensa tarko ne.6Cikin zunubin mugun mutum nan akwai tarko, amma mutum mai adalci yana waƙoƙi da farinciki.7Mutum mai adalci na sane da yancin talakawa; mugun mutum ba shi da wannan ilimin.8Masu ba'a sukan cinna wa birni wuta, amma waɗanda ke da hikima suna juyar da hasala.9Lokacin da mutum mai hikima ya yi jayayya da wawa, yana fusata yana kuma dariya, ba za a kuma sami hutawa ba.10Masu zubda jini suna tsanar masu gaskiya su kuma nemi ran kamilai.11Wawa yana bayyana dukkan haushinsa, amma mutum mai hikima na danne shi ya kuma kãme kansa.12Idan mai mulki ya saurari ƙarairayi, dukkan shugabanninsa zasu zama mugaye.13Matalauci da wanda ke azzalumi sun zama ɗaya, gama Yahweh ya bada haske ga idanunsu dukka.14Idan sarki ya shar'anta matalauta da gaskiya, kursiyinsa zai kafu har abada.15Sanda da tsautawa na bada hikima, amma ɗan da ba ya sami horo ba na kawo wa mahaifiyarsa kunya.16Yayin da mugayen mutane ke riƙe da iko, kurakurai na ƙaruwa, amma adalai zasu ga faduwar mugayen mutane.17Ka hori ɗanka zai kuma baka hutu; zai kawo wa ranka jin daɗi.18Inda babu furtacciyar ruya mutane kan yi yadda suka ga dama, amma wanda ya kula da shari'a mai albarka ne.19Bawa ba zai tsautu da magana kawai ba, ko da ya fahimta, ba zai juya ba.20Ko ka ga mutum mai saurin magana? Ya fiye a sa zuciya ga wawa da wannan.21Duk wanda ya shagwaɓa bawansa tun yana matashi, a ƙarshe akwai wahala.22Mutum mai fushi na garwaya husuma kuma mai hasala na aikata zunubai masu yawa.23Girman kan mutum ne ke kãda shi, amma wanda ke da ruhun saukin kai za a ba shi ɗaukaka.24Shi wanda ya yi tarayya da ɓarawo maƙiyin ransa ne; yana jin la'ana bai kuma ce komai ba.25Tsoron mutum tarko ne, amma wanda ya dogara ga Yahweh za a kiyaye shi.26Dayawa ne masu neman ganin fuskar mai mulki, amma daga wurin Yahweh adalci ke zuwa ga mutum.27Mutum marar gaskiya abin ƙyama ne ga mutane masu adalci, amma wanda ke mai adalci abin ƙi ne ga mugun mutum.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba zato ba tsammani Allah zai karya shi"
"kuma babu wanda zai iya warkar da shi." Cuta wani magana ne ga kowane irin mummunan yanayi. AT: "kuma babu wanda zai iya taimaka masa"
Cikakken sunan "adalci" ana iya fassara shi azaman jimlar suna. AT: "ta hanyar yin abin da ke dai-dai" ko "ta hanyar yin dokoki masu adalci"
da sanin ya gaya wa maƙwabcinsa abin da ba gaskiya ba don makwabcin ya yi abin da mai magana yake so ya yi
Marubucin ya kwatanta fadan mutum da sanya mutumin har ya faɗa cikin tarko. AT: "sanya tarko don kama mutumin"
Lokacin da mugu ya yi zunubi, sai ka ga kamar ya faɗa cikin tarko. Yana son yin mugunta ga wasu mutane, amma Allah zai hukunta shi.
Anan kalmar "birni" tana wakiltar mutanen da suke zaune a cikin garin. Ana maganar masu izgili da ke haifar da mutane da rikice-rikice kuma mai yiwuwa su zama masu tashin hankali ana maganarsu kamar sun ƙone garin ne. AT: "haifar da rikici ga mutanen birni"
Wawa yakan yi fushi ƙwarai da gaske kuma yana ƙoƙari ya hana mai hikima yin magana ko kuma alƙalin kotu ya yanke hukunci.
Ana magana akan ayyukan mai mulki ta hanyar faɗin sakamakon da zai haifar. AT: "kamar dai yana koya wa jami'ansa mugaye"
Wannan karin magana yana nufin "Yahweh yana rayar da su duka biyu."
Marubucin yayi magana kamar sanda da tsawatarwa mutane ne waɗanda zasu iya ba da hikima azaman kyauta ta zahiri. AT: "Idan iyaye suka yi amfani da sandar akan yaron kuma suka tsawata masa, yaron zai zama mai hikima" ko "Idan iyaye suka ladabtar da ɗansu kuma suka gaya masa lokacin da ya yi kuskure, yaron zai koyi rayuwa mai hikima"
Cikakken sunan "faduwa" ana iya fassara shi da kalmar aikatau "fadua" wanda magana ce ta rasa ikon yin mulki. AT: "waɗancan mugayen mutane sun faɗi" ko "waɗancan mugayen mutane sun rasa ikon yin mulki"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah zai albarkaci wanda ya kiyaye doka"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. "Ba za ku iya gyara bawan kawai ta hanyar magana da shi"
"wanda ya bawa bawansa damar kauce wa aiki kuma wanda ya fi kyautatawa bawansa fiye da yadda yake mu'amala da sauran bayi"
Wannan karin magana yana nufin "mutumin da yake saurin yin fushi."
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane za su ba da girmamawa ga mutumin da ke da tawali'u" ko kuma "mutumin da ke da tawali'u zai karɓi girmamawa daga mutane" ko "Yahweh zai sa mutane su girmama mutumin da yake da tawali'u"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai kiyaye wanda ya dogara gare shi"
Kalmar "fuska" wani magana ne ga mai mulki yana sauraron mutane yana gaya masa abin da suke so ya yi sannan kuma ya aikata shi. AT: "Mutane da yawa suna son mai mulkin nasu ya kula da su"
mutumin da ya kamata a ƙi. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Misalai 3:31.
1Maganganun Agu ke nan ɗan Yãke - furcin: Wannan mutumin ya gaya wa Itiyel da Ukal:2Tabbas ni kamar wata dabba ce ba mutum ba kuma bani da fahimta irin na mutum.3Ban koyi hikima ba, bani kuma da ilimi game da Mai Tsarkin.4Wane ne ya haura cikin sama ya kuma sauko? Wane ne ya tattara iska cikin hannuwansa? Wane ne ya tattara ruwaye cikin mayafi? Wane ne ya kafa iyakokin dukkan duniya? Mene ne sunansa, kuma mene ne sunan ɗansa? Tabbas ka sani.5Kowacce maganar Allah gwadajjiya ce; garkuwa ce ga duk waɗanda ke ɓuya gare shi.6Kada ka ƙara a bisa maganarsa, domin kada ya hore ka, kuma za a iske ka maƙaryaci.7Abu guda biyu na tambaya gare ka, kada kuma ka hana mani kamin na mutu:8Kada ka bar wofi da ƙarya su kusance ni. Kada ka ba ni ko talauci ko arziki, ka dai ba ni abincin da nake buƙata.9Gama idan na samu dayawa, ina iya ƙaurace maka in ce, "Wane ne Yahweh?" Ko idan na zama matalauci, ina iya sata har in kawo reni ga sunan Allahna.10Kada ka zargi bawa a gaban ubangidansa, don kada ya la'anta ka kuma har a kama ka da laifi.11Akwai wata tsara da ke la'anta mahaifinsu kuma ba ta albarkatar mahaifiyarsu.12Akwai tsarar da ke ganin kanta mai tsarki ce a gaban idanun ta, amma duk da haka basu wanku daga ƙazantarsu ba.13Akwai tsarar da fuskarsu take ɗage sama, dubi yadda girar idanunsu ke ɗage can sama!14Akwai wata tsara wadda haƙoransu na takobi ne, kuma mataunansu kamar wuƙaƙe, domin su hallaka matalauta daga duniya mabuƙata kuma daga cikin 'yan adam.15Matsattsaku na da 'yan mata biyu: "Bayar kuma bayar" suke kuka. Akwai abu guda uku da basu ƙoshi, guda huɗu da basu cewa, "Ya isa":16Lahira; da mahaifar da bata ɗaukar ciki; da ƙasar da bata ƙoshi da ruwa; da kuma wutar da bata cewa, "Ya isa!"17Idanun da suka yi wa mahaifi ba'a ko suka rena rashin biyayya ga mahaifiya, hankakin kwari zasu ƙwaƙule idanunsa, kuma angulai zasu cinye namansa.18Akwai abubuwa guda uku masu ban mamaki gare ni, har huɗu da ban fahimce su ba:19hanyar gaggafa a sararin samaniya; hanyar macijiya a bisa kan dutse; hanyar jirgi a bisa kan teku; da hanyar ɗan saurayi tare da 'yar budurwa.20Ga hanyar mazinaciya: tana cin abinci ta kuma share baki tana cewa, "Ban yi wani abin da ke ba dai-dai ba."21A ƙarƙashin abubuwa guda uku duniya ke girgiza, kuma a ƙarƙashin guda huɗu bata iya jurewa:22lokacin da bawa ya zama sarki; yayin da wawa ya ƙoshi da abinci;23macen da aka ƙi lokacin data yi aure; baiwar da kuma ta gãji uwargijiyarta.24Akwai abubuwa huɗu cikin duniya 'yan ƙanƙanana ne amma suna da hikima sosai:25tururuwa hallitu ne marasa ƙarfi, amma suna tanadin abincinsu cikin rani;26remaye hallitu marasa ƙarfi, amma suna gina gidajensu cikin duwatsu.27Fãra basu da sarki, amma dukkansu suna cincirindo-cincirido.28Haka ma ƙadangare, kana iya riƙe shi cikin hannunka biyu, duk da haka kana samun su a cikin fadodi.29Akwai abubuwa uku suna da koƙari cikin ayyukansu haka ma huɗu da ke da takama a yadda suke tafiyarsu:30zaki, mai ƙarfi cikin namun jeji - ba shi juya baya daga kowanne abu,31zakara mai cara; bunsuru; da kuma sarkin da sojojinsa ke tsaye kusa da shi.32Idan ka yi wauta, kana ɗaukaka kanka, ko idan kana shirye-shiryen mugunta - ka ɗibiya hannuwanka a bakinka.33Kamar yadda kaɗaɗɗar madara ke fitar da mai da kuma kamar yadda hanci ke haɓo yayin da aka buge shi, haka ayyukan da aka aiwatar da su a cikin fushi.
Waɗannan sunayen maza.
Cikakken sunan "fahimta" ana iya fassara shi azaman aiki. AT: "Ban fahimci komai ba kamar yadda ya kamata mutane su fahimce su"
Cikakken sunan "ilimi" ana iya fassara shi azaman aiki. AT: "kuma ban san komai game da Mai Tsarki ba"
Marubucin yayi maganar iska kamar wani abu ne da mutum zai iya kamawa ya riƙe a hannunsa. AT: "ya kama iska a hannunsa"
"ya sanya iyaka ga inda duniya ta kare" ko "ya sanya iyaka a cikin iyakokin duniya"
Marubucin yayi amfani da waɗannan tambayoyin don umurtar mai karatu ya ba da amsa. AT: "Faɗa mini sunansa da sunan ɗansa, idan kun san su."
Kalmar “garkuwa” wani magana ce ta wani abu da ke kare mutum. AT: "yana kare waɗanda suka zo kuma ya roƙe shi ya kāre su"
Mai iya yiwuwa su ne 1) "Kada ku yarda mutane su yi magana a kan ƙarya da ƙarairayi a gare ni" ko kuma 2) "Kada ku ƙyale ni in yi maganar banza da ƙarya"
Marubucin yayi magana kamar "talauci" da "wadata" abubuwa ne na zahiri da wani zai iya baiwa wani. AT: "Kada ku yarda in zama talaka ko kuma mai arziki sosai"
Wannan yana bayanin yanayin tunanin da bai faru ba amma yana yiwuwa idan marubucin ya zama mai arziki.
Wannan yana bayanin yanayin tunanin da bai faru ba amma yana yiwuwa idan marubucin ya talauce.
yi ƙarya game da wani mutum tare da sha'awar cutar da shi
iri ko aji ko rukuni
Idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. AT: "sun ɗauki kansu tsarkakakku" ko "sun gaskanta cewa su tsarkaka ne"
Kalmomin "wanke" da "ƙazanta" suna maganar Allah mai gafartawa mutane waɗanda suke yin zunubi kamar yana wanke ƙazantar jiki ta mutane. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah bai gafarta musu zunubansu ba"
Wannan yana bayanin mutanen da suke zaton sun fi sauran mutane kyau. Idanunsu suna nuna cewa suna da girman kai, kuma yadda suke kallon wasu yana nuna cewa suna ganin sun fi waɗancan mutanen.
Wannan misali ne na wani abu wanda koyaushe yake son ƙari. AT: "Kwadayi yana da 'ya'ya mata biyu"
Wata ma'ana mai yiwuwa ita ce "kuma dukansu sunaye Ka ba Ni."
Wannan amfani da lambobin "uku" da "huɗu" tare a nan wataƙila na'urar waƙa ce. AT: "Akwai abubuwa guda huɗu waɗanda ba a taɓa gamsuwa ba, waɗanda ba sa taɓa cewa, "Ya isa"
Amfani da lambobi "uku" da "huɗu" a nan wataƙila na'urar waƙa ce. AT: "Akwai wasu abubuwa wadanda suka bani mamaki wadanda ban iya fahimta ba -- hudu daga cikinsu sune:"
"Zuciya" tana nufin tsakiyar. AT: "a tsakiyar teku" ko "a kan tekun budewa"
Wannan kamar wani kalmomin ne zina sannan yin wanka.
Amfani da lambobi "uku" da "huɗu" a nan wataƙila na'urar waƙa ce. "Akwai wasu abubuwa da suke sa kasa ta girgiza, ba za ta iya jurewa ba. Hudu daga cikinsu su ne:"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "wawa wanda yaci abinci ya ci"
Wato, mutane sun kyamace ta kafin tayi aure; da zarar ta yi aure, za ta fi ta yadda take kafin ta yi aure. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "macen da mutanen kirki suka ƙi ta yayin da take aure" ko "mace mai banƙyama lokacin da ta yi aure"
ke kula da gida
dabba mai kananan kunnuwa zagaye, gajerun kafafu, babu wutsiya
karamin dabba mai rarrafe mai kafa hudu, dogo, siriri, da jela
Amfani da lambobi "uku" da "huɗu" a nan wataƙila na'urar waƙa ce. AT: "Akwai wasu abubuwan da ke tafiya da mutunci. Hudu daga cikin waɗannan sune"
mai martaba ko mai martaba, kamar sarki
babban kaza namiji mai tafiya cikin takama
karfi da motsawa
1Maganganun sarki Lemuwel - umarnin da mahaifiyarsa ta koya masa.2Mene ne, ya ɗana? Mene ne, ɗan mahaifata? Me kake so, ɗan alƙawarina?3Kada ka bada ƙarfinka ga mata, ko hanyarka ga waɗanda ke hallakar da sarakai.4Ba girman sarakai ba ne, Lemuwel, ba girman sarakuna bane su sha giya, ko masu mulki su yi kwaɗayin abin sha mai bugarwa,5domin lokacin da suka sha sukan manta da abin da aka umartar, su kuma juyar da yancin dukkan ƙuntattu.6Ka bada abin sha mai bugarwa ga wanda ke hallaka inabi kuma ga waɗanda ke cikin ƙunci.7Zaya sha ya manta da talaucinsa kuma ba za shi tuna da wahalarsa ba.8Ka yi magana a madadin waɗanda basu iya magana, don dalilin dukkan masu hallaka.9Ka yi magana a fili ka kuma shar'anta dai-dai da ma'aunin adalci ka kuma yi roƙo sabili da nawayar matalauta da mabuƙatan mutane.10Wa ke iya samun mace cikakkiya? Darajarta ta fi duwatsu masu daraja.11Zuciyar maigidanta ta yarda ya ita, kuma ba zai taɓa talaucewa ba.12Tana yin abubuwan alheri dominsa ba mugunta ba dukkan kwanakinta.13Takan nemi ulu da lilin, ta kuma yi aiki cikin jin daɗi da hannuwanta.14Tana kama da fataken jirage; tana kawo abincinta daga nesa.15Takan tashi da dare ta bai wa iyalinta abinci, tana kuma raba wa bayinta mata aikinsu.16Takan lura da gona ta kuma saya, da ribar hannuwanta takan dasa gonar inabi.17Tana yi wa kanta ado da ƙarfi ta kuma maida kafaɗunta ƙarfafa.18Takan san abin da zai zama riba mai kyau gare ta; dukkan dare fitilarta ba ta mutuwa.19Tana ɗora hannunta bisa mazarin sãƙa, kuma ta riƙe murɗaɗɗen zaren.20Tana miƙa hannuwanta zuwa ga matalauta; tana kuma miƙa hannuwanta zuwa ga mutane mabuƙata.21Bata tsoron sanyi ta dalilin iyalinta, gama dukkan iyalinta na sanye da kayan sanyi.22Tana yiwa gadonta shimfiɗa, tana kuma sanye da tufafi masu kyau na lilin masu laushi na shunayya.23Maigidanta sananne ne a ƙofofi, lokacin da ya ke zama da shugabannin ƙasar.24Takan ɗinka riguna ta sayar, tana kuma sayar da ɗamara ga fatake.25Tana yafe da ƙarfi da daraja, kuma tana yiwa lokaci mai zuwa dariya.26Tana buɗe bakinta cikin hikima kuma dokar alheri na a bakinta.27Tana lura da tafarkin iyalanta kuma bata cin abincin zaman banza.28Yaranta na tashi su kira ta mai albarka, kuma mijinta na yabonta, cewa,29"Mata dayawa sun aikata dai-dai, amma ke kin wuce su gaba ɗaya."30Kayan kwalliya abin yaudara ne, kyau abin banza ne, amma mace mai tsoron Yahweh, za a yabe ta.31Ka ba ta 'ya'yan hannuwanta kuma bari ayyukanta su yabe ta a bakin ƙofofi.
Mai maganar yana son mai sauraro ya lura da kyau kuma ya girmama wanda yake magana da shi.
Mahaifa mahaifa ce ga mutum. Zai fi kyau a yi amfani da kalmar ladabi ga ɓangaren jikin da jarirai ke girma a cikinsu kafin a haife su.
"ko kuma ba da damar waɗanda ke halakar da sarakuna su ba ku shawara"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. Mai iya yiwuwa su ne 1) "abin da Allah Ya hukunta" ko 2) "abin da sarakuna da kansu suka hukunta"
"waye rayuka masu ɗaci" ko "waɗanda ke cikin wahala"
Jawabi na nufin amfani da kalmomi don kare mutanen da ba ruwansu. AT: "Kare waɗanda ba za su iya kare kansu ba"
Dalilin yana wakiltar mutumin da dalilin sa yake. AT: "don mutane su kula da duk waɗanda ke hallaka daidai"
Marubucin yayi tambaya don nuna cewa ya fara sabon sashe. AT: "Ba maza da yawa za su iya samun mace mai ƙwarewa ba." ko "Ba maza da yawa zasu iya samun matar da zata iya yin abubuwa da yawa da kyau."
"Ta fi daraja fiye da jauhari"
Ana iya bayyana waɗannan kalmomin da kyau. AT: "koyaushe zai sami abin da yake buƙata"
Mai yiwuwa ma'anar ita ce kalmar "ni'ima" tana bayyana 1) yadda take ji yayin da take aiki, "da farin ciki da hannunta," ko 2) yadda take ji game da ulu da lilin, "da hannunta kan abubuwan da take jin daɗin aiki. tare da "
"tana fadawa bayinta mata irin aikin da kowannensu zai yi a wannan ranar"
Kudin da ta samu daga aikin da ta yi da ulu da lilin
Sanya tufafi tsari ne na aiki. AT: "Tana shirya kanta don aiki mai wuya"
"tana karfafa hannayenta ta hanyar yin aikinta"
Wannan wataƙila ƙari ne: tana aiki har dare, amma ba daga magariba zuwa wayewar gari ba. AT: "Tana kona fitila cikin dare yayin da take aiki"
Hannun karin magana ne don taimakon da mace ke amfani da hannunta don bayarwa. AT: "yana taimakawa matalauta"
A nan "mulufi" ba yana nufin launi na zane, amma cewa tufafi masu tsada ne da dumi. AT: "ku sami tufafi masu tsada, masu dumi"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane suna girmama mijinta"
yin dokoki da sasanta jayayya
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. Sunayen "ƙarfi" da "girmamawa" ana iya fassara su da sifa da kuma fi'ili, bi da bi. AT: "Kowa ya ga tana da ƙarfi, don haka suna girmama ta"
Wannan wataƙila ƙari ne don nuna cewa ba ta tsoro. AT: "baya tsoron abin da zai faru nan gaba"
Bude bakinta aikin karin magana ne don magana. AT: "tana magana cikin hikima" ko "tana magana da hikima"
Jumlar "akan harshenta" tana nufin magana ne, kasancewar harshe ɓangaren bakin ne. Kalmar "dokar alheri" tana nufin koyarwarta mutane su zama masu kirki. AT: "tana koyawa mutane zama masu kirki"
Kalmar "hanyoyi" tana nufin yadda mutane suke rayuwa. AT: "ta tabbatar da cewa dukkan iyalinta suna rayuwa ta hanyar da za ta gamshi Allah"
Don "cin burodin" wani abu yana nufin aikata wani abu. AT: "ba ta da aikin komai"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) a zahiri "tsayawa da" ko 2) azaman metonym, "a raye."
cewa abubuwa masu kyau sun same ta saboda ta yi abubuwan alheri. Ana iya fassara wannan azaman magana kai tsaye. AT: "ku taya ta murna" ko kuma "ce," ay, Uwa!"
AT: "Mace mai kirki za ta iya yaudarar mutane" ko "Mace mai kyawawan halaye na iya zama da gaske mugunta" Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Misalai 11:15.
Za a yabe ta saboda ayyukanta, ba ayyukanta ba. Waɗanda ke “ƙofofin” su ne manyan mutanen gari waɗanda ke gudanar da kasuwanci da sha’anin shari’a kusa da ƙofar garin. AT: "mai yiwuwa mutanen gari su yaba mata saboda ayyukan da tayi"
1Waɗannan ne maganganun malami, zuriyar Dauda kuma sarki a Yerusalem.2Malami ya faɗi wannan. "Kamar turirin hayakin raɓa, kamar hurawa a cikin iska, komai na ɓacewa, su na barin tambayoyi masu yawa.3Wacce riba ce 'yan'adam suke samu daga dukkan aikin da suke yin aiki tuƙuru akai a ƙarƙashin rana?4Tsara ɗaya ta tafi, wata tsarar kuma ta zo, amma duniya ta tabbata har abada.5Rana na fitowa, kuma tana faɗuwa, tana kuma sake saurin komawa wurin da ta fito.6Iska na hurawa kudu tana kuma zagayawa kewaye zuwa arewa, koyaushe ta na tafiya kewaye bisa tafarkinta ta kuma sake dawowa.7Dukkan koguna suna gangarawa zuwa teku, amma teku bai taɓa cika ba. Inda koguna su ke tafiya, a can kuma suke sake tafiya.8Komai ya zama a gajiye, ba bu kuma wanda zai iya yin bayani. Ido bai ƙoshi da abin da ya ke gani ba, ko kuma kunne ya wadatu da abin da ya ke ji ba.9Duk abin da ya kasance shi ne zai kasance, duk kuma abin da aka taɓa yi shi ne za'a yi. Ba bu wani abu sabo a ƙarƙashin rana.10Akwai wani abu game da abin da za'a ce, 'Duba, wannan sabo ne'? Duk abin da ya wanzu ya riga ya wanzu da daɗewa, a lokacin shekarun da suka zo da daɗewa kafin mu.11Babu wanda ya ke kamar ya tuna da abubuwan da suka faru a zamanin dã, da abubuwan da suka faru daga bisani sosai da abin da zai faru a nan gaba bai yi kama da za'a tuna da shi ba ma."12Ni ne Malamin, kuma ni ne nake sarki a bisa Isra'ila a Yerusalem.13Na miƙa raina ga bincike da nemowa ta wurin hikima duk abin da ake yi a ƙarƙashin sama. Cewa nema gajiyayyen aiki ne da Allah ya ba 'ya'yan ɗan'adam suyi ta aiki da shi.14Naga dukkan ayyukan da ake yi a ƙarƙashin rana, kuma duba, dukkan su ɗungum turirin hayaƙi ne da bin iska.15Murɗaɗɗe ba za a iya miƙar da shi ba! Abin da ya ɓace ba za a iya ƙidaya wa ba!16Nayi magana da zuciyata cewa, "Duba, na sami hikima fiye da waɗanda suke kafin ni a Yerusalem. Raina yaga babbar hikima da ilimi."17Sai na miƙa zuciyata in san hikima da kuma hauka da wawanci. Sai na kai ga fahimtar cewa wannan ma wani yunƙuri ne na kiwon iska.18Gama a cikin yalwar hikima akwai ruɗewa sosai, shi kuma wanda ke ƙara ilimi yana ƙara baƙinciki.
Wannan na magana game da yadda komai a rayuwa ke ɓacewa kuma bai da daɗewa kamar yadda komai ke kama da ɓacewar turir ko iska. AT: "Kamar turiri hayaƙin raɓa ke ɓacewa kuma kamar hurawa a cikin iska ke ɓacewa, komai ke ɓacewa kuma bai daɗewe"
Marubucin na amfani da wannan tambayar domin ya jajjada cewa aikin mutum wofi ne kuma ba shi daɗewa. Za'a iya rubuta wannan tambayar kamar magana. "Yan adam ba su da wata riba ... a kalkashin rana."
Wannan na nufin abubuwan da ake yi a duniya. AT: "a duniya"
Mai rubutun ya na bayanna yadda shirin rayuwa ya ke kamar yadda ya gane ta.
Wannan na magana game da da yadda rana ke tafiya a ƙarshen rana kuma nan da nan ta ne shirye ta sake fitowa, kamar ita mutum ne da ke gudu da sauri daga wurin da ta tafi daga inda ta fito. AT: "Dawowa wurin da sauri" ko "tafi wurin da sauri"
"Komai ya zama abun gajiya" Tun da shike mutum bai iya bayyan waɗannan abubuwan, to ya zama wofi a gwada.
A nan "ido" na waƙiltar dukan mutum. AT: "Mutum ba ya isa da abun da idanunsa suka gani"
za'a iya juya faɗar wannan aikace. AT: "duka abinda ya faru a dã shine abinda zai sake faruwa"
Ana yin wannan tabayar ne don a jajjada cewa mutum ba zai iya cewa akwai wani abu sabo ba. Za a iya rubuta wannan kamar magana. AT: "Babu wani abu sabo game da za a ce, 'Duba, wannan sabo ne.'"
Za a iya juya wannan a aikace. AT: "game da wani zai ce"
A nan marubucin na nufin kansa ta wurin "raina" don ya jajjada tunaninsa. AT: "Na mika" ko "Na mika raina"
Waɗannan furci guda biyu na nufin abu ɗaya kuma ƙarin bayani ne domin bincike.
"'yan'adam"
Marubucin na anfani da wannan kalma don ya jawo hankali zuwa ga abinda zai ce a nan gaba. AT: "Haƙiƙa" ko "tabbas"
A nan marubucin na nufin kansa ta wurin AT: "zuciya" don ya jajjada abinda yake ji. AT: "Na yi magana da kai na"
Kalmonin su na nufin "hauka" da kuma "wawanci" ka maimaita ma'anar ka kuma nuna wawancin tunani da kuma hali, a jere.
Marubucin ya ce koyon ilimi da hauka da kuma wawanci bai da anfani ne kamar ƙoƙarin tare iska. Dubi yadda aka juya wannan Mai Wa'azi 1:14. AT: "mara anfani kamar ƙoƙarin tare iska"
1Na cewa zuciyata, "Zo yanzu, zan gwada ki da murna. Sai ki more jin daɗinki." Amma duba, wannan ma 'yar taƙaitacciyar iska ce.2Game da dariya na ce, "Taɓin hankali ce," game da jin daɗi kuma, "Ina amfanin shi?"3Na nemo a zuciyata yadda zan biya buƙatar marmarina da ruwan inabi. Na bar raina ya bishe ni da hikima kodaya ke har wa yau ina riƙe da wawanci. Na so in samo abu mai kyau da mutane za suyi a ƙarƙashin sama a lokacin kwanakin rayuwarsu.4Na aiwatar da manyan abubuwa. Na gina gidaje domin kaina na kuma dasa garkunan inabi.5Na ginawa kaina lambuna da tashoshin shaƙatawa; na dasa dukkan ire-iren itatuwa masu ba da 'ya'ya a cikin su.6Na ƙirƙiro tafkunan ruwa domin su bada ruwa ga jejin da ake renon itatuwa.7Na sawo bayi maza da bayi mata; An haifa ma ni bayi a fãdata. Kuma ina da manyan garkunan shanu da garkunan tumaki da awaki, fiye da duk wani sarki da ya yi mulki kafin ni a Yerusalem.8Na kuma tarawa kaina azurfa da zinariya, dukiyar sarakuna da larduna. Na samar wa kai na mawaƙa maza da mata - abin farincikin 'ya'yan 'yan'adam - da ƙwaraƙwarai masu yawa.9Sai na zama mafi girma da dukiya fiye da dukkan waɗanda suke kafin ni a Yerusalem, kuma hikimata ta kasance tare da ni.10Duk abin da idanuna suka yi marmari, ban hana masu ba. Ban hana wa zuciyata duk wani jin daɗi ba, saboda zuciyata na farinciki cikin dukkan aikin ƙarfina kuma jin daɗi shi ne ladata domin dukkan aikina.11Daga nan na duba dukkan ayyukan da hannuwa na suka aiwatar, da aikin da nayi, amma kuma, kowanne abu turiri ne da yunƙurin kiwon iska. A ƙarƙashin rana babu wata riba a cikin su.12Daga nan na juya in yi la'akari da hikima, da kuma hauka da wawanci. Gama me sarki na gaba zai yi wanda zai zo bayan sarki, wanda ba a riga anyi ba?13Daga nan na fãra fahimtar cewa hikima na da daraja bisa wawanci, kamar yadda haske yafi duhu.14Mutum mai hikima ya kan yi amfani da idanunsa cikin kansa ya ga inda ya ke tafiya, amma wawa yana tafiya cikin duhu, ko da ya ke na san al'amura iri ɗaya ne ke faruwa da dukkan su.15Daga nan na ce a cikin zuciyata, "Abin da ya fãru da wawa, ni ma zai fãru da ni. To ina ban-banci idan ina da wayau sosai?" Sai na kammala a cikin zuciyata, "Wannan ma turirin hayaƙi ne kawai."16Domin mutum mai hikima, kamar wawa, ba a tunawa da shi har dogon lokaci sosai. A cikin kwanaki masu zuwa an riga an manta da komai. Mai wayau na mutuwa kamar yadda wawa ke mutuwa.17Sai rayuwa ta gundure ni saboda dukkan aikin da ake yi a ƙarƙashin rana mugunta ce a gare ni. Wannan kuwa saboda komai turiri ne kawai da yunƙurin kiwon iska.18Na ƙi jinin dukkan abin da na aiwatar wanda na aikata a ƙarƙashin rana saboda tilas in bar su baya ga mutumin da zai zo bayana.19Gama wa ya sani ko zai zama mutum mai hikima ko wawa? duk da haka zai zama shugaba bisa komai ƙarƙashin rana wanda aikina da hikimata suka gina. Wannan ma turirin hayaƙi ne.20Saboda haka zuciyata ta fãra razana bisa dukkan aikin da nayi a ƙarƙashin rana.21Domin za a sami wanda ya ke aiki tare da hikima, tare da ilimi, da ƙwarewa, amma zai bar duk abin da ya ke da shi ga mutumin da bai yi wani abu kamar sa ba. Wannan ma turirin hayaƙi ne da tsautsayi mai girma.22Domin wacce riba taliki ya samu wanda ya yi aiki tuƙuru kuma ya yi ƙoƙari a zuciyarsa ya kammala aikin ƙarfinsa a ƙarƙashin rana?23Kowacce rana aikin shi cike da ciwo da gajiya, sa'an nan da dare ransa ba ya samun hutawa. Wannan ma turirin hayaƙi ne.24Babu wani abin da ya fiye wa kowa baya ga ya ci ya sha ya ƙoshi da abin da ke mai kyau cikin aikinsa. Naga cewa wannan gaskiyar ta zo daga hannun Allah ne.25Gama wane ne zai iya ci ko ya sami wani irin jin daɗi idan ba daga Allah ba?26Domin ga dukkan wanda ya ke faranta masa rai, Allah na bayar da hikima da ilimi da farinciki. Duk da haka, ga mai zunubi yana bayar da aikin tattarawa da adanawa domin ya bayar da su ga wanda ya ke farantawa Allah rai. Wannan ma ɗungum turirin hayaƙi ne da yunƙurin kiwon iska.
A nan marubucin na nufin kansa ne da ya ce "zuciyarsa" domin ya bayyana yadda yake ji. AT: "Na ce wa zuciyata"
A nan kalman "ka" ya na nufin kansa. AT: "Zan gwada kaina da abubuwan da su ke sani murna"
Za a iya bayyana kalman nan "daɗi" a aikace. AT: "Zan more abubuwan da suke sa ni jin daɗi"
Wannan na magana tunani mai zurfi na tsawon lokaci kamar ya na nema. Kuma, marubucin na maganar yadda yake ji da tunaninsa kamar su "zuciyar shi ne." AT: "Na yi tunani mai zurfi"
Za a iya bayyan kalman nan "marmarina" kamar maganar baki. AT: "zan yi anfani da ruwan inabi domin in yi murna"
Marubucin wataƙila ya faɗa wa mutane su yi aiki. AT: "Na ji mutane sun gina gidaje sun kuma shuka garkunan inabi"
"a tanaji ruwa don ƙurmin daji"
"Ina da bayi da aka haifa mani a fadata" ko "Bayina sun haifa mani 'ya'ya kuma suma bayi na ne"
Wannan ya na nufin zinariya da dukiyar da wasu makwabtan ƙasashe aka tilasta masu su biya wa sarkin Isra'ila. AT: "wanda na samu daga dukiyar sarakuna da masu mulkin larduna"
Wannan na nufin cewa ya na da kwarakwarai mata da ya ji ɗaɗinkwana da su, kamar yadda kowane namiji ke jin ɗaɗin kwana da mata. AT: "Ina jin dadin mata na da kwarakwarai na, fiye da kowane namiji zai ji"
"Na ci gaba da nuna hikima" ko "Na ci gaba da zama mai hikima"
AT: "Duk abinda idanuna suka gani kuma suka yi marmari"
Ana iya fadin wannan haka. AT: "Na samo wa kaina"
Marubucin yayi anfani da tamabaya domin yi wa kansa ƙorafin cewa sarki ma zuwa ba zai iya yin wani abu fiye da wanda ya riga yayi ba. AT: "Gama sarki na gaba ba zai yi komai ba ... wanda ba a riga anyi ba."
Wannan na maganar yadda hikima ta fi wawanci, ta wurin kwatanta yadda haske yafi duhu.
Wannan na maganar mutum mai hikima da ke yanke shawarar hikima kamar tafiya da kula da inda yake tafiya. AT: "Mutum mai hikima yana kamar mutum wanda yake anfani da idanunsa domin ya ga inda za shi"
Marubucin yayi anfani da wannan tambayar domin ya nuna babu riba domin hikima.AT: "Saboda haka babu banbanci domin ina da hikima."
Za a iya faɗin wannan a aikace. AT: "da mutane sun manta da komai da ɗaɗewa"
Za a iya faɗin wannan a aikace. AT: "dukkan aikin da mutane suke yi"
"ya dame ni"
"zuwa ga mutumin da ya gaji shi baya na"
Marubucin ya yi wannan tambayar don ya jajjada cewa babu wanda halin mutumin da zai gaji dukiyar shi. AT: "Gama wa ya sani ko zai zama mutum mai hikima ko wawa."
Wannan kalma "shi" na nufin magajin marubucin.
"mummunar bala'i"
Waɗannan maganganun biyu na nufin abu ɗaya ne kuma suna jajjada yadda mutumin ya duƙufa yin aiki sosai.
A nan zuciyar mutum ake nufin da "rain sa" don a jajjada tunaninsa mai zurfi. AT: "zuciyarsa bai huta ba" ko "ya ci gaba da damuwa"
A nan an wajabta Allah da "hannunsa" domin a jajjada yadda yake biya buƙatun mutane. AT: "daga Allah"
Kalman nan "shi" yana nufin 1) Allah ko 2) mai zunubin. Kalman nan "ga" yana nufin abinda mai zunubi ya tara a wurin ajiya. Wannan juyin wata hanya ce ta fadar haka batare da nuna wanda yake ba da abinda muka tara ba. AT: "domin wanda shi faranta wa Allah rai ya same ta"
1Game da kowanne abu akwai tsaidajjen lokaci, da zamani domin kowanne dalili ƙarƙashin sama.2Akwai lokacin haihuwa da lokacin mutuwa, lokacin dasawa da lokacin tuge dashe-dashen,3lokacin kashewa da lokacin warkarwa, lokacin yagawa da lokacin ginawa.4Akwai lokacin kuka da lokacin dariya, lokacin makoki da lokacin rawa,5lokacin zubar da duwatsu da lokacin tattara duwatsu, lokacin rungume wasu mutane da lokacin janyewa daga rungumewa.6Akwai lokacin dubawa domin abubuwa da lokacin tsayawa daga dubawar, lokacin ajiye abubuwa da lokacin zubar da abubuwa,7lokacin yaga sutura da lokacin gyara sutura, lokacin yin shiru da lokacin magana.8Akwai lokacin ƙauna da lokacin ƙiyayya, lokacin yaƙi da lokacin salama.9Wacce riba ma'aikaci ke ci cikin aikin ƙarfinsa?10Naga aikin da Allah yaba talikai su kammala.11Allah ya yi kowanne abu ya dace domin nasa lokaci. Ya sa madawwamin lokaci a zukatansu. Amma 'yan'adam ba zasu fahimci ayyukan da Allah ya yi ba, daga farkonsu har ya zuwa ƙarshensu.12Nasan babu abin da ya fiye wa kowa baya ga ya yi farinciki ya kuma yi abin da ke mai kyau dukkan tsawon rayuwarsa -13kowa kuma ya ci ya sha, ya kuma fahimci yadda zai ji daɗin abin da ke zuwa daga dukkan aikinsa. Wannan kyauta ce daga Allah.14Nasan cewa dukkan abin da Allah ya yi yana dawwama har abada. Babu abin da za a ƙãra akai ko a ɗauke, saboda Allah ne ya yi domin mutane su kusance shi tare da girmamawa.15Kowanne abu da ke wanzuwa ya rigaya ya wanzu; kowanne abu da zai wanzu ya rigaya ya wanzu. Allah ya sa talikai su nemi ɓoyayyun abubuwa.16Na kalli muguntar da ke ƙarƙashin rana, inda ya kamata a yi hukunci, a gurbin adalci, mugunta ce ke wurin.17Na ce a zuciyata, "Allah zai shar'anta mai adalci da mugu a lokacin da ya dace domin kowanne al'amari da kowanne aiki."18Na ce a zuciyata, "Allah na gwada talikai ya nuna masu cewa kamar dabbobi suke."19Gama ƙaddarar ɗan'adam da ƙaddarar dabbobi ƙaddara ce iri ɗaya domin su. Mutuwar ɗaya kamar mutuwar ɗayan ce. Lumfashin iri ɗaya ne domin dukkan su. Babu wata daraja game da ɗan'adam fiye da ta dabbobi. Domin kowanne abu ba lumfashi ne kawai ba?20Kowanne abu na tafiya wuri ɗaya. Kowanne abu ya zo daga turɓaya, kuma kowanne abu zai koma ga turɓaya.21Wa ya sani ko ruhun ɗan'adam na tafiya sama kuma ruhun dabbobi na tafiya ƙasa cikin ƙasa?22Sai kuma na gane cewa babu abin da ya fiye wa kowa banda ya ji daɗin aikinsa, domin wannan ne hidimarsa. Wa zai maido da shi baya yaga abin da ke fãruwa bayansa?
Marubucin ya ci gaba da lisafta yanayi ta rayuwa daga fanni ɗaya zuwa ga wata.
Wannan na nufin abubuwan da ake yi a duniya. Dubi yadda za ka juya wannan a Mai Wa'azi 1:3. AT: "a duniya"
rungume wani a ƙafata domin nuna ƙauna ko aboƙantaka
Wannan tambaya ce mai sanya zurfin tunani don maida mai karatun ya kula da kan maganar tautaunawa mai zuwa a gaba. Juya "wane riba ne ... samu" kamar yadda kayi a Mai Wa'azi 1:3. AT: "Ma'aikacin bai sami ko riba ba a aikinsa"
"Allah ya sa lokaci da ke dai-dai domn komai ya faru" ko "Allah ya sanya lokaci da ke daidai don kowane abu ya faru"
A nan kalman "a"yana nufin mutane. AT: "ya sa lokaci madawwami a zukatansu"
Wannan na nufin farko da ƙarshe da kuma duka da ke a tsakanin su.
"ya koyi yadda zai ji daɗi" ko "ya ji daɗi"
Za a iya faɗin wanna a aikace. AT: "Babu wanda zai iya ƙara komai ko ya rage komai daga ciki"
Wannan kalmomin biyu na nufin abu ɗaya da karin bayani a kan halin mugunta.
"a inda ya kamata akwai adalci"
Wnnan na magana game da masu adalci da masu mugunta. AT: "waɗanda suke da adalci da waɗanda suke da mugunta" ko "mutane masu adalci da mjutane masu mugunta"
A nan marubucin ya ce mutane na kama da dabbobi. A aya ta gaba marubucin ya yi bayyana yadda mutane ke kama da dabbobi.
Kamar dabbobi, mutane duka ke mutuwa. Dole ne dukansu su shaƙi iska ɗaya. Komai na zuwa ne daga turɓaya, kuma koma na komawa ne ga turɓaya.
Marubucin ya yi tambaya domin jajjada cewa gaskiya babu wanda ya san me ke faruwa idan mutane da dabbobi suka mutu. Za a iya rubuta wannan tambayar kamar magana. AT: "Babu wanda ya sani ko ruhu ... cikin ƙasa."
Marubucin yayi amfani da wannan tambayar don ya jajjada cewa babu wanda zai ga abunda zai faru bayan ya mutu. Za a iya rubuta tambayar kamar magana. AT: "Babu wanin mu da ya san abunda zai faru da mu bayan mun mutu."
1Na sake yin tunani game da cutarwar da ke faruwa a ƙarƙashin rana. Duba kuma, hawayen mutanen da aka cuta, babu kuma wanda zai ta'azantar da su! Iko na hannun masu cutar da su, babu kuma wanda zai ta'azantar da su!2Sai na yi la'akari da cewa waɗanda suka mutu sun fi waɗanda ke da rai morewa, waɗanda har yau suna raye.3Duk da haka, wanda ya fisu dukka morewa shi ne wanda bai riga ya rayu ba, wanda bai riga ya ga ayyukan muguntar da ake yi ba ƙarƙashin rana.4Daga nan naga cewa kowanne aikata aiki da aikin ƙwarewa ya zama kishin maƙwabcin wa ni. Wannan shi ma turirin hayaƙi ne da yunƙurin kiwon iska.5Wawa yana naɗe hannuwansa kuma baya aiki, domin wannan abincinsa jikinsa ne.6Amma gwamma riba kaɗan tare da aikin natsuwa da hannuwa biyu cike da aikin ƙoƙarin kiwon iska.7Daga nan na sake yin tunani game da ƙarin aikin wofi, ƙarin turirin hayaƙi mai ɓacewa a ƙarƙashin rana.8Akwai wani irin mutum da ya ke shi kaɗai. Bai da kowa, ba ɗa ko ɗan'uwa. Babu ƙarshe ga dukkan aikinsa, idanunsa ba su ƙoshi da neman wadata. Yana mamaki, "Domin wa nake wahala ina hana wa kaina jin daɗi?" Wannan ma turirin hayaƙi ne, al'amari marar kyau.9Mutum biyu za su yi aiki fiye da ɗaya; tare za su sami biya mai kyau game da aikinsu.10Domin idan ɗaya ya fãɗi, ɗayan zai iya ɗaga abokinsa. Duk da haka, baƙinciki na biye da wanda ke shi kaɗai sa'ad da ya fãɗi idan babu wanda zai iya ɗaga shi.11Idan biyu suka kwanta tare, za su iya jin ɗumi, amma ta yaya ɗaya zai ji ɗumi shi kaɗai?12Za a iya fin ƙarfin mutum ɗaya shi kaɗai, amma biyu za su iya yin tsayayya da hari, igiya uku a murɗe ba za su yi saurin tsinkewa ba.13Gwamma wani ya zama matashi talaka amma mai wayau da tsohon sarki wawa wanda ya daina sanin yadda ake sauraron kashedi.14Wannan gaskiya ne koda saurayin ya zama sarki daga kurkuku, ko kuma an haife shi talaka a masarautarsa.15Na kalli kowa wanda ya ke da rai kuma yana yawonsa a ƙarƙashin rana, tare da matashin da ke tasowa ya maye gurbinsa.16Babu ƙarshen dukkan mutanen da suke so suyi biyayya da sabon sarki, amma daga ba ya yawancin su ba zasu sake yabonsa ba. Tabbas wannan al'amari turirin hayaƙi ne da yunƙurin kiwon iska.
"Na duba kuma na gani"
A nan "hawaye" na wajabtar kuka. AT: "mutanen da aka ƙuntata wa na kuka"
Wannan na nufin cewa masu ƙuntata masu na da iko. A nan "hannunsu" na wajabta abun da suka mallaka. AT: "Masu ƙuntata masu na da Iko"
"Wanda bai riga ya an haifa ba ya fi su duka biyun"
Wannan na nufin waɗanda suka mutu da kuma waɗanda suke da rai. AT: "duka waɗanda suka mutu da kuma waɗanda ke a raye"
Ma'anar na iya zama haka 1) makwabcin ya na kishin abinda makwabcinsa ke da shi ko 2) makwabcinsa ya kyashin kwarewar makwabcinsa.
Waɗannan bayani biyu na jajjada sanin cewa abubuwan nan banza ne da kuma wofi.
Naɗe hannu alama ce ta ragonci kuma wata hanya ce ta cewa mutumin yaƙi yin aiki. AT: "Wawa ya ƙi yayi aiki"
Wannan na magana a kan mutumin da ke rushe kansa kamar yan cin naman jikinsa. AT: "saboda haka, ya jawo wa kansa ɓarna" ko "domin haka, ya rushe kansa"
"kimani kaɗan"
a banza, ba riba
Wannan mutumin bashi da iyali. AT: "ba shi da iyali"
A nan an wajabta mutumin gabaki ɗaya ta wurin "idanunsa" don a jajjada muraɗin zuciyarsa. AT: "ba shi ƙoshi ba"
A nan anyi maganar ƙunci kamar mutum ne da zai iya bin wani daban. AT: "wanda yake shi kaɗai a lokacin da ya faɗi yane cikin ƙunci"
Marubucin ya na magana ne a kan mutane biyu da suke ba wa juna ɗumi a dare mai sanyi. AT: "Idan mutum biyu suka kwanta tare da dare, zasu zama da ɗumi"
Za a iya rubuta wannan a aikace. AT: "Wani zai iya cin ƙarfin mutumin da ke shi ƙadai"
"amma mutum biyu"
"kare kai idan an kawo hari"
"matashi mai hikima"
"bayan zama a bursuna"
Wannan na nufin cewa yana da iyaye talakawa. AT: "an haife shi ga iyaye talakawa wanda zai zauna a kasar yayi mulkinta wata rana"
Maimakon zaɓen saurayi mai hikima, mutanen suka zaɓi dan sarki, wanda mai yiwuwa ba shi da hikima ko kaɗan.
Wannan ƙarin magana ne da ake amfani a jajjada yawan lambar mutane. AT "Akwai mutane da yawa"
1Ka kiyaye takawarka sa'ad da ka je gidan Allah. Ka matsa kusa ka saurara fiye da miƙa hadayar wawaye, waɗanda basu fahimci cewa suna yin abin da ba dai-dai ba.2Kada ka yi saurin magana da bakinka, kada kuma ka yi saurin barin zuciyarka ta fito da wani al'amari a gaban Allah. Allah na sama, amma kai ka na duniya, sai ka bari maganganunka su zama kaɗan.3Idan kana da abubuwa da yawa da za ka yi kuma ka da mu a kai, zai yiwu ka sami miyagun mafarkai. Kana ƙara yawan maganganun da zaka furta, kana ƙara yawan abubuwan shirme da zaka iya faɗa.4Sa'ad da ka ɗauki alƙawari ga Allah, kada ka yi jinkirin aikatawa, domin Allah ba ya jin daɗin wawaye. Ka yi abin da ka yi alƙawarin za ka yi.5Gwamma kada ka ɗauki alƙawari da ka ɗauki wanda ba ka aiwatar ba.6Kada ka bar bakinka yasa jikinka ya yi zunubi. Kada ka cewa manzon firist, "Wannan alƙawari kuskure ne." Meyasa za ka ba Allah haushi ta wurin alƙawarin ƙarya, kana tunzura Allah ya rushe aikin hannuwanka?7Gama a cikin yawan mafarkai, kamar a cikin yawan maganganu, akwai turirin hayaƙi marar ma'ana. Sai ka ji tsoron Allah.8Sa'ad da kaga ana zaluntar matalauci kuma ana karɓe masa hakkinsa da ke dai-dai a cikin lardinka, kada ka yi mamaki kamar cewa babu wanda ya sani, saboda akwai mutane da ke kan mulki waɗanda ke lura da waɗanda ke ƙarƙashinsu, akwai kuma waɗanda suka fisu iko sama da su.9Bugu da ƙari, amfanin ƙasar domin kowa ne, sarki kuma kansa yana ɗaukar amfani daga gonakin.10Duk wanda ke ƙaunar azurfa ba zai ƙoshi ba da azurfa, duk kuma wanda ke ƙaunar dukiya a koyaushe yana son ƙãri. Wannan, shi ma, turirin hayaƙi ne.11Yadda wadata ke ƙaruwa, haka ma mutanen da ke cin ta. Ina amfanin dukiya ga mai ita baya ga ya yi ta kallon ta da idanunsa?12Barcin ma'aikaci mai daɗi ne, ko ya ci kaɗan ko da yawa, amma dukiyar mai arziki bata barin shi ya yi barci sosai.13Akwai muguntar da na gani a ƙarƙashin rana: dukiyar da mai ita ya ɓoye, ita ce sakamakon azabarsa.14Sa'ad da mai arziki ya rasa dukiyarsa ta wurin rashin sa'a, ɗansa, wanda ya haifa, za a bar shi ba komai a hannuwansa.15Yadda mutum ya zo daga mahaifar mahaifiyarsa, haka ma zai tafi tsirara. Ba zai tafi da ko ɗaya daga cikin aikin ƙarfinsa ba cikin hannunsa.16Wani mugun abin kuma shi ne yadda mutum ya zo, haka ya ke tafiya. To wacce riba ce ke akwai game da shi wanda ya ke aiki domin iska?17A lokacin kwanakinsa ya ci tare da duhu kuma ya ƙuntata kwarai tare da ciwo da fushi.18Duba, abin da na ga yafi kyau da dacewa kuma shi ne mu ci mu sha mu kuma ji daɗin riba daga dukkan aikinmu, yayin da muke aiki tuƙuru ƙarƙashin rana a lokacin kwanakin rayuwarmu wadda Allah ya ba mu. Gama wannan ne hidimar mutum.19Duk wanda Allah ya ba arziki da dukiya da ikon karɓar rabonsa ya kuma yi farinciki cikin aikinsa - wannan kyauta ce daga Allah.20Domin ba ya yawan tunawa da kwanakin rayuwarsa, saboda Allah ya sa yana ta hidima da abubuwan da ya ke jin daɗin aiwatarwa.
A nan "tafiya" wata kalma ce mai nufin halin mutum. AT: "Ka bi a hankali yadda halin ka yake"
A nan maganare nan "tare da bakinka"na jaddada kuma na bayyana cewa mutum na magana. AT: "kayi magana"
"kada ka yi magana dayawa"
Ya na nufin cewa wawanci ne ka yi jinkirin cika alƙawarin da ka yi wa Allah. AT: "ka da kayi wawanci a yin shi, domin Allah ba ya jin daɗin wawayen mutane"
A nan "bakin mutum"na wakiltar jawabin, kuma "naman jikin""mutumin na wakiltar shi kan shi. Kada ka bar abinda ka faɗa ya sa kayi zunubi"
A nan "hannun" mutum ne ke wakiltar shi. AT: "lalata duk abinda ka yi"
AT: "mutane suna zaluntar matalauta suna kuma karbe masu hakkinsu"
Marubucin yayi magana a kan abubuwa marasa amfani da marasa ma'ana kamar hazo. Dubi yadda ka juya shi a Mai Wa'azi 1:14. AT: "mara amfani kamar turiri" ko "mara amfani"
Wannan na magana a kan mutane masu kashe dukiya kamar suna "cinye" shi. AT: "wa yayi amfani da shi"
Wannan na magana a kan barcin mutumin da ke cikakke kuma na salama kamar ya na da daɗi kamar abinda akae ci. AT: "Barcin ma; aikaci na da salama"
ämma dukiyar mai arziƙi na ajiye shi a farke da dare." Wannan na magana cewa mai arziƙi ba ya iya barci don damuwa game da kuɗin sa kamar mutum ne da ba zai bar shi yayi barci ba. AT: "amma masu arziƙi basu barci da da kyau domin suna damuwa a kan kuɗinsu"
Za'a iya gadɗin wannan a aikace. AT: "mai dukiya ya ɓoye dukiyarsa"
Ma'ana ma yiwuwa 1) "ta masifa" or 2) "ta muguwar yerjejeniyar harka."
Ya na nufin cewa mutum na tsirara a lokacin da aka haife shi. Bugu da ƙari a kan rashin tufafi, a nan "tsirara" yana jaddada yadda aka haifi mutane ba da komai ba. AT: "mutum tsirara yake kuma bashi da komai da aka haife shi ... zai yi rayuwarsa haka"
Wannan na nufin mutuwa. AT: "zai mutu"
A nan "kwanakinsa"na wakiltar rayuwarsa. AT: "rayuwarsa"
Marubucin yayi amfani da kalman a nan domin ya jawo hankalin masu karatu ga abinda zai ce a nan gaba. AT: "Maida hankali" or "ka saurara"
Ma'ana mai yiwuwa su ne 1) "Domin wannan ladan mutum ne" ko 2) "Domin waɗannan abubuwa ne da ya bar mutum ya yi"
Waɗannan kalmomin suna nufin abu ɗaya ne. Suna nufin kuɗi da abinda kuɗi zai saya.
"ya karɓi abinda aka ba shi"
"ci gaba da aiki"
1Akwai wata mugunta da na gani a ƙarƙashin rana, kuma ta yi babban nauyi bisa mutane.2Allah zai iya ba mutum arziki, dukiya, da daraja yadda bai rasa wani abin da ya ke marmari ba domin kansa, amma daga nan Allah bai bashi ikon jin daɗin su ba. Maimako, wani daban ke amfani da abubuwansa. Wannan turirin hayaƙi ne, muguwar azaba.3Idan mutum ya zama mahaifin 'ya'ya ɗari kuma ya rayu shekaru masu yawa, yadda kwanakin shekarunsa masu yawa ne, amma idan zuciyarsa bata ƙoshi da abu mai kyau ba kuma ba a bizne shi ba, daga nan na ce gwamma jaririn da aka haifa matacce da shi.4Wannan irin jariri ma an haife shi a wofi kuma ya wuce cikin duhu, sunansa kuma ya rage ɓoyayye.5Ko da ya ke wannan ɗan bai ga rana ba ko kuma ya san wani abu, ya huta koda ya ke wancan mutum bai huta ba.6Koda mutum zai yi rayuwa shekaru dubu biyu amma bai koyi ya ji daɗin abubuwa masu kyau ba, yana tafiya wuri guda kamar kowa da kowa.7Dukkan aikin mutum domin bakinsa ne, duk da haka ɗanɗanonsa ba ya ƙoshi.8Tabbas, wacce moriya mai wayau ya ke da ita bisa wawa? Wacce moriya matalauci ya ke da ita koda ya san yadda zai aiwatar a gaban sauran mutane?9Gwamma a ƙoshi da abin da idanu ke gani da ayi marmarin abin da ɗanɗano ke sha'awa barkatai, wanda shi ma turirin hayaƙi ne da yunƙurin kiwon iska.10Duk abin da ya wanzu an riga an ba shi sunansa, kamannin mutum kuma an riga an san shi. Sai ya zama marar amfani ayi saɓani da babban mai hukunta kowa.11Ana ƙãra maganganun da ake faɗa, ana ƙãra yawan aikin wofi, to ina moriyar wannan ga mutum?12Gama wa yasan abin da ke mai yau domin mutum a cikin rayuwarsa a lokacin, lissafin kwanakinsa na wofi ta inda ya ke wucewa kamar inuwa? Wa zai gayawa mutum abin da zai fãru a ƙarƙashin rana bayan da ya mutu?
A nan an yi maganar mugunta kamar wani anu da ke da nauyin ɗauka. AT: "ta jawo wahala ga mutane"
Wannan abu mara kyau biyu ne. AT: "ya na da komai"
"bai ba shi iyawa ba"
Waɗannan maganganun na nufin abu ɗaya ne kuma an haɗa su tare don a jajjada. AT: "rayuwar shekaru masu yawa"
Wannan na nufin mutum ta wurin "zuciyarsa" ba domin jajjada yadda yake ji. AT: "ba shi wadace da abubuwa masu kyau"
Wannan na magana a kan cewa ba wanda ya san sunan jaririn kamar ɓoyeyyen abu ne"
"shekaru 2,000"
Wannan na nufin cewa ya mutu kamar dukan mutane. AT: "ya mutu kuma ya je wuri ɗaya kamar kowanne mutum"
A nan sa abinci cikin bakinsa na wakiltar ciyar da shi. AT: "domin ya sa abinci a bakinsa" ko "a ciyar da shi"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "bai wadatar da son cin abincinsa ba"
"yadda za ya gudanar da kansa
Mutum na iya ganin waɗannan abubuwa domin ya riga ya gansu. AT: "abinda mutum yake da shi"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "mutane sun rigaya sun bada suna wa duk abinda ya rigaya ya kasance"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "mutane sun rigaya sun san yadda 'yan adam suke kama"
mara amfani, ba riba
Wannan tattausan furci ne wa mutuwa. AT: "bayan ya mutu"
1Suna mai kyau ya fi turare mai tsada, kuma ranar mutuwa ta fi ranar haihuwa.2Gwamma a je gidan makoki da a je gidan biki, domin makoki yana zuwa ga dukkan mutane a ƙarshen rayuwa, to mutanen da ke raye tilas su ɗauki wannan a zuciya.3Ɓacin rai ya fi dariya, domin bayan baƙinciki a fuska sai farinciki a zuciya ya zo.4Zuciyar mai hikima na gidan makoki, amma zuciyar wawaye na gidan biki.5Gwamma a saurari tsautawar mai hikima da a saurari waƙar wawaye.6Domin kamar ƙarar ƙayoyin da ke ƙonewa a ƙarƙashin tukunya, haka ma dariyar wawaye. Wannan, ma, turirin hayaƙi ne.7Babu shakka ƙwace na sa mutum mai hikima ya zama wawa, kuma cin hanci na ɓãta zuciya.8Gwamma ƙarshen al'amari da farkonsa; kuma mutane masu haƙuri a ruhu sun fi mutane masu girman kai a ruhu.9Kada ka yi saurin fushi a ruhunka, domin fushi na zama cikin zukatan wawaye.10Kada ka ce, "Me ya sa kwanakin dã suka fi waɗannan?" Domin ba saboda hikima ka yi wannan tambaya ba.11Hikima, kamar gãdo, mai kyau ce, waɗanda ke ganin rana na moriyar ta.12Domin hikima na bada kariya kamar yadda kuɗi ke bada kariya, amma darajar ilimi shi ne hikima na ba da rai ga duk wanda ke da ita.13Yi la'akari da ayyukan Allah: Wa zai miƙar da duk abin da ya tanƙwarar?14Sa'ad da lokutta ke da kyau, ka zauna da murna cikin kyaun nan, amma sa'ad da lokutta suka ɓaci, yi la'akari da wannan: Allah ya bar dukkan su su wanzu gefe da gefe. Domin wannan dalili, babu wanda zai san wani abu da ke zuwa bayansa.15Naga abubuwa masu yawa a cikin kwanakina marasa ma'ana. Akwai mutane masu adalci da ke hallaka duk da adalcinsu, akwai kuma mutane masu mugunta da ke yin tsawon rai duk da muguntarsu.16Kada ka zama mai adalcin kai, mai hikima a idanunka. Meyasa za ka hallakar da kanka?17Kada ka zama mai yawan mugunta ko wawanci. Meyasa za ka mutu kafin lokacinka?18Yana da kyau ka riƙe wannan hikimar, kuma kada ka saki adalci. Domin talikin da ke da tsoron Allah zai kiyaye dukkan farillansa.19Hikima na da ƙarfi sosai a cikin mutum mai wayau, fiye da shugabanni goma a cikin birni.20Babu mutum mai adalci a duniya da ke aikata nagarta kuma bai taɓa yin zunubi ba.21Kada ka saurari dukkan maganar da aka furta, saboda kana iya jin bawanka na la'antar ka.22Haka nan kuma, ka sani da kanka cewa a cikin zuciyarka kana yawan la'antar wasu.23Dukkan waɗannan na tabbatar ta wurin hikima, na ce, "Zan yi wayau," amma ya fi abin da zan iya zama.24Hikima na nesa kuma da zurfi sosai. Wa zai same ta?25Na juya zuciyata in koya kuma in jaraba kuma in biɗi hikima da bayanan zahiri, in kuma fahimci cewa mugunta sakarya ce kuma wawanci hauka ne.26Na gano cewa abin da yafi mutuwa ɗaci shi ne ko wacce mata wadda zuciyarta ke cike da tarkuna da tãrurruka, wadda kuma hannuwanta sarƙoƙi ne. Duk wanda ya gamshi Allah zai kucce daga gare ta, amma zata ɗauke mai zunubi.27"Yi la'akari da abin da na gãno," cewar Malamin. "Ina ta tãra gãnowa bisa gãnowa domin in samo bayanin zahiri.28Wannan ne har yanzu nake nema, amma ban same shi ba. A cikin dubu na sami namiji ɗaya mai adalci, amma a cikin dukkan waɗannan ban sami mace ɗaya ba.29Wannan ne kawai na gãno: Cewa Allah ya halicci 'yan'adam dai-dai, amma suka tafi neman wahalhalu da yawa."
A nan ana amfani da "sunan" mutane don wakiltar sunansu. AT: "Suna mai kyau"
Wannan karin magan ne. AT: "dole ne yayi tunani da kyau game da wannan"
A nan mutane ana nufin masu hikima ta wurin "zuciyarsu." Wannan na magana game da mutum mai hikima na makoki kamar yana a cikin gidan makoki. AT: "Masu hikima su na tunani sosai game da mutuwa"
A nan ana nufin wawayen mutane ta wurin "zuciyarsu." Wannan na maganar wawayen suna tunanin abinda ke sa su jin daɗi ne kɗai kamar kasancewa a gidan biki. AT: "amma wawayen mutane suna tunanin jin dadi ne kawai"
Ana iya bayyana kalman nan "tsautawa" kamar Fi'ili. AT: "idan masu hikima sun tsauta maka"
"a saurari wawaye su yi waƙa"
Wannan na nufin sa mutum ya ba da kuɗi da karfi ko wasu abubuwa masu muhimmanci soboda kada wani mutum ya cuce shi. Wannan ba dai dai bane.
A nan kalman nan "zuciya"na nufin tunani. AT: lalata iyawar mutum ya yi tunani kuma ya yi hukunci da kyau"
A nan kalman nan "ruhu" yana nufin halin mutum. AT: "mutane masu haƙuri sun fi mutane masu girman kai" ko "halin haƙuri yafi halin girman kai"
A nan kalman nan "ruhu" na nufin halin mutum. AT: "Kada ka yi saurin fushi" ko "Kada ka zama da mugun zuciya"
Mutumin yayi wannan tambaya ne domin ya nuna ɓacin ransa a zamanin yanzu. AT: "Abubuwa sun fi kyau a da fiye da yanzu"
A nan marubucin yayi amfani da wani magana don ya tsauta wa tambayar mutumin. AT: "idan kana da hikima za ka yi wannan tambayar ba"
Wannan karin magana ne. AT: "waɗanda ke da rai"
Maána mai yiwuwa su ne 1) marubucin yayi amfani da kalmomin nan "sani" da "hikima" na nufin abu ɗaya, ko 2) "amfanin sanin hikima shine yana ba da rai."
Marubucin yayi amfani da wannan tambayar domin ya jajjada cewa babu wanda zai iya canja abinda Allah ya yi. AT: "Babu wanda zai miƙar da abinda ya tankwara. "
Kalman nan "lokaci" karin magana ne na "abubuwan da ke faruwa." AT: "A lokacin da abubuwa masu kyau ke faruwa ... a lokacin da abubuwa marasa kyau ke faruwa"
Wasu maanar sune 1) "dukkan abinda zai faru nan gaba" 2) "dukkan abinda ya faru a duniya bayan mutuwarsa ko 3) "dukkan abinda ya faru da shi bayan mutuwarsa."
"a rayuwa ta mara ma'ana"
"duk da su mugaye ne"
Marubucin yayi amfani da wannan tambayar ne domin yayi ƙarin bayani a kan nuna kai mai-adalci yana iya ɓata mutum. AT: "Babu dalilin ɓata kanka"
Marubucin yayi amfani da wannan tambayar don ya jajjada cewa babu wani dalili da zai sa mutane suyi abinda zai kashe su da wuri. Za'a iya rubuta wannan tambayar a bayane. AT: "Babu dalilin da zai sa ka mutu kamin lokacin ka."
"zai yi dukan abinda Allah yake jira ya yi"
"Hikima na sa mutum ya zama da iko; ta na sa shi ya zama da iko fiye da shugabanni goma a cikin birni"
"yana yin abubuwa masu kyau kuma ba ya aikata zunubi"
Za' a iya rubuta wannan a aikace. AT: "dukkan abinda mutane suke cewa"
"kai kanka ka sani." A nan ana amfani da "kanka" don a jajjada kalman nan "sani."
A nan tunanin mutum na wakiltar "zuciyar shi." AT: "cikin tunaninka"
"ya fi iya sani na" ko "ban iya yin shi ba"
Hikima yana da wuyan ganewa.Idan akwai fahimta,kaɗan ne. Yana buƙatan fahimta mai zurfi fiye da ganewar marubucin. AT:"da wuyan ganewa"
"dalilin kasancewar abubuwa." Ana iya bayyana kannan kalman nan "bayanai" kamar fi' ili. AT: "yadda za' a iya bayyana abubuwa masu yawa a rayuwa"
Marubucin yace fasiƙar matar ta na kamar tarkon da masu farauta ke kama dabbobi. Marubucin na maganar fasiƙar mata kamar ta kama maza kamar yadda mai farauta yake kama dabbobi. "Zuciyarta" na wakiltar tunanin ta da emoshen. AT: "duk wat matar da ta nemi ta kama maza"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "za ta kama mai zunubi"
Za'a iya bayyana kalman nan "ganowa" kamar fi'ili. Ana amfani da kalman nan "ƙarawa" a nan kamar karin magana. AT: "gãnowa bisa gãnowa"
Babu mata masu adalci da aka samu a cikin rukuni mutum 1,000.
Ma'anar na iya zama 1) "sunyi shiri na zunubi dayawa" 2) "sun maida rayuwarsu ya zama da wahala."
A nan kalman "su" yana nufin "al'umma." Wannan na magana a kan al'umma na chanjawa daga zama adalai zuwa marasa adalci kamar suna tafiya daga wani wuri zuwa wani wuri.
1Wane ne mutum mai hikima? Wanda ya san abin da al'amuran rayuwa ke nufi? Hikima a cikin mutum nasa fuskarsa ta haskaka, kuma taurin fuskarsa ya canza.2Ina ba ka shawara da ka yi biyayya da dokar sarki saboda rantsuwar Allah na kiyaye shi.3Kada ka yi garajen barin gabansa, kada kuma ka goyi bayan abin da ba dai-dai ba, domin sarki na yin abin da ya so.4Maganar sarki ke mulki, to wane ne zai ce masa, "Me ka ke yi?"5Duk wanda ke kiyaye dokar sarki yana kaucewa cutarwa. Zuciyar mutum mai hikima takan gane dai-dai lokacin daya dace a aiwatar da abu.6Domin ga kowanne al'amari akwai yadda ya dace da lokacin da ya dace, saboda matsalolin mutum manya ne.7Babu wanda ya san abin da ke zuwa a gaba. Wane ne zai gaya mashi abin da ke zuwa?8Babu wanda ke mulki bisa lumfashinsa yadda zai tsaida lumfashin, babu kuma wanda ke da iko bisa ranar mutuwarsa. Babu wanda ake sallama daga bataliyar sojoji a lokacin yaƙi, kuma mugunta ba ta kuɓutar da waɗanda ke bayinta.9Na gãno dukkan wannan; Na sanya zuciyata ga kowanne irin aiki da ake yi a ƙarƙashin rana. Akwai lokacin da wani taliki ke muzgunawa wani talikin domin cutarwar wannan taliki.10Sai naga ana bizne miyagu a sarari. An ɗauke su daga wuri mai tsarki aka kuma bizne su mutane kuma suka yabe su a cikin birni inda suka aiwatar da ayyukan muguntarsu. Wannan ma wofi ne.11Sa'ad da zartar da hukunci gãba da aikin mugunta ba a aiwatar dashi ba da sauri, yana jarabtar zukatan 'yan'adam da su aikata mugunta.12Koda ya ke mai zunubi yana aikata mugunta sau ɗari kuma duk da haka ya yi tsawon rai, duk da haka na sani cewa zai fi kyau ga waɗanda ke girmama Allah, ga waɗanda ke tsayawa a gabansa suna kuma nuna masa girma.13Amma ba zai zama da lafiya ba game da mugun mutum; rayuwarsa ba za tayi tsawo ba. Kwanakinsa kamar inuwa ce mai wucewa saboda ba ya darjanta Allah.14Akwai wani turirin hayaƙi marar amfani - wani abun kuma da ake yi a duniya. Abubuwa na faruwa da mutane masu adalci yadda suke faruwa da mutane masu mugunta, kuma abubuwa na faruwa da mutane masu mugunta yadda suke faruwa da mutane masu adalci. Na ce shi ma wannan turirin hayaƙi ne marar amfani.15Sai na shawarta murna, saboda mutum ba ya da wani abu a ƙarƙashin rana fiye da ya ci ya sha ya kuma yi murna. Murna ce za ta yi masa rakiya cikin aikin ƙarfinsa domin dukkan kwanakin rayuwarsa waɗanda Allah ya bashi a ƙarƙashin rana.16Sa'ad da na bada zuciyata in san hikima in kuma fahimci aikin da ake yi a duniya, aikin da yawanci ake yi ba bu barci domin idanu koda rana ko da dare,17daga nan na yi la'akari da dukkan ayyukan Allah, kuma da cewar mutum ba zai iya fahimtar aikin da ake yi ba a ƙarƙashin rana. Ko ta yaya mutum ya yi aiki tuƙuru domin ya sami amsoshi, ba zai same su ba. Koda ya ke mutum mai hikima zai bada gaskiyar cewa ya sani, lallai bai sani ba.
Marubucin yayi wannan tambayar sani ne domin ya bada amsa kan abinda zai faɗa a nan gaba.
Wannan yana nufin fuskar mutumin zai nuna cewa yana da hikima. AT: "ya nuna a fuskarsa"
Ma'anar mai yiwuwa 1) kada kayi garajen barin gabansa ko 2) Wannan wata magana ce da ke faɗin aminci wa sarki kamar zama a gabansa. AT: "Kada ka rabu da sarki"
Wannan tambaya ce da ke tsautawa. Za'a iya rubuta wannan tambayar a bayani. AT: "Bai kamata kayi abindakake yi ba."
A nana "zuciyar" na wakiltar tunaninsa. AT: "Mutum mai hikima yana ganewa."
Wannan tambayar yana nuna babu wanda ya san abinda ke zuwa nan gaba Za'a iya rubuta wannan tambayar a bayani. AT: "Babu wanda zai iya fadar abinda ke zuwa nan gaba"
Kamar yadda babu wanda ke da ikon hana kansa yin lumfashi,babu kuma wanda zai ci gaba da rayuwa idan lokacin mutuwarsa yayi.
Wannan na magana a kan mugunta kamar itace shugaba wanda ke da bayi. AT: "ba za'a ceci mugayen mutane ba don yin mugunta"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "kowanne irin aiki da mutane ke yi"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. Miyagun mutane da suka mutu an bizne su da daraja. AT: "Mutane suna bizne miyagu a sarari"
A nan ana wakiltar mutane ta wurin "zuciyarsu" a jajjada son su da marmarin su. AT: "jawo 'yan adam"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "Allah zai tsawanta rayuwarsa"
Wannan na maganar rayuwar mutum mai mugunta na wucewa da sauri da cewa ta na kamar inuwar da ke ɓacewa da sauri. AT: "Ranakunsa zasu wuce da sauri kamar inuwar da ke ɓacewa"
"marar anfani" ko "wofi". Abinda ya faru da bai kamata ya faru ba.Kamar abubuwa masu kyau da ke faruwa da miyagun mutane da kuma abubuwa marasa kyau da ke faruwa da mutanen kirki.
Wannan karin magana ne. AT: "har tsawon lokacin da Allah ya bar shi yayi rayuwa"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "aikin da mutane ke yi a duniya"
Ma'ana mai yiwuwa 1) "aikin da Allah ke yi a ƙarƙashin rana" ko 2) "aikin da Allah ya bar mutane na yi a kalkashin rana"
1Gama na yi tunani game da dukkan wannan a raina in sami fahimta game da mai adalci da mutane masu hikima da ayyukansu. Dukkan su suna cikin hannuwan Allah. Babu wanda ya sani wataƙila ƙauna ko ƙiyayya zata zo ga wani.2Kowa na fuskantar ƙaddara ɗaya. Ƙaddara ɗaya ce ke jiran mutane masu adalci da miyagu, masu kyau, masu tsarki da marasa tsarki, da mai miƙa hadayu da wanda ba ya hadaya. Kamar yadda masu kyau suke mutuwa, haka kuma mai zunubi. Kamar yadda mai rantsuwa zai mutu, haka kuma mutumin da ke jin tsoro ya ɗauki wa'adi.3Akwai muguwar ƙaddara ga kowanne abu da ake yi a ƙarƙashin rana, al'amari ɗaya ne ke faruwa da su dukka. Zukatan 'yan'adam na cike da mugunta, kuma hauka na cikin zukatansu yayin da suke raye. Sai bayan wannan su tafi wurin matattu.4Domin duk wanda ya ke tare da dukkan masu rai, akwai bege, kamar yadda kare mai rai yafi mataccen zaki.5Domin mutane masu rai sun san cewa za su mutu, amma matattu basu san komai ba. Basu da wani sakamako kuma saboda an manta da tunawa da su.6Ƙaunarsu, ƙiyayyarsu, da kishinsu, sun ɓace da daɗewa. Ba za su sake samun wuri ba kuma cikin kowanne abu da ake yi ƙarƙashin rana.7Ka yi tafiyar ka, ka ci gurasarka da farinciki, ka kuma sha ruwan inabinka da zuciya mai murna, domin Allah ya tabbatar da shagalin ayyuka masu kyau.8Bari suturunka koyaushe su zama farare kanka kuma shafaffe da mai.9Ka zauna da murna tare da matar daka ke ƙauna dukkan kwanakin rayuwarka marasa amfani, kwanakin da Allah ya baka a ƙarƙashin rana a zamanin kwanakinka marasa amfani. Wannan ne sakamakonka a rayuwa domin aikinka a ƙarƙashin rana.10Duk abin da hannunka ya samu ya yi, ka aikata shi da dukkan ƙarfinka, saboda babu aiki ko bayani ko ilimi ko hikima a Lahira, in da kake tafiya.11Na ga wasu abubuwa na burgewa a ƙarƙashin rana: Tseren ba na mutane masu sauri ba ne. Yaƙin ba na mutane masu ƙarfi ba ne. Gurasa ba ta mutane masu hikima ba ce. Arziki ba na mutane masu fahimta ba ne. Tagomashi ba na mutane masu ilimi ba ne. Maimako, lokaci da sarari ke shafar su dukka.12Tabbas, babu wanda ya san sa'ad da lokacinsa zai zo. Kamar yadda ake kama kifi cikin tãru mai haɗari, ko ake kama tsuntsaye cikin tarko, a na yi wa 'ya'yan 'yan'adam tarko da miyagun lokutta da ke faɗowa bisan su farat ɗaya.13Na kuma ga hikima a ƙarƙashin rana ta hanyar da na kalle ta babba a gare ni.14Akwai wani ƙaramin birni mai mutane ƙalilan a ciki, wani babban sarki kuma ya zo gãba da shi ya yi masa sansani ya kuma gina manyan ramukan sansani gãba da shi.15To a cikin birnin an sami matalauci, mutum mai wayau, wanda ta wurin hikimarsa ya ceci birnin. Duk da haka daga baya, babu wanda ya tuna da wannan mutum matalauci.16Sai na kammala, "Gwamma hikima da ƙarfi, amma aka rena hikimar mutumin nan matalauci, maganganunsa kuma ba a ji su ba."17Maganganun mutane masu hikima da aka furta a hankali an fi jin su fiye da kururuwar duk wani sarki cikin wawaye.18Hikima tafi makaman yaƙi, amma mai zunubi ɗaya zai lalata abubuwan nagarta masu yawa.
"Nayi tunani mai zurfi game da dukkan wannan"
A nan kalman nan "su" na nufin "mutane masu adalci da mutane masu hikima" haka kuma "ayyukansu"
Wannan na nufin dukan mutane, jajjada cewa akasin abubuwa biyu na adalci da miyagun mutane.
Wannan na nufin dukan mutane, jajjada cewa akasin abubuwa biyu na mutane masu tsarki da na mutane marasa tsarki.
Wannan na nufin dukan mutane, jajjada akasin abubuwa biyu na mutane masu alheri da mutane masu zunubi.
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "dukan abinda ya faru"
A nan kalman nan "zuciyarsu" na nufin tunanin da emoshen ɗin su. AT: "'Yan adam na cike da mugunta, kuma tunaninsu na hauka ne"
mutuwa
Wannan na nufin mutanen da ke da rai da mutanen da suka mutu. AT: "da ke da rai ... waɗanda suka mutu"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "mutane sun manta dasu"
A nan kalman nan "zuciya" yana nufin lamiri. AT: "ka sha ruwan inabinka da murna"
Sanya tufafi farare da kuma shafe kai da mai dukka alama ce ta murna da buki.
Mutum ya ƙaunaci matar da yake da ita. AT: "Da shike kana da matar da kake ƙaunarta, ka yi zaman farinciki da ita"
Kalman nan "wancan" na nufin zaunawa da farin ciki tare da matarsa.
Wannan karin magana ne. AT: "abinda ya faru da lokacin da ya faru ya shafe su duka"
"ya shafe dukan abubuwa." A nan kalman "su duka" yana nufin tsare, gwagwarmaya, gurasa, dukiya da kuma ƙwarjini.
Wannan karin magana ne. AT: "wasu lokatai basu tsammanin su faru da su" ko "kwatsam ya faru da su"
A nan "sarki" na wakiltar kansa da kuma sojojin sa. AT: "babban sarki da kuma sojojinsa"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "a cikin birnin, mutane sun tarar da mutum matalauci, mai hikima" ko "mutum matalauci, mai hikima ya zauna a cikin birnin"
Za'a iya fadɗin wannan a aikace. AT: "mutane sun rena hikimar mutumin matalauci"
za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "ba su saurari abinda ya ke ba" ko "ba su ji shawararsa ba"
A nan "ji" na wakiltar ganewa. Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "ya fi sauƙi a gane kalmomin da mutane masu hikima suka faɗa shiru"
1Kamar yadda mataccen ƙuda yana sa turare ya yi wãri, haka wawanci ƙarami zai iya shan ƙarfin hikima da daraja.2Zuciyar mai hikima na gusawa dãma, amma zuciyar wawa na gusawa hagu.3Sa'ad da wawa ke tafiya akan hanya, tunaninsa kasasshe ne, yana tabbatar wa da kowa cewa shi wawa ne.4Idan hankalin mai mulki ya tashi gãba da kai, kada ka bar aikinka. Natsuwa na iya kwantar da fushi mai girma.5Akwai muguntar da na gani a ƙarƙashin rana, wani irin kuskure da ke zuwa daga shugaba:6A na ba wawaye matsayin shugabanci, yayin da mutane na ƙwarai ake basu ƙasƙantattun matsayi.7Na ga bayi na hawa dawakai, kuma mutane na ƙwarai na tafiya kamar bayi bisa ƙasa.8Duk wanda ya ke ginin rami zai iya faɗawa a ciki, duk kuma sa'ad da wani ya fasa katanga, maciji na iya sarar sa.9Duk wanda ke yankan duwatsu za su iya ji masa rauni, kuma mutumin da ke sarar katako yana cikin haɗari dashi.10Idan bãkin ƙarfe ya dushe, kuma mutum bai wãsa shi ba, daga nan tilas ya yi amfani da ƙarfi sosai, amma hikima na bayar da mafita domin nasara.11Idan maciji ya yi sara kafin a yi masa makari, daga nan babu wani amfani domin mai makarin.12Maganganun bãkin mutum mai hikima na cike da alheri, amma leɓunan wawa na lanƙwame shi.13Sa'ad da maganganu suka fãra kwararowa daga bãkin wawa, wawanci na fitowa, a ƙarshe kuma bãkinsa na kwararowa da haukan mugunta.14Wawa yana ruɓanɓanya maganganu, amma babu wanda ya san abin da ke zuwa. Wane ne ya san abin da ke zuwa bayansa?15Aikin wawaye na gajiyar da su, yadda ba zasu san ma hanyar zuwa gari ba.16Kaiton ki, ƙasa, idan sarkin ki ƙaramin yaro ne, idan kuma shugabanninki suka fara shagali da safe!17Amma mai albarka ce ke, ƙasa, idan sarkin ki ɗa ne na ƙwarai, idan kuma shugabannin ki na cin abinci lokacin da ya dãce, domin ƙarfi, kuma ba domin buguwa ba!18Saboda ƙyuya rufin gida na ruftawa, kuma saboda hannaye marasa aiki gida na zuba.19Mutane na shirya abinci domin dariya, ruwan inabi yana kawo jin daɗi ga rayuwa, kuɗi kuma na cika buƙata domin komai.20Kada ka la'anci sarki, ko a tunaninka ma, kada kuma ka la'anci mutane masu arziki a cikin ƙuryar ɗakinka. Domin tsuntsuwar sararin sama na iya ɗaukar maganganunka; duk abin da ke da fukafukai zai iya baza al'amarin.
Kamar yadda ƙuda ke ɓata turare, haka wawanci ke ɓata mutuncin mutum domin hikima da ɗaukaka.
Wannan na nufin yadda ya ke yi. AT: "shi wawa ne"
A nan mai mulki na wakiltar "emoshen ɗinsa" AT: "Idan mai mulki ya yi fushi da kai"
"Ta wurin kwantad da hankali za ka iya sa mai ƙeta doka yayi shiru"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "Masu mulki na ba wa wawaye shugabanci"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "ana ba wa mutane masu nasara ƙasƙantattun matsayi"
Wannan na nufin maciji da ke ɓoyewa a cikin katanga.
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "duwatsun na iya cutar da su"
Mai hikima zai wasa ruwan reza kuma ba sai yayi aiki da wuya ba.
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "kafin maciji charmer it"
Ana wakiltar jawabin mai hikima ta wurin "bakinsa." AT: "Abubuwan da mai hikima ke faɗa na cike da alheri"
Ana wakiltar jawabin wawa da "leɓuna." Wannan na maganar wawa na lalata kansa ta wurin jawabinsa kamar suna cinye shi. AT: "Abubuwan da wawan mutum faɗa ya lalata shi"
Ana wakiltar jawabin wawa da "bakinsa." AT: "Da wawa ya fara magana"
Wannan karin magana ne. AT: "ci gaba da magana"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "Wawaye sun gaji ta wurin wahalarsu" ko "wawaye na jin gajiya ta wurin aikin da suke yi"
Ma'ana mai yiwuwa 1) "ya yi yawa har ma bai iya samun hanyar zuwa garin ba." Cewa wawan mutumin ya gaji sosai daga aikin wuya har ma bai iya gano hanyar ko'ina ba. ko 2) "saboda bai san hayar zuwa garin ba." Cewa wawan mutumin ya gaji daga aikin wuya domin bai da isasshen sanin zuwa gida.
A wannan ayar marubucin yana magana da ƙasar kamar wani mutum ne.
Wannan na nufin cewa sarkin ba shi da isasshen kwarewa ko bai gama wayo ba.
Mutum mai ƙiwuya ba ya ci gaba da kula da gidan kullum. AT: "domin mai ƙiwuya ba ya kyara gidansa, soron zai nitse ciki"
Ana iaya bayyana kalman nan "dariya" kamar fi'ili. AT: Mutane na shirya abinci domin su yi dariya"
Ana wakiltar tunanin mutum da "zuciyarsa." AT: ko a cikin tunaninka"
"mutane masu arziƙi a cikin ɗakin kwananka." Wannan na nufin cewa ya kamata kada ka dage mutane ko a lokacin da kake a wurin zaman kanka inda babu wanda zai ji ka.
1Ka aika da gurasar ka bisa ruwaye, domin za ka same ta kuma bayan kwanaki masu yawa.2Ka raba da bakwai, har ma da mutane takwas, domin baka san bala'o'in da ke zuwa bisa duniya ba.3Idan giza-gizai suka cika da ruwa, suna juye kansu bisa duniya, idan kuma itace ya fãɗi zuwa kudu ko zuwa arewa, inda itacen ya fãɗi, nan zai tsaya.4Duk wanda ke kallon iska ba zai yi shuka ba, duk kuma wanda ke kallon giza-gizai ba zai yi girbi ba.5Kamar yadda ba ka san tafarkin iska ba, ko yadda ƙasusuwan jariri ke girma a cikin mahaifar mai ciki, haka nan kuma ba za ka gãne aikin Allah ba, wanda ya halicci komai.6Da safe ka shuka irinka; har yamma, ka yi aiki da hannuwanka bisa ga buƙata, domin ba ka san wanda zai wadata ba, ko safe ko yamma, ko wannan ko wancan, ko dukkan su biyu zasu yi kyau.7Gaskiya haske yana da daɗi, kuma abu mai gamsarwa ne ga idanu su kalli rana.8Idan wani ya rayu shekaru masu yawa, bari ya yi murna cikin dukkan su, amma bari ya yi tunani game da kwanakin duhu masu zuwa, domin zasu zama da yawa. Kowanne abu da ke zuwa turirin hayaƙi ne mai wucewa.9Ka yi farinciki, saurayi, a cikin ƙuruciyarka, bari kuma zuciyarka ta yi farinciki cikin kwanakin ƙuruciyarka. Ka runtumi sha'awoyi masu kyau na zuciyarka, da duk abin da ke cikin ganin idanunka. Duk da haka, ka sani cewa Allah zai kawo ka cikin hukunci domin dukkan waɗannan abubuwa.10Ka kori fushi daga zuciyarka, ka kuma yi watsi da duk wani zafi a cikin jikinka, saboda ƙuruciya da ƙarfinta turirin hayaƙi ne.
Ma'ana mai yiwuwa 1) wannan magana da ke nufin mutum ya zama mai hannu sake shima mutane za su saka masa, ko 2) mutum ya sa jarinsa a ƙetaren kogi zai sami riba daga gareshi.
A nan "kudu" da "arewa" na wakiltar kowanne hanya. AT: "a kowanne hanya"
Ma'ana mai yiwuwa 1) "Duk manomin da ke kallon inda iska yake fitowa ba zai iya yin shuka ba domin iska na hurowa ta inda zai yi shukan" ko 2) "Duk manomin da yake sa hankalinsa ga iska ba zai yi shuka ba"
Wannan na maganar iska na hurawa kamar iska tayi tafiya a hanya. AT: "kamar yadda ba ka san inda iskar ta fito ba ko inda take tafiya"
A nan "hannu" na wakiltar dukan mutum. AT: "ka ci gaba da aiki"
A nan kalman nan "su" na nufin shekarun da mutum ke a raye.
Ma'ana mai yiwuwa 1) "Dukan abubuwan da ke faruwa bayan mutuwa" ko 2) "Dukan abubuwan da za su faru nan gaba"
Wadannan furucin guda biyu na nufin abu ɗaya kuma idan an haɗa su wuri ɗaya don a jajjada cewa ya kamata mutumin yayi farin ciki a lokacin ƙuruciyarsa.
Ana maganar ƙin yin fushi kamar fushi abu ne da ake tkora dole. Kuma, "zuciya" na wakiltar emoshen ɗin mutum. AT: "Ka ƙi yin fushi"
1Ka kuma tuna da mahaliccinka a kwanakin ƙuruciyarka, kafin kwanaki masu wuya su zo, kafin kuma shekarun su iso waɗanda za ka ce, "Ba ni da marmari a cikin su,"2ka yi wannan kafin hasken rana da na wata da na taurari su duhunta, baƙaƙen giza-gizai kuma su dawo bayan ruwan sama.3Wannan lokacin ne sa'ad da masu tsaron făda zasu yi rawar jiki, kuma a tanƙwarar da mazaje masu ƙarfi, mataye masu niƙa kuma su tsaya saboda basu da yawa, waɗanda kuma su ke dubawa ta taga sun dena gani sosai.4Wannan lokacin ne sa'ad da aka kulle ƙofofi cikin tituna, ƙarar niƙa kuma ta tsaya, sa'ad da mazaje ke firgicewa ta muryar tsuntsu, kuma muryoyin waƙoƙin 'yanmata suka dushe.5Wannan lokacin ne sa'ad da mazaje suka zama masu jin tsoron tuddai da haɗarorin da ke bisa hanya, sa'ad da kuma itacen almon ke yaɗo, sa'ad da kuma fãri suke jan kansu tare, sa'ad da kuma marmari na ɗabi'a ya karye. Daga nan mutum ya tafi madawwamin gidansa masu makoki kuma su gangara bisa tituna.6Ka tuna da mahaliccinka kafin a datse igiyar azurfa, ko a kwankwatse kwanon zinariya, ko tulu ya farfashe a rafi, ko gargaren murɗo ruwa ya fashe a rijiya,7kafin turɓaya ta koma ƙasa in da ta fito, kuma ruhu ya koma ga Allah wanda ya bayar dashi.8"A tsakiyar turirin hayaƙi," a faɗar Malamin, "komai turirin hayaƙi ne mai bajewa."9Malamin mai hikima ne kuma ya koyar da mutane ilimi. Ya yi bincike kuma ya yi juyayi kuma yasa misalai masu yawa a jere.10Malamin ya nemi ya rubuta kuma yana amfani da zahirin, cikakkun maganganun gaskiya.11Maganganun mutane masu hikima kamar zugazugai suke. Kamar ƙusoshin da ake bugawa da zurfi haka nan maganganun gwanayen da suka ƙware wajen tattara misalansu, wanda makiyayi ɗaya ya koyar.12Ɗana, ka zama a faɗake game da wani abin kuma: yin litattafai da yawa, wanda bai da ƙarshe da yawan bincike yana kawo gajiyarwa ga jiki.13Ƙarshen al'amari bayan an ji komai, shi ne tilas ka ji tsoron Allah ka kuma kiyaye dokokinsa, domin wannan gabaɗaya shi ne aikin ɗan'adam.14Domin Allah zai kawo kowanne aiki zuwa hukunci, tare da duk wani ɓoyayyen abu, ko mai kyau ne ko mugu.
Wannan karin magana ne. AT: "ka tuna"
Ana maganar lokaci mai zuwa kamar "shekaru sun zo" AT: "kafin ka zama tsofo lokacin da zaka ce, "ba na jin daɗin rayuwa kuma"
Marubucin yayi bayani akan gida wanda ayyuka daban daban ke faruwa.Wannan misali ne akan jikin mutum yayinda yake tsufa.
"masu ƙarfi sun zama da rauni"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "mutane sun rufe oƙfofin da suka kai titi"
A nan "'yan mata" wata kalma ce da ke nufin tsuntsaye. AT: "waƙoƙin tsuntsaye sun shuɗe"
Wannan na nufin mutuwa. AT: "sa'an nan mutumin ya tafi wurin mattatu har abada" ko "sa'an nan mutumin ya mutu kuma ba zai taɓa dawowa rauwa ba"
Ma'ana mai yiwuwa 1) cewa masu makoki sun tafi titi su halarci jana'iza, ko 2) cewa masu makoki sun tafi titi zuwa gidan mutumin da ke gab da mutuwa.
Marubucin ya kwatanta mutuwa da fasassun abubuwa. Mutuwa zai fasa jiki kamar yadda mutane sukan fasa kaya cikin kuskure lokacin da suke anfani da su.
A nan kalman nan "turɓaya" na nufin jukin mutum da ya ruɓe.
Dubi yadda zaka juya wannan a Mai Wa'azi 1:1
"tunani sosai game da kuma shiryawa" ko "tunani sosai game da kuma rubuta wa"
Marubucin ya kwatanta malami wanda yake anfani da kalmomi yayi koyarwa da kuma makiyayi dake anfani da kayansa ya jagoranci garkensa.
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "wanda makiyayi ɗaya ya koyas"
Za'a iya faɗin maganar nan "wajen yin" a fi'ili. AT: "Mutane ba za su daina rubuta litattafai da yawa ba"
A nan "jiki" na wakiltar dukan mutum, AT: "yana sa mutum gajiya"
"karshen karewar al'amari"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "bayan ka ji komai"
1Waƙar Waƙoƙi ta Suleman ce. Matar tana magana da kanta ne2Oh, da ma zai sumbace ni da sumbatar bakinsa, matar kuma tana yin magana da mutumin, gama ƙaunarka ta fi ruwan inabi.3Manka na shafawa yana da ƙanshi mai daɗi, sunanka na kama da turare mai kwararowa, zuwa ga 'yammatan da kake ƙauna.4Ka ɗauke ni mu yi gudu tare. Matar tana yin magana da kanta. Sarkin ya kawo ni cikin ɗakunansa. Matar tana yin magana da mutumin. Muna yin murna; muna farinciki game da kai; bari muyi bukin ƙaunarka; ta fi ruwan inabi. Dai-dai ne waɗansu mata su yi sha'awar ka. Matar tana magana da waɗansu matan.5Ni baƙa ce amma kyakkawa, ku 'yammatan Yerusalem - baƙaƙe kamar rumfunan Kedar, kyawawa kamar labulen Suleman.6Kada ku ƙyale ni saboda ni baƙa ce, saboda rana ta gasa ni. 'Ya'yan mahaifiyata suna fushi da ni; sun maida ni mai tsaron garka, amma ban iya tsare tawa garkar ba. Matar tana magana da mutumin.7Ka gaya mani, wanda raina ya ke ƙauna, ina kake kiwon garkenka? Ina kake sa garkenka su huta da tsakiyar rana? Me yasa zan zama kamar wadda take kai da kawo wa a kusa da garkunan abokanka?8Mutumin yana magana da matar. Idan baki sani ba, wadda ta fi sauran mataye kyau, ki bi sawun garkena, ki kiwaci 'yan awakinki kusa da rumfar makiyaya.9Ƙaunatacciyata, ina kwatanta ki da goɗiya a cikin dawakin karusar Fir'auna.10Kumatunki kyawawa ne masu ban sha'awa, wuyanki da sarƙoƙin lu'uluai.11Zamu yi maki kayan ado na zinariya da azurfa. Matar tana magana da kanta.12Sa'ad da sarkin ya ke kwance a kan shimfiɗarsa, yana jin daɗin ƙanshin turaren.13Ƙaunataccena yana kama da jakar mur sa'ad da ya kwanta a tsakanin nonnana.14Ƙaunataccena kamar fure ya ke a garkar En Gedi. Mutumin yana magana da matar.15Ki saurara, kina da kyau, ƙaunatacciyata; ki saurara, kina da kyau; idanunki suna sheki.16Matar tana magana da mutumin. Ka saurara, kana da kyau, ƙaunataccena. Shuke-shuke masu taushi sune gadonmu.17Kalankuwar gidanmu ta al'ul ce, raftarmu ta fir ce.
Duba and
sashi na farko na littafin ya fara ne a 1:2
"waƙa mafi kyau" ko "waƙa mafi dacewa"
"wanda ya ke game da suleman" ko " wanda suleman ya ƙaga"
" mai wanda ka sa a jikin ka"
"ƙamshi mai dadi
matar ta ga ne masoyin ta na da suna mai kyau.AT:"sunan ka na da kyau kamar ƙamshin mai wanda ke kwararowa waje".
" ka kawo ni tare da kai". Kalman nan "kai" ya na nufin shi masoyin ta.
kalman nan "mu" ya na nufin budurwar tare da masoyin ta.
"saboda kai"
"bari in yi yabo"
dukkan ma su ƙaunar ka sun yi gaskiya
" fata ta baƙi ne, amma ni kyaykyawa ce"
makiyaya na yaren kedar su na anfani da baƙin gashin akuya domin gina gidajensu.matar ta na kwatatanta fatar ta da wadan nan rufunan.
ta na kwatanta fatar ta da kyawawan labulen da suleman ya shirye domin fadar sa ko kuma haikali.
"gasashe"
"ƴan'uwa na maza daga matar babana".waɗannan yan'uwan maza watakila su na da uwa ɗaya amma ubansu kowa da nasa.
" mutmin da ya tsare garkarku nan"
Matar ta na kwatanta kanta da garkar.AT:"amma ban iya na kula da kaina ba."
"yi kiwon garkenka"
"ka sa garken ka su kwanta"
AT:"ka gaya mi ni domin kada in yi ta kai da kawo wa a cikin garken abokai na yayin da nake neman ka"
" kai da kawowa"
"abokai" ko "abokan-aiki"
"ki bi bayan garken"
"sawun ƙofaton garken a ƙasa"
"ki kiwaci yan awakinki" ko "ki bar 'yan awakinki su ci"
Kaunataccen matar ya ci gaba da magana
"wanda nake ƙauna"
an kwatanta kaunatacciyar matar da kyawawan dawaki mata.
"dawakan fir'auna da ke jan karusar"
"da taɓin azurfa"
"ya zauna a teburin sa"
"ya ba da kanshin sa mai dadi"
mai ne wanda mutane su ke samu daga nard mai tsada ko mur(tsiro ne da ke da ruwan foda kaɗan ko farin fure)yana kuma sa fatar jiki ta yi laushi ya kuma ba da kanshi mai daɗi
" a gareni,kaunataccena yana kamar"
"ya na kwance a tsakanin nonnana dukkan tsawon dare."Mata sukan safa mur mai tsada kaɗan tsakanin nonnansu domin ci gaba da bada kanshi mai dadi.
fure daga karamin itacen da ke a hamada da ake afani da shi domin yin turare
Kalman nan "duba" ya na ƙara jaddadawa ne ga abinda ke biye.AT:"kwarai"
Kurciya alama ce ta tsabta,rashin aibu,hankali da kuma kauna.AT:idanunki su na a natse su na kuma sheƙi kamar idanun kurciya.
kalman nan "duba" anan ya na kara jaddada abinda ya na biye ne.AT "kwarai"
"mai kyaun gani" ko "kaunatacce" ko "kyaykyawa"
shuka wanda su ke kore,da danshi,dake kuma yaɗuwa
"su ne gadonmu" matar ta bayyana yadda suke kwance akan shuka mai laushi a waje kamar suna kan gado ne
matar ta bayyana jejin kamar gidansu ne.AT:"rassan itacen al'ul suna kamar kalankuwar gidan mu.
mayan katako ne wanda ke rike jinkan gida
"rassan fir kuma kamar raftar gidanmu"
katakai ne da ke rike jinkan gida
1Ni furen kallo ce ta Sharon, fure na bakin kwari. Mutumin yana magana da matar.2Kamar fure a cikin ƙayoyi, haka ƙaunatacciyata take a cikin 'yammata.3Matar tana magana da kanta. Kamar itacen tsada a cikin itatuwan jeji, haka ƙaunataccena ya ke a cikin samari. Na kan zauna a cikin inuwarsa da jin daɗi mai yawa, ina jin daɗin 'ya'yan itatuwansa.4Ya kawo ni gida mai ruwan inabi, tutarsa a kaina ƙauna ce. Matar tana magana da mutumin.5Ka farfaɗo dani da waina ka wartsakar da ni da 'ya'yan tsada, gama ƙaunata ta kasa. Matar tana magana da kanta.6Na yi matashin kai da hannunsa na hagu, hannunsa na dama kuma ya rungume ni.7Matar tana magana da sauran mata. Ku 'yammatan Yerusalem, ina so ku yi rantsuwa, da bareyi da batsiyoyi na jeji, ba zaku farka da ƙauna ba sai ta gamsu.8Matar tana magana da kanta. Akwai motsin ƙaunataccena! Saurara, gashi yana zuwa, yana sassarfa a kan duwatsu, yana tsalle a kan tuddai.9Ƙaunataccena yana kama da barewa ko ɗan kishimi; duba, ga shi a tsaye bayan katangarmu, yana leƙowa ta taga, yana kallo cikin assabari.10Ƙaunataccena yayi magana da ni yace, "Tashi, ƙaunatacciyata; kyakkyawata, ki zo mu fita.11Duba, hunturu ya wuce, ruwa ya ɗauke kuma ya tafi.12Furanni sun fito a kan ƙasa; lokacin aske itatuwa da kukan tsuntsaye ya zo, kuma an ji motsin kurciyoyi a ƙasarmu.13'Ya'yan ɓaure sun nuna, inabi kuma yana sheƙi; sun bayar da ƙanshinsu. Tashi, ƙaunatacciyata, kyakkyawata, mu fita.14Kurciyata a kogon dutse, a cikin wani asirtaccen kogon dutse, bari in ga fuskarki. Bari in ji muryarki, gama muryarki tana da zaƙi, kuma fuskarki abin ƙauna ce." Matar tana magana da mutumin.15Ka kamo mana diloli, 'yan dilolin da suke ɓata gonaki, gama gonarmu tana sheƙi.16Ƙaunataccena nawa ne, ni kuma tasa ce; yana kiwo a cikin furanni na annashuwa. Matar tana magana da mutumin.17Ka tafi, ƙaunataccena, kafin iskar asubahi ta buso inuwoyi kuma su ɓace. Ka zama kamar barewa ko kamar 'yar batsiya a kan dutse mara laushi.
Duba: and
Matar ta kwatanta kanta da furen dake cikin kwari domin ta nuna cewa ita daga kauye take wanda bata buƙatar dukkan sa hankalin da kaunataccenta ya ke nuna mata.
yankin ƙasa wanda ya ke da fadi,babu itatuwa ya na kuma ciyawa da furenni da ke girma a cikinta
Matar ta kwatanta kanta da furen da ke cikin kwari kamar yadda ta kwatanta kanta da fure na kan tudu
fure mai kanshi wanda ke da siffar kakaaki
wannan yana nufin wuri mai faɗi wanda ke tsakannin manyan duwatsu
mutumin ya na nufin matar ta fi dukkan sauran matan kyau da armashi fiye da sauran yanmatan,kamar yadda fure yafi kyau da armashi fiye da sauran ƙayoyi da ke kewaye da ita.
duba yadda ka juya wannan a 1:9
"wa su 'yanmata"
Kamar yadda itacen tsada ya fi kwantar da hankali da kwarjini fiye da kowane irin itace a cikin jeji haka nan kaunataccen matar yake da kwantar da hankali da kwarjini fiye da sauran samarin.
Matar ta sami matuƙar farin ciki da gamsarwa a kusantar kaunataccenta.
Matar ta kwatatanta daɗin kaunataccenta da daɗin 'yayan itace.
Matar da ta yi ɗari ɗari da shiga ɗaki mai ruwan inabi,amma ƙaunar ƙaunataccenta ya nuna mata haya ya kuma ba ta ƙarfin gwiwa domin ta shiga.AT:"amma ƙaunarsa ta bishe ni ta kuma bani ƙarfin hali kamar tuta"
"Ka farfaɗo da ni" ko "Ka ba ni karfi"
"domin ƙauna ta ta yi ƙarfi har ina jin na kasa."
"yammatan Yerusalem"
Anan sashi na biyu na littafin ya fara
Matar ta kwatanta kanta da barewa da ɗan kishimi domin yana da sauri,da kyau,da kuma alheri kamar sauran dabbobin.
"Tashi"
Kalman nan "Duba" anan karin bayani ne.AT: "kwarai"
A Isra'ila,ana ruwan sama ne kaɗai da hunturu
AT: "Ka iya ganin furenni" ko "Mutane na iya ganin furenni."
AT: "kana iya jin motsin kurciyoyi" ko " mutane na iya jin motsin kurciyoyi"
Kaunataccen matar ya na magana
ƙaunataccen matar yana kwatanta matar da kurciya domin ta na da fuska mai kyau da kuma murya mai kyau kamar na kurciya kuma domin zai kasance tare da ita a wurin da yake da nisa da mutane kamar yadda kurciya ke zama a inda ya ke da nisa da mutane.
"a cikin wani asirtaccen kogon dutse."Wannan furcin yana nuna inda ƙaunataccen yake so ya ga fuskar matar
Ana iya juya wannan haka "yan diloli." Wannan dabbobin suna kama da ƙananan karnuka kuma ana yawan anfani da su a raira waƙa domin nuna samari da suka matsu su ɓata budurwa.
Ana iya juya wannan haka "yan diloli."Wadannan dabbobin suna kama da ƙananan karnuka kuma ana yawan anfani da su a waƙokin ƙauna domin a nuna samari da suka matsu su ɓata budurwa.
Wannan ya na nufin budurwa wanda ta ke a shirye domin aure da kuma haifuwa.Duba yadda ka juya wannan a 2:12.
Matar ta kwatanta inuwoyi kamar su na guduwa daga hasken rana."inuwoyin sun bace."
1Ina jiran sa da dare a bisa gadona wato shi wanda raina ya ke ƙauna, na neme shi, amma ban same shi ba.2Na ce da kaina, "Zan tashi in shiga cikin birni, a kan hanyoyi da wuraren shaƙatawa; zan neme shi wato shi wanda raina ya ke ƙauna." Na neme shi amma ban same shi ba.3Masu gãdi suka same ni sa'ad da suke aikinsu na zagayawa a cikin birni. Na tambaye su, "Ko kun gan shi wanda raina ya ke ƙauna?4Na wuce su kenan sai na sami shi wanda raina ya ke ƙauna. Sai na riƙe shi na hana shi ya tafi sai da na kawo shi gidan su mahaifiyata, a cikin ɗakin wadda ta ɗauki cikina.5Matar tana magana da waɗansu matayen. Ina so ku yi rantsuwa, ku 'yammatan Yerusalem, da bareyi da batsiyoyin jeji, ba zaku tashi ku nuna ƙauna ba sai ta yarda.6Matar tana magana da kanta. Mene ne wancan mai tahowa daga jeji kamar umudin hayaƙi, tare da kayan ƙanshi masu ƙăwa, tare da dukkan hodar da 'yan kasuwa ke sayarwa?7Duba, gadon Suleman ne; kewaye da mayaƙa sittin, sojoji sittin na Isra'ila.8Dukkan su gwanayen mãshi ne ƙwararru a wajen yaƙi. Kowanne mutum yana da mashinsa a gefe, shiryayye saboda ta'adanci cikin dare.9Sarki Suleman yayi wa kansa kujera ta alfarma da itacen Lebanon.10An yi ginshiƙanta da azurfa; bayanta kuma an yi shi da zinariya, da wurin zama na ƙyallen shunayya. Daga ciki 'yammatan Yerusalem sun yi mata ado na ƙauna. Matar tana magana da matayen Yerusalem.11Ku je waje, ku 'yammatan Sihiyona, ku hangi Sarki Suleman, yana ɗauke da rawani wanda mahaifiyarsa ta naɗa masa a ranar aurensa, a cikin ranar da ya ke farinciki a zuciyarsa.
An sake maimaita wannan domin ƙarin bayani.
Kalman nan "wurin shaƙatawa" yana nuna tsakiyar birni inda hanya ta gamu.Wuri ne wanda mutane suke yawan saye da sayarwa,kasuwa ce,da kuma wuri wanda mutane suke taruwa domin yin taɗi.
"wanda ta dauki cikina" ko "wanda ta dauke ni a cikinta."Wannan yana nufin mahaifiyata.
Duba yadda ka juya a 2:7
A nan sashi na Uku na littafin ya fara
Mutane suna tafiya daga jeji zuwa Yerusalem.Saboda jejin yana ƙasa da kwarin Yodan kuma Yerusalem yana sama cikin tuddai,dole mutane su hau zuwa sama domin su kai Yerusalem.
"wajen yaki"
"saboda ta'adanci" ko "saboda su yaƙa"
"ta yi kyau da ƙauna" ko "an yi mata ado da ƙauna." Wannan yana nufin matan sun shirya wurin zaman da kyau ta hayar nuna ƙaunar su ga Suleman.
1Oh, ke kyakkyawa ce, ƙaunatacciyata; kina da kyau. Idanunki suna kama da kurciya a cikin lulluɓinki. Gashinki kamar garken awaki suna gangarowa daga Dutsen Giliyad.2Haƙoranki kamar kazganyar da a ka yi wa sabon aski, tana fitowa daga wurin yi mata wanka. Kowanne da na kusa dashi, ba wani a cikin su da ya faɗi.3Leɓunanki kamar jan zare; bakinki abin ƙauna ne. Kumatunki suna sheƙi da santsi a cikin lulluɓinki.4Wuyanki yana kama da hasumiyar Dauda da a ka gina da jerin duwatsu, wadda a ka rataye garkuwoyi dubu a kanta, dukkan garkuwoyin sojoji ne.5Nonnanki kamar bareyi biyu, tagwayen bareyi, suna kiwo cikin furanni.6Sai asuba ta yi inuwa ta ɓace, zan je dutsen mur da tudun kayan ƙanshi.7Ke kyakkyawa ce a kowanne sashi, ƙaunatacciyata babu inda kike da cikas.8Mu tafi tare daga Lebanon, amaryata. Mu tafi tare daga Lebanon; ki tawo daga ƙololuwar Dutsen Amana, daga ƙololuwar Dutsen Senir da Harmon daga kogon zakuna, daga kogon dutsen damisoshi.9'Yar'uwata, kin sace zuciyata, amaryata, kin sace zuciyata, da kika dube ni sau ɗaya kawai, da abin wuyanki guda ɗaya kaɗai.10'Yar'uwata, ƙaunarki tana da kyau, amaryata! Ƙaunarki ta fi ruwan inabi, ƙanshin turarenki yafi kowanne kayan ƙanshi.11Amaryata, leɓunanki suna ɗigo da zuma; zuma da madara suna ƙarƙashi harshenki; ƙanshin tufafinki yana kama da ƙanshin Lebanon.12'Yar'uwata, amaryata tana kama da lambun da a ka kulle, kullallen lambu, maɓulɓula wadda a ka hatimce.13Rassanki suna kama da rukunin itatuwa masu bada 'ya'ya na musamman, da itacen lalle da nardi,14Nardi da saffron da man ƙanshi da kalamus da kirfi da kayan yaji iri-iri da aloyis da dukkan kayan ƙanshi mafi kyau.15Ke maɓulɓular lambu ce, rijiya mai sabon ruwa, ƙorama mai gangarowa daga Lebanon. Matar tana magana da mutumin.16Ki taso iskar arewa; ki zo iskar kudu; ki busa a kan lambuna domin kayan yaji suba da ƙanshinsu. Dămă ƙaunataccena zai zo cikin lambunsa yaci zaɓaɓɓun 'ya'yan itatuwa.
Duba: and
Awaki baƙaƙe ne a yawancin lokuta kuma idan suna tafiya cikin tuddai gashinsu yana zama kamar doguwar kitso a gashin mace.
Bayan an yi wa kazganya aski,ana kuma wanke fatar su na zama fari fat.Wannan furcin yana kwatanta farin haƙorin matar da kuma farin fatar kazganyar bayan an aske gashin ta.
yana nufin kazganyar ta na fitowa daga cikin ruwa.AT: "fitowa daga cikin ruwa bayan mutane sun yi mata wanka"
ƙaunataccen ya ci gaba da yabon matar.
Kaunataccen ya ci gaba da yabon matar
Mata suna da sarkan wuya wanda yake rufe wuyan su duka wanda aka yi masa ado na jeri.ƙaunataccen ya kwatanta wannan jerin adon da jerin duwatsu na hasumiya.AT: "wanda ke da jerin duwatsu."
ƙaunataccen ya ci gaba da yabon matar
ƙaunataccen ya na nuna marmarinsa na jin daɗin nonuwanta ta wurin kwatanta su da tuddai ko duwatsun da shi yake so.Nonnanta suna a zagaye sun kuma tsaya kamar tuddai da duwatsu.Su na ƙanshi kamar mur da kayan ƙanshi
Kaunataccen ya ci gaba da magana da matar
ƙaunataccen yana so amaryar sa ta taho da shi su gujewa wurin da ke da hatsari.Wannan misali ne ba su akan tuddai ko koguna.
sunan wata tudu ce kusa da Damaskus
sunan tudu ne kusa da Amana da Harmon.Wasu mutane suna tunanin wannan yana nufin tudun Hermon.
ƙaunataccen ya ci gaba da magana da matar
Da idanunuwan matar da abin wuyar ta sun sace ta zuwa ga ƙaunataccenta.
ƙaunataccen ya ci gaba da yabon matar
ƙaunataccen yana tunanin sumbar matar ya na kamar zakin zuma da madara; ko,tana maganar da ke da daɗi kamar madara da zuma.
ƙaunataccen ya ci gaba da yabon matar
"lambu ne wanda aka kulle."ƙaunataccen ya kwatatanta matar da lanbun da aka kulle domin ita ta sa ce kadai kuma shi kadi ne zai ji daɗinta.Ya na kuma iya cewa ita budurwa ce da ba ta san namiji ba.
ƙaunataccen ya kwatanta yadda matar ta ke da muhimmanci ta wurin kwatantata da lanbu mai abubuwan ban mamaki.
Kaunataccen ya ci gaba da yabon matar.
"Ke maɓulɓular lambu ce." ƙaunataccen ya kwatanta gamsuwarsa da maɓulɓular ruwa mai Kyau.
1Na shigo cikin lambuna, 'yar'uwata, amaryata; na tattaro mur da kayan ƙanshina. Ina shan zumana da saƙarsa; na sha ruwan inabina da madarata. Abokai suna yin magana da mutumin da matar, Ku ci, abokai, ku sha ku bugu da ƙauna. Matar tana magana da kanta.2Ina barci, amma zuciyata ba barci take yi ba. Ƙaunataccena yana ƙwanƙwasa ƙofa yana cewa, "Ki buɗe mani, 'yar'uwata, abin ƙaunata, kurciyata, ke tawa marar cikas, gama kaina ya jiƙa da raɓa, sumata kuma da danshin dare."3Na tuɓe rigata; in sake maida ita ne? Na wanke ƙafafuna; in sake sawa su yi dauɗa?"4Ƙaunataccena yasa hannunsa a kan marfin ƙofa, kuma zuciyata tana wajensa.5Na tashi in buɗe ƙofa saboda ƙaunataccena; hannuwana nashe-nashe da mur, yatsuna da danshin mur, a kan mariƙin ƙofa.6Na buɗe ƙofar saboda ƙaunataccena, amma ƙaunataccena ya juya ya tafi. Zuciyata ta nutsa sa'ad da yayi magana. Na neme shi, amma ban same shi ba; na kira shi amma bai amsa mani ba.7Masu gadi suka tarar dani sa'ad da suke aikinsu na zagaya birni. Suka buge ni suka ji mani ciwo; masu gadin da ke kan ganuwa suka ɗauke gyalena daga gare ni. Matar tana magana da matan birni.8Ina so ku yi rantsuwa, ku 'yammatan Yerusalem, idan kuka haɗu da ƙaunataccena - Me zaku sanar da shi? - ina ciwon ƙauna. Matan birni suna magana da matar.9Da me ƙaunataccenki ya fi wani ƙaunataccen, ke mafi kyau a cikin mata? Me yasa ƙaunataccenki ya fi wani ƙaunataccen, da kika ce mu ɗauki alkawari kamar wannan?10Matar ta na magana da matan birni. Ƙaunataccena wankan tarwaɗa ne yana sheƙi, fitacce ne shi a cikin dubu.11Kansa zinariya ce mai tsaftar gaske; sumarsa nannaɗe take baƙa wulik kamar hankaka.12Idanunsa kamar kurciyoyi a bakin ƙoramar ruwa, sun yi wanka da madara, sun tsaya kamar lu'ulu'ai.13Kumatunsa suna kama da kwamin kayan ƙanshi, yana bada ƙanshi mai gamsarwa. Leɓunansa abin kallo ne, nashe-nashe da ruwan mur.14Hannayensa kamar zinariyar da a ka yi wa dajiya da lu'ulu'ai; kwankwasonsa kamar hauren giwar da a ka dalaye da duwatsun saffayar.15Ƙafafunsa kamar ginshiƙan da a ka yi da zinariya tsantsa, fitowarsa kamar Lebanon, zaɓabbe kamar itacen sidar.16Bakinsa yana da zaƙin gaske; shi cikakkaken abin ƙauna ne. Wannan shi ne Ƙaunataccena, kuma wannan shi ne abokina, 'yammatan Yerusalem.
Duba: and
Mutumin yana kawatanta matar da lambu.A daren ranar auren su,mutumin ya sami zarafin jin daɗin matar.Saboda haka ya kwatanta wannan da shiga lambu.
Mutumin ya kira matar 'yar'uwarsa domin yana ƙaunarta kwarai kamar yadda ya ƙaunaci 'yar'uwarsa.AT: "wanda nake ƙaunarta."
A nan sashi na huɗu na littafin ya fara
Matar ta mori abu kamar ɗoki domin bayyana mafarkinta domin a fassara shi a hanyoyi biyu :1)matar ta bayyana mafarki na wata dare wanda ƙaunatacenta ya zo gidanta; 2) matar ta bayyana mafarkinta na fara kwana da masoyinta.
AT: "amma zuciyata ba barci take ba." AT: "amma marmarina na nan."
fassarar yana iya zama kamar haka 1) ƙaunataccen ya miƙa hannunsa ta ramin kofar domin ya bude kofar ko 2) wannan yana bayayana fara juma'i.Anan "hannu" yana iya zama a kwatankwacin azzakarin namiji.
Ma'anar na iya zama kamar haka 1) matar ta fita daga gadonta domin ta kawo kaunataccenta cikin gida ko 2)" Na shirya kaina domin yin juma'i da ƙaunataccena."
Kalmomin nan "hannuwa" da kuma "yatsu" na iya nufin al'aurar mace.
matar ta cigaba da yin bayani a kan mafarkinta
"zuciyata ta bar ni,lokacin da yayi magana." AT:"lokacinda ya yi magana na ji kamar na mutu."
waɗanda ke gadi da kuma kular birnin da dare
"ji mani ciwo"
Kalmar nan "ni" na nufin budurwa.
ƙaunarsa ya na da karfi har ya sata ciwo.
Dubi yadda ka juya "mafi kyakkyawa cikin mata" 1:8.
"menene ya sa ƙaunatacciyarka ta fi"
Ya nuna matar tana bayyana fatar jikin ƙaunataccenta.AT: "ya na sheƙi kuma sumarsa nannaɗe."
"fitacce ne a cikin dubu." AT: "fiye da kowa" ko "babu kamarsa sai dai shi."
Matar ta cigaba da bayyana kaunataccenta.
Matar ta na anfani ne da misalin ta na fadar cewa idanun kaunataccenta su na kamar danshi a bakin ƙorama.
Matar ta ci gaba da yin bayani a kan kaunataccenta.
Wannan yana baiyana yadda kumatunsa suke kamar kayan ƙanshi domin yadda suke bada ƙanshin su.
Matar ta kwatatanta lebunansa da lili saboda su na da kyau da ƙanshi mai daɗi.
Matar ta ci gaba da bayyana kaunatacenta.
"hannanyensa kamar zinariyar da aka yi wa dajiya da lu'ulu'ai" Matar da yi anfani da wannan hoton ne domin ta ce hannayensa suna da kyau da kuma armashi.
safayar wani dutse ne mai haske da daraja.Irin wannan saffayar wataƙila ruwan kwoi ne ko kuma ruwan zinariya.
Matar ta ci gaba da bayani a kan kaunataccenta.
"ya na kama da Lebanon." Lebanon ƙasa ce mai kyau da tuddai da kuma itatuwa.
Matar ta ci gaba da bayani a kan kaunataccenta.
Matar ta na anfani da wannan domin ta nuna yadda sumbar sa ke da daɗi na ƙaunataccenta ko kalmoninsa masu daɗi daya faɗa.
1Ina ƙaunataccenki ya tafi, ke mafi kyau a cikin mata? Wacce hanya ƙaunataccenki ya bi, domin mu neme shi tare da ke? Matar tana magana da kanta.2Ƙaunataccena ya gangara zuwa lambunsa, wurin kwamin kayan ƙanshi, domin yayi kiwo a lambu kuma ya ɗebo furen kallo.3Ni ta ƙaunataccena ce, ƙaunataccena kuma nawa ne; yana kiwo a cikin furanni da farinciki. Mutumin yana magana da matar.4Kina da kyau kamar Tirzah, abin ƙaunata, ƙauna kamar Yerusalem, mai ban sha'awa da gamsarwa kamar tutocin nasara na sojoji.5Ki juyar da idanunki daga wajena, gama suna ɗaukar mani hankali. Gashinki yana kama da garken awakin da ke gangarowa daga magangarin Giliyad.6Haƙoranki suna kama da tumakin da a ka yi wa aski suna fitowa daga wurin da a ka yi masu wanka. Kowacce da 'ya'uwarta ba wadda take baƙinciki.7Kumatunki sumul-sumul a cikin lulluɓinki. Mutumin yana magana da kansa.8Akwai sarauniyoyi sittin, ƙwaraƙwarai tamanin, 'yammata kuwa sun fi a ƙirga.9Kurciyata, marar aibi, ita kaɗai ce; ita kaɗai ce ɗiya a wurin mahaifiyarta; tana da tagomashi a wurin matar da ta haife ta. 'Yammata sun gan ta sun kira ta mai albarka; sarauniyoyi da ƙwaraƙwarai ma sun ganta sun yabe ta: Ga abin da sarauniyoyin da ƙwaraƙwaran suka ce,10"Wace ce wannan da ta fito kamar tauraron asubahi, kyakkyawa kamar wata, mai haske kamar rana, mai ban sha'awa kamar sojoji da tutocinsu?" Mutumin yana magana da kansa.11Na gangara cikin rukunin itatuwa domin in ga waɗanda suke yin girma a cikin kwari, in gani ko inabi sun yi lingaɓi, in gani ko itatuwan rumman suna yin fure.12Na yi murna sosai na ji kamar ina cikin karusar sarki. Ƙawayen matar suna magana da ita.13Ki dawo, ki dawo, ke sahihiyar mata; ki dawo, ki dawo domin mu kalle ki. Matar tana magana da ƙawayenta. Me yasa kuke kallon sahihiyar mata, kamar rawa a tsakanin sojoji biyu?
Duba: and
AT: "ki gaya mana domin mu neme shi tare da ke."
Duba bayani akan wannan hoton a 5:1
Duba yadda ka juya "kwamin kayan ƙanshi" a 5:13.ƙaunataccen ya zo ya ji daɗin jikin matar wanda suna kamar kayan ƙanshi.
A nan sashi na biyar na littafin ya fara
ƙaunataccen ya kwatanta kyaun matar da armashi da kyau kuma da armashin birni.
ban sha'awa kamar tutocin sojoji-Kyaun matar ya na da iko har ya sa ƙaunataccenta ya rasa abin yi,kamar sojoji na kusatowa.
ƙaunataccen ya ci gaba da yabon matar.
"tsoratar da ni." Idannuwan matar su na da kyau har sun sa ƙaunataccenta ya na jin hankalinsa ya ɗauke da kuma fargaba domin bashi iya ja da ikon.
ƙaunataccen ya ci gaba da yabon matar.
Duba yadda ka juya a 4:3
"Akwai sarauniyoyi sittin,kwarakwarai tamanin."
Kalman nan,"sun fi a kirga" yana nufin babu wanda zai iya kirga su. AT: "yammata da yawa"
Abinda sarauniyoyi da kwarakwarai su ka ce game da 'yammata.Ko da shike wasu fassarar su na tunanin ƙaunataccen matar shi ma yana magana a wannan ayar.
Sun yi wannan tambaya ne domin su ce yarmatan ta na da armashi.AT: "wannan mace ce mai ban sha'awa! Ta bullo kamar asubahi."
Kaunataccen ya gama magana da kansa
ƙaunataccen ya yi anfani da wannan hotun domin ya bayyana murnar sa. (Duba: figs simile)
"ki dawo,ki dawo." Wannan maimai ci ne.
abin mamaki ne a ga matar ta na rawa tsakanin ma su rawa biyu.
1Ƙafafunki sun yi kyau sosai a cikin takalmanki, ɗiyar sarki! Tsarin cinyoyinki sun yi kama da lu'ulu'ai, aikin ƙwararre a sassaƙa.2Cibiyarki tana kama da bangaji; dãma kada ta rasa gaurayayyen ruwan inabi. Cikinki yana kama da tarin alkama kewaye da furen kallo.3Nonnanki biyu suna kama da tagwayen bareyi.4Wuyanki yana kama da hasumiyar hauren giwa, idanunki tafki ne cikin Heshbon a ƙofar Bat Rabbim. Hancinki kamar hasumiya ce cikin Lebanon wadda ta ke fuskantar Damaskus.5Kanki yana bisanki kamar Karmel; gashin kanki shunayya ne mai duhu-duhu. Kitsonki ya ɗauke hankalin sarki.6Ke kyakkyawa ce kuma abin ƙauna, ƙaunatacciyata, tare da jin daɗi!7Kina da tsawo kamar itacen dabino, nonnanki suna kama da kurshen 'ya'yan itace.8Na ce, "Ina so in hau wannan itacen dabino; zan kama rassansa." Dãmã nonnanki su zama kamar kurasan zaitun, damã ƙanshin hancinki ya zama kamar 'ya'yan tsada.9Dãmã kitsonki ya zama kamar ruwan inabi mafi kyau, ya malala a hankali domin ƙaunataccena, ya gangara leɓunan waɗanda suke yin barci.10Matar tana magana da mutumin. Ni ta ƙaunataccena ce, yana marmari na.11Kazo, ƙaunataccena, bari mu je ƙauye; bari mu kwana a can cikin ƙauyuka.12Bari mu tashi da sassafe mu tafi gonaki; bari mu gani ko inabi sun yi lingaɓi, ko furanninsu sun buɗe, mu gani ko itatuwan rumman sun yi fure. A can zan baka ƙaunata.13Tsiretsire suna ba da ƙanshinsu; akwai dukkan zaɓaɓɓun 'ya'yan itatuwa a ƙofar wurin da mu ke tsaye, da sabo da tsoho, waɗanda na ajiye saboda kai, ƙaunataccena.
wannan yana nufin kamar yadda yake a 6:13 ƙaunataccen matar ya na bayyana ta lokacin da take rawa.AT: "ƙafafunki su na da kyau a cikin takalmanki lokacinda kike rawa."
kaunataccen matar ya ci gaba da kwatantata
kaunataccen matar ya ci gaba da kwatantata
sunan birnin da ke gabas da Kogin Urdun
"da ke barin mutane su kalla zuwa Damaskus"
Kaunataccen matar ya ci gaba da kwatantata
ƙaunataccen ya bayyana abin da zai so yayi da ƙaunatacciyarsa
ƙaunataccen ya ci gaba da baiyyana abinda zai yi da ƙaunatacciyarsa
Duba yadda ka juya "Ni ta kaunataccena ce" 6:2
"kuma yana marmari na" ko "kuma yana so na"
Matar ta ci gaba da magana da ƙaunataccenta.
Matar ta ci gaba da magana da ƙaunataccenta
1Dãmã kai ɗan'uwana ne, wanda a ka yi renon sa da nonnan mahaifiyata. Daga nan duk inda na ganka a waje, sai na sumbace ka, kuma ba wanda zai rena ni.2Zan yi maka jagora in kawo ka gidan mahaifiyata - ita wadda ta koyar da ni. Dã na baka ruwan inabi mai ƙanshi ka sha da wani abin sha daga itatuwan rumman. Matar tana magana da kanta.3Na tãda kai da hannun hagunsa hannun damansa kuma yana rungume da ni.4Matar tana magana da waɗansu mata. Ina so ku yi rantsuwa, ku 'yammatan Yerusalem, ba zaku shiga tsakani ku dame mu ba sai mun gama ƙaunarmu.5Matan Yerusalem suna magana. Wace ce wannan da ke fitowa daga cikin jeji, tana jingina da ƙaunataccenta? Matar tana magana da mutumin. Na tashe ka a ƙarƙashin itacen tsada; a can mahaifiyarka ta ɗauki cikin ka; a can ta haife ka, ita ta haife ka.6Ki sani kamar hatimi a zuciyarki, kamar hatimi a hannunki, gama ƙauna tana da ƙarfi kamar mutuwa. Ƙarfin kishi kamar Lahira; harshensa yana ƙonewa; harshen wuta ne mai ci, harshen wutar ya fi kowacce wuta zafi.7Ruwa mai yawa ba zai iya kashe ƙauna ba, ko rigyawa ma ba zata iya share ta ba. Koda mutum zai bayar da dukkan abin da ya mallaka a gidansa saboda ƙauna, za a rena abin da ya bayar.8'Yan'uwan matar suna magana da junansu. Muna da 'yar'uwa ƙarama, nonnanta ko fitowa basu yi ba. Me zamu yi wa 'yar'uwarmu sa'ad da za a ba da ita aure?9Inda ita ganuwa ce, da sai mu gina hasumiyar azurfa a kanta. Inda ita ƙofa ce, da sai mu yi mata ado da katakon al'ul.10Matar tana magana da kanta. Ni ganuwa ce, amma nonnana yanzu suna kama da hasumiya ƙayatacciya; Ina kama da mai kawo salama a idanunsa. Matar tana magana da kanta.11Suleman yana da gona a Ba'al Hamon. Ya sa waɗansu su kula da ita. Kowannen su zai kawo masa kuɗi azurfa dubu daga 'ya'yan itatuwanta.12Gonata, tawa ce sosai, tana gabana; Suleman, kuɗi azurfa dubu naka ne, azurfa ɗari biyu kuma na masu kula da 'ya'yan itatuwan gonar ne.13Mutumin yana magana da matar. Ke da kike zaune a cikin lambuna, abokaina suna sauraren muryarki; bari nima in ji muryarki.14Matar tana magana da mutumin. Ka yi hanzari ƙaunataccena, ka zama kamar barewa ko batsiya a kan duwatsu inda kayan ƙanshi suke.
Duba: and
Matar ta yi marmarin nuna wa ƙaunataccenta ƙauna a fili kamar yadda zata yi wa ɗan'uwanta.Ba ta na cewa mace na da daman ta yi juma'i da ɗanuwanta ba ne.
Matar ta ci gaba da magana da kaunataccenta
Ana iya juya wannan haka "kuma za ta koyar da ni." Saboda matar bata iya yin juma'i ba,ta na tunanin ƙaunataccenata ko mahaifiyarta za ta koyar da ita yadda ake jumai.
Duba yadda ka juya shi a 2:7
Duba yadda ka juya shi a 2:7
Anan sashi na shidda na littafin, ya fara
AT: "Duba wannan matar da ke fitowa." Duba yadda ka juya irin wannan furcin a 6:10.
Matar ta ci gaba da magana a kan kaunataccenta
ma'anar na iya zama haka 1) saboda hatimi ya na da anfani a wurin mutane,mutane su kan sa shi a wuyar su ko kuma a kan hannunsu kullum.Matar ta na so ta kasance da kaunataccenta kullum kamar hatimi ko 2) Hatimi ya na nuna wanda ya mallaki abin da ya ke da hatimin. Matar ta na so ta zama hatimi a zuciyar kaunataccenta da hannunsa domin ta nuna dukkan tunaninsa,marmarinsa,da kuma ayyukansa su zama nata,
Matar ta ci gaba da magana da kaunataccenta
Kauna tana da karfi kamar wuta wanda ke da zafi da ba za a iya kashe ta ba ko da ruwan teku.
"yar'uwa karama"
AT: " namiji ya iso kuma ya na so ya aure ta"
'Yan'uwan matar sun ci gaba da magana tsakaninsu.
Domin nonnanta kanana ne,ta na da kirji mara fadi kamar katanga ko kofa.'Yan'uwanta maza suka yi mata ado domin su sa 'yar'uwarsu ta yi kyau.
Nonuwanta matar suna kama da hasumiya,
Wannan sunan birni ne a arewacin Isra'ila.
"saboda muryarki"
"bari nima inji ta." kalman "ta" ya na nufin muryar matar
Duba yadda ka juya a 2:16.
"duwatsu inda kayan ƙanshi suke" Matar ta na anfani da wannan hoton domin ta gaiyaci ƙaunataccenta ya zo domin ya ji daɗinta.Duba: yadda ƙaunataccenta yayi anfani da hoton duwatsun mur da duwatsun turare a 4:6.
1Wahayin Ishaya ɗan Amoz, wanda ya gani game da Yahuda da Yerusalem, a kwanakin Uziya, da Yotam, da Ahaz, da Hezekiya, sarakunan Yahuda.2Ku saurara, ku sammai, ke duniya, ki kasa kunne; gama Yahweh ya yi magana: "Na yi renon 'ya'ya na girmar da su, amma sun tayar mani.3Sã ya san mai shi, jaki kuma ya san inda ubangijinsa ke ciyar da shi, amma Isra'ila ba ta sanni ba, Isra'ila ba ta fahimta ba,"4Kaito! Al'umma, masu zunubi, mutanen da zunubi ya danne su ƙasa, zuriyar masu aikata mugunta, 'ya'ya masu aikin lalata! Sun yi watsi da Yahweh, sun rena Mai Tsarki na Isra'ila, sun ware kansu daga gare shi.5Donme a ke ta dukan ku har yanzu? Me ya sa kuke ta tayarwa akai akai? Dukkan kai yana ciwo, dukkan zuciya kuma ta yi rauni.6Tun daga tafin sawu har zuwa kai ba inda ba ciwo; sai ciwuka ne da ƙoƙƙojewa, da sababbin raunuka; ba'a rufe su ba, ba'a tsabtace su ba, ba'a naɗe su ba, ko kuma a sa masu mai.7Ƙasarku ta zama kufai; an ƙone biranenku; filayenku - a idonku, bãƙi na hallaka su - an yi watsi da su, an yi kaca-kaca da su ta hannun bãƙi.8Ɗiyar Sihiyona an barta kamar 'yar bukka a garkar inabi, kamar 'yar rumfa a lambun kukumba, kamar birnin da aka yiwa sansani.9Idan dã Yahweh mai runduna bai bar mana ragowa ƙalilan ba, da mun zama Sodom, mun kuma zama kamar Gomora.10Ku ji maganar Yahweh, ku shugabannin Sodom; ku saurari shari'ar Allahnmu, ku mutanen Gomora:11"Mene ne yawan hadayunku a gare ni?" in ji Yahweh. Ina da isassun baye-bayen ƙonawa na raguna, da kitsen manyan dabbobi; da jinin bijimai, da raguna, ko awaki waɗanda bana jin daɗi.12Lokacin da kuka zo gare ni wa ya buƙaci wannan daga gare ku, don ku tattaka harabaina?13Kada ku ƙara kawo baye-bayenku marasa ma'ana, na ƙi ƙonennan turare, ba zan yarda da bukukuwanku na sabon wata ba da na Asabaci - Ba zan yarda da wannan taron ba.14Na ƙi bukukuwanku na sababbin watanni da keɓaɓɓun ranaku; sun zama nawaya a gare ni; Na gaji da jurewa da su.15Don haka lokacin da kuka buɗe hannuwanku kuna addu'a na ɓoye fuskata daga gare ku; koda ya ke kun yi addu'o'i da yawa, Ba zan ji ba; hannuwanku sun cika da jini.16Yi wanka ku tsabtace kanku; ku cire mugayen ayyukanku daga fuskata, ku dena mugunta;17Ku koyi yin abin kirki; ku nemi adalci, ku dena danniya, ku yi adalci ga marayu, ku kare gwauraye."18Sai ku zo mu tattauna tare," in ji Yahweh; koda zunubanku sun yi kamar jangarura za su yi fari kamar ƙanƙara; koda sun yi jawur kamar jini, za su zama kamar ulun auduga.19In kun yarda kuka yi biyayya za ku ci mafi kyau daga cikin ƙasar,20Amma idan kuka ƙi kuka yi tayarwa, to takobi zata haɗiye ku," domin bakin yahweh ne ya furta haka.21Yadda birni mai aminci ya zama karuwa! Ita da dã take cike da adalci, amma yanzu ta cika da masu kisan kai.22Zinariyarki ta zama marar tsarki, ruwan inabinki ya gauraye da ruwa.23Sarakunanki masu tayarwa ne da kuma abokan ɓarayi; kowa na ƙaunar cin hanci, yana gudu domin ya ci haram. Ba su kare marayu ba, ba su kuma yiwa gwauruwa shari'ar adalci ba a lokacin da ta zo gare su.24Saboda haka sai ku ji abin da Yahweh mai runduna ya faɗi, Mai Iko na Isra'ila: "Kaiton su! Zan ɗauki fansa a kan maƙiyana, in kuma nuna ramuwata a kan magabtana;25Zan juya hannuna gãba daku, zan tace ku kamar yadda ake tace ƙarfe in kawar da ƙazantarku dukka.26Zan maido da mahukuntanku kamar farko, mashawartanku kuma kamar na can farko; bayan wannan za a kira ku birnin adalci, gari kuma mai aminci."27Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma ta wurin adalci.28Masu tayarwa da masu zunubi za a murje su tare, waɗanda suka yi watsi da Yahweh kuma za a kawar dasu.29Don za ku ji kunyar wurare masu tsarki na itatuwan rimi da kuke marmari, za a kuma kunyata ta wurin lambun da kuka zaɓa.30Gama za ku zama kamar itacen rimi wanda ya kaɗe, kamar kuma lambun da ba ruwa.31Ƙaƙƙarfan mutum zai zama kamar ƙeƙasesshe, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duk za a ƙone su tare, ba kuma mai kashe su."
"Wannan wahayin ne na Ishaya ... wanda Yahweh ya nuna masa" ko "Wannan shi ne abin da Allah ya nuna wa Ishaya"
Amoz shi ne mahaifin Ishaya.
"Yahuda" yana nufin masarautar kudu ta Isra'ila. "Yerusalem" shine birni mafi mahimmanci. Sunayen wuraren suna wakiltar mutanen da ke zaune a cikinsu. AT: "waɗanda ke zaune a Yahuda da Yerusalem" ko "mutanen Yahuda da Yerusalem"
Wannan karin magana ne kuma yana nufin lokacin da kowane sarki yayi sarauta. Sun yi sarauta ɗayan bayan ɗayan, ba duka a lokaci guda ba. AT: "lokacin da Uziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya suka kasance sarakunan Yahuda"
Ishaya yayi magana da mutanen Yahuda ta hanyar waƙa.
Ko da yake an yi annabcin waɗannan don mutanen Yerusalem da Yahuda su ji, Ishaya ya san ba za su saurara ba. Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) yana magana ne a cikin zagi, kamar dai "sammai" da "ƙasa" za su iya sauraron abin da Yahweh ya ce, ko 2) kalmomin "sammai" da "ƙasa" kalmomi ne masu raɗaɗi da rahama don duk mai rai a ko'ina. AT: "ku da ke rayuwa a sama ... ku da ke rayuwa a duniya"
Wannan sunan Allah ne wanda ya bayyana wa mutanensa a Tsohon Alƙawari. Duba translationWord shafi game da Yahweh game da yadda za a fassara wannan.
Yahweh yana magana kamar maganarsa abinci ce kuma kamar Isra'ilawa yaransa ne. AT: "Na kula da mutanen da ke zaune a Yahuza kamar yara na"
Wannan yana iya nufin "amma mutanen Isra'ila ba su san ni ba, ba su fahimci cewa ni ne wanda ke kula da su ba."
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) Ishaya yana faɗi abubuwa biyu daban-daban game da su. AT: "Al'ummar Isra'ila, ku masu zunubi" ko 2) yana faɗin abu ɗaya kawai game da su. AT: "ƙasar masu zunubi"
Wani abu mai nauyi wanda mutum zai iya ɗauka shine kwatancin zunuban su da yawa. AT: "zunubin nasu kamar jaka ce mai nauyi a kafaɗunsu wanda ke wahalar da su yin tafiya"
Kalmar "zuriya" wani magana ga mutanen da suke aikata abin da wasu suka aikata. AT: "mutanen da suke aikata mugunta iri ɗaya suna ganin wasu suna aikatawa"
"Sun rabu da Yahweh"
Ishaya yayi amfani da waɗannan tambayoyin don tsawata wa mutanen Yahuda. Ana iya fassara tambayoyin azaman maganganu. Hakanan za'a iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kuna ci gaba da yin abubuwan da ya kamata Yahweh ya hukunta muku. Kuna ci gaba da yi masa tawaye."
Wannan magana yana kwatanta al'ummar Isra'ila da mutumin da aka buge. AT: "Kuna kamar wanda kansa ya yi rauni kuma zuciyarsa ta raunana" ko "Kuna kamar wanda duk hankalinsa da zuciyarsa ba su da lafiya"
Wannan magana yana kwatanta azabar da Allah ya ba Isra'ila ga raunuka na zahiri. Ana iya bayyana shi cikin tsari mai aiki. AT: "babu wanda ya rufe, ya tsarkaka, ko bandeji, ko ya kula da su da mai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sun lalata ƙasarku" ko "Makiyanku sun lalata ƙasarku"
'Yar' birni na nufin mutanen birni. AT: "Mutanen Sihiyona" ko "Mutanen da ke zaune a Sihiyona"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "baƙi sun kifar da ƙasarku" ko "wata rundunar baƙi ta ci ta da yaƙi kwata-kwata"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "ya zama ƙarami kamar bukka a gonar inabi ko rumfa a gonar kukumba" ko 2) "an bar ta yadda manomi ke barin bukka a cikin gonar inabi ko rumfa a cikin lambun kukumba idan ya gama da su "
"'yan tsira"
Yadda Yahuda za ta kasance kamar Sodom da Gomora za a iya bayyana a sarari. AT: "Da Allah ya hallakar da mu, kamar yadda ya lalata biranen Sodom da Gomora"
Ishaya yana kwatanta mutanen Yahuda da Sodom da Gomora don ya nanata irin zunubin da suka yi. AT: "ku shugabanni masu zunubi kamar na Sodom ... ku mutanen da ke mugaye kamar waɗanda suka rayu a Gomora"
Allah yana amfani da tambaya don tsawata wa mutane. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "sadaukarwarku da yawa ba komai a gare ni!"
Kalmar "tattake" tana nufin takawa da murkushewa da ƙafafun mutum. Allah yana amfani da tambaya don tsawata wa mutanen da ke zaune a Yahuda. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "babu wanda ya gaya muku ku yi tattaki a farfajiyoyi na!"
"Kada ka kawo mini wasu kyaututtukanka marasa amfani"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Ba zan iya barin ku ku hallara ba saboda muggan ayyukan da kuke aikatawa" ko 2) "Ba zan iya barin kaina in ga kuna taruwa saboda muggan ayyukan da kuke aikatawa ba."
Kalmomin "sabon wata" wata wani magana ne ta bikin sabon wata. AT: "bikinku na sabon wata da sauran bukukuwanku na yau da kullun"
Wannan yana kwatanta yadda Allah yake ji game da bikin mutane da ɗaukar abu mai nauyi. AT: "nauyi ne mai nauyi da na gaji da ɗaukarsa"
Wannan shine dalilin da yasa Allah ba zai saurari addu'o'in su ba. Jinin yana iya nufin tashin hankalin da suka yi wa mutane. AT: "saboda kamar hannayenku sun kasance cike da jinin waɗanda kuka cutar da su" ko "saboda kuna da laifin tashin hankali"
Anan Allah yana kamanta mutumin da ya daina yin zunubi da wanda yake wankan jikinsa. AT: "Ku tuba ku wanke zunubin daga zuciyarku kamar yadda kuke wanke ƙazantar daga jikinku"
Allah bai ce masu su yi munanan ayyukansu a wani wuri ba, amma su daina yin su. AT: "ku daina aikata miyagun ayyukan da na ga kuna yi"
"ku yi adalci ga yaran da ba su da uba"
Yahweh cikin alheri da ƙauna yana gayyatar mutane su saurari abin da zai faɗa. "Da fatan za ku saurare ni. Bari" ko "Ku mai da hankali; Ina so in taimake ku. Bari"
"bari muyi tunani game da wannan tare" ko "muna buƙatar tattauna wannan" ko "me za mu yi?" Yahweh yana gayyatar mutane su tattauna abin da ke zuwa a nan gaba. Anan kalmar "mu" tana nufin Yahweh kuma ya haɗa da mutanen Yahuda.
Ishaya yana magana ne game da mutane kamar suna sanye da tufafi waɗanda ya kamata su zama farin ulu da na zunubansu kamar dai suna da jajaje a jikin tufafin. Idan Yahweh ya gafarta musu zunubansu, zai zama kamar tufafinsu sun sake fari.
Anan, "shirye" da "masu biyayya" ana amfani dasu tare don bayyana ra'ayi ɗaya. AT: "Idan da yarda za ku yi biyayya"
"Kasar za ta fitar da abinci mai kyau domin ku ci"
"amma idan kun ƙi saurara kuma maimakon ku yi min biyayya"
Kalmar "takobi" tana nufin magabtan Yahuda. Har ila yau, kalmar “mai cinyewa” tana kwatanta maƙiyan Yahuda masu zuwa don su kashe su da dabbar daji da ke kai hari da cin sauran dabbobi. AT: "makiyanku za su kashe ku"
Wannan motsin rai ya nuna fushin Ishaya da ɓacin ransa game da mutanen Yerusalem. AT: "Duba yadda mutanen Yerusalem, waɗanda suka kasance da aminci ga Allah"
Ishaya ya kwatanta mutanen da matar da ba ta da aminci ga mijinta amma tana kwana da wasu maza don kuɗi. Mutanen ba su da aminci ga Allah amma suna bauta wa allolin ƙarya. AT: "tana yin kamar karuwa"
Kalmar "ta" tana nufin Yerusalem da mutanenta. Waɗanda suka rubuta Littafi Mai Tsarki galibi suna kiran biranen mata. AT: "amma yanzu mutanen Yerusalem masu kisan kai ne"
Zai yiwu ma'anoni su ne cewa Ishaya ya yi amfani da azurfa da ruwan inabi a matsayin kwatanci na 1) mutanen Yerusalem. AT: "Kuna kamar azurfar da ba ta da tsarki, kuma kamar ruwan inabi wanda yake gauraye da ruwa" ko 2) kyawawan ayyukan da mutane suka yi a dā. AT: "Kun kasance kuna aikata kyawawan ayyuka, amma yanzu ayyukanku marasa kyau sun sa kyawawan ayyukanku sun zama marasa amfani"
"Shugabanninku sun yiwa Allah tawaye"
"suna abokai da mutanen da suke sata daga wasu"
"ba sa kare wadanda ba su da uba"
Duk waɗannan kalmomin suna nufin abu ɗaya ne. Kalmomin "ɗaukar fansa a kan magabtana" sun fi yin magana game da Yahweh yana yin duk abin da ya kamata ya yi wa waɗanda suke aiki da shi don ya yi farin ciki. Kalmomin "ɗaukar fansa a kan magabtana" sun fi magana game da Yahweh dai-dai da hukunta maƙiyansa. AT: "Zan hukunta waɗanda suka yi adawa da ni" ko "Zan yi abin da ke faranta min rai ga waɗanda suke ƙoƙari na, kuma zan hukunta magabtana dai-dai"
Anan "hannu" yana nufin ikon Allah wanda zai yi amfani da shi don azabtar da mutanensa. AT: "Zan fara amfani da dukkan ƙarfina a kanku"
Anan ana maganar yadda Allah yake kankare zunubin mutanensa kamar tana raba karfe daga munanan abubuwa da aka gauraye dashi. Kalmomin "kamar yadda yake da tace karfe" suna ƙara wani magana, saboda ana amfani da lye a sabulu, ba a cikin ƙarfe na ƙarfe ba. AT: "kuma kamar wuta tana cire datti daga azurfa, zan kawar da dukkan mugunta daga cikinku"
Waɗannan hanyoyi biyu ne na magana game da ɓangare na farko ko farkon tarihin Isra'ila, lokacin da Isra'ila ta fara zama al'umma.
Anan "birni" da "gari" suna nufin mutanen da ke zaune a Yerusalem. AT: "garin da mutane suke masu adalci da aminci ga Allah"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "Yahweh zai fanshi Sihiyona saboda mutanen da ke wurin suna aikata abin da yake dai-dai, kuma zai fanshe waɗanda suka tuba saboda sun aikata abin da Yahweh ya ce da-idai ne"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah zai halakar da waɗanda suka yi tawaye kuma suka yi masa zunubi"
Waɗannan jimlolin suna nufin wuraren da mutanen Yahuda suke bautar gumaka.
Ruwa yana ba da rai ga bishiyoyi da lambuna. Mutanen sun rabu da Yahweh, wanda ya ba su rai.
"Ƙaƙƙarfan mutum" ko "Duk wanda yake da iko." Wannan na iya nufin mutanen da suke da mahimmanci kuma suke tasiri ga sauran mutane.
Wannan yana kwatanta ayyukan mutum ko ayyukan mugunta da tartsatsin wuta wanda ya faɗo kan wuta ya hura wuta. AT: "aikinsa zai zama kamar walƙiya wacce ta kunna wuta"
1Abubuwan da Ishaya ɗan Amoz ya ji a wahayi game da Yahuda da Yerusalem.2Zai zamana a kwanaki na ƙarshe za a kafa tsaunin gidan Yahweh a can ƙololuwar tsaunuka, za a tada shi bisa dukkan tuddai, dukkan al'ummai kuma za su kwararo gare shi.3Mutane da yawa za su zo su ce, "Ku zo mu je kan tsaunin Yahweh, zuwa gidan Allah na Yakubu, don ya koya mana waɗansu hanyoyinsa, mu kuma yi tafiya cikin tafarkunsa." Gama daga Sihiyona shari'a za ta fito maganar Yahweh kuma daga Yerusalem.4Zai hukunta tsakanin al'ummai ya kuma yanke shawara ga mutane da yawa; za su mayar da takkubansu garemani, mãsunsu kuma su maida su almakashin yanke rassa; al'umma ba za ta sake tayar da takobi gãba da al'umma ba, ko kuma su sake horar da kansu don yaƙi.5Gidan Yakubu, ku zo, sai muyi tafiya cikin hasken Yahweh.6Gama ka yi watsi da mutanenka, gidan Yakubu, saboda sun cika da al'adu daga gabas suna kuma karatun sihiri kamar Filistiyawa, suna kuma shan hannuwa da 'ya'yan băƙi.7Ƙasarsu ta cika da zinariya da azurfa, kuma wadatarsu ba ta da iyaka; ƙasarsu kuma ta cika da dawakai, karusarsu ba ta da iyaka.8Hakannan kuma ƙasarsu ta cika da gumaka; suna bautawa aikin hannun mutum na hannuwansu, abubuwan da yatsunsu suka yi.9Za a sunkuyar da mutane ƙasa, mutum zai faɗi ƙasa; don haka kada ka tada su tsaye.10Ku je wurare masu duwatsu ku ɓuya a ƙarƙashin ƙasa don ku ɓoye wa hukuncin Yahweh daga kuma ɗaukakar ikonsa.11Za a ƙasƙantar da kallon girman kan mutum, fahariyar mutune kuma za a ƙasƙantar da ita, Yahweh kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.12Gama akwai ranar Yahweh mai runduna găba da duk masu girman kai da masu kumbura, găba kuma da duk marasa kunya -13kuma da dukkan itatuwan Labanon waɗanda suka yi girma sosai da kuma găba da dukkan itatuwan rimi na Bashan.14Waccan ranar ta Yahweh mai runduna za ta yi găba da dukkan dogayen tsaunuka, da tuddai da suka yi tsayi,15gãba kuma da doguwar hasumiya, gãba kuma da kowacce katanga marar gwami,16gãba kuma da dukkan jiragen ruwa na Tarshish, gãba kuma da dukkan kyawawan abubuwan tafiya a ruwa.17Za a saukar da girman kan mutum ƙasa, taƙamar mutum kuma zata fãɗi; Yahweh kaɗai za a ɗaukaka a waccan rana.18Gumakan za su shuɗe ɗungum.19Mutane za su shiga kogonnin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa, domin ɓuya daga razanar Yahweh, da kuma darajar ɗaukakarsa, a lokacin daya tashi domin ya razana duniya.20A ranar nan mutane za su watsar da gumakansu na azurfa da zinariya da suka yiwa kansu domin su bauta masu - za su watsar da su a gidan mujiya da jemagu.21Mutane za su shiga cikin matsin duwatsu da kuma cikin tsagar fasassun duwatsu domin su ɓuya daga hasalar Yahweh, kuma daga darajar martabarsa, a lokacin da ya tashi domin ya razana duniya.22Ku dena dogara ga mutum, wanda numfashinsa a ƙofofin hancinsa ya ke, domin kuwa wacce daraja ya ke da ita?
"zuwa gaba"
Ana iya bayyana wannan 1) azaman bayani. AT: "tsauni na gidan Yahweh zai tsaya" ko 2) cikin sigar aiki. AT: "Yahweh zai kafa tsaunin da aka gina haikalinsa a kansa"
Ishaya yayi maganar girmamawa cikin kwatanci kamar dai tsayi ne na zahiri. Ana iya bayyana wannan 1) cikin sigar aiki. AT: "Yahweh zai girmama shi fiye da kowane tsauni" ko 2) a matsayin suna na mutanen da suke bauta a can. AT: "Yahweh zai girmama mutanen da suke bauta a can fiye da yadda yake girmama sauran mutane"
Kalmar "hanyoyi" karin magana ne na yadda mutum yake rayuwa. Idan yarenku yana da kalma ɗaya tak don ƙasar da mutane suke tafiya a kanta, za ku iya haɗa waɗannan jimlolin. AT: "yana iya koya mana nufinsa domin mu yi masa biyayya"
Waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya. Ishaya yana nanata cewa dukkan al'ummai zasu fahimci cewa ana samun gaskiya a Yerusalem. AT: "Mutanen Sihiyona za su koyar da shari'ar Allah, kuma mutanen Yerusalem za su koyar da kalmar Yahweh"
"Yahweh zai yi hukunci"
"za su mayar da takubansu a matsayin kayan aikin shuka iri." Gamaho wani ruwa ne wanda mutane ke amfani da shi don haƙa cikin ƙasa don su shuka iri a can.
"za su dunkule mashinansu cikin ƙugiya" ko kuma "za su sanya mashinansu su zama kayan aikin kula da tsirrai." Cikakken matse wuƙa ce da mutane suke amfani da ita don yanke rassan shuke-shuke da ba a so.
"babu wata al'umma da za ta daga takobinta kan wata al'umma." Takobin ishararren yaƙi ne. AT: "wata al'umma ba za ta yi yaƙi da wata ƙasa ba"
"Ku zuriyar Yakubk." Kalmar "gida" na nuna ta mutanen da ke zaune a gidan, dangi. Anan "Yakubu" yana wakiltar jama'ar Yahuda, amma zai fi kyau a yi amfani da "Yakubu" a nan.
Ishaya yayi magana game da mutane suna koyo sannan suna aikata abin da Yahweh yake so suyi kamar suna tafiya da dare tare da fitilar da Yahweh ya tanada don su ga hanyar. AT: "bari mu koyi yadda Yahweh yake so mu rayu sannan mu rayu ta wannan hanyar"
Ishaya yayi magana kamar mutane kwantena ne waɗanda suke cike da wani abu daga gabas. Mai yiwuwa ma'anoni shine ya yi magana akan 1) ayyukan da mutanen gabas suke aikatawa. AT: "suna aikatawa a duk lokacin da mugayen abubuwan da mutanen da ke zaune a ƙasashen gabashin Isra'ila suke aikatawa" ko 2) mutane, musamman waɗanda ke da'awar yin magana da mutanen da suka mutu, waɗanda suka zo daga gabas don aikata mugunta. AT: "masanan da yawa sun zo daga gabas kuma yanzu suna zaune a can"
suna kokarin fadawa gaba ta hanyar duban abubuwa kamar sassan dabbobi da ganyaye
Waɗannan jumlolin biyu kusan suna da abu ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa waɗannan ba allahn gaske bane. Idan yarenku bashi da cikakkiyar kalma don abin da wani yayi, zaku iya haɗa waɗannan jimlolin biyu zuwa ɗaya. AT: "abubuwan da su da kansu suka yi"
Kalmar "yatsun hannu" yana wakiltar ga mutane da kansu. AT: "abubuwan da suka yi da yatsunsu"
Anan kasancewa ƙasa ƙasa yana wakiltar mutanen da aka wulakanta su gaba ɗaya saboda sun fahimci duk abin da suka dogara da shi ba shi da amfani, kuma ba za su iya yin komai don taimakon kansu ba. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah zai kunyata mutane, kuma za su gane cewa duk abin da suka dogara da shi ba shi da amfani"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne mutane su shiga 1) kogwanni a kan tsaunuka masu tsayi ko 2) wuraren da akwai manyan duwatsu da yawa waɗanda za a ɓoye a cikinsu.
AT: "don gujewa daga firgitawar Yahweh" ko "daga Yahweh saboda za ku ji tsoron shi ƙwarai"
"Yahweh zai saukar da duban mutum." Wani mutum mai "girman ido" yana kallon sama da kowa don ya nuna musu cewa ya fi su. Anan duk mutane sunyi laifi da tunanin sun fi Yahweh kyau, kuma yadda suke kallon waɗanda suke bauta wa Yahweh, alama ce ta girman kansu. AT: "Yahweh zai ba da kunya ga dukkan mutane saboda suna ganin sun fi shi kyau"
Wanda "aka tashe shi" yana alfahari kuma yana ganin kansa ya fi sauran mutane. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanene ke alfahari kuma wanda ya ɗaukaka kansa sama da sauran mutane" ko "wanene yake alfahari kuma yake ganin ya fi sauran mutane"
"Duk mai girman kai za a saukar da shi." Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai ƙasƙantar da shi"
Waɗannan kalmomin kwatanci ne don girman kan Isra'ilawa. Sun kuma bayyana a cikin Ishaya 2: 2.
Waɗannan suna nuni ne ga abubuwan da mutane zasu gina a kewayen biranensu don su iya kare kansu daga abokan gaba. Su na wakiltar ga Isra'ilawa "girman" kai da imani cewa ba su da bukatar Yahweh kuma suna iya tsayawa kan kowane irin hukunci da Yahweh zai same su saboda zunubansu.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zai ƙasƙantar da kowane mai alfahari" ko "Zai ƙasƙantar da kowane mutum mai alfahari"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane za su yabi Yahweh kawai"
"Duk gumaka za su shuɗe" ko "Ba za a ƙara samun gumaka"
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 2:9.
Jauhari ƙananan dabbobi ne waɗanda suke tono kuma suna rayuwa a ƙasan ƙasa. Jemagu ƙananan dabbobi ne masu yawo waɗanda wani lokaci suke rayuwa a cikin kogo. AT: "ga dabbobin"
Idan yarenku ba shi da kalmomi biyu daban don "kirki" da "tsaguwa," sararin da ke bayyana tsakanin bangarorin dutse biyu lokacin da ya rabu, za ka iya haɗa waɗannan jimlolin biyu zuwa ɗaya.
"Lokacin da Yahweh ya ɗauki mataki ya sa mutanen duniya su firgita ƙwarai da shi." Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 2:17.
1Duba, Ubangiji Yahweh mai runduna, yana gab da ya kawar da Yerusalem da kuma goyon bayansa daga Yahuda, da samar da gurasa da kuma ruwa,2mutum mai iko da mayaƙi, da mai hukunci, da annabi da masu dubarsu, da dattijo;3jagoran hamsin, da mazaunan birnin da ake girmamawa, da mashawarci, da shahararen masassaƙi, da gwanayen masu sihirinsu.4Zan sa matasa kawai su zama shugabanninsu, matashi kuma zai mulke su.5Za a tsanantawa mutane, za su tsananta wa junansu da kuma maƙwabtansu; yaro zai wulaƙanta dattijo, ƙasƙantattu kuma su ƙalubalanci masu martaba.6Mutum zai sami ɗan'uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, 'Kana da riga; ka yi mulkin mu, kuma bari wannan kangon ya kasance a hannuwanka,'7Ranar zai yi ihu ya ce, 'Ba zan iya zama mai warkarwa ba; ba ni da gurasa ko sutura. Ba za ku mai da ni shugaban mutane ba,'"8Gama Yerusalem ta yi tuntuɓe, Yahuda kuma ta faɗi, saboda maganganunsu da ayyukansu na gãba da Yahweh, suna rena idanunsa na ɗaukaka9Suka duba shaidunsu a fuskarsu suna gãba da su; suna maganar zunubansu kamar Sodom; ba su ɓoye shi ba. Kaiton su! Gama sun kammalawa kansu bala'i.10Faɗawa mai adalci cewa komai zai yi dai-dai, domin za su ci 'ya'yan ayyukansu.11Kaiton mugu! abin zai yi masa muni sosai, gama za'a sãka masa abin da ya aikata.12Mutanena 'ya'yansu su ne masu wahalshe su, mata ne kuma ke mulkinsu. Mutanena masu yi maku jagora suna ɓatar da ku suna kuma rikitar da hanyar tafarkinku.13Yahweh na tsaye domin ya faɗi laifin mutanensa; yana tsaye domin ya zarge su.14Yahweh zai zo da hukunci gãba da dattawan mutanensa da kuma shugabanninsu: "Kun lallatar da garkar inabi; ganimar matalauci na gidajenku.15Donme kuke ƙuje mutanena, kuke kuma musgunawa matalauta?" Wannan furcin Ubangiji Yahweh mairunduna ne.16Yahweh yace saboda 'yan matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya suna ɗaga wuya sama, suna kuma jujjuya idanunsu, suna rangwaɗa a lokacin da suke tafiya kayan adon ƙafafunsu na ƙãra.17Saboda haka Ubangiji zai saukar masu da ciwon ƙuraje a bisa kawunan 'yan matan Sihiyona, Yahweh kuma zai sa su yi saiƙo.18A wannan ranar Ubangiji zai cire masu kyawawan kayan adonsu na ƙafa, da maɗaurin kansu, da kayan adonsu masu siffofin wata,19da 'yankunne, da abin hannu, da kayan lulluɓi;20'yankwalaye, da sarkar ƙafa, da ɗamara; da akwatunan turare, da layunsu na neman sa'a.21Zai cire zobba da kayan adon hanci;22da suturun bukukuwa, da alkyabbobi, da mayanai, da jakkunan hannu;23da madubai na hannu, da linin mai kyau, da ƙyallayen kai, da kuma zannuwa.24A maimakon ƙanshin turare za su yi wari; a maimakon sarƙa kuma igiya; a maimakon gyararriyar suma kuma saiƙo, a maimakon sutura mai ƙawa kuma kayan makoki; tsaga maimakon kyau.25Mazajenku za su fãɗi da takobi, jarumawanku kuma za su fãɗi a wurin yaƙi.26Ƙofofin Yerusalem za su yi makoki da baƙinciki; za ta kuma zauna a ƙasa a kaɗaice.
Wannan jerin nau'ikan mutane ne da wasu suka dogara da su. Tunda basa magana game da wasu keɓaɓɓun mutane, duk ana iya fassara su da sunaye kamar yadda yake a cikin UDB. AT: "masu mutuntawa ... masu ba da shawara ... ƙwararrun masu fasaha ... masu sihiri"
Waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya daidai. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Zan sanya matasa a matsayin shuwagabanninsu, kuma waɗannan samarin za su mallake su" ko 2) "samari" wani magana ne ga maza masu sauƙi da wauta. AT: "Zan sanya a kansu shugabannin da ba su balaga ba, kamar matasa, kuma waɗannan mugayen shugabannin za su mulke su"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kowa zai zalunci wasu kuma zai wulakanta maƙwabcinsa"
Anan “hannaye” suna wakiltar hukuma. AT: "ɗauki nauyin wannan ɓarnar" ko "yi sarauta kan wannan ɓarnar"
Rashin yin biyayya ga Allah ana magana ne kai ka ce tana faɗuwa da faɗuwa.
Maganganu na girman kai a fuskokin mutane ana maganarsu kamar maganganun mutane ne waɗanda zasu iya ba da shaida akan mutanen masu girman kai. AT: "Girman kai a fuskokinsu yana nuna cewa suna adawa da Yahweh"
Bala'i yana nan tafe, amma mutane sun gama yin abin da zai sa ta zo. Ana magana game da musibar a nan kamar dai su kansu bala'in ne. AT: "Gama sun yi duk abin da zai haifar da bala'i"
"Ka gaya wa wanda yake yin abin da yake daidai cewa zan kyautata masa"
Ana magana akan ayyuka kamar bishiyoyi ne masu bada 'ya'yan itace waɗanda za'a iya ci. 'Ya'yan itacen suna tsaye don ladan aikata kyawawan ayyuka. AT: "domin zasu sami ladar ayyukansu na alheri" ko "don zasu sami ladarsu saboda kyawawan abubuwan da suka aikata"
Ya zama ruwan dare gama gari a Gabas ta Tsakiya don yin magana game da shugabannin ƙasa kamar suna makiyaya. Yayinda makiyaya ke jagorantar tumaki akan kyawawan hanyoyi zuwa aminci, shugabanni ya kamata su koyawa mutane gaskiya kuma su taimaka musu suyi abin da yake dai-dai. Shugabannin Yahuda ba sa yin haka. AT: "shugabanninku suna kama da makiyaya marasa kyau waɗanda ke ɓatar da ku daga hanyoyi masu kyau kuma ba sa nuna muku inda za ku tafi"
Ishaya yayi magana game da hukuncin da Yahweh ya yanke na cutar da mutane kamar dai Yahweh yana kawo zargi ne a cikin kotu game da mutanen Isra'ila. Kashi na biyu na wannan layin yana ma'anar abu ɗaya kamar na farko, amma ya faɗi gaba ɗaya kaɗan. AT: "Kamar dai Yahweh ya ɗauki matsayinsa a cikin kotu kuma a shirye suke su tuhumi mutanen"
Anan "ku" yana nufin dattawa da masu mulki. Yahweh yana maganar mutanensa kamar suna gonar anab. Kamar wanda ya ƙi kula da gonar inabi don inabin ya daina ba da ’ya’yan inabi, dattawa da shugabanni suna hana Isra’ilawa bauta wa Allah. AT: "Mutanena kamar gonar inabi ne, kuma kun lalata ta"
Yahweh yayi wannan tambaya don ya zargi shugabannin mutane. Ana iya bayyana wannan zargin a matsayin sanarwa. AT: "Ina fushi da ku mugayen mutane saboda kuna murkushe mutanena kuna murƙushe fuskokin talakawa!"
Sihiyona, ma'ana a nan birnin Yerusalem, ana maganar ta kamar mace da 'ya'yanta mata. AT: "matan Sihiyona"
"ta hanyar girman kai" (Duba: idiom)
Anan abin da Ubangiji ya sa wasu suke yi ana maganarsa kamar yadda Ubangiji ke yin shi da kansa. AT: "Ubangiji zai sa wasu su cire"
wani siraran abu mai matukar kyau wanda ake amfani da shi wajen rufe mata kai da fuska
doguwar, sakakkiyar tufafi dauke da kayan adon da aka sanya a kan sauran tufafin kowa ya gani
zane da aka sa a kan kafadu a wajen tufafin
kyalle mai taushi wadanda attajirai ke sakawa
Faduwa tana wakiltar kashewa, kuma takobi yana wakiltar yaƙi. AT: "Za a kashe mutanenku a yaƙi, kuma za a kashe mazanku a yaƙi" ko "Abokan gaba za su kashe sojojinku a yaƙi"
Anan ƙofofin birni suna wakiltar mutanen da suke zaune a wuraren taron jama'a kusa da ƙofar garin. AT: "Mutanen Yerusalem za su zauna a ƙofar gari suna kuka da baƙin ciki"
1A wannan rana mata bakwai za su riƙe namiji ɗaya su ce, "Mă ciyar da kanmu, mu yiwa kanmu suturar da za mu sa. Amma ka yarda a kira mu da sunanka domin a kawar mana da kunya."2A wannan ranar rassan Yahweh za suyi kyau da kuma ɗaukaka, 'ya'yan itatuwan ƙasar kuma za su yi zaƙi, da kuma jin daɗi ga waɗanda suka ragu a Isra'ila.3Zai kasance a wannan ranar da wanda ya ragu a Sihiyona da kuma wanda ya ragu a Yerusalem za a kira shi mai tsarki, da kuma duk wanda aka rubuta sunansa a matsayin mazaunin Yerusalem.4Wannan zai faru a lokacin da Ubangiji zai share tsaurin idon 'yan matan Sihiyona, ya kuma goge jinin da ya manne daga tsakiyar Yerusalem, ta wurin ruhun hukunci da kuma ruhun harshen wuta.5Sa'an nan dukkan sassan Tsaunin Sihiyona da kuma kan wuraren taruwarta, Yahweh zai yi girgije da hayaƙi da rana, da kuma hasken harshen wuta da dare; zai zama inuwa a kan dukkan ɗaukaka.6Za ta bada inuwa da rana daga zafi, da kuma mafaka da kuma maɓoya daga hadari da ruwan sama.
Wannan jumlar na nufin "bari mu aure ka."
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "reshe" wani magana ne wanda ke wakiltar albarkatun da Yahweh zai sa su girma a ƙasar Isra'ila. AT: "Yahweh zai sa albarkatun cikin Isra'ila su zama kyawawa" ko 2) "reshe" yana magana wanda ke nufin Almasihu.
'Ya'yan itacen "wani lokacin kawai yana wakiltar abincin da aka samar a ƙasar, wani lokacin kuma yana wakiltar albarkar ruhaniya. Mai yiwuwa ma'anoni a nan su ne 1) Allah zai sa ƙasa ta sake fitar da kyakkyawan abinci. AT: "mutanen da suka rage a cikin Isra'ila za su more mafi kyawun abinci daga ƙasar" ko 2) "Masihu na gaba zai kawo albarkar ruhaniya ga mutanen ƙasar."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "duk wanda sunansa yana cikin jerin mutanen da ke zaune a Yerusalem"
Wannan furcin yana magana akan zunubi kamar datti ne na zahiri. AT: "bayan da Ubangiji ya kankare zunuban 'yan matan Sihiyona kamar yadda wani ya wanke kazanta"
"Tabon jini" anan yana nuna tashin hankali da kisan kai. AT: "zai kwashe waɗanda ke Yerusalem waɗanda ke cutar da marasa laifi"
Wannan shine yadda Allah zai cire zunubi daga Yerusalem. A nan mai yiwuwa “ruhu” yana wakiltar aikin hukunci da konewa. AT: "ta hanyar hukunci da harshen wuta"
Mai yiwuwa su ne 1) alfarwa don kare birni mai ɗaukaka, ko 2) alfarwa mai ɗauke da ɗaukakar Allah wanda zai kiyaye garin. Idan aka bi ma'anar farko, to yana iya kara nufin cewa garin yana da ɗaukaka domin Yahweh yana nan a ciki.
1Sai in raira waƙa ga ƙaunataccena, waƙar ƙaunataccena game da garkar inabinsa. Wadda nake ƙauna sosai yana da garka a tudu mai dausayi.2Ya gyara ta, ya cire duwatsu, ya kuma shuke ta da irin inabi mai matuƙar daraja. Ya gina hasumiya a tsakiyar gonar, ya kuma kafa wurin matse ruwan inabi. ya jira ta bada 'ya'ya amma sai 'ya'yan inabin jeji kawai ta yi.3To yanzu, mazauna Yerusalem da mutanen Yahuda, ku yi hukunci tsakanina da garkar inabita.4Me kuma zan ƙara yi wa garkar inabita, da ban taba yi mata ba? Lokacin da na dube ta ta bada 'ya'ya me yasa ta bada 'ya'yan inabin jeji?5Yanzu zan fada maku abin da zan yi da garkata: Zan cire shingen, zan mayar da ita makiyaya, zan rushe garunta, za a kuma tattaketa ƙasa6Zan watsar da ita, ba zan yi mata noma ko kaftu ba. A maimakon haka ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su tsiro a cikin ta. Zan kuma umarci giza-gizai kada su yi ruwa a kanta.7Domin garkar inabin Yahweh mai runduna ita ce gidan Isra'ila, mutanen Yahuda kuma dashensa ne da ya ke jin daɗi; ya jiraci adalci, a maimakon haka sai kisa; a maimakon adalci kuma, sai ihun neman taimako.8Kaiton su masu yawo gida gida, waɗanda ke haɗa wurare daga wannan wuri zuwa wancan wuri, har sai ba ɗakunan da suka ragu sai kai kaɗai za a bari a cikin ƙasar!9Yahweh mai runduna ya faɗa mani, gidaje da yawa za su zama kufai, har ma da manyan gidajen nan masu ban sha'awa, ba mazauna.10Domin kadada goma ta garkar inabi za ta bada garwa ɗaya ne kacal, sannan mudun iri zai bada ɗangongoni ne kawai.11Kaiton masu tashi da asuba domin neman ƙaƙƙarfan ruwan inabi, waɗanda ba su kwantawa da wuri har sai ruwan inabi ya bugar da su.12Suna shagali da sarewa da garaya da tambari da algaita da ruwan inabi, amma ba su fahimci aikin Yahweh ba Ba su kuma yi la'akari da aikin hannuwansa ba.13Saboda haka mutanena suka tafi bautar talala saboda rashin fahimta; Shugabaninsu masu daraja suka zauna a cikin yunwa, talakawansu kuma ba su da wani abin sha.14Domin haka Lahira ta maida marmarinta babba ta kuma buɗe bakinta sosai; da masanansu da mutanensu da shugabanninsu da masu duba na cikinsu da kuma waɗanda ke murna a cikin su, sun ɗunguma Lahira.15Za a tilastawa mutum ya sunkuya ƙasa, Za'a ƙasƙantar da mutum; idanun masu taƙama za su wulaƙanta.16Yahweh mai runduna zai ɗaukaka cikin adalcinsa, Allah Mai Tsarki nan zai nuna kansa da tsarki cikin adalcinsa.17Bayan wannan sai tumakai su yi kiwo kamar a makiyayarsu, a kuma cikin kangaye, 'yan raguna za su yi kiwo kamar bãƙi.18Kaiton masu cire laifofinsu da sarƙoƙi marasa amfani da masu birgima cikin zunubi kamar an ɗaure su da igiya.19Kaiton masu cewa, "Bari Allah ya yi sauri, bari ya hanzarta ya yi aikinsa, domin mu ga ya faru; kuma bari shirye-shiryen Mai Tsarki na Isra'ila su zo, domin mu sansu."20Kaiton masu kiran mugunta nagarta, nagarta kuma mugunta; waɗanda suka mai da duhu haske, haske kuma duhu; suka kuma mai da ɗaci zaƙi, zaki kuma ɗaci!21Kaiton masu hikima a fuskarsu, masu daraja kuma a cikin fahimtarsu!22Kaiton shahararrun shan ruwan inabi, da waɗanda s ka shahara a wajen gauraya ruwan inabi mai ƙarfi;23Waɗanda suka ƙyale mugu saboda a biya su, suka kuma zalunci marar laifi a kan hakinsa!24Saboda haka kamar yadda harshen wuta ke lanƙwame kututture, kamar kuma yadda busasshiyar ciyawa ke shiga harshen wuta haka saiwarsu za ta mutu, kyansu kuma ya gushe kamar ƙura. Wannan zai faru saboda sun ƙi shari'un Yahweh mai runduna, saboda kuma sun rena maganar Mai Tsarki na Isra'ila.25Saboda haka fushin Yahweh yana kan mutanensa. Ya miƙa hannusa gãba da su ya kuma hore su. tsaunuka sun razana, gawawwakinsu sun zama kamar sharar da a ka zubar a bakin hanyonyi. A cikin duk waɗannan abubuwa fushinsa bai sauka ba; a maimakon haka hannunsa har yanzu yana miƙe.26Zai ɗaga alama ta tuta don al'ummai masu nisa zai kuma yi fĩto ga waɗanda ke ƙarshen duniya. Ku duba, za su zo a guje a kan lokaci kuma.27Ba yagewa ko tuntuɓe a cikinsu; babu masu rurrumi ko bacci. Ba su kuma kwance ɗammararsu ba, ko kuma shimfiɗar takalmansu da ta yage.28Kibawunsu na da tsini kuma dukkan bakkunansu a tanƙware; kofatan dawakansu kuma kamar curin dutse, gargaren karusarsu kuma kamar hadari ya ke.29Gurnaninsu kuma kamar na zãki; za su yi ruri kamar matasan zãki. Za su yi ruri su fizge abin da suka farauto su kuma ja shi su tafi, ba kuma wanda zai kuɓutar da su.30A wannan ranar za su yi ruri kamar yadda tekuna ke ruri. In wani ya dudduba ƙasar zai ga duhu da shan wuya; ko ma da haske za a mai da shi duhu ta wurin giza-gizai.
Ishaya ya faɗi wani misali game da wani manomi da gonar inabinsa. Manomin yana wakiltar Allah kuma gonar inabin tana wakiltar mutanen Yahuda, masarautar kudu ta Isra'ilawa.
"abokina ƙaunataccena"
"Ya shirya ƙasa." Wannan jumla yana nufin amfani da kayan aiki don haƙa cikin ƙasa don shirya shi don shuka.
"Ya yi wani dogon gini a tsakiyar gonar inabin don ya kula da shi." Wani zai tsaya a saman hasumiyar don kallon gonar inabin kuma ya tabbatar da cewa babu dabbobi ko mutane da suka shiga ciki. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari.
Waɗannan maganganun gaba ɗaya suna magana ne ga duk mutanen da ke zaune a Yerusalem da Yahuda, don haka ana iya fassara su da sunaye da yawa. AT: "duk ku mazaunan Yerusalem da Yahuda"
Tunanin sararin raba abubuwa biyu galibi ana amfani dashi don bayyana ra'ayin zaɓar ɗaya ko ɗaya daga waɗannan abubuwan. AT: "yanke shawarar wanda ya aikata daidai, Ni ko gonar inabi na"
Maigidan yayi amfani da wannan tambayar don yin bayani game da gonar inabinsa. Waɗannan tambayoyin za a iya fassara su azaman sanarwa. AT: "Na yi duk abin da zan iya yi wa gonar inabin na!"
"dauke iyakar daji." Gandun daji jere ne na bishiyoyi ko ƙananan bishiyoyi waɗanda aka dasa domin kiyaye lambun ko wani yanki. Anan "shinge" mai yiwuwa yana nufin bishiyoyin ƙaya wanda aka dasa don ya girma akan bangon dutse da ke kewaye da gonar inabin.
"Zan bar dabbobi su je can su ci abinci." Wannan wurin ciyawa ne inda dabbobi ke cin abinci.
"Zan hallaka shi"
Ishaya ya bayyana kwatancin gonar inabin.
Ishaya ya faɗi cewa gonar inabin a cikin misalin tana wakiltar mutanen Isra'ila. AT: "Ga gonar inabin Yahweh Mai Runduna tana wakiltar gidan Isra'ila" ko "Mutanen Isra'ila suna kama da gonar inabin Yahweh, Ubangijin rundunonin mala'iku"
Ana yin magana a kan mutanen Yahuda kamar kurangar inabi da Yahweh ya dasa. Ana iya bayyana wannan azaman misali. AT: "Mutanen Yahuza kamar itacen inabi ne wanda Yahweh ya dasa don yardar Yahweh"
Ana iya canza wannan ta yadda za a iya nuna kalmar nan ta "adalci" ta hanyar kalmar aikatau "yi abin da ke daidai." Cikakken sunan "kisan" ana iya bayyana shi da "kashe juna." AT: "Yahweh ya jira mutane su yi adalci, amma maimakon haka sai suka kashe juna"
Ishaya ya ba da sanarwar hukuncin Allah.
"ga waɗanda suka ƙwace gidaje da yawa, kuma waɗanda suka ƙara karɓar filaye." Ishaya ya ɗauka cewa masu sauraronsa sun san cewa doka ta hana wani karɓar ƙasa daga dangi har abada. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari.
"ba tare da kowa yana rayuwa a ciki ba"
"Lita 220 na iri zai samar da lita 22 ne kawai." "Homer" ɗaya yayi dai-dai da mudu goma.
Wannan yana nufin mutanen da basa yin komai tsawon rana amma suna shan giya.
A nan ana maganar ikon ruwan inabi don sa masu shan sa su bugu kamar yana sa su wuta, ma’ana, yana cinna musu wuta. AT: "har sai sun bugu da giya"
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda za'a nuna kalmar "aikatawa" azaman kalmar "aikata" ko "halitta." AT: "abin da ya aikata" ko "abin da ya halitta"
Waɗannan ayoyin suna faɗar abin da zai faru da mutane saboda sun yi wa Allah rashin biyayya.
A cikin annabci abubuwan da zasu faru a nan gaba galibi ana magana dasu kamar sun riga sun faru. Wannan ya nanata cewa lalle annabcin zai cika. AT: "makiya daga wasu ƙasashe za su ɗauki mutanena, Isra'ila, a matsayin bayi"
Abin da ba su fahimta ba ana iya bayyana shi a sarari. AT: "saboda ba su fahimci Yahweh ko shari'arsa ba"
Wannan jumlar tana magana ne game da Lahira, wanda yake nan kabari, ga dabba da ke shirin cin sauran dabbobi. Yana nuna cewa mutane da yawa, mutane da yawa zasu mutu. AT: "Mutuwa kamar dabba ce mai yunwa wacce ta buɗe bakinta don cin mutane da yawa"
Annabin yayi magana game da nan gaba kamar yana faruwa yanzu. AT: "Yawancin mutanen Isra'ila, manyan mutanensu da talakawa, shugabanninsu da waɗanda ke jin daɗin bukukuwa na daji, za su shiga Lahira"
Abubuwa na gaba ana maganarsu kamar sun riga sun faru.
Kallon ƙasa wani lokaci alama ce ta jin kunya. Duba yadda kuka fassara irin waɗannan kalmomin a cikin Ishaya 2:11. AT: "idanun mutane masu alfahari za su ƙasƙantar da kai saboda kunya" ko "mutanen da suka yi alfahari yanzu sun ji kunya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane za su yabi Yahweh mai runduna saboda shi mai adalci ne"
Yahweh zai halakar da birnin Yerusalem, wanda ake kira "gonar inabi" a cikin Ishaya 5: 1. Zai zama da amfani ga komai sai dai tumaki su ci ciyawa a wurin.
Waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya dai-dai. Suna magana ne game da mutanen da suka ci gaba da yin zunubi da gangan kamar dai suna yin amfani da dukkan ƙarfinsu don jan keken da ke da nauyi. Allah zai hukunta su saboda zunubansu. AT: "Kaiton waɗanda suka yi aiki tuƙuru don yin zunubi kamar mutumin da ke jan amalanke da igiya"
Ana magana game da shirin Allah kamar abubuwa ne waɗanda zasu iya zuwa da kansu. AT: "bari Allah Mai Tsarki na Isra'ila ya cika shirinsa"
Waɗanda suke yin waɗannan abubuwa daidai suke da waɗanda "suke kiran mugunta da mai kyau, da kuma mai kyau mara kyau." Waɗannan abubuwan suna adawa ne kuma mutane sun san bambanci tsakanin su, amma wasu mutane suna yin ƙarya kuma suna faɗin cewa abubuwa marasa kyau suna da kyau. AT: "Suna kama da mutanen da ke kiran duhu haske da haske duhu. Suna kama da mutanen da ke kiran abubuwa masu ɗaci mai daɗi da abubuwa masu daɗi masu ɗaci"
A nan sunan kalmar "idanu" yana nufin tunaninsu. AT: "ga waɗanda suka ɗauka kansu masu hikima ne"
"suna tunanin sun fahimci komai"
Wannan nassi yana magana ne game da lalatattun alkalai a kotunan shari'a.
"kada ku yiwa mutane marasa adalci adalci"
Waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya dai-dai. Allah zai azabtar da mutanen da aka bayyana a cikin Ishaya 5: 18-23. AT: "kamar yadda wuta ke cin ciyawa da ciyawa"
Ishaya yayi magana akan waɗannan mutane kamar suna shuka mai mutuwa. AT: "za su mutu kamar shukar da tushenta ya ruɓe kuma furanninta ya bushe kuma iska ta busa shi"
Ishaya yayi magana game da fushin Yahweh kamar wuta ce. AT: "Yahweh yana da fushi ƙwarai"
Anan “hannu” yana nufin ikon Allah da ikonsa. AT: "ya nuna ikonsa akansu"
Gawarwakin an bar su kwance a tituna kamar datti. Wannan yana nuna cewa da yawa zasu mutu amma babu wanda zai kasance can ya binne su. Hakanan za'a iya fassara kalmar "shara" a matsayin "ƙi" ko "taki."
Ishaya ya faɗi abu ɗaya ta hanyoyi biyu daban-daban. An yi magana game da Allah yana sa sojojin al'umman da suke nesa da Yahuda su zo su kawo hari kamar ana so ya ɗaga tuta da bushewa don kiran su zuwa Yahuda. AT: "Zai kira sojojin ƙasashen da suke nesa da Yahuda kuma ka ce musu su zo "
Ishaya ya ci gaba da bayanin sojojin da za su kai wa Yahuda hari. Ya bayyana ta kamar ta riga ta kasance
Ishaya ya kwatanta maƙiyin da ke kashe mutanen Yahuza da zaki mai kashe dabba mai rauni. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) zakuna suna yin sauti ba kamar ruri ba kafin su buga, ko kuma 2) marubuci yana amfani da kalmomi biyu don ma'ana iri ɗaya.
Anan duhu yana wakiltar wahala da bala'i. Ana iya bayyana wannan kwatancin ta hanyar aiki. AT: "gizagizai masu duhu za su toshe hasken rana gaba ɗaya"
1A cikin shekarar da sarki Uziya ya mutu, na ga Ubangiji zaune a kan kursiyi; yana da tsayi da kuma martaba, gezar tufarsa kuma ta cika haikalin.2A sama da shi kuma da serafim; kowannen su yana da fuka-fukai shida; kowannen su yana rufe fuska da guda biyu, ya kuma rufe ƙafafu da guda biyu, yana kuma shawagi da guda biyu.3Suna kiran juna suna cewa, "Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki," shi ne Yahweh mai runduna! Dukkan duniya ta cika da ɗaukakarsa."4Harsashen ginin ƙofofinsa sun girgiza a lokacin da suka tada murya, sai kuma hayaƙi ya cika gidan.5Sa'an nan na ce "kaitona! Gama na hallaka domin ni mutum ne dake da leɓuna marasa tsarki, ina kuma rayuwa a cikin mutane marasa tsarkin leɓuna, saboda idanuna sun ga Sarki, Yahweh, Yahweh mai runduna!"6Daga nan sai ɗaya daga cikin serafim ɗin yawo shawagi wurina; yana da garwashi jawur a hannunsa, wanda ya ɗauko daga bagadi.7Sai ya taɓa bakina da shi ya kuma ce, "Duba wannan ya taɓa leɓunanka; an kawar da laifofinka, an kuma gafarta zunubanka."8Na ji muryar Ubangiji tana cewa, "Wa zan aika; wa kuma zai tafi dominmu?" Daga nan sai na ce, "Ga ni; ka aike ni."9Ya ce ka je ka faɗawa mutanen nan, za ku ji amma ba za ku gane ba; za ku gani amma ba za ku sani ba.'10Mai da zuciyarsu ta zama marar tunani, kunnuwansu kuma su kurmance, idanunsu kuma su makance. A maimakon haka za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su kuma fahimta da zuciyarsu, kuma daga nan su juyo su kuma warke."11Sai na ce Ubangiji har tsawon wanne lokaci? '"Ya amsa "Har sai birane sun zama kangaye ba mazauna a ciki, gidaje kuma sun zama ba mutane, ƙasar kuma ta zama yasasshiya,12Har sai Yahweh ya kora mutanen waje, kaɗaicin ƙasar kuma ya haɓaka.13Koda kashi ɗaya cikin goma na mutanen suka ragu a cikinsa, duk da haka za a ƙara hallaka shi; zai zama kamar ranar da aka datse itacen rimi wanda gungumensa ya ragu, iri mai tsarki na cikin kututture."
Kalmomin "maɗaukaki" da "ɗaukaka" suna nanata cewa kursiyin ya kasance mai girma sosai kuma ya fi kowane abu kewaye da shi. Tsayin kursiyin yana wakiltar yadda Ubangiji yake da girma.
"cika gidan sarki." Kalmar da aka yi amfani da ita don haikalin a nan galibi ana amfani da ita don ma'anar gidan sarakuna.
Kalmar "serafim" jam'i ne na seraf. Wannan yana nufin Ubangiji ya zauna akan kursiyin kuma seraphim suna tsaye ko tashi sama kusa da Ubangiji suna shirye suyi masa hidima.
Kalmomin "fuka-fukai" da "seraph" an fahimta. AT: "da kowane fukafukai kowane seraph ya rufe fuskarsa, kuma da fikafikansa biyu ya rufe ƙafafunsa, kuma ya tashi da fuka-fukai biyu"
"Serafim suka kira juna suna cewa" ko "Halittu masu fuka-fukai sun yiwa juna da'awa"
Maimaita kalmar "tsarki" sau uku yana nuna cewa Allah mai tsarki ne gaba ɗaya. AT: "Yahweh mai runduna mai tsarki ne gaba da komai" ko "Yahweh Mai runduna cikakke ne mai tsarki"
Wannan yana magana ne game da duniya kamar dai kwantena ne kuma ɗaukaka sune abubuwan da ke cikin akwatin. AT: "Duk abin da ke duniya tabbaci ne na ɗaukakar Allah"
"Lokacin da serafim suka yi kira, sai sautinsu ya girgiza ƙofofin da tushe"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "hayaki ya cika haikalin" ko "hayaki ya cika fadar"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ina cikin babbar matsala! Abubuwa masu ban tsoro za su same ni"
Wadannan kalmomin guda biyu suna faɗin abu ɗaya. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya ɗauke zunubanku kuma ya gafarta zunubanku"
Anan “murya” tana wakiltar Ubangiji da kansa. AT: "Ubangiji ya ce"
An nuna cewa Yahweh zai aiko wani ya yi magana da saƙon sa ga Isra'ilawa. AT: "Wanene zan aika ya zama manzo ga mutanena"
Da alama "mu" yana nufin Yahweh da membobin majalisarsa na sama wanda yake magana da su.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) abubuwan da ake aikatawa "ba su fahimta" kuma "ba su fahimta" suna bayyana abin da Allah ke haifar da shi. AT: "Za ku saurara, amma Yahweh ba zai bari ku fahimta ba; za ku duba da kyau, amma Yahweh ba zai baku damar fahimta ba" ko 2) maƙasudin "Ku saurara" ku "ga" bayyana ra'ayin "idan." AT: "Ko da kun saurara ba za ku fahimta ba; koda kuwa kun lura da kyau, ba za ku fahimta ba"
Anan “zuciya” tana wakiltar tunanin mutum. Ana magana da mutumin da ba ya tunani sosai kuma ya kasa fahimta da kuma damuwa da abin da ke faruwa kamar zuciyarsa ba ta da hankali. AT: "Ku sa waɗannan mutane su kasa fahimta" ko "Sanya tunanin waɗannan mutane ya zama mara kyau"
"sanya shi yadda ba za su ji ba, kuma sanya shi yadda ba za su iya gani ba." Ishaya yana sa mutane su fahimci saƙon Yahweh ko abin da yake yi ana magana ne kamar dai Ishaya yana sanya su kurma ne kuma makafi.
Mutanen da suke iya fahimtar saƙon Yahweh da abin da yake yi ana maganarsu kamar mutane suna iya gani da ji a zahiri.
"Har sai dukkan biranen da gidaje sun lalace kuma babu wanda ke zaune a wurin"
Anan "fadawa" wani karin magana ne da ke nufin zama mummunan abu. AT: "ƙasar ta zama kango kufai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "rundunoni za su sake lalata ƙasar Isra'ila"
Wannan magana yana nufin cewa har ma bayan da Yahweh ya hallaka Isra’ila, zai ware wasu mutane daga cikin Isra’ilawa don su bauta masa.
1A kwanakin Ahaz ɗan Yotam ɗan Uziya, sarkin Yahuda, Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya da sarkin Isra'ila, suka je Yerusalem domin su yaƙe ta, amma ba su iya yin nasara da ita ba.2Sai aka sanar da gidan Dauda cewa Aram ya haɗa kai da Ifraim. Sai ya tsorata, haka ma zuciyar mutanensa, kamar yadda itatuwan jeji ke kaɗawa a cikin iska.3Sai Yahweh yace da Ishaya, "Ka tafi tare da ɗanka Shiya-Yashub ku sadu da Ahaz a ƙarshen kwararon babban wurin da aka datse ruwa, a kan hanya zuwa Filin masu wanki da guga.4Ka ce da shi, 'Ka lura, ka tsaya a natse, kada ka ji tsoro ko ka razana saboda waɗannan 'yan guma-gumai na wuta, ta wurin zafin fushin Rezin da Aram, da Feka ɗan Remaliya.5Aram, Ifraim da ɗan Remaliya sun ƙulla mugun abu găba da kai; sun ce,6"Bari mu kai wa Yahuda hari mu firgita ta, mu kuma fasa cikinta mu naɗa sarkinmu a can, wato ɗan Tabil."7Ubangiji Yahweh yace, "Ba zai faru ba; ba zai faru ba,8saboda shugabar Aram ita ce Damaskus, shugabar Damaskus kuma ita ce Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar, za'a watsa Ifraim kuma ba za su zama al'umma ɗaya ba9Shugabar Ifraim ita ce Samariya, shugaban Samariya kuma shi ne ɗan Remaliya. Idan ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya ba, tabbas ba za ku zama da kariya ba.""'10Sai Ubangiji ya sake yin magana da Ahaz,11"Ka roƙi alama daga Yahweh Allahnka; ka yi roƙonta ko a cikin zurfafa ko a can sama."12Amma Ahaz yace "ba zan yi tambaya, ko kuma in gwada Yahweh ba."13Domin haka Ishaya ya amsa, "Ku saurara, gidan Dauda. Ya ku mutane ashe bai isheku ba ku gwada haƙurin jama'a? Dole ne kuma ku gwada haƙurin Allahna?14Saboda haka Ubangiji da kansa zai ba ku alama, duba budurwa za ta yi juna biyu za ta haifi ɗa, za a kira sunansa Imanuwel.15Zai ci fãra da ruwan zuma a lokacin da ya ƙi mugunta ya kuma zaɓi nagarta.16Gama kafin yaron ya san ƙin mugunta da zaɓar nagarta, ƙasar sarakunan nan guda biyu da kuka ji tsoronsu za ta zama kufai.17Yahweh zai sauko maku da wata rana a kan mutanenku da gidan mahaifanku ranar da ba a taɓa ganin ta ba tun da Ifraim ya bar Yahuda - zai aiko maku da sarkin Asiriya."18A wannan lokacin Yahweh zai yi kira na tashi daga ƙoramu masu nisa na Masar, kuma da na zuma daga ƙasar Asiriya.19Duk za su zo su zauna a dukkan kwazazzabai, a cikin kogonnin duwatsu, a kan dukkan ƙayayuwa, da a kan dukkan makiyaya.20A wannan lokacin Ubangiji zai yi aski da rezar da aka yi haya daga hayin Kogin Yuferitis - sarkin Asiriya - da kai da gashin ƙafafu; za a kuma share gemu.21A wannan rana mutum zai yi kiwon 'yar karsana da tumaki guda biyu,22Kuma saboda yalwar madarar da za su bayar, zai ci cuku, ga duk waɗanda suka ragu a ƙasar za su ci cuku da ruwan zuma.23A wannan lokacin, a inda a kwai dubu na inabi da ya kai azurfa dubu, a wurin ba za a ga komai ba sai sarƙarƙiya da ƙayayuwa.24Mutane za su fita farauta da bãka, saboda dukkan ƙasar za ta cika da ƙaya da sarƙaƙiya.25Za su tsaya nesa da dukkan tuddan da aka nome da fartanya, domin tsoron sarƙaƙiya da ƙayayuwa; amma zai zama wurin da dabbobi da tumaki za su yi kiwo.
"Lokacin da Ahaz ... yake sarkin Yahuda" Wannan shi ne lokacin da abubuwan suka faru.
Waɗannan sunayen maza ne.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "gidan Dauda ya ji rahoton" ko "wani ya ba da rahoto ga gidan Dauda"
Girgizar da zukatansu ke yi da wannan labarin an kwatanta su da yadda bishiyoyi ke girgiza lokacin da iska ta busa su. AT: "Ahaz da mutanensa sun firgita ƙwarai"
Masu fassarawa na iya ƙara ƙarin alamar ƙwallon kafa da ke cewa, "Sunan Shiya Yashub na nufin "sauran za su dawo." Ma'anar na iya ba Ahaz fata.
"inda ruwan yake malala daga cikin ramin kuma ya shiga tafkin na sama"
Kalmomin "tsoro" da "tsoratarwa" ma'anarsu ɗaya kuma ana iya fassara su azaman kalma ɗaya. AT: "tsoro"
Kalmomin "Aram" da "Ifraim" suna nufin sarakunan waɗannan ƙasashe. Hakanan, "Ifraim" tana wakiltar masarautar arewacin Isra'ila. AT: "Rezin Sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, sarkin Isra'ila"
Anan "ku" ɗaya ne kuma yana nufin Ahaz.
Anan "kai" metonym ne don mafi mahimmanci. An nuna cewa Rezin mutum ne kawai, don haka ba zai iya dakatar da shirin Yahweh ba. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Sarkin Damaskus shine Rezin, wanda ke kawai mutum"
Anan "Ifraim" yana nufin duk masarautar arewacin Isra'ila. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "sojoji za su hallaka Ifraim, kuma ba za a sake samun jama'ar Isra'ila ba"
Wannan yana nufin Feka shine sarkin Samariya da Isra'ila dukka. AT: "Sarkin Samariya shi ne Feka, wanda ke da rauni"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Idan kuka ci gaba da yin imani da ni, tabbas za ku kasance cikin aminci"
Yahweh yana amfani da kalmar "zurfin" da "tsawo" yana nufin Ahaz zai iya tambayar shi komai.
Kalmar "gida" na nuna ga dangin da ke zaune a gidan. AT: "Sarki Ahaz, ku da mashawartan ku"
Waɗannan tambayoyin sun nanata cewa sarki ya yi zunubi ƙwarai. AT: "Kuna gwada haƙurin mutane! Yanzu ma kun gwada haƙurin Allahna!"
Wasu fassarorin na da da kuma wasu juzu'an na fassara, "budurwa zata yi ciki, yayin da wasu ke fassara" budurwa zata yi ciki. "
Masu fassara na iya ƙara alamar hasumiya da ke cewa: "Sunan Imanuwel yana nufin "Allah tare da mu."
Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) "A lokacin da yaro ya isa cin naman alade da zuma, zai iya ƙin abin da ke mugu kuma ya zaɓi abin da ke mai kyau." Wannan ya nanata cewa yaro zai kasance ƙarami sosai lokacin da ya san zaɓar abin da yake daidai maimakon kuskure ko 2) "A lokacin da yaro ya isa ya ƙi mugunta kuma ya zaɓi abin da ke mai kyau, zai kasance yana cin naman alade da zuma." Mutanen Yahuda sun ɗauki yaro da alhakin aikata abin da yake daidai lokacin da yake ɗan shekara goma sha biyu. Wannan ya nanata cewa a cikin shekaru goma sha biyu mutane za su iya cin ɗanɗano da zuma mai yawa saboda yawancin mutanen Isra'ila za a kashe su ko a kwashe su.
Ishaya ya ci gaba da bayanin alamar cewa Allah zai ba gidan Dauda.
Anan "mugayen" da "masu kyau" suna nufin mugunta da kyawawan abubuwa gaba ɗaya. AT: "ƙi aikata mugunta kuma zaɓi zaɓi don aikata ayyukan ƙwarai"
kafin yaro ya san ƙin mugunta kuma ya zaɓi mai kyau
Anan ana magana akan sojojin Masar da Asiriya kamar kwari ne da zasu mamaye ƙasar Isra’ila. Ana iya bayyana wannan azaman misali. AT: "don sojojin Masar da Asiriya, kuma sojojinsu za su kasance ko'ina kamar ƙudaje da ƙudan zuma"
Ishaya ya ci gaba da bayanin lokacin da sojojin Asiriya za su farma Isra’ila.
Kalmar "rezar" kwatanci ne na sarkin Asiriya da rundunarsa, kuma Yahweh yana magana akan sarki kamar sarki ne mutum wanda zai yi aikin Yahweh sannan ya karɓi kuɗi daga wurin Yahweh. AT: "Ubangiji zai kirawo sarkin Asiriya daga hayin Kogin Yuferitis don ya yi masa aiki ya aske ku"
"reza shima zai share." Idan yarenku yana buƙatar mutum ya zama batun "zai ... shara," kuna iya cewa, "Ubangiji ma zai yi shara."
Kalmomin "sarƙaƙƙu" da "ƙaya" duk suna nufin tsire-tsire marasa amfani, ƙaya. Ba lallai ba ne a fassara kalmomin dukka. AT: "bishiyoyin ƙaya" ko "ƙaya mai ƙaya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane za su nisanci tsaunuka inda suka taɓa shirya ƙasa don shuka amfanin gona"
1Yahweh yace mani, "Ka ɗauki babban allo ka yi rubutu a kansa, 'Maha-Shalal-Hash-Baz.'2Zan kira amintattun shaidu su tabbatar mani, Yuriya Firist, da Zakariya ɗan Yebirekiya."3Na je wurin annabiya, ta kuwa yi juna biyu ta haifi ɗa. Sai Yahweh yace mani, "Ka kira sunansa 'Maha-Shalal-Hash-Baz.'4Gama kafin yaron ya san yin kuka har ya furta, 'Babana da Mamata,' sarkin Asiriya zai kwashe dukiyar Damaskus da ganimar Samariya."5Sai Yahweh ya sake yi mani magana,6"Saboda waɗannan mutanen sunƙi tausassun ruwayen Shilowa, amma suna murna kan Rezin da ɗan Remaliya,7don haka Ubangiji ya kusa kawo ruwayen Kogi a kansu, masu ƙarfi da yawa, sarkin Asiriya da dukkan ɗaukakarsa. Za ya hau kan dukkan magudanansa ya yi ambaliya kan iyakokinsa.8Rafin zai shafe har zuwa cikin Yahuda, ambaliyar zata ratsa, har sai ta kai wuyanka. Miƙawar fikafikansa zai cika iya faɗin ƙasarka, Imanuwel."9Ku mutanen za a daddatsa ku gunduwa-gunduwa. Ku saurara, dukkan ku manisantan ƙasashe: ku yi ɗammara domin yaƙi za a kuwa daddatse ku, ku yi shiri za a kuwa gutsuttsuraku.10Ku yi shiri, amma bãza ku iya aiwatarwa ba; ku ba da umarni, ba za a kiyaye ba, gama Allah yana tare da mu.11Yahweh ya yi magana da ni, da hannunsa mai ƙarfi a kaina, ya dokace ni kada in yi tafiya cikin tafarkin mutanen nan.12Kada ku kira maƙida akan kowanne abin da mutanen nan suke kira maƙida, kada ku ji tsoron abin da suke tsoro, kada ku firgita kuma.13Amma Yahweh mai runduna za ku girmama a matsayin maitsarki; shi ne wanda dole za ku ji tsoro, shi ne dole zai zama abin razanar ku.14Zai zama wuri maitsarki; amma zai zama dutse abin bugu da pã abin sa tuntuɓe ga dukan gidajen Isra'ila, zai zama tarko da azargiya ga mutanen Yerusalem.15Mutane da yawa za su yi tuntuɓe a kansa su faɗi su karye, su zama azargiya kuma su kamu.16Ka ɗaure shaida ta, ka hatimce umarni na musamman, ka kuma bada su ga alma'jiraina.17Zan jira Yahweh, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yakubu; Zan jira shi.18Duba, Ni da 'ya'yan da Yahweh ya bani domin alamu ne da al'ajibai cikin Isra'ila daga Yahweh mai runduna, wanda ya ke zaune akan Tsaunin Sihiyona.19Za su ce maku, "Ku tuntuɓi mãsu duba da bokaye" waɗanda suke kashe murya suna surkulle. Shin ko mutane ba za su tuntuɓi Allahnsu ba? za su tuntuɓi matattu a madadin masu rai?20Ga shari'a da kuma shaida! idan ba su faɗi waɗannan abubuwan ba, saboda ba bu hasken wayewar gari a garesu.21Za su ratsa ta cikin ƙasa da babbar damuwa da yunwa. Idan suna jin yunwa, za su yi fushi su la'anta sarkinsu da Allahnsu, yayin da suka ɗaga fuskokinsu sama.22Za su du bi duniya kuma za su ga wahala, duhu, da azabtarwa. Za a koresu zuwa cikin ƙasar duhu.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Yahweh yana magana: "Zan kira mutane masu gaskiya su zama shaidu" ko 2) Ishaya yana magana: "Na kira mutane masu gaskiya su zama shaidu" ko 3) Yahweh yana umurtar Ishaya: "Kira mutanen kirki ya zama shaidu."
Ana iya bayyana a sarari cewa Ishaya ya auri annabiya. AT: "Na kwana da matata, annabiya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sarkin Asiriya zai kwashe dukiyar Damaskus da ta Samariya"
Kalmomin "ruwa mai laushi" magana ne na dokar Ubangiji. AT: "Saboda mutanen nan sun ƙi dokar Yahweh, wanda yake kama da ruwan Shiloah mai taushi"
Cikakkiyar ma’anar ana iya bayyana ta a sarari. AT: "yana farin cikin cewa sojojin Asiriya sun ci Rezin, sarkin Aram, da Feka, ɗan Remaliya, sarkin Isra'ila"
Kogin yana wakiltar sojojin Asiriya. AT: "rundunar daga Asiriya, wacce ke da ƙarfi kamar babban kogi"
Rundunar Asiriya tana kamar ambaliyar ruwa. AT: "andarin sojoji za su zo kamar kogi yana hawa zuwa wuyan ku"
Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) kamar yadda "Kogin" a cikin wani magana ya tashi, '' fikafikansa'' yana malalowa ya rufe abin da ya kasance busasshiyar ƙasa ko kuma 2) Ishaya ya canza magana kuma yanzu yana magana game da Yahweh a matsayin tsuntsu wanda ke kare ƙasar, "Amma fukafukansa da suka miƙe zasu rufe."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan kakkarya rundunoninku gunduwa-gunduwa"
Ishaya yayi magana kamar mutane a wasu ƙasashe zasu ji shi. AT: "Ku saurara, ku duka mutanen da ke nesa"
Wannan ainihin abu ɗaya ne, an bayyana sau biyu don girmamawa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kuna iya shirya kanku don yaƙi, amma zan ci ku"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kuna iya shirin kai wa Yahuza hari, amma ba za ku yi nasara ba"
Anan “hannunsa mai ƙarfi a kaina” salon magana ne wanda ke nufin ikon Yahweh. AT: "Yahweh ya yi magana da ni ta hanya mai ƙarfi"
Wannan magana ce ta kai tsaye wacce ta ƙare da 8:17. AT: "ya gargaɗe ni kuma ya ce, 'Kada ku yi irin wannan mutanen.'"
Idan kun fassara wannan azaman magana kai tsaye, zaku iya fassara shi tare da Yahweh yana magana da mutum na farko: "Amma zaku ɗauke ni, ya Yahweh Mai Runduna, a matsayin mai tsarki. Kuma za ku ji tsoro kuma ku ji tsoro na"
Kalmar nan "wuri maitsarki" wani magana ne na Yahweh yana kiyaye mutanensa lafiya kuma yana kiyaye su. AT: "Zai kiyaye su idan sun je wurinsa"
Kalmomin "tarko" da "tarko" suna nufin kusan abu ɗaya ne kuma suna jaddada cewa lokacin da Yahweh ya yanke hukuncin hukunta mutanen Yerusalem ba za su iya tserewa ba. AT: "zai yiwa mazaunan Yerusalem tarko don haka ba za su tsere shi ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane da yawa za su yi tuntuɓe a kan dutsen, kuma idan sun faɗi ba za su tashi ba. Kuma mutane da yawa za su shiga cikin tarkon, kuma ba za su iya fita ba"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya dai-dai. AT: "Rufe rubutun nan da kyau tare da wannan saƙon da aka rubuta a kansa"
Anan "I" yana nufin Ishaya.
"Ni da 'ya'yan da Yahweh ya ba ni, alamu ne kamar na gargaɗi Isra'ilawa." 'Ya'yan su ne Shiya Yashub da Maher-Shalal-Hash-Baz, wadanda sunayensu sako ne ga mutanen Isra'ila. (Duba: Ishaya 7: 3 da Ishaya 8: 1)
Kalmar "su" tana nufin waɗanda ba su dogara ga Yahweh ba. Kalmar "ku" jam'i ne kuma tana nufin waɗanda suka dogara da Yahweh.
Waɗannan tambayoyin suna nuna cewa ya kamata mutane su nemi Allah maimakon wautar ƙoƙarin magana da mutanen da suka mutu. AT: "Amma mutane su nemi Yahweh ya shiryar da su. Kada su nemi amsoshi daga waɗanda suka mutu."
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Ku mai da hankali ga umarnin Allah da koyarwarsa" ko 2) "To ya zama dole ku tuna da koyarwa da shaidar da na bayar." (Ishaya 8:16).
"mummunan bakin ciki"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai kore su cikin duhu gaba ɗaya"
1Amma za a kawar da baƙin duhun daga wurin ta wadda take cikin azaba a dã. A kwanakin da ya ƙasƙantar da ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali, amma cikin kwanaki na ƙarshe zai ɗaukakata, ta hanyar teku, ƙetaren Yodan, Galili ta al'ummai.2Mutanen da suka yi tafiya cikin duhu sun ga babban haske; waɗanda suka zauna cikin ƙasa ta inuwar mutuwa, haske ya haskaka bisansu.3Ka riɓanya al'umma; ka ƙara farincikin su. Suna murna gaban ka kamar murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane suke murna sa'ad da suke raba ganima.4Gama karkiyar kayansa, katakon dake gicciye da kafaɗarsa, sandar mai azabta masa, ka rafke su kamar a ranar Midiyan.5Gama dukkan takalman mayaƙa cikin hayaniyar yaƙi da tufafi mirginannu cikin jini za a ƙone su, su zama abin rura wuta.6Gama a gare mu an haifi yaro, a gare mu an bada ɗa; mulki kuma zai kasance a kafaɗarsa; za a kira sunansa Al'ajibi Maishawara, Allah maigirma, Uba Madawwami, Sarkin Salama.7Ƙaruwar mulkinsa da salama bata da iyaka, ya yin da ya ke mulki kan kursiyin Dauda, da bisa mulkinsa, a kafa shi a kuma tabbatar dashi cikin gaskiya da adalci daga wannan lokaci har abada kuma. Himmar Yahweh Mairunduna zai yi wannan.8Sai Ubangiji ya aika da magana gãba da Yakubu, sai ta faɗo kan Isra'ila.9Dukkan mutane za su sani, har Ifraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana cikin girmankai da taurin zuciya,10"Tubala sun faɗi, amma za mu sake gini da sassaƙaƙƙun duwatsu; an sare durumi ƙasa, amma zamu sa itatuwan sidas amadadinsu."11Domin haka Yahweh zai tayar masa da Rezin, abokin gabarsa, zai harzuƙa maƙiyansa,12Suriyawa daga gabas, da kuma Filistiyawa daga yamma. Da baki buɗe za su cinye Isra'ila. A cikin waɗannan duka, fushinsa bai juya ba; maimakon haka, hannunsa har yanzu a miƙe ya ke.13Duk da haka mutane ba za su juya wajen shi wanda ya buge su ba, ba kuwa za su nemi Yahweh mai runduna ba.14Domin haka Yahweh zai datse ma Isra'ila kai da wutsiya, reshen dabino da gazarinsa, cikin rana ɗaya.15Shugaba da mutum maidaraja su ne kai; da annabi mai koyar da ƙarya shi ne wutsiya.16Waɗanda ke shugabantar jama'ar nan sun karkataddasu, waɗanda suke binsu kuma an haɗiye su.17Domin wannan Ubangiji ba za ya yi murna da majiya karfinsu ba ba kuma zai tausayawa marayunsu da gwaurayensu ba, domin kowannensu marasa allahntaka ne da masu aikata mugunta, kowanne baki kuma yana faɗin wauta. Cikin waɗannan duka fushinsa ba zai juya ba; maimakon haka, hannunsa har yanzu a miƙe ya ke.18Mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin sarƙaƙƙiya da ƙayayuwa; tana ƙone ƙungurmin daji, wanda ke tashi cikin tuƙuƙin hayaƙi.19Ta wurin hasalar Yahweh mairunduna ƙasa ta ƙone, mutane kuma sun zama kamar abin rura wuta. Ba mutumin daya bar ɗan'uwansa.20Za su fizge abinci a hannun dama duk da haka za su ji yunwa, za su ci abinci a hannun hagu duk da haka ba za su ƙoshi ba. Kowanne zai ci naman dantsen hannunsa.21Manasse zai lanƙwame Ifraim, Ifraim kuma Manasse, tare kuma za su kaima Yahuda farmaki. Cikin waɗannan duka, fushinsa yana nan, maimakon haka, har yanzu hannunsa a miƙe ya ke.
Ishaya yayi magana akan mutanen da suka ɓace a ruhaniya kamar suna tafiya cikin cikakken duhu. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai cire duhu daga cikin wanda ke cikin wahala"
"Ƙasa" tana nufin mutanen da suke zaune a wani yanki. AT: "A da, Ubangiji ya ƙasƙantar da mazaunan Zebulun da Naftali"
Anan "shi" yana nufin Galili wanda yake wakiltar mutanen da suke zaune a wurin. AT: "amma nan gaba, Ubangiji zai girmama mutanen Galili na al'ummu, wanda ke kan hanyar tsakanin Bahar Teku da Kogin Yodan"
Anan “haske” yana wakiltar bege da kubutarwa.
Jumlar "inuwar mutuwa" karin magana ce wacce ke nufin cikakkiyar duhu. AT: "ƙasar da ke cikin duhu mafi duhu"
Ishaya ya ci gaba da bayanin lokacin da Allah zai ceci Isra'ilawa. Kodayake waɗannan abubuwan zasu faru a nan gaba (Ishaya 9: 1), Ishaya ya bayyana su kamar dai sun riga sun faru. Wannan yana nanata cewa tabbas zasu faru.
Kalmar "ku" tana nufin Yahweh. Kalmar "su" tana nufin mutanen Isra'ila ne, amma Ishaya ya haɗa kansa da wani ɓangare na Isra'ila. AT: "Ya Ubangiji, za ka ƙara yawan mutanenmu da farin cikinmu"
An bayyana farin cikin da Ubangiji zai ba Isra’ilawa kamar irin farin cikin da mutane suke yi sa’ad da suka kawo girbi ko kuma suka raba ganima mai tamani. AT: "Za su yi farin ciki a gabanku kamar yadda mutane suke murna yayin da suka tattara amfanin gonarsu ko lokacin da yaƙi ya ƙare kuma sojoji suka raba abin da suka ɗauka"
Katako ɓangare ne na karkiyar da ke wucewa a kafaɗun bijimin.
Ishaya yayi magana akan ikon da azzalumi ke da shi akan mutanen Yahuda kamar itacen itace da mutum yake amfani da shi don bugun shanu don haka za su yi aiki.
Kalmar "rana" karin magana ta wacce ke iya nufin abin da ke faruwa sama da kwana ɗaya kafin ya faru. AT: "kamar lokacin da kuka ci Midiyanawa"
Ana iya bayyana hakan ta hanyar fassara shi azaman sabon jumla. AT: "konewa. Za ku sanya takalman da tufafin su zama man wuta ga wutan"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Kalmar "mu" tana nufin mai magana da mai sauraro don haka ya hada duka. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Gama Yahweh zai bamu yaro"
Ana magana akan ikonsa na mulki kamar tufafi wanda alama ce ta ikonsa. AT: "zai sa alkyabbarsa ta sarauta a kafaɗarsa" ko "yana da ikon yin sarauta kamar sarki."
"Idan lokaci yayi zai mulke mutane da yawa kuma zai basu damar zama cikin lumana da kwanciyar hankali"
Ana iya fassara wannan azaman sabuwar jumla. AT: "mulkinsa. Zai kafa kuma ya kare masarautarsa, kuma zai yi abin da ya dace da adalci"
"Aika kalma" ma'ana tayi magana. AT: "Ubangiji yayi magana game da mutanen Isra'ila"
Abin da za su sani ana iya bayyane shi. AT: "Dukkan mutane za su sani Ubangiji ya hukunta su, har ma da waɗanda suke a Ifraim da Samariya"
Cikakkiyar ma’anar ana iya bayyana ta a sarari. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Za mu maye gurbin tubalin gama gari na biranenmu da dutse mai tsada, kuma za mu dasa manyan itatuwan al'ul inda manyan bishiyoyi suka tsiro" (Duba: da figsactivepassive)
Anan "Rezin" yana wakiltar kansa da sojojinsa. AT: "Saboda haka, Yahweh zai kawo wa Rezin da rundunarsa gāba da Isra'ilawa"
Jumlar "zuga" wani karin magana ne da ke nufin tunzura su su kai hari. AT: "Yahweh zai sa makiyan Isra'ila su kawo hari"
"Cinye" shine yadda dabbobin daji ke cin abincinsu. AT: "Kamar dabbar daji da ke cin abincinta, sojojin abokan gaba za su hallaka mutanen Isra'ila"
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 1:9.
Ishaya ya bayyana wannan kwatancin a cikin aya ta 15. “Kan,” ɓangaren dabbar da mutum zai so ya zama, shi ne “shugaba da mutum mai daraja,” kuma “jela,” ɓangaren datti na dabba, shi ne ” annabin da ke koyar da karya."
"Reshen dabino" yayi girma akan bishiyar kuma abin kwatance ne ga mutanen da suke da mahimmanci da mulkin wasu. “Iwa” yana girma a cikin ruwa mara ƙaranci kuma kwatanci ne na mutanen da ba su da talauci kuma ba su da muhimmanci kuma wasu ne ke mulkar su.
Ana maganar shugabannin da ke haifar da mutane ga rashin biyayya kamar yadda shugabannin suka jagorance su akan hanyar da ba ta dace ba. AT: "Shugabannin Isra'ila sun sa mutane sun yi wa Allah rashin biyayya"
Wannan kwatanci ne wanda za'a iya bayyana shi cikin sigar aiki. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) AT: "waɗanda suke jagoranta sun ruɗe" ko 2) AT: "Yahweh yana rusa waɗanda suke jagoranta"
Kalmar "bakin" tana nufin mutum. AT: "kowane mutum yana magana da maganganun wauta"
Ana magana game da mugayen ayyukan mutane kamar wuta ce mai hallakarwa. Wannan wutar tana kona koda sarƙaƙƙu da ƙayoyi, tsire-tsire waɗanda suke girma a wuraren da mutane ba sa rayuwa a ciki, da kuma "dazuzzuka na gandun daji" inda babu wanda ya taɓa rayuwa, domin ta riga ta lalata wuraren da mutane suke rayuwa.
Fassara "Yahweh Mai Runduna" kamar yadda yake a cikin Ishaya 1: 9. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kamar wuta mai cin ƙasar, tsananin fushin Ubangiji zai hallaka mutanen Isra'ila"
Don '' kiyaye 'wani na nufin ya cece su daga cutarwa. AT: "Babu wanda ya yi wani abu don taimaka wa ɗan'uwansa ya tsere"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) mutane za su ji yunwa har za su so su ci ko za su ci naman hannuwansu ko 2) kalmar "hannu" kwatanci ce ga maƙwabcin mutum.
"Duk da cewa duk waɗannan abubuwan sun faru, har yanzu yana cikin fushi, da kuma hannunsa." Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 5:25.
Ishaya yayi magana kamar Yahweh shine mutumin da zai doki wani mutum da dunƙulensa. Wannan kwatanci ne na Yahweh na azabtar da Isra'ila. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 5:25. AT: "har yanzu zai kasance a shirye don hukunta su"
1Kaitonsu waɗanda ke zartar da hukuncin zalunci suke rubuta umarnan rashin gaskiya.2Suna hana wa mabuƙata adalci, mutanena suna yi masu ƙwace su hana masu haƙƙinsu, gwamraye sun zama ganimarsu, sun maida marayu ganimarsu!3Me za kuyi a ranar hukunci lokacin da hallakarwa ke zuwa daga nesa? wurin wa za ku gudu domin neman taimako, kuma ina za ku bar dukiyarku?4Ba abin daya rage, za ku laɓe ƙarƙashin 'yan sarƙa, ko ku faɗi tsakanin kisassu. Cikin dukkan waɗannan abubuwa, fushinsa ba zai sauka ba; maimakon haka, har yanzu hannunsa a miƙe ya ke.5Kaiton Asriyen, kulkin fushina, sandar hannunka a bin harzuƙata ne!6Na aike shi gãba da al'umma mai girmankai, gãba da mutane masu ɗauke da ambaliyar fushina. Na umarce shi ya ɗauki ɓãtattu, ya kwashi ganima, ya tattake su kamar laka cikin tituna.7Amma ba haka ya ke nufi ba, bai kuma yi tunanin haka ba. Amma shi a cikin zuciyarsa ne ya kawar da al'umma masu yawa.8Gama ya ce, "Shugabannina ba sarakuna ba ne dukkansu?9Kalno ba kamar Karkemish ba ce? Hamat ba kamar Arfad ba ce? Samariya ba kamar Damaskus ba ce?10Kamar yadda hannuna ya yi nasara da mulkokin tsafi, wanda ƙerarrun gumakansu sun fi na Yerusalem da Samariya,11kamar yadda na yi da Samariya da gumakanta marasa amfani, ba zan yi irin wannan kuma ga Yerusalem da gumakanta ba?"12Sa'ad da Ubangiji ya gama aikin sa akan Tsaunin Sihiyona da bisa Yerusalem, zan hukunta jawabin faɗin ran sarkin Asiriya da homarsa.13Domin yace, "Da karfina da hikimata Na yi aiki. Ina da fahimta, na kuma kawas da iyakoki na mutane. Na sace taskokin su, kamar sã na nakasadda mazauna nan wurin.14Hannuna ya tsaya, kamar sheƙa, dukiyar dangogi, kuma kamar wanda ya tattara ƙwan da aka ƙyale. Na tattaro dukkan duniya. Ba bu wanda ya motsa fiffike, ko ya buɗe baki balle suyi ƙara."15Ko gatari zai iya yiwa mai sara da shi alfahari? ko zarto zai iya ɗaukaka kansa bisa wanda ya ke yanka da shi? sai kace sanda zata iya ɗaga mai ɗaukar ta, ko kuma kulkin katako zai ɗaga mutum.16Domin haka Yahweh mai runduna zai aiko da ramewa cikin jarumawansa; ƙarƙashin ɗaukakarsa kuma za a kunna ƙonewa kamar wuta.17Hasken Isra'ila kuma zai zama wuta, Mai Tsarkin nasa kuma harshen wuta, za ya ƙone ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya ya cinye su rana ɗaya.18Yahweh kuma zai cinye darajar kurminsa da gonarsa mai albarka, rai duk da jiki; zai zama kamar lokacin da ran marar lafiya ya suma.19Sauran itatuwan kurmin za su zama 'yan kaɗan, ƙaramin yaro zai iya ƙirga su.20A wannan rana, ringin Isra'ila, da iyalin Yakubu waɗanda suka tsira, ba za su dogara ga wanda ya ci nasara da su ba, amma lallai za su dogara ga Yahweh, MaiTsarkin nan na Isra'ila.21Ringi na Yakubu za su juya zuwa ga Allah mai iko.22Ko da shike mutanenka, Isra'ila, suna kama da yashin teku, sai ringi daga cikin su za su komo. An zartar da dokar Hallakarwa, kamar yadda adalci mai malalowa ya wajabta.23Gama Yahweh mai runduna, daf ya ke da hallakar da dukkan ƙasar kamar yadda ya ayyana.24Domin wannan Ubangiji Yahweh mai runduna yace, "Mutanena da suke zaune cikin Sihiyona, kada ku ji tsoron Asiriyen. Zai buge ku da sanda ya ɗaga kerensa ga bada ku, kamar yadda Masarawa suka yi.25"Kada ku ji tsoron sa, gama a cikin ɗan lokaci kaɗan fushina a kanku zai ƙare, fushi na zai kai ga hallakarwarsa."26Daga nan Yahweh mai runduna zai tayar da bulala akansu, kamar yadda ya fatattaki Midiyan a Tsaunin Oreb. Zai ɗaga sandarsa bisa teku ya ɗaga ta sama kamar yadda ya yi a Masar.27A wannan rana, nauyin kayansa an ɗauke shi daga kafaɗarki kuma karkiyarsa an ɗauke daga wuyanki, kuma karkiyarki zata lalace saboda ƙibar.28Maƙiyi ya zo Ayiyat ya ratsa ta Migron; a Mikmash ya ajiye abubuwan daya tanada.29Sun ƙetare suka sauka a Geba. Rema tana rawar jiki Gibiya ta Saul kuma ta gudu.30Ki yi kuka da ƙarfi, ɗiyar Galim! ki saurara, Laisha! ke talautattar Anatot!31Madmena tana gudu, mazaunan Gebim sun gudu domin su ɓuya.32A wannan rana zai sauka a Nob zai girgiza damtsensa a tsaunin ɗiyar Sihiyona, tudun Yerusalem.33Duba, Ubangiji Yahweh mai runduna zai sassare rassa da ban razana; itatuwan da suka fi tsawo za'a sare su, maɗaukaka kuma za'a ƙasƙantar dasu.34Za ya sassare kuramen jeji da gatari, Lebanon kuma cikin ɗaukakarsa zata faɗi.
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. AT: "ga waɗanda suke yin dokoki da ƙa'idodin da ba su dace da kowa ba"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya dai-dai. AT: "Ba su da adalci ga matalauta da mabukata a cikin mutanena"
Ishaya ya kwatanta marayu da dabbobin da sauran dabbobi ke farauta da cinsu. Wannan ya nanata cewa marayu basu da iko kuma alkalai na iya cutar dasu cikin sauki. AT: "cutar da yara waɗanda ba su da iyaye kamar dabba da ke bin abin farautarta"
Ishaya yayi amfani da tambaya don tsawata wa waɗanda suke cikin Yahuda waɗanda ke cutar talakawa da raunanan mutane. AT: "Ba ku da inda za ku nemi taimako, kuma ba za ku sami inda za ku ɓoye dukiyarku ba!"
"makiyanku za su iya kama ku a matsayin fursuna ko su kashe ku"
"Duk da cewa duk wadannan abubuwan sun faru, har yanzu yana cikin fushi." Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 5:25.
Duk waɗannan kalmomin suna nufin abu ɗaya ne. Ubangiji yana kamanta sarkin Asiriya da makamin da mutum yake riƙe a hannunsa kuma ya buga wasu mutane da shi. Ya nanata cewa sarkin Asiriya da sojojinsa kayan aiki ne da Yahweh yake amfani da su don hukunta Isra'ila. AT: "wanene zai zama kamar makami a hannuna wanda zan yi amfani da shi don nuna fushina"
Yahweh yayi magana akan fushin sa kamar wanda ya fi ruwa karfi fiye da kwantena; "mutane" suna ƙoƙari su ɗauki wannan kwandon, amma yana da nauyi, kuma Yahweh yana ci gaba da zuba ruwa koda bayan ya fara malala. AT: "wanda nake ci gaba da yin fushi koda bayan na hukunta su"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Yahweh ya kwatanta sojojin Asiriya da ke kai wa Isra'ila hari da mutanen da ke tattaka cikin laka waɗanda ba su damu da abin da zai faru da lakar ba. AT: "tattake su har sai sun zama kamar laka" ko 2) mutane suna taka kan wasu mutane don haka suna kwance cikin laka kuma ba sa iya tashi. Wannan wani magana ne na fatattakar su gaba daya. AT: "ka kayar da su gaba daya" (Duba: da figss_metaphor)
Ma'anar "wannan" da "wannan hanyar" za a iya bayyana a sarari. AT: "Amma sarkin Asiriya ba ya nufin yin abin da na gaya masa, kuma ba ya tunanin zan yi amfani da shi a matsayin makami na"
Kalmomin "lalata" da "kawar da" ma'ana abu ɗaya abu ne mai asali. Ana amfani dasu don girmamawa. AT: "Yana son halakar da ƙasashe da yawa gaba ɗaya"
Sarkin Asiriya yayi amfani da tambaya don jaddada abin da yayi imanin cewa ya kamata kowa ya riga ya sani. AT: "Na naɗa shugabannin runduna na sarakuna a kan ƙasashen da na ci da yaƙi!"
Wadannan duk sunayen garuruwa ne.
"Hannun" a nan yana nufin ƙarfin soja. AT: "Kamar yadda dakaru masu ƙarfi suka ci nasara" ko "Kamar yadda na ci nasara"
Kalmar "Samariya" tana nufin mutanen da suke zaune a wurin, kuma "ta" tana nufin birnin Samariya. Garuruwa da al'ummomi galibi ana maganarsu kamar suna mata. AT: "kamar yadda na yi wa mutanen Samariya da gumaka marasa amfani"
Sarkin Asiriya ya yi amfani da wannan tambayar don ya jaddada tabbacin cewa zai ci mutanen Yerusalem da yaƙi. AT: "Lallai zan yi wa Yerusalem da gumakanta haka!"
Yahweh yana magana kansa kamar shi wani ne. "Lokacin da ni, Ubangiji, na gama aikina a kan Dutsen Sihiyona da a kan Yerusalem, zan hukunta shi"
"Zan hukunta sarkin Asiriya saboda maganar girman kansa da ya yi, da girman kansa a fuskarsa"
Anan kalmar "I" tana nufin sarkin Assuriya. Shi ne shugaban sojojin Assuriya kuma ya yaba wa abin da sojojin suka yi a kan umurninsa. AT: "Ni da runduna na sun kawo" ko "mun kawo
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Sarkin Asiriya ya kunyata mutanen ƙasashen da ya ci nasara ko 2) ya cire sarakunan al'ummai don haka ba su ƙara yin sarauta.
Sarkin Asiriya ya kamanta karɓar dukiyar al'ummai da na wanda yake karɓar ƙwai daga sheƙan tsuntsu. Wannan yana jaddada yadda ya kasance mai sauƙi a gare shi da rundunarsa su ci waɗancan masarautun. AT: "Sojoji na sun wawushe dukiyar daga al'ummu kamar yadda mutum ke karbar kwai daga gida"
Sarkin Asiriya yana maganar mamaye al'ummai kamar yana tattara ƙwai. AT: "kamar yadda mutum yake daukar kwai daga gurbi lokacin da tsuntsayen ba ya nan don kare su, haka ma runduna ta ta kwashe dukiyar al'umma"
Wannan yana kwatanta al'ummomi da tsuntsu wanda ke zaune a hankali yayin da ake ɗaukar ƙwan nata. Wannan ya nanata cewa al'ummu ba su yi komai ba yayin da sojojin Asiriya suka kwashe dukiyoyinsu. AT: "Kuma kamar tsuntsun da ba ya sauti ko ya fuka fukafukinsa lokacin da wani ya saci ƙwai nata, al'ummomi ba su yi komai ba kamar yadda muka ɗauke taskarsu"
Waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya kuma ana amfani dasu don ƙarfafa ma'anar tambayoyin guda biyu da ke gabanta. Ana iya fassara wannan azaman sabuwar jumla. AT: "Kuma sanda ko sanda ba za su iya daga mutumin da ya dauke ta ba"
Babu tabbacin ko Yahweh ko Ishaya suna magana. Ana iya sake amfani da wannan ta yadda za a nuna kalmar 'ramewa' a matsayin kalmar aikatau ta yi rauni. AT: "Saboda haka ni, Ubangiji Yahweh Mai Runduna, zan sa sojoji masu ƙarfi na sarki su zama marasa ƙarfi"
Yahweh yana kwatanta hukuncinsa da wuta. Wannan yana nanata cewa hukuncinsa zai lalata ɗaukaka da girman mulkin Asiriya. AT: "Zan lalata girmansa kamar ina kunna wuta don kona duk abin da yake alfahari da shi"
Kalmomin "hasken Isra'ila" na nufin Yahweh. Babu tabbacin ko Yahweh ko Ishaya suna magana. AT: "Ni, Yahweh, hasken Isra'ila, zan zama kamar wuta, mai iya hallaka duk wanda ba ya girmama ni"
"Ni, Yahweh, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, zan zama kamar harshen wuta." Duba yadda kuka fassara "Mai Tsarki" a cikin Ishaya 1: 4.
"Wuta za ta ƙone ta cinye ƙaya da sarƙar Sarkin Asiriya." Mai maganar yayi kwatancen rundunar sarkin Assuriya da ƙayoyi da sarƙaƙƙiya. Wannan yana nanata yadda Allah zai hallakar dasu cikin sauki. AT: "Zan hallakar da Asiriyawa kamar wuta mai ƙaya da ƙayayuwa"
Zai yiwu ma'anar ita ce 1) "Yahweh zai halakar da manyan gandun daji da gonaki a cikin ƙasar Asiriya" ko 2) "Yahweh zai halakar da sojojin Asiriya kamar yadda wuta ke cin manyan dazuzzuka da gonaki."
Ana iya bayyana ma'anar a bayyane. AT: "wannan ya tsere daga sojojin Asiriya"
"ba za su ƙara dogara ga Sarkin Asiriya ba, wanda ya cutar da su"
Wannan ya nuna cewa akwai mutane da yawa na Isra'ila. AT: "sun yi yawa da yawa, kamar yashi a bakin teku"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya zartar cewa zai halakar da yawancin wadanda ke zaune a Isra'ila"
Ana iya fassara wannan azaman sabuwar jumla. AT: "Wannan dole ne a yi shi don cikakkiyar adalci" ko "Yahweh dole ne ya yi hakan domin shi cikakken mai adalci ne"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) AT: "halakar da komai a cikin ƙasa kamar yadda ya ƙuduri aniyar aikatawa" ko 2) AT: "halakar da mutane a cikin ƙasar kamar yadda ya ƙudura niyyar yi."
Ishaya yayi magana game da Sarkin Asiriya da rundunarsa kamar mutum ɗaya ne. AT: "Sarkin Asiriya da rundunarsa"
Kalmomin “sanda” da “sandar” na nuni ga gungumen itace da mutane ke amfani da shi a matsayin kulake don bugun dabbobi da sauran mutane. Ishaya yayi magana akan yadda Asiriyawa zasu mallaki Isra’ilawa kamar su Asiriyawa suna bugun Isra’ilawa da sanduna. AT: "Zai mallake ku kuma ya yi muku bayi"
Cikakken sunan "lalata" ana iya fassara shi azaman aiki. AT: "Zan halakar da shi saboda ina fushi da shi"
"zai doke Asiriyawa da bulala." Allah ba zai yi amfani da bulala ba da gaske. Wannan yana nufin ikon Allah na azabtar da Asiriyawa sosai. AT: "zai azabtar da Asiriyawa azaba kamar da bulala"
Wannan yana nufin lokacin da Allah ya taimaki wani mutum mai suna Gideon ya cinye sojojin Midiyanawa.
Wannan yana magana ne game da Allah wanda ya ceci mutane daga Assuriyawa kamar su sojojin Masar ne. Wannan yana nufin lokacin da Allah ya sa ruwan Bahar Maliya ya tsage don Isra'ilawa su tsere daga rundunar Masarawa kuma sojojin Masar su nutsar da shi. AT: "Zai taimake ku ku tsere daga sojojin Asiriya kamar yadda ya taimaka wa kakanninku suka tsere daga sojojin Masar"
"Yahweh zai ɗaga nauyin da Asiriyawa suka ɗora a wuyanka, zai kuma kawar da karkiyar da suka sa a wuyanku." Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Kalmomin "nauyi" da "karkiya" na nuni ga bauta. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai cire Asiriyawa da suka zalunce ku kuma zai hana su sanya ku bayin su"
Anan "Rama" da "Gibiya" na Saul" suna nufin mutanen da suke zaune a waɗannan garuruwan. AT: "Mutanen Rama sun yi rawar jiki da mutanen Gibiya na Saul sun gudu"
Kalmar "ɗiya" a nan tana nufin mutanen da ke zaune a cikin birni. AT: "Galim" ko "mutanen Galim"
Waɗannan sunaye ne na wasu birane da ƙauyuka kusa da Yerusalem waɗanda sojojin Asiriya suka bi ta hanyar haifar da tsoro tsakanin mutane. Duk waɗannan suna nuni ga mutanen da suke zaune a waɗannan wuraren.
Anan "shi" da "nasa" suna nufin Sarkin Asiriya da sojojinsa. Mutane za su girgiza daɗaɗɗu ga mutanen da suke barazanar. AT: "sojojin Asiriya zasu tsaya a Nob kuma suyi barazanar"
Kalmomin "dutse" da "tudu" sunaye ne ga mutanen da suke zaune a kansu. Kalmomin "dutsen 'yar Sihiyona" suna kusan kusan daidai da kalmomin "tudun Yerusalem." Duba yadda aka fassara su a cikin Ishaya 2:14. AT: "mutanen Dutsen Sihiyona da mutanen da ke zaune a kan tuddai a Yerusalem"
"zai yanke manyan rassa na bishiyoyi." Don a bayyane cewa wannan yana nufin sojojin Asiriya, ana iya fassara shi da wani misali: Zai hallakar da sojojin Asiriya kamar ƙarfafan mutane waɗanda ke datse manyan rassa na bishiyoyi.
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda ba za a iya amfani da kalmar nan ta "ruɓewa" azaman kalmar "yi amo ba." AT: "kuma rassan zasu fadi kasa su yi amo mai firgitarwa" ko "kuma rassan za su fado kasa da hayaniya mai karfi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "zai sare manyan bishiyoyi"
"Dazukan Lebanon ba za su ƙara yin girma haka ba." Wannan wataƙila kwatanci ne ga sojojin Asiriya. AT: "Yahweh zai fatattaki sojojin Asiriya, kamar yadda suke da ƙarfi"
1Zai toho daga cikin kututturen Yesse, reshe kuma daga cikin sa zai bada 'ya'ya.2Ruhun Yahweh kuma zai zauna bisansa, Ruhun hikima da fahimta, da Ruhun umarni da iko, da Ruhun sani dana tsoron Yahweh.3Marmarin sa zai kasance tsoron Ubangiji; ba zaiyi shari'a bisa ga abin da idanunsa suka gani ba, ba kuwa zai yi hakunci bisa ga abin da kunnensa ya ji ba.4Maimakon haka zai shar'anta talakwa bisa ga adalci bisa ga dai-daita kuma zai yanke shawara ga masu tawali'u na duniya. Zai bugi duniya da sandar bakinsa, da numfashin leɓunansa kuma zai kashe miyagu.5Adalci zai zama ɗammarar ƙugunsa, aminci kuma ɗammara kewaye da kwatangwalonsa.6Kyarkeci zai zauna tare da rago, damisa kuma zata kwanta tare da ɗan'akuya, ɗan maraki da ɗan zaki tare da kiwataccen ɗan maraƙi, za su zauna tare, ɗan yaro kuwa zai bishe su.7Saniya da kerkeci za su yi kiwo tare, 'ya'yansu za su kwanta wuri ɗaya. Zaki zai ci ciyawa kamar sã.8Jariri zai yi wasa a bakin ramin maciji, yayayyen yaro kuma zai sa hannunsa a kogon maciji.9Ba za su cutar ko hallakar ba a ko'ina kan tsaunina mai tsarki; gama duniya za ta cika da sanin Yahweh, kamar yadda ruwaye suka rufe teku.10A wannan rana, tushen Jesse zai tsaya a matsayin tuta ga mutane. Al'ummai za su neme shi, wurin hutun sa kuma zai zama abin ɗaukaka.11A wannan rana, Ubangiji zai sake sa hannunsa domin ya fanshi sauran mutanensa da suka rage a Asiriya, Masar, Fatros, Kush, Ilam, Shina, Hamat, da tsibirai na teku.12Zaya kafa tuta domin al'ummai ya tattara korarru na Isra'ila warwatsattsu na Yahuda daga kusurwoyi huɗu na duniya.13Zai juyar da kishin Ifraim, masu azabtar da Yahuda kuma zai datse su. Ifraim ba zai yi kishin Yahuda ba, Yahuda kuma ba zai ƙara kishin Ifraim ba.14Maimakon haka zasu sauko bisa tuddan Filistiyawa a wajen yamma, tare za su washe 'ya'yan gabas. Za su kai hari ga Idom da Mowab Mutanen Ammon kuma za su yi masu biyayya.15Yahweh zai hallakar da dukkan kwarurruka na Tekun Masar. Da iskarsa mai ƙonewa zai karkaɗe hannunsa bisa kan Kogin Yufiretis zai raba su zuwa rafuffuka bakwai, domin a iya ƙetarewa da takalmi a ƙafa.16Zai kasance akwai karabka domin sauran mutanensa, waɗanda suka ragu za su dawo daga Asiriya, kamar yadda akayi ga Isra'ila cikin ranar da suka taso daga ƙasar Masar
Kututture shine abin da ya rage daga itacen bayan an sare shi. ''Kututturen Jesse'' yana wakiltar abin da ya rage na masarautar da ɗan Yesse Dauda ya taɓa zama sarki.
Dogaro da shi yana wakiltar kasancewa tare da shi da kuma taimaka masa. Kalmar "shi" tana nufin wanda zai zama sarki.
Anan kalmar "ruhu" tana nufin iyawa ko inganci da Ruhun Yahweh zai bashi. AT: "kuma zai sa ya sami hikima da fahimta, wa'azi da ƙarfi, ilimi da tsoron Yahweh"
Kalmomin "abin da idanunsa suka gani" yana nufin ganin abubuwan da ba su da mahimmanci don yanke wa mutum hukunci dai-dai. AT: "ba zai hukunta mutum ba kawai ta hanyar ganin yadda mutumin yake kama"
"kuma ba zai yanke shawara da abin da kunnuwansa suka ji ba." Kalmomin "abin da kunnuwansa suka ji" yana nufin jin abin da mutane ke faɗi game da wani. AT: "kuma ba zai hukunta mutum ba kawai ta hanyar jin abin da wasu ke faɗi game da shi"
Kalmar nan "ƙasa" a nan tana wakiltar mutane a duniya. Bugun su da sandar bakinsa yana wakiltar hukunta su, kuma wannan hukuncin zai kai ga hukunci. AT: "Zai yi hukunci ga mutanen duniya, kuma za a hukunta su"
Sanya adalci kamar ɗamara yana wakiltar zama adali. Zai yiwu ma'anoni su ne 1) adalcin sarki zai ba shi damar yin sarauta. AT: "Adalcinsa zai zama kamar ɗamara a kugu" ko 2) adalcin sarki zai nuna ikonsa na yin mulki. AT: "Zai yi mulkin adalci"
Sanya aminci kamar ɗamara yana wakiltar kasancewa da aminci. Zai yiwu ma'anoni su ne 1) amincin sarki zai ba shi damar yin sarauta, ko 2) amincin sarki zai nuna ikonsa na mulki. AT: "amincinsa zai zama kamar ɗamara a ɗamarar sa" ko "zai yi mulki cikin aminci"
Ishaya ya bayyana yadda duniya zata kasance lokacin da sarki yake sarauta. Za a sami cikakken zaman lafiya a duniya. Ana nuna wannan ta hanyar zaman lafiya cewa za'a kasance har tsakanin dabbobi. Dabbobin da ke yawan kashe wasu dabbobi ba za su kashe su ba, kuma duk za su kasance cikin aminci tare.
Kalmomin suna magana ne game da waɗannan dabbobin gaba ɗaya, ba ga takamaiman rago ko akuya ba. Duk waɗannan dabbobi ne masu cin ciyawa da ciyawa. Sauran dabbobi wasu lokuta sukan kawo hari su cinye su. AT: "raguna ... youngan akuya ... calan maruƙa ... masu kiba ... Shanu ... shanu"
Waɗannan jimlolin suna nufin waɗannan dabbobin gaba ɗaya, ba ga takamaiman kerkeci ko damisa ba. Waɗannan duk dabbobi ne masu ƙarfi da ke kai hari da cin waɗansu dabbobi. AT: "Kyarkeci ... damisa ... zakuna ''
Yaro zai kula da su kuma ya kai su wurare masu kyau don shan ruwa da cin ciyawa ko ciyawa.
Ana iya bayyana a sarari cewa jaririn zai kasance cikin aminci saboda macijin ba zai sare shi ba. AT: "Yara za su yi wasa lafiya bisa ramin macijin"
"Tsattsarkan dutse" shi ne Tsaunin Sihiyona, a Yerusalem. AT: "akan duka tsaunin tsattsarkan Yahweh"
Kalmomin "ilimin Yahweh" yana wakiltar mutanen da suka san Yahweh. AT: "duniya za ta cika da waɗanda suka san Yahweh" ko "waɗanda suka san Yahweh za su rufe duniya"
Ana amfani da wannan jimlar don nuna yadda duniya za ta cika da mutanen da suka san Yahweh. Zai iya zama a bayyane cewa yana yin hakan idan kalmominta sun yi daidai da kalmomin a cikin jumlar da ta gabata. AT: "kamar yadda tekuna ke cike da ruwa"
Wannan yana nufin ɗan Yesse da na Sarki Dauda wanda zai zama sarki wanda aka ba da labarinsa a cikin Ishaya 11: 1. AT: "Sarkin zuriyar Jesse" ko "sarkin ya fito ne daga Jesse"
Tutar wata tuta ce da sarki zai daga ta a matsayin alama ga mutane su ganta su zo wurinsa. AT: "zai zama alama ga mutane" ko "zai jawo hankalin mutane su zo wurinsa"
Hannu yana nuni ga ikon Allah. AT: "Ubangiji zai sake yin amfani da ikonsa don dawo da ragowar mutanensa"
Abubuwan da za a iya fahimta su ne 1) "Ubangiji zai sanya sarki a matsayin tuta ga al'ummu" ko 2) "Sarki zai kafa tuta ga al'ummu"
"mutanen Yahuda waɗanda aka warwatse ko'ina cikin duniya"
An hoton duniya kamar tana da kusurwa huɗu, kuma waɗancan kusurwoyin sune mafi nisan wurare. Wannan yana nufin ko'ina cikin duniya inda waɗannan mutane zasu kasance. AT: "tun daga wurare masu nisa na duniya" ko "daga ko'ina cikin duniya"
A nan Yahuda yana nufin zuriyar masarautar kudu. Ana iya bayyana wannan jumlar a cikin tsari mai aiki. AT: "zai hana mutanen Yahuda adawa" ko "zai hana mutanen Yahuda ƙiyayya"
Mutanen Isra'ila da na Yahuza an nuna su kamar tsuntsayen da suke tashi da sauri don afkawa mutum ko dabba. AT: "za su tafi da sauri zuwa tsaunukan Filistiyawa don su farma mutanen wurin"
Jijjiga hannunsa akan wani abu yana wakiltar ikonsa don canza shi. AT: "Da ikonsa zai sa iska mai tsananin iska ta busa a Kogin Yufiretis"
"don mutane su tsallake ta koda suna sanye da takalmin takalminsu"
Babbar hanya babbar hanya ce wacce mutane da yawa zasu iya hawa kanta. "Yahweh zai yi hanya"
"lokacin da suka fito daga ƙasar Masar"
1A wannan rana za ka ce, "Zan gode maka, Yahweh. Koda shike ka yi fushi da ni, fushinka ya juya, ka kuwa yi mani ta'aziya.2Duba, Allah shi ne cetona; zan dogara, ba kuwa zan ji tsoro ba, gama Yahweh, hakika, ƙarfina ne da waƙata. Ya zama cetona,"3Da farinciki za ku ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.4A wannan rana za ku ce, "Kuyi godiya ga Yahweh ku kuma kira ga sunansa; ku bayyana ayyukan sa a wurin al'ummai, ku yi shelar sunansa maɗaukaki ne.5Ku raira ga Yahweh, gama ya aikata al'amura mafifita, bari wannan ya zama sananne ko'ina a duniya.6Ku tada murya ku yi sowa ta murna, ku mazaunan Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra'ila dake tsakiyarku mai girma ne."
Ana maganar fushin Allah kamar mutum ne wanda zai iya juyawa ya tafi. Yana nufin cewa Allah ya daina yin fushi. AT: "Ba ku da sauran fushi da ni"
Ana magana game da Allahn da ke haifar da ceton wani kamar Allah ne wannan ceton. Ana iya bayyana kalmar 'tsira' ta ƙuruciya tare da sunan "mai ceto" ko kuma kalmar aikatau "cece". AT: "Allah ne ya sa na sami ceto" ko "Allah ne mai cetona" ko "Allah shi ne wanda ya cece ni"
Ana maganar Allah sa wani ya zama mai ƙarfi kamar Yahweh ne ƙarfin su. AT: "Yahweh yana ƙarfafa ni"
"Ya cece ni"
Ishaya yayi magana akan ceton mutane kamar suna samun ceto yadda mutane suke samun ruwa daga rijiya. AT: "zaku yi murna lokacin da ya cece ku, kamar yadda mutane suke murna yayin da suka debo ruwa daga rijiya"
Za a iya nuna kalmar "ayyukan" tare da jumlar "abin da ya aikata." AT: "Faɗa wa mutane game da manyan abubuwan da ya aikata"
Anan “sunansa” yana nufin Yahweh. AT: "ku shelanta cewa an ɗaukaka shi" ko "shelar cewa shi mai girma ne"
"saboda Allah na Isra'ila, wanda ke zaune a cikinku, mai iko ne" ko "saboda Allah Mai Tsarki na Isra'ila yana da ƙarfi kuma yana zaune tare da ku"
1Kenan game da Babila, wanda Ishaya ɗan Amoz ya karɓa:2A bisa buɗaɗɗen tsauni ku ɗaga tutar alama, ku tada murya gare su, ku kaɗa hannu gare su domin su shigo ƙofofin hakimai.3Na umarci tsarkakana, I, Na kira masu iko na su aiwatar da fushina, su waɗanda nake fahariya da su da waɗanda aka ɗaukaka.4Hayaniyar mutane cikin duwatsu, sai kace na mutane da yawa! Hayaniya ta mulkokin al'ummai a tattare! Yahweh mai runduna yana tattara runduna domin yaƙi.5Sun zo daga ƙasa mai nisa, tun daga iyakacin sama. Yahweh kenan da kayan yakinsa na hukunci, domin hallaka dukkan ƙasa.6Ku yi kuka, gama ranar Ubangiji ta kusa; zata zo da hallakrwa daga Mai iko.7Domin haka dukkan hannuwa za su maƙale, kowacce zuciya kuma za ta narke.8Za su firgita; zafi da baƙinciki za su kama su, kamar mace cikin naƙuda. Za su dubi junansu cikin mamaki, fuskokinsu za su zama kamar gaushen wuta.9Duba, ranar Yahweh tana zuwa da hasala da fushi mai zafi, za'a maida ƙasar kango, za'a hallakar da masu zunubin daga cikin ta.10Taurarin sama ba za su bada haskensu ba. Rana za ta duhunta a lokacin fitowarta, wata kuma ba zai haskaka ba.11Zan hori duniya domin muguntarta da Miyagu domin zunubansu. Zan kawo ƙarshen alfarmar masu girmankai in ƙasƙantar da alfarmar mutane masu ban tsoro.12Zan sa maza su yi ƙaranci fiye da zinariya mai daraja, samun mutum kuma ya zama da wuya fiye da tsattsarkar zinariya ta Ofir13Domin wannan zan sa sammai su yi rawar jiki, duniya kuma za ta girgiza ta gusa daga wurinta, ta wurin hasalar Yahweh mai runduna, da cikin ranar fushinsa mai zafi.14Kamar barewar da aka farauto ko tumakin da ba su da makiyayi, kowanne mutum ya juya ga bin mutanensa, zai gudu zuwa ƙasarsa.15Duk wanda aka samu za a kashe shi, duk wanda aka kama kuma zai mutu da kaifin takobi.16Jariransu kuma za a yayyanka su akan idanunsu. Gidajensu za a washesu, matan su kuma za a yi masu fyaɗe.17Duba, Ina gab da tayar da Medes domin su kai masu hari, waɗanda ba za su kula da azurfa ba, ba kuma za su yi murna saboda zinariya ba.18Mãsunsu za su soki samari. Ba za su tausayawa jarirai ba kuma ba zasu bar yara ba.19Daga nan Babila, mafi daraja a mulkoki, jamalin fahariyar Kaldiyawa, Allah zai juyadda su kamar yadda ya yi da Sodom da Gomora.20Ba za a zauna ciki ko rayuwa a ciki ba daga tsara zuwa tsara. Balarabe ba zai kafa rumfarsa a can ba, makiyaya kuma ba za su bar garken su su huta a can ba.21Amma namomin jeji za su kwanta a wurin. Gidajensu za su cika da mujiyoyi; Jiminai da Gadai za su yi ta tsalle can.22Kuraye za su yi kuka a cikin kagarorinsu, diloli kuma a cikin fadodinsu masu kyau. Lokacinta ya kusa, kwanakinta kuma ba za a jinkirtasu ba.
Kalmar "su" tana nufin sojoji daga wata ƙasa.
"wadanda na ware wa kaina" ko "rundunar da na ware wa kaina"
Yin fushin Allah yana wakiltar azabtar da mutane saboda fushin Allah. AT: "Na kira manyan mayaƙana don azabtar da mutanen Babila saboda sun fusata ni"
Kalmomin "akwai" an fahimta. Kalmomin "taro" da "mutane da yawa" ma'anarsu ɗaya. AT: "Akwai hayaniyar mutane da yawa a cikin tsaunuka" ko "Akwai hayaniyar taron mutane da yawa a tsaunuka"
Kalmomin "akwai" an fahimta. Kalmomin “mulkokin” da “al’ummai” a nan suna nuni ga abu ɗaya. AT: "Akwai hayaniyar hayaniya da masarautu da yawa da suka hallara"
Wani abu da yake shirin faruwa ba da daɗewa ba ana maganarsa kamar yana zuwa kusa. AT: "ranar Yahweh zata zo ba da daɗewa ba"
Kalmar "shi" tana nufin ranar Yahweh. "Ya zo tare da hallaka" yana nufin halakar za ta faru a wannan ranar. "Hallaka daga Maɗaukaki" yana nufin cewa Madaukaki zai hallaka su. AT: "a wannan ranar, Allah Maɗaukaki zai hallaka su"
Ba zato ba tsammani mutane suna jin mummunan zafi da baƙin ciki kamar ana jin zafin da baƙin cikin mutanen da ke kama su. AT: "ba zato ba tsammani za su ji mummunan zafi da azaba"
Ranar da za ta zo da fushi da fushi na nufin cewa za a yi fushi da fushi a wannan ranar. Ana iya bayyana sunayen suna "fushi" tare da sifofin "fushin." AT: "a ranar Yahweh, zai yi fushi da tsananin fushi"
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda za'a iya amfani da kalmar nan ta "lalata" da kalmar aikatau. AT: "lalata ƙasar"
"Taurari a sararin sama"
"mugayen mutane"
Kaskantar da kai galibi yana wakiltar kasancewa da tawali’u. Rage girman kan mutane yana nuna sanya su masu tawali'u. AT: "zai ƙasƙantar da maras tausayi"
Ofir sunan wani wuri ne inda akwai zinariya tsantsa.
Ubangiji yana maganar mutanen Isra'ila marasa tsaro kamar barewa ko tunkiyar da mafarauta ko dabbobin daji ke bi. AT: "Kamar barewar da ke gudu da sauri lokacin da mutane ke farautar su, kuma kamar tumakin da ba su da makiyayi da ke gudu daga namun daji"
Tumakin da ba su da makiyayi ba su da wanda zai kāre su daga dabbobin daji da za su kawo musu hari kuma su kashe su.
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Maƙiyi zai kashe da takobi duk wanda suka samu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Abokan gaba kuma za su farfasa jariransu gunduwa-gunduwa" ko "Makiyan za su doke jariransu har sai sun mutu"
Wannan yana nufin cewa za'a sace duk wani abu mai mahimmanci daga gidajensu. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Maƙiyi zai washe gidajen mutane" ko "Maƙiyi zai sace duk wani abu mai mahimmanci daga gidajen mutane"
Sanya mutane suna son yin wani abu ana maganarsu kamar motsa su. AT: "Ina gab da sanya mutanen Mediya su so su afka musu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "masarautar da mutane suka fi so"
Ana iya fassara sunayen suna "ƙawa" da "girman kai" tare da siffofi. Kalmar "ɗaukaka" tana nufin kyakkyawar surar Babila. AT: "kyakkyawan birni wanda Kaldiyawa ke alfahari da shi"
Wadannan kalmomin guda biyu suna nufin abu ɗaya ne. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba wanda zai rayu a ciki"
An fahimci kalmomin "za su yi kuka". AT: "jackal za su yi kuka a cikin kyawawan fadoji"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. "Lokacinta" da "kwanakinta" duka suna nuni ga lokacin da Allah ya zaɓa domin a halaka Babila. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Lokacin da duk wannan zai faru ga mutanen Babila ya kusa, kuma babu abin da zai dakatar da shi"
1Yahweh zai ji tausayin Yakubu; zai sake zãɓen Isra'ila ya sake dawo da su cikin ƙasarsu, bãƙi za su haɗa kai da su, za su haɗa kansu da gidan Yakubu.2Al'ummai za su ɗauke su su kai su garinsu. Gidan Isra'ila zai ɗauke su ya kai su ƙasar Yahweh a matsayi bayi maza da mata. Za su bautadda waɗanda suka kwashe a dã, za su yi mulkin waɗanda suka ƙuntata masu.3A wannan rana Yahweh ya ba ku hutu daga baƙinciki da wahalarku kuma daga aiki mai wahala wanda aka sa ku yi,4za ku raira wannan waƙar ta habaici gãba da sarkin Babila, "Yadda ƙarshen mai azabtarwa ya zo, fushin masu girmankai ya ƙare!5Yahweh ya karya sandar mugu, ikon masu mulkin nan,6wanda ya bugi mutane cikin fushi da naushi kowanne lokaci, ya mallaki al'ummai da fushi, da harin da ba mai hanawa.7Dukkan duniya tana zaune cikin hutu kuma shiru; sun fara biki da raira waƙa.8Har itatuwan sayfres suna murna da kai tare da Sidas na Lebanon; suka ce, 'Tunda aka ƙasƙantar da kai, ba bu wani mai saran itace da ya zo ya sare mu ƙasa.'9Lahira daga ƙasa na marmarin saduwa da kai idan ka je can. Ta tayar da mattatu domin ka, dukkan sarakunan duniya an sa sun tashi daga kursiyinsu, dukkan sarakunan al'ummai.10Dukkansu za su yi magana su ce maka, 'Ka zama marar ƙarfi kamar mu.11Ka zama irin mu. An yi ƙasa da alfarmarka har Lahira duk da ƙarar amon tamburanka. An shimfiɗa tsutsotsi ƙarƙashinka, tsutsotsi sun rufe ka.'12Yadda ka faɗo daga sama, tauraron rana, ɗan asubahi! Yadda aka sãre ka ƙasa, kai wanda kayi nasara da al'ummai!13Sai ka ce a cikin zuciyarka, 'Zan hau cikin sama, Zan ɗaukaka kursiyina bisan taurarin Allah, zan zauna bisa tsaunin taruwar jama'a, cikin ƙarshen arewa.14Zan hau can bisa maɗaukakan gajimarai; Zan maida kaina kamar Allah Mai Iko.'15Yanzu angangaradda kai zuwa Lahira, zuwa ƙarshen rami.16Waɗanda suka ganka za su zuba maka ido kuma za su saurare ka. Za su ce, 'Ko shi ne mutumin da ya sa duniya ta yi rawa, wanda ya girgiza mulkoki,17wanda ya mai da duniya kamar jeji, wanda ya juyadda biranenta ya kuma hana 'yan yãrinsa komawa gida?'18Dukkan sarakunan al'ummai, dukkan su cikin daraja suke kwance, kowannen su cikin kabarinsa.19Amma kai an jefar da kai can waje da kushewarka kamar reshen da a ka jefar. Mattatu sun rufe ka kamar riga, waɗanda a ka sara da takobi, masu gangarowa zuwa ramin duwatsu.20Ba za ka bi su cikin jana'iza ba, saboda ka hallaka ƙasarka kuma ka kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaton zuriyar masu mugunta ba har abada."21Ka shira yanka domin 'ya'yansa, saboda zunubin kakanninsu, don kada su tashi su mallaki duniya su cika dukkan duniya da birane.22"Zan tashi in yi gãba da su"-wannan furcin Yahweh mai runduna ne. Zan datse wa Babila sũna, zuriya da tsãra" - wannan furcin Yahweh ne.23Zan maishe ta mallakar mujiyoyi, da kuma tabkunan ruwa, kuma zan share ta tsintsiyar hallakarwa" - wannan shi ne furcin Yahweh mai runduna.24Yahweh mai runduna ya rantse ya ce, "Hakika, kamar yadda na ayyana, haka zai faru; kamar yadda na shirya haka zai faru:25Zan karya mutumin Asiriya cikin ƙasa ta kuma bisa kan duwatsu zan tattake shi ƙarƙashin sawu. Daga nan za a kawar da karkiyarsa daga gare su kayansa kuma daga kafaɗarsu."26Wannan shi ne shirin da a ka ƙadartawa dukkan duniya, wannan kuma shi ne hannun da a ka miƙar kan dukkan al'ummai.27Gama Yahweh mai runduna ya shirya haka; wa zai hana shi? hannun Sa a miƙe ya ke, wa za ya juyadda shi?28A cikin shekarar da sarki Ahaz ya mutu wannan furcin yazo:29Kada ku yi murna, dukkan ku Filistiyawa, cewa sandar da ya buge ki ya karye. Gama daga cikin tsatson maciji ƙasa mai dafi za ta fito, zuriyarsa kuma za ta zama wuta mai firiyar maciji.30Ɗan farin talaka zai yi kiwon tumaki a makiyayata, mabuƙaci kuma zai kwanta cikin tsaro. Zan kashe tsatsonka da yunwa dukkan waɗanda suka tsira za su mutu.31Ki yi kururuwa, ƙofa, ki yi kuka, birni, dukkan ku za ku narke, Filistiya. Gama daga arewa girgije mai hayaƙi ke fitowa, ba kuma mai ratsewa cikin dagarsa.32Ta yaya za a amsa wa 'yan saƙon al'umman nan? Wato Yahweh ne ya kafa Sihiyona, daga cikin ta ne raunanan mutanensa za su sami mafaka.
Anan "Yakubu" yana nufin zuriyar Yakubu. AT: "Yahweh zai yi rahama ga zuriyar Yakubu"
Gidan Yakubu yana nufin zuriyar Yakubu, Isra'ilawa. AT: "ku haɗa kai da zuriyar Yakubu"
"Al'ummai za su dawo da zuriyar Yakubu zuwa ƙasar Isra'ila"
"Sojojin Isra'ila za su kwaso waɗanda suka kamo Isra'ilawa"
Kalmar "ku" ɗaya ce, amma tana nufin mutanen Isra'ila ne. Hakanan, "wahala" da "baƙin ciki" ma'anar abu ɗaya daidai kuma ana amfani dasu tare don girmamawa. AT: "daga abubuwan da suka jawo muku wahala mai yawa"
"Azzalumi ya zo karshe." Wannan kirari ne.
Wataƙila sandar miyagu tana nufin sandar da mugaye zasu bugi wasu mutane da ita. Karya sandar tana wakiltar lalata ikonsu don zaluntar mutane. AT: "Yahweh ya lalata ikon mugaye"
"kai musu hari ba tare da tsayawa ba"
Wannan yana nufin kowa da kowa a duniya. AT: "kowa da kowa a duniya"
Ishaya yayi maganar bishiyoyi kamar dai mutane waɗanda zasu iya murna. Wannan ya nanata cewa babban abu ne cewa Allah ya dakatar da sarkin Babila wanda har ma ɗabi'a za ta yi farin ciki idan za ta iya. AT: "Zai zama kamar ma idan bishiyoyin cyprus da itacen al'ul na Lebanon sun yi murna a kanku"
Ana magana da Lahira kamar mutum ne mai ɗoki ya sadu da baƙinsa. Wannan yana nuna cewa sarki ya mutu. AT: "Lahira kamar mai gida ne mai son saduwa da ku"
"yana rayar da matattu a gare ku, duk sarakunan duniya." Ana magana da Lahira kamar mutum ne wanda zai iya farka waɗanda suke cikinta. AT: "Duk matattun sarakunan duniya a cikin Lahira suna tashi don gaishe ku"
Kalmar "su" tana nufin matattun sarakuna a Sheol, kuma kalmar "ku" tana nufin sarkin Babila.
Sarakunan da suka mutu za su yi magana game da sarkin Babila wanda ba shi da ɗaukaka kamar darajarsa ta gangara zuwa Lahira. AT: "Daukakarka ta ƙare lokacin da Allah ya aike ka nan Lahira"
Maganar da ke ƙasan gawarsa ana maganarsa kamar tabarma ko gado. AT "Kuna kwance akan gadon tsutsotsi" ko "Kuna kwance akan ƙwayoyi da yawa"
Tauraron rana tauraro ne mai haske wanda yake wayewa kafin wayewar gari. Mutanen Isra'ila za su koma zuwa ga sarkin Babila dangane da wannan tauraruwa don su nuna cewa ya taɓa zama babba, amma yanzu bai kasance ba. AT: "Kun kasance kamar tauraron asuba mai haske, amma kun fado daga sama"
Mutanen Isra'ila za su yi magana game da sarkin Babila kamar wanda aka sare shi itace. AT: "An kayar da ku kamar itacen da wani ya sare ƙasa"
Wannan yana magana ne game da tatsuniyar da mutane da yawa a Gabas ta Tsakiya suka sani, cewa gumakan Kan'aniyawa sun haɗu a majalissar a kan dutse a arewacin Siriya. Zama a kan dutse yana wakiltar mulki tare da gumakan. AT: "Zan yi mulki a kan dutsen da gumakan suke haduwa"
"a mafi yawan wuraren arewa." Da alama an kira dutsen a arewa Zaphon. Wasu sifofin zamani sun ce "can nesa da gefen Zaphon."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Amma yanzu Allah ya saukar da ku zuwa Lahira"
Mutanen za su yi amfani da wannan tambayar ko dai su yi wa sarkin Babila ba'a, ko kuma su nuna mamakinsu ga abin da ya faru da shi. AT: "Tabbas, wannan ba mutumin bane"
Mai iya yiwuwa su ne 1) ƙasa ta yi rawar jiki yayin da rundunar sarki ke tafe don cinye mutane, ko 2) wannan yana nufin mutanen duniya da ke rawar jiki don tsoron sa.
"wanda ya sanya wuraren da mutane suke zama a jeji"
Wannan yana nufin cewa an binne gawarwakinsu ta hanya mai daraja. AT: "duk sarakunan da suka mutu ana binne su ta hanya mai kyau"
Yin jifa daga kabari yana nuna rashin binnewa. AT: "Amma ba a binne ku ba. Gawarwarku an bar ta a ƙasa"
Wannan yana wakiltar gawawwaki da yawa a saman jikinsa. AT: "Gawarwakin mutanen da suka mutu gaba ɗaya sun rufe jikinku" ko "Gawarwakin sojojin da suka mutu suna jingina a saman jikinku"
Ramin yana nufin ko dai zuwa lahira, ko kuma wani rami a ƙasa inda ake zubar da gawawwaki da yawa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba wanda zai sake yin magana game da zuriyar masu aikata mugunta"
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda ba za a iya amfani da kalmar nan ta "yanka" ba tare da kalmar aikatau. AT: "Ku shirya don kashe 'ya'yan sarkin Babila"
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda za'a nuna kalmar nan "mugunta" azaman kalmar "aikata zunubi ƙwarai." AT: "saboda kakaninsu sun yi zunubi mai girma"
Anan "tashi" yana wakiltar ko dai ya zama mai ƙarfi ko kai hari. AT: "don haka ba za su yi ƙarfi ba" ko "don haka ba za su kawo hari ba"
Kalmar "ta" tana nufin birnin Babila. Garuruwa galibi ana maganarsu kamar mata. AT: "Ni ma zan yi shi"
Sanadiyyar zama dausayi ko kududdufai na tsayayyen ruwa inda ake maganar birni da sanya garin cikin waɗancan abubuwa. AT: "a cikin wurin da akwai koramai da ke tsaye"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. AT: "abubuwan da na tsara zasu tabbata"
Karya yana wakiltar kayarwa. AT: "Zan kayar da Asiriyawa a cikin ƙasata" ko "Zan sa Asiriyawa a cikin ƙasata ta kayar da su"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Cire karkiya da nauyi na wakiltar 'yanta mutane daga bautar. AT: "Sannan zan 'yantar da Isra'ilawa daga bautar Asiriya kamar cire nauyi daga kafadarsu"
Manufar "an yi niyya" ana iya bayyana ta tare da fi'ili mai aiki. AT: "Wannan shi ne shirin da Allah Ya nufa ga duniya baki daya"
Ana magana akan Allah yana shirye ya hukunta al'ummu kamar ya ɗaga hannunsa don ya buge su. Kalmar "hannu" na iya wakiltar ikonsa ma. AT: "wannan ikon Yahweh ne na hukunta dukkan al'ummu" ko "ta haka ne Yahweh zai hukunta al'umman"
Sandar da ta bugu a Filistiya wakiltar wani sarki ne wanda ya aiki rundunarsa don su yi yaƙi da su. Karyewa yana wakiltar ko dai ya mutu ko kuma an ci shi. AT: "sarkin da ya aiko sojojinsa a kanku ya mutu" ko "sojojin da suka kawo muku hari sun ci nasara"
Wadannan jimlolin guda biyu siffofin 'ya'yan maciji ne wadanda suka fi macijin cutarwa. Suna wakiltar magajin sarki kasancewa mai iko da zalunci fiye da sarki na farko.
Wannan yana wakiltar mutane mafi talauci. AT: "Mafiya talauci" ko "Mafi talauci daga mutanena"
Anan "tushenku" yana nufin mutanen Filistiya. AT: "Zan kashe mutanenku da yunwa wanda zai kashe duk waɗanda suka tsira"
Narkewa yana wakiltar zama mai rauni saboda tsoro. AT: "za ku zama da rauni da tsoro"
Wannan yana nuna cewa babbar runduna tana zuwa daga arewa. AT: "Gama daga arewa babbar runduna tana zuwa da gajimare hayaƙi"
Marubucin yayi amfani da wannan tambayar don gabatar da koyarwarsa game da yadda yakamata Isra’ilawa suyi magana da manzanni. AT: "Ta haka za mu amsa wa manzannin Filistiya."
1Furci game da Mowab. Lallai, a dare ɗaya Ar ta Mowab ta zama marar amfani an hallaka ta, Lallai, a dare ɗaya Kir ta Mowab ta zama marar amfani an hallaka ta.2Sun hau saman masujada, mutanen Dibon sunje sammai don su yi kuka; Mowab na makoki kan Nebo da Medeba. Duk kawunansu an aske su kwal duk gemunsu kuma an yanke su.3A cikin titunansu suna saye da tsummoki; a kan benayen su da dandalinsu kowannensu yana koke-koke, sun narke da hawaye.4Heshbon da Ileyale sun yi kira domin taimako; a na jin muryarsu har Yahaz. Domin haka mayaƙa na Mowab suna kira domin neman taimako; su kadai suna rawar jiki.5Zuciyata tana kuka domin Mowab; sanannun ta suna gudu zuwa Zowa da Iglat Shelishiya. Sun hau zuwa wajen Luhit suna kuka; hanyar zuwa Horonayim sun tada murya da ƙarfi kan hallakarsu.6Ruwayen Nimrim sun bushe; ciyawa ta yi yaushi, sabuwar ciyawa ta mutu, ba sauran ɗanyen abu.7Yalwar abin da suka samar da wanda suka ajiye, za su ɗauka su haye kwazazzabon foflas.8Kukan ya zaga wajen iyakar Mowab; kuwwarta har ta fi Iglaim da Biya Ilim.9Domin ruwayen Dimon cike suke da jini; amma zan kawo wanda ya fi zafi akan Dimon. Zaki zai kai hari ga waɗanda suka tsira a Mowab da kuma sauransu da suka rage a cikin ƙasar.
Waɗannan su ne sunayen birane da garuruwa a Mowab.
Kalmomin "lalatattu" da "halakarwa" ma'anarsu ɗaya ce kuma suna ƙarfafa cewa birnin ya lalace gaba ɗaya. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sojojin abokan gaba za su hallaka Ar na Mowab gaba ɗaya"
Wadannan sunaye sunaye suna nufin mutanen da suke zaune a wurin. AT: "Mutanen Mowab za su yi kuka saboda abin da ya faru da biranen Nebo da Medeba"
Suna yin hakan ne don nuna tsananin baƙin cikinsu. AT: Dukkansu za su aske kawunansu kuma su yanke gemu kuma su yi baƙin ciki "
Wannan ya ci gaba da annabci game da mutanen Mowab. Allah ya bayyana abubuwan da zasu faru a nan gaba kamar suna faruwa a yanzu. (Duba: Ishaya 15: 1).
Suna yin hakan ne don nuna tsananin baƙin cikinsu. AT: "suna sanya tsummoki suna makoki"
Waɗannan su ne sunayen birane da garuruwa.
Girgizar jiki alama ce ta tsoro kuma tana wakiltar tsoro. AT: "za su cika da tsoro gaba ɗaya" ko "suna rawar jiki da tsoro"
Anan Allah yana wakiltar “zuciya” wanda ke ƙarfafa motsin zuciyar sa. Allah yayi maganar babban bakin cikinsa kamar zuciyarsa tayi kuka. AT: "Ina mai bakin ciki game da abin da ke faruwa ga Mowab"
Waɗannan su ne sunayen birane da garuruwa.
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda ba za a iya amfani da kalmar nan "hallaka" azaman kalmar "lalacewa" ba. AT: "saboda an lalata garinsu"
Kukan mutane da sauran waɗanda suke jinsa ana maganarsu kamar kukan ya fita.AT: "Mutanen ko'ina a yankin Mowab suna ihu"
Kalmomin "ya tafi" an fahimta. Waƙar mutane da sauran waɗanda suke jin ta ana magana ne kamar dai marin ya tafi nesa da waɗannan wurare biyu. AT: "marin har ya kai ga Igalim da Biya Ilim" ko "mutane har ma da Iglaim da Biya Ilim suna makoki"
Anan "I" yana nufin Yahweh. Har ila yau, "Dimon" yana nufin mutanen da suke zaune a can. AT: "amma zan haifar da matsala ga mutanen Dimon"
1Ku aika da raguna domin mulkin ƙasa daga Selah cikin jeji; zuwa tsaunin ɗiyar Sihiyona.2Kamar tsuntsaye masu yawo, kamar sheƙar da aka warwatsar haka matan Mowab a mishigan Kogin Arnon.3"Ka bada umarni, ka tabbatar da adalci; ka sa inuwa ta zama dare a cikin tsakiyar rana; ka ɓoye yasassu; kada ka bashe da waɗanda ba kome ba.4Ka barsu su zauna a cikin ku, 'yan gudun hijira daga Mowab; ka zama maɓuya gare su daga mai lalatarwa." Gama zalunci zai tsaya, hallakarwa kuma zata tsaya, waɗannan da suke tattaka mutane za su ɓace a ƙasar.5A cikin alƙawarin aminci kuma za'a kafa kursiyi, ɗaya kuma daga cikin rumfar Dauda da aminci zai zauna can, zai yi shari'a yana neman adalci, yana aikata gaskiya.6Mun ji labarin girmankan Mowab, girmankansa da fahariyarsa da fushinsa. Amma taƙamarsa duk bakomai ba ne.7Sai Mowab tayi koke-koke domin Mowab - dukkan su suna makoki, ku da a ka lalatar ɗungum, domin wainar kauɗar inabin Kir Hareset.8Gonakin Heshbon sun bushe duk da kuringar inabin Sibma. Sarakunan al'ummai sun tattake zaɓaɓɓun inabin da suka kai zuwa Yaza, da suka yaɗu zuwa cikin jeji. Rassanta sun yaɗu waje; sun fita zuwa ƙetaren teku.9Domin wannan zan yi kuka tare da Yaza domin kuringar Sibma. Zan dausayar da ku da hawaye na, Heshbon da Ileyale. Gama na kawo ƙarshen farincikinku game da amfanin gonakinku damina da na kaka.10Murna da farincikinku an ɗauke su daga 'ya'yan itatuwan kuramenku, ba sauran waƙa, ba sowa cikin gonakinku. Ba mai taka ruwan inabi a wurin matsewa, gama na kawo ƙarshen sowa ga mai takawar.11Domin haka zuciyata na tsãki kamar girayar Mowab, can cikina kuma domin Kir Hareset.12Sa'ad da Mowab ya gajiyar da kansa a wuri mai bisa kuma ya shiga masujada ya yi addu'a, addu'o'insa ba za su yi komai ba.13Wannan ita ce maganar da Yahweh ya faɗi game da Mowab da farko.14Yahweh ya sake yin magana, "Cikin shekara uku, ɗaukakar Mowab za ta ɓace; duk da yawan mutanensa, sauran da za su ragu za su zama 'yan kaɗan marasa amfani."
Mowabawa za su aiko wa sarkin Yahuda da raguna don ya kiyaye su daga maƙiyansu.
Wannan sunan birni ne.
Dukkan mutanen Mowab, waɗanda suka haɗa da mata, an tilasta su su gudu daga gidajensu. AT: "Kamar tsuntsayen da ba su da gida, matan Mowab za su tsallaka kogin zuwa wata ƙasa" (Duba:
Zafin tsakiyar rana yana wakiltar Mowabawa wahala daga abokan gaba, kuma inuwa tana wakiltar kariya daga abokan gaba. Kwatanta inuwa zuwa dare yana nuna cewa suna son kariya mai ƙarfi. AT: "Ka kare mu gaba ɗaya daga maƙiyanmu babban inuwa yana kare mutane daga zafin rana"
"Bada 'yan gudun hijira daga Mowab su zauna tare da ku." Anan "ku" yana nufin mutanen Yahuda.
Bayar da buyayyar wuri ana maganarsa a matsayin wurin buya. AT: "a ba su wuri don ɓoyewa daga waɗanda ke ƙoƙarin halakar da su" ko "ɓoye su daga waɗanda suke son hallaka su"
Anan “kursiyi” yana nufin ikon yin sarauta kamar sarki. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai kasance mai aminci ga alkawarin kuma zai naɗa sarki"
Anan "rumfar Dauda" yana wakiltar gidan Dauda, har da zuriyarsa. Zama akan karaga yana wakiltar mulki.AT: "zuriyar Dauda zai yi mulki da aminci"
Kalmomin "Mowab" da "nasa" na nuni ga mutanen Mowab. AT: "Mun ji cewa mutanen Mowab suna da girman kai, masu girman kai, masu alfahari da fushi"
"Amma abin da suke faɗi game da kansu ba komai bane" ko "Amma abin da suke alfahari da shi ba gaskiya ba ne"
"saboda babu wainar inabi a Kir Hareset"
An san ƙasar Mowab da gonakin inabi. Anan Allah ya bayyana ƙasar Mowab a matsayin babban gonar inabi. Wannan ya nanata cewa masu mulki, wanda ke nufin runduna, sun lalata komai na Mowab gaba ɗaya.
A cikin 16: 9-10 kalmar "I" tana nufin Yahweh.
Allah yayi magana game da tsananin baƙin cikinsa ga waɗannan wurare kamar zai yi kuka da yawa kuma hawayensa da yawa za su zubo a kansu. AT: "Zan yi kuka mai yawa saboda ku"
'Ihun murna' na wakiltar mutane suna ihu don farin ciki game da girbin 'ya'yan itacensu. AT: "Saboda abin da zan yi, ba za ku ƙara ihu da murna ba lokacin da kuka girbe gonakinku na 'ya'yan itacen bazara"
Anan "ihu" yana nufin farin cikin mutanen da ke matse inabi don samar da ruwan inabi. AT: "saboda haka mutanen da ke matse inabin ba sa ihu da murna"
Kalmomin "zuciyata" suna wakiltar Yahweh ne da kuma yadda yake ji. Ya kwatanta nishinsa da sautin waƙar baƙin ciki da aka kaɗa da garaya. AT: "Don haka na yi nishi kamar waƙar baƙin ciki a kan garaya"
Kalmar "cikina ta ciki" tana wakiltar Yahweh. An fahimci kalmar "shaka" daga jumlar da ta gabata. AT: "nishi a cikina saboda Kir Hareset" ko "Ina baƙin ciki ƙwarai game da mutanen Kir Hareset"
"ba za a amsa addu'arsa ba"
Kalmar "Mowab" tana nufin mutanen Mowab.
"Kasar Mowab ba za ta ƙara zama mai ɗaukaka ba"
1Furci game da Damaskus.2Biranen Arowa za su zama kufai. Za su zama inda garkuna za su riƙa kwanciya, ba kuwa mai tsoratar dasu.3Biranensu masu kagara za su ɓace daga Ifraim, mulki kuma daga Damaskus, da ringin Aram - za su zama kamar ɗaukakar mutanen Isra'ila - wannan furcin Yahweh mai runduna ne.4Zai zama kuma a ranar nan darajar Yakubu zata zama 'yar siririya, ƙibar jikinsa zata saɓe.5Zai zama kamar kwanakin da maigirbi ya tattara hatsin dake tsaye, hannunsa kuma yana yankan zangarku. zai zama kamar lokacin da mutum ke kalar zangarku cikin kwarin Refayim.6Za'a bar kala, duk da haka, kamar lokacin da itacen zaitun ke kakkaɓewa: biyu ko uku cikin reshe mafi bisa, huɗu ko biyar a cikin rassa mafi bisa na itace mai 'ya'ya - wannan furcin Yahweh ne, Allah na Isra'ila.7A wannan rana mutane za su dubi mahaliccinsu, idanunsu za su dubi Mai Tsarki na Isra'ila.8Za su dubu bagadai, aikin hannuwansu, ba kuwa za su dubi abin da yatsunsu suka yi ba, sandunan Ashera ko siffofin rana.9A wannan rana ƙarfafan biranensu za su zama kamar wuraren da aka bar su kufai cikin kurmi a ƙwanƙolin tsaunuka, da aka bar su saboda mutanen Isra'ila wannan zai zama hallaka.10Domin kun manta da Allah mai cetonku, kun kuma yi watsi da dutsen ƙarfinku. Kuna dasa tsire-tsiren da suka gamshe ku, kuna dasa rassan inabi da kuka karɓa wurin baƙo,11A cikin rana kayi dashe da shinge da noma. Bada daɗewa ba irinka zai yi girma, amma girbinka zai gaza a cikin ranar baƙinciki da matsananciyar azaba.12Kaito! ga hayaniyar mutane da yawa, wannan ruri na kama da rurin tekuna, da gudun al'ummai, suna gudu kamar gudun ruwaye masu girma!13Al'ummai za su yi ruri kamar gudun ruwaye masu yawa, amma Allah zai tsauta masu. Za su gudu nesa za'a runtume su kamar ƙai-ƙai a kan tsaunuka gaban iska, kamar guguwa kuma gaban hadari.14Da yamma, ga, razana! Kafin safiya kuma za su tafi! wannan shi ne rabon waɗanda suke yi mana sata, rabon waɗanda suke yi mana fashi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. "Dukkan mutane za su watsar da biranen Arowa"
Ifraim ce mafi girma a cikin Isra'ila. Anan tana wakiltar duk masarautar arewacin Isra'ila. AT: "Garuruwa masu ƙarfi za su ɓace daga Isra'ila"
Kalmomin "zasu ɓace" an fahimta daga jumlar da ta gabata. Damaskus ita ce wurin da sarkin Aram yake sarauta. Mulkin da ya ɓace yana wakiltar sarki wanda ba shi da ikon sarauta. AT: "mulkin zai ɓace daga Damaskus" ko "ba za a sami ikon sarauta a cikin Damaskus ba"
Ana amfani da wannan jimlar a nan don yiwa muhimmin abin da zai faru. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
Anan "Yakubu" yana nufin mulkin Isra'ila. Isra'ila ba za ta ƙara zama mai ɗaukaka ba. Maimakon haka zai zama mai rauni da talauci.
Wannan kwari ne inda mutane ke girma da girbin abinci da yawa.
Kalmar "Kalata" a nan tana wakiltar mutanen da za su ci gaba da zama a Isra'ila. AT: "Amma za a sami wasu mutane kaɗan a Isra'ila"
Mutane suna girbin itatuwan zaitun ta hanyar girgiza su domin 'ya'yan zaitun ɗin su faɗo. AT: "kamar thean zaitun da suka rage a kan itacen zaitun bayan mutane sun girbe su"
Neman Allah anan yana wakiltar fatan cewa zai taimake su. AT: "mutane za su yi fatan Mahaliccinsu, Mai Tsarki na Isra'ila, zai taimake su"
Duba zuwa bagadan yana wakiltar bautar gumaka tare da fatan gumakan za su taimaka musu. AT: "Ba za su bauta wa gumaka a bagadansu ba" ko "Mutanen Isra'ila ba za su je bagadansu ba kuma su nemi gumakansu su taimake su"
Anan ana wakiltar mutane da “hannayensu” don jaddada cewa sun yi bagadai ko gumaka. AT: "wanda suka yi da hannayensu" ko "wanda su da kansu suka gina"
Ana iya bayyanawa a bayyane wanda ya bar waɗannan ƙasashe. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "cewa Hiviyawa da Amoriyawa suka bari bayan mutanen Isra'ila sun zo"
Anan "ku" yana nufin mutanen Isra'ila. Kalmar nan "an manta da ita" baya nufin basu da ƙwaƙwalwar ajiyar Allah. Yana nufin basu daina yi masa biyayya ba. AT: "Ba ku da sauran biyayya"
"Allah mai kubutar da kai"
Wannan yana kwatanta Allah da babban dutse wanda mutane zasu iya hawa don guje wa abokan gaba ko ɓoye a baya. AT: "sun yi watsi da Allah, wanda yake kamar dutsen da ke kare ku" ko "sun yi watsi da wanda ke kiyaye ku"
Hayaniya ce da hayaniya. AT: "Sautin mutane da yawa, yana da ƙarfi kamar teku"
Sojojin abokan gaba suna nuna karfi ne mai karfi wanda babu wanda zai iya dakatar da shi. AT: "Al'ummai suna ta shigowa kamar ruwa mai ƙarfi"
Ana maganar abin da ya same su kamar wani yanki ne da suka gada. AT: "Wannan shine abin da ke faruwa ga waɗancan"
1Kaiton ƙasa ta motsin fukafukai wadda, take rafukan Kush.2Wadda take aika jakadu ta hanyar teku, a cikin ruwaye ta jiragen iwa Ku tafi ku, jakadu masu sauri, wurin dogayen al'ummai masu taushin fata, wurin mutanen da a ke tsoron su nesa da kusa, al'umma mai ban razana mai tattakewa, wadda ruwaye sun raba ƙasarta.3Dukkan ku mazaunan duniya da waɗanda ke zaune a duniya, idan kuka ga alama a kan duwatsu, ku duba; idan aka busa ƙaho, ku saurara.4Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗi mani, "A hankali zan lura daga gidana, kamar gumi cikin hasken rana, kamar hazon ƙyasashi a lokacin girbi.5Kafin girbi, ya zo sa'ad da fure ya kaɗe, huda tana zama nunannun 'ya'yan inabi, zai datse maɓulɓula da ƙugiya mai tsini, zai sare ya kuma kwashe rassan da suka barbaje.6Za a bar su tare saboda tsuntsayen duwatsu da dabbobin duniya. Tsuntsaye za su yi damina a kansu, kuma dukkan dabbobin duniya za su yi lokacin sanyi a kansu."7A wancan lokacin dogayen mutane masu taushin jiki za su kawo hadaya ga Yahweh, daga mutanen da a ke tsoro nesa da kusa, ƙarfafan al'ummai masu ban razana, waɗanda rafuka suka raba ƙasarsu, zuwa wurin da ya ke na sunan Yahweh mai runduna, zuwa Tsaunin Sihiyona.
Mai iya yiwuwa "tsattsauran fikafikai" su ne 1) jiragen ruwan da suke da filafili ana maganarsu da cewa suna da fikafikai. AT: "Bone ya tabbata ga waɗanda ke zaune a ƙasar bayan kogunan Kush, waɗanda jiragen ruwa da yawa suna kama da ƙwari a kan ruwa" ko 2) rudun fikafikan yana nufin hayaniyar kwari da ke da fikafikai, wataƙila fara.
Ana amfani da kalmomin "nisa" da "kusa" tare ma'ana "ko'ina." AT: "mutanen da ake jin tsoron su a ko'ina" ko "mutanen da kowa a cikin ƙasa ke tsoro"
Taka ƙasa yana wakiltar cinye sauran ƙasashe. AT: "al'ummar da ke da ƙarfi kuma ta ci wasu ƙasashe"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. AT: "Dukkanku mutanen duniya"
Alamar da ƙaho sun kasance suna kiran mutane zuwa yaƙi. Umurnin kallo da saurara umarni ne na kulawa da shirya don yaƙi. AT: "ku mai da hankali yayin da aka ɗaga alama a kan duwatsu kuma aka busa ƙaho"
An yi amfani da ƙahonin don kiran mutane zuwa yaƙi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ku mai da hankali lokacin da kuka ji karar ƙaho na yaƙi"
Abin da Allah zai kiyaye za'a iya fada a sarari. AT: "A hankali zan lura da waccan al'ummar daga gidana" ko "Daga gidana, a hankali zan kalli abin da mutanen wannan al'ummar suke yi"
Waɗannan jumlolin suna nuna yadda Allah zai dubata cikin nutsuwa.
Yahweh zai datse rassan kafin inabin ya nuna. AT: "Yahweh zai yanke rassan da wuka kafin 'ya'yan itacen su"
Allah yana da alama ya canza daga faɗi misalin zuwa magana kai tsaye game da ƙasar. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Wadanda aka kashe za a bar su tare" ko "Kamar rassan da aka yanke aka jefar, gawawwakin wadanda aka kashe za a bar su a kasa"
"kowane irin namun daji"
Kalmar "suna" tana nufin Yahweh. AT: "zuwa Tsaunin Sihiyona, inda Yahweh Mai Runduna yake zaune"
1Furci game da Masar. Duba, Yahweh ya hau girgije mai sauri ya taho Masar; gumakan Masar za su razana a gabansa, zuciyar masarawa za ta narke a cikin su.2"Zan haɗa masarawa gãba da masarawa: Mutum zai yi faɗa gãba da ɗan'uwansa, mutum gãba da maƙwabcinsa; birni kuma gãba da birni, mulki kuma gãba da mulki.3Ruhun Masar zai karaya daga ciki. Zan rushe shawararsa, koda ya ke sun nemi shawarar gumakai, da ruhun matattu, da masu duba, da masu aiki da ruhohi.4Zan bada masarawa a hannun mugun shugaba, sarki mai ƙarfi zai yi mulkin su - wannan shi ne furcin Yahweh Ubangiji mai runduna."5Ruwayen teku za su bushe, rafi zai bushe ya zama ba komai.6Rafuka za su yi wari; ƙoramun Masar kuma za su shanye su bushe; iwa da jema za su yi yaushi.7Iwar dake kusa da Nilu, da bakin gãɓar Nilu, da dukkan gonakin da a ka shuka a gefen Nilu za su bushe, za a kore su, kuma ba za su kasance ba.8Masunta za su yi kuka su yi makoki, da dukkan masu jefa ƙugiya cikin Nilu za su yi makoki, kuma masu jefa tãru za su yi baƙinciki.9Masu aikin tsifar zare da waɗanda ke saƙar farar tufa za su rame.10Za a murƙushe masu aikin tufafi na Masar; masu aikin lada za su yi baƙinciki a cikin su.11Sarakunan Zowan wawaye ne gaba ɗaya. Shawarar mashawartan Fir'auna mafiya wayo ta zama rashin hankali. Yaya za ka iya cewa da Fir'auna, "Ni ɗan mutane masu hikima ne, ni ɗan sarakunan dã ne?"12Ina mazajenka masu wayau suke? Bari su gaya maka su kuma sanasshe ka abin da Yahweh mai runduna ke shiryawa game da Masar.13Sarakunan Zowan sun zama wawaye, an ruɗi sarakunan Memfis; sun sa Masar ta bauɗe, su da suke duwatsun kusurwar kabilunta.14Yahweh ya sa ruhun lalacewa cikin tsakiyarta, suka kuma sa Masar ta bauɗe cikin dukkan abin da take yi, kamar mashayi mai tangaɗi cikin amansa.15Ba abin da wani zai iya yi domin Masar, ko kai ko wutsiya, ko rassan dabino ko iwa.16A wannan rana, Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki da tsoro saboda ɗagaggen hannun Ubangiji mai runduna a kansu.17Ƙasar Yahuda za ta zama sanadin tangaɗin Masar. Dukkan sa'ad da wani ya tuna masu da ita, za su ji tsoro, saboda shirin Yahweh, kan abin da ya ke shiryawa gãba da su.18A wannan rana za a sami birane biyar cikin ƙasar Masar da za su yi magana da harshen Kan'ana su yi rantsuwa su yi amana da Yahweh mai runduna. Ɗaya daga waɗannan za a kira shi Birnin Rana.19A wannan rana za a sami bagadin Yahweh a tsakiyar ƙasar Masar, da dutsen daya zama ginshiƙi na kan iyakar Yahweh.20Zai zama kamar alama da shaida ga Yahweh mai runduna a cikin ƙasar Masar. Idan suka yi kuka ga Yahweh saboda mai tsananta masu, zai aiko masu da mai ceto da mai kariya, zai kuma cece su.21Yahweh zai zama sananne a Masar, a wannan rana Masarawa za su san da kasancewar Yahweh. Za su yi sujada da hadayu da baye-baye, za su yi wa'adodi ga Yahweh, su cika su kuma.22Yahweh zai azabci Masar, yana azabtarwa da warkarwa kuma. Za su juyo ga Yahweh; zai ji addu'arsu ya warkar dasu.23A wannan rana za a sami karabka tsakanin Masar da Asiriya, Asiriye zai zo Masar, Bamasare kuma zai je Asiriya; Masarawa kuma za su yi sujada tare da Asiriyawa.24A cikin wannan rana, Isra'ila za ta zama ta uku tare da Masar da Asiriya, za su zama albarka a tsakiyar duniya;25Yahweh mai runduna zai albarkace su ya ce, "Mai albarka ce Masar, jama'ata; Asiriya, aikin hannuwana; da Isra'ila, abin gãdona."
Ana ganin Yahweh a hoto kamar yana hawa kan gajimare kamar yana cikin karusai.
An kwatanta gumakan a matsayin suna jin tsoro yayin da Yahweh yake zuwa. AT: "Gumakan Masar suna rawar jiki da tsoro a gaban Yahweh"
Narkar da zuciya yana wakiltar rasa ƙarfin gwiwa. AT: "Masarawa ba su da sauran ƙarfin hali"
An fahimci kalmomin "za su yi yaƙi" daga jumlar da ta gabata. AT: "mutum zai yi yaƙi da maƙwabcinsa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan raunana ruhun Masar daga ciki"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Yahweh zai sa shawarar da ya bayar ta zama ba ta da amfani ko kuma 2) Yahweh zai sa shi ya kasa ba da wata shawara. Ana iya sake amfani da wannan ta yadda za a nuna kalmar nan ta 'shawara' a matsayin kalmar aiki 'nasiha'. AT: "Zan rikitar da masu ba sarki shawara"
Anan "hannu" yana nufin iko. AT: "Zan ba da Masarawa a hannun maigida mai ƙarfi"
Masarawa suna kiran Kogin Nilu da "teku." Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya dai-dai. AT: "Kogin Nilu zai ƙafe gaba ɗaya"
"Iwa" da "jema" suna nufin nau'ikan tsire-tsire na ruwa iri biyu. AT: "tsire-tsire a gefen kogin zai mutu kuma ya ruɓe"
"filayen kusa da Nilu inda mutane suka shuka amfanin gona"
Don kamun kifi, wasu mutane suna sanya ɗan abinci kaɗan a ƙugiya, a ɗaura ƙugiya a kirtani, a jefa ƙugiya a cikin ruwa. Lokacin da kifi yayi kokarin cin abincin, bakinsa zai makale a jikin mutum, sai mutumin ya fitar da kifin daga cikin ruwa.
Don kamun kifi, wasu mutane sukan jefa raga a kan ruwa. Lokacin da kifi ya kama shi, sai su zare tarun da kifin daga cikin ruwa.
"Waɗanda ke aiki tare da tsefe"
"Mutanen Masar da suke yin zane"
"zai ji bakin ciki sosai"
Wadannan jimlolin guda biyu suna da ma'ana iri daya. Ko dai sarakunan Zoan suma mashawartan masu hikima ne ko Fir'auna, ko kuma wasu gungun mutane ne da suma aka nuna su wawaye ne.
Ishaya ya yi amfani da wata tambaya don ya yi wa masu hikima ba'a. Kalmar "ku" tana nufin Fir'auna. AT: "Ba ku da maza masu hikima." ko "Mazanku wawaye ne."
Ishaya yana nuna cewa yakamata masu hikima su iya fahimtar shirin Allah, amma Ishaya bai gaskanta cewa suna da hikima ba. AT: "Idan da gaske suna da hikima, da za su iya gaya muku abin da Yahweh Mai Runduna yake shiryawa game da Masar"
Ana magana da sarakunan Zowan da Memfis kamar dai sune ginshiƙan gine-gine saboda suna da mahimmancin al'umma. AT: "shugabannin sun sa Masar ta ɓace"
Ishaya yayi magana game da hukuncin Yahweh kamar dai Masar ta kasance ƙoƙon ruwan inabi. Yana magana ne game da Yahweh yana sa shugabanni tunaninsu ya gurbata kamar tunaninsu gurɓatacce ruwa ne da Yahweh ya haɗu da ruwan inabin. AT: "Yahweh ya hukunta su ta hanyar karkatar da tunaninsu" ko "Yahweh ya hukunta Masar da karkatar da tunaninsu shugabanninta tunani, kamar yadda abubuwan maye ke rikitar da tunanin mutane"
Ishaya yayi magana akan mutanen Masar suna aikata abin da ba daidai ba kamar an sanya su suyi ta yawo kamar mashayi.
Wannan yana nanata cewa mutanen Masar zasu kasance cikin tsoro da rashin taimako idan Allah ya hukunta su.
Anan “hannu” yana nufin ikon Allah, kuma ɗaga hannu a kansu yana wakiltar hukunta su. AT: "saboda Yahweh Mai Runduna ya ɗaga ikonsa mai ƙarfi don azabtar da su"
“ƙasar Yahuda” da “Masar” suna nuni ga mutanen da ke waɗannan wuraren. Masarawa za su yi tuntuɓe domin suna tsoro. AT: "Mutanen Yahuda za su sa Masarawa su yi tuntuɓe" ko "Mutanen Yahuda za su sa Masarawa su firgita ƙwarai"
Anan, "su" da "su" suna nufin Masarawa kuma "ita" tana nufin mutanen Yahuda. AT: "Duk lokacin da wani ya tunatar da Masarawa game da mutanen Yahuza, Masarawa za su ji tsoro"
Wannan yana nufin mutanen waɗancan garuruwan. AT: "mutanen da ke biranen Masar biyar za su yi magana"
Wannan yana nufin Ibraniyanci, yaren mutanen Allah da ke zaune a ƙasar Kan'ana. Anan Kan'ana yana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin. AT: "yaren mutanen Kan'ana"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane za su kira ɗayan waɗannan biranen"
Maganar "iyakar" tana nufin iyakar Masar. AT: "ginshiƙin dutse ga Yahweh a iyakar Masar"
Ana iya bayyana sunayen suna "alamar" da "shaida" da kalmomin aiki "nuna" kuma a tabbatar." AT: "bagaden zai nuna kuma ya tabbatar da cewa Yahweh Mai Runduna yana cikin ƙasar Masar"
"Yahweh zai aiko wani ya ceci Masarawan tare da shi"
Anan "Masar" tana nufin mutanen Masar. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai sa mutanen Masar su san shi"
"za su yi alkawura ga Yahweh kuma su kiyaye su" ko "za su yi wa'adi ga Yahweh kuma za su yi abin da suka yi alkawarin yi"
Anan, "Masar" na nufin mutanen Masar. AT: "Yahweh zai wahalar da mutanen Masar"
Babbar hanya babbar hanya ce wacce mutane da yawa zasu iya hawa kanta.
Abu na bautar su ana iya bayyane. AT: "Masarawa da Asiriyawa za su bauta wa Yahweh"
Sunayen ƙasashe uku suna wakiltar mutanen waɗannan ƙasashen. AT: "Isra'ilawa zasu zama na uku tare da Masarawa da Asiriyawa"
Sunayen al'ummomin uku suna nuni ne ga mutanen waɗannan al'ummomin. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Na albarkace ku, ya ku mutanen Masar, saboda ku mutanena ne; kuma na albarkace ku, ya ku mutanen Asiriya, saboda na halicce ku; kuma na albarkace ku, ya Isra'ila, saboda na mallake ku lafiya"
1A cikin shekarar da Tartan ya zo Ashdod, sa'ad da Sargon sarkin Asiriya ya aiko shi, ya yi faɗa gãba da Ashdod ya amshe ta.2A wannan lokaci Yahweh ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz yace, "Ka je ka tuɓe tsummokara daga ƙugunka, ka tuɓe takalma daga ƙafafunka." Ya yi haka, ya yi tafiya huntu ba takalma a ƙafafunsa.3Yahweh yace, "Kamar yadda bawana Ishaya ya yi tafiya huntu ba takalma a ƙafafunsa shekara uku, wannan alama ce da al'ajibi dangane da Masar da Kush -4ta haka sarkin Asiriya zai tafi da kamammu na Masar, da korarru na Kush, tsoho da yaro, huntu ba takalmi, da ɗuwawunsu a waje, domin Masar ta kunyata.5Za su karaya su ji kunya, saboda Kush begensu da Masar darajarsu.6Mazaunan wannan yanki a cikin wannan rana za su ce, 'Hakika, wannan shi ne tushen begenmu, inda mu kan ruga neman taimako domin a cece mu daga sarkin Asiriya, to yanzu, ta yaya za mu tsira?"'
Ashdod yana nufin sojojin Ashdod. AT: "ya yi yaƙi da sojojin Ashdod kuma ya kayar da ita"
"yana yawo ba tare da tufafi ba kuma ba takalmi." A nan kalmar “tsirara” mai yiwuwa tana nufin sanya tufafinsa ne kawai.
Sarki ya umarci rundunarsa su yi wannan aikin. AT: "Sarkin Assuriya zai sa rundunarsa ta jagoranci waɗanda aka kamo"
Ana iya bayyana a sarari cewa zasu fara kai hari da kame mutane. AT: "zai afkawa Masar da Kush kuma ya kama mutanensu ya jagorance su"
"tsoro da kunya"
Fata da ɗaukaka suna nuni ga amincewarsu da ƙarfin soja na waɗannan ƙasashe. AT: "saboda sun dogara da karfin sojojin Kush da na Masar"
mutanen da ke zaune a ƙasashen da ke iyaka da Bahar Teku
1Furci game da hamada ta wajan teku. Kamar guguwa mai sharewa ta bi ta Negeb, ta zo tana wucewa ta cikin jeji, daga ƙasa mai ban tsoro.2An ba ni ruya mai ban razana: mutum marar imani yana yin rashin imani, mai hallakarwa yana hallakarwa. Jeka ka kai hari, a kan Ilam; yi sansani, Midiya; zan tsaida dukkan rurinta.3Saboda haka kwankwasona ya cika da ciwo; ciwo kamar irin ciwon mace mai naƙuda ya kama ni; abin da na ji ya durƙusar da ni; abin da na gani ya tada hankalina.4Zuciyata tana bugawa; na kaɗu da tsoro. Hasken asuba lokacin da nike so, amma ya kawo razana a gare ni.5Sun shirya teburi, sun shimfiɗa dardumai, sun ci sun sha; ku tashi, yarimai, ku shafe garkuwoyinku da mai.6Gama abin da Yahweh yace da ni ke nan, "Jeka, ka sa mai tsaro; dole ya faɗi abin da ya gani.7Sa'ad da ya ga karusa, da tagwayen mahaya, a kan jakuna, da raƙuma, sai ya natsu ya yi lura sosai."8Mai tsaron ya yi kuka, "Ubangiji, a kan kagara nike tsaye dukkan yini, kullum, a kan aikina nike dukkan dare."9Ga karusa tana zuwa da mutum da tagwayen mahaya. Ya yi kira, "Babila ta faɗi, ta faɗi, dukkan sassaƙaƙƙun siffofin allolinta kuma sun ragargaje har ƙasa."10Masussukaina da sheƙaƙƙu, yaran masussukata! Abin da na ji daga Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, shi na furta maku.11Furci game da Duma. Wani ya kira ni daga Siya, "Mai tsaro, me ya rage na dare?" Mai tsaro, me ya rage na dare?"12Mai tsaro ya ce, "Safiya ta kan zo haka ma dare. Idan kana so ka yi tambaya, sai ka yi tambaya; ka sake dawowa kuma."13Furci game da Arebiya. A cikin jejin Arebiya za ku kwana, ku fataken Dedaniyawa.14Ku kawo ruwa saboda masu jin ƙishi; mazauna ƙasar Tema, ku kawo gurasa ga masu gudun hijira.15Gama sun gudo daga takobi, daga takobin da a ka zaro, daga bakan da ke a ɗane, kuma daga nawayar yaƙi.16Gama abin da Yahweh ya faɗa mani ke nan, "A cikin shekara ɗaya, kamar yadda ma'aikacin da a ka ɗauka domin shekara ɗaya zai gani, dukkan darajar Keda za ta ƙare.17Maharba kaɗan kawai, da jarumawan Keda 'yan kaɗan za su rage," gama Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi.
Wannan yana nufin mutanen da ke zaune a Babila a matsayin hamada ne, duk da cewa Allah bai mai da shi hamada ba tukuna. Wannan taron tabbas zai faru. AT: "game da mutanen da ke zaune a ƙasar da ba da daɗewa ba za ta zama hamada"
Ishaya ya kwatanta sojojin da za su kawo wa mutane hari da hadari mai iska. Za su kasance masu sauri da ƙarfi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya nuna mini hangen nesa mai wahala"
Anan "ta" tana wakiltar duk mutanen da ke shan wahala saboda mutanen Babila. Yahweh zai sa su daina nishi lokacin da ya aika rundunar Ilam da Midiya don su hallakar da Kaldiyawa.
Wahayin da Ishaya ya gani yana da matukar damuwa yana haifar masa da ciwo na zahiri. Anan yayi bayanin ciwo da takurawar da yake ji a tsakiyar ɓangaren jikinsa.
Ishaya ya kwatanta ciwon da yake ji da zafin matar da ta haihu. Wannan yana jaddada babban ciwo da yake ji.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Abin da na ji ya sa ni lankwasawa cikin zafi"
Anan "Su" suna nufin shugabannin Babila.
Sojoji za su sanya mai a kan garkuwar fatarsu don su kasance masu laushi kuma ba su fasa yayin yaƙi.
"gaya wa mai tsaro ya tsaya a bangon Yerusalem"
"soja yana hawa cikin keken doki, dawakai biyu suna jan sa"
Anan "Ubangiji" yana nufin mutumin da yake da iko wanda ya umurci mai tsaro ya tsaya a bangon Yerusalem.
Ana magana game da kasancewar magabtansu gaba ɗaya da Babila kamar Babila ta faɗi. Anan "Babila" yana wakiltar mutanen Babila. AT: "Mutanen Babila sun sha kaye gaba ɗaya"
Ana magana game da mutanen Isra'ila da suke shan wahala saboda mutanen Babila kamar mutanen hatsi ne da aka sussuƙa kuma aka yi shewa.
An maimaita wannan don jaddada cewa mutumin da ke yin tambayar yana cikin damuwa da damuwa.
"Tambaye ni yanzu abin da kuke son sani, amma kuma ku dawo daga baya ku sake tambaya"
Arabiya bata da daji. AT: "Nesa nesa da hanya a cikin Arabiya" ko "A cikin dazuzzukan Arabiya"
Anan "takobi" da "baka" suna wakiltar sojojin da suka afka wa mazaunan Tema. AT: "daga abokan gabansu wadanda suka far musu da takuba da bakuna"
An yi magana game da ta'addanci da wahala da ake fuskanta yayin yaƙi kamar yaƙi ya kasance nauyi ne a kan mutane. AT: "daga munanan yaƙe-yaƙe"
"a matsayin leburin da aka yi haya zai kirga kwanakin shekara." Ma'aikacin da aka ɗauka aiki ya mai da hankali don ƙididdige ranakun domin ya yi daidai lokacin da aka biya shi don yin aiki. Wannan yana nufin za a ci Keda cikin shekara ɗaya dai-dai.
Wannan yanki ne a cikin Larabawa. Keda tana wakiltar jama'ar Keda. AT: "na mutanen Keda"
1Furci game da Kwarin Wahayi: Mene ne dalilin da ya kai dukkan ku bisan gidaje?2Shi ne domin ka ji birni cike da hargowa, birni cike da bukukuwa? Matattunka bada takobi a ka kashe su ba, kuma ba a dãgar yaƙi suka mutu ba.3Dukkan masu mulkinku sun gudu tare, amma an kamo su ba tare da an yi amfani da baka ba; dukkan su an kamo su tare, koda ya ke sun gudu nesa.4Saboda haka sai na ce, "Kada ku dube ni, zan yi kuka mai zafi; Kada ku yi ƙoƙarin ta'azantar da ni game da hallakar ɗiyar mutanena."5Gama akwai ranar hargitsi, tana tattakowa, da ruɗami domin Ubangiji Yahweh mai runduna, a Kwari na Wahayi, da rushewar ganuwoyi, da mutane suna kuka ga duwatsu.6Ilam ya ɗauki kwãri, da mahayan karusai da mahayan dawakai, Kir kuma ya ajiye garkuwa a fili.7Zai zama zaɓaɓɓun kwarurrukan ku za su cika da karusai, masu hawan dawaki kuma za su ja dãgarsu a ƙofa.8Ya ɗauke kariyar Yahuda; a cikin wannan rana ka duba kayan yaƙi a Fada wadda ke Jeji.9Kun ga tsagogin birnin Dauda, suna da yawa, ku ka kuma ɗebo ruwa daga tafki na gangare.10Kun ƙirga gidajen Yerusalem, kun fasa gidaje domin ku ƙara ƙarfin ganuwa.11kun gina wurin tãra ruwa a tsakanin ganuwowin biyu na tsohon tafki. Amma ba ku kula da wanda ya yi birnin ba, wanda ya shirya shi tun da daɗewa.12Ubangiji Yahweh mai runduna ya yi kira a wannan rana domin kuka, domin makoki, domin aske kawuna, da sanya tsummokara.13Amma duba, maimakon haka, sai buki da annashuwa, da yanka shanu da tumaki, da cin nama da shaye-shayen ruwan inabi; bari mu ci mu sha, gama gobe za mu mutu.14An bayyana mani haka a kunnuwana daga wurin Yahweh mai runduna: "Babu shakka ba za a gafarta maku wannan muguntar ba, ko kun mutu," inji Ubangiji Yahweh mai runduna.15Ubangiji Yahweh mai runduna, yace, "Jeka wurin shugaban nan, wurin Shebna, mai lura da gidan, ka ce,16"Me ka ke yi a nan, wane ne ya ba ka izini ka gina kabari domin kanka, sassaƙa kabari ya ke yi a wurare masu tsawo, yana sassaƙawa kansa wurin hutawa a cikin dutse?"'17Duba, Yahweh ya kusa jefar da kai, ƙaƙƙarfan mutum, ya kusa jefar da kai ƙasa; zai cafke ka da ƙarfi.18Ba shakka zai yi majaujawa da kai, kamar ƙwallo zai wurga ka a cikin ƙasa mai girma. Can za ka mutu, can kuma karusanka masu daraja za su kasance; za ka zama abin kunyar gidan shugabanka!19Zan tumɓuke ka daga matsayin ka daga wurin da kake aiki. Zan jawo ka har ƙasa.20Zai zama a wannan rana zan kira bawana Iliyakim ɗan Hilkiya.21Zan tufasantar da shi da alkyabbarka in ɗaura masa ɗamararka, zan maida muƙaminka a hannunsa. Za ya zama uba ga mazaunan Yerusalem da gidan Yahuda.22Zan ɗora mabuɗin gidan Dauda a kafaɗarsa; zai buɗe, kuma ba mai kullewa; zai kulle, kuma ba mai buɗewa.23Zan kafa shi, kamar ƙusa a wuri mai tsaro, zai zama mazaunin ɗaukaka domin gidan ubansa.24Za su rataya masa dukkan ɗaukakar gidan ubansa, 'ya'ya da zuriya-zuriya, kowanne ƙaramin wurin ajiya daga ƙoƙuna zuwa dukkan moɗaye.25A wannan rana - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - ƙusar da a ka kafa a wuri mai ƙarfi za ta cire, ta karye, ta kuma faɗi, nauyin dake kanta kuma zai yanke - Gama Yahweh ya furta.
A nan "kwari" yana nufin waɗanda suke zaune a kwarin, wato Yerusalem. AT: "game da waɗanda ke zaune a kwarin wahayi" ko "game da waɗanda ke zaune a Yerusalem"
Ishaya ya yi amfani da tambaya don tsawata wa mutanen Yahuda. AT: "Bai kamata ku je ku tsaya a saman gidajenku ba."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sojojin abokan gaba ba su kashe mutanenku ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "amma abokan gaba sun kame shugabanninku wadanda ba sa dauke da baka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "abokan gaba sun kame su baki daya"
Anan “diya” tana wakiltar mutane kuma tana iya nufin jin daɗin Ishaya na ƙaunarsu. AT: "na mutanena waɗanda nake ƙauna" ko "na mutanena"
"Gama akwai lokaci"
"Lokacin da Yahweh Mai Runduna zai sa tsoro, tattakewa, da rikicewa"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "mutane a cikin duwatsu za su ji kukansu" ko 2) "kukan mutane zai yi kuwwa daga tsaunuka"
AT: "Yahweh zai kwashe duk abin da ya kare mutanen Yahuda"
A nan jimlar "a duba zuwa" na nufin amincewa da wani abu. AT: "don kare kanku za ku sami makaman"
Anan "kidaya" yana nufin sun binciki gidajen don samo kayan da zai taimaka musu sake gina katangar garin.
"Kun yi wurin ajiya"
Wannan alama ce ta makoki da tuba.
Anan "ci ku sha" yana wakiltar yin liyafa da yawan cin abinci da ruwan inabi. AT: "muna iya samun nishadi yanzu ta hanyar ci da shan duk abin da muke so, don za mu mutu nan ba da daɗewa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Tabbas ba zan gafarta muku waɗannan zunuban da kuka aikata ba, ko da kuwa kun mutu"
Anan "gida" yana wakiltar waɗanda ke cikin gidan sarki. AT: "wanene ke kula da duk waɗanda ke aiki a cikin fada"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don tsawata wa Shebna. AT: "Ba ku da dama ... a cikin dutsen!"
Sojojin abokan gaba suna zuwa suna ɗaukar Shebna a matsayin bayi zuwa wata ƙasa ana maganarsu kamar Yahweh yana jefa shi kamar ƙwallo a cikin wata ƙasa.
Anan "gida" yana wakiltar mutanen da ke aiki a cikin gidan sarki. AT: "za ku ba da kunya ga duk waɗanda ke cikin gidan maigidanku"
Ana magana akan Yahweh wanda zai sa Shebna ya daina aiki a cikin gidan sarki kamar Yahweh zai jefa shi ƙasa.
"Zai faru a wancan lokacin"
Ana magana game da Yahweh da zai sa Eliyakim ya ɗauki matsayin Shebna a cikin gidan sarki kamar dai Yahweh zai sa Eliyakim a tufafin Shebna wanda ke wakiltar ikonsa a cikin gidan sarki.
Anan "mabuɗin" yana wakiltar hukuma. Wannan yana magana ne akan Eliyakim yana da ikon da babu wanda zai iya adawa dashi kamar yana da mabuɗin gidan sarauta kuma babu wanda zai iya kulle ko buɗe ƙofar. AT: "Zan sanya shi ya kula da waɗanda ke aiki a gidan sarki, kuma idan ya yanke shawara ba wanda zai iya adawa da shi"
Ana yin magana game da ikon da ke tabbatar da ikon Eliyakim a cikin gidan sarki kamar Eliyakim ɗan togo ne kuma Yahweh zai sa shi a bangon fādar.
Anan "mazaunin ɗaukaka" yana wakiltar wurin girmamawa. AT: "Eliyakim zai kawo girmamawa ga danginsa"
Wannan ya ci gaba da magana game da Eliyakim azaman peg. Zuriyarsa za su zama kamar kofunan da aka rataye a kan turmin. Wannan yana nufin za a girmama zuriyarsa saboda shi.
Ana magana akan Yahweh wanda ke sa Shebna ya rasa ikonsa a cikin gidan sarki kamar Shebna ɗan toka ne a bangon da ya karye ya faɗi ƙasa. Wannan yana nanata cewa Shebna yana tsammanin ikonsa amintacce ne amma Allah zai cire shi.
Anan “nauyi” yana wakiltar iko da ikon Shebna. Ana magana akan shi kamar wani abu ne rataye a fegi wanda yake wakiltar Shebna. Ana magana game da abin da ya sa Shebna ya rasa ikonsa da ikonsa kamar wani zai sare abin da ya rataye a kan turmin.
1Furci game da Taya: Ku yi ruri, ku jiragen Tarshish; domin babu gida ko wurin tsayawa; daga ƙasar Sifuros an bayyana masu.2Ku yi shiru, ku mazauna bakin teku; 'yan kasuwar Sidon, masu tafiya kan teku, sun cika ku.3A kan manyan ruwaye ga hatsin Shiho, girbin Nilu ne amfaninta; kuma ta zama wurin cinikin al'ummai.4Ki ji kunya, ke Sidon; gama teku ya yi magana, babba na teku. Ya ce, "Ban yi naƙuda ba ban haihu ba, ban yi renon samari ba, ban tarbiyantar da 'yammata ba."5Sa'ad da rahoton ya zo ga Masar, za su yi baƙinciki saboda Taya.6Ku haye zuwa Tarshish; ku yi kuka, ku mazauna bakin teku.7Wannan ya faru da ku ne, birni mai farinciki, wanda tushenta tun daga zamanin dã ne, wadda ƙafafunta sun kai ta can nesa zuwa bãƙin wurare ta zauna?8Wane ne ya shirya wa wannan gãba da Taya haka, mai bada rawwuna ce, wadda 'yan cinikinta yarimai ne, wanda dillalanta masu daraja ne na duniya?9Yahweh mai runduna ne ya shirya haka domin ya ƙasƙantar da girman kanta da dukkan darajarta, ya kunyatar da dukkan masu martabarta a duniya.10Ki nome gonarki, kamar mai noma a Nilu, ke ɗiyar Tarshish. Ba sauran wurin kasuwanci a Taya.11Yahweh ya kai hannunsa bisa teku, ya girgiza mulkoki; ya bada umarni game da Fonisiya, ta rushe ƙarfafan wurarensu.12Ya ce, "Ba za ki ƙara yin farinciki ba, ke mai shan tsanani ɗiyar budurwa ta Sidon; ki tashi, ki wuce zuwa Sifuros; Amma ko can ma ba za ki sami hutu ba."13Dubi ƙasar Kaldiyawa. Waɗannan mutane yanzu ba su; Asiriyawa sun maida ita daji domin dabbobin jeji. Sun kafa hasumiyoyin sansaninsu; sun rushe fãdojinta; sun maida ita tsibin kufai.14Ku yi ruri, ku jiragen Tarshish; gama an rushe mafakarku.15A wannan rana, za a manta da Taya har shekara saba'in, kamar kwanakin sarki. Bayan shekara saba'in ɗin wani abu zai faru da Taya kamar yadda ya ke a cikin waƙar karuwa.16Ɗauki molo, ki zagaya birnin, ke karuwar da a ka manta da ita; ki kaɗa su da kyau, ki yi waƙoƙi masu yawa, domin a tuna dake.17Zai zama bayan shekara saba'in, Yahweh zai taimaki Taya, za ta fara samun kuɗi ta wurin aikin karuwanci, za ta bada hidimarta ga dukkan mulkokin duniya.18Ribarta da abin da take samu za a keɓe shi ga Yahweh. Ba za a tara su ko a ajiye su a ma'aji ba, gama za a bada ribarta ga waɗanda suke zama a gaban Yahweh domin ayi amfani da su a ba su abinci isashshe saboda su sami tufafi mafi daraja.
"Wannan shi ne abin da Yahweh ya hurta a kan Taya"
Ana iya bayyana wannan jumlar a cikin tsari mai aiki. AT: "mutanen sun ji labarin Taya lokacin da suke ƙasar Sifiros"
Ishaya yayi magana da mutanen da ke zaune a bakin teku kamar zasu ji shi.
Shihor sunan wani kwari ne da ke kusa da Kogin Nilu a Masar wanda aka san shi da samar da hatsi. AT: "Mutanen sun yi tafiya a kan babban teku don jigilar hatsi daga Shihor a Masar"
“Girbin Kogin Nilu” yana nufin hatsin da aka girba a kusa da Kogin Nilu kuma aka ɗora shi a kan kogin sannan zuwa Foniciya.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Yahweh ya bayyana birnin Taya a matsayin uwa mai magana game da mutanen da ke zaune a cikin garin kamar 'ya'yanta, ko 2) Yahweh yana bayyana Bahar Rum da cewa tana magana. Mutanen Taya sun ɗauki teku a matsayin allahnsu kuma ubansu. A kowane ma'anar mai magana yana baƙin ciki saboda an lalata ɗiyanta.
"Yi hanya zuwa Tarshish." Tarshish ita ce ƙasa mafi nisa da mutanen Taya suka yi kasuwanci don kasuwanci. Zai zama kawai mafaka ga waɗanda suka tsere daga Taya.
Yahweh yana amfani da tambaya don ya yi wa Taya ba'a. Ana iya fassara waɗannan tambayoyin azaman sanarwa. AT: "Haƙiƙa wannan ya faru da ku waɗanda ke cike da farin ciki a cikin tsohon garin Taya ... ku zauna."
Anan "birni" yana wakiltar mutane. AT: "mutanen farin ciki waɗanda ke zaune a cikin garin Taya"
Anan “kambi” na nufin ikon da mutum yake da shi a matsayin mai mulkin mutane. AT: "wanda ya ba mutane iko su mallaki wasu"
Ana kwatanta 'yan kasuwa da sarakuna don jaddada yawan ikon da suke da shi lokacin da suka je ƙasashe daban-daban. AT: "wanda 'yan kasuwar sa kamar sarakuna suke"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda dillalansa mutanen duniya ke ba da girma mafi girma"
"su tozarta su saboda suna alfahari da girman kansu"
'Yar' birni tana wakiltar mutanen birni. AT: "mutanen Tarshish" ko "mutanen da ke zaune a Tarshish"
Ana magana da Yahweh ta amfani da ikonsa don sarrafa teku da mutanen masarauta masu iko kamar Yahweh ya miƙa hannunsa ya girgiza masarautu.
Anan “hannu” yana nufin ikon Allah da ikonsa. AT: "ya nuna ikonsa akan teku"
Anan "budurwa budurwa" tana wakiltar mutanen Sidon. AT: "mutanen Sidon, saboda wasu mutane za su zalunce ku"
"Kaldiyawa" a nan akwai wani suna ga mutanen Babila. AT: "Duba abin da ya faru da ƙasar Babilawa" ko "Duba abin da ya faru da Babila"
Anan “jiragen ruwa” suna wakiltar mazaje a cikin jiragen. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 23: 1.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "domin makiya sun lalata maka mafaka"
Tun da mutane ba za su ƙara zuwa Taya don sayo ko sayar da kaya ba, zai zama kamar sun manta da garin. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "shekara saba'in zai zama kamar mutane sun manta da Taya"
"kamar shekarun sarki" ko "wanda yake kusan tsawon ran sarki"
Wannan yana magana ne game da mutanen Taya kamar suna karuwa (aya 15). Kamar yadda karuwa wacce ba ta da farin jini a yanzu za ta iya raira waƙa a kan tituna don dawo da tsoffin ƙaunatattunta, mutanen Taya za su yi ƙoƙari su sa mutane daga wasu ƙasashe su dawo gare su don ci gaba da kasuwanci don mutanen Taya su zama masu arziki da iko sake.
Anan "Taya" tana wakiltar mutanen da suke zaune a Taya. AT: "Yahweh zai taimaki mutanen Taya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "'Yan kasuwa ba za su adana kuɗaɗen su ba"
"waɗanda suka yi biyayya da bautar Yahweh"
"don haka za su sami isasshen abincin da za su ci"
1Duba, Yahweh ya kusa mayar da duniya kango, ya lalata ta, ya ɓata fuskarta, ya watsar da mazauna cikinta.2Za ya zama cewa, kamar yadda ya ke da mutane, haka kuma firist; kamar yadda iyayengiji suke haka bayi za su zama, kamar yadda uwargijiya take, haka kuyangarta za ta zama, kamar yadda mai sayarwa ya ke, haka mai saye za ya zama; kamar yadda mai bada bashi ya ke, haka mai karɓar bashin za ya zama; kamar yadda mai karɓar bashi da ruwa ya ke, haka mai bada wa da ruwa.3Duniya za ta zama kango ta zama huntuwa sarai; gama Yahweh ya faɗi wannan magana.4Ƙasa za ta yanƙwane ta bushe, duniya za ta koɗe ta watse, sanannun mutane na duniya za su lalace.5Duniya ta ƙazamtu daga mazaunanta saboda sun karya dokoki, sun wofinta farillai, sun karya alƙawari na har abada.6Saboda haka, la'ana ta cinye duniya, an sami mazaunan ta da laifi. Mazauna duniya sun ƙone, mutane kuma kaɗan suka rage.7Sabon ruwan inabi ya bushe, kuringar ta yi yaushi, dukkan masu farinciki a zuciya suna nishi.8Ƙarar murna ta kacau-kacau ta ƙare, bukukuwan waɗanda suke farinciki; murnar masu garaya ta ƙare.9Ba sa shan ruwan inabi su yi waƙa, kuma barasa ta yi ɗaci ga masu shan ta.10An rushe birni mai ruɗani; an rufe kowanne gida ba kowa a ciki.11Ana kuka a kan hanyoyi saboda ruwan inabi; dukkan farinciki ya duhunta, murnar birnin ta shuɗe.12A cikin birnin sai kufai, an rushe birnin, an ɓalle ƙofarsa zuwa kango.13Domin haka zai kasance a dukkan duniya cikin al'ummai, kamar yadda a ke bugun itacen zaitun, kamar yadda a ke kãlar inabi bayan an gama girbi.14Za su tada muryoyi su yi sowa ga darajar Yahweh, kuma za su yi sowa ta murna daga teku.15Saboda haka daga gabas ku ɗaukaka Yahweh, a cikin tsibiran teku ku ɗaukaka sunan Yahweh, Allah na Isra'ila.16Mun ji waƙoƙi daga wuri mafi nisa na duniya, "Ɗaukaka ga mai tsarki!" Amma na ce, "Kaito na, na lalace, na lalace! Mazambata sun yi zamba; i, mazambata sun yi zamba ƙwarai."17Razana, da rami da tarko suna kanku, mazaunan duniya.18Shi wanda ya gudu saboda jin ƙarar razana zai faɗa rami, kuma shi wanda ya fito daga tsakiyar rami tarko zai kama shi. Tagogin sama za su buɗe, tussan duniya kuma za su girgiza.19Za a rushe duniya sarai, duniya zata tsage, duniya zata girgiza ƙwarai.20Duniya zata yi tangaɗi kamar mutum mashayi ta yi tangaɗi gaba da baya kamar bukka. Zunubinta zai yi mata nauyi zata faɗi ba zata ƙara tashi ba.21Zai zama a wannan rana, Yahweh zai hukunta rundunar sama a can sammai, sarakunan duniya kuma a duniya.22Za a tattara su tare, 'yan sarƙa a cikin rami, za a rufe su a cikin kurkuku; bayan kwanaki da yawa zai yi masu hukunci.23Sa'an nan rana zata ƙasƙanta wata kuma ya ji kunya, gama Yahweh zai yi mulki a Tsaunin Sihiyona da cikin Yerusalem a gaban dattawansa cikin daraja.
"sa duniya ta zama kufai" ko "lalata duk abin da ke cikin duniya"
Wannan jimlar tana nuna muhimmin abu. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
"wanda yake bin bashi." Kalmar "sha'awa" na nufin karin kudin da wani zai biya domin ya ciyo bashi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai lalata duniya gaba ɗaya kuma zai cire komai da kima"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. AT: "Duk abin da ke duniya zai bushe ya mutu"
Mutanen da ke yin zunubi kuma suka sa duniya ba ta zama karɓaɓɓe ga Allah ba ana maganarsu kamar mutane sun mai da duniya da jiki ƙazamta. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane sun ƙazantar da duniya"
"ba su kiyaye dokokin Allah da ƙa'idodinsa ba, kuma sun karya alkawarin Allah madawwami"
Yahweh yana la'anar duniya da hallakar da ita ana magana ne kamar la'ana ce ko dai dabbar daji da ke cin duniya gaba ɗaya ko kuma wata wuta da ta ƙone duniya gaba ɗaya.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai bayyana cewa mutane suna da laifi"
Waɗannan kayan kida ne. Duba yadda kuka fassara waɗannan a cikin Ishaya 5:12.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai rushe birnin rikicewa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane za su rufe gidajensu su bar su fanko"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. AT: "duk farin ciki zai tafi daga doron ƙasa"
Bayyanar kalmar "lalacewa" ana iya bayyana ta a matsayin "kufai" ko "wofi." AT: "Garin ya zama kango" ko "An bar garin fanko"
Wannan yana kwatanta al'ummomi bayan da Yahweh ya lalata ƙasar da bishiyoyi da inabai bayan an tsinke theira fruitan itacensu. Wannan yana nufin cewa mutane kaɗan ne za su rage a ƙasar.
Kalmomin "ɗaga muryoyinsu" magana ce da ke nufin magana da ƙarfi. AT: "Za su raira waƙa kuma su yi ihu game da ɗaukakar Yahweh"
A nan “teku” na nufin Tekun Bahar Rum wanda ke yamma da Isra’ila. AT: "kuma waɗanda ke yamma zuwa ga teku za su yi ihu da murna"
Kalmomin "a gabas" yana wakiltar mutanen da ke zaune a gabashin Isra'ila. Ishaya yana umurtan waɗannan mutane kamar suna tare dashi. Amma, yana magana da mutane a nan gaba bayan da Allah ya lalata duniya. AT: "Saboda haka kowane mutum daga ƙasashe masu nisa a gabas zai tsarkake Yahweh"
Ishaya yana ba da umarni ga mazaunan tsibirin da ke cikin Tekun Bahar Rum kamar suna tare da shi. Amma, yana magana da mutane a nan gaba bayan da Allah ya lalata duniya. AT: "kowa a cikin tsibiran zai ba da ɗaukaka"
Ishaya ya maimaita wannan maganar don ya jaddada baƙin cikin sa. Ya damu ƙwarai domin ya ga mutanen da suke yaudarar wasu kuma ba sa yin abin da suka yi alkawarin yi. AT: "Na zama mai rauni sosai"
Ishaya ya maimaita wannan maganar don ya jaddada baƙin cikin sa. AT: "Lallai, waɗanda ke yaudarar yanzu suna yaudarar wasu" ko "Lallai, masu yaudarar sun yi yaudara"
"Ku mutanen duniya za ku fuskanci firgita, rami, da tarko"
Wannan yana magana ne game da yawan ruwan sama da ke zubowa daga sama kamar Jehovah ya buɗe taga a cikin sama ya bar ruwan ya zubo. AT: "Sama za ta tsage kuma ambaliyar ruwa za ta faɗi"
Kalmar "tushe" a al'adance tana nufin tsarin dutse wanda ke ba da goyan baya ga gini daga ƙasa. Anan ya bayyana wani irin tsari wanda akayi tunanin zai tallafawa kuma ya rike duniya a matsayin. Ishaya yace hatta tsarin da zai rike duniya zai girgiza. AT: "ƙasa za ta girgiza ƙwarai" ko "za a yi mummunan girgizar ƙasa"
Ana iya bayyana waɗannan jumloli masu amfani a cikin sigar aiki. AT: "Duniya za ta tsage kuma ta tsage; duniya zata girgiza da karfi"
Waɗannan kamannin suna nuna yadda ƙasa za ta girgiza gaba da baya.
Wannan yana magana ne game da duniya kamar mutum ne kuma zalunci ya kasance abu mai nauyi. Mutum yayi ƙoƙari ya ɗauki nauyi mai nauyi amma nauyi yana sa mutum ya faɗi ya kasa tashi tsaye. Anan duniya tana wakiltar mutanen duniya ne waɗanda suka sa Yahweh ya hallaka duniya saboda zunubansu. AT: "Zunuban mutane suna da yawa kuma don haka Yahweh zai halakar da duniya, kuma ƙasa za ta zama kamar mutumin da ya faɗi ba zai iya tashiwa ba"
Mai watsa shiri sojoji ne. Anan “rundunar sama” tana nufin ruhohi masu iko da yawa a cikin sammai. Ana iya bayyana a sarari cewa su mugaye ne. AT: "halittu masu iko" ko "mugayen ruhohin"
Anan "rami" yana nufin ɗaki mai duhu ko rami a cikin kurkuku. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai tara su a matsayin fursunoninsa kuma ya kulle su a cikin kurkukun kurkuku"
An bayyana rana da wata a matsayin mutumin da yake jin kunyar kasancewa a gaban wani mai iko. A gaban Yahweh, hasken wata da na rana ba zai fi haske ba.
1Yahweh, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka, zan yabi sunanka; saboda ka yi abubuwan ban mamaki, abubuwan da a ka shirya tun dã, cikin cikakken aminci.2Gama ka mayar da birnin juji, birni mai daraja ya zama kufai, wurin zaman baƙi ya zama ba birni ba kuwa.3Saboda haka ƙarfafan mutane za su ɗaukaka ka; birnin al'ummai 'yan ta'adda zai ji tsoronka.4Gama ka zama mafaka ga wanda ya ke matalauci, mafaka ga fakirai mabuƙata - wurin fakewa daga hadari, wurin fakewa daga zafin rana. Sa'ad da hucin marasa hankali ya ke kamar haɗari mai buga bango,5kamar zafi a busasshiyar ƙasa, ka sha ƙarfin hayaniyar bãƙi, kamar yadda inuwar giza-gizai sukan sha ƙarfin zafi, haka aka amsa waƙar 'yan ta'adda.6A kan wannan tsaunin Yahweh mai runduna zai yiwa dukkan mutane liyafa da abubuwa masu ƙiba, zaɓaɓen ruwan inabi, da nama mai taushi, liyafar ruwan 'ya'yan itace.7A kan wannan tsaunin zai rushe abin da ya rufe dukkan mutane, saƙaƙƙen mayafin lulluɓe dukkan al'ummai.8Zai haɗiye mutuwa har abada, Ubangiji Yahweh zai share hawaye daga dukkan fuskoki; zai ɗauke ƙasƙancin mutanensa daga duniya dukka, gama Yahweh ya faɗe shi.9A wannan rana za a ce, "Duba, wannan shi ne Allahnmu, mun jira shi, shi kuma zai cece mu. Wannan shi ne Yahweh, mun jira shi, za mu yi murna da farinciki cikin cetonsa."10Gama a wannan tsaunin Yahweh zai ɗora hannunsa; za a tattake Mowab daga wurinsa, kamar yadda ake tattake ciyawa cikin ramin dake cike da taki.11Za su buɗe hannuwansu a tsakiyarsa, kamar yadda mai iyo ya kan buɗe hannunsa ya yi iyo.12Amma Yahweh zai ƙasƙantar da girman kansu, duk da hikimar hannuwansu. Zai rushe hasumiyoyinsu mai tsawo har ƙasa ta zama turɓaya.
Anan “suna” yana wakiltar Yahweh. AT: "yabaku"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "abubuwan da kuka tsara tun da daɗewa"
AT: "saboda ku masu gaskiya ne"
Anan "birni" da "al'ummomi" suna wakiltar mutanen da suke zaune a wurin.
Ana magana akan mutane marasa azanci da suke zaluntar mutanen Allah kamar suna hadari mai bangon bango.
Wannan yana kwatanta makiya na bayin Allah da zafin rana da ke busar da ƙasar. Wannan yana jaddada irin yadda makiya suke jawo wa mutanen Allah wahala.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kamar lokacin da gajimare ya wuce sama kuma ya shawo kan zafi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "za ku hana mutane marasa tausayi daga yin waƙa"
Anan "abubuwa masu ƙiba" na nufin mafi kyawun abinci.
Ana magana akan mutuwa, wahala, da baƙin ciki kamar dai su gajimare ne ko yanar gizo wanda ya rufe kowa da kowa a duniya.
An ambaci Yahweh yana sa mutane su rayu har abada kamar zai haɗiye mutuwa.
An ambaci Yahweh da ya sa mutane su daina jin kunya kamar kunya a matsayin wani abu da Yahweh zai cire.
“Hannu” yana wakiltar ikon Allah. Hannun Yahweh don ya ɗora a kan "wannan dutsen" yana nufin zai kare mutanensa. AT: "Karfin Yahweh zai kasance a kan dutsen" ko "Gama a kan Tsaunin Sihiyona Yahweh zai kiyaye mutanensa"
Ana magana akan hallaka Yahweh a kan mutanen Mowab kamar zai tako kansu ya murƙushe su. An kwatanta wannan da yadda mutane suka tattaka tattaka don cakuda shi da taki.
"Mutanen Mowabawa za su tunkuɗa hannayensu ta cikin taki"
Ana magana akan ya ƙasƙantar da mai girman kai kamar a ce girman kai wani abu ne mai girma kuma Yahweh zai sa ya zama ƙasa.
Wannan yana magana ne game da Yahweh yana sa sojoji su rusa ganuwar kamar shi da kansa zai rushe su. AT: "Zai aika da sojoji su kawo ganuwar kagararku zuwa ƙasa, ga ƙura"
1A wannan rana za a yi wannan waƙar a ƙasar Yahuda: Mu na da birni mai ƙarfi; Yahweh yasa ceto ya zama ganuwarsa da kagararsa.2A Buɗe ƙofofin, domin al'umma mai adalci da take riƙe gaskiya ta shiga ciki.3Wanda ya tsayar da hankalinsa a kanka, za ka riƙe shi cikin cikakkiyar salama, domin ya dogara gare ka.4Ku sa dogara cikin Yahweh, har abada; gama cikin Yah, Yahweh, dutse ne na har abada.5Gama waɗanda suke zama cikin girman kai zai ƙasƙantar da su; zai rushe tsararren birni, zai rushe shi har ƙasa; ya mayar da shi turɓaya.6Fakirai da matalauta za su tattake shi da ƙafafunsu har ƙasa.7Hanyar mai adalci an shirya ta, Mai Adalcin nan; ka shirya tafarkin mai adalci ka maishe ta miƙaƙƙa.8I, a tafarkin hukuncinka, Yahweh, za mu jira ka; sunanka da ɗabi'arka su ne marmarinmu.9Na ji marmarinka cikin dare; i, ruhuna a cikina ya neme ka da gaske. Gama sa'ad da hukucinka ya zo duniya, mazaunan duniya suna koyo game da adalci.10Bari a nuna wa mai mugunta tagomashi, amma ba zai koyi adalci ba. A cikin ƙasar masu tafiya dai-dai, shi mugunta ya ke yi kuma darajar Yahweh shi bai san ta ba.11Yahweh, an tada hannunka sama, amma su ba su lura ba, amma za su ga himmar ka domin mutane za su ji kunya, saboda wutar magabtanka za ta cinye su.12Yahweh, za ka kawo mana salama; gama hakika ka cika dukkan ayyukanmu domin mu.13Yahweh Allahnmu, waɗansu shugabanni baya ga kai sun yi mulki a kanmu; amma sunan ka kaɗai muke yabo.14Sun mutu, ba za su tsaya ba sun shuɗe, ba za su tashi ba. Hakika, ka zo cikin hukunci, ka hallaka su, ko tunawa da su ba a yi.15Ka sa al'umma ta ƙaru, Yahweh, al'umma ta ƙaru ta wurin ka; ka ɗaukaka, an darjantaka; ka faɗaɗa dukkan iyakokin ƙasar.16Yahweh, a cikin matsala suka dube ka, sai da horon ka ya zo kansu sa'an nan suka yi addu'a.17Kamar mace mai juna biyu sa'ad da lokacin haihuwar ta ya yi kusa, tana zafin ciwon naƙuda ta kuma yi kuka gare ka, haka muke a gaban ka, Ubangiji.18Muna da juna biyu, muna cikin naƙuda, amma ya zama kamar mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba, kuma mazaunan duniya ba su faɗi ba.19Matattun ka za su rayu; jukkunan su da suka mutu za su tashi. Ku farka ku raira waƙar farinciki, ku mazauna cikin ƙura; gama raɓarku raɓar haske ce, ƙasa kuma za ta fito da matattunta.20Ku tafi ku mutanena, ku shiga ɗakunanku ku rufe ƙofofi; ku ɗan ɓoye kaɗan, har sai hasalar ta wuce.21Gama, duba, Yahweh ya kusa fitowa daga wurinsa ya hori mazaunan duniya saboda muguntarsu; ƙasa za ta buɗe zubar da jinin da ta yi, ba zata ƙara ɓoye waɗanda ta kashe ba.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutanen da ke ƙasar Yahuda za su rera wannan waƙar"
Wannan yana nufin birnin Yerusalem.
Ana magana akan ikon Allah na kare da ceton mutanensa kamar cetonsa bango ne a kewayen birni.
Anan "ƙasa" tana wakiltar mutane. AT: "mutanen kirki masu aminci"
Anan "hankali" yana wakiltar tunanin mutum. Hakanan "ku" yana nufin Yahweh. Kalmomin "ya tsaya akan ku" karin magana ne. AT: "Mutumin da ke ci gaba da tunanin ku"
Ana magana akan Yahweh da yake da iko don kāre mutanensa kamar shi dutse mai tsayi ne inda mutane zasu iya zuwa don tserewa daga abokan gaba.
An ambaci Yahweh yana ƙasƙantar da masu girmankai kamar a ce masu girmankai ne, zai sa su ƙasƙantar da kai.
Duk maganganun guda biyu ma'anarsu daya. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Talakawa da wadanda ake zalunta za su tattake kangon birnin"
Yin abin da Yahweh ya hukunta daidai ne ana maganar yin tafiya akan tafarkinsa. AT: "Muna jiranka, ya Yahweh, yayin da muke ci gaba da yin abin da ka ga ya dace"
Anan “suna” da “ɗabi'arka” suna wakiltar halin Yahweh wanda yake wakiltar Yahweh da kansa. AT: "Abin da kawai muke so shi ne girmama ku"
Ana son a san Yahweh da dokokinsa sosai ana magana kamar mutum yana neman neman Yahweh. AT: "Ina matukar son in san ku sosai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ko da Yahweh mai alheri ne ga mugaye, har yanzu ba su koyon yin abin da ke daidai"
Anan "ƙasa" tana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin. AT: "A ƙasar da mutane suke aikata abin da yake dai-dai"
Anan "sani" yana wakiltar fahimtar wani abu. AT: "bai san cewa Yahweh mai girma bane"
Ana magana akan Yahweh don azabtar da mugaye kamar ana ɗaga hannuwansa kuma yana shirin buga miyagu.
"amma fãsiƙai mutane ba su lura"
Anan "gani" yana wakiltar fahimtar wani abu. AT: "za su gane cewa kuna kwazo don albarkaci mutanenku"
Ana magana game da azabtarwa da hallakar da magabtansa gaba ɗaya kamar zai aiko da wuta wanda za ta ƙone su sarai.
Anan “suna” yana wakiltar mutumin Allah. AT: "amma muna yabonka kai kaɗai"
"ba za su dawo da rai ba"
Yakan sa mutane su daina tuna waɗanda ya hallakar ana maganarsu kamar Yahweh ya sa tunaninsu ya lalace ko ya mutu.
An maimaita wannan sashin don ƙarfafawa. Anan "ƙasa" tana wakiltar mutane. AT: "Kun yawaita mutane a cikin ƙasarmu ƙwarai"
Anan "su" suna nufin mutanen Isra'ila. Wannan zai hada da Ishaya. AT: "mun dube ku"
Cikakken sunan "horo" za'a iya bayyana shi azaman kalma. AT: "lokacin da kuka hore su"
Wannan yana kwatanta mutane da mace mai haihuwa. Wannan yana jaddada wahalar su da kuka lokacin da Yahweh ya hore su.
"amma kamar dai iska kawai muka haifa" ko "kamar ba mu haifi komai ba." Wannan kamanceceniya ce da ke jaddada cewa wahalar mutane ba ta haifar da komai ba. AT: "amma ba wani abin kirki da aka samu daga gare ta"
Anan “ƙasa” tana wakiltar mutanen da suke rayuwa a duniya. Ma'anar ba tabbatacciya ce, amma kamar alama tana nufin cewa jama'ar Isra'ila' AT: Aa su iya ceton kansu ko wasu mutane ta hanyar kayar da abokan gabansu a yaƙi ba.
"kuma ba mu sanya azzaluman mutanen duniya su faɗa cikin yaƙin ba"
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda za a nuna kalmar “mutu” a matsayin kalmar ta mutu. AT: "Mutanenku da suka mutu za su sake rayuwa"
Wannan hanyar ladabi ce ta magana game da waɗanda suka mutu. AT: "waɗanda suka mutu kuma aka binne su"
"kasa za ta haifi wadanda suka mutu." An ambaci Yahweh yana sa matattu su dawo da rai kamar ƙasa za ta haifi waɗanda suka mutu. AT: "kuma Yahweh zai sa waɗanda suka mutu su tashi daga ƙasa"
Anan “nawa” yana nufin Ishaya. Har ila yau, "mutane" yana nufin mutanen Isra'ila.
Fassara sunan lakabi "fushin" azaman sifa "fushi". AT: "har sai Yahweh bai yi fushi da mu ba"
Yahweh yana bayyana duk kisan da aka yi a duniya don ya hukunta masu kisan kai ana magana ne kamar dai ƙasa da kanta za ta bayyana duk wanda aka kashe.
1A wannan rana Yahweh zai hori Lebiyatan macijin nan mai gudu da takobinsa mai girma, mai karfi, mai ban tsoro, Lebiyatan macijin nan mai tafiya a shagide, zai kashe babban dodon ruwa dake cikin teku.2A wannan rana: kuringar inabi, ta yi masa waƙa.3"Ni, Yahweh, ni ne mai kare shi; zan yi masa banruwa kowanne lokaci. zan yi tsaron sa dare da rana yadda ba wanda zai cuce shi.4Ban ji haushi ba, Oh, dãma akwai sarƙaƙiya da ƙaya! Zan far masu a filin daga in ƙone su tare duka;5sai dai idan sun nemi kariyata, sun nemi salama da ni; bari su nemi salama da ni.6A rana mai zuwa, Yakubu zai yi sauya; Isra'ila zaya bunƙasa ya yi fure; su cika sararin ƙasa da 'ya'ya."7Yahweh, ya kaiwa Yakubu da Isra'ila hari kamar yadda ya kaiwa al'umman da suka kai masu hari? An kashe Yakubu da Isra'ila kamar yadda aka kashe al'umman da suka kashe su?8Ka yi fama bisa mizanin da ya yi dai-dai, ka sallami Yakubu da Isra'ila suka tafi; ka kore su da iska mai ƙarfi sun tafi, a wannan rana ta iskar gabas.9Haka a wannan rana, za a rufe muguntar Yakubu, wannan shi ne cikakken 'ya'yan kawar da zunubi: sa'ad da zai farfasa duwatsun bagadi ya yi masu gutsu-gutsu kamar alli, ba za a sami sifofin Asheran ko bagadin turarenta a tsaye ba.10Gama birni mai ganuwa ya zama kufai, an watsar da mazauna a ciki an yashe su kamar jeji. A can ɗan maraƙi ya ke kiwo yana cin rassansa.11Sa'ad da ƙiraruwan suka bushe, za a kakkarye su. Mataye za su hura wuta da su, gama mutane ne marasa fahimta. Wanda ya yi su ba za ya ji tausayin su ba, shi wanda ya yi su ba za ya nuna masu jinƙai ba.12Rana zata zo inda Yahweh zai yi shiƙa tun daga Kogin Yuferitis har zuwa Wadi ta ƙasar Masar, ku kuma mutanen Isra'ila za a tattaro ku ɗai-ɗai da ɗai-ɗai.13A wannan rana za a busa babban ƙaho; lalatattu na ƙasar Asiriya za su zo, da yasassu na ƙasar Masar, cikin Isra'ila za su yi sujada ga Yahweh a kan tsauni mai tsarki cikin Yerusalem.
Ana magana akan Yahweh da yake da iko ya hallaka magabtansa kamar yana da ƙarfi, takobi babba.
Wannan yana nufin Lebiyatan.
"Ni, Yahweh, na tsare gonar inabin"
An fahimci cewa Yahweh ba zai sake yin fushi da mutanensa ba. AT: "Ba na fushi da mutanena kuma"
Anan Ishaya ya haɗu da hotuna daban-daban don magana akan magabtan Yahweh. Yana maganar su kamar su ƙayayuwa da ƙaya ne amma kuma kamar sojoji a cikin rundunar.
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda za'a nuna kalmar nan ta "kariya" azaman kalmar "kare." AT: "sai dai idan sun neme ni in kare su"
Wannan yana magana ne game da yini kamar yana tafiya kuma ya isa wani wuri. AT: "Nan gaba"
Yahweh yana sa mutanen Isra'ila su sami ci gaba ƙwarai don su iya taimaka wa wasu mutane ana magana akan su kamar itacen inabi ne wanda yake ba da fruita fruitan itace da yawa wanda zai iya rufe duniya.
An yi amfani da tambaya don bambanta tsananin azabar Allah. AT: "Lallai Yahweh ya hukunta al'umman abokan gaba fiye da yadda ya hukunta mutanen Isra'ila."
Wannan tambayar ita ma ana amfani da ita don bambanta tsananin azabar Allah. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh bai kashe mutanen Isra'ila kamar yadda suka kashe maƙiyansu daga wasu ƙasashe ba."
An yi magana akan ikon Yahweh na tura mutanensa zuwa wata ƙasa kamar Jehovah yana amfani da numfashinsa don busa su zuwa wata ƙasa. AT: "ikon Yahweh ya kore su kamar iska mai ƙarfi daga gabas"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai kankare zunubin daga Isra'ilawa" ko "Yahweh zai gafarta zunuban Isra'ilawa"
Wannan yana magana ne game da sakamakon aiki kamar dai 'ya'yan itacen da ke girma kamar bishiya ko itacen inabi. AT: "sakamakon"
Anan "shi" yana nufin Yakubu wanda yake wakiltar zuriyarsa. AT: "Za su rurrushe duka bagadan da suke miƙa hadaya ga gumakan ƙarya, za su kuma kawar da gumakan Asheran da bagadan da suke ƙona turare ga gumakan ƙarya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Garuruwan da suke da ƙarfi kuma suna da mutane da yawa a cikinsu zasu zama fanko kamar hamada"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Lokacin da rassa suka bushe, mata za su zo su fasa su kuma kunna wuta tare da su"
Duk sassan jumlar abu daya suke nufi. AT: "Saboda ba su fahimta ba, Yahweh, wanda ya yi su, ba zai yi musu jinƙai ba"
An yi maganar AT yana tattara mutanensa don ya dawo da su daga baƙi zuwa ƙasar Isra’ila kamar yana sussukar alkama don ware hatsi da ƙaiƙayi.
Ishaya ya ambaci Kogin Yuferitis da Kogin Masar don nufin cewa Yahweh zai dawo da mutanen Isra’ila da aka kai su bautar talala a ƙasashe kusa da waɗancan ruwa, wato Asiriya da Masar. Kogin Yuferitis yana arewa maso gabashin Isra'ila, kuma Wadi na Masar yana kudu maso yammacin Isra'ila.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wani zai busa ƙaho da ƙarfi"
Ana iya bayyana bayanan da aka fahimta sarai. AT: "waɗanda ke gudun hijira kuma suke mutuwa a ƙasar Asiriya da ƙasar Masar za su koma ƙasar Isra'ila"
1Kaiton rawanin girman kai na fure da kowanne mashayan Ifraim ke sanye da shi, kyaun darajarsu na dushewa kamar yadda kyaun fure ke dushewa, haka ma rawanin dake kan waɗanda suka bugu da ruwan inabi a Kwari mai tãki, inda ruwan inabi ya rinjayi wasu!2Duba, Ubangiji yana aiko da wani babba, kuma ƙaƙƙarfa; kamar hadari mai ƙanƙara, da iska mai lalatarwa, kamar ruwan sama mai kwararowa da ambaliyar ruwaye; zai jefar da kowanne rawanin fure a ƙasa.3Masu rawanin girman kai na fure mashaya na Ifraim za a tattake a ƙarƙashin sawu.4Furen ɗaukakarsa mai ƙyau, dake kan kwari mai arziki, zai zama kamar nunannen ɓaure na fãri da damuna, zai zamana, sa'ad da wani ya dube shi, tun yana hannunsa, zai haɗiye su.5A ranar nan Yahweh mai runduna zai zama rawani mai daraja da kambi mai kyau ga sauran mutanensa da suka rage,6ruhun adalci ga mahukunta, ƙarfi kuma ga waɗanda suka kori abokan gãba daga ƙofofinsu.7Amma har ma waɗannan suna tangaɗi da ruwan inabi mai ƙarfi. Da firist da annabi suna tangaɗi da ruwa mai ƙarfi, ruwan inabi ya haɗiye su. Suna tangaɗi da ruwan inabi mai ƙarfi, suna tangaɗi a wahayi da rashin sanin abin yi.8Hakika duk teburorin sun ƙazantu da haraswa, har ma babu tsabtaccen wuri.9Su waye zai koya wa sani, kuma ga suwa zai fasara saƙon? Ga waɗanda aka yaye daga nono, ko kuma waɗanda a ka cire daga mama?10Gama doka ce bisa doka, doka bisa doka; ka'ida bisa ka'ida; nan ɗan-kaɗan can ɗan-kaɗan.11Hakika, da leɓunan ba'a da kuma bãƙon harshe zai yiwa mutanen nan magana.12A dã ya ce masu, "Wannan shi ne hutu, a bada hutu ga wanda ya gaji; wannan shi ne wartsakewa ɗin," amma ba za su kasa kunne ba.13Haka maganar Yahweh za ta zama ma su doka bisa doka, doka bisa doka; ka'ida bisa ka'ida, ka'ida bisa ka'ida; nan ɗan kaɗan, can ɗan kaɗan; domin su tafi da baya su faɗi, a karya su, a sa masu tarko, a kama.14Ku saurari maganar Yahweh, ku masu ba'a, ku da ke mulki bisa waɗannan mutane dake Yerusalem.15Wannan zai faru domin kun ce, "Mun yi alƙawari da mutuwa, da muka ƙulla yarjejeniya. Saboda haka lokacin da babbar bulala mai bin kan kowa zata ratsa, ba zai iso wurin mu ba. Gama mun mai da ƙarya mafaƙarmu, mun sami mafaka a rumfa cikin ƙarya."16Saboda haka Ubangiji Yahweh yace, "Duba: Zan kafa harsashin dutse a Sihiyona, dutsen da aka jaraba, dutsen kusurwa mai daraja, tabbataccen harsashi, duk wanda ya gaskata ba za ya kunyata ba.17Zan sa gaskiya ta zama sandar gwaji, adalci kuma igiyar awo. Ƙanƙara za ta share mafaƙar ƙarairayi, kuma rigyawa zai sha kan maɓuya.18Za a tada alƙawarin ku da mutuwa, yarjejeniyar da ku ka ƙulla da Lahira za a soke. Sa'ad da rigyawa mai ruri ke wucewa, za a sha kanku.19Duk lokacin da za su wuce, za su sha kanku, daga safiya zuwa safiya za su yi ta aukowa, kuma dare da rana za su wuce kuma da rana da dare zai zo. Sa'ad da aka fahimci saƙon, zai sa firgita.20Gama gadon ya gajarce da mutum ya miƙe a bisansa, bargon kuma bashi da fãɗin da zai isa ya rufe kansa."21Yahweh zai miƙe kamar a kan Dutsen Ferazim, zai tashi kansa kamar a cikin Kwarin Gibiyan domin ya yi aikinsa, bãƙon aikinsa, ya kuma yi bãƙon aikinsa.22Saboda haka kada ku yi ba'a, domin kada a karfafa sarƙarku. Na ji daga wurin Ubangiji Yahweh mai runduna, dokar hallaka a kan duniya.23Ku natsu ku saurari muryata; ku natsu ku saurari maganganuna.24Manomin dake huɗa dukkan rana domin shuka, ya kanyi huɗar ƙasar ne kawai? Zai yi ta huɗa ne kawai yana fasa ƙasa?25Lokacin da ya shirya ƙasar, ba yakan yafa tamba ba, ya warwatsa riɗi, sai ya sa alkama a jere, da bali a inda ya kamata, da kuma wasu irin a gefuffuka?26Allahnsa yana gaya masa abin yi; yana koya masa da hikima.27Bugu da ƙari 'ya'yan tamba ba a sussukasu da haƙoran ƙarfe, ba a kuma bin kan riɗi da tayar karusa; amma akan buga tamba da 'gora, riɗi kuma da sanda.28Akan niƙa tsaba domin abinci amma bada laushi ba, koda shike ƙafafun kekensa dana dawakansa sukan warwatsar da shi, dawakansa ba sa murƙushesu.29Wannan ma daga Yahweh mai runduna ya ke fitowa, shi kuwa mai al'ajibi ne a cikin bishewa mafifici cikin hikima.
"waɗanda suka bugu da giya"
Anan "ɗaya" yana nufin sarki mai ƙarfi wanda shima yake wakiltar rundunarsa mai ƙarfi. AT: "Ubangiji ya aiko sarki tare da rundunarsa mai ƙarfi"
Ana magana da sarki da rundunarsa mai ƙarfi da ke hallaka mutanen Samariya da birni kamar dai sarki zai jefar da gwal ɗin mutane a ƙasa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sojojin abokan gaba za su murkushe masu girman kai na Samariya kamar suna murkushe furanni a ƙafafunsu"
Wannan yana magana ne game da sojojin abokan gaba da suka ga kyan Samariya kuma suka washe shi da sauri kamar dai su mutane ne waɗanda suka ga ɓaure na farko a lokacin kuma suka cinye shi da sauri.
Ana magana da Yahweh kamar dai zai zama kyakkyawan rawanin da mutanen da suka girmama shi kamar sarkinsu na gaske za su saka.
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda za a nuna alamun suna "adalci" da "ƙarfi" azaman siffofi. Waɗannan kalmomin na iya fara sabon jumla. AT: "Yahweh zai sa alƙalai su zama masu adalci kuma zai sa su ƙarfafa waɗanda suke"
Anan "juya baya" kalma ce da ke nufin kayar da yaƙi. AT: "Yahweh zai sa sojoji su yi ƙarfi don su ci magabtansu a lokacin da abokan gaba suka kawo hari garinsu"
Wannan baya nufin takamaiman firist ko annabi. Yana nufin firistoci da annabawa gaba ɗaya. AT: "Firistoci da annabawa"
Shan su sosai da ba za su iya yin tunani yadda ya kamata ba ana maganar su kamar giya ta haɗiye su. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "giya tana haifar musu da rudani"
Kamar yadda suke maye da yawa don yin tafiya daidai, sun bugu sosai don fahimtar wahayin da Allah ya ba su ko yanke shawara mai kyau.
Manyan annabawa da firistoci sun yi amfani da tambaya don sukar Ishaya, wanda yake ƙoƙarin gyara su. AT: "Manyan annabawa da firistoci sun ce," shouldIsaya bai kamata ya koya mana saƙon saƙon Yahweh ba!"
Manyan annabawa da firistoci sun yi amfani da tambaya don sukar Ishaya, saboda suna jin cewa yana bi da su kamar jarirai.AT: "Bai kamata ya dauke mu kamar jarirai ba!"
A nan “leɓɓa” da “harshe” suna wakiltar baƙi waɗanda suke magana da wani yare dabam da na Isra’ilawa. An nuna cewa wannan yana nufin sojojin Asiriya da za su kawo wa Isra'ila hari. AT: "Yahweh zai yi magana da wannan mutanen ta hanyar sojojin abokan gaba wadanda za su yi magana da wani baƙon harshe"
Cikakken sunan "hutawa" za a iya bayyana shi azaman sifa ne. AT: "Nan ne wurin hutawa"
Ana iya bayyana kalmar 'hutawa' azaman aiki. AT: "bari duk wanda ya gaji ya zo ya huta"
Waɗannan su ne kalmomin da mashaya firistoci da annabawa suka kasance suna sukar yadda Ishaya yake koya musu. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 28:10.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "domin sojojin Asiriya su zo su fatattake su kuma su kama su a matsayin fursunoni"
Duk waɗannan maganganun suna nufin abu ɗaya ne. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) shugabannin Yerusalem sun yi amfani da sihiri ko sihiri don ƙoƙarin yin yarjejeniya da gumakan wurin matattu don waɗannan alloli su tsare su daga mutuwa ko 2) wannan kwatanci ne da yake magana game da shugabannin sun yi yarjejeniya da shugabannin Masar. Shugabannin Yerusalem suna da kwarin gwiwa cewa Masarawa za su kare cewa kamar sun yi yarjejeniya da gumakan wurin matattu.
Wannan yana magana ne game da hukuncin Yahweh da azaba kamar dai bulala ce da zata buge mutane. Kuma ana magana da bulala kamar ambaliyar ruwa ce da za ta ratsa Yerusalem. AT: "A sakamakon haka, lokacin da kowa yake wahala da mutuwa, babu abin da zai cutar da mu"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Ana maganar “karya” da “ƙarya” kamar dai su wurare ne da mutum zai iya zuwa ya ɓoye. Shugabannin Yerusalem ba za su ce sun dogara da ƙarya ba. Sun yi imanin cewa suna cikin aminci da gaske. Amma Ishaya ya san ba su da lafiya, saboda sun dogara da ƙarairayi. AT: "Don ƙarya da ƙarairayi sun zama kamar wurin da za mu iya ɓoyewa daga haɗari"
Ana magana akan aiko Yahweh kakkarfa don taimaka wa Isra'ilawa kamar dai Yahweh yana gina tushe mai ƙarfi don gini.
"Duk wanda ya dogara ga wannan dutsen kafuwar ba zai yi nadama ba"
Gwajin Yahweh bisa ga adalcinsa da adalcinsa don sanin idan mutane masu adalci ne kuma ana magana da su kamar shi magini ne ta amfani da kayan aiki don ƙaddara cewa wani abu daidai yake daidai kuma dai-dai yake.
Wannan yana magana ne game da "karya" kamar dai su wurare ne da mutum zai iya zuwa ya buya. Suna wakiltar abin da shugabannin Yerusalem suka dogara da shi don kiyaye su daga azabar Yahweh. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) shugabanni su amince da ƙarairayin da suka faɗa don kare kansu ko 2) shugabanin sun amince cewa alkawarin da suka yi da gumakan ƙarya na wurin matattu zai kiyaye su ko 3) shugabannin sun aminta da cewa yarjejeniyar da suka kulla tare da Masarawa zai basu kariya. Duba yadda kuka fassara makamancin kalmar a cikin Ishaya 28:15.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan warware alkawarin da kuka yi da mutuwa, kuma zan soke yarjejeniyar da kuka yi da Lahira"
Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) "ambaliyar ruwa" synecdoche ne wanda ke wakiltar komai gaba ɗaya wanda zai haifar da hallaka ko 2) "ambaliyar" kwatanci ne da ke nuni ga sojojin abokan gaba da Yahweh zai aiko don halakar da mutanen Yerusalem.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "zai mamaye ku" ko "zai hallaka ku"
Wataƙila wannan karin magana ne da mutane suka sani a lokacin. Yana nufin cewa abin da suka yi imani zai kiyaye shi daga azabar Yahweh zai ɓata musu rai kamar gado da ya yi gajere sosai ko kuma bargo da ke kunkuntar.
Waɗannan suna nufin wuraren da Allah ya ci nasara bisa sojojin abokan gaba ta mu'ujiza.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya. Wannan aikin baƙon abu ne domin Allah yana amfani da sojojin ƙasashen waje don fatattakar mazaunan Yerusalem maimakon ya taimaki mutanen Yerusalem su fatattaki abokan gaba.
An yi magana game da azabtar da mutanen har ma da tsananin azaba kamar zai ɗaure igiyoyinsu. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai ƙara ɗaure ku" ko kuma "Yahweh zai yi muku horo mafi tsanani"
AT: "cewa zai hallaka mutane ko'ina cikin ƙasar"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya dai-dai. Ana amfani da jimla ta biyu don ƙarfafa ta farko.
Ishaya yayi amfani da tambayoyin magana don sa mutane suyi tunani sosai. AT: "Manomi ba ya huɗa ƙasa a kai a kai kuma yana ci gaba da aikin ƙasa ba tare da ya taɓa shuka iri ba."
"Lokacin da manomi ya huɗa ƙasa"
Ishaya yayi amfani da tambaya don sa mutanen Yerusalem suyi tunani sosai. Idan yarenku bashi da kalma ga kowane ɗayan waɗannan, ana iya bayyana su gaba ɗaya. AT: "tabbas zai shuka kowane nau'in iri a madaidaiciyar hanya kuma a wuraren da suka dace."
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. AT: "Yahweh yana taimaka wa manomi ya san yadda zai kula da kowane irin shuka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "manomi ba ya raba ƙwaya ta tamba da shuka da kulki mai nauyi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kuma baya birgima mai taya a kan kwayar kumin"
Ishaya ya bayyana madaidaiciyar hanyar da manomi zai iya raba iri da shukar. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "amma ya doki tamba da sanda, kuma ya doke kumin da sanda"
Wannan ya kammala misalin da aka fara a cikin Ishaya 28:23. Darasin da ke cikin kwatancin ya nuna cewa manoma suna da hikima don sauraron umarnin Yahweh game da shuka da kuma sussuka. Amma shugabannin Yerusalem wawaye ne don ba su saurari umarnin Yahweh da yake magana ta bakin Ishaya.
1Kaiton Ariyel, Ariyel birnin da Dauda ya kafa zango! A ƙara shekara kan shekara; bari bukukuwa su kewayo.2Amma zan kafa wa Ariyel dãga, zata yi ta makoki da kururuwa; kuma zata zamar mani kamar Ariyel.3Zan kafa dãga gãba dake in kewaye ki, zan yi maki kwanto gãba dake da kuma soro, zan kafa wuraren faƙo gãba dake.4Za a jawo ki ƙasa za ki yi magana daga ƙasa; muryarki zata dushe a cikin ƙura. Muryar ki zata zama kamar ta ruhu dake fitowa daga ƙasa, maganar ki kuma zata zama rarrauna daga cikin ƙura.5Yawan masu kawo maki hari za su zama kamar 'yar ƙura, ɗunbin mugayen nan kamar dusa dake wucewa. Zai faru, ba zato ba tsammani, farat ɗaya.6Yahweh mai runduna zai zo maki, da tsawa, da raurawar ƙasa, da ƙara mai tsanani, da babbar iska, da gawurtaccen hadari, da harshen wuta mai hallakarwa,7Zai zama kamar mafarki, wahayi da dare: Taron dukkan al'ummai za su yaƙi Ariyel da kagararta. Za su hare ta da ita da garunta domin su matsa mata.8Zai zama kamar lokacin da mayunwacin mutum ya ke mafarki yana cin abinci, amma da ya farka, cikininsa ba komai. Zai zama kamar lokacin da wani mutum yana jin kishin ruwa, sai ya yi mafarki yana shan ruwa, amma lokacin da ya farka, yana suma, kishin ruwansa ba a kashe ba. I, haka zai zama ga dukkan al'umman da za su yaƙi Dutsen Sihiyona.9Ku jiwa kanku mamaki, ku kuma yi mamaki; ku makantar da kanku, ku zama makafi! Ku bugu, amma bada ruwan inabi ba, amma bada giya ba.10Gama Yahweh ya kwararo maku ruhun barci mai nauwi. Ya rufe maku idanu, ku annabawa, ya lulluɓe kawunanku, masu gani.11Dukkan wahayi ya zamar maku kamar maganganun littafin da a ka kulle, wanda mutane za su ba masani, su ce, "Karanta wannan." Shi kuma zai ce, "Ba zan iya ba gama an kulle."12Idan an bada littafin ga wanda bai iya karatu ba, cewa,"Karanta wannan," zai ce, "Ban iya karatu."13Ubangiji yace, "Waɗannnan mutane suna kusatowa gare ni da bakunansu, suna kuma girmamani da leɓunansu, amma zuciyarsu tana nesa da ni. Girman da suke ba ni na dokokin mutane ne da a ka riga a ka koya.14Saboda haka, duba, zan ci gaba in yi abin ban mamaki cikin mutanen nan, al'ajibi kan al'ajibi. Hikimar masanansu zata lalace kuma fahimtar masu tattalinsu zasu ɓace."15Kaiton waɗanda suke ɓoye wa Yahweh shirye-shiryensu, waɗanda ayyukansu suke cikin duhu. Suna cewa, "Wa ke ganinmu, wa kuma ya san mu?"16Kuna juya abubuwa na sama zuwa ƙasa! Za a kwatanta mai ginin tukwane kamar yumɓu, har da abin da a ka yi zai ce game da wanda ya yi shi, "Ba shi ya yi ni ba," ko abin da a ka sarrafa ya cewa wanda ya sarrafa shi, "Bai fahimta ba"?17A ɗan lokaci kaɗan, za a maida Lebanon fili, filin kuma zai zama kurmi.18A ranar nan kurma zai ji maganganun littafi, idanun makafi kuma za su gani daga cikin duhu baƙiƙƙirin,19Waɗanda a ka murƙushe za su sake yin murna a cikin Yahweh, matalauta kuma a cikin mutane za su yi farinciki cikin Mai Tsarkin na Isra'ila.20Gama miyagu za su ƙare, masu ba'a za su ɓace. Za a datse dukkan masu ƙaunar aikata mugunta,21waɗanda ta wurin magana su kan maida mutum mai laifi. Suna kafa tarko ga mai neman a yi mashi adalci a ƙofa su kuma kãda mai adalci da holoƙan ƙarairayi.22Saboda haka ga abin da Yahweh ya faɗi game da gidan Yakubu - Yahweh wanda ya fanshi Ibrahim, "Yakubu ba zai ƙara jin kunya ba, ko kuma fuskarsa ta turɓune.23Amma sa'ad da zai dubi 'ya'yansa, aikin hannuwana, za su tsarkake sunana. Za su tsarkake sunan Mai Tsarki na Yakubu za su kafu cikin tsoron Allah na Isra'ila.24Waɗanda suka ɓata cikin ruhaniya za su sami fahimta, masu gunaguni za su koyi ilimi."
Anan "Ariyel" yana wakiltar mutanen da suke zaune a cikin garin Ariyel. AT: "Kaiton abin da zai kasance ga mutanen Ariyel"
"Dauda ya zauna" ko "Dauda ya rayu"
"Ku ci gaba da yin bikinku shekara da shekara." Wannan magana ce ta izgili. Yahweh ya gaya wa mutane su ci gaba da yin bukukuwan idinsu a inda suke miƙa masa hadaya, amma ya san hakan ba zai hana shi hallaka su ba.
Kalmomin "makoki" da "kururuwa" ma'anarsu abu ɗaya ne da kuma jaddada tsananin baƙin ciki. AT: "za su yi baƙin ciki sosai"
Kalmar "zan" tana nufin Yahweh. Wannan yana wakiltar Yahweh ne wanda ya sa sojojin abokan gaba suka kewaye Yerusalem. AT: "Zan umarci sojojin magabtanku su kewaye ku"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Maƙiyinka zai saukar da kai" ko "Maƙiyinka zai ƙasƙantar da kai"
Duk waɗannan maganganun suna nufin abu ɗaya ne. Suna jaddada cewa mutanen da suka taɓa yin magana da kalmomin alfahari za su kasance masu rauni da baƙin ciki bayan abokan gaba sun ci su da yaƙi. AT: "za ku iya magana ne kawai da rada da rauni kamar ruhun da ke magana daga inda matattu suke zaune"
"sojoji da yawa da zasu kawo muku hari"
Mai fassara na iya samar da kalmar aikatau "za ta zama." AT: "sojojin da ba su nuna muku jinƙai ba za su zama kamar ƙaiƙayi"
Kalmar "ku" tana nufin mutanen Yerusalem. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Yahweh Mai Runduna zai zo ya taimake ku" ko 2) "Yahweh Mai Runduna zai zo ya azabtar da ku."
Maganar "hangen nesa na dare" daidai yake da "mafarki." Kalmomin guda biyu suna jaddada cewa ba da daɗewa ba zai zama kamar runduna mai mamaye ba ta taɓa kasancewa ba.
Kalmar "ta" tana nufin Ariel wanda yake wakiltar mutanen da ke wurin. AT: "sansaninsu. Za su afkawa garin Ariyel da kariyarta kuma su sa mutane su kasance cikin tsananin damuwa"
Anan "Dutsen Sihiyona" yana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin. AT: "Ee, wannan zai kasance abin da zai faru ga sojoji daga al'ummomin da ke yaƙi da mutanen da ke zaune a kan Dutsen Sihiyona"
Kalmar "kanku" tana nufin mutanen Yerusalem. Dalilin da yasa suke mamakin za'a iya bayyana su a sarari. AT: "Ka yi mamakin abin da zan gaya maka"
Mutanen da ba su kula da abin da Yahweh ya faɗa ana maganarsu kamar suna makantar da kansu. AT: "ci gaba da kasancewa jahilai da ruhaniya ga abin da nake nuna muku"
Mutane suna rashin hankali da rashin fahimtar abin da Yahweh yake yi, ana maganarsu kamar suna maye. AT: "Ku zama marasa azanci kamar mashayi, amma ba don kun sha giya da yawa ko giya ba"
Anan "ruhun" yana nufin "a sami halayyar" bacci. Ana magana game da Yahweh mai sa mutane suyi bacci kamar "ruhun" wani ruwa ne da ya zubo kan mutane. Hakanan "bacci mai nauyi" kwatanci ne wanda yake nufin mutanen basu da hankali kuma basa iya fahimtar abin da Yahweh yake yi. AT: "Dalilin da yasa ba ku da hankali shi ne saboda Yahweh ya sa ku barci cikin ruhaniya"
Sauran annabawan da ke Yerusalem sun kasa ji ko fahimtar saƙon Allah. AT: "Duk abin da Yahweh ya bayyana shine a gare ku kamar littafin da aka hatimce"
Ana iya bayyana wannan azaman sabon jumla. AT: "an hatimce. Mutum na iya ɗaukar littafin da aka hatimce ga wanda zai iya karantawa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Idan mutum ya kai littafin ga wanda ba zai iya karantawa ba"
Kalmomin "bakin" da "lebe" suna wakiltar abin da mutane ke faɗi. Anan ma yana wakiltar faɗin wani abu amma ba ma'anarsa da gaske ba. AT: "Mutanen Yerusalem suna nuna kamar suna bauta mani kuma suna girmama ni da abin da suke faɗi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Suna girmama ni ne kawai saboda abin da mutane ke gaya musu su yi"
"Saboda haka, ku duba ku gani! Zan aikata abubuwan al'ajabi a cikinku, ba za ku iya bayaninsu ba"
Duk wadannan maganganun guda daya suke nufi. Yahweh yana nuna cewa mutane masu hikima ba zasu iya fahimta ko bayyana abin da Yahweh yayi ba ana magana akan su kamar dai hikimarsu da fahimtarsu zata shuɗe.
Mutanen da suke ƙoƙarin yin shiri ba tare da Yahweh sun sani ba ana maganarsu kamar suna ɓoye shirye-shiryensu a cikin wani wuri mai zurfi inda Yahweh baya iya gani. AT: "waɗanda suke ƙoƙarin ɓoye shirinsu daga Yahweh" ko "waɗanda suke ƙoƙarin hana Yahweh gano abin da suke shirin yi"
Ana nuna cewa suna aikata mugunta a ɓoye. AT: "waɗanda ke aikata mugunta a cikin duhu don haka ba wanda zai iya ganin su"
Wannan karin magana ne da ke nufin gurbata gaskiya. AT: "Kuna yin abubuwa sabanin yadda ya kamata su kasance" ko "Kun karkatar da gaskiya"
Ana amfani da wannan tambayar don tsawata wa mutanen Yerusalem. AT: "A bayyane yake, bai kamata a ɗauki maginin tukwane kamar yumɓu ba ... 'Bai fahimta ba.'"
Anan "Lebanon" tana wakiltar manyan dazuzzuka na itacen al'ul a cikin Lebanon. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah zai juya manyan gandun daji na Lebanon zuwa gona"
Mai yiwuwa ma'anoni sune 1) wannan a zahiri kuma Yahweh zai sa kurma su ji kuma makafi su gani ko 2) wannan kwatanci ne wanda ke nufin Yahweh zai sa mutane su ji kuma su fahimci saƙonsa ko 3) yana iya nufin duka zaɓuɓɓukan 1 da 2. (Duba: fiigs_metaphor)
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya dai-dai. AT: "Talakawa da waɗanda ake zalunta za su sake yin farin ciki saboda abin da Yahweh, Mai Tsarki na Isra'ila ya yi"
Za a iya bayyana karin magana na ɗan lokaci "marasa tausayi" a matsayin sifa. AT: "Ga mutane marasa tausayi za su gushe" ko "Gama ba za a sake zama azzalumai mutane ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai kawar da duk waɗanda suke son aikata mugunta"
Wannan yana nufin bayar da shaida a kotu game da wani. AT: "wanda ya ba da shaida a kan mutum kuma ya sanya shi ya zama mai laifi" ko "wanda ya ce a kotu cewa mutumin da ba shi da laifi ya yi laifin yin wani abu ba daidai ba"
Wannan yana iya nufin lokacin da Yahweh ya kira Ibrahim daga ƙasarsa kuma ya aike shi zuwa ƙasar alkawari.
Anan “hannaye” suna wakiltar ikon Yahweh da aikinsa. AT: "Lokacin da suka ga dukkan yaran da na ba su da duk abin da na yi"
Anan “suna” yana wakiltar Yahweh. Yahweh yana kiran kansa "Mai Tsarki na Yakubu." AT: "Za su girmama ni, Mai Tsarki na Yakubu"
Anan “ruhu” yana wakiltar yanayin mutum. AT: "Waɗanda suka yi kuskure cikin abin da suke tunani" ko "Waɗanda ba su da kyau a halayensu"
1"Kaiton 'ya'yan tawaye," wannan ne furcin Yahweh. Suna shirye-shirye, amma ba daga gare ni ba; suna ƙulla yarjejeniya da wasu al'ummai, amma ba Ruhuna ya bishe su ba, saboda haka suna ƙara zunubi kan zunubi.2Sun kama hanya su gangara zuwa Masar, amma ba su nemi bishe wa daga gare ni ba. Suna neman kariya daga Fir'auna, sun nemi mafaƙa a inuwar Masar.3Saboda haka kariyar Fir'auna zata zama abin kunyarku, fakewa a inuwar Masar, zai zama ƙasƙancinku,4koda shike hakimansu suna Zowan, jakadunsu sun iso Hanes.5Dukkansu za su ji kunya domin mutanen da ba za su iya taimakonsu ba, waɗanda ba taimako ba ne ko tallafawa, amma abin kunya ne, har ma abin ƙasƙanci."6Furci game da dabbobin Negeb: Cikin ƙasar wahala da hatsari, da zakanya da kuma zaki, da kububuwa da miciji mai dafi yana shawagi, su kan labta arzikinsu bisa jakkai, da kayayyakinsu masu daraja bisa doron raƙuma, su kaiwa mutanen da ba za su iya taimaka masu ba. Gama taimakon7Masar na banza ne; Saboda haka na kirata Rahab, wadda ta zauna shuru.8Yanzu ka tafi, ka rubuta shi a gabansu a kan allo, ka maka shi a kan allon fata, domin a adana shi da kyau saboda lokaci mai zuwa ya zama shaida.9Gama mutanen nan 'yan tawaye ne, 'ya'ya maƙaryata, waɗanda ba za su ji umarnin Yahweh ba.10Sukan cewa masu duba, "Kar ku gani," ga kuma annabawa, "Kada ku faɗa mana annabcin gaskiya; ku faɗa mana maganganun wãsawa, annabcin ruɗami,11Kun kauce daga hanya, kun saki tafarki; kun sa Mai Tsarkin na Isra'ila ya daina magana a fuskarmu."12Saboda haka Mai Tsarki na Isra'ila yace, "Domin kun ƙi wannan magana, kun dogara ga zilama da ruɗi, kun jingina gare shi,13saboda haka wannan zunubi zai zamar maku kamar ɓangaren shashe dake shirin faɗuwa, kamar curi a kan bango mai tsayi wanda faɗuwarsa zata zo nan da nan, farat ɗaya."14Zai fasa shi kamar yadda tukunyar magini ke farfashewa; ba zai ƙyale ta ba, don kada a sami cikin farfasassun koda ɗan kaskon da za a ɗauko ɗan garwashin wuta daga sauran garwashin, ko a kwarfo ruwa daga cikin randa.15Gama wannan shi ne Ubangiji Yahweh, Mai Tsarki na Isra'ila yace, "Cikin komowa da hutu za ku tsira; cikin natsuwa da dogara ƙarfin ku zai tabbata. Amma ba ku yarda ba,16Kuka ce, 'A a, za mu gudu a kan dawakai,' haka za ku gudu; kuma, 'Za mu hau kan dawakai masu zafin gudu,' haka masu bin ku za su yi sauri.17Dubu za su gudu a tsoratawar mutum ɗaya; a tsoratawar biyar za ku gudu har sai sauranku da suka rage sun zama kamar sandar tuta a kan tsauni, ko kamar 'yar tuta a kan tudu."18Duk da haka Yahweh yana jira ya yi maku alheri, saboda haka a shirye ya ke ya nuna maku jinƙai. Gama Yahweh Allah ne mai adalci; masu albarka ne dukkan waɗanda suke jiransa.19Gama waɗansu mutane za su zauna a cikin Sihiyona, cikinYerusalem, ba za su ƙara yin kuka kuma ba. Hakika zai yi maku alheri da ya ji ƙarar kukan ku. Idan ya ji shi, zai amsa maku.20Koda shike Yahweh yana ba ku gurasar wahala da ruwan matsaloli, haka kuma, malaminku ba zai ƙara ɓoye kansa ba, amma za ku ga malamin ku da idanunku.21Kunnuwan ku za su ji magana a bayan ku, cewa, "Wannan ita ce hanya, yi tafiya a cikinta," sa'ad da kuka juya zuwa dama ko kuka juya zuwa hagu.22Za ku tozartar da sassaƙaƙƙun siffofin ku da a ka dalaye da azurfa da kuma sarrafaffun siffofinku na zinariya. Za ku zubar da su kamar ƙazamtattun tsunmokaran al'ada. Za ku ce masu, "Ku fita daga nan."23Zai bada ruwan sama domin iri lokacin da kuka yi shuka a ƙasa, da gurasa tare da yalwa daga ƙasa, amfani kuma zai zama da yawa. A ranar nan shanunku za su yi kiwo a makiyaya mai fãɗi.24Shanun noma da jakkai, da suke huɗa, za su ci gyararren abinci wanda aka sheƙe da cebur da matankaɗi.25Bisa kowanne dogon tsauni, da bisa kowanne dogon tudu, za a sami maɓuɓɓugai da rafuka masu gudanar da ruwa, a ranar gawurtaccen kisa sa'ad da hasumiyoyi za su faɗi.26Hasken wata zai zama kamar hasken rana, hasken rana zai ninka sau bakwai, kamar hasken kwana bakwai. Yahweh zai ɗaure karayar mutanensa ya warkar da ƙujewar raunin da ya yi masu.27Duba, sunan Yahweh ya zo daga wuri mai nisa, yana ƙũna da fushinsa kuma a cikin turmuƙin hayaƙi. Leɓunansa suna cike da zafi, harshensa kuma na kama da wuta mai cinyewa.28Numfashinsa yana kama da ambaliya wanda ruwansa ya kai har tsakiyar wuya, domin ya rairaye al'ummai da matankaɗin hallakarwa. Numfashinsa linzami ne a muƙamuƙan mutane yasa su warwatse.29Za ku sami waƙa da dare sa'ad da kuke biki mai tsarki, da murna a zuciya, kamar yadda wani zai tafi da sarewa bisa tsaunin Yahweh, zuwa ga Dutsen Isra'ila.30Yahweh zai sa aji muryarsa mai daraja, ya nuna motsin hannunsa cikin zafin fushinsa da harshen wuta, tare da guguwa, hadari, da ƙanƙara.31Gama da jin muryar Yahweh, Asiriyawa za su razana; zai fyaɗe su da sanda.32Kowanne dukkan sanda da Yahweh ya ƙaddara masu za a bi bayansa da waƙoƙin tambura da molo sa'ad da ya ke yaƙi da faɗa da su.33Domin an shirya wurin ƙũna tuntuni. Hakika, an shirya shi domin sarki, Allah ya shirya shi da zurfi da kuma faɗi. Tarin kuwa a shirye ne da wuta da kuma itace da yawa. Numfashin Yahweh, kamar rafin ƙibiritu ne da zai cinna masa wuta.
Yahweh yana magana akan mutanensa kamar su yayansa.
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda ba za a iya bayyana ma'anar “tsare-tsaren” azaman kalmar “shiri” ba. AT: "Suna shirin yin abubuwa, amma ba sa tambayar ni abin da nake so su yi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "amma Ruhuna bai bishe su ba"
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda za'a nuna kalmar nan ta "kariya" azaman kalmar "kare." AT: "Suna roƙon Fir'auna ya kare su"
AT: "Saboda haka za ku ji kunya saboda kun dogara ga Fir'auna don ya kare ku; za a wulakanta ku saboda kun dogara ga Masarawa don kiyaye ku"
Ana maganar kariyar Masar daga sojojin abokan gaba kamar inuwa ce wacce ke kare wani daga zafin rana.
Wannan yana nufin waɗannan nau'ikan dabbobi gaba ɗaya. AT: "inda zakin zaki da zakuna ke zaune, kuma inda macizai da macizai suke"
Akwai shahararrun labarai game da dodo mai suna Rahab. Sunan Rahab na nufin "ƙarfi" ko "girman kai." AT: "Ina kiran Masar mai girman kai mai girma wanda ba ya yin komai"
Wannan yana magana ne game da lokaci kamar yana tafiya kuma ya isa wani wuri. AT: "na nan gaba"
Wannan yana magana ne game da mutanen Yahweh kamar yaransa ne. Ana iya fassara wannan azaman sabuwar jumla. AT: "Suna nuna kamar yara ne waɗanda suke yin ƙarya kuma basa jin abin da Yahweh ya umurta"
Yadda Yahweh yake son mutanensa su yi magana ana magana ne kamar wata hanya ce ko tafarki da za su bi. Ana magana akan rashin biyayya ga Yahweh kamar dai mutumin ya kauce daga hanyar Yahweh.
"kun ƙi wannan saƙon"
Mai yiwuwa ma'anonin su ne 1) shugabannin Yahuda sun dogara ga shugabannin Masar waɗanda ke mulki ta hanyar zalunci da yaudarar wasu ko 2) shugabannin Yahuda sun zalunci kuma sun yaudari mutanensu don su karɓi kuɗinsu su aika wa Masarawa shugabanni a matsayin biyan bashin kariya.
Wannan misalin yana nufin cewa Allah zai halakar da mutanen Yahuza ba zato ba tsammani saboda zunubansu.
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda za'a nuna kalmar nan ta "faduwa" azaman kalmar "faduwa". AT: "hakan zai fado kwatsam"
Anan "shi" yana nufin ɓangaren da ke shirin faɗuwa. Bangaren bango kwatanci ne wanda yake wakiltar mutanen Yahuda da zunubin da aka ambata a cikin Ishaya 30: 12-13.
Wannan misalin yana nufin cewa guntun bango zai farfashe da sauri kuma gaba ɗaya kamar tulun yumɓu wanda ya faɗi ƙasa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "babu wanda zai iya samu" ko "ba za a samu ba"
Ana magana akan tuba kamar a wajan Yahweh yake komawa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan cece ku daga abokan gabanku idan kuka tuba kuma ku huta da sanin cewa zan kula da ku"
Natsuwa a nan tana nufin rashin damuwa da damuwa. Ana nuna cewa basu damu ba saboda sun dogara ga Yahweh. AT: "Za ku yi ƙarfi idan kun yi shuru kuma kuka dogara gare ni"
An fahimci kalmar "mai warwarewa". AT: "Sojoji dubu zasu tsere saboda barazanar sojan makiyi guda daya; saboda barazanar sojojin abokan gaba guda biyar dukkan sojojinku zasu gudu"
Wannan misalin yana nufin cewa mutane kadan zasu rage wanda zasu zama kamar tuta ɗaya a saman tsauni.
"zai taimake ka"
Anan "gurasa" da "ruwa" sun zama abincin mai talauci. Duk jimlar tana wakiltar mawuyacin lokaci da talaucin mutane.
Anan “idanu” suna wakiltar mutum dukka. AT: "ku da kanku za ku ga malaminku"
Ana magana akan rashin biyayya ga Yahweh kamar dai mutum ya juya hagu ko dama daga hanyar Yahweh.
Wannan misalin yana nufin zasu watsar da gumakan su kamar datti.
Wannan yana maganar gumaka kamar zasu ji kuma su tashi su bar wani wuri. Yahweh yana nufin cewa mutane ba za su ƙara buƙata ko son gumakan ba.
Anan “gurasa” tana wakiltar abinci ne gaba ɗaya. AT: "zai sa ƙasa ta samar muku da wadataccen abinci da za ku ci"
An yi amfani da manyan shafuka da cokula masu yatsu don jefa hatsi a iska don iska za ta kwashe ƙaiƙayi, ta bar ɓangaren da za a ci. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda kuka sheka da shebur da fulawa"
"Lokacin da Yahweh ya karkashe maƙiyanku ya kuma sa hasumiyarsu masu ƙarfi su fado"
"rana za ta haskaka kamar rana bakwai" ko "rana za ta bayar da haske a rana guda kamar yadda ta saba yi a cikin kwanaki bakwai"
Yahweh yana ta'azantar da mutanensa kuma yana kawo ƙarshen wahalar su ana magana ne kamar zai sa bandeji akan raunukan su.
Anan “suna” yana wakiltar Yahweh. AT: "Yahweh ya zo"
A nan “leɓɓa” da “harshe” kalmomi ne masu wakiltar Yahweh yana magana. Kuma, Yahweh yana magana da tsananin fushi da ƙarfi wanda ake magana da shi kamar harshensa wuta ne. AT: "Lokacin da yake magana fushinsa kamar wuta ce da ke lalata komai"
Wannan yana kwatanta iskar da ke fitowa daga bakin Yahweh zuwa ambaliyar don jaddada ikon lalata ta.
Yahwehwanda yake da iko ya sa shirin mutane ya kasa ko kuma sa su a halaka ana magana akan shi kamar numfashin sa kamar birki ne wanda yake kange mutane daga madaidaiciyar hanya.
Ana iya sake amfani da wannan don haka kalmar "waƙa" ta bayyana azaman kalma. AT: "Za ku raira waƙa"
Wannan magana ya nuna yadda mutane za su yi farin ciki.
Anan “zuciya” tana wakiltar yanayin mutum. AT: "za ku yi murna"
Ana magana akan Yahweh da yake da iko ya kare mutanensa kamar dutse ne wanda mutane zasu hau kuma su tsere daga abokan gaba. AT: "zuwa dutsen kariya na Isra'ila" ko "wanda yake kamar dutsen kariya ne ga Isra'ila"
Anan “hannu” yana wakiltar ikon Allah. An nuna cewa Yahweh zai nuna ikonsa ta hanyar hallaka magabtan mutanensa. AT: "ku nuna cewa yana da iko ta hanyar hallaka makiyanku"
Ana magana da fushin Yahweh kamar hadari ne ko wuta. AT: "cikin fushi wannan kamar hadari ne da harshen wuta" ko "cikin tsananin fushi"
"tare da hadari cike da iska, ruwan sama, da ƙanƙara"
Ishaya yayi magana game da tsoron Asirya kamar Asiriya wani abu ne wanda muryar Yahweh ta ragargaje. AT: "Asiriya za ta firgita"
An yi magana game da Yahweh wanda zai sa sojoji su ci Asiriya kamar Yahweh zai buge Asiriyawa da sanda.
An yi magana game da Yahweh wanda zai sa sojojin abokan gaba su ci Asiriyawa kamar Yahweh jarumi ne wanda zai yi yaƙi tare da sojojin abokan gaba.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Tun da daɗewa Yahweh ya shirya wuri don ƙonawa"
An nuna cewa wannan yana nufin sarkin Asiriya. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya shirya shi don sarkin Asiriya"
Wannan yana magana ne game da numfashin Yahweh kamar dai kogin wuta ne wanda zai kunna tsibin wuta.
1Kaiton waɗanda suke gangarawa zuwa Masar domin neman gudummuwa suna jingina ga dawakai, suna dogara ga karusai, (domin suna da yawa), da kuma mahayan dawakai (domin sun zarce ƙididdiga). Amma ba su damu da Mai Tsarki na Isra'ila ba, ba su kuma neman Yahweh!2Duk da haka yana da hikima, zai kuwa kawo masifa ba zai janye maganarsa ba. Zai tashi gãba da gidan mugunta, gãba kuma da kai gudummuwa ga masu aikata zunubi.3Masar mutum ne ba Allah ba, dawakansu kuma jiki ne ba ruhu ba. Lokacin da Yahweh zai miƙar da hannunsa, dukka da wanda ya yi gudummuwar zai yi tuntuɓe, wanda kuma a ka yiwa gudummuwar zai faɗi; su biyun za su hallaka tare.4Ga abin da Yahweh yace mani, "Kamar yadda zaki, har ma ɗan zaki ya kan yi ruri a kan dabbar da ya kashe, sa'ad da a ka kira ƙungiyar makiyaya a kansa, amma ba ya rawar jiki saboda muryoyinsu, ko ya sulale domin ƙararsu; haka Yahweh mai runduna zai sauko ya yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona, a kan tudun nan.5Kamar tsuntsaye masu shawagi bisa sheƙarsu, haka Yahweh mai runduna zai tsare Yerusalem; zai tsare ya kuma cece ta sa'ad da ya ke wuce wa bisanta ya kare ta.6Ki komo wurinsa shi wanda kika juya nesa daga gare shi, mutanen Isra'ila.7Domin a cikin wannan rana kowanne zai jefar da gumakansa na azurfa da gumakansa na zinariya wanɗanda hannuwanku ne cikin zunubi suka yi su.8Asiriya zata faɗi da kaifin takobi, takobin da ba mutum ne ya ke wurgawa ba zata hallaka shi. Zai gujewa takobi, matasanta za su yi aikin tilas.9Za su karai saboda razana, sarakunansu za su tsorata idan sun ga tutar yaƙin Yahweh - wannan furcin Yahweh ne - wanda wutarsa ke cikin Sihiyona, tanderun wutarsa kuma tana cikin Yerusalem.
Ana amfani da kalmar "sauka" a nan saboda Masar tana ƙasa da Hawan sama da Yerusalem.
Duba yadda kuka fassara wannan sunan a cikin Ishaya 1: 4.
Anan kalmar "kawo" na nufin "haddasawa." AT: "zai haifar da bala'i"
Anan Masar tana nufin sojojin Masar. AT: "Sojojin Masar mutane ne"
Wannan yana magana ne game da mutanen da suka dogara da dawakansu don taimaka musu kamar suna dogaro ne akan dawakansu. AT: "dogaro ga dawakansu"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Yin tuntuɓe da faɗuwa kalmomi ne na gazawa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "waɗannan abubuwa biyu zasu faru: Zan hallaka Masar, wanda ya taimake ku, kuma zan halakar da ku, wanda Masar ta taimaka"
"zaki ko mace mai zaki." Wannan maimaitawa ce tare da duka kalmomin suna nufin zaki mai zafin gaske. AT: "zaki"
Kalmomin "an yi kira akansa" na nufin a aika shi ya kori zaki. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da wani ya aika makiyaya su kori zaki"
Dukansu jimlolin suna magana ne kan Dutsen Sihiyona. AT: "a kan Dutsen Sihiyona"
A nan an kwatanta yadda Yahweh yake kāre Yerusalem da yadda uwa tsuntsu take kāre tsuntsaye jariransu a cikin gidansu.
Wannan yana magana ne akan yadda Yahweh yake kiyayewa da tseratar da Yerusalem, yana mai bayyana shi a matsayin tsuntsayen da ke shawagi akan garin. AT: "zai kare da kuma ceton garin daga abokan gaba"
"Ku koma zuwa ga wanda kuka yi wa tawaye"
1Duba, wani sarki zai yi sarauta cikin adalci, yarimai kuma za su yi mulki da gaskiya.2Kowanne ɗayansu zai zama kamar wurin faƙewa daga iska da kuma mafaka daga hadari, kamar rafukan ruwa a ƙeƙasasshiyar ƙasa, kamar inuwar babban dutse a ƙasar gajiya.3Sa'an nan idanun waɗanda suke gani ba za su dushe ba, kuma kunnuwan waɗanda suke ji za su ji sarai.4Mai saurin baki zai yi tunani da kyau tare da ganewa, mai nauyin baki kuma zai yi magana da kyau da sauƙi kuma.5Ba za a ƙara kiran wawa nagari ba, ko a ce da mayaudari mai aminci.6Domin wawa yakan faɗi wauta, zuciyarsa takan shirya mugunta da mugayen ayyuka, yana kuma faɗar ƙarya akan Yahweh. Yakan tsiyatar da mayunwata, masu jin ƙishirwa kuma ya sa su rasa abin sha.7Dabarun mayaudari mugaye ne. Yakan ƙago mugayen shirye-shirye, domin ya lalatar da matalauta da ƙarairayinsa, koda matalaucin ya faɗi abin dake dai-dai.8Amma nagarin mutum yakan yi shiri nagari; kuma saboda nagargarun ayyukansa zai tsaya.9Ku tashi, ku matan dake zaman sake, ku saurari murya ta; ku 'ya'ya mata 'yan ba ruwanmu, ku saurare ni.10Gama nan gaba kaɗan da shekara guda ƙarfin halinku za a karya, ku mata masu zaman sake, gama ba za a sami girbin inabi ba, kuma ba amfanin da za a tattara a rumbuna.11Ku yi rawar jiki don tsoro, ku mata masu zaman sake; ku yi damuwa, ku masu ƙarfin hali; ku tuɓe ƙyawawan tufafinku, ku tsirance kanku; ku ɗaura tsummokin makoki a kwankwasonku.12Za kuyi kururuwa domin gonakinku masu yalwa, da inabinku masu 'ya'ya.13Ƙasar mutanena zata cika da ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya, har ma a cikin dukkan gidaje da aka taɓa yin farinciki a birnin bukukuwa.14Gama za a yasar da fãda, birnin mai cincirindon mutane zai koma kango; da tudu da benen tsaro za su zama kogonni har abada, abin murna ga jakan jeji, wurin kiwo domin garkuna;15har sai an kwararo Ruhu a kanmu daga bisa, jeji kuma ya zama gonaki masu bada amfani, gonaki masu bada amfani kuma su zama kamar kurmi.16Sa'an nan hukunci za ya kasance a jeji; adalci kuma ya kasance a gonaki masu amfani.17Aikin adalci zai zama salama; sakamakon adalci, kwanciyar hankali da gabagaɗi har abada.18Mutanena za su zauna a cikin mazauni na salama, a cikin tsararrun gidaje, da natsattsun wuraren hutawa.19Amma koda an yi ƙanƙara ko kuma jeji duk ya ƙone, aka kuma rushe birnin gaba ɗaya,20ku da kuka yi shuka a bakin rafuffuka za a albarkace ku, da dukkan ku da kuke aika shanunku da jakai su yi kiwo.
Wannan yana kwatanta sarki da hakimai waɗanda ke kare mutane da mafaka. AT: "masu mulki za su kare mutane kamar yadda matsuguni yake yi a cikin hadari"
Wannan wani kwatancen ne da yake nuna cewa masu mulki zasu biya bukatun mutane. AT "za su tanadar wa mutane kamar magudanan ruwa a cikin busasshen wuri"
Wannan wani kwatancen ne da ke nuna cewa masu mulki zasu samarwa mutane ta'aziyya da hutu. AT: "za su samar wa mutane hutu kamar yadda babban dutse ke ba inuwa ga mutanen da suka gaji"
Ishaya ya ci gaba da bayanin mutane bayan Allah ya dawo da masu mulki na gaskiya a cikin Yahuda
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki.AT: "Ba wanda zai ba wawa wa girma"
Anan ana ambaton wawa daga zuciyarsa don jaddada tunanin cikin sa. AT: "yana shirya mugayen abubuwa a cikin zuciyarsa"
"Matalauta" yana nufin talakawa. Har ila yau, kalmar "lalata" ba tana nufin kashe su ba ne illa cutar da su ta hanyar yin ƙarya game da su. AT: "cutar da talakawa ta hanyar yin karya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Hakanan, Ishaya yayi magana game dasu basu da ƙarfin gwiwa kamar yardarsu abubuwa ne na zahiri da ya karye. AT: "ba za ku ƙara kasancewa da tabbaci ba"
Wannan yana nufin cewa babu 'ya'yan inabi masu kyau da za a girba. AT: "ba za ku sami 'ya'yan inabi da za ku girba ba"
Anan "tsirara" ba lallai bane ya zama tsiraici, amma don sanya ƙaramin sutura kamar su kayan ciki. AT: "cire maka kyawawan tufafi ka sanya kanka ba tufafi" ko "cire tufafi masu kyau"
Wannan wani aiki ne na bakin ciki ko makoki. AT: "sanya tsummoki a kugu kugu yayin da kuke baƙin ciki"
Wannan yana nufin cewa za su yi kuka da ƙarfi yayin da suke baƙin cikin abin da ya faru ga gonakinsu masu amfani da inabi. AT: "Za ku yi kuka saboda abin da ya faru ga filayenku masu daɗi da inabai masu amfani"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Don mutane za su watsar da fadar kuma taron za su watsar da garin"
Wannan yana magana ne game da kagara da gidan kallon da aka watsar kamar sun zama kogo. AT: "tsauni da gidan kallo za su zama fanko"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "har sai Yahweh ya zubo da Ruhu"
Waɗannan jimlolin guda biyu daidai suke kuma duka suna ba da sakamakon adalci. Wadannan za a iya hade su. AT: "Sakamakon mutane na yin adalci shi ne za a sami kwanciyar hankali, da nutsuwa, da amincewa har abada"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "yana lalata daji kuma yana lalata garin gaba ɗaya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Wannan yana nufin albarkar Yahweh ga dukan mutanensa kuma yana magana akan abubuwan da ya dace mutanensa suyi. AT: "Yahweh zai albarkace ku, yayin da kuka dasa amfanin gonarku a gonaki kusa da rafuffuka kuma yayin da kuke aika sa da jakinku don su yi kiwo a makiyaya"
1Kaiton ka, mai ɓatawa ba a ɓata ka ba! Kaiton ka mai cin amanar waɗanda ba su ci amanarka ba! Lokacin da ka bar ɓatawa, za a ɓata ka. Lokacin da ka daina cin amana, za a ci amanar ka.2Yahweh, ka yi mana alheri; muna jiranka; ka zama damtsenmu kowacce safiya, cetonmu kuma a lokacin wahala.3Da jin ƙararka mai amo mutanen suka gudu; lokacin da ka tashi, al'ummai sai su watse.4Akan tara ganimarka kamar yadda fãri ke taruwa, kamar yadda fãri ke tsalle haka mutane ke tsalle a kanta.5Daukaka ga Yahweh, yana zaune a mafificin wuri. Zai cika Sihiyona da gaskiya da adalci.6Shi zai zama kafuwarmu a lokatanki, ceto a yalwace, hikima, da ilimi; da tsoron Yahweh shi ne dukiya mai tamani.7Duba, manzannin suna kuka a tituna; 'Jakadun masu begen salama, suna kuka mai zafi.8An yasar da karabku; ba bu sauran matafiya. Ana ta tada alƙawari, an wofintar da shaidu, kuma ba nuna bangirma ga ɗan adam.9Ƙasar tana makoki, duk ta yi yaushi; Lebanon ta kunyata ta kuma yi yaushi; Sharon kamar ƙasar filin hamada take; Bashan kuma da Kamel sun kakkaɓe ganyayensu.10"Yanzu ne zan tashi," inji Yahweh; "Yanzu ne za a ɗagani sama; yanzu za a fifita ni.11Kun ɗauki cikin ƙai-ƙai, kun haifi ciyawa; numfashinku wuta ce da zata cinye ku.12Mutanen za a ƙona su su zama danƙo, kamar yadda a ke sassare sarƙaƙƙiya a ƙone ta.13Ku da kuke nesa, ku ji abin da na yi; kuma ku da ke kusa, ku shaidi ƙarfina."14Masu zunubi a Sihiyona sun tsorata; makyarkyata ta kama marasa tsoron Allah. Wane ne a cikin mu zai iya zama da wuta mai ruruwa? Wane ne a cikin mu zai iya zaunawa da madawwamin ƙone-ƙone?15Shi wanda ya ke tafiya bisa adalci yana magana da gaskiya; wanda ke ƙin ribar zilama, yana ƙin karɓar toshi, ba ya shirye-shiryen ta'addanci; ba ya duban mugunta -16zai kafa gidansa a kan tuddai; Mafaƙarsa zai zama kagarar duwatsu; zai dinga samun abincinsa da ruwan shansa a kan kari.17Idanunku za su ga sarki cikin jamalinsa; za su ga babbar ƙasa.18Zuciyarka zata tuna da razanar da ta faru; ina magatakarda, ina mai auna kuɗi? Ina ya ke mai ƙididdiga hasumiyoyi?19Ba za ku ƙara ganin mutanen nan masu tawaye ba, mutane masu baƙon harshe, waɗanda ba ku fahimce su ba.20Dubi Sihiyona, birnin bukukuwanmu; idanunku za su ga Yerusalem kamar mazauni mai lafiya, rumfar da ba za a kawas ba, ƙusoshin ta ba za a tumbuƙe su ba, kuma igiyoyinta ba za a katse su ba.21Maimakon haka, Yahweh cikin daraja zai kasance tare damu, a wuri mai manyan koguna da rafuffuka. Ba jirgin ruwan yaƙi da zai bi ta cikinsa, ba kuma manyan jiragen da za su bi ta wurin.22Domin Yahweh ne alƙalinmu, Yahweh ne mai bamu shari'a; Yahweh ne sarkinmu; shi zai cece mu.23An kwance maɗaurinka, ba za su iya riƙe tirken tutar jirgin ruwa da ƙarfi ba; ba za su iya baza tutar jirgin ruwa ba; sa'ad da za a raba babbar ganima, har gurgu ma zai sami rabo.24Mazaunan wurin ba za su ce, "Ba ni da lafiya ba," mutanen dake zaune a can za a gafarta zunubansu.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda wasu ba su halakar ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wasu za su hallaka ku"
Wannan yana nufin duk ranar, ba kawai safiya ba. AT: "kowace rana"
Wannan yana nufin lokutan da suke fuskantar matsala. AT: "" lokacin da muke da matsala "
Mai yiwuwa ma'anonin "babbar kara" sune 1) yana nufin muryar Yahweh. AT: "Mutane suna gudu saboda sautin babbar muryarku" ko 2) tana nufin manyan sautunan sojojin Yahweh. AT: "Mutanen suna gudu saboda sautin rundunan sojojinku"
Ana iya rubuta wannan ta hanyar aiki. AT: "al'ummai sun watse"
Wannan yana kwatanta irin saurin da mutanen Yahweh suke da shi yayin da suka tara ganima daga abokan gaba zuwa ga farin fara yayin da suka tara abinci. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutanenku suna tara ganima daga abokan gaba da tsananin zafin nama kamar yadda fara ta ke wanda ke cinye tsire-tsire masu tsire-tsire"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya fi kowa"
Wannan yana maganar Yahweh yana mulkin Sihiyona da adalcinsa da adalcinsa kamar yana cika Sihiyona da gaskiya da adalci. AT: "Zai mallaki Sihiyona da gaskiya da adalci"
Wannan yana magana ne game da Yahweh yana sa mutanensa su sami tsaro kamar dai shi ne kwanciyar hankali da kansa. Jumlar "zamaninku" tana nufin rayuwarsu. Madadin fassara: "Zai sanya ku amintattu a duk rayuwarku"
Wannan yana magana ne game da tsoron Yahweh kamar wata taska ce da Yahweh ya ba mutanensa. AT: "juyawa Yahweh zai zama kamar wata babbar dukiyar da zai ba ku" ko "jin tsoron Yahweh zai kasance muku da daraja kamar taska"
Wannan yana nufin suna kuka saboda ba su yi nasarar yin sulhu ba. AT: "jami'an diflomasiyyar suna fatan zaman lafiya amma ba su yi nasara ba don haka suke kuka mai zafi"
Dukkanin jumlolin suna jaddada cewa babu matafiya akan manyan hanyoyi. Wadannan za a iya hade su kuma a bayyana su cikin tsari. AT: "Mutane ba su yin tafiya a kan manyan hanyoyi"
Wannan nassi na iya nufin ishara ga yanayin lalacewar Isra’ila, ko kuma tana iya nufin kasawar al’ummar ta kulla yarjejeniyoyin zaman lafiya da Asiriya. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane suna karya alkawarin da suka yi, mutane suna watsi da shaidar shaidu, kuma mutane ba sa girmama juna"
Wannan yana maganar ƙasar ta bushe kamar dai mutum ne yake makoki. AT: "ƙasar ta bushe kuma shuke-shuke nata bushewa"
Anan "Lebanon" tana wakiltar bishiyar Lebanon. Wannan yana magana ne akan bishiyoyi suna bushewa kuma suna ruɓewa kamar suna mutumin da yake jin kunya. Madadin fassara: "Itatuwan Lebanon suna bushewa kuma suna lalacewa"
Anan Bashan da Karmel suna wakiltar bishiyoyin su. AT: "babu sauran ganye akan bishiyun a cikin Bashan da Karmel"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna nanata cewa ana ɗaukaka Yahweh. AT: "yanzu zan daukaka kaina kuma na nuna cewa na cancanci kowa ya girmama ni"
Wannan yana maganar Asiriyawa suna yin shiri kamar suna daukar ciki kuma suna haihuwar shirinsu kamar yadda uwa take haihuwar jariri. Wannan yana magana ne game da shiryeshiryensu marasa amfani ta hanyar kwatanta su da ƙaiƙayi. AT: "Kuna yin shiryeshiryen da ba su da amfani kamar ƙaiƙayi da ciyawa"
Wannan yana kwatanta yadda mutane za a kone gawawwakin kamar yadda ake kona ƙaya. Haka nan, ana iya bayyana wannan a cikin sigar aiki. AT: "Wuta za ta ƙone mutane gawarwakin zuwa lemun tsami kamar yadda manomi yana sare ƙaya kuma ya ƙone su "
Yahweh yana amfani da kalmomin "can nesa" da "kusa" yana nufin duka mutane. Ana iya bayyana kalmar "ƙarfin" da sifa "mai girma." AT: "Duk mutane ko'ina suna jin abin da na yi kuma sun yarda cewa ni mai iko ne"
Wannan yana magana ne akan mutane marasa tsoron Allah suna rawar jiki kamar suna rawar jiki abokan gaba ne da suka kama su. AT: "marasa tsoron Allah suna rawar jiki" (Duba: personification)
Wadannan tambayoyin na magana suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa babu wanda zai iya rayuwa tare da wuta. Anan wuta tana wakiltar hukuncin Yahweh. AT: "Ba wanda zai iya rayuwa tare da wutar zafi! Babu wanda zai iya rayuwa tare da ƙonewa madawwami!" ko "Ba wanda zai iya rayuwa yana ɗaukar hukuncin Ubangiji, yana kama da wuta madawwami!"
Anan tafiya tana nufin zama. AT: "Wanda ya rayu"
Za a iya nuna kalmar jumlar "ribar zalunci" azaman kalmar magana. AT: "wanda ya ƙi dukiyar da ke zuwa daga cutar wasu mutane"
Ana kiran rigunan sarauta da "kyawunsa." AT: "sarki a cikin kyawawan tufafi"
Wannan yana nufin masu sauraro ta hanyar "zukatansu." "Ta'addancin" yana nufin yakin su da Asiriyawa. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Za ku tuna da ta'addancin da Asiriyawa suka yi muku lokacin da suka kawo hari"
An yi wannan tambayar don jaddada cewa jami'an Asiriyawa sun tafi. Wadannan tambayoyin ana iya rubuta su azaman maganganu. AT: "Jami'an Assuriya wadanda suka kirga kudin harajin da aka tilasta mana mu biya su sun bace! Wadannan mutane da suka kirga hasumiyarmu sun tafi!"
Wannan yana nufin cewa suna da idin su da idin su a wannan garin. AT: "garin da muke da idodinmu" ko "garin da muke yin bukukuwanmu"
Wannan yana magana ne akan Sihiyona amintacce kuma ya tabbata kamar ya kasance amintaccen rumfar ne. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki kuma a rubuce azaman sabon jumla. AT: "zai kasance amintacce, kamar alfarwar da ba wanda zai taɓa cirewa"
Wannan wani ɓangare ne na kwatancin da ya kwatanta Sihiyona da amintaccen rumfar Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda tasirinsa ba wanda zai taɓa cirewa kuma igiyarsa ba wanda zai taɓa fasawa"
Wannan yana nufin Ishaya kuma ya haɗa da mutanen Yahuda.
Mai iya yiwuwa: 1) Sojojin Assuriya kamar jirgin ruwa ne wanda ba zai iya motsawa ta cikin ruwa ba: igiyoyin da ke tallafawa mast da jirgin ruwa sun kwance kuma sun daina tallafawa mashin, don haka jirgin ɗin bashi da wani amfani Ishaya 33: 1 ko 2) mutanen Yahuda ba sa cikin yaƙi: "Kun kwance igiyoyin da ke goyan bayan tambarinku; tutar ba ta ƙara tashi".
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da suka raba taskar"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai gafarta zunuban mutanen da suke zaune a wurin"
1Ku matso kusa, ku al'ummai, ku saurara; ku natsu, ku mutane! Duniya da dukkan cikarta dole su saurara, duniya, da dukkan abin da ke fitowa a cikinta.2Gama Yahweh yana fushi da dukkan al'ummai, da hasala ga dukkan rundunar yaƙin su; ya hallakar da su gaba ɗaya, ya bashe su ga yanka.3Za a jefar da gawawwakin matattunsu waje. Warin gawawwakin su zai bazu ko'ina; duwatsu kuma za su shanye jininsu.4Dukkan taurarin sama za su dushe, za a naɗe sammai kamar naɗaɗɗen littafi; dukkan taurarinsu za su dushe, kamar yadda ganyayen inabi suke karkaɗewa su faɗi daga itacen, kuma kamar yadda nunannun ɓaure ke faɗuwa daga jikin itacensa.5Sa'ad da takobina ya sha ya ƙoshi a sama; duba, yanzu zai gangara a kan Idom, akan mutanen da na keɓe domin hallakarwa.6Takobin Yahweh na ɗiɗɗigar da jini da kitse, tana ɗiɗɗigar da jinin 'yan raguna da na awaki, rufe da kitsen ƙodojin raguna. Gama Yahweh yana da hadaya a Bozra da kuma babban yanka a ƙasar Idom.7Za a kashe bijiman jeji tare da su, ƙananan bijimai tare da manyansu. Ƙasarsu za ta bugu da jini, ƙurarsu za ta yi ƙiba da kitse.8Gama zata zama ranar sãkayya ga Yahweh da shekarar kuma da zai sãka masu sabili da Sihiyona.9Kogunan Idom za a mai da su baƙin danƙo, ƙurarta kuma ta zama ƙibiritu, ƙasarta kuma ta zama baƙin danƙo mai cin wuta.10Zata ci wuta dare da rana; hayaƙinta zai tashi sama har abada; daga tsara zuwa tsara zata zama yasasshiyar ƙasa; ba wanda zai ratsa ta tsakiyarta har abada abadin.11Tsuntsaye jeji da dabbobi za su zauna a wurin; mujiya da hankaka za su yi sheƙar su a cikin ta. Kamar yadda mai gini ya ke amfani da igiyar gwaji haka zai auna ƙasar domin rusarwa da hallakarwa.12Ba za a bar wa shugabaninta komai da za su kira masarauta ba, kuma dukkan hakimanta ba za su zama komai ba.13Ƙayayuwa za su cika fãdodinta, tsidau da dundu a wuraren tsaronta. Zai zama mazaunin diloli, farfajiyar jiminai.14Dabbobin jeji da kuraye za su tattaru a can, awakan jeji za su kira junansu da kuka. Dabbobin jeji masu yawon dare za su tare a nan su kuma samar wa kansu wurin hutawa.15Mujiyoyi za su yi sheƙa, za su nasa ƙwayayensu su ƙyanƙyashe, su ƙyanƙyashe su kuma tsare 'yan ƙananansu. I, a can hankaki za su taru, kowanensu da abokin tarayyarsa.16Ku binciko daga naɗaɗɗen littafin Yahweh; ba ko ɗayansu da za a rasa. Ba wanda zai rasa ɗan'uwan tarayyarsa; gama bakinsa ya umarta shi, ruhunsa kuma ya tattara su.17Ya jefa ƙuri'a domin mazaunansu, hannunsa kuwa ya auna masu shi da igiya. Za su mallaketa har abada; daga tsara zuwa tsara za su zauna a can.
Wannan shine na biyu na jimloli guda biyu masu layi daya. Ana iya samar da kalmomin da aka fahimta a cikin wannan jumlar. AT: "duniya, da duk abubuwan da suka zo daga gare ta dole ne su saurara"
Sau da yawa annabawa suna magana akan abubuwan da zasu faru a nan gaba kamar dai sun riga sun faru. Wannan ya jaddada taron tabbas zai faru. AT: "zai hallaka su gaba daya, zai ba da su ga yanka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba wanda zai binne mamatan su"
"Za a rufe duwatsu cikin jininsu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Wannan yana kwatanta abin da Yahweh zai yi a sama ga mutumin da yake mirgina gungurawa. AT: "Yahweh zai narkar da sararin samaniya kamar yadda mutum yake nade nadewa"
Yahweh ya bayyana kansa a matsayin jarumi mai ɗaukar takobi. Kalmar "sha ta cika" tana magana ne game da takobin Yahweh kamar dai mutum ne wanda ya ci ya ƙoshi. Yahweh yayi amfani da wannan hoton don ya nanata cewa za a yi halaka mai yawa a sama kuma a faɗi yadda aka gama. AT: "idan na gama lalata abubuwa a sama"
Kalmar "shi" tana nufin takobin Yahweh. Wannan yana ci gaba da kwatanci game da Yahweh yana lalata abubuwa da takobi. AT: "Zan zo in hukunta mutanen Idom, mutanen da na keɓe domin in hallaka"
Za a iya bayyana kalmomin "sadaukarwa" da "yanka" a nan kamar kalmomin aiki. AT: "Gama Yahweh zai sadaukar da mutane da yawa a Bozra kuma ya kashe mutane da yawa a ƙasar Edom"
Wannan yana bayanin yawan jinin da zai jika a ƙasa ta hanyar kwatanta ƙasar da maye. AT: "Ƙasarsu za ta jike da jini"
Anan "ƙura" na nufin datti a ƙasa. Wannan yana bayanin yawan kitsen da zai jika cikin datti ta hanyar kwatanta shi da mutumin da ya zama mai daga yawan cin kitse na dabbobi. AT: "datti zai cika da kitsen dabbobi"
Anan "rana" kalma ce ta magana a cikin lokaci; ba 'rana' ta zahiri bane. AT: "zai zama lokacin da Yahweh zai rama"
Wannan yana nufin cewa zai ɗauki fansa a kansu ne saboda yadda suka yi yaƙi da mutanen Yerusalem a baya. AT: "zai basu hukuncin da ya kamace su saboda abin da suka yi wa Sihiyona"
Ruwa da ƙasa ba su da amfani don sha ko noman abinci saboda an ƙone shi kuma an lulluɓe shi a farar fatar kuma an yi magana da ƙibiritu kamar dai rafukan da suke ƙasa da ainihin ƙasar za su zama farar fata da ƙibiritu. AT: "Kogunan da ke Idom za su cika da farar ƙasa kuma ƙasa za a rufe ta da farar wuta mai ƙonewa da farar konewa"
Wannan yana magana ne game da Yahweh kamar dai shi mai kirki ne kamar yadda yake kawo hallaka a Idom. AT: "Yahweh zai auna wannan ƙasar a hankali; zai auna ta ne don yanke shawarar inda zai haifar da lalacewa da lalacewa"
"Manyan Idomawa ... sarakunan Idom"
dabbobin da suke farke da aiki da dare
Kalmomin "littafin Yahweh" yana nufin yana ƙunshe da saƙonnin da Yahweh ya faɗa. AT: "Karanta a hankali abin da aka rubuta a cikin wannan gungura mai ɗauke da saƙonnin Yahweh"
An ambaci Yahweh da “bakinsa” don ya nanata abin da ya faɗa. AT: "don Yahweh ne ya umarce shi"
Kalmomin "tsara zuwa tsara" na nuni ga dukkan tsararraki na mutanen da zasu rayu a nan gaba. AT: "har abada za su" ko "koyaushe za su"
1Jeji da Hamada za su yi farin ciki; hamada kuma za ta yi murna ta faso da fure. Kamar tsire-tsire,2zata faso da furanni ainun ta yi murna da farin ciki da waƙa; za a ba shi darajar Lebanon, da kuma ɗaukakar Karmel da Sharon; za su ga ɗaukakar Yahweh, mafificiyar ɗaukakar Allahnmu.3Ku ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi, ku tsaida gwiwoyin masu kaɗuwa.4Ku ce wa matsorata, "Ku ƙarfafa, kada ku ji tsoro! Duba, Allahnku zai zo da ramako, da kuma sakamakon Allah. Zai zo kuwa ya cece ku."5Sa'an nan idanun makafi za su gani, kunnuwan kurame kuma za su ji.6Sa'an nan gurgu zai yi tsalle kamar barewa, bebe zai raira waƙa, gama ruwa zai malalo daga cikin Hamada, koguna kuma cikin jeji.7Yashi mai ƙuna zai zama tafki, ƙasa mai ƙishin ruwa kuma zata zama maɓuɓɓugar ruwa; a mazaunin diloli, inda dă suka kwanta, za a tarar da ciyawa da iwa.8Wata karafka zata kasance a wurin ana kiran ta Hanya Mai Tsarki. Marar tsarki ba zai bi ta kanta ba. Amma zata kasance domin wanda ya yi tafiya a cikinta. Ba wawan da zai bi ta kanta.9Ba zakin da zai kasance a wurin, ba wata muguwar dabba da zata kasance a kanta; ba za a same su ba a can, amma fansassu ne za su yi tafiya a can.10Baratattun Yahweh za su komo za su taho suna waƙa zuwa Sihiyona, madawwamin farinciki zai kasance a kansu; murna da farinciki za su mamaye su; baƙinciki da ajiyar zuciya za su shuɗe.
Waɗannan jimlolin biyu suna da ma'ana iri ɗaya. Wadannan wurare an bayyana su da cewa suna da farin ciki, kamar yadda mutum yake murna, saboda sun sami ruwa kuma suna fure. AT: "Zai zama kamar jeji da Araba suna murna kuma hamada za ta yi farin ciki"
Wannan yana maganar hamada kamar tana murna da waka kamar mutum. AT: "zai zama kamar komai yana murna da waka"
Waɗannan jimlolin guda biyu ma'anar abu ɗaya ne kuma suna jaddada bayyanar Yahweh.
Kalmomin "hannaye marasa ƙarfi" da "gwiwoyi masu girgiza" suna wakiltar mutum mai tsoro. AT: "Starfafa waɗanda hannayensu suka yi rauni kuma gwiwoyinsu suka girgiza saboda tsoro"
Anan ana ambaton mutane da zukatansu, wanda ke jaddada abubuwan da suke ciki. AT: "ga waɗanda suke tsoro"
Ana iya sake amfani da wannan ta yadda za'a nuna kalmomin "ramuwar gayya" da "sakamako" azaman kalmar "azaba". Kalmomin "fansa" da "sakamako" ma'ana ɗaya ce kuma sun nanata cewa Allah zai hukunta maƙiyan Yahuda. AT: "Allahnku zai hukunta maƙiyanku saboda abin da suka aikata"
Wadannan ayoyin sun fara bayanin makomar daukaka ga mutanen Allah.
"Makaho" yana nufin mutanen da suke makafi. Ana kiransu da “idanunsu” don jaddada warkaswar su. AT: "makafi zasu gani"
Barewa na iya yin tsalle nesa da nesa. Yin tsalle kamar barewa babban ƙari ne saboda iya motsi cikin sauri da sauƙi. AT: "gurgu ne zai yi tsalle"
Ana iya samar da fi'ilin da aka fahimta. AT: "koramu za su gudana a cikin jeji"
Wannan yana nufin cewa maɓuɓɓugan ruwa zasu bayyana a cikin sandararriyar ƙasa. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "maɓuɓɓugan ruwa za su bayyana a cikin ƙasa mai ƙishi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Babbar hanya za ta kasance a wurin da ke da suna Hanya Mai Tsarki"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba wanda zai same su a wurin"
Yin "fansa" na nufin "ceto". Wannan yana nufin mutanen da Yahweh ya cece. AT: "Waɗanda Yahweh ya cece su"
Wannan yana amfani da kan mutum don nufin mutum gaba ɗaya. AT: "za su sami farin ciki na har abada"
Wannan yana magana ne game da mutane ba sauran baƙin ciki da nishi ta hanyar ba da waɗannan motsin zuciyar mutum ikon gudu. AT: "ba za su ƙara yin baƙin ciki da nishi ba"
1A shekara ta goma sha huɗu ta sarki Hezekiya, Senakerib sarkin Asiriya, ya tasar wa dukkan biranen Yahuda da kagararsu ya kuma kame su.2Sai sarkin Asiriya ya aika da babban shugaban soja daga Lakish zuwa Yerusalem ga sarki Hezekiya tare da babban soja. Ya gabaci dai-dai magudanar kwarin da ya ke kawo ruwa, a babbar hanyar filin da masu wankin tufafi suka tsaya a kanta.3Shugabannin Isra'ilawa waɗanda suka fito wajen birnin su yi magana da su su ne Hilkiya ɗan Iliyakim, shugaba mai kula da fãda, Shebna sakataren sarki, da Yowa ɗan Asaf, wanda ke rubuta matakan gwamnati.4Sai shugaban sojoji yace da su, "Ku faɗawa Hezekiya babban sarki, sarkin Asiriya, yace, 'Me kake dogara da shi?5Ka na maganganun wofi marar amfani, cewa akwai shawara da ƙarfin yaƙi. To yanzu ga wa kake dogara? Wane ne ya baka ƙarfin zuciya da za ka yi mani tawaye?6Duba, kana dogora da Masar, da tsabgar da kake amfani da ita a matsayin sandar tafiya, amma duk mutumin da ya dogara da ita, zai karye ya soke hannunsa. Wannan shi ne Fir'auna sarkin Masar zai yiwa dukkan wanda ya dogara gare shi.7Amma idan ka ce da ni, "Mu na dogara ga Yahweh Allahnmu," ba shi ne wanda ya ke a manyan wurare da bagadai Hezekiya ya ɗauke, ya kuma ce Yahuda da Yerusalem, '"Dole ku yi sujada a wannan bagadi a Yerusalem ba"?8Saboda haka yanzu, zan ba ka abu mai kyau daga maigidana sarkin Asiriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, idan har za ka iya samin masu hawansu.9Ya ya zaka iya kaucewa ko ɗaya daga cikin barorin shugabana? Kana sa dogara ga karusai da mahaya dawakai na Masar!10To yanzu, na tafi can ba tare da Yahweh ba in tasar wa wannan ƙasar, har in lalatar da ita? Yahweh yace da ni, "Ka faɗawa wannan ƙasar har ka lalatar da ita.'""11Sa'an nan Iliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa suka ce da babban shugaba, "Ka yi magana da barorinka a cikin harshen Aremiyanci, Aremaik, domin muna gane shi. Kada ka yi magana da mu da harshen Yahuda a kunnuwan mutane waɗanda suke a kan garu."12Amma babban kwamanda ya ce, "Babban sarki ya aiko ni ga shugabanku kuma ya faɗi waɗannan maganganu? Ba ya aiko ni ga jama'ar da suke a kan garu ba, waɗanda za su ci kashinsu su kuma sha fitsarinsu tare da ku ba?"13Sai shugaban sojoji ya tsaya ya tada murya da ƙarfi a cikin Yahudanci, cewa, "Ku saurari magana daga babban sarki, sarkin Asiriya.14Sarki yace, 'Kada ku yarda Hezekiya ya ruɗe ku, shi ba zai iya cetonku ba.15Kada kuma ku bari Hezekiya ya saku ku dogara ga Yahweh, cewa, '"Yahweh zai tabbatar da cetonku; wannan birni ba za a bada shi a hannun sarkin Asiriya ba.'"16Kada ku saurari Hezekiya, domin wannan shi ne abin da sarkin Asiriya yace: 'Ku nemi salama tare da ni kuma ku fito wuri na. Sai kowannenku ya ci daga cikin 'ya'yan inabin gonarsa, daga kuma itacen ɓaurensa, ya kuma sha ruwa daga rijiyon kansa.17Za ku yi wannan har saina zo na ɗauke ku zuwa wata ƙasa mai kama da irin ta ku, ƙasa mai hatsi da sabuwar inabi, ƙasa ta gurasa da kuringar inabi.'18Kada ku bar Hezekiya ya ruɗe ku, cewa, 'Yahweh zai kuɓutar da ku.' Ko akwai wasu allolin mutanen da suka cece su daga hannun sarkin Asiriya?19Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarwayim? Sun ceci Samariya daga ikona?20A cikin dukkan allolin waɗannan ƙasashe, akwai wani da ya ceci ƙasarsa daga ikona, ya ya kuke ganin kamar Yahweh zai ceci Yerusalem daga ikona?21Amma mutane suka tsaya tsit ba bu kuma wanda ya maida martani, don umarnin sarki, "Kada ku amsa masa."22Sai Iliyakim ɗan Hilkiya, wanda ya ke bisa iyalin, Shebna marubuci, da Yowa ɗan Asaf mai kula da tarihi, suka zo wurin Hezekiya da tufaffinsu a kekkece, kuma suka faɗa masa maganganun da shugaban mayaƙa ya faɗa.
Anan Sennacherib yana wakiltar kansa da sojojinsa. AT: "Sennacherib da rundunarsa ... sun afka wa dukkan garuruwa masu garu"
Wasu juyi na Littafi Mai-Tsarki sun fassara wannan da "Rabshakeh." Wannan kalmar Asiriya ce ga ɗaya daga cikin manyan shugabannin sojoji a Asiriya.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan sunan da ya dace da mutane ke kiran filin da shi ko 2) wannan sunan gama gari ne da mutane suka saba magana game da filin, "masu wanki filin" ko "filin da maza ke wanke ulu" ko "filin da mata suke wankin tufafi." Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 7: 3.
"ya ce wa Eliyakim, da Shebna, da Yowa"
Sarkin Asiriya yayi amfani da wannan tambayar don ƙalubalantar Hezekiya da kuma cewa bashi da tushe mai kyau na amincewa. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Ba ku da tabbataccen tushe don dogaro da ku."
"kuna da majalisa da karfin fadawa cikin yaki." Jumlar "ƙarfi don yaƙi" tana nufin samun isassun sojoji da ƙarfi da makamai. AT: "kuna da isasshen majalisar soja, maza masu ƙarfi, da makamai don zuwa yaƙi"
Sarkin Asiriya ya yi amfani da tambayoyi don ya yi wa Hezekiya ba'a don ya gaskata yana da ƙarfin tawaye. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Duk wanda kuka dogara da shi, ba za ku sami ƙarfin halin yin tawaye da ni ba."
Wannan ya ci gaba da saƙon Sarkin Asiriya zuwa ga Hezekiya. Babban kwamandan yana magana ne da saƙon ga mutanen Hezekiya (Ishaya 36: 4).
Anan "Masar" tana nufin sojojin Masar. AT: "dogaro da sojojin Masar"
Wannan yana magana ne game da Masar, musamman dakarunta da Fir'aunanta, kamar dai itaciyar daɗaɗaɗa ce don jaddada cewa dogaro da su ba zai taimaka musu ba amma zai cutar da su ne kawai. AT: "wannan kamar tafiya ne tare da sandar da aka tsattsage sandar sandar. Idan mutum ya jingina a kansa, sai ta makale a hannunsa ta huda shi"
Ana iya rubuta wannan azaman faɗakarwa kai tsaye. "Yahuda" da "Yerusalem" suna nufin mutanen da suke zaune a cikinsu. AT: "ya gaya wa mutanen Yahuda da Yerusalem cewa dole ne su yi sujada a wannan bagadin kawai a Yerusalem."
Babban kwamandan ya ci gaba da yi wa Hezekiya da sojojinsa ba’a ta wajen nuna cewa ba shi da sojoji da yawa.
Babban kwamandan ya yi amfani da wata tambaya don yi wa Hezekiya da mutanen Yahuda ba'a. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Na zo nan tare da umarnin Yahweh don halakar da Yerusalem."
Anan "Yahweh" yana nufin umarnin Yahweh. AT: "ba tare da umarnin Yahweh ba"
Wannan yana nufin fada da mutane da haifar da barna a wurin da suke zaune. ƙasar da aka ambata a nan ita ce Yerusalem. AT: "a kan wannan mutanen kuma ku lalatar da ƙasarsu ... Kai wa waɗannan mutane hari kuma ku lalata ƙasarsu"
Eliyakim, da Shebnah, da Yowa sun nuna kansu a matsayin shugabannin barorin. Wannan hanyar ladabi ce don magana da wanda ya sami iko sosai.
Kalmomin "magana a kunnen wani" na nufin yin magana a inda zasu ji ku. AT: "inda mutanen da suke kan bango za su ji mu"
Babban kwamandan ya yi amfani da wannan tambaya don ya nanata cewa saƙonsa na dukan mutanen Yahuza ne. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Tabbas, maigidana ya aiko ni don in yi magana da wannan sakon zuwa gare ku da kuma duk wanda zai iya ji."
Babban kwamandan yayi amfani da wannan tambayar don jaddada cin mutuncin sa. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Maigidana ya aike ni ga duk wanda ya ji wannan, wanda zai iya ... ku."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ba zai ba da Yerusalem a hannun sarkin Asiriya ba"
Wannan karin magana yana nufin yarda a hukumance don yin aiki da juna cikin lumana. AT: "Bari mu yarda mu sami zaman lafiya"
Anan sarkin Asiriya yana nufin sojojinsa kamar kansa. AT: "har sai runduna ta ta zo ta ɗauka"
Wadannan kalmomin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani dasu tare don ƙarfafa yadda ƙasar zata kasance mai wadata.
Babban kwamandan ya ci gaba da magana da saƙon Sarkin Asiriya ga mutanen Yahuda (Ishaya 36:16).
An ambaci ikon sarki a matsayin "hannunsa." AT: "ikon sarki"
Babban kwamandan ya yi amfani da waɗannan tambayoyin don ya yi wa mutanen Yahuda ba'a. Waɗannan tambayoyin na iya haɗuwa kuma a rubuta su azaman sanarwa. AT: "Gumakan Hamat, da Arfad, da Sefarwayim, da na Samariya ba su ceci mutanensu daga hannuna ba."
Babban kwamandan ya yi amfani da wannan tambaya don ya yi wa mutanen Yahuda ba'a. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "babu wani allah wanda ya cece ... kuma Yahweh ba zai cece ku a Yerusalem daga ƙarfina ba."
Wannan karin magana yana nufin cewa shi ne mai lura da al'amuran gidan sarauta. AT: "mai kula da gidan sarauta"
Fādawan Hezekiya suka yayyage tufafinsu don nuna baƙin ciki da baƙin ciki. Ana iya bayyana ma'anar wannan. AT: "tare da tufafinsu da yage saboda suna cikin damuwa matuka"
1Ya zamana a lokacin da sarki Hezekiya ya ji abin da suka faɗa, ya kekkece tufafinsa, ya rufe jikinsa da tsummoki, ya kuma shiga gidan Yahweh.2Ya aika Iliyakim, mai kula da fada, da Shebna marubucin shari'a, da dattawa firistoci, dukkansu suka rufe jikinsu da tsummoki, zuwa wurin Ishaya ɗan Amoz, annabi.3Suka ce da shi, "Hezekiya yace, 'Wannan rana ce ranar wahala da wulaƙanci da kunya, mun zama kamar lokacin da za a haifi yaro, amma uwar ba ta da ƙarfin da zata haifi yaron.4Watakila Yahweh Allahnka zai ji maganganun shugaban mayaƙansa, wanda sarkin Asiriya uban gidansa ya aiko domin ya wulaƙanta Allah mai rai, ya kuma tsawata wa maganganu waɗanda Yahweh Allahnka ya ji. Yanzu sai ka yi addu'a domin ringin da har yanzu suna nan.'"5Sa'ad da barorin sarki Hezekiya suka zo wurin Ishaya,6sai Ishaya yace da su, "Ku faɗawa ubangidanku: 'Yahweh yace, "Kada ku ji tsoron irin maganganun da kuka ji, waɗanda dasu barorin sarkin Asiriya suka wulaƙanta ni.7Duba, zan sa ruhu a cikinsa, zai kuma ji jita-jitar da zata sa ya koma ƙasarsa. Zan sa shi ya faɗi ƙasa da takobi a cikin ƙasarsa.'"'8Sai shugaban mayaƙan ya koma ya kuma sami sarkin Asiriya yana yaƙi da Libna, domin ya ji sarki ya tafi daga Lakish.9Sa'ad da Senakerib ya ji Tirhaka sarkin Kush da Masar sun haɗu domin su yi yaƙi da shi, sai kuma ya aika da manzanni zuwa wurin Hezekiya tare da saƙo:10"Ka ce da Hezekiya, sarkin Yahuda, 'Kada ka bari Allahnka wanda kake dogara da shi ya ruɗe ka, cewa, 'Yerusalem ba zata faɗa hannun sarkin Asiriya ba."11Ku gani, ku kuma ji abubuwan da sarakunan Asiriya suka yiwa dukkan ƙasashe ta wurin lalata su ga baki ɗaya. Kuna tsammani za ku kuɓuta?12Ko allolin al'ummai sun kuɓutar da su, al'umman da ubannina suka lalata akwai Gozan, da Haran, Rezef, da kuma mutanen Iden a Tel-assa?13Ina sarkin Hamat, da sarkin Arfad, da sarkin biranen Sefarwayim, da Hena, da kuma Iwwa?'"14Hezekiya ya karɓi wannan wasiƙar daga hannun manzannin ya kuma karanta ta. Sai ya shiga gidan Yahweh ya baza ta gabansa.15Hezekiya ya yi addu'a ga Yahweh:16"Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, kai da ka zauna a sama da kerubim, kai kaɗai ne Allah a kan dukkan mulkokin duniya. Kai ka yi sammai da duniya.17Ka juyo da kunnuwanka, Yahweh, ka ji mu. Buɗe idanuwanka, Yahweh, ka gani, ka kuma ji maganar Senakerib, wanda ya aika don ya yi ba'a ga Allah mai rai.18I' gaskiya ne, Yahweh, sarakunan Asiriya sun lalata dukkan al'ummai da ƙasashensu.19Suka sa allolinsu a cikin wuta, domin su ba alloli ba ne amma ayyukan hannunwan mutane ne, itace da dutse ne kawai.20Saboda haka Asiriyawa sun lalata su. Yanzu dai, Yahweh Allahnmu, ka cece mu daga ikonsa, saboda dukkan mulkokin duniya su sani kai kaɗai ne Yahweh."21Sai Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo wurin Hezekiya, cewa, "Yahweh, Allah na Israila yace, 'Domin ka yi addu'a gare ni a kan Senakerib sarkin Asiriya,22wannan ita ce maganar da Yahweh ya faɗa a kansa: "Akwai budurwar yariya ta Sihiyona ta rena ka kuma tana yi maka dariyar ba'a; budurwar Yerusalem tana girgiza kanta gare ka.23Wa ka rena ka kuma ci mutunci sa? Gãba da wa ka ɗaga muryarka, ka kuma ɗaga idanuwanka na girmankai? Gãba da Mai Tsarki na Isra'ila.24Ta wurin barorinka ka rena Ubangiji ka kuma ce, 'Da yawan karusaina har na kai ƙololuwar duwatsu, zuwa tsayin Lebanon. Zan sare dogayen itatuwan sida dana sifuros zaɓuɓɓu, na kuma kai wurare mafi nisa, na jeji mafi 'ya'ya.25Na gina rijiyoyi na kuma sha ruwa; Na busar da dukkan kogunan Masar ƙarƙashin sawayena.'26Baka ji yadda na ƙudura a yi haka tuntuni kuma na aiwatar tun zamanin ḍã? Yanzu ne nake cikawa. Kana nan ne domin ka mai da birane gagara-shiga zuwa tulin kango.27Mazaunan su, masu ƙaramin ƙarfi, sun warwatse da kunya. Sun zama tsire-tsire a gona, ɗanyar ciyawa, ciyawar dake kan rufi ko a fili, kafin iskar gabas.28Amma na san zaman ka, da fitar ka, da kuma zuwan ka, na san yadda ka harzuƙa gãba da ni.29Domin harzuƙar ka ta gãba da ni, kuma don girmankanka ya iso kunnuwana, zan sa ƙugiya a hancinka, linzami na kuma a bakinka; zan komar da kai hanyar da ka biyo."30Wannan ita ce zata zama alama domin ka: A wannan shekara zaku ci gyauro, a kuma shekara ta biyu zaku shuka daga abin da ya tsiro daga gauron. Amma a shekara ta uku dole zaku yi shuka ku kuma girɓe shi, ku dasa kuringar inabi ku kuma ci 'ya'yanta.31Su da suke ringi na gidan Yahuda da waɗanda kuma suka tsira za su sake kafuwa su haifi 'ya'ya.32Domin daga Yerusalem ringin za su fito; daga Dutsen Sihiyona waɗanda suka tsira za su zo. Himmar Yahweh mai runduna zai yi wannan.'"33Saboda Yahweh ya faɗi wannan a kan sarkin Asiriya: "Ba zai shiga wannan birnin ba kuma ba zai harba kibiya a nan ba. Ba zai zo gare shi ba tare da garkuwa ko ya kafa sansanin tudu gãba da ita.34Ta hanyar da ya zo ta hanyar kuma zai koma; ba zai shiga wannan birni ba - wannan furcin Yahweh ne.35Zan kare wannan birnin zan kuma ceto shi, domin ni kaina da kuma bawa na Dauda."36Sai mala'ikan Yahweh ya fito ya fãɗa wa sansanin Asiriyawa, ya kashe sojoji 185,000. Da mutanen suka tashi da sassafe, sai suka ga jukunan matattu a kwakkwance ko'ina.37Senakerib sarkin Asiriya ya ƙyale Isra'ila ya koma gida ya zauna a Nineba.38Daga bisani, yayin da ya ke sujada a gidan Nisrok allahnsa, 'ya'yansa Adramelek da Shareza suka kashe shi da takobi. Sai suka tsere zuwa ƙasar Ararat. Isahadon ɗansa ya yi sarauta a matsayinsa.
Ana amfani da wannan jimlar a nan don yiwa wani muhimmin al'amari alama a cikin labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
Wannan alama ce ta nuna bakin ciki da damuwa. AT: "ya yayyaga tufafinsa kuma ya lulluɓe da tsummoki saboda yana cikin damuwa ƙwarai"
"Mutanen da Hezekiya ya aiko suka ce wa Ishaya"
Wannan kwatancen anyi shi ne don jaddada cewa suna cikin lokacin wahala mai yawa. AT: "Ya yi kama da ranar da yaro ya shirya haihuwa, amma uwa ba ta da ƙarfin haihuwar ɗanta"
A nan kalmar "kalmomin da Yahweh Allahnku ya ji" tana nufin abin da sarkin Asiriya ya ce. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "Yahweh Allahnku zai tsauta wa sarkin Asiriya saboda abin da ya faɗa"
Wannan yana nufin mutanen da suka rage a Yerusalem. AT: "ga 'yan ƙalilan daga cikinmu da suke har yanzu"
Kalmomin "sanya ruhu a cikinsa" yana nufin cewa Allah zai rinjaye shi ya yanke shawara takamaiman. Kalmar "ruhu" a nan tana nufin hali mai ƙarfi ko ji. AT: "Zan yi tasiri a kansa ta yadda idan ya ji wani rahoto, zai koma ƙasarsa"
Kalmomin "fadi da takobi" karin magana ne da ke nufin cewa maƙiyinsa zai kashe shi da takobi. AT: "Kuma a can a cikin ƙasarsa, zan sa makiyansa su kashe shi da takubbansu"
"Tirhaka" sunan mutum ne. Ya tattara rundunarsa don su kasance a shirye su yi yaƙi. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari. AT: "Tirhaka sarkin Kush da Masar sun tattara rundunarsa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Kalmar "hannu" tana nufin ikon soja na sarki. AT: "Sarkin Asiriya da rundunarsa ba za su ci ku a Yerusalem ba"
Sarkin Asiriya ya yi amfani da wannan tambayar don ya yi wa Hezekiya da sojojinsa ba'a. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Don haka ku ma ba za ku sami ceto ba." ko "Don haka tabbas babu wanda zai cece ku ko dai!"
Sarkin Asiriya ya yi amfani da wannan tambayar don ya yi wa Hezekiya da sojojinsa ba'a. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Al'ummai allah bai 'yantar da al'umman da kakannina suka rusa ba ... Tel Assa! "
Waɗannan mutanen sun lalata garuruwan da aka lissafa ta hanyar cinye su da rundunarsu. Anan kalmar "uba" tana nufin mahaifinsa da sauran kakanninsa wadanda suka kasance sarakuna. AT: "wanda kakannina suka halaka tare da sojojinsu"
Waɗannan su ne wuraren da Asiriyawa suka ci da yaƙi.
Anan an ambaci manzannin da “hannun” don jaddada cewa da kansu suka ba da shi ga sarki. AT: "cewa manzannin sun bashi"
Haikalin Yahweh ya kasance a cikin maɗaukaki a Yerusalem, saboda haka ana maganar “hawa”.
"shimfiɗa wasiƙar a gaban Yahweh." Kasancewa a cikin gidan Yahweh ana ɗaukarsa ɗaya ne da kasancewa a gaban Yahweh. Harafin was birgima ce wacce za a iya kwance ta a yada.
Kuna iya bayyanawa a sarari cewa kerubobin sune waɗanda suke kan murfin akwatin alkawari. Marubutan Littafi Mai-Tsarki sau da yawa suna magana game da akwatin alkawari kamar dai matashin sawun Yahweh ne wanda ya dogara da ƙafafunsa yayin da yake zaune a kan kursiyinsa a sama. AT: "ku da kuke zaune a kan kursiyinku a saman kerubobi a kan akwatin alkawari"
"kai kadai ne Allah". Wannan karin magana yana nufin samun iko da kuma mulkin duk masarautu. AT: "ku sami iko akan dukkan masarautu"
Wannan yana nufin cewa ya halicci komai. AT: "Kun yi komai"
"Karkata kunnenka" ko "Juya kai." Wannan yana nufin juya kanku domin ku ji wani abu mafi kyau.
Wannan magana ce gaba ɗaya. Sarakunan sun lalata yawancin ƙasashe na kusa, amma ba lallai bane duk ƙasashe. AT: "yawancin al'ummomi da ƙasashensu"
Wannan yana jaddada cewa mutane sun yi waɗannan gumaka da hannayensu don haka basu da daraja. AT: "saboda sun kasance gumakan ƙarya waɗanda mutane suka yi da itace da dutse"
"daga ikon sarkin Asiriya"
"shi ne abin da Yahweh ya ce"
Waɗannan maganganu ne. Duk waɗannan jimlolin suna da ma'ana iri ɗaya. 'Yar' birni na nufin mutanen da ke zaune a cikin birni. Duba yadda kuka fassara makamancin magana a cikin Ishaya 1: 8. AT: "Mutanen Sihiyona ... mutanen Yerusalem"
Wannan yana nufin magana da ƙarfi kamar muryar mutum abu ne da suka ɗaga sama. AT: "shin ka yi ihu"
Wannan karin magana ne wanda ke nufin kallon wani abu cikin girman kai, la'akari da kanku mafi mahimmanci da ya kamata. AT: "an yi alfahari da shi" ko "an yi alfahari da shi"
Anan Senakerib yayi maganar kansa yana cin abubuwa da yawa. Haƙiƙa yana cin su da yaƙi da runduna da karusan da ya ba da umarni. AT: "Mun tafi ... Za mu yanke ... za mu shiga"
Anan Sennakerib yana wuce gona da iri kan yawo da yawo ta kogin Masar yana mai cewa ya bushe kogunan lokacin da ya bi tawagarsa ta cikinsu. AT: "Na ratsa duk rafin Masar kamar sun bushe ƙarƙashin ƙafafuna"
Yahweh ya yi niyya ga sojojin Sennakerib su hallaka biranen da suka hallakar. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "Na tsara cewa sojojinku za su rusa biranen kuma su sa su zama tulin tarin abubuwa"
Karin maganar "kawo wani abu ya wuce" na nufin haifar da takamaiman abu ya faru. AT: "Ina sa shi ya faru" ko "Ina sa waɗannan abubuwan su faru"
Wannan yana magana ne game da raunin birane da rauni a gaban sojojin Asiriyawa ta hanyar kwatanta biranen da ciyawa. AT: "Garuruwa suna da rauni kamar ciyawar da ke cikin filaye a gaban rundunoninku. Suna da rauni kamar ciyawar da ke tsirowa a saman rufin gidaje kuma iska mai zafi ta gabas ta ƙone ta"
Wannan yana nufin dukkan ayyukan rayuwa. AT: "Na san duk abin da kuke yi"
Ana iya bayyana kalmar "fushi" a matsayin fi'ili. AT: "yadda kuka fusata da ni"
Wannan yana magana ne game da Yahweh yana jin jawabin sarki kamar maganar sarki wani abu ne da yake tafiya zuwa kunnensa. AT: "Na ji kuna magana da girman kai"
Mutum yayi amfani da ƙugiya kuma ya ciji ya jagoranci dabba kusa. Wannan yana magana ne game da Yahweh yana sarrafa sarki kamar sarki na dabba ne Yahweh yana sarrafawa da ɗan ƙugiya da ƙugiya. AT: "Zan mallake ku kamar yadda mutum yake sarrafa dabbarsa ta hanyar sanya ƙugiya a hancinsa kuma kaɗan a cikin bakinsa"
Wannan yana nufin sanya sarki ya koma ƙasarsa ta asali. Ana iya bayyana ma'anar wannan. AT: "Zan tilasta muku ku koma ƙasarku"
"sa hannu a gare ka, Hezekiya." Anan "ku" ɗaya ne kuma yana nufin Hezekiya.
Wannan ya bayyana abin da mutane za su ci. An fahimci kalmomin "zaku ci" daga jumlar da ta gabata. AT: "a shekara ta biyu zaku ci abinda ya girma" ko "shekara mai zuwa zaku ci abinda ya tsiro"
Anan “gidan” Yahuda yana nufin zuriyarsa. AT: "zuriyar Yahuda"
Wannan yana magana ne game da mutanen Yahuda sun zama masu ni'ima kamar dai shukeshuke ne waɗanda za su yi jijiya kuma su ba da 'ya'ya. AT: "zai yi nasara kamar shukar da ta yi jijiya kuma ta ba da 'ya'ya"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani da su tare don ƙarfafa ragowar mutanen da za su rayu.
Wannan yana magana ne akan Yahweh yana yin wani abu saboda himmarsa kamar dai "himmar sa" da gaske tana aikata aikin. AT: "Saboda kishinsa, Yahweh Mai Runduna zai yi wannan" ko "Yahweh na runduna zai yi hakan saboda kishinsa"
Anan sarkin Asiriya yana nufin shi da sojojinsa. AT: "sun zo ... ba za su shiga ba"
"domin abubuwa su fi kyau a gare ni da kuma bawana Dauda"
Anan Senakerib yana nufin duka shi da sojojinsa. Dukansu suka tashi daga Isra'ila suka koma Asiriya. Senakerib ya koma garin Nineba. AT: "Sennakerib da rundunarsa sun bar Isra'ila sun koma gida, Senakerib kuwa ya zauna a Nineba"
"kamar yadda Sennakerib yake sujada"
Wannan sunan allahn karya ne.
Waɗannan sunayen maza.
1A kwanakin da Hezekiya ya ke ciwo har ya kusa mutuwa. Sai Ishaya ɗan Amoz, annabi, ya zo wurinsa, ya ce masa, "Yahweh yace, 'Ka kintsa komai dai-dai a gidanka; gama mutuwa za ka yi, ba za ka rayu ba,'"2Sai Hezekiya ya juya ya sa fuskarsa a bango ya yi addu'a ga Yahweh.3Ya ce, "Idan ka yarda Yahweh, ka tuna yadda na yi tafiya a gabanka da dukkan zuciyata da aminci, yadda na yi abin da ke dai-dai a idanunka." Sai Hezekiya ya yi kuka da ƙarfi.4Sai maganar Yahweh ta zo wurin Ishaya, cewa,5"Tafi ka ce da Hezekiya, shugaban mutanena, 'Wannan shi ne abin da Yahweh, Allah na Dauda kakanka, ya ce: Na ji addu'arka, na kuma ga hawayenka. Duba, ina shirin ƙara maka shekaru goma sha biyar nan gaba.6Daga nan zan cece ka da wannan birnin daga hannun sarkin Asiriya, kuma zan kãre wannan birni.7Wannan zai zama alama a gare ka daga Yahweh, zan yi abin da na alƙawarta.8Duba, zan komar da inuwa baya da taki goma na hawan benen Ahaz. Saboda haka inuwa ta koma baya da taki goma a kan hawan benen inda ta yi gaba.9Wannan ita ce rubutacciyar addu'ar Hezekiya sarkin Yahuda, lokacin da ya ke rashin lafiya daga nan kuma ya warke:10"Na ce tsakanin ƙarshen rayuwata zan koma daga ƙofofin Lahira; zan ƙarashe sauran shekaru a can.11Na ce ba zan ƙara ganin Yahweh, Yahweh a cikin ƙasar rayayyu ba; ba kuma zan ƙara duban wani mutum ko mazaunan duniya ba.12An datse raina an kuma tafi da shi daga gare ni kamar rumfar makiyayin tumaki; na naɗe raina kamar gado; kana sare ni daga masaƙa; tsakanin rana da dare zaka ƙarar da raina.13Na yi ta kuka har gari ya waye; kamar zaki yana kakkarya dukkan ƙasussuwana. Tsakanin rana da dare kana ƙarashe raina.14Kamar muryar ƙaramin tsuntsu; na yi kuka kamar kurciya; idanuna sun gaji don dubar sama. Ubangiji, an matsa mani; ka taimake ni.15Me zan iya faɗa? Ya yi magana da ni, ya yi haka, zan yi tafiya a hankali dukkan shekaruna sabili da baƙinciki ya rinjaye ni.16Ubangiji, wahalolin daka aiko suna da kyau a gare ni; ka dawo mani da raina; ka maido mani da raina da kuma lafiyata.17Domin amfani na ne na ji irin wannan baƙincikin. Ka cece ni daga kududufin hallaka; domin ka jefar da dukkan zunubaina bayanka.18Gama Lahira ba ta yi maka godiya; mutuwa ba ta yabonka; waɗanda suka tafi can cikin rami ba za su bege cikin amincinka ba.19Mutum mai rai, mutum mai rai, shi ne zai iya yi maka godiya, kamar yadda na ke yi a wannan rana, uba yana bayyanawa 'ya'ya irin amincinka.20Yahweh yana kusa da ceto na, za mu kuma yi buki tare da kaɗe-kaɗe da waƙoƙi dukkan ƙwanakin ranmu cikin gidan Yahweh."21Yanzu Ishaya yace, "Bari su ɗauki 'ya'yan ɓaure su cura a kuma sa shi akan marurun, zai kuma warke."22Hezekiya kuma ya ce, "Me zai zama alama da yasa zan iya zuwa gidan Yahweh?"
Wannan yana nufin shirya iyalinka da waɗanda ke kula da lamuran ku don su san abin da zasu yi bayan kun mutu. Ana iya rubuta wannan a sarari. AT: "Ya kamata ku gaya wa mutane a cikin fadar ku abin da kuke so su yi bayan kun mutu"
Wannan karin magana ne. Anan "tafiya" na nufin "rayuwa." Jumlar tana nufin rayuwa a cikin hanyar da Yahweh yake so. AT: "ya rayu a gabanka da aminci" ko "ya bauta muku da aminci"
Ganin Yahweh yana wakiltar hukuncin Yahweh ko kimantawarsa. AT: "me ya faranta maka rai" ko "abin da kuke ganin ya yi kyau"
Wannan karin magana ne da ake amfani da shi don gabatar da wani abu da Allah ya faɗa wa annabawansa ko mutanensa. AT: "Yahweh ya faɗi wannan saƙon" ko "Yahweh ya faɗi waɗannan kalmomin"
Anan “hannun” sarki yana nufin ƙarfinsa. AT: "ikon sarkin Asiriya"
Ana kiran waɗannan matakala ta wannan hanyar domin an gina su ne lokacin Ahaz yana sarki. Kuna iya bayyana wannan bayanin a sarari.
"cewa kafin na tsufa." Wannan yana nufin mutuwa a tsakiyar shekaru, kafin tsufa.
Wannan yana maganar mutuwa kamar Lahira masarauta ce da ke da ƙofofin da mutum zai shiga. AT: "Zan mutu kuma in tafi Lahira"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kafin in rayu duk tsawon shekaruna zan tafi kabari"
Wannan yana magana ne game da yadda Yahweh ke kawo ƙarshen rayuwar Hezekiya da sauri ta hanyar kwatanta shi da yadda makiyayi zai cire alfarwarsa daga ƙasa. AT: "Yahweh ya karɓi raina da sauri kamar makiyayi ya tattara alfarwarsa ya tafi da ita"
Wannan yana magana ne game da Yahweh cikin sauri ya kawo ƙarshen rayuwar Hezekiya ta hanyar kwatanta shi da yadda mai saƙa yake yanke ƙyallen rigarsa daga dutsen ya mirgine shi. AT: "kuna gamawa da rayuwata da sauri, kamar mai saƙa yana yanke rigar sa daga mashin idan ya gama"
Hezekiya yayi magana game da yadda yake cikin matsanancin ciwo ta hanyar kwatanta shi da yadda jikin zakoki suka tsage jikinsa. AT: "Ciwo na kamar na ce zaki ya tsage ni"
Duk waɗannan maganganun suna nufin abu ɗaya kuma suna jaddada yadda kukan Hezekiya ya kasance abin baƙin ciki da tausayi. Haɗaɗɗiya da kurciya nau'ikan tsuntsaye ne. AT "Kukan na mai ban tausayi ne - suna ji kamar hayaniyar haɗiye da kurar kurciya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Rashin lafiyata tana damuna"
"saboda ina cike da bakin ciki" ko "saboda ina bakin ciki sosai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kuna iya mayar min da raina"
Hezekiya yayi maganar Yahweh yana gafarta zunubansa kamar abubuwa ne waɗanda Yahweh ya yar da a baya kuma ya manta da su. AT: "Gama kun gafarta zunubaina duka kuma baku sake tunanin su ba"
Anan "Lahira" da "mutuwa" suna nufin "mutanen da suka mutu." AT: "Ga waɗanda suke cikin Lahira ba sa gode muku; matattu ba sa yabonku"
"wadanda suka gangara zuwa kabari"
Anan "mu" yana nufin Hezekiya da mutanen Yahuda.
"Ku bar bayin Hezekiya"
1A wannan lokacin sai Maduk-Baladan ɗan Baladan, sarkin Babila, ya aika da wasiƙu tare da kyauta ga Hezekiya; domin ya ji cewa Hezekiya ya yi ciwo ya kuma sami lafiya.2Hezekiya kuwa ya ji daɗin waɗannan abubuwa; har ya kuma nuna wa manzannin ɗakin dukiyarsa - wato su azurfa, da zinariya, da kayan yaji, da mai mai daraja, da daƙin kayayyakinsa na yaƙi, da dukkan abin da ke cikin gidansa. Babu sauran wani abu da ya ke da shi a gidansa, ko cikin dukkan mulkinsa, wanda Hezekiya bai nuna masu ba.3Sai Ishaya annabi ya zo wurin sarki Hezekiya ya kuma tambaye shi, "Me waɗannan mutane suka ce da kai? Daga ina suka zo?" Hezekiya yace, "Sun zo wuri na daga ƙasa mai nisa ta Babila."4Ishaya ya yi tambaya, "Me suka gani a gidanka?" Hezekiya ya amsa, "Sun ga dukkan abin da ya ke a gidana. Babu wani abu mai daraja da ban nuna masu ba."5Sai Ishaya yace da Hezekiya, "Saurari maganar da Yahweh mai runduna:6'Duba, ranaku sun kusa zuwa da za a kwashe komai a fadarka, abubuwan da kakaninka suka tara har ya zuwa yau, za a ɗauke su zuwa Babila. Ba abin da za a rage, in ji Yahweh.7'Ya'ya da aka haifa maka, waɗanda kai ka haife su - za a ɗauke su, kuma za su zama bãbãnni a fadar sarkin Babila.'"8Sai Hezekiya ya cewa Ishaya, "Maganar Yahweh wadda ka faɗa tana da kyau." Domin ya yi tunani, "Za a sami salama da kwanciyar rai a zamanina."
Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "Lokacin da manzannin sarki suka iso, sai Hezekiya ya yi murna da abin da suka kawo masa"
"ya nunawa manzannin duk irin darajar da yake da ita"
Wannan ƙaramin ƙari ne kamar yadda Hezekiya ya nuna musu abubuwa da yawa, amma ba komai ba. Hakanan, ana iya bayyana hakan da gaskiya. AT: "Hezekiya ya nuna musu kusan komai a cikin gidansa da cikin mulkinsa"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma ana amfani da su tare don jaddada yadda Hezekiya ya nuna wa mutanen.
Ana iya bayyana wannan da kyau. AT: "Na nuna musu dukkan abubuwa masu daraja a cikin fada na"
Duba yadda kuka fassara wannan jumlar a cikin Ishaya 1: 9.
Ana iya bayyana wannan da kyau. AT: "lokacin da sojojin makiya za su kwashe komai a cikin fada ... su koma Babila"
"'Ya'yanku maza"
"Babiloniyawa za su kama su"
1"Ta'aziya, ta'azanta mutanena," in ji Allahnka.2"Yi magana mai taushi ga Yerusalem; ka yi mata shela cewa yaƙinta ya zo ƙarshe, laifofinta kuma an gafarta mata, za ta sami ruɓi biyu daga hannun Yahweh domin dukkan zunubanta."3Wata murya ta koka, "A cikin jeji shirya hanyar Yahweh; a shirya ta miƙaƙƙiya a cikin Hamada doguwar hanya domin Allahnmu."4Kowanne kwari zai cika, za a baje kowanne tsauni da tudu; ƙasa mai kwazazzabai kuwa za ta zama sumul, wurare kuma masu gargada za su zama sarari;5kuma ɗaukakar Yahweh zata bayyana, dukkan mutane kuwa za su gan shi tare; gama bakin Yahweh ne ya faɗi haka.6Wata murya na cewa, "Yi kuka." Wata ta amsa, "Kukan me zan yi?" "Dukkan yan adam ciyawa ne, dukkan alƙawarinsu da amincinsu kamar furannin jeji.7Ciyawa ta kan bushe, furanni kuma su yanƙwane sa'ad da numfashin Yahweh ya hura a kansu; ba bu shakka mutane ciyawa ne.8Hakika ciyawa ta kan bushe, furanni kuwa kan yi yaushi, amma maganar Allahnmu zata tsaya har abada."9bisa tsauni mai tsayi, Sihiyona, mai ɗauke da labari mai daɗi. Ki yi kuwwa da ƙarfi, yaYerusalem. Ke da kika kawo labari mai daɗi, daga muryarki, kada kuwa ki ji tsoro. Ki faɗa wa biranen Yahuda, "Ga Allahnku!"10Duba, Ubangiji Yahweh yana zuwa kamar mayaƙi mai nasara, damtsensa mai ƙarfi zai yi masa mulki. Ga shi, da sakamako tare da shi, kuma waɗanda ya ceto sun sha gabansa.11Zai ciyar da garkensa kamar makiyayi, zai tattara 'yan tumakin a damtsensa, ya kuma ɗauke su kusa da zuciyarsa, kuma a hankali zai bida tumaki masu shayar da nono.12Wa ya taɓa auna ruwaye da tafin hannunsa, ko ya auna sararin sama da tafin hannunsa, ko ya iya riƙe ƙurar duniya a kwando, ko ya iya auna nauyi tsaunika a sikeli, ko tuddai a ma'auni?13Akwai wanda zai iya fahimtar tunanin Yahweh, ko ya ba shi umarni a matsayin mashawarcinsa?14Daga wurin wa ya taɓa karɓar umarni? Wane ne ya koya masa yadda zai yi abubuwa, ya kuma koya masa sani, ko ya nuna masa hanyar fahimta?15Duba, al'ummai na kamar digon ruwa a bokiti, kuma suna kama da ƙura a sikeli; duba, yana auna tsibirai kamar ɗan ɗigo.16Lebanon bata da isasshen fetur, ko dabbobin dajinta ba su isa baikon konawa ba.17Dukkan al'ummai ba isassu ba ne a gare shi; an ɗauke su ba a bakin komai bane a gare shi.18Da wa za ka iya ƙwatanta Allah? To da wanne gunki za ka kamanta da shi?19Gunki! Masassaƙi ne ya yi shi: makera suka dalaye da zinariya kuma suka sa shi cikin abin da suka yi da azurfa.20Domin miƙa baiko wani ya zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba; ya nemi ƙwararren maƙeri da zaya yi masa siffar gunkin da ba zaya fãɗi ba.21Ashe ba ka sani ba? Ashe ba ka ji ba? Ba a faɗa maka ba tun daga farko? Ba ka fahimta ba tun daga fara kafa harsashin duniya?22Shi wanda ya ke zaune a bisa bangon duniya; mazaunanta suna kama da fãri a gabansa. Ya miƙar da sammai kamar labule kuma ya baza su kamar rumfa domin a zauna ciki.23Yana maida masu mulki ba komai ba kuma yana maida masu mulkin duniya yadda ba a san da zamansu ba.24Suna kama da dashe kasafai, dashen da a ka shuka kasafai, dashen da bai yi ko saiwar da ta shiga ƙasa ba, sa'ad da ya hura a kansu sai su yi yaushi, kuma iskar ta hure su kamar ƙaiƙayi.25"To, da wane ne za a kwatanta ni, ko akwai wani mai kama da ni?" in ji shi Mai Tsarki.26Dubi sararin sama a bisa! Wane ne ya halicce dukkan waɗannan taurarin? Shi ne wanda ya ke masu jagora kuma ya kira su bisa ga sunan kowa. Ta wurin ikonsa da girmansa da kuma ta wurin karfi da iko, ba ko ɗayansu da ya ɓace.27Me ya sa kuka ce, Yakubu, kuma kuka ce, Isra'ila, "Hanya ta a ɓoye take daga Yahweh, kuma Allahna bai damu da baratarwata ba"?28Ba ku sani ba? Ba ku kuma ji ba? Madawwamin Allah, Yahweh, shi ne mahaliccin ƙarshen duniya, ba ya taɓa jin gajiya ko kasala ba; ba shi da iyakar fahimta.29Yana ƙarfafa masu jin gajiya; masu kasala kuma ya kan sabunta ƙarfinsu.30Duk da matasa ma sukan ji kasala da gajiya, samari kuma sukan yi tuntuɓe su faɗi:31Amma waɗanda suke dogara ga Yahweh zai sabunta ƙarfinsu; za su tashi da fikafikai kamar gaggafa; za su yi gudu kuma ba za su gaji ba; za su yi tafiya amma ba za su suma ba.
Annabin yana maganar Yerusalem kamar mace ce da Yahweh ya gafarta. A matsayin haka, Yerusalem tana wakiltar mutanen da ke zaune a wannan garin. AT: "Yi magana mai daɗi ga mutanen Yerusalem"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne cewa kalmar "yaƙi" tana nufin 1) zuwa yaƙin soja ko 2) zuwa aikin bautar.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya yafe mata laifinta"
Wadannan layuka biyu suna layi daya kuma suna nufin abu daya ne. Mutanen da suka shirya kansu don taimakon Yahweh ana maganarsu kamar suna shirya hanyoyi don Yahweh ya bi ta.
Waɗannan jumlolin suna bayyana yadda mutane za su shirya babbar hanya don Yahweh. Ana iya bayyana su a cikin tsari mai aiki. AT: "Cika kowane kwari, kuma ku daidaita kowane dutse da tudu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai bayyana ɗaukakarsa"
Kalmar "nama" tana nufin mutane. Mai maganar yana magana ne game da mutane kamar ciyawa suke, domin dukkansu biyu suna mutuwa da sauri. AT: "Duk mutane kamar ciyawa suke"
Mai maganar yana kwatanta amincin alkawari na mutane da furannin da suka yi furanni sannan suka mutu da sauri. AT: "da sauri sun daina kasancewa da aminci ga alkawarin, kamar dai yadda furen filin ya mutu da sauri"
Mai yiwuwa ma'anonin su ne 1) "lokacin da Yahweh ya busa masa numfashi a kanta" ko kuma 2) "lokacin da Yahweh ya aiko da iska don ya busa akan ta."
Marubucin yayi magana ne game da Sihiyona kamar dai manzo ne wanda ya ba da labari mai daɗi daga ƙwanƙolin dutse.
Marubucin yayi magana game da Yerusalem kamar dai manzo ne wanda ya ba da labari mai daɗi.
Anan kalmar “damtsen” tana wakiltar ikon Allah. AT: "yana mulki da babban iko"
Marubucin yayi magana game da mutanen Yahweh kamar tumaki kuma ya Yahweh kamar shi makiyayinsu ne. AT: "Zai kula da mutanensa kamar yadda makiyayi ke ciyar da garkensa"
Ana magana da Yahweh sanin yawan ruwa a cikin tekuna kamar Yahweh yana riƙe da ruwa a hannunsa. (Duba: rquestion)
"Sanda" shine ma'aunin tsayi tsakanin babban yatsa da karamin yatsa lokacin da hannu ya miko. Yahweh ana magana akan sanin tsawon sama ana maganarsa kamar ya auna shi da hannunsa.
Anan kalmar "hankali" bawai tana nufin tunanin Yahweh bane kawai, amma har da sha'awar sa da kuma motsawar sa.
Wannan tambayar ta zance tana jiran amsar mara kyau kuma tana jaddada cewa babu wanda ya taɓa yin hakan. AT: "Bai taɓa karɓar umarni daga kowa ba."
Wannan tambayar ta tsammani amsar mara kyau kuma tana jaddada cewa babu wanda ya taɓa yin waɗannan abubuwa. AT: "Ba wanda ya koya masa sahihiyar hanyar yin abubuwa. Ba wanda ya koya masa ilimi. Ba wanda ya nuna masa hanyar fahimta."
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) ɗigon ruwa wanda ya faɗo cikin guga ko 2) ɗigon ruwa da yake ɗiga daga guga.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh yana kallon su kamar ƙura a kan ma'auni"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "yana kallon su a matsayin ba komai"
Ishaya ya yi amfani da tambayoyi iri biyu don ya nanata cewa babu wani gunki da za a iya kwatanta shi da Allah. AT: "Babu wani wanda za ku iya kwatanta Allah da shi. Babu wani tsafi da za ku iya kamanta shi."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki.AT: "Shin mutane ba su gaya muku tun farko ba?"
Annabin yayi magana game da Yahweh wanda ya halicci duniya kamar ƙasa gini ne wanda Yahweh ya kafa harsashin gininsa. AT: "daga lokacin da Yahweh ya halicci duniya"
Annabin yayi magana game da Yahweh yana mulkin duniya kamar Yahweh yana zaune akan kursiyi a bisa ƙasa.
Annabin ya kwatanta yadda Yahhweh yake ɗaukan mutane da yadda mutane za su ɗauki ciyawa. Kamar yadda ciyawar ƙanana suke ga humansan adam, haka humansan Adam kanana kuma masu rauni a gaban Allah.
Annabin yayi magana game da Yahweh na cire masu mulki daga mulki kamar dai Yahweh iska mai zafi ce wanda ke bugo shuke-shuke kuma yana sa su bushe.
Wannan magana yana fadada kwatancin masu mulki kamar shuke-shuke da Yahweh kamar iska mai sa su bushe. Iskar hukuncin Yahweh za ta kawar da shuke-shuke da suka bushe kamar yadda iska take kwashe ciyawa.
Yahweh yayi amfani da tambayoyi iri biyu masu maimaita magana don jaddada cewa babu wani kamarsa. AT: "Babu wani wanda za ku iya kwatantani da shi. Babu wani wanda nake kama da shi."
Wannan babbar tambaya ce wacce ke tsammanin amsar, Ya Yahweh. AT: "Yahweh ne ya halicci dukkan waɗannan taurari!"
Kalmomin "girman ƙarfinsa" da "ƙarfin ikonsa" sun zama ninki biyu wanda ya nanata ikon Yahweh. AT: "Da ƙarfinsa da ƙarfinsa mai ƙarfi"
Wadannan kalmomin guda biyu duk suna nufin mutanen Isra'ila. AT: "Me yasa kuke ce, ya jama'ar Isra'ila"
Ba a ambaci Yahweh ba tare da sanin abin da ya same su ba kamar Yahweh bai ga hanyar da suke tafiya ba. AT: "Yahweh bai san abin da ya faru da ni ba"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Allahna ba ya damuwa da wasu da ke zaluntata" ko kuma 2) "Allahna bai damu da ya bi da ni dai-dai ba."
Waɗannan layi biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa Yahweh yana ƙarfafa waɗanda ba su da ƙarfi.
Mutanen da suke samun ƙarfi daga Yahweh ana maganarsu kamar mutane suna iya tashi kamar gaggafa suna tashi. Mikiya tsuntsu ne da ake yawan amfani dashi azaman alama don ƙarfi da ƙarfi.
Wadannan layuka guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. Mutanen da suke samun ƙarfi daga Yahweh ana maganarsu kamar suna iya gudu da tafiya ba tare da gajiya ba.
1"Ku yi shiru ku kasa kunne gare ni, ku manisantan ƙasashe; bari ƙasashe su sabunta ƙarfinsu; bari su matso kusa su yi magana; bari mu taru ga yin jayayya a kan saɓanin.2Wane ne wannan da ya motso wani daga gabas, ana kiransa cikin adalci ga aikinsa? Ya bada ƙasashe a gare shi ya kuma taimaka masa har ya yi nasara a kan sarakuna. Ya maida su ƙura da takobinsa, kamar ciyawar da iska ta hure da bakansa.3Yana biye da su har ma ya wuce lafiya, da sauri ƙwarai da ƙyar ƙafarsa take taɓa ƙasa.4Wane ne yasa wannan ya faru kuma su wane ne suka yi waɗannan ayyuka? Wane ne ya kirawo tsararraki tun daga farko? Ni, Yahweh, na farko, da na ƙarshe, Ni ne shi.5Tsibirai sun gani kuma sun ji tsoro; ƙarshen duniya ta girgiza; sun nufo har sun zo.6Kowanne ya taimaki makwabcinsa, kowanne kuma ya cewa ɗayan, 'Yi ƙarfin hali.'7Masassaki yana ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma wanda ya ke aiki da guduma yana ƙarfafa shi wanda ya ke aiki da tubalin ƙarfe, haka nan ya ke cewa mai walda, yana da kyau.' Suna buga ƙusoshi masu ƙarfi domin kada su tuntsure,8Amma kai, Isra'ila, bawana, Yakubu wanda na zaba, zuriyar Ibrahim abokina,9kai wanda na kawo ka daga maƙurar duniya, kuma wanda na kira daga wurare masu nisa, wanda na ce, 'kai ne bawana,' Na zaɓe ka ban kuma ƙi ka ba.10Kada ka ji tsoro, ina tare da kai. Kada ka damu da komai, ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka, zan kuma taimake ka, zan tallafe ka da hannunna na dama mai adalci.11Duba, za su ji kunya da ƙasƙanci, dukkan su da suke fushi da kai; za su zama ba komai ba za su kuma lalace, waɗannan da suke gãba da kai.12Za ka neme su amma ba za ku same su ba; wato waɗanda suke gãba da kai; za su zama kamar ba komai ba, ba bu shakka za su zama ba komai ba.13Gama Ni, Yahweh Allahnku, zan riƙe ka da hannun dama, ina faɗi maka, 'Ka da ka ji tsoro; ina taimakonka.'14Kada ka ji tsoro, kai tsutsa Yakubu, da ku mutanen Isra'ila; zan taimake ku - wannan furcin Yahweh ne, mai fansarku, Mai Tsarki na Isra'ila.15Duba, zan sa ku zama kamar ceburin sussuka mai kaifi, sabo mai baki biyu; za ku sussuke tsaunuka ku lalatar da su; za ku niƙe tuddai kamar ƙaiƙayi.16Za ku sheƙesu, iska kuma zata hure su; iska kuma zata warwatsa su. Za ku yi murna cikin Yahweh, za ku yi murna a cikin Mai Tsarki na Israi'la.17Waɗanda ake takurawa da mabuƙata za su nemi ruwa, amma ba bu, harsunansu za su bushe da ƙishi; Ni Yahweh, zan amsa addu'arsu; Ni Allah na Isra'ila, ba zan yashe su ba.18Zan sa kogunan ruwa su yi gudu daga gangare, maɓuɓɓugan ruwa su yi gudu a tsakiyar kwarurruka; zan sa hamada ta zama kududdufan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓuɓɓugan ruwa.19Zan sa itatuwan sida, da gawo su tsiro a jeji, da itacen ci-zaƙi, da itacen zaitun. Zan dasa siferas a hamada, tare da marke da wuraren renon itacen siferas.20Zan yi wannan domin mutane su gani, su sani, su kuma fahimta tare, hannun Yahweh ya yi wannan, Mai Tsarki na Isra'ila ya halitta shi.21"Faɗi maganarka," Inji Yahweh, "Faɗi jayayyarka mai kyau don gumakunka," inji Sarkin Yakubu.22Bari ku kawo ma na jayayyarku; ku zo ga ba ku furta ma na abin da da zai faru, saboda mu san waɗannan abubuwa sosai. Ku sa su faɗa mana yadda furcin za su zama, domin mu yi tunani a kansu mu kuma san yadda su ka cika.23Ku faɗa game da abubuwan da za su faru nan ga ba, domin mu san ko ku alloli ne; ku yi wani abu mai kyau ko bala'i, ko ma cika da jin tsoro ya kuma burgemu.24Ku duba, ku allolin wofi ne kuma ayyukan kuma na wofi ne; wanda ya zaɓe ku ma abin ƙyama ne.25Na ta da wani daga arewa, kuma ya zo; daga fitowar rana na kira shi wanda ya yi kira bisa sunana, wanda zai tattake masu mulki kamar laka, kamar yadda maginin tukwane ya ke tattake yumɓu.26Wa ne ne ya faɗa ma na wannan tun daga farko, ko ma sani? Kafin wannan lokaci, ko mu ce, "Ya yi dai-dai"? Babu ɗayansu da ya yi dokar haka, i, ba kuwa wanda ya ji kuna faɗar wani abu.27Ni ne na farko da na ce da Sihiyona, "Duba ga su a nan;" Na aika manzo zuwa Urshalima.28Sa'ad da na duba, ba bu wani, ko ma a cikinsu wanda zai ba da shawara mai kyau, wanda idan Na yi tambaya, zai iya amsawa da magana.29Duba, dukkansu a wofi su ke, ayyukansu na wofi ne; zubin siffofinsu na ƙarfe adadin iska su ke, wofi ne kuma.
Anan "ni" yana nufin Allah.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya. Na biyu yayi bayanin dalilin na farko. AT: "to, bari su zo kusa don su yi magana kuma su yi magana da ni"
Mayar da su turɓaya da tattaka magana ce ko ƙari don lalata duk abin da mutanen waɗannan ƙasashe suka yi. Sojojin mutum ɗaya daga gabas za su ci waɗannan ƙasashe da warwatsa mutane a sauƙaƙe.
"Mai mulki daga gabas yana bin al'umman duniya"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa shi ne ya yi waɗannan abubuwa. AT: "Na aiwatar kuma na cika waɗannan ayyukan."
Anan kalmar "tsararraki" tana wakiltar duk tarihin ɗan adam, wanda Yahweh ya ƙirƙira kuma ya tsarashi cikin tarihi. Tambayar magana tana jiran amsar, Yahweh. AT: "Na tattara al'ummomin bil'adama tun daga farko."
Kuna iya fassara "tsibirai" kamar yadda kuka fassara "yankunan bakin teku" a cikin Ishaya 41:1.
Wuraren da suke nesa da duniya ana maganarsu kamar su ne wuraren da duniya ta kare. A "wurare mafi nisa na duniya"
Anan "shi" yana nufin gunkin da suka yi.
Waɗannan layuka biyu suna da ma'ana ɗaya kuma suna jaddada cewa Yahweh yana dawo da Isra'ilawa zuwa ƙasarsu daga ƙasashe masu nisa.
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Jumla na biyu a cikin maganganu marasa kyau abin da na farko ya faɗi a cikin kyakkyawar magana.
Ana magana akan ƙarfafa Yahweh ga mutanensa kamar yana riƙe da su da hannunsa.
"duk waɗanda suka yi fushi da kai za su ji kunya da kunya"
"waɗanda suka yi hamayya da ku za su zama kamar komai kuma za su hallaka"
Ana magana akan Yahweh yana taimakon Isra'ilawa kamar yana riƙe da hannun dama.
Anan "Yakubu" da "mutanen Isra'ila" ma'ana ɗaya ce. AT: "Ya ku mutanen Isra'ila da kuke kamar tsutsotsi"
Duba yadda kuka fassara wannan jumlar a cikin Ishaya 1: 4.
Yahweh yayi magana game da baiwa Isra’ila damar cin magabtansu kamar yana mai da al’ummar masussuka wanda zai daidaita tsaunuka.
Wannan kwatanci ne na biyu. Tsaunuka kwatanci ne na hatsi, kuma hatsi masussuka ishara ce ga Isra’ilawa da suka ci ƙasashe maƙiyan maƙiyan da ke kusa da su. AT: "zaku tumɓi maƙiyanku ku fatattake su kamar hatsi ne, duk da cewa sun yi ƙarfi kamar duwatsu"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya. AT: "iska za ta kwashe su"
Yahweh yana magana ne game da mutanen da suke cikin tsananin buƙata kamar suna ƙishi ƙwarai, da kuma tanadin da ya yi musu kamar ya sa ruwa ya bayyana a wuraren da yawanci ba zai bayyana ba.
Waɗannan nau'ikan bishiyoyi ne.
Anan kalmar "hannu" tana wakiltar Yahweh da kansa. AT: "Yahweh ya yi wannan"
A cikin waɗannan ayoyin, Yahweh yana ba'a da mutane da gumakansu. Yana ƙalubalantar gumaka don faɗin abin da zai faru a nan gaba, amma ya san ba za su iya ba.
Kalmomin "mai kyau" da "mugunta" suna haifar da haɗin kai kuma suna wakiltar komai. AT: "ku yi komai kwata-kwata"
Anan "ku" jam'i ne kuma yana nufin gumaka. AT: "mutumin da ya zaba muku gumaka"
Yahweh yayi maganar nada mutum kamar ya tayar da mutumin. AT: "Na nada guda ɗaya"
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) cewa wannan mutumin ya roƙi Yahweh don nasararsa ko 2) cewa wannan mutumin yana bauta wa Yahweh.
"Lallai, babu wani daga gumaka da ya hukunta shi. Lallai, ba wanda ya ji ku gumakan suna faɗin wani abu"
"ba gunki ɗaya ba"
Yahweh yayi magana akan rashin darajar gumakan kamar gumakan iska ne kuma babu komai. AT: "gumakansu duk basu da amfani"
1Duba, bawana, wanda na riƙe; zaɓaɓɓena, wanda na ke jindaɗin sa. Na sa Ruhuna a bisansa; za ya kawo hukunci ga al'ummai.2Ba za ya yi kuka ko sowa ba, ko ya sa a ji muryarsa a tituna ba.3Murzajjen kara ba za ya karya shi ba, lagwanin da ba ya ci sosai ba za ya ɓice shi ba: a cikin aminci za ya zartar da hukunci.4Ba za ya suma ba ko ya karaya har sai ya kafa hukunci a duniya; Ƙasashen tsibirai kuma suna jiran shari'arsa.5Ga abin da Allah Yahweh ya faɗa - shi wanda ya halicci sammai kuma ya shimfiɗasu, shi wanda ya yi duniya da dukkan abin da take fitarwa, shi wanda ya ke bayar da numfashi ga mutanen dake cikin ta da kuma rai ga waɗanda ke zaune a cikin ta:6"Ni, Yahweh, na kira ka cikin adalci kuma zan ri ƙe hannunka. Zan kiyayeka in sanya ka alƙawari domin mutane, haske kuma ga al'ummai,7Domin a buɗe idanun makafi, za a sako da 'yan kurkuku daga can cikin kogo da kuma waɗanda aka tsare a gidan tsaro waɗanda ke zaune a cikn duhu.8Ni ne Yahweh, sunana kenan; bazan raba ɗaukakata da wani ba ko yabona da sassaƙaƙƙun gumaka.9Duba, abubuwan da suka wuce sun faru, yanzu ina gaf da furta sabobbin al'amura. Kafin su fara afkuwa zan gaya maku game da su."10Ku raira sabuwar waƙa ga Yahweh, da kuma yabonsa daga ƙarshen duniya; ku waɗanda ke gangarawa zuwa teku, da dukkan abin da ke ciki, ƙasashen tsibirai da dukkan mazaunan cikin su.11Bari hamada da biranenta su koka, ƙauyuka kuma inda keda ke zaune, ku yi sowa ta farinciki! bari mazauna Sela su raira; bari su yi sowa daga ƙololuwar tsaunuka.12Bari su bada ɗaukaka ga Yahweh su kuma furta yabonsa a ƙasashen tsibirai.13Yahweh za ya fita a matsayin mayaƙi; a matsayin mutumin yaƙi za ya motsa himmarsa. Za ya yi sowa, I, za ya yi kururuwar koke-koken yaƙinsa; za ya nuna wa maƙiyansa ikonsa.14Na yi shiru na dogon lokaci; na tsaya cik na hana kaina; yanzu zan yi kuka kamar macen dake cikin naƙuda; zan yi nishi da huci.15Zan rusar da tsaunuka da tuddai in kuma sa ganyayensu su bushe; zan maida koguna tsibirai in kuma sa lakarsu su bushe.16Zan kawo makafi bisa hanyar da ba su sani ba; bisa tafarkun da ba su san zan bi da su ba. Zan mayarda duhu ya zama haske a gabansu, zan sa karkatattun wurare su miƙe. Zan yi waɗannan abubuwa, ba kuma zan yashe su ba.17Za a komar da su baya, za a san ya su cikin kunya gabaɗaya, wato su waɗanda suka sa dogararsu ga sassaƙaƙƙun siffofi, su waɗanda suke cewa sarrafaffun siffofin ƙarfe, "Ku ne allolinmu."18Ka saurara, kai kurma; ka duba, kai makaho, domin ka sami gani.19Wane ne makaho idan ba bawana ba? ko kurma kamar manzona wanda na aika? Wane ne ya yi makantar abokin alƙawarina, ko makaho kamar bawan Yahweh?20Kana ganin abubuwa da yawa, amma baka fahimta; kunnuwa a buɗe, amma ba bu mai ji.21Ya gamshi Yahweh ya yabawa hukuncinsa kuma yasa shari'arsa a bar ɗaukaka.22Amma waɗannan mutane ne waɗanda a ka yiwa fashi a ka kuma washe su; an datse su dukka a ramuka, sun zama abin washe wa ba bu kuma mai fansarsu, ba bu wanda kuma ya ce, "A maido da su!"23Wane ne a cikin ku za ya saurari wannan? Wane ne za ya saurara kuma ya ji a nan gaba?24Wane ne ya miƙa Yakubu ga ɗan fashi, Isra'ila kuma ga masu kwasar ganima? Ba Yahweh bane, wanda muka yiwa zunubi, wanda suka ƙi tafiya cikin hanyoyinsa, wanda kuma suka ƙi yin biyayya da shari'arsa?25Domin wannan ya zubo da fushinsa mai zafi a bisansu, da masifar yaƙi. Ya haska kewaye da su, amma ba su lura ba; ya ƙona su, amma ba su yi hattara ba a zukatansu.
"Duba, bawana" ko "Ga bawana"
"Tare da wanda nake matukar farin ciki"
Yahweh yayi magana game da mutane marasa ƙarfi da marasa ƙarfi kamar an murƙushe su da busassun sanduna.
Annabin yayi magana game da Yahweh wanda ya halicci sammai da ƙasa kamar sammai da ƙasa ƙyalle ne wanda Yahweh ya shimfiɗa.
Waɗannan jimlolin suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa Yahweh yana ba kowane mutum rai. Kalmar "numfashi" metonym ce ta rayuwa. AT: "yana ba da rai ga mutanen da ke rayuwa a duniya"
Anan "ku" ɗaya ne kuma yana nufin bawan Yahweh.
Ana haifar da makaho da gani kamar ana bude idanunsu ne. Hakanan, Yahweh yayi magana game da bawansa wanda zai ceci waɗanda aka tsare bisa kuskure kamar bawansa yana maido da gani ga makafi. AT: "don bawa makafi damar gani"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Ana iya samar da kalmar a jimla ta biyu. AT: "don sakin fursunoni daga kurkuku, da kuma sakin wadanda suka zauna cikin duhu daga gidan da suke tsare"
Ana iya samar da kalmar daga jimlar da ta gabata. AT: "kuma ba zan raba yabo na ba da gumakan da aka sassaka"
"da dukkan halittun da ke rayuwa a cikin teku, da duk wadanda ke zaune a gabar teku"
Wannan yana nufin mutanen da suke zaune a hamada da biranen.
A nan "su" na nufin mutanen da ke bakin teku.
An gwada Yahweh da jarumi wanda a shirye yake ya fatattaki magabtan mutanensa.
Wadannan layuka guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. Rashin aikin Yahweh an bayyana shi da nutsuwa da nutsuwa.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna nuna cewa Yahweh ya kiyaye kansa daga aiki. AT: "Na kiyaye kaina daga yin komai"
Aikin Yahweh a matsayin jarumi mai ihu ana kwatanta shi da mace mai ciki wacce ke kuka saboda azabar nakuda. Wannan yana jaddada aikin da ba makawa kwatsam bayan tsawon aiki.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "cewa ba su taɓa tafiya ba" ko 2) "waɗanda ba su san su ba."
Yahweh yayi magana akan mutanensa marasa taimako kamar basu gani saboda sunyi tafiya cikin duhu, kuma yana taimakonsu kamar ya sa haske ya haskaka cikin duhun.
Ƙafirta yarda da waɗanda suke bautar gumaka ana magana ne da su kamar yana tilasta su su juya baya ne kuma su juya akasin hakan. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan ƙi su kuma in kunyata su"
Yahweh yayi waɗannan tambayoyin na zance don tsawata wa mutanensa kuma ya nanata cewa babu wani makaho ko kurma kamar su. AT: "Babu wanda ya makanta kamar bawana. Babu wanda ya kurma kamar manzo na wanda na aiko."
Yahweh yayi waɗannan tambayoyin na zance don tsawata wa mutanensa kuma ya nanata cewa babu wani makaho ko kurma kamar su. AT: "Babu wanda ya makanta kamar abokin alkawarina. Babu wanda ya makanta kamar bawan Yahweh."
"Ko da yake kun ga abubuwa da yawa, amma ba ku fahimci abin da suke nufi ba"
Ana magana da ikon ji kamar dai kunnuwa sun bude. A nan kalmar "ji" na nufin fahimtar abin da mutum ya ji. AT: "mutane suna ji, amma babu wanda ya fahimci abin da suka ji"
"Yahweh yana farin cikin girmama adalcinsa ta hanyar daukaka shari'arsa." Kashi na biyu na jimlar yana bayanin yadda Yahweh ya cika kashi na farko.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Amma abokan gaba sun wawashe kuma sun washe wannan mutane"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "makiya sun kama su duka cikin rami sun tsare su a kurkuku"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya. Ishaya yayi amfani da wannan azaman babban tambaya don jaddada amsar da zai bayar a cikin jumla ta gaba. AT: "Zan gaya muku wanda ya ba da Isra'ilawa ga 'yan fashi da ganima."
Anan kalmar "mu" tana nufin mutanen Isra'ila da kuma Ishaya.
Kalmar "su" kuma tana nufin mutanen Isra'ila da Ishaya. Kalmomin guda biyu ma’anarsu daya. A farkon, yin biyayya ga dokokin Yahweh ana magana ne da shi kamar yana tafiya cikin hanyoyin da Yahweh ya umurce su da su bi.
Ishaya yayi magana akan fushin Yahweh kamar wani ruwa ne wanda za'a iya zubowa. AT: "ya nuna musu yadda ya fusata"
Ana iya fassara kalmar "lalata" tare da fi'ili. AT: "ta hanyar lalata su da yaƙi"
Kula da wani abu da kuma koyo daga gare shi ana magana ne kamar yana sanya wannan abu a zuciyar mutum. AT: "ba su ba da hankali ba" ko "ba su koya daga gare ta ba"
1Amma yanzu ga abin da Yahweh ya faɗa, shi wanda ya halicceka, Yakubu, shi wanda ya yi ka, Isra'ila: "Kada ka ji tsoro, gama na fansheka; na kiraka da sunanka, kai nawa ne.2Sa'ad da ka bi ta cikin ruwaye, zan kasance tare da kai; ta cikin koguna kuma, ba za su sha kanka ba. Sa'ad da ka yi tafiya ta cikin wuta ba za ka ƙone ba, harsashen wutar kuwa ba za ya lalatar da kai ba.3Gama ni ne Yahweh Allahnka, mai tsarki na Isra'ila, mai cetonka. Na ba da Masar diyya a kanka, Itiyofiya da Seba misanya dominka.4Tunda kana da tamani da muhimmanci a idanuna, ina ƙaunarka; saboda haka zan bayar da mutane misanya dominka, wasu mutanen kuma misanya domin rayuwarka.5Kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; zan kawo zuriyarka daga gabas, in tattaro ka daga yamma.6Zan cewa arewa, 'Miƙosu,' kudu kuma, 'Kada ka riƙesu,' A kawo 'ya'yana maza daga ne sa, 'ya'yana mata kuma daga lungun sassan duniya,7dukkan wanda ake kira da sunana, wanda na halitta domin ɗaukakata, wanda na yi, I, wanda na halitta.8Fito da mutane makafi, koda ya ke suna da idanu, da kuma kurame, koda ya ke suna da kunnuwa.9Dukkan al'ummai ku tattaru wuri ɗaya, dukkan mutane kuma ku taru. Wane ne a cikinsu za ya furta wannan, ya kuma yi mana shelar al'amuran farko? Bari su kawo shaidunsu su tabbatar da gaskiyarsu, bari su saurara su kuma tabbatar, 'Gaskiya ne.'10Ku ne shaiduna," Yahweh ya furta, "Bawana kuma wanda na zaɓa, domin ku sani ku kuma gaskata da ni, ku kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu wani allah da a ka yi, kuma ba za ayi wani ba bayana.11Ni, ni ne Yahweh, kuma babu wani mai ceto sai ni.12Na furta, na ceto, kuma na yi shela, kuma babu wani allah a tsakaninku. Kune shaiduna," Yahweh ya furta, '"Ni ne Allah.13Daga wannan rana har zuwa nan gaba ni ne shi, kuma babu wanda za ya ceci wani daga hannuna. Na aikata, wane ne za ya canza?"14Wannan ne abin da Yahweh yace, Mai fansarku, Mai tsarki na Isra'ila: "Sabili da ku na yi aike a Babila na turasu dukka zuwa gudun hijira, na maida farincikin Babiloniyawa zuwa waƙoƙin makoki.15Ni ne Yahweh, Mai tsarkinku, Mahaliccin Isra'ila, Sarkinku."16Wannan shi ne abin da Yahweh yace (Wanda ya buɗe hanya ta cikin teku da kuma tafarki ta cikin manyan ruwaye,17wanda ya bida karusa da doki, sojoji da babbar runduna. Suka faɗi tare; ba za su sake tashi ba; an kawar da su, aka ɓice su kamar lagwanin da ke ci.)18Kada ku yi tunani akan waɗannan abubuwa da suka wuce, ko ku kula da abubuwan dã can.19Duba, ina gaf da yin sabon abu; yanzu ya fara faruwa; ba ku yi la'akari ba? zan yi hanya a hamada da magudanan ruwa a cikin jeji.20Dabbobin jeji za su girmamani, diloli da jiminai, saboda na bayarda ruwa a jeji, da koguna a hamada, domin zaɓaɓɓun mutanena su sha,21waɗannan mutane waɗanda na yi su domin kaina, domin su maimaita yabbaina.22Amma ba ku yi kira gare ni ba, Yakubu; kun gaji da ni, Isra'ila.23Ba ku kawo mani ko ɗaya daga cikin tumakinku ba a matsayin baye-bayen ƙonawa, ko kuka girmamani da hadayunku ba. Ban ɗora maku nauyin baye-bayen hatsi ba, ko na gajiyar daku da kawo turare.24Ba ku sawo mani ƙiraren ƙanshi da kuɗi ba, ko kuwa ku zubo mani kitsen hadayunku ba; amma kuna ɗoramani nauyin zunubanku, kun gajiyar da ni da miyagun ayyukanku.25Ni, I, Ni, Ni ne wanda na ke share kurakuranku sabili da ni; kuma bazan sake tunawa da zunubanku ba.26Ku tuna mani da abin da ya faru, bari mu yi mahawara tare; ku kawo ƙararku, domin a tabbatar da ku marasa laifi.27Ubanku na farko ya yi zunubi, kuma shugabanninku sun yi mani laifi.28Saboda haka zan gurɓata tsarkakan shugabanni; zan miƙa Yakubu ga lalacewa ɗungum, Isra'ila kuma ga wulaƙantaccen ƙasƙanci."
Duk sassan jumlar abu daya suke nufi. AT: "wanda ya halicce ku, ya jama'ar Isra'ila"
Waɗannan maganganun guda biyu ma'anarsu ɗaya ce kuma suna ƙarfafa cewa mutane ba za su sami lahani ba saboda Yahweh yana tare da su.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba zai ƙone ku ba"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna jaddada cewa Yahweh zai ba magabcin Isra'ila damar cinye waɗannan al'umman maimakon Isra'ila.
Kalmomin "masu daraja" da "na musamman" ma'anarsu abu ɗaya ne kuma suna nanata yadda Yahweh yake daraja mutanensa. AT: "Saboda kuna da daraja a wurina"
Dukansu jimlolin suna nufin abu ɗaya. AT: "saboda haka zan bar abokan gaba su ci sauran al'ummomi maimakon ku"
Hanyoyin "gabas" da "yamma" suna wakiltar daga kowane bangare. AT: "Zan kawo ku da zuriyar ku daga kowane bangare"
Anan don a kira shi da sunan wani yana wakiltar kasancewa na wannan mutumin. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "duk wanda na kira da suna na" ko "duk wanda yake nawa"
Duk waɗannan suna nufin abu ɗaya kuma suna jaddada cewa Allah ne ya yi mutanen Isra'ila.
Wannan tambayar ta lafazi ta shafi gumakan da mutanen ƙasashe ke bauta wa. Amsar da aka bayar ita ce babu ɗayansu da zai iya wannan. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Babu wani allahnsu da zai iya bayyana wannan ko ya sanar da mu abubuwan da suka gabata."
Yahweh yana ƙalubalantar gumakan da al'ummai suke bauta wa don samar da shaidu waɗanda za su ba da shaidar cewa sun sami damar yin waɗannan abubuwa, kodayake ya san cewa ba za su iya yin hakan ba. AT: "Waɗannan alloli ba su da shaidu da za su tabbatar da gaskiyarsu, shaidun da za su saurara kuma su tabbatar, 'Gaskiya ne'"
Anan kalmar "kafa" tana nuna cewa Yahweh yana magana ne game da gumakan da mutane suka yi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Babu wani daga cikin gumakan da mutane suka kirkira da ya kasance a gabana"
"babu wani daga cikin waɗancan allohi da zai wanzu bayan ni"
"Ni kadai zan iya cetonka"
Anan kalmar “hannu” tana wakiltar ikon Yahweh. AT: "babu wanda zai iya ceton kowa daga hannuna"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar yana cewa babu wanda zai iya juya hannunsa. Ana iya fassara shi azaman bayani. Juyawa baya yayi yana wakiltar dakatar dashi daga yin wani abu. Duba yadda kuka fassara makamancin kalmar a cikin Ishaya 14:27. AT: "babu wanda zai iya mayar da ita." ko "ba wanda zai iya dakatar da ni."
Duba yadda kuka fassara wannan jumlar a cikin Ishaya 1: 4.
Ana iya samarda abin da kalmar "aika" a fassara. AT: "Na aika sojoji zuwa Babila"
"ka saukar da dukkan mutanen Babila 'yan gudun hijira"
Ana maganar mutuwa kamar tana fadowa kasa. AT: "Duk sun mutu tare; ba za su sake rayuwa ba"
Ana magana da mutanen da ke mutuwa kamar suna ƙone fitilun kyandir da wani ya kashe. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "rayukansu sun ƙare, kamar mutum ya kashe wutar kyandir mai ƙuna"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna jaddada cewa ba za su damu da abin da ya faru a baya ba.
Anan dabbobi suna girmama Yahweh kamar mutane.
Yahweh ya ci gaba da magana da Isra'ilawa.
Wannan tsiro ne mai daɗin ƙamshi mai amfani da shi don yin man shafawa. Bai girma a ƙasar Isra'ila ba don haka dole ne mutane su saya daga sauran al'ummomi.
Waɗannan duka abu ɗaya suke nufi kuma suna jaddada gunaguni da Yahweh yake da mutanensa.
Ana maganar gafarar zunubai kamar 1) share su ko share su ko 2) share rubutaccen zunuban. AT: "wanda ya gafarta maka laifukan ka kamar wanda ya goge waniabu" ko "wanda ya gafarta maka laifukan ka kamar wanda ya goge bayanan zunubai"
"tuna"
Yahweh ya kalubalanci mutane su ba da hujja cewa ba su da laifi daga tuhumar da ya gabatar a kansu, kodayake ya san cewa ba za su iya yin hakan ba. AT: "gabatar da shari'arku, amma ba za ku iya tabbatar da cewa ba ku da laifi"
Wannan yana nufin wanda ya kafa Isra'ila kuma yana iya wakiltar ko dai Ibrahim ko Yakubu.
Anan don "miƙa" yana wakiltar saka wani a ƙarƙashin ikon wani. Za a iya fassara kalmar “lalacewa” da kalma ta magana. AT: "Zan sa abokan gaba su hallaka Yakubu gaba ɗaya"
Ana iya samar da fi'ili daga jumlar da ta gabata, wanda da wannan jimlar tare da ita. Za a iya fassara kalmar "ƙasƙanci" tare da jimla ta magana. AT: "Zan ba abokan gaba izini da wulakanta Isra'ila"
1Ka saurara yanzu, bawana Yakubu, da Isra'ila, wanda na zaɓa:2Ga abin da Yahweh yace, shi wanda ya yi ka ya kuma nasa ka cikin mahaifa wanda kuma za ya taimake ka: "Kada ka ji tsoro, bawana Yakubu; da kai kuma, Yeshurun, wanda na zaɓa.3Gama zan zubo da ruwa a bisa ƙasa mai ƙishi, da magudanan ruwa a bisa busasshiyar ƙasa; zan zubo da Ruhuna a bisa zuriyarku, da albarkata a bisa 'ya'yanku.4Za su tsiro daga cikin ciyawa, kamar itatuwan kurmi dake gefen magudanan ruwa.5Wani za ya ce, 'Ni na Yahweh ne,' wani kuma za ya yi kira ga sunan Yakubu, wani kuma zaya rubuta a kan hannunsa, 'Na Yahweh ne,' ya kuma raɗawa kansa suna da sunan Isra'ila."6Wannan ne abin da Yahweh yace - Sarkin Isra'ila da mai fansarsa, Yahweh mai runduna: "Ni ne farko, ni ne kuma ƙarshe; babu kuma wani Allah sai ni.7Wane ne kamar ni? bari ya yi shela kuma ya yi mani bayanin al'amuran da suka afku tunda na kafa mutanen dã, bari kuma su yi bayanin al'amuran da za su zo.8Kada ku ji tsoro ko ku firgita. Ba na furta maku ba tuntuni, na kuma shelarda shi? Ku ne shaiduna: Akwai wani Allah baya gare ni? Babu wani Dutse; bansan da wani ba."9Dukkan masu sarrafa gumakai ba komai bane; abubuwan da suke jiwa daɗi wofi ne; shaidunsu basu gani ko sanin wani abu, kuma za a sa su sha kunya.10Wane ne za ya yi allah ko ya sarrafa gumaka da ke wofi?11Duba, dukkan abokan tarayyar shi za su sha kunya; masu sassaƙa shi mutane ne kawai. Bari su ɗauki matsayinsu tare; za su noƙe kuma za a sa su sha kunya.12Maƙeri na aiki da kayan aikinsa, ya yi su, ya zuga su a garwashi. Ya siffantashi da guduma ya aikatashi da ƙarfin damtsensa. Ya ji yunwa, ƙarfinsa ya ƙare; bai sha ruwa ba sai ya sume.13Kafinta yana gwada katako da abin gwaji, za ya yi mashi zane-zane da abin salo. Da kayan aikinsa zai yi masa siffofi, ya zãne shi da abin zãne. zai yi shi siffa-siffa bisa ga siffar mutum, kamar mutum mai ban sha'awa, domin ya zauna a cikin gida.14Yana saro itatuwan sida, ko ya zaɓo itatuwan sifares ko itacen rimi. Yana ɗaukowa kansa itatuwa daga jeji. Za ya dasa itacen fir ruwan sama kuma za ya sa ya yi girma.15Sai mutum ya yi amfani da shi ya kunna wuta kuma ya ji ɗumi. I, yana kunna wuta ya gargasa gurasa. Daga ciki kuma yana ɗauka ya yi wa kansa allah sai ya rusuna masa; ya yi wa kansa gumaka kuma ya rusuna masa.16Daga cikin katakan yana yin amfani da wasu ya kunna wuta, ya kuma gasa nama a kai. Ya ci ya ƙoshi. yana ɗunɗuma kansa sai ya ce, "Ah, na ji ɗumi, na ga wutar."17Sauran itatuwan da suka rage kuma sai ya yi allah da su, siffar da ya sassaƙa kuma; sai ya rusuna masa yana ba shi girma, sai ya yi addu'a gare shi yana cewa, "Cece ni, gama kai ne allahna."18Ba su sani ba, balle kuma su fahimta, domin idanunsu makafine ba su kuma gani, kuma zukatansu ba su ganewa.19Babu mai yin tunani, ko su yi nazari su ce, "Daga cikin katakon na yi abin wuta da wasu; I, kuma na gasa gurasa bisa garwashin. Na gasa nama bisa garwashin na ci. To ya ya zan ɗauki sauran katakon da ya rage in yi abin ƙazanta da shi domin sujada? Ya ya zan rusuna ga wani kututturen katako?"20Ya yi kamar toka ya ke ci; ruɗaɗɗiyar zuciyarsa ta sa ya kauce. Baya iya ceton kansa, ko kuwa ya ce, "Wannan abin da ke hannun damana ba allahn gaskiya ba ne."21Yi tunani a kan waɗannan abubuwa, Yakubu, da Isra'ila, domin kai bawana ne: na yi ka, kai bawana ne; Isra'ila bazan manta da kai ba.22Na share, ayyukan tawayenka sarai, kamar girgije mai kauri, kamar girgije kuma, zunubanka sun dawo mani, gama na fanshe ka.23Ku raira, ku sammai, gama Yahweh ya yi wannan; ku yi sowa, ku zurfafan duniya. Ku fashe da waƙa, ku tsunuka, kai daji da duk itatuwan da ke cikinka; gama Yahweh ya fanshi Yakubu, kuma za ya nuna ɗaukakarsa a Isra'ila.24Wannan ne abin da Yahweh yace, mai fansarka, wanda ya yi ka daga cikin mahaifa: "Ni ne Yahweh, wanda ya yi dukkan abubuwa, wanda shi kaɗai ya shimfiɗa sammai, shi kaɗai ya sarrafa duniya.25Ni wanda na lalata kayan tsafin masu maganar wofi na kuma wulaƙanta masu karanta kayan tsafin; Ni wanda na juyarda hikimar masu hikima na kuma maida shawararsu wawanci.26Ni, Yahweh, wanda ke tabbatarda maganganun bawansa wanda kuma ke sa hasashen manzanninsa su afku, wanda ya cewa Yerusalem, 'Za a sake zaunawa a cikinki,' da kuma garuruwan Yahuda, 'Za a sake ginaku, kuma zan ɗaga rusassun wurarensu';27wanda ya ke cewa teku mai zurfi, 'Ki bushe, kuma zan busar da igiyoyinki.'28Yahweh ne ya faɗa game da Sairus, 'Makiyayina ne shi, za ya aiwatar da dukkan nufina; za ya zartar da doka game da Yerusalem, 'Za a sake ginata,' game da haikalin, 'Bari a sake kafa harsashensa.'"
Wannan yana nufin zuriyar Yakubu. AT: "zuriyar Yakubu, bayina"
Yahweh yayi magana akan ƙirƙirar al'ummar Isra'ila kamar sun ƙirƙira al'ummar kamar jariri a cikin mahaifar uwarsu. AT: "wanda ya halicce ku, kamar yadda na ƙirƙira jariri a cikin mahaifa"
Ana iya samar da kalmar daga jimlar da ta gabata. AT: "ku, Yeshurun, wanda na zaɓa, kada ku ji tsoro"
Yahweh yayi magana game da bada Ruhunsa ga Isra’ilawa kamar yana sa ruwa ya zubo da rafuka masu gudu a kan sandararriyar ƙasa.
Yahwehi yayi maganar bada Ruhunsa ga mutane kamar dai Ruhunsa yana da ruwa wanda ya zubo musu. AT: "Zan ba Ruhuna ga zuriyarku"
Ana iya samar da kalmar daga jimlar da ta gabata. AT: "Zan kwarara wa 'ya'yanku albarkata" ko "Zan ba da albarkata ga' ya'yanku"
"wani mutum zai ce shi zuriyar Yakubu ne"
"kira kansa zuriyar Isra'ila"
Duba yadda kuka fassara wannan jumlar a cikin Ishaya 1: 9.
Wannan jimlar tana nanata yanayin Yahweh na har abada. Mai iya yiwuwa su ne 1) "Ni ne wanda na fara komai, kuma ni ne mai kawo karshen komai" ko 2) "Ni ne wanda ya rayu koyaushe, kuma nine wanda zan rayu koyaushe."
Yahweh yayi amfani da wannan tambaya ta zance don jaddada cewa babu wani kamarsa. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Idan kowa ya yi zaton shi kaman ni ne, to ya sanar"
Yahweh yayi amfani da maganganu iri biyu don ya ƙarfafa ƙarfafawarsa. AT: "Kada ku ji tsoro"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa shi ne wanda ya annabta abubuwan da suka faru yanzu. Ana iya fassara wannan azaman bayani. Kalmar "sanar" ma'anarta dai-dai take da "ayyanawa." AT: "Na bayyana muku waɗannan abubuwan tuntuni."
Yahweh ya sake amfani da wata tambaya don ya nanata cewa babu wani Allah. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Babu wani Allah sai ni."
"gumakan da suke faranta musu rai ba su da amfani"
Wannan jumlar tana nufin waɗanda suke bautar waɗannan gumakan kuma suke da'awar cewa su shaidun gumakan ne iko. AT yana magana ne game da rashin fahimtar gaskiya kamar su makafi ne. AT: "waɗanda suke ba da shaida ga waɗannan gumakan sune kamar makafi wadanda ba su san komai ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "za su ji kunya" ko "gumakan su za su ba su kunya"
Yahweh yana amfani da wannan tambayar don tsauta wa waɗanda suke yin gumaka. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Wawaye ne kawai zasu kirkiro allah ko su yi gunkin da ba shi da amfani."
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan yana nufin abokan tarayya na mai sana'a da ke yin gunki. AT: "duk abokan aikin mai sana'a" ko 2) wannan yana nufin waɗanda suka haɗa kansu da gunkin ta hanyar bautar shi. AT: "duk waɗanda suke bautar gunki"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "zai ji kunya" (Duba:
"Ku bar su duka su hallara a gabana"
"ƙirƙirar gunki" ko "ƙirƙirar gunkin"
An yi amfani da zaren don zayyano siffar gunkin a cikin katako.
"Kafinta yana sarewa" ko "mai katako yana sarewa"
Wannan ɓangaren jumlar yana faɗi dai-dai da na farkon da ya ƙarfafa shi.
Yahweh yayi magana akan waɗanda basu iya fahimtar wautar bautar gumaka kamar makafi ba.
Anan mutane suna wakiltar ta hanyar "zukatansu." AT: "ba za su iya fahimta ba"
Yahweh ya ce ya kamata wadannan mutane su yiwa kansu wadannan tambayoyin na zance. Tambayoyin suna jiran amsoshi marasa kyau kuma suna nanata irin wautar da mutum zai yiwa waɗannan abubuwan. Wadannan tambayoyin ana iya fassara su azaman maganganu. AT: "Kada yanzu na sanya ... wani abu mai banƙyama don bauta. Kada in sunkuyar da kaina ga sandar itace."
Yahweh yayi magana akan mutumin da yake bautar gunki kamar wannan mutumin yana cin ƙushin itacen itacen da ya yi gunkin. Kamar yadda cin tokar ba ya amfanar da mutum, haka ma bautar gunki.
Zuciya tana wakiltar mutum na ciki. AT: "ya ɓatar da kansa saboda an yaudare shi"
"Mutumin da yake bautar gumaka ba zai iya ceton kansa ba"
Wannan yana nufin mutanen da suka fito daga zuriyar Yakubu, Isra'ila. AT: "ku zuriyar Isra'ila"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba zan manta da ku ba"
Duk wadannan maganganun guda daya suke nufi. Allah ya kawar da zunubansu cikin sauri da sauƙi kamar iska zata iya kwashe gajimare.
Anan Ishaya yayi magana akan bangarori daban-daban na halitta kamar su mutane kuma ya umurce su da su yabi Yawheh.
"ku mafi ƙarancin sassan duniya." Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) cewa wannan yana nufin wurare masu zurfin gaske a ƙasa kamar kogwanni ko kankara kuma ya samar da haɗuwa tare da "sammai" a cikin jumlar da ta gabata ko 2) cewa wannan yana nufin wurin matattu.
Duba yadda kuka fassara wannan kalmar a cikin Ishaya 41:14.
Yahweh yayi magana akan ƙirƙirar al'ummar Isra'ila kamar sun ƙirƙira al'ummar kamar jariri a cikin mahaifar uwarsu. Duba yadda kuka fassara makamancin magana a cikin Ishaya 44: 2. AT: "wanda ya halicce ku, kamar yadda na ƙirƙira jariri a cikin mahaifa"
Yahweh yayi maganar kirkirar sammai kamar suna yarn da ya shimfida. Duba yadda kuka fassara irin wannan magana a cikin Ishaya 42: 5.
Yahweh yana faɗin abu ɗaya sau biyu don jaddada cewa shi kaɗai, Yahweh, yake sa annabceannabce su cika.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane za su sake zama a can"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane za su sake gina su"
Yahweh yayi magana game da mulkin Sairus da kare mutanen Isra'ila kamar dai Sairus makiyayinsu ne.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari mutane su sake gina garin"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Bari mutane su kafa harsashin gininsa"
1Ga abin da Yahweh ya faɗi wa shafaffensa, ga Sairus, wanda nake riƙe da hannun damansa, domin inci ƙarfin al'ummai a gabansa, in tuɓe makaman sarakuna, in kuma buɗe ƙofofi a gabansa, domin ƙofofin su zauna a buɗe:2Zan shiga gabanka in rusar da duwatsu; zan farfasa ƙofofin tagullar in kuma dardatse sandunan ƙarfensu,3zan baka taskokan duhu da kuma dukiyoyin da a ka ɓoye, domin ka sani cewa Ni ne, Yahweh, wanda ya kira ka da sunanka, Ni, Allah na Isra'ila.4Saboda Yakubu bawana, da Isra'ila zaɓaɓɓena, na kira ka da sunanka: Ina baka daraja kaɗan, koda ya ke ba ka sanni ba.5Ni ne Yahweh, babu wani kuma; babu wani Allah sai ni. zan shirya ka domin yaƙi, koda ya ke ba ka sanni ba;6domin mutane susan cewa daga tasowar rana, daga kuma yamma, cewa babu wani allah sai ni: Ni ne Yahweh, babu kuma wani.7Ni na yi haske kuma na halicci duhu; Ina kawo salama in kuma ƙirƙiro bala'i; Ni ne Yahweh, wanda ke yin dukkan waɗannan abubuwa.8Ku sammai, ku kwararo ruwa daga sama! bari sararin sammai su kwararo da adalci. Bari duniya ta shanyesu, domin ceto ya tsiro, da adalci kuma su yi girma tare. Ni, Yahweh, na halicce su dukka.9Kaiton duk wani wanda ke gardama da wanda ya halicce shi, ga wanda ya ke kamar kowacce tukunyar yunɓu a cikin tukwanen yunɓu a ƙasa! yunɓun za ya iya cewa mai yin tukwanen, 'Me kake yi?' ko 'Aikin naka baya da abin riƙewa a jikinsa'?10Kaiton wanda za ya cewa Mahaifi, 'Mahaifin wa kake yi?' ko kuwa ga mace, 'Me kike haihuwa?'11Ga abin da Yahweh yace, Mai Tsarki na Isra'ila, Mahaliccinka: 'Me yasa kake tambayoyi game da abin da zan yi domin 'ya'yana? zaka gaya mani abin da zan yi game da aikin hannuwana?'12Ni na yi duniya kuma na halitta mutum a kanta. Hannuwana ne suka shimfiɗa sammai, kuma na umarci dukkan taurari su bayyana.13Na motsa Sairus cikin adalci, kuma zan miƙar da tafarkunsa dukka. Zai gina birnina; za ya bar mutanena 'yan gudun hijira su koma gida, ba kuma da farashi ba ko cin hanci,'" Yahweh mai runduna ya faɗa.14Ga abin da Yahweh ya faɗa, "Za a kawo maku cinikayyar Masar da fataucin Itiyofiya tare da Sabiyawa, mutane masu doguwar siffa. Za su zama naku. Za su biyo ku, tafe cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku suna roƙonku suna cewa, 'Tabbas Allah na tare daku, babu kuma wani sai dai shi.'"15Hakika kai ne Allah wanda ka ɓoye kanka, Allah na Isra'ila, Mai ceto.16Dukkansu za su kunyata su wulaƙanta tare; masu sassaƙa gumakai za su yi tafiya cikin ƙasƙanci.17Amma Yahweh za ya ceci Isra'ila da madawwamin ceto; ba za ku sake shan kunya ba ko ƙasƙanci.18Ga abin da Yahweh ya faɗa, shi wanda ya halicci sammai, Allahn gaskiya wanda ya ƙirƙiro duniya, ya halittata, ya kafa ta. Ya halittata, ba a matsayin jujiba, Ya zãna ta domin a zauna a cikinta: "Ni ne Yahweh, babu wani kuma.19Ban yi magana a asirce ba, a wani ɓoyayyen wuri; Ban cewa zuriyar Yakubu, 'Ku neme ni a wofi ba!' Ni ne Yahweh, Mai yin magana a gaskiya; Ina furta abubuwan da ke dai-dai.20Ku tattaro kanku ku zo! ku taru wuri ɗaya, ku 'yan gudun hijira daga cikin al'ummai! basu da Ilimi, su waɗanda ke ɗaukar sassaƙaƙƙun siffofi su kuma yi addu'a ga allolin da ba su iya ceto.21Ku zo kusa ku furta mani, ku kawo shaida! bari su yi mugun shirinsu tare. Wane ne ya nuna wannan tundã can? Wane ne ya yi shelar shi? Ba Ni ne ba, Yahweh? Babu wani Allah sai dai ni, Allah baratacce Mai ceto kuma; babu wani baya gare ni.22Ku juyo gare ni ku sami ceto, ku dukkan ƙarshen duniya; gama Ni ne Allah, babu wani kuma.23Na yi rantsuwa da kaina, maganar dokar adalci tawa, kuma ba za ta koma baya ba: 'A gare ni kowacce gwiwa zata durƙusa kuma kowanne harshe za ya rantse.24Za su ce mani, "A cikin Yahweh ne kawai akwai ceto da ƙarfi kuma.""' Ma su jin haushina kuma za su sha kunya.25A cikin Yahweh dukkan zuriyar Isra'ila za su barata; za su yi taƙama a cikinsa.
An yi magana game da Yahweh na taimakon Sairus da kuma sa shi ya yi nasara kamar yana riƙe da hannun dama.
Yahweh yayi magana akan cire matsalolin da zasu iya hana nasarar Cyrus kamar tana daidaita tsaunuka a gabansa.
A nan “duhu” na nufin wuraren da suke ɓoye. AT: "taskoki a wurare masu duhu" ko "taskoki a asirtattun wurare"
Waɗannan duka suna nufin zuriyar Isra'ilawa.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Zan ƙarfafa ku don yaƙi" ko 2) "Zan sa ku in yaƙi."
Tun da rana ta fito a gabas, wannan jumlar tana haifar da raɗaɗi kuma tana nufin ko'ina cikin duniya. AT: "daga kowane wuri a duniya"
Duk waɗannan maganganun suna yin abubuwan yabo waɗanda ke jaddada cewa Yahweh shine mahaliccin komai.
Yahweh yayi magana game da adalcinsa kamar ana ruwan sama a ƙasa, da adalcinsa da cetonsa kamar tsire-tsire waɗanda ke tsirowa a ƙasa.
Yahweh yana magana kansa kamar shi maginin tukwane ne, kuma game da wanda zai yi jayayya da shi kamar dai wannan mutumin da sauran 'yan adam duka tukwanen yumbu ne. AT: "kamar tukunya guda tsakanin sauran tukwanen tukwane da aka warwatse a kasa"
Yahweh yayi wannan tambaya don tsawata wa waɗanda ke jayayya da shi game da abin da yake yi. AT: "Kada yumbu ya ce wa maginin tukwane ... a kansa!"
Yarinyar da ba a haifa ba ya yi waɗannan tambayoyin don ya tsawata wa iyayensa don sun haife shi. Ana iya fassara waɗannan azaman maganganu. AT: "Bai kamata ku zama uba na ba ... Yakamata ku haife ni." ko "Ba ku ba ni uba daidai ... Ba ku ne kuke haifa mini daidai ba."
Duba yadda kuka fassara wannan jumlar a cikin Ishaya 1: 4.
Wannan yana nufin mutanen Isra'ila.
Anan kalmar "hannaye" tana wakiltar Yahweh. AT: "abubuwan da na yi"
Anan kalmar "hannaye" tana wakiltar Yahweh. AT: "Ni ne na"
Yahweh yayi magana akan halittar sammai kamar suna yarn da ya shimfida. Duba yadda kuka fassara irin wannan magana a cikin Ishaya 42: 5.
Anan kalmar "adalci" tana nufin aiki mai kyau. Zai yiwu ma'anoni su ne 1) cewa Yahweh ya zuga Sairus don yin abin da ya dace ko 2) cewa Yahweh daidai ne ya iza Sairus.
Yahweh yayi magana akan kawar da cikas da sa Cyrus ya yi nasara kamar yana daidaita hanyoyin da Cyrus yake tafiya a kansu.
Wannan yana nufin Yerusalem.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutanen Masar, da Kush, da kuma dogayen mutanen Seba, za su kawo muku abin da suka samu da kuma kayan kasuwancinsu"
Kalmomin "kunya" da "ƙasƙantattu" ma'anarsu abu guda ɗaya kuma suna nanata ƙarfin kunya. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Abubuwan bautarsu za su bar su duka suna jin kunya gaba ɗaya"
Rayuwa cikin ci gaba da kaskanci ana maganarsa kamar tana tafiya cikin kaskanci. AT: "za a ci gaba da wulakanta"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "amma ya tsara ta yadda mutane za su iya rayuwa a kanta"
Yahweh ya ci gaba da magana.
mutanen da suka gudu daga gidajensu don haka abokan gaba ba za su kama su ko su kashe su ba
Yahweh yana ci gaba da magana da 'yan gudun hijirar
A nan kalmar "su" tana nufin 'yan gudun hijira daga cikin al'umman da ke bautar gumaka.
Yahweh yana amfani da tambayoyi don jaddada cewa shine ya gaya musu waɗannan abubuwa zasu faru. AT: "Zan gaya muku wanda ya nuna wannan tun da daɗewa. Zan gaya muku wanda ya sanar da shi. Ni ne Yahweh."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ka juyo gare ni zan cece ka"
Anan wannan jumlar tana wakiltar mutanen da suke rayuwa a "iyakokin duniya." AT: "ku da ke rayuwa a mafi nisa a duniya" ko "dukkan ku da kuke rayuwa a duniya"
Kalmomin "gwiwa" da "harshe" suna wakiltar mutane. AT: "Kowane mutum zai durƙusa a gabana, kuma kowa zai rantse"
A nan kalmar '' barata '' ba tana nufin Yahweh ya gafarta zunubansu ba, amma don tabbatar wa al'ummai cewa Isra'ila dai-dai ne ta bauta masa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai baratar da duk zuriyar Isra'ila" ko "Yahweh zai baratar da duk zuriyar Isra'ila"
1Bel ta rusuna, Nebo ta sunkuya; an ɗauke gumakansu a bisa dabbobi da bisashen ɗaukar kaya. Waɗannan gumakai da kuka ɗauko kaya ne masu nauyi a bisa dabbobin da suka gaji.2Gaba ɗaya sun sunkuya ƙasa, durƙushe a ƙasa; basu iya fanso siffofin, su kansu kuma sun tafi cikin bauta.3Ku saurareni, gidan Yakubu, dukkanku ragowar gidan Isra'ila, waɗanda nake ɗauke daku tun kafin a haifeku, a ɗauke tun daga mahaifa.4Har zuwa tsufanku Ni ne shi, kuma zan ɗaukeku har sai gashinku ya zama furfura. Na halicceku kuma zan riƙeku; zan ɗaukeku kuma zan fansheku.5Da wa za ku kwatantani? da wa kuke tunanin na yi kama, domin ku kwatantamu?6Mutane sukan zubo da zinari waje daga Jaka sukan kuma gwada azurfa a bisa ma'auni. Sai su yi hayar maƙeri, sai ya narka ya yi masu allah; sai su rusuna su kuma yi mashi sujada.7Za su ɗagashi su ɗora a kafaɗa su ɗaukeshi; sai su ajiye a wurin zamansa, zai tsaya a wurin zamansa ba kuma zai matsa daga wurin ba. Za su yi kuka zuwa gare shi, amma ba za ya iya amsawa ba ko kuwa ya ceci wani daga matsalarsa.8Ku yi tunani game da waɗannan abubuwa; kada ku yi watsi dasu, ku fitsararru!9Ku yi tunani game da abubuwan farko, na lokutan da suka wuce, gama Ni ne Allah, babu wani kuma, Ni ne Allah, babu wani kama da ni.10Ina sanar da ƙarshen tun daga farko, tukunna kuma abin da bai riga ya faru ba; Na faɗa, "Shirina za ya faru, kuma zan yi yadda nake so."11Na kira tsuntsun ganima daga gabas, mutumin dana zaɓa kuma daga ƙasa mai nisa; I, na faɗa; Zan kuma aiwatar da shi; ina da manufa, zan kuma aikata.12Ku saurareni, ku mutane marasa ji, waɗanda ke nesa da yin abin dake dai-dai.13Ina kawo adalcina kusa; baiyi nisaba, kuma cetona baya jira; zan bada ceto kuma ga Sihiyona kyauna kuma ga Isra'ila.
gumakan da ke wakiltar Bel da Nebo
"Bel da Nebo ba za su iya ceton hotunansu ba"
Ishaya yayi magana akan mutanen da suke ɗauke da gumakan nan kamar ana kwashe allolin ƙarya waɗanda suke wakilta zuwa bauta.
Anan “ni” yana nufin Yahweh.
Yahweh yayi magana akan taimako da ceton Isra’ilawa kamar yana ɗauke da su. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda na ɗauka"
Yahweh yayi maganar al'ummar Isra'ila sun tsufa sosai kamar sun tsufa tsohuwa.
Yahweh yana amfani da tambayoyi don jaddada cewa babu wani kamarsa. AT: "Babu wani wanda za ku iya kwatanta ni da shi. Ban yi kama da kowa ba, don a kamanta mu."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "domin ku kwatanta mu"
"Su" suna nufin mutanen da suke yin gumaka kuma "shi" yana nufin gunkin da suka ƙirƙira.
Yahweh ya ci gaba da magana da mutanensa.
Wannan yana maimaita wannan ra'ayin don ƙarfafawa. Za a iya samar da fi'ili daga kalmar farko don na biyu. AT: "Ina sanar da ƙarshen tun daga farko, kuma ina sanar da abin da bai riga ya faru ba tukuna"
Wannan maimaita ra'ayi ɗaya don ƙarfafawa.
Yahweh yayi magana akan mutane taurin kai suna aikata ba dai-dai ba kamar suna nesa da aikata abin da ke dai-dai.
Yahweh yayi magana game da ceton mutanensa ba da daɗewa ba kamar cetonsa mutum ne wanda ba ya jiran ya yi aiki. Cikakken sunan "ceto" ana iya fassara shi da kalmar aikatau. AT: "Ba zan jira in cece ku ba"
1Sauko ki zauna cikin turɓaya, ke budurwa ɗiyar Babila; zauna ƙasa babu kursiyi, ɗiyar Kaldiyawa. Baza a sake kiranki mai kwarjini da taushi ba.2Ɗauki dutsen niƙa ki niƙa gari; kware lulluɓinki, ki tuɓe doguwar rigarki, buɗe ƙafafunki, ki tsallake rafuffuka.3Za a buɗe tsiraccinki, I, za a ga kunyarki: I zan ɗauki fansa kuma bazan bar kowa ba.4Mai fansarmu, Yahweh mai runduna sunansa, Mai tsarki na Isra'ila.5Ki zauna shiru ki tafi cikin duhu, ke ɗiyar Kaldiyawa; domin ba za a sake kiranki sarauniyar masarautai ba.6Na yi fushi da mutanena; na lalata gãdona na miƙasu cikin hannunki, amma ba ki nuna masu jinƙai ba; ki ka ɗora kaya mai nauyi bisa tsofaffin mutanen.7Ki ka ce, "Zan yi mulki har abada a matsayin sarauniya ni kaɗai." ba ki yi la'akari da abubuwannan ba a zuciyarki, ba ki kuwa duba yadda za su kasance ba.8To yanzu saurari wannan, ke da kika ƙaunaci annashuwa kika zauna a tsare; ke da kika ce a zuciyarki, "Zan wanzu, babu kuma wani kamar ni; Bazan taɓa zaunawa kamar gwauruwa ba, ko in taɓa fuskantar rashin 'ya'ya ba."9Amma abubuwan nan biyu za su zo maki a lokaci guda a rana ɗaya: rashin 'ya'ya da gwauranci; da cikakken ƙarfi za su afko maki, duk da sihirinki da surkullen ki masu yawa da layunki.10Kin dogara ga muguntarki; ki ka ce, "Babu mai gani na"; hikimarki da iliminki sun kai ki ga hallaka, amma kika ce a zuciyarki, "Na wanzu, babu kuma wani kama da ni."11Bala'i za ya afko maki; ba za ki iya korar shiba da surkullenki. Lalacewa zata faɗo maki; ba za ki iya kawar da ita ba. Babbar hasara zata afko maki nan da nan, kafin ki farga.12Ki yi naciya wurin zuba magungunanki da sihirorinki mãsu yawa waɗanda kika yi aminci wurin nanatawa tun cikin kuruciyarki; watakila za ki yi nasara, watakila za ki kori bala'in.13Kin gaji da yawan zuwa wurin bokayenki; bari su waɗannan mutanen su tashi su ceceki - su waɗanda ke shawagi a sammai suna duba taurari, waɗanda ke furta sabobbin watanni - bari su ceceki daga abin da zaya faru dake.14Duba, za su zama kamar haki, wuta za ta cinye su. Ba za su ceci kan su ba daga cikin harsashen. Babu garwashin da za su ji ɗumi dashi babu kuma wutar da za su zauna a gefe!15Ga abin da za su zama a gare ki, su waɗanda kika yi aiki tare da su, kika yi saye da sayarwa tare da su da ki na yarinya, dukkansu kuma su ka ci gaba da aikata abubuwansu na wawanci; da kika yi kukan neman taimako kuma, ba bu wanda zai iya ƙwato ki."
A cikin wannan surar, Yahweh yana magana da Babila game da faɗuwarsa kamar ita sarauniya ce da aka wulakanta.
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya dai-dai. Zama cikin ƙura alamar wulakanci ne.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane ba za su sake kiran ku da daɗi ko tsattsauran ra'ayi ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Za ku zama tsirara"
Anan kalmar "kunya" kalma ce ta al'aura ga mutum. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane za su ga kunyarku" ko "mutane za su ga al'aurarku" (Duba: da
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "don mutane ba za su ƙara kiranku ba"
Anan "I" yana nufin Yahweh.
Yahweh yayi magana game da Isra'ilawa kasancewar su mallaka ta musamman kamar dai su ne gadon sa ko gadon sa. AT: "Na ƙazantar da mutanena, waɗanda su ne mallaka ta musamman"
Anan kalmar “hannu” tana wakiltar ikon Babila. AT: "Na sanya su ƙarƙashin ikonku"
Babila tayi magana game da mulki na har abada akan al'ummu da yawa kamar sarauniya ce da zata yi sarauta har abada.
Wannan yana magana ne game da ɓacin ran Babila yayin tunanin cewa ba za ta taɓa rasa matsayinta na wadata da mutunci ba. AT: "waɗanda suke tsammanin kuna da lafiya"
"Ba zan taɓa zama bazawara ba"
"kwatsam a lokaci guda"
Yahweh ya ci gaba da yin magana da Babila game da faɗuwarsa kamar ita sarauniya ce da aka wulakanta.
Anan kalmar "zuciya" tana nufin mutum ne na ciki. AT: "ka ce wa kanka"
Yahweh yayi magana game da masifa kamar wanda ya ci Babila. AT: "Za ku fuskanci bala'i" (Duba: figs+metaphor)
Yahweh yayi magana cewa ana lalata Babila kamar dai lalata abu ne wanda ya faɗo kan birnin. AT: "Za ku fuskanci hallaka" ko "Wasu za su hallaka ku"
Yahweh ya yi wa Babila ba'a ta wurin gaya mata ta ci gaba da yin sihiri don ta guji abubuwa marasa kyau, amma ya san cewa hakan ba zai taimaka mata ba.
Yahweh yana kwatanta masu sihiri da matsafa da ciyawar da ke ci da sauri cikin wuta. Wannan yana nufin cewa Yahweh zai hallaka su cikin sauƙi kamar yadda wuta ke cin ciyawa, don haka ba su da ikon ceton Babila.
Yahweh ya jaddada cewa wannan wuta ce mai hallakarwa ta hanyar faɗi cewa ba shine wanda mutane zasuyi amfani dashi don ɗumi kansu ba.
1Ku saurara, ya gidan Yakubu, waɗanda a ke kira da suna Isra'ila, waɗanda kuma kuka fito daga tsatson Yahuda; ku da kuka yi rantsuwa da sunan Yahweh kuka kuma tono Allahn Isra'ila, amma bada gaske ba ko kuma ta hanyar adalci.2Domin suna kiran kansu mutanen birni mai tsaki masu dogara kuma ga Allahn Isra'ila. Yahweh mai runduna ne sunansa.3Na furta abubuwa tunda daɗewa; sun fito daga bakina, na sa a sansu, sai nan da nan kuma na yi su, su ka kuma kasance.4Saboda na sani ku masu taurinkai ne, tsokar wuyanku ta cije kamar karfe, goshinku kuma kamar tagulla,5domin wannan na furta waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na sanardaku, domin kada ku ce, 'Gunkina ya yi wannan,' ko kuwa 'Sassaƙaƙƙen siffana ko sarrafaffen siffar ƙarfena ya ƙaddara waɗannan abubuwa.'6Kun ji game da waɗannan abubuwa; ku duba dukkan alamunnan; kuma ku, ba za ku yarda da cewa abin da na faɗi gaskiyane ba? Daga yanzu zuwa nan gaba, zan nunamaku sabobbin abubuwa, ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.7Yanzu, ba daga baya ba, za su kasance, kuma kafin yau ba ku taɓa ji game da su ba, saboda haka ba za ku iya cewa, 'I, na san da su ba.8Ba ku taɓa ji ba; ba ku sani ba; ba a bayyana abubuwan nan a kunnuwanku ba kafin yanzu. Domin na san ku macutane sosai, kuma ku masu taurinkai ne tunda a ka haife ku.9Sabili da sunana zan yi jinkirin fushina, domin darajata kuma zan dakata daga lalatar daku.10Duba, na tãce ku, amma ba kamar azurfa ba; Na tsarkakeku cikin garwashin azaba.11Sabili da kaina, sabili da kaina zan aiwatar; domin tayaya zanbar sunana ya wulaƙanta? ba zan bayar da ɗaukakata ga wani dabam ba.12Ku saurareni, Yakubu, da Isra'ila, wanda na kira: Ni ne shi; Ni ne farko, Ni ne kuma ƙarshe.13I, hannuna ya kafa harsashen duniya, hannun damana kuma ya shimfiɗa sammai; Idan na yi kira gare su, suna tashi tsaye tare.14Ku tattara kanku, dukkanku, ku saurara! wane ne a cikinku ya yi shelar waɗannan abubuwa? Wanda Yahweh ya zaɓa za ya cika nufinsa a kan Babila. Za ya aiwatar da nufin Yahweh a kan Kaldiyawa.15Ni, na faɗa, I, na kiraye shi, na kawo shi, kuma za ya yi nasara.16Ku zo kusa da ni, ku saurari wannan: Tun daga farko ban yi magana a asirce ba; sa'ad da ya faru, ina nan." Yanzu Ubangiji Yahweh ya aike ni, da Ruhunsa kuma.17Ga abin da Yahweh, Mai fansarku, Mai tsarki na Isra'ila ya faɗa, "Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ke koya maku yadda za ku yi nasara, wanda ke bida ku a hanyar da za ku bi.18Inda ace kawai kunyi biyayya da dokokina! da salamarku da wadatarku sun malala kamar kogi, cetonku kuma kamar raƙuman teku.19Da yawan zuriyarku yakai kamar rairayi, 'ya'ya kuwa daga mahaifarku kamar ƙwayoyin rairayi; da baza a datse sunansu ba ko kuwa a gogesu daga gabana.20Ku fito daga Babila! ku tsere daga Kaldiyawa! da ƙarar kuka mai ƙaraurawa ku yi shelar shi! ku sanar da wannan, ku sa ya bazu zuwa iyakar duniya! Ku ce, 'Yahweh ya fanshi bawansa Yakubu.'21Ba su ji ƙishi ba da ya bida su ta cikin jeji; Ya sa ruwa ya kwararo daga dutse dominsu; Ya fasa dutse, ruwayen kuwa suka ɓulɓulo.22Babu salama ga mugu - inji Yahweh."
Anan "gida" yana nufin zuriyar Yakubu. AT: "zuriyar Yakubu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki.AT: "wanda kowa yake kiran mutanen Isra'ila"
"kira ga Allah na Isra'ila"
Wannan yana nufin Yerusalem.
"Baki" yana nufin wani yana magana. AT: "Na yi magana da waɗannan abubuwa"
Wannan yana faɗin abu ɗaya sau biyu don ƙarfafawa.
Yahweh yayi amfani da tambaya don tsawata wa Isra'ilawa saboda rashin yarda da abin da ya kamata su sani gaskiya ne. AT: "kuna da taurin kai kuma ba za ku yarda da abin da na faɗa gaskiya ne ba."
Yahweh yayi magana akan bayanin abu kamar yana bayyana shi. Kalmar "kunnuwa" tana wakiltar mutanen da suke sauraro. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ban bayyana muku waɗannan abubuwan ba tukunna"
Yahweh yayi maganar farkon al'ummar kamar dai ita ce haihuwarta.
Anan kalmar "suna" tana nufin sunan Yahweh. AT: "Saboda suna na zan jinkirta fushina"
Wannan bangare na jimla yana nufin abu guda kamar na farko.
Yahweh yayi magana akan amfani da wahala don tsarkake mutanensa kamar suna da karafa masu tamani kuma wahala masifa ce wacce yake tata su.
Duk waɗannan biyu suna magana ne ga mutanen Isra'ila.
Wannan jimlar tana nanata yanayin Yahweh na har abada. Mai iya yiwuwa su ne 1) "Ni ne wanda na fara komai, kuma ni ne mai kawo karshen komai" ko 2) "Ni ne wanda ya rayu koyaushe, kuma nine wanda zan rayu koyaushe. " Duba yadda kuka fassara makamancin wannan jimla a cikin Ishaya 44: 6.
Anan “hannu” yana nufin Yahweh. AT: "Na aza harsashin ginin duniya, kuma na shimfida sammai"
Yahweh yayi amfani da wata tambaya don ya nanata cewa gumakan ba su faɗi waɗannan abubuwan ba. AT: "Babu ɗayan gumakanku da ya gaya muku wannan."
Anan "ally" yana nufin Cyrus. Duk waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya kuma ana amfani dasu don ƙarfafawa.
Ana iya bayyana wannan da kyau. AT: "Na yi magana a bayyane kuma karara"
Anan “naka” yana nufin mutanen Isra’ila.
Yakan koya wa mutane yadda za su yi rayuwa ana maganarsu kamar yana jagorantar su ne su bi kan madaidaiciyar hanyoyi.
Yahweh ya bayyana wani abu da zai iya faruwa amma bai faru ba.
Ana iya samar da kalmar daga jimlar da ta gabata. AT: "cetonka zai gudana kamar raƙuman ruwan teku"
Yahweh yayi magana akan zuriyar Bani Isra'ila kamar 'ya'yan da al'ummar ta haifa.
Ana maganar mutanen Isra'ila ana halakarwa kamar ana yanke sunansu, kamar yadda mutum zai yanke yanki ko yanke reshe daga itace, ko gogewa. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Da ban yanke sunansu ba, ban kuma shafe su ba"
Wuraren da suke nesa da duniya ana maganarsu kamar su ne wuraren da duniya ta kare. Wannan jumlar kuma tana haifar da merism kuma tana nufin ko'ina a tsakanin ƙarshen. AT: "zuwa duk wurare mafi nisa na duniya" ko "zuwa duk duniya"
Wannan yana nufin zuriyar Yakubu. AT: "mutanen Isra'ila, bayinsa"
Wannan yana nufin wani abin da ya faru a tarihin mutanen Isra'ila lokacin da Yahweh ya kula da su yayin da suke zaune a cikin hamada bayan sun tsere daga Masar.
1Ku saurare ni, ku dake gaɓar tekuna! ku kasa kunne gare ni, ku manisantan mutane. Yahweh ya kira ni tun da a ka haife ni da suna na, sa'ad da mahaifiyata ta kawo ni cikin duniya.2Ya maida bakina kamar takobi mai kaifi; ya ɓoye ni a inuwar hannunsa; ya maida ni gogaggiyar kibiya; a cikin kwarinsa ya ɓoye ni.3Ya ce mani, "Kai bawana ne, Isra'ila, wanda ta wurinka ne na nuna ɗaukakata."4Amma sai na ce, "Koda ya ke nayi zaton nayi aiki a banza, na ɓata karfina a banza, duk da haka adalcina yana ga Yahweh, kuma sakamakona na gun Allahna."5Yanzu Yahweh ya yi magana - wanda ya sifanta ni daga haihuwata in zama bawansa, za ya maida Yakubu kuma gare shi, domin a tattaro Isra'ila zuwa gare shi, gama an ɗaukaka ni a gaban Yahweh, kuma Allahna ya zama ƙarfina -6sai ya ce, "Abu mafi ƙanƙanta kai ka zama bawana da zan sa ya sake kafa kabilun Yakubu, ya kuma farfaɗo da tsirarrun Isra'ila. Zansa ka zama haske ga Al'ummai, domin ka zama cetona ga duk karshen duniya."7Wannan ne abin da Yahweh yace, mai 'Fansar Isra'ila, Mai Tsarkin Nan nasu, gare shi wanda a ka rena ransa, al'ummai suka ƙi shi, da kuma barorin masu mulki, "Sarakuna za su ganka su miƙe, kuma "hakimai za su ganka su rusuna, saboda Yahweh mai aminci ne, wato Mai Tsarkin nan na Isra'ila, wanda ya zaɓe ka."8Ga abin da Yahweh ya faɗi, "A lokacin dana shirya nuna tagomashina zan ba ka amsa, kuma a ranar ceto zan taimake ka; zan yi maka kariya, in kuma bada kai a matsayin alƙawari domin mutanen, domin a sake gina ƙasar, a kuma sake raba gãdon da ya lalace.9Za ka cewa 'yan kurkuku, 'Ku fito waje;' ga waɗanda ke ramuka masu duhu, 'Ku nuna kanku.' Za su yi kiwo a hanyoyi, kuma dukkan sararin gangare zai zama makiyayarsu.10Ba za su ji yunwa ko ƙishi ba, ko kuwa zafi ko rana ta buge su, domin shi mai yi masu jinƙai zai jagorance su; zai bishe su har ga maɓulɓulan ruwa.11Daga nan zan sa dukkan tsaunuka su zama hanya, in kuma sa karafku su zama miƙaƙƙu."12Duba, waɗannan za su zo daga nesa, waɗansu daga arewa da yamma; waɗansu kuma daga ƙasar Sinim.13Ku yi waƙa, sammai, da murna, duniya; fashe da waƙoƙi ku duwatsu! Gama Yahweh zai ta'azantar da mutanensa, ya kuma ji tausayin nãsa masu tsanancin wahala.14Amma Sihiyona ta ce, "Yahweh ya yashe ni, kuma Ubangiji ya manta da ni."15Mace za ta iya mantawa da jaririnta, da ke shan nononta, har ta rasa jin tausayin ɗan da ta haifa? I, za su iya mantawa, amma Ni ba zan manta daku ba.16Duba, na zana sunanki a tafin hannuwa na; katangunki na gabana a kowanne lokaci.17'Ya'yanki suna dawowa da sauri, yayin da waɗanda suka lalatar dake suna watsewa.18Duba kewaye ki gani, suna tattarowa suna zuwa gare ki. Lallai hakika idan ina raye - wannan Yahweh ne ya faɗa -za ki sa su kamar kayan ado, ki kuma sanya su kamar amarya.19Koda shi ke ke lalatacciya ce kuma kufai, ƙasa ce da dã a ka hallakar, yanzu za ki yiwa mazaunan ƙasar ƙanƙanta, kuma masu takura maki za su yi nisa dake.20'Ya'yan da a ka haifa a lokacin da a ka yi maki rashi za su faɗa a kunnuwanki, 'Wurin ya yi mana ƙanƙanta, a yi mana ƙãri, saboda mu zauna a nan.'21Sa'an nan za ki tambayi kanki, 'Wane ne ya haifi waɗannan 'ya'yan domina? An yi mani rashi kuma ni bakarariya ce, mai gudun hijira da sakakkiya ni ke. Wane ne ya yi renon waɗannan yaran? Duba, ni kaɗai a ka bari; daga ina waɗannan suke?"'22Wannan ne abin da Ubangiji Yahweh yace, "Duba, Zan tayar da hannuna ga al'ummai; Zan tayar da tutar alamata ga mutane. Za su zo da 'ya'yanki maza a hannuwansu su kuma taho da 'ya'yanki mata a kafaɗunsu.23Sarakuna za su zama kamar ubanninki, kuma sarauniyoyinsu kamar masu renonki; za su rusuna maki da fuskokinsu ƙasa suna lasar ƙurar ƙafafunki; kuma za ki san cewa ni ne Yahweh; waɗanda suke jira na ba za su kunyata ba."24Za a iya karɓe ganima daga jarumi, ko a ƙubutar da kamammu daga 'yan ta'adda?25Amma ga abin da Yahweh yace, "I, za a karɓe kamammun daga jarumi, kuma a washe ganimar; Gama zan yi tsayayya da magabcinki in kuma ceci 'ya'yanki.26Zan ciyar da masu tsananta maku da naman jikinsu; kuma za su bugu da jininsu, kamar a ce ruwan inabin ne. Sai dukkan 'yan adam su sani cewa Ni, Yaweh, ne mai cetonku da mai fansarku, Maɗaukaki na Yakubu."
Anan kalmar "bakin" tana wakiltar kalmomin da yake fada. An kwatanta kalmominsa da takobi mai kaifi don jaddada cewa za su yi tasiri. AT: "Ya sanya maganata tayi tasiri kamar takobi mai kaifi"
Ana magana game da Yahweh yana kare bawansa kuma ya ɓoye manufarsa kamar hannun Yahweh ya rufe inuwa a kansa.
Bawan Yahweh yana iya aiwatar da ƙudurin Yahweh yadda yakamata ana maganarsa kamar bawan mai kaifi ne, sabo ne.
"Yahweh yace"
"Kai ne bawana, wanda nake kira Isra'ila"
Wannan bangare na jimlar yana nufin daidai da sashin da yake gabanta. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "don dawo da mutanen Isra'ila ga kansa"
Idanu suna wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya girmama ni"
Bawan da ke kawo saƙon Yahweh zuwa ga Al'ummai kuma yana taimaka musu su fahimce shi ana magana ne kamar Yahweh ya sanya bawan haske wanda yake haskakawa tsakanin Al'ummai. Duba yadda kuka fassara makamancin magana a cikin Ishaya 42: 6.
A nan kalmar “rai” tana wakiltar mutumin. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ga wanda mutane suka raina, wanda al'ummai suka ƙi kuma suka riƙe shi bayi"
Anan "ku" yana nufin bawan Yahweh.
Ana iya fassara kalmar "ceto" a matsayin fi'ili. AT: "idan lokaci ya yi da zan cece ku"
Anan kalmar "alkawari" wani magana ga wanda ya kulla ko yin sulhu. Duba yadda kuka fassara makamancin magana a cikin Ishaya 42: 6. AT: "sanya ku matsakanci na alkawari da mutane"
Anan kalmar "ƙasa" tana wakiltar biranen ƙasar da aka lalatar. AT: "don sake gina rusassun wuraren a cikin ƙasar"
Yahweh yayi magana akan mutanen da suke rayuwa cikin yanci da wadata kamar su tumaki da suke da makiyaya da yawa da zasu yi kiwo.
Anan kalmar "zafi" tana bayanin kalmar "rana." Mutanen da ke fama da zafin rana ana maganarsu kamar zafi ya same su. AT: "kuma ba za su wahala daga zafin rana ba"
Yahweh yayi magana kansa a cikin mutum na uku. Yana maganar kare mutane da kula dasu kamar shine makiyayinsu. AT: "Ni, wanda nayi masu rahama ... zan shiryar da su"
Wurin wannan wurin bashi da tabbas, amma yana iya nufin yanki a cikin kudancin Masar.
Ishaya ya juya hankalinsa daga mutanen Isra'ila ya yi magana da sammai, ƙasa, da duwatsu kamar mutane.
Kalmar "Sihiyona" wani suna ne na Yerusalem. Ishaya yayi maganar birni kamar mace ce da ke gunaguni cewa Yahweh ya manta da ita.
Yahweh yana amfani da tambaya don taimaka wa mutanensa su fahimci cewa ba zai taɓa mantawa da su ba ko kuma ya daina kula da su. AT: "Mace ba za ta manta da jaririn da ke shayarwa ba ko kuma ta daina kula da dan da ta haifa ba."
Yahweh ya ci gaba da magana da Sihiyona.
Yahweh yayi magana game da mika wuyarsa ga Sihiyona kamar dai ya rubuta sunanta a tafin hannayensa.
Yahweh yana maganar koyaushe tunanin Sihiyona kamar dai koyaushe ganuwarta tana gabansa. Kalmar "ganuwar" ishara ce ta gari. AT: "Ina ci gaba da tunani game da bangonku" ko "A koyaushe ina tunanin ku"
Yahweh yayi magana akan mutanen da zasu dawo zama a Yerusalem kamar ifya theyan garin. AT: "Mazaunanku suna hanzarin dawowa"
Kalmomin "sharar gida" da "kufai" suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna jaddada cewa abokan gaba sun lalata Sihiyona kuma sun bar ta fanko. AT: "Duk da cewa kun kasance kango gaba ɗaya"
An yi maganar maƙiyin da ke hallaka Sihiyona kamar sun cinye ta. AT: "waɗanda suka hallaka ku"
Yahweh yayi magana game da lokacin da mutanen Yahweh suka kasance cikin ƙaura kamar garin da aka rasa 'ya'yanta. Waɗanda aka haifa yayin da mutane suke gudun hijira ana maganarsu a matsayin 'ya'yan garin. AT: "Waɗanda za su zauna a cikinku, waɗanda aka haifa yayin da mutane suke gudun hijira"
Sihiyona tana magana game da mutanen da suke dawowa su zauna a cikin birnin kamar waɗancan mutanen 'ya'yanta ne. Tambayar ta Sihiyona ta nuna mamakinta cewa yara da yawa yanzu sun zama nata.
Sihiyona ta bayyana kanta a matsayin macen da ba ta iya haihuwar yara ba. Ta nuna dalilan da suka sa ta mamaki.
Bugu da ƙari, Sihiyona ta yi amfani da tambayoyi don bayyana mamakin ta. AT: "Duba, an bar ni ni kaɗai; yanzu duk waɗannan yaran da ban tayar da su ba sun zo wurina."
Yahweh ya ci gaba da magana da Sihiyona kamar dai mace. Ya bayyana yadda ta sami damar samun yara da yawa.
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. AT: "Zan ɗaga hannuna na yi alama da tuta ga mutanen ƙasashe masu zuwa"
Yahweh yayi magana akan mutanen da zasu zauna a Yerusalem) kamar 'ya'yan birni. Ya kuma yi magana game da mutanen wasu ƙasashe suna taimaka wa Isra'ilawa su koma Yerusalem kamar suna ɗauke da Isra'ilawa.
Yahweh yana maganar mutanen da za su zauna a Sihiyona kamar su 'ya'yan birni ne. Kalmomin "iyayen da aka goya su" da "kuyangin mama" na nuni ne ga maza da mata wadanda suka zama masu kula da yara. AT: "Sarakuna da sarauniya na sauran al'ummomi za su samar wa mazaunan ku"
Waɗannan jimlolin suna nuni da isharar da mutane suka yi amfani da ita don bayyana cikakkiyar biyayya ga babba.
Ishaya yayi amfani da tambaya don bayyana wahalar karɓar komai daga hannun jarumi ko jarumi mai ƙarfi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutum ba zai iya karɓar ganima daga jarumi ko ya ceci waɗanda aka kama daga mugayen sojoji ba."
Yahweh ya ce zai yi abin da galibi ba shi yiwuwa mutane su yi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan ɗauki waɗanda aka kama daga jarumi, kuma zan ceci ganimar"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) azzalumai za su ji yunwa har su ci naman abokansu da suka mutu. AT: "Zan sa azzalumanku su ci naman su" ko 2) Yahweh yayi magana akan azzaluman suna yaƙi da hallaka kansu kamar suna cin kansu. AT: "Zan sa azzalumanku su hallaka kansu, kamar suna cin naman nasu"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) azzalumai za su ji ƙishirwa har su sha jinin abokansu da suka mutu. AT: "za su sha abokansu" ™ jini kuma su zama kamar raunanan mutane waɗanda suka bugu da giya "ko 2) Yahweh yana magana game da azzalumai suna yaƙi da hallaka kansu kamar suna shan jinin kansu. AT: "za su zub da kawayensu da yawa jini zai zama kamar suna maye ne da giya"
1Wannan ne abin da Yahweh ya faɗi, "Ina takardar saki da na saki mahaifiyarku? ga waɗanne masu bina bashi na sayar daku? Duba, an sayar daku domin laifofinku ne, domin kuma tayarwarku, a ka kori mahaifiyarku.2Me yasa na zo amma babu kowa a wurin? Me yasa na yi kira amma babu wanda ya amsa? Hannu na ya gajarce ga fansar ku ne? Ko babu iko a gare ni da zan ƙuɓutar da ku? Duba, ga tsautawata na busar da teku; na maida koguna hamada; kifayensu suka mutu domin rashin ruwa suka ruɓe.3Na suturtar da sararin sama da duhu; Na rufe shi da tsummoki."4Ubangiji Yahweh ya bani harshe kamar na ɗaya daga cikin waɗanda a ka koyar dasu, saboda in yi maganar ƙarfafawa ga gajiyayyu; yana farkar da ni daga safiya zuwa safiya; ya kan tasar da kunnena ga saurarawa kamar waɗanda a ka koyar dasu.5Ubangiji Yahweh ya buɗe kunne na, kuma ban zama mai tayarwa ba, ban kuma koma baya ba.6Na bada bayana ga masu bugu na, kuncina kuma ga masu tuge mani gemu; ban ɓoye fuskata ba daga ayyukan ban kunya da tofa miyau ba.7Gama Ubangiji Yahweh zai taimake ni; saboda haka ba zan wulaƙanta ba; don haka na maida fuskata kamar dutsen ƙyastawa, domi na san ba zan kunyata ba.8Shi wanda zai yi mani adalci yana kusa, Wane ne zai yi jayayya da ni? Bari mu tsaya mu fuskanci juna. Wane ne mai tuhuma ta? Bari ya zo kusa da ni.9Duba, Ubangiji Yahweh zai taimake ni. Wane ne zai furta ni mai laifi ne? Duba za su koɗe kamar tufafi; ƙwaro mai cin kaya zai cinye su ɗungum.10Wane ne a cikinku ke tsoron Yahweh? Wane ne ke biyayya da muryar bawansa? Wa ke tafiya a cikin zurfafan duhu ba tare da haske ba? Sai ya dogara da sunan Yahweh ya kuma jingina ga Allahnsa.11Ku duba, dukkan ku masu kunna wuta, masu tanadawa kansu cociloli: ku yi tafiya cikin hasken wuta da harsunan wutar da kuka kunna. Wannan ne abin da ku ka karɓa daga gare ni: za ku kwanta a wurin azaba.
Yahweh ya yi wannan tambayar ta zance domin mutane su samar da “takardar saki,” wanda zai ba da dalilin da ya sa Yahweh ya tura su bauta. AT: "Nuna mini takaddun saki wanda na saki mahaifiyarku da shi."
Yahweh yayi wannan tambayar don ya jaddada cewa bai siyar dasu bane saboda yana bin bashi bashi. Ana nuna cewa wannan shine abin da mutane suka yi tunani. AT: "Ban siyar da ku ba saboda na bin wani bashi."
Yahweh ya ba da dalilin aika mutanen zuwa ƙaura, waɗanda yake magana a kansu kamar ya sayar da su ne kuma ya saki mahaifiyarsu. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Na siyar da ku saboda zunubanku, kuma na sake mahaifiyarku saboda tawayenku"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Yahweh yana amfani da tambayoyi don ya nanata cewa mutane suna gudun hijira saboda ba su amsa masa ba, ba don ba ya son ya cece su ba. AT: "Lokacin da na zo wurinku, ya kamata ku kasance can, amma ba kwa kasance. Lokacin da na kira ku, ya kamata ku amsa, amma ba ku amsa ba." ko "Lokacin da na zo in yi magana da kai, ba ku amsa mini ba."
Yahweh yayi amfani da tambayoyi iri biyu don ya tsawata wa mutane don sun gaskata cewa bai isa ya cece su ba. AT: "Tabbas hannuna bai yi gajarta ba da zan fanshe ku, kuma ina da ikon cetonku!" ko "Lallai ina da ikon kubutar da ku daga abokan gabanku."
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Yahweh yayi magana akan sanya sama tayi duhu kamar yana sanye da tsummoki. AT: "Ina sanya sama duhu, kamar tana sanye da tsummoki a cikin tsummoki"
Kalmar "harshe" tana wakiltar abin da yake faɗa. Zai yiwu ma'anoni su ne 1) Yahweh ya ba shi damar yin magana kamar wanda ya koyi magana da gwaninta. AT: "Ubangiji Yahweh ya ba ni ikon zama ƙwararren mai magana" ko 2) Yahweh ya koya masa abin da zai faɗa. AT: "Ubangiji Yahweh ya ba ni ikon faɗin abin da ya koya mani"
Ana ba da ikon taimaka wa bawansa ya ji kuma ya fahimta kamar Ubangiji ya buɗe kunnensa. AT: "Ubangiji Yahweh ya bani ikon ji da kuma fahimtar sa" (Duba:
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Rashin bin abin da Yahweh ya faɗa ana maganarsa kamar tana juya mutum baya gare shi. Ana iya bayyana wannan a cikin kyawawan sharuɗɗa. AT: "Na yi biyayya ga abin da ya fada"
Ana barin mutane su doke shi su cire gemu ana magana ne kamar yana ba su baya da kunci. AT: "Na bar mutane su doke ni a baya na kuma cire gemuna daga kumatuna"
Boye fuska yana nufin kare kai. AT: "Ban kare kaina ba lokacin da suka yi min ba'a kuma suka tofa mani yawu"
Duk da cewa an wulakanta bawan, ba zai ji kunya ba saboda ya yi biyayya ga Yahweh. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "saboda haka ba zan ji kunya ba"
Bawan yana duban gaba tare da gaba gaɗi, cikin aminci ga kiran Yahweh. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "don na san cewa maƙiyana ba za su iya ba ni kunya ba"
Bawan ya yi amfani da waɗannan tambayoyin don jaddada cewa babu wani wanda zai iya zarginsa da kuskure. AT: "Idan wani zai yi adawa da ni, bari mu tsaya ... Idan wani zai zarge ni, to ya zo"
Bawan yayi amfani da wannan tambayar don tabbatar da cewa babu wanda zai iya bayyana shi mai laifi. AT: "Babu wanda zai iya bayyana ni mai laifi."
Babu wanda ya rage don zargin bawan da laifi, ana maganarsa kamar masu tuhuma riguna ne masu sirara kuma asu ne ke cin su.
Anan kalmar "murya" tana wakiltar abin da bawan ya fada. AT: "yayi biyayya ga bawansa"
Bawan yana magana ne game da mutanen da suke wahala kuma suke jin babu taimako kamar suna tafiya a cikin wuri mai duhu. AT: "yana wahala kuma yana jin mara taimako"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Anan kalmar "suna" tana wakiltar Yahweh ne da kansa. Ana magana akan dogaro ga Allah kamar dogaro ne akan shi. AT: "dogara ga Yahweh, Allahnsa"
A nan “kwanta” yana nufin mutuwa. Mutu mai zafi ana magana akan shi kamar yana kwance a wurin da zasu ji zafi. AT: "Za ku mutu da wahala mai girma"
1Ku saurare ni, ku da ke biɗar ayyukkan adalci, ku dake neman Yahweh: Ku dubi dutsen da aka sassaƙo ku da kuma mahaƙar duwatsu inda aka yanko ku.2Ku duba Ibrahim, mahaifinku, da Saratu wadda ta haife ku; gama tun yana mutum guda, na kirawo shi, na albarkace shi na maida shi mai yawa.3I, Yahweh zai ta'azantar da Sihiyona; zai ta'azantar da dukkan kufanta; jejinta ya maida kamar gonar Iden, kuma sararin hamadarta a gefen kogin Yodan ya maida kamar lambun Yahweh; za a sami farinciki da murna a cikinta, godiya, da ƙarar waƙa.4Ku kasa kunne gare ni, mutane na; ku kuma saurare ni mutane na. Gama zan zartar da doka, kuma zan sa hukuncina ya zama haske domin al'ummai.5Adalci na ya kusato; ceto na zai fito, kuma hannu na zai hukunta al'ummai; ƙasashen kurmi za su jira ni; domin damtsena za su jira ni da ɗoki.6Ku ɗaga idanuwanku ga sararin sama, sai ku kalli duniya a ƙasa, gama sammai za su ɓace kamar hayaƙi, duniya za ta shuɗe kamar tufa, kuma mazaunanta za su mutu kamar ƙudaje. Amma cetona zai ci gaba har abada, gama adalcina ba zai taɓa daina aiki ba.7Ku saurare ni, ku da kuka san abin da ya ke dai-dai, ku dake da dokokina a zukatanku: kada ku ji tsoron zage-zagen mutane, ko ku karaya saboda wulaƙancinsu.8Gama ƙwaro mai cin kaya zai cinye su kamar tufafi, tsutsa kuma ta cinye su kamar ulu; amma adalci na zai dawamma har abada, cetona kuma ga dukkan tsararraki."9Farka, farka, ka suturtar da kanka da ƙarfi, damtsen Yahweh. Tashi kamar kwanakin dã, tsararraki na zamanan dã. Ba kai ba ne ka ragargaza Rahab, kai da ka soke dodon ruwa?10Ba kai ka busar da teku ba, ruwayen manyan zurfafa, ka kuma maida tsakiyar teku hanya domin wucewar tsararraki?11Waɗanda Yahweh ya fansa za su dawo su zo Sihiyona tare da kukan farinciki tare kuma da murna har abada a kawunansu; kuma murna da farinciki za su mallake su, baƙinciki da makoki za su tsere daga gare su.12Ni, Ni, ne shi wanda ke ta'azantar da ku. Me ya sa kuke tsoron mutane, waɗanda za su mutu, da 'ya'yan ɗan Adam, wanɗanda aka yi su kamar ciyawa?13Donme ku ka mance da Yahweh wanda ya yi ku, wanda ya miƙar da sammai ya kuma kafa harsasan duniya? Kun kasance a cikin fargaba kowacce rana saboda zafin fushin mai zalunci sa'ad da ya shirya ya yi hallaka. Ina hasalar mai zaluncin?14Wanda ya rusuna ƙasa, Yahweh zai hanzarta 'yantar da shi; ba zai mutu kuma ya je rami ba, ko ya rasa gurasa ba.15Gama Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ke motsa teku saboda raƙuman ruwa su yi ruri - Yahweh mai runduna ne sunan sa.16Na sa maganata a bakinka, kuma na rufe ka da inuwar hannuna, domin in dasa sammai, in kafa harsasan duniya, in kuma cewa Sihiyona, 'ku mutanena ne.'"17Farka, farka, tashi tsaye Yerusalem, ke da kika bugu a hannun Yahweh daga kwanon fushinsa; ke da kika bugu daga kwanon, har zuwa dago-dago daga ƙoƙon tangadi.18Babu kowa a cikin dukkan 'ya'yanta maza da ta haifa da zai yi mata jagora; babu kowa kuma daga cikin 'ya'yanta maza waɗanda ta rayar da su da zai riƙe hannunta.19Waɗannan matsalolin biyu sun faru dake - wa zai yi makoki tare dake? - kaɗaici da hallaka, da yunwa da takobi. Wane ne zai ta'azantar dake?20'Ya'yanki maza sun some; suna kwance a kowacce kwanar tituna, kamar barewa a tarko; suna cike da fushin Yahweh, da tsautawar Allahnki.21Amma yanzu ki ji wannan, ke da a ke muzguna wa ke bugaggiyar nan amma bada ruwan inabi ba22Ubangijinki Yahweh, Allahnki wanda ke kãriyar ki ya ce, "Duba, na ɗauki ƙoƙon tangaɗi daga hannun ki -kwanon, wadda shi ne ƙoƙon fushi na. domin kada ki sake shan sa kuma.23Zan sa shi a hannun masu ba ki wuya, waɗanda suka ce maki, 'Ki kwanta a ƙasa don mu yi tafiya bisan ki; kin maida bayanki kamar ƙasar da a ke takawa, kamar kuma tituna domin su yi tafiya akai."
Anan kalmar "ni" tana nufin Yahweh.
Allah yayi magana game da al'ummar Isra'ila kamar gini ne da aka yi da duwatsu kuma kamar kakanninsu dutse ne ko dutse ne wanda Allah ya yanke shi. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "kakanninku, waɗanda suke kamar dutsen da aka yanyanka ku kuma ma'adinan da aka sare ku"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "dutsen da na sari ku daga ciki"
Allah yana maganar kakansu kamar mahaifinsu ne. AT: "Ibrahim, kakanka" ko "Ibrahim, kakanka"
Allah yana maganar matar Ibrahim kamar ita ce mahaifiyarsu kuma ta haife su. AT: "matar Ibrahim, Saratu, wacce duk ku zuriyarta ne"
Wannan yana nufin lokacin da bai sami yara ba tukuna. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "lokacin da bashi da 'ya'ya"
Birnin Sihiyona, wanda kuma ake kira Yerusalem, a nan yana wakiltar mutanen Sihiyona. AT: "Yahweh zai ta'azantar da mutanen Sihiyona"
Anan "wuraren ɓata" suna wakiltar mutanen da ke zaune a waɗancan yankuna na kufai. AT: "zai ta'azantar da mutanen da ke zaune a duk wuraren ɓarnarta"
Murna da murna ma'ana ɗaya ce. Samun wurin yana wakiltar kasancewa a wurin. AT: "za a sake yin murna da farin ciki a Sihiyona"
Anan adalcin Allah yana wakiltar shari'arsa, kuma haske yana wakiltar sanin abin da ke daidai. Wannan yana nufin mutanen al'ummomi zasu fahimta kuma suyi biyayya da dokar Allah. AT: "dokina zai koya wa al'ummai abin da yake daidai" ko "al'ummomi za su san dokokina"
Tunanin "kusa" yana wakiltar "ba da daɗewa ba." Adalcin Allah kusa yana wakiltarsa ba da daɗewa ba yana nuna adalcinsa. Zai yi haka ne ta hanyar cika alkawuransa da ceton mutane. AT: "Nan ba da jimawa ba zan nuna adalcina"
Allah yayi maganar ceton mutane kamar ceton sa abu ne wanda zai iya zuwa gare su. AT: "Zan ceci mutane"
Anan hannun Allah yana wakiltar ikonsa, kuma hukunci yana wakiltar mulki. AT: "Zan mallaki al'umman duniya da ƙarfina"
Ɗaga idanun yana wakiltar kallon wani abu a sama. AT: "Duba sama"
“Ceto” na Allah anan yana wakiltar sakamakon ceton sa, wanda shine yanci. AT: "Zan cece ku, za ku sami 'yanci har abada"
“Adalcin” Allah a nan yana wakiltar shi yana mulkin adalci. AT: "dokokina na adalci ba zai taɓa ƙarewa ba" ko "Zan yi mulki na adalci har abada"
Kasance da dokar Allah a cikin zuciya yana wakiltar sanin dokar Allah da kuma son yin biyayya da ita. AT: "wanda ya san kuma ya girmama doka ta"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kuma kada ku yi rashin ƙarfin gwiwa lokacin da suka cutar da ku"
Allah yana maganar mutanen da suke zagin adalai kamar su tufafin ulu, kuma ana hallakar dasu kamar kwari ne suka cinye su.
“Ceto” na Allah anan yana wakiltar sakamakon ceton sa, wanda shine yanci. Kasancewa "ga dukkan tsararraki" yana wakiltar har abada. AT: "Zan cece ku, kuma za ku sami 'yanci har abada"
Ana magana akan ƙarfi kamar wasu irin tufafi ne da mutane zasu sa don ƙarfafa kansu a yaƙi. AT: "sanya kanka da ƙarfi"
Mai magana yayi amfani da tambaya don jaddada ikon Yahweh na aikata manyan abubuwa. AT: "Ku ne kuka murƙushe Rahab, ku kuka huda dodo."
Bugu da kari, mai maganar yana amfani da tambayoyi don jaddada ikon Yahweh na aikata manyan abubuwa. Wannan yana nufin Yahweh ya buɗe Jar Teku don Isra’ilawa su ƙetara su tsere daga sojojin Masarawa. AT: "Kun bushe teku ... domin wadanda aka fansa su wuce ta ciki."
Yin "fansa" na nufin "ceto". Wannan yana nufin mutanen da Yahweh ya cece. AT: "Waɗanda Yahweh ya cece su"
Wannan yana amfani da kan mutum don nufin mutum gaba ɗaya. AT: "za su yi murna har abada"
Wannan yana magana ne game da mutane ba sauran baƙin ciki da makoki ta hanyar yin magana da waɗannan motsin zuciyar kamar suna iya gudu. AT: "ba za su ƙara yin baƙin ciki da baƙin ciki ba"
Wannan tambayar ta lafazi tana jaddada cewa mutanen da suke da kariyar Ubangiji kada su ji tsoron mutane. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Kada ku ji tsoron maza ... kamar ciyawa."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "su wanene kamar"
"wanda ya fadada sama." Wannan yana magana ne game da Yahweh wanda ya halicci sammai kamar yana shimfida su ne kamar yadda mutum zai iya shimfiɗa babban mayafi. AT: "wanda ya shimfiɗa sammai kamar tufa"
Kalmar "tushe" a al'adance tana nufin tsarin dutse wanda ke ba da goyan baya ga gini daga ƙasa. Anan ya bayyana wani irin tsari wanda akayi tunanin zai tallafawa kuma ya rike duniya a matsayin. Duba yadda kuka fassara wannan jumlar a cikin Ishaya 24:18.
"azzaluma mai tsananin fushi lokacin da ya yanke shawarar haifar da halaka"
Yahweh yayi amfani da wata tambaya don ya nanata cewa mutane kada su ji tsoron waɗanda suke so su zalunce su. Azzalumai ba su da wata barazana a gare su. Ana iya rubuta wannan azaman bayani. AT: "Fushin azzalumi ba barazana ba ce!"
Wannan yana nufin mutanen Isra’ilawa waɗanda bayin Babila ne. Wannan jumlar tana bayanin yadda suke aiki. AT: "Bawan"
Anan “gurasa” tana wakiltar abinci ne gaba ɗaya. Ana iya rubuta wannan ta hanya mai kyau. AT: "kuma ba zai zama ba tare da abinci ba"
Wannan yana magana ne game da Yahweh yana sa teku ta motsa kuma raƙuman ruwa su tashi kuma su faɗi kamar yana motsa teku kamar yadda mutum ke motsa abubuwan kwano da babban cokali. AT: "wanda ya sa tekun ya girgiza" ko "wanda ya sa tekun ke motsawa sama da kasa"
Wannan yana magana ne game da YAhweh yana gaya wa Ishaya abin da zai faɗa kamar dai kalmominsa abubuwa ne na zahiri da Yahweh ya sa a bakin Ishaya. AT: "Na gaya muku abin da za ku ce"
“Hannun” Yahweh yana nufin ƙarfinsa. Wannan yana maganar Yahweh yana kare Ishaya kamar hannunsa na rufe shi don kare shi. AT: "ƙarfi na ya kiyaye ku" ko "Na kiyaye ku kuma na kiyaye ku"
Kalmar "shuka" na nufin kafa wani abu a cikin ƙasa. Anan an ambaci Yahweh da kafa sammai da ƙarfi kamar sammai tanti ne da zai shimfiɗa ya kuma kafa shi da wuri tare da turakun alfarwa. AT: "domin in kafa sammai"
Kalmar "tushe" a al'adance tana nufin tsarin dutse wanda ke ba da goyan baya ga gini daga ƙasa. Anan ya bayyana wani irin tsari wanda akayi tunanin zai tallafawa kuma ya rike duniya a matsayin. Duba yadda kuka fassara makamancin kalmar a cikin Ishaya 24:18.
"Ka zama faɗake ka tashi." Maimaita kalmar "a farke" yana nanata hanzarin kiran da zai tayar da mutanen Isra'ila. Ba'a amfani dashi don tashe su daga bacci na zahiri.
Yahweh yayi maganar azabtar da mutanensa kamar ya tilasta musu su sha daga kwanon da aka cika da fushinsa. Kuma a l whenkacin da suka sha daga kwanon fushinsa, suka yi tangaɗi kamar dai sun sha giya da yawa.
Anan an ambaci Yahweh da hannunsa don jaddada cewa shine ya ba da kwanon ga mutanensa. AT: "wanda ya baku"
"Daga cikin ƙoƙon da ya sa ka kaɗaɗa kamar ka bugu da ruwan inabi"
Matsalolin biyu suna nuni da kalmomin biyu masu zuwa: "lalacewa da lalacewa" da "yunwa da takobi."
Kalmomin "yunwa" da "takobi" suna kwatanta masifar da zata auka wa mutane. "Takobin" yana nufin "yaƙi." AT: "da yawa daga cikinku sun mutu saboda yunwa da yaƙi"
Wannan shine gaba ɗaya. Yaran da yawa za su kwana a kan titi, amma ba lallai ba ne a kowace kusurwa. AT: "suna kwance akan titi"
“Fushin Yahwehi” yana nuni ne ga azabtar da mutanensa saboda fushin da yake yi da su. Wannan yana magana ne game da mutanen da aka azabtar da su kamar sun cika da fushin Yahweh. Hakanan, ana iya rubuta kalmar "tsawatarwa" azaman aiki. AT: "Yahweh ya hore su sosai saboda ya yi fushi da su kuma ya tsawata musu"
Yahweh yayi amfani da kalmar "ɗaya" a nan don ya koma ga mutanen da ake zalunta. AT: "ku mutane masu zalunci da mashaya"
Wannan yana magana ne game da mutanen da suka bugu da giya saboda suna shan wahala kamar sun maye ne saboda an tilasta su su sha kwanon fushin Yahweh. AT: "ku da kuka bugu da giyar tashan fushin Yahweh" ko "ku da kuke yin maye, saboda kun sha wahala sosai"
Yahweh yayi magana game da azabtar da mutane kamar dai ya tilasta musu su sha daga cikin kwanon da ya cika da fushinsa. Duba yadda kuka fassara makamancin magana a cikin Ishaya 51:17. AT: "kwano wanda yake cike da fushina" ko "ƙoƙon da aka cika da fushina"
An nuna cewa ta hanyar sanya ƙoƙon fushinsa a hannunsu zai tilasta musu su sha abin da ke cikin ƙoƙon. AT: "Zan tilasta wa masu azabtar da ku shan ruwan inabin kwanon fushina"
Wannan yana kwatankwacin yadda makiyansu suka bi bayansu da yadda mutane suke tafiya akan titi. AT: "kuna kwance a tituna don abokan gabanku su iya takawa a bayanku"
1Farka, farka, ki sa ƙarfinki, Sihiyona; ki sa sababbin tufafinki, Yerusalem, Birni mai tsarki, gama marasa kaciya da kazamtattu ba za su sake shigar ki ba.2Girgiza kanki daga ƙura; tashi ki zauna, Yerusalem; cire sarƙa daga wuyanki, ɗaurarriya, ɗiyar Sihiyona.3Gama ga abin da Yahweh ya faɗi, "An sayar dake a banza, kuma za a fanshe ki ba tare da ƙuɗi ba."4Gama ga abin da Ubangiji Yahweh ya faɗi, "Da farko mutane na zun je can Masar domin zama na 'yan kwanaki; Asiriya bada dadewa ba ta muzguna masu.5Yanzu me nake da shi a nan - wannan furcin Yahweh ne - ganin an ɗauke mutane na babu dalili,? Waɗanda suke mulkinsu suka yi ba'a - Wannan furcin Yahweh ne - kuma aka ci gaba da saɓon suna na dukkan rana.6Saboda haka mutane na za su san sunana; za su sani a ranan nan cewa ni ne wanda ya ce, "I, Ni ne!"7Yaya kyaun sawayen manzo mai kawo labarai ma su daɗi ya ke akan duwatsu, wanda ke shelar salama. wanda ke riƙe da saƙonni masu daɗi, wanda ya shelar ceto, wanda ya cewa Sihiyona, "Allahnki na mulki!"8Ki saurara! masu tsaronki sun ɗaga muryoyinsu, tare suna sowa don murna, gama za su gani, kowanne idonsu, dawowar Yahweh zuwa Sihiyona.9Ku fashe da waƙoƙin farinciki tare, ku duk kufan Yerusalem; Gama Yahweh ya ta'azantar da mutanensa; ya fanso Yerusalem,10Yahweh ya buɗe damtsensa mai tsarki a gaban dukkan al'ummai; dukkan duniya za su ga ceton Allahnmu.11Tafi, tafi, fita daga nan; kar ki taɓa wani kazamtaccen abu; tafi daga cikinta; ku tsarkake kanku, ku da ke ɗauke da taskokin Yahweh.12Gama ba za ku tafi a cikin hanzari ba, ko ku tafi a cikin fargaba ba; gama Yahweh zai tafi gabanku; kuma Allah na Isra'ila zai kasance a bayanku.13Duba, bawana zai yi aiki da hikima; za ya zama da ɗaukaka sosai, kuma za a ɗaukaka shi,14Kamar yadda da yawa suka yi fargaba da kai - kamanninsa ya lalace fiye da kowanne mutum, kuma fasalinsa bai sake yin kama da wani abu na mutum ba.15Duk da haka, bawa na zai yayyafa al'ummai masu yawa sarakuna kuma za su rufe bakunansu saboda shi. Gama abin da ba a taɓa faɗa masu ba, za su gani, kuma abin da ba su taɓa ji ba, za su gane.
Yin magana da ƙarfi kuma ana maganarsa kamar ƙarfi tufafin da mutum yake sakawa ne. AT: "ku yi ƙarfi"
Wadannan siffofin sunaye za a iya bayyana su azaman sifofi. AT: "Waɗanda ba a yi musu kaciya ba ko waɗanda ba su da tsabta"
Anan "Yerusalem" tana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin. AT: "Mutanen Yerusalem, ku zauna ku girgiza ƙurar kanku"
An nuna cewa mutanen Yerusalem suna sanye da sarƙoƙi saboda bayi ne yayin bauta a Babila. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari.
Wannan yana magana ne game da Yahweh kamar dai shi ne mai mallakar Isra'ilawa. Tunda shi mai hakkin ne yana iya basu ko kuma ya mayar dasu duk lokacin da yake so. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Na siyar da ku ba komai, kuma zan fanshe ku ba tare da kuɗi ba"
Anan "farawa" yana nufin farkon tarihin Isra'ila kamar yadda suka fara zama mutane.
"ya tafi ... Masar." Abu ne gama gari a yi amfani da kalmar "ka gangara" lokacin da ake maganar tafiya daga Kan'ana zuwa Masar.
Asiriya tana nufin mutanen Asiriya. AT: "mutanen Asiriya sun wulakanta su"
Yahweh yana amfani da tambaya don sa mutane su mai da hankali ga abin da zai faɗa. Ana iya fassara wannan tambayar ta lafazi a matsayin sanarwa. AT: "Yanzu ku kalli abin da ke faruwa ... an sake kwashe mutanena ba komai."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Na ga abokan gaba suna kwashe mutanena ba komai"
Anan “suna” yana wakiltar sunan Yahweh. AT: "Saboda haka mutanena zasu san ko wanene ni da gaske"
Anan "ƙafa" na wakiltar ɗan aike wanda yake tafiya. AT: "Yana da kyau ka ga manzo yana zuwa kan tsaunuka don yin busharar bushara"
Wannan karin magana ne. AT: "ihu da ƙarfi"
Ishaya yayi magana game da kango na Yerusalem kamar dai su mutane ne da zasu iya yin murna. Wannan yana wakiltar mutanen Yerusalem waɗanda aka ci da yaƙi. AT: "ku mutanen da kuke rayuwa a cikin kango Yerusalem"
Anan "Yerusalem" tana wakiltar mutane. AT: "ya fanshi mutanen Yerusalem"
Anan “al’ummai” da “ƙasa” suna wakiltar mutanen dukkan al’ummai a duk faɗin duniya.
An ɗauka ilimi ne cewa mutanen Isra'ila bayi ne a Babila. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "ku fita daga ƙasar da kuke bayi"
Wani abu da Yahweh ya faɗa bai dace a taɓa ko a ci ba ana maganarsa kamar ba shi da tsabta a zahiri. AT: "kada ku taɓa komai wanda Yahweh ba zai karɓa ba"
Ana magana da Yahweh yana kare mutanensa daga abokan gabansu kamar dai shi jarumawa ne waɗanda ke gaba da mutane da kuma mayaƙan da suka tsaya a bayan mutane don kare su.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Waɗannan jimlolin guda biyu "maɗaukakiya kuma an ɗaukaka su" kuma "za a ɗaukaka su" suna da ma'ana ɗaya kuma suna nanata cewa Yahweh zai girmama bawansa. Dubi yadda kuka fassara wata magana makamancin wannan a cikin Ishaya 33:10. AT: "Zan ba bawana mafi girma girmamawa"
Ana nuna cewa bawan yana da mutunci saboda abokan gaba sun buge shi da mummunan rauni. Cikakkiyar ma’anar wannan ana iya bayyana ta a sarari. AT: "makiyansa sun buge jikinsa sosai da har bai sake zama kamar mutum ba"
Bawan da zai sa mutanen al'ummai su zama karɓaɓɓu ga Yahweh ana magana akan shi kamar bawan firist ne wanda ya yayyafa jinin hadaya don ya sami wani abu ko wani abu mai karɓa ga Yahweh.
Jumlar "rufe bakunansu" karin magana ne. AT: "sarakuna za su daina magana" ko "sarakuna za su yi shiru"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "abin da ba wanda ya gaya musu" ko "wani abu da ba wanda ya gaya musu"
1Wane ne ya gaskata da abin da ya ji daga gare mu, kuma ga wane ne aka bayyana hannun Yahweh?2Gama ya yi girma a gaban Yahweh kamar 'yar itaciya, kuma kamar tsiro daga cikin busasshiyar ƙasa; ba shi da wani kyakkyawan jamali ko daraja; sa'ad da muka ganshi, babu wani kyau da zai rinjaye mu.3Mutane suka rena shi suka kuma ƙi shi; mutumin baƙinciki, kuma wanda ya saba da raɗaɗi. Kamar wanda mutane ke ɓoye fuskarsu daga gare shi; aka rena shi; muka kuma ɗauke shi ba a bakin komai ba.4Amma tabbas ya sungumi cututtukanmu ya kuma ɗauke baƙincikinmu; duk da haka mun yi zaton cewa Allah ne ke hukunta shi, Allah ya mazge shi, ya kuma azabta.5Amma an soke shi saboda ayyukan tayarwarmu; aka ragargaje shi saboda zunubanmu. Hukunci domin salamarmu ya kasance a kansa, kuma ta wurin raunukansa muka warke.6Dukkanmu kamar tumaki muka bijire; kowannenmu ya juya zuwa hanyarsa, kuma Yahweh ya ɗora masa laifuffukanmu dukka.7An muzguna masa; duk da haka sa'ad da ya ƙasƙantar da kansa, bai buɗe bakinsa ba; kamar ɗan ragon da za'a kai yanka, kuma kamar tumakin dake tsaye shiru a gaban masu sausaya, haka shi ma bai buɗe bakinsa ba.8Ta wurin wulaƙantarwa da hukuntawa aka kayar da shi; wane ne daga wancan tsara ya sake yin tunani a kansa? Amma an datse shi daga ƙasar masu rai; saboda laifuffukan mutanena aka yanke masa hukunci.9Suka sa kabarinsa tare da ma 'yan ta'adda, tare da mai arziki a mutuwarsa, koda ya ke bai yi tawaye ba, ko kuwa wata ruɗarwa a bakinsa.10Duk da haka, nufin Yahweh ne a murkushe shi a sa shi ciwo. Sa'ad da ya mai da kansa baiko domin zunubi, zai ga 'ya'yansa, zai daɗa tsawon kwanakinsa, kuma dalilin Yahweh zai cika ta wurinsa.11Bayan wahalar rayuwarsa, zai ga haske kuma ya gamsu da saninsa. Bawana mai adalci zai baratar da mutane da yawa; zai ɗauki laifuffukansu.12Saboda haka zan ba shi nasa kason a cikin yawan mutane, kuma zai raba ganimar da mutane da yawa, domin ya sa kansa ga mutuwa, aka kuma ƙidaya shi tare da masu kurakurai. Ya ɗauki zunuban mutane da yawa ya kuma yi roƙo domin masu kurakurai.
Abin da Ishaya ya gano yana da ban mamaki ƙwarai da gaske har yana mamaki ko waɗanda suke zaman talala za su gaskata da shi. "Mu" ya haɗa da shi da waɗanda suke gudun hijira. AT: "Yana da wahala kowa ya gaskanta abin da muka ji"
Arm yana nufin ikon Allah. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya bayyana ikonsa ga mutane."
Anan "shi" yana nufin bawan Allah wanda Ishaya ya kwatanta shi da ƙaramin itace. Wannan ya nanata cewa zai bayyana a raunane.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane sun dauke shi a matsayin ba komai kuma suka ƙi shi"
"mutum mai sanin kowane irin bakin ciki"
"Fuska" tana wakiltar hankalin mutum ko kuma tarayyarsa. Faceoye fuskokin mutum yana nufin juya baya ga wani. AT: "wanda mutane suke juya masa baya"
''Kai'' ko ɗaukar abu kamar cuta da baƙin ciki yana wakiltar ɗaukar sa. AT: "ya ɗauki cututtukanmu da baƙin ciki a kansa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "amma duk da haka mun zaci Allah yana azabtar da shi kuma yana wahalar da shi"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa bawan ya sha wahala saboda zunuban mutane. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ya ba maƙiyi damar soka shi kuma su kashe shi saboda zunubanmu"
Wannan yana nufin zaman lafiya tare da Allah. Ana iya bayyana wannan a bayyane. AT: "Ya yarda da wannan hukuncin ne domin mu rayu cikin jituwa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki.AT: "ya warkar da mu ta wahalar raunuka"
Tumaki sukan bar hanyar da makiyayin yake bi da su. Ishaya yana nufin cewa muna yin abin da muke so maimakon abin da Allah ya umurta.
“Laifinmu” anan yana wakiltar laifin zunubinmu. AT: "laifin zunubin kowane ɗayanmu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sun wulakanta shi"
"Baki" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. Bude bakin mutum yana nufin magana. AT: "bai nuna rashin amincewa ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kamar yadda rago yayi tsit yayin da mutum ya yanka shi"
Wannan tambayar ta jaddada cewa babu wanda yake tunani game da shi. AT: "babu wanda ya kula da abin da ya same shi." ko "babu wani daga cikin tsaransa da ya kula da abin da ya same shi."
"Yankewa" a nan yana nufin mutuwa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Amma ya mutu" ko "Amma mutuwa ta ɗauke shi"
"Baki" yana wakiltar abin da mutum ya faɗa. AT: "kuma bai yaudari kowa ba lokacin da yake magana"
A nan, "zuriya" na nufin mutanen da Yahweh ya gafarta saboda hadayar bawan.
Wannan yana magana game da sanya shi rayuwa don ƙarin lokaci. AT: "Yahweh zai sa bawansa ya sake rayuwa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai cika nufinsa ta hanyar bawansa"
Kalmar "ɗauki" na nufin ɗauka. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "laifofinsu" na wakiltar azabar zunubansu ne. AT: "zai ɗauki hukuncinsu" ko "za a hukunta shi saboda zunubansu" ko 2) "muguntar su "shi ne metonym wakiltar laifi" AT: "zai ɗauki alhakin laifinsu a kan kansa" ko "zai kasance da alhakin zunubansu"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. "Rabon" da "ganima" suna nuni ne ga sarki bayan yaƙin nasara ya raba ganima ko lada tare da sojojinsa. Wannan yana nufin Allah zai girmama bawansa ƙwarai saboda sadaukarwarsa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "an ba mutane damar ɗaukar shi a matsayin mai laifi"
1"Yi waƙa, ke bakarariya, ke da ba ki haihu ba; ki fashe da waƙar farinciki ki yi kuka da karfi, ke da ba ki taɓa yin naƙudar haihuwa ba. Gama 'ya'yan yasassa sun fi na matar da aka aura," inji Yahweh.2Ki faɗaɗa girman rumfarki, ki baza labulen rumfarki da faɗi; bada ƙwauro ba; ki daɗa tsawon igiyoyinki; ki miƙar da dirkokinki,3Gama za ki bazu ta hannun dama da ta hagu, har sai zuriyarki sun mamaye al'ummai sun kuma sake kafa yasassun birane.4Kada ki ji tsoro domin ba za ki ji kunya ba, ko ki karaya ba gama ba za a wulaƙanta ki ba; za ki mance da abin kunyar kuruciyarki da wulaƙancin yashewarki.5Gama wanda ya Yiki shi ne mijinki; Yahweh mai runduna shi ne sunansa. Mai Tsarkin nan na Isra'ila shi ne mai Fansarki; Shi a ke kira Allahn dukkan duniya.6Gama Yahweh ya sake kirawo ki a matsayin matar da aka yasar da take kuma cikin ƙunci a ruhu. Kamar matar da a kuruciyarta aka aurota sa'an nan aka ƙi ta," inji Allahnki.7Gama na yashe ki na ɗan lokaci kaɗan, amma da tausayi mai girma zan tattara ki.8A sa'ad da na yi fushi mai zafi, na ɓoye fuskata daga gare ki na wani lokaci; amma da madawwamin alƙawari aminci zan yi maki jinƙai - inji Yahweh, wanda ya ƙubutar dake.9Gama wannan kamar ruwayen Nuhu ne a gare ni: kamar yadda na rantse cewa ruwayen Nuhu ba za su sake shan kan duniya ba, saboda haka na rantse cewa ba zan yi fushi dake ko in kwaɓe ki ba.10Koda shi ke tsaunuka za su iya faɗuwa kuma tuddai su girgizu, duk da haka madawwamiyar ƙauna ta ba zata rabu da ke ba, ko alƙawarin salamata ya girgiza ba - inji Yahweh, wanda ke yi maki jinƙai.11Mai ƙunci, wanda guguwa ke kora kuma marar ta'aziyya, ku duba, zan sa shiryayyar hanya da dutsen tukoyis, in kuma kafa harsashenki da saffiyes.12Zan sa sorayenki da duwatsu masu ƙawa ƙofofinki kuma da duwatsu masu walƙiya, da kuma katangarki ta waje da kyawawan duwatsu.13Sa'an nan Yahweh zai koyar da dukkan 'ya'yanku; kuma salamar 'ya'yanku zata yi yawa.14A cikin adalci zan sake kafa ku. Ba za ku ƙara fuskantar tsanantawa ba, gama ba za ku ji tsoro ba; kuma ba abin ban tsoro da zai yi kusa da ku ba.15Duba, idan wani ya tada rikici, ba zai zama daga gare ni ba, duk wanda ya tada rikici da ku, za ku yi nasara a kansa.16Duba na halici maƙeri, mai hura garwashin wuta ya ƙera makamai na aikinsa, Ni kuma na hallici mai hallakarwa domin ya hallakar.17Babu makamin da aka ƙera gãba da kai da zai yi nasara; kuma zan kayar da duk wanda ya tuhume ka. Wannan shi ne gădon bayin Yahweh, kuma kariyarsu daga gare ni take. wannan furcin Yahweh ne."
Wannan magana tana nufin abu ɗaya da sashin farko na jumlar.
Wani abin da zai faru a nan gaba ana maganarsa kamar ya faru a baya. Wannan yana nanata cewa lallai lamarin zai faru. AT: "Ga 'ya'yan matan da aka lalatar za su fi yawa"
Wannan yana ci gaba da managa da ya fara a cikin Ishaya 54: 1. Yahweh yana gaya wa mutanen Yerusalem su shirya domin Yahweh zai yawaita mutanensu ana maganarsu kamar yana faɗar wa mace ta faɗaɗa alfarwarta don ba yara da yawa dama.
A nan "ku" na mufuradi ne kuma yana nufin mace bakarariya. Tana wakiltar kanta da dukkan zuriyarta. AT: "Don ku da zuriyarku za ku bazu"
Anan "al'ummai" suna wakiltar mutane. AT: "zai cinye mutanen wasu ƙasashe"
Yahweh yana gayawa mutane cewa a gaba ba zasu ma tuna da abin kunyar da suka ji ba yayin da magabtansu suka ci su ana magana kamar Yahweh yana gaya wa mace cewa ba za ta ƙara yin tunani game da kunyar da ta fuskanta na rashin haihuwa ba. da kuma sa mijinta ya watsar da ita.
Ana magana game da Yahweh mai kauna da kulawa ga mutanensa kamar shi ne mijinta.
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 5:16.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "shi ne Allah na duk duniya"
Anan “ruhu” yana wakiltar yanayin mutum. AT: "baƙin ciki" ko "sanya baƙin ciki"
Ana magana da fushin Yahweh sosai kamar fushin sa ambaliya ne wanda ya mamaye mutane. AT: "Lokacin da na fusata ƙwarai"
Anan "ɓoye fuskata" wani karin magana ne da ke nufin Allah ya watsar da mutanensa kuma ya bar su wahala. AT: "Na yi watsi da ku"
Kalmar "aminci" za a iya bayyana a matsayin "aminci." Duba yadda kuka fassara "amincin alkawari" a cikin Ishaya 16: 5. AT: "amma saboda koyaushe ina cika alƙawarin da na ɗauka da ku" ko "amma saboda ina da aminci koyaushe don yin abin da na yi alkawarin aikatawa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "tuddai na iya girgiza"
An ambaci Yahweh yana ci gaba da ƙaunar mutanensa kamar dai ƙaunarsa ba za ta juya wa mutane baya ba. AT: "Ba zan daina ƙaunarku ba"
Yahweh ba zai warware alkawarinsa da mutane ba ana maganarsa kamar alkawarinsa abu ne wanda ba za a girgiza shi ba. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kuma ba zan warware alkawarina na salama ba" ko "kuma tabbas zan ba ku salama kamar yadda na yi alkawari a cikin alkawarina"
Anan Yahweh yayi magana da birnin Yerusalem kamar tana sauraron sa. Anan Yerusalem tana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin. AT: "Kun wahalar da mutanen Yerusalem"
"ba tare da ta'aziyya ba"
Yahweh ya bayyana a cikin kyakkyawan yanayi yadda zai mayar da Yerusalem kuma ya sake sa ta zama kyakkyawa. Kodayake ana iya wuce gona da iri, ya kamata ku fassara wannan kamar yadda Yahweh ya bayyana shi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kuma Yahweh zai koya wa yaranku duka"
Cikakken sunan "adalci" ana iya bayyana shi azaman sifa "dai-dai." Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan sa ku sake samun ƙarfi saboda za ku yi abin da yake daidai"
Ba wani daga cikin birni ko bare wanda zai sake firgita mazaunan Yerusalem.
Wannan karin magana ne. AT: "yana haifar da matsala" ko "damun ku"
Wannan karin magana ne. AT: "za ku ci su da yaƙi"
An yi magana akan magabtan da ba sa nasara a kan mutanen Yahweh kamar makamansu ba za su yi nasara a kan mutanen Yahweh ba. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Makiya na iya kulla makami don kawo muku hari amma ba za su ci ku ba"
Sakamakon da Yahweh zai bayar ga waɗanda suka bauta masa an faɗi kamar ana ba da lada wani abu ne da za su gada.
1Ku zo, kowannen ku dake jin kishin ruwa, ku zo wurin ruwan, ku da baku da kuɗi, ku zo, ku saya, ku ci, ku zo ku sayi ruwan inabi da madara kyauta da arha kuma.2Me ya sa kuke auna azurfa domin abin da ba abinci ba, kuma me yasa kuke aiki domin abin da ba ya ƙosarwa? Ku saurare ni sosai ku ci abin dake da kyau, ku kuma yi farinciki cikin ƙoshi.3Ku juyo da kunnuwanku ku zo gare ni! Ku saurara, domin ku rayu! Zan yi madawwamin alƙawari da ku - ingantacce, amintacciyar ƙauna dana alƙawarta wa Dauda,4Duba, na sashi a matsayin shaida ga al'ummai, a matsayin shugaba da mai ba da umarni ga mutane.5Duba, za ku kira ga al'umman da baku san su ba; kuma al'umman da basu san ku ba za su rugo gunku saboda Yahweh Allahnku, Mai Tsarki na Isra'ila wanda ya ɗaukaka ku."6Ku nemi Yahweh tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.7Bari mai mugunta ya bar tafarkinsa, haka nan mai zunubi ya bar tunane-tunanensa. Bari ya komo wurin Yahweh, sai ya yi masa jinƙai, da kuma Allahnmu wanda zai gafarta masa a yalwace.8Gama tunane-tunanena ba dai-dai ne da tunane-tunanenku ba, kuma hanyoyinku ba dai-dai da nawa ba - wannan furcin Yahweh ne -9gama kamar yadda sammai ke nesa da duniya, haka hanyoyina ke nesa da taku, haka kuma tunane-tunanena ke nesa da tunane-tunanenku.10Gama kamar yadda ruwa da ƙanƙara ke saukowa daga sama, kuma basu komawa sai sun jiƙa ƙasa, susa amfaninta su tsiro su bada 'ya'ya ga manomin da ya yi shuka ya kuma bada abinci ga mai ci,11haka nan ne maganata wadda ta fito daga bakina zata kasance - ba za ta komo gare ni a banza ba, amma zata yi nasara a kan abin da na aike ta ta aiwatar.12Gama za ku fita da farinciki, a kuma jagorance ku a cikin salama; Tsaunuka da tuddai za su farfashe da murnar ihu a gabanku, kuma dukkan itatuwan filaye za su tafa hannuwansu.13A maimakon ƙayoyin saura, itatuwa masu ganyaye za su fito; kuma a maimakon itacen ƙaya, itacen ganye mai kyau zai fito, kuma zai zama domin Yahweh, domin sunansa, kamar madawwamiyar alama da ba za a tsige ba."
Yahweh ya ci gaba da magana da mazaunan Yerusalem da ke cikin bauta ta bakin Ishaya
Akwai hankali a cikin wannan bayanin tunda mutum yawanci dole ne ya yi amfani da kuɗi don siyan wani abu. Wannan yana nanata alherin ban mamaki na Yahweh na ba da waɗannan abubuwa kyauta.
Yahweh yana yin waɗannan tambayoyin don ya tsauta wa mutane. Yana magana ne game da mutanen da ke neman farin ciki banda Yahweh kamar suna siyan abubuwan da zasu ci waɗanda ba abinci ba kuma suna aiki don abubuwan da ba zasu iya gamsar da su ba. AT: "Bai kamata ku auna azurfa ba ... abinci, kuma kada ku yi aiki ... ku gamsar"
Anan kalmar “gurasa” tana wakiltar abinci ne gaba ɗaya. Ana nuna cewa mutane suna siyan abubuwan da zasu ci waɗanda ba abinci bane da gaske. AT: "don abubuwan da za a ci waɗanda ba abinci ba ne da gaske"
Mutanen da suka dogara ga Yahweh don albarka da farin ciki ana maganarsu kamar suna cin kyakkyawan abinci wanda ke faranta musu rai.
Ana maganar sauraro ko kula da wani kamar ana juya kunnen mutum ne ga wani. AT: "Kula"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan yana nufin abin da Yahweh ya yi wa sarki Dauda a da ko 2) yana nufin abin da Allah zai yi ta ɗayan zuriyar Dauda.
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 1: 4.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ku nemi Yahweh yayin da har yanzu ba ku same shi"
Kalmar "mugaye" tana nufin mugaye. Yahweh yayi magana akan mugayen mutane da basu daina yin zunubi ba kamar zasu daina tafiya akan hanyar da suke tafiya. AT: "Bari mugaye su canza yadda suke rayuwa"
Ana iya samar da kalmar daga jimlar da ta gabata. AT: "bari mutum mai zunubi ya bar tunaninsa"
Yahweh yayi magana akan abubuwan da yake aikatawa da kuma yadda yake tunanin sun fi ko sama da abinda mutane suke yi kuma suke tunani, kamar dai yadda sama ta fi ƙasa nesa.
Anan kalmar "bakin" tana wakiltar Yahweh ne da kansa. AT: "kalmar da na faɗi"
Anan bayanin kalmar komawa ga Yahweh yana nufin cewa ta kammala aikin da Yahweh ya aike ta ta kammala. Cewa ba za ta dawo "wofi ba" yana nufin cewa ba za ta kasa cika aikinta ba. AT: "ba zai kasa kammala aikinsa ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan bi da ku cikin salama"
Yahweh yayi magana akan duwatsu, tuddai, da bishiyoyi kamar dai mutane ne masu murya da hannu, suna murna yayin da Yahweh ya ceci mutanensa.
Ana magana akan wani abu da ya daina wanzuwa kamar an yanke shi, kamar yadda ake yanke reshen bishiya ko kuma an yanke yanki da tufafi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wannan ba zai taɓa ƙarewa ba" ko "wanda zai dawwama har abada"
1Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗi, "Ku yi abin dake dai-dai; ku yi abin da ya kamata; gama cetona ya yi kusa, kuma adalcina na gaf da bayyana.2Mai albarka ne mutumin dake yin wannan, wanda kuma ya riƙe shi kam-kam. Ya kiyaye ranar Asabaci, ba ya ƙazamtata, yana kuma kiyaye hannunsa daga aikin mugunta."3Kada bãƙon da ya zama mai bin Yahweh yace, "Yahweh zai tuge ni daga cikin mutanensa." Kada bãbã yace, "Duba, ni busasshen itace ne."4Gama wannan ne abin da Yahweh yace, "Ga bãbãnni da ke kiyaye Asabataina kuma suna zaɓen abin dake faranta mani rai, su kuma riƙe alƙawaraina kam-kam,5dominsu ne zan kafa alama a cikin gidana da ganuwata abin tunawa da yafi samun 'ya'ya maza da mata. Zan ba su madawwamin abin tunawa da ba za a taɓa datsewa ba.6Haka ma bãƙin da suka haɗa kansu da Yahweh - su ɓauta masa, waɗanda kuma suke son sunan Yahweh, su ɓauta masa, duk wanda ke lura da Asabaci, da wanda ke kãre kansa daga ƙazamta, da wanda ya riƙe alƙawari na kam-kam7- zan kawo su ga tsarkakken tsaunina in sa su yi farinciki a gidan addu'a ta; baye-bayensu na ƙonawa da hadayunsu za su samu karɓuwa a bagadina. Gama za'a kira gidana gidan addu'a domin dukkan al'ummai,8Wannan ne furcin Ubangiji Yahweh, wanda ya tattara korarrun Isra'ila - Zan sake tattaro waɗansu in haɗa tare da su."9Dukkanku namomin jeji na saura, ku zo ku lanƙwame, dukkan ku dabbobin cikin kurmi!10Dukkan matsaransu maƙafi ne, ba su fahimta ba. Su dukka karnuka dake shiru ne waɗanda ba su iya yin haushi. Suna mafarki, kuma a kwance suna ƙaunar yin barci.11Karnukan na da babban marmarin ci; Ba za su taba samun abin da ya ishe su ba; su makiyaya ne da ba su da ganewa; dukkansu sun juya ga ta su hanya, kowannensu na ƙyashin mugun ribar kansa.12"Zo," suka ce "bari mu sha ruwan inabi da barasa mai karfi," Gobe zai zama kamar yau, rana mai girma fiye da yadda a ke tsammani."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Da sannu zan cece ku kuma in nuna muku cewa ni mai adalci ne"
Anan “hannun” yana wakiltar mutum duka kuma yana mai da hankali ga ayyukan mutum ko halayensa. AT: "baya aikata mugunta"
Wannan yana nufin bãbã na iya yin tunanin ba za su iya zama ɓangare na mutanen Allah ba saboda sun lalace ta hanyar jefa mutum (kuma saboda wannan dalilin ba su da yara). Isra'ilawa ba sa yin aikin sihiri; baƙi sun yi, wani lokaci don horo. Bãbã waɗanda suka karɓi bangaskiyar Ibraniyanci sun sani cewa yawanci ba a ba su izinin yin sujada a cikin haikalin. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya. AT: "a cikin bangon haikalina"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wannan ba zai taɓa ƙarewa ba" ko "ba za a taɓa mantawa da shi ba"
Wannan na nufin bãƙin waɗanda suka shiga jama'ar Yahweh.
“Sunan” Yahweh yana wakiltar kansa. AT: "waɗanda ke son Yahweh"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "gidana zai zama gidan addu'a"
Allah yana kiran rundunonin wasu al'umman ta hanyar kwatanta su da dabbobi don su zo su afka wa Isra'ilawa.
Wannan yana nufin shugabannin Isra'ila ba za su iya ko watakila ba sa son ganin abin da ke gudana a cikin al'umma.
Yakamata shugabanni su bude bakinsu su gargadi mutane, amma basuyi hakan ba. Kwatanta wani da kare a cikin wannan al’ummar babban cin mutunci ne.
Wannan yana nufin shugabannin ba sa kawo maganar gargaɗin Allah ga Isra'ila amma sun fi son ta'aziyyar kansu.
Yahweh ya ci gaba da gwada miyagun shugabannin Isra'ila da karnuka.
1Adali ya hallaka, babu wanda ya kula, kuma mutanen amintaccen alƙawari sun taru a can, amma ba wanda ya gane cewa an ɗauke mai adalici ne daga mugunta.2Ya shiga cikin salama; suna hutawa a cikin gadajensu, waɗanda ke tafiya a cikin kamilcinsu3Amma ku zo nan, ku 'ya'yan masu sihiri, 'ya'yan mazinaciya da matar da ta karuwantar da kanta. Wane ne kuke yi masa ba'a da murna?4Gãba da wa kuke buɗe bakunanku kuke gwalo? Ku ba 'ya'yan tayarwa ba ne, 'ya'yan zamba?5Kuna ɗuma kanku ku da kuke kwance tare ƙarƙashin itacen rimi, ƙarƙashin kowanne koren itace, ku dake kashe 'ya'yanku a cikin rafuffukan da suka ƙone da ƙarƙashin duwatsu masu maratayi6A cikin abubuwa masu laushi na rafin gangare su ne aka ba ku. Wato kayan ibadarku. Kun zuba ruwan baikon abin sha gare su kuka kuma ɗaga baikon hatsi. A waɗannan abubuwan ne ya kamata in ji daɗi?7Kun shirya gadonku a ƙwanƙwolin tsauni; kun kuma tafi sama can domin ku miƙa hadayu.8A bayan ƙofa da ƙyaurayen kuka shirya alamunku; kun yashe ni, kun yi wa kanku tsiraici, sai kuka haura sama; kuka yi gadonku da faɗi. Kuka yi yerjejeniya da su; kuka ƙaunaci gadajensu; kuka ga tsiraicinsu.9Kun tafi wurin Molek da mai; kun ruɓanɓanya turare. Kun aika jakadunku nesa; kun gangara zuwa Lahira.10Kun gaji saboda doguwar tafiyarku, amma ba ku taɓa cewa, "babu bege ba." Kun sami rai a hannuwanku; saboda haka ba ku karaya ba.11Wane ne kuke damuwa dominsa? Wane ne kuke jin tsoronsa da yawa har ya sa kuka aikata abin ruɗi, harma kun manta da ni ko ku yi tunani akai na? Saboda na yi shiru na dogon lokaci, harma yanzu kun dena jin tsoro na.12Zan sanar da dukkan ayyukan adalcinku in kuma faɗi dukkan abin da kuka yi, amma ba za su taimake ku ba.13Sa'ad'da kuka yi kũka, bari tarin gumakanku su 'yantar daku. Maimakon haka iska za ta ɗauke su dukka, wani numfashi zai ɗauke su dukka. Duk da haka wanda ya yi mafaka a cikina zai gaje ƙasar ya kuma mallaki tsarkakken tsaunina.14Zai ce, 'Gina, gina! A shãre hanya! Cire dukkan abin sa tuntuɓe a hanyar mutanena!'"15Gama ga abin da mai girma maɗaukaki Kaɗai yace, wanda ke zaune har abada, wanda sunansa tsarki ne, "Ina zaune a maɗaukakin wuri mai tsarki, tare da shi kuma mai karyayye da ƙasƙantaccen ruhu, in falkar da ruhun masu ƙasƙantar da kai, in farkar da zuciyar masu tawali'u.16Gama ba zan yi zargi har abada ba, ko in yi fushi har abada ba, domin ruhun mutum zai some a gabana, rayyukan dana halitta,17Saboda da zunubinsa na ribar ƙwãce, Na yi fushi, Na kuma hukunta shi; Na ɓoye fuskata na kuma yi fushi, amma ya koma da baya cikin hanyar zuciyarsa.18Na ga hanyoyinsa, amma zan warkar da shi. Zan jagorance shi in kuma ta'azantar da shi in kuma ƙarfafa waɗanda ke makoki dominsa,19kuma ni na hallici diyan lebuna. Salama, salama, ga waɗanda ke nesa da na kusa - inji Yahweh - Zan warkar da su.20Amma miyagu suna kama da haukan teku, wanda ba zai huta ba, kuma ruwayen suna amayar da taɓo da laka.21Babu salama domin mugu - inji Allah."
AT: "mutanen da ke da aminci ga alkawarin" ko "mutanen da ke da aminci"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "cewa mutanen kirki sun mutu, kuma Yahweh yana ɗauke su daga dukkan mugunta"
"Masu adalci za su shiga salama"
Wannan yana nufin ainihin zina da na ruhaniya. Sun bar bautar Allah kuma yanzu suna bautar wasu alloli da gumaka tare da ainihin karuwanci a cikin bukukuwan Kan'ana na arna.
Yahweh yayi amfani da wata tambaya don tsawata wa mutane. Wannan baya magana game da haihuwar su ba amma halin ruhaniya ne. AT: "Ku 'ya'yan tawaye ne,' ya'yan yaudara!"
Duk waɗannan ayyukan suna haɗuwa da bautar gumaka. Itacen oak bishiya ne na Kan'aniyawa. Mutane suna tsammanin irin wannan aikin zai ƙara yawan haihuwa ga mutane da ƙasar.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Ainihin ma'anar cikin Ibraniyanci ba bayyananne bane. AT: "wannan shine rabonku" ko "wannan shine gadonku"
Yahweh yana amfani da tambaya don tsawata wa mutane. AT: "Tabbas, waɗannan abubuwan ba sa faranta mini rai."
Wannan yana nufin kwana tare da karuwai a matsayin ɓangare na bautar gumakan ƙarya.
"Kun kulla yarjejeniya da su"
Mutanen ba su tafi Lahira ba, Lahira. Madadin haka, Yahweh yana nunawa da ƙari cewa mutane suna shirye su je ko'ina su samo sababbin gumaka don bauta.
Bayan ƙoƙari sosai, masu bautar gumaka sun ga har yanzu suna da ƙarfin ci gaba. Anan "hannu" yayi daidai da "ƙarfi" ko "iyawa."
Waɗannan jimlolin guda biyu ma'anarsu ɗaya ce kuma suna ƙarfafa hakan, duk da cewa ya kamata mutane su tuna da Yahweh, amma ba su yi hakan ba.
Yahweh yana da ba'a, yana kiran mugayen ayyukansu da ake kira adalci.
Yahweh yana ba'a da mutane da gumakansu. Ya gaya wa gumaka su ceci mutanen ko da ya san ba za su iya ba.
Wannan faɗin abu ɗaya ne ta hanyoyi biyu don ƙarfafawa cewa gumaka ba su da komai kuma ba su da amfani. AT: "iska, ko ma numfashi, za ta tafi da su"
"Tsattsarkan dutse" shi ne Tsaunin Sihiyona, a Yerusalem. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 11: 9.
Yahweh yana da tabbaci kuma yana da hanzari cewa a sami hanya madaidaiciya kuma madaidaiciya don mutane su dawo gare shi kuma ba tare da cikas ga bautar Yahweh ba. Wannan yana amsa kuwwa Ishaya 40: 3.
Kalmomin “babba” da “ɗaukaka” suna da ma’ana iri ɗaya a nan kuma sun nanata cewa ana ɗaukaka Yahweh. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 6: 1 da kuma Ishaya 33:10. Duba yadda kuka fassara makamancin kalmar a cikin Ishaya 52:13.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna jaddada cewa Yahweh zai ƙarfafa da ƙarfafa waɗanda suka ƙasƙantar da kansu a gabansa.
Wannan yana nufin Allah ya ba da mutanensa kuma ya daina taimaka musu ko albarkar su.
Wannan yana nufin Isra'ilawa sun ci gaba da ƙin Allah na gaskiya don na ƙarya. Anan "baya" da "hanya" kalmomin wuri ne waɗanda ke wakiltar motsawa da ji.
"hanyoyin su." Anan "nasa" yana nufin mutanen Isra'ila.
"Zan ta'azantar kuma in kwantar da hankalin waɗanda ke baƙin ciki saboda wahalar da mutane ke ciki saboda halayensu na zunubi"
A nan “’ya’yan leɓɓa ”na nufin abin da mutum ya faɗa. AT: "Ina sa su su yaba kuma su gode mani"
Wannan yana kwatanta mugaye da ruwan da ke bakin teku wanda ke sa ruwan ya ƙazantu.
1Yi kuka da ƙarfi; kada ku dena. Ku ɗaga muryarku kamar kakaki. Ku ta'azantar da mutanena a kan tayarwarsu, da kuma gidan Yakubu a kan zunubansu.2Duk da haka suna nema na kullum suna kuma fahariya a sanin hanyoyina, kamar al'umma dake yin aɗalci da ba su yashe da dokokin Allahnsu ba. Suna tambayata hukuncin aɗalci; Suna jin daɗin tunani a kan Allah ya kusance su.3Me yasa muka yi azumi,' suka ce, 'amma ba ka gani ba? Me yasa muka ƙasƙantar da kanmu, amma ba ka kula ba?' Duba, a ranar azuminku, kuna neman jin daɗinku kuna kuma danne dukkan ma'aikatanku,4Duba, kuna azumi ku yi faɗace-faɗace, kuma ku bugu da hannun mugunta; ba za ku yi azumi yau wanda za ku sa a ji muryarku a sama ba.5Wannan shi ne lallai irin azumin da zan so: Ranar da wani zai ƙasƙantar da kansa, ya sunkuyar da kansa kamar ciyawa, kuma ya yafa tsummokara da toka a ƙarƙashinsa? Kun tabbata za ku kira wannan azumi, rana wadda ta gamshi Yahweh?6Wannan ba shi ne azumin dana zaɓa ba: A saki miyagun sarƙoƙi, a kwance igiyoyin karkiya, a sa waɗanda aka ragargaza su sami 'yanci, a kuma karya kowacce karkiya?7Ko kuma ku raba gurasarku da mayunwata ku kuma shigo da marasa mazauni cikin gidanku ba?" Idan ku ka ga wani tsirara, sai ku suturtar da shi; kuma kada ku ɓoye kanku daga 'yan'uwa.8Sa'an nan hasken ku zai faso a buɗe kamar fitowar rana, kuma warkewarku zata tsiro nan da nan; adalcinku zai sha gabanku, kuma ɗaukakar Yaweh zata biyo bayanku.9Sa'an nan ne za ku yi kira, kuma Yahweh zai amsa; za ku yi kukan neman taimako, kuma zai ce, "Ga ni nan." Idan har kuka ɗauke daga tsakiyarku karkiya, da zargi, da maganganun mugunta,10idan ku da kanku kuka tanada wa mayunwata kuma kuka biya buƙatun gajiyayyu; sa'an nan ne haskenku zai keto daga cikin duhu, kuma duhunku zai zama kamar rana tsaka.11Sa'an nan Yahweh zai jagoranceku a kullum kuma ya ƙosar da ku a wuraren da babu ruwa, ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambu mai laima, kuma kamar maɓulɓular ruwa, wanda ruwansa ba ya ƙarewa.12Waɗansunku za su sake gina lalatattun kufaye; za ku tada kufayen tsararraki da yawa; za a kira ku "Masu gyaran Garu," "Masu maido da titunan da za a zauna."13Dãma a ce kun juyo da ƙafafunku daga tafiya a ran Asabaci, kuma daga yin abin son ranku a ranata mai tsarki. Dãma a ce kun kira ranar Asabaci abin farinciki, kuma harma ku kira sha'anin Yahweh tsarki da martaba. Dãma a ce kun girmama ranar Asabacina wurin barin sha'anin kanku, ku kuma bar neman jin daɗin kanku da kuma kun ƙi faɗar maganganun kanku.14Sa'an nan za ku yi farinciki cikin Yahweh; kuma zan sa ku yi yawo a ƙwalƙwolin duniya; zan ciyar daku daga gãdon Yakubu mahaifinku - gama bakin Yahweh ya faɗa."
Wannan yana nufin ihu da ƙarfi. Anan "naku" yana nufin Ishaya.
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Tare suna ƙarfafa gaggawa don fuskantar mutanen Yahweh.
Mutanen Isra'ila suna amfani da tambayoyi don yin gunaguni ga Allah saboda suna ganin yana ƙin kulawarsu.
Wannan ya nuna cewa suna fada da mugunta. "Dunkulallen hannu" yana wakiltar fushin da ke da ƙarfi a zahiri.
Wannan yana nufin mutumin yana durƙusa, amma ba shi da tawali'u da gaske. "Kyauta" yana wakiltar tsire-tsire mai rauni wanda yake lanƙwasa cikin sauƙi.
Yahweh yana amfani da tambaya don tsawata wa mutane. AT: "Tabbas ba kwa tunanin irin wannan azumin zai faranta min rai!"
Duk waɗannan maganganun suna nufin ya kamata su taimaki waɗancan mutanen da miyagu ke cutar da zaluntar su.
Wannan jimlar tana wakiltar fara cin abincin ne ta hanyar mai gida ya kekketa burodin.
"Karya buɗe" a nan wani karin magana ne wanda ke nufin lokacin da haske ya fara haskakawa sosai. Wannan yana nufin cewa idan suka taimaki mutanen da ke cikin buƙata, ayyukansu za su zama kamar fitilu da wasu za su gani, kamar lokacin da rana ta fito bayan dare mai duhu. Ko kuma hasken na iya nufin hasken Yahweh, yana haskaka su yana kuma sa musu albarka.
Wannan yana nufin Allah zai albarkace kuma ya dawo da su da sauri, kamar yadda rauni ya warkar da sauri.
Wannan yana magana ne game da lokacin da Allah ya kare Isra'ilawa yayin da suka tsere daga Masar. Wannan yana nufin Allah zai sake kare su daga abokan gaba idan za su yi abin da ke dai-dai.
"Hasken ku" yana wakiltar ayyukan alherin da zai zama misali ga kowa, kuma "duhu," munanan ayyuka, za a shawo kansa ta kyawawan ayyukansu.
"Ruwa" yana wakiltar duk abin da suke buƙata don rayuwa mai wadatarwa koda kuwa maƙwabtansu ba su da wadatar su.
"Lambu mai ruwa" yana wakiltar yalwa da yalwa don zasu sami duk abin da suke buƙata.
"Maɓuɓɓugar ruwa" tana wakiltar tushen wadata a ƙasar da ruwa yake da daraja.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane za su kira ku"
Anan ana wakiltar mutane da "ƙafafunsu". Allah bai bar doguwar tafiya ko aiki a ranar hutu ba. AT: "kun daina tafiya da yin abin da kuke so ku yi a ranar Asabar, ranar tsarkakakkiya"
Wannan yana nufin Allah yana ɗaukaka al'umma a cikin suna da iko saboda rayuwar adalci.
1Duba, hannun Yahweh bai gajarce bada ba zai iya ceto ba; kunnensa bai kurmance ba, da ba zai iya ji ba.2Ayyukanku na zunubi, duk da haka, su suka raba ku daga Allahnku, kuma zunubanku sun sashi ya ɓoye fuskarsa daga gare ku daga kuma sauraronku.3Gama hannayenku sun haramtu da jini kuma yatsunku da zunubi. Leɓunanku na faɗin ƙarya kuma harsunanku na faɗin tsokana.4Babu mai kira cikin aɗalci, kuma babu mai gudanar da ƙararsa cikin gaskiya. Suna dogara da maganganun wofi, suna faɗin ƙarairayi; Suna ɗaukar cikin masifa su kuma haifi zunubi.5Suna ƙyanƙyashe ƙwayayen maciji mai dafi su kuma sãƙa yanar gizo-gizo. Duk wanda ya ci daga ƙwansu zai mutu, kuma idan aka fasa ƙwan, zai ƙyanƙyashe maciji mai dafi.6sãƙarsu ba za a iya yin tufafi da su ba, kuma ba za su iya rufe kansu da ayyukansu ba. Ayyukansu ayyukan zunubi ne, kuma ayyukan ta'addanci na cikin hannayensu.7Kafafunsu na gudu gun mugunta, kuma suna gudu domin su zubar da jini. Tunaninsu tunanin zunubi ne; ta'addanci da hallakarwa ne hanyoyisu.8Ba su san tafarkin salama ba, kuma babu adalci a tafarkinsu. Sun ƙago karkatattun tafarkuna; Duk wanda ya yi tafiya kan waɗannan tafarku ba zai san salama ba.9Saboda haka adalci ya yi nesa daga gare mu, kuma ayyukan adalci ba su kai wurinmu ba. Mun jira haske, amma muna ganin duhu; muna neman haske amma muna tafiya a duhu.10muna laluɓar bango kamar maƙafi, kamar waɗanda basu gani. Mu na yin tuntuɓe da rana kamar da asussuba; a cikin jarumai muna kama da matattun mutane.11Muna ihu kamar damusai da makoki kamar kurciyoyi; muna jiran adalci amma babu ko ɗaya, domin kuɓutarwa, amma tana nesa da mu.12Gama yawan zunubanmu suna gabanmu, kuma zunubanmu na shaida gãba damu; gama laifofinmu na tare damu, kuma mun san zunubanmu.13Mun yi tayarwa, muna musanta Yahweh kuma mun juya daga bin Allahnmu. Mun faɗi yaudara da juyin baya, mun ɗauki cikin gunaguni daga zuciya da maganganun ƙarya.14An kori adalci baya, kuma ayyukan adalci sun tsaya nesa; gama gaskiya ta yi tuntuɓe a dandali, na gaske ba zai iya zuwa ba.15Aminci ya tafi, kuma wanda ya juya ga barin mugunta ya maida kansa abin zargi. Yahweh ya gani kuma bai ji daɗi ba cewa babu adalci.16Ya ga babu wani mutum, ya kuma yi mamakin cewa babu wanda zai shiga tsakani. Saboda haka damtsensa ya kawo ceto dominsa, kuma ayyukan adalcinsa suka tallafe shi.17Yasa ayyukan adalci su zamar masa sulke da ƙwalƙwalin ceto a kansa. Ya suturta kansa da rigunan ɗaukar fansa ya yafa himma ya zama alkyabbarsa.18Ya biya su gwargwadon abin da suka yi, hunkuncin fushi ga maƙiyansa, da ramako ga magabtansa, da kuma horo ga tsibirai wannan ne ladarsu.19Saboda haka za su ji tsoron sunan Yahweh daga yamma, da ɗaukakarsa daga fitowar rana; gama zai zo kamar rafi mai kwararowa, wand numfashin Yahweh ke tunkuɗawa.20Mai fansa zai zo Sihiyona, da kuma ga waɗanda suka juyo daga ayyukan tayarwarsu cikin Yakubu - wannan furcin Yahweh ne.21Ni dai, wannan shi ne alƙawari na da su - inji Yahweh - ruhuna wanda ya ke bisanku, da maganganuna waɗanda na sa a bakinku, ba za su bar bakinku ba, ko su fita daga bakin 'ya'yanku, ko su fita daga bakin 'ya'yan 'ya'yanku ba - inji Yahweh - daga wannan lokaci zuwa har abada."
"Hannun" yana wakiltar ƙarfi da iyawa. Hannun "gajere" bashi da iko da iyawa. AT: "Yahweh yana da cikakken iko"
"Fuska" yana wakiltar kasancewa da kallo. AT: "Zunubanku sun sa shi juya maka baya"
Anan “hannaye” da “yatsu” na nuni ga ayyukansu. Wannan yana nufin suna da laifi na aikata mugunta da abubuwan zunubi. "Naku" jam'i ne. AT: "Gama kun aikata zunubai masu ƙarfi"
Sassan jikin da ke yin magana suna wakiltar abin da mutane suke faɗi. AT: "Kuna faɗin ƙarya da abubuwa marasa kyau"
"Samun ciki" da "haihuwa" suna nanata yadda suke shirin yin abubuwa na zunubi da kyau. A nan "su" har yanzu suna nufin mutanen Isra'ila. AT: "suna aiki tuƙuru don aikata abubuwan zunubi"
Kwai na maciji mai dafi ya faxi cikin macizai masu haɗari. "Macizai masu dafi" suna wakiltar muguntar da mutane ke aikatawa wanda ke cutar da shi da ƙari. AT: "Suna yin mugunta da ke yaɗuwa don ƙara mugunta"
Cin kwai mai guba zai kashe wanda ya ci shi kuma yana wakiltar halakar kai. Karya kwan ya baiwa matashi maciji mai guba ƙyanƙyashewa kuma yana wakiltar yaɗuwar barna. AT: "Ayyukan da suke yi zai lalata su kuma zai yada lalata ga wasu"
Wannan yana nufin ba za a iya rufewa da ɓoye ayyukansu na zunubi ba, kamar yadda yanar gizo ba za ta iya zama sutura da rufe wani ba. AT: "Za a fallasa munanan ayyukansu a matsayin marasa amfani"
Anan ana wakiltar mutane da "ƙafafunsu". Wannan yana magana akan suyi wani abu da sauri yayin da ƙafafunsu suke gudu zuwa gare shi. AT: "Suna da saurin aikata mugunta"
"hanyoyi" suna wakiltar hanyar rayuwarsu. AT: "ba sa yin abin da yake daidai" ko "duk abin da suke yi rashin adalci ne"
"Hanyoyi masu karkatattu" suna wakiltar hanyar rayuwar da ta lalace. AT: "Suna faɗar da aikata abubuwa marasa gaskiya. Suna yaudara"
Anan "mu" yana nufin Ishaya da mutanen Isra'ila. "Nesa" yana wakiltar cewa adalci ya tafi da wuyar samu. AT: "adalci ya tafi kuma yana da matukar wahalar samu"
Kowane ɗayan waɗannan jimlolin na nufin cewa mutane suna jiran alherin Allah, amma da alama ya watsar da su.
Wannan yana nufin cewa saboda Allah baya zuwa gare su, suna jin babu taimako, ba su sami madaidaiciyar hanya ba kuma sun yanke tsammani game da rayuwa ta gaba, ba tare da begen rayuwa mai kuzari ba.
Waɗannan suna magana ne akan sautukan da mutane suka yi saboda suna cikin damuwa da baƙin ciki.
Anan "namu" yana nufin Ishaya da mutanen Isra'ila.
Ishaya ya bayyana zunuban a matsayin mutumin da ke zuwa gaban Allah don ya bayyana cewa mutane masu laifi ne.
"Tare da mu" yana wakiltar kasancewa da sanin su. AT: "domin muna sane da laifukanmu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutanen suna mayar da adalci baya"
"Yahweh ya firgita cewa babu wanda ya taimaki waɗanda ke wahala." ko "Yahweh ya yi mamakin cewa babu wanda ya zo ya taimaki waɗanda suke wahala."
“Hannun” Yahweh yana wakiltar iyawarsa da ikonsa. AT: "Yahweh yayi amfani da ikonsa don ceton mutane"
"sulken kirji," "hular kwano," "tufafi," da "mayafi" tufafi ne na yaƙi da faɗa. Ishaya ya bayyana Yahweh kamar yadda ya ɗora waɗannan don horon mutanensa.
Anan “suna” yana nufin suna da halayen Yahweh. AT: "ku ji tsoron Yahweh"
Kananan kwari a cikin Yahuza sun bushe mafi yawan shekara har sai kwatsam, ruwan sama mai ƙarfi ya mai da su ruwa mai gudu. Lokacin da hakan ta faru sai hayaniya da iska suka yi yawa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda numfashin Yahweh yake tuƙawa"
"sakon da na baku kuyi magana"
1Tashi, haskaka; gama haskenki ya iso, kuma ɗaukakar Yahweh ta taso a bisanki.2Koda shi ke duhu zai rufe duniya, kuma duhu mai kauri ga al'ummai; duk da haka Yahweh zai tashi bisanki, kuma za a ga ɗaukakarsa a bisanki.3Al'ummai za su zo ga haskenki, sarakuna kuma ga sheƙin haskenki dake tashi.4Duba ko'ina ki gani. Suna tattarowa domin su zo gare ki. 'Ya'yanki maza za su zo daga nesa, kuma 'ya'yanki mata za su ɗaukosu a hannuwansu.5Sa'an nan za ki duba ki cika da farinciki, kuma zuciyarki zata yi ambaliya, domin za a zuba maki yalwar teku, kuma arzikin al'ummai za su zo gare ki.6Ayarin raƙuma za su rufe ki, takarkaran Midiyan da Ifa; dukkansu za su zo daga Sheba; za su kawo zinari da kayan ƙanshi, kuma za su raira waƙar yabon Yahweh.7Dukkan garkunan Kedar za a tara maki, ragunan Nebayot za su biya buƙatunki; za su zama karɓaɓun baiko a kan bagadina; kuma zan darjanta gidana mai daraja.8Su wane ne waɗannan dake shawagi kamar girgije, kuma kamar kurciyoyi da za su mafaƙarsu?9Ƙasashen gãɓar tekuna suna nema na, kuma jiragen ruwa na Tarshish suna jagoranci, domin su kawo 'ya'yanki maza daga nesa, zinariyarsu da azurfarsu na tare da su, domin sunan Yahweh Allahnki, da kuma domin Mai Tsarkin Nan na Isra'ila, saboda ya daukaka ki.10'Ya'ya maza na bãƙi za su gina garunki, kuma sarakunanki za su yi maki bauta; koda ya ke a cikin fushina na hore ki, duk da haka a cikin alheri na zan yi maki jinƙai.11Ƙofofinki ma zasu kasance a buɗe kullum; ba za a rufe su da rana koda dare ba, saboda a kawo arzikin al'ummai da sarakunansu dake masu jagora.12Hakika, al'ummai da masarautu da ba za su ɓauta maki ba za su lalace; waɗannan al'umman za su hallaka kakaf.13Ɗaukakar Lebanon za ta zo gare ki, itatuwan fir da makamantansu za su ƙawata masujadata; kuma zan darjanta wurin sa ƙafafuna.14Za su zo gare ki su yi rusuna, 'ya'yan ki maza waɗanda suka ƙasƙantar dake; za su rusuna a ƙafafunki; za su kira ki Birnin Yahweh, Sihiyona ta Mai Tsarkin Nan na Isra'ila.15A maimakon ki ci gaba da zaman wadda aka yashe ta aka ƙita, ba kuma wanda ya wuce ta wurinki, zan maishe ki abin fahariya na har abada, abin murna daga tsara zuwa tsara.16Za ki kuma sha madarar al'ummai, kuma za a rene ki a kirjin sarakuna; za ki sani cewa Ni, Yahweh, ni ne Mai cetonki da mai Fansarki. Mai Girman nan na Yakubu.17A maimakon tagulla zan kawo maki zinariya, a maimakon ƙarfe zan kawo azurfa; a maimakon katako, tagulla, kuma a maimakon duwatsu, karfe. Zan sa salama ta zama gwamnoninki, adalci kuma masu mulkinki.18Ba za a ƙara jin tashin hankali a ƙasarki ba, ko hallakarwa ko aukawar ɓarna a yankin; amma za ki kira garunki Ceto, ƙofofinki kuma Yabo.19Rana ba za ta ƙara zama haskenki da rana ba, ko hasken wata ya haskaka a kanki; amma Yahweh zai zama haskenki na har abada, Allahnki kuma shi ne darajarki.20Ranarki ba za ta ƙara faɗuwa ba, ko watanki ya dushe ya ɓace ba; Gama Yahweh zai zama haskenki har abada, kuma ranakun makokinki za su ƙare.21Dukkan mutanenki za su zama adalai; za su karɓi mallakar ƙasar na dukkan lokaci, reshen shuka ta da aikin hanuwana, domin a ɗaukaka Ni22Ƙarami ɗaya zai zama dubu, mafi ƙanƙanta guda kuma al'umma mai ƙarfi; Ni, Yahweh, zan aiwatar da waɗannan abubuwa da sauri idan lokacin ya yi.
Wannan yana nuni ne ga kyawawan ayyukan da Yahweh ya yi wa mazaunan Yerusalem. Yanzu suna nuna wannan ɗaukaka ta abin da suke yi da kuma faɗi kuma suna da bege a nan gaba.
Duk waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya kuma an haɗa su don ƙarfafawa. Suna nufin "duhu na ruhaniya." Wannan yana nufin duk sauran mutanen duniya ba za su san Yahweh ko yadda za su faranta masa rai ba. Wannan kwatanci ne na hukuncin Allah.
Wannan yana nufin hasken kasancewar Allah zai bayyana ga Isra'ilawa, kuma zai nuna hanyar da zasu bi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutanen al'ummai za su ga ɗaukakarsa a kanku"
"Su" suna nufin sauran mutanen Isra'ila waɗanda zasu hallara don komawa Yerusalem.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "za su ɗauki 'ya'yanku mata a hannuwansu" ko "za su ɗauke' ya'yanku mata a cinyarsu"
Waɗannan jimlolin suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna jaddada cewa za su yi farin ciki ƙwarai saboda abin da zai faru a Yerusalem.
yanki a cikin Arabiya
Waɗannan sune sunayen yankuna a cikin Arabiya.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutanen Kedar za su tattara muku garkensu"
"Ni, Yahweh, zan karɓe su a kan bagade"
Yahweh yana amfani da tambayoyi da hotunan waƙoƙi don jawo hankali a nan. Ya kamanta tasoshin jiragen ruwa zuwa gajimare da kurciyoyi. Wannan kuma hoton Isra’ilawa ne da suka dawo ƙasar da suke. AT: "Duba, na ga wani abu kamar gajimare yana motsi da sauri kuma kamar kurciya da ke komawa mafakarsu."
"Yahweh ya girmama ka, ya jama'ar Isra'ila"
Anan "rana" da "dare" tare suna nufin "koyaushe." Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba wanda zai taɓa rufe su"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "domin mutanen al'ummu su kawo arzikinsu, tare da sarakunansu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan hallaka mutanen waɗannan al'ummomin gaba ɗaya"
Wannan yana nufin Lebanon ta shahara da kyawawan bishiyoyi, musamman cypress da itacen al'ul. Ba a san ainihin ganewar dukkanin bishiyoyin ba.
Wannan yana nufin haikalin Yahweh.
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 1: 4.
"tare da kowa yana guje wa ƙasarku" ko "tare da duk baƙin da ke guje wa ƙasarku"
Wannan yana nufin wadata da yalwar da za a kwashe daga ƙasashen waje. Duk sassan biyu suna maimaita ra'ayi iri ɗaya don ƙarfafawa.
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 49:26.
Yahweh ya bayyana “salama” da “adalci” a matsayin sarakunan mutane. Wannan yana nufin za a sami cikakken zaman lafiya da adalci a ƙasar Isra'ila.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba za a sake samun rahoton tashin hankali a cikin ƙasarku ba"
Duk ayoyin suna maimaita wannan ra'ayin iri ɗaya don ƙarfafawa.
Wata ba zai shuɗe ba a zahiri. Wannan karin gishirin yana cewa hasken rana da wata zasu fi haske kamar hasken Yahweh.
Yahweh yana kwatanta mutane da ƙananan harbe-harbe waɗanda suke zuwa wanda ya dasa kamar dai shi mai kula da lambu ne. Yahweh ya sanya mutanensa a cikin ƙasar Isra’ila. Hakan yana ba mutane fata.
Yahweh yana kwatanta Isra'ilawa da wani abu da gwanintarsa ta aikin hannu.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "domin dukkan mutane su girmama ni"
1Ruhun Ubangiji Yahweh na bisana, domin Yahweh ya shãfe ni in yi shelar labari mai daɗi ga ƙuntattu. Ya aike ni in warkar da waɗanda suka karye a zuci, in yi shelar 'yanci ga kamammu, da kuma buɗewar kurkuku domin waɗanda suke a ɗaure.2Ya aike ni in yi shelar shekarar tagomashi ta Yahweh, ranar ramuwar gayya ta Allahnmu, in kuma ta'azantar da dukkan masu makoki.3Ya aike ni - in ba masu makoki cikin Sihiyona - in ba su rawani a maimakon toka, mai na farinciki a maimakon makoki, alƙyabba ta yabo a maimakon ruhun baƙinciki, domin a kira su rimayen adalci, dashen Yahweh, domin ya sami ɗaukaka.4Za su sạke gina rusassun birane nadã; za su gyara lalatattun wurare. Za su gyara rusassun birane, lalatattu tun daga tsararrakin da suka rigaya suka wuce.5Bãƙi za su tsaya su ciyar da garkunanki, 'ya'yan baƙi kuma za su yi maki aiki a gonakinki dana garkunan inabinki.6Za a kira ku firistocin Yahweh; za su kira ku bayi na Allahnmu. Za ku ci wadatar al'ummai, kuma za ku yi fahariya cikin arzikinsu.7A maimakon kunyar ki zaki sami riɓi biyu; kuma a maimakon ƙasƙanci za su yi farinciki da rabonsu. Haka za su sami riɓi biyu na rabon ƙasarsu; murna zata zama tasu har abada.8Gama Ni, Yahweh, ina kaunar shari'ar gaskiya, kuma na ƙi fạshi da shari'ar zalunci. Na tabbata zan sạka masu, kuma zan yi madawwamin alƙawari dasu.9Zuriyarsu za su zama sanannu a cikin dukkan al'ummai, kuma 'ya'yan tsatsonsu cikin mutane. Dukkan wanda ya gan su zai tabbatar da su, cewa su ne mutanen da Yahweh ya sawa albarka.10Zan yi farinciki sosai cikin Yahweh; cikin Allahna zan yi murna sosai. Gama ya suturce ni da mayafan ceto; ya suturceni da rigar adalci, kamar yadda ango ke ƙawata kansa da rawani, kuma kamar yadda amarya takan ƙawata kanta da kayan ado.11Gama kamar yadda ƙasa take fito da dashe-dashenta, kuma kamar yadda gona takan sa shuke-shukenta su tsiro, haka Ubangiji Yahweh zai sa adalci da yabo su tsiro a gaban dukkan al'ummai.
“Ruhu” anan Ruhu Mai Tsarki ne na Yahweh wanda ke tilasta ko motsa mutumin. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 11: 2 ko a cikin Ishaya 42: 1.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya. Sun bayyana cewa tabbas Allah zai bada yanci ga kamammun.
Duk waɗannan jimlolin suna nuni ne ga lokaci ɗaya. "Shekarar" da "rana" duka takamaiman misalai ne waɗanda ke wakiltar mafi girma duka.
Mutane suna saka mai a kansu kuma suna sanye da kyawawan tufafi masu tsada a lokacin biki da farin ciki.
Wannan yana nufin Yahweh ya sa mutane su zama masu ƙarfi da ƙarfi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "domin rayuwar mutane ta daukaka shi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane za su kira ku"
Wannan mai yiwuwa yana nufin yanki biyu na ƙasa.
Waɗannan jimloli guda biyu suna nufin abu ɗaya. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane daga wasu ƙasashe za su san zuriyarsu"
"I" yana nufin mutanen Allah suna magana azaman mutum ɗaya wanda Yahweh ya mayar da shi.
Mutanen Allah suna magana kamar mutum ɗaya yanzu suna da ceto da adalci kamar yadda bayyanar su ta bayyane ga kowa. "Gargaji" da "tufafi" tufafi ne da kowa zai iya gani.
Wannan yana faɗin abu ɗaya ta hanyoyi biyu. Gaskiyar cewa duk abin da Allah ya ce zai yi tabbas zai faru idan aka kwatanta shi da gaskiyar cewa ƙwaya yakan tsiro bayan ya yi shuka. AT: "Kamar yadda iri da aka shuka a cikin lambu ya tsiro daga ƙasa ya girma"
1Saboda Sihiyona ba zan yi shuru ba, saboda da kuma Yerusalem ba zan yi tsit ba, har sai adalcinta ya bayyana da haske sosai, kuma cetonta kamar fitila mai ci bal-bal.2Al'ummai za su ga adalcinki, dukkan sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki. Za a kira ki da sabon suna wanda Yahweh zai zaɓa.3Za ki zama kambi mai daraja cikin hannun Yahweh, kuma rawanin sarauta a cikin hannun Allahnki.4Ba za a ƙara ce dake, "Yasasshiya" ba; ko ƙasarki ba za a ce da ita, "Watsattsiya ba." Hakika, za a ce dake "Farincikina na cikin ta," ƙasarki kuma "Aurarra," gama Yahweh na farinciki dake, kuma ƙasarki za ta yi aure.5Hakika, kamar yadda saurayi matashi yakan auri 'yar budurwa, haka 'ya'yanki za su aure ki, kuma kamar yadda ango ke farinciki da amaryarsa, Allahnki zai yi farinciki dake.6Na sa masu tsaro a bisa ganuwarki, Yerusalem; ba za su yi shuru ba dare da rana. Ku da kuke tunasshe da Yahweh, kada ku tsagaita.7Kada ku ba shi hutu har sai ya sake kafa Yerusalem ya kuma maishe ta abin yabo a duniya.8Yahweh ya yi rantsuwa da hannunsa na dama da kuma hannunsa mai iko, "Hakika ba zan ƙara bada hatsinki ya zama abinci ga maƙiyanki ba. Bãƙi ba za su sha sabon ruwan inabinki ba, wanda ke kika aikinta ba.9Gama waɗanda suka yi girbin hatsinsu za su ci su kuma yabi Yahweh, kuma waɗanda suka tsinke 'ya'yan inabisu za su sha ruwan inabin a cikin wurarena masu tsarki."10Ku shigo, ku shigo ta cikin ƙofofi! Ku shirya hanya domin mutane! Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku tattara duwatsu! Ku tada tutar alama sama domin al'ummai!11Duba, Yahweh yana sanarwa zuwa ga iyakar duniya, "Ku cewa ɗiyar Sihiyona: Duba, Mai cetonki yana zuwa! Ki gani, ladarsa na tare da shi, kuma sakamakonsa ya sha gabansa."12Za su kira ki, "tsarkakakkiyar jama'a; fansassu na Yahweh," kuma za a kira ki "Biɗaɗɗiya; birnin da ba a yashe shi ba."
Wataƙila shine "I" yana nufin Ishaya.
Duk kalmomin biyu suna tabbatarwa mutane cewa daga ƙarshe Allah zai zo ya ceci Isra'ilawa kuma zai kasance kamar yadda haske yake.
Waɗannan suna nufin abu ɗaya kuma ana haɗuwa don girmamawa. Sun ce Yerusalem za ta zama birni masarauta a ƙarƙashin ƙarfi da ikon Allah. Hannun Yahweh alama ce ta ƙarfin da ikonsa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane ba za su ƙara faɗi game da ku ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kuma mutane ba za su ƙara cewa game da ƙasarku ba"
Anan "'ya'ya maza" yana nufin mutanen Isra'ila kuma "ku" yana nufin Yahuda, ƙasar Isra'ila. Wannan yana nufin mutane zasu mallaki ƙasar kamar yadda mutum ya mallaki ƙaramar matarsa.
Wannan yana jaddada farin cikin Allah game da alaƙar sa da mutanen sa.
Wannan yana magana ne game da annabawa, jami'ai, ko kuma mala'iku, waɗanda koyaushe suna yin addu'a domin mutanen Yerusalem kamar masu tsaro waɗanda ke kiyaye birni koyaushe. Duba yadda kuka fassara "masu tsaro" a cikin Ishaya 52: 8 da Ishaya 56:10.
Wannan yana nufin suna ci gaba da roƙon Yahweh ko kiran juna. AT: "suna roƙon Yahweh sosai a cikin yini duka"
Anan "shi" yana nufin Yahweh.
Hannun dama da hannu suna wakiltar iko da iko. AT: "ta ikonsa da ikonsa"
Wannan yana nufin Yahweh ba zai bar magabta su ci Isra’ilawa da ƙwace hatsinsu ba kuma. Wataƙila maƙiya sun ɗauki hatsi a baya azaman haraji ko ciyar da sojojinsu.
An tsara waɗannan maganganun tare don ƙarfafawa da kammalawa.
An maimaita kalmar "zo ta hanyar" don nuna gaggawa.
Kalmar "gina" an maimaita shi don nanata cewa Yahweh yana buƙatar hanyan da sauri. “Babbar Hanya” tana wakiltar hanyar da mutane za su iya dawowa. Wannan yayi dai-dai da Ishaya 40: 3 da Ishaya 57:14.
"Dauke duwatsu daga kan hanya don ya zama lami." Duwatsu suna wakiltar duk cikas ga saurin tafiya.
Wuraren da suke nesa da duniya ana maganarsu kamar su ne wuraren da duniya ta kare. Wannan jumlar kuma tana haifar da merism kuma tana nufin ko'ina a tsakanin ƙarshen. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 40:28. A "wurare mafi nisa na duniya" ko "duk duniya"
"'Yata" tana wakiltar mutanen Yerusalem (Sihiyona).
Waɗannan sassan suna wakiltar ra'ayi ɗaya don ƙarfafawa. Dubi yadda kuka fassara makamancin magana a cikin Ishaya 40:10. (Duba:
1Wane ne wannan da ya ke zuwa daga Idom, yafe da jar tuffa daga Bozara? Wane ne shi cikin kayan sarauta, yana takawa da ƙarfin hali sabili da girman ƙarfinsa? Ni ne, ina maganar adalci da kuma ikon yin ceto.2Me yasa kayayyakinka suka yi jạ, kuma me yasa suka yi kamar ka daɗe kana tattaka 'ya'yan inabi a wurin matatsar inabi?3Na tattaka 'ya'yan inabi a matatsar inabi ni kaɗai, kuma babu wani daga cikin al'ummai da ya yi tare da ni. Na tattakesu a cikin fushina na kuma rugurgujesu cikin hasalata. Jininsu ya ɗiɗɗiga a kan kayana kuma ya ɓaɓɓata tufafina.4Gama ina hangen ranar ramuwa, kuma shekara domin fansata ta rigaya ta zo.5Na duba, kuma babu wani da zai yi taimako. Na yi mamaki cewa babu mai taimako, amma hannuna ya kawo mani nasara, kuma fushina mai tsanani ya iza ni.6Na tattake mutanen a cikin fushina na kuma sa sun bugu cikin hasalata, na kuma zubar da jininsu a fuskar ƙasa.7Zan faɗi amincin ayyukan alƙawarin Yahweh, ayyukan yabo na Yahweh. Zan faɗi dukkan abin da Yahweh ya yi mana, da kuma manyan alherinsa zuwa gidan Isra'ila. Wannan tausayi da ya nuna mana sabili da jinƙansa, da kuma ayyuka masu yawa na amintaccen alƙawarinsa.8Gama ya ce, "Hakika sụ mutanena ne, 'ya'ya masu biyayya." Ya zama Mai cetonsu.9Cikin dukkan wahalarsu, shima ya wahala, sai mala'ika daga gare shi ya cecesu. Cikin ƙaunarsa da jinƙansa ya cecesu, ya kuma ɗagasu sama ya kuma bishesu a cikin dukkan zamanan dã.10Amma suka yi tayarwa suka ɓata wa Ruhunsa Mai Tsarki rai. Saboda haka yạ zama abokin gạbarsu ya kuma yaƙesu.11Mutanensa suka yi tunani game da kwanakin dã na Musa. Suka ce, "Ina Allah, wanda ya fito da su daga teku da makiyayin garkensa? Ina Allah, wanda ya sanya Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu?12Ina Allah, wanda yasa darajar ikonsa ya tafiya tare da hannun daman Musa, ya kuma raba ruwa a gabansu, domin ya yiwa kansa suna na har abada?13Ina Allah, wanda ya bi da su ta cikin ruwa mai zurfi? Kamar doki mai gudu a hanya mai kyau, ba su yi tuntuɓe ba.14Kamar shanu da suke gangarawa zuwa cikin kwari, Ruhun Yahweh ya ba su hutuwa. Sai ka bida da mutanenka, domin ka yiwa kanka suna mai yabo.15Ka duba daga sama ka kuma kula daga wurinka mai tsarki da kuma maɗaukakin mazauni. Ina himmarka da kuma manyan ayyukanka? Tausayinka da ayyukan juyayinka an hana mana su.16Gama kai ne ubanmu, ko da shi ke Ibrahim bai sanmu ba, kuma Isra'ila bai fahimcemu ba, kai, Yahweh, kai ne ubanmu. 'Mai fansarmu' sunanka kenan tun zamanan dã.17Yahweh, me yasa ka sạmu muka bijire daga hanyoyinka ka kuma taurare zukatanmu, har ba mu yi maka biyayya ba? Ka dawo ta dalilin bayinka, kabilun gãdonka.18Mutanenka sun mallaki wurinka mai tsarki na ƙaramin lokaci, amma maƙiyanmu suka tattake ta.19Muka zama kamar waɗanda ba ka taɓa mulkinsu ba, kamar waɗanda ba a taɓa kiransu da sunanka ba."
Ishaya yayi magana azaman mai tsaro yana amfani da tsarin tambaya da amsa don gabatar da wannan bayani game da hukuncin Ubangiji akan Idom, maƙiyin Isra’ila. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Ni, Yahweh, ina zuwa daga Idom, saye da ja daga Bozara"
Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Jan da ke jikin tufafinku ya zama kamar kuna matse inabi ne a matsewar ruwan inabi."
Anan "I" yana nufin Yahweh. Wannan hoton yana nuna Yahweh yana lalata abokan gaba.
"lokacin ramuwa" ko "lokacin ramuwa"
Anan “shekara” na nuni ga takamaiman lokacin da Yahweh ya sanya domin dawo da Isra’ila. AT: "lokacin fansa na"
Wannan yana nufin Yahweh ya sa su mamaki da azanci ta wurin cikakken fushinsa da ukubarsa.
Anan “jini” yana wakiltar rayuwar magabtan Yahweh wanda ke ta malalo don su mutu.
Anan "I" yana nufin Ishaya.
Anan "mu" yana nufin Ishaya da mutanen Isra'ila.
"Duk wahalar da muke sha." Anan "nasu" yana nufin mutanen Isra'ila. Ishaya ya haɗa kansa a matsayin memba na mutane.
Wannan wakili ne wanda aka aiko daga gaban Allah.
Wannan yana nufin lokacin da Allah ya kare kuma ya ceci Isra'ilawa daga Masarawa shekaru da yawa da suka gabata. Cikakkiyar ma'anar wannan bayanin za a iya bayyana a sarari.
"amma mun yi tawaye." Anan "su" suna nufin mutanen Isra'ila. Ishaya ya haɗa kansa a matsayin memba na mutane.
Labarin Yahweh ta hanyar mu'ujiza ya raba ruwan Tekun Iwa domin Isra'ilawa su haye su tsere wa Masarawa ana ɗaukar ilimi.
Ana kiran shugabanni a wasu lokuta "makiyaya." AT: "shugabannin mutanensa"
Anan “hannun dama” yana wakiltar ikon Yahweh ta wurin Musa. Wannan yana nufin ikon Allah ne ya ba Musa damar raba ruwan Tekun Reed.
Wannan yana nufin cewa Isra'ilawa suna da ƙafafun kafa kamar dawakai a cikin fili a kan tafiyetafiyensu zuwa Isra'ila daga Masar.
Wannan hoton yana nuna shanu suna shiga cikin kwari inda akwai ciyawa da ruwa kuma yana jaddada cewa Allah ya jagoranci Isra'ilawa kuma ya kula da su.
Anan "sunan yabo" yana nufin girmamawa da mutuncin mutum. AT: "don tabbatar da cewa kun sami mutunci mai daraja don kanku"
Marubucin yayi amfani da tambaya don bayyana zurfin juyayi da damuwa saboda da alama Allah baya taimakon su. Ana iya fassara wannan tambayar ta lafazi a matsayin sanarwa. AT: "Ba mu ga himmar ku da ayyukanku masu girma ba!"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ka kiyaye tausayin ka da tausayin mu daga gare mu"
Waɗannan kakannin na Isra’ila ba za su iya tantance zuriyarsu ba saboda sun canza sosai. "Ibrahim" da "Isra'ila" suna wakiltar mutane daga abubuwan da suka gabata.
Rashin yin abin da Yahweh yayi umarni ana maganarsa kamar mutum ya ɓace daga madaidaiciyar hanya. AT: "me yasa kuke yin abin da ba daidai ba"
Wannan yana nufin zama mai juriya ga koyarwar Yahweh ta ƙi sauraro da biyayya. Anan "zuciya" tana wakiltar muradi, ji da sha'awar su.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Kalmar "suna" tana nufin dangantakar iyali. AT: "wanda bai taba zama na danginku ba"
1Ai ya, dãma ace ka tsaga sammai ka sauko ƙasa! Da tsaunuka sun girgiza a gabanka,2kamar yadda wuta ke chinye ƙananan kurmi, ko wuta tasa ruwa ya tafasa. Ai ya, dãma dai sunanka ya zama sananne a wurin magabtanka, domin al'ummai su yi rawar jiki a gabanka!3A dã, da kayi abubuwan ban mamaki waɗanda ba mu zata ba, kạ sauko ƙasa, kuma tsaunuka suka girgiza a gabanka.4Tun a zamanin dã ba wanda ya taɓa ji ko ya fahimta ko ya gani da ido wani Allah in banda kai, wanda ya ke yin abubuwa ga wanda ya jira gare shi.5Ka kan zo ka taimaki waɗanda suke farinciki da aikata abin dake na adalci, su dake tunawa da hanyoyinka suna kuma yin biyayya dasu. Kạ yi fushi a lokacin da muka yi zunubi. Ta hanyoyinka kullum za a cecemu.6Gama dukkan mu mun zama kamar wanda ya ƙazamtu, kuma dukkan aikin adalcinmu kamar tsumman jinin haila. Dukkanmu mun yi yaushi kamar ganyaye; kurakuranmu, kamar iska, sun kwashe mu nesa.7Babu ko ɗaya mai kira bisa sunanka, wanda ya ke ƙoƙarin ya kama ka. Gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace a cikin hannun kurakuranmu.8Duk da haka, Yahweh, kai ne ubanmu; mu ne yimɓu. Kai ne maginin tukunya; kuma dukkanmu aikin hannunka ne.9Kada ka yi fushi sosai, Yahweh, kada koyaushe ka tuna da zunubanmu gãba damu. In ka yarda ka dube mu dukka, jama'arka.10Biranenka masu tsarki sun zama jeji; Sihiyona ta zama jeji, Yerusalem kuma kango.11Haikalinmu mai tsarki mai kyau, inda dã ubanninmu suka yabe ka, an rusar da su da wuta, kuma dukkan abin dake da muhimmanci yạna a lalace.12Ta ƙaƙa za ka jure wannan, Yahweh? Ta ƙaƙa za kayi shuru ka kuma ci gaba da ƙasƙantar damu?
Idan Yahweh ya nuna kansa sosai ta hanyar tsaga sama. Kalmomin "tsattsagewa" suna nuni ne da yage wani kyalle.
Duwatsu sun yi rawar jiki kamar na girgizar ƙasa.
Wannan yana iya jaddada yadda sauƙin kasancewar Allah zai sa duwatsu da mutane su yi rawar jiki.
Anan “ido” yana nufin mutum duka. AT: "kuma ba wanda ya gani"
Wannan karin magana ne da ke nufin "tuna".
"Ragowar jinin haila" wani kyalle ne da mace take amfani da shi a lokacin da watan yake yin jini daga mahaifarta. Wannan yana nufin duk ƙoƙarin da suka yi na faranta wa Allah rai ya faskara. Wannan hukuncin ya kasance mai ban tsoro.
Ishaya ya gwada mutanen Isra'ila da ganyen da suka bushe lokacin da suka mutu.
Wannan yana nufin zunubansu, a zaman jama'a, shine dalilin gazawar su. Ishaya ya kwatanta laifofi da iska kamar ƙarfi don wahalar azabar Yahweh.
Wannan yana nufin Allah ya ba da mutanensa kuma ya ba su wahala.
Wannan yana nufin Allah ya halicci mutanen Isra'ila.
Wannan yana nanata cewa an lalata biranen kuma babu mai zama a ciki.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki.AT: "Abokan gaba sun lalata haikalinmu mai kyau da kyau, inda kakanninmu suka yabe ku, da wuta"
Suna amfani da tambayoyi don nuna bacin ransu domin har yanzu Allah bai zo ya taimake su ba. AT: "Don Allah kar ka tsaya, ya Yahweh! Da fatan kar ka yi shiru ka ci gaba da wulakanta mu!"
1"Na shirya da su same ni su waɗanda ba su tambaya ba; Na shirya domin su same ni su waɗanda ba su neme ni ba. Na ce, 'Ga ni nan! Ga ni nan!' ga al'ummar da ba su kira bisa sunana ba.2Na miƙa hannayena dukkan yini zuwa ga mutane masu taurin zuciya, masu tafiya a cikin tafarkin da ba dai-dai ba, waɗanda suka yi tafiya bisa ga tunaninsu da shirye-shiryensu!3Sụ jama'ane dake tozartani a koyaushe, suna miƙa hadayu a cikin gonaki, suna kuma ƙona turare bi sa ginin tuballa.4Sukan zauna cikin maƙabarta suna tsaro dukkan dare, suna kuma cin naman alade tare da romon ruɓaɓɓen nama a cikin kwanoninsu.5Suna cewa, "Tsaya nesa, kada ka zo kusa da ni, gama nafi ka tsarki.' Waɗannan abubuwa hayaƙi ne cikin hancina, wutar da take ƙonewa duk yini.6Duba, a rubuce ya ke a gabana: Ni ba zan yi shuru ba, gama zan yi masu sãkayya; zan sãka masu a cikin cinyarsu,7domin zunubansu da zunuban ubanninsu tare," Yahweh ya faɗa. "Zan sãka masu domin ƙona turare a bisa tsaunuka da kuma ba'ar da suke yi mani a bisa tuddai. Saboda haka zan auna masu ayyukansu na dã a cikin cinyarsu."8Ga abin da Yahweh ke cewa, "Kamar yadda a ke samun ruwan inabi daga nonon 'ya'yan inabi, lokacin da wani na cewa, 'Kada ka lalata shi, gama akwai abu mai kyau a cikinsa; Ga abin da zan yi domin barorina: Ba zan lallatar da su dukka ba.9Zan fito da zuriya daga Yakubu, kuma daga Yahuda waɗanda za su mallaki tsaunukana. Zaɓaɓɓuna za su mallaki ƙasar, kuma bayina za su zauna a wurin.10Sharon zata zama makiyaya domin garkena, kuma Kwarin Ako wurin hutawar garkuna, domin mutanena masu nema na.11Amma ku da kuka yashe da Yahweh, waɗanda suke mantawa da tsaunina mai tsarki, masu shirya teburi domin allahn Sa'a, su kuma cika moɗar ruwan inabi mai gauraye domin Ƙaddara.12Zan ƙaddara ku ga takobi, kuma dukkanku za ku rusuna ga kisa, domin a lokacin da nayi kira, ba ku amsa ba; da nayi magana, ba ku saurara ba. Amma ku ka aikata abin dake mugu a gabana kuka kuma zaɓi ku aikata abin da ba zan ji daɗinsa ba."13Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ke faɗi, "Duba, bayina za su ci, amma ku za ku ji yunwa; duba, bayina za su sha, amma ku za ku ji ƙishi; duba, bayina za su yi murna, amma ku za ku kunyata.14Duba, bayina za su yi sowa da farinciki domin murnar zuciya, amma ku za ku yi kuka saboda da zafin zuciya, kuma za ku yi makoki saboda karayar ruhu.15Za ku bar sunanku abin la'antawa domin zaɓaɓɓuna su yi managa; Ni, Ubangiji Yahweh, zan kasheku; Zan kira bayina da wani suna.16Duk wanda ya furta albarka ga ƙasar zaiyi albarka ta wurina, Allah na gaskiya. Duk wanda ya yi rantsuwa a duniya zai rantse da ni, Allah na gaskiya, gama matsalolin dã za a manta da su, gama za su ɓoye daga idanuna.17Gama duba, ina dab da halitta sabobbin sammai da kuma sabuwar duniya; kuma al'amuran dã ba za a tuna dasu ba ko su zo ga rai.18Amma ku za kuyi murna da farinciki har abada a cikin abin da zan hallita. Ga shi, ina dab da halitta Yerusalem abin farinciki, mutanenta kuma abin fahariya.19Zan yi murna bisa Yerusalem in kuma ji daɗi bisa mutanena; kuka da ihu saboda matsala ba za a ƙara ji a cikinta ba.20Ba zai ƙara faruwa ba ɗan jinjiri ya rayu kwanaki kaɗan; ko tsohon mutum ya mutu kafin lokacinsa. Wanda ya mutu yana shekara ɗari za a ce da shi matashi. Duk wanda ya kãsa kaiwa shekara ɗari za a ɗauke shi la'ananne ne.21Za su gina gidaje su kuma zauna ciki, kuma za su shuka garkunan inabi su ci amfaninsu.22Ba za su ƙara gina gida wani daban ya zauna ciki ba; ba za su shuka, wani ya ci ba; gama kamar kwanakin itatuwa haka zai zama kwanakin jama'ata. Zaɓaɓɓuna za su kere ayyukan hannuwansu a shekaru.23Ba za su yi aiki a banza ba, ko su haifi kaito. Gama sụ 'ya'yan waɗanda Yahweh yasa masu albarkata ne, kuma da zuriyarsu tare da su.24Kafin su kira, Zan amsa; kuma a lokacin da suke magana, Zan ji.25Damisa da ɗan rago za su yi kiwo tare, kuma zaki zai ci ciyawa kamar sã; amma ƙura ce za ta zama abincin maciji. Ba za su ƙara cutarwa ko su hallakar a kan dukkan tsaunina mai tsarki," inji Yahweh.
Anan "I" yana nufin Yahweh.
"Yada hannayena" a nan aikin mutum ne don nuna roƙo ko buƙata mai ƙarfi. AT: "A koyaushe ina roƙon mutane masu taurin kai da su karɓi taimako na"
Wannan yana nuni ne ga tuntubar matattu, aikin da Yahweh ya hana.
Yahweh bai ba Isra’ilawa cin nama daga aladu ba.
Yahweh yana kwatanta waɗannan mutanen waɗanda ke ci gaba da ba shi haushi da shan taba wanda ke ba da haushi ga numfashin mutum.
Yahweh ya kwatanta mutanen Isra’ila da wuta mai ci a hankali wanda ke fitar da hayaƙi ba tare da tsayawa ba yayin da yake fusata.
"Ku lura kuma ku kula"
Wannan yana nufin Allah zai yi musu azaba daidai gwargwado. Wannan magana tana kwatanta Yahweh yana hukunta mutane don zub da ƙafafunsu yayin da suke zaune.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da kuka sami ruwan 'ya'yan itace a gungu"
Ana iya bayyana wannan da kyau. AT: "Zan keɓe wasu daga cikinsu masu adalci"
Wannan yana nufin mafi girman wurare a Yerusalem da duk Yahudiya.
Wannan sunan kwari ne mai yuwuwa daga Yerusalem zuwa kudu da Yeriko. Wannan ma yanki ne mai kiwo mai dausayi.
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 11: 9.
Mutane za su kawo abinci da abin sha su ajiye a gaban gunkin a matsayin bautar su.
"Takobin" yana wakiltar makaman yaƙi da Yahweh zai yi amfani da su don hukunta waɗanda ba su amsa kiran Yahweh ba.
Dukansu jimlolin suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana maimaita su don ƙarfafawa.
"Ka lura kuma ka mai da hankali" Yahweh ya maimaita wannan don girmamawa.
Waɗannan jimlolin suna da ma'ana iri ɗaya kuma maimaitawa don ƙarfafawa ne.
Wannan furucin yana kwatanta jin takaici da baƙin ciki ga wani abu da zai zama mara kyau saboda matsin lamba.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ni, Allah wanda ke faɗin gaskiya koyaushe, zan albarkace shi"
"ɓoye daga idona" yana wakiltar hankali da ƙwaƙwalwar Yahweh. AT: "Ba zan sake yin tunanin su ba"
Dukansu maƙiya ne waɗanda ke wakiltar duk abin da ke tsakanin.
Duk waɗannan maganganun suna nufin abu ɗaya kuma an haɗa su don ƙarfafawa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba zaku ma yi tunanin abin da ya faru ba a da"
Kuna iya bayyana wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "ba wanda zai sake jin kuka da kukan damuwa a cikin ta"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane za su ɗauke shi matashi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane za su ɗauki wannan mutumin a matsayin la'ananne"
"Gama mutanena zasu rayu muddin itatuwa suna rayuwa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "su 'ya'yan waɗanda Yahweh ya albarkace su"
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 11: 9.
1Wannan shi ne abin da Yahweh ya ke cewa, "Sama kursiyina ne, ƙasa kuma matashin sawuna. To ina gidan da za ku gina mani? Ina wurin da zan iya hutawa?2Hannuwana suka yi dukkan waɗannan abubuwa; haka waɗannan abubuwa suka zo suka kasance - wannan shi ne abin da Yahweh ya furta. Wannan shi ne mutumin dana zaɓa, karyayye da tawali'u a ruhu, kuma wanda ya ke rawar jiki ga maganata.3Shi wanda ya yanka rago ya kuma kashe mutum; shi wanda ya yi hadayar ɗan rago ya kuma karya wuyan kare; shi wanda ya miƙa baikon hatsi ya miƙa jinin alade; shi wanda ya miƙa turare na tunawa shima yasa wa mugunta albarka. Sun zaɓi hanyoyin kansu, kuma suna fahariya da aikin ƙazamtarsu.4Ni ma haka zan zaɓi masu horonsu; zan kawo a bisansu abin nan da suke tsoro, domin a lokacin dana yi kira, ba bu wanda ya amsa; dana yi magana, ba bu wanda ya saurara. Suka aikata abin da ke mugu a gabana, suka zaɓi su yi abin dake ɓata mani rai."5Ku saurara ga maganar Yahweh, ku da kuke rawar jiki da maganarsa, "Yan'uwanku da suka ƙi ku suka ware ku sabili da sunana suka ce, 'Bari Yahweh ya ɗaukaka, sa'an nan za mu ga murnar ku'; amma za a kunyatar dasu.6Hayaniyar yaƙi na fitowa daga birnin, hayaniya daga haikali, hayaniyar Yahweh yana sãka wa maƙiyansa.7Kafin ta shiga naƙuda, ta haihu; kafin zafi ya abko mata, ta haifi ɗa namiji.8Wane ne ya taɓa jin abu kamar haka? Wane ne ya taɓa ganin abubuwa kamar haka? Ana iya haihuwar al'umma a rana ɗaya? Al'umma tana iya haihuwa a ɗan ƙanƙanin lokaci? Duk da haka da Sihiyona ta shiga naƙuda, nan da nan ta haifi 'ya'yanta.9Zan kawo jinjiri a cikin ƙofar fita in kuma hana a haifi jaririn?- Yahweh yana tambaya. Ko ina kawo jariri lokacin haihuwa amma sai in hana shi fitowa?- Allahnka na tambaya."10Ku yi farinciki da Yerusalem ku yi murna dominta, dukkanku masu ƙaunarta; ku yi farinciki da ita, dukkanku da kuke makoki a kanta!11Gama za kuyi reno ku kuma ƙoshi; da nonnanta za ku ta'azantu; Gama za ku sha ku ƙoshi ku kuma ji daɗin yalwar ɗaukakarta.12Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Ina gab da zubo wadata bisanta kamar kogi, kuma arzikin al'ummai kamar ambaliyar kogi. Za kuyi reno kusa da ita, a ɗauke ku cikin hannuwanta, a karkaɗa ku da murna a gwuiwarta.13Kamar yadda mahaifiya ke ta'azantar da ɗanta, haka ni ma zan ta'azantar daku, kuma za ku ta'azantu a cikin Yerusalem."14Za ku ga wannan, kuma zuciyarku za tayi farinciki, kuma ƙasusuwanku za su tsiro kamar 'yan ciyayi. Za a bayyana hannun Yahweh ga bayinsa, amma zai nuna fushinsa gãba da maƙiyansa.15Gama duba, Yahweh yana zuwa da wuta, kuma karusansa suna zuwa kamar guguwar iska domin ta kawo zafin fushinsa da kwaɓarsa tare da harshen wuta.16Gama Yahweh yana shar'anta 'yan adam da wuta da kuma takobinsa. Waɗanda Yahweh ya kashe za su yi yawa.17Sun keɓe kansu suna tsabtace kansu, domin su shiga gonaki, suna bi ta tsakiyar waɗanda suke cin naman alade da abubuwan ban ƙyama kamar kũsu. "Za su kawo ga ƙarshe - wannan shi ne furcin Yahweh.18Gama na san ayyukansu da tunaninsu. Lokaci na zuwa da zan tara dukkan al'ummai da yarurruka. Za su zo su ga ɗaukakata.19Zan sa gaggarumar alama a tsakaninsu. Sa'an nan zan aiko da masu tsira daga gare su zuwa ga al'ummai: Zuwa ga Tarshish, Fut, da Lud, masu harbi da suke jan bakansu, zuwa ga Tubal, da Yaban, da kuma zuwa iyakar ƙasashen bakin ruwa da ke nesa inda ba su taɓa ji game da ni ko suka ga ɗaukakata ba. Za su furta ɗaukakata a tsakiyar al'ummai.20Za su dawo da dukkan 'yan'uwanku daga cikin al'ummai, abin baiko ga Yahweh. Za su zo bisa dawakai, da karusai, da cikin kekunan shanu, da bisa jakuna, da kuma bisa raƙuma, zuwa ga tuduna mai tsarki Yerusalem - inji Yahweh. Gama jama'ar Isra'ila za su kawo baiko na hatsi a cikin kwanuka masu tsabta cikin gidan Yahweh.21Zan zaɓi wasu daga cikinsu su a matsayin firistoci da kuma Lebiyawa - inji Yahweh22Gama kamar yadda sabuwar sammai da sabuwar duniya da zan halitta za su dawwama a gabana - wannan shi ne furcin Yahweh - haka zuriyarku za su dawwama.23Daga wata ɗaya zuwa na gaba, kuma daga wannan Asabaci zuwa na gaba, dukkan mutane za su zo su rusuna mani - inji Yahweh.24Za su fito waje su dubi gawawakin jama'ar da su ka yi mani tayarwa, gama tsutsotsin da za su ci su ba za su mutu ba, kuma wutar da za ta haɗiyesu ba za ta ɓice ba; kuma za su zama abin ƙi ga dukkan masu rai."
Yahweh ya kamanta sama da kursiyi da ƙasa da matashin sawun sa don ya nanata girman sa.
Yahweh yana amfani da tambayoyi don ya nanata cewa mutane ba za su iya gina masa wurin zama ba.
Yahweh yana wakilta da hannunsa wanda ke ƙarfafa ikonsa. AT: "Duk na yi waɗannan abubuwa"
Anan "karye" da "tuba" yana nufin mutum mai tawali'u da gaske wanda yake wahala don imaninsa.
Waɗannan jimloli huɗun duk suna bayanin hanyoyi daban-daban da mugayen mutane suke aikatawa kuma sun zo ga ma'ana ɗaya don girmamawa.
"Sun zaɓi su aikata mugunta waɗanda suke keta hanyoyin Yahweh"
Anan gani yana wakiltar hukunci ko kimantawa. AT: "abin da nake ganin mugunta ne" ko "abin da ke mugu a cikin hukunci na"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ɗaukaka Yahweh" ko "Bari Yahweh ya ɗaukaka kansa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "amma zan basu kunya"
Yahweh yayi bayanin hukuncin munafurcin masu bauta.
Sautin yana wakiltar ainihin fadan da ake yi a cikin haikalin yayin da Yahweh yake zartar da hukuncin.
Yahweh yana magana game da Sihiyona kamar mace ce da za ta haihu. Ko da yake an lalata Sihiyona kuma mutane ba su ƙara zama a wurin ba, Yahweh ya yi alkawarin cewa ba tare da ɓata lokaci ba kuma da ɗan ƙoƙari wata al'umma za ta fito daga gare ta.
Yahweh yana amfani da tambayoyi don jaddada yadda wannan taron zai kasance na musamman. Jerin tambayoyin yana gina tashin hankali har sai an ambaci Sihiyona.
Yahweh yana amfani da tambayoyi don jaddada cewa ba zai kasa cika alkawuran da ya yi wa mutanen Yerusalem ba.
Yahweh ya ci gaba da magana game da Yerusalem kamar uwa ce da mazaunan Yerusalem kamar dai su sabbin yara ne (Ishaya 66: 7).
Wannan yana nufin Yerusalem za ta zama wurin aminci da kwanciyar hankali don mutanen Allah. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Gama za ta gamsar da ku da madararta; za ta ta'azantar da ku da nononta"
Wannan yana nufin Yerusalem za ta zama wurin aminci da kwanciyar hankali don mutanen Allah.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "za ta dauke ku a hannunta kuma ta yi maku durkusa da farin ciki"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "saboda haka zan ta'azantar da ku a Yerusalem"
"Ciyawar mai laushi" tana girma da sauri kuma tana kamantawa da lafiyar bayin Allah masu aminci.
Anan "hannu" yana nufin ikonsa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai bayyana ikonsa ga bayinsa"
Bayyanar Yahweh a Tsohon Alƙawari galibi ana tare da wuta wanda yake wakiltar fushin Yahweh da hukuncinsa.
Guguwa tana wakiltar ayyuka masu ƙarfi na Yahweh don hukuncinsa yayi tasiri.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai kashe mutane da yawa"
"Waɗannan" su ne waɗanda suke bauta wa Yahweh amma suka saɓa wa dokokinsa.
Wannan shine wurin da mutane zasu je bautar gumaka.
Wannan yana bayanin shugaban waɗanda suka tafi bautar gumaka.
Anan "I" yana nufin Yahweh.
Waɗannan su ne sunayen yankunan da suke nesa da ƙasar Isra'ila.
A nan "su" suna nufin baƙon da ya tsira kuma ya yi wa al'ummai shaida. Za su koma Yerusalem tare da Isra’ilawa da aka kai su bauta.
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ishaya 65:17.
Tsutsotsi suna wakiltar mummunan lalacewa da ruɓewa waɗanda hukuncin Yahweh ne akan miyagu.
Wuta ma tana wakiltar hukuncin Yahweh.
Ana iya bayyana wannan da kyau. AT: "zai ƙone har abada"
1Waɗannan su ne kalmomin Irmiya ɗan Hilkiya, ɗaya daga cikin firistocin Anatot cikin ƙasar Benyamin.2Maganar Yahweh ta zo gare shi a kwanakin Yosiya ɗan Amon, sarkin Yahuda, cikin shekara ta goma sha uku ta mulkinsa.3Ta kuma zo cikin kwanakin Yehoyakim ɗan Yosiya, sarkin Yahuda, har sai watan biyar na shekara goma sha ɗaya ta Zedekiya ɗan Yosiya, sarkin Yahuda, lokacin da aka kwashe mutanen Yerusalem a matsayin 'yan fursuna.4Maganar Yahweh tazo gare ni, cewa,5"Kafin In sifanta ka a cikin ciki, Na zaɓe ka; kafin ka fito daga cikin ciki Na keɓe ka; Na sa ka zama annabi ga al'ummai."6Sai na ce, "Ah, Ubangiji Yahweh!" Na ce, "Ni ban san yadda zan yi magana ba, gama ni yaro ne."7Amma Yahweh yace mani, "Kada ka ce 'Ni ƙaramin yaro ne.' Dole ka tafi duk inda Na aike ka, kuma ɗole ka faɗi duk abin da Na umarce ka!8Kada ka ji tsoron su, gama Ina tare da kai domin in cece ka - wannan furcin Yahweh ne."9Daga nan sai Yahweh ya miƙa hanunsa ya taɓa bakina, yace mani, "Yanzu, Nasa maganata a cikin bakinka.10Yau na sanya ka bisa kan al'ummai da kan mulkoki, ka tunɓuke ka kuma rushe, ka hallakar, ka kuma juyar, ka gina ka dasa."11Sai maganar Yahweh ta zo wurina, cewa, "Me ka gani, Irmiya?" Na ce, "Na ga reshen almond."12Yahweh yace mani, "Ka gani da kyau, gama ina kiyaye maganata domin in cika ta."13Maganar Yahweh ta sake zuwa wuri na karo na biyu, cewa, "Me ka gani? Na ce, "Na ga tukunya mai zafi, wadda fuskarta na ɓullowa, tana kaucewa daga arewa.14"Yahweh ya ce mani, "Bala'i zai fito daga arewa akan dukkan mazaunan ƙasar nan.15Gama ina kiran dukkan kabilun mulkokin arewa, inji Yahweh. Zasu zo, kowanne ɗayan su zai kafa kursiyin sa a ƙofofin shiga Yerusalem, gãba da dukkan ganuwar da ta kewaye ta, kuma gãba da dukkan biranen Yahuda.16Zan furta hukunci gãba da su domin dukkan muguntarsu cikin yãshe ni, ta wurin ƙona turare ga waɗansu alloli, cikin kuma yin sujada ga abubuwan da suka ƙera da hannuwansu.17Ka shirya kanka! Ka tashi ka faɗa masu duk abin da na umarce ka. Kada ka firgita a gaban su, ko in firgitar da kai a gabansu!18Duba! Yau, na maishe ka tsararren birni, ginshiƙin ƙarfe, da bangaye na tagulla gãba da dukkan ƙasar - gãba da sarakunan Yahuda, da hakimansu, firistocinsu, da mutanen ƙasar.19Zasu yi yaƙi gãba da kai, amma ba zasu yi nasara da kai ba, gama zan kasance tare da kai in cece ka - wannan furcin Yahweh ne."
Waɗannan sunayen mutane ne.
Wannan sunan wani gari ne.
Ana amfani da wannan karin magana ne don sanar da cewa Allah ya ba shi saƙonni. AT: "Yahweh ya ba shi saƙonni" ko "Yahweh ya yi magana da Irmiya"
Wannan sunan Allah ne wanda ya bayyana wa mutanensa a Tsohon Alƙawari. Duba translationWord shafi game da Yahweh game da yadda za a fassara wannan.
Ana amfani da wannan karin magana don gabatar da saƙo na musamman daga Allah. AT: "Yahweh ya ba ni saƙo. Ya ce" ko "Yahweh ya yi mini wannan saƙon"
Hakanan za'a iya bayyana wannan ba tare da nufin mahaifa ba. AT: "kafin a haife ku"
Yahweh yana magana kansa da sunansa don bayyana tabbacin abin da yake furtawa. AT: "wannan shi ne abin da Yahweh ya bayyana" ko "wannan shi ne abin da ni, Yahweh, na ayyana"
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) wannan kwatanci ne da ke wakiltar Yahweh yana ba Irmiya iko na musamman ya yi magana. AT: "Sai ya zama kamar Yahweh ya taɓa bakina" ko 2) Irmiya yana ganin wahayi kuma Yahweh ya yi wannan a zahiri don ba wa Irmiya ikon yin magana. AT: "Sai Yahweh ya taɓa bakina da hannunsa"
Zai tumbuke, ya ruguza, ya rusa ya hamɓarar da wasu al'ummomi, kuma zai gina ya dasa wasu ƙasashe.
Yahweh ya nuna wa Irmiya hangen nesa na ruhaniya.
Wannan yana nuna tabbacin cewa zai aikata abin da ya faɗa. AT: "Ina tuna maganata don aiwatar da ita" ko "Ina ba da tabbacin zan yi abin da na ce"
Ana amfani da wannan karin magana ne don sanar da cewa Allah ya ba shi saƙonni. AT: "Yahweh ya ba shi saƙonni" ko "Yahweh ya yi magana da Irmiya"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan yana wakiltar mulkin. AT: "zai yi mulki a ƙofofin Yerusalem" ko 2) wannan yana wakiltar yanke hukunci Yerusalem. AT: "zai yi hukunci a Yerusalem"
"Zan sanar da yadda zan hukunta su"
Anan "a ragargaje" yana wakiltar tsananin tsoro, kuma "farfasa" yana wakiltar sanya Irmiya firgita sosai. AT: "Kada ku firgita ... Zan firgita ku"
Wannan yana nufin mutanen Yahuda.
1Maganar Yahweh tazo gare ni, cewa,2"Kaje ka yi shela ga kunnuwan Yerusalem. Ka ce, 'Yahweh ya faɗi wannan: Na tuna a madadin ki da alƙawarin aminci cikin ƙuruciyarki, ƙaunarki a lokacin da muna tashe, lokacin da kika bi ni cikin jeji, ƙasar da ba'a taɓa shuka ba.3An keɓe Isra'ila ga Yahweh, nunan farin girbinsa! Dukkan waɗanda suka ci daga nunan farin sun ɗauki laifinsu; bala'i ya afko masu - wannan furcin Yahweh ne."'4Kuji maganar Yahweh, ya gidan Yakubu, dukkanku iyalin gidan Isra'ila.5Yahweh ya faɗi haka, "Wanne laifi ubanninku suka iske tare da ni, da suka yi nisa daga bi na? Da suka bi alloli marasa amfani su kansu kuma suka zama marasa amfani?6Basu ce, "Ina Yahweh, wanda ya fito da mu daga ƙasar Masar ba? Ina Yahweh, wanda ya bishe mu cikin jeji, zuwa cikin ƙasar Araba da ramummuka, a cikin ƙasar fari da duhu mai zurfi, ƙasa wadda ba wanda ke ratsawa ba kuma wanda yake zama ciki?'7Amma na kawo ku cikin ƙasar Kamel, domin ku ci 'ya'yan itatuwanta, da sauran abubuwa masu kyau! amma da kuka zo, kuka ƙazantar da ƙasata, kun maida abin gãdona ya zama abin ƙyama!8Firist bai ce, 'Ina Yahweh ba?' masanan shari'a kuma basu da mu da ni ba! Makiyaya sun yi mani laifi. Annabawa suka yi annabci domin Ba'al suka kuma bi al'amura marasa amfani.9Saboda haka har yanzu zan zarge ku - wannan furcin Yahweh ne - kuma zan zargi 'ya'yan 'yayanku.10Domin ƙetarewa zuwa gaɓar Kittim ku kuma duba. Ku aika da manzanni zuwa Kedar ku bincika ku gani ko an taɓa yin wani abu irin wannan.11Ko al'umma ta musanya allolinta, ko da shike su ba alloli ba ne? Amma mutane na sun musanya darajarsu da abin da ba zai taimakesu ba.12Ku girgiza, sammai, saboda wannan! ku yi rawar jiki ku kuma firgita - wannan furcin Yahweh ne.13Gama mutanena sun aikata mugayen abubuwa biyu gãba da ni: Sun yi watsi da maɓuɓɓugan ruwayen rai, sun gina wa kansu randuna, hudaddun randuna waɗanda ba zasu iya riƙe ruwa ba.14Ko Isra'ila bawa ne? An haife shi a gidan ubangidansa? To don me ya zama abin washewa?15'Yan zakuna sun yi masa ruri. Suna surutai da yawa sun kuma mai da ƙasarsu wurin tsoratarwa. An lalatar da biranensu ba sauran mazauna a ciki.16Kuma, mutanen Memfis da Tafanhes zasu aske ƙoƙon kanku.17Ba ku ne kuka yi wa kanku wannan ba lokacin da kuka yashe da Yahweh Allahnku, yayin da yake bishe ku a hanya?18Yanzu fa, me ya kai ku hanyar Masar kuka kuma sha ruwayen Shihor? Don me kuka bi hanyar zuwa Asiriya kuma kuka sha ruwayen kogin Yufiratis?19Muguntarku ta tsauta maku, rashin bangaskiyarku kuma ya hore ku. Don haka ku yi tunani akai, kuma ku fahimci cewa mugunta ce kuma da ɗaci idan kuka yashe da Yahweh Allahnku, kuma baku da tsoro na - wannan furcin Ubangiji Yahweh mai runduna ne.20Gama na karye karkiyar da kake da ita tun zamanin dã; na yanke sarƙƙoƙinka. Duk da haka ka ce, 'Ba zan yi bauta ba!' da shike ka russuna wa kowanne tudu mai tsawo da gindin kowanne itace mai ganye, kai mazinaci.21Na dasa ka a matsayin zaɓaɓɓen inabi, cikakke daga iri marar aibi. Amma ta yaya ka canza kan ka zuwa gurɓatacce, inabi marar amfani.22Gama ko da ka wanke kanka cikin kogi ko ka wanke da sabulu mai ƙarfi, zunubinka ya ɓata ka a gaba na - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.23Ta yaya zaka ce, 'Ban ƙazantu ba! Ban bi Ba'aloli ba?' Dubi abin da ka yi a cikin kwarurruka! Yi la'akari da abin da kayi, kai raƙumi ne mai gaggawar tafiya mai gudu nan da can,24jakar jeji wadda ta saba da zaman jeji, a cikin zuffarta tana numfasa iska! Wa zai tsai da sha'awarta? Babu daga cikin mazajen da ke buƙatar ya gajiyar da kansa wajen binta; a lokacin barbararsu zasu same ta.25Dole ka tsaida ƙafafunka daga zama marar takalmi kuma maƙogwaronka daga jin ƙishi! Amma ka ce, 'Ba bege! A'a, Ina ƙaunar bãƙi kuma zan bi su!'26Kamar yadda ɓarawo yake jin kunya idan an kama shi, haka gidan Isra'ila zai ji kunya - su, da sarakunansu, hakimansu, da firistocinsu da annabawa!27Waɗannan su suke cewa itace, 'Kai ubana ne,' ga dutse kuma, 'Kai ka haife ni.' Gama bayansu ke fuskanta ta ba fuskokinsu ba. Duk da haka a kwanakin matsaloli zasu ce 'Ka tashi ka cece mu!'28Duk da haka ina allolin da kuka yi wa kanku? Bari su tashi in sun ga dama su cece ku a lokacin damuwarku, gama yawan allolinku yawan biranenku, ya Yahuda!29To don me kuke zargi na a kan yi ba dai-dai ba? Dukkan ku kun yi mani zunubi - wannan furcin Yahweh ne.30A banza na hukunta mutanenku. Ba zasu karɓi horo ba. Takobinku ya cinye annabawanku kamar zaki mai hallakarwa!31Ku 'yan wannan tsara! Ku saurari maganata, maganar Yahweh! Na zama jeji ga Isra'ila? Ko ƙasa mai baƙin duhu? Don me mutanena zasu ce, 'Bari mu yi yawo mu zagaya, ba zamu ƙara zuwa wurin ka ba?'32Zai yiwu budurwa ta manta da kayan adonta na zinariya ko amarya da kayan lulluɓin ta? Duk da haka mutanena sun manta da ni kwanaki ba iyaka!33kin shirya hanyarki da kyau don ki nemi ƙauna. Kin koyar da halayenki ga mugayen mata.34A cikin tufafinki an iske jinin ran marasa laifi, mutane talakawa. Waɗannan mutane ba a same su cikin ayyukan sata ba.35Amma kin ce, 'Ni mara laifi ce; lallai fushinsa ya juya daga gare ni.' Amma duba! zan kawo hukunci a kan ki domin kin ce, 'Ban yi zunubi ba.'36Don me kike ɗauka da sauƙi haka batun canza hanyoyinki? Masar zata kunyatar da ke kamar yadda Asiriya ta yi maki.37Kema za ki fita daga can a wulaƙance, da hannayen ki a kanki, gama Yahweh ya ƙi waɗanda kika dogara gare su, don haka ba za ki sami taimako daga gare su ba."
"Je ka yi magana a inda mutanen Yerusalem za su ji ka"
"Na tuna da kai"
Allah yayi magana game da dangantakarsa da Isra'ilawa kamar sun ɗaura aure. AT: "lokacin da muka amince da farko cewa za mu auri juna"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ƙasar da babu wanda ya shuka iri" ko "ƙasar da ba abinci ya tsiro"
Yakubu da Isra'ila sunaye biyu ne na mutum ɗaya, kuma waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin rukuni ɗaya ne na mutane. AT: "dukkan ku zuriyar Yaƙubu"
Yahweh yana amfani da waɗannan tambayoyin don ya ce tunda bai yi laifi ba, bai kamata mutanensa su ƙi shi ba kuma su bauta wa gumaka. AT: "Ban yi wa kakanninku laifi ba, don haka bai kamata su yi nisa da bina ba, kuma bai kamata su bi gumaka marasa amfani ba. Yin hakan su da kansu sun zama marasa amfani!"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya. AT: "kun yi zunubi kuma kun sanya ƙasar da na ba ku abin ƙyama a gare ni!"
Wannan tambayar ta nuna cewa suna son yin biyayya ga Yahweh. AT: "Muna buƙatar yin biyayya ga Yahweh!"
Ana maganar shugabannin kamar suna makiyaya kuma mutanen da suka bi su tumaki ne. AT: "Shugabanninsu sun yi min laifi"
Anan "an bi" yana wakiltar biyayya ko sujada. AT: "yayi biyayya ga abubuwa marasa amfani" ko kuma "yi sujada ga abubuwa marasa amfani"
"al'ummominku masu zuwa"
Kittim tsibiri ne da ke yamma da Isra'ila. A yau ana kiran ta Cyprus. Tana wakiltar dukkan ƙasashe zuwa yamma da Isra’ila. AT: "tafi yamma zuwa hayin tekun zuwa Kittim"
Allah ya yi amfani da wannan tambayar ya gaya wa Isra'ilawa cewa sauran al'umman suna ci gaba da bautar gumakansu. Basu canzawa suna bautar wasu alloli. AT: "Za ku ga cewa babu wata al'umma da ta taɓa musanya gumaka ... alloli."
Allah yana maganar kansa kamar shi maɓuɓɓugan ruwan rai ne. AT: "sun watsar da ni, maɓuɓɓugansu na ruwan rai" ko "sun watsar da ni, wanda yake kamar maɓuɓɓugan ruwan rai"
Allah ya yi magana game da allolin ƙarya kamar dai su rami ne da mutane suke haƙa domin samun ruwa. AT: "sun tafi ga gumakan ƙarya, waɗanda suke kamar rijiyoyin da suka haƙa wa kansu"
Duk da cewa Yahweh yana magana da Isra'ilawa, ya yi amfani da mutum na uku kamar yana magana da wani game da Isra'ila. AT: "Isra'ila, kai bawa ne? An haife ku a gida? Don haka me ya sa kuka zama ganima?"
Rudani sauti ne mai karfi wanda dabbar daji ke yi idan ya kawo hari.
Masarawa suna aske kan bayinsu don yi musu alama a matsayin bayi.
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don tunatar da Isra'ila cewa laifin su ne cewa abokan gaba suka kawo musu hari. AT: "Kun jawo wa kanku wannan ne ta hanyar barin Ubangiji Allahnku yayin da yake jagorantarku a kan hanya."
Yahweh yana amfani da waɗannan tambayoyin don tunatar da mutanensa cewa babu wani amfani da zai roƙi Masar da Asiriya su taimake su. AT: "Ba zai taimake ka ba ka je Masar ka sha daga ruwan Kogin Shihor, ko ka je Asiriya ka sha daga ruwan Kogin Yufiretis."
Duk waɗannan jimlolin suna nufin cewa hukuncinsu sakamakon mummunan halayensu ne. AT: "Saboda kun kasance mugaye kuma marasa aminci, zan hore ku"
Anan "karya karkiyarku" ť kuma "yage muku ƙugiyoyinku" ť misalai ne don 'yantar da su daga bautar. Jama'ar Isra'ila suka zama bayi a ƙasar Masar. AT: "Tun da daɗewa na sake ku daga bauta, amma har yanzu kun ƙi bauta mini!"
Abin da suka durƙusa za a iya bayyana shi a sarari. Anan "mazinaci" a misalai ne ga wanda yaci amanar Allah. AT: "Kun rusuna wa gumaka kuna bauta musu a maimakon ni, kamar matar da take yin zina da ba ta da aminci ga mijinta"
Allah yayi magana akan sanya mutanensa su zama babbar al'umma a cikin Kan'ana kamar dai su zuriyar innabi ne wanda ya shuka. AT: "Ni, Yahweh, na fara ku da kyakkyawar farawa, kamar manomin da ke amfani da kyakkyawan iri don shuka mafi kyau irin itacen inabi"
Allah yayi magana game da Isra’ila tana bautar waɗansu alloli kamar suna kamar rakumi na mata waɗanda ke gudu zuwa wurare daban-daban suna neman raƙumi ɗa da za su aura. AT: "Kun kasance kamar raƙumar mace mai saurin gudu da gaba tana neman raƙumi ɗa wanda zai aura tare da shi"
Allah ya yi magana game da Isra'ilawa suna bautar gumaka kamar suna jakin jeji na daji da ke gudu don neman jakuna maza. AT: "Kuna kamar yarinya ce ta jaki da ke zaune a jeji. Lokacin da take son yin aure sai ta zama ba ta da iko kuma tana yawan shan iska don neman abokin aure"
Allah yayi magana game da Isra'ila suna son su bauta wa waɗansu alloli kamar suna gudu a cikin hamada suna neman waɗancan allolin. AT: "Na gaya muku ku daina gudu nan da can kuna bin gumakan ƙarya, domin duk abin da yake yi shi ne takalmanku sun tsufa kuma sun sa ku ƙishirwa ƙwarai"
Wannan karin magana yana nufin wani ya gano cewa abin da mutumin ya yi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da wani ya same shi" ko "lokacin da mutane suka san cewa ya saci abubuwa"
Anan "itace" da "dutse" suna wakiltar gumakan da aka sassaka daga itace da dutse. Waɗannan kalmomin suna ƙarfafa cewa gunkin an yi shi da abubuwa na yau da kullun kuma bai cancanci a bauta masa ba. AT: "Waɗannan mutane su ne waɗanda suke ce wa katako, "Kai ne mahaifina," da kuma ga dutse da aka sassaka, "Kai haife ni."
"Bayayyakinsu suna wajena; fuskokinsu ba sa wurina." Wannan yana nuna musu suna kin Allah. AT: "sun juya daga wurina" ť ko "sun juya mini baya ba fuskokinsu ba" ko "sun ƙi ni gaba ɗaya"
Maganar "wannan tsara" tana nufin mutanen da suka rayu lokacin Irmiya. AT: "Ku da ke raye a yau, ku mai da hankali ga abin da Ni, Yahweh, na ce muku"
Anan "jeji" ť da "ƙasa mai duhu" "misalai ne don haɗari. Allah yayi amfani da wannan tambayar don tsawata wa Isra'ilawa saboda aikatawa kamar yana da haɗari. AT: "Kuna yi kamar na kasance kamar jeji ko ƙasa mai duhu a gare ku"
Allah yayi amfani da wannan tambayar don gabatar da tunanin tuna abubuwan da suke da mahimmanci ga wani. AT: "Kun san cewa budurwa ba za ta taɓa mantawa da sanya kayan adon ta ba, kuma amarya ba za ta taɓa mantawa da sanya mayafin ta ba."
Allah yana maganar rashin mutuncin mutanensa kamar suna koyawa karuwai yadda zasu zama marasa aminci ga mazajensu kuma su sami wasu mazan su zama masoyansu.
Idan sun sami mutane cikin aikata laifin sata, wannan na iya zama uzuri don kashe su. Amma mutanen da suka kashe ba su da laifi. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba ku gano waɗannan mutane suna satar abubuwa ba" ko "Amma kun kashe su duk da cewa ba sa ma satar komai"
Anan ana magana da fushi kamar mutum ne wanda zai iya juya baya ga Isra'ila. Juyawarsa yana wakiltar dakatarwar Yahweh yana fushi da Isra'ila. AT: "tabbas Yahweh ya daina yin fushi da ni"
Yahweh yana tsawata wa Isra'ilawa saboda sun canza daga wata masarauta zuwa wata don taimako amma ba su dogara ga Allah don taimako ba.
"Za ku fita daga Masar"
1"Idan mutum ya saki matarsa, ta fita daga wurinsa ta kuma zama matar wani, zai sake komawa wurinta kuma? Ƙasar ba zata ƙazantu ba gaba ɗaya? Kin zama kamar karuwa mai masoya da yawa; yanzu kuma kina so ki sake dawowa wurina? - wannan furcin Yahweh ne.2Ki ɗaga idanun ki sama ki duba tsaunuka! ko akwai wurin da ba kiyi lalata ba? A bakin hanya kin zauna kina jiran masoyanki, kamar Balarabe cikin jeji. Kin ƙazantar da ƙasar da karuwancinki da kuma mugunta.3Don haka an hana ruwan bazara ruwan kaka kuma bai zo ba. Amma fuskar ki akwai girmankai, kamar fuskar karuwa. Ba ki jin kunya.4Ba yanzu kika kira gare ni ba: 'Ubana! Abokina na kurkusa tun daga ƙuruciyata!5Koyaushe zai yi ta fushi? Kullum zai riƙe fushinsa har ƙarshe?' Duba! Wannan shi ne abin da kika ce, amma kin yi dukkan muguntar da kika iya yi!"6A kwanakin sarki Yosiya sai Yahweh ya ce mani, "Ka ga abin da Isra'ila marar amana ta aikata? Ta hau bisa kan kowanne tudu mai tsawo ƙarƙashin kowanne itace mai ganyaye, a can ta zama kamar karuwa.7Na ce, 'Bayan ta yi dukkan waɗannan al'amura, zata koma wurina,' amma bata komo ba. Daga nan sai 'yar uwarta mai cin amana Yahuda ta ga waɗannan abubuwa.8Sai na ga haka, Isra'ila maci amana ta aikata zina na kore ta na bata takardar kisan aure, 'yar uawrta maci amana Yahuda bata ji tsoro ba; ita ma ta fita ta aikata kamar karuwa.9Karuwancinta ba wani abu ba ne a gare ta; ta ƙazantar da ƙasa, ta kuma aikata zina da duwatsu da itatuwa.10Daga nan bayan dukkan waɗannan, 'yaruwarta maci amana Yahuda ta komo wurina, amma ba da dukkan zuciyarta ba, amma da ƙarya - wannan furcin Yahweh ne."11Daga nan sai Yahweh ya ce mani, "Adalcin Isra'ila ya fi na Yahuda maci amana!12Ka je kayi shelar waɗannan maganganu zuwa ga arewa. 'Ki dawo, ya Isra'ila mai cin amana! - wannan furcin Yahweh ne - ba kulluyaumin zan yi fushi da ke ba. Tun da ni mai aminci ne-wannan furcin Yahweh ne - ba zan zauna cikin fushi ba har abada.13Ki yarda da zunubinki, gama kin aikata laifuffuka gãba da Yahweh Allahnku; kin raba hanyoyin ki da bãƙi ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa! Gama baki saurari muryata ba! - wannan furcin Yahweh ne.14Ku juyo, mutane maciya amana! - wannan furcin Yahweh ne - mijinki ne! zan ɗauke ki, ɗaya daga cikin birni, biyu daga cikin iyali, zan kawo ki Sihiyona!15Zan baku makiyaya gwargwadon zuciyata, kuma zasu yi kiwon ku da sani da fahimta.16Sa'annan zai kasance a sa'ad da zaku riɓanɓanya ku bada 'ya'ya a waɗannan kwanaki - wannan furcin Yahweh ne - daga nan ba zasu ƙara cewa, "Sanduƙin akwatin alƙawari na Yahweh ba!" Wannan al'amarin ba zai ƙara zuwa cikin zuciyarsu ba, gama ba zasu ƙara tunawa ko su yi kewarsa ba. Kuma ba za a ƙara yin wani ba.'17A lokacin nan za su yi shela game da Yerusalem, 'Wannan shi ne kursiyin Yahweh,' daga nan sauran al'ummai za su taru a Yerusalem a cikin sunan Yahweh. Ba za su ƙara yin tafiya cikin taurin kai da muguntar zuciyar su ba.18Cikin kwanakin nan, gidan Yahuda zai yi tafiya da gidan Isra'ila. Tare za su zo daga kasar arewa zuwa ƙasa wadda na ba kakannin ku a matsayin gãdo.19Amma ni, Nace, Yadda nake so in girmamaku a matsayin ɗa in baku ƙasa mai daɗi abin gãdo wanda ya fi kyau fiye da wanda ke cikin sauran al'ummai!' Da sai in ce, 'Zaku kira ni "baba na". 'Ba zaku juya daga bina ba.20Amma kamar mace mai cin amanar mijinta, kun yashe ni, ku gidan Isra'ila - wannan furcin Yahweh ne."21An ji murya bisan filaye, kuka da godon mutanen Isra'ila! Gama sun canza hanyoyinsu; sun manta da Yahweh Allahnsu,22"Ku juyo, ku mutane maciya amana! Zan warkar da yaudarar ku!" Duba!! Zamu zo wurin ka, gama kai ne Yahweh Allahnmu!23Hakika ƙarairayi sun zo daga tuddai, muryoyi masu ruɗar wa daga duwatsu; hakika Yahweh Allahnmu shi ne ceton Isra'ila.24Duk da haka gumaka abin kunya sun cinye abin da kakanninmu suka yi wahalarsa - garkunansu na shanu da na awaki, 'ya'yansu maza da mata!25Bari mu kwanta cikin kunya. Bari kunyar mu ta rufe mu, gama mun yi zunubi ga Yahweh Allahnmu! Mu da kakanninmu, tun daga lokacin ƙuruciyar mu har zuwa yau, bamu saurara ga muryar Yahweh Allahnmu ba!"
Allah ya yi amfani da wannan tambayar don ya tunatar da mutane cewa mai aure ba zai koma wurin matarsa ba idan ta auri wani, domin ya san cewa ƙasar za ta zama ƙazamta. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Ya san cewa idan ya yi hakan, ƙasar za ta ƙazantu sosai."
Allah yayi amfani da wannan tambayar domin tunatar da mutane cewa mutum ba zai taba komawa ga matarsa ba idan wani mutum ya aure ta. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "ba zai sake dawowa gare ta ba."
Anan "idanunku" suna wakiltar kallon wani abu. AT: "Duba sama"
Girman kai da ke bayyana a fuskar mutum ana maganarsa kamar fuska ita kanta tana da girman kai. AT: "Amma yanayin fuskarka yana nuna cewa kai mai girman kai ne, kamar fuskar karuwanci"
Ana magana da mutanen Isra’ila kamar Isra’ila mace ce. AT: "Mutanen Isra'ila sun hau" ko "Sun hau"
Kan duwatsu da ƙarƙashin bishiyoyi masu inuwa wurare ne da mutane ke bautar gumaka. An yi amfani da kalmar "kowane" as a matsayin gama gari don nuna cewa mutane suna bautar gumaka a wurare daban-daban.
Anan karuwanci ba "komai bane" yana wakiltar Yahuda da ba ruwanta dashi. AT: "Ba ta damu da karuwancinta ba" ko "Ba ta jin kunyar karuwancinta"
Yahweh yana magana kansa da sunansa don bayyana tabbacin abin da yake furtawa. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Irmiya 1: 8. AT: "wannan shi ne abin da Yahweh ya bayyana" ko "wannan shi ne abin da ni, Yahweh, na ayyana"
Anan “zuciya” tana wakiltar muradin Yahweh ko kuma nufinsa. Kalmomin "bayan zuciyata" salon magana ne wanda ke bayyana mutanen da suke yin nufin Allah. AT: "makiyaya masu aikata abin da na ga dama" ko "makiyaya masu aikata abin da nake so"
Kalmar "ku" tana nufin mutanen Isra'ila. Jumlar "bada 'ya'ya" karin magana ce don samun zuriya da yawa. AT: "zaku karu da yawa a lamba"
Anan "yi tafiya tare" yana wakiltar kasancewa ɗaya. AT: "mutanen Yahuda za su haɗu da mutanen Isra'ila"
kalmar "ni" tana nufin Yahweh
Wannan kirari ne wanda yake bayyana nufin Allah. AT: "Ina so da yawa in dauke ku a matsayin ɗana ... al'umma"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane suna jin amo"
"mutanen Isra'ila suna kuka da roƙo da ƙarfi"
Anan "tuddai" na wakiltar bautar gumakan mutane akan tsaunuka. Mutanen yanzu sun fahimci cewa waɗannan allolin ƙarya ba za su iya yi musu ja-gora ba kuma su taimake su. AT: "Allolin ƙarya da muke bautawa a kan tsaunika ba za su iya mana jagora ba"
Waɗannan jumlolin suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa mutane suna sane da halayen rashin kunya. AT: "Bari mu wulakanta gaba daya"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "lokacin samartakanmu" yana nufin lokacin da kowane mutum yake saurayi. AT: "daga lokacin da muke ƙuruciya" ko 2) "lokacin ƙuruciyarmu" na nuna da ke nuni da lokacin da Isra'ila ta fara zama al'umma. AT: "daga lokacin da muke fara zama al'umma"
1Idan kuka juyo, Isra'ila - wannan furcin Yahweh ne - zai zama gare ni zaku juyo. Idan kuka kawar da ƙazantattun abubuwa daga gabana kuma baku ƙara bari na ba,2Dole ku zama da gaskiya, marasa aibi, da masu adalci lokacin da kuke rantsuwa, 'Da ran Yahweh.' Sa'annan ne al'ummai za su albarkaci kansu a cikinsa, kuma a cikinsa zasu yi ɗaukaka."3Gama Yahweh ya faɗi haka ga kowanne mutum da ke cikin Yahuda da Yerusalem: 'Ku yi huɗar ƙasarku, kada kuma ku yi shuka cikin ƙayayuwa.4Kuyi wa kanku kaciya ga Yahweh, ku cire loɓar zuciyarku, mazajen Yahuda da mazaunan Yerusalem, in ba haka ba fushina zai fita kamar wuta, ya ƙone har ba wanda zai kashe shi, saboda muguntar ayyukanku.5Ka sanar cikin Yahuda, bari a ji a Yerusalem. Ka ce, "A busa ƙaho cikin ƙasar." Ayi shela a ce, "Mu taru. Bari mu shiga zuwa birane masu kagara."6A ɗaga alamar tuta kuma ta fuskanci wajen Sihiyona, ku gudu don ku tsira! kada ku tsaya, gama zan kawo bala'i daga arewa da babbar faɗuwa.7Zaki yana zuwa daga cikin kurminsa wani kuma wanda zai hallakar da al'ummai yana shirin fita. Zai bar wurinsa ya kawo tsoratarwa a ƙasarku, zai mai da biranenku su zama kangaye, inda ba mai zama ciki.8Saboda haka, ku yi ɗammara da tsummoki, ku yi makoki kuna kururuwa. Gama ƙarfin fushin Yahweh bai juya daga gare mu ba.9Zai zama kuma a ranar nan - wannan furcin Yahweh ne. a ranar nan, zuciyar sarki da hakimansa zata mutu. Firistoci zasu tsorata annabawa kuma zasu razana."10Sai nace, "Ah! Ubangiji Yahweh. Lallai ka ruɗi waɗannan mutane da Yerusalem ta wurin cewa, 'Zaku sami salama.' Duk da haka takobi tana sara gãba da ransu."11A wannan lokaci za'a ce da waɗannan mutane da Yerusalem, "Iska mai ƙuna daga wajen filayen hamada, zata yi wajen ɗiyar mutanena. Ba zata sheƙe ba ko kuwa ta tsarkake su.12Iska da ta fi wannan ƙarfi zata zo bisa ga umarni na, yanzu kuma zan furta shari'a a kansu.13Duba, yana kai hari kamar giza-gizai, karusansa kuma suna kamar hadari. Dawakansa sunfi gaggafa sauri. Kaiton mu, gama zamu zama hallakakku!14Ki wanke zuciyar ki daga mugunta ya Yerusalem, domin ki tsira. Har yaushe zuzzurfan tunaninki zai kasance yadda za a yi zunubi?15Gama murya na kawo labari daga Dan, an ji zuwan masifa daga tuddan Ifraim.16Kasa al'ummai su yi tunani akan wannan: Duba, ka sanar da Yerusalem cewa magewaya suna zuwa daga ƙasa mai nisa su tada muryar yaƙi akan biranen Yahuda.17Zasu zama kamar masu tsaron nomammiyar gona gãba da ita kewaye, domin tayi mani tayaswa wannan shi nefurcin Yahweh -18halinki da ayyukanki ne suka yi maki waɗannan abubuwa. Wannan zai zama hukuncinki. Zai zama da muni! Zai buga har zuciyarki.19Ya zuciyata! Zuciyata! Ina cikin baƙin ciki a zuciyata, zuciyata tana binbini a cikina. Ba zan iya yin shiru ba, gama na ji ƙarar ƙaho, gangamin yaƙi.20Bala'i na bin bala'i; gama dukkan ƙasar ta zama kango. Farat ɗaya rumfunana an hallaka su, labulena kuwa nan da nan.21Har yaushe zan ga tutar? Zan ji ƙarar ƙaho?22Saboda wautar mutanena - basu sanni ba. Mutane ne masu halin wauta basu da fahimta. Masu azanci ne wajen mugunta, amma basu da sanin yin abu mai kyau.23Na duba ƙasar. Duba! ta zama wofi da fanko. Gama babu haske domin sammai.24Na duba duwatsu. Duba, suna rawar jiki dukkan tsaunuka suna girgiza.25Na duba. Duba, babu ko ɗaya, kuma dukkan tsuntsayen sammai sun gudu.26Na duba. Duba, fadamun sun zama jeji dukkan biranenta sun rurrushe a gaban Yahweh, da zafin fushinsa."27Ga abin da Yahweh yace, "Dukkan ƙasar zata zama kango, amma ba zan hallakar da ita dungum ba.28Saboda wannan dalili, ƙasar zata yi makoki, sammai daga bisa kuma zasu duhunta. Gama na sanar da manufofi na; ba zan sake nufi na ba; ba kuwa zan juya ga barinsa ba.29Kowanne birni zai gudu daga ƙarar mahayan dawakai da maharba; zasu ruga cikin kurmi. Kowanne birni zai hau sama cikin wurare masu duwatsu. Za a bar biranen, ba za a sami wanda zai zauna cikinsu ba.30Yanzu da kika zama kango, me za ki yi? Ko da kike sa tufafi na mulufi, kike ado da kayan zinariya, kina sa idanunki su zama manya saboda shafe shafe, mazan da suka yi sha'awar ki yanzu sun yashe ki. Maimakon haka, suna ƙoƙarin ɗaukar ranki.31Na ji sautin baƙin ciki, wahala kamar a lokacin haihuwar ɗan fari, sautin muryar ɗiyar Sihiyona. Tana haki. Ta baza hannayenta, ta ce, 'Kaitona! Ina suma saboda waɗannan masu kisan kai."
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan umarni ne da ke jaddada wanda ya kamata su koma zuwa gare shi. AT: "sa'annan ku dawo wurina" ko "to ku bauta min" 2) wannan maimaita magana ce ta farko, wacce ke bayyana wani yanayi. AT: "idan za ku dawo wurina" ko "idan za ku sake fara yi mini sujada"
Anan "abubuwan banƙyama" na nufin gumaka, waɗanda Allah ya ƙi. AT: "Idan kuka cire gumakanku masu banƙyama daga gabana"
Anan "yawo" a misalai ne na rashin aminci. AT: "idan kun kasance masu aminci a gare ni"
Yahweh ya gaya wa mutane su shirya rayuwarsu kamar yadda manomi ke shirya ƙasa don shuka.
Yahweh ya bayyana mutane a gare shi ta fuskar alamar alkawari ta zahiri. AT: "Ku keɓe kanku gaba ɗaya ga Yahweh"
Yahweh yayi maganar yin fushi ƙwarai kamar fushin sa wuta. AT: "fushina zai yi ƙuna kamar wuta kuma ba wanda zai iya dakatar da shi" ko "Zan yi fushi ƙwarai, kuma babu wanda zai iya dakatar da ni"
Waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya dai-dai. Tare suna jaddada umarnin.
Allah yayi maganar runduna mai ƙarfi kamar zaki mai ƙarfi. AT: "Wata rundunar mayaƙa mai ƙarfi da rashin tausayi ta gabato"
Wannan karin magana yana nufin fara motsi. AT: "yana fara tafiya"
Anan makiya ana shirye su kashe mutane ana maganarsu kamar takobi mutum ne wanda yake kashe mutane. AT: "makiyanmu a shirye suke su yanka mu da takubbansu"
Anan "iska mai ƙuna" tana wakiltar maƙiyi mai tsananin tsoro da rashin tausayi.
Kalmomin "sheƙe" da "tsarkakewa" na nuni ga busa fata marasa amfani daga hatsi. Iska kawai ake buƙata don hakan. AT: "Ba zai zama iska mai sauƙi ba don hura ƙaiƙayi daga hatsi"
"ku sanar da hukuncinsu"
"Wannan mummunan abu ne". Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "don zasu lalata mu" ko "don zasu hallaka mu duka"
Wannan gargaɗi ne ga mutanen da ke zaune a Yerusalem su tuba. "Tsabtace zuciyar ka" na nuna ta cire sharri daga rayuwarsu. AT: "Mutanen Yerusalem, ku daina yin mugunta" ko "Mutanen Yerusalem, ku daina yin mugunta"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane suna jin labarin bala'in da ke zuwa daga Ifraimu"
A hankali a tsare birni don hana mutane shiga da fita ana magana kamar suna kula da hankali don hana mutane sata daga gare ta. AT: "za su kiyaye Yerusalem a hankali kamar masu tsaro waɗanda ke kiyaye gonar da ta dace"
Anan "zuciya" mai yiwuwa tana nufin motsin rai, kuma "buge zuciyar ka sosai" - mai yiwuwa yana nufin haddasa musu wahala mai tsanani. AT: "Zai zama kamar ya bugi zuciyar ku" ko "Zai sa ku wahala mai ban tsoro"
"Zuciyata tana bugawa da karfi." Anan "zuciya" tana nufin sashin jiki. Yana da rikici saboda yana bugawa da ƙarfi da sauri fiye da al'ada.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Abokan gaba sun lalata tantina ba zato ba tsammani"
Kalmomin "sun lalace" ana fahimtar su daga jumlar da ta gabata. AT: "rumfunana sun lalace nan da wani lokaci"
Irmiya ya yi amfani da waɗannan tambayoyin don ya nuna damuwarsa game da ganin tutar yaƙi da kuma jin ƙarar ƙaho na dogon lokaci. Yana fatan cewa yakin zai ƙare ba da daɗewa ba. Ana iya bayyana shi azaman tsawa. AT: "Oh, yaya zan yi fatan cewa yaƙin ya ƙare, kuma a saukar da tuta, kuma sautin ƙahon sojoji ya tsaya"
Kalmar "duba" a nan tana faɗakar da mu da mu kula da bayanan ban mamaki da suka biyo baya.
Wannan wahayin annabci ne game da yadda ƙasar Isra’ila za ta kasance bayan an ɗauke mutanen duka zuwa bauta.
"Duk ƙasar Yahuda za ta kasance kufai" ko "duk ƙasar Yahuza za ta zama kango"
Anan "birni" yana wakiltar mutanen da ke zaune a cikin birni.
Waɗannan jimloli guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya. Na biyu yana karfafa tunani a farkon. AT: "Garuruwan za su kasance fanko. Ba wanda zai rage ya zauna a cikinsu"
Allah ya yi magana game da al'umman da Yahuda ta dogara da su don wadata da kasuwanci kamar su maza ne da suka yi sha'awar Yahuda. Waɗannan al'umman za su ƙi Yahuda lokacin da suka ga hukuncin Allah.
An yi amfani da wannan misalin don nuna yadda Yahuda za ta kasance cikin baƙin ciki ƙwarai. AT: "damuwa mai tsanani kamar zafi da wahalar da mace take sha yayin haihuwa"
1"Yi gudu ta titunan Yerusalem; yi bincike cikin dandalin birninta, kuma. Daga nan ka duba kayi tunani akan wannan: Ko za a sami mutum ɗaya ko akwai wanda ya ke aikata adalci yana ƙoƙarin aikata aminci, daga nan zan yafewa Yerusalem.2Kodashike suna cewa, 'Mun rantse da ran Yahweh,' duk da haka suna rantsuwa kan ƙarya."3Yahweh, idanunka ba aminci suke kallo ba? Ka bugi mutanen, duk da haka basu ji zafi ba, ka hallaka su gaba ɗaya, amma duk da haka sunƙi kaɓar horo. Sun sa fuskokinsu sun taurare fiye da dutse, gama sun ƙi tuba.4Sa'annan nace, "Hakika waɗannan mutane talakawa ne. Su wawaye ne, gama basu san tafarkun Yahweh ba, ko umarnan Allahnsu ba.5Zan tafi wurin muhimman mutane domin in sanar da saƙonnin Allah gare su. Gama sun san hanyoyin Yahweh, da umarnan Allahnsu." Amma dukkan su sun karya karkiyarsu tare, sun tsintsinke sarƙoƙin da suka ɗaure su ga Allah.6Domin wannan zaki daga cikin kurmi zai kai masu hari. Kyarkeci daga Araba zai lalata su. Damisa za ta zo gãba da biranensu. Duk wanda ya fita daga cikin birninsa za a yayyage shi. Gama laifofinsu sun ƙaru. Ayyukan rashin amincinsu kuwa basu da iyaka.7Don me zan gafarta wa waɗannan mutane? 'Ya'yansu sun yashe ni kuma sunyi rantsuwa ga waɗanda ba alloli ba ne. Na ciyar dasu sun ƙoshi, amma sun aikata zina, sun riƙa tafiya suna cincirindo zuwa gidajen karuwai.8Dawakai ne su cikin zafi. Suna yawo suna jira a haɗu, kowanne mutum yana neman matar maƙwabcinsa.9Don haka ba zan hukunta su ba? - wannan furcin Yahweh ne - kuma ba zan ɗaukar wa kai na fansa a kan irin wannan al'ummar ba?10Ku hau sama gun garkunan inabinta ku gano ku hallaka. Amma kada ku hallakar da ita duka. Ku gyara inabinsu, gama waɗannan inabin ba daga Yahweh suke ba.11Gama gidajen Isra'ila dana Yahuda sun bashe ni gaba ɗaya - wannan furcin Yahweh ne.12Sun faɗi ƙarya game da Yahweh kuma suka ce, "Ba zai yi kome ba; ba wata cuta da zata zo kanmu, ba kuwa zamu ga takobi ko yunwa ba.13Annabawa zasu zama iska, maganar bata cikin su, bari duk abin da suka faɗi ayi masu."14Yahweh, Allah mai runduna ya faɗi wannan, "Saboda ka faɗi haka, duba, duba zansa maganata cikin bakinka. Zata zama kamar wuta, mutanen nan kuma zasu zama kamar itace! Gama zata cinyesu.15Duba!! zan kawo wata al'umma daga nesa, ya gidan Isra'ila - wannan furcin Yahweh ne - al'ummace wadda ta wanzu, kuma daɗaɗɗiyar al'umma! Al'umma ce wadda baka san yaren su ba, ba kuwa zaka fahimci abin da suke faɗi ba.16Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari ne. Dukkansu sojoji ne.17Zasu cinye amfanin da ka girbe, haka 'ya'yanka maza da mata, da abincinka. Zasu cinye garken tumakinku da na awaki da kuma garken shanunku; zasu cinye kuringar anab naka dana ɓaure. Zasu rurrushe biranenka masu ganuwa da takobi waɗanda ka dogara gare su.18Amma ko a cikin waɗancan kwanaki - wannan furcin Yahweh ne - bani da nufin in hallakar da ku baki ɗaya.19Zai faru idan ku, Isra'ila da Yahuda, kun ce, 'Don me Yahweh Allahnmu ya yi mana dukkan waɗannan abubuwa?' Sai kai, Irmiya, kace masu, 'Kamar yadda kuka yashe da Yahweh kuka yi sujada ga baƙin alloli a cikin ƙasarku, haka kuma dole ku bauta wa baƙi a cikin ƙasar da ba taku bace.20Ka sanar da wannan a gidan Yakubu bari a ji a gidan Yahuda. Kace,21'Ku ji wannan ku wawayen mutane waɗanda basu da fahimta; kuna da idanu amma baku gani, kuna da kunnuwa amma ba ku ji.22Baku ji tsoro na ba - wannan furcin Yahweh ne - ko kuyi rawar jiki a fuskata ba? Na sa yashi ya zama iyakar teku, bisa madauwamin umarni wanda ba zai ƙetare ba - koda shike teku yana tashi ya na faɗuwa, duk da haka bai karya shi ba, ko da sun yi ruri ba zasu ƙetare ba.23Amma waɗannan mutane suna da kangararriyar zuciya. Sun yi tayarwa sun tafi abinsu.24Gama a cikin zuciyarsu ba su ce, "Bari mu ji tsoron Yahweh Allahnmu, wanda yake bada ruwa na farko da na ƙarshe a lokacinsu ba, ya ke tabbatar mana da makonnin girbl." Laifofinku sun hana waɗannan faruwa.25Zunubanku sun hana abubuwa masu kyau su zo gare ku.26Gama an sami miyagun mutane tare da mutanena. Suna fako kamar yadda wani ke laɓewa ya kama tsuntsaye; suna ɗana tarko su kama mutane.27Kamar yadda keji yake cike da tsuntsaye, haka gidajensu suke cike da ha'inci da ruɗi. Don haka sun yaɗu sun zama masu arzaki.28Sun yi ƙiba; suna ƙyalli da lafiyarsu. Suna keta haddin kowacce mugunta. Basu sauraron roƙon mutane ko dalilin marayu. Sun azurta duk da ba sa nuna adalci ga masu bukata.29Bazan hukunta su saboda waɗannan abubuwa ba - wannan furcin Yahweh ne - kuma ba zan ɗaukar wa kaina fansa a kan al'umma irin wannan ba?30Abubuwan banƙyama da tsoratarwa sun faru a cikin ƙasar.31Annabawa suna anabci da ha'inci, firistoci suna mulki da ikonsu. Mutanena kuma suna son haka, amma me zai faru a ƙarshe?"'
"duba ka bincika"
"wa ke yin abin da ke dai-dai"
Irmiya ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa abin da Yahweh yake so shi ne aminci. Son mutane su zama masu aminci ana magana akan neman aminci. AT: "kuna neman aminci." ko "kuna son mutane su zama masu aminci."
Allah ya azabtar da mutanensa ta hanyoyi daban-daban. A nan ana magana ne kamar dai ya buge su. AT: "Kuna azabtar da mutane, amma ba su kula"
Irmiya yana magana.
Karkiyar da sarƙoƙi suna wakiltar dokar da ke ɗaure Allah da mutanensa.
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa bashi da dalilin gafartawa waɗannan mutanen. AT: "Saboda abubuwan da suke yi, ba zan iya gafartawa waɗannan mutane ba."
Wannan na iya zama kwatanci na rashin aminci ga Allah da kuma bautar gumaka, amma bautar gumaka har da karuwanci. AT: "sun kasance marasa aminci a gare ni kuma sun tafi da yawa zuwa gidajen karuwai"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa abubuwan da suke yi suna da muni ƙwarai da gaske cewa ba zai sami jinƙai ba amma zai hukunta su. AT: "Saboda suna yin waɗannan abubuwan, zan hukunta su ... lallai zan rama wa kaina a kansu."
A cikin ayoyi 10-13 Yahweh yayi magana da magabtan Isra’ila. Ana iya bayyana wannan a cikin zance. AT: "Ku makiya Isra'ila, ku hau kan gonakinta na inabi" farfajiyoyi "
"kar ku hallaka su gaba daya"
Karin magana "ka fado mana" na nufin "ka same mu." AT: "Babu wata cuta da za ta same mu" ko "babu wanda zai cutar da mu"
Anan "gani" kwatanci ne na ƙwarewa, kuma "takobi" alama ce ta yaƙi. AT: "ba za mu fuskanci yaƙi ko yunwa ba"
Anan “sanya maganata a bakinku” yana wakiltar sa Irmiya ya yi maganar saƙon Allah. AT: "Zan sa ku faɗi sakona"
"Domin sakona zai cinye su." Sakon Yahweh game da yadda zai hukunta mutanensa, saboda haka yana magana kamar saƙonsa zai hallaka su kamar yadda wuta take lalata itace. AT: "Gama lokacin da kuka faɗi sakona, zai hallaka mutanen Isra'ila kamar yadda wuta ke lalata itace"
Waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya kuma suna jaddada tsawon lokacin da ƙasar ta kasance. Wannan yana magana ne game da al'ummar da Yahweh zai kawo wa Isra'ilawa daga nesa. AT: "tsohuwar al'umma ce kuma mai dawwama"
Waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa Isra'ilawa ba su san yaren waɗannan mutanen ba. Yana iya nufin cewa Isra'ilawa ba su da dangantaka da su sosai. AT: "Al'umma ce wacce ba zaku iya fahimtar yarenta kwata-kwata ba"
Kabarin da aka bude shine wanda aka shirya don sanya gawawwaki da yawa a ciki. Sojojin makiya za su kashe mutane da yawa. AT: "Sojojin wannan ƙasar za su yi amfani da kibiyoyinsu su kashe mutane da yawa" ko "Saboda kibiyoyin dakarunta, mutane da yawa za su mutu kuma a binne su"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Don haka sojojin wannan al'ummar za su ci abincin da kuke tsammanin girbi"
Takobin takamaiman abin da mutane ke amfani da shi wajen yaƙi. AT: "Za su yi amfani da makamansu don cinye garuruwanku masu ƙarfi waɗanda kuka amince da su don su tsare ku"
"ba zai halakar ba"
Maganar "waɗannan abubuwa" tana nufin aika runduna don kai musu hari. AT: "anyi duk waɗannan abubuwa don cutar damu" ko "aika sojojin ƙasashen waje don su kawo mana hari"
"Fada wannan"
Anan "ba zai iya gani ba" yana da metonym don rashin fahimta. AT: "baku fahimta ba"
Anan "ba zai ji ba" yana wakiltar rashin fahimta. AT: "baku fahimta ba"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa mutane suna da wauta ƙwarai saboda ba sa tsoron Yahweh. AT: "Wauta ce ba ku tsoron ni ... fuska!"
AT: "mai taurin kai da tawaye"
Kalmar "sun" tana nufin mutane. Anan “tafi” yana wakiltar rashin biyayya ga Allah. AT: "Sun yi tawaye kuma sun ƙi biyayya gare ni"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Gama na sami mugaye a cikin mutanena"
Anan "babba" yana wakiltar mai ƙarfi. AT: "waɗannan mugayen mutane sun zama masu ƙarfi da wadata"
Yin magana akan aikata kowane nau'i na mugayen abubuwa ana maganarsa kamar akwai iyaka mai raba wasu mugayen abubuwa daga abubuwan da suka fi mugunta. AT: "Suna aikata kowane irin mummunan abu" ko "Har ma suna aikata mafi munanan abubuwa"
Waɗannan su ne mugunta da firgici waɗanda aka ambata a aya ta 30.
"Annabawa suna annabcin karya" ko "Annabawa suna yin karya lokacin da suke annabci"
"amma me za ka yi a ƙarshen wannan duka?" Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa mutane za su yi nadama idan suka hukunta su saboda hakan. AT: "amma daga ƙarshe zan hukunta ku kuma zaku yi nadama game da muguwar halinku"
1Ku nemi mafaka, mutanen Benyamin, ta wurin fita daga Yerusalem. Ku busa ƙaho cikin Tekowa. Ku tada tuta kan Bet Hakkerem, tun da mugunta tana bayyana daga arewa; babbar hallakarwa na zuwa.2Za a hallaka ɗiyar Sihiyona, kyakkyawar mace 'yar lele.3Makiyaya da garkunansu zasu tafi wurinsu; zasu kafa rumfunansu kewaye dasu; ko wannen su zai yi kiwo tare da hannunsa.4Ka miƙa kanka ga allolin domin yaƙin. Mu tashi, bari mu kai hari da rana. Bashi da kyau gama hasken rana yana dushewa, inuwoyin yamma suna faɗuwa.5Amma bari mu tashi da dare mu kai hari mu hallaka matsaranki."6Gama Yahweh mai runduna ke faɗar haka: Ku sare itatuwanta, ayi tudu da aikin kewaye gãba da Yerusalem. Wannan shi nebirnin daya cancanci a kai wa hari, domin cike yake da zalunci.7Kamar yadda rijiya take bada ruwa, haka birnin yake sarrafa mugunta. Ana jin tashin hankali da rashin lafiya a cikinta, cuta da rauni kullum suna gabana.8Ki karɓi horo ya Yerusalem ko in juya daga gareki in sa ki cikin hallaka, ƙasar da babu mai zama ciki.9Yahweh mai runduna ya faɗi wannan, "Hakika zasu yi kalar waɗanda suka ragu a Isra'ila kamar kuringar inabi. Ka sake sa hanunka ka tsinki inabi daga kuringa.10Ga wa zan sanar in kuma yi gargaɗi domin su ji? Duba! Kunnuwansu marasa kaciya ne; ba su iya saurarawa! Duba! Maganar Yahweh tazo gare su domin ta kwaɓesu, amma basu so ba."11Amma na cika da hasalar Yahweh. Na gaji da daurewa a cikinta, Yace mani, "Ka zuba ta kan yara cikin tituna, da kan taron majiya ƙarfi. Gama kowanne miji za a ɗauke shi da matarsa; da kowanne tsoho mai yawan shekaru.12Za a ɗauki gidajensu aba waɗansu, gonakinsu da matansu gaba ɗaya. Gama zan kai hari ga mazaunan ƙasar da hannuna - wannan furcin Yahweh ne.13Yahweh ya furta cewa daga ƙaraminsu zuwa babbansu, dukkansu suna haɗama wajen cin ƙazamar riba.14Daga annabi zuwa Firist, kowannensu yana aikata yaudara. Sun warkar da raunukan mutane na sama sama, suna cewa, 'Salama, Salama,' alhali kuwa ba salamar.15Suna jin kunya lokacin da suka aikata abin ƙyama? Basu jin kunya; basu san yadda zasu juye ba, Don haka zasu faɗi cikin masu faɗowa; za a kawo su ƙasa lokacin hukuncinsu, inji Yahweh.16Yahweh yace, "Ka tsaya a mararrabar hanya ka duba, ka tambayi daɗaɗɗun tafarkun hanyoyi. 'Ina wannan hanya mai kyau take?' kayi tafiya kanta ka samarwa kanka wurin hutu. Amma mutane suka ce, 'Ba zamu je ba'17Na sa maku matsara ku saurari muryar ƙaho. Amma suka ce, 'Ba zamu saurara ba.'18Don haka ku saurara, al'ummai! ku duba, ku zama shaidar abin da zai same su.19Ki ji, ke duniya! Zan kawo masifa kan mutanen nan - 'ya'yan tunaninsu. Ba su saurari maganata ko dokata ba, amma sun ƙi ta."20"Mene ne ma'anar wannan turare mai ƙanshi na lubban da ake kawowa daga sheba a gare ni? ko wannan ƙanshi mai daɗi daga ƙasa mai nisa? ƙonannun hadayunku ba abin karɓa ba ne a gareni ko sadakokinku.21Domin wannan Yahweh yace, 'Duba, zan sa sanadin tuntuɓe akan waɗannan mutane. Za suyi tuntuɓe a kan sa - Ubanni da 'ya'ya maza tare. Mazaunan tare da maƙwabtansu kuma zasu hallaka.'22Yahweh yace, 'Duba, al'umma tana zuwa daga ƙasar arewa. Za a zuga babbar al'umma su taso daga ƙasa mai nisa.23Zasu ɗauki kibau da mãsu. Masu mugunta ne basu da tausayi. Ƙararsu na ruri kamar teku, suna kuma hawan dawakai, sun fita a jere kamar mayaƙan mutane, gãba da ke, ɗiyar Sihiyona.'"24Mun ji rahotanni game dasu hannuwanmu kuma sun yi sanyi cikin azaba. Azaba ta kama mu kamar mace mai naƙuda.25Kada ku fita zuwa filaye, kada ku yi tafiya kan hanyoyi, gama takubban abokan gaba da tsoratarwa suna koina.26Ɗiyar mutanena, ki sanya tsummoki ki kuma yi birgima cikin toka; ki yi makoki da kuka mai zafi kamar na tilon ɗa, gama mai hallakarwar zai zo kanmu ba zato.27"Irmiya, Na maishe ka mai gwada mutanena, kamar mai gwada ƙarfe, zaka duba suka auna hanyoyinsu.28Mutane ne da suka fi kowa rashin ji, suna yawon ɓata waɗansu. Dukkansu jan karfe da baƙin ƙarfe suke, masu aikata cin hanci.29Mazuga suna zuga da wutar dake ƙonesu; dalma tana cinyewa cikin harshen wuta. Tacewar ta ci gaba tsakaninsu, amma bashi da amfani, saboda ba a kawar da muguntar ba.30Za a kira su azurfar da aka ƙi, gama Yahweh ya ƙi su."
Ana amfani da ƙaho don gargaɗi cewa za a kai wa mutane hari. AT: "Ku busa ƙaho a Tekowa don faɗakar da mutane cewa za a kawo musu hari"
Mai yiwuwa ma'anoni sune 1) siginar hayaƙi ne daga wuta. AT: "kunna wuta don kunna hayaki a Bet Hakkerem don faɗakar da mutane game da abokan gaba masu zuwa" ko 2) AT: "Ka daga wata tuta a saman garin Bet Hakkerem don yi wa mutane kashedi game da abokan gaba masu zuwa"
Ana yawan magana da sarakuna a matsayin makiyayan mutanensu. AT: "Sarakuna da sojojin su zasu je wurin su"
Sojojin da ke kai harin suna kokarin tabbatar da cewa allolinsu za su taimaka musu yayin yakin ta hanyar yin bukukuwa da kuma yin sadaukarwa a gare su. AT: "Ku shirya don yaƙi ta hanyar tsarkake kanku da sadaukarwa ga gumakan"
Sarakunan sun faɗi wannan ne da yammacin ranar da suke son sojojinsu su ci gaba da yaƙi duk da cewa dare ya yi.
Anan "an cika shi da zalunci" yana wakiltar mutane a koyaushe suna zaluntar mutane. AT: "saboda mutanenta koyaushe suna zaluntar juna"
Anan "wannan birni yana ci gaba da haifar da mugunta" yana wakiltar mutane a cikin garin da ke ci gaba da aikata mugunta.
Anan Allah yana magana da mutanen Yerusalem kamar yana magana da birnin ne da kansa. AT: "Ku karɓi horo, ya ku mutanen Yerusalem ... ku mai da ƙasarku kufai, ƙasar da ba kowa a ciki"
Yahweh yayi magana game da abokan gaba suna kai hari ga waɗanda suka rage kamar abokan gaba za su ɗibi inabin da ya rage a gonar inabi bayan da wasu sun girbe shi. AT: "Bayan halakar da Isra'ila, tabbas za su dawo don afka wa mutanen da ke raye"
Yahweh yana umartar magabci da ya auka wa waɗanda suka rage a Isra’ila kamar dai magabcin sun tsinke ’ya’yan inabi da suka rage a gonar inabi bayan da wasu sun girbe. AT: "Ku dawo ku farma mutanen Isra'ila waɗanda suka rage" ko "Kamar mutanen da suka sake ɗebo inabi daga inabin da suka riga suka girbe, ku dawo ku farma mutanen da suka rage"
Allah yayi maganar azabtar da Isra'ilawa kamar fushinsa ruwa ne wanda yake son Irmiya ya zubo musu. AT: "Cikin fushin azabtar da yara a tituna da kungiyoyin samari"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Saboda abokan gaba za su kama kowane mutum tare da matarsa"
Kalmomin "za'a juya shi ga wasu" an fahimta daga jumlar da ta gabata. AT: "kuma za a ba da filayensu da matansu ga wasu"
Kalmomin "daga ƙarami zuwa babba" ya nuna cewa dukkan mutanen Isra'ila suna cikin kalmar "dukkansu," komai muhimmancinsu. AT: "dukkansu, gami da mafi ƙarancin ƙarfi, mafi ƙarfi, da kowane ɗayansu, masu son zuciya ne"
"Lafiya lau, duk lafiya," amma ba lafiya
Allah yayi amfani da wannan tambayar don ya nuna fushin sa cewa mutane basa jin kunyar zunubansu. AT: "Sun aikata manyan zunubai, kuma ba sa jin kunya"
Anan "fadowa" tana wakiltar kashewa. AT: "za a kashe su tare da sauran waɗanda aka kashe"
Hanyoyi na nufin hanyoyin da mutane ke rayuwarsu. Yahweh yana so Isra’ilawa su tambayi abin da ke kyakkyawar hanyar rayuwarsu kuma su yi hakan.
Yahweh yayi magana game da annabawansa kamar dai su masu tsaro ne waɗanda aka aiko su faɗakar da mutane game da haɗari.
"nan gaba kadan zan hukunta wadannan mutanen"
A nan “ba su kula da maganata ba” tana nufin rashin sauraron abin da Allah ya faɗa, kuma “ƙi shi” yana nufin ƙin bin dokar Allah. AT: "Ba su saurari abin da na ce ba. Maimakon haka sun ƙi bin dokokina"
Allah yana amfani da waɗannan tambayoyin don tsawata wa mutane. AT: "Turare daga Sheba da ƙamshi mai daɗi daga ƙasa mai nisa ba komai a gare ni." ko kuma "Ba na son hadayunku na ƙonawa na lubban daga Sheba ko raƙuman ƙanshi mai daɗi daga ƙasa mai nisa."
"Ina gab da sanya cikas a gaban wannan mutanen." Yahweh yayi magana game da masifun da zai kawo wa Isra'ilawa kamar su ne tubalin da mutane suka yi tuntuɓe.
Kasancewa da ''zuga'' yana nufin shirya yin wani abu. AT: "ana shirin zuwa daga ƙasa mai nisa"
Ƙaredarar amo da sojoji ke yi ana kwatanta su da babbar kara ta teku. AT: "Sautin da suke yi yana da ƙarfi sosai, kamar sautin teku"
"hannayenmu sun yi rauni saboda muna cikin damuwa"
Irmiya ya nuna ƙaunar Yahweh ga mutanensa ta wurin yi musu magana a matsayin ɗiya. AT: "Mutanena, ku da kuke kamar 'yata a gare ni" ko "Ya ku ƙaunatattun mutane"
"saboda sojojin abokan gaba ba zato ba tsammani za su zo su kawo mana hari"
Yahweh ya gwada Irmiya yana gwada mutanensa da wanda yake gwada ƙarfe don ya ga yadda yake da kyau.
Allah yana maganar azabtar da mutanensa kamar azurfa kuma yana tafasa azurfar a cikin wuta mai zafi. Waɗannan jimlolin suna jaddada cewa wanda yake dafa ƙarfen yana aiki tuƙuru.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Za ku ci gaba da tsaftace su" ko "Za ku ci gaba da ƙoƙarin tsarkake su"
1Maganar da ta zo ga Irmiya daga Yahweh, cewa,2Ka tsaya a ƙofar gidan Yahweh ka shaida wannan maganar! Kace, 'Ji maganar Yahweh, dukkan kuna Yahuda, ku da kuke shiga waɗannan ƙofofin kuyi ma Yahweh sujada.3Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗa haka: Ku gyara hanyoyinku da ayyukanku da kyau, haka kuwa zan ƙyale ku ku ci gaba da zama a nan wurin.4Kar ku miƙa kanku ga maganganun ƙarya ku kuma ce, "Haikalin Yahweh! Haikalin Yahweh! Haikalin Yahweh!"5Gama idan kun tabbatar da ayyukanku da hanyoyinku da kyau; idan kun aiwatar da adalci da gaskiya tsakanin mutum da makwabcinsa -6idan baku zalunci wanda ke zaune a ƙasar ba, da maraya da gwauruwa kuma baku zubar da jini a banza a nan wurin ba, kuma baku bi waɗansu allolin da zasu yi maku illa ba -7sa'annan zan ƙyale ku ku zauna a nan wurin, a ƙasar dana bayar ga kakanin ku daga zamanin zamanai da zuwa har abada.8Duba!! kun amince da maganganu na ruɗami da ba zasu taimake ku ba.9Kuna sata da kisan kai da zina? kuna rantsuwar ƙarya da kuma miƙa turare ga Baal kuma kuna bin waɗansu allolin da baku sani ba?10Sa'annan sai kuzo ku tsaya a gabana a wannan gidan da ake kira da sunana kuma a ce, "An cece mu," saboda kawai kuyi dukkan waɗannan abubuwan banƙyama?11Wannan gidan dake ɗauke da sunana, ya zama ƙogon mafasa a idanunku? Amma duba, Na gani - wannan furcin Yahweh ne.'12Saboda haka ku je wuri na dake shiloh, inda na bar sunana ya zauna nan da farko, kuma duba abin da nayi da ita saboda muguntar mutanena Isra'ila.13Don haka yanzu, ta dalilin yin waɗannan ayyuka - wannan furcin Yahweh ne - Nayi magana da ku lokuta zuwa lokuta, amma baku ji ba. Na kira ku amma baku amsa ba.14Saboda haka, abin da nayi a Shilo, Zan kuma yi ma gidan nan da ake kira da sunana, gidan da kuka amince, wannan wuri da na baku da kakaninku.15Gama zan aikar da ku waje daga gare ni kamar yadda na aikar da dukkan 'yan uwanku, dukkan zuriyar Ifraim.'16Kai kuwa, Irmiya, kar ka yi wa mutanen nan addu'a, kuma kar ka ɗaga muryar makoki ko ka faɗi addu'a a madadinsu, kuma kada ka roƙe ni, gama ba zan ji ka ba.17Baka ga abin da suke yi a biranen Yahuda da titunan Yerusalem ba?18Yaran na tattara katako kuma Ubanin na kunna wuta! Matayen na ƙwaba ƙullu don yin gurasa domin sarauniyar sammai kuma suna zubo da hadayun ruwan inabi ga waɗansu alloli domin su tsokane ni.19Da gaske tsokana ta suke yi? - wannan furcin Yahweh ne - ba kansu suke tsokana ba, har kunya ta kasance a kansu?20Hakika Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan, 'duba, fushina da hasalata zasu kwararo a wannan wurin, a kan mutum da dabba, a itatuwa na fili da 'ya'yan itace na ƙasa. Zata ƙone kuma ba za a ɓice ta ba.'21Yahweh mai runduna, Allahn Isra'ila ya faɗi haka, 'Ku ƙara baye -bayen ƙonawa akan hadayarku da naman daga garesu.22Gama sa'adda na fito da kakaninku daga ƙasar Masar, ban nemi komai daga gare su ba. Ban basu ko umurni a kan zancen baye - baye na ƙonawa da hadayu ba.23Na basu wannan umurnin ne, "Ku saurare muryata, sai in zama Allahnku ku kuma ku zama mutanena. Saboda haka kuyi tafiya a hanyoyin da nake umurtar ku, don ya tafi maku dai-dai."24Amma basu saurara ko su kula ba. Sun rayuwa ta bishewar shirye-shiryen taurin zuciyarsu, saboda haka suka koma baya, maimakon gaba.25Tun daga ranar da kakaninku suka fito daga ƙasar Masar har zuwa wannan ranar, Na aike kowanne ɗaya daga cikin barorina da annabawa na a gare ku. Nayi naciya yayin da nake aikar da su.26Amma basu saurare ni ba. Basu kula ba. Maimako, suka taurare wuyansu. Sun ma fi kakanninsu mugunta.'27Saboda haka ka sanar da waɗannan maganganun gare su, amma ba zasu saurare ka ba. Faɗi waɗannan abubuwan a gare su, amma ba zasu ba ka amsa ba.28Kace masu Wannan ce al'ummar da ba zata saurari muryar Yahweh Allahnta ba kuma bata karɓi horaswa ba. An hallaka an datse gaskiya daga bakunansu.29Ku yanke gashinku ku kuma yi wa kanku aski, ku kuma zubar da gashin kanku. Ku raira waƙar jana'iza a kan buɗaɗɗun wurare. Gama Yahweh ya ƙi kuma ya watsar da wannan tsara a cikin hasalarsa.30Gama 'ya'ya maza na Yahuda sun yi mugunta a idona - wannan furcin Yahweh ne - Sun sa abubuwan ƙyamarsu a cikin gidan da ake kira da sunana, domin su ƙazamtar dashi.31Sa'annan suka gina babban wurin Tofet wanda ke cikin kwarin Ben Hinom. Sun yi haka don su ƙone 'ya'yansu maza da mata a wuta - abin da ban umurta ba, ko ya shiga zuciyata ba,32Saboda haka duba, rana na zuwa - Wannan furcin Yahweh ne - yayin da ba za'a ƙara kiran wurin Tofet ko kwarin Ben Hinnom ba. Zai zama kwarin yanka; za a binne jikkuna a Tofet har sai babu wurin da ya rage.33Gawawwakin waɗannan mutanen zasu zama abincin tsuntsayen sararin sama da dabbobin duniya, kuma babu wanda zai tsoratar da su.34Zansa ƙarshen titunan Yahuda da na Yerusalem, ƙarar murna da ƙarar farin ciki, ƙarar ango da amarya, gama ƙasar zata zama lalatacciya."
Ana amfani da wannan karin magana don gabatar da saƙo na musamman daga Allah. AT: "Wannan shi ne saƙon da Yahweh ya ba Irmiya. Ya ce," ko "Wannan shi ne saƙon da Ubangiji ya yi magana da Irmiya:"
Yahweh ya ci gaba da ba Irmiya saƙonsa ga mutanen Yahuda.
"Idan kun inganta hanyoyinku da ayyukanku, to, zan bari ku ci gaba"
Karin magana mai ma'ana "da kanka" yana jaddada haɗarin mutum ga Isra'ilawa. AT: "Kada ku amince da kalmomin yaudara don kare ku, kuna cewa"
AT: "kayi hukunci dai-dai"
"yi adalci baƙo"
Anan zubar da jinin mara laifi yana wakiltar kashe waɗanda basu cancanci kisa ba. AT: "kashe mutanen da ba su da laifi"
Wadannan tambayoyin suna tsammanin amsar tabbatacciya don nuna cewa Allah ya san zunuban da suke aikatawa. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Kayi sata, ka kashe, kuma ka yi zina. Ka rantse ... kuma ka bi waɗansu alloli waɗanda ba ka san su ba."
Wannan tambayar tana buƙatar amsa mai kyau don sanya batun cewa Allah ya san munafuncin maganganunsu da ayyukansu. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "To ku zo ku tsaya ... don haka kuna iya aikata waɗannan abubuwan ƙazantar."
Wannan ƙaddara ce ta haikalin Yahweh. Ana iya bayyana shi cikin tsari mai aiki. AT: "gidan da ke nawa" ko "haikalin da kuke bauta mini"
Anan "inda na bari sunana ya zauna" karin magana ne wanda ke nufin wannan shine wurin da ake bautawa Yahweh. AT: "wurin da nake Shiloh inda na fara bawa mutanena damar bautata" (Duba: fgis_idiom)
Wannan kalmomin yana magana ne wanda yake nufin anyi wani abu sau da yawa. AT: "akai-akai" ko "dagewa"
Waɗannan jimloli huɗun kowane ma'anarsu ɗaya ce kuma ana maimaita su don ƙarfafawa.
Wannan tambayar tana buƙatar amsa mai kyau. Ana iya bayyana shi azaman bayani. AT: "suna tsokanar kansu, don haka kunya ta same su!" ko "suna damuwa kuma suna kawo kunya akan kansu!"
Yahweh yayi maganar fushin sa kamar wani abu ne wanda za'a iya zubowa. AT: "Zan hukunta wannan wurin"
Wannan sanarwa ce ta izgili da ke jaddada cewa babu wani abu daga cikin sadakokinsu da Yahweh ya karɓa. AT: "Ku ci gaba da cin hadayar ƙonawa tare da hadayunku da naman daga gare su"
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) sun ƙi su mai da hankali ga Yahweh, maimakon su yi masa biyayya da ƙwazo. AT: "sun rabu da ni maimakon su kusance ni" ko kuma 2) sun ci gaba da zama da rauni maimakon ingantawa. AT: "sun daɗa muni maimakon mafi kyau"
Waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya kuma ana maimaita su don ƙarfafawa.
Wannan karin magana ne wanda ke nufin sun kasance masu taurin kai. AT: "sun zama masu taurin kai" ko "sun yi tsayayya da ni"
Wadannan jimlolin guda biyu sun ce abu daya, Na biyu ya jaddada sakon na farkon. AT: "Ka gaya musu sakona, amma ba za su saurare ku ba ko amsa muku ba."
Wannan yana nufin mutanen Yahuda. AT: "mutanen Yahuda"
Waɗannan kalmomin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma ana maimaita su don ƙarfafawa.
Wannan sunan wani wuri ne da Isra’ilawa ke yanka sacrificeda 'ya'yansu ga allahn ƙarya ta ƙona su da wuta.
Wannan sunan kwari ne a kudu da birnin Yerusalem, inda mutane suke yanka hadaya ga gumakan ƙarya.
"za su binne mutanen da suka mutu"
"mutanen Yahuda"
"namomin jeji na ƙasar"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma ana maimaita su don ƙarfafawa. AT: "sautukan mutane na murna da farin ciki"
1Wannan ne furcin Yahweh - a lokacin nan zasu fitar da kasusuwan sarakunan Yahuda da ofisoshinsu, kasusuwan firistoci da annabawa, da kasusuwan mazaunan Yerusalem daga kaburbura.2Sa'annan zasu shimfiɗa su a waje a hasken rana da wata da dukkan tauraron sararin sammai; waɗannan abubuwan na sararin sama da suka bi suka kuma bauta masu, da suka kuma bisu suka nemesu, kuma suka yi masu sujada. Baza a binne ko a tattara kasusuwan kuma ba, zasu zama kamar kashin dabba a fili.3A dukkan ragowar wuraren da na kore su zuwa, zasu zaɓi mutuwa a maimakon rai domin kansu, dukkan waɗanda aka bar su daga wannan muguwar al'umma - Wannan ne furcin Yahweh mai runduna.4Saboda haka ka faɗa masu, 'Yahweh yace haka: Akwai wanda ya faɗi kuma bai tashi ba? Akwai wanda ya ɓace da bai yi ƙoƙarin dawowa ba?5Meyasa waɗannan mutanen, Yerusalem, suka juya baya da daɗewa cikin rashin bangaskiya? Sun rungume yaudara kuma sun ƙi su tuba.6Na kula na kuma saurara, amma basu yi maganan dai - dai ba; ba wanda ke nadama da muguntarsa, ba wanda yace, "Mene ne na yi?" Dukkansu sun tafi wurin da suke so, kamar dokin da ke sauri zuwa fagen fama.7Ko shamuwar sama ma ta san lokutan da suka dace; kurciyoyi kuma, da dila da zalɓe. Suna kiyaye lokacin ƙaurarsu, amma mutanena ba su san dokokin Yahweh ba.8Yaya zaku ce, "Mu masu hikima ne, don umurnin Allah na tare da mu"? Hakika ku duba! alƙalamin ƙarya na magatakarda ya ƙirƙiro ƙarya.9Mutane masu hikima zasu ji kunya. Zasu tsorata su kuma cafku. Duba! Sun ƙi maganar Yahweh, to mene ne amfanin hikimarsu?10Saboda haka zan bada matayensu ga waɗansu, filayensu kuma ga waɗansu su mallaka, don daga mafi ƙanƙantarsu zuwa babbansu, kowannensu ya na haɗamar cin ƙazamar riba! Daga annabi zuwa firist, dukkansu suna aikata ha'inci.11Sun warkar da raunin mutanena sama - sama, suna cewa, "Salama, Salama," sa'adda babu salama.12basu ji kunya ba ne a sa'adda suke ayyukan banƙyama? Basu ji kunya ba; basu san yadda zasu kunyata ba! Saboda haka zasu faɗi cikin faɗaɗɗu; za a kawo su ƙasa sa'adda ake horar da su, inji Yahweh.13Zan tuge su kakaf - wannan furcin Yahweh ne - baza a sami inabi a itacen inabi ba, ko 'ya'ya a itacen ɓaure ba, gama ganyen zai bushe, kuma abin da na basu zai ƙuɓuce masu.14Me yasa muke zama a nan? kuzo mu taru; bari mu je garuruwa masu garu, kuma mu yi shiru a can cikin mutuwa. Gama Yahweh Allahnmu zai sa muyi tsit. Zai sa mu sha guba, tunda mun yi masa laifi.15Muna fatan salama, amma babu wani abu mai kyau. Muna fatan lokacin warkarwa, amma duba, za a sami razana.16Firjin dawakansa aka ji daga Dan. Dukkan duniya ta girgiza saboda haniniyar ingarmun ƙarfafan dawakansa. Gama zasu zo su cinye ƙasar da wadatarta, birni da masu zama cikinsa.17Gama ku duba! Ina aikar da macizai a cikinku, kãsayen da ba zaku samu makarinsu ba. Zasu cije ku -Wannan furcin Yahweh ne."'18Baƙincikina ba shi da ƙarshe, kuma zuciyata na ciwo.19Duba!! Muryar ihun ɗiyar mutanena daga ƙasa mai nisa! Babu Yahweh a Sihiyona ne? Ko ba sarkin a cikinta? Me ya sa suke cakuna ta zuwa fushi da sassaƙaƙƙun sifofinsu da banzayen bãƙin gumakansu?20Girbi ya ƙare, damuna kuma ta wuce. Amma ba a cece mu ba.21Na raunana saboda raunin ɗiyar mutanena. Nayi makokin a kan abubuwan tsoron da suka same ta; Na tsorata.22Babu wani magani a Giliyad ne? Babu mai warkarwa a can ne? Me zai hana warkarwar ɗiyar mutanena ta faru?
Kalmar "su" anan tana nufin mutanen Yahuda. Waɗannan jimlolin guda uku suna nufin abu ɗaya kuma ana maimaita su don ƙarfafawa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba wanda zai tattara ƙasusuwansa ko sake binne su"
Kalmar "su" tana nufin mutanen Yahuda.
Waɗannan tambayoyin sun nuna cewa hanyar da mutanen Yahuda suke yi ba ta da ma'ana. Ana iya fassara su azaman sanarwa. AT: "Kun san cewa lokacin da wani ya faɗi, yakan tashi, kuma idan wani ya ɓace, yana ƙoƙari ya nemi hanyar dawowa."
Yahweh yana cewa hanyar da mutanen Yahuda suke yi ba ta da ma'ana. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Ba ya da ma'ana cewa mutanen nan, Yerusalem, sun juya baya cikin rashin imani na dindindin."
Cikakken sunan "mugunta" ana iya fassara ta amfani da sifa "mugu." AT: "don mugaye"
"tafi nasu hanya"
Bayanin da aka kawo shi ne cewa wadannan nau'ikan tsuntsayen sun san lokutan da ya dace su yi kaura, wanda ke nufin tashi daga wani wuri zuwa wani a lokuta daban-daban na shekara don ciyarwa ko kiwo.
Yahweh ya yi wannan tambayar ne don ya sa mutanen Yahuda su yi tunani a kan abin da suke faɗa. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Kuna tsammani kuna da hikima saboda kuna da dokar Yahweh tare da ku."
Alƙalami yana wakiltar kalmomin da marubuta ke rubutawa. AT: "Abubuwan ƙarya da marubuta ke rubutawa"
Wannan tambayar tana buƙatar amsa mara kyau kuma an shiryata don sa masu sauraro suyi tunani game da ƙaramin abin da suke ɗauka na hikima ya cancanci gaske yayin da suka ƙi maganar Yahweh. AT: "don haka abin da suke tsammani mai hikima ne ba zai amfane su da komai ba."
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) raunuka suna wakiltar matsalolin da mutane suke da shi sakamakon zunubinsu. AT: "Suna yi kamar dai matsalolin mutanena ba su da girma, kamar ƙananan raunuka" ko 2) raunukan suna wakiltar zunubin mutane. AT: "Suna yi kamar zunuban mutanena ba su da nauyi, kamar ƙananan raunuka"
An yi wannan tambayar don motsa aiki. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Bai kamata mu tsaya anan ba."
"Birni masu garu" birane ne masu katanga da kagara masu ƙarfi. Duba yadda kuka fassara irin waɗannan jimlolin a cikin Irmiya 4: 4.
Wannan karin magana ne don hukuncin da Yahweh zai yi wa mutanensa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutanen Dan sun ji zagin dawakinsa"
Wannan karin magana ne wanda abin kwatance ne ga mutanen Yahuda suna rawar jiki don tsoro. AT: "Dukan mutanen ƙasar suna girgiza da tsoro"
Yin laya yana nufin raira waƙa ko yin kiɗa don sarrafa macizai.
A nan kalmar "cinye" na nufin cin abinci. Karin magana ne kan yadda makiya suka zo suka lalata kasar da mazaunanta. AT: "za su zo su halakar"
Kalmar "na" tana nufin Irmiya. AT: "Ina bakin ciki sosai"
Anan “zuciya” tana wakiltar Irmiya, yana mai jaddada yadda yake ji da motsin rai. AT: "Ina jin ciwo a cikina ƙwarai"
Wadannan tambayoyin guda biyu suna da ma'ana iri daya. Suna nuna cewa mutanen Yahuda suna mamakin abin da ya sa Yahweh bai cece su ba. AT: "Me yasa Yahweh ba zai cece mu ba idan shi sarki ne a Sihiyona?"
"Lokacin girbi ya wuce"
Waɗannan maganganun suna bayyana ra'ayi ɗaya a cikin hanyoyi fiye da ɗaya don ƙarfafawa.
An yi waɗannan tambayoyin don su nuna cewa mutanen Yahuda ba su sami ceto ba. AT: "Akwai magani a Giliyad, kuma akwai masu warkarwa a can, don haka ku gaya mani dalilin da ya sa warkar da ƙaunatattun mutane ba zai faru ba."
1Da ma kaina zai ɓullo da ruwa, kuma idanuna su zama maɓuɓɓular hawaye! Gama ina tunanin yin kuka rana da dare domin waɗanda ke cikin ɗiyar mutanena da aka kashe.2Da ma wani zai bani wuri domin matafiya a hamada su zauna, inda zan je in rabu da mutanena. Da ma zan iya barin su, tunda dukkansu mazinata ne, ƙungiyar maciya amana!3Yahweh ya furta, "Sun tanƙwasa bakkunan ƙarerayinsu da na harsunansu, amma ba don wani amincinsu ne ya sa suka yi ƙarfi a duniya ba. Suna ta ci gaba daga aikin mugunta ɗaya bayan ɗaya. Basu san ni ba."4Kowannen ku, yayi hankali da maƙwabcinsa kuma kada ya amince da kowanne irin ɗan'uwa. Gama kowanne ɗan'uwa hakika mayaudari ne, kuma kowanne maƙwabci mai kushe ne.5Kowanne mutum yana yiwa maƙwabcisa ba a kuma ba ya faɗin gaskiya. Harsunansu na koyar da abubuwan ƙarya. Sun rafke daga aikata laifi.6Zamanku na cikin ruɗu; a cikin yaudararsu sun ƙi su shaida ni - Wannan furcin Yahweh ne."7Yahweh mai runduna ya faɗi haka, "Duba, Ina gab da tsabtace su in kuma gwada su, gama me zan iya yi, saboda abin da mutanena suka yi?8Harsunansu kibiyoyi masu kaifi ne; suna faɗin abubuwan rashin aminci. Da bakunansu suna shaida salama ga maƙwabtansu, amma da zukatansu suna shirya masu maƙarƙashiya.9Ba zan hukuntasu saboda waɗannan abubuwan ba - wannan shi ne furcin Yahweh - kuma ba zan rama wa al'umma irin wannan ba?10Zan raira waƙar makoki da kururuwa saboda duwatsu, kuma za a raira wakar jana'iza domin wuraren kiwo. Gama an ƙone su don kar kowa ya wuce ta wurinsu. Ba zasu ji kukan wata dabba ba. Tsuntsaye da namomin daji sun gudu sun tafi.11Saboda haka Zan maida Yerusalem tsibin kufai, maɓoyar diloli. Zan maida biranen Yahuda kufai inda ba mazauna."12Wanne mutum ne ke da isasshiyar hikima ya gane wannan? Ga wane ne bakin Yahweh yayi magana, kuma zai faɗe shi? Me yasa ƙasar ta lalace an kuma hallakar da ita kamar hamadar da ba wanda zai iya wucewa ta cikinta?13Sai Yahweh yace, "Saboda sun ƙi dokokin da na shirya a gare su, saboda basu saurari muryata ko su yi aiki da ita ba.14Saboda sun yi tafiya da taurarrar zuciyarsu suka kuma bi Ba'aloli kamar yadda ubanninsu suka koya masu suyi.15Saboda haka Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka, 'Duba, Ina gab da sa mutanen nan suci abinci mai ɗaci da ruwan dafi.16Sa'annan zan watsar dasu cikin al'ummar da basu sani ba da su da kakaninsu. Zan aikar da takobi ya bi su har sai na hallaka su kakaf."'17Yahweh mai runduna ya faɗi haka, "Kuyi tunani a kan wannan: Ku kira masu waƙar jana'iza; bari su zo. Ku aiko a kira matayen da suka ƙware a makoki; bari suzo.18Bari su yi sauri su raira waƙar makoki a kanmu, saboda idanuwanmu su iya zubar da hawaye kuma girar idanuwanmu ta malalo da ruwa.19Gama an jin muryar kuka a Sihiyona, 'Yaya muke lalacewa. Mun ji kunya sosai, gama mun yi watsi da ƙasar tun da suka rurrushe gidajenmu.'20Saboda haka ku mataye, ku ji maganar Yahweh; ku kula da saƙonni dake zuwa daga bakinsa. Sa'annan ku koyar da 'ya'yanku mata waƙar makoki, kuma kowacce mace maƙwabciya waƙar jana'iza.21Gama mutuwa ta iso ta tagoginmu; ta shigo cikin fãdodinmu. Ta hallaka yara daga waje, da 'yan maza a dandalin biranen.22Ka faɗi haka, 'Wannan furcin Yahweh ne - gawawwakin mutane zasu faɗo kamar kashin dabbobi a gonaki, kuma kamar dammunan masu girbi, kuma babu wanda zai tara su."'23Yahweh ya faɗi haka, "Kada ka bar mutum mai hikima yayi taƙama da hikimarsa, ko jarumi a cikin ƙarfinsa. Kada ka bar mai arziki yayi taƙama da arzikinsa.24Gama idan mutum yayi taƙama da wani abu, bari ya zama a wannan, cewa yana da fahimta kuma ya san ni. Gama ni ne Yahweh, wanda yake aiki da alƙawarin aminci da adalci da ayyukan adalci a duniya. Gama a cikin waɗannan ne nake murna - wannan furcin Yahweh ne."25Duba, kwanaki na zuwa - wannan furcin Yahweh ne - sa'adda zan horar da dukkan masu kaciya a jiki kawai.26Zan horar da Masar da Yahuda da Idom da mutanen Ammon da Mowab da dukkan mutanen da ke yanke gashin kansu suna sanƙo. Domin dukkan waɗannan al'umman marasa kaciya ne, kuma dukkan gidan Isra'ila suna da zuciya marar kaciya."
Wannan Irmiya ke magana. Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna nanata yawan baƙin cikin Irmiya. AT: "Ina fatan in kara yin hawaye"
Wannan yana nufin gini ga mutanen da ke tafiya a cikin jeji, inda za su iya tsayawa su yi barci a cikin dare.
Ana faɗar ƙarya ana yin ta ne da harsunan miyagu. Hakanan, tunda ba'a iya karban karyar da aka fada ba, ana fadin karya kamar dai kibiya kibiya ne. Maza masu amfani da baka dole ne su taka kwansu da kwarkwata don iya ɗaura igiyoyin, don haka ana maganar maƙaryata a nan kamar suna yin ɗamarar baka ne ta hanyar amfani da harsunansu. AT: "liesaryarsu kamar kibiyoyi ne waɗanda suke harbawa da harsuna"
Aikata aikata wani mummunan aiki bayan wani ana maganarsa kamar masu aikata mugunta suna tafiya daga wannan aikin zuwa wani. AT: "Suna ci gaba da aikata mugunta"
"yi hattara kada ka yarda da dan'uwanka Isra'ilawa, kuma kar ma ka yarda da dan uwanka"
"Dukkanin mutane suna izgili da junan su, kuma basa fadin gaskiya"
Anan ana wakiltar mutane da “harsunansu” don ƙarfafa maganganunsu. AT: "Suna koyar da abubuwa na yaudara"
Yahweh yayi magana akan zama tsakanin mutanen da suke maƙaryata kamar suna zaune a tsakiyar yaudara. AT: "Gidanku yana cikin gidajen maƙaryata" ko "Kuna zaune a tsakiyar maƙaryata"
Wannan yana magana ne da harsunan mutane kamar an kibiya musu kibiyoyi saboda yadda mutane suke cutar da wasu ta maganganun su. Anan 'yarukan' su ke wakiltar jawaban su. AT: "Kalmomin nasu kamar kibiyoyi ne masu kaifi da ke cutar wasu mutane"
Anan maganganun mutane suna wakiltar ta "bakinsu". AT: "Suna magana, suna cewa suna son zaman lafiya tare da maƙwabtansu"
Anan 'zukatan' su ke wakiltar sha'awar mutane. Wannan yana magana ne game da su suna son cutar da maƙwabtansu kamar dai dabba ce da ke tsugune tana jiran kawo wa abincinta hari. AT: "amma ainihin abin da suke so shi ne halakar da maƙwabtansu"
Yahweh yana makokin ƙasar Isra'ila kamar dai mutum ne wanda ya mutu.
"Babu wanda zai ji amon shanu a wurin"
"wuraren da babu mutane"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar ta zance don jaddada cewa mutum mai hikima ne kawai zai fahimci abubuwan da ya faɗa. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Mutanen da ke da hikima kawai za su iya fahimtar waɗannan abubuwa."
Yahweh yayi magana akan mutanen da basa yin biyayya ga shari'arsa kamar wani abu ne da suka yi nesa da shi. AT: "sun ƙi doka ta"
Anan “muryar” Yahweh tana wakiltar abin da yake faɗa. AT: "ba su kula da abubuwan da nake gaya musu"
Anan "tafiya" kalma ce ta "rayuwa." AT: "ko rayuwa yadda na gaya musu su rayu"
"To zan tilasta su su bar nan su zauna a kasashe daban-daban"
Anan kalmar "takobi" tana nufin rundunar abokan gaba. AT: "Zan aika da sojoji don su yaƙi su"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. Sun jadadda cewa dole ne su kira mawakan jana'iza su zo. AT: "Ku samo matan da suka sami horo a zaman makoki ku kawo wadancan matan nan"
Jumlar "aikawa da ita" karin magana ne. AT: "Aika mutane don neman matan da suka kware a zaman makoki"
Anan Yahweh ya faɗi abin da mutanen Yahuza za su ce idan halakar ta zo. Kalmomin "mu" da "namu" na nufin mutanen Yahuza ne kuma ba ya haɗa da Yahweh. Ana iya rubuta wannan a maimakon umarni daga Yahweh zuwa ga mutane. AT: "Ka gaya musu su yi sauri su rera waka don makoki domin ku, don haka idanunku na iya zub da hawaye idanunku na idanu suna kwarara da ruwa"
"Abin kunyarmu yana da girma, saboda makiya sun rusa mana gidaje kuma dole ne mu bar kasar Isra'ila"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna ƙarfafa umarnin don a saurari abin da Yahweh ya ce. AT: "ku saurari abin da Yahweh ya ce. Kula da maganarsa"
Ana iya samar da fi'ilin da aka fahimta. AT: "koya wa kowace mace maƙwabta waƙar jana'iza"
Mutanen Yahuda za su kwatanta mutuwa da wanda zai hau ta tagogi don ya fāɗa wa mutanen da ke ciki, ya faɗa wa mutane a fāda, da tituna, da dandalin birni. (Duba: personification)
Waɗannan jimlolin guda biyu ma'anarta ɗaya ce kuma suna jaddada gawarwakin mutane da yawa. AT: "gawawwaki za su fado ko'ina a wurin"
"Ba wanda zai tara gawawwakin"
"Kada mai hankali ya yi girman kai saboda yana da hikima"
"Kada mawadaci ya yi alfahari saboda yana da arziki"
"ya fahimci ko wanene ni kuma ya san ni." Duk waɗannan jimlolin suna da ma'anoni iri ɗaya. Suna ƙarfafa mutane su san wane ne Yahweh kuma suna fahimtar ko wanene shi.
Wannan yana nufin mutanen Isra'ila waɗanda suka shiga alkawarin Yahweh ta wurin kaciya a zahiri, amma waɗanda ba su canza halayensu ba ta bin dokokinsa. AT: "duk waɗancan mutanen da suka canza jikinsu ta hanyar yi musu kaciya amma waɗanda basu canza halayensu na ciki ba"
Wannan wataƙila yana nufin mutanen da suka yanke gashinsu don girmama allolin arna. Wasu sifofin zamani suna fassara wannan furcin Ibraniyancin a matsayin "duk mutanen da ke zaune a gefen hamada."
“Zuciya” tana wakiltar nufin mutum da abin da yake so. “Zuciya maras kaciya” tana wakiltar halayen mutum ne da ba ya bin Yahweh da dokokinsa. Har ila yau, "gidan" Isra'ila yana nufin mutanen Isra'ila. AT: "duk mutanen Isra'ila ana musu kaciya ne kawai a waje kuma basu canza zukatansu ba"
1"Ku ji maganar da Yahweh yake sanar daku, ya gidan Isra'ila.2Yahweh ya faɗi haka, 'Kar ku koyi hanyoyin al'ummai, kuma kada ku da mu da alamun cikin sammai, domin al'ummai na damuwa da waɗannan ne.3Gama al'adun addinin mutanen nan na banza ne. Suna sare itace a cikin jeji, kuma gwanayen sassaƙa na sassaƙa katako.4Sa'annan suka ƙayata shi da azurfa da zinari. Sun inganta ƙarfin shi da guduma da ƙusa don kada ya faɗo.5abin da suka yi da hanuwansu yana kama da mutummutumi a gonar kukumba, saboda su, ma, ba zasu iya cewa komai ba, kuma ɗaukarsu ake yi domin ba zasu iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu, gama ba zasu iya jawo mugunta, ko kuma su iya yin wani abu maiƙyau ba."'6Babu wani kamarka, Yahweh. Kai mai girma ne, kuma sunanka na da girma cikin iko.7Wane ne ba ya jin tsoron ka, sarkin al'ummai? Don ka cancanci haka, gama babu wani kamar ka a cikin dukkan mazaje masu hikima na al'ummai ko dukkan mulkokinsu masu martaba.8Dukkansu iri ɗaya ne, su daƙiƙai da wawaye ne, almajiran gumaka da ba kome ba ne sai itace.9Suna kawo sarafaffiyar azurfa daga Tarshish da zinariya daga Ufaz waɗanda ƙwararru suka yi, da hannuwan maƙera. Tufafinsu na mulifi da shunayya ne. Gwanayensu ne suka yi dukkan waɗannan abubuwan.10Amma Yahweh shi ne Allah na gaskiye. Shi ne Allah mai rai da madawamin sarki. Fushinsa yakan girgiza duniya, kuma al'ummai ba zasu jure fushinsa ba.11Zaka yi magana da su kamar haka, "Allolin da basu yi sammai da duniya ba zasu lalace daga duniya kuma daga ƙarƙashin waɗannan sammai."12Amma shi ne wanda yayi duniya ta ikonsa, ya kuma kafa ta ta wurin hikimarsa, kuma ta fahimtarsa ya miƙar da sammai.13Muryarsa ta yi ƙugin ruwa a sammai, ya kuma kawo hayaƙi daga kurewar duniya. Yakan yi walƙiyoyi domin ruwan sama ya kuma aikar da iska daga taskokinsa.14Kowanne mutum ya zama jahili da marar ilimi. Kowanne maƙerin zinariya zai sha kunya ta dalilin gumakansa. Gama ƙerarrun siffofinsu ƙarya ne; Babu rai a cikinsu.15Basu da amfani, aikin masu ba'a; zasu lalace a lokacin horonsu.16Amma Allah, madogarar Yakubu, ba haka yake ba, gama shi ne yayi dukkan abubuwa. Isra'ila kabilar gãdonsa ne; Yahweh mai runduna ne sunansa.17Ku tattara kayayyakinku ku bar ƙasar, ku mutanen dake zaune a wuraren dake kewaye da yaƙi.18Gama Yahweh ya faɗi haka, "Duba, Ina gab da jefar da mazaunan ƙasar waje a wannan lokacin. Zan kawo masu ƙunci, kuma zasu kuwa same shi a hakan."19Kaito na! Saboda karyayyun ƙasusuwana, raunina ya sami lahani. Saboda haka na ce, "Tabbas wannan azaba ce, amma zan jure."20An lalatar da rumfata, kuma dukkan igiyoyin rumfata an yanke su biyu. An ɗauke 'ya'yana daga gare ni, saboda haka basu nan. Babu wanda zai yi shimfiɗa a rumfata ko mai ɗaga labulolin rumfata.21Gama makiyayan wawaye ne kuma ba sa biɗar Yahweh; saboda haka basu wadata ba, kuma dukkan garkensu an warwatsar.22Rohotonin labarai sun iso, "Duba! Tana zuwa, babbar girgizar ƙasa tana zuwa daga ƙasar arewaci ta sa biranen Yahuda su zama kufai, maɓuya domin diloli."23Na sani, Yahweh, cewa hanyar mutun ba daga kansa take fitowa ba. Babu mutumin dake jagorar tafiyarsa da takawar kansa.24Ka tsauta mani, Yahweh, da adalci, ba a cikin fushinka ba domin kada ka hallaka ni.25Ka kwarara hasalarka ga al'umman da basu san ka ba, da iyalan da basu kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yakubu sun kuma haɗiye shi saboda su hallakar da shi kakaf su kuma rushe mazauninsa.
"Kada ku yi kamar yadda sauran al'ummomi suke yi"
"da baƙon abubuwa a sama"
Yahweh kawai ya tunatar da su kada su koyi hanyoyin al'ummai kuma kada su damu da abubuwan da ke faruwa a sama.
Irmiya ya yi wannan tambayar ta zance don ya nanata cewa kowa ya ji tsoron Yahweh. Anan ya kira Yahweh a matsayin "sarkin al'ummai." Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Kowa ya kamata ya ji tsoronku, ya ku al'ummomin duniya."
Kalmomin "marasa azanci" da "wawaye" ma'anarsu abu guda ne kuma suna jaddada irin wautar da mutane suke yi wa bautar gumaka. AT: "Dukansu wawaye ne, su almajirai ne"
"suna kokarin koyo daga gunki wanda kawai itace kawai"
"Mutanen sun yi wa gumaka sutura da zane mai launin shuɗi da shunayya"
Wannan yana magana ne game da gumakan da suka ɓace kuma suka rasa mahimmancinsu kamar suna mutuwa. Wannan yana nanata rashin karfinsu. AT: "zai ɓace daga duniya"
Anan an wakilta Yahweh da “murya” don ƙarfafa jawabinsa. Kalmar "rugugin ruwa" na nufin guguwa mai ƙarfi. AT: "Muryar sa tana haifar da hadari a sararin sama"
Wannan yana nufin cewa yana haifar da dusar ƙanƙara kuma ta zama gajimare. Jumlar "iyakar duniya" tana nufin dukkan duniya. AT: "yana sa gajimare ya mamaye kowane yanki na duniya"
"karancin ilimi ne" ko "bai sani ba"
Anan "Yakubu" yana wakiltar mutanen Isra'ila. Allah kasancewarsu "rabo" magana ce wacce take nufin suna bauta masa. AT: "yanki na Isra'ila" ko "wanda mutanen Isra'ila ke bauta wa"
"Tattara kayanku"
Anan Yahweh yayi maganar sa mutane su bar ƙasar kamar wasu abubuwa ne da yake jefawa daga cikin kwantena. AT: "Zan sa mutanen da ke zaune a ƙasar su bar wannan ƙasar"
Irmiya yayi magana game da mutane "wahala kamar dai waɗanda suka sami rauni a raunin ƙasusuwa da kamuwa da cuta. AT: "Kaitonmu! Kamar dai mun karye ƙasusuwa da raunin cutar"
Anan Irmiya yayi magana game da abokan gaba sun lalata garinsu kamar an lalata alfarwansu. AT: "Kamar dai babban tanti namu ya lalace; an yanke igiyoyin da suka ɗaga shi" ko "Maƙiyi ya lalata garinmu kwata-kwata"
Anan Irmiya yayi magana akan basu da zuriyar da zasu sake gina garinsu kamar garinsu tanti ne da yake bukatar sake ginawa. AT: "Babu wanda zai sake gina garinmu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kuma makiyansu sun watse duk garkensu"
Anan "al'ummai" suna nufin mutanen da ke zaune a cikinsu. AT: "A cikin fushinku, hukunta al'ummomi" ko "A cikin fushinku, hukunta al'ummomin mutane"
Waɗannan jimlolin guda uku suna da ma'ana iri ɗaya. Irmiya ya maimaita wannan ra'ayin har sau uku don ya nanata halakar Isra'ila. Wannan yana magana ne akan sojojin makiya wadanda suka afkawa mutanen Isra’ila kamar dai sojojin wata dabba ce mai zafin rai ta afkawa kuma ta cinye abincin ta. AT: "Gama sun afkawa mutanen Isra'ila da kakkausar murya kuma sun cinye su don hallaka su gaba daya"
"rushe gidajensu"
1Maganar da tazo ga Irmiya daga Yahweh, cewa,2"Ka saurari maganganun wannan alƙawari, kuma ka furta su ga kowanne mutum a Yahuda da kuma ga mazaunan Yerusalem3Ka ce masu, 'Yahweh, Allah na Isra'ila ya faɗi haka: La'ananne ne duk wanda ba ya sauraron maganganun wannan alƙawari.4Wannan shi nealƙawarin da na umurci kakaninku su cika a ranar dana fito da su daga ƙasar Masar, Daga tanderun sarrafa ƙarfe. Nace, "Ku saurari muryata ku kuma yi dukkan waɗannan abubuwan kamar yadda na umurce ku, gama zaku zama mutane na ni kuma In zama Allahnku."5Kuyi mani biyayya saboda in cika rantsuwar da na yi ma kakaninku, rantsuwar cewa zan ba su ƙasar dake kwararo da madara da zuma, inda kuke zama a yau." Sa'annan Ni Irmiya, na amsa nace, "I, Yahweh!"6Yahweh yace mani, "Kayi shelar waɗannan abubuwan a cikin biranen Yahuda da titunan Yerusalem. Kace, Ku saurari maganganun wannan alƙawari ku kuma aikata su.7Gama na yi ta bayar da tsarkakan umarnai na ga kakaninku daga ranar da na fitar dasu daga ƙasar Masar har zuwa wannan lokacin, nayi ta faɗakar da su cewa, "Ku saurari muryata."8Amma basu saurara ko su kula ba. Kowanne mutum yana tafiya a cikin taurarriyar muguntar zuciyarsa. Saboda haka na kawo dukkan la'anonin cikin wannan alƙawarin da na umurta su zo gare su. Amma mutanen basu yi biyayya ba duk da haka."9Biye da haka Yahweh yace mani, "An gano tawaye a cikin mutanen Yahuda da mazunan Yerusalem.10Sun juya zuwa zunuban kakaninsu na farko, waɗanda sun ƙi su saurari maganata, maimakon haka suka bi waɗansu alloli suka bauta masu. Gidan Yahuda da na Isra'ila sun karya alƙawarina da na kafa da kakaninsu.11Saboda haka Yahweh ya faɗi haka, 'Duba, Ina gab da kawo bala'i a kansu, bala'in da ba zasu iya kuɓutar da kansu ba. Sa'annan zasu yi kira gare ni, amma ba zan saurare su ba.12Biranen Yahuda da mazaunan Yerusalem zasu je su yi kira ga allolin da suka bada baye-baye gare su, amm hakika ba zasu sami ceto ta wurinsu a lokacin bala'insu ba.13Gama ke Yahuda, allolinki sun ƙaru dai - dai da yawan biranenki. Kin yi yawan bagadanki masu ban kunya a Yerusalem, da turaren bagadai domin Ba'al, dai - dai da yawan titunanta.14Saboda haka kai kanka, Irmiya, kada kayi wa mutanen nan addu'a. Kada kayi kuka ko addu'a a madadin su. Gama ba zan saurara ba sa'adda suka kira ni a lokacin bala'insu.15Me ya sa ƙaunatacciyata, wadda take da mugayen ƙudurori da yawa, take ta aikata su a gidana? Naman hadayunki ba zasu iya taimakonki ba. Kina farinciki saboda mugayen ayyukanki.16A baya Yahweh ya kira ki itacen zaitun mai duhuwa, kyakyawa mai 'ya'yan da ake so. Amma zai cinna wuta a kanta wadda zata yi ƙara kamar iskar guguwa; rassanta zasu kakkarye.17Gama Yahweh mai runduna, shi wanda ya dasa ku, ya furta bala'i gãba da ku saboda mugayen ayyukan da gidan Isra'ila da na Yahuda suka yi - sun sa na husata ta wurin yiwa Ba'al baye-baye."'18Yahweh ya sa na san waɗannan abubuwan, saboda haka na sansu. Kai, ya Yahweh, ka sa na ga ayyukansu.19Ina kama da ɗan rago mai sauƙin kai wanda ake ja zuwa mayanka. Ba ni da sanin cewa sun yi maƙarƙashiya gãba da ni, "Bari mu lalatar da itacen da 'ya'yansa! Bari mu datse shi daga ƙasar masu rai saboda kada a sake tunawa da sunansa."20Duk da haka Yahweh mai runduna Mai yin shari'ar adalci ne wanda yake bincike zuciya da tunani. Zan shaidi sakayyarka game da su, gama na danƙa maganata a gare ka.21Saboda haka Yahweh ya faɗi haka game da mutanen Anatot dake biɗar ranka, "Suka ce, 'Kada ka kuskura kayi annabci da sunan Yahweh, ko ka mutu ta hannun mu.'22Domin haka Yahweh mai runduna ya faɗi haka, 'Duba, Ina gab da hukunta su. Samarinsu masu ƙarfi zasu mutu ta takobi. 'Ya'yansu maza da mata zasu mutu saboda yunwa.23Babu waninsu wanda za a bari, domin Ina tahowa da masifa gãba da mutanen Anatot, a shekarar hukuncinsu."'
"mutanen da ke zaune a Yerusalem"
"ƙasar da madara da zuma ke gudana." Allah yayi magana game da kasar tana da kyau ga dabbobi da tsirrai kamar su madara da zuma daga wadancan dabbobi da tsirrai suna yawo a cikin kasar. AT: "ƙasar da take kyakkyawa don kiwon dabbobi da noman amfanin gona"
Anan "tafiya" salon magana ne game da rayuwar mutum. Kalmar "zuciya" alama ce ta mutum don sha'awa da motsin zuciyar mutum. AT: "Kowane mutum ya ƙi canzawa kuma yana rayuwa ne ta muguwar sha'awarsa" ko "Kowane mutum ya ƙi canzawa kuma yana ci gaba da aikata mugayen abubuwan da suke so su yi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Akwai makirci"
"mutanen da ke zaune a Yerusalem"
Ana amfani da wannan kalmar anan don jawo hankalin wani game da abin da za'a faɗa a gaba. AT: "Saurara" ko "Kula da abin da zan gaya muku"
Yahweh yayi amfani da wannan tambaya ta zance don jaddada cewa mutanen Yahuza basu da ikon kasancewa a cikin haikalinsa. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Myaunataccena, wanda yake da mummunar manufa, bai kamata ya kasance a gidana ba."
cikin Tsohon Alkawari sau da yawa ana kwatanta mutane da bishiyoyi ko tsirrai. Waɗanda suka kasance cikin wadata da koshin lafiya an yi maganarsu kamar itaciya, itaciya mai 'ya'ya. AT: "A da Yahweh ya ce ku kamar bishiyar zaitun ce mai ganye"
Wannan magana tana ci gaba da kwatancin itace. Wutar tana tsaye ne don halakar mutane.
Wannan yana magana ne akan sanya Yahweh na Isra'ila da na Yahuda a wuraren da suke zaune kamar itacen da Yahweh ya dasa. AT: "wanda ya dasa ku kamar manomi ya shuka bishiya" ko "wanda ya sanya ku ku zauna a ƙasar Isra'ila da Yahuda"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "cewa makiyana ke kai wa mayanka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane ba za su ƙara tuna sunansa ba"
maza a mafi ƙarfi lokacin rayuwarsu
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba zan bar ɗayansu ba"
1Kai adali ne, Yahweh, duk lokacin dana kawo rashin jituwata a gare ka. Hakika zan faɗa maka dalilin ƙarata: Me yasa hanyoyin mugaye suke yin nasara? Dukkan marasa bangaskiya suna cin nasara?2Ka dasa su kuma suka yi saiwa. Sun ci gaba da bada 'ya'ya. Kana kusa da su a cikin bakunansu, amma nesa daga zuciyarsu.3Duk da haka kai, Yahweh, ka san ni. Kana gani na kuma kana gwada zuciyata gare ka. Ka ɗauke su kamar tunkiyar da ake kaiwa mayanka, ka ware su domin ranar yanka!4Yaushe ƙasar zata ci gaba da bushewa, kuma tsire-tsiren kwace gona ke yaushi saboda muguntar mazaunanta? Dabbobi da tsuntsaye an ɗauke. Hakika, mutanen sun ce, "Allah ba zai ga abin da zai faru da mu ba."5Yahweh yace, "hakika, idan kai, Irmiya, kayi tsere da sojojin ƙafa suka kuma gajiyar da kai, to yaya zaka yi gasa gãba da dawakai? Idan ka faɗi a lafiyayyar karkara, ƙaƙa zaka yi a kurmin Yodan.6Gama ko 'yan'uwanka da gidan mahaifinka sun basheka sun kuma ƙi ka ƙiri-ƙiri. kada ka amince da su, ko sun faɗi maka abubuwa masu daɗi.7Na yashe da gidana; Na rabu da gãdona. Na bada ƙaunatacciyata cikin hannuwan maƙiyanta.8Abar gãdona ta zamar mani kamar zaki a kurmi; ta kafa kanta gãba da ni da muryarta, saboda na ƙi jininta.9Ashe mallakar da nake ji da ita ta zama dabbare-dabbaren tsuntsu, wacce manyan tsuntsaye ke farauta gãba da ita a kewaye? Tafi ka tattaro dukkan namomin jeji ka kuma kawo su su lanƙwameta.10Makiyaya da yawa sun lalatar mani da garkar inabi. Sun tattake kan dukkan nawa rabon ƙasar; sun maida kyakkyawan rabona hamada da kufai.11Sun maida ita ba komai. Ina makoki domin ta; ba ta da komai. Dukkan ƙasar an maida ita kango, gama ba wanda ya ɗauke abin a zuciya.12Masu hallakarwa sun zo gãba da dukkan tsaunukan cikin hamada, gama takobin Yahweh tana hallakarwa daga wannan iyakar ƙasa zuwa waccan. Babu kwanciyar hankali a ƙasar domin kowacce hallita mai rai.13Sun shuka alkama sun girbi ƙayayuwa. Sun gaji da aiki amma basu samu ribar komai ba. Saboda haka ku ji kunyar ribarku saboda fushin Yahweh."14Yahweh ya faɗi haka a kan dukkan maƙwabtana, mugayen da suka taɓa mallakar dana sa mutanena Isra'ila suka gada, "Duba, Nine wanda ke gab da tumɓuke su daga ƙasarsu, kuma zan jawo gidan Yahuda daga cikinsu.15Sa'annan bayan na tumɓuke waɗancan al'ummai, zai zamana zan sake jin tausayinsu in kuma komo da su; Zan komar da su - kowanne mutum ga gãdonsa da ƙasarsa.16Zai kuwa zamana idan waɗancan al'umman zasu himmantu su koyi hanyoyin mutanena, su yi rantsuwa da sunana 'In dai Yahweh na raye' kamar dai yadda suka koya ma mutanena suyi rantsuwa da Ba'al, to su ma zasu ginu a cikin mutanena.17Amma idan ba wanda ya saurara, sai in tumɓuke wannan al'ummar. Hakika za a tumɓuke ta a kuma hallakata - wannan furcin Yahweh ne."
Anan “bakuna” suna wakiltar abin da mutum ya faɗa. Kuma, "zukata" suna wakiltar abin da mutum yake tunani ko yake ji. Hakanan, ana magana akan kasancewa da aminci kamar yana kusa da mutum, kuma rashin aminci yana magana ne kamar yana nesa da mutum. AT: "Suna faɗin kyawawan abubuwa koyaushe game da ku, amma ba sa ƙaunarku ko girmama ku"
Anan Irmiya ya roki Yahweh ya shirya azabtar da miyagu kamar tumaki ne da za a kwashe su yanka. AT: "ɗauke mugaye, kamar tumaki don yanka" ko "Shirya don azabtar da waɗannan mugaye"
Asarsu ta bushe kuma ruwan sama bai zo azaba ga mutane ba mugunta.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki.AT: "Dabbobin da tsuntsayen sun tafi" ko "Dabbobin da tsuntsayen duk sun mutu"
Wannan tambaya ta zance yana nuna cewa ba zai iya yin gudu tare da dawakai ba. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "ba za ku taɓa yin takara da kyau da dawakai ba."
Wannan yana nufin yayin da mutum yake gudu. AT: "Idan kun faɗi yayin da kuke gudu"
Wadannan jimlolin guda uku suna da ma'ana iri daya. Na farko da na biyu yana karfafa tunani a na uku.
"Sun murkushe ƙafafunsu"
Kalmar "ita" na nufin Ƙasar Alƙawari.
Anan Yahweh yayi magana game da sojojin da yake amfani da su don azabtar da mutanensa a matsayin "takobinsa". An bayyana “takobinsa” a nan kamar dai babbar dabba ce da ta auka wa mutane kuma ta cinye su. AT: "don runduna takobina ne da nake amfani da shi don azabtar da ku" ko "don zan aika rundunonin hallaka don su kawo muku hari"
Wannan yana nufin duk ƙasar da take ta mutanensa.
"ya ba jama'ata Isra'ila gādo"
Anan Yahweh yayi maganar sa mutanen Yahuda su bar ƙasashen sauran al'ummu kamar dai su shuke-shuke ne da yake cirowa daga ƙasa. AT: "Zan sa gidan Yahuda su bar ƙasashensu su ma"
Wannan yana magana ne game da mutane sun zama masu wadata kamar su gini da ake ginawa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan gina su a tsakiyar mutanena" ko "Zan sanya su masu wadata kuma za su zauna tare da mutanena"
Allah yana maganar tilasta mutane su bar ƙasarsu kamar dai su shuke-shuke ne da yake cirowa daga ƙasa. AT: "Ina sanya waɗannan al'ummomin su bar ƙasashensu kuma su koma wurare daban-daban"
1Yahweh yace da ni haka, "Jeka ka sayi lilin na yin ɗamara kuma ka sa shi kewaye da kwankwasonka, amma kar ka sa shi a ruwa da farko"2Saboda haka na sayi ɗamarar kamar yadda Yahweh ya jagorance ni, sai na rataya kewaye da kwankwasona.3Daga nan maganar Yahweh ta zo a gare ni karo na biyu, cewa,4"Ka ɗauki ɗamarar da ka saya wadda ke kewaye da kwankwasonka, ka tashi ka tafi yanzu zuwa Ferat. Ka ɓoye ta nan a ƙogon tsaguwar dutse."5Sai na tafi na ɓoye ta a Ferat, kamar yadda Yahweh ya umarce ni.6Bayan kwanaki da yawa, Yahweh yace mani, "Tashi ka koma Ferat. Ka ɗauki ɗamarar da na ce ka ɗauka daga wurin da ka ɓoye."7Sai na koma Ferat na kuma haƙo ɗamarar a inda na ɓoye ta, kuma duba, ta lalace dukka kuma babu amfani.8Sai maganar Yahweh tazo gare ni, cewa,9Yahweh ya faɗi haka: Ta dai wannan hanyar zan hallakar da gagarumin kumbura kan Yahuda a Yerusalem.10Waɗannan miyagun mutanen da suka ƙi su raurari maganata, waɗanda ke tafiya a cikin taurin zuciyarsu, waɗanda ke bin bayan waɗansu alloli suyi masu sujada suka kuma russuna masu - zasu zama kamar wannan ɗamarar da ba ta da amfani.11gama kamar yadda ɗamarar nan ta ke manne wa ƙwanƙwason wani, haka na maida gidan Isra'ila da dukkan gidan Yahuda su manne mani - wannan furcin Yahweh ne - su zama mutanena, su kawo mani shahara, a ko'ina da yabo, da girmamawa. Amma ba su saurare ni ba.12Saboda haka, dole ka faɗa masu wannan magana, 'Yahweh, Allah na Isra'ila, yace: Za a cika kowanne gora da ruwan inabi.' Zasu ce da kai, "Ashe bamu sani hakika cewa kowanne gora za a cika shi da ruwa ba?'13Sai kace da su, Yahweh ya faɗi haka: Duba, Ina gab da cika dukkan mazaunan wannan ƙasa da buguwa, sarakunan dake zaune a kursiyin Dauda da firistoci da annabawa da mazaunan Yerusalem.14Sa'annan zan sa su kara da junansu, iyaye maza da 'ya'yansu tare - wannan shi ne furcin Yahweh - Ba zan ji tausayinsu ko juyayinsu ba, kuma ba zan kiyaye su daga hallaka ba."'15Ku saurara ku kuma natsu. Kada ku kumbura kai, gama Yahweh yayi magana.16Ku girmama Yahweh Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin kuma yasa ƙafafunku su yi tuntuɓe akan duwatsu da hasken asuba. Gama kuna begen haske, amma zai maishe da wurin duhu baƙƙi ƙirin, zuwa baƙin girgije.17Saboda haka idan ba zaku saurara ba, zan yi kuka ni kaɗai saboda kumbura kanku. idanuwa na zasu yi kuka ƙwarai kuma su zub da hawaye, domin an ɗauke garken Yahweh zuwa bauta.18Kace da sarki da kuma mahaifiyar sarki, 'Ku sauko daga bisa kursiyoyinku, gama rawwunanku masu daraja sun faɗi daga kawunanku.'19Biranen cikin Negeb za a rufe su, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a ɗauke Yahuda zuwa bauta, dukkan ƙasar zuwa bauta.20Ku ta da idanuwanku ku ga waɗanda ke tahowa daga arewa. Ina garken da ya baku, garken dake kyakkyawa a gare ku?21Me zaku ce sa'adda Allah ya naɗa a kanku shugabanin da kuka koyar su zama muhimman aminanku? Ashe ba waɗannan ba ne mafarin zafin azabai da zasu mamaye ku kamar mace mai naƙuda?22Sa'annan zaku iya cewa a zuciyarku, 'Me yasa waɗannan abubuwan suke faruwa da ni?' Zai zama domin yawan zunubanku ne shi yasa an ɗaga ɗantofinku kuma an wulaƙanta ku.23Mutanen Kush zasu iya sake launin fatarsu, ko kuwa damisa zata iya sake dabbare-dabbarenta? Idan haka ne, to ku kanku, duk da dai kun saba da yin mugunta, zaku iya yin nagarta.24Saboda haka zan watsar da su kamar ƙaiƙayi da kan lalace a iskar hamada.25Wannan shi ne abin da na baku, rabon da nayi doka dominku - wannan Furcin Yahweh ne - saboda kun mance da ni kun dogara ga ruɗu.26Saboda haka kuma Ni kaina zan kware ɗantofinku, kuma za a ga tsiraicinku.27Na ga zinarki da haniniyarki, da muguntar karuwancinku akan tuddai da cikin gonaki, na kuma ga waɗannan abubuwa masu ban ƙyama! kaiton ki, Yerusalem! Har tsawon wanne lokaci ne zaki sake wankuwa kuma?"
Karin magana "kalmar Yahweh ta zo ga" ana amfani da ita don gabatar da saƙo na musamman daga Allah. AT: "Yahweh ya sake ba ni sako a karo na biyu. Ya ce" ko "Yahweh ya yi min wannan sakon na biyu:"
Anan Yahuda da Yerusalem suna nufin mutanen da suke zaune a wurin. AT: "na mutanen Yahuda da Yerusalem"
Wannan karin magana ne. AT: "waɗanda ke da taurin kai kuma kawai suke aikata abin da suke so"
"sa dukkan mutanen wannan ƙasa su bugu"
Anan kursiyin da sarkin Yahuda yake zaune an wakilta shi "kursiyin Dauda." AT: "sarakunan da ke zaune a kan gadon sarautar Yahuda" ko "sarakunan al'ummar Yahuda"
Anan kalmomin "kowane mutum" na nuni ga maza da mata. AT: "Bayan haka zan sa mutane su yi faɗa da juna, har iyaye da yara za su yaƙi juna"
"ƙarya imani kansa ya zama mai muhimmanci"
Anan ana ambatar mutum da "ƙafafunsa" don jaddada cewa yana tafiya. AT: "kafin ya sa ku tafiya da faduwa yayin da kuke tafiya"
Sarki da uwar sarauta suna sanya rawanin kamfani don wakiltar matsayin su na sarki da uwar sarauniya. Hakanan, wannan taron bai faru ba tukuna, amma an rubuta shi anan kamar dai ya riga ya faru. Ana iya rubuta wannan a cikin lokaci na gaba. AT: "don ba za ku ƙara zama sarki da uwa ta sarauniya ba, saboda rawaninku, girman ku da ɗaukakarku, za su faɗi"
Wannan yana nufin cewa garuruwan za su kewaye makiya, wadanda ba za su bar kowa ya shiga ko fita daga cikin garuruwan ba. AT: "Za a rufe biranen da ke Negev, kuma ba wanda zai iya shiga cikinsu ko fita daga cikinsu"
Anan kalmar "duba" kalma ce wacce take nufin a kula kuma a san abin da ke faruwa. Hakanan, "Bar idanunku sama" yana wakiltar kallon wani abu. AT: "Ku kula kuma ku lura da waɗanda ke zuwa daga arewa"
An yi wannan tambayar don jaddada cewa sojojin abokan gaba za su kama mutanen Yahuda. An yi wannan tambayar kamar an riga an kama mutanen Yahuda duk da cewa wannan bai faru ba tukuna. Ana iya rubuta tambayar azaman sanarwa kuma a cikin yanayi na gaba. AT: "Na ba ku mutanen Yahuza ku kula da su, kamar kyawawan garken tumaki, amma sojojin abokan gaba za su kama su."
Ana amfani da wannan tambayar don ƙarfafawa cewa mutanen da shugabannin Yahuza suke tsammanin suna zaman lafiya da su za su ci su. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Mutanen da kuka zaci abokanka ne za su ci ku da mulkinku."
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don faɗawa mutane cewa kamun su kawai farkon wahalar da zasu sha. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Waɗannan abubuwan da za ku sha wahala kamar farkon nakuda ne na mata lokacin haihuwa."
Ana amfani da wannan tambayar ne don bayyana misalin wani abu da ba zai yiwu ba. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. Hakanan, kalmar da aka fahimta "iya" ana iya samarda ita a cikin magana ta biyu. AT: "Mutanen Kush ba za su iya canza launin fatar su ba kuma damisa ba za ta iya sauya tabon ta ba."
Wannan bayanin abin ban dariya ne saboda misalai game da Kushiyawa da damisa yanayi ne da ba zai yiwu ba. Wannan yana nuna cewa idan waɗancan abubuwan da basu yiwu ba zasu iya faruwa to zasu iya yin kyau. AT: "Kamar yadda waɗannan abubuwan basa yiwuwa, haka kuma ba zai yuwu ba a gare ku da kuke aikata mugunta koyaushe ku aikata alheri"
"Zan watsar da su kamar ƙaiƙayi wanda iska ke kaɗawa." Yahweh yana cewa zai warwatsa mutanensa a ko'ina cikin duniya kamar yadda iska ke watsuwa.
AT: "Wannan shi ne abin da zai faru da ku"
Wannan yana nufin cewa Yahweh zai sa su ji kunya. Hakan ba ya nufin cewa zai yi musu fyaɗe. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kamar dai ni da kaina zan ƙwace muku rigunanku don kowa ya ga al'aurarku kuma za ku ji kunya"
1Wannan ita ce maganar Yahweh da tazo wurin Irmiya game da fari,2"Bari Yahuda ta yi makoki; bari ƙofofinta su lalace. Suna kuka domin ƙasar; kukansu domin Yerusalem ta hau sama.3Manyansu sun aiki barorinsu su ɗebo ruwa. Da suka je maɓuɓɓuga, sun tarar ba ruwa. Sai dukkansu suka koma ba tare da samun kome ba, sun lulluɓe kawunansu don kunya da ƙasƙanci.4Domin wannan ƙasar ta tsage, domin babu ruwan sama a ƙasar. Manoma sun sha kunya har sun lulluɓe kawunansu.5Ko dama barewa ma a saura ta kan gudu ta bar 'ya'yanta sabuwar haihuwa, don ba ciyawa.6Jakunan jeji sukan tsaya akan huntun sararinsu na haki kamar diloli. Idanuwansu ba sa gani, domin ba abinci."7Ko da yake zunubanmu suna shaida gãba da mu, Yahweh, kayi taimako saboda sunanka. Gama rashin amincinmu yayi yawa; mun yi maka zunubi.8Kai ne begen Isra'ila, mai cetonta a lokacin wahala, ƙaƙa zaka zama kamar baƙo a ƙasar, kamar mai tafiyar yawon buɗe ido wanda ya kwanta a gefen hanya don ya kwana ɗaya?9Ƙaƙa zaka zama kamar jarumin da ya kãsa iya ceton kowa? Duk da haka kana nan a tsakiyarmu, Yahweh, da sunanka ake kiranmu. Kada ka barmu!10Yahweh yace wannan akan waɗannan mutanen: "Tun da suna ƙaunar yawace-yawace, basu iya daina wa ba."11Yahweh ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da laifofinsu ya kuma hukunta zunubansu. Yahweh yace mani, "Kada kayi addu'a domin lafiyar waɗannan mutane.12Ko da sun yi azumi, ba zan saurare kukansu ba, kuma ko da sun mika hadaya ta ƙonawa da hadayar abinci, ba zan karɓe su ba. Amma zan kawo ƙarshensu da takobi, yunwa, da annoba."13Sai na ce, "Ah, Ubangiji Yahweh! Duba!! Annabawa suna gayawa mutane, 'Ba zaku ga takobi ba; babu yunwa domin ku, amma zan baku dawwamammen tsaro a wannan wuri.'"14Yahweh yace mani, "Annabawa suna annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba, ko kuwa in basu wani umarni ko kuma in yi magana da su. Amma ƙarairayi da wahayin ƙarya ne, ƙaryar duba da suke yi marar amfani suna fitowa daga tunaninsu waɗanda suke annabcin ƙarya ne."15Saboda haka ga abin da Yahweh yace, "Akan annabawan da suke yin annabci da sunana amma ba ni ne na aikesu ba - waɗanda suka ce baza a yi takobi ko yunwa ba a ƙasar. Waɗannan annabawa zasu hallaka da takobi da yunwa.16Kuma mutanen da suka yi wa annabci za a jefar dasu waje cikin titunan Yerusalem domin yunwa da takobi, har ma babu wanda zai binne su - su, da matayensu da 'ya'yansu maza da mata - don zan sa muguntarsu a kansu.17Faɗa masu wannan magana: 'Bari idanuna suyi ta zub da hawaye, dare da rana. Kada su daina, saboda akwai babbar aukawar budurwa 'yar mutane na -babban rauni marar warkewa.18Idan na tafi cikin saura, akwai su da yawa da aka kashe da takobi! Idan kuma na shiga cikin birni, akwai cututtukan da yunwa ta kawo. Gama annabi da firist yawace-yawace suke ta yi a ƙasar, kuma basu sani ba.'"19Ka ƙi Yahuda kenan dungum? Kana ƙin Sihiyona ne? Me yasa zaka azabtar da mu sa'adda babu warkarwa domin mu? Muna begen salama, amma ba wani abin kirki - don lokacin warkewa, amma ku gani, sai dai tsoro kaɗai.20Mun yarda, Yahweh, laifofinmu da muguntarmu da ta kakanninmu, gama mun yi maka zunubi.21Kada ka ƙi mu! Saboda darajar sunanka, kada kuma ka ƙasƙantar da darajar kursiyinka. Ka tuna kada kuma ka karya alƙawarinka da mu.22A cikin gumakan al'ummai marasa amfani akwai mai iya sa sammai su bada ruwa? Ba kai kaɗai ba ne, Yahweh Allahnmu, wanda yayi wannan? Mun sa bege a gare ka, gama kai ne mai yin waɗannan abubuwa dukka.
Yahweh, ta bakin annabi Irmiya, yanzun nan yayi magana game da zina da mutane suka yi.
Kalmomin "hawa" kalma ce. AT: "Suna kira da babbar murya cikin addu'a saboda Yerusalem"
Yahweh, ta bakin annabi Irmiya, ya ci gaba da gaya wa mutane game da fari.
Wannan yana nufin cewa babu wata ciyawa da barewar za ta ci. AT: "don babu ciyawar da za su ci"
Anan “sunan” Yahweh yana nufin sunansa. AT: "saboda mutuncin ku" ko "domin kowa ya ga cewa ku manya ne kuma ku cika alkawuran ku"
Wannan wani suna ne na Yahweh. AT: "Kai ne begen Isra'ila"
Wannan yana magana ne game da yiwuwar Yahweh bai iya taimakon mutanensa ba kamar shi jarumi ne mai rikitarwa wanda ya kasa ceton kowa. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Ba ku da komai don taimaka mana, kamar wanda ya yi al'ajabi ko kamar jarumi wanda ba shi da ikon ceton mu."
Irmiya ya yi ta addu'a yana roƙon Yahweh kada ya bar su su kaɗai.
"suna son ɓata daga gare ni." Wannan yana magana ne akan mutane marasa aminci ga Yahweh kuma basa masa biyayya kamar sun ɓace daga wurin da yake.
Anan "takobi" yana wakiltar yaƙi, kuma don "gani" yana wakiltar fuskantarwa. AT: "Ba za ku fuskanci wani yaƙi ba"
Anan ana maganar "tsaro" kamar wani abu ne wanda wani zai iya bawa wani. AT: "Zan baku damar zama cikin aminci" ko "Zan ba ku izinin zama lafiya"
Anan ana magana da "hankali" kamar suna wuri maimakon damar tunanin tunani. AT: "cewa suna tunanin kansu"
Wannan jumlar tana nufin magana da ƙarfi da ikon Yahweh ko a matsayin wakilinsa. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Irmiya 14:14.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Wannan yana nufin cewa dukkan iyalai za su mutu kuma mutane za su jefa gawawwakin su a kan tituna maimakon binne su. AT: "Sannan mutanen da suka yi musu annabci za su mutu da yunwa da takobi kuma mutane za su jefa gawawwakinsu a titunan Yerusalem"
yanke ko karyewar fata wacce baza ta iya warkewa ba
1Sai Yahweh yace da ni, "Ko da Musa ko Sama'ila zasu tsaya a gabana, duk da haka ba zan nuna wa waɗannan mutanen tagomashi ba. Ka kore su daga gabana, don su yi tafiyarsu.2Zaya zama sa'ad da suka ce da kai, 'Ina zamu tafi?' Sai ka faɗa masu, Yahweh ya faɗi wannan: Waɗanda an ƙaddara su mutu su tafi ga mutuwa; waɗanda suke na takobi su tafi ga takobi. Waɗanda suke na yunwa su tafi ga yunwa; kuma waɗanda suke na bauta su tafi ga bauta.'3Zansa su kasance kashi huɗu - wannan furcin Yahweh ne - takobi na kisan wasu ne, karnuka su yayyaga wasu, tsutsaye sararin sama da dabbobin duniya don su cinye su kuma hallakar da wasu.4Zan kuma sa su zama abin banƙyama ga dukkan mulkokin duniya, saboda abin da Manassa ɗan Hezekiya, sarkin Yahuda, ya aikata a Yerusalem.5Amma wa zai ji tausayinki, Yerusalem? Wa zai yi baƙinciki domin ki?6Kun yashe ni - wannan furcin Yahweh ne - kun koma baya daga gare ni. Saboda haka zan buge ku da hannuna in kuma hallaka ku. Ni na gaji da nuna maku jinƙai.7Saboda haka zan sheƙe su da abin shiƙa a ƙofofin garuruwan ƙasar. Zansa su makoki. Zan hallaka mutanena tun da ba zasu juyo daga mugayen hanyoyinsu ba.8Zan yawaita gwaurayensu fiye da yashi a bakin teku. Game da uwayen samari zan aika da hallakarwa da tsakar rana. Zan sa azaba da razana su auko masu farat ɗaya.9Uwar da ta haifi 'ya'ya baƙwai zata yi yaushi ta suma. Faɗuwar ranarta zata zo tun da rana. Zata ji kunya da wulaƙanci, don zan bada waɗanda suka ragu ga takobi a gaban abokan gãbarsu -wannan furcin Yahweh ne."10Kaito na, mahaifiyata! Domin ke kika haife ni, ni ne mutum mai jayayya da gardama cikin dukkan ƙasar. Ban bada rance ba, ko wani ya bani rance, duk da haka dukkansu suna zagina.11Yahweh yace: "Ba zan ceto ka domin alheri ba? Babu shakka zansa abokan gãbarka su roƙi taimako a lokacin bala'i da masifa.12Wani zai iya karya ƙarfe? Musamman ƙarfe daga arewa wanda aka haɗa da tagulla?13Zan bada wadatarku da dukiyarku ganima kyauta ga abokan gãbarku. Zan yi wannan saboda dukkan zunubanku da kuka aikata a dukkan iyakarku.14Zansa ku bautawa abokan gãbarku a cikin ƙasar da ba ku sani ba, gama wuta zata kama, zata kunnu a cikin fushina gãba da ku."15Yahweh, ka sani! Ka tuna da ni ka kuma taimake ni. Ka kawo mani fansa ka kuma sãka wa waɗanda suke tsananta mani. Kai mai haƙuri ne, amma kada ka bar su su tafi da ni; ka sani na sha wahala saboda kai.16An sami magangaanunka, na kuwa cinyesu. Maganganunka sun zamar mani abin murna da farincikin zuciyata, gama ana kira na da sunanka, Yahweh, Allah mai runduna.17Ban zauna cikin ƙungiyar waɗanda suke annashuwa ko murna ba. Na zauna ni kaɗai saboda hannunka mai iko, gama ka sa na cika da haushi.18Me yasa azabata ta ƙi ƙarewa kuma raunukana ba sa warkewa? Zaka yaudare ni kamar ruwaye, ruwaye masu ƙafewa?19Domin wannan ga abin da Yahweh yace, "Idan ka tuba, Irmiya, sai in komo da kai, sa'annan zaka tsaya a gabana ka kuma bauta mani. Gama idan ka ware abubuwan dake banza daga abubuwa masu daraja, zaka zama kamar bakina. Sai mutanen su dawo wurinka, amma kai ba zaka koma wurinsu ba.20Zan maishe ka kamar garun tagulla da ba za a iya hudawa ba ga waɗannan mutane, zasu yi yaƙi da kai. Amma ba zasu yi nasara a kanka ba, gama ina tare da kai don in cece ka kuma in kuɓutar da kai -wannan furcin Yahweh ne -21gama zan kuɓutar da kai daga hannun mugaye kuma zan fanshe ka daga hannun marasa tausayi."
Yahweh ya maimaita wannan ra'ayin na korar mutanensa don ƙara ƙarfafa shi.
Manassa mugun sarki ne wanda ya aikata mugunta da yawa a Yerusalem. AT: "saboda muguntar abubuwan da Manassa ... ya aikata a Yerusalem"
Yahweh yayi amfani da wannan tambaya ta zance don jaddada cewa babu wanda ya isa ya yi makoki domin Yerusalem. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Babu wanda ya isa ya tausaya muku, Yerusalem. Babu wanda ya isa ya yi baƙin ciki saboda halakar ku."
Waɗannan jimlolin guda biyu ma'anar abu ɗaya ne kuma suna ƙarfafa cewa mutane, hakika, sun rabu da Yahweh.
"fiye da hatsin yashi a bakin teku." Wannan kwatancen ƙari ne da aka yi amfani dashi don jaddada lambar da ba za a iya lissafawa ba. AT: "fiye da yadda zaku iya kirgawa"
Kalmomin "kunya" da "jin kunya" ma'anarsu abu ɗaya ne kuma suna ƙarfafa tsananin kunyar. AT: "Zata ji kunya gaba daya"
Irmiya ya yi kamar ya yi magana da mahaifiyarsa a matsayin wata hanya don jaddada yadda yake baƙin ciki.
Amsar a fakaice ga wannan tambaya ta magana ita ce "eh." Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Lallai zan cece ku har abada!"
Anan kalmomin "bala'i" da "damuwa" ma'anarsu abu ɗaya ne. Suna nanata yawa ko tsananin bala'in. AT: "a lokacin babban masifa"
Kalmar "dukiya" ma'anarsu ɗaya ce kuma tana nufin duk wani abu da mutane suke ɗauka da tamani.
"zuwa ƙasar da baƙon ku"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Na ji sakonka"
Irmiya yana rokon Yahweh kada ya haƙura da zunuban maƙiyansa. Jumlar "ɗauke ni" tana nufin an kashe shi. AT: "Da fatan kar ku ci gaba da haƙuri da su kuma ku ƙyale su su kashe ni"
"mutane sun san cewa ina bauta muku"
Irmiya ya yi amfani da wannan tambaya ta zance don ya jaddada ciwo. Yana maganar ciwon nasa kamar dai rauni ne na zahiri. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Ciwo na yana ci gaba, yana kama da rauni wanda ba zai warke ba."
Irmiya ya yi amfani da wannan tambaya ta zance don jaddada cewa yana jin kamar ba zai iya dogaro da Yahweh ba. Yana magana game da wannan kamar dai Yahweh rafi ne wanda ya kafe. AT: "Yana jin kamar ba za ku iya dogaro da ni ba, kamar rafin da zan je neman abin sha sai kawai in ga ya bushe."
An kwatanta Irmiya da bakin Yahweh domin za a yi amfani da shi wajen faɗin saƙon Yahweh. AT: "za ku yi magana a madadin ni"
Wannan yana magana ne game da mutanen da suke yaƙi da Irmiya kamar dai rundunar sojoji ce da suka yaƙi. AT: "za su yi yaƙi da ku" ko "za su yi adawa da ku"
1Sai maganar Yahweh tazo gare ni, cewa,2"Kada ka auri mata domin kanka, kuma kada ka sami 'ya'ya maza da 'ya'ya mata domin kanka a wannan wuri.3Gama Yahweh yace waɗannan 'ya'ya maza da mata waɗanda za a haifa a wannan wuri, da kuma iyayensu mata waɗanda zasu haife su, da iyayensu maza da zasu sa a haife su a wannan ƙasa,4'Zasu mutu da muguwar cuta. Baza a yi makoki ko a bisne su ba. Zasu zama kamar juji a ƙasa. Gama ƙarshe zai kasance ta wurin takobi da yunwa, kuma gawarwakinsu zasu zama abincin tsuntsayen sararin sama da nanamomin ƙasar.'5Gama maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa, 'Kada ka shiga gidan da ake makoki. Kada kayi makoki ko ka nuna damuwa dominsu, gama na ɗauke salamata daga waɗannan mutanen, da ƙaunata da jinƙaina - wannan furcin Yahweh ne.6Babba da yaro zasu mutu a wannan ƙasa. Baza a bizne su ba kuma ba wanda zai yi makoki domin su ko su tsattsage jikinsu ko su aske kansu ƙwal domin su.7Tilas kada wani ya raba abinci a cikin makoki don ya ta'azantar da su saboda matattu, tilas kuma kada wani ya bada ƙoƙon ta'aziya ga mahaifinsa ko mahaifiyarsa don ya ta'azantar da su.8Tilas kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ka ci ka sha tare da su.'9Gama Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, 'Duba, a gaban idanunka, da zamaninka a kuma wannan wuri, na kusa kawo ƙarshen muryar murna da muryar farinciki, data ango data amarya.'10Zai kasance idan ka bayyana dukkan waɗannan maganganu ga waɗannan mutane, zasu kuwa ce maka, 'Me yasa Yahweh ya furta dukkan wannan babbar masifa a kanmu? Mene ne laifinmu da zunubin da muka yi wa Yahweh Allahnmu?'11Sai kace da su, 'Domin kakanninku sun rabu da ni - wannan furcin Yahweh ne - sun bi wasu alloli har sun bauta masu sun kuma sunkuya sun yi masu sujada. Sun rabu da ni, kuma basu kiyayye dokokina ba.12Gama ku kuma kun kawo mugunta fiye da ta kakanninku, ku gani, kowannenku yana tafiyar taurinkai da mugun nufi a zuciyarsa; ba wanda yake saurare na.13Saboda haka zan jefar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasa wadda ku ko kakanninku baku sani ba, a can zaku bauta wa wasu alloli dare da rana, gama ba zan nuna maku wani tagomashi ba.'14Saboda haka, duba, kwanaki suna zuwa - wannan furcin Yahweh ne - da baza a ƙara cewa, 'Na rantse da ran Yahweh, wanda ya fito da mutanen Isra'ila daga ƙasar Masar ba.'15amma, 'Na rantse da ran Yahweh, wanda ya fito da mutanen Isra'ila daga ƙasar arewa kuma daga ƙasashen da ya warwatsa su.' Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba kakanninsu.16Duba!! Zan aika domin masunta da yawa - wannan furcin Yahweh ne - zasu kuwa kama mutane su fitar waje. Bayan wannan zan aika domin mafarauta da yawa don su farauto su daga dukkan tsaunuka da tuddai, da cikin kogunan dutse.17Gama idona yana dukkan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke ba a gare ni. Muguntarsu kuma ba a ɓoye take ba daga idanuwana.18Zan fara saka masu ruɓi biyu domin laifinsu da zunubi domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun siffofin gunkinsu, kuma domin sun cika gãdona da gumakansu na banƙyama."19Yahweh, kai ne kagarata da mafakata, wurin tsarona a ranar wahala. Al'ummai zasu zo gunka daga ƙurewar duniya za a kuma ce, "Babu shakka kakanninmu sun gãji yaudara. Su fanko ne; babu riba a cikinsu.20Mutane zasu iya yiwa kansu alloli?' amma su ba alloli ba ne."21Saboda haka duba!! Zansa su sani a wannan lokacin, zansa su san hannuna da ikona, don haka zasu sani cewa sunana Yahweh ne.
'Ya'yan da aka haifa a ƙasar ana kwatanta su da taki a ƙasa don a nuna cewa za su zama abin ƙyama kuma babu wanda zai binne su. Dubi yadda kuka fassara wata magana makamancin wannan a cikin Irmiya 8: 2.
Jumlar "zo ga ƙarshe" hanya ce mai taushi da za a ce za su mutu. Kalmar "takobi" tana wakiltar rundunar da sojoji ke yaƙi da takuba. Yankin yana wakiltar mutuwa a yaƙi. AT: "za su mutu a yaƙi ko yunwa"
Wannan yana nufin kowane irin mutane kuma yana amfani da girma don nuni zuwa ga mahimmancin su. AT: "Da mahimmancin da maras muhimmanci" ko "Mutane da yawa, ko da kuwa yaya mahimmancin su suke,"
Yankan kai da aske kai ayyuka ne na alama da ke nuna tsananin baƙin ciki, musamman ma lokacin da wani da muke ƙauna ya mutu.
Waɗannan jimloli guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. Allah ya faɗi abu iri ɗaya sau biyu don ƙarfafawa. Al’ada ce ta kai abinci ko ruwan inabi ga mutanen da danginsu suka mutu. Yahweh ya cire kowane jin daɗi daga mutane saboda zunubansu.
Wannan yana nufin mutane suna yin biki a bukukuwan aura.
Kalmomin "sunkuyar da kai ga" yana nufin ainihin abu iri ɗaya ne da "bauta" kuma yana bayyana matsayin da mutane suke amfani da shi wajen bauta. Allah ya faɗi ainihin abu ɗaya sau biyu don ƙarfafawa.
Yahweh yana maganar ayyukan mutum kamar mutum yana tafiya akan hanya. Anan kalmar "zuciya" tana wakiltar tunani ko so. AT: "taurin kai yana aikata mugayen abubuwa da yake son aikatawa"
Yahweh yayi magana akan fitar da mutane da karfi daga ƙasar kamar yana jefa su daga ƙasar. AT: "tilasta ku ku bar wannan ƙasar ku tafi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da mutane ba za su ƙara cewa"
Anan kalmar "ido" tana wakiltar Yahweh wanda yake ganin duk abin da suke yi. AT: "Ina kallon duk abin da suke yi"
A nan kalmar "su" na iya nufin ko dai ga mutane ko kuma ayyukansu. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba za su iya ɓoye mini ba" ko "ba za su iya ɓoye mini hanyoyi ba"
Anan kalmar "idanu" tana wakiltar Yahweh wanda yake gani. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba za su iya ɓoye mini muguntarsu ba"
Anan kalmar "kasashe" tana wakiltar mutane daga al'ummu. AT: "Mutane daga al'ummomi za su je wurinku" ko "Mutanen al'ummomi za su zo wurinku"
A nan kalmar "yaudara" tana nufin gumakan ƙarya. AT: "kakanninmu ba su gaji komai ba sai gumakan ƙarya"
A nan kalmomin "Su" da "su" suna nuni ne ga gumakan ƙarya waɗanda kakanni suka koyar da su suyi imani da shi. Kalmomin biyu suna nufin ainihin abu ɗaya, tare da na biyu yana bayanin yadda suke "wofi ne."
Mutanen suna yin wannan tambayar ta lafazin ne don jaddada cewa mutane ba za su iya yin allah da kansu ba. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Mutane ba za su iya yin gumaka da kansu ba. Abubuwan da suke yi ba alloli ba ne"
1"Zunubin Yahuda a rubuce yake da alƙalamin ƙarfe mai bakin lu'u-lu'u. An zana shi a allon zuciyarsu da ƙahon bagadinku.2Har 'ya'yansu masu na tunawa da bagadansu da sandunan Ashtarot ɗinsu a gindin itatuwa shimfiɗe akan kuma tuddai masu tsayi.3Dutsena a buɗaɗɗiyar ƙasar, dukiyarku da dukkan wadatarku zan bada su ganima, tare da wuraren tsaunukanku, saboda zunubin da kuka aikata a dukkan ƙasashen.4Zaku rasa gãdon da na baku. Zansa ku bautawa abokan gãbarku a ƙasar da baku sani ba, gama kun kunna wuta cikin fushina, wadda zata yi ta ci har abada."5Yahweh yace, "Mutumin dake dogara ga ɗan adam la'ananne ne; wanda ya maida jiki ƙarfinsa wanda ya juya zuciyarsa daga Yahweh.6Gama zai zama kamar ƙaramin jeji a Hamada ba kuma zai ga wani abu mai kyau yana zuwa ba. Zai zauna a wurare masu duwatsu a cikin daji, ƙeƙasarshiyar ƙasar da ba mazauna.7Amma mai albarka ne mutumin da yake dogara ga Yahweh, gama Yahweh ne dalilin madogararsa.8Domin yana kamar itacen da aka dasa gefen rafi, wanda saiwoyinsa suka bazu zuwa cikin rafin. Ba zai ji tsoron zafi ba a duk lokacin da yazo, domin kullum ganyensa kore ne. Ba zai da mu da shekarar fari ba, ba kuma zai fasa yin 'ya'ya ba.9Zuciya ta fi kome rikici. Cuta gare ta matuka; wa zai iya gane ta?10Ni ne Yahweh, wanda yake binciken tunani, wanda yake gwada zukata. Ina ba kowane mutum gwargwadon al'amuransa, da kuma gwargwadon ayyukansa.11Makwarwar da ta ƙwanta kan ƙwan da ba ita ta saka ba. Mutum zai iya zama mai arzaƙi ta rashin gaskiya, amma lokacin da yayi rabin shekarunsa sun yi, wannan arzaƙin zai bar shi, a ƙarshe zai zama wawa."12"Wurin haikalinmu kursiyi ne mai daraja, an ɗaukaka shi tun daga farko.13Yahweh shi ne begen Isra'ila. Dukkan waɗanda suka rabu da kai zasu ji kunya. Waɗanda suke cikin ƙasar waɗanda suka juya daga gare ka za a rubuta su akan ƙura. Domin sun rabu da Yahweh, maɓuɓɓugar ruwan rai.14Warkar da ni, Yahweh, zan kuwa warke! Ka cece ni, zan kuwa cetu. Gama kai ne waƙar yabona.15Duba!, suna ce mani, 'Ina maganar Yahweh take? Tazo mana!'16Amma ni, ban gudu daga zama makiyayi da yake binka ba. Ban kuma so zuwan ranar bala'i ba. Ka kuwa san abin da ya fito daga leɓunana. An yi su a gabanka.17Kada ka zamar mani abin ban razana. Kai ne mafakata a ranar masifa.18Bari waɗanda suke runtumata su kunyata, amma kada ka barni in kunyata. Bari su karaya, amma kada ka bar ni in karaya. Ka aika masu da ranar masifa gãba da suka kuma rugurkujesu da hallaka riɓi biyu."19Yahweh ya faɗa mani wannan: "Ka tafi ka tsaya a ƙofar jama'a wadda sarakunan Yahuda suke shiga da fita ta cikinta, ka kuma tafi dukkan ƙofofin Yerusalem.20Ka ce da su, 'Ku ji maganar Yahweh, ku sarakunan Yahuda da dukkan ku mutanen Yahuda, da kowanne mazaunin Yerusalem waɗanda ke shiga ta waɗannan ƙofofi.21Yahweh ya faɗi wannan: "Kuyi hankali saboda rayukanku kada ku kuma ɗauki kaya a ranar Asabar ku kawo su ta ƙofofin Yerusalem.22Kada ku kawo kaya daga gidajen ku a ranar Asabar. Kada ku yi kowanne irin aiki, sai dai ku kiyaye ranar Asabar da tsarki, kamar yadda na umarce kakanninku su yi.'"23Basu saurara ba ko su mai da hankali, amma suka taurare wuyansu don kada su ji ni ko su karɓi horaswa.24Zai kasance idan dai kun saurare ni - wannan furcin Yahweh ne - kada ku kawo kaya ta ƙofofin wannan birni a ranar Asabar amma maimako ku tsarkake ranar Asabar ta Yahweh kada kuma ku yi kowanne irin aiki a cikinta,25sa'an nan ne sarakuna, da 'ya'yan sarakuna, da waɗanda ke zaune akan kursiyin Dauda za su shiga ta ƙofofin wannan birni su na hawan karusai da dawakai, su da shugabaninsu, da mutanen Yahuda da mazauna Yerusalem, wannan birni kuma za a zauna cikinsa har abada.26Zasu zo daga biranen Yahuda daga kuma dukkan kewayen Yerusalem, daga ƙasar Benyamin da ta kwarurruka, daga duwatsu, da ta Negeb, suna kawo baye-bayen na ƙonawa da hadayu, baye-bayen hatsi da na turare, baye-bayen godiya ga gidan Yahweh.27Amma idan baku saurare ni ba - ku kiyaye ranar Asabar ba kuma ku ka ɗauki kaya masu nauyi kuka shiga ta ƙofofin Yerusalem a ranar Asabar ba - sai in cinna wa ƙofofin wuta, zata kuwa cinye tsararrun wurare na Yerusalem, ba kuwa zata kasu ba."
Yahweh yayi magana akan zunuban Yahuda suna da girma don haka ba zasu iya daina aikata su ba kamar wani ya sassaka zunubansu har abada.
Ana magana game da ɗabi'ar zunubin mutane kamar dai an zana zunubansu a cikin zukatansu. Kalmar "zukata" tana nufin mutum duka: tunaninsu, motsin zuciyar su, da ayyukan su. AT: "an zana shi a cikin halittunsu"
Kalmomin "dukiya" ma'anarsu ɗaya ce kuma tana nufin duk wani abu da suke ɗauka da muhimmanci.
Yahweh yayi magana game da ƙasar kamar gadon da ya ba mutanen Yahuda a matsayin mallaka ta har abada. AT: "Za ku rasa ƙasar da na ba ku a matsayin gado"
Yahweh yayi magana akan zafin fushinsa kamar fushin sa wuta ce da take cin wuta ga waɗanda yake fushi da su. AT: "Kun fusata ni da fushin na zai zama kamar wuta ce da za ta ƙone har abada"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan la'ance duk mutumin da ya dogara ga ɗan adam"
A nan kalmar “nama” tana wakiltar mutane. AT: "ya dogara ga mutane ne kawai don ƙarfi"
Anan kalmar "zuciya" tana nufin tunani da motsin rai. AT: "yana juyar da ibadarsa ga Yahweh"
Mutumin da ya dogara ga Yahweh zai ci gaba koyaushe, kamar bishiya yayin da aka dasa ta a rafin kogi. Ba ya shafar lokacin da babu ruwan sama. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "zai zama kamar itacen da wani ya shuka ta ruwa"
Yahweh yayi magana akan itace wanda yake debo ruwansa daga rafi wanda zafin rana da fari basu shafeshi ba kamar itace bashi da tsoron wadannan abubuwa. AT: "Zafin ba zai shafe shi ba idan ya zo ... Ba a cutar da shi a cikin shekara ta fari"
Anan kalmar "zuciya" tana nufin tunani da tunanin mutane. AT: "Hankalin ɗan adam ya fi yaudara"
Mai magana yayi amfani da wannan tambaya ta zance don jaddada cewa babu wanda zai iya fahimtar zuciyar mutum. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "ba wanda zai iya fahimtarsa."
Ana maganar wadata kamar su bayin da za su watsar da mai gidansu. AT: "zai rasa dukiyarsa"
Irmiya yayi maganar haikalin kasancewa “kursiyi mai ɗaukaka” domin a can ne Yahweh yake zaune kuma yake mulki.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "za ku rubuta waɗanda ke biyunku a cikin ƙasa waɗanda suka juya muku baya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "da gaske kun warkar da ni ... da gaske za ku cece ni"
Mutanen sun yi amfani da wannan tambayar don su yi wa Irmiya ba'a domin abubuwan da ya faɗa ba su faru ba tukuna. Hakanan za'a iya fassara shi azaman bayani. AT: "Ina abubuwan da Yahweh ya gaya muku za su faru?" ko "Abubuwan da Yahweh ya gaya muku za su faru ba su faru ba."
Irmiya yayi maganar shugabanci da kulawa da mutane kamar shi makiyayi ne mai kulawa da tumaki. Yana magana ne game da barin wannan aikin kamar yana guje masa.
A nan kalmar “leɓɓa” na wakiltar Irmiya wanda ya yi magana. Kalmar "shela" ana iya fassara ta da kalma ta magana. AT: "sanarwar da na yi magana" ko "abubuwan da na shelanta"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ku kawo kunya ga masu bibiyar ni, amma kada ku kawo min kunya"
Wannan jimlar tana nufin abu ɗaya ne kamar na baya kuma yana ƙara ƙarfafa addu'ar Irmiya. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ka sa su ji tsoro, amma kada ka tsoratar da ni"
"don kare rayukanku"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa mutane sun ƙi saurara. AT: "Sun ƙi saurara" ko "Sun ƙi yin biyayya"
Anan kursiyin da sarkin Yahuda yake zaune an wakilta shi "kursiyin Dauda." Madadin fassara: "waɗanda ke zaune a kan gadon sarautar Yahuda" ko "sarakunan ƙasar Yahuda"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane za su zauna a wannan birni har abada"
"Zan sanya ƙofofin Yerusalem wuta"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane ba za su iya fitar da shi ba"
1Maganar da ta zo ga Irmiya daga Yahweh, cewa,2"Tashi ka tafi gidan maginin tukwane, domin a can zaka ji maganata.3Sai na gangara zuwa gidan maginin tukwanen, duba yana aikin tukwane akan na'urar ginin tukwanen.4Amma abin da yake mulmulawa da yunɓu ya lalace a hannunsa, sai ya canja tunaninsa ya sake wani abu dabam wanda yake gani yana da kyau a idanunsa.5Sa'annan maganar Yahweh tazo gare ni, cewa,6"Ba zan iya yin haka da ku ba kamar wannan maginin tukwanen, gidan Isra'ila? -wannan furcin Yahweh ne. Duba! Kamar yadda yumɓu yake a hannun maginin tukwane - haka nan kuke a hannuna, gidan Israi'la.7A lokaci ɗaya, zan iya yin shela wani abu akan al'umma ko mulki, cewa zan kora ta, in kakkaryata, ko hallaka ta.8Amma idan al'umma wadda na yi magana a kanta ta juyo daga muguntarta, sai in janye masifar da nayi niyyar kawo mata.9A wani lokaci, zan iya yin shelar wani abu akan wata al'umma ko mulki, cewa zan gina ko in kafa ta.10Amma idan ta aikata mugunta a idanuna ta wurin rashin sauraron muryata, daga nan zan janye abu mai kyau da na ce zan yi domin su.11To yanzu, yi magana da jama'ar Yahuda da mazaunan Yerusalem ka ce, 'Yahweh ya faɗi wannan: Duba, ina gab da shirya masifa gãba da ku. Ina gab da tsara wata dabara gãba da ku. Ku tuba, kowanne mutum daga muguwar hanyarsa, da haka hanyoyinku da ayyukanku zasu kawo maku alheri.12Amma zasu ce, 'Wannan bashi da amfani. Zamu yi kamar yadda muka tsara. Kowanne ɗayan mu zai yi bisa ga muguntarsa, da tattaurar zuciyarsa take marmari.'13Saboda haka Yahweh ya faɗi wannan, 'Tambayi al'ummai, wane ne ya taɓa jin irin wannan? Budurwa Isra'ila ta yi mugun abu ƙwarai.14Dusar ƙanƙara Lebanon ta taɓa rabuwa da tsaunuka a gefenta? Ko rafuffukan duwatsu masu gangarowa daga nesa sun taɓa lalacewa, waɗannan rafuffuka masu sanyi?15Duk da haka mutanena sun manta da ni. Suna baye-baye ga gumaka marasa amfani waɗanda aka sasu tuntuɓe a cikin tafarkunsu; sun bar tsofaffin tafarku don suyi tafiya a tafarku masu sauƙi.16Ƙasarsu zata zama abar banƙyama, ta zama abin tsaki har abada. Duk wanda ya wuce ta wurin zai razana ya kuma kaɗa kansa.17Zan warwatsa su gaban maƙiyansu kamar iskar gabas. Zan nuna masu bayana, amma ba fuskata ba, a ranar masifarsu.'"18Sai mutanen suka ce, "Kuzo, mu shirya maƙarƙashiya akan Irmiya, tun da yake shari'a bata lalace daga wurin firist ba, ko shawara daga mutane masu hikima ba, ko maganganu daga annabawa ba. Kuzo, mu kai ƙararsa ta wurin maganarmu kada mu yarda ko mu kula da duk wani abin da zai faɗa."19Ka saurare ni, Yahweh, ka saurari murya abokan gãbata.20Lallai ne masifa daga gare su ta zama ladana don yin abin kirki gare su? Duk da haka sun gina rami domina. Ka tuna yadda na tsaya a gabanka na yi magana akan lafiyarsu, da zai sa a janye fushinka daga gare su.21Saboda haka ka miƙa 'ya'yansu ga yunwa, ka kuma bashe su a hannun masu amfani da takobi. Bari matansu su zama masu makoki da gwauraye, mazajensu a kashe su, samarinsu a kashe su da takobi a yaƙi.22Bari a ji kururuwa daga gidajensu, don maharan da ka aika masu farat ɗaya. Gama sun haƙa rami don su kama ni sun kuma kafa wa ƙafafuna tarkuna.23Amma kai, Yahweh, ka san dukkan maƙarshiyarsu a kaina don su kashe ni. Kada ka gafarta masu muguntarsu da zunubansu. Kada kuma ka shafe zunubansu daga gabanka. A maimakon haka, bari a jefar da su a gabanka. Ka yi gãba dasu a lokacin fushinka.
"bitar mai ginin tukwane." Tukwane shine mutumin da yake yin tukwane daga yumɓu.
Kalmar nan "lalace" tana nufin wani abu game da tukunya ya sa maginin tukwane bai ji daɗi ba. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "tukunyar da maginin tukwane yake yi da hannayensa ba mai kyau ba"
Gwanin maginin tukwanen ƙaramin tebur ne da ke jujjuyawa. Wani maginin tukwane yana amfani da shi wajen yin tukwane.
Da wannan tambayar, Yahweh ya jaddada ikonsa na yin abin da ya ga dama da Isra'ila. AT: "An bani izinin yin aiki a kanku, ya jama'ar Isra'ila, kamar yadda maginin tukwane yake yi da yumɓu."
Yahweh yana kwatanta ikonsa na sake Isra’ila kamar yadda ya ga ya dace da yadda maginin tukwane yake iya sake yin yumɓu kamar yadda ya ga dama.
Wadannan maganganun guda biyu suna da ma'ana iri daya. A cikin magana ta farko, Yahweh yayi maganar lalata mulkin kamar masarautar shuka ce ko gini da zai rushe.
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Yahweh yayi maganar karfafa masarautu kamar gini ne da zai gina, da kuma cewa shuke-shuke ne wadanda zai shuka.
Anan kalmar "murya" tana wakiltar kalmomin da Yahweh yake faɗa. Anan, "rashin sauraro" karin magana ne wanda yake nufin basa biyayya. AT: "rashin yin biyayya ga abin da na fada"
Yahweh yayi magana akan tsara bala'i kamar dai masifa wani abu ne wanda ya samar, kamar maginin tukwane zai zama yumbu. Jumla ta biyu ta maimaita irin ra'ayin kamar na farkon ta amfani da kalmomi daban-daban. AT: "Ina gab da tsara wata dabara da zan kawo muku bala'i"
Kalmomin “hanyoyi” da “ayyuka” duka suna nuni ne ga ayyukan mutum da kuma salon rayuwar sa gaba ɗaya. AT: "saboda haka ayyukanku za su haifar muku da alheri"
Anan kalmar “zuciya” tana wakiltar tunanin mutum ko nufinsa. AT: "abin da muguntarsa, taurin kansa yake so" ko "duk abin da mugayen abubuwan da muke so da taurin kai muke son yi"
Anan kalmar "kasashe" tana wakiltar mutane a cikin al'ummu. Yahweh ya yi wannan tambayar don ya tsauta wa mutanen Yahuda. AT: "Ka tambayi al'ummomin idan ɗayansu ya taɓa jin labarin irin wannan." ko "Babu wani wuri a duniya da wani ya taɓa jin irin wannan abu."
Ya zama gama gari a koma ga al'ummomi kamar suna mata. Yahweh yayi magana game da Isra'ila tsarkakakku kuma masu aminci a gare shi kamar ita budurwa ce kuma Isra'ilawa sun ci amanarsa kamar tana "aikata mummunan aiki." AT: "Isra'ila, wacce kamar budurwa ce, ta aikata wani abin ban tsoro"
Yahweh yayi wannan tambaya don jaddada cewa rafuffukan tsaunuka basa daina gudana. Yayi maganar koramu sun bushe kamar sun lalace. AT: "Waɗannan kogunan sanyi masu sanyi waɗanda suka zo daga nesa nesa ba sa daina gudana."
Yahweh yana maganar salon rayuwar mutum kamar wata hanya ce da yake tafiya, da kuma rayuwa rashin aminci a gare shi kamar dai mutumin ya yi tuntuɓe ne a kan hanyar. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wannan ya sa suka yi tuntuɓe a hanyoyinsu" ko "yana kama da sun yi tuntuɓe yayin tafiya a kan hanya"
Yahweh yayi magana akan sa mutane su gudu a gaban abokan gabansu kamar dai shi ne iskar gabas mai watsa ƙura da tarkace. AT: "Zan kasance kamar iskar gabas in warwatsa su a gaban abokan gabansu" ko "Zan watsa su a gaban abokan gabansu kamar yadda iskar gabas take watsa ƙura da tarkace"
"Zan juya wa su baya, ba fuskata ba." Juya baya ga wani aiki ne na alama wanda ke wakiltar ƙin yarda da juya fuska ga wani aiki ne na alama wanda ke wakiltar ni'ima. AT: "Zan ƙi su kuma ba zan yi musu alheri ba"
Ana iya samar da kalmomin "ba zai taɓa halaka ba" ga ɗayan waɗannan jumlolin. Hakanan za'a iya bayyana wannan ta hanyar tabbatacce. AT: "doka ba za ta taɓa halaka daga firistoci ba, kuma shawara ba za ta taɓa halaka daga masu hikima ba, kuma kalmomi ba za su taɓa halaka daga annabawa ba" ko "firistoci koyaushe suna da doka, masu hikima koyaushe za su ba da shawara, kuma annabawa koyaushe za su yi magana "
Mutanen suna magana akan yin maganganu masu cutarwa game da Irmiya kamar maganganunsu makami ne da suke kai masa hari. AT: "faɗi abin da zai cutar da shi"
Irmiya yayi wannan tambayar don ya jaddada cewa kyawawan ayyuka bai kamata a saka musu da abubuwa marasa kyau ba. AT: "Bala'i daga garesu bai kamata ya zama ladana na kyautatawa gare su ba."
Anan kalmar "hannaye" tana wakiltar iko. AT: "sa waɗanda suke amfani da takobi su mallake su" ko "sa su mutu a yaƙi"
Ana iya samar da kalmar daga jimlar da ta gabata. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "bari mutane su kashe samarinsu da takuba a wajen yaƙi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "bari mutane su kifar da su a gabanku"
1Yahweh ya faɗi wannan, "Tafi ka sayo tulun yumɓu a wurin maginin tukwane sa'ad da kana tare da dattawan mutane da kuma firistoci.2Sai ku tafi Kwarin Ben Hinnom na ƙofar Kasko, a wurin zaka yi shelar maganar da zan faɗa maka.3Ka ce, 'Ku ji maganar Yahweh, sarakunan Yahuda da mazaunan Yerusalem! Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, "Ku gani, na kusa kawo masifa akan wannan wuri, duk kuma kunuwan kowanne da zai ji zai karkaɗa.4Zan yi wannan domin mutanen sun rabu da ni sun ƙazantar da wannan wuri. A wannan wuri sun miƙa hadayu ga wasu alloli da basu san su ba. Kakaninsu, da sarakunan Yahuda sun cika wannan wuri da jinin marasa laifi.5Sun ginawa Ba'al bagadi don su ƙona 'ya'yansu maza a matsayin baye-bayen ƙonawa gare shi - abin da ban umarta ba, ko in furta, ban ma yi tunanin haka ba.6Saboda haka, ku gani, rana tana zuwa - wannan furcin Yahweh ne - wadda wannan wuri baza a ƙara kiransa Tofet, Kwarin Ben Hinnom ba, domin zai zama Kwarin Yanka.7A wannan wuri zan wofinta shirin Yahuda da na Yerusalem. Zansa a kashe su da takobi a gaban abokan gãbarsu ta hannun waɗanda suke neman ransu. Sa'annan zan ba da gawawwakinsu su zama abincin tsutsayen sammai da na namomin jeji.8Zan mai da wannan birni kango da kuma abin tsaki, domin duk wanda ya wuce wurin zai yi mamaki da tsaki, akan dukkan annobar.9Zansa su ci naman 'ya'yansu maza da mata; kowanne mutum zai ci naman maƙwbcinsa cikin damuwa da azaba akan abin da ya faru da su daga wurin abokan gãbarsu da waɗanda suke neman ransu.'"10Sa'annan sai ka fasa tulun yumɓun a gaban mutanen da suka tafi tare da kai.11Ka kuwa ce masu, 'Yahweh mai runduna yace wannan: Haka zan yi wannan abu ga waɗannan mutane na wannan birni - wannan furcin Yahweh ne - kamar yadda Irmiya ya fashe tulun yumɓun yadda ba wanda zai iya gyara shi kuma. Mutane zasu bizne matattu a Tofet har sai an rasa wurin da ya rage da za a sake bizne matattu kuma.12Wannan shi ne abin da zan yi da wannan wuri da mazaunansa idan na maida wannan birni kamar Tofe -wannan furcin Yahweh ne -13saboda haka gidajen Yerusalem da na sarakunan Yahuda zasu zama kamar Tofet - dukkan gidajen waɗanda akan rufinsu ne ƙazaman mutane suke sujada ga dukkan taurarin sararin sama da suke zuba abin sha na baye baye ga wasu alloli.'"14Sai Irmiya ya komo daga Tofet, inda Yahweh ya aike shi don yayi annabci. Ya tsaya a filin gidan Yahweh, yace da dukkan mutane.15"Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, y faɗi wannan, 'Ku gani, na kusa auka wa wannan birni da dukkan garuruwansa da dukkan masifu da na ambata gãba da shi, tun da sun taurare wuyansu sun kuma ƙi jin maganganuna.'"
Wannan sunan kwari ne a kudu da birnin Yerusalem, inda mutane suke yanka hadaya ga gumakan ƙarya. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Irmiya 7:31.
A nan "kunnuwa ... za su tsuji" wani karin magana ne da ke nufin kowa zai gigice da abin da ya ji. AT: "zai girgiza duk wanda ya ji labarin"
A nan kalmar "su" tana nufin mutanen Yahuda.
Anan “jinin marar laifi” yana wakiltar kisan mutanen da ba su san komai ba. Yahweh yayi maganar kashe mutane da yawa kamar cika wuri da jini. AT: "an kashe mutane da yawa marasa laifi a wannan wurin"
Anan kalmar "hankali" tana nufin tunanin Yahweh. AT: "kuma ban taɓa tunani game da shi ba"
Karin magana "ka faɗo da takobi" na nufin mutuwa a yaƙi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan sa makiyansu su kashe su da takuba"
Ana iya samar da kalmar daga jimlar da ta gabata. Karin maganar "faduwa ... ta hannun" na nufin mutum ya kashe shi, tare da kalmar "hannu" wakiltar mutum duka. AT: "Zan ba wa waɗanda suke son kashe su damar kashe su"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba wanda zai iya sake gyara shi"
Ana iya samarda kalmomin "gidajen" anan. AT: "gidajen sarakunan Yahuza"
Wadannan kalmomin guda biyu duk suna magana akan mutane masu taurin kai. A cikin magana ta farko, Yahweh yayi magana akan mutane masu taurin kai kamar sun yi wuyan wuyansu. AT: "da taurin kai ya ƙi saurare"
1Fashur ɗan Immer firist - shi babban jami'i ne - ya ji Irmiya yana annabcin waɗannan maganganu a gaban gidan Yahweh.2Saboda haka Fashur ya bugi annabi Irmiya sa'annan ya sa shi cikin turu wanda ke ƙofar bisa ta Benyamin a gidan Yahweh.3Ya zamana kashegari sa'adda Fashhur ya fitar da Irmiya daga turun. Sai Irmiya yace da shi, "Yahweh bai kira sunanka Fashhur ba, amma ya baka suna Magor Missabib.4Domin Yahweh ya faɗi wannan, 'Duba, zan maishe ka abin tsoro, kai da dukkan waɗanda kake ƙauna, amma zasu mutu da takobi ta wurin abokan gãbarsu idanunka kuma zasu gani. Zan kuma bada dukkan jama'ar Yahuda a hannun sarkin Babila. Shi kuwa zai maida dasu bayi a Babila ko kuwa ya kai masu hari da takobi.5Zan ba shi dukkan dukiyar wannan birni da kuma dukkan arzikinta da dukkan abubuwa masu tamani da dukkan dukiyar sarakunan Yahuda. Zan miƙa waɗannan abubuwa a hannun abokan gãbarsu zasu kuma washe su. Zasu ɗauke su su kuma kai su Babila.6Amma kai, Fashhur, da dukkan mazauna gidanka zasu tafi bauta. Kai zaka tafi Babila a can zaka mutu. Kai da dukkan waɗanda kake ƙauna kuma kayi masu annabcin ƙaryar waɗannan abubuwa a wurin za a bizne ka.'"7Yahweh, ka ruɗe ni, na kuwa ruɗu. Ka fi ni ƙarfi, ka kuma rinjaye ni. Na zama abin dariya dukkan yini, kowa yana ta yi mani ba'a.8Amma duk lokacin da zan yi magana, na kan kira da murya in yi magana da ƙarfi, 'Hargitsi da hallakarwa.' Sai maganar Yahweh ta zama abin zargi da abin ba'a a dukkan yini.9Idan na ce, 'Ba zan ƙara yin tunani akan Yahweh ba. Ba kuwa zan ƙara yin magana da sunansa ba.' Sai in ji kamar wuta a cikin zuciyata, an sa ta a cikin ƙasusuwana. Sai in yi ƙoƙarin danne ta amma ba zan iya jurewa ba.10Na kan ji jita-jita ta banrazana daga wurin mutane da yawa a dukkan kewaye. 'Dole mu bada rahoto!' Waɗanda ke kusa da ni su dubawa su gani ko zan faɗi. 'Watakila za a ruɗe shi. Idan haka ne, sa'annan ma iya rinjayarsa har mu ɗauki fansarmu a kansa.'11Amma Yahweh yana tare da ni kamar jarumi mai iko, don haka masu runtumata zasu yi tangaɗi. Baza su ci nasara da ni ba. Zasu ji kunya ƙwarai domin ba zasu yi nasara ba. Ba zasu daina jin kunya ba, kuma ba za a manta ba.12Amma kai, Yahweh mai runduna, mai gwada adali wanda yake ganin zuciya da tunani. Bari in ga sakayyar da zaka yi masu tun da na kawo ƙarata a gare ka.13Raira waƙa ga Yahweh! A yabi Yahweh! Gama ya kuɓutar da rayukan waɗanda ake zalunta daga hannun mugaye.14Bari ranar da aka haife ni ta zama la'ananniya. Kada ka bar ranar da uwata ta haife ni ta yi albarka.15Bari mutumin da ya kai wa mahaifina labari ya zama la'annane, wanda yace, An haifa maka ɗa namiji,' don yasa ka farin ciki.16Bari wannan mutum ya zama kamar biranen da Yahweh ya kaɓantar ba tare da ya ji tausayinsu ba. Bari ya ji kuka don neman taimako da wayewar gari, da rana kuma ya ji gangamin yaƙi,17domin bai kashe ni tun ina ciki ba, ya sa uwata ta zama kabarina, cikin mahaifar da zata dawwama har abada.18Me yasa na fito daga cikin mahaifa in ga damuwa da azaba, don kwanakina su cika da kunya?"
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) cewa Fashhur da kansa ya buge Irmiya ko 2) cewa Fashhur ya umurci wasu mutane su doke Irmiya.
Kalmomin magana "faɗuwa da takobi" na nufin cewa za su mutu a yaƙi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "maƙiyansu za su kashe su da takuba" ko "maƙiyansu za su kashe su a yaƙi"
Anan kalmar "idanu" tana wakiltar Fashhur. AT: "zaku ganshi"
Anan kalmar "hannu" tana nufin iko. AT: "Zan ba sarkin Babila damar cinye Yahuda dukka"
Yahweh ya maimaita wannan ra'ayin sau huɗu don ƙarfafawa. Babila za ta kwashe dukiyar Isra'ila, har da dukiyar sarki.
Sanya abubuwa a hannun mutane yana nuna baiwa mutane abu ko barin mutane su dauki abubuwan. AT: "Zan ba maƙiyanku waɗannan abubuwan" ko "Zan ƙyale magabtanku su mallaki waɗannan abubuwan"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "A can, mutane za su binne ku da duk ƙaunatattunku waɗanda kuka yi musu annabcin abubuwa na yaudara"
Waɗannan jimlolin guda biyu ma'anar abu ɗaya ne kuma suna jaddada yadda wasu suke yi masa ba'a.
Anan "kalma" tana nufin sakon Yahweh. Za a iya fassara kalmomin "zargi" da "izgili" tare da jimloli na magana. AT: "mutane suna zagina da izgili gare ni a kowace rana saboda na yi shelar saƙon Yahweh"
Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) "Ba zan taɓa ambaton Yahweh ba ko faɗin wani abu game da shi" ko 2) kalmar "suna" tana wakiltar iko. AT: "Ba zan ƙara yin magana a matsayin manzonsa ba"
A nan kalmomin "zuciya" da "ƙasusuwa" suna wakiltar ainihin cikin Irmiya. Irmiya yayi maganar rashin iya magana game da sakon Yahweh kamar sakon Yahweh wuta ce da take ci a cikin sa. AT: "Maganar Yahweh kamar wuta ce da take ci a ciki na sosai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zai yiwu mu iya yi masa wayo"
Irmiya ya kwatanta Yahweh yana taimakonsa kuma yana kāre shi daga abokan gaba zuwa jarumi mai iko.
Kalmar "hankali" alama ce ta abin da mutum yake tunani da yanke shawara, kuma kalmar "zuciya" alama ce ta abin da mutum yake ji da sha'awa. AT: "ku san tunanin kowane mutum da yadda yake ji"
Anan kalmar "hannu" tana wakiltar ƙarfi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "waɗanda mugaye suka zalunta da ƙarfinsu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "La'anar ranar da aka haife ni" ko "Bari mutane su la'anta ranar da aka haife ni"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kada ku albarkaci ranar da mahaifiyata ta haife ni" ko "Kada mutane su albarkaci ranar da mahaifiyata ta haife ni"
A nan kalmar "shi" tana nufin "wannan mutumin."
Irmiya ya yi amfani da wannan tambaya ta zance don yin gunaguni cewa babu wani kyakkyawan dalili da za a haife shi. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Babu wani dalili da ya sa aka haife ni kawai don ganin matsaloli da azaba ... kunya."
Anan kalmar “kwanaki” tana wakiltar duk kwanakin rayuwar Irmiya. AT: "rayuwata cike da kunya"
1Wannan ita ce maganar da ta zo wa Irmiya daga Yahweh lokacin da sarki Zadakiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da Zafaniya ɗan Ma'aseya firist gare shi. Suka ce da shi,2"Nemi shawara daga Yahweh a madaddin mu, don Nebukadnezza sarkin Babila yana kawo ma na yaƙi. Me yiwuwa Yahweh zai yi abin ban al'ajabi domin mu, kamar yadda ya saba a lokatan baya, wanda ya sa shi ya janye daga wurin mu."3Sai Irmiya ya ce da su, "Wannan shi ne abin da dole za ku ce da Zadakiya,4Yahweh, Allah na Israila, ya faɗi wannan: Duba, zan juya baya ga kayan yaƙin da su ke hannunka, waɗanda ka ke yaƙi da su gãba da sarkin Babila da Kaldiyawa waɗanda suke kusa da ku daga wajen garun! Gama zan tara su a cikin tsakiyar wannan birnin.5Ni kaina zan yi faɗa da kai da duk ƙarfina, da kuma hasalata da zafin fushina.6Gama zan faɗawa mazaunan wannan birnin, mutum da dabba. Za su mutu da babbar annoba.7Bayan wannan - wannan shi ne furcin Yahweh - Zadakiya sarkin Yahuda, da bayinsa da mutanen, da duk wanda ya rage a cikin wannan birni bayan annoba, da takobi da kuma yunwa, zan bashe su dukka a hannun Nebukadnezza sakin Babila, da kuma hannun abokan gãbarsu, da hannun waɗanda suke neman rayukansu. Daga nan shi kuma zai kashe su da kaifin takobi. Ba zai ji tausayinsu ba, ko ya rage su, ko kuma ya yi juyayinsu ba.'8Game da waɗannan mutane dole ka ce, 'Yahweh ya faɗi wannan: Duba ina kusa da sa hanyar rai da hanyar mutuwa a gabanku.9Shi wanda ya zauna a wannan birnin zai mutu da takobi, da yunwa da kuma annoba; amma shi wanda ya fita zai ba da kansa ga Kaldiyawa waɗanda suka kewaye ku gãba da ku zai rayu. Zai tserar da ransa.10Gama na ƙudura zan yi gãba da wannan birni in kuma kawo masa masifa ba alheri ba - wannan furcin Yahweh ne. An ba da shi a hannun sarkin Babila, shi kuwa zai ƙone shi da wuta.'11A game da gidan sarkin Yahuda kuwa, ku ji maganar Yahweh.12Ya gidan Dauda, Yahweh ya ce, 'Ku aikata adalci kowace safiya. Ku ceci wanda aka yi masa ƙwace daga hannun mai tsananta masa, ko kuma hasalata ta fita kamar wuta ta yi ƙuna, harma ba mai iya kashe ta, saboda mugayen ayyukanku.13Duba, mazaunan kwari! Ina gãba da ku, dutsen da ya ke a fili - wannan furcin Yahweh ne - ina gãba da wanda yake cewa, "Wane ne zai iya saukowa ƙasa don ya yi gãba da mu?" Ko kuwa "Wane ne zai iya shiga gidajenmu?"14Na sa sakamakon ayyukanku su yi gãba da ku - wannan furcin Yahweh ne - kuma zan kunna wuta a cikin kurmin, za ta cinye duk abin da ya ke kewaye da ita.'"
Wannan ladabi ne, amma neman gaggawa. AT: "Da fatan za ku yi magana da Yahweh don mu ... ku afka mana"
"zai sa shi ya tafi"
Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) kayan yaƙi na nufin sojojin da ke ɗauke da su kuma "hannu" yana wakiltar iko. AT: "sojojin da kuka umarta" ko 2) kayan yaƙin makamai ne na zahiri kuma "hannunka" suna wakiltar sarki da sojojinsa. AT: "makaman da ku da sojojinku kuke ɗauka"
Duk waɗannan jimlolin maganganu ne na magana wanda ke nuni da babban iko. AT: "tare da iko mai girma"
"waɗanda ke zaune a Yerusalem"
Yahweh yana ba mazaunan Yerusalem zaɓi wanda zai nuna ko suna rayuwa ko suna mutuwa.
Wannan aikin na alama yana wakiltar miƙa wuya. AT: "mika wuya ga"
Wannan karin magana yana nufin ya "yanke hukunci sosai." AT: "Na yanke shawara na yi adawa da wannan birni"
Wannan na iya zama taken 21:12 - 23: 8. AT: "Ku saurari abin da Yahweh ya ce game da sarkin Yahuza, da danginsa, da barorinsa"
Cikakken sunan "adalci" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "Kullum ku yiwa mutanen da kuke mulka adalci a kansu"
Anan ana maganar azabar Yahweh kamar wuta ce da za ta cinye waɗanda suka aikata mugunta. AT: "Zan hukunta ku kuma in hallakar da ku a cikin fushina da sauri kuma gaba ɗaya"
"Na yi adawam, Yerusalem" ko "Zan hukunta, mutane Yerusalem"
Sakamakon munanan ayyukansu ana magana ne azaman 'ya'yan itace waɗanda suka tsiro daga waɗannan ayyukan. AT: "Zan hore ku yadda kuka cancanta saboda abubuwan da kuka aikata"
1Wannan shi ne abin da Yahweh ya ce, "Ka gangara zuwa gidan sarkin Yahuda ka faɗa ma sa wannan magana a can.2Ka ce, 'Sarkin Yahuda, ka saurari maganar Yahweh - kai da ke zaune akan gadon sarautar Dauda - da kai, da barorinka, da mutanenka da ke shigowa ta waɗannan ƙofofi.3Yahweh ya faɗi wannan, "Ku aikata gaskiya da adalci, kuma duk wanda aka yi masa ƙwace - ku cece shi daga hannun masu zalumtarsa. Kada ku wulaƙanta wani baƙon da ke ƙasarku, ko maraya ko kuwa gwauruwa. Kada a yi ta'addanci ko a zubar da jinin marar laifi a wannan wurin.4Domin idan hakika ku ka yi waɗannan abubuwa, sarakunan da ke zaune kan kursiyin Dauda za su shiga cikin ƙofofin gidan nan haye cikin karusa da dawakai, shi, da barorinsa, da jama'arsa!5Amma idan ba ku kasa kunne ga waɗannan zantattuka waɗanda na yi shelar su ba - wannan furcin Yahweh ne - to wannan masarauta za ta zama kufai.'"6Gama Yahweh ya faɗi wannan game da gidan sarkin Yahuda, 'Kai kamar Giliyad ka ke, kamar ƙolƙolin Lebanon ka ke a gare ni. Duk da haka zan maisheka jeji, da kuma birane da ba mazauna.7Gama zan ƙaddara masu lalatarwa su tashi gãba da ku! Mutane da makamansu za su daddatse itatuwan sidarku mafi kyau su kuma zuba su a wuta.8Sa'annan al'ummai da yawa za su shige ta wannan birni. Kowanne mutum zai ce wa na kusa da shi, "Me ya sa Yahweh ya yi haka game da wannan babban birni?"9Sa'annan ɗayan zai amsa, "Saboda sun yi watsi da alƙawarin Yahweh Allahnsu suka russuna wa waɗansu alloli suka yi masu sujada."10Kada ku yi kuka domin wanda ya mutu ko ku yi makoki dominsa; amma ku yi kuka mai zafi sabili da wanda ya kusa tafiya, domin ba zai ƙara dawowa ya ga ƙasar asalinsa ba.'11Domin Yahweh ya faɗi haka game da Yehoahaz ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wanda ya gaji sarauta a madadin ubansa Yosiya, 'Ya tafi daga nan wurin ba zai sake komowa ba.12Zai mutu a can inda suka kai shi zaman talala, kuma ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.'13Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, benayensa kuma ta hanyar rashin gaskiya, ya sa makwabcinsa ya yi masa aiki a banza, bai kuma bashi al'bashinsa ba;14yana cewa, 'Zan gina wa kaina babban gida mai manyan ɗakuna a sama.' Sai ya sa masu manyan tagogi, ya kuma rufe su da itacen sida, ya kuma yi masu jan shafe.15Wannan ne zai maishe ka sarki mai adalci, da ka ke son ka sami katakan sida? Ko mahaifinka bai ci ya sha ba, duk da haka ya yi gaskiya da adalci? Sai komai ya tafi dai - dai da shi.16Ya shari'anta da alheri ga matalauta da fakirai. Ya yi kyau a lokacin nan. Wannan ba shi ne ma'anar sanina ba? - wannan ne furcin Yahweh.17Amma ba kome a zuciyarka da idanunka sai dai damuwa domin muguwar ribarka da kuma domin zubar da jinin marasa laifi, da aikata danniya da murƙushe waɗansu.18Sabili da wannan Yahweh ya faɗi haka game da Yehoiyakim ɗan Yosiya, sarkin Yahuda: Ba za su yi makoki domin sa ba, suna cewa, 'Kaito, ɗan'uwana!' ko, 'Kaito, 'yar'uwata!' Ba za su yi makoki dominsa ba, suna cewa, 'Kaito, ubangida!' ko, 'Kaito, mai martaba!'19Za a binne shi kamar yadda ake binne jaki, a janye shi a jefar nesa da ƙofofin Yerusalem.20Ku haura kan duwatsun Lebanon ku yi ihu. Ku tada muryarku a Bashan. Ku yi ihu daga duwatsun Abarim, gama duk abokanku za a hallaka su.21Na yi maku magana sa'ad da ku ke zaune lafiya, amma kun ce, 'Ba za mu kasa kunne ba.' Al'adarku ce wannan tun kuna samari, gama ba ku saurari muryata ba.22Iska za ta kora dukkan makiyayanku, abokanku kuma za su tafi bautar talala. Sa'annan lallai za ku kunyata ku ƙasƙantu ta wurin miyagun ayyukanku. Ku da kuke zaune cikin 'Lebanon,'23ku da ku ke shaƙatawa cikin ginin itatuwan sida, za ku zama abin tausayi sa'ad da azabar naƙuda ta afko maku, azaba kamar ta mace mai naƙudar haifuwa!"24"Na rantse da zatina - wannan furcin Yahweh ne - ko da kai, Yehoiyacin ɗan Yehoiyakim, sarkin Yahuda, zoben hannun damana ne, zan cire ka.25Gama na bashe ka a hannun masu neman ranka da kuma hannun waɗanda ka ke jin tsoro a gabansu, wato hannun Nebukaneza sarkin Babila da Kaldiyawa.26Zan jefar da kai da mahaifiyarka wadda ta haife ka cikin wata ƙasa, ƙasar da ba nan aka haife ka ba, kuma can za ka mutu.27Game da ƙasar nan da suke so su koma, ba za su dawo nan ba.28Wannan ita ce tukunyar da aka rena aka kuma farfasa? Wannan shi ne mutumin nan Yehoiyacin tukunyar da ba ta gamshi kowa ba? Me ya sa suka jefar da shi waje da shi da zuriyarsa, kuma suka zubar da su cikin ƙasar da ba su santa ba?29Ƙasa, Ƙasa, ƙasa! Ki ji maganar Yahweh!30Yahweh ya faɗi wannan, "Rubuta akan mutumin nan Yehoiyacin: Ba zai haifu ba. Ba zai yi albarka ba a kwanakinsa, ba kuma wani a zuriyarsa da zai ci nasara ko kuma ya ƙara zama a kursiyin Dauda ya yi mulki bisa Yahuda ba."
Waɗannan ƙofofin ƙofofin gidan sarki ne. AT: "mutanenku waɗanda suka zo ziyarci sarki"
"kubutar da duk wanda aka sata daga hannun azzalumi"
Anan "zub da jini ... jini" yana da alaƙa da kisan kai, kuma "jini" yana nufin mutanen da aka kashe. AT: "Kada ku kashe mutanen da ba su da laifi"
Sunan sarauta "kursiyi" yana nufin ikon sarauta kamar Dauda. AT: "sarakuna, masu mulki kamar David a gabansu"
Wannan jumlar ƙamus ce wacce ke bayyana sarakuna da ƙarfi da arziki.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan yana nufin gidan sarauta inda sarki yake zaune ko 2) "gida" na nuna ga dangin da ke zaune a gidan, waɗanda suke jerin sarakunan sarakunan Yahuda. AT "gidan sarautar Yahuda"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Kuna da kyau kamar Giliyad ko ƙwanƙolin Lebanon" ko 2) "Kuna ba ni farin ciki mai yawa kamar na Gileyad ko na Lebanon."
Abin da ya kasance kyakkyawa a dā an faɗi cewa ya zama fanko kuma ba kowa. AT: "sa ku zama wofi kamar hamada"
Anan "al'ummomi" na nufin mutane daga waɗannan al'ummomin da suka wuce. AT: "Sannan mutane da yawa daga al'ummomi daban-daban za su wuce ta wannan birin"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya. Jimlar "sunkuyar da kai ƙasa" tana bayyana matsayin da mutane suke amfani da shi wajen bauta. AT: "sun bauta wa wasu alloli"
"kada ku sake dawowa don ganin ƙasar Isra'ila" ko "kada ku sake ganin mahaifarsa"
Sunan a Ibraniyanci shine "Shallum," amma an fi saninsa da Jehoahaz.
Kalmar "gida" na nuna ga dangin da ke zaune a gidan. A wannan yanayin yana nufin Jehoahaz
Yahweh yayi wannan tambaya ta magana don tsauta wa Yehoyakim saboda fadarsa mai tsada. AT: "Samun gidan sarautar itacen al'ul ba zai sa ka zama sarki nagari."
Yahweh ya yi wannan tambayar don ya tunatar da Yehoyakim game da misalin mahaifinsa, sarki Yosiya. AT: "Mahaifinku sarki Yosiya ya ji daɗin rayuwarsa, amma ya aikata ... adalci."
Yahweh ya yi wannan tambaya ta magana don ya tsawata wa Yehoyakim saboda bai bi gurbin mahaifinsa ba, sarki Yosiya. AT: "Wannan shine ma'anar sanina."
Wannan neman kuɗi ne ta hanyar yaudara ko kuma ta amfani da hanyoyin da ba su dace ba.
"yin rikici da wasu don neman kudi"
An yi maganar jana'izar Yehoyakim daidai da yadda mutane suke binne jaki. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Za su binne gawarsa kamar yadda za su binne mushen jaki; za su ja shi su jefa shi"
Wani tsauni wanda yake kudu maso gabashin Yerusalem.
"Na yi magana da kai lokacin da kake lafiya"
Sauraro sunan meton ne na yin biyayya. AT: "ba ku yi biyayya da ni ba"
Wannan kalma ce "" Yahweh yayi amfani da ra'ayin "makiyayi" ta hanyoyi biyu daban-daban. A nan "makiyaya" kwatanci ne ga shugabannin Yerusalem, kuma iska "tana jagorantar" su. Iskar tana wakiltar Yahweh. AT: " Zan tafi da shugabanninku kamar dai iska ta kwashe su "
Yahweh yana magana akan fadar masarauta kamar "Lebanon" da "gine-ginen itacen al'ul" saboda an gina ta da itacen al'ul mai yawa. AT: "Ku da ke zaune a fādar da aka yi da itacen al'ul na Lebanon"
Zafin da sarki zai ji idan makiyansa suka kayar da shi zai yi zafi sosai kamar zafin da mace take ji yayin haihuwa. AT: "lokacin da kuka ji zafi kamar na zafin mace a yayin haihuwa"
Yahweh yayi magana da Yekoniya kamar zai yiwu ya zama zoben hannun Yahweh.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Na sanya wa waɗanda suke neman ranku damar su kama ku"
Wannan yana nufin ƙasar Yahuda.
Ana maganar Yehoiachin a matsayin tukunya wacce sam ba ta da daraja kuma ba ta son kowa. Tambayoyin sun jaddada cewa bashi da daraja ko abokai. AT: "Yehoiachin bashi da amfani kamar fashewar jirgi kuma babu wanda ke farin ciki da shi."
Wannan tambayar ta magana tana bayyana abin da zai faru da Yehoiachin mara amfani. AT: "Saboda haka abokan gaba za su cire Yehoiachin da danginsa daga ƙasar kuma su kai su baƙon ƙasar."
AT: "yi biyyaya da maganar Yahweh"
1"Kaiton makiyayan da ke lalatarwa suke kuma warwatsar da tumakin makiyayata - wannan furcin Yahweh ne."2Saboda haka Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan game da makiyayan da ke kiwon mutanensa, "Kun warwatsar da garkena kun kore su nesa. Ba ku lura da su ba. Sabili da haka na kusa in hukunta ku saboda muguntar da ku ka aikata - wannan ne furcin Yahweh.3Ni da kaina zan tattara ragowar garkena daga dukkan ƙasashen da na kora su, zan kuma dawo da su wurin kiwo, inda za su hayayyafa su kuma ƙaru.4Sa'anna zan tanada makiyaya bisansu waɗanda za su yi kiwon su domin kada su ƙara tsorata ko su zama karyayyu. Ba za a rasa ko ɗayansu ba - wannan furcin Yahweh ne.5Duba, kwanaki suna zuwa - wannan ne furcin Yahweh - da zan tada wa Dauda reshe mai adalci. Shi zai yi mulki kamar sarki; zai yi aiki da hikima ya sa gaskiya da adalci su kasance a ƙasar.6A kwanakinsa Yahuda zai tsira, Isra'ila zai zauna lafiya. Ga sunan da za a kira shi da shi: Yahweh shi ne adalcinmu.7Saboda haka duba, kwanaki suna zuwa - wannan ne furcin Yahweh - da ba za su ƙara cewa, "Na rantse da ran Yahweh wanda ya fito da mutanen Isra'ila daga ƙasar Masar ba.'8Maimakon haka za su ce, 'Na rantse da ran Yahweh, wanda ya fitar ya kuma dawo da zuriyar gidan Isra'ila daga ƙasar arewa da dukkan ƙasar da aka kora su.' Sa'annan za su zauna a ƙasar da ke tasu."9A game da annabawan, zuciyata ta karai, dukkan ƙasusuwana su na kaɗuwa, na zama kamar bugaggen mutum, kamar mutumin da ruwan inabi ya rinjaye shi, saboda Yahweh da kuma zantattukansa masu tsarki.10Domin ƙasar ta cika da mazinata. Sabili da waɗannan ne ƙasar ta bushe. Wuraren kiwo a jeji sun ƙeƙashe. Tafarkun annabawan nan mugaye ne; ba su mori ikonsu yadda ya kamata ba.11Gama da annabawan da firstocin dukka biyu sun ƙazamtu. Har ma na ga muguntarsu a cikin gidana! - wannan ne furcin Yahweh -12Sabili da haka tafarkinsu zai zama kamar wuri mai santsi cikin duhu. Za a ture su ƙasa. Za su faɗa a cikinta. Gama zan aiko da masifa găba da su a shekarar da zan hukunta su - wannan ne furcin Yahweh.13Gama na ga annabawan da ke cikin Samariya su na yin abin kyama: sun yi annabci da Ba'al sun karkatar da jama'ata Isra'ila.14A cikin annabawan da ke Yeruselem na ga mugayen abubuwa: Su na yin zina su na aikata ƙarya. Su na ƙarfafa hannun miyagu; ba wanda yake juyowa daga muguntarsa. Dukkan su sun zama kamar Soduma a gareni, mazamnan su kuma kamar Gwamarata!"15Saboda haka Ubangiji mai runduna ya faɗi wannan game da annabawan, "Duba, na kusa in sa su su ci abu mai ɗaci su sha ruwa mai dafi, gama ƙazamta ta bazu daga annabawa da ke cikin Yeruselem har zuwa dukkan ƙasar."16Ubangiji mai runduna ya ce, "Kada ku saurari maganganun annabawan da ke yi maku annabci. Sun zurma ku! Suna sanar da wahayi daga nasu tunani, ba daga bakin Yahweh ba.17Kullum su na faɗa wa waɗanda su ka rena ni, 'Yahweh ya ce akwai salama dominku,' Gama kowanne mai tafiya a cikin tattaurar zuciyarsa ya kan ce, 'Masifa ba za ta auko kanmu ba.'18Duk da haka wa ya tsaya a majalisar Yahweh? Wa ya gani ya kuma ji maganarsa? Wa ya natsu ya kasa kunne ya saurari maganarsa?19Duba, akwai hadarin da ke dannowa daga Yahweh! Hasalar sa na fita, guguwa kuma na juyawa ko'ina. Tana zagayawa kewaye da kan mugaye.20Fushin Yahweh ba zai huce ba sai ya gama aiwatawa da cika nufin zuciyarsa. A ƙarshen kwanaki, za ku gane shi.21Ban aiki waɗannan annabawan ba. Haka kawai su ka bayyana. Ban shaida masu kome ba, amma duk da haka su ka yi annabci.22Inda sun kasance a majalisar shawarata, da sun sa jama'ata su ji maganata; da sun sa su su juyo daga mugayen maganganunsu da kuma mugayen ayyukansu.23Ni Allah ne na kusa kaɗai - wannan ne furcin Yahweh - ba kuma Allah na nesa ba?24Akwai wani da zai iya ɓoye wa a wurin da ba zan ganshi ba? - wannan ne furcin Yahweh - ko ni ban cika sammai da ƙasa ba? - wannan ne furcin Yahweh.25Na ji abin da annabawan su ka faɗi, waɗanda suke annabcin ƙarya cikin sunana. Sukan ce, 'Na yi mafarki! 'Na yi mafarki!26Har yaushe za a ci gaba da haka, annabawa masu annabcin ƙarya daga tunaninsu, da kuma annabci daga ruɗun da ke cikin zuciyarsu?27Su na shirin sa mutanena su manta da sunana ta wurin mafarkan da su ka sanar, kowanne ga maƙwabcinsa, kamar dai yadda kakaninsu su ka manta da sunana su ka so sunan Ba'al.28Annabin da ya ke da mafarki, bari ya sanar da mafarkin. Amma ga wanda na sanar da shi wani abu, bari ya sanar da maganata da gaskiya. Me ya haɗa ciyawa da al'kama? - wannan ne furcin Yahweh - Maganata ba kamar wuta ta ke ba? - wannan ne furcin Yahweh -29kuma kamar guduma mai farfasa duwatsu gutsu - gutsu?30To ku duba, ina găba da annabawan - wannan ne furcin Yahweh - da kowanne ɗayan da ya saci magana daga wani mutum ya kuma ce maganar ta zo daga gareni.31Duba, ina găba da annabawan - wannan ne furcin Yahweh - masu amfani da harshensu su yi shelar annabci.32Duba, ina găba da annabawa da ke mafarkan ƙarya - wannan ne furcin Yahweh - sa'annan su yi shela da haka su ke ɓad da mutanena da ƙarairayinsu da kuma fariya. Ina găba da su, gama ban aike su ba ko in ba su umarni. Saboda haka lallai, ba za su taimaki mutanen nan ba - wannan ne furcin Yahweh.33Lokacin da waɗannan mutane, ko annabi, ko firist ya tambayeku, 'mene ne nawaiyar Yahweh?' za ka ce masu, 'Ku ne nawaiyar, kuma zan jefar da ku - wannan ne furcin Yahweh.34Game da annabawan, da firistoci, da kuma mutanen da ke cewa, 'Wannan shi ne nawaiyar Yahweh' zan hukunta wannan mutum da gidansa.35Kuna ci gaba da cewa, kowanne mutum ga makwabcinsa da kuma kowanne mutum ga ɗan'uwansa, 'Me Yahweh ya amsa?' kuma 'Me Yahweh ya furta?36Amma ka da ku ƙara yin magana akan 'nawayar Yahweh,' gama nawaiyar ita ce maganar kowanne mutum, kuma kun karkatar da maganganun Allah mai rai, Ubangiji mai runduna, Allahnmu.37Ga abin da za ku ce wa annabi, 'Wace amsa ce Yahweh ya ba ku? ko kuma, 'Me Yahweh ya ce?'38Amma idan kun ce, 'Nawaiyar Yahweh,' wannan shi ne abin da Yahweh ya ce: 'Sabili da kun faɗi wanɗannan maganganu, 'Nawaiyar Yahweh,' lokacin da na aika maku, cewa, 'Ba za ku ce, "Nawaiyar Yahweh,"' ba.39saboda haka, duba, na kusa ɗaukar ku in jefar da ku nesa da ni, tare da birnin dana ba ku da kakanninku.40Sa'annan zan sa maku madawwamiyar kunya da zargi a kanku wanda ba za a taɓa mantawa ba.'"
A cikin ayoyi na 1-4, Yahweh yana nufin Isra’ila a matsayin makiyayarsa, Isra’ilawa kamar tumakinsa, da shugabannin Isra’ilawa a matsayin makiyaya. Makiyaya suna da aikin kiyaye tumakin, amma shugabannin ba sa yin haka.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya. Na biyu yana karfafa tunani a farkon.
Yahweh yana nufin ƙasar Isra’ila kamar makiyaya ce mai kyau ga mutanensa. Wannan kyakkyawar makiyayar itace matattara don tanadin bukatun su. AT: "zuwa makiyaya mai kyau" ko "zuwa inda za a biya duk bukatunsu"
Kalmar "karuwa" ta bayyana yadda zasu "bada 'ya'ya." AT: "za su ƙaru sosai a lamba"
Kalmomin "a ragargaje" yana nufin cewa wani ya sa su jin tsoro kuma ma'anarsu ɗaya ce da "tsoro." Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "babu wanda zai sake tsoratar da su"
Ana maganar wannan sarki na gaba wanda ya fito daga zuriyar Dauda kamar dai shi reshen reshe ne da ke kan bishiya. ATa: "zuriyar kirki"
Abubuwan suna na "gaskiya" da "adalci" za'a iya bayyana su azaman ayyuka. AT: "sa mutane su yi adalci da gaskiya"
Anan “Isra’ila” na nufin mutanen Isra’ila. AT: "mutanen Isra'ila za su zauna cikin aminci"
Wannan yana nufin yadda aka kama kabilun Isra’ila goma na arewa kuma suka bazu tsakanin ƙasashe kewaye.
Wannan karin magana yana nufin zurfin baƙin ciki. AT: "Ina bakin ciki ƙwarai"
Anan rawar jiki tana tattare da tsoro. AT: "Ina tsoro ƙwarai"
Mutanen da suka bugu ba sa iya kame kansu. Hakanan, Irmiya ya rasa ikon kansa saboda tsoron azabar Yahweh. AT: "Ni kamar mashayi ne; Ba zan iya kame kaina ba"
Annabawa da firistoci sun ƙazantu da zunubi kamar yadda ruwa zai iya ƙazantar da ƙazanta. AT: "annabawa da firistoci masu zunubi ne"
Ana magana game da haɗarin ayyukansu kamar suna gab da faɗuwa daga zamewar gefen dutsen a cikin duhu kuma suka ji wa kansu rauni. AT: "akwai abubuwan da suke da rikitarwa da haɗari, kamar tafiya a kan wani wuri mai santsi a cikin duhu"
Yahweh yana magana game da masifa a matsayin abokin gaba wanda zai aiko don ya faɗa wa firistoci da annabawan ƙarya. AT: "Zan sanya musu masifa"
Anan “hannaye” na nufin mutum duka. AT: "Suna ƙarfafa waɗanda suke aikata mugunta" ko "Suna ƙarfafa mutanen da suke aikata mugunta"
Wannan na iya zama yanayi mai kyau. AT: "kowa yana ci gaba da zunubinsa"
Sadom da Gomora biranen mugaye ne ƙwarai har Allah ya hallaka su da wuta daga sama. AT: "Dukansu sun zama mugaye kamar Sodom ... sun zama kamar Gomora"
"Annabawa sun sa ku gaskata abin da ba gaskiya ba!"
Anan "hankula" na nufin tunanin annabawan karya. AT: "wahayin da suka hango"
A nan “bakin” yana nufin abin da Yahweh ya ce. AT: "ba abin da Yahweh ya ce ba"
Waɗannan jimlolin guda uku duk suna magana ne game da babban hadari wanda ke misaltawa don fushin Yahweh. Ana iya bayyana wannan azaman misali. AT: "Fushin Yahweh yana zuwa kamar guguwa mai ƙarfi, yana fita da fushi da guguwa kamar guguwa"
An yi magana da fushin Yahweh kamar iska mai guguwa da ke kewaye da miyagu. AT: "Yana zuwa kan miyagu kamar guguwar iska"
Anan “nufin zuciya” na nuni ga abubuwan da Yahweh yake so ya faru. AT: "ya kammala kuma ya cika duk hukuncin da ya shirya"
Yahweh ya faɗi abin da zai faru idan firistoci da annabawan ƙarya sun halarci taron majalisar Yahweh a sama. Wannan yanayin tunanin ba shi yiwuwa. AT: "idan da gaske sun saurare ni"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don tsawata wa firistoci da annabawan ƙarya don tunanin cewa bai ga muguntar da suke yi ba. AT: "Ba wanda zai iya ɓoyewa cikin ɓoyayyen wuri don haka ba zan iya ganinsa ba."
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa yana ko'ina a sama da ƙasa. AT: "Ina ko'ina, a sama da ƙasa."
Yahweh ya yi wannan tambayar don ya nanata cewa wannan wani abu ne wanda bai kamata ya ci gaba ba. AT: "Wannan bai kamata ya ci gaba ba, annabawa suna faɗar ƙarya waɗanda su da kansu suka ƙirƙira su."
Anan kalmar "suna" na nufin cikakkiyar halittar Yahweh. AT: "manta da ni ... manta ni" ko "manta wanene ni ... manta wanene ni"
Yahweh yayi amfani da waɗannan tambayoyin don ya nanata cewa kalmarsa ta fi maganar mutane ƙarfi. Ta wannan hanyar, maganarsa kamar wuta ce ko guduma. AT: "Maganata tana da ƙarfi kamar wuta ... kuma tana da ƙarfi kamar guduma mai farfasa dutse."
Yahweh ya ci gaba da isar da sakonsa game da annabawan karya da firistoci wanda ya fara a cikin Irmiya 23: 9 kuma ya kammala a cikin Irmiya 23:40.
Anan “kaya” na nufin saƙo ko annabci daga Yahweh.
Don "ɓata" wani abu shine murɗe shi ko gurbata shi. AT: "kun canza saƙon Allah mai rai, Yahweh Mai Runduna, Allahnmu, don faɗi abin da kuke so ya faɗi ba abin da Allah ya ce ba"
A nan "ku" ɗaya ne kuma yana nufin Irmiya.
Yahweh yayi magana game da tura waɗannan firistocin da annabawan ƙarya zuwa zaman talala kamar suna wani abin da zai jefar da nisa. AT: "Ina gab da koro ku daga wurina"
1Yahweh ya nuna mani wani abu. Duba, ga kwanduna biyu na 'ya'yan baure a gaban haikalin Yahweh. (Wannan wahayi ya faru bayan da Nebukadnezza, sarkin Babila, ya kai waɗannan mutane bautar talala: Yehoyacin ɗan Yehoyakim, sarkin Yahuda, da shugabannin Yahuda, da masassaƙa, da masu ƙira da kwasao daga Yerusalem ya kawo su Babila.)2Ɗaya kwandon ɓauren na da ƙyau sosai, kamar nunar fari na ɓaure, amma ɗaya kwandon ɓauren ba shi da kyau ko kaɗan har ma ba za a iya cin su ba.3Yahweh ya ce mani, "Me ka gani, Irmiya?" Na ce, '"Ya'yan ɓaure. 'Ya'yan ɓaure masu kyau sosai da marasa kyau har ma ba za a iya cinsu ba."4Sai maganar Yahweh ta zo gareni, cewa,5"Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Zan dubi 'yan bautar talala na Yahuda da tagomashi, kamar kyawawan 'ya'yan ɓauren nan, 'yan bautar talala waɗanda na kore su daga nan zuwa ƙasar Kaldiya.6Zan kafa idanuna a kansu domin in yi masu alheri, in kuma dawo da su wannan ƙasar. Zan gina su, ba zan rushe su ba. Zan dasa su, ba zan tumbuƙe su ba.7Sa'annan zan ba su zuciyar da za su sanni, gama ni ne Yahweh. Za su zama mutanena, zan kuma zama Allahnsu, haka za su juyo gareni da dukkan zuciyarsu.8Amma kamar 'ya'yan ɓauren nan marasa kyau har da ba za a iya cinsu ba-ga abin da Yahweh ya ce - Zan yi haka da Zedekiya, sarkin Yahuda, da shugabanninsa, da kuma sauran da ke a Yerusalem waɗanda suka rage a cikin ƙasar nan ko kuwa su ka tafi su zauna cikin ƙasar Masar.9Zan maishe su abin tsoro, abin masifa, a idanun dukkan mulkokin duniya, abin kunya abin zargi da karin magana, da dariya, da la'ana a duk wuraren da na warwatsa su.10Zan aika da takobi, yunwa, da annoba găba da su, har sai an hallakasu daga ƙasar da na basu da kakanninsu."
Ana amfani da wannan ɓangaren labarin don bayar da bayanan tarihi don nuna lokacin da abubuwan da suka faru suka faru.
mutane masu ƙwarewa wajen gina abubuwa
mutane masu ƙwarewa wajen ƙirƙirar abubuwa da ƙarfe
Ɓaure masu kyau suna wakiltar waɗancan Yahudawan da aka kai bauta zuwa ƙasar Kaldiya.
Anan "saita idanuna" yana nufin zai gansu. Ganin su wata alama ce ta kulawa da su. AT: "Zan albarkace su"
Wadannan kalmomin guda biyu suna da ma'anoni iri daya. Na biyu yana karfafa tunani a farkon. AT: "Zan taimaka musu su ci gaba a cikin Kaldiya"
Yahweh yayi magana akan waɗanda aka komo daga zaman talala kamar shuke-shuke da Yahweh zai shuka a ƙasa mai kyau ba zai cire ba. AT: "Zan kafa su a cikin ƙasa, kuma ba zan kawar da su ba"
Waɗannan kalmomin suna nufin abu ɗaya kuma suna ƙarfafa yadda Yerusalemzai hukunta mutanen Yerusalem. Zasu zama wani abu da zai firgita wasu mutane idan suka ganshi.
"Zan kashe su da yaki, yunwa da cututtuka"
Anan “takobi” yana nufin yaƙi ko sojojin abokan gaba. AT: "Zan aika sojojin abokan gaba" ko "Zan aika yaƙi"
1Wannan ita ce maganar da ta zo wurin Irmiya game da dukkan mutanen Yahuda. Ya zo ne a shekara ta huɗu ta Yehoyakim ɗan Yosiya, sarkin Yahuda. Wannan ita ce shekara ta fari ta Nebukadnezza, sarkin Babila.2Annabi Irmiya ya yi shelar wannan ga dukkan mutanen Yahuda da dukkan mazaunan Yerusalem.3Ya ce, "Shekaru ashirin da uku, tun daga shekara ta sha uku ta Yosiya ɗan Amon, sarkin Yahuda, har zuwa yau, maganar Yahweh ta na ta zuwa gare ni, ni kuma na yi maku magana akai-akai, amma ba ku kasa kunne ba.4Yahweh ya aika maku dukkan bayinsa annabawa akai-akai, amma ba ku saurare su ba ko ku kasa kunne.5Waɗannan annabawa sun ce, 'Bari kowanne mutum ya juyo daga hanyar muguntarsa da lalatattun ayyukansa ya dawo ƙasar da Yahweh ya bayar a zamanin dã ga kakanninku da ku kuma, a matsayin madawwamiyar kyauta.6Saboda haka kada ku bi waɗansu alloli ku yi masu sujada ko ku russuna masu, kuma kada ku cakune shi da ayyukan hannuwanku domin kada ya azabtar da ku.'7Amma ba ku saurare ni ba - wannan ne furcin Yahweh - haka ku ka cakune ni da aikin hannuwanku in cutar da ku.8Domin haka Ubangiji mai ruduna ya faɗi wannan, 'Saboda ba ku saurari maganganuna ba,9duba, ina gaf da aiko da umarni domin a tara dukkan mutanen arewa - wannan ne furcin Yahweh - da Nebukadnezza bawana, sarkin Babila, zan kawo su gãba da ƙasar nan da mazaunanta, gãba kuma da dukkan al'umman da ke kewaye da ku. Gama zan keɓe su domin halakarwa. Zan mai da su abin tsoro, abin yi wa tsaki, da kuma kufai har abada.10Zan kawo ƙarshen ƙarar murna da ƙarar farinciki, ƙarar ango da ƙarar amarya, ƙarar dutsen niƙa da hasken fitila.11Sa'annan dukkan wannan ƙasa za ta zama kufai da abin tsoro, kuma waɗannan al'ummai za su bauta wa sarkin Babila shekaru saba'in.12Za ya zama kuwa bayan shekaru saba'in sun cika, zan hukunta sarkin Babila da al'umman nan, ƙasar Kaldiyawa - wannan ne furcin Yahweh - saboda kurakuransu in maishe ta kango marar matuƙa.13Sa'anan kuma zan yi wa ƙasar nan abin gãba bisa ga dukkan maganar da na faɗi, da kuma dukkan abin da aka rubuta a cikin wannan littafi wanda Irmiya ya yi annabci gãba da dukkan al'ummai.14Kuma wasu al'umman da yawa da manyan sarakuna za su bautar da waɗannan al'ummai. Zan sãka masu bisa ga abin da su ka aikata da kuma ayyukan hannuwansu."'15Gama Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗa mani wannan, "Ka ƙarɓi wannan ƙoƙon ruwan inabi na hasalata daga hannuna ka sa dukkan al'umman da na aike ka gun su su sha shi.16Gama za su sha sa'anan su yi tuntuɓe ko ina su sheƙa da gudu daga takobin da nake aikowa cikinsu."17Sai na ƙarɓi ƙoƙon daga hannun Yahweh, na kuma să dukkan al'umman da Yahweh ya aike ni su sha shi:18Yerusalem, biranen Yahuda da sarakunanta da shugabanninta-a maida su kufai da abin tsoro, da kuma abin tsaki da la'antarwa, kamar yadda suke a yau.19Sauran al'ummai dole su sha shi: Fir'auna Sarkin Masar da barorinsa; shugabanninsa da dukkan mutanensa;20dukkan baƙin mutane ruwa biyu da dukkan sarakunan da ke ƙasar Uz; dukkan sarakunan da ke ƙasar Filistiya - Ashkelon, Gaza, Ekron, da ragowar Ashdod;21Idom da Mowab da mutanen Ammon.22Sarakunan Taya da Sidon, sarakunan gãɓar tsallaken teku,23Dedan, Tema, da Buz da dukkan waɗanda suke aske gashin gefen kawunansu suma sai da suka sha shi.24Waɗannan mutanen suma dole suka sha shi: dukkan sarakunan Arebiya da dukkan sarakunan mutane masu ruwa biyu da ke zaune a jeji;25dukkan sarakunan Zimri, da dukkan sarakunan Elam, da dukkan sarakunan Madayana;26dukkan sarakunan arewa, waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa - kowanne da ɗan'uwansa da dukkan masarautar da ke duniya da ke a fuskar ƙasa. A ƙarshe, sarkin Babila zai sha a bayansu.27Yahweh ya ce mani, "Yanzu dole ka faɗa masu, 'Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Ku sha ku bugu, sa'anan ku haras, ku faɗi ƙasa, kada ku tashi kafin in aiko da takobi a tsakanin ku.'28Idan kuwa sun ƙi su ƙarɓi ƙoƙon daga hannunka su sha, za ka ce masu, 'Yahweh mai runduna ya faɗi wannan, Dole ne lallai ku sha shi.29Ku duba, na kusa kawo masifa akan birnin da ake kira da sunana, to ku da kanku ya kamata a tsirar da ku daga horo ne? Ba za ku tsira ba, gama ina kawo takobi gãba da dukkan mazaunan ƙasar! - wannan ne furcin Yahweh mai runduna.'30Dole ka yi annabcin dukkan waɗannan maganganu gãba da su, kuma ka ce masu, 'Yahweh zai yi ruri daga sammai zai yi ihu da muryarsa daga wurin zamansa mai tsarki, zai yi ruri da ƙarfi gãba da nasa; kuma zai yi ihu, kamar waɗanda suke matse 'ya'yan inabi gãba da dukkan mazaunan duniya.31Zizar yaƙi zata buga ta kai dukkan bangon duniya, gama Yahweh yana kawo ƙara gãba da dukkan al'ummai, zai kuma kawo hukunci kan dukkan talikai. Zai ba da mugaye ga takobi - wannan ne furcin Yahweh.'32Ubangiji mai runduna ya faɗi wannan, 'Duba, masifa tana tasowa daga al'umma zuwa al'umma, kuma babban hadari ya danno daga manisantan wurare na duniya.33Sa'anan waɗanda Yahweh ya kashe za su zama daga wannan bangon duniyan zuwa wan can; ba kuma za a yi makokinsu ba, ko a tattarasu, ko kuma a binne su. Za su zama kamar taki a ƙasa.34Ku yi makoki, makiyaya, ku yi ihu domin taimako! Ku yi birgima a cikin ƙura, ku iyayengijin garke, gama ranar da za a yanka ku ta zo; za a warwatsa ku sa'ad da ku ka faɗi kamar kyawawan tukwane.35Babu mafaka domin makiyaya, ba sauran mafita domin iyayengijin garke.36Ku ji koke-koken makiyaya da makokin iyayengijin garke, gama Yahweh yana lalatar da makiyayarsu.37Haka makiyayarsu mai salama za a lalatar da ita sabili da zafin fushin Yahweh.38Kamar ɗan zaki, da ya baro maɓuyarsa, gama ƙasarsu zata zama abin ban tsoro saboda fushin mai tsanantawa, saboda kuma zafin fushinsa.'"
Waɗannan su ne na ƙarshe daga cikin Isra'ilawa.
Duba yadda kuka fassara wannan a cinkin Irmiya 11:6.
Irmiya yayi magana akan mutanen da suka daina yin wani abu kamar dai waɗancan mutanen suna juya baya ga wannan aikin.
Kalmar "shi" tana nufin Yahweh. Mai yiwuwa ma'anoni ga kalmar "aikin hannuwanku" su ne 1) ishara ce ga gumakan da mutane suka yi da hannayensu. AT: "kada ku tsokane Yahweh da gumakan da kuka yi" ko kuma 2) Kalmomin magana ne da ke nuni ga ayyukan mutum, tare da kalmar "hannaye" kasancewa synecdoche wanda ke wakiltar mutumin da ya aikata waɗannan ayyukan. AT: "kada ku tsokane Yahweh ta hanyar abin da kuke aikatawa"
Duba yadda kuka fassara makamancin wannan jimlar a cikin Irmiya 25: 6. Mai yiwuwa ma'anoni ga kalmar "aikin hannuwanku" su ne 1) ishara ce ga gumakan da mutane suka yi da hannayensu. AT: "kun tsokane ni don in cutar da ku saboda gumakan da kuka yi da hannayenku" ko 2) Kalmomin magana ne da ke nuni ga ayyukan mutum, tare da kalmar "hannaye" kasancewa ne synecdoche cewa wakiltar mutumin da ya aikata waɗannan ayyukan. AT: "kun tsokane ni in cutar da ku saboda abubuwan da kuke aikatawa"
"saboda haka, zan yi cutar da ku"
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Irmiya 7:34.
Ana iya fassara kalmomin "lalacewa" da "tsoro" tare da jimlar magana. AT: "Zan sa wannan ƙasa ta zama kufai da wani abu da ke firgita mutane"
Za a iya fassara kalmar "lalacewa" azaman sifa. AT: "kufai har abada"
Yahweh yayi maganar azabtar da al'umman al'umman saboda abin da sukayi kamar yana biyansu.
Kalmar "al'ummai" tana wakiltar mutanen al'ummai. Yahweh yayi magana akan mutanen da suke fuskantar fushinsa kamar zasu sha ruwan inabin da yake cikin ƙoƙon. AT: "sa dukkan mutanen al'ummu ... su sha ruwan inabin"
Anan kalmar "takobi" tana wakiltar yaƙi. AT: "saboda yaƙe-yaƙe da nake haifar da faruwa a tsakanin su"
Kalmar "al'ummai" tana wakiltar mutanen al'ummai. AT: "Na sanya dukkan mutanen ƙasashe ... su sha ruwan inabin daga ƙoƙon"
Za a iya fassara jigon "mai ban tsoro" tare da jimlar magana. AT: "abin da ke firgita mutane"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) mutanen da kakanninsu suka fito daga ƙungiyoyin mutane daban-daban ko 2) baƙin da suka zauna a Masar.
Wannan wataƙila yana nufin mutanen da suka yanke gashinsu don girmama allolin arna. Wasu sifofin zamani suna fassara wannan furcin Ibraniyancin a matsayin "duk mutanen da ke zaune a gefen hamada." Duba yadda kuka fassara makamancin wannan jimla a cikin Irmiya 9:26.
Wannan karin magana ne wanda ke nufin kowane mutum, ɗayan bayan ɗaya. AT: "daya bayan daya"
Anan kalmar "takobi" tana wakiltar yaƙi. AT: "kafin yaƙe-yaƙe da zan jawo faruwa tsakaninku"
Wannan yana nufin Yerusalem kuma ana iya fassara shi a cikin aiki. AT: "garin da na kira da suna na" ko "Yerusalem, wanda na kira da sunana"
Anan kalmar "takobi" tana wakiltar yaƙi. Yahweh yayi maganar shelar yaƙi da mutane kamar yana kiran takobi a kansu. AT: "Ina shelar yaƙi da duk mazaunan ƙasar" ko "Ina kawo yaƙi da duk mazaunan ƙasar"
Irmiya yayi maganar Yahweh yana ihu da ƙarfi kamar yana ruri kamar zaki.
Anan kalmar “nama” tana wakiltar mutumtaka. AT: "akan dukkan mutane" ko "akan dukkan mutane"
Mai yiwuwa ga wannan kwatancin su ne 1) Yahweh yayi magana game da sojojin Babila da halakar da zai haifar kamar hadari ne mai girma ko 2) Yahweh yayi magana game da fushinsa mai girma kamar dai hadari ne mai saurin kawo hallaka.
Ta ambaton ƙarshen duniya, wannan jimlar tana wakiltar ko'ina a tsakanin ƙarshen ƙarshen. AT: "a wannan rana zai mamaye duniya duka"
Wannan alama ce ta baƙin ciki, baƙin ciki ko damuwa.
Yahweh yana maganar shugabannin Isra'ila kamar dai su makiyaya ne waɗanda ke da alhakin kiyayewa da kulawa da mutane, waɗanda, a bayyane, ana maganarsu kamar su tumaki.
Yahweh yana magana ne game da kasar da shugabanni ke tunanin cewa suna zaune lafiya kamar dai "wuraren kiwo" ne wanda suke kula da tumakin
Ana iya sanya wannan cikin tsari mai aiki. AT: "Yahweh zai lalata wuraren kiwo na lumana saboda tsananin fushinsa"
An yi magana game da azabtar da mutanensa cikin tsananin fushinsa kamar Yahweh na zaki wanda ya bar kogonsa don neman ganima.
1A farkon mulkin Yehoyakim ɗan Yosiya, wannan maganar ta zo daga Yahweh cewa,2"Yahweh ya faɗi wannan: Ka tsaya a filin haikalina ka yi magana akan dukkan biranen Yahuda waɗanda suke zuwa su yi sujada a gidana. Yi shelar dukkan maganganun da na umarce ka ka faɗa masu. Kada ka rage ko wata kalma!3Mai yiwuwa su kasa kunne, har kowanne mutum ya juyo ya bar mugayen hanyoyinsa, nima in janye masifar da nake niyyar saukar masu saboda mugayen ayyukansu.4Saboda haka dole ka ce masu, 'Yahweh ya faɗi wannan: Idan baku kasa kunne gare ni kun yi biyayya da dokokina da na sa agabanku ba -5Idan baku kasa kunne da maganar bayina annabawa waɗanda na ke aiko maku-amma ba ku ji ba! -6to zan maida gidan nan kamar Shiloh; zan maida birnin nan la'ana a idanun dukkan al'umman da ke a duniya.'"7Da firistoci, da annabawa da dukkan jama'a sun ji annabi Irmiya yana shelar waɗannan maganganu a haikalin Yahweh.8Ananan da Irmiya ya gama shelar dukkan maganar da Yahweh ya umarce shi ya faɗa wa dukkan mutane, sai firistoci, da annabawa da dukkan mutane suka kama shi suka ce, "Zaka mutu lallai!9Me yasa ka yi annabci a cikin sunan Yahweh ka ce wannan gida zai zama kamar Shiloh kuma wannan birni zai zama kufai, har ba mazauna?" Gama dukkan mutanen sun tada tarzoma gãba da Irmiya a cikin haikalin Yahweh.10Daganan sai shugabannin Yahuda suka ji waɗannan maganganu suka tashi daga gidan sarki su ka tafi gidan Yahweh. Su ka zauna a ƙofa a Sabuwar Ƙofa ta haikalin Yahweh.11Sai firistoci da annabawa suka yi wa shugabanni da dukkan mutane magana. Suka ce, "Dai-dai ne mutumin nan ya mutu, domin ya yi annabci gãba da birnin nan, kamar yadda kuka ji da kunnuwanku!"12Sai Irmiya ya yi magana da dukkan shugabanni da dukkan mutane yace, "Yahweh ya aiko ni in yi annabci gãba da haikalin nan da kuma birnin nan, in faɗi dukkan maganganun nan da kuka ji.13Saboda haka yanzu fa, sai ku gyara al'amuranku da kuma ayyukanku, ku saurari muryar Yahweh Allahnku domin ya janye masifar da ya yi shela gãba da ku.14Ni da kaina-ku dube ni! - ina hannunku. Ku yi mani abin da kuka ga yayi dai-dai a idanunku.15Amma lallai ya kamata ku sani idan ku ka kashe ni, kuna jawo wa kanku al'hakin jinin marar laifi da kuma wannan birni da mazaunan da ke a cikinsa, gama lallai Yahweh ya aiko ni wurinku in yi shelar waɗannan maganganu a kunnuwanku."16Daga nan shugabannin da dukkan mutane suka cewa firistoci da annabawa, "Ba dai-dai ba ne mutumin nan ya mutu, gama ya yi mana shelar abubuwa a cikin sunan Yahweh Allahnmu."17Sai wasu maza suka tashi daga cikin dattawan ƙasar suka yi wa dukkan taron mutanen magana.18Suka ce, "Mika Ba-morashe ya yi annabci a zamanin Hezekiya sarkin Yahuda. Ya yi wa dukkan mutanen Yahuda magana yace, 'Yahweh mai runduna yace: Za a huɗa Sihiyona kamar gona, Yerusalem za ta zama tsibin juji, dutsen haikali zai zama dutsen da ciyayi suka sha kansa.'19To, Hezekiya sarkin Yahuda da dukkan Yahuda sun kashe shi ne? Ashe bai ji tsoron Yahweh ya nemi alheri a fuskar Yahweh domin Yahweh ya janye masifar da ya faɗa masa ba? Ko dai-dai ne muyi mugunta mafi girma gãba da rayyukanmu?"20Ananan wani mutum kuma ya yi annabci cikin sunan Yahweh - Yuriya ɗan Shemaya daga Kiriyat Yarim-shi ma ya yi annabci gãba da birnin nan da kuma ƙasannan, ya amince da dukkan maganganun Irmiya.21Amma da sarki Yehoyakim da dukkan sojojinsa da shugabanninsa suka ji maganarsa sai sarki ya yi ƙoƙari ya kashe shi, amma da Yuriya ya ji sai ya tsorata, ya gudu ya tafi Masar.22Sai sarki Yehoyakim ya aiki mutane su tafi Masar - Elnatan ɗan Akbor da waɗansu mutanen aka aike su su bi Yuriya zuwa Masar.23Suka ɗauko Yuriya daga Masar suka kawo shi wurin sarki Yehoiyakim. Sai Yehoiyakim ya kashe shi da takobi ya aika gawarsa makabartar da ke waje inda ake rufe mutane marasa galihu.24Amma hannun Ahikam ɗan Shafan yana tare da Irmiya, saboda haka ba a bada shi ga hannun mutane su kashe ba.
"Kada ka bar komai daga abin da na fada maka!"
Wannan halakar ne da sharaɗi. Idan Yahuda ta tuba, Allah ba zai hallaka ba sai dai ya warkar da su.
AT: "Idan bakayi min biyayya da dokar da na baku ba"
Yahweh ya lalata wurin bautar a Shiloh, kuma yana barazanar lalata wannan wurin bautar.
"don duk al'umman duniya su ganni nayi hakan"
Mai yiwuwa su ne 1) Mutanen sun zaɓi yin imani da ƙaryar salama ta ƙarya kuma ba sa son fuskantar gaskiya, ko 2) mutane sun yi imani da sauran annabawa suna shelar zaman lafiya kuma sun ga Irmiya a matsayin annabin ƙarya wanda ya kamata a jefe shi saboda batar da mutane.
Ana iya fassara wannan tsawatarwa azaman sanarwa. AT: "Bai kamata ku yi annabci ba ... mazaunin."
"kun ji"
"mutanen da ke yin sujada a haikalin Yahweh da waɗanda ke zaune a birnin Yerusalem"
Muryar na iya fahimtar abin da mutum yake yi, kuma ana iya fassara kalmar iri ɗaya "saurara" ko "yi biyayya." AT: "ku yi biyayya ga Yahweh"
Kalmomin "mai kyau" da "daidai" suna nufin abu ɗaya. Ido wata alama ce ta tunanin mutum. AT: "Ku yi min duk abin da kuke ganin shi ne daidai da abin yi"
Sunan mutumin suna ne na ƙarfin ikonsa. AT: "tare da ikon Yahweh Allahnmu"
"Sihiyona" da "tudun haikalin" suna nufin wuri ɗaya. Idan manomi ya huce gona, sai ya juye duk wata datti ya kuma tumbuke dukkan tsire-tsiren da ke tsiro a wurin. Wani kurmi yana cike da dazuzzuka har babu wanda zai iya amfani da shi don komai. Waɗannan kwatancin biyu ba za su iya zama gaskiya a zahiri a lokaci ɗaya, amma suna ƙarfafa cewa Yahweh zai ba maharan damar lalata yankin haikalin gaba ɗaya.
Masu magana suna ƙoƙarin sa masu sauraro su yarda da abin da suke faɗa. AT: "Kun sani sarai cewa Hezekiya ... bai kashe shi ba."
Masu magana suna ƙoƙarin sa masu sauraro su yarda da abin da suke faɗa. AT: "Kun sani sarai cewa ya ji tsoron Yahweh kuma ya sanya fushin Yahweh don Yahweh ... su."
"ji abin da ya ce"
Hannun alama ce ta ƙarfin da hannu ke motsawa. Ahikam ba soja bane, saboda haka yana iya magana da mutane kuma ya canza ra'ayinsu. AT: "Ahikam ... ya iya taimaka wa Irmiya" ko "Ahikam ... ya iya hana mutane cutar Irmiya"
Waɗannan sunayen maza ne
Hannun alama ce ta ƙarfin da hannu ke motsawa. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Ahikam bai ba mutane damar ikon kashe Irmiya ba" ko kuma "mutane ba za su iya kashe Irmiya ba saboda Ahikam bai ba su ikon yin hakan ba"
1A farkon sarautar Zedekiya ɗan Yosiya, sarkin Yahuda, wannan magana ta zo ga Irmiya daga Yahweh.2Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗa mani, "Ka yiwa kanka karkiyar itace. Ka sa su a wuyanka.3Sa'annan ka aika su wurin sarkin Idom, sarkin Mowab, sarkin mutanen Ammon, sarkin Taya, da kuma sarkin Sidon. Ka aika da su ta hannun jakadun sarki da suka zo Yerusalem gun Zedekiya sarkin Yahuda.4Ka ba su umarni domin iyayengijinsu ka ce, 'Ubangiji mai runduna, Allah na Isra'ila ya ce: Wannan shi ne abin da zaku ce da iyayengijinku,5Ni da kaina na yi duniya ta wurin ƙarfina mai girma da miƙaƙƙen hannuna. Ni ne nayi mutane da dabbobi a kan fuskar duniya, nakan kuma ba da ita ga wanda na ga ya dace a idanuna.6Saboda haka yanzu, ina bada dukkan ƙasar nan a cikin hannun bawana, Nebukadnezza, sarkin Babila. Kuma ina bada abubuwa masu rai na jeji su bauta masa.7Gama dukkan al'ummai za su bauta masa, da ɗansa da kuma jikokinsa, har sai lokaci domin ƙasarsa ya zo. Sa'annan al'ummai da yawa da manyan sarakuna za su ci ƙarfinsa.8Saboda haka duk al'umma da mulkin da bai bauta wa Nebukadnezza, sarkin Babila ba, bai kuma ba da wuyansa ya yi karkiya da sarkin Babila ba-zan hukunta wannan al'umma da takobi, yunwa, da annoba - wannan furcin Yahweh ne-har sai na hallaka ta ta hannunsa.9Saboda haka kada ku saurari annabawanku, da masu mafarkanku, masu dubanku, masu sihiri, da matsubbata, waɗanda suke ta yi maku magana suna cewa, 'Kada ku bauta wa sarkin Babila,'10Gama suna yi maku annabcin ƙarya domin su kora ku nesa da ƙasarku, gama zan kore ku, zaku kuma mutu.11Amma al'ummar da ta bada wuyanta ta yi karkiya da sarkin Babila, ta kuma bauta masa, zan bar su su huta a ƙasarsu - wannan furcin Yahweh ne-zasu kuma noma ta su gina mazauninsu a ciki.""'12Sai na yi magana da Zedekiya sarkin Yahuda na ba shi wannan saƙon, 'Ku ba da wuyanku ku yi karkiya da sarkin Babila ku bauta masa da shi da mutanensa, zaku kuwa rayu.13Donmi zaku mutu-da kai da mutanenka-da takobi, yunwa da annoba, kamar yadda na faɗa game da al'ummar da ta ƙi ta bauta wa sarkin Babila?14Kada ku saurari maganganun annabawan da suka ce maku, 'Kada ku bauta wa sarkin Babila,' gama suna yi maku annabcin ƙarya ne.15Gama ni ban aikesu ba-wannan furcin Yahweh ne - gama annabcin ƙarya suke yi cikin sunana domin in kore ku ku tafi ku hallaka, da ku da annabawan da suke maku annabci."16Na yi shelar wannan ma firistoci da dukkan mutane na ce, "Yahweh ya faɗi wannan yace: Kada ku kasa kunne ga maganganun annabawaku da su kayi maku annabci suka ce, 'Duba! ana dawo da kayayyakin gidan Yahweh daga Babila yanzu!' Annabcin ƙarya suke yi maku,17Kada ku saurare su. Ku bauta wa sarkin Babila ku rayu. Don me wannan birni zai zama kufai?18Idan su annabawa ne, kuma idan lallai maganar Yahweh ta zo gare su, to su roƙi Yahweh mai runduna kada ya aika kayan haikalinsa da suka rage, na gidan sarkin Yahuda, da na Yerusalem zuwa Babila.19Yahweh mai runduna ya faɗi haka game da ginshiƙai da babban daro da aka sani a matsayin "Tekun" da mazauninta, da sauran kayayyakin da suka rage a wannan birni -20kayayyakin da Nebukadnezza sarkin Babila bai ɗauka ba lokacin da ya tafi da Yehoyacin ɗan Yehoiyakim, sarkin Yahuda bautar talala daga Yerusalem zuwa Babila tare da dukkan hakiman Yahuda da na Yerusalem.21Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan game da kayayyakin da suka rage a gidan Yahweh, da gidan sarkin Yahuda da Yerusalem,22'Za a kawo su Babila, kuma za su kasance a can har sai ranar da na aza a zo domin su - wannan ne furcin Yahweh - sa'annan zan komo da su in maido su a wannan wuri."'
Hannun magani ne na mutum. AT: "Ku sami jakadun waɗannan sarakunan", waɗanda ... Yahuda, ku ɗauke su "
An umarci Irmiya ya ba da sarkoki da karkiya ga kowane jakada da saƙo ga kowane sarki game da sarƙoƙin da karkiyar.
Kalmomin "ɗaga hannu" yana nufin babban iko kuma yana ƙarfafa magana ta farko. AT: "ta ikon da nake da shi sosai"
Wata ma'ana mai yuwuwa "Ina ba ta duk wanda nake so."
Kasancewa bawan sarki ana maganarsa azaman dabba a kafaɗun da sarki ya sanya karkiya don ta iya yin aiki mai nauyi. AT: "kuma wanda mutanensa ba da son ransu suke bayin sarki ba"
Kasancewa bawan sarki ana maganarsa azaman dabba a kafaɗun da sarki ya sanya karkiya don ta iya yin aiki mai nauyi. Duba yadda ake fassara kalmomi masu kama da haka a cikin Irmiya 27: 8. AT: "al'ummar da mutanenta ke son zama bayin sarki da yardar rai"
"yi gidajensu a cikin ƙasarsu"
Irmiya ya yi amfani da wannan tambayar don ya gargaɗi sarki cewa ayyukansa za su kai ga mutuwa. AT: "Gama idan baku yi haka ba, tabbas za ku mutu ... sarki."
Yahweh yana faɗakar da mutane game da duk annabawan ƙarya da bai aiko ba kuma waɗanda ke musu ƙarya.
Kalmomin "da suna na" suna wakiltar magana da ƙarfi da ikon Yahweh ko a matsayin wakilinsa. Anan waɗannan annabawan suna da'awar cewa sun karɓi saƙonsu daga Yahweh, amma hakan bai samu ba. Cikakken sunan "yaudara" za'a iya fassara shi azaman kalmar "yaudara." AT: "suna cewa suna magana ne don ni lokacin da suke annabci, amma suna yaudarar ku"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane suna dawo da duk abubuwan zinariya da suka kwaso daga haikalin Yahweh!"
Yahweh yana amfani da tambaya don faɗakar da mutane. AT: "Kuna iya kiyaye wannan birni daga zama kufai idan kun yi abin da Yahweh yake so ku yi."
Waɗannan abubuwa ne waɗanda suke cikin haikalin. "Tekun" babban kwano ne da tagulla.
Yahweh yana magana kansa da sunansa don bayyana tabbacin abin da yake furtawa. AT: "wannan shi ne abin da Yahweh ya bayyana" ko "wannan shi ne abin da ni, Yahweh, na ayyana"
1Sai ya kasance a cikin shekarar nan, a farkon mulkin Zedekaya sarkin Yahuda, a shekara ta huɗu kuma a wata na biyar, Annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibiyon, yayi magana da ni a gidan Yahweh a gaban firistoci da dukkan mutane. Yace,2"Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, Ya faɗi wannan: Na karya karkiyar da sarkin Babila ya ɗora maku.3A cikin shekara biyu a wannan wuri zan maido da dukkan kayayyakin gidan Yahweh wanda Nebukadnezza sarkin Babila ya ɗauke daga wannan wuri ya tafi dasu Babila.4Daga nan kuma a wannan wurin zan maido da Yehoiyacin ɗan Yehoiyakim, sarkin Yahuda, da dukkan kamammun Yahuda waɗanda aka aika Babila - wannan furcin Yahweh ne - Gama zan karya karkiyar sarkin Babila."5Sai Annabi Irmiya yayi magana da Annabi Hananiya a gaban firistoci da dukkan mutanen dake tsaye a gidan Yahweh.6Irmiya Annabi yace, "Bari Yahweh yayi haka! bari Yahweh ya tabbatar da maganganun daka anabta a wannan wuri ya maido da kayayyakin gidan Yahweh, da dukkan kamammu daga Babila.7Duk da haka, ka saurari maganar da nake shelarwa a kunnuwanka da kunnuwan dukkan mutane.8Annabawan da suka wanzu da daɗewa kafin ni da kai sunyi anabci game da al'ummai masu yawa gãba da manyan masarautu, game da yaƙi, da yunwa, da annoba.9Hakanan Annabin da yayi anabcin za a yi salama - Idan maganarsa ta tabbata, to za a sani cewa lallai annabi ne wanda Yahweh ya aiko."10Amma annabi Hananiya ya tashi ya ɗauki karkiyar dake wuyan annabi Irmiya ya karya ta.11Daga nan sai Hananiya yayi magana a gaban dukkan mutanen yace, "Yahweh ya faɗi haka: kamar dai haka, cikin shekara biyu zan karya kowace karkiya daga wuyan dukkan al'ummai wanda Nebukadnezza sarkin Babila ya ɗora masu." Daga nan annabi Irmiya yayi tafiyarsa.12Bayan da annabi Hananiya ya karya karkiyar dake wuyan annabi Irmiya, sai maganar Yahweh tazo ga Irmiya, cewa,13"Kaje kayi magana da Hananiya kace, 'Yahweh ya faɗi haka: ka karya karkiyar itace, a maimako zan yi karkiyar ƙarfe.'14Gama Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka: na ɗora karkiyar ƙarfe a bisa wuyan dukkan waɗannan al'ummai domin su bauta wa Nebukadnezza sarkin Babila, kuma zasu bauta mashi. Na kuma bashi bisashen jeji dake cikin gonaki domin yayi mulki a kansu."15Kuma annabi Irmiya ya cewa annabi Hananiya, "Ka saurara Hananiya! Yahweh bai aiko ka ba, amma kai da kanka kasa mutanen nan su gaskata ƙarya.16Saboda haka Yahweh ya faɗi wannan: duba, ina gab da aika ka daga wannan duniya. A wannan shekarar zaka mutu, tunda kayi shelar tawaye ga Yahweh."17A cikin watan bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.
Wannan shine wata na biyar a kalandar Ibrananci. Lokacin rani ne. Lokaci ne na ƙarshe na watan Yuli da kuma farkon watan Agusta akan kalandar Yamma. Wannan ya faru bayan Zedekiya ya yi shekara uku yana sarauta.
Hanananiya yayi magana akan mutanen suna cikin bauta kamar shanu ne waɗanda Babiloniyawa suka ɗora musu karkiya don sanya su yin aiki mai nauyi. AT: "Na sanya shi don haka ba za ku sake zama bayin sarkin Babila ba" ko "Na 'yantar da ku daga bautar ga sarkin Babila" (Duba:
Hananiya ta ci gaba da magana.
Rubutun Ibraniyanci yana da "Yeconiya," wanda shine bambancin sunan "Yehoyiachin." Yawancin sifofin zamani suna da "Yehoyiachin" don a bayyane cewa ana magana da sarki ɗaya.
"Annabawan da suka rayu tuntuni kafin ku da ku"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "sa'annan zaku sani cewa shi annabin gaskiya ne kuma Yahweh ya aike shi"
AT: "Kun karya karkiya mara ƙarfi, amma zan maye gurbinsa da karkiyar da ba za ku iya karya ta ba"
Wannan shi ne wata na bakwai na kalandar Ibraniyanci. Lokaci ne na karshen watan Satumba da kuma farkon watan Oktoba akan kalandar yamma.
1Waɗannan ne maganganun dake cikin littafin da annabi Irmiya ya aika daga Yerusalem zuwa ga ragowar dattawan daga cikin kamammun da kuma firistoci, da annabawa, da dukkan mutanen da Nebukadnezza ya tura bauta daga Yerusalem zuwa Babila.2Wannan ya faru ne bayan da aka aika da sarki Yehoyacin, da mahaifiyar sarki, da manyan dagatai, da shugabannin Yahuda da Yerusalem, da masu sana'o'in hannu daga Yerusalem.3Ya aika da wannan littafi ne ta hannun Elasa ɗan shafan da Gemariya ɗan Hilkiya waɗanda Hezekaya, sarkin Yahuda, ya aika ga Nebukadnezza sarkin Babila.4Littafin yace, "Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan ga dukkan kamammu waɗanda nasa suka tafi bauta daga Yerusalem zuwa Babila,5'Ku gina gidaje ku zauna a cikinsu. Ku shuka gonaki kuci amfaninsu.6Ku auri mataye ku haifi 'ya'ya maza da mata. Ku aurowa 'ya'yanku maza mataye, ku aurar da 'ya'yanku mata ga mazaje. Bari su haifi 'ya'ya maza da mata kuma ku ƙaru ta haka ba zaku zama 'yan kaɗan ba.7Ku biɗi salamar birnin da na aika daku bauta, ku yi roƙo gare ni a madadinsa tunda zaku kasance da salama idan yana cikin salama.'8Gama Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, Ya faɗi wannan, 'Kada ku bar annabawanku dake zaune a tsakaninku da masu sihirinku su ruɗe ku, kada kuma ku saurari mafarke-mafarken da ku da kanku kuke yi.9Gama suna ruɗin ku cikin anabcin da suke yi a cikin sunana. Ban aike su ba - wannan furcin Yahweh ne.'10Gama Yahweh ya faɗi wannan 'Idan Babila ta yi mulkinku har shekaru saba'in, zan taimake ku in aiwatar da maganata mai nagarta game da ku in sake maido da ku a wannan wuri.11Gama ni da kaina na san irin shirye-shiryen da nake da su dominku - wannan furcin Yahweh ne- shirye-shirye na salama ba na bala'i ba, domin in baku gaba mai kyau da bege.12Daga nan zaku yi kira a gare ni, zaku je ku yi addu'a a gare ni, zan kuma saurare ku.13Gama zaku neme ni ku kuma same ni, tunda zaku neme ni da dukkan zuciyarku.14Daga nan zan samu gare ku - wannan furcin Yahweh ne - zan kuma maido da kadarorinku; zan tattaro ku daga cikin dukkan al'ummai da wuraren da na warwatsar da ku - wannan furcin Yahweh ne - gama zan maido da ku wannan wuri daga inda nasa kuka tafi bauta.'15Tunda kunce Yahweh ya tado maku da annabawa a Babila,16Yahweh ya faɗi wannan game da wanda ke zaune bisa kursiyin Dauda da dukkan mutanen da ke zaune a cikin birnin, 'yan'uwanku waɗanda basu tafi tare da ku cikin bauta ba -17Yahweh Mai runduna ya faɗi haka, 'Duba, ina gab da aiko da takobi, da yunwa da cuta a kansu. Gama zan maishe su kamar ruɓaɓɓen ɓauren da ba a iya ci.18Daga nan zan runtume su da takobi, da yunwa, da annoba in maida su abin tsoratarwa ga dukkan mulkokin duniya.-abin ƙyama, abin la'ana da tsãki, abin kunya cikin dukkan al'ummai inda na warwatsa ta.19Wannan saboda basu saurari maganata ba ne - wannan furcin Yahweh ne-wanda na aika masu ta wurin bayina annabawa. Na aike su sau da yawa, amma baku saurara ba-wannan furcin Yahweh ne.'20Domin wannan ku da kanku ku saurari maganar Yahweh, dukkanku 'yan bautar da ya kora daga Yerusalem zuwa Babila,21Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan game da Ahab ɗan Kolaiya da Zedekaya ɗan Ma'ãseya, waɗanda suke yi maku anabcin ƙarya a cikin sunana: Duba, ina gab da sanya su cikin hannun Nebukadnezza sarkin Babila. Zaya kashe su a kan idanun ku.22Daga nan za a furta la'ana game da waɗannan mutane daga bakin ɗaurarrun Yahuda da ke Babila. La'anar zata ce: Dãma Yahweh ya maida kai kamar Zedekaya da Ahab, waɗanda sarkin Babila ya gashe cikin wuta.23Wannan zaya faru ne saboda abubuwan kunya da suka aikata a Isra'ila da suka yi zina da matayen maƙwabtansu suka kuma furta maganganun ƙarya a cikin sunana, abubuwan da ban taɓa umurtar su ba su faɗa. Gama Ni ne na sani; Ni ne shaida-wannan furcin Yahweh ne."'24Game da Shemaiya Nehelamiye, ka faɗi wannan:25Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Domin ka aika da wasiƙu a cikin sunanka zuwa ga dukkan mutanen Yerusalem, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma'ãseiya firist, da dukkan firistoci, kãce,26Yahweh ya maida kai firist a maimakon Yehoaida firist, domin kayi shugabancin gidan Yahweh. Kai ne ke mulkin dukkan mutanen dake girgije-girgije suna maida kansu annabawa. Sai ka sanya su a turu da sarƙoƙi.27To yanzu, me yasa baka tsautawa Irmiya na Anatot ba, wanda ya maida kansa annabi mai tsayayya da kai?28Gama ya aika mana a Babila yana cewa, 'Lokaci ne mai tsawo za ayi. Ku gina gidaje ku zauna a ciki, ku shuka gonaki ku ci amfaninsu.""'29Zefanaya firist ya karanta wannan wasiƙa a kunnen annabi Irmiya.30Sai maganar Yahweh tazo ga Irmiya, cewa,31"Ka aika magana ga dukkan 'yan bauta kace, 'Yahweh ya faɗi wannan game da Shemaiya Nehelamiye: Saboda Shemaiya yayi maku anabci wanda Ni da kaina ban aike shi ba, kuma yasa kun gaskata ƙarya,32Domin wannan Yahweh ya faɗi haka: Duba, Ina gab da horon Shemaiya Nehelamiye da zuriyarsa. Ba za a sami wani mutum da zaya tsaya masa ba a cikin mutanen nan. Ba zai ga alherin da zan yiwa mutanena ba - wannan furcin Yahweh ne - Gama yayi shelar tawaye gãba da Yahweh."'
"an yi shela daga Yerusalem"
uwar sarki
Waɗannan sunayen maza.
Yahweh yana gaya musu zasu kasance a wurin na dogon lokaci.
AT: "Iyaye sukan shirya auren 'ya'yansu"
Zaman lafiya na gari abin birgewa ne ga mutanen da ke zaune lafiya. AT: "Kuyi duk abin da za ku iya don mutanen garin su zauna lafiya"
Yahweh ya ci gaba da magana da Isra’ilawa da aka kama.
Yahweh ya ci gaba da magana game da abin da zai faru da fursunonin Isra'ila.
Isra’ilawa da aka kama
Wannan yana nuna cewa Yahweh zai ba su abin da suke so.
"Zan sake sa abubuwa su sake zama lafiya a gare ku" ko "Zan sa ku sake rayuwa da kyau"
Zama a kan karagar mulki alama ce ta mulki a matsayin sarki. AT: "sarkin da ke mulkin Isra'ilawa kamar yadda Dauda ya yi"
Kalmar "takobi" alama ce ta yaƙi. Ana magana da takobi, yunwa, da cuta a matsayin mutane waɗanda za su iya bin umarnin Yahweh don cutar da Isra'ilawa. AT: "Zan hukunta su ta hanyar sa su mutu a yaƙi, daga yunwa, da kuma rashin lafiya"
Waɗannan kalmomin duka suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna bayyana yadda sauran al'umman za su yi idan suka ga abin da Yahweh ya yi wa mutanen Yahuda.
Waɗannan sunayen maza.
Anan "hannu" shine metonym na ikon da hannu yake yi. AT: "Zan ba da izinin Nebukadnezza, sarkin Babila ya ci su da yaƙi"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kamammun Yahuda a Babila za su la'anta game da waɗannan mutane"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu daya, kuma Yahweh yana maimata su don girmamawa.
Waɗannan suyanen maza ne
Wannan sunan kungiyar mutane.
Shemaiah ya yi amfani da tambaya don tsawata wa mutanen Yerusalem saboda rashin tsawata wa Irmiya. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Ina son ku tsawata wa Irmiya na Anathoth ... a kanku."
Dubi yadda kuka fassara irin waɗannan kalmomin a cikin Irmiya 29: 4.
Yahweh yana magana kansa da sunansa don bayyana tabbacin abin da yake furtawa. AT: "wannan shi ne abin da Yahweh ya bayyana" ko "wannan shi ne abin da ni, Yahweh, na ayyana"
1Maganar da ta zo wa Irmiya daga Yahweh, cewa,2"Ga abin da Yahweh, Allah na Isra'ila, yace, 'Ka rubutawa kanka a littafi dukkan maganganun dana furta maka a littafi.3Gama duba, kwanaki suna zuwa - wannan ne furcin Yahweh - da zan maido da kaddarorin mutanena, Isra'ila da Yahuda. Ni, Yahweh, Na faɗi wannan. Gama zan maido da su ƙasar da na ba kakanninsu, zasu kuma mallake ta."'4Waɗannan ne maganganun da Yahweh ya furta game da Isra'ila da Yahuda,5"Gama Yahweh ya faɗi wannan, 'Munji muryar rawar jiki da fargaba bata salama ba.6Ku yi tambaya ku ji ko Namiji na haihuwar ɗa. To yaya naga kowanne mutum mai ƙuruciya da hannu a kwankwaso kamar macen da zata haihu? Yaya fuskokinsu suka koɗe?7Kaito! Gama wannan rana babba ce, babu wata kamar ta. Zata zama lokacin fargaba domin Yakubu, amma za a cece shi daga ita.8Gama zaya kasance a wannan rana - wannan furcin Yahweh ne Mai runduna - zan karya karkiyar daga wuyan ku, zan ɓalle sarƙoƙinku, domin bãƙi ba zasu sake bautar da ku ba.9Amma zasu yi sujada ga Yahweh Allahnsu su kuma bautawa Dauda sarkinsu, wanda zan naɗa sarki a kansu.10To kai, Yakubu bawana, kada kaji tsoro - wannan furcin Yahweh ne - kada kuma ka firgita, Isra'ila. Gama duba, Ina gaf da maido da kai daga nesa, Zuriyarka kuma daga ƙasar bauta. Yakubu zai dawo ya zauna cikin salama; za a kãre shi, kuma babu sauran tsoratar wa.11Gama ina tare da ku - wannan furcin Yahweh ne - domin in cece ku. Daga nan zan kawo cikakken ƙarshen dukkan al'ummai inda na warwatsar da ku. Amma tabbas bazan kawo ƙarshenku ba, koda yake na horar da ku bisa adalci kuma tabbas bazan barku babu horo ba.'12Gama Yahweh ya faɗi wannan, 'Rauninku ba ya warkuwa; rauninku ya sami lahani.13Babu wanda za yayi roƙo domin ku; babu wani magani da zai warkar da rauninku.14Masoyanku dukka sun manta da ku. Ba zasu neme ku ba, gama na yi maku rauni da raunin maƙiyi da kuma horon ubangida mai mugunta saboda kurakuranku masu yawa da zunubanku marasa ƙirguwa.15Me yasa kuke neman taimako domin rauninku? zafinku baya warkuwa. Saboda kurakuranku masu yawa da zunubanku marasa ƙirguwa, na yi maku waɗannan abubuwa.16Domin wannan duk waɗanda ke cinye ku za a cinye su, kuma dukkan magabtanku zasu tafi cikin bauta. Domin dukkan waɗanda suka washe ku za su zama abin washewa, kuma dukkan waɗanda suka maida ku ganima zan maida su ganima.17Gama zan kawo warkarwa gare ku; zan warkar da ku daga raunukanku - wannan furcin Yahweh ne - zan yi wannan saboda sun kira ku: Yasassu. Babu wanda ya kula da wannan Sihiyonar."'18Yahweh ya faɗi wannan, "Duba, Ina gab da maido da kaddarorin rumfunan Yakubu in kuma ji tausayin gidajensu. Daga nan za a gina birni a bisa rusassun wurarensu, mafaka mai ƙarfi kuma zata kasance inda take a dã.19Daganan waƙar yabo da ƙarar shagulgula zasu fito daga gare su, gama zan ƙãra su ba kuma zan rage su ba; zan darjanta su domin kada su wulaƙanta.20Daga nan mutanensu zasu zama kamar dã, taronsu kuma zaya tabbata a gabana yayin da zan horar da masu tsananta masu a yanzu.21Shugabansu zaya fito daga cikin su. Zaya ɓullo daga cikin su yayin da zan jawo shi kusa yayin da kuma ya matso gare ni. Idan ban yi haka ba wane ne zai iya zuwa kusa da ni? - wannan furcin Yahweh ne.22Daganan zaku zama mutanena, ni kuma in zama Allahnku.23Duba, iskar fushin Yahweh, da hasalarsa, tana fita waje. Iska ce marar tsaitsayawa. Zata yi guguwa bisa kawunan mutane masu mugunta.24Fushin Yahweh ba zai dawo ba har sai ya aiwatar kuma ya haifar da nufe-nufen zuciyarsa. A ranakun ƙarshe, zaku fahimci wannan."
AT: ""rubuta a cikin gungura saƙon da na fada maka"
"Zan sa abubuwa su kasance lafiya ga mutanena, Isra'ila da Yahuda," ko "Zan sa jama'ata, Isra'ila da Yahuda, su sake rayuwa da kyau." Duba yadda kayi fassarar kalmomin nan a cikin Irmiya 29:14.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "mutane suna kururuwa cikin tsoro saboda babu zaman lafiya" ko kuma 2) "ku yi kururuwa cikin fargaba saboda babu zaman lafiya."
Mace da zata haihu tana cikin tsananin ciwo kuma ta kasa yin komai. Samarin sun firgita sosai har jikinsu ya yi rauni, kuma sun kasa yin faɗa. AT: "Samarin suna riƙe da cikinsu kamar mace mai haihuwa; dukkansu ba su da lafiya saboda suna tsoro."
Sunan Yakubu sunaye ne ga zuriyar mutumin. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "don zuriyar Yakubu, amma zan tsamo su daga gare ta"
Kasancewa bawa ana maganarsa da sanya karkiya kamar dabba da sanya sarƙoƙi kamar fursuna.
Yahweh ya ci gaba da magana game da zuriyar Yakubu. AT: "za ku bauta wa Yahweh Allahnku ... sarkinku ... a kanku"
"Yakubu" da "Isra'ila" sunaye biyu ne na kakannin Isra'ilawa, kuma waɗannan sunaye sunaye ne na Isra'ilawa. AT: "zuriyar Yakubu ... ku jama'ar Isra'ila"
Cikakken sunan "kamewa" ana iya fassara ta amfani da sunan "ɗaure". AT: "daga wurin da aka kama su"
Amma ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "tabbas zai hukunta ku"
Wannan yana nufin cewa Yahweh ya yi musu horo mai tsanani har babu wani wanda zai taimake su.
"Ba sa son su zama abokanka"
Yahweh ya bi da mutanensa kamar yadda zai yi wa maƙiyinsa.
Yahweh yayi tambaya anan don sa mutane suyi tunanin dalilin da yasa suke neman taimakonsa yanzu. AT: "Kuna kira don taimako don rauninku saboda ba ku yi mini biyayya ba." ko "Kada ku yi kira don taimako don raunin ku."
Ana maganar lalata al-umma a matsayin cin ta ko cin ta. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Don haka waɗanda suka hallaka ku, maƙiyansu za su hallaka su" ko "Don haka zan halakar da duk wanda ya hallaka ku"
Fadawa a nan shine a kwaso abubuwa daga abokan gaba wanda ya ci, kuma abubuwan da mutum ya ƙwace sune ganima.
Wuraren da mutane suke zaune sunaye ne na mutanen da suke zaune a wuraren. AT: "Ina gab da dawo da dukiyar zuriyar Yakubu, kuma zan tausaya musu"
"Sa'annan za su raira waƙoƙin yabo da murna"
"Zan sa su kara yawansu, ba sai sun zama 'yan kadan ba"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan kafa su a matsayin mutane a gabana"
Wannan yana maganar fushin Allah da azabarsa kamar hadari. Wannan ya nanata ikonsa da ikonsa na hallaka miyagu.
1"A wannan lokaci - wannan furcin Yahweh ne- Zan zama Allahn dukkan iyalan Isra'ila, su kuma zasu zama mutanena."2Yahweh ya faɗi wannan, "Mutanen da zuka tsira daga takobi sun sami tagomashi a jeji; zan fita in bayar da hutawa ga Isra'ila."3Yahweh ya bayyana gare ni a baya kuma yace, "Na ƙaunace ka, Isra'ila, da madawwamiyar ƙauna. Saboda haka na jawoka zuwa gare ni da amintaccen alƙawari.4Zan sake gina ki domin ki ginu, budurwa Isra'ila. Zaki sake ɗaukar tamburanki ki fita da raye-rayen murna.5Zaki sake dasa gonakin inabi a tsaunukan samariya; manoman zasu dasa kuma suyi amfani da 'ya'yan.6Gama rana tana zuwa wadda masu tsaron tsaunukan Ifraim zasu yi shela, 'Ku tashi, mu tafi Sihiyona ga Yahweh Allahnmu.'7Gama Yahweh ya faɗi wannan, "Ku yi sowa ta farinciki game da Yakubu! Ku yi sowa cikin jindaɗi game da manyan mutanen al'ummai! Bari aji yabo. Ku ce, 'Yahweh ya ceci mutanensa, ragowar Isra'ila.'8Duba, ina gab da kawo su daga ƙasashen arewa. Zan tattaro su daga sassan duniya mafi nisa. Makaho da gurgu zasu kasance a cikin su; Mataye masu ciki da waɗanda ke kusa da haihuwa zasu kasance tare da su. Babban taro ne zaya dawo a nan.9Za su zo da kuka; zan bishe su yayin da sukeyin roƙo. Zansa suyi tafiya zuwa maɓulɓulan ruwa a bisa miƙaƙƙiyar hanya. Ba zasu yi tuntuɓe akai ba, gama zan zama Uba ga Isra'ila, Ifraim kuma zaya zama ɗan farina."10Ku saurari maganar Yahweh, al'ummai. Ku yi rahoto har ga ƙasashen kurmi dake nesa. Ku al'ummai dole ku ce, 'Wanda ya warwatsa Isra'ila yana tattara ta kuma yana tsaronta kamar yadda makiyayi ke tsaron tumakinsa.'11Gama Yahweh ya ceto Yakubu ya kuma fanso shi daga hannun wanda yafi ƙarfinsa sosai.12Daga nan zasu zo su yi farinciki bisa tuddan Sihiyona. Fuskokinsu zasu haskaka saboda alherin Yahweh, bisa hatsi da ruwan inabi, bisa mai da 'ya'yan garken awakinsu da na tumaki da kuma na shanu. Gama rayuwarsu zata zama kamar fadamar da ake yiwa banruwa, ba kuma zasu ƙara jin baƙinciki ba daɗai.13Daga nan budurwai zasu yi farinciki da rawa, samari kuma da tsofaffi zasu kasance tare. Domin zan canza makokinsu zuwa bukukuwa. Zan ji tausayin su insa su yi farinciki a maimakon baƙinciki.14Daga nan zan mamaye rayuwar firistoci da yalwa. Mutanena zasu cika kansu da nagartata-wannan ne furcin Yahweh."15Yahweh ya faɗi wannan: "An ji murya a Ramah, kururuwa da kuka mai ɗaci. Rahila ce ke kukan 'ya'yanta. Taƙi ta ta'azantu game da su, gama basu a raye."16Yahweh ya faɗi wannan, "Ki tsai da muryarki daga kuka idanunki kuma daga hawaye; gama akwai sakamako game da aikinki - wannan ne furcin Yahweh - 'ya'yanki zasu dawo daga ƙasar maƙiya.17Akwai bege domin gabanki - wannan furcin Yahweh ne- zuriyarki zasu dawo cikin kan iyakokinsu."18Babu shakka naji bakincikin Ifraim, 'Ka horar da ni, kuma na horu kamar maraƙin da ba horarre ba. Ka maido da ni kuma zan sami maiduwa, gama kai ne Yahweh Allahna.19Gama bayan na juyo zuwa gare ka, nayi nadama; bayan na horu, na mari cinyata. Na ji kunya kuma na ƙasƙantu, gama na ɗauki tsarguwar ƙuruciyata.'20Ifraimu ba ɗa na ne mai daraja ba? Ba ƙaunataccena ba ne, ɗan da nake jin daɗinsa? Gama duk sa'ad da na yi maganar tsayayya da shi, babu shakka ina tunawa da shi a raina da ƙauna. Ta haka zuciyata ke marmarin sa. Babu shakka zanji tausayin sa - wannan furcin Yahweh ne."21Ku kafawa kanku alamun hanya. Ku sanyawa kanku alamun jagora. Ku shirya tunaninku a tafarki mai kyau, hanyar da zaku bi. Ku dawo, budurwan Isra'ila! Ku dawo cikin waɗannan biranen naku.22Har yaushe zaki ci gaba da shakka, ɗiya marar aminci? Gama Yahweh ya halicci wani sabon abu a duniya - mace ta kewaye namiji maji ƙarfi.23Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, "Idan na maido da mutanen zuwa cikin ƙasarsu, zasu faɗi wannan cikin ƙasar Yahuda da kuma biranenta, 'Bari Yahweh ya albarkace ka, kai wuri mai adalci inda ya ke zaune, kai dutse mai tsarki.'24Gama Yahuda da biranenta zasu zauna tare a wurin, kamar yadda manoma da waɗanda suka fita da garkunansu.25Gama zan bada ruwa ga gajiyayyu domin su sha, kuma zan cika dukkan sumammu."26Bayan wannan sai na farka, sai na lura da cewa barcina ya wartsakar da ni.27Duba, ranaku suna zuwa - wannan ne furcin Yahweh - Inda zan shuke gidajen Isra'ila dana Yahuda da zuriyoyin mutane dana bisashe.28A baya, Na keɓe su ciki tsaro domin in tunɓuke su in yage su, in tuntsurar, in lalatar, in kuma kawo masu bala'i. Amma a kwanaki masu zuwa, zan lura da su, domin in gina su in kuma dasa su - wannan furcin Yahweh ne.29A cikin waɗannan kwanaki babu wanda zaya sake cewa, 'Ubanni sun ci inabi masu tsami, amma haƙoran 'ya'ya ne suka dãsashe.'30Gama kowane mutum zaya mutu cikin kurakuransa; Duk wanda ya ci inabi masu tsami, haƙoransa ne zasu dãsashe.31Duba, kwanaki suna zuwa - wanna furcin Yahweh ne - inda zan kafa sabon alƙawari tare da gidan Isra'ila da kuma gidan Yahuda.32Ba zaya zama kamar alƙawarin dana kafa da Ubanninsu ba a kwanakin da na ɗauko su na kamo hannusu na fito da su daga ƙasar masar. Waɗannan kwanakin ne inda suka karya alƙawarina, duk da cewa ni miji ne a gare su - wannan furcin Yahweh ne.33Amma wannan ne alƙawarin da zan kafa da gidan Isra'ila bayan waɗannan kwanaki - wannan furcin Yahweh ne: Zan sanya shari'ata a cikinsu in rubuta ta a zukatansu, gama zan zama Allahnsu, zasu kuma zama mutanena.34Daganan babu sauran wani mutum ya koyawa maƙwabcinsa, ko wani mutum ya koyawa ɗan'uwansa ya ce, 'Ka san Yahweh!' gama dukkan su, daga mafi ƙanƙantarsu har ya zuwa mafi girmansu, zasu san ni - wannan furcin Yahweh ne - Gama zan gafarta kurakuransu ba kuma zan sake tunawa da zunubansu ba."35Yahweh ya faɗi wannan - shi ne wanda yake sanya rana ta haskaka da rana ya kuma jejjera wata da taurari su haskaka da dare. Shi wanda ke sanya teku na motsi raƙuman ruwanta kuma na ruri. Sunansa Yahweh Mai runduna.36Sai idan waɗannan dawwamammun abubuwan sun ɓace daga gare ni - wannan furcin Yahweh ne- ko zuriyar Isra'ila zasu daina zama al'umma a gabana."37Yahweh ya faɗi wannan, "Sai idan za a iya ɗaukar gwajin sammai dake nesa, sai kuma idan za a iya gano harsashin duniya dake can ƙasa, shi ne zan iya yashe da dukkan zuriyar Isra'ila saboda dukkan abin da suka yi - wannan furcin Yahweh ne."38Duba, kwanaki suna zuwa - wannan furcin Yahweh ne - sa'ad da za a sake gina birnin domina, daga hasumiyar Hananel zuwa Ƙofar kwana.39Daga nan layin gwajin zai fita ya ƙara nisa, zuwa tuddun Gerab da kewayen Goya.40Dukkan kwarin gawawwaki da tokarsu, da dukkan filayen kurmi har ya zuwa Kwarin Kidron har zuwa kwanar Ƙofar Doki da ke gabas, za a keɓe domin Yahweh. Ba za a sake rusarwa ko tuntsurar da birnin ba, har abada."
Wannan yana nufin lokacin Allad zai hukunta miyagu.
Irmiya yayi magana kansa kamar shi mutanen Isra'ila ne.
Yahweh da gangan ya maimaita ra'ayin cewa zai gina Isra'ila don ƙarfafa ta. Idan yarenku zai iya amfani da fi'ili mai aiki kawai kuma yana da wata hanya don ƙarfafa ra'ayin, kuna so ku yi amfani da shi a nan. AT: "Zan sake gina ku" ko "Ku tuna da wannan. Zan gina ku"
Ya zama gama gari a koma ga al'ummomi kamar suna mata. Koyaya, "budurwa" tana sanya mutum yin tunani game da budurwa wacce ba ta taɓa yin aure ba don haka ba ta taɓa samun damar kasancewa mara imani ga mijinta ba. Sabili da haka, kiran Isra’ila budurwa, amfani da harshe ne mai ban dariya. AT: "Isra'ila, wanda ya yi ƙarya ya nuna shi mai cikakken aminci ne gare ni" ko "jama'ata marasa imani Isra'ila"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Sa kowa ya ji yabonka"
"har yanzu mutane suna raye"
"kawo Isra'ilawa"
Anan "Ifraim" wani suna ne na "Isra'ila." AT: "Zan zama kamar uba ga mutanen Isra'ila, kuma za su zama kamar ɗana na fari"
Yahweh yana magana kansa kamar shi wani, kuma yana magana game da mutanen Isra'ila kamar suna mace mara taimako. AT: "Na sa mutanena Isra'ila suka warwatse a cikin al'umman duniya, amma yanzu na dawo da su gida na tsare su"
Makiyayi yana kula da kuma kiyaye garken tumakinsa, kuma Yahweh yana alƙawarin kulawa da kuma kare Isra’ilawa.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna jaddada cewa Yahweh ne ya ceci mutanen Isra'ila. AT: "Gama Yahweh ya ceci Isra'ilawa daga abokan gabansu wanda ya fi ƙarfin su"
Wannan yana nufin za su kasance masu ƙarfi da lafiya, kuma za su ci gaba.
Duniya "taba" ita ce gama gari. Isra'ilawa kusan koyaushe suna jin daɗi.
"Yahweh zai canza"
Cikakken sunan "yawa" ana iya fassara shi da "kyawawan abubuwa masu yawa." Ana maganar rayuwar firistoci kamar dai filin da zai jike gaba ɗaya idan aka yi ruwan sama mai yawa a kansa. Life is metonym ga mutum. AT: "Zan ba firistoci duk kyawawan abubuwan da suke so" ko "Zan gamsar da firistoci da kyawawan abubuwa"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Na ji murya a Ramah"
Rahila matar Yakubu (Isra'ila) ce kuma mahaifiya ga ƙabilun Yosef da Benyamin. Sunanta wani yanki ne na matan Isra’ila da ke kuka saboda mutanen Babila sun kashe ’ya’yansu ko kuma sun tafi da su.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba za ta bar kowa ya ta'azantar da ita ba, saboda 'ya'yanta sun mutu"
Mai magana yana maimaita kalmar don nuna ko dai Yahweh ya hukunta shi sosai ko kuma Ifraimu ya koyi abin da Yahweh yake so ya koya masa ta hanyar horonsa. Kalmomin "An hukunta ni" za a iya fassara su cikin aiki. AT: "Kun hukunta ni. Ee, kun hukunta ni mai tsanani" ko "Kun hukunta ni, kuma na koya daga gare ku lokacin da kuka hukunta ni"
Kalmomin "kunya" da "ƙasƙantattu" ma'anarsu abu ɗaya ne kuma sun ƙarfafa ra'ayin kunya. AT: "Na ji kunya gaba daya"
Yahweh yana magana da taushi, yana kokarin ta'azantar da mutane. Waɗannan tambayoyin ana iya fassara su azaman maganganu. AT: "Ifraim ɗana ne ƙaunatacce. Heana ƙaunatacce ne, mai farin ciki.
Waɗannan umarni da lokutan “kanka” da “naka” da “kai” ana magana da su ne zuwa “Isra’ila budurwa” kuma haka guda suke.
Allah yana magana ne akan Isra’ila da ta canza.
Yahweh yana gaya wa mutanensa cewa yana haƙuri da su domin ba sa masa biyayya. AT: "Kada ku yi jinkiri don fara yi min biyayya."
Anan wannan yana nufin mutanen Yahua.
Yerusalem tana saman dutse, kuma an gina haikalin a wuri mafi girma a Yerusalem. AT; "Bari Yahweh ya albarkaci waɗanda suke zaune a Yerusalem tare da Yahweh, inda haikalin yake"
Kalmar "gida" ishara ce ga dangin da ke zaune a gidan, a wannan yanayin jama'ar Isra'ila da mutanen Yahuda. Hakanan ana maganar gidan kamar fili ne wanda Yahweh zai shuka iri a ciki, kuma ana magana akan mutane da dabbobin da suke kiwon don abinci, madara, da fatu kamar su ɗin. AT: "Zan sa mutanen Isra'ila da na Yahuda su zama mutane da yawa tare da dabbobi da yawa"
"nemi hanyoyin da za mu tunɓuke su"
Yahweh yana magana kansa da sunansa don bayyana tabbacin abin da yake furtawa. AT: "wannan shi ne abin da Yahweh ya bayyana" ko "wannan shi ne abin da ni, Yahweh, na ayyana"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna jaddada cewa dokar Yahweh za ta zama ɓangare a cikinsu, maimakon kawai a rubuce a kan dutse. Anan "zuciya" tana wakiltar "motsin rai" ko "hankali." AT: "Dokata za ta kasance wani ɓangare na tunaninsu da motsin zuciyar su"
Wannan jumlar tana nufin kowane mutum, daga ƙarami mai mahimmanci zuwa mafi mahimmanci. AT: "kowane ɗayansu"
Waɗannan jimlolin suna nuni ne ga dukan halitta.
Ana maganar lokaci na gaba kamar "ranaku suna zuwa." AT: "nan gaba ... za a sake gina birni" ko "za a sami wani lokaci ... lokacin da za a sake gina garin"
Waɗannan su ne sunayen wuraren.
1Wannan ce maganar da ta zo wa Irmiya daga Yahweh a shekara ta goma ta sarautar sarki Zedekiya na Yahuda, a shekara ta sha takwas ta Nebukadnezza.2A wannan lokaci, sojojin sarkin Babila sun yi wa Yerusalem sansani, Annabi Irmiya kuma yana cikin kurkukun harabar 'yan tsaro dake cikin gidan sarkin Yahuda.3Zedekiya sarkin Yahuda ya sanya shi cikin kurkuku ya kuma ce, "Me yasa kake anabci kana cewa, 'Yahweh ya faɗi wannan: Duba, ina gab da miƙa wannan birni cikin hannun sarkin Babila, kuma zaya ci shi da yaƙi.4Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kubce ba daga hannun Kaldiyawa, gama babu shakka za a miƙa shi cikin hannun sarkin Babila. Bakinsa kuma za ya yi magana da bakin sarkin, idanunsa kuma zasu ga idanun sarkin.5Za ya ɗauki Zedekiya zuwa Babila, zaya zauna a can har sai na gama horar da shi - wannan furcin Yahweh ne. Koda yake za ka yi yaƙi da Kaldiyawa, ba zaka yi nasara ba."'6Irmiya ya ce, "Maganar Yahweh tazo gare ni, tana cewa,7'Duba, Hanamel ɗan Shallum kawunka na zuwa wurin ka kuma zai ce, "Ka saiwa kanka gonata da ke Anatot, domin kai ne ka ke da 'yancin sayen ta.""'8Daga nan, kamar yadda Yahweh ya furta, Hanamel, ɗan-ɗan kawuna, Yazo wuri na a harabar 'yan tsaro, sai ya ce da ni, "Ka sayi gonata dake a Anatot cikin ƙasar Benyamin, domin kai ne ke da 'yancin gãdo, kuma 'yancin saye na gare ka. Ka sai wa kanka." Daga nan na sani cewa wannan maganar Yahweh ce.9Sai na sayi gonar da ke Anatot daga wurin Hanamel, ɗan-ɗan kawuna, sai na gwada mashi azurfar, shekel sha bakwai a nauyi.10Sai na rubuta a takarda na hatimce ta, na kuma kawo shaidu su shaida. Sai na gwada mashi azurfar a ma gwaji.11Sai na ɗauki takardar kammala saye da aka hatimce, bisa ga shari'a da ka'idoji, da kuma takardar kammala saye da ba a hatimce ba.12Sai na bada hatimtacciyar takardar ga Baruk ɗan Neriya ɗan Masiyya a gaban Hanamel, ɗan kawuna, da kuma shaidun da suka sa hannu a hatimtacciyar takardar, a kuma gaban Yahudawan da ke zaune a harabar 'yan tsaron.13Sai na bada umarni ga Baruk a gaban su. Nace,14Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Karɓi takardunnan, dukkan takardun kammala sayen da wannan da aka hatimce da waɗannan da ba a hatimce ba, sai ka sanya su a cikin tukunyar ƙasa domin suyi ƙarko na dogon lokaci.15Gama Yahweh Mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Za a sake sayen gidaje, da gonaki, da garkunan inabi a cikin wannan ƙasar."16Bayan da na bada rasiɗin saye ga Baruk ɗan Neriya, sai nayi addu'a ga Yahweh nace,17Kaito, Ubangiji Yahweh! Duba! Kai ka ɗai ka halitta Sammai da duniya ta wurin babban ƙarfinka da ɗagaggen hannunka. Babu abin da ka faɗa wanda zai gagare ka ka yi.18Kana nuna amintaccen alƙawarinka ga dubbai kana kuma zubo da tsarguwar mutane bisa cinyoyin 'ya'yansu bayansu. Kai ne mai girma Allah mai iko kuma; Yahweh Mai runduna ne sunanka.19Kai babba ne a hikima mai girma kuma cikin ayyuka, idanunka a buɗe suke ga dukkan hanyoyin mutane, domin kaba kowanne mutum abin da ya cancanci halinsa da ayyukansa.20Ka yi alamu da al'ajibai a ƙasar Masar. Har yazuwa yau a nan ƙasar Isra'ila da kuma cikin dukkan 'yan adam, kasa sunanka ya zama sananne.21Gama ka fito da mutanenka Isra'ila daga ƙasar Masar da alamu da al'ajibai, da hannu mai ƙarfi, da ɗagaggen hannu, da kuma babbar razana.22Daga nan ka basu wannan ƙasar - wanda ka rantsewa Ubanninsu zaka basu - ƙasar dake zubo da madara da zuma.23Sai suka shiga suka mallake ta. Amma ba su yi biyayya da muryarka ba ko suka zauna cikin biyayya da shari'arka ba. Ba su yi komai ba game da abin da ka umarce su su yi, sai ka kawo dukkan wannan bala'i a kansu.24Duba! Tarin sansanin ya kai har birnin domin ya ci shi da yaƙi. Gama saboda Takobi, da yunwa, da annoba, an bayar da birnin cikin hannun Kaldiyawa da suke yaƙi da shi. Gama abin da kace zaya faru yana faruwa, kuma duba, kana kallo.25Daga nan kai da kanka kace mani, "Ka sai wa kanka gona da azurfa kuma ka kawo shaidu su shaida, duk da cewar ana bayar da wannan birni a hannun Kaldiyawa."26Maganar Yahweh ta zo ga Irmiya, tana cewa,27Duba! Ni ne Yahweh, Allahn dukkan 'yan adam. Akwai abin da ya gagare ni in yi?28Saboda haka Yahweh ya faɗi wannan, "Duba, ina gab da bayar da wannan birni cikin hannun Kaldiyawa da Nebukadnezza, sarkin Babila. Za ya ci shi da yaƙi.29Kaldiyawan da ke yaƙi da birnin nan za su zo su cinna mashi wuta su ƙone shi, tare da gidajen da ke kan rufin wuraren da mutane ke yiwa Ba'al sujada suke kuma zuba baye-bayen shayarwa ga wasu alloli domin su cakune ni.30Gama mutanen Isra'ila da Yahuda babu shakka mutane ne da ke ta aikata mugunta a gaban idanuna tun daga ƙuruciyarsu. Babu shakka mutanen Isra'ila sun ɓata mani rai ta wurin ayyukan hannuwansu - wannan furcin Yahweh ne.31Yahweh ya furta cewa wannan birni na tunzura fushina da hasalata tun daga ranar da aka gina shi. Haka yake har zuwa wannan rana. To zan kawar da shi daga fuskata32saboda dukkan muguntar mutanen Isra'ila da ta Yahuda, abubuwan da suka yi domin su cakune ni - su, da sarakunansu, da dagatansu, da firistocinsu, da annabawansu, da kuma kowane mutum a Yahuda da dukkan mazaunan Yerusalem.33Sun juya mani bayansu a maimakon fuskokinsu, koda yake da ɗoki na koyar da su. Nayi ƙoƙari in koyar da su, amma babu wani cikinsu da ya saurara domin ya ɗauki gyara.34Suka jera haramtattun gumakansu a cikin gidan da ake kira da sunana, suka gurɓata shi.35Suka gina dogayen wurare domin Ba'al a kwarin Ben Hinnom domin su sanya 'ya'yansu maza da mata cikin wuta domin Molek. Ban umarcesu ba. Bai taɓa shiga tunanina ba cewa zasu aikata wannan abin ƙyama su sa Yahuda ya yi zunubi.'36To saboda haka yanzu, Ni, Yahweh, Allah na Isra'ila, Na faɗi wannan game da birnin, birnin da kuke cewa, 'An bayar da shi cikin hannun sarkin Babila ta wurin takobi, da yunwa, da annoba.37Duba, ina gab da tattaro su daga kowace ƙasa inda na kora su cikin fushina, da hasalata, da babban jin haushina, Ina gab da maido su cikin wannan wuri in kuma sa su iya zama cikin tsaro.38Daga nan zasu zama mutanena, Ni kuma in zama Allahnsu.39Zan basu zuciya ɗaya da hanya ɗaya na girmama ni kullum domin ya zama alheri a gare su da kuma zuriyarsu bayansu.40Daga nan tare da su zan kafa madawwamin alƙawari, cewa bazan juya daga yi masu alheri ba. Zan sa girmamawa domi na a zukatansu, ta haka ba zasu sake juyawa daga gare ni ba.41Daga nan zan yi farinciki wurin yi masu alheri. Da aminci zan dasa su cikin ƙasar nan da dukkan zuciyata da dukkan raina.42Gama Yahweh ya faɗi wannan, 'Kamar yadda na kawo dukkan wannan babban bala'i a bisa mutanen nan, haka zan kawo masu dukkan abubuwan alherin da nace zan yi domin su.43Daga nan za a sayi gonaki a cikin wannan ƙasar, wadda kuke cewa, "Wannan busasshiyar ƙasa ce, wadda babu mutum balle dabba. An bayar da ita cikin hannun Kaldiyawa."44Za su sayi gonaki da azurfa su kuma rubuta cikin hatimtattun takardu. Zasu tattara shaidu a cikin ƙasar Benyamin, a dukkan kewayen Yerusalem da biranen Yahuda, a cikin birane a cikin garuruwan tudu da kuma ƙasashen kwari, da kuma biranen Negeb. Gama zan maido da kaddarorinsu - wannan furcin Yahweh ne."'
Wannan yanki ne da ke hade da fadar sarki wanda ke kewaye da gine-gine kuma a ciki suke tsare fursunoni.
Zedekiya ya yi amfani da tambaya don tsawata wa Irmiya. AT: "Ba dai-dai ba ne a gare ku ku ci gaba da annabci da faɗi"
Yahweh yana maganar birni kamar ƙaramar abu ce da wani zai iya ba wa wani. Kalmar "hannu" alama ce ta iko ko iko da hannu ke yi. AT: "Ina gab da sanya wannan birni a ƙarƙashin ikon sarkin Babila" ko "Zan kusan barin sarkin Babila ya yi abin da ya ga dama da wannan birni"
Anan “baki” da “idanu” suna wakiltar mutum duka. AT: "Zedekiya da kansa zai gani kuma ya yi magana kai tsaye tare da Nebukadnezza"
Waɗannan sunayen maza.
Shekel gram 11 ne. AT: "shekel 17" ko "gram 187"
"da mutane sun kalle ni na sayi filin saboda su iya fadawa wasu cewa na sayi filin"
Waɗannan sunayen maza ne.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutanen Isra'ila za su sake siyan gidaje, gonakin inabi da filaye a cikin wannan ƙasar"
Wannan yana nufin hatimin da aka liƙa da maɓallin da ba a rufe ba.
Kalmomin "ɗaga hannu" ishara ce don ƙarfin hannu, saboda haka kalmomin "ƙarfinku mai girma" da "ɗaga hannunku da aka ɗaga" sun zama rubanya. AT: "ta karfinku mai girma"
Kalmar nan "laifi" ƙira ce ta nuna wa Yahweh horo saboda mutane da laifin aikata mugunta. Ana yin magana game da azabtar da mutane kamar Yahweh yana zuba babban akwati cike da ruwa ko ƙananan abubuwa a cikin ƙasan mutane yayin da suke zaune. AT: "kuna azabtar da yara saboda zunuban iyayensu"
Bude idanu wata alama ce ta abin da mutum ya gani. Yadda mutum yake rayuwa ana maganarsa kamar yana tafiya akan hanya. AT: "Kun ga duk abin da mutane suke yi"
Nau'in suna "gudanarwa" da "ayyuka," waɗanda suke daidai da ma'ana, ana iya fassara su azaman kalmomi. AT: "kuma zai sakawa kowa gwargwadon yadda kyawawan abubuwan da suke aikatawa suke"
Wannan yana nufin wani abin da ya faru a dā lokacin da Allah ya yi amfani da ikonsa ya ’yantar da Isra’ilawa daga bautar ƙasar Masar.
Kalmomin "hannu mai ƙarfi" alama ce ta ƙarfi, kuma kalmar "ɗaga hannu" ta nuna alama ce ta ƙarfin hannu, don haka jimlolin "hannu mai ƙarfi" da "ɗaga hannu" suka zama rubanya. AT: "ta karfinku mai girma"
"ƙasar da madara da zuma ke gudana." Allah yayi magana game da kasar tana da kyau ga dabbobi da tsirrai kamar su madara da zuma daga wadancan dabbobi da tsirrai suna yawo a cikin kasar. AT: "ƙasar da ke da kyau don kiwon dabbobi da noman amfanin gona"
Muryar wani magana ga saƙon da mai magana ke ba shi. AT: "Amma ba su yi biyayya ga abin da kuka ce ba"
Manyan tarin datti da duwatsu waɗanda abokan gaba suka gina a kewayen garin don su tsaya a kansu kuma su kai masa hari ana maganarsu kamar su ne maharan da kansu suka kai ƙwace garin. AT: "Tudun tudu na abokan gaba sun yi kusa da birni cewa abokan gaba za su iya kame garin"
Anan “hannu” na nufin iko ko iko. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "kun ba Yerusalem ga sojojin Kaldiya"wa
Yahweh yayi amfani da tambaya don jaddada cewa zai iya yin komai. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Babu abin da ya min wuya in yi."
"don in yi fushi ƙwarai"
A nan kamfani "idanu" yana wakiltar abin da Allah yake gani. Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) "yin abin da na ɗauka na mugunta" ko 2) "aikata mugunta da sanin ina kallo"
Mutum saurayi kwatanci ne ga jama'ar Isra'ila da farko ya zama al'umma.AT: "tun suna ƙuruciya" ko "daga lokacin da suka zama al'umma"
Anan "birni" na wakiltar ga mutanen da suke zaune a can. Kalmomin "fushi" da "fushi" ma'ana abu ɗaya ne kuma suna jaddada yadda yake fushin sosai. AT: "mutanen Yerusalem sun fusata ni sosai tun ranar da suka gina garinsu"
"Suna ci gaba da fusata ni ko da yanzu"
Mutum ya juya fuskarsa ga wani don nuna cewa yana sauraro, da bayansa ya nuna wanda ya ƙi saurara. AT: "Maimakon su saurare ni da kyau, sai suka ƙi sauraren kwatakwata" ko "Sun ƙi saurara"
"don koyon yadda ake aiki dai-dai"
Anan “suna” yana wakiltar Yahweh. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "gidan da yake nawa" ko "ginin da suke bauta min a ciki"
Anan "ku" jam'i ne. Zai yiwu ma'anoni su ne 1) wannan yana nufin Irmiya da waɗanda suke tare da shi, ko kuma 2) yana nufin duka mutane.
Anan “hannu” na nufin iko ko iko. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya ba da shi ga sarkin Babila" ko "Yahweh ya ba wa sarkin Babila iko ya mallake ta"
Mutanen Isra'ila za su so yin aiki tare don girmama Yahweh.
"madawwami yarjejeniya"
"ka daina yin alheri"
Anan "su" yana nufin mutanen Isra'ila.
Yahweh yayi maganar sa mutanensa su zauna a ƙasar har abada kamar suna dasa shukoki a cikin lambu. AT: "Zan zauna har abada Isra'ilawa a cikin wannan ƙasar"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Sa'annan mutane za su sayi filaye a wannan ƙasar"
Anan "hannu" yana nufin metonym don iko ko sarrafawa. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya ba shi ga Kaldiyawa" ko "Yahweh ya ba wa Kaldiyawa iko a kansa"
"Rubutun da aka hatimce" su ne ayyukan da mutum zai sa hannu don siyan ƙasa. Sauran mutane za su kasance shaidu don tabbatar da sayan.
1Daga nan maganar Yahweh ta zo ga Irmiya karo na biyu, yayin da yake kulle a harabar 'yan tsaro, cewa,2"Yahweh mahalicci, ya faɗi wannan - Yahweh, wanda yake halittawa domin ya tabbatar-Yahweh ne sunansa,3Ku kira gare ni, Ni kuma zan amsa maku. Zan nuna manyan abubuwa a gare ku, asirai da baku fahimta ba.'4Gama Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan game da gidajen da ke cikin wannan birni da gidajen sarakunan Yahuda waɗanda suka rushe saboda mamayewar sansani da takobi,5Kaldiyawa suna zuwa su yi yaƙi su kuma cika waɗannan gidaje da gawawwakin mutane waɗanda zan kashe cikin fushina da hasalata, yayin da na ɓoye fuskata daga wannan birni saboda dukkan muguntarsu.6Amma duba, Ina gab da kawo warkarwa da lafiya, zan warkar da su in kawo masu yalwa, salama da aminci.7Gama zan maido da kaddarorin Yahuda da Isra'ila; Zan kuma gina su kamar da farko.8Daga nan zan tsarkake su daga dukkan kurakuran da suka yi a gare ni. Zan gafarta dukkan kurakuran da suka yi a gare ni, da kuma dukkan hanyoyin da suka yi tsayayya a gare ni.9Gama wannan birni zai zame mani abin farinciki, waƙar yabo da girmamawa daga dukkan al'umman duniya waɗanda zasu ji dukkan abubuwan alheri da zan yi domin shi. Daga nan zasu ji tsoro su girgiza saboda dukkan abubuwan alheri da salama da zan bayar a gare su.10Yahweh ya faɗi wannan, 'A wannan wurin wanda yanzu kuke cewa, "Kufai ne, wurin da babu mutum balle dabba," a biranen Yahuda da kuma titunan Yerusalem waɗanda suke kufai babu mutum balle dabba, da za a sake ji a ciki11Ƙarar farinciki da ƙarar murna, ƙarar ango, da ƙarar amarya, ƙarar waɗanda suka ce, yayin da suke kawo baye-bayen godiya ga gidan Yahweh, "Ku bada godiya ga Yahweh Mai runduna, gama Yahweh nagari ne, kuma ƙaunarsa marar kasawa ta dawwama har abada!" Gama zan maida kaddarorin ƙasar nan kamar yadda suke a dã,' inji Yahweh.12Yahweh Mai runduna ya faɗi wannan: 'A wannan kufan wuri, inda yanzu babu mutum balle dabba-a dukkan biranen za a sami saura inda makiyaya zasu hutar da garkunansu.13A cikin biranen da ke ƙasar tudu, da kwari, da kuma Negeb, a cikin ƙasar Benyamin da dukkan kewayen Yerusalem, da kuma cikin biranen Yahuda, garkuna kuma zasu sake bi ta ƙarƙashin hannuwan masu ƙirga su,' inji Yahweh.14Duba! kwanaki na zuwa - wannan furcin Yahweh ne-inda zan aikata abin da na yi alƙawari game da gidan Isra'ila da kuma gidan Yahuda.15A cikin waɗannan kwanaki da kuma cikin wannan lokaci zan sa reshen adalci ya tsiro domin gidan Dauda, zaya aiwatar da hukunci da kuma adalci a cikin ƙasar.16A waɗannan kwanaki za a ceci Yahuda, Yerusalem kuma zata zauna cikin tsaro, gama ga yadda za a kira ta, "Yahweh ne adalcinmu."'17Gama Yahweh ya faɗi wannan: 'Daga zuriyar gidan Dauda ba za a taɓa rasa mutum da zaya zauna a kursiyin gidan Isra'ila ba,18ko kuwa a rasa mutum daga Lebiyawa firistoci da zaya tsaya a gabana ya ɗaga baye-baye na ƙonawa ba, ya ƙona baye-bayen abinci ba, ya kuma aiwatar da baye-baye na hatsi a dukkan lokaci."'19Maganar Yahweh ta zo ga Irmiya, cewa,20Yahweh ya faɗi wannan: 'Idan zaku iya karya alƙawarina da rana da dare yadda ba za a sake yin rana ko dare ba a lokuttansu,21to zaku iya karya alƙawarina da Dauda bawana, yadda ba za a sake samun ɗan da zai zauna a kursiyinsa ba, da kuma alƙawarina da Lebiyawa Firistoci bayina.22Kamar yadda baza a iya ƙirga rundunar sama ba, ko kuma a iya gwada yashin da ke bakin teku, hakanan zan kawo ƙaruwa ga zuriyar Dauda bawana da kuma Lebiyawa da ke bauta a gabana."'23Maganar Yahweh ta zo ga Irmiya, cewa,24"Ba ku yi la'akari da abin da mutanen nan suka furta ba da suka ce, 'Iyalai biyu da Yahweh ya zaɓa, yanzu ya watsar da su'? Ta wannan hanya sun wulaƙanta mutanena, suna cewa ba al'umma ba ce kuma a gaban mu.25Ni, Yahweh, Na faɗi wannan, 'Idan da ban kafa alƙawarin rana da dare ba, ban kuma kafa dokokin sama da duniya ba,26to shi ne zan watsar da zuriyar Yakubu da Dauda bawana, har da ba zan kawo wani daga gare su ba da za ya yi mulki bisa zuriyar Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu ba. Gama zan maido da kaddarorinsu in nuna masu jinƙai."'
Wannan yanki ne da ke hade da fadar sarki wanda ke kewaye da gine-gine kuma a ciki suke tsare fursunoni. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Irmiya 32: 2.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. Mai yiwuwa ma'anonin su ne 1) mutane sun rusa gidaje don yin bango don kare Kaldiyawa. AT: "cewa mutane sun ruguza don kare shinge da takobi" ko kuma 2) AT: "gidajen da Kaldiyawa suka rurrushe don yin tudun mun tsira don su yi yaƙi"
Kalmomin "fushi" da "fushi" suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna ƙarfafa tsananin fushinsa. AT: "cikin tsananin fushina"
"Zan sa abubuwa su zama lafiya ga Yahuda da Isra'ila kuma" ko "Zan sa Yahuda da Isra'ila su sake rayuwa da kyau." Duba yadda ake fassara kalmomi masu kama da haka a cikin Irmiya 29:14.
Kalmar "waƙa" ishara ce ta abin da mutane za su rera waƙar game da shi. AT: "wani abu game da shi wanda dukkanin kungiyoyin duniya za su rera waƙoƙin yabo da girmamawa a gare ni, Yahweh"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa Yahuza ta zama kango.
Wannan yana nufin aikin makiyayi yana kirga tumakinsa yayin da tumaki ke tafiya karkashin hannunsa. AT: "makiyaya za su sake ƙidaya tumakinsu kamar yadda tumakin ke tafiya"
Ana maganar lokaci na gaba kamar "Kwanaki suna zuwa." AT: "Nan gaba ... zan yi" ko "Za a sami lokacin ... lokacin da zan yi"
Kalmar "gida" ishara ce ga dangin da ke zaune a gidan. A wannan yanayin yana nufin mulkin Isra'ila ... Yahuda.
"ɗan zuriyar Sarki Dauda"
Waɗannan kalmomin suna fara bayanin zato wanda ke bayyana halin da ba zai taɓa faruwa ba.
Ba wanda zai iya ƙidaya taurari a sararin sama, ko yashi a bakin teku, ba wanda zai iya ƙidaya zuriyar Dauda da Lebiyawa waɗanda suke bauta wa Yahweh.
Ana amfani da wannan karin magana don gabatar da saƙo na musamman daga Allah. AT: "Yahweh ya ba wa Irmiya saƙo. Ya ce," ko "Yahweh ya yi wannan saƙon ga Irmiya:"
1Maganar da ta zo wurin Irmiya daga Yahweh, lokacin da NebuKadnezza sarkin Babila da dukkan rundunarsa, tare da dukkan sarakunan duniya, su harabobin da ke a ƙarkashin ikonsa, kuma dukkan mutanensu suna zuwa yaƙi gãba da Yerusalem da dukkan biranenta, cewa:2'Yahweh, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Jeka ka yi magana da Zedekiya sarkin Yahuda ka kuma ce masa, 'Yahweh ya faɗi wannan: Duba, ina gab da miƙa wannan birni cikin hannun sarkin Babila. Zai ƙone shi.3Ba zaka tsira daga hannunsa ba, gama lallai za a kama ka a miƙa ka a cikin hannunsa. Idanunka za su dubi idanun sarkin Babila; zai yi magana da kai fuska da fuska yayin da kake tafiya zuwa Babila.'4Saurari maganar Yahweh, Zedekiya sarkin Yahuda! Yahweh ya faɗi wannan game da kai, 'ba za ka mutu ta hanyar takobi ba.5Za ka mutu cikin salama. Kamar yadda aka yi wa kakanninka jana'izar ƙonawa, sarakuna magabatan ka, haka za su ƙone jikinka. Za su ce, "kaito, shugaba!" Za su yi maka makoki. Yanzu dai na faɗi_ wannan furcin Yahweh ne."6Sai Irmiya annabi ya furta wa Zedekiya sarkin Yahuda dukkan waɗannan maganganu a Yerusalem.7Rundunar sarkin Babila suka yi yaƙi da Yerusalem da dukkan sauran biranen Yahuda: Lakish da Azeka. Waɗannan biranen Yahuda sun kasance kamar birane masu tsaro mai ƙarfi.8Maganar da ta zo ga Irmiya daga wurin Yahweh bayan da Zedekiya sarki ya yi alƙawari da dukkan mutanen Yerusalem, domin ya furta 'yanci gare su da9cewa bari kowane ya 'yantar da bawansa Bayahude, namiji da ta mace, wato mutum na iya ɗaukan bawa Ba-yahude, wanda ya ke ɗan uwansa.10Sai dukkan shugabanni da mutanen suka ɗauki alƙawari kowannensu da cewa su 'yantar bayinsu maza da mata domin kada su sake zama bayi. Suka yi biyayya su ka 'yantar su.11Amma bayan haka sai suka canza zuciyarsu. Suka dawo da bayin da suka 'yantar. Suka tilasta masu su sake zama bayi.12Sai maganar Yahweh ta zo ga Irmiya, cewa,13"Yahweh, Allah na Isra'ila, yana cewa, 'Ni da kaina na yi alƙawari da ubanninku a ranar da na fito da su daga ƙasar Masar, daga gidan bauta. A wannan lokaci ne na ce,14A duk ƙarshen kowacce shekara bakwai, kowanne mutum dole ya 'yantar da ɗan'uwansa, BaIbrane wanda ya sayar da kansa gare ka ya kuma yi maka bauta na shekaru shida. Ka sake shi ya tafi cikin 'yanci." Amma ubanninku ba su saurare ni ba ko su ba da kunnuwansu gare ni.15Yanzu ku da kanku kuka tuba ku ka fara ayyukan da ke dai-dai a gabana. Ku ka furta yanci, kowanne mutum ga maƙwabcinsa, kuma ku ka yi alƙawari a gabana a wannan gida da ake kiransa da sunana.16Amma kuka juya ku ka ƙazamtar da sunana; kuka sa kowanne mutum ya dawo da bayinsa maza da mata, waɗanda kuka 'yantar domin su tafi inda ransu ke so. Ku ka tilasta masu su sake zama bayinku.'17Saboda haka Yahweh ya faɗi wannan, 'Ku da kanku ba ku saurare ni ba. Dama kun furta 'yanci, kowannen ku, zuwa ga 'yan'uwanku da dangi Isra'ilawa. Don haka duba! Ina dab da furta 'yanci gare ku--- wannan furcin Yahweh ne- 'yanci ga takobi, ga annoba, da yunwa, gama zan maishe ku abin tsoro a fuskar kowacce masarauta a duniya.18Sa'an nan zan hori mutanen da suka karya alƙawarina, waɗanda suka ƙi su kiyaye maganganun wannan alƙawari wanda suka ɗauka a gabana a lokacin da suka yanka bajimi kashi biyu suka kuma ratsa tsakanin kason,19daga nan sai shugabannin Yahuda da na Yerusalem, da bãbãnni da kuma firistoci, da kuma dukkan mutanen ƙasar suka ratsa tsakanin bajimin.20Zan ba da su cikin hannun maƙiyansu da kuma cikin hannun waɗanda suke neman rayukansu. Jikkunansu zasu zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namomin jeji a duniya.21Haka zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda da shugabanninsa cikin hannun makiyansu da kuma cikin hannun waɗanda suke neman ransu, da kuma cikin hannun rundunar sarkin Babila da ya tashi tsaye gãba da ku.22Duba, ina dab da bãda ummarni--- wannan furcin Yahweh ne-- kuma zan dawo da su zuwa ga wannan birni su kuma yaƙe shi su kuma karɓe shi, su kuma ƙona shi. Gama zan juyar da birnin Yahuda zuwa yasassun kufai inda ba za a sami mazauna cikinsa ba."
Wannan yana nufin duk garuruwan da ke kewaye da Yerusalem.
Anan kalmar "hannu" ishara ce ta kulawar da hannu ke yi. AT: "Ba za ku kuɓuta daga ikonsa ba"
Kalmar "takobi" wani magana ce ta mutuwa a yaƙi. AT: "Ba za ku mutu a yaƙi ba"
Waɗannan su ne sunayen garuruwa.
"Kawai garuruwan Yahuda masu garu waɗanda Babiloniyawa ba su kama su ba tukuna"
Ana amfani da wannan karin magana don gabatar da saƙo na musamman daga Allah. Koyaya, ainihin sakon baya farawa har sai Irmiya 34:12. AT: "Yahweh ya ba wa Irmiya sako" ko "Yahweh ya yi magana da Irmiya"
"Kowane ɗayanku ya 'yanta wa' yan'uwansa Ibraniyawa waɗanda suka sayar da kanku gare ku, suka zama bayinku"
"Dole ne ka sake su daga bautar da kake yi"
"Idanu" a nan metonym ne don ra'ayin mutum ko ra'ayinsa. AT: "abin da nake ganin ya dace"
Sunan mutum ishara ce ga abin da mutane suke ɗauka da shi. AT: "daina aikata abin da ke daidai kuma ya aikata mugunta waɗanda suka sa mutane suka ɗauka cewa ni mugu ne"
Irmiya ya yi amfani da baƙin ƙarfe ya ce '' 'yancin' 'da mutane za su more da gaske zai sha wuya. AT: "Zan sanar da ku masifa ... wahala daga takobi, annoba, da yunwa"
"yarda da ni" ko "kafa yayin da nake kallo"
Wannan hanya ce mai ladabi da za a ce suna son kashe su. AT: "neman kashe su"
"kawo sojojin Babila"
1Maganar da ta zo wurin Irmiya daga wurin Yahweh a kwanakin Yehoiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, cewa,2"Jeka wurin iyalin Rekabawa ka yi magana da su. Sai ka kawo su zuwa gidana, cikin ɗaya daga cikin ɗakunan da ke can, sai ka ba su inabi su sha."3Sai na ɗauki Ya'azaniya ɗan Irmiya ɗan Habazziniya tare da 'yan'uwansa, dukkan 'ya'yansa, da dukkan iyalin Rekabawa.4Sai na kawo su zuwa gidan Yahweh, zuwa cikin ɗakunan 'ya'yan Hanan ɗan Igdaliya, mutumin Allah. Waɗannan ɗakunansu na kurkusa da ɗakunan shugabanni, wanda ke sama da ɗakin Ma'aseiya ɗan Shallum, mai tsaron ƙofa.5Sai na ajiye kwanuka da kofuna cike da inabi a gaban Rekabawa na ce masu, "Ku sha inabi."6Amma suka ce, "ba za mu sha inabi ba, gama kakanmu, Yonadab ɗan Rekab, ya umurcemu, 'Kada ku sha kowanne inabi, ko ku ko zuriyarku, har abada.7Kuma, kada ku gina gidaje, ko ku shuka iri, ko ku shuka gonakin inabi; wannan ba na ku ba ne. Gama dole ku zauna cikin bukkoki dukkan kwanakinku, domin ku rayu da kwanaki masu yawa a cikin ƙasar da kuke zaman baƙunci.'8Mun yi biyayya da muryar Yonadab ɗan Rekab, kakanmu, cikin dukkan abin da ya umurce mu, da kada mu sha inabi a duk kwanakinmu, mu, da matayenmu, da 'ya'yanmu, da kuma 'ya'ya matanmu.9Ba zamu taɓa gina gidaje mu zauna ciki ba, ko mu yi gonar inabi, ko fili, ko mu ajiye iri wurinmu.10Mun daɗe da zama a cikin bukkoki kuma mun yi biyayya mun kuma aiwatar da dukkan abin da Yonadab kakanmu ya umurce mu.11Amma da Nebukadnezza sarkin Babila ya kawo farmaki ga ƙasar, muka ce, 'Zo, dole ne mu je Yerusalem domin mu tsira daga rundunar Kaldiyawa da Aremiyawa.' Shi ya sa mu ke zama a Yerusalem."12Sai maganar Yahweh ta zo ga Irmiya, cewa,13"Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka, 'Ka je ka ce da jama'ar Yahuda da mazauna Yerusalem, "Ba za ku karɓi gyara ku kuma saurari maganata ba?--- wannan shi ne furcin Yahweh.14Maganganun Yonadab ɗan Rekab da ya yi wa 'ya'yansa a matsayin umurni, kada su sha kowanne inabi, an yi la'akari da haka har zuwa yau. Sun yi biyayya da umurnin kakansu. Amma a nawa, Ni da kai na ina ta naciya wurin shaida maku, amma ba ku saurare ni ba.15Na aika zuwa gare ku dukkan bayina, su annabawa. Na yi naciya da aiken su su ce, 'Bari kowanne mutum ya juyo ga barin muguwar hanyarsa ya kuma aikata ayyuka na gari; kada wani ya sake yin tafiya bisa ga tafarkin wasu alloli ko ya kuma yi masu sujada. A maimakon haka, ku dawo zuwa ga ƙasar da na ba ku da kuma kakanninku.' Duk da haka ku ka ƙi ku saurare ni ko ku bada hankalinku gare ni.16Domin zuriyar Yonadab ɗan Rekab sun kula da umurnin kakansu da ya ba su, amma waɗannan jama'a suka ƙi su saurare ni."17Sai Yahweh, Allah mai runduna da kuma Allah na Isra'ila, ya faɗi haka, 'Duba, Ina kawo masifa bisa Yahuda da kuma bisa kowanne mai zama cikin Yerusalem, dukkan masifar da na furta game da su domin na yi magana da su, amma ba su saurara ba; Na yi kira gare su, amma ba su amsa ba."'18Irmiya ya cewa iyalin Rekabawa, "Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, na faɗin haka: Kun saurari umurnan Yonadab kakanku kuka kuma yi biyayya da su dukka- kun yi biyayya da dukkan abin da ya dokace ku ku yi-19sai Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, 'A kullum za a sami wani daga zuriyar Yonadab ɗan Rekab da zai bauta mani."'
Wannan kungiyar mutane ne.
Waɗannan sunayen maza.
Waɗannan sunayen maza.
"zauna shekaru masu yawa a cikin ƙasar." "Kwana" yana nufin tsayin lokaci. (Duba: synecdoche)
Kalmar "murya" yana nufin ta umarnin da Yonadab ya yi magana. AT: "umurnin Yonadab"
Yahweh yana gaya wa Isra'ilawa su saurari tsawatarwa a hankali. AT: "Lallai ne ku sami wannan gyara kuma ku saurari maganata."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "'Ya'yan Yonadab ɗan Rekab sun kiyaye umarnin mahaifinsu kada su sha ruwan inabi"
Bin bayan allah wani kwatanci ne na bin dokokin wannan allah.
Wannan kungiyar mutane ne.
Waɗannan sunayen maza.
1Sai ya kasance a cikin shekara ta huɗu ta Yehoyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, da wannan maganar ta zo ga Irmiya daga Yahweh, ya kuma ce,2"Ka ɗaukar wa kanka naɗaɗɗen littafi ka rubuta dukkan maganar da na faɗa maka game da Is'raila da Yahuda, da kowacce al'umma. Ka yi haka da duk abin da na faɗa tun daga zamanin Yosiya har zuwa yau.3Watakila jama'ar Yahuda za su saurara da dukkan masifar da na yi niyyar kawo wa bisan su. Watakila kowanne zai juyo daga barin muguwar hanyarsa, da haka zan gafarta kurakuransu da zunubansu."4Sai Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, sai kuma Baruk ya yi rubutu cikin naɗadɗen littafi, sa'ada da Irmiya ya ke magana, dukkan maganganun Yahweh da aka faɗa masa.5Bayan wannan Irmiya ya bada umurni ga Baruk. Ya ce, "Ina cikin kurkuku kuma ba zan iya zuwa gidan Yahweh ba.6Saboda haka sai ka tafi ka karanta daga cikin naɗaɗɗen littafin da ka rubuta daga maganar da na faɗa. A ranar azumi, dole ne ka karanta maganganun Yahweh jama'a suna sauraro cikin gidansa, haka kuma a cikin kunnuwan dukkan Yahuda waɗanda suka fito daga birane. Furta waɗannan maganganu a gare su.7Wataƙila roƙonsu na jinkai kai zuwa ga Yahweh. Wataƙila kowannen su zai juyo daga muguwar hanyarsa, da yake fushi da hasalar da Yahweh ya furta game waɗannan mutane masu zafi ne."8Sai Baruk ɗan Neriya ya aiwatar da dukkan abin da Irmiya annabi ya doka ce shi ya yi. Ya karanta maganganun Yahweh da babbar murya a cikin gidan Yahweh.9Sai ya zama kuma a cikin shekara ta biyar ga watan tara na Yehoiyakim ɗan Yosiya, sarkin Yahuda, sai dukkan jama'ar Yerusalem da kuma mutanen da suka zo Yerusalem daga biranen Yahuda suka yi shelar azumi don girmama Yahweh.10Sai Baruk ya karanta maganganun Irmiya da ƙarfi a cikin gidan Yahweh, daga cikin ɗakin Gemariya ɗan Shafan marubuci, a cikin harabar da ke bisa, dab da mashigin ƙofa ta gidan Yahweh. Ya yi wannan a kunnuwan dukkan jama'a.11Yanzu Mikaiya ɗan Gemaraya ɗan Shafan ya ji dukkan maganganun Yahweh daga cikin naɗaɗɗen littafi.12Ya gangara zuwa gidan sarki, zuwa ga ɗakin sakatare. Duba, dukkan shugabanni na nan zaune: Elishama sakatare, da Delaya ɗan Shemaya, da Elnatan ɗan Akbor, da Gemaraya ɗan Shafan, da kuma Zedekiya ɗan Hananiya, da dukkan shugabanni.13Sai Mikaiya ya kawo masu rahoton dukkan maganganun da ya ji Baruk ya karanta da ƙarfi jama'a suna saurare.14Sai dukkan shugabanni suka aiki Yehudi ɗan Netanaya ɗan Shelemaya ɗan Kushi, zuwa ga Baruk. Yehudi ya ce wa Baruk, "Ɗauki naɗaɗɗen littafin cikin hannunka, naɗaɗɗen littafin da ka karanta ga sauraron jama'a, ka kuma zo." Sai Baruk ɗan Neraya ya ɗauki naɗaɗɗen littafin cikin hannunsa ya tafi wurin shugabannin.15Sai suka ce masa, "Zauna ka kuma karanta muna jinka." Sai Baruk ya karanta naɗaɗɗen littafin.16Sai ya zama sa'ad da suka ji dukkan waɗannan maganganu, kowanne mutum ya juya yana kallon na kusa da shi cikin tsoro suka ce wa Baruk, "Dole ne mu kai rohoton dukkan waɗannan maganganu ga sarki."17Sai su ka tambayi Baruk, "Gaya mana, ta yaya ka rubuta dukkan waɗannan maganganu daga bakin Irmiya?18Baruk ya ce masu, "Ya furta dukkan maganganun gare ni, ni kuma na rubuta su da tawada cikin wannan naɗaɗɗen littafi."19Sai shugabannin su ka cewa Baruk, "Ka tafi, ka ɓoye kanka, da Irmiya, kuma. Kada ka bar wani ya san inda ku ke."20Sai su ka ajiye naɗaɗɗen littafin a cikin ɗakin Elishama sakatare, kuma suka tafi wurin sarki cikin haraba suka kuma faɗawa sarki komai.21Sa'annan sarki ya aiki Yehudi ya kawo naɗaɗɗen littafin. Yehudi ya ɗauko shi daga ɗakin Elishama sakatare. Sa'annan ya karanta wa sarki da dukkan shugabanni da suke tsayawa kusa da shi.22Yanzu sarki na zama a gida lokacin hunturu a cikin wata na tara, kuma wutar kasko na ci a gaban shi.23Ya zama kuwa da Yehudi ya karanta shafi uku ko huɗu, sarkin za ya datse su da wuƙa ya jefa cikin wuta cikin kaskon wuta har dukkan naɗaɗɗen littafin ya ƙare.24Amma babu wani ko sarki ko wani daga cikin bayinsa da ya ji dukkan waɗannan maganganun ya kuma tsorata, basu kuma yayyage tufafinsu ba.25Elnatan, da Delaya, da kuma Gemariya sun riga sun roƙi sarki da kada ya ƙona naɗaɗɗen littafin, amma ya ƙi ya sauraren su.26Sai sarkin ya umarci Yeramil, na dangi, da Seraya ɗan Aziriyel, da kuma Shelemiya ɗan Abdil domin su damƙe Baruk sakatare da kuma Irmiya annabi, amma Yahweh ya riga ya ɓoye su.27Sai maganar Yahweh ta zo wa Irmiya bayan sarki ya ƙona naɗaɗɗen littafin da kuma maganganun da Baruk ya rubuta daga furcin bakin Irmiya, cewa,28"Ka koma, ka ɗaukar wa kanka wani naɗaɗɗen littafi, ka kuma rubuta cikin sa dukkan maganganun da suke a cikin naɗaɗɗen littafin na farko, wanda Yehoyakim sarkin Yahuda ya ƙona.29Sa'annan dole ka faɗi wannan ga Yehoyakim sarkin Yahuda: 'Ka ƙona wannan naɗaɗɗen littafi, kana cewa, 'Don me ka yi rubutu a cikinsa, 'Sarkin Babila lallai zai zo ya hallakar da wannan ƙasar, gama za ya hallakar da mutum da kuma dabba a cikinta'?""'30Saboda haka Yahweh ya faɗi wannan game da kai, Yehoiyakim sarkin Yahuda: "Babu zuriyarka da za ta taɓa zama a kan kursiyin Dauda. Game da kai, gawarka za a jefa ta a waje cikin zafin rana da kuma cikin sanyin dare.31Gama zan yi maka horo, da zuriyarka, da kuma bayinka domin kurakuranku duka. Zan kawo a bisanka, da bisan dukkan mazamnan Yerusalem, da kuma a bisa kowanne mutum cikin Yahuda dukkan masifun da na tsoratar daku da su, amma baku ba da hankali ga wannan ba."32Sai Irmiya ya ɗauko wani naɗaɗɗen littafi ya kuma miƙa shi ga Baruk ɗan Neriya marubuci. Baruk ya rubuta ciki daga bakin Irmiya dukkan maganganun da suka kasance a cikin naɗaɗɗen littafin da Yehoyakim sarkin Yahuda ya ƙona. Bugu da ƙari kuma, aka ƙara maganganu da yawa makamantan waɗannan cikin wannan naɗaɗɗen littafin.
Yehoyakim ya yi sarautar Yahuda fiye da shekara uku. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Irmiya 25: 1.
"daga lokacin da Yosiya yake sarauta har zuwa yau"
Yahweh yana maganar salon rayuwar mutum kamar yana da "hanya" ko hanyar da mutum yake bi. AT: "muguwar hanyar rayuwarsa"
"A lokacin da Irmiya yake magana, Baruk ya rubuta a littafin da dukan maganar Ubangiji wadda Yahweh ya faɗa wa Irmiya"
"don haka dukan mutanen Yahuza waɗanda suka zo daga garuruwansu za su iya jin su."
"Yahweh zai ji su suna rokon jinƙai kuma suyi kamar yadda suka roƙa"
Yahweh yana maganar salon rayuwar mutum kamar yana da "hanya" ko hanyar da mutum yake bi. AT: "muguwar hanyar rayuwarsa"
Wannan shine wata na tara a kalandar Ibraniyanci. Lokaci ne na ƙarshen Nuwamba da kuma farkon ɓangaren Disamba akan kalandar Yamma. "bayan Yehoyakim ... ya yi sarautar Yahuda fiye da shekaru huɗu, a cikin watan tara"
Wannan sunan mutum ne.
"a ƙofar sabon ƙofar gidan Yahweh"
"zuwa dakin magatakarda"
"duk sauran jami'an"
Kalmar "su" tana nufin jami'ai a cikin Irmiya 36:12.
"don haka za mu iya jin kun karanta shi" Duba yadda aka fassara kalmomin irin wannan a cikin Irmiya 2: 2.
Ana amfani da wannan jimlar a nan don yiwa wani muhimmin al'amari alama a cikin labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
"yaya aka yi ka rubuta"
"sanya littafin a dakin Elishama yadda zai zama lafiya"
"kasko yana gabansa da wuta mai kuna"
"zai yanke wannan bangare na gungura kashe"
"har sai da takardar ta tafi gaba daya"
"ya roƙi sarki"
Waɗannan sunayen maza.
"ɗauki wani gungura don kanka kuma"
Yehoyakim ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa bai kamata Irmiya ya rubuta cewa sarkin Babila zai zo ya kawo hari ba. AT: "Bai kamata ku rubuta ... dabba a ciki ba!" ko "Ka yi kuskure da ka rubuta ... dabba a ciki"! "
Zama a kan karagar mulki alama ce ta mulki a matsayin sarki. AT: "zai kasance yana mulkin Isra'ilawa kamar yadda Dauda ya yi"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane zasu jefa gawar ku a waje"
Cikakken sunan "shifta" ana iya fassara shi azaman kalma. AT: "yayin da Irmiya yake magana, Baruch ya yi rubutu a kai"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Bugu da ƙari, Irmiya da Baruch sun ƙara kalmomin nan masu yawa waɗanda suka yi daidai da kalmomin da ke cikin littafin na farko"
1Yanzu Zedekiya ɗan Yosiya ya yi sarauta a madadin Yehoiyacin ɗan Yehoyakim. Nebukadnezza sarkin Babila ya naɗa Zedekiya sarki bisa ƙasar Yahuda.2Amma Zedekiya, da bayinsa, da mutanen ƙasa ba su saurari maganganun Yahweh da ya furta ta hannun Irmiya annabi ba.3Sai sarki Zedekiya, da Yehukal ɗan Shelemiya, da kuma Zefanaya ɗan Maseya firist ya aika saƙo zuwa ga Irmiya annabi. Su ka ce, "Yi addu'a a madadinmu ga Yahweh Allahnmu."4Yanzu Irmiya na shigowa da fitowa a cikin mutanen, gama ba a rigaya an saka shi cikin kurkuku ba.5Rundunar Fir'auna suka fito daga Masar, sai kuma Kaldiyawa waɗanda suke kafa wa Yerusalem sansani suka ji labari game da su sai kuma su ka bar Yerusalem.6Sai maganar Yahweh ta zo ga Irmiya annabi, cewa,7"Yahweh, Allahn Isra'ila, ya faɗi wannan: Ga abin da za ka faɗi wa sarkin Yahuda, domin ya aike ka neman shawara wurina, 'Duba, rundunar Fir'auna, wacce ta kawo maku taimako, tana dab da komawa Masar, ƙasarta.8Su Kaldiyawa za su dawo. Za su yaƙi wannan birni, su karɓe shi, su kuma ƙona shi.'9Yahweh ya faɗi wannan: Kada ku ruɗi kanku kuna cewa, 'Hakika Kaldiyawan na tafiya suna barin mu,' domin ba za su tafi ba.10Ko da ace kun ci dukkan rundunar Kaldiyawan da yaƙi da ke yaƙi da ku da har ace raunannun mutane ne aka bari cikin runfunansu, za su tashi sama su kuma ƙone wannan birnin."11Haka ya zama lokacin da rundunan Kaldiyawa su ka bar Yerusalem lokacin da rundunar Fir'auna ke gabatowa,12sai Irmiya ya fito Yerusalem domin ya tafi kasar Beyamin. Ya bukaci ya mallaki wani ɗan fili a nan a tsakanin mutanensa.13Sa'ad da ya ke a bakin Ƙofar Benyamin, wani shugaban matsara na wurin. Sunansa Iriya ɗan Hananiya. Ya riƙe annanbi Irmiya gama kuma ya ce, "Kana zanzarewa zuwa ga Kaldiyawa."14Amma Irmiya ya ce, "Wannan ba gaskiya ba ne. Ba zanzarewa na ke yi ba zuwa ga Kaldiyawa." Amma Iriya ya ƙi ya saurare shi. Ya ɗauki Irmiya ya kawo shi wurin shugabanni.15Shugabannin suka ji haushin Irmiya. Suka yi ma sa duka suka sa shi cikin kurkuku, wanda ya ke cikin gidan Yonatan marubuci, gama sun maishe shi kurkuku.16Sai aka sa ka Irmiya cikin kurkuku na ƙarƙashin ƙasa, inda ya zauna ranaku da yawa.17Sai sarki Zedekiya ya aika da wani wanda ya kawo shi zuwa ga fada. A gidansa, sarkin ya tambaye shi a asirce, "Akwai wata magana daga Yahweh?" Irmiya ya amsa, "Akwai magana: Za a miƙa ka cikin hannun sarkin Babila."18Sai Irmiya ya ce wa sarki Zedekiya, "Ta yaya na yi maka zunubi, ko bayinka, ko waɗannan mutane da har ka saka ni cikin kurkuku?19Ina annabawanka, waɗanda suka yi maka anabci kuma suka ce sarkin Babila ba zai zo gãba da kai ko gãba da wannan birnin ba?20Amma ka saurara yanzu, shugabana sarki! Bari roƙona shi zo gare ka. Kada ka maida ni zuwa ga gidan Yonatan marubuci, don kada in mutu a can."21Sai sarki Zedekiya ya ba da umarni. Bayinsa suka tsare Irmiya cikin harabar matsara. Aka ba shi curin gurasa kowace rana daga layin matoya, har sai da dukkan gurasar ta ƙare cikin birnin. Haka Irmiya ya zauna cikin harabar matsaran.
Rubutun Ibraniyanci yana da "Koniya," wanda shine bambancin sunan "Yehoiyakin." Yawancin sifofin zamani suna da "Yehoiyakin" don a bayyane cewa ana magana da sarki ɗaya.
"Yahweh ya furta"
Hannun magani ne na mutum. AT: "ya sa annabi Irmiya ya yi shela"
Duba yadda kuka fassara sunayen waɗannan mutanen a cikin Irmiya 21: 1.
Anan "zuwa da dawowa" wani karin magana ne wanda ke nufin ya sami 'yanci motsawa. AT: "Irmiya ya sami damar zuwa duk inda yake so tare da kowa"
Kalmar "kai" tana nufin mutane biyu waɗanda sarki Zedekiya ya aika wa Irmiya, da Yehukal ɗan Shelemiya, da Zafaniya ɗan Ma'aseya, firist.
Kalmar "ni" tana nufin Yahweh.
Kwatanta yadda kuka fassara "don yaƙi da shi da ɗaukar shi, da ƙona shi" a cikin Irmiya 34:22..
Kalmar "kanku" tana nufin Sarki Zedekiya da sauran mutanen Yahuda.
Mutanen Yahuda suna ganin za su tsira domin Kaldiyawa sun tafi. AT: "Tabbas muna cikin aminci saboda Kaldiyawa suna barinmu"
"Ya zo game da hakan." Ana amfani da wannan jumlar a nan don alamar farkon sabon ɓangaren labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
"wani yanki"
"a cikin danginsa." Irmiya ya fito ne daga garin Anatot a ƙasar Bienyamin.
"karya ne"
"Yonatan, wanda yake marubuci ne." Wannan sunan mutum ne.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "jami'an sun sanya Irmiya a cikin wani daki wanda yake ƙarƙashin ƙasa"
Kalmar "hannu" alama ce ta iko ko iko da hannu ke yi. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Lallai zan sanya ku ƙarƙashin ikon Sarkin Babila" ko "Lallai zan ba sarkin Babila damar yin duk abin da yake so tare da ku"
Irmiya ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa bai yi wani laifi ba. AT: "Ban yi muku wani laifi ba ... kurkuku."
Irmiya ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa sauran annabawan suna ƙarya amma bai yi wani laifi ba domin ya faɗi gaskiya. AT: "Annabawanku da suka yi annabci ... a kan wannan ƙasar ba shakka sun yi kuskure, amma yanzu ya bayyana cewa gaskiya na gaya muku."
"ba za su kawo muku hari ko kuma kai hari wannan ƙasa ba"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Har ila yau bayinsa sun ba Irmiya gurasa"
"daga titin da masu yin burodin ke aiki"
1Shefatiya ɗan Matan, da Gedaliya ɗan Fashhur, da Yehukal ɗan Shelemiya, da kuma Fashhur ɗan Malkiyah su ka ji maganganun da Irmiya ya ke furtawa ga dukkan mutanen. Yana cewa,2"Yahweh ya faɗi haka: Duk mai zama cikin wannan birni za a kashe shi da takobi, da yunwa, da kuma annoba. Amma kowanne da ya fita zuwa ga Kaldiyawa za shi rayu. Zai tsira da ransa, shi rayu.3Yahweh ya faɗi wannan: Wannan birni za a ba da shi ga hannun rundunar sarkin Babila, kuma za ya karɓe shi."4Sai shugabannin suka ce wa sarkin, "Bari wannan mutum shi mutu, gama ta wannan hanya yana raunanar da hannuwan mazaje mayaƙa waɗanda suka rage a wannan birni, da kuma hannun dukkan mutane. Ya na furta waɗannan maganganu, gama wannan mutum bai kula da lafiyar waɗannan mutane ba, sai dai bala'i."5Sai sarki Zedekiya ya ce, "Duba, yana cikin hannunku da shi ke babu sarkin da ya isa shi yi tsayayya da ku."6Sai su ka ɗauki Irmiya su ka jefa shi cikin ramin Malkiyah, ɗan sarki. Ramin na cikin harabar masu tsaro. Suka zurara Irmiya ƙasa da igiyoyi. Babu ruwa cikin ramin, amma taɓo ne, sai kuma ya nutse ƙasa cikin taɓon.7Yanzu Ebed Melek Ba-Kushi yana cikin ubanni na gidan sarki. Ya ji cewa an jefa Irmiya cikin rami. Yanzu sarkin yana zama a Kofar Benyamin.8Sai Ebed Melek ya tafi daga gidan sarki ya yi magana da sarki. Ya ce,9"Shugabana sarki, waɗannan mutane sun aikata mugunta ta yadda suka yi da Irmiya annabi. Sun jefar da shi cikin rami domin ya mutu cikinsa da yunwa, tun da babu wani abincin da ya rage cikin birnin."10Sai sarkin ya bada umurni ga Ebed Melek Ba-Kushe. Ya ce, "Ka ɗauki shugabancin mutane talatin daga nan ka kuma ciro annabi Irmiya daga ramin kamin ya mutu."11Sai Ebed Melek ya ɗauki shugaban waɗannan mutanen ya tafi gidan sarki, zuwa ga ɗakin ajiyar kaya na ƙarƙashin gidan. Daga nan ne ya ɗauko tsummokara da kuma koɗaɗɗun kaya sai kuma ya zurara su da igiyoyi ga Irmiya cikin ramin.12Ebed Melek mutumin Kush ya cewa Irmiya, "Sanya tsummokaran da koɗaɗɗun kayan a ƙarƙashin hannunka da kuma bisa igiyoyin." Irmiya kuwa ya yi haka.13Sai suka jawo Irmiya da igiyoyin. Da haka suka fito da shi daga cikin ramin. Irmiya kuma ya zauna cikin harabar masu tsaro.14Sai sarki Zedekiya ya aika magana ya kuma kawo Irmiya annabi wurin sa, zuwa cikin mashigi na uku cikin gidan Yahweh. Sarkin ya cewa Irmiya, "Ina so in tambaye ka wani abu. kada ka hana mani amsar."15Irmiya ya ce da Zedekiya, "Idan na amsa maka, lallai ba za ka kashe ni ba? Amma idan na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba."16Amma sarki Zedekiya ya rantse wa Irmiya a asirce ya kuma ce, "Na rantse ga Yahweh mai rai, wanda ya yi mu, ba zan kashe ka ba ko in miƙa ka cikin hannuwan waɗannan mutanen nan da suke neman ranka ba."17Sai Irmiya annabi ya cewa sarki Zedekiya, "Yahweh, Allah mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka: Idan ka fita zuwa ga shugabannin Babila za ka rayu kuma ba za a kone wannan birni ba. Kai da iyalin ka za ku rayu.18Amma idan ka ƙi fita zuwa ga shugabannin sarkin Babila, to za a miƙa wannan birnin cikin hannun Kaldiyawa. Za su kona shi, kai kuma ba za ka tsira daga hannun su ba."19Sarki Zedekiya ya cewa Irmiya, "Amma ina jin tsoron mutanen Yahuda waɗanda suka ƙaurace zuwa ga sansanin Kaldiyawa domin ana iya miƙa ni cikin hannuwansu, domin su wulaƙanta ni sosai."20Irmiya ya ce, "Ba zasu miƙa ka cikin hannuwansu ba. Kai dai ka yi biyayya da saƙon Yahweh da nake faɗa maka, domin komai ya zamar maka lafiya lau, domin kuma ka rayu.21Amma idan ka ƙi ka fita, wannan shi ne abin da Yahweh ya nuna mani.22Duba! Dukkan matayen da aka rage a gidanka, sarkin Yahuda, za a fito da su zuwa ga shugabannin sarkin Babila. Waɗannan matayen za su ce maka, 'Abokananka sun ruɗe ka; sun rusar da kai. Ƙafafunka yanzu sun nutse cikin taɓo, kuma abokanka za su gudu.'23Gama dukkan matayen ko da 'ya'yanka ma za a fito da su zuwa ga Kaldiyawa, kai kuma da kanka ba za ka tsira daga hannunsu ba. Za a kama ka ta hannun sarkin Babila, kuma za a ƙona wannan birnin."24Sai Zedekiya ya cewa Irmiya, "Kada ka sanar da kowa game da wannan maganganu, don kada ka mutu.25Idan shugabannin suka ji labari na yi magana da kai, idan kuma suka zo su ka ce maka, "Ka faɗi mana abin da ka faɗi wa sarki kuma kada ka ɓoye mana, ko mu kashe ka,26sa'annan dole za ka amsa masu da cewa, na yi roƙo ne da zuciya ɗaya ga sarki da kada ya komar da ni gidan Yonatan don kada in mutu a can."27Sai dukkan shugabannin suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi abin da ya gaya wa sarki, shi kuma sai ya amsa masu yadda sarki ya umarce shi da ya faɗi. Sai suka daina magana da shi, domin ba su ji tattaunawar da aka yi tsakanin Irmiya da sarkin ba.28Sai Irmiya ya zauna a cikin harabar masu tsaro har zuwa ranar da aka karɓe Yerusalem.
Waɗannan sunayen maza
Wanda ya ba da kansa ga Babiloniyawa zai tsere da rai, kodayake zai rasa dukiyarsa.
Kalmar "hannu" alama ce ta iko ko iko da hannu ke yi. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan ba sojojin sarkin Babila damar cin Yerusalem"
Hannaye masu rauni sunaye ne ga mutumin da yake tsoro. AT: "yana sa sojoji da duk mutanen garin su rasa ƙarfin gwiwa"
"Gama Irmiya baya aiki don ya taimaki mutanen nan ya zama lafiya, amma yana aiki ne don mummunan abubuwa su faru da mutanen nan"
Wannan yanki ne da ke hade da fadar sarki wanda ke kewaye da gine-gine kuma a ciki suke tsare fursunoni.
Wannan yana nuna yadda "suka jefa shi cikin rijiyar."
Wannan sunan wani mutum ne daga Kush.
A nan kalmar "yanzu" alama ce ta layin babban labari inda mai ba da labarin ke ba da bayanan baya game da abin da sarki yake yi.
Wataƙila Sarki Zedekiya yana saurara kuma yana yin shari’a.
"anyi amfani da igiyoyi don saukar dasu"
"tsakanin hannayenka da igiyoyi"
A nan kalmar "su" tana nufin wasu daga cikin mutum talatin da suke tare da Ebed-Melek.
Irmiya ya yi amfani da wannan tambayar don bayyana imaninsa cewa sarki zai kashe shi idan ya amsa da gaskiya. AT: "Idan na faɗi gaskiya, lalle za ku kashe ni"
"Kamar yadda Yahweh, wanda ya halicce mu, yake da rai." Wannan hanya ce ta yin alkawari mai girma. Sarkin ya faɗi hakan ne don jaddada cewa abin da zai faɗa na gaba gaskiya ne. AT: "Na rantse da Yahweh, wanda ya halicce mu"
Wannan jimlar tana wakiltar so ko ƙoƙarin kashe wani. AT: "ƙoƙarin kashe ku"
Sunan rukunin mutane suna ne ga mutanen wannan rukunin. AT: "Allah na mutanen Isra'ila"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "sojojin Babila ba za su ƙone wannan birni ba"
Kalmar "hannu" ta nufin ta iko da hannu ke yi. AT: "ba za ku kuɓuta daga ikonsu ba"
Kalmar "hannu" alama ce ta iko ko iko da hannu ke yi. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Kaldiyawa na iya sanya ni ƙarƙashin ikon mutanen Yahuda waɗanda suka gudu" ko "Kaldiyawa na iya ƙyale mutanen Yahuda waɗanda suka gudu su yi duk abin da suke so tare da ni"
A nan kalmar "su" tana nufin mutanen Yahuza da suka fice.
Kaldiyawa ba za su ba da ku ga Yahudiya ba. " Anan "ku" yana nufin Zedekiya.
A nan kalmar "wannan" tana nufin abin da Irmiya zai faɗa a gaba.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Abokanka sun yaudare ku"
Sarki yanzu ba shi da komai.
Kalmar "hannu" na nufin ta iko ko iko da hannu ke yi. AT: "ba zai tsere daga ikonsu ba"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "har zuwa ranar da sojojin Babila suka kame Yerusalem"
1A shekara ta tara na watan goma na Zedekiya sarkin Yahuda, Nebukadnezza sarkin Babila ya zo da dukkan rundunarsa gãba da Yerusalem ya kuma kafa mata sansani.2A shekara ta sha ɗaya da kuma wata na huɗu na Zedekiya, a rana ta tara ga wata, aka rusar da birnin.3Sai dukkan shugabannin sarkin Babila suka zo suka zauna a ƙofa ta tsakiya: Nagal Shareza, da Samgar Samgal Nebo, da kuma Sarsekim, shugaba mai muhimmanci. Nagal Shareza shugaba ne babba kuma dukkan sauran sun zama shugabannin sarkin Babila.4Sai ya zamana da Zedekiya sarkin Yahuda, da dukkan mayaƙan sa suka gan su, suka gudu. Suka fita da dare daga birnin ta hanyar gonar gidan sarki, ta cikin ƙofa ta tsakanin ganuwa biyun. Sarkin ya fita ta bangon hanyar Araba.5Amma rundunar Kaldiyawa suka runtume su suka kuma cimma Zedekiya a cikin filin Kogin Yodan kwari kusa da Yeriko. Sai suka cafko shi suka kawo shi wurin Nebukadnezza, sarkin Babila, a Ribla cikin ƙasar Hamat, inda Nebukadnezza ya yanke masa hukunci.6Sarkin Babila ya kashe 'ya'yan Zedekiya a fuskarsa a Ribla. Ya kuma kashe dukkan muhimman mutanen Yahuda.7Sai ya cire idanuwan Zedekiya ya kuma ɗaure shi da sarƙoƙin jan karfe domin ya tafi da shi Babila.8Sai Kaldiyawan suka ƙone gidan sarki da gidajen mutane. Suka kuma rushe ganuwar Yerusalem.9Nebuzaradan, hafsan masu tsaron sarki, ya kwashe sauran mutanen waɗanda aka rage cikin birnin zuwa bauta. Wannan ya haɗa har da waɗanda suka yi ƙaura zuwa ga Kaldiyawa da kuma sauran mutanen waɗanda aka rage cikin birnin.10Amma Nebuzaradan babban hafsan masu tsaron sarki ya bar sauran mutanen waɗanda suke fakirai waɗanda basu da wani abu na kansu su zauna a cikin Yahuda. Ya kuma ba su gonakin inabi da filaye a wannan rana.11Nebukadnezza sarkin Babila ya ba da umarni game da Irmiya ga Nebuzaradan hafsan masu tsaron sarki. Ya riga ya ce,12"Ka ɗauke shi ka kula da shi. Kada ka ji ma sa rauni. Yi ma sa duk abin da ya ce ma ka.13Sai Nebuzaradan hafsan masu tsaron sarki, Nebushazban babban bãbãn, Nagal Shareza babban shugaba, da dukkan muhimman shugabannin sarkin Babila su ka aiki mutane waje.14Mutanensu su ka ɗauki Irmiya daga harabar masu tsaro su ka miƙa shi cikin hannun Gedaliya ɗan Ahikam ɗan Shafan, ya kai shi gida, sai Irmiya ya zauna a tsakanin mutanen.15Yanzu dai maganar Yahweh ta zo ga Irmiya tun ya na a tsare a cikin harabar masu tsaro, cewa,16"Yi magana da Ebed Melek mutumin Kush ka ce, "Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Duba, ina dab da cika maganganuna da na furta game da wannan birni bala'i kuma ba alheri ba. Gama za su faru dukka a idanunka a wannan rana.17Amma zan cece ka a wannan rana- wannan ne furcin Yahweh- kuma ba za a bashe ka cikin hannun mutanen da ka ke jin tsoronsu ba.18Gama babu shakka zan tsirar da kai. Ba za ka faɗi ga takobi ba. Za ka tsira da ranka, tun da ka yarda da ni- wannan shi ne furcin Yahweh."
Wannan bayan Zedekiya ya zama Sarkin Yahuda fiye da shekaru goma, a cikin wata na huɗu na kalandar Ibrananci. Rana ta sha ɗaya tana kusa da farkon watan yuli a kan kalandar yamma. AT: "A rana ta tara ga watan huɗu na shekara ta goma sha ɗaya cewa Zedekiya ya zama sarki"
Waɗannan sunayen maza.
"a tsakiyar shiga garin." Abu ne gama gari ga shugabanni su zauna a ƙofar gari don tattauna muhimman batutuwa.
"Sun bar garin da daddare suna fita a hanyar a cikin lambun sarki"
Wannan ita ce ƙasa a ƙarshen kwarin.
"ya yanke shawarar yadda za'a hukunta shi"
"mutanen sarki suka makantar da Zedekiya." Yi amfani da kalmomin gama gari don makantar da mutum. A bayyane yake cewa Sarkin Babila ya zare idanun Zedekiya daga kansa. Ya kamata mai karatu ya kuma fahimci cewa wataƙila wasu sun taimaka wa Sarkin Babila ya makantar da Zedekiya.
Wannan sunan mutum ne.
Wannan tabbas shine gaba ɗaya. AT: "mutanen da har yanzu suke zaune a cikin birni"
Waɗannan sunayen maza.
Kila iya buƙatar bayyana bayyane mutanen da mai magana yake magana game da su. AT: "daga cikin mutanen da suka rage a Yahuda"
Karin magana "kalmar Yahweh ta zo ga" ana amfani da ita don gabatar da saƙo na musamman daga Allah. AT: "Yahweh ya ba da sako ga Irmiya yayin da yake ... matsara. Ya ce," ko "yayin da Irmiya yake ... tsare, Yahweh ya yi masa wannan saƙon:"
"Zan kawo masifa a kan wannan birni, ba kamar yadda na ce zan yi ba"
Anan "hannu" yana nufin iko. Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "mazan da kuke jin tsoro ba za su cutar da ku ba" ko "Ba zan bari kowa ya sanya ku ƙarƙashin ikon mutanen da kuke jin tsoronsu ba"
Takobin ishara ce don mutuwa a yaƙi. AT: "Ba wanda zai kashe ku da takobinsa" ko "Ba za ku mutu a yaƙi ba"
1Maganar ta zo wurin Irmiya daga wurin Yahweh bayan da Nebuzaradan babban hafsan masu tsaron sarki ya sa ke shi a Rama. Ya sami Irmiya a ɗaure da sarƙoƙi a tsakiyar dukkan 'yan sarƙar Yerusalem da Yahuda waɗanda aka kwashe zuwa ga ƙasar bauta a Babila.2Shugaban matsara ya ɗauki Irmiya ya kuma ce ma sa, "Yahweh Allahnka ya umarta wannan masifar domin wannan wurin.3Don haka Yahweh ya kawo hakan. Ya aikata kamar yadda ya umarta, tun da ku mutanen nan kun yi ma sa zunubi kuma ba ku yi biyayya da muryar sa ba. Shi ya sa wannan abu ya faru da ku mutanen nan.4Amma yanzu duba! Na sa ke ka yau daga sarƙokin da ke hannuwanka. Idan ka ga ya dace a idanunka ka bi ni zuwa Babila, sai ka bi ni, ni kuwa zan kula da kai. Amma idan ba ya dace a idanunka ba da ka biyo ni zuwa Babila, to kada ka yi haka. Duba dukkan ƙasar da ke a gabanka. Ka tafi duk inda ya ke da kyau da kuma dai - dai a idanunka ka tafi."5Da Irmiya ba ya amsa ba, Nebuzaradan ya ce, "Tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam ɗan Shafan, wanda sarkin Babila ya ɗora wa haƙin kula da biranen Yahuda. Ka zauna da shi a tare da sauran mutanen ko ka tafi ko inda da ya yi ma ka kyau a idanunka ka tafi." Sai hafsan masu tsaron sarki ya bashi abinci da 'yar kyauta, daga nan ya sallame shi.6Sai Irmiya ya tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam, a Mizfa. Ya zauna tare da shi a tsakiyar mutanen da aka bari cikin kasar.7Yanzu wa su hafsoshin Yahuda waɗanda har yanzu su na a cikin harabar-- su da mutanensu-- su ka ji cewa sarkin Babila ya ɗora Gedaliya ɗan Ahikam, gwamna bisa ƙasar. Sun kuma sa ke ji cewa ya sa shi a matsayin mai kula da mazajen, mataye, da yara waɗanda su ne fakiran mutane a cikin ƙasar, waɗanda ba a kwashe ga hijira zuwa ƙasar Babila ba.8Sai su ka tafi wurin Gedaliya a Mizfa. Waɗannan mutane su ne Ishmayel ɗan Netaniya; Yohanan da Yonatan, 'ya'yan Kariya; da Seraya ɗan Tanhumet; su 'ya'yan Ifai mutumin Netofatiyawa; da Ya'azaniya ɗan Ma'akatiyawa-- su da mutanensu.9Gedaliya ɗan Ahikam ɗan Shafan ya ɗauki alƙawari da su da 'ya'yansu ya ce masu, "Ka da ku ji tsoro da za ku bauta wa shugabannin Kaldiyawa. Ku zauna a cikin ƙasar ku kuma bauta wa sarkin Babila, da haka komai zai yi maku dai - dai.10Duba, ina zama a Mizfa domin in sami ganin Kaldiyawa da su ka zo gare mu. Sai ku girbe inabi, da kayan itatuwa na damuna, da kuma mai ku adana su a cikin dururruka. Ku zauna a biranen da ku ka mallaka."11Sai dukkan mutanen Yahuda da ke a Mowab, a tsakanin mutanen Ammon, da kuma cikin Idom, da kuma a kowacce ƙasa su ka ji cewa sarkin Babila ya bar ragowar Yahuda su zauna, har ya aza Gedaliya ɗan Ahikam ɗan Shafan bisan su.12Saboda haka dukkan mutanen Yahuda su ka dawo daga dukkan wuraren da aka tarwatsa su. Su ka dawo zuwa ga ƙasar Yahuda, zuwa ga Gedaliya a Mizfa. Su ka girbe inabi da amfanin itatuwa na damina mai yawan gaske.13Yohanan ɗan Kareya da dukkan shugabannin rundunar da su ke baje cikin ƙasar su ka zo wurin Gedaliya a Mizfa.14Su ka ce ma sa, "Ko ka sa ni da cewa Balis sarkin mutanen Ammon ya aiko Ishmel ɗan Netaniya da ya kashe ka?" Amma Gedaliya ɗan Ahikim bai yarda da su ba.15Sai Yohanan ɗan Kareya ya yi magana a asirce da Gedaliya a Mizfa kuma ya ce, "Ka bar ni in tafi in kashe Ismayel ɗan Netaniya. Babu wanda zai sani. Don me za shi kashe ka? Don me za a bar Yahuda da aka tara maka su wartwatsu kuma ragowar Yahuda su hallaka?16Amma Gedaliya ɗan Ahikam ya ce wa Yohanan ɗan Kareya, "Kada ka aikata wannan abu, gama ka na faɗin ƙarya ne bisa Ismayel."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda sojoji za su tafi da shi zuwa Babila a zaman talala"
AT: "Yahweh ya yi abin da ya gaya muku zai yi"
AT: "Tun da yake ku Yahudawa kun yi wa zunubi ga Yahweh, ba ku yi biyayya da umarninsa ba"
"daga cikin Yahuda"
"wanda ya zauna a Yahuda"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "waɗanda sojojin abokan gaba ba su aika zuwa Babila ba"
mutane daga yankunan Maakah
"yi rantsuwa ga kwamandojin Yahuda"
"Ku zauna a cikin biranensu"
"agowar mutanen Yahuda"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "inda mutanen Babila suka kora su"
Yohanan da kwamandojin sun yi amfani da tambaya ta lafazi don faɗakar da Gedaliah. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Ya kamata ku fahimci cewa Baalis, sarkin Ammonawa, ya aiko Isma'il ɗan Netaniya don ya kashe ku!"
"Babu wanda zaiyi tunanin nayi hakan"
Johanan yayi amfani da tambaya mai ma'ana don ƙoƙarin canza tunanin Gedaliya. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Bai kamata ku ƙyale shi ya kashe ku ba."
Yohanan yayi amfani da tambaya mai ma'ana don ƙoƙarin sa Gedaliya ya yi tunanin abin da zai faru idan Gedaliya ya aikata abin da Gedaliya yake shirin yi. AT: "Idan kuka yi haka, duk Yahuda da aka tara zuwa gare ku za a warwatse kuma ragowar Yahuda za a hallaka su."
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "kyale Kaldiyawa su halakar da ragowar Yahuda" ko "kuma su bar ragowar Yahuda su halaka"
1Amma ya kasance a wata na bakwai Ismayel ɗan Netaniya ɗan Elishama, daga gidan sarauta, da waɗansu shugabanni na sarki, su ka zo su goma tare da shi wurin Gedaliya ɗan Ahikam, Mizfa. Su ka ci abinci tare a can Mizfa.2Amma Ismayel ɗan Netaniya da mutanen nan goma da ke tare da shi su ka tashi suka farmaki Gedaliya ɗan Ahikam ɗan Shafan da takobi. Ismayel ya kashe Gedaliya, wanda sarkin Babila ya sa ya mulki ƙasar.3Daga nan sai Ismayel ya kashe dukkan mutanen Yahudiya da ke goyon bayan Gedaliya a Mizfa da mayaƙan Kaldiyawan da ya samu a can.4To a rana ta biyu bayan kisan Gedaliya, amma ba wanda ya sani.5Waɗansu mutane su ka zo daga Shekem, da kuma Shilo, da Samariya su tamanin waɗanda su ka aske gemunsu, su ka kuma kece tufafinsu, su ka yayyanka jikkunansu - ɗauke da baye - baye na abinci da turaren itacen lubban a hannuwansu don su je gidan Yahweh.6Sai Ismayel ɗan Netaniya ya tafi daga Mizfa don ya sadu da su akan hanyarsu ta komawa, suna tafe su na kuka. A lokacin da ya gansu sai ya ce da su, "Ku zo wurin Gedaliya ɗan Ahikam!"7Sai ya zamana bayan sun zo birnin, sai Ismayel ɗan Netaliya ya yayyanka su ya zura su cikin rami, tare da mutanen da ke tare da shi.8Amma akwai mutane goma daga cikinsu da su ka ce da Ismayel," kada ka kashe mu, don muna da tanaji a filin: da alkama, da sha'ir da mai da ruwan zuma." Don haka bai kashe su tare da abokan tafiyarsu ba.9Rijiyar da Ismayel ya zuba gawawwakin waɗanda ya kashe ta na da girma ita ce rijiyar da sarki Asa ya haƙa don kariya daga sarkin Ba'asha na Isra'ila. sai Ismayel ɗan Netaniya ya cikata da gawawwaki.10Abu na gaba shi ne Ismayel ya kame dukkan mutanen da ke a Mizfa, da 'ya'yan sarki 'yan mata da duk sauran mutanen da su ka ragu a Mizfa waɗanda Nebuzzradan shugaban masu tsaro ya ba Gedaliya ɗan Ahikam. To sai Ismayel ɗan Netaniya ya kame su ya tafi ya ƙetare da suzuwa wurin mutanen Ammon.11Amma Yohannan ɗan Kareya da dukkan hafsoshin da ke tare da shi suka ji dukkan muguntar da Ismayel ɗan Netaniya ya yi.12To sai su ka kwashi dukkan mutane don su yaƙi Ismayel ɗan Netaniya. su ka same shi a babban kwarin Gibeyon.13Sai ya zamana a lokacin da dukkan mutanen da ke tare da Ismayel su ka ga Yohanan ɗan Kareya da dukkan hafsoshin da ke tare da shi, sai suka yi murna.14Sai dukkan mutanen da Ismayel ya kame a mizfa su ka juya suka koma ga Yohannan ɗan Kareya.15Amma Ismayel ɗan Netaniya ya gudu tare da mutane takwas daga Yohannan. Ya je wurin mutanen Ammon.16Sai Yohannan ɗan Kareya da dukkan hafsoshin da ke tare da shi su ka kwashe mutanen daga Mizfa, suka kuɓutar da su daga Ismayel ɗan Netaniya. Hakan ya faru ne bayan Ismayel ya kashe Gedaliya ɗan Ahikan. Yohannan da abokan tafiyarsa su ka ɗauki ƙarfafan mazaje, da mayaƙa, da mata da yara, da bãbãnni waɗanda aka kuɓutar a Gibeyon.17Daga nan sai su ka je su ka ɗan tsaya a Gerut Kimham, wanda ke kusa da Betelehem. Su na tafiya don su je Masar18saboda Kaldiyawa. Suna tsoron su tunda yake Ismayel ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wanda sarkin Babila ya sa ya yi mulkin ƙasar.
Ana amfani da wannan jumlar a nan don alamar farkon sabon ɓangaren labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
Waɗannan sunayen maza ne.
Samun abubuwa a hannun anan mai yiwuwa kwatanci ne na ɗaukar waɗancan abubuwan ko samun su a cikin kayan su. AT: "a wurinsu"
Ana amfani da wannan jimlar a nan don yin alama a inda aikin ya fara. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
An bayyana a cikin Irmiya 41: 8 cewa Isma'il da mutanensa ba su kashe duka mutanen 80 ba. Kuna iya bayyana a nan cewa sun kashe yawancin mazajen 80. AT: "Isma'ilu ɗan Netaniya, tare da mutanen da suke tare da shi, suka kashe yawancin mutanen 80 kuma suka jefa su cikin rami"
kayayyakin da za a yi amfani da su don biyan bukatun na gaba
Anan Isma'il yana wakiltar kansa da mutanensa. AT: "An kama Isma'il da mutanensa"
"tafiya zuwa ƙasar Ammonawa"
Waɗannan sunayen maza ne.
" Suka same Isma'il da mutanensa"
Ana amfani da wannan jimlar a nan don yiwa wani muhimmin al'amari alama a cikin labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
Anan "mutane" na nufin waɗanda Isma'ilu da mutanensa suka kama.
"Shi" yana nufin Isma'ila wanda yake wakiltar kansa da mutanen takwas tare da shi. AT: "Sun je wurin mutanen Ammon"
Marubucin ya tsayar da labarin don komawa ga abin da ya gabata don a fahimci tsarin abubuwan da suka faru.
Wannan sunan wani wuri ne.
Ana nuna cewa suna tsoron kada Kaldiyawa su kawo musu hari. AT: "saboda suna tsammanin Kaldiyawa za su iya kawo musu hari"
Anan "ƙasa" tana wakiltar mutane. AT: "mai kula da mutanen Yahuda"
1Daga nan dukkan hafsoshin da Yohanan ɗan Keriya, da Yezaniya ɗan Hoshayiya, da dukkan mutanen tun daga ƙanana ya zuwa manya suka zo wurin annabi Irmiya.2Su ka ce da shi, "bari kukanmu ya zo gareka.3Kayi addu'a zuwa ga Yahweh Allahnka a madadinmu da muka ragu tun da ya ke ba mu da yawa, kamar yadda ka gani. Ka roƙi Yahweh Allahnka ya faɗa mana abin da za mu yi da kuma hanyar da za mu bi"4Annabi Irmiya ya ce da su, "Na ji ku. Duba, zan yi addu'a ga Yahweh Allahnku kamar yadda ku ka bukata. Kuma duk amsar da Yahweh ya bayar zan faɗa muku. Ba zan ɓoye muku komai ba."5Su ka cewa Irmiya, "Dama Yahweh ya zama amintaccen shaida na gaskiya a tsakaninmu, idan ba mu yi duk abin da Yahweh Allahn ka ya ce mu yi ba.6Ko da mai kyau ne ko kuma mara kyau, za mu yi biyayya da muryar Yahweh Allahnmu, wanda mu ke aiken ka wurinsa, don komai ya yi mana dai - dai a lokacin da muka yi biyayya da muryar Yahweh Allanmu."7Bayan kwana goma, maganar Yahweh ta zo wurin Irmiya.8Sai Irmiya ya kira Yohanan ɗan Kareya da dukkan hafsoshin da ke tare da shi, da kuma dukkan mutane daga ƙanana zuwa manya.9Sai ya ce da su, "Wannan shi ne abin da Yahweh Allah na Isra'ila - wanda ku ka aike ni wurin sa don in kai roƙonku gare shi - ya ce,10Idan kun koma wannan ƙasar ku ka zauna to zan gina ku ba zan keta ku ba; Zan dasa ku ba zan tuge ku ba, don zan kawar da masifar da na aukar a kan ku.11Kada ku ji tsoron sarkin Babila, wanda ku ke jin tsoro. Kada ku ji tsoron sa - wannan shi ne abin da yahweh ya furta - da shi ke Ina tare da ku don in cece ku in kuma kuɓutar da ku daga hannunsa.12Gama zan yi maku jinkai. Zan kuma ji tausayinku, zan kuma dawo da ku ƙasarku.13Amma in kun ce "ba za mu zauna a wannan ƙasa ba" - in ba ku saurari muryata ba, muryar Yahweh Allanku.14In kun ce, "A a! Za mu je ƙasar Masar, inda ba za mu ga wani yaƙi ba, inda ba za mu ji ƙarar ƙaho ba, kuma ba zamu ji yunwa domin abinci ba, can za mu zauna."15Yanzu sai ku saurari muryar Yahweh, ku da ku ka rage a Yahuda. Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, Ya faɗi wannan, 'In dai har ku ka je Masar, don ku je ku zauna a can,16To takobin da ku ke jin tsoro za ta kashe ku a can ƙasar Masar. Yunwar da ku ke damuwa a kanta yanzu za ta kora ku zuwa Masar, kuma za ku mutu a can.17Don haka duk waɗanda su ka gudu Masar don su zauna a can za su hallaka ta wurin takobi, da yunwa, ko annoba. Kuma ba wanda zai tsira daga wannan masifar da zan aukar masu.18Domin Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Kuma kamar yadda fushina ya yi ƙuna a kan mazauna Yeruselem, hakanan zan saukar da matsanancin fushina a kanku in ku ka je Masar. Za ku zama abin la'ana da reni, abin la'antawa, da abin ƙasƙantarwa, kuma ba za ku ƙara ganin wannan wurin ba.'"19Sai Irmiya ya ce,'" Yahweh ya faɗi wannan a kanku - ku da ku ka rage a Yahuda. Kada ku je Masar! Don tabbas kun san ni sheda ne a kanku a yau.20Domin kun yaudari kanku sosai a lokacin da ku ka aike ni ga Yahweh Allahnku ku ka ce, ka yi addu'a ga Yahweh Allahnmu dominmu. Duk abin da Yahweh Allahnmu ya ce, ka faɗa mana, za mu yi shi.'21Domin yau na ba ku rahoto, amma ba ku saurari muryar Yahweh Allahnku ko kuma duk abin da ya aiko ni wurinku.22To yanzu sai ku san cewa tabbas zaku mutu ta wurin takobi, da yunwa, da annoba, a wurin da kuke son ku tafi ku zauna."
Wannan hanya ce da za a koma ga mutane daga kowane matsayin zamantakewar. Anan "mafi ƙanƙanci" da "babba" suna wakiltar waɗanda suka fi ƙanƙanta da waɗanda suka fi muhimmanci. AT: "dukkan mutane daga kowane irin matsayin zamantakewar al'umma" ko "dukkan mutane, gami da mafi ƙanƙanta da mahimman mutane"
"Bari mu gabatar da bukatar mu ta gaggawa a gare ku." Cikakken sunan "roƙo" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "Saurari yadda muke roƙo tare da ku"
Kalmomin "kar a hana muku komai" wani karin magana ne da ke nufin sanar da wani abu. Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Zan gaya muku duk abin da Yahweh ya gaya mani"
Anan waɗannan kalmomin suna raba ma'anoni iri ɗaya. Sun bayyana Yahweh a matsayin mashaidi wanda ba wanda zai iya musanta shi. AT: "amintacce"
Mutanen sun ambaci duk iyakar don jaddada cewa za su yi biyayya ko da menene amsar Yahweh. AT: "Duk abin da ya amsa"
Wannan hanya ce da za a koma ga mutane daga kowane matsayin zamantakewar. Anan "mafi ƙanƙanci" da "babba" suna wakiltar waɗanda suka fi ƙanƙanta da waɗanda suka fi muhimmanci. AT: "ga dukkan mutane daga kowane matsayin zamantakewar al'umma" ko "ga dukkan mutane, gami da mafi ƙanƙanta da mahimman mutane"
Yahweh yana nuna wa Isra’ilawa kamar bango ne da za a iya gina ko ya rushe. AT: "Zan sa ku ci gaba kuma ba zan halakar da ku ba"
Anan ana magana da bala'i a matsayin wani abu da mutum zai iya sanyawa wani. AT: "Zan hana masifar da na haddasa ta same ku"
Kalmomin “ceton” da “ceto” suna nufin abu ɗaya kuma suna nanata cewa lalle ne, Yahweh zai cece. AT: "don ceton ku gaba ɗaya"
Anan "murya" tana wakiltar umarni. Rashin yin biyayya kamar mutane basu ji umarnin Yahweh ba. AT: "idan ba ku yi biyayya da dokokina ba, duk da cewa ni Yahweh ne, Allahnku"
Duk waɗannan kalmomin suna bayyana kasancewa cikin yaƙi ta hanyar ikon gani ko jin shi. AT: "inda ba za mu fuskanci wahalar yaƙi ba"
Ana amfani da yunwar abinci don bayyana yunwa.
Anan “takobi” yana wakiltar yaƙi. Ana magana game da Isra'ilawa da ke fuskantar yaƙi koda kuwa sun tafi Masar kamar takobi zai bi mutane. AT: "za ku fuskanci mummunan sakamakon yaƙi"
Isra'ilawa da suke fuskantar yunwa har a cikin Masarana magana da su kamar yunwa za ta bi su. AT: "Kuna damu da yunwa a Isra'ila amma idan kuka tafi Masar za ku sha wahala da yunwa a can"
Yahweh yana azabtar da mutane saboda ya fusata sosai an yi maganarsa kamar fushin ruwa ne da ya zubo kan mutane. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan yi fushi ƙwarai in hukunta ku" (Duba: figa_activepassive)
Duk waɗannan maganganun ma'anar abu ɗaya ne kuma suna jaddada irin mummunan halin da al'ummai zasu yiwa mutanen Yahuda bayan Yahweh ya hukunta su. AT: "Mutane za su firgita idan suka ga abin da ya faru da ku. Zasu la'anta ku kuma su yi muku ba'a"
Kalmomin "kasance mai shaida akan" kalma ce da ke nufin ba da gargaɗi. AT: "Na yi muku gargaɗi"
Wannan karin magana ne. AT: "za mu yi"
Anan “takobi” yana wakiltar yaƙi. Madadin fassara: "za ku mutu a yaƙi"
Sun so su zauna a Masar. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "a Masar, inda kuka yi tunanin za ku sami aminci"
1Sai ya zamana bayan Irmiya ya gama shaidawa mutane dukkan maganar Yahweh Allahnsu wadda Yahweh Allahnsu ya faɗi masa ya faɗa.2Azariya ɗan Hosheya, Yohanan ɗan Kareya, da dukkan mutane kangararru su ka ce da Irmiya, '"ƙarya ka ke faɗi. Yahweh Allanhmu bai aiko ka ka faɗi cewa kada ku je Masar ku zauna a can ba'3Domin Baruk ɗan Neriya ya na zuga ka ka bada mu a hannun Kaldiyawa, don kaima ka jawo mana mutuwa ka kuma mai da mu kamammu a Babila."4Domin haka Yohannan ɗan Kareya, da dukkan shugabannin mayaƙa da dukkan mutane su ka ƙi sauraron muryar Yahweh da ta ce su zauna a Yahuda.5Yohanan ɗan Kareya da shugabannin mayaƙa su ka kwashe dukkan waɗanda su ka rage a Yahuda waɗanda su ka dawo daga dukkan al'uman da aka warwatsa su su zauna a cikin ƙasar Yahuda.6Su ka kwashe maza da mata, da yara da 'ya'ya mata na sarki, da duk wanda Nebuzaradan, hafsan sarki da matsaran sarki, ya sa suka kasance tare da Gedeliya ɗan Ahikam ɗan Shafan. Hakannan su ka ɗauki Annabi Irmiya da Baruk ɗan Neriya.7Su ka tafi zuwa ƙasar Masar, a Tafenhes, saboda ba su saurari muryar Yahweh ba.8To sai maganar Yahweh ta zo ga Irmiya a Tafanhes, cewa,9"Ka ɗauki manyan duwatsu a hannunka, da kuma a gaban mutanen Yahuda, ka ɓoye su a kankare a gefen hanyar zuwa ƙofar gidan Fir'auna a Tafanhes."10Daga nan sai ka ce da su, Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila ya faɗi wannan, 'Duba ina gab da aika manzannina zuwa Babila a matsayin bayina. Zan kafa mulkinsa akan waɗannan duwatsu wanda kai Irmiya ka binne. Nebukadzza zai kafa daularsa a kansu.11Domin zai zo ya kawo hari ga ƙasar Masar. Duk wanda aka ƙaddara ga mutuwa zai mutu. Duk wanda aka ƙaddara ga bauta za a ɗauke shi zuwa bauta. Duk wanda aka ƙaddara ga takobi za a bada shi ga takobi.12Daga nan zan kunna wuta a haikalun allolin Masar. Nebukadnezza zai ƙone su ko kuma ya kwashe su. Zai tsarkake ƙasar Masar kamar yadda makiyaya ke tsabtace tufafinsu. Zai fita daga wurin nan da ɗaukaka.13Zai karye ginshiƙan nan na dutse na Heliyofolis a ƙasar Masar. Zai ƙone haikalun allolin Masar.'"
Ana amfani da wannan jumlar a nan don alamar farkon sabon ɓangaren labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
Waɗannan sunayen maza ne.
Anan "murya" tana wakiltar umarni. Kuma a nan "sauraro" na nufin "biyayya." AT: "ba zai yi biyayya da umarnin Yahweh ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "inda Yahweh ya warwatsa su"
Waɗannan sunayen maza ne
Wannan sunan garin ne.
Duk “kursiyin” sarki da “kango” ana amfani dasu don nuni ga ikon masarauta. AT: "Zan sa shi ya zama sarki a kan jama'ar Misira. Zai ɗora kursiyinsa da tanti a kan waɗannan duwatsun da kuka binne"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kowa zai mutu wanda na yanke shawara dole ne ya mutu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutanen Babila za su kama duk waɗanda na yanke shawara dole ne su shiga cikin bauta"
Anan “takobi” yana wakiltar yaƙi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kowa zai mutu a yaƙi wanda na yanke shawara zai mutu a yaƙi"
Wannan sunan birni ne. Sunan yana nufin "garin rana." A cikin wannan birni akwai haikalin da suke bautar allahn rana.
1Maganar ta zo ga Irmiya game da dukkan mutanen Yahudiya da ke zaune a ƙasar Masar, waɗanda ke zaune a Migdol, da Tafenhas, da Memfis, da ƙasar Fatros.2Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan: Ku da kan ku kun ga duk waɗannan masifu da na aukar a Yeruselem da dukkan biranen Yahuda. Duba, yau sun zama kangaye. Ba wanda zai zauna a cikinsu.3Wannan saboda miyagun abubuwan da su ka yi domin su yi mani laifi ta wurin zuwa su ƙona turare da kuma bautawa waɗansu alloli. Waɗannan alloli ne da ko su da kansu, ko ku, ko kakanninku ba su sani ba.'4Don haka na dinga aikawa da dukkan bayina annabawa gare su. Na aike su su ce, 'Ku dena aikata abubuwan ban ƙyamar da na ke ƙi.' ba su saurara ba.5Amma sun ƙi saurare. Suka ƙi maida hankali ko su juyo daga muguntarsu ta wurin ƙona turare ga wasu alloli.6Sai razanata da fushina su ka yi ƙuna a kan biranen Yahuda da titunan Yerusalem. Don haka suka zama kango da abin banzatarwa, kamar yadda ya ke a yau'7To yanzu Yahweh, Allah mai runduna Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, "Don me ku ke aikata babbar mugunta gãba da kanku? Don me ku ke jawowa kanku abin da zai sa a datse ku daga cikin Yahuda - mazaje da mataye, yara da jarirai? Ba za a rage ko ɗayanku ba.8Ta wurin aikin muguntarku kun yi ma ni laifi ta wurin ayyukan hannuwanku, ta ƙona turare ga waɗansu alloli a ƙasar Masar, inda ku ka je ku zauna. Kun je can ne don a hallaka ku, don ku zama la'antattu da abin reni a cikin dukkan al'umman duniya.9Kun manta da ayyukan muguntar da kakanninku su ka yi da muguntar da sarakunan Yahuda da matansu su ka yi? Kun manta da muguntar da ku da kanku da matanku ku ka aikata a cikin ƙasar Yahuda da titunan Yerusalem?10Har ya zuwa yau, ba su yi tawa'li'u ba. Ba su girmama shari'una ba ko dokokina da na sanya a gabansu ba, su da kakanninsu, ba su kuma yi tafiya a cikinsu ba.'11Don haka Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, "Duba, ina gab da sa fuskata gãba da ku don in kawo muku masifa in kuma hallakar da dukkan Yahuda.12Don zan kwashe sauran mutanen Yahuda waɗanda su ka je Masar su zauna a can. Zan yi wannan don dukkan su su hallaka a ƙasar Masar. Za su faɗi ta wurin takobi da yunwa. Tun daga ƙaraminsu har zuwa babbansu za su faɗi ta wurin takobi da yunwa. Za su mutu su kuma zama abin reni da abin ƙyama.13Don zan hori mutanen dake zaune a ƙasar Masar kamar yadda na hori mutanen Yeruselem da takobi, da yunwa. da annoba,14yadda ba wani ragowar Yahuda waɗanda su ka tafi su zauna a cikin ƙasar Masar da zai kucce ko ya tsira ko ya dawo ƙasar Yahuda, wadda su ke marmari su dawo su zauna; Ba waninsu da zai dawo, sai dai 'yan kima da su ka kutto a nan.'"15Daga nan duk waɗanda su ka san matansu na ƙona turare ga waɗansu alloli, da kuma dukkan matayen da ke a babbar taruwa, da dukkan mutanen da ke zaune a ƙasar Masar ta kwari da tudu, a Fatros su ka amsa wa Irmiya.16Su ka ce, "Game da maganar da ka faɗa, mana a cikin sunan Yahweh ba za mu saurare ka ba.17Don hakika za mu yi duk abin da mu ka ce za mu yi - ƙona turare ga sarauniyar sama da zuba baye - baye na sha a gabanta Kamar yadda kakanninmu, da sarakunanmu, da shugabanninmu su ka yi a titunan Yerusalem. Daga nan za mu ƙoshi da abinci mu wadatu, ba tare da fuskantar wata masifa ba.18Sa'ad da mu ka dena yin waɗannan wato ƙin miƙa baiko ga sarauniyar sama da kuma ƙin miƙa baye - baye na sha a gare ta, duk za mu talauce mu kuma mutu ta wurin takobi da yunwa."19Sai matayen suka ce, "lokacin da mu ke yin baye - baye na turare a gaban sarauniyar sama da zuba baye - baye na sha a gare ta, ashe saɓawa mazanmu muka yi da muka aikata waɗannan abubuwa, yin waina a cikin siffarta da kuma zuba baye - baye na sha gare ta?"20Daga nan sai Irmiya ya ce da dukkan mutanen -ga maza da mata, kuma dukkan mutanen da su ka amsa masa - ya yi shela ya ce,21"Ashe Yahweh bai tuna da turaren da ku ka ƙona a biranen Yahuda da titunan Yerusalem - ku da kakanninku, da sarakunanku da shugabanninku, da kuma mutanen ƙasar ba? Domin Yahweh ya tuna da wannan; ya fãɗo cikin tunaninsa.22Daga nan ba zai ƙara jurewa da shi ba saboda miyagun ayyukanku da ku ka yi, saboda ayyukan ban ƙyamar da ku ka aikata. Sai ƙasarku ta zama yassashiya, da abin reni, da la'anta ta zama ba wanda ke zaune a cikinta har ya zuwa yau.23Saboda kun ƙona turare kun kuma yi zunubi ga Yahweh, don kun ƙi sauraron muryarsa, da shari'unsa ba da kuma ƙa'idojinsa ba, ko alƙawaransa ba, da dokokinsa ba shi ya sa wannan masifar ta same ku kamar yadda ya ke a yau."24Sai Irmiya ya ce da dukkan taron mutanen da kuma dukkan matayen, "Ku ji maganar Yahweh, dukkan mutanen Yahuda da ke ƙasar Masar.25Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila ya faɗi wannan, 'Ku da matayenku duk kun furta da bakinku kun kuma ɗauki duk abin da ku ka ce,"Hakika za mu aiwatar da alƙawuran da mu ka yi cewa za mu yi sujada ga sarauniyar sama, mu kuma zuba baye-baye na sha a gareta." Yanzu sai ku cika alƙawuranku, ku kuma aikatasu.'26Don haka ku ji maganar Yahweh, ku dukkan mutanen Yahuda da ke a ƙasar Masar, duba na rantse da sunana mai girma - in ji Yahweh. Ba za a sa ke kiran sunana ta bakin wani daga cikin mutanen Yahuda ba a dukkan ƙasar Masar, ku da yanzu ke cewa, "Na rantse da ran Ubangiji Yahweh."27Duba, ina lura da su don in aukar masu da masifa ba abu na gari ba. Duk wani mutumin Yahuda da ke a Masar zai hallaka ta wurin takobi da yunwa har sai dukkan su sun ƙare.28Daga nan sai waɗanda su ka tsira daga takobin su dawo daga ƙasar Masar zuwa ƙasar Yahuda, 'yan kimansu kawai. Da haka dukkan waɗanda su ka ragu a Yahuda da suka je Masar don su zauna a can za su san ko maganar waye zata zama gaskiya - tawa ko tasu.29Wannan zai zamar maku alama - wannan shi ne furcin Yahweh - da na ke shirya maku a wannan wurin, don ku san cewa maganata tabbas za ta hare ku tare da masifa.'30Yahweh ya faɗi wannan, duba ina gab da in bada Fir'auna Hofra sarkin Masar ga hannun maƙiyansa da kuma hannun masu so su hallaka shi. Zai zama kamar yadda na ba da Zedekiya sarkin Yahuda ga sarki Nebukadnezza sarkin Babila, maƙiyinsa wanda ya biɗi ransa.'"
Ana nuna cewa kalmar da ta zo wurin Irmiya daga Yahweh ce. Ana amfani da wannan karin magana don gabatar da saƙo na musamman daga Allah. AT: "Wannan sakon da Yahweh ya ba Irmiya" ko "Wannan shi ne saƙon da Ubangiji ya yi magana da Irmiya"
Ana amfani da kalmar "kanku" don ƙarfafawa don ƙayyade mutanen Yahudiya waɗanda ke zaune a ƙasar Masar.
Yin magana da fushi da azabtar da mutane ana magana ne kamar fushin da fushin ruwa ne ana iya zuba kan mutane. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Na yi fushi sosai kuma na hukunta su"
Kalmomin "kango" da "lalacewa" ma'anarsu abu ɗaya ne. Tare suna jaddada cikakkiyar lalacewar Yahuda da Yerusalem. AT: "sun lalace gaba ɗaya" :
Yahweh yana amfani da waɗannan tambayoyin don tsawata wa mutane don aikata abubuwan da suka sa shi hukunta su. AT: "Kuna aikatawa ... kanku. Kuna haddasawa ... da jarirai."
Yahweh ya tsauta wa mutane saboda rashin tunani game da mugayen halayensu da yadda Yahweh ya hukunta su. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Kuyi tunanin abin da ya faru da ku da matanku lokacin da kuka aikata mugunta a ƙasar Yahuza da titunan Yerusalem."
Ana kiran Yerusalem ta ɓangaren garin da mutane suke tafiya. Wannan yana nufin mutane suna aikata mugayen abubuwa a wuraren taron jama'a. AT: "Yerusalem" ko "wuraren jama'a na Yerusalem"
Wannan karin magana yana nufin ya "yanke hukunci sosai." AT: "Na yanke shawara in yi adawa da ku"
Wannan hanya ce mai taushi da za a ce wani zai mutu.
Wannan hanya ce da za a koma ga mutane daga kowane matsayin zamantakewar. Anan "mafi ƙanƙanci" da "babba" suna wakiltar waɗanda suka fi ƙanƙanta da waɗanda suka fi muhimmanci. AT: "dukkan mutane daga kowane irin matsayin zamantakewar al'umma" ko "dukkan mutane, gami da mafi ƙanƙanta da mahimman mutane"
Anan "takobi" yana wakiltar abokan gaba ɗauke da makamai. AT: "ta hanyar sanya makiya kashe wasu daga cikinsu, wasu kuma yunwa ta kashe su, wasu kuma su mutu saboda cuta"
Wannan yana nufin yankin kudancin Masar. Wani lokaci ana kiranta "Fatros."
Anan "da sunan Yahweh" yana nufin "a cikin ikon Yahweh" ko "a matsayin wakilin Yahweh." AT: "Ba za mu yi biyayya ga wannan sakon da kuka ce Yahweh ya ce ku fada mana ba"
Wannan lakabi na allahiyar ƙarya da mutanen Yahuda suke bauta wa. Wannan baiwar allah kuma ana kiranta "Asherah."
Mutanen Yahuda suna tsammanin za su ci gaba saboda sarauniyar sama za ta albarkace su idan suka bauta mata.
Matan suna ikirarin ba su da laifi saboda mijinta ya yarda da abin da suke yi. AT: "mazajenmu sun san abin da muke yi ... mata."
Irmiya ya yi amfani da tambaya don tsawata wa mutanen. AT: "Lallai Yahweh ya san game da ... ƙasar."
"ya daina iya haƙuri da shi"
Ana iya sake bayyana wannan don cire sunayen suna "lalacewa," "tsoro," da "la'ana." AT: "Sannan Yahweh ya sa ba kowa a cikin ƙasar. Ya mai da shi wuri mai ban tsoro da ban tsoro. Mutane suna amfani da sunan don la'antar wasu. Kuma wannan haka yake har zuwa yau"
Anan “bakuna” da “hannuwa” suna wakiltar mutum duka. AT: "kun aikata abin da kuka alkawarta yayin da kuka faɗi"
"Kamar yadda Ubangiji Yahweh na da rai." Mutane suna amfani da wannan magana don nuna cewa abin da za su faɗa a gaba gaskiya ne. Wannan hanya ce ta yin alkawari mai girma. AT: "Na rantse da gaske" ko "Na rantse da Ubangiji Yahweh"
Yahweh yana jawo bala'i a kan mutane kamar yadda ya alkawarta an yi maganarsa kamar maganarsa za ta auka musu. AT: "abin da na fada zai faru kuma za ku sami bala'i"
Anan "hannu" yana wakiltar ƙarfi ko iko. AT: "Zan ba wa abokan gaba waɗanda suke son kashe Fir'auna Hofra, sarkin Masar, damar kayar da shi"
Wannan sunan mutum ne.
1Wannan ita ce maganar annabi Irmiya da ya faɗawa Baruk ɗan Neriya. Wannan ya faru a lokacin da ya rubuta a cikin naɗaɗɗen littafi wanda Irmiya ya yi masa shifta - wannan ya faru a watan huɗu na sarautar Yahoaikim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, sai ya ce,2Yahweh Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan a gareku, ina faɗa maka wannan Baruk:3Ku ka ce, 'Kaito na, domin Yahweh ya ƙara ƙunci ga raɗaɗina. Da nishe - nishena sun gajiyar da ni; ban sami hutu ba.'4Wannan shi ne abin da tilas za ka faɗa masa; Dubi abin da na gina, yanzu ina rushewa. Abin da na dasa, yanzu ina tumɓukewa - Zan yi wannan a dukkan duniya.5Amma ko kana begen manyan abubuwa domin kanka? Kada ka yi begen haka. Don duba, masifa za ta aukowa dukkan mutane - wannan furcin Yahweh ne - amma zan ba ka ranka a matsayin ganimarka a duk inda ka je.'"
Kalmomin "na doka" an fahimta. AT: "a shekara ta huɗu ta mulkin Yehoyakim"
"Gama na riga na wahala amma yanzu Yahweh ya sa ni cikin baƙin ciki kuma"
Ana iya bayyana kalmar ta "nishi" a matsayin "kuka". AT: "Na gaji saboda kuka sosai"
Yahweh yana gaya wa Irmiya abin da zai faɗa wa Baruk.
Yahweh yayi amfani da tambaya don bayyana cewa ya san Barukyana fatan wasu suyi masa ta musamman. AT: "Na san kuna fatan manyan abubuwa da kanku." ko "Na san kuna fatan wasu za su girmama ku."
1Wannan ita ce maganar Yahweh da ta zo wurin Irmiya annabi game da al'ummai.2Game da Masar: "Wannan game da sojan Fir'auna Neko ne, sarkin Masar da ke Karkemish a wajan kogin Yuferetis. Wannan shi ne sojan Nebudkadnezza sarkin Babila ya cinye a yaƙi a shekara ta huɗu ta mulkin Yehoyakim ɗan Yosiya, sarkin Yahuda:3A sami ƙananan garkuwoyi da manyan garkuwoyi a shirya su ka fita ka yi yaƙi.4Ka sa linzamin doki; Ka ɗaura sirdi ka kuma sa hular kwano; ka wasa mãshi ka ɗaura kayan yaƙi.5Me nake gani a nan? sun cika da fargaba suna kuma guduwa, don an yi nasara da sojojinsu. Suna gudu don neman tsira basa kuma waigen baya. Fargaba na ko'ina - wannan shi ne abin da Yahweh ya furta -6masu hanzari baza su iya gudu ba, sojojin kuma ba za su tsira ba. Sun yi tuntuɓe a arewa suka faɗi a gefen Kogin Yuferetis.7Wane ne wannan da ya tashi kamar Nilu, wanda ruwayensa ke tunbatsa sama da ƙasa kamar koguna?8Masar na tashi kamar Nilu, kamar kogunan da suke tumbatsa sama da ƙasa. Masar ta ce Zan tashi in rufe duniya. Zan hallakar da birane da mazaunansu.9Ku dawakai ku hau sama ku yi fushi, ku karusai. Bari sojoji su fita waje, Kush da Fut, mutanen da ke fasaha da garkuwa, da mutanen Ludim, mutanen da suka shahara a tanƙwara bakkunansu.'10Wannan ranar zata zama ranar ramako ce ga Ubangiji Yahweh mai runduna, zai kuma sakawa kansa akan magaftansa. Takobi za ta ci ta ƙoshi. zata ƙoshi da jininsu. Don za a yi hadaya ga Yahweh Ubangiji mai runduna a arewacin ƙasar a gefen Kogin Yuferetis.11Ku je Gileyad ku sami magani, budurwan Masar. A banza kuke sawa kanku magani mai yawa. Ba za ku warke ba.12Al'ummai sun ji labarin kunyarku. Duniya ta cika da makokinku, don sojoji suna tuntuɓe da juna, dukkansu su ka fãɗi tare."13Wannan ita ce maganar da Yahweh ya faɗawa annabi Irmiya bayan Nebukadnezza sarkin Babila ya kawo wa Masar hari:14"Ka sanar a Masar, ka kuma yi shela a Migdol, da Memfis, da Tafanhes. Ku sami wurinku ku shirya kanku, don takobi zai haɗiye waɗanda ke kewaye da ku.'15Don me jarumawanki fuskarsu a sunkuye ƙasa? Ba za su tsaya ba, saboda Ni, Yahweh, na ture su ƙasa.16Ya ƙara yawan waɗanda su ka yi tuntuɓe. Kowanne soja ya fãɗi kusa da ɗan uwansa. Su na cewa, 'Ku tashi. Bari mu tafi gida. Bari mu koma wurin mutanenmu, zuwa ainahin ƙasarmu. Bari mu bar wannan takobin da ya ke doddoke mu ƙasa.'17Su ka yi shela a can, 'Fir'auna sarkin Masar mai kwakazo ne kawai, wanda ya bar zarafinsa ya sille.'18Na rantse da zatina inji Sarki, wanda sunansa shi ne Yahweh mai runduna - wani zai zo mai kama da Dutsen Tabor da Dutsen Karmel na bakin teku.19Ku kwaso wa kanku jakkuna don za ku tafi hijira, ku da ku ke zaune a Masar. Domin Memfis zata zama wofi, zata zama kango, ba kuma wanda zai zauna a can.20Masar kyakkyawar maraƙa ce, amma ƙwaro mai harbi na zuwa daga arewa. Yana zuwa.21Sojojin hayar da ke cikinta kamar bijimi mai ƙiba suke, amma su ma za su juya su gudu. Ba za su iya tsayuwa tare ba, don ranar masifarsu na zuwa gãba da su, lokacin horonsu ne.22Masar ta fito kamar maciji tana kuma rarrafawa, don maƙiyanta suna tattaki gãba da ita. Suna tunkararta kamar masu yankan katako da gatura.23Za su sassare dazuzzuka - wannan shi ne abin da Yahweh ya furta-duk da yake abin ya na da ban razana. Domin magabta za su zama da yawa sosai fiye da fara ba za su ƙidayu ba.24Za a kunyatar da Masar. Za a miƙa ta ga hannun mutane daga arewa."25Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya ce, "Duba, ina gab da in hori Amon na Tebes, da Fir'auna, da Masar da allolinta, da sarakunanta wato masu mulkinta, da masu dogara da su.26Zan miƙa su ga wanda ke neman rayukansu, da kuma hannun Nebukadnezza sarkin Babila da bayinsa. Daga nan bayan wannan za a sake zama a Masar kamar a kwanakinta na can baya - wannan furcin Yahweh ne27Amma kai, bawana Yakubu, kada ka ji tsoro. Kada ka razana, Isra'ila, don duba, Ina gab da in komo da ku daga manisanta wurare, zuriyarku kuma daga ƙasar bautarsu. Daga nan sai Yakubu ya dawo, ya sami salama, ya kuma sami tsaro, kuma ba sauran wanda zai razana shi.28Kai, bawana Yakubu, kada ka ji tsoro - wannan shi ne furcin Yahweh - don ina tare da kai, kuma zan halakar da dukkan al'ummai a inda na warwatsa ku. Amma ba zan hallaka ku dukka ba. Duk da haka zan hore ku da adalci hakika ba zan bar ku ba horo ba."
Wannan jumlar tana nuni da cewa wannan sakon an yi shi ne don al'ummar Masar.
Wannan jumlar tana nufin "kaifafa" mashin.
Kalmar "Ni" a nan tana nufin Yahweh. Yahweh yayi amfani da tambaya don gabatar da wahayin kuma ya jawo hankali ga abin da zai faɗa a gaba. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Duba abin da ke faruwa a nan" (Duba: rquestion)
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa babu wani, ko da mafi ƙarfi da sauri, da zai iya tserewa. Za a iya bayyana sifa na ɗan lokaci "mai saurin" a matsayin sifa. AT: "koda soja mafi saurin gudu ba zai iya tserewa ba"
Kogin Nilu yana ambaliyar bankunan sau ɗaya a shekara, yana rufe yankin da ke kewaye da ruwa. Yahweh yana kwatanta masarautar Masar da Nilu saboda mutanen Masar suna tsammanin sun isa su hallaka birane a duk ƙasashe.
Anan "Masar" tana wakiltar dukkan mutanen Masar. AT: "Masarawa suka tashi ... Masarawa suka ce ... Za mu yi"
Anan "dawakai" da "karusai" suna wakiltar sojojin da suke amfani da dawakai da karusai a yaƙi. Shugabannin Masar suna ba sojojinsu umarnin fara yaƙi. AT: "Ku tafi zuwa yaƙi, ku sojoji a kan dawakai. Ku yi yaƙi da ɓacin rai, ku sojoji a cikin karusai"
Kalmomin "lanƙwasa baka" na nufin a jan zaren baka da kibiya don harba kibiyar. AT: "gwani ne wajen harba kibiyoyi daga bakunan su" ko "gwanin kyau da kwari da baka"
Wannan yana maganar takobin Yahweh kamar yana cinye mutane yana shan jini. Duk waɗannan jimlolin suna faɗin abu iri ɗaya kuma an haɗa su don jaddada cewa za a sami halakar gaba ɗaya. AT: "Zan hallaka maƙiyina kwata-kwata. Zai zama kamar takobina ya cinye su kuma ya bugu da jininsa"
An yi maganar Yahweh don ɗaukar fansa ta hanyar sa Masarawa su yi rashin nasara a yaƙi da Babila kamar rundunar Masar za ta zama hadaya ga Yahweh. AT: "Gama Masarawa za su zama kamar hadaya"
Ana maganar mutanen Masar kamar su budurwa 'yar Masar. AT: "mutanen Misira"
Anan "ƙasa" ishara ce ga mutanen duniya kuma janar ce ga mutanen da suka san abin da ya faru da Masar. Duk mutanen duniya da suka ji kukan Masarawa ana magana da su kamar makokinsu sun cika duniya. AT: "Duk mutanen duniya suna jin kukanku"
Waɗannan sunayen garuruwan ne
Kalmar "takobi" a nan tana wakiltar sojoji masu ɗauke da makamai. Maganar abokan gaba da ke kashe mutane ana maganarsu kamar takubbansu suna cin mutane. AT: "makiyanku za su kashe mutane a kewayenku"
Wasu juya sun fassara wannan da "Me yasa Afis ya gudu? Me ya sa sa bijimin bai tsaya ba?" Afis wani allahn Bamasare ne wanda yake wakiltar sifar bijimi. Bijimi sau da yawa alama ce don ƙarfi. Abin da ya sa ke nan ULB da wasu juzu'in na Littafi Mai-Tsarki suka fassara wannan a matsayin "ƙarfaffa" ko "ƙarfafan mutane," wanda ke nufin sojoji.
"Yahweh yana sa da yawa daga cikin sojojinku su yi tuntuɓe"
Anan "takobi" yana wakiltar sojojin abokan gaba waɗanda ke ɗauke da makamai. AT: "Mu gudu daga abokan gabanmu saboda suna kashe mu"
Wadannan kalmomin guda biyu suna cewa al'ummar Masar ba ta da wani muhimmanci. Jimlar "kawai hayaniya" kalma ce da ke nufin mutum ya ce zai yi wani abu amma bai aikata ba. AT: "Fir'auna yana alfahari da yawa amma ba zai iya yin abin da zai yi alfahari da shi ba"
Wannan yana nufin ƙasar Babila wacce za ta mamaye ƙasar Masar kamar yadda waɗannan tsaunuka biyu suke zuwa filayen da ke kewaye da su.
"Shirya zuwa gudun hijira"
Ana maganar al'ummar Masar, wacce ta kasance mai matukar karfi da ci gaba, ana magana da ita kamar wata kyakkyawar yarinya saniya. AT: "Masar kamar kyakkyawar karsana ce"
Marubucin ya kamanta sojoji da “ƙibaƙan bijimai” domin sojojin suna da kulawa ta ƙwarai da Masarawa kamar yadda manomi ke kula da sa kuma ya mai da shi kiba.
'Tattaunawa tare' ma'anar karin magana ne don a kasance da haɗin kai. Marubucin yana cewa sojoji ba zasu yi yaƙi a matsayin ƙungiya ɗaya ba amma zasu gudu suna tunanin ceton kansu kawai.
Wannan yana ci gaba da magana game da sojojin abokan gaba suna kai hari kan Masarawa kamar dai sojojin sojojin yankan itace ne suna sare itatuwa. AT: "Sojojin abokan gaba za su kashe Masarawa da yawa kamar masu saran itace" duk da cewa akwai itatuwa da yawa "
Anan "hannu" yana wakiltar ƙarfi ko iko. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ni, Yahweh, zan ba da izinin mutane daga arewa su ci Masarawa"
"Amon" shi ne sarkin gumakan Masar. "Tebes" ita ce babban birnin yankin arewacin Masar, kuma anan tana wakiltar mutanen Tebes. AT: "Amon, allahn Tebes" ko "Amon, allahn mutanen Tebes"
Anan "hannu" yana wakiltar ƙarfi ko iko. "Nebukadnezza ... bayinsa" sunaye musamman "waɗanda ke neman rayukansu." AT: "ma'ana, zan ba da izini ga Nebukadnezza, sarkin Babila da barorinsa don su ci Masarawa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sannan bayan wannan, mutane za su sake rayuwa a Masar"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya. Anan "Yakubu" da "Isra'ila" suna wakiltar mutanen Isra'ila. Yahweh yana jaddada cewa kada mutane su ji tsoro. AT: "mutanen Isra'ila, bayina, kada ku ji tsoro"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "tabbas zai hukunta ku"
1Wannan ita ce maganar Yahweh da ta zo ga annabi Irmiya game da Filistiyawa. Wannan maganar ta zo gare shi kafin Fir'auna ya kai wa Gaza hari.2Yahweh ya faɗi wannan: Duba, tunbatsar ruwa na tasowa daga arewa. Zai zama kamar ambaliyar koguna! Daga nan za su share ƙasar da duk abin da ke cikinta, da biranenta da mazaunanta! Saboda haka kowa zai yi kukan neman taimako, kuma dukkan mazaunan ƙasar za su yi makoki.3Da jin motsin sawayen ƙarfafan dawakansu 'kofatansu na ruri akan karusansu da kuma ƙarar gargarensu, ubanni ba za su taimaki 'ya'yansu ba saboda rashin ƙarfinsu.4Domin rana na zuwa da zata warwatsa dukkan Filistiyawa, ta datse daga Taya da kuma Sidom da kuma daga duk wanda ya tsira ya ke kuma so ya taimake su. Don Yahweh yana warwatsa Filistiyawa, waɗanda su ka ragu a tsibirin Kafto.5Saiƙo zai aukawa Gaza. Ashkelon kuma mutanen da aka bari a kwarurrukansu za a sa su su yi shiru. Makokinku zai kai wanne lokaci?6Kaito, takobin Yahweh! Har yaushe za ta kasance har sai kun yi shiru? Ku koma ga watsewarku! Ku dena ku yi shiru.7Ta yaya zai huta, sa'ad da Yahweh ya umarce shi. Sa'ad da ya umarta a kaiwa Ashkelon hari da kuma ƙasashen da ke gefen teku?"
Kalmomin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya. Ana maganar rundunar abokan gaba kamar ambaliyar ruwa. AT: "runduna a arewa za ta zo kamar ambaliyar ruwa. Za su yi ƙarfi kamar ambaliyar ruwa"
Wannan yana ci gaba da magana game da sojojin daga arewa a matsayin ambaliyar ruwa. AT: "kamar ambaliyar ruwa, sojojin daga arewa zasu lalata ƙasar"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma an haɗa su don ƙarfafa babbar kara da za su yi. AT: "a babbar amo na ƙafafun karusai"
Wannan yana magana ne game da rana kamar dai wani abu ne da yake tafiya yana isowa a wani wuri. AT: "Gama a wannan ranar, sojojin abokan gaba za su fatattaki Filistiyawa duka kuma za a datse su daga Taya"
Yahweh yayi amfani da wata tambaya don ya nanata cewa mutanen Ashkelon ba za su daina yin makoki ba. Yahweh yana magana da mutane kamar yana magana da mace ɗaya, wacce ke misalta garin da kanta. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Za ku yanke kanku har abada cikin baƙin ciki."
Filistiyawa suna magana da takobin Yahweh kamar dai mutum ne wanda zai ji su. AT: "Ya Yahweh, kai da ke riƙe da takobinka! Yaushe za ku daina buge mu da takobinku? Dakatar da takobinku ku mayar da shi cikin mayafinsa!"
Irmiya ya yi amfani da tambaya don ya ce takobi ba zai iya tsayawa ba tunda Yahweh ya ba ta umarnin ci gaba da kisan. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Ba zai iya tsayawa ba, gama Yahweh ne ya umarce shi. Ya umarce ... teku."
1Ga Mowab, Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi wannan, "Kaiton Nebo, domin an warwatsa ta. An cinye KIriyata an ƙasƙantar da ita. An ɓalle hasumiyarta an wulaƙanta ta.2Mowab ba ta da sauran wata daraja. Maƙiyansu a Heshbon sun shirya mata masifa. Sun ce Ku zo mu hallakar da ita a matsayinta na ƙasa. Mahaukatanta suma za su hallaka - takobi za ta bi bayanku.'3Ku saurara! Ƙarar kururuwa na tafe daga Horoniyam, inda akwai kango da kuma babbar hallakarwa.4An hallakar da Mowab. 'Ya'yanta sun yi kuka har aka ji su.5Sun je kan tsaunukan Luhit suna kuka, Domin akan hanya zuwa Horoniyam, an ji ƙara mai ban razana saboda hallakarwa.6Tsere! Ku ceci rayukanku ku zama kamar dajin yunifa a jeji.7Domin saboda dogararku ga ayyukanku da dukiyarku, kuma za a kame ku. Daga nan sai Kemosh ya tafi zaman bauta, tare da firistocinsa da shugabanninsa.8Domin mai hallakarwa zai zo kowanne birni; ba birnin da zai tsira. Don haka kwari zai lalace, filin ƙasa kuma za a ɓaɓɓata shi, Kamar yadda Yahweh ya faɗa.9Ku bada fukafukai ga Mowab, don tilas ne ta tashi ta gudu. Biranenta za su zama ɓatattun ƙasashe, inda ba mai zama a cikinsu.10Dama duk wanda ke ragwanci cikin aikin Yahweh ya zama la'ananne! Dama duk wanda ya janye takobinsa daga zubar da jini ya zama la'annanne!11Mowab tana jin tana da tsaro tun tana matashiya. Ta zama kamar ruwan inabin da ba a taba canja masa gora ba. Ba ta taɓa zuwa bauta ba. Don haka yana jin komai dai - dai ne kamar dã; ɗanɗanonsa bai canza ba.12To duba, ranaku na zuwa - wannan shi ne abin da Yahweh ya furta - lokacin da zan aika masa da waɗanda za su juye shi su kuma juye dukkan tukwanensa su kuma farfasa butocinsa.13Daga nan sai Mowab su ji kunyar Kemosh kamar yadda ya faru ga gidan Isra'ila, yadda su ka ji kunyar Betel, abin dogararsu.14Yaya za ku ce 'Mu sojoji ne, jarumawan yaƙi'?15Za a washe Mowab za kuma a kai wa biranenta hari. Don kyawawan matasanta sun gangara mayanka. Wannan furcin sarki ne! Sunansa Yahweh mai runduna ne.16Masifar Mowab na gab da auko mata; bala'i ya kusa sauka da sauri.17Dukkan ku da ke kewaye da Mowab, ku yi kuka; da ku da kuka san ƙarfinta, ku yi sowar wannan, Kaiton, sanda mai ƙarfi, sandar daraja, an karye ta.'18Sauko daga wurinki mai daraja ki zauna a busasshiyar ƙasa, ke ɗiya mai zama a Dibon. Domin wanda zai hallaka Mowab yana kawo ma ki hari, wanda zai hallakar da madogaranki.19Ku tsaya akan hanya ku yi tsaro, ku mutanen da ke a Arowa. Ku yi tambaya ga wanda ya ga wanda ke gudu don ya tsira. ku ce Me ya faru?'20Mowab ta kunyata, don an warwatsa ta. Ku kaɗa kai ku yi makoki; Ku yi ihun neman taimako. Ku faɗawa mutanen yankin kogin Arnon cewa an hallakar da Mowab.21Yanzu horo ya sauko kan ƙasa mai duwatsu, ga Holon, da Jakza, da Mefat,22ga Dibon, ga Nebo, da Bet diblataim,23ga Kiriyataim, da Bet Gamul, da Bet Meyon,24ga Keriyot da Bozra, da kuma ga dukkan biranen da ke ƙasar Mowab - da manisanta, da biranen da ke nesa da kusa.25An kawar da ƙahon Mowab; an karya damtsenta - wannan furcin Yahweh ne.+26Ka sa ya bugu, don ya yi girman kai gãba da Yahweh. Bari Mowab ta yi birgima a kan hararwarta, ka sa ta zama abin ba a.27Domin ko Isra'ila bata zama abin dariya a gare ku ba? An same shi cikin ɓarayi, saboda haka ku ka kaɗa kanku gare shi ku ka yi kuma ta yin magana a kansa?28Ku yi watsi da birane ku tattaru a gefen gari, ku mazaunan Mowab. Ku zama kamar kurciyar da ke sheƙa a bakin rami a cikin duwatsu.29Mun ji labarin girman kan Mowab - da tayarwarta, da kumbura kanta, yadda ta ke ɗaukaka kanta da mugayen tunane tunanenta na zuciya.30Wannan furcin Yahweh ne - Ni da kaina na san maganganunsa na banza, waɗanda ba komai ba ne, kamar ayyukansa.31Don haka zan kawo makoki ga Mowab, zan kuma tada muryar makoki ga dukkan Mowab zan yi makoki saboda mutanen Kir Hareset.32Zan yi kuka dominku fiye da yadda na yi don Yazer, da kuringar Sibmah! Rassanki sun zarce ƙetaren Tekun Gishiri sun kai har Yazer. masu hallakarwa sun kawo hari ga 'ya'yan itatuwan inabinki na damina.33Don an kawar da biki da farinciki daga 'ya'yan itace da kuma ƙasar Mowab. Na kawo ƙarshen ruwan inabi daga wurin matsawarsu. Ba zasu matse su da sowace - sowacen farinciki ba. Duk wani sowace - sowace ba zai zama sowace - sowacen murna ba.34Daga sowace - sowace a Heshbon tun daga can Eleyele, an jiwo ƙararsu a Yahaz, daga Zowar har zuwa Horoniyaim da Eglat Shelishiya, tun daga ma can rafuffukan Nimrim da suka bushe.35Don zan kawo ƙarshen kowa a Masar wanda ke miƙa hadayu a manyan wurare da ƙona turare ga allolinsa - wannan furcin Yahweh ne.36Don haka zuciyata tana makoki domin Mowab kamar sarewa. Zuciyata tana makoki kamar gungume saboda mutanen Kir Hereset. Dukiyar da suka ribato ta ƙare.37Don dukkan kawuna sun yi saiƙo an kuma aske duk wani gemu. Tsage - tsage yana a kowanne hannu, sun kuma yafa tufafin makoki a kwankwasonsu38A kwai makoki a ko'ina, a cikin dukkan gine-ginen Mowab da kuma Cibiyoyin kasuwancin Mowab. Don na hallakar da Mowab kamar tukwanen da ba wanda ke so - wannan furcin Yahweh ne.39Yadda aka farfasa su! Yadda su ka yi ruri cikin makokinsu! Mowab ta juya bayanta cikin kunya! Don haka Mowab zata zama abin ba a da firgita ga dukkan waɗanda suka kewaye shi."40Gama Yahweh ya faɗi wannan, "Duba, maƙiyi zai zo yana jewa kamar gaggafa, yana buɗe fuka-fukansa a kan Mowab.41An kame Keriyot da dukkan hasumiyoyinta an ƙwance su. Don a waccan ranar zukatan sojojin Mowab za su zama kamar na zukatan matan da ke naƙuda a lokacin haihuwa.42Don haka za a hallakar da Mowab ta zama ba sauran mutane, don ya mai da kansa ya zama babba gãba da yahweh.43Masifa da rami, da tarko suna zuwa kanku, ku mazauna Mowab - wannan furcin Yahweh ne.44Duk wanda ya gudu saboda firgita zai faɗa rami, kuma duk wanda ya fito daga rami tarko zai kama shi, don zan aukar masu da wannan a shekarar fushina na ramako a kansu - wannan furcin Yahweh ne.45Waɗanda su ka tsere za su tsaya a inuwar Heshbon ba tare da wani ƙarfi, ba don wuta za ta tashi daga Heshbon, da harshen wuta daga tsakiyar Sihon. Zata cinye goshin Mowab da tsakiyar kawunan mutane masu ɗaga kai.46Kaiton ki, Mowab! an hallakar da mutanen Kemosh, Don an kwashe 'ya'yanki maza a matsayin bayi, 'yan matanki kuma zuwa bauta.47Amma zan dawo da nasarar Mowab a kwanaki masu zuwa - wannan furcin Yahweh ne." Hukuncin Mowab ya ƙare a nan.
Anan "an wulakanta Kiriathaim" yana wakiltar mutanen da ake wulakantawa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Abokan gaba sun kwace garin Kiriayatim kuma sun wulakanta mutanen da ke zaune a wurin"
"Mutane sun daina girmama Mowab" ko "Mutane sun daina yabon Mowab"
"Mahaukatanta" ga wani gari a cikin Mowab. AT: "Makiyansu zasu lalata garin Mahaukatanta"
Wadannan kalmomin guda biyu suna nufin abu daya ne. Tare suna jaddada cikakkiyar hallaka.
Cikakken sunan "halakarwa" ana iya bayyana shi a matsayin "halakakke." AT: "saboda garinsu ya lalace"
Kalmar "ku" tana nufin mutanen Mowab.
Ana kwatanta mutanen da ke gudu daga garuruwansu zuwa cikin hamada da daji ko shrub da ke tsirowa a cikin hamada. AT: "ku zama kamar itacen shukane wanda ya tsiro a jeji"
Ana iya bayyana kalmar 'amana' ta ƙuruciya azaman aiki. AT: "saboda kun dogara"
Anan "kwari" da "fili" suna wakiltar biranen da mutanen da ke waɗannan wuraren sauran. AT: "Don haka sojojin abokan gaba za su lalata duk abin da ke cikin kwari da a filayen"
Ana magana da taimaka wa mutane kamar za su sanya fikafikan mutane don su tashi sama. AT: "Taimakawa mutanen Mowab su tsere kamar kuna ba su fukafukai don su tashi"
Anan Yahweh yayi magana akan Mowab kamar mutum. A nan yana wakiltar mutanen Mowab. Duk aukuwar "shi" da "nasa" ana iya bayyana su a matsayin "su," "nasu," ko "su." AT: "Ko da tun daga zamaninsu na farko, mutanen Mowab sun sami kwanciyar hankali ... Su ne ... giyarsu ... Ba su taɓa tafiya ba ... sun ɗanɗana ... dandano"
Don giya ya ɗanɗana mai kyau, dole ne a bar shi ba da daɗewa ba kuma ba a zuba shi daga wata tukunyar zuwa wancan ba. Yahweh ya kwatanta mutanen Mowab, waɗanda suke da wadata domin babu wanda ya taɓa cinye su kuma ya kama su a matsayin ganima, ga ruwan inabin da ba shi da damuwa kuma yana da ɗanɗano mai kyau.
"Ku saurara da kyau saboda akwai lokaci"
Ga Yahweh yana magana da sojojin Mowab. Yahweh yayi amfani da tambaya don tsawata wa sojoji. AT: "Ba za ku sake cewa ba, "Muna sojoji ne, mayaƙan mayaƙa masu ƙarfi.""
An yi magana mafi kyawu daga mutanen Mowabawa da suka tafi yaƙi ana kashe su kamar dabbobi ne da aka kai wurin yanka. AT: "za a yanka samarinsu masu kyau duka" ko "sojojin abokan gaba za su kashe mafi kyawun mazajen Mowabawa"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa halakar Mowab za ta faru ba da daɗewa ba. AT: "Makiyan Mowab za su hallaka ta ba da daɗewa ba"
Ana maganar mutanen Dibon kamar 'yar Dibon ce. AT: "ku mutanen da ke zaune a Dibon"
"sojojin abokan gaba waɗanda za su hallaka Mowab"
Waɗannan su ne biranen Mowab.
Duk wadannan maganganun guda daya suke nufi. Anan "ƙaho" da "hannu" suna wakiltar ƙarfi. Samun waɗannan ɓarna ko ɓata yana nufin rasa ikon mutum. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mowab ya zama mai rauni; mutane ba su da ikon yin yaƙi kuma"
Anan ana magana akan mutanen da suke fuskantar horon Yahweh kamar suna shan giya ne, suna yin wauta don mutane suyi musu dariya. AT: "Zan sa ku zama kamar mashayi"
Yahweh ya ci gaba da magana game da mutanen Mowab kamar su mashayi. AT: "Yanzu mutanen Mowab za su zama kamar mutumin da yake birgima a cikin amai ... abin ba'a
Yahweh yayi amfani da tambaya don tunatar da mutanen Mowab yadda suka yi da mutanen Isra’ila. AT: "Kun kasance kuna yi wa Isra'ilawa dariya da dariya."
Anan Yahweh yayi amfani da tambaya don tsawata wa mutanen Mowab saboda yadda suka kunyata da Isra'ilawa duk da cewa basu yi wani laifi ba. AT: "Duk da cewa su ba barayi bane, amma har yanzu kun girgiza kan ku ... game dashi."
Anan "bakin rami" karin magana ne wanda ke nufin ƙofar kogo. AT: "ƙofar kogo" ko "buɗewa a cikin kankara"
Duk waɗannan kalmomin suna da ma'anoni iri ɗaya. Ana amfani dasu tare don jaddada girman girman mutanen Mowab.
Duk wadannan maganganun guda daya suke nufi. AT: "Zan yi kuka mai ƙarfi saboda mutanen Mowab"
Wannan sunan tsohon babban birin Mowab.
Ana iya bayyana sunayen suna "bikin" da "murna" azaman kalmomin aiki. Ana iya bayyana jumlar "an ɗauke su" ta hanyar aiki. AT: "Mutanen Mowabawa ba za su ƙara yin murna da farin ciki ba saboda bishiyoyin 'ya'yansu"
"Na dakatar da ruwan inabi daga matsewar ruwan inabi" ko "Na hana mutane yin giya"
Waɗannan su ne sunayen sauran biranen Mowab.
Anan “zuciya” tana wakiltar mutum duka. Ana kwatanta kukan mutum na baƙin ciki da kiɗan baƙin ciki da ake kunnawa a sarewa a wurin jana'iza. AT: "Ina kuka da bakin ciki saboda Mowab. Kukana na kama da waƙar baƙin ciki da mutum ke bugawa a sarewa a wurin jana'iza"
Waɗannan su ne abubuwan da Mowabawa suka yi lokacin da suke makoki ko baƙin ciki.
Kalmar "I" tana nufin Yahweh
Anan Mowab yana wakiltar mutane. Juya baya alama ce ta jin kunya. AT: "Mutanen Mowab sun juya baya don kunya" ko "Mutanen Mowab suna jin kunya kuma ba za su nuna fuskokinsu ba"
Waɗannan jumlolin suna kwatanta yadda dakaru masu ƙarfi za su sauko kan Mowab su ci ta da yaƙi kamar yadda gaggafa take saukowa don kame abin da ta kama.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Abokan gaba sun kwace Keriyot kuma sun kwace mafaka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Don haka abokan gaba za su hallaka mutanen Mowab"
Wannan yana nufin mutanen da suka sami damar guduwa yayin halakar Mowab.
Waɗannan kalmomin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna jaddada cewa halakar Mowab za ta fara kuma yaɗu daga Heshbon, inda sarki Sihon ya taɓa zama. AT: saboda gobara za ta ƙone a Heshbon, wanda shine garin da Sarki Sihon ya rayu tun da daɗewa
Anan "goshin" da "saman kawunan" suna wakiltar mutanen Mowab baki ɗaya. AT: "Zai ƙone duka mutanen Mowab da suka yi alfahari sosai"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sojojin makiya sun hallaka mutanen da ke bauta wa Kemosh"
1Ga abin da Yahweh ya ce, game da mutanen Ammon, Isra'ila ba ta da 'ya'ya ne? Babu wanda zai gãji wani abu a Isra'ila? Me ya sa Molek ya ke zaune a Gad, mutanen sa kuma su na zaune a cikin biranen sa?2To duba, kwanaki su na zuwa - wannan furcin Yahweh ne - sa'ad da zan ba da alamar yaƙi gãba da Rabbah a cikin mutanen Ammon, za ta zama yasasshen tsibi kuma a ƙone ƙauyukanta da wuta. Gama Isra'ila zai mallaki waɗanda su ka mallake shi." cewar Yahweh.3Yi ruri cikin makoki, da Heshbon, gama za a ragargaza Ai! Ɗiyar Rabba, ki yi kururuwa! Sa kayan makoki. Yi makoki da kai da kawowa a wofi, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da shuganninsa.4Me ya sa ki ke fahariya da kwarurrukanki, kwarurrukan masu ba da 'ya'ya sosai, ke kangararriyar ɗiya? Ke da ki ke dogara da dukiyarki kuma kin ce, "wane ne za ya iya zuwa ya yi gãba da ni?'5Duba, na kusa kawo maki tsoro, wannan shi ne furcin Ubangiji Yahweh Mai Runduna - wannan abin tsoro zai zo daga dukkan waɗanda su ke maƙwabtanki. Zai watsar da kowanne ɗayan ku. Ba wanda zai tattaro waɗanda suka gudu.6Amma bayan haka zan dawo da kaddarorin mutanen Ammon - wannan shi ne furcin Yahweh."7A kan Idom, Yahweh mai runduna ya ce haka, "Ba sauran hikimar da za a samu a Teman? Shawara mai amfani ta ƙare daga masu fahimta? Hikimar su ta lalace?8Ku gudu! Ku koma baya! Ku jira cikin ramummuka cikin ƙasa, mazauna Dedan. Gama zan kawo hallaka ga Isuwa, a kan shi lokacin da zan hore shi.9Idan masu girbin inabi su ka zo wurin ku, ba za su rage kaɗan ba? Idan ɓarayi ne da daddare, ba za su saci abin da su ke so ba?10Amma na tuɓe Isuwa ya zama huntu, na tono wuraren ɓoyon sa domin kada ya ƙara ɓoye wa. 'ya'yansa da 'yan uwansa da maƙwabtansa an hallakar da su, shi kuma ya tafi.11Ku bar marayunku, zan lura da su rayukansu, gwaurayenku su dogara gare ni."12Gama Yahweh ya faɗi haka, "Duba waɗanda ba su cancanta ba tabbas za su sha daga cikin ƙoƙon. Kai da kanka, ka na tsammani za ka tafi ba tare da horo ba? Ba zai yi wu ba, domin tabbas zaka sha.13Gama na rantse da kaina, wannan furcin Yahweh ne - Bozra za ta zama abin tsoro, abin reni, lalatatta, da abin la'antarwa. Dukkan biranenta za su lalace har abada.14Na ji magana daga wurin Yahweh, an aika da manzo zuwa ga al'ummai, 'ku taru ku kai mata hari, ku yi shiri domin yaƙi.'15Duba, idan an gwada da sauran al'ummai na mai da ke 'yar ƙarama, abin reni ga mutane.16Saboda tsoron ka, girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, mazauna can ƙoli, ku da ku ke a can bisa tsaunuka masu tsawo domin ka sa sheƙar ka can sama kamar gaggafa. Zan dawo da kai ƙasa daga can - wannan ne furcin Yahweh.17Idom za ta zama abin tsoro ga dukan mai wuce ta. Kowanne mutum zai yi rawar jiki da tsaki saboda dukkan masifunta.18Kamar yadda aka kaɓantar da Sodom da Gomora da maƙwabtansu," Yahweh ya faɗi, "ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai tsaya a can.19Duba, zai tashi kamar zaki daga jejin Yodan zuwa wuraren kiwo masu kyau. Domin nan da nan zan sa Idom ta gudu daga wurin ta, zan sa wani zaɓaɓɓe ya lura da ita. Gama wanene kama da ni, wane ne kuma zai yi mani sammaci? Akwai makiyayin da zai iya yin tsayayya da ni?"20Ji shirye-shiryen da Yahweh ya yi gãba da Idom, shirye-shiryen da ya yi gãba da mazaunan Teman. Ba shakka za a janye su har ɗan ƙaramin garken dabbobi. Wuraren kiwon su za su zama rusasssun wurare.21Duniya za ta girgiza da ƙarar faɗuwar su. An ji sowace - sowacen ƙunci daga Tekun Iwa.22Duba, wani zai kawo hari kamar gaggafa, ya kawo su-ra ya buɗe fuka-fukansa a kan Bozra. Daga nan a wannan rana zuciyar sojojin Idom za ta zama kamar zuciyar macen da ke cikin naƙuda."23Game da Damaskus: "Hamat da Arfad za su ji kunya, saboda sun ji labarin hallaka. Sun narke! hankalin su ya ta shi kamar tekun da ya kasa kwantawa.24Damaskus ta raunana ƙwarai, ta juya ta gudu; tsoro ya kama ta. Ƙunci da ciwo ya kama ta kamar mace mai hafuwa.25Yaya birnin yabo ba a yashe shi ba, garin farincikina?26Saboda haka samarinta za su faɗi a wuraren cinikaiyarsu, jarumawanta za su hallaka a rannar- wannan shi ne furcin Yahweh mai runduna"27"Gama zan kunna wuta a kan ganuwar Damsakus, za ta cinye kagara mai ƙarfi ta Ben Hadad."28Game da Kedar da mulkokin Hazor, ga abin da Yahweh ya ce da Nebukadnezza, (gama Nebukadnezza sarkin Babila zai kai wa waɗannan wurare hari): "Tashi ka kai wa Kedar hari ka hallaka waɗannan mutanen na gabas.29Za a kwashe bukkokinsu da garkunansu, duk da labulen bukkokinsu da kayan aikinsu; za a kore raƙumansu daga wurinsu, mazaje za su yi masu ihu su ce, "Ga abin tsoro a kowanne gefe!"30Ku gudu! Ku yi ragaita can nesa! Ku tsaya a cikin ramuka a ƙasa ku mazauna Hazor - wannan furcin Yahweh ne. Gama Nebukadnezza sarkin Babila ya ƙulla shiri gãba da ku. Ku gudu! Ku koma baya!31Tashi ka kai wa al'ummar da ke zaune lafiya hari cikin sauƙi, "Yahweh ya ce" Ba su da ƙofofi ko makarai, mutanen hakanan suke zaune su kaɗai.32Gama raƙumansu za su zama ganima, kayansu masu yawa za su zama ganimar yaƙi. Sa'annan zan sa iska ta watsar da su, su waɗanda ke aske gefen gashinsu, zan kawo masu hallaka daga kowanne gefe - haka Yahweh ya furta.33Hazor za ta zama wurin kwanciyar diloli, ta lalace har abada. Ba wanda zai zauna a wurin, ba mutumin da zai tsaya a can.34Wannan ce maganar Yahweh da ta zo ta wurin Irmiya annabi game da Elam. Wannan ya faru a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda, ya ce,35"Yahweh Mai runduna ya faɗi wannan: Duba, na kusa karya 'yan baka na Elam, a karfinsu mafi yawa.36Gama zan kawo iskoki huɗu daga kusurwoyi huɗu na sammai, zan watsar da mutanen Elam ga dukkan waɗannan iskokin. Waɗanda su ka watse daga Elam babu al'ummar da za su je.37Zan ragargaza Elam a gaban abokan gãbar su da waɗanda ke neman ransu. Domin zan kawo masu hallaka da zafin fushina - haka Yahweh ya furta - Zan aika takobi a bayansu har sai na hallakar da su.38Sa'annan zan kafa kursiyina a Elam in hallakar da sarkinta da shugabanninta daga can - abin da Yahweh ya furta kenan -39Zai zama a cikin kwanaki masu zuwa zan dawo da martabar Elam - abin da Yahweh ya furta kenan."
Yahweh yayi amfani da tambaya don bayyana cewa ya kamata Isra'ilawa su zauna a Gad maimakon waɗanda ke bauta wa Molek. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Akwai Isra'ilawa da yawa da zasu gaji ƙasar Isra'ila. Mutanen da suke bautar gunkin ƙarya, Molek, bai kamata su zauna a Gad ba."
Ana maganar lokaci na gaba kamar "ranaku suna zuwa." Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Irmiya 7:32. AT: "nan gaba ... zan yi" ko "za a sami lokacin ... lokacin da zan yi"
Mai yiwuwa ma'anoni 1) "'ya'ya mata" suna wakiltar matan da ke zaune a Rabbah. AT: "matan Rabba" ko 2) ana magana da mutane gabaɗaya kamar 'ya'yan Rabba ne. AT: "mutanen Rabba"
Yahweh yayi amfani da tambaya don tsawata wa mutane don yin alfahari game da ɗiyan itacen da yake girma a kwarinsu. Ana iya fassara wannan tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Kada ku yi alfahari da kwarinku ... diya."
Ana iya bayyana kalmar ta '' ta'addanci '' azaman kalmar 'tsoratarwa'. Ana iya bayyana kalmar "za a warwatse" a cikin tsari mai aiki. AT: "Zan sa duk waɗanda ke kusa da ku su firgita ku. Kowannen ku ya gudu zuwa hanyoyi daban-daban"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don tsawata wa mutane. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Da alama babu sauran masu hikima a cikin gundumar Teman a Idom!"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don tsawata wa mutane. Ana iya fassara wannan tambaya azaman bayani. AT: "Shawararsu ba ta da hikima."
Yahweh yana amfani da tambaya don sa mutane suyi tunani game da yadda masu girbin inabi suka bar waɗansu 'ya'yan inabi a baya. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Idan masu girbin inabi ... tabbas za su bar wasu inabi a baya."
Yahweh yana amfani da tambaya don sa mutane suyi tunanin yadda ɓarawo suke ɗaukar abin da suke so kawai. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Idan ɓarayi ... za su ɗauki abin da suke so kawai."
Anan "ƙoƙon" wani yanki ne mai wakiltar abin da ke cikin ƙoƙon da mutane za su sha. Mutanen da ke fuskantar azabar Ubangiji ana magana ne kamar azabar Yahweh ruwa ce a cikin ƙoƙo kuma mutane dole ne su sha shi. AT: "lallai ne ku dandana azaba ta ... domin lallai kun ga azaba ta" ko "Lallai zan ci gaba da azabtarwa ... don kuwa lalle zan hukunta ku" (Duba:
Yahweh yayi amfani da tambaya don jaddada mutanen Edom sun yi zunubi kuma tabbas za a hukunta shi. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Tabbas, dole ne ku sani cewa ku da kanku za ku ga hukunci na saboda zunubanku."
Kalmar "I" tana nufin Irmiya.
Yahweh ya ci gaba da magana game da abin da zai faru da Idom.
An nuna cewa mutane sun yi gidaje a cikin manyan wurare don su tsira daga makiya. AT: "ku zauna cikin aminci kamar gaggafa a tsaunukan tsaunuka"
Kalmar "tsaki" tana nufin sautin da ke nuna ban tsoro. AT: "girgiza daga tsoro da kuzari"
Yahweh ya faɗi abu ɗaya sau biyu don ya nanata cewa Idom ba za ta dawwama ba.
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa babu wanda yake kama da shi. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Don babu wanda ya yi kama da ni, babu wanda zai iya tara ni."
Yahweh yayi amfani da tambayar don nuna babu wanda zai kayar da shi. A nan "makiyayi" kwatanci ne na "sarki" ko "mai mulki." Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Babu wani sarki da zai iya tsayayya da ni!"
"mutanen da ke zaune a Teman"
Wannan yana ci gaba da magana akan hukuncin Ubangiji a kan mutanen Idom kamar dai zai zo kamar zaki ya fāɗa wa tumakin. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zai ja su, har da ƙaramar garken"
Anan ana maganar ƙasar Idom kamar makiyaya don garken tumaki. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zai mayar da wuraren kiwo nasu zuwa wuraren da suka lalace" ko "Zai kawar da mutanen da ke zaune a wurin gaba ɗaya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutanen da ke Tekun Iwa za su ji mutanen Idom suna kuka"
Wannan misalin yana nufin cewa lokacin da sojojin abokan gaba suka kawo hari zai kasance na mugu da ba zata.
Anan "zukata" suna wakiltar motsin zuciyar mutum. Duba yadda kuka fassara makamancin magana a cikin Irmiya 48:41. AT: "Sojojin Idom za su firgita kamar matar da za ta haihu"
Yahweh ya faɗi abin da zai faru da mutanen Damaskus.
Ruwan teku yana motsawa koyaushe kuma baya tsayawa. An kwatanta wannan da mutanen da ba za su iya hutawa ba saboda suna cikin damuwa game da mummunan labarin da suka ji.
Wasu fassarori suna fassara wannan tare da mutanen Damaskus suna magana. AT: "Mutanen Damaskus suna cewa, 'Mashahurin birni, wanda ya taɓa faranta mana rai, yanzu ya zama fanko.'"
Yahweh ya faɗi abin da zai faru da mutanen Damaskus.
Wannan suna ko lakabin sarkin Damaskus.
Irmiya yayi magana game da abin da zai faru da Kedar.
Wannan sunan ƙungiyar mutanen mai nesa a gabashin Isra'ila.
Wannan shi ne sunan masarauta ko yanki mai nesa gabas da Isra'ila.
Yahweh yana ci gaba da magana game da abin da zai faru da Kedar da mulkokin Hazor.
Anan "al'umma" tana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin. AT: "Kai wa wannan al'umma hari, wanda jama'arta ke jin amintuwa da kwanciyar hankali"
Anan "kowane iska" yana wakiltar al'ummomi. AT: "Bayan haka zan aika zuwa ga al'ummomi ta kowane bangare"
Wadannan layin guda biyu ma'anarsu abu daya kuma suna nanata cewa Hazor zata zama ba kowa a ciki.
Yahweh yana magana akan abin da zai faru da Elam.
Anan "iskoki hudu daga kusurwa huɗu" wani karin magana ne wanda yake wakiltar iska mai hurawa daga kowane bangare. AT: "Zan sa iskoki su hura daga kowane bangare"
Ana iya bayyana wannan a cikin tsari mai kyau. AT: "Zan watsa mutanen Elam ga kowace al'umma a duniya"
Yahweh ya ci gaba da magana game da abin da zai faru da Elam.
Anan “kursiyi” yana wakiltar ikon Yahweh na yin sarauta da yin hukunci a matsayin sarki. AT: "Zan hukunta mutanen Elam"
1Ga abin da Yahweh ya furta game da Babila, ƙasar Kaldiyawa, ta hannun Irmiya annabi,2"Faɗawa al'ummai kuma ka sa su, su saurara. Ka sa alama kuma ka sa su saurara. kada ka rufe ta. Ka ce, 'An ɗauke Babila, an kuyatar da Bel. Marduk ta razana, an sa gumakanta cikin kunya; siffofinta sun razana.3Wata al'umma daga arewa zata taso mata, domin ta mayar da ƙasarta kango. Ba wanda zai zauna cikinta ko mutum ko dabba, duk za su gudu.4Ga abin da Yahweh ya furta a cikin waɗannan kwanaki da wannan lokaci, mutanen Isra'ila da na Yahuda - zasu taru su je suna neman Yahweh Allahnsu da kuka.5Za su tambayi hanyar zuwa Sihiyona su nufi wurin ta suna cewa, za mu je mu haɗa kanmu da Yahweh da dauwamamman alƙawarin da ba za a manta ba."6Mutane na sun zama garken da ya ɓace, makiyayansu sun bauɗar da su cikin duwatsu; suna juya su daga wannan tudu zuwa wancan. Sun tafi sun mance wurin da suka fito.7Kowa ya je wurin su yana cinye su. Abokan gãbar suna cewa, 'Ba mu yi zunubi ba gama sun yi zunubi ga Yahweh, gidansu na gaskiya -Yahweh begen kakanninsu.8Ku fita daga tsakiyar Babila; ku fice daga ƙasar Kaldiyawa; ku zama kamar dan akuyan da ya tafi kafin sauran garke.9Duba, na kusa ta da ruɗami, in tada wata ƙungiya ta manyan al'ummai daga arewa su yi gãba da Babila. za su haɗa kan su gãba da ita. Za a ci Babila da yaƙi daga can. Kibiyoyinsu kamar na babban maharbin da ba ya dawowa hakanan.10Kaldiya za ta zama ganima. Dukkan waɗanda suka washe ta za su gamsu - haka Yahweh ya furta.11Kun yi farinciki, kun yi shagali sa'ad da aka washe abin gãdona, kun yi tsalle kamar ɗan maraki a wurin kiwonsa, kun yi haniniya kamar ƙaƙƙarfan doki.12Saboda haka mahaifiyarku zata ji kunya ƙwarai; za a ƙasƙantar da wadda ta haife ku. Zata zama mafi ƙanƙanta cikin al'ummomi, ta zama jeji ta zama busasshiyar ƙasa ta zama hamada.13Saboda Yahweh ya yi fushi, Babila za ta zama kufai mai zama a cikinta, za ta lalace sarai. Dukkan wanda ya wuce zai yi mamakin lalacewar Babila, ya yi tsaki saboda dukkan raunukanta.14Ku da ke kewaye da ita, ku shirya ku kai wa Babila hari. Dukkan wanda ya ɗana baka dole ya harbe ta, kada ku mayar da kibiyoyinku, gama ta yi wa Yahweh zunubi.15Ku yi mata ihu a ko'ina! Ta ba da kai, hasumiyoyinta sun faɗi; an rushe ganuwoyinta, wannan fansa ce da Yahweh ya ɗauka. Ku ɗauki fansa a kanta! Ku yi mata kamar yadda ta yi.16Ku hallaka manoma, da wanda ya shuka iri da wanda ya yi amfani da lauje a lokacin girbi cikin Babila. Bari kowanne mutum ya koma wurin mutanensa ya gudu daga takobin mai azabtarwa; bari su gudu su koma ƙasarsu.17Isra'ila tumaki ne da suka watse zakuna suka kore su. Da farko sarkin Asiriya ya cinye shi; sa'annan Nebukadnezza sarkin Babila ya karya ƙasusuwansa.18Saboda haka Yahweh Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka: Duba, na kusa in hori sarkin Babila da ƙasarsa, kamar yadda na hori sarkin Asiriya.19Zan dawo da Isra'ila ƙasarsa; zai yi kiwo a Karmel da Bashan. Sa'annan za ya ƙoshi a ƙasar kan tudu ta Ifraim da Giliyad.20Yahweh ya ce, a cikin waɗanan kwanaki da wannan lokaci, za a nemi laifi a Isra'ila, amma ba za a samu ba. Zan biɗi zunubi game da Yahuda, amma ba zan samu ba, gama zan gafartawa waɗanda na keɓe."21"A tasar wa ƙasar Meratayim, gãba da ita da mazaunan Fekod. Sa masu takobi, kuma a keɓe su domin hallakarwa - abin da Yahweh ya furta kenan-- ku yi dukkan abin da nake umurtarku.22Zizar yaƙi da mummunar hallakarwa suna cikin ƙasar.23Yadda aka datse gudumar dukkan ƙasashe kuma aka hallakar. Yadda Babila ta zama rusasshen wuri cikin al'ummai.24Na ɗana maki tarko kuma kin kamu, ke Babila, kuma baki sani ba! An same ki kuma an kama ki, domin kin yi tsayayya da Yahweh.25Yahweh ya buɗe wurin ajiyar kayan yaƙinsa kuma yana fito da kayan yaƙin domin aiwatar da fushinsa. Akwai aiki domin Ubangiji Yahweh mai runduna a ƙasar Kaldiyawa.26Ku kai ma ta hari daga nesa. Ku buɗe rumbunanta ku tara ta kamar tsibin hatsi. Ku keɓe ta domin hallakarwa. kada ku rage ma ta komi.27Ku kashe dukkan bijimanta, ku kai su wurin yankawa. Kaiton su, ranarsu ta zo - lokacin horonsu.28Akwai motsin waɗanda suke gujewa, waɗanda suka rage, daga ƙasar Babila. Waɗannan za su ba da labarin ɗaukar fansa da Yahweh Allahnmu ya yi domin Sihiyona, da ɗaukar fansa domin haikalinsa."29A kira maharba gãba da Babila - dukkan waɗanda su ka ɗana bakkunansu. Ku yi zango gãba da ita, kuma kada kowa ya tsira. Ku sãka mata kamar yadda ta yi. ku yi mata bisa ga ma'aunin da ta yi amfani da shi. Gama ta rena Yahweh, Mai Tsarki na Isra'ila.30Haka samarinta za su faɗi a cikin dandalin birni, kuma dukkan mayaƙanta zasu hallaka a wannan rana - Wannan shi ne furcin Yahweh."31Duba, Ina gãba da ke, ke mai takama - wannan shi ne furcin Ubangiji Yahweh mai runduna - gama ranarki ta zo, ke mai taƙama, lokacin da zan hore ki.32Domin masu taƙama su yi tuntuɓe su faɗi. Ba wanda zai tashe su. Zan kunna wuta a cikin biranensu; za ta cinye komi da komi da ke kewaye da shi.33Yahweh mai runduna ya ce wannan: An tsanantawa mutanen Isra'ila, tare da mutanen Yahuda. Dukkan waɗanda suka kamasu su na riƙe da su; sun hana su su tafi.34Mai kuɓutar da su mai ƙarfi ne. Yahweh mai runduna ne sunansa. Lallai zai duba matsalar su da gaskiya, domin ya kawo hutu a ƙasar, ya kuma kawo husuma ga mazaunan Babila.35Takobi na gãba da Kaldiyawa, haka Yahweh ya furta, da kuma Babila da mazaunanta da shuganninta da masu hikimarta.36Takobi na gãba da masu faɗar maganganun banza! Za su zama wawaye! Takobi na gãba da sojojinta! za su cika da tsoro.37Takobi yana zuwa gãba da dawakansu, da karusansu da dukkan mutane mazauna cikin tsaƙiyar Babila, domin su zama kamar mataye. Takobi ya na zuwa gãba da ɗakunan ajiyarta, kuma za a washe su.38Fari ya na zuwa kan ruwayenta domin su bushe. Domin ta zama ƙasar gumaka lalatattu, sun yi kamar mutane marasa hankali ta wurin gumakansu.39Ta zama hamada inda namun daji za su zauna da diloli da 'ya'yan jimina su zauna a cikinta. Ba lokacin da za a ƙara zama a cikinta. Ba za a ƙara zama cikinta ba daga tsara zuwa tsara.40Kamar yadda Yahweh ya kaɓantar da Sodom da Gomora da maƙwabtansu - abin da Yahweh ya furta ke nan - ba wanda zai zauna a can; ba mutumin da zai tsaya cikinta."41Duba, wasu mutane suna zuwa daga arewa; babbar al'umma da sarakuna masu yawa an izo su daga manisantan wuraren duniya.42Zasu ɗauko bakkuna da mãsu. Su masu masifa ne ba su da tausayi. Tafiyar su tana kama da rurin teku, sun haye bisa dawakai, a jere bisa layi kamar mutane domin yaƙi, gaba da ke, ɗiyar Babila.43Sarkin Babila ya ji rahoto game da su, sai hannayensa suka yi sanyi cikin ƙunci. Azaba ta kama shi kamar mace mai haihuwa.44Duba! Ya fito kamar zaki daga tuddan Yodan zuwa wuraren kiwo. Gama nan da nan zan sa su gudu daga wurin, kuma zan sa wani zaɓaɓɓe ya lura da wurin. Gama wane ne kama da ni, kuma wa za ya ba ni sammaci? Wanne makiyayi ne zai iya tsayayya da ni?45To saurari shirye-shiryen da Yahweh ya yi gãba da Babila, shirye-shiryensa da ya shirya gãba da ƙasar Kaldiyawa. Lallai za a janye su, har ma da ɗan karamin garke. Wuraren kiwon su za su zama kango.46Duniya za ta girgiza da rurin yaƙin yin nasara da Babila, al'ummai za su ji kukansa na ƙunci."
Hannun magani ne na mutum. AT: "ta wurin Irmiya, wanda annabi ne"
Waɗannan layin suna da ma'ana ɗaya kuma suna jaddada cewa Yahweh ya kunyata gumakan Babila.
Cikakken sunan "lalacewa" ana iya fassara shi azaman aiki. AT: "lalata ƙasarta"
Waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya kuma suna jaddada mahimmancin wancan lokacin na gaba. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Irmiya 33:15.
Wannan yana nuna cewa za'a kiyaye alkawarin har abada. Ana iya bayyana shi cikin tsari mai aiki. AT: "cewa babu wanda zai manta da shi"
Ana magana da kai wa Isra'ilawa hari kamar dabba ta ci su. Ana iya bayyana wannan azaman misali. AT: "ya cinye su kamar dabbar daji za ta cinye abincinta"
Awaki maza suna da 'yanci fiye da sauran garken. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) ya kamata su kasance farkon waɗanda za su bar Babila ko 2) su jagoranci sauran Isra'ilawa daga Babila.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Waɗannan ƙasashe za su kama Babila"
An kwatanta mutanen Babila da karusai masu yin kuwwa saboda murna.
Wadannan jimlolin guda biyu ma'anarsu abu daya kuma suna jaddada tsananin kunyar ta. Kalmomin "uwa" da "wacce ta haife ku" suna nufin Babila ne ko kuma birnin Babila.
Waɗannan kalmomin suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna jaddada cikakken ƙarancin ƙasar. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) wannan kwatanci ne ga wurin da ba kowa ko kuma 2) wannan yana nufin Babila a zahiri ta zama jeji marar amfani.
Wannan yana nufin sojojin da suke amfani da baka da kibiya don yaƙi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "al'ummai sun ruguza ganuwarta"
"Siikila kayan aikin gona ne da mutane ke amfani da shi don girbin hatsi. Tare da kalmar da ta gabata, Yahweh yana cewa duk shuki da girbi za su daina a Babila.
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Tare suna ƙarfafa umarnin ga baƙi su gudu daga Babila su koma ƙasashensu.
Yahweh yayi magana game da Isra'ila kamar tumaki waɗanda suke ƙoƙarin tserewa daga zakoki masu jin yunwa. Ana iya bayyana wannan kwatancen azaman kamanceceniya da cikin sigar aiki. AT: "Isra'ila tana kama da tumakin da zakuna suka watse suka kora"
Ana maganar halakar Isra’ilawa da Asiriya kamar Isra’ilawa tumaki ne da Asiriya ta ci.
Ana maganar halakar Isra’ila ta hannun Nebukadnezzar idan tunkiya ce da zaki ya murƙushe ƙasusuwanta. AT: "an hallakar da Isra'ila"
Ana magana da Isra'ila kamar tumaki masu cin ciyawa. AT: "za su ci abincin da ya tsiro a Karmel da Bashan"
Waɗannan layin biyu suna nufin abu ɗaya dai-dai. Tare suna jaddada cewa Yahweh zai gafarta zunuban Isra'ila gaba ɗaya.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai nemi laifi a cikin Isra'ilawa, amma ba zai samu ba"
Wannan wani suna ne ga Babila. Wannan suna ne da ke nufin "tawaye biyu."
Wannan wani suna ne na Kaldiyawa. Wannan suna ne da ke nufin "ziyara."
Wannan yana nufin sa takobi ya sauko kan mutane ya kashe su. AT: "Ku kashe su"
Ana magana akan sojojin Babila kamar guduma. Ana maganar halakar wannan rundunar kamar ana yanke guduma ne a ruguje ta. Ana iya bayyana wannan azaman misali. AT: "Ƙwararrun sojojin Babila waɗanda suka ci dukan al'ummu kamar guduma ne waɗanda za a farfashe su su lalace"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Na kama ku ... Na same ku kuma na kama ku"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) rage birni zuwa tarkacen duwatsu waɗanda suke kama da tsattsarkar hatsi ko 2) tara ganimar garin kamar tarin hatsi.
Yahweh ya ci gaba da faɗar yadda za a halakar da mutanen Babila da Kaldiya.
Mai yiwuwa ma'anar "bijimai" shi ne 1) sojoji ko 2) samari masu ƙarfi. Ana maganar kashe su ana kai su wurin yanka.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan halakar da duk mayaƙanta"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya. Jumla ta biyu tana bayyana "ranar" da jimlar farko ta ambata. AT: "Ranar da zan hukunta ku ta zo"
Ana maganar wutar da ke cin biranen Babila kamar wutar dabba ce ta cinye su.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutanen Babila suna zaluntar mutanen Isra'ila da na Yahuda"
Kalmar "su" tana nuni ne ga mutanen Isra'ila da Yahuda waɗanda aka kama kuma aka kwashe su.
Anan “takobi” yana wakiltar yaƙi. AT: "Ba da daɗewa ba yaƙi zai faru da ... kuma zuwa"
"Ayyukan su wauta ne, kuma kowa zai ga cewa su wawaye ne"
"za su firgita"
Ana magana da rauni na sojojin Babila kamar suna mata. Ana iya bayyana wannan a sarari. AT: "dukkansu za su zama masu rauni kamar mata"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "dabbobin daji da kuraye" ko kuma 2) "aljanun daji da mugayen ruhohi."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba wanda zai rayu a cikin ta"
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna nanata cewa Babila ba za ta kasance da kowa ba. Ana iya haɗuwa da su. AT: "ba wanda zai sake rayuwa a wurin"
Wannan jumlar tana nufin lokacin da Midiya da Fasiya suka ci Babila a shekara ta 539 kafin haihuwar Yesu. Anan “al’umma” tana wakiltar sojojinsu. AT: "sojojin babbar al'umma da sarakuna da yawa"
Kalmomin "an tsara su dai-dai" yana nufin cewa sun tsara kansu kuma suna hawa cikin layi-layi. Kalmomin "a matsayinsu na mayaƙi" yana nuna cewa a shirye suke su yi yaƙi. AT: "suna kan dawakai a layin da aka sanya su, kuma a shirye suke don yaƙi"
Anan "su" suna nufin mutanen Babila; kalmar "shi" tana nufin mamayewa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda zan zaba"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya nuna babu wanda zai kayar da shi. A nan "makiyayi" kwatanci ne na "sarki" ko "mai mulki." AT: "Babu wani sarki da zai iya tsayayya da ni."
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma ana amfani dasu tare don girmamawa. AT: "tsare-tsaren da Yahweh ya yanke wa mutanen Babila da Kaldiya"
Wannan yana ci gaba da maganar Ubangiji yana azabtar da mutanen Babila kamar zai zo kamar zaki ya fāɗa wa tumakin. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zai ja su, har da ƙaramar garken"
Anan ana maganar ƙasar Babila kamar makiyaya don garken tumaki. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zai mayar da wuraren kiwo nasu zuwa wuraren da suka lalace" ko "Zai hallaka mutanen da ke zaune a wurin gaba ɗaya"
1Ga abin da Yahweh ya faɗi: Duba, na kusa tado da iskar mai hallakaswa a kan Babila da mazauna cikin Leb Kamai.2Zan aika da baƙi ga Babila, za su warwatsar da ita su lalata kasarta, gama za su auko mata ta kowanne gefe a ranar hallakarwa.3Kada ku bari maharba su ɗana bakkunansu; kada ku bari su sa kibiya. Kada ku ƙyale samarinta, ku keɓe dukkan sojojinta domin hallakarwa.4Gama mutanen da suka sami rauni za su faɗi a ƙasar Kaldiyawa; matattu za su faɗi a cikin titunanta.5Gama Isra'ila da Yahuda Allah bai yashe su ba, Yahweh mai runduna, ko da yake ƙasar ta na cike da laifofin da a ka yi wa Mai Tsarki na Isra'ila.6Ku gudu daga cikin Babila, kowa ya tsira da kansa. Kada ku hallaka cikin muguntarta. Gama lokacin ɗaukar fansar Yahweh ne. Zai rama komai a kanta.7Dã Babila ƙoƙon zinari ce a hannun Yahweh wadda ta sa dukkan duniya suka bugu; dukkan al'ummai suka sha ruwan inabinta suka sami taɓin hankali.8Ba da jimawa ba Babila za ta fadi za a hallaka ta. Ku yi makoki dominta! Ku ba ta magani domin ciwonta; ko ƙila zata warke.9Mun so mu warkar da Babila, amma ba ta warke ba. Bari mu barta, mu tafi kasarmu. Gama muguntarta ta kai har sama, ta taru a cikin giza-gizai.10Yahweh ya ce mu ba mu da laifi. Ku zo, mu faɗi ayyukan Yahweh Allahnmu a cikin Sihiyona.'11Ku wãsa kibiyoyi ku kuma ɗauki garkuwoyi. Yahweh ya na zuga ruhun sarkin Medes a kan shirin hallaka Babila. Wannan fansa ce ta Yahweh, fansa saboda hallaka haikalinsa.12Ku tada tuta a kan ganuwoyin Babila, ku tsananta tsaro; ku sa masu tsaro ku shirya kwanton ɓauna; gama UBANGIJI zai aikata abin da ya ce game da mazaunan Babila.13Ku mutanen da ke zaune a bakin rafuka masu ruwa da ku mutane masu arzikin dukiya, ƙarshenku ya zo. An rage tsawon zaren rayuwarku.14Yahweh mai ruduna ya rantse da ran sa, ' zan cika ku da mutane, kamar cincirindon fara, za kuma su tãda muryar yaƙi gãba da ku.'15Ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa. Ta wurin fahiminsa ya shimfiɗa sammai.16Idan ya yi tsawa, sai ruwaye su yi ruri a cikin sammai, gama ya kan kawo turiri daga ƙarshen duniya. Ya kan yi walƙiya domin ruwa ya kuma aiki iska daga cikin taskokinsa.17Kowanne mutum ya zama marar fahimi, marar sani. Kowanne maƙerin tama gumakansa sun kunyatar da shi. Gama sifofinsa na zubi ƙarya ce kawai babu rai a cikin su.18Ba su da amfani, aikin ruɗi ne kawai, za su lalace a ranar horonsu.19Amma Yahweh, rabon Yakubu ba kamar waɗannan ya ke ba, gama shi ne ya cura dukkan abu. Isra'ila ne harshen gãdonsa; Yahweh mai runduna ne sunansa.20Kai ne gudumata da kayan yaƙina. Da kai zan ragargaza al'ummai in hallaka mulkoki.21Da kai zan ragargaza dawakai da mahayansu; da kai zan ragargaza karusai da masu tuƙa su.22Da kai zan ragargaza kowanne mutum da kowacce mace. Da kai zan ragargaza tsoho da yaro. Da kai zan ragargaza samari da budurwai.23Da kai zan ragargaza makiyayi da garkensa. Da kai zan ragargaza manoma da ƙungiyarsu, Da kai zan ragargaza gwamnoni da jami'ansu.24Kana gani zan sakawa Babila da dukkan mazauna Kaldiya, bisa ga dukkan muguntar da suka yi a cikin Sihiyona - abin da Yahweh ya furta kenan.25Duba, ina gãba da kai, dutsen hallakarwa - abin da Yahweh ya furta kenan - wanda ke hallaka dukkan duniya. Zan miƙa hannuna gãba da kai in gangarar da kai daga can ƙoli, in mai da kai ƙonannen dutse.26Yadda ba za su ɗauki wani dutse daga wurinka su kafa tushen gini da shi ba. Za ka lalace sarai har abada - haka Yahweh ya furta.27A kafa tuta bisa duniya. A busa ƙaho bisa al'ummai, a kira al'ummai su kai mata hari: Ararat, Minni da Ashkenaz. A sa wani jarumi ya kai mata hari, a zo da dawakai kamar cincirindon fãri.28A shirya al'ummai su kai mata hari: Sarkin Medes da gwamnoninsa, da dukkan jami'ansa da dukkan ƙasashen da ke ƙarƙashin mulkinsa.29Gama ƙasar za ta girgiza ta kasance cikin azaba, tun da shirye - shiryen Yahweh ya ci gaba a kan Babila, domin ya maida ƙasar Babila lalatacciyar ƙasa inda ba mazauna.30Sojojin da ke Babila sun dena faɗa; sun koma cikin maɓoyarsu. Ƙarfinsu ya ƙare; sun zama mata - gidajenta suna cin wuta, an kakkarya makaran ƙofofinta.31Wani manzo ya tafi ya yi shela ga wani manzo, wani mai gudu ya tafi ya gaya wa wani mai gudu ya kai wa sarkin Babila rahoton an ƙwace birninsa tun daga ƙarshe har zuwa ƙarshe.32An ƙwace magangarin rafi an ƙone ciyawar fadamu, kuma mayaƙan Babila sun rikice.33Gama Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗi haka: Ɗiyar Babila ta zama kamar masussuka. Lokaci ya yi da za a tattake ta ƙasa. Da jimawa kaɗan lokacin girbi zai zo mata.34Nebukadnezza sarkin Babila ya lanƙwame ni; ya kore ni cikin ruɗami ya kuma maishe ni tukunyar da ba komi a ciki. Ya haɗiye ni kamar dodo, ya cika cikinsa da abinci na mai kyau, ya share ni sarai.'35Shi wanda ya ke zaune a Sihiyona zai ce, 'Ta'addancin da a ka yi mani da jikina ya koma kan Babila.'Yerusalem za ta ce, ' Bari jinina ya zauna a kan Kaldiya.'36Saboda haka ga abin da Yahweh ya ce: Duba, ina kusa da goya ma ki baya cikin matsalar ki in ɗauki fansa domin ki. Duba zan busar da ruwayen Babila, in sa mabulbulolinta su ƙafe.37Babila za ta zama juji, kogunan diloli, wurin jin tsoro, abin tsãki, inda ba kowa a ciki.38Mutanen Babila za su yi ruri tare kamar 'yan zakoki. Za su yi ƙara kamar 'ya'yan zaki.39Sa'ad da su ka ji zafi saboda haɗama, zan shirya masu liyafa; zan sa su bugu domin su yi murna, sa'annan su yi barci wanda ba za su ƙara tashi ba - abin da Yahweh ya furta kenan -40Zan tura su kamar ragunan yanka, kamar raguna da bunsura.41An ci Babila da yaƙi! An kame yabon dukkan duniya. Abin da mamaki yadda Babila ta zama kango a cikin al'ummai.42Teku ya zo kan Babila! Rurin balalloƙan ruwa ya cika ta.43Biranenta sun zama lalatattu, ƙasa busasshiya da kuma jeji, ƙasar da babu mai zama a ciki, ba talikin da ke wucewa ta wurin.44Saboda haka zan hori Bel cikin Babila; zan fitar daga bakinsa abin da ya haɗiye, al'ummai ba za su ƙara gangarowa wurinsa da baye - bayensu ba. Ganuwoyin Babila za su faɗi.45Mutanena, ku fice daga cikin tsakiyarta. Bari kowanne ɗayanku ya tsira da ransa daga fushin hasalata.46Kada ku bari zuciyarku ta yi suwu saboda labarin da ku ka ji cikin ƙasar, gama labaran za su zo shekara ɗaya. Bayan wannan shekara mai zuwa akwai labarai, tashin hankali zai zo cikin ƙasar. Mai mulki zai yi gãba da mai mulki.47Saboda haka, duba, kwanaki za su zo inda zan hori sassaƙaƙƙun gumaka na Babila. Dukkan ƙasarta za ta ji kunya, dukkan waɗanda a ka yanka za su faɗi cikin tsakiyarta.48Sa'annan sama da ƙasa, da dukkan abin da ke cikin su za su yi farin ciki a kan Babila. Gama masu hallakarwa za su zo dominta daga arewa - haka Yahweh ya furta.49Kamar yadda Babila ta kashe mutane su ka faɗi a Isra'ila, haka kuma za a kashe mutane su faɗi a cikin tsakiyar Babila.50Masu tsira daga takobi, ku tafi! Kada ku tsaya cik. Ku tuna da Yahweh daga nesa; bari Yerusalem ta zo cikin lamirinku.51Mun ji kunya, domin mun ga wulaƙanci; kunya ta rufe fuskokinmu, gama bãƙi sun shiga wurare masu tsarki na gidan Yahweh.52Domin haka, duba, kwanaki suna zuwa - haka Yahweh ya furta - sa'ad da zan hukunta sassaƙaƙƙun gumakanta, waɗanda suka ji rauni zasu yi nishi cikin ƙasarta dukka.53Ko da Babila zata hau cikin sammai ta inganta hasumiyarta, masu hallakarwa zasu auko mata daga wurina - haka Yahweh ya furta.54Kukan baƙinciki ya fito daga Babila, babbar ribɗewa ta fito daga ƙasar Kaldiyawa.55Gama Yahweh ya na hallakar da Babila. Yana sa muryarta mai ƙara ta lalace. Abokan gabarsu su na ruri kamar balalloƙan ruwaye masu yawa; ƙarar su ta yi ƙarfi ƙwarai.56Gama masu hallakarwa sun zo kanta - a kan Babila! - kuma an kama jarumawanta. An kakkarya bakkunansu, gama Yahweh Allah ne mai ɗaukar fansa; ba shakka zai ɗauki fansa.57Zan sa hakimanta da masu mulkinta da sojojinta su bugu, su yi barcin da ba za su tashi ba - wannan furcin sarki ne: Yahweh mai runduna ne sunansa.58Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Ganuwar Babila mai kauri za a rushe ta sarai, za a ƙone dogayen ƙofofinta. Sa'annan mutane masu kawo mata ɗauki za su yi aikin wofi; dukkan abin da al'ummai su ka yi ƙoƙarin yi mata za a ƙone shi."59Wannan ita ce maganar da Irmiya annabi ya umurtawa Seraya dan Neriya dan Maseya, sa'ad da ya tafi da Zedekiya sarkin Yahuda zuwa Babila a cikin shekara ta hudu ta mulkinsa. A lokacin Seriya shi ne babban jami'i.60Irmiya ya riga ya rubuta a cikin naɗaɗɗen littafi dukkan hallakar da za ta zo a kan Babila - dukkan waɗannan maganganu da aka rubuta game da Babila.61Irmiya ya ce da Seraiya, "Sa'ad da ka je Babila za ka gani kuma za ka karanta waɗannan maganganu da ƙarfi.62Sa'annan za ka ce, 'Yahweh, kai da kanka ka furta cewa za ka hallaka wannan wuri, kuma ba mutum ko dabba da zai zauna a cikinta, za ta zama lalatacciya har abada.'63Sa'ad da ka gama karanta wannan naɗaɗɗen littafi, ka ɗaura masa dutse ka jefa shi cikin tsakiya Ifratis.64Ka ce, 'Haka Babila zata nitse. Ba zata tashi ba saboda bala'in da na ke aiko wa gãba da ita, kuma za su faɗi."' Nan maganganun Irmiya suka tsaya.
Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) "iska mai halakarwa" ko 2) "ruhun mai hallakarwa." Wannan yana nufin cewa Yahweh zai sa ko kuma ya sa sojojin abokan gaba su je su yaƙi Babila.
Wannan sunan suna na Kaldiya, yankin Babila. Ba a bayyana dalilin da ya sa Irmiya ya yi amfani da wannan sunan a nan ba, don haka kuna so ku fassara a matsayin "Kaldiya" ko "Babila."
Jumlar "ranar" ita ce karin magana ta Ibraniyanci don "yaushe." AT: "lokacin da na halakar da Babila"
Yahweh yana son harin ya zama kwatsam har maharba ba su da lokacin shirya yaƙi.
Kalmar "duniya" ishara ce ta mutanen da ke zaune a cikin al'umman da ke kewaye da Babila. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Sanya waɗannan mutanen maye zai iya zama kwatanci na Yahweh na hukunta waɗannan al'umman ta hanyar barin Babila ta ci su da yaƙi. AT: "Babila ƙasa ce mai ƙarfi wacce Yahweh yayi amfani da ita don azabtar da duk mutanen al'umman da ke kewaye da ita da azaba mai tsanani" ko 2) Zai iya zama abin kwatance ga waɗannan al'ummomin da suke haɗuwa da Babila wajen bautar gumaka da tashin hankali. AT: "Babila ƙasa ce mai arziki da ƙarfi, kuma sauran al'ummomi suna son yin zunubi kamarta"
Ana magana game da Laifi kamar abu ne wanda za a iya zama saniya. Kalmomin "zuwa sama" da "zuwa gajimare" ƙari ne ga wani abu wanda yake da ƙarfi sosai. AT: "Don Babila tana da laifi ƙwarai"
"Ka ba da alama don kai wa bangon Babila hari"
Ana maganar rayuwar mutane kamar su zaren da Allah zai iya yankewa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Rayukanku za su ƙare da sauri"
Ana magana da yawan sojojin makiya yayin da ake maganarsu kamar su fara ne da suka mamaye garin. AT: "tare da adadi mai yawa na sojoji"
Waɗannan jimlolin suna kwatanta muryar Yahweh da babbar kara da tsawa da ruwan sama suke yi.
"karancin ilimi ne" ko "bai sani ba"
"Kai, sojojin Babila, kuna"
AT: "zaku ganshi lokacin dana biya"
Yahweh yayi magana game da Babila kamar ba babbar “dutsen hallaka ba” amma yanzu dutse ne da ya lalata. AT: "Zan ... sanya ku tarin duwatsu marasa amfani"
Yahweh ya kwatanta dawakai da yawa kamar tarin fara. AT: "kawo dawakai da yawa tare da sojoji da sauri"
Isasar ƙira ce ga mutanen da suke zaune a ƙasar. Girgiza da kasancewa cikin baƙin ciki kalmomi ne na tsoro ƙwarai. AT: "mutanen da ke zaune a cikin Babila za su girgiza da tsoro kuma su kasance cikin baƙin ciki"
wahala da baƙin ciki wanda zai kawo wa mutum hawaye
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "makiya sun mamaye duk garin"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "makiya sun mamaye duk hanyoyin hawan kogin"
"'Yar Babila" a nan akwai wani suna ga mutanen da ke zaune a cikin Babila.
Mutane suna sussukar hatsi ta wurin tattaka shi a masussuka, kuma Yahweh yana magana akan mutanen da suke azabtar da 'yar Babila kamar suna sussukar hatsi.
Girbi kwatanci ne na sakamakon ayyukan da mutane suka yi a da. Babila za ta fuskanci sakamakon zunubin mutanenta. AT: "Allah zai hukunta ta saboda zunubanta"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne (1) "ya sa na kasa tunani sosai" ko (2) "ya danne ni."
Wannan yana ci gaba da magana game da Babila kamar ta dodo. Wannan yana nuna a wata hanyar ra'ayin da ya gabata cewa Babila ta ƙwace komai daga Isra'ila. Anan "abinci" yana wakiltar duk kyawawan abubuwan da suke wurin a da.
Duk waɗannan jimlolin suna nufin mace.
gine-ginen da suka zama tarin duwatsu
gida ga karnukan daji
"ba wanda ya rayu"
Makiyan Babila sun ci nasara a kanta. "Balalloƙan" suna wakiltar kungiyoyin mutane da yawa da suka mamaye Babila. Kalmomin "teku" da "ruwa" galibi suna wakiltar al'ummomi.
"Biranen Babila"
Bel shine babban allahn mutanen Babila kuma yana wakiltar duk ƙasar da kuma mutanen da suke bauta mata.
Al’ummai da yawa da suka zo Babila don yin hadaya ga Bel ana maganarsu a matsayin kogi da yake tafiya tare. AT: "mutanen wasu ƙasashe ba za su ƙara zuwa cikin manyan rukuni ba"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da kuka ji labarin da ke cikin ƙasar"
Mai mulkin suna ne ga ƙasashen da ke ƙarƙashin ikonsa. AT: "Kasashe za su yi yaƙi da sauran ƙasashe"
Ana maganar mutanen Babila kamar su ne garin da kanta, kuma ana maganar garin kamar mace. AT: "mutanen Babila ... kasarsu ... wadanda aka yanka ... tsakiyar su"
Ana kallon sama da ƙasa kamar mutane ne.
kalmomin da wani mutum yayi amfani da su don cutar da wani
yin kuka saboda zafi ko baƙin ciki
Ana bayyana wannan tunani ta hanyoyi daban-daban guda biyu don girmamawa.
Ruwan igiyoyin ruwa na tekun da ambaliyar ruwa suna yin amo mai ƙarfi, kuma makiya za su yi amo da ƙarfi yayin da suke zuwa.
Ana iya canza wannan jumlar don samun aiki. AT: "makiyanta sun kame mayaƙanta"
Waɗannan yana nufin Babila.
Waɗannan sunayen maza ne.
Idan yarenku yana da kalma ga dabbobi waɗanda yawanci suke rayuwa tare da mutane, kuna iya amfani da shi a nan, saboda Irmiya 51:36 ya ce Babila za ta zauna da namun daji.
Dutse da littafin za su ɓace a cikin ruwa, ruwan zai lalata littafin, kuma Babila ba za ta ƙara zama kamar birni ba ko kuma ta sami gine-ginen da mutane za su zauna a ciki ba.
1Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa'ad da ya fara mulki; ya yi mulki a Yerusalem shekara goma sha ɗaya. Sunan mahaifiyarsa Hamutal ne; ita ɗiyar Irmiya ce daga Libna.2Ya yi mugunta a gaban Yahweh; ya yi dukkan abin da Yohoaikim ya yi.3Ta wurin fushin Yahweh dukkan waɗannan abubuwa suka faru a Yerusalem da Yahuda, har sai lokacin da ya kore su daga gabansa. Sa'annan Zedekiya ya yi wa sarkin Babila tawaye.4Ya zama a cikin shekara ta tara ta mulkin Zedekiya, a cikin wata na goma, a cikin rana ta goma ga watan, Nebukadnezza sarkin Babila, ya zo da dukkan mayaƙansa gãba da Yerusalem. Suka yi zango daura da ita, suka kafa sansanin yaƙi kewaye da ita.5Suka kewaye birnin ba shiga ba fita, har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.6A cikin wata na hudu, a kan rana ta tara ga watan yunwa ta yi tsanani a cikin birnin har ma ba abin da mutane za su ci a ƙasar.7A ka ɓalle birnin aka shiga, dukkan mayaƙa su ka gudu su ka fice daga cikin birnin ta hanyar da ke tsakanin ganuwa biyu a cikin dare, ta lambun sarki, duk da ce wa Kaldiyawa su na kewaye da birnin. Su ka tafi wajen Arabah.8Amma sojojin Kaldiyawa su ka bi sarki su ka cimma Zedekiya a filin Kogin Yodan kusa da sararin kwarin Yariko. Dukkan mayaƙansa su watse daga wurinsa.9Suka kama sarki suka kawo shi wurin sarkin Babila a Riblah cikin ƙasar Hamat, inda ya yanke ma sa hukunci.10Sarkin Babila ya yanka 'ya'yan sarki Zedekiya maza ya na gani, kuma a Riblah ya yanka dukkan shugabannin Yahuda.11Sa'annan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya, ya ɗaure shi da sarƙa ta jan ƙarfe ya kawo shi Babila. Sarkin Babila ya sa shi a kurkuku har zuwa ranar mutuwarsa.12To, a cikin wata na biyar, a kan rana ta goma ga wata, a shekara ta goma sha tara ta mulkin Nebukadnezza sarki, sarkin Babila, Nebuzaradan ya zo Yeruselem. Shi ne jami'in masu tsaron sarki, shi kuma bawan sarkin Babila ne.13Ya ƙone gidan Yahweh, da fadar sarki da dukkan gidajen Yerusalem; ya kuma ƙone kowanne gini mai mahimmanci.14Ganuwar da ta kewaye Yerusalem kuma, mayaƙan Babiloniyawa da ke tare da jami'in masu tsaron sarki suka rushe su.15Su marasa galihu da sauran mutanen da su ka ragu a cikin birni, waɗanda su ka bijire su ka tafi wurin sarkin Babila da sauran masu aikin hannu - Nebuzaradan jami'in masu tsaron sarki ya kwashe su ya kai su bauta.16Amma Nebuzaradan jimi'in masu tsaron sarki ya bar waɗansu cikin marasa galihu a ƙasar domin su yi aiki a garkar inabi da gonaki.17Game da ginshikai na tagulla da ke na gidan Yahweh kuwa, da diraku, da babban bangaji na tagulla da ake kira "Teku" da su ke cikin gidan Yahweh, Kaldiyawa su ka kakkarya su gutsu - gutsu suka kwashe dukkan tagullan suka koma da su Babila.18Tukwanen, da ceburan, da tsinkunan gyara fitilu, da bangazai, da dukkan kayan aikin na tagulla waɗanda firistoci suka yi hidima da su a haikali - Kaldiyawa suka kwashe su dukka suka tafi da su.19Daruka da tasoshin ƙona turare, da bangazai, da tukwane, da maɗorin fitilu, da kaskuna, da darurruka da aka yi da su zinariya da waɗanda aka yi su da azurfa - jami'in masu tsaron sarki ya kwashe su dukka.20Ginshiƙai guda biyu, da babban bangajin tagulla da aka sa ni da "Teku," da bijimai guda goma sha biyu na tagulla da su ke karkashin dirakun, abubuwan da Sulaiman ya yi domin gidan Yahweh, ɗauke da tagulla da ta wuce gaban aunawa.21Ginshikan kamu sha takwas ne kowannen a tsayi, da layikan da su ke kewaye da su kuma kowanne kamu goma sha biyu ne. Kowannen su kaurin yatsu hudu ne masu rami.22Akwai gammon tagulla a bisan sa. Gammon tsawon kamu biyar ne, an yi masa aikin dajiya da siffofin 'ya'yan manta'uwa waɗanda a ka yi da tagulla. Ɗaya ginshikin da nashi 'ya'yan manta uwar dai - dai su ke da na farin.23Don haka akwai manta'uwa tasa'in da shida bisa gefen gammunan, da manta'uwa guda ɗari a bisa kewayen aikin dajiyar.24Jami'in masu tsaron sarkin ya dauki Seraiya babban firist tare da Zafaniya da firist na biyu da masu tsaron ƙofa su uku a matsayin 'yan kurkuku.25Daga cikin birni kuwa ya kama jami'in da ke kula da sojoji da mutane bakwai masu ba sarki shawara, waɗanda suke cikin birni har wannan lokaci. Ya kuma kama jami'in sojojin sarki wanda shi ne ke shigar da mutane aikin soja, tare da waɗansu mahimmam mutane guda sittin waɗanda su ke cikin birni.26Sai Nebuzaradan jami'in masu tsaron sarki ya ɗauko su ya kawo su wurin sarkin Babila a Ribla.27Sarkin Babila ya kashe su a Ribla cikin ƙasar Hamat. Ta haka Yahuda ta fita daga ƙasarta ta tafi bauta.28Waɗannan su ne mutanen da Nebukadnezza ya kai bauta cikin shekara ta bakwai, mutanen Yahuda su 3,023.29A cikin shekara ta takwas ta Nebukadnezza, ya ɗauki mutane 832 daga Yerusalem.30A cikin shekara ta ashirin da uku ta Nebukadnezza, Nebuzaradan, jami'in masu tsaron sarki ya ɗauki mutum 745 cikin mutanen Yahudiya ya kai su bauta. Dukkan waɗanda a ka kai bauta su ne mutum 4,600.31Ya zama kuma a cikin shekara ta talatin da bakwai ta hijira Yehoyacin, sarkin Yahuda, a cikin wata na goma sha biyu, a kan rana ta ashirin da biyar ga wata, sai Awel-Marduk, sarkin Babila ya saki Yehoyacin sarkin Yahuda daga kurkuku. Wannan ya faru ne a cikin shekarar da Awel-Marduk ya fara mulki.32Ya yi masa maganar alheri, ya ba shi wurin zama da ya fi na sauran sarakunan da suke tare da shi daraja a Babila.33Awel-Marduk ya cire wa Yehoiyacin kayan 'yan sarƙa. Yehoyacin ya yi ta cin abinci a teburin sarki dukkan sauran rayuwarsa,34a kan ba shi kuɗin cin abinci kullum har mutuwarsa.
Wannan sunan mace.
Wannan sunan wani wuri ne.
Ana amfani da wannan jumlar a nan don alamar farkon sabon ɓangaren labarin.
bayan Zedekiya ya yi shekara takwas yana sarauta, a watan kalanda na goma, a rana ta goma ga watan
"Sojojin Nebukadnezza sun kafa sansani daura da Yerusalem"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Babiloniyawa sun fasa bangon da ke kewaye da birnin"
Wannan ta nufin bangon lambun sarki da na birni
Idanun ido ne na mutum gaba ɗaya. Ya kamata mai karatu ya kuma fahimci cewa wataƙila wasu sun taimaki sarkin Babila ya kashe 'ya'yan Zedekiya. AT: "ya tilasta wa Zedekiya kallo lokacin da sarkin Babila ke yanka 'ya'yan Zedekiya"
Nebukadnezza ya yi sarauta shekara goma sha takwas, wata huɗu, da kwana tara. Wannan shine wata na biyar a kalandar Ibraniyanci. Lokacin rani ne. Rana ta goma tana kusa da farkon watan Agusta a kan kalandar Yamma.
"mutanen da suka fi talauci a ƙasar"
Wannan kwandon ruwa ne da ake amfani da shi wajen bautar Yahweh.
Ginshiƙan ba su da fili a ciki.
Wannan shine saman kowane ginshiƙi.
Wannan shi ne mutanen da suke tsaron ƙofar gar.i
Wannan sunan birni ne.
Wannan shine watan sha biyu kuma na ƙarshe na kalandar Ibraniyanci. Rana ta ashirin da biyar tana kusa da tsakiyar Maris a kan kalandar Yamma.
Ya zama sarkin Babila bayan Nebukadnezzar.
"Evil-Marduk ya yi magana mai kyau ga Yehoiyacin"
"wurin zama a teburin da ke kusa da inda Evil-Marduk ya zauna"
1Ƙasar da dã ke cike da mutane yanzu tana zaman kaɗaici. Ta zama kamar gwauruwa ko da ya ke babbar al'umma ce dã. Dã gimbiya ce a cikin al'ummai, amma yanzu an sa ta aikin bauta na dole.2Tana kuka da koke-koke da dare, kuma hawayenta sun rufe kumatunta. Babu masoyinta da ke yi mata taimako. Dukkan abokananta sun yashe ta. Sun zama maƙiyanta.3Bayan talauci da ƙunci, Yahuda ta tafi zaman bauta. Tana zaune a cikin al'ummai kuma ta rasa samun hutawa. Dukkan masu korarta a guje sun wuce ta a cikin damuwarta.4Hanyoyin Sihiyona na makoki saboda babu waɗanda suka zo bukukuwan da aka shirya. Dukkan ƙofofinta sun zama yasassu. Firistocinta na nishi. 'Yanmatanta na cikin da baƙinciki kuma ita kanta tana cikin cikakken ƙunci.5Magabtanta sun zama iyayengijinta; maƙiyanta sun azurta. Yahweh ya ƙuntata mata domin yawan zunubanta. An kai ƙananan 'ya'yanta bauta ga magabcinta.6Kyau ya rabu da ɗiyar Sihiyona. 'Ya'yan sarakunanta sun zama kamar bareyin da ba za su iya samun abinci ba, kuma suna tafiya da ƙyar a gaban masu farautarsu.7A kwanakin ƙuncinta da rashin wurin zamanta, Yerusalem zata tuna da dukiyoyinta masu daraja wadda take da su a kwanakin dã. Sa'ad da mutanenta suka faɗi a hannun abokan gãba, babu wanda ya taimaketa. Abokan gãba sun gan ta sun kuma yi dariya ga hallakarta.8Yerusalem ta yi zunubi ƙwarai, saboda haka ta zama abin ƙi kamar wani abin ƙyama. Dukkan waɗanda ke girmama ta sun yashe ta tun da suka ga tsiraicinta. Tana nishi tana ƙoƙarin juyawa.9Ta zama marar tsabta a karkashin zannuwanta. Ba ta yi tunani a kan kwanakinta masu zuwa ba. Faɗuwarta abin takaici ne. Babu wanda zai ta'azantar da ita. Ta yi kuka cewa "Dubi wuyar da nake sha, Yahweh, gama makiyana sun ƙaru da yawa!"10Abokin gãba yasa hannunsa a dukkan dukiyoyinmu masu daraja. Ta ga al'ummai sun shigo wurinta mai tsarki, ko da ya ke ka umarcesu kada su shiga wurin taruwar jama'arka.11Dukkan mutanenta sun yi nishi sa'ad da suke neman abinci. Sun ba da dukiyoyinsu masu daraja domin abincin da zai rayar da su. Yahweh, ka dube ni ka kula da ni, gama na zama marar daraja.12Wato a wurinku ba komai ba ne, dukkanku da ke wucewa? Ku duba ku gani ko akwai wani mai shan azaba kamar ni, tun da Yahweh ya azabtar da ni a ranar fushinsa mai zafi.13Daga can bisa ya aiko da wuta a ƙasusuwana, kuma ta cinye su. Ya yafa raga domin ƙafafuwana ya kuma maida ni baya. Ya maida ni kullum a yashe da somewa. Karkiyar laifofina a ɗaure suke a hannunsa.14An ɗaura su tare an sa su a kan wuyana. Ya sa ƙarfina ya ƙare. Ubangiji ya bashe ni a hanun maƙiyana, kuma ba zan iya tsayawa ba.15Ubangiji ya tura majiya ƙarfina gefe waɗanda ke yi mani kariya. Ya kira taron jama'a găba da ni don su murƙushe jarumawana. Ubangiji ya tattake ɗiyar Yahuda budurwar nan, a wurin matse ruwan inabi.16Saboda waɗannan abubuwa na yi kuka. Idanuwana, ruwa na zubowa ƙasa daga Idanuwana tun da mai ta'azantar da ni wanda zai 'yantar da raina yana nesa da ni. 'Ya'yana sun lalace saboda maƙiyin ya yi nasara.17Sihiyona ta shinfiɗa hannuwanta da făɗi; ba wanda zai ta'azantar da ita. Yahweh ya umarci waɗanda ke kusa da Yakubu su zama abokan găbarsa. Yerusalem ta zama abin rashin tsabta a garesu.18Yahweh mai adalci ne, gama na tayar wa dokokinsa. Ku ji, dukkan mutane, ku kuma ga damuwata. Budurwaina da jarumawana sun tafi bauta.19Na yi kira ga abokaina, amma sun zama maciya amana a gareni. Firistocina da dattawana sun hallaka a cikin birnin, sa'ad da suke neman abinci na ceton ransu.20Duba, Yahweh, gama ina cikin kunci; cikina ya ɗuri ruwa, sai na damu a cikin zuciyata, gama ni mai tayarwa ne sosai. A waje, takobi ya sa uwa makoki, a cikin gida kuma babu kome sai mutuwa.21Sun ji nishina, amma ba mai ta'azantar da ni. Dukkan maƙiyana sun ji batun matsalata kuma sun yi murna cewa kai ka yi haka. Kã kawo ranar da ka alƙawarta; yanzu bari su zama kamar ni.22Bari dukkan muguntarsu ta zo gabanka. Ka yi masu yadda ka yi mani saboda laifofina. Nishe-nishe na da yawa kuma zuciyata ta some.
An yi amfani da nau'ikan karin waƙoƙi a cikin wannan littafin.
Marubucin Makoki ya rubuta game da birnin Yerusalem kamar mace ce.
Wannan jumla tana kwatanta Yerusalem da macen da ba ta da kariya saboda mijinta ya mutu.
Wannan na magana ne a kan Yerushalima da aka girmama kamar ita gimbiya ce. AT: "Da ita kamar gimbiya ce a cikin al'ummai"
"an maida da ita baiwa ta dole" Za a iya juya wannan a aikace. AT: "amma yanzu ta zama baiwa"
Marubucin ya bayyana Yerusalem kamar ta na da motsin zuciya kamar mutum. Birnin kuma na tsaye a matsayin mazaunanta. AT: "mazaunan birnin suna kuka da makoki ... kuma hawayen su ya rufe kuncin su"
Kalmar nan "kuka" da koke-koke wat nishi da mutun yakan yi idan yana kuka da ƙarfi. AT: "kuka da karfi"
A nan Yahuda na nufin mazaunanta. AT: "mutanen Yahuda sun tafi bauta" ko "an kwashi mutanen Yahuda zuwa wata ƙasa.
A nan an kwatanta masarautar Yahuda da mace. "Ita" ' kuma na wakiltar mazaunan Yahuda. AT: "Mutanen ta sun tafi ... sun samu"
"rasa samun hutu" ko "koyaushe a cikin tsoro"
Wannan na magana a kan mutanen Yahuda da magapta suka kama kamar su mace ce da masu bin ta suka kama ta.
Za a iya bayyana kalman nan "damuwa" a wani yanayi. AT: "a lokacin damuwarta" ko "a lokacin da take damuwa"
Marubucin yayi magana game da hanyar da take zuwa Sihiyona suna makoki kamar su mutane ne.
"bukukuwan da Allah ya ce su yi"
Wannan kalmar "ta" na nufin Sihiyona. AT: "dukan ƙofofin Sihiyona sun zama kango"
"Magabtan Sihiyona suna mulkinta; maƙiyanta sun ci nasara"
Wannan na magana a kan duk wani abin da ke da kyau a Sihiyona da aka lalata kamar "kyau" mutum ne da bar Sihiyona. AT: An lalace duk abin da ke da kyau game da yar Sihiyona.
Wannan sunan take ne na Yerusalem, wanda ake magana a nan kamar mace ce.
Wannan na magana a kan yerima Sihiyona ba ta da komai da za ta ci kamar barewar da baza ta iya samun ciyawa ta ci ba. AT: "Yariman ta suna cikin yunwa, suna kamar barewa da baza ta iya neman ciyawa su ci ba"
Barewa wata dabba ce mai matsakaici, mai cin -ciyawa, wadda mutane ke yawan farautarta domin abinci. Kuma, ita dabba ce mai kyaun gani.
"ba su da ƙarfin guduwa daga" or "ba su da ƙarfi a da"
"mutumin da yake farautarsu"
"A lokacin ƙuncinta da rashin wurin zamanta"
A nan "Yerushalima" na maganar mutanen da ke zama a can. Maganar nan "kira ga zuciya" wata karin magana ce. AT: "mutanen Yerusalem za su tuna" ko "Yerusalem za su tuna"
Wannan na nufin arzikinsu masu kyau.
"a dã." Wannan na nufin lokaci kafin a kama mutanen Yerusalem. AT: "kafin bala'in ya faru"
Kalmar nan "hannu" na nufin sojojin abokan gaba. AT: "Lokacin da magabci ya ci nasara ya kuma kama mutanenta"
Wannan yana nuna cewa sun yi murna da yi wa Yerusalem ba'a lokacin da aka lalata ta.
Za a iya bayyana wannan kalma "hallaka" a aikace. AT: "saboda ta halaka" ko kuma "yayin da suka halaka ta"
Wannan na maganar Yerusalem da ake yi wa ba'a kamar yadda ake yi wa mata ba'a a lokacin da bata da tsabta. Bisa ga dokokin Musa, ana maishe mata mara tsabta a lokacin zubda jini na wata wata. AT: "Zunubin Yerusalem ya maida ita da datti kuma mara tsabta, saboda haka bata karɓu ba a wurin Allah"
Wannan ya kwatanta Yerusalem kamar mata wadda ta yi zunubi, yayin da ya tsaya domin mazaunan Yerusalem. AT: "Mutanen Yerusalem sun yi zunubi sosai"
"ita tsirara." An bayyana Yerusalem a matsayin macen da an nuna wa kowa tsiraicinta don a kunyata ta.
Maganar nan "faɗiwar ta" karin magana ne. AT: "faɗuwarta ya bada mamaki" ko "waɗanda suka ga halakar ta sun ji mamaki"
Ma'anar na iya yiwuwa 1) marubucin Makoki yana magana kai tsaye ga Yahweh ko 2) an bayyana yadda Yerusalem ke magana da Yahweh kamar tana magana da mutun.
Wannan karin magana ne. AT: "ya kwace arziƙin ta" ko "ya sata"
Kalmar "ta" na nufin Yerusalem.
Kalmar nan "Ka" na nufin Yahweh.
Kalmar nan "ta" na nufin Yerusalem wanda ake mata take kamar mace. AT: "mazaunanta" ko "mazaunan birnin"
"don ceto rayukansu" ko "maido da karfinsu"
A nan Yerusalem ta fara yin magana da Yahweh kai tsaye.
Wannan zargi ne na mutanen da ke wucewa a Yerusalem kuma ba sa kula da lafiyan ta. Za'a iya rubuta wannan tambayar a matsayin wani magana. AT: "Duk ku dake wucewa ya kamata ku kula sossai da wahalarta!"
Waɗannan kalmomi suna da ma'ana iri daya. tare suna gayyatar mai karatu don fahimta ta hanyar cewa babu wanda ya wahala sosai.
Za'a iya rubuta wannan a aikace. AT: "azabar da Yahweh ya sa mani"
Anyi anfani da kalman nan kamar karin magana. AT: "lokacin da yayi fushi mai zafi"
Wannan na magana a kan Yahweh yana horas da Yerusalem kamar Yerusalem mutum ne da Yahweh ke horaswa. AT: "ya aika horo mai azaba a cikin jiki na, kuma ya lalata ni" ko "ya aika horo mai lalataswa a cikin tsakkiyar Yerusalem, kuma ya lalata birnin"
A nan "wuta" na waƙiltar azaba kuma "ƙasusuwa" na waƙilta cikin jikin wani. AT: "ya aika azaba a cikin ƙasusuwa na" or "ya aika azaba a cikin jiki na"
"ya bashe ni a cikin hannun maƙiyana." A nan ana waƙiltar ikon maƙiyansu ta wurin "hannunsu" AT: "ya bada ni ga ikon maƙiyana" ko "ya bar maƙiyan sun ci mani"
"sojoji mafi karfi"
A nan sojoji abokan gaba da suka kai wa Yerusalem hari, ana ambaton su kamar mutane da suka taru ne domin zargi da la'anta wani. AT: "sojoji da yawa"
Wannan na nufin mazaje majiya ƙarfi a lokacin rayuwarsu.
Wannan na maganar Yerusalem ba ta da kowa da zai ta'azantar da ita kamar tana da mai ta'aziya, amma wai yana da nisa. Za'a iya bayyana kalman nan "mai ta'aziya" a aikace. AT: "ba wanda zai ta'azantar da ni, ya kuma rayar da raina"
A nan Yerusalem bata magana game da kanta kuma; amma marubucin ya bayyana Yerusalem. Yayi maganar Sihiyona kamar mata ce da ta ɗaga hannunta don ta nemi taimako. AT: "Sihiyona ta nemi taimako"
"mutane da ke kusa da Yakubu" ko "ƙasashe da suka kewaye Yakubu"
Za'a iya bayyana wannan kalma "damuwa" kamar "damuwa" AT: "duba yadda nake makoki"
A nan ana waƙiltar dukan mutanen Yerusalem waɗanda aka kai bauta da "budurwai" da "jarumai na"waɗanda aka ɗauka. AT: "Mutane da yawa, tare da budurwai na da jarumai na, sun tafi bauta"
Wannan na nufin sun yaudare shi. "Sun yaudare ni"
A nan matar, na waƙiltar Yerusalem, na nufin "zuciyarta" don a jajjada yadda take ji. AT: "zuciyarta ta karaya" ko "na damu sosai"
"Takobi" kwantanci ne na maƙiyi. AT: "maƙiyi ya kashe mamar yara"
"Mutane sun ji nishi na." Yerusalem ta cigaba da magana kamar dai ita mace ce.
Kalmar nan "Kai" na nufin Yahweh.
Wannan roƙo ne wa maƙiyan Yerusalem su wahala kamar yadda mutanen Yerusalem suka wahala. AT: "yanzu bari su wahala kamar ni"
1Ubangiji yã rufe ɗiyar Sihiyona a karkashin gizagizan fushinsa. Ya jefar da darajar Isra'ila ƙasa daga sama zuwa duniya. Bai tuna da matashin sawunsa a ranar fushinsa ba.2Ubangiji yã haɗiye yã kuma ƙi jin tausayin dukkan garurruwan Yakubu. A ranar fushinsa ya jefar da ƙayatattun biranen ɗiyar Yahuda a ƙasa; a cikin rashin girmamawa ya saukar da mulkin da shugabaninsa ƙasa.3Da zafin fushinsa ya datse kowanne ƙaho na Isra'ila. Ya cire hannun damansa daga gaban maƙiyi. Ya ƙone Yakubu kamar harshen wuta da ke cinye dukkan abin da ke kewaye da shi.4Kamar maƙiyansa ya ɗana bakansa gare mu, ya yi shirin harbi da hannun damansa. Ya yayyanke dukkan masu faranta masa rai a rumfar ɗiyar Sihiyona; Ya zuba fushinsa kamar wuta.5Ubangiji ya zama kamar maƙiyi. Ya haɗiye Isra'ila. Ya haɗiye dukkan fadodinta. Ya hallakar da wuraren mafakarta. Ya ƙara baƙinciki da makoki cikin ɗiyar Yahuda.6Ya kai wa rumfar sujadarsa hari kamar bukkar gona. Ya rusa wurin tsattsarkan taron jama'a. Yahweh yasa a mance da tattsarkar Asabar da taron jama'a a Sihiyona, gama ya wofintar da sarki da firist cikin zafin fushinsa.7Ubangiji ya ƙi bagadinsa ya kuma musanci tsarkakan haikalinsa. Ya ba da bangayen fadodinta ga hannun maƙiyi. Sai suka ta da ihu a gidan Yahweh, kamar ranar ayyanannen idi.8Yahweh ya ƙudura ya hallakar da garun birnin ɗiyar Sihiyona. Ya miƙar da igiyar gwaji kuma bai ɗauke hannunsa daga rusar da garun ba. Ya sa kagara da garu suyi makoki; ya wofintar da su tare.9Ƙofofinta sun lume cikin ƙasa; ya rusar ya kuma karya shingayen kofofinta. Sarkinta da 'ya'yan sarkinta na cikin al'ummai, babu doka kuma, har anabawanta sun rasa wahayi daga Yahweh.10Dattawan ɗiyar Sihiyona na zaune shiru a ƙasa. Sun watsa ma kawunansu ƙasa suna kuma sanye da tufafin makoki. 'Yan matan Yerusalem sun russunar da kawunansu ƙasa.11Hawayen idanuwana sun gaji da zubowa; cikina ya kiɗime, dukkan raina na cike da baƙinciki saboda rushewar ɗiyar mutanena, yara da jarirai sun some a titunan birnin.12Suka cewa uwayensu, "Ina hatsi da ruwan inabi?" sa'ad da suka some kamar mutumin da ya ji ciwo a titunan birnin, rayukansu suka kasance cikin baƙinciki a hannuwan uwayensu13Me zan ce maki, ɗiyar Yerusalem? Me zan kwatanta ta'aziyar da zan yi maki 'yar Sihiyona? Ciwonki na da girma kamar teku. Wa zai iya warkar da ke?14Anabawanki sun gano wahayin ƙarya dana wofi domin ki. Ba su fallasar da laifofinki har da farfaɗo da ke daga hasarar bauta ba, amma suka fitar da maganganun ƙarya dana kaucewa daga hanya.15Dukkan waɗanda suka wuce a hanya suna tafa maki hannuwansu. Suna tsãki suna kaɗa kai gãba da 'yar Yerusalem suna cewa, "Ba wannan ne birnin da ake kira 'Cikakken Kyau,' 'Farin Cikin dukkan Duniya' ba?"16Dukkan maƙiyanki sun buɗe bakunansu suna maki ba'a. Suna gwalo da cizon baki da cewa, "Mun haɗiye ta! Wannan ce ranar da muke jira! Muna jiran ganinta!"17Yahweh ya aikata abin da ya shirya zai yi. Ya cika maganarsa. Ya tumɓuke ki da rashin tausayi, gama ya bai wa maƙiya dama su yi farinciki a kan ki; ya ɗaga ƙahon maƙiyanki.18Zuciyarsu ta yi kuka ga Ubangiji, garun 'yar Sihiyona! Ki sa hawayenki su kwararo ƙasa kamar kogi dare da rana. Kar ki ba kanki da idanunki hutu,19Tashi, yi kuka da dare, sau da yawa da almuru! Ki zubo da zuciyarki kamar ruwa a gaban fuskar Ubangiji. Ki ɗaga hannuwanki gareshi domin rayukan 'ya'yanki waɗanda suka some da yunwa a kowanne gefen titi.20Duba, Yahweh, ka kula da waɗanda ka yi masu haka. Shin mata zasu iya cinye 'ya'yan cikinsu, 'ya'yan da suka yi renonsu? Yana yiwuwa a kashe firist da annabi a rumfar sujada ta Ubangiji?21Matasa da tsofaffi na kwance a ƙurar titunan. "Yan mata da samari sun făɗi ta takobi; kã yanka su ba tare da tausayinsu ba.22Kã yi kira, kamar yadda kake kiran mutane a ranar idi, ina fargaba a kowanne gefe, a ranar fushin Yahweh, babu wanda zai kuɓuta ko ya rayu; waɗanda na lura na kuma tasar da su, maƙiyana sun hallakar da su.
Sabuwar waka ya fara. Marubucin Makoki yayi amfani da hanyoyi daban-daban domin ya nuna yadda mutanen sun rasa tagomashi daga wurin Allah.
Wannan yana maganar fushin Yahweh a kan Yersalem. Manufar na iya zama 1) Allah ya so ya kawo bala'i ga mazauna Yerusalem ko 2) Allah ya rigaya ya cutar da mutanen. .
Wannan magana "darajar Israila" na nufin Yerusalem. Wannan shafi na magana a kan mutanen Yerusalem sun rasa tagomashi daga Ubangiji kamar an jefa su ne daga gaban sa. Maganar nan "daga sama zuwa duniya" babban nisa ne da ke wakiltar yawan rashin tagomashin= daga Ubangiji. AT: " Yerusalem, darajar Israila, ta rasa dukan tagomashi da Ubangiji" or "Yerusalem ta rasa dukan tagomashi daga Ubangiji"
Wannan na magana a kan Ubangiji yana ɗaukar ƙarfin Israila kamar yana yanke masu ƙahonninsu. Kalman nan ƙaho" na nufin ƙahon dabba, ba abin kiɗi ba. AT: "ya ɗauke dukan ƙarfin Israila"
A nanana wakiltar kariyar Ubangiji ta wurin "hannun damansa." AT: "ka daina ƙare mu daga abokan gabanmu"
"Diyar Sihiyona"wani suna ne wa Yerusalem, wanda aka yi magana a nan kamar mace ce. Maganan nan "rumfar ɗiyar Sihiyona" na magana Yerusalem kamar "rumfa" domin jajjada cewa gida ce wa waðanda ke zama a can. AT: "waɗanda ke zaune a Yerusalem"
Za'a iya bayyana kalmonin nan "makoki" da baƙin ciki" AT: "Ya sa mutane da yawa a cikin ɗiyar Yahuda suna baƙin ciki da makoki"
karamin bukka domin tara kayan aiki na gona ko kuma mafaka na mai tsaron lambu
Za'a iya faɗar wannan a aikace. AT: "Ya sa mutane a Sihiyona su manta da muhinmin taro da Asabaci.
ya juya ... ga abokan gaba.
Kalmar nan "ta" na iya nufin kaikali ko Yerusalem. Fassarar na iya yiwuwa 1) "bangayen fadodinta haikali" ko 2) "bangayen fadodin Yerusalem"
Wannan kwatanci ne mai ban tsoro tsakanin farin ciki, hayyaniyar buki na Isra'ila da babbar murya game da Babila.
Wannan ma magana a kan shirin rushe katanga kamar ya gwada shi kamin ya rushe shi, domin ya san yawan yadda zai rushe. AT: "Ya auna tsawon katangar "ya na kamar ya gwada katangar"
Za'a iya faɗar wannan ba tare da munana biyu ba. Kuma, a nan ana nufin Ubangiji ta wurin "hannunsa." "da hannunsa ya rushe ganuwar" ko "ya rushe katangar"
An yi maganar katangu da kagaru kamar mutane ne da suka yi makoki kuma suka mutu. AT: "Domin ya rushe kagaru da katangu, suna kama da mutane da ke makoki kuma suka rasa ƙarfinsu.
Tsoffin biranen suna da ainihin "katanga" don kiyaye mahara, da layin waje na "kagaru" don kiyaye maharan daga katangar.
Sau da yawa mutane suna zaunawa a ƙasa don su nuna makoki. AT: "zaune a ƙasa, yin makoki shiru"
Wannan shi ne wani mataki na makoki. AT: "sun rusuna da kansa su a ƙasa suna baƙin ciki"
Wannan karin magana ne. AT: "na yi kuka har sai da na kasa iya yin kuka kuma"
Kalman nan "kiɗime" na nufin tafiya a kewaye cikin rikici, kullum a juyawar siffar zobe. Wannan baya nufin cewa a zahiri ciki na kiɗimewa, amma na bayyana yadda marubucin yake ji. AT: "ciki na na ciwo" "ciki na yi mani zafi"
Wannan tambaya ce da ke roƙon wani abinda za'a ci. Yaran suna faɗa wa mamarsu cewa suna jin yunwa. Wannan kalmar "hatsi da ruwan inabi" hanya ce ta cewa abinci da abin sha. AT: "Ka bamu wani abu mu ci mu sha.
Marubucin na amfani da wannan tambayar domin ya bayyana cewa bai san abinda zai ce ba don ya taimake Yerusalem. Za'a iya faɗin waannan tambayar kamar bayani. "Babu abin da zan ce maki ... Yerusalem."
Marubucin yayi amfani da tambayar nan don ya bayyana cewa ba zai iya yi wa Yerusalem ta'aziya ba. Za'a iya faɗin wannan kamar bayani. "Babu abinda zan kwatanta da ke ... Sihiyona."
"Wanene zai iya sake gyara ta?" Marubucin yayi amfani da tambayar nan don ya bayyana cewa babu wanda zai iya sake gyara Yerusalem zuwa yadda take a da. Za"a iya faɗin wannan a bayani. "Ba wanda zai iya warkar da ke"
Waɗannan ayyuka ana amfani dasu ne domin ba'a da cin mutuncin wasu. AT: "yi maka ba'a ta wurin tafa hannuwansu ... tsaki da kaɗa kawunansu"
Ana amfani da wannan tambayar domin ba'a . Za'a iya rubuta wannan kamar bayani. AT: "Wannan birni wanda suke kira 'Kammalalliyar Kyakkyawa', 'Farin cikin duk Duniya' ba kyau ko farin ciki ko kuma"
A nan mutane sun yi magana a kan hallaka da Yerusalem kamar yadda dabbobi ke haɗiye abincinsu. AT: "Mun gama hallaka Yerusalem gaba ɗaya"
Wannan na nufin abokan gaba sunyi farin ciki domin sun ci nasara da su. AT: "farin ciki a kan cin nasara da kai"
A nan " ƙaho"
A nan kalman nana "zuciya" na wakiltar dukan mutum na jajjada sadarin kasancewar mutum. Ma'ana mai yiwuwa na waɗanda suka yi kuka1) Mutanen Yerusalem. AT: "Mutanen Yerusalem sunyi ihu wa Ubangiji daga cikin zurfin zuciyarsu" ko 2) "an suffanta katangar da mutum" AT: "Ku katangu, kuyi kuka ga Ubangiji daga cikin zurfin zuciyarku"
Wannan na maganar nmutane masu kuka sosai har hawayensu sun zuba kamar kogi. AT: "kuka sosai, hawaye da yawa"
Wadannan akasin biyu na lokacin rana na nufin dukan lokaci. AT: "a kowanne lokaci"
Kalman nan "kowanne" a nan ƙarin magana ne na "mai yawa." AT: "inda titin suka haɗu" ko "a gefen titi"
Wannan tambaya ce da ake yi don jajjada cewa ba daidai bane mata su ci yaran su. Za'a iya rubuta wannan kamar bayani. AT: "kada mata su cinye 'ya'yan cikinsu ... don"
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "Ko ya kamata abokan gaba su yanka firist da annabi"
Ya nufa a nan cewa yana nufin mattattun mutane. AT: "Gawawwakin matasa da tsofaffi duka sun kwanta a turɓaya"
"kamar suna zuwa idi." Wannan na maganar yadda Yahweh ya tara abokan gabansa kamar ya gayyace su zuwa idi.
A nan ana nufin mutanen da marubucin ke fargaban su kamar "tsoron sa" AT: "mahara da na ke tsoron su"
1Ni ne mutumin da yaga wuya a ƙarƙashin sandar fushin Yahweh.2Ya kore ni waje ya kuma sanya ni in yi tafiya cikin duhu a maimakon haske.3Hakika ya juye hannuwansa gãba da ni ba sau ɗaya ba, ba sau biyu ba a dukkan rana.4Ya maida naman jikina da fatar jikina banza; ya karya kassusuwana.5Ya kewaye ni kamar birnin da aka kawo masa hari, ya kuma kewaye ni da baƙinciki da matsananciyar wahala.6Yasa na zauna a wurare masu duhu, kamar waɗanda suka mutu da daɗewa.7Ya gina garu kewaye da ni kuma ba zan iya kuɓuta ba. Yasa sarƙoƙina sun nawaita8kuma ko da na yi kiran neman taimako, sai ya ƙi jin addu'ata9Ya tare hanyata da garun sassaƙaƙƙun duwatsu; ya maida hanyoyina karkatattu.10Ya yi kamar damisa da ke mani kwanto, Zaki na boyewa;11ya bauɗar da hanyoyina, ya yashe ni.12Ya ja bakansa ya sa na zama abin da kibiyarsa zata harba.13Ya soke ƙodojina da kiɓiyoyin kwarinsa.14Na zama abin dariya ga dukkan mutane, wani abin yi wa zambo a dukkan yini.15Ya cika ni da ɓacin rai ya kuma tilasta ni sha ruwan ɗaci.16Ya haƙorana niƙa da tsakuwa; ya tura ni ƙasa cikin ƙura.17An raba raina da salama; Na mance da mene ne ma farinciki.18Saboda haka na ce, "jimirina ya ƙare haka kuma begena ga Yahweh"19Tuna da azabata da yawace-yawacena, ɗacin rai da baƙinciki.20Ina ci gaba da tunawa da ita ina kuma russunawa ƙasa a cikin rai na.21Amma ina nazarin wannan a zuciyata saboda haka ina da bege:22Kaunar Yahweh madawwamiya ba ta ƙarewa kuma tausayinsa baya zuwa ga ƙarshe,23suna sabuntuwa kowacce safiya; amincinka mai girma ne.24"Yahweh ne gãdona". Na ce, saboda haka zan yi bege a cikinsa.25Yahweh managarci ne ga waɗanda ke jiransa, kuma ga mai nemansa.26Ya yi kyau a yi shiru a jira ceton Yahweh.27Abu nagari ne mutum ya jure karkiya a cikin ƙuruciyarsa.28Bari ya zauna shiru shi kaɗai sa'ad da aka ɗora masa shi.29Bari ya sa bakinsa a ƙura - mai yiwuwa akwai bege.30Bari ya ba da kuncinsa ga mai marinsa, kuma bari ya cika da abin kunya.31Gama Ubangiji ba zai ƙi mu har abada ba,32Amma koda ya ke ya jawo ɓacin zuciya, zai ji tausayinmu bisa ga yawan kaunarsa marar ƙarewa,33Gama ba ya ƙuntatawa daga zuciyarsa, ko cakuna ga 'yan adam.34Domin a rugurguza a karkashin kafafunsa dukkan ɗaurarrun duniya,35a hana yiwa mutum adalci a gaban maɗaukaki,36a hana adalci ga mutum - Ubangiji ba zai amince da abubuwa haka ba.37Wa ya yi magana kuma ta cika, idan ba Ubangiji ya umarta ta ba?38Ba daga bakin Maɗaukaki ne masifu da nagargarun abubuwa ke fitowa ba?39Ta yaya wani rayayye zai yi gunaguni? Ta yaya mutum zai yi gunaguni game da hukuncin zunubansa?40Bari mu auna hanyoyinmu mu gwada su, mu kuma juyo ga Yahweh.41Bari mu daga zukatanmu da hannuwanmu ga Allah a sammai.42"Mun yi laifofi da tayarwa, kuma baka gafarta ba.43Ka rufe kanka da fushi ka kuma kore mu, ka kashe kuma ba ka keɓe mu ba.44Ka rufe kanka da giza-gizai yadda babu addu'ar da zata wuce ciki.45Ka maishe mu kamar ƙazantaccen juji na wofi a cikin al'ummai.46Dukkan maƙiyanmu sun la'anta mu,47fargaba da tsoro da lalacewa da hallaka sun auko mana.48Idanuwana na fitar da maɓulɓulan hawaye saboda mutanena da aka hallaka.49Idanuwana za su zubar da hawaye marar ƙarewa; babu tsayawa,50har sai ya dubo ƙasa kuma Yahweh zai duba daga sama.51Idanuwana sun sa ni matsananciyar wahala saboda dukkan 'yan matan birnina.52Maƙiyana na farauta ta kamar waɗanda ke kamun tuntsu; suna ta farauta ta ba dalili.53Sun jefa ni cikin rami suka kuma jefe ni da dutse,54har ruwa ya zuba a bisa kaina. Na ce, "An datse ni!'55Yahweh, na kira sunanka daga rami mai zurfi.56Ka ji muryata sa'ad da na ce, 'Kada ka rufe kunnuwanka ga kukana na neman taimako.'57Ka zo kusa a ranar da na kira ka; ka ce, 'kada kaji tsoro.'58Ubangiji, ka yi mani kariya, ka cece ni!59Yahweh, ka ga abu marar kyau da aka yi mani; ka zama alƙalina.60Ka ga zagi da ƙulle-ƙullen da suke yi mani.61Ka ji reninsu, Yahweh, da dukkan shirin da suke yi a kai na.62Leɓunan waɗanda suke yi mani tayarwa, da zarginsu sun zo gãba da ni dukkan rana.63Duba yadda suke zama da tashi; suna yi mani ba'a da waƙoƙinsu.64Yahweh, ka rama mani bisa ga abin da suka yi.65Za ka bar zukatansu a rashin kunya! Da ma hukuncinka ya auka masu!66Ka rarakesu a cikin fushinka ka hallaka su daga ƙarƙashin sammai, Yahweh!"
Fara wani sabon waka. A nan marubucin na magana a kan wahalar da mutanensa suka sha. Yana magana game da su kamar Allah ya kai masa hari shi ƙadai. Ko da shike, marubucin ya so yayi magan domin kowa a birnin.
Zama "a ƙarƙashin sandar" na wakiltar cin duka da sanda. Marubucin yayi maganar hukuncin Allah kamar Allah ya duke shi da sanda. AT: "saboda Yahweh yaji haushi sosai kuma ya duke ni da sanda" ko "saboda Yahweh ya ji haushi sosai kuma ya hukunta ni sosai"
A nan "duhu"na wakiltar wahala. AT: "ya sa na wahala sosai ba tare da bege ba, kamar mutum mai tafiya a cikin duhu maimakon haske"
A nan "ya juya hannunsa a kai na"na wakiltar kai masa hari. Marubucin na maganar Allah na sa abubuwa marasa kyau su faru da shi kamar Allah ya kai masa hari. AT: "ya kai masa hari" ko "ya sa abubuwa marasa kyau da yawa su faru da ni, kamar wanda ya kai ma wani hari"
A nan "bakin ciki"na wakiltar wahala.
Wannan na wakiltar Allah ya sa shi ya sha baƙin ciki sosai da wahala. AT: "ya sa na sha baƙin ciki da wahala" ko "ya sa na sha wahala da samun matsaloli da yawa"
Marubucin yayi magana game da Allah yana ƙin ya saurari addu'oin shi kamar Allah na kulle kunnuwansa domin kada addu'oin marubucin su shiga cikinsu. AT: "ya ƙi jin addu'ata"
Marubucin na maganar Allah na sa shi ya ci gaba da shan wahala kamar Allah na hana shi daga kuɓucewa daga shan wahalar ta wurin tare hanyar sa. AT: "kamar ya tare ne daga hanya ta"
"katangar da aka yi da sassaƙƙun duwatsu." Mutane za su sassaƙa duwatsu a siffofin na yau da kullum da suke daidai domin a gina katanga mai ƙarfi.
Ma'ana mai yiwuwa sune 1) "ya ja ni daga kan hanya" ko 2) "ya sa hanyata ta juyo a ta hanya da ba dai-dai ba"
Ana magana a kan Allah kamar shi mayaƙi ne.
Marubucin na magana a kan zurfin baƙin cikin da ya ji kamar Allah ya harbi ƙodajinsa da baka AT: Bakin ciki na na da girma. Ya na kamar ya soke ƙodojina da bakokin kwarinsa"
Ƙodoji jijiyoyin ciki ne da ke ciyar da fitsari a cikin mafitsara. Su magana ne mai nuna yadda mutum ke ji. AT: "da zurfi a cikin jikina" ko "zuciyata"
A nan "baƙin ciki"na wakiltar wahala. Ana maganr shi kamar abu ne da zai iya cika mai magana. AT: "Ya sa na sha wahala sosai"
Marubucin na maganar Allah na wulaƙanta shi kamar Allah ya tura shi zuwa cikin tokar wuta a ƙasa.
Ma'ana mai yiwuwa 1) Goguwa marubucin basu da salama. AT: "Ba ni da salama a raina" ko 2) "marubucin bai ji salama ba" AT: "Bana jin salama a raina"
Wasu shafuna na juya wannan kamar "daukaka" ko "adonsa."
Madaci itace ne da ruwansa ke da daci a sha. A tare da "madaci" da "baƙin ciki" na wakiltar wahala sosai.
Marubucin na magana a kan zurfin rashin jin dadinsa da fid da zuciya kamar sun rusuna. AT: "Ina da baƙin ciki" ko "na karaya"
"na yi bege"
Ana iya bayyana maganana nan "kaunar mara iyaka" da "ƙauna da aminci." AT: "Yahweh ba ya daina ƙaunar mutanensa da aminci"
Kalman nan "ka" na nufin Yahweh.
A lokacin da Allah ya ba wa kowanne ƙabilar Israila ƙasar su, ya kira shi gado. Marubucin na maganar Yahweh ya zama dukan buƙatunsu kamar Yahweh ne gadon da ya karba. AT: "Domin Yahweh yana tare da ni, ina da duk abin da nake buƙata"
A nan "kyau" na nufin alheri. AT: Yahweh na da alheri wa waɗanda da ke jiransa" ko "Yahweh na yin abubuwa masu kyau ga waɗanda ke jiransa"
"a lokacin da aka ɗora masa ƙarƙiya." A nan ƙarƙiya na wakiltar wahala. AT: "a lokacin da ya sha wahala"
Sanya bakinsa a cikin ƙura na wakiltar russunawa ƙasa tare da fuskar shi a ƙasa. AT: "Bari ya kwanta tare da bakinsa a ƙura"
kalman nan "shi" na nufin duk wanda ke wahala kuma ya jira Yahweh. A nan "bada kuncin sa" na wakiltar barin wani bugi kuncin sa. AT: "Bari ya bar mutane du duke shi a fuska"
"koda shike Ubangiji ya sa mutane su wahala" ko "koda shike ya raunana mutane"
Wannan na nufin mutane gabaki ɗaya. AT: "'yan adam" ko "mutane"
"Idan mutane sun murƙushe ... idan sun hana mutum adalci ... idan sun hana adalci"
A nan "ƙarƙashin ƙafafu" na wakiltar cin mutunci da kuma musgunawa mutane. AT: "a ci mutunci" ko "a musguna"
Za'a iya bayyana wannan a sarari da cewa wannan na nufin bada umurni wani abu ya faru. AT: "ya bada umurni cewa wani abu ya faru"
AT: "Allah ya zartas da masifa ko nasara ga kowane mutun.
A nan "baki" na wakiltar abinda Allah ya ce ko ya umurta. AT: "daga umurnin mafi girma na sama" ko "saboda mai girma na sama" ko "domin mai girma na sama ya bada umurnin"
A nan "ɗaga zukatanmu sama" na wakiltar yin addu'a da gaskiya. Al'ada ce ga Ba'isra'ile su daga hannayensu lokacin yin addu'a ga Allah. AT: "Bari mu yi addu'a da gaskiya tare da ɗaga hannuwanmu" ko "Bari mu ɗaga hannayenmu sama kuma mu yi adu'a da gaskiya.
Kalmar nan "laifofi" da "tawaye" na da ma'ana ɗaya. Tare suna cewa zalumci dai-dai yake da tayarwa ga Yahweh.
A nan ana magana akan fushi kamar dai wata sutura ce da Allah ya dora. Ibraniyawa sau da yawa su kan yi magana game da motsin zuciya kamar dai sutura ne. AT: "Ka ta yin fushi"
Wannan na wakiltar cewa Allah na ƙin sauraron addu'ar mutane. AT: "Ka ƙika saurari addu'oin mu. yana kamar ka sa girgije tsakanin mu a matsayin garkuwa don kiyaye addu'ainmu"
Wannan na nufin faɗiwa a cikin rami. A nan yana wakiltar cewa an yi masa tarko ta kowanne hanya.
"ya faru da mu"
Waɗannan kalmomin biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna nufin yadda da aka lalata Yerusalem. AT: "hallaka wa ga baki ɗaya"
A nan marubucin na maganar babban yawa hawayen kamar maɓulɓula ne. AT: "Hawaye suna kwarara daga idanuna kamar yadda ruwa na kwararowa cikin kogi"
Za'a iya fadin wannan a aikace. AT: "domin maƙiya sun hallaka mutane na"
Wannan kalman "Idanu na"na wakiltar abinda ya gani. AT: "Abin da na ke gani yana sa ni baƙin ciki"
Ma'ana mai yiwuwa sune 1) matan Yerusalem ko 2) dukkan mazaunan Yerusalem.
"Sun jefa ni a cikin rami" ko "Sun sanya ni a rijiya"
Ma'anar mai yiwuwa sune 1) "sun jefe ni da duwatsu" ko 2) "sun rufe rijiyar da dutse"
Sunan Allah na wakiltar halin sa, kuma a nan, "kiran sunan ka"na wakiltar dogara ga halin Allah da kiran shi domin taimako. AT: "Na kira ka don neman taimako"
A nan "murya" na wakiltar abinda ya ce. AT: "Ka ji abin da na ce"
A nan "kulle kunnen ka"na wakiltar ƙin sauraro. AT: "Kada ka ƙi sauraro"
Marubucin yana magana cewa Allah ya hana maƙiyansa daga kashe shi kamar Allah yayi jayayya dominsa kamar yadda lauya kan yi jayayya ga wanda yake kare shi, kuma ya kare shi daga mutuwa. AT: "ka cece ni daga maƙiya na" ko "kamar kayi jayayya a kaina a kotu"
Za'a iya bayyana waɗannnan jumlolin guda biyu "zage-zage" da "ƙulle-ƙulle" kamar fi'ili. AT: "Ka ga yadda suka zage ne kuma suka yi ƙulle-ƙulle a kai na sau da yawa"
Za'a iya bayyan kalman nan "wulakanci" tare da fi'ilin nan "ba'a" ko "izgili." Za'a iya fadin wannan a a sarari cewa shirye-shiryen su na cutar da shi ne. AT: "ka ji yadda suke mani ba'a ... kuma dukan abubuwan da suka shirya suyi mani" ko "ka ji izgilin da suka yi mani ... kuma suka shirya hanyoyin da za su cutar da ni"
Marubucin na maganan abokan gaban suna zargin shi dukan rana kamar zargin su sojoji ne da ke zuwa su kai masa hari dukan rana. AT: "Maganar da abokan gaba na suke faɗa kuma suka zarge a cikin dukan ranan"
A nan leɓunan na wakiltar abinda abokan gaba shi suka ce. AT: "kalmomin ... abokan gaba na"
Waɗannan matakai biyu na wakiltar dukan abin da mutane ke yi. AT: "dukan abin da suke yi"
Za'a iya bayyana kalman nan "la'ana" tare da fi'ili nan "la'anta" ko "la'ana." AT: "hukunta su" ko "la'anta su"
A nan "daga ƙarƙashin sammai"na wakiltar ko'ina a duniya. AT: "a duk inda suke a duniya"
1Zinariyar ta zama gurbatacciya; tatacciyar zinariyar ta sake kamanni! An watsar da tsarkakakkun duwatsu a kwanar kowanne titi.2'Yan mazan Sihiyona masu daraja sun cancanci nauyin tacacciyar zinariya, amma yanzu ba suma cancanci tulunan yumɓu ba, aikin hannuwan maginin tukwane!3Har ma diloli kan iya ba 'ya'yansu nono amma ɗiyar mutanena ta zama mai mummunan hali irin na garken jiminai da ke hamada.4Harshen jariri saboda ƙishin ruwa ya liƙe a dasashinsa; yaran na neman abinci amma babu kome dominsu.5Waɗanda suka saba da idin abinci mai tsada sun gamu da yunwa a tituna; waɗanda aka san su da sa kyawawun kaya, yanzu suna kwance a juji wofi.6Hukuncin ɗiyar mutanena ya fi na Sodom, wadda aka kawar da ita a ɗan lokaci kaɗan kuma babu wanda ya tada hannu na taimakonta7Shugabaninta sun ɗara dusar ƙanƙara rashin aibi, sun kuma fi madara fari; jikunansu sun fi murjani kyau, fasalinsu kamar shudin saffiya.8Yanzu kammaninsu yafi kunkunniya baƙi. Ba sa ganuwa a tituna. Fatarsu ta liƙe a kasusuwansu; ta zama busasshiya kamar katako.9Waɗanda aka kashe su da takobi suna da farinciki fiye da waɗanda aka kashe da yunwa, wanɗanda su ne suka zama lalatattun da aka sokesu da rashin wani girbi daga gona.10Hannuwan mata masu tausayi sun dafa 'ya'yansu; suka zamar masu abinci a lokacin da ake hallakar da ɗiyar mutanena.11Yahweh ya nuna dukkan fushinsa; ya zubo zafin fushinsa. Ya kunna wuta a Sihiyona da ta cinye tushenta.12Sarakunan duniya, ba su amince ba, da haka ma dukkan mazaunann duniya ba su amince ba cewa maƙiyan ko masu adawa za su iya shiga ƙofofin Yerusalem.13Wannan ya faru ne saboda zunuban annabawanta da laifofin firistocinta waɗanda suka zubar da jinin adalai a cikinta.14Sun yi ta gararamba cikin makanta a tituna. Sun zama ƙazantattu sosai ta wurin jini da babu wanda aka yarda ya taba tufafinsu.15"Fita! Marar tsabta!" mutane na ta ihun kiransu. "Fita! Fita! Kar ku taɓa!" Haka suke gararamba; mutane faɗi a cikin al'ummai, "Ba za su ƙara zama a nan kuma ba."16Yahweh da kansa ya watsar da su; bai sake kula da su kuma ba. Ba su girmama firistoci ba, kuma ba su nuna wani alheri ga dattawa ba.17Idanuwanmu sun gaji da neman taimako a banza; daga wurin duban maƙiyanmu mun dubi al'ummar da ba za ta iya kuɓutar da mu ba.18Suka bi duk inda muka nufa, bamu iya tafiya a titunanmu ba. Ƙarshenmu ya kusato kuma an lisafta kwanakinmu, ƙarshenmu ya zo.19Masu fafarar mu sun fi gaggafan sararin sama sauri. Suna korar mu zuwa duwatsu kuma suna yi mana kwanton ɓauna a cikin jeji.20Numfashin hancinmu - keɓaɓɓu na Yahweh - shi ne wanda aka cafko a ramukansu; wanda aka ce game da shi, "a ƙarkashin inuwarsa ne za mu zauna cikin al'ummai."21Ki yi farinciki da murna, ɗiyar Idom, ke da kike zaune a ƙasar Uz. Amma a gare ki kuma za a fara shan ƙoƙon; za ki bugu har sai kin tuɓe kanki tsirara.22Ɗiyar Sihiyona, hukuncinki zai kawo ga ƙarshe, ba zai ƙara kwanakin bautarki ba. Amma zai hukunta ɗiyar Idom, zai hukunta; zai buɗe zunubanki
Fara sabuwar waka. .
Wannan zai iya nufin an rushe haikalin kuma an watsar da duwatsun a dukan birnin. Zai kuma iya nufin cewa an watsar da mutane ne.
"a duk inda tituna suka haɗu" ko "ta dukkan hanyoyi"
Anan an yi maganar mutanen birnin kamar 'yan mazan birnin ne. Ma'ana mai yiwuwa sune 1) wannan na nufin matasan Yerusalem kaɗai ko 2) wannan na nufin dukkan mutanen Yerusalem.
Marubucin na maganar yaran Sihiyona masu daraja kamar an maishe su tulunan yumɓu marasa tsada. AT: "mutane suna ɗaukar su marasa anfani kamar tukunyar yumɓu waɗanda maginan tukwane suka gina."
karen daji mai tsanani
An kwatanta mutanen Yerusalem da jiminai domin suna wa yaransu mugunta.
manyan tsuntsaye da ke watsi da wau kwayayensu
Waɗannan mutanen kuma basu da gidaje, don haka suna zama a waje a bakin tituna
Saka tufafin mulufi alama ce da ke nuna cewa mutun mai arziki ne.
Wannan wata suna ce ta Yerusalem, wanda ake magana a nan kamar mace ce. Dubi yadda zaka juya wannan a Makoki 2:11. AT: "mutane na"
kalman nan "wadda" na nufin Saduma. Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "wadda Allah ya hallakar a ɗan lokaci kaɗan"
Zaá iya fadin wannan a aikace. AT: "babu wanda ya tada hannu na taimakonta"
Ma'ana mai yiwuwa 1) Shugabannin Yerusalem na da kyaun gani domin suna da lafiyar jiki ko 2) shugabannin na da halin tsarki kamar yadda sabon garin ƙanƙara da madara suke kamar fari fat
"Shugabanin Yerusalem"
launin dutse mai karfi da ya fito daga teku wanda ake anfani dashi kamar kayan ado
dutse mai tsada da ake amfani da shi a cikin kayan ado
Wannan na iya zama domin 1) rana ta duhunta fatar shugabanin ko 2) toka daga wutar da ta ƙone Yerusalem ta rufe fuskokinsu.
Busasshen fatar su na kwantancin busasshen katago.
A nan "katako" na wakiltar harin abokin gaba. Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "Waɗanda sojoji abokan gaba suka kashe"
A nan "yunwa"na wakiltar jin yunwa sosai. Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "waɗanda aka yunwa ta kashe"
"waɗanda suka zama sirara kuma raunana"
A nan "girbi daga gona" na wakiltar abincin ci. Ana maganar rashin abinci a nan kamar takobi ne da ke sukar mutane. Maganar karamcin abinci anan kamar takobi. AT: "wanda yunwa ta kashe"
Yahweh ya yi fushi, ya aikata duk abin da ya ga dama domin ya nuna fushin sa.
Ana maganar hukuncin Allah wa mutanensa kamar fushinsa na ƙone ruwa mai zafi da yake zuba ma su. AT: "domin zafin fushinsa, ya hukunta mutanensa" ko "a zafin fushi ya amsa wa mutanensa"
Wannan na iya nufin fushin Allah kamar wuta ne wanda ya hallaka Yerusalem. AT: "Allah ya sa maƙiya su kona Yerusalem da wuta"
"Sarakunana duniya da sauran mazaunan duniya basu amince ba"
Waɗannan kalmomin biyu na nufin abu daya ne kuma suna nanata cewa waɗanan mutane ne masu son cutar da Yerusalem. AT: "kowane irin abokan gaba"
Waɗannan layukan guda biyu suna da ma'ana iri ɗaya kuma suna daɗaɗawa cewa waɗannan shugabannin ruhaniya suna da alhakin faduwar Yerusalem. AT: "mumunan zunuban annabawanta da laifofin firistocinta"
Firistoci da annabawa sun yi kisan kai. A nan "zubar da jini"na wakiltar kisa. AT: "waɗanda su ka kashe masu adalci"
A nan "ƙazantu" na wakiltar rashin karɓuwa a wurin Allah. Domin firistoci da annabawa sun yi kishe mutane, sun kazamtu bisa ga al'ada, ba za su bauta wa Allah ba ko su kassance a cikin sauran mutane ba.
"Tafi daga nan! Tafi daga nan! Kada ka taɓa mu"
"watsar da annabawa da firistoci"
A nan "kula da mu"na wakiltar damuwa game da su kuma yana taimakon su. AT: "ba ya kula da su ba kuma"
Idanuwansu sun gaji na wakiltar neman su da kuma da rashin samun abinda suke nema. Wadannan magannganu biyu gaba ɗaya na jajjada cewa suna ƙoƙari sosai don ya samu taimako. AT: "Mun ci gaba da nema, amma ba mu sami ko wani mutum da zai taimake su ba"
A nan "matakin mu" na wakiltar inda suka je. AT: "Abokan gaban mu sun bi mu duk inda muka je"
A nan "kusa" wani kalma ne mai nufin "jim kaɗan" AT: "ƙarshenmu zai zo jim kaɗan" ko "Abokan gabanmu za su hallaka mu jim kaɗan"
Marubucin na kwatanta saurin masu bin su da saurin gaggafa mai tashi. gaggafai na tashi da sauri su don su kama wasu dabbobi. AT: "Waɗanda suke bin mu suna da sauri fiye da gaggafai"
Wannan magana ce mai nufin sarki. Ana maganar shi ne kamar numfashi; numfashi ke ajiye jiki da rai, kuma sarki na ajiye mutanensa da rai ta wurin mulkinsu da kyauda kare su daga abokan gaba. AT: "Wanda yake kamar numfashi a hancin mu" ko "Wanda yake kare rayukan mu"
"Yin farin ciki da yin murna na nufin abu ɗaya ne kuma na jajjada tsananin murnan. Marubucin yayi amfani da waɗannan kalmomin don ya zolaye mutanen. Ya sani cewa mutanen Idom zasu yi murna cewa Yerusalem ta hallaka. AT: "yi murna sosai"
Ana maganar mutanen ƙasar Idom kamar su mata ne. Su abokan gaban Isra'ila ne.
Kofin magana ce don ruwan inabin da ke a ciki. Ruwan inabin wata magana ce wa hukunci. AT: "Yahweh kuma zai hukunta ku"
"Yahweh ba zai sa lokacin ku a bauta yayi tsawo ba" ko "Yahweh ba zai sa ku zauna a bauta da daɗewa ba"
1Tuna, Yahweh, da abin da ya same mu. Ka duba ka ga abin ban kunyarmu.2Gãdonmu an bayar ga bãƙi, gidajenmu ga bãƙi.3Mun zama marayu, marasa ubanni, kuma waɗanda uwayensu sun zama kamar gwauraye.4Dole mu biya zinariya don ruwan shanmu, kuma dole mu biya zinariya kafin mu samu abincinmu.5Waɗanda suke rarakarmu sun matso kusa da mu. mun gaji kuma ba mu samu hutu ba.6Mun ba da kanmu ga Masar da Asiriya don mu samu isasshen abinci.7Ubanninmu sun yi zunubi, kuma yanzu basu nan, kuma muna ɗaukar alhakin laifofinsu.8Bãyi suna mulki a kanmu, kuma babu wanda zai kuɓutar da mu daga hannunsu.9Muna samun abincinmu ta sadaukar da ranmu ne kawai, saboda takobin cikin jeji.10Zafin fatarmu kamar zafin tanderu don tsananin yunwa.11Ana yi wa mata fyaɗe a Sihiyona, har da 'yan mata ma a biranen Yahuda.12'Ya'yan sarakuna na rataya kansu da hannuwansu, kuma ba a nuna girmamawa ga dattawa.13An sa samari su yi niƙan hatsi dole da dutsen niƙa, samari kuma suna jiri da kayan itace masu nauyi.14Dattawa sun bar kofar birnin kuma samarin sun bar raira waƙoƙinsu.15Farincikinmu ya ƙare kuma rawarmu ta koma makoki.16Rawani ya faɗo ƙasa daga kanmu; kaiton mu, don mun yi zunubi!17Domin wannan, zuciyarmu ta kamu da ciwo, kuma idanuwanmu sun dushe, saboda wannan idanuwanmu sun rage ƙarfi.18gama Tsaunin Sihiyona ya zama ƙango, diloli ke yawo a kansa.19Amma kai, Yahweh, mulkinka har abada ne, kuma za ka zauna a kan kursiyinka daga tsara zuwa tsara.20Meyasa ka mance da mu har abada? Meyasa ka bar mu har tsawon kwanaki da yawa?21Ka komo da mu zuwa gare ka ya Yahweh, kuma zamu komo. ka sabunta kwanakinmu kamar yadda suke a dã -22har sai in ka ƙi mu ɗungum kuma ka yi fushi da mu fiye da misali.
Raira sabuwar waka.
"Tuna" a nan karin magana ne. AT: "Yahweh, yi tunani game da abinda ya farui da mu"
"kalli halin kunyar da muke ciki"
Mutanen Yerusalem basu da wanda zai kare su, domin ko mazajensu sun mutu a yaƙi ko kuma sun tafi bauta. Wannan na magana a kan cewa mutane basu da baba da masu gida kamar sun zama marayu da gwamraye ko.
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "Maƙiyanmu suna sayar mana da itacen da ya kassance namu"
"Abokan gabanmu da ke bin mu." Wannan na nufin sojojin Babila.
Wannan na nufin sun mutu. AT: "sun rigaya sun mutu"
A nan "laifofinsu" na wakiltar hukuncin da da suka karɓa saboda zunuban kakanninsu. AT: "Mun ɗauki hukuncin domin zunuban su"
Ma'ana yiwuwa su ne 1) "Yanzu mutane da suke mulkinmu sun zama bayin kansu ga majiɓitan ubangijin su a Babila" ko 2) "Mutane da suke bauta a Babila yanzu sun malleke mu"
A nan kalmar nan "hannu" na nufin iko. AT: "Ya kubutar da mu daga ikonsu"
A nan ana wakiltar mafasa da takobi ta wurin "takobinsu" AT: "saboda akwai mutane a cikin jeji waɗanda suke kashe waɗansu da takobi"
Waɗannan maganganun biyu na da ma'ana kusa ɗaya kuma domin jajjada cewa ana cin mutuncin mata. Ana gane lalmomin nan "fyaɗe su" a sashin wannan maganar na biyu kuma za'a iya sake maimaitawa. AT: "Ana fyaɗen matan Sihiyona, kuma ana fyaɗen budurwan Yerusalem a cikin biranen Yahuda"
Ma'ana mai yiwuwa sune 1) kalman nan "su" na nufin abokan gabansu. AT: da hannuwansu , sun rataye yarimai ko 2) sun ɗaura yarimai tare da gefen igiya ɗaya da kuma ɗayan gefen don kada tafin ƙafafuwan yarimai su taɓa ƙasa ba.
Za'a iya faɗin wannan a aikace. AT: "Sun tilastawa matasa maza"
Inda dattawa ke zama su bada shawara na doka, amma kuma wuri ne da mutane ke haɗuwa domin shaƙatawa.
A nan kalman nan "zuciya" na nufin dukan mutum kuma na jajjada yadda yake ji. AT: "farin cikin mu"
Ma'ana mai yiwuwa sune 1) "Bamu sake saka furanni a kawunanmu domin bukukuwa" ko 2) "Rawani" na wakiltar sarkinsu kuma 'kai' wurin ikon a mutane. Na wakiltar "bamu da sarki"
Wannan na nufin suna samunsa da wuya su gani domin suna kuka. AT: "kuma ba mu iya gani da sauƙi saboda idanuwanmu na cike da hawaye"
Waɗannan mugayen karnukan daji ne. Duba yadda zaku juya wannan a Makoki 4:3.
A nan zama a kursiyi na wakiltar mulkin sarki. AT: "mulkin a matsayin sarki"
Wannan karin magana ne. AT: "koyaushe"
Marubucin na amfani da wannan tambayar don ya bayyana yadda yake ji cewa yahweh ya manta da su. AT: "Kamar dai zaka manta da mu har abada ne ko kuma ba za ka iya zuwa wurin mu har na tsawon lokaci ba!"
A nan "ranaku"na wakiltar rayukansu. AT: "kyautata rayuwar mu, kamar suke a dã" ko "ka sanya mu zama da girma kamar yadda muke a dã"
Ma'ana mai yiwuwa sune 1) marubucin na cike da tsoron cewa Yahweh yayi fushi sosai kuma bashi da niyar maido da su ko 2) yana cewa, Yahweh yayi fushi da da ba zai maido da su ba.
1A cikin shekara ta talatin, a wata na huɗu, rana ta biyar ga wata, ya kasance kuwa ina zaune cikin 'yan bauta a bakin Kogin Keba. Sai sammai suka buɗe, kuma Na ga wahayoyin Allah.2A rana ta biyar a wannan watan - shekara ta biyar kenan ta mijirar sarki Yehoyacin.3Maganar Yahweh ta zo ga Ezekiyel ɗan Buzi firist, a cikin ƙasar Kaldiyawa a hanyar Kogin Keba, hannun Yahweh kuma yana kansa a wurin.4Daga nan sai na duba, sai ga iskar hadari na tasowa daga arewa; babban girgije mai wuta na haskakawa kewaye da shi da kuma a cikinsa, haske na kewaye da shi da cikinsa, kuma wutar tana da launin rawaya cikin girgijen.5Daga cikin tsakiyarsa siffar waɗansu masu rai huɗu. Wannan shi ne bayyanuwar su: suna da kamannin mutum,6amma kowannensu yana da fuskoki huɗu, kowacce halittar kuma nada fikafikai huɗu.7Ƙafafunsu a miƙe suke, amma tafin sawayensu kamar kofaton ɗan maraƙi yana sheƙi kamar gogaggiyar tagulla.8Duk da haka suna da hannayen mutane a ƙarƙashin kowanne sashi huɗu na fukafukansu, dukkan su huɗun, fuskokinsu da fukafukansu haka suke:9fukafukansu na taɓa fukafukan ɗaya halittar, a cikin tafiyarsu ba su juyawa; maimakon haka, kowannensu a miƙe yake ɗoɗar.10Kamannin fuskokinsu na kama da fuskar mutum. Su huɗun suna da fuskar zaki a sashin dama, su huɗun suna da fuskar bijimin sã sashin hagu. Su huɗun kuma suna da fuskar gaggafa.11Fukafukansu haka suke, fukafukansu kuma a shimfiɗe suke a sama, domin kowacce halitta nada fiffike biyu da ke taɓa fiffiken halittar, kuma fukafukan biyu sun rufe jikkunansu.12Kowanne ɗayansu ya tafi ɗoɗar, domin duk inda ruhu ya jagorance su suje, suna tafiya ba tare da sun juya ba.13Game da kamannin rayayyun halittun nan kuwa, bayyanuwarsu na kama da garwashin wuta mai ci, kamar bayyanar cociloli; hasken wuta kuma na kai da komowa tsakanin halittun, kuma akwai haskawar walƙiya.14Rayayyun halittun nan suna matsawa da sauri gaba da baya, bayyanarsu kuma kamar walƙiya take!15Daga nan sai na dubi rayayyun halittun nan, sai ga wani gargare a ƙasa a gefen rayayyun halittun tare da fuskokinsu huɗu.16Wannan shi ne bayyanuwa da tsarin gargarorin; kowanne gargare na kama da dutse mai tamani, dukkan su huɗun kamannin su ɗaya ne; bayyanuwarsu da ƙirarsu sai ka ce gargare mai ratsawa ta wani gargaren.17Yayin da suke matsawa, suna tafiya ta kowanne kusurwarsu huɗu, ba tare da sun juya ba yayin da suke tafiya.18Zancen gammon gargarensu, masu tsawo ne da kuma ban tsoro, domin gammon gargaren na cike da idanu a kewaye.19Duk sa'ad da rayayyun halittan nan suke matsawa, gargarorin na matsawa a gefensu. Sa'ad da rayayyun halittar suka tashi daga duniya, gargarorin suma su kan tashi sama.20Duk inda Ruhu zai tafi, sukan tafi, sai gargarorin su tashi a gefensu, gama ruhun rayayyun halittun yana cikin gargarorin.21Duk sa'ad da halittun suke matsawa, gargarorin suma suna matsawa; idan kuma halittun suka tsaya cik, gargarorin suma sukan tsaya cik; idan halittun suka tashi daga ƙasa, gargarorin sukan tashi a gefensu, saboda ruhun rayayyun halittun yana cikin gargarorin.22A bisa kawunan rayayyun halittun nan akwai kamannin miƙaƙƙen sarari; yana kama da abu mai banmamaki da ƙyalli a miƙe bisa kawunansu sama.23A ƙarƙashin sararin, kowanne fukafukan halittun a miƙe suke sak kowanne yana taɓa fukafukan ɗaya rayayyen halittar. Kowannen rayayyen halittar kuma yana da fiffike biyu domin su rufe kansu; kowanne yana da biyu domin ya rufe jikinsa.24Daga nan sai naji ƙarar fikafikansu. Kamar ƙarar ruwaye masu yawa. Kamar muryar mai Iko dukka a duk sa'ad da suke matsawa. Kamar ƙarar iskar hadari. Kamar ƙarar rundunar sojoji. Duk sa'ad da suka tsaya cik, sukan saukar da fukafukansu.25Sai murya ta zo daga saman sararin sama da kansu duk sa'ad da suka tsaya cik suka kuma sãki fukafukansu.26A bisa sararin nan da ke sama da kansu akwai kamannin kursiyi da ke kama da bayyanuwar dutsen tama, a bisa kamannin kursiyin kuma akwai kamannin da ya yi kama da bayyanuwar mutum.27Na ga siffa da bayyanuwar ƙarfe mai haskakawa da wuta a cikinsa tun daga bayyanuwar kwankwasonsa har sama; naga kuma daga bayyanuwar kwankwasonsa har zuwa ƙasa sai ka ce bayyanuwar wuta da haske ko'ina kewaye.28Kamar bayyanuwar bakangizo cikin giza-gizai a ranar da aka yi ruwa haka bayyanuwarar sheƙin hasken da ke kewaye da shi yake. Wannan kamar bayyanuwarar kamannin ɗaukakar Yahweh ne. Sa'ad da na gani, Na faɗi bisa fuskata, sai na ji murya tana magana.
Wannan ita ce shekara ta talatin ta rayuwar Ezekiyel.
"rana ta biyar ga wata na huɗu." Wannan shi ne wata na huɗu na kalandar Ibraniyanci. Rana ta biyar tana kusa da ƙarshen Yuni a kan kalandar Yamma.
Ana amfani da wannan jimlar a nan don yiwa wani muhimmin al'amari alama a cikin labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
Kalmar "I" tana nufin Ezekiyel. "Na kasance daya daga cikin kamammun"
"Allah ya nuna min abubuwa na ban mamaki
Karin magana "kalmar Yahweh ta zo ga" ana amfani da ita don gabatar da saƙo na musamman daga Allah. AT: "Yahweh ya ba wa Ezekiyel sako"
Wannan kogi ne da mutanen Kaldiya suka haƙa don ba wa lambuna ruwa. "Kogin Keba"
Kalmar "hannu" galibi ana amfani da ita don nuni ga ƙarfi ko aikin wani. Mutum tare da hannunsa akan wani mutum yana da iko akan wannan mutumin. AT: "Yahweh na sarrafa shi"
Ezekiel ya ci gaba da kwatanta wahayinsa.
Ana iya fassara wannan azaman sabon jumla: "Guguwar tana da gajimare mai girma da wuta tana walƙiya a ciki"
Anan sunan mara bayyanan "kamance" yana nufin cewa abin da Ezekiel ya gani yayi kama da waɗannan abubuwa. Ana iya fassara kalmar da kalmar magana. AT: "abin da yayi kama da rayayyun halittu guda huɗu"
Cikakken sunan "bayyanuwa" za a iya fassara shi azaman kalmar magana. AT: "halittun nan huɗu sun yi kama da mutane"
"amma kowanne daga cikinsu yana da fuskoki daban-daban da fikafikansa guda hudu." Kowane taliki yana da fuska a gaba, yana da fuska a bayansa, yana da fuska a kowane gefen kansa.
"amma ƙafafunsu suna kama da kofon maraƙi" ko "amma ƙafafunsu suna kama da na maraƙi"
"sun kasance masu haske kamar tagulla wanda aka goge." Wannan yana bayanin ƙafafun halittu. AT: "kuma suna haske kamar tagulla"
"halittun basu juya ba yayin da suke motsi"
Ezekiyel yana bayanin fuskokin talikan a gefensu na gaba. Cikakken sunan “sura” na nufin abin da Ezekiyel ya gani ya yi kama da fuskar mutum. Ana iya fassara kalmar da kalmar magana. AT: "Fuskar kowace halitta tana kama da fuskar mutum"
"Fuskar da ke gefen dama na kowane mutum ya yi kama da na zaki"
"Fuskar da ke gefen hagu na kan kowannensu ya yi kama da na sa"
"Fuska a bayan kan kowannensu tana kama da fuskar gaggafa"
Ana iya fassara wannan a matsayin sabon jumla: "Sauran fikafikan biyu na kowace halitta sun rufe jikinsa"
"Kowane halitta yana motsi da fuskar sa ido"
Anan sunan mara bayyanan "kamance" yana nufin cewa abin da Ezekiyel ya gani yayi kama da waɗannan abubuwa. Duk “kamannin” da “bayyanar” sunaye ne waɗanda ba za a iya amfani da su ba waɗanda za a iya fassara su azaman kalmomin aiki. AT: "Dangane da yadda halittu masu rai suke, sun yi kama da garwashin wuta"
"walƙiya ta fito daga wuta."
Walƙiya tana walƙiya sannan kuma ta ɓace da sauri, kuma halittun sun tashi daga wannan wuri zuwa wancan da sauri. Cikakken sunan bayyanuwa" za a iya fassara shi azaman aiki. AT: "Rayayyun halittun suna ta sauri da baya, kuma suna kama da walƙiya"
"Wannan shine yadda ƙafafun suke da yadda aka yi su"
"Beril" wani irin dutse ne mai daraja galibi launin rawaya ko launin zinare. AT: "bayyanannu da rawaya kamar dutse lu'ulu'u" ko "mai haske da rawaya kamar dutse mai daraja"
A nan sunan "kamanni" wanda ba a taɓa gani ba yana nuni ga yadda ƙafafun huɗu suke Ana iya fassara kalmar da kalmar magana. AT: "dukkan ƙafafun ƙafafun sun yi kama ɗaya"
Ezekiyel ya ci gaba da kwatanta wahayinsa.
"gefunan sun kasance masu tsayi da ban tsoro" ko "gefunan ɗin da suke da tsayi da ban tsoro"
"saboda gefunan suna da idanu da yawa kewaye da ƙafafun huɗun"
Halittun suna yawo a sama bayan sun bar ƙasa. AT: "Don haka lokacin da halittun suka bar ƙasa suka hau sama"
Kalmar "su" tana nufin halittu.
"gargarorin sun tafi sama tare da rayayyun halittun"
Anan sunan mara bayyanan "kamanni" yana nufin cewa abin da Ezekiyel ya gani yayi kama da "sararin mai fa'ida." Ana iya fassara kalmar da kalmar magana. AT: "abin da ya yi kama da sararin mai fa'ida"
"kuma an fadada dome a saman kawunan halittu" ko "kuma shimfidar dome ta dauki sarari da yawa akan kawunan halittun"
"Kowane talikan yana da fukafukai biyu, wadanda suke rufe jikinsu"
Ezekiyel ya ci gaba da faɗi game da wahayinsa game da rayayyun halittu.
Wannan kawai yana nufin "ruwa mai yawa." Zai iya nufin babban kogi ko babban ambaliyar ruwa ko raƙuman ruwa da ke buguwa a teku. Duk waɗannan suna da ƙarfi sosai.
Littafi Mai Tsarki wani lokaci yakan kira tsawa “muryar Maɗaukaki”. AT: "Ya yi kama da muryar Allah Maɗaukaki" ko "Ya yi kama da tsawar Mai Iko Dukka"
"Wani wanda yake saman sararin yayi magana." Idan kuna buƙatar faɗin muryar waye wannan, mai yiwuwa ya kamata ku gane ta muryar Yahweh ce (Ezekiyel 1: 3).
Anan sunan ɗan 'kamance' na nufin abin da Ezekiyel ya gani yayi kama da kursiyi. Ana iya fassara kalmar da kalmar magana. AT: "wani abu ne wanda yayi kama da kursiyi"
Ana iya fassara sunayen suna "kamanni" da "bayyanar" tare da kalmomin baki. Idan kuna buƙatar gaya ko wanene wannan, tabbas yakamata ku bayyana shi a matsayin Yahweh (Ezekiel 1: 3). AT: "wani abu mai kama da abin da ya bayyana na mutum"
Ezekiyel ya ci gaba da faɗi game da wahayin.
Jikin mutumin da ke saman kwatangwalo yana kama da wani ƙarfe mai haske wanda yake da wuta a ciki. Cikakken sunan "bayyanuwa" za a iya fassara shi azaman aiki. AT: "daga abin da ya zama kamar kwankwasonsa sama"
Cikakken sunan "bayyanuwa" za a iya fassara shi azaman aiki. AT: "duk kewaye da shi a kasa abin da ya zama kamar kwankwasonsa, na ga abin kamar wuta da haske mai haske"
1Ya ce mani, "Dan mutum, tashi bisa sawayenka; daga nan zan yi magana da kai."2Daga nan, da ya yi magana da ni, sai Ruhu ya shiga cikina, yasa na tsaya bisa sawayena, na kuma ji shi yana magana da ni.3Ya ce mani, "Dan mutum, ina aiken ka zuwa wurin mutanen Isra'ila, ga al'ummai masu tayarwa, da suka tayar mani. - da su da kakanninsu sun yi mani zunubi har ya zuwa yau!4Zuriyarsu masu tsaurin fuskoki ne zukatansu kuma kangararru ne. Ina aiken ka wurinsu, kuma za ka ce masu, 'Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya ce.'5Ko su saurara ko kada su saurara. Gama su gida ne mai tayarwa, amma a ƙalla za su sani cewa akwai annabi a tsakiyarsu.6Kai, ɗan mutum, kada ka ji tsoron su ko maganganunsu. Kada ka ji tsoro, koda yake kana tare da sarƙaƙƙiya da ƙayayuwa koda yake kuma kana zaune da kunamai. Kada ka ji tsoron maganganunsu ko ka damu da irin fuskokinsu, da shike su gida ne mai tayarwa.7Amma za ka faɗi maganganuna a gare su, ko su ji ko kada su ji, gama suna cika da tayarwa.8Amma kai, ɗan mutum, ka saurari abin da nake faɗa maka. Kada kayi tayarwa kamar wannan gidan mai tayarwa. Ka buɗe bakinka kaci abin da Na ke shirin ba ka!"9Daga nan Na duba, sai a ka miƙo mani hannu; cikin sa rubutaccen littafi ne naɗaɗɗe.10Ya baza shi a gaba na; yana da rubutu cikinsa da bayansa, abubuwan da aka rubuta a kai sune koke-koke da makoki da kuma kaito.
Ezekiyel ya ci gaba da faɗi game da wahayin da ya gani.
Idan yarenku dole ne ya gane wanda yake magana, zai fi kyau a gano mai magana a matsayin "wanda yayi kama da mutum" (Ezekiyel 1:26). Ba "Ruhu" bane.
"Dan mutum" ko "ɗan adam." Allah ya kira Ezekiyel wannan don ya nanata cewa Ezekiyel ɗan adam ne kawai. Allah madawwami ne kuma mai iko, amma mutane ba haka suke ba. AT: "Mutum mai mutuwa" ko "Mutum"
"ko da yanzu" ko "har ma a yau." Wannan yana nufin cewa jama'ar Isra'ila suna ci gaba da rashin biyayya ga Allah.
Allah ya ci gaba da magana da Ezekiyel.
Kalmomin "fuskoki masu taurin kai" suna nuni ga yadda suke aiki a waje, kuma kalmomin "masu tauraruwar zuciya" suna nuni ga yadda suke tunani da ji. Tare suna jaddada cewa jama'ar Isra'ila ba za su canza yadda suke rayuwa don yin biyayya ga Allah ba.
Wannan yana nuna kyan gani ga dangin da ke zaune a gidan, a wannan yanayin Isra'ilawa, zuriyar Yakubu cikin shekaru da yawa. AT: "rukunin mutane"
"wanda suka ƙi ji shi annabi ne"
Waɗannan kalmomin suna kwatanta mutanen Isra'ila waɗanda ba za su yi wa Ezekiyel kirki ba yayin da ya gaya musu abin da Allah ya ce.
"Kada ku ji tsoron abin da suke fada."
Kalmomin "fuskokinsu" wani magana ne ga saƙon da mutane suke furtawa da fuskokinsu. AT: "ka daina sha'awar yi min hidima saboda yadda suke kallon ka"
Allah ya ci gaba da magana da Ezekiyel.
"sun yi tawaye sosai" ko "gaba ɗaya sun yi min tawaye"
Kamar dai 1) wani mutum a sama ya miƙa hannunsa zuwa ga Ezekiyel kuma duk abin da Ezekiyel ya gani daga hannu zuwa gwiwar hannu ko kafaɗa ko 2) “wanda ya yi kama da mutum” (Ezekiyel 1: 26) ya mika hannunsa.
"wani gungura wanda yake da rubutu a kai"
Ana iya sake bayyana wannan don cire sunayen suna "makoki," "makoki," da "kaito." AT: "wani ya yi rubutu a kansa cewa waɗannan mutane za su yi kuka, su yi baƙin ciki yadda za su kasance idan wani da suke ƙauna ya mutu, kuma abubuwa marasa kyau sun same su"
1Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ka ci abin da ka samu. Ka ci littafin nan, daga nan ka tafi ka yi magana da gidan Isra'ila."2Sai na buɗe bakina, ya kuma ciyar da ni da littafin.3Ya ce mani, "Dan mutum, ka ciyar da tunbinka ka kuma ƙosar da cikinka da littafin da Na ba ka!" Sai na ci shi, a cikin bakina yana da zaƙi kamar zuma.4Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ka tafi gidan Isra'ila ka faɗi maganganu na a gare su.5Gama ba'a aike ka wurin mutane masu bãƙon harshe ba, ko waɗanda harshensu yake da wahala ba, amma zuwa gidan Isra'ila -6ba wurin mutane masu yawa ba da bãƙon harshe ko waɗanda harshensu keda wuya ba, waɗanda ba za ka iya fahimtar kalmominsu ba. Tabbas idan da na aike ka wurinsu, da za su saurare ka.7Amma, gidan Isra'ila ba za su yadda su saurare ka ba, gama ba su yadda su saurare ni ba. Gama dukkan gidan Isra'ila masu taurinkai ne masu taurin zuciya kuma.8Duba! Na sa fuskarka ta taurare kamar fuskokinsu girarka kuma ta taurare kamar girarsu.9Na maida girarka kamar lu'u-lu'u, yafi tsagewar dutse! kada ka ji tsoron su ko ka karaya da irin fuskokinsu, tunda gida ne mai tayarwa."10Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, dukkan kalmomin dana sanar da kai ka ɗauke su cikin zuciyarka ka kuma ji su da kunnuwanka!11Daga nan ka tafi wurin 'yan bauta mutanenka, ka yi magana da su. Ka ce masu, 'Wannan ne abin da Ubangiji Yahweh ya ce,' ko su ji ko kada su ji."12Daga nan sai Ruhu ya ɗaga ni sama, a baya na kuma sai na ji babbar muryar girgizar ƙasa: "Albarka ta tabbata ga ɗaukakar Yahweh daga wurinsa!"13ƙarar fukafukan masu ran nan ne yayin da suke taɓa junansu, da ƙarar gargarorin da ke tare da su, da ƙarar babbar girgizar ƙasa.14Sai Ruhu ya ɗauke ni sama ya tafi da ni, na kuma tafi da ɓacin rai cikin ruhuna da zafin fushi, gama hannun Yahweh yana danne ni da iko!15Sai na tafi wurin 'yan bauta a Tel-abib waɗanda suke zama a bakin kogin Keba, na zauna cikinsu har kwana bakwai, zugum cikin mamaki.16Daga nan ya kasance bayan kwanaki bakwai ɗin sai maganar Yahweh ta zo gare ni, tana cewa,17"Ɗan mutum, Na maida kai mai tsaro domin gidan Isra'ila, domin haka sai ka ji maganar bakina, ka kuma ba su gargaɗi na.18Sa'ad da na ce da mugu, 'Hakika za ka mutu' kai kuma ba ka gargaɗe shi ba ko ka yi maganar gargaɗi ga mugu a kan miyagun ayyukansa ba, domin ya rayu - mugun za ya mutu saboda zunubinsa, amma zan biɗi haƙƙin jininsa a hannunka.19Amma idan ka gargaɗi mugun, kuma bai juya daga muguntarsa ba ko yabar miyagun ayyukansa ba, zai mutu domin zunubinsa, amma kai za ka ceci ranka.20Kuma idan adali ya juya daga adalcinsa ya aikata ba abin da dai-dai ba, kuma na sa abin tuntuɓe a gabansa, zai mutu. Saboda ba kagargaɗe shi ba, zai mutu cikin zunubansa, ba kuwa zan tuna da ayyukansa na adalci da ya yi ba, amma zan biɗi haƙƙin jininsa a hannunka.21Amma idan ka gargaɗi adalin mutum ya daina yin zunubi shi kuwa bai ƙãra yin zunubi ba, lallai zai rayu tun da shi ke an gargaɗe shi; kai kuma ka ceci ranka."22Hannun Yahweh yana kaina a wurin, sai ya ce mani, "Tashi! Ka fita zuwa sarari, a can kuma zan yi magana da kai!"23Sai na tashi na fita zuwa cikin sarari, a can ne ɗaukakar Yahweh na tsayawa, kamar ɗaukakar dana gani a gefen Kogin Keba; sai na faɗi a bisa fuskata.24Sai Ruhu ya sauko mani ya tsaida ni bisa sawayena; sai ya yi magana da ni, ya ce mani, "Jeka ka kulle kanka cikin gidanka,25domin yanzu, ɗan mutum, za su sa igiyoyi a kanka su ɗaureka domin kada ka iya fita cikinsu.26Zan sa harshenka ya liƙe wa rufin bakinka, za ka kasa yin magana, ba za ka iya tsauta masu ba, da shi ke su gidane masu tayarwa.27Amma sa'ad da na yi magana da kai, Zan buɗe bakinka za ka ce masu, 'Wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗi,' Wanda ya ji, ya ji, Wanda ya ƙi ji ya ƙi ji, gama su gida ne mai tayarwa!"
Ezekiel ya ci gaba da faɗi game da wahayin da ya gani.
Wannan yana nufin littafin da Allah ya bashi (Duba: Ezekiyel 2: 9).
Kalmar "ciki" tana nufin bangaren jikin da mutane zasu iya gani daga waje. Kalmar "ciki" tana nufin kayan ciki na ciki.
"waɗanda ke magana da baƙon harshe ko wahala"
"Ba zan aike ku zuwa ga wata babbar al'umma wacce mutanenta ke magana da baƙon harshe ba"
Waɗannan suna nufin abu ɗaya dai-dai. AT: "mai tsananin tawaye" ko "mai taurin kai"
Fuskar wuya wani magana ne ta taurin kai. AT: "Na sanya ku masu taurin kai kamar yadda suke"
"Na sanya bakinku kamar dutse mafi wuya, ya fi ƙanƙarar dutse wuya"
Anan “zuciya” tana wakiltar tunanin mutum. AT: "ku tuna da su kuma ku saurara da kyau"
Kalmar "kamammu" tana nufin mutanen Isra'ila ne da suke zaune a Babila.
Wasu sifofin sun ɗauki "Albarka ... wuri!" a matsayin kalmomin da "babbar girgizar ƙasa" ta faɗa: "Na ji a baya na jin ƙarar girgizar ƙasa, wanda ke cewa, "ɗaukakar Yahweh ta tabbata a wurinsa!"" Wasu sun fahimci sautin girgizar kamar sautin ɗaukakar Yahweh yana barin wurinsa, "kamar yadda ɗaukakar Yahweh ta bar wurinsa, na ji motsin girgizar ƙasa a bayana."
Ezekiyel yana ganin ya yi fushi saboda Yahweh ya aike shi ya yi magana da Isra'ilawa da ke zaman talala, don haka ya tayar wa Yahweh kansa. Koda yake ya kamata ya yi magana da su, ya zauna a shiru har kwana bakwai, koda yake ya ji fushin Yahweh “yana matsewa da ƙarfi” a kansa.
Kalmomin "ɗaci" da "fushi" nau'ikan fushi ne. Ana iya bayyana wannan azaman jumla daban. AT: "Na kasance mai daɗi kuma ruhuna yana cike da fushi" ko "Na kasance mai tsananin haushi da fushi"
Ezekiyel yayi maganar baƙin ciki da gajiya saboda Yahweh ya umurce shi da yin abubuwan da ba ya so ya yi kamar Yahweh yana tura shi ƙasa.
"na kasa yin komai saboda nayi matukar mamaki"
Ezekiyel ya ba da labarin gogewarsa a Tel-Aviv.
Allah ya gaya wa Ezekiyel ya gargaɗi mutanen Isra'ila kamar yadda mai tsaro zai gargaɗi mutanen birni idan maƙiya sun zo, don su shirya su tsira.
Wannan karin magana ne na ɗaukar wani da laifi ko kuma laifin kisan kai. AT: "bi da ku kamar kun kashe shi ne"
Kalmar "mugayen ayyuka" tana nufin abu ɗaya ne da "mugunta." AT: "baya barin aikata mugunta"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "sa wani mummunan abu ya same shi" ko 2) "sa shi yin zunubi a bayyane."
"zai mutu a matsayin mai zunubi" ko "zai mutu a matsayin mai laifi saboda ya saba min"
Kalmar "hannu" galibi ana amfani da ita don nuni ga ƙarfi ko aikin wani. AT: "ikon Yahweh"
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 1:27.
Wannan shi ne mafi kyawun fassara a zahiri.
"saman bakinka"
"Zan sanya ka iya magana"
"wanda ya ƙi saurarawa ba zai saurara ba"
1"Amma kai, ɗan mutum, sai ka ɗaukarwa kanka tubali ka sa a gabanka. Ka sassaƙa birnin Yerusalem a kansa.2Daga nan kayi sansani kewaye da shi, sai ka gina kagarai gãba da ita. A kuma tayar da masu kai mata hari, a kuma sa mata sansani kewaye da ita.3Daga nan ka ɗaukarwa kanka faifan ƙarfe ka kuma yi amfani da shi a matsayin katangar ƙarfe tsakaninka da birni ka kuma sa fuskarka gãba dashi, gama za a yi masa sansani, kuma kai zaka sa sansanin gãba dashi. Wannan zai zama alama ga gidan Isra'ila.4Daga nan, sai ka kwanta a gefen hannunka na hagu sai ka sa zunubin gidan Isra'ila a kansa; za ka ɗauki zunubinsu bisa ga yawan kwanakin da kake kwantawa gãba da gidan Isra'ila.5Ni da kaina na sanya maka kwana ɗaya ya wakilci shekara ta hukuncinsu: kwanaki 390! Ta haka nan, za ka ɗauki zunubin gidan Isra'ila.6Idan ka gama waɗannan kwanaki, sai ka sake kwanciya a sashin hannunka na dama kuma, gama za ka ɗauki zunubin gidan Yahuda har kwana arba'in. Na sanya maka kwana ɗaya domin shekara guda.7Ka sa fuskarka wajen sansanin Yerusalem, da hannunka marar rufi ka yi anabci gãba da ita.8Duba! I na sanya maɗaurai a kanka yadda ba za ka juya daga wannan sashi zuwa wancan ba har sai lokacin da ka gama kwanakin sansaninka.9Ka ɗaukar wa kanka alkama, bali, wake, acca, gero da maiwa; ka sa su cikin tukunya ɗaya ka yi gurasa da su bisa ga yawan kwanakin da za ka kwanta a sashinka. Za ka ci su har kwanaki 390.10Abincin da za ka ci zai zama bisa ga awo, shekel ashirin kowacce rana, za ka ci bisa ga lokutan da a ka ƙaiyade kowacce rana.11Daga nan za ka sha ruwa, bisa ga aunawa sau shida bisa ga ka'ida za ka sha.12Za ka ci a matsayin waina ta bali, amma za ka toya ta a kan idonsu da kãshin da ke fitowa daga jikin mutum!"13Gama Yahweh ya ce, "Wato abincin da 'ya'yan Isra'ila za su ci zai zama marar tsabta, a can cikin al'ummai inda na kora su."14Amma, Na ce, "Kaito! Ubangiji Yahweh! Ban taɓa ƙazantuwa ba! Ban taɓa cin mushe ba ko abin da namun jeji suka kashe, tun ina matashi har yanzu, kuma ba wani ƙazantaccen nama da ya taɓa shiga bakina!"15Sai ya ce mani, "Duba, na baka kãshin shanu maimakon kãshin mutum a kansa za ka shirya abincinka."16Ya sake ce mani, "Ɗan mutum! Duba! Ina karya sandar abincin da ke cikin Yerusalem, za su ci abinci suna aunawa cikin juyayi za kuma su sha ruwa lokacin da suke aunawa cikin rawar jiki.17Saboda za su rasa abinci da ruwa, kowanne mutum zai dubi ɗan'uwansa da damuwa su kuma lalace saboda laifinsu."
Yahweh ya ci gaba da magana da Ezekiyel. Ya gaya wa Ezekiyel ya ɗauki tubali da datti da guntun itace ya yi kamar shi ne Yahweh yana halaka birnin Yerusalem.
Wataƙila kuna buƙatar bayyana a fili cewa Ezekiyel zai sassaka hoto. AT: "zana hoton birnin Yerusalem"
Wannan umarni ne na duban samfurin birni a matsayin alama ta azabtar da birni. AT: "ku kalli gari" ko "ku kalli garin yadda za'a cutar da shi"
Yahweh ya ci gaba da magana da Ezekiyel.
Mai iya yiwuwa su ne 1) "a alamance suna ɗauke da hukuncin zunuban Isra'ilawa" ko 2) "wahala ta wurin kwanciya a gefenku saboda zunubinsu."
AT: "kwance fuskantar mulkin Isra'ila a cikin maƙiya iri"
AT: "Ni da kaina na umarce ka da ka kwanta a gefenka tsawon adadin ranakun da zan hukunta su"
Kalmar "gida" magana ne ga dangin da ke zaune a gidan, a wannan yanayin 'ya'yan Yahuza ne na shekaru da yawa. Dubi yadda kuka fassara waɗannan kalmomin a cikin Ezekiel 3: 1. AT: "kungiyar mutanen Yahuza" ko "mutanen Yahuza"
"Zan sanya ku yin hakan wata rana a kowace shekara da zan hukunta su"
Maɗaurai sune igiyoyi ko sarƙoƙi waɗanda suke hana mutum motsawa. Ba a bayyana ba ko kalmar "shaidu" magana ne ga wani abu da Yahweh yake yi kamar yana ɗaure Ezekiyel ne ko kuwa yana amfani da igiyoyi na zahiri.
Ruhun ya ci gaba da magana da Ezekiyel.
Waɗannan nau'ikan hatsi ne.
"za ku dafa shi a kan wuta wanda aka yi shi da sassan dattin mutum." Yarenku na iya samun hanyar bayyana wannan cikin ladabi.
"Ban taɓa cin nama mara kyau ba"
"Zan dakatar da ba da abinci ga Yerusalem"
Kuna iya bayyana dalilin da yasa zasu raba burodin. "za su rarraba burodinsu a hankali saboda suna tsoron kada a sami wadataccen abu"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "kowa zai kalli ɗan'uwansa kuma ya damu da yawan abincin da ɗan'uwansa yake ci da ɓatarwa" ko 2) "kowane ɗayansu zai firgita kuma ya ɓace"
1"Daga nan kai, Ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi kamar askar mai aski domin kanka, ka aske kanka da gemunka, daga nan ka ɗauki ma'auni ka raba gashin kanka uku.2Ka ƙone kashi ɗaya cikin wuta a tsakiyar birnin lokacin da kwanakin yiwa birnin sansani suka cika, ka ɗauki kashi ɗaya na gashin ka buge shi da takobi ko'ina kewayen birnin. Daga nan sai ka watsar da kashi ɗaya a iska, daga nan zan zare takobi in runtumi mutanen.3Amma ka ɗibi gashi kaɗan daga cikinsu ka ɗaure su cikin rigarka.4Daga nan sai ka ɗebi gashi mafi yawa ka jefa cikin tsakiyar wuta; ka ƙone su cikin wuta; daga nan wuta za ta fito ta shiga dukkan gidan Isra'ila."5Ubangiji Yahweh ya faɗi haka, "Wannan ita ce Yerusalem na sanya ta a tsakiyar al'ummai, na kuma kewaye ta da sauran ƙasashe.6Amma ta ƙi shari'ata yayin da ta aikata mugunta fiye da yadda sauran ƙasashe suka yi, ta tayarwa umarnaina fiye da ƙasashen da ke kewaye da ita. Mutanen sunƙi hukuntaina ba su kuma yi tafiya cikin farillaina ba."7Domin wannan Yahweh ya ce, "Saboda kunfi al'ummai waɗanda ke kewaye daku taurinkai ba ku yi tafiya cikin umarnaina ba kuma ba ku kiyaye dokokina ba ko ma dokokin al'umman da ke kewaye daku,"8domin wannan Yahweh ya ce, "Duba! nima ina gãba da ke. Zan aiwatar da hukuntai a tsakiyarki domin al'ummai su gani.9Zan yi maku abin da ban taɓa yi ba da kuma irin wanda ba zan sake yin irin sa ba, saboda dukkan ayyukan banƙyamarku.10Domin wannan a tsakiyarki ubanni za su ci naman 'ya'yansu, 'ya'ya kuma za su ci naman iyayensu, da shi ke zan aikata hukunci a kanku zan kuma watsar da dukkanku da kuka rage ko ina11Na rantse da raina - Wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - hakika saboda kun tozartar da wurina mai-tsarki da dukkan kayanku na banƙyama da al'amuranku na banƙyama, domin wannan Ni da kaina zan rage yawanku; idona kuma ba zai dube ku da rahama ba, ba kuma zan bar ku ba.12Kashi ɗaya cikin ukunku za su mutu da annoba, da yunwa kuma za su ƙare a tsakiyarku. Kashi ɗaya cikin ukunku kuma za su faɗi da kaifin takobi kewaye daku. Sulusin na ukun kuma zan watsar da su a kowanne sashi, in kuma zare takobi in fafare su.13Daga nan fushina zai kammala, zan kuma sa zafin hasalata akansu ya huce. Zan gamsu, kuma za su sani cewa Ni, Yahweh na yi magana cikin fushina sa'ad da na gama aikin hasalata gãba da su.14Zan maishe ku kango abin raini ga al'umman da ke kewaye daku, a kan idon duk wanda ke wucewa.15Hakan nan Yerusalem za ta zama wani abin wulaƙantarwa da ba'a ga mutane, abin gargaɗi da tsoratarwa ga al'ummai da ke kewaye daku. Zan zartar da hukuntai gãba daku cikin fushi da hasala, da tsautawa mai zafi - Ni, Yahweh na furta wannan!16Zan aikar da kibau masu zafi na yunwa gãba daku da za su zama dalilin da zan hallaka ku. Zan ƙara maku yunwa zan kuma datse abincin da kuke dogara da shi.17Zan aikar da yunwa da bala'o'i gãba daku za ku zama marar 'ya'ya. Annoba da jini za su ratsa ta tsakiyarku, zan kawo takobi gãba daku - Ni, Yahweh na furta wannan."
Yahweh ya ci gaba da magana da Ezekiyel. Duk wuraren "birni" suna nufin "birni" wanda Ezekiyel ya sassaka akan tubalin (Ezekiyel 4: 1).
"aske kanka da fuskarka" ko "cire gashin kai da gemu daga fuskarka"
"Lokacin da kwanakin kewaye Yerusalem suka ƙare" ko "lokacin da kwanakin suka ƙare da za ku nuna yadda Yerusalem za ta kewaye ta"
"ku buge ta da takobinku ko'ina cikin garin"
"'yan gashi daga tara"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "tsumma a hannayenku" ("hannayenku") ko 2) "ƙarshen ƙyallen rigar da ke jikin rigarka" ("kwalliyarka") ko 3) ninki a cikin rigar a inda take an saka shi a ɗamara .
"daga can wuta za ta tashi ta cinye dukkan Isra'ilawa." Yahweh yayi magana akan yadda zai hukunta Isra’ila kamar zai cinna wuta a gidan da kuma na Isra’ilawa kamar su dangin da ke zaune a wannan gidan amma a wancan lokacin a waje.
Mai yiwuwa ma'anar su ne 1) sauran al'ummomi a kowane gefen Yerusalem ko 2) "sun fi duk sauran al'ummomi muhimmanci."
"Mutanen Isra'ila da Urushalima sun ƙi bin dokokina."
Yahweh ya ci gaba da magana da Isra'ilawa da Yahuda.
"saboda zunubinku ya fi na" ko "saboda kun fi tawaye"
"Zan hukunta ku ta hanyoyi daban-daban" ko "Zan hukunta ku".
Yahweh ya ci gaba da magana da mutanen Isra'ila da Yerusalem.
"kamar yadda ban taɓa yi ba kuma ba zan sake yi a irin wannan hanyar ba" ko "kamar yadda ban taɓa yi ba kuma ba zan taɓa yi ba".
Wataƙila Ezekiyel yana faɗin abin da gaske zai faru idan mutane ba su da abinci.
"Zan tilasta dukkanku da kuka rage zuwa wurare daban-daban."
"da duk wadancan abubuwan naka wadanda na tsana." Wataƙila kuna buƙatar bayyana a sarari cewa wannan yana magana ne ga gumaka: "tare da gumakanku duka, waɗanda na ƙi" ko "tare da gumakanku masu banƙyama."
Ido wani magana ne na mutumin da ido yake. AT: "Ba zan tausaya muku ba"
"da yawa daga cikinsu za su mutu saboda yunwa"
"Ba zan kara yin fushi ba saboda zan yi duk abin da na so yi saboda na fusata"
"lokacin da na gama hukunta su"
Yahweh ya ci gaba da magana da Isra'ilawa da Yahuda.
Kalmar "kibiyoyi" na nuna ta azaba mai zafi da mutane ke ji idan sun daɗe da abinci. AT: "zai sa ku ji zafin yunwa mai tsanani"
Ana magana da rashin lafiya da mutuwar tashin hankali kamar suna sojoji ne masu ratsawa ta cikin gari suna kashe duk wanda zasu iya. AT: "Mutane da yawa za su mutu saboda cuta, wasu kuma da yawa za su mutu a yaƙi"
1Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, ka sa fuskarka gãba da tsaunukan Isra'ila ka yi anabci a kansu.3Ka ce, "Tsaunukan Isra'ila, ku ji maganar Ubangiji Yahweh! Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan ga tsaunuka da tuddai ga rafuffuka da kwarurruka: Duba! Zan kawo takobi gãba da ku, zan kuma hallaka wurarenku masu daraja.4Daga nan bagadanku za su zama kangaye ginshiƙansu za a hallakar da su, zan jefar da gawarwakinku gaban gumakansu.5Zan jera gawarwakin mutanen Isra'ila a gaban gumakansu, in warwatsar da ƙasusuwanku wajen bagadanku.6Duk inda kuka zauna, biranen za su zama marasa amfani, wuraren bisa kuma za su zama kufai, domin bagadanku su zama kufai su zama kangaye. Daga nan za'a farfashe su kuma za su ɓace, za a datse ginshiƙanku ayyukanku kuma za a shafe su kaf.7Matattu za su faɗi a tsakiyarku kuma za ku sani Ni ne Yahweh.8Amma zan tsare ringi daga cikin ku, waɗansu kuma za su tsere wa takobi daga cikin al'ummai, sa'ad da aka warwatsar da ku ko'ina cikin ƙasashe.9Daga nan su da suka tsira za su tuna da ni cikin al'ummai inda za a kai su bauta, za su tuna yadda zuciyata tayi ƙũna ta wurin zuciyarsu mazinaciya wadda ta juya daga gare ni, ta idanunsu kuma da ke ƙara sasu bin gumakansu. Za su ji ƙyamar kansu suna duban dukkan muguntar da suka aikata da dukkan ƙazantarsu.10Za su sani cewa Ni ne Yahweh. Saboda wannan dalilin Na ce Zan kawo wannan muguntar a gare su.11Ubangji Yahweh ya ce: Ka tãɓa hannayenka ka buga ƙafarka! Ka ce, 'Kaito!' saboda dukkan miyagun ayyukan ƙazanta na gidan Isra'ila! Gama za su faɗi ta kaifin takobi da yunwa da annoba.12Na nesa za su mutu ta annoba, na kusa zai faɗi ta wurin takobi. Waɗanda suka rage suka rayu za su mutu da yunwa. Ta haka ne zan cika hasalata a kansu.13Daga nan za ku sani ni ne Yahweh, sa'ad da matattunsu suka kwanta wurin gumakansu, kewaye da bagadansu, a kan kowanne tudu mai bisa - kan dukkan ƙwanƙoli tsaunuka, da ƙarƙashin kowanne itace mai inuwa kuma da rimi mai kauri - da wurare inda suke ƙona turare ga dukkan gumakansu.14Da hannuna zan kai sãra in maida ƙasar kango da kufai, tun daga jeji har zuwa Dibla, ko'ina a dukkan wuraren zamansu. Daga nan za su sani cewa Ni ne Yahweh."
Yahweh yana gaya wa Ezekiyel yayi magana da tsaunuka kamar su mutane ne don Isra'ilawa su ji kalmomin kuma su san cewa kalmomin Ezekiyel na su ne.
Wannan karin magana ne da ake amfani da shi don gabatar da wani abu da Allah ya faɗa wa annabawansa ko mutanensa. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiel 3:16. AT: "Yahweh ya faɗi wannan saƙon" ko "Yahweh ya faɗi waɗannan kalmomin"
Wannan umarni ne na duban duwatsu a matsayin alama ta azabtar da mutane a wurin. Duba yadda kuka fassara wani magana makamancin wannan a cikin Ezekiyel 4: 3. AT: "ku dube duwatsun Isra'ila" ko "ku dube duwatsun Isra'ila domin mutanen da ke wurin su cutu"
Kalmar "takobi" na nufin ga sojoji waɗanda ke kashe mutane ta amfani da takobi. AT: "Ina kawo sojoji su zo su kashe ku"
Waɗannan su ne maganar da Yahweh ya yi wa jama'ar Isra'ila.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane ba za su ƙara yin sujada a bagadanku ba kuma maƙiyinku zai lalata ginshiƙanku"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Sojojin maƙiyi za su lalatar da biranen ku"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. Duba yadda kuka fassara "ginshiƙai" a cikin Ezekiyel 6:4. AT: "za su sare ginshiƙanku"
"Za ku ga makiya sun kashe mutane da yawa"
Kalmar "takobi" ishara ce ga sojoji waɗanda ke kashe mutane ta amfani da takobi. AT: "wasu waɗanda sojoji ba sa kashewa"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da na warwatsa ku a cikin kasashe daban-daban" ko "lokacin da na tilasta muku zama a wasu ƙasashe"
Yahweh yayi magana game da Isra'ilawa kamar mace ce wacce take kwana da mutane da yawa. AT: "Na yi bakin ciki saboda sun kasance kamar matar da ta bar ni in kwana tare da wasu maza"
Ezekiyel zai yi wannan aikin na alama don ya ja hankalin mutane. Wannan ba tafi bane.
"Zan gamsar da fushina a kansu" ko "Zan hukunta su har sai na kara yin fushi"
Wata ma'ana mai yuwuwa ita ce "tudu, a kan dukkan duwatsu masu duwatsu, a ƙarƙashin kowane itace mai dausayi, da ƙarƙashin kowane itacen oak mai kauri"
1Kalmar Yahweh ta zo wurina, cewa,2"Kai, Ɗan mutum - Ubangiji Yahweh ya faɗi haka ga ƙasar Isra'ila." 'ƙarshe! ƙarshe ya zo ga iyakoki huɗu na ƙasar.3Yanzu ƙarshenki yana kanki, gama ina aikar da fushina a kanki, zan shar'anta ki bisa ga ayyukanki; zan kuma kawo dukkanharamtattun ayyukanki a kanki.4Gama idanuna ba za su tausaya maki ba, ba kuma zan keɓe ki ba. Maimakon haka, Zan kawo al'hakin al'amuranki a kanki, haramtattun ayyukanki kuma a cikinki, domin ki sani cewa Ni ne Yahweh.5Ubangiji Yahweh ya ce: Bala'i! Bala'i na musamman! Duba, yana zuwa.6Lallai matuƙa tana zuwa. Matuƙa ta farka a kanki. Duba, tana zuwa!7hukuncinku zai zo maku ku mazaunan ƙasar. Lokaci ya zo; ranar hallaka ta kusa, tsaunuka kuma ba za su ƙara yin murna ba.8Yanzu bada daɗewa ba zan zuba maku hasalata in cika fushina a kanku lokacin da nake hukunta ku bisa ga al'amuranku in kuma kawo dukkan al'hakin ƙazantarku a kanku.9Gama idanuna ba za su tausaya ba, ba kuma zan keɓe ku ba. Kamar yadda kuka yi haka zan yi maku; haramtattun ayyukanku za su kasance a tsakiyarku domin ku sani cewa Ni ne Yahweh wanda yake hukuntaku.10Duba, ranar! Duba, tana zuwa! hukunci ya fita waje! Sandar tayi fure, girmankai ya yi toho!11Tashin hankali ya yi girma zuwa cikin sandar mugunta - babu wani daga cikinsu, ko wani daga cikin taronsu, ko daga cikin wadatarsu, babu wani abu nasu mai muhimmanci da zai dawwama!12Lokaci na zuwa; lokaci ya zo kusa. Kada ka bari mai saye ya yi farinciki, ko mai sayarwa ya yi makoki, tunda fushina yana kan dukkan taronsu!13Gama mai sayarwa ba zai dawo ƙasar da ya yi sayarwa ba muddan dukkansu suna raye, saboda wahayin game da dukkan taron ba za a sauya ba; kuma saboda zunubansu, ba waninsu da zai ƙarfafa!14Sun busa ƙaho sun shirya komai, amma ba bu mai takawa zuwa yaƙi; tunda fushina yana kan dukkan taron jama'ar.15Takobi na waje, yunwa kuma da annoba suna cikin ginin. Waɗanda ke cikin saura za su mutu da takobi, yayin da yunwa da annoba kuma za su cinye waɗanda ke cikin birnin.16Amma waɗansu za su tsira daga cikinsu, za su gudu zuwa tsaunuka. Kamar kurciyoyin kwarurruwa, dukkansu za su yi makoki - kowanne mutum saboda laifinsa.17Kowanne hannu zai zama raunanne kowacce gwiwa kuma za ta zama marar ƙarfi kamar ruwa,18za su sa tsummoki, tsoro kuma zai rufe su; kunya za ta kasance a kowacce fuska, saiƙo kuma a dukkan kawunansu.19Za su jefar da azurfarsu cikin karafku zinariyarsu kuma za ta zama kamar juji. Azurfarsu da zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Yahweh. Rayukansu ba za su tsira ba, ba za a ƙosar da yunwarsu ba, domin laifofinsu sun zama dalilin tuntuɓe.20A cikin taƙamarsu suka ɗauki Kyaun kayan duwatsun adonsa, da su kuma suka yi siffofinsu na gumaka da ƙazantattun abubuwansu. Domin wannan, Ina maida waɗannan abubuwa su zama marasa tsarki a gare su.21Daga nan zan bada waɗannan abubuwa a cikin hannun bãƙi a matsayin ganima ga kuma miyagun duniya a matsayin ganima, za kuma su ƙazantar da su.22Daga nan zan juyar da fuskata daga gare su sa'ad da suka ƙazantar da ƙaunataccen wurina; 'yan adawa za su shiga su ƙazantar da shi.23Kayi sarƙa, saboda ƙasar ta cika da hukuncin jini, birnin kuma na cike da tashin hankali.24Domin in kawo ƙasashe mafi mugunta, za su kuma mallaki gidajensu, zan kuma kawo ƙarshen girmankan masu ƙarfi, gama za a ƙazantar da wurarensu masu tsarki!25Tsoro zai auko! Za su nemi salama, amma ba za a samu ba.26Masifa biye da masifa za ta zo, kuma za a samu jita-jita bayan jita-jita. Sa'an nan za su nemi wahayi daga wurin annabi, amma shari'a za ta lalace daga Firist shawara kuma daga wurin dattawa.27Sarki zai yi makoki yarima kuma zai rufe kansa da fargaba, yayin da kuma hannayen mutanen ƙasar makyarkyata cikin tsoro. Bisa ga hanyoyinsu zan aikata masu wannan! Zan hukunta su bisa ga matakinsu har sai sun sani cewa Ni ne Yahweh.'"
Wannan ya fara annabcin Allah game da Isra'ila.
Wannan karin magana ne da ake amfani da shi don gabatar da wani abu da Allah ya faɗa wa annabawansa ko mutanensa. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 3:16. AT: "Yahweh ya faɗi wannan saƙon" ko "Yahweh ya faɗi waɗannan kalmomin"
"duk ƙasar" ko "Iyakoki huɗu" suna zuwa arewa, gabas, kudu, da yamma.
Ana maganar "karshen" kamar dan fashi ne ya afkawa mutane. AT: "an gama rayuwar ku"
"gwargwadon ayyukan da kuka aikata" ko "saboda mugayen ayyukan da kuke aikatawa"
"Zan hukunta ku saboda aikata abubuwan da na tsana ƙwarai"
Waɗannan su ne maganar da Yahweh ya yi wa jama'ar Isra'ila.
Wadannan furucin ana nufin su sanya hanyar ta da karfi sosai. AT: "Ga shi, mummunan bala'i yana zuwa, wanda ba wanda ya taɓa fuskantar irinsa"
Hukuncin da ke zuwa ana ɗaukarsa kamar maƙiyi ne ya farka daga barci.
Kalmar "tsaunin" wani magana ne ga mutanen da ke zaune a kan tsaunuka. AT: "mutanen da ke kan tsaunai ba za su ƙara yin farin ciki ba"
"Da sannu yanzu"
Yahweh yayi amfani da kalmomin "zubo" da "cika" don magana akan fushin sa kamar dai ruwa ne ya zuba a cikin tulu. Waɗannan jimlolin suna nuna cewa Yahweh zai hukunta mutane sosai. AT: "Zan yi muku horo mai tsanani saboda ina fusata sosai"
Ido magana ne na mutumin da ido yake. AT: "Ba zan dube su da tausayi ba" ko kuma "Ba zan tausaya musu ba"
Waɗannan su ne maganar Yahweh game da Isra'ila.
"Ga shi, rana tana zuwa!" Kila iya buƙatar bayyana ranar da ke zuwa. AT: "Duba! Ranar da zan hukunta ku tana zuwa!"
Mai yiwuwa ma'anonin su ne 1) "Mutanen Isra'ila sun yi alfahari da girman kai" ko 2) "Mutanen Isra'ila sun zama masu girman kai da girman kai."
Duk “lokacin” da “ranar” suna nufin lokacin da Allah zai hukunta mutanen Isra’ila. AT: "Hukuncin Isra'ila zai faru ba da daɗewa ba"
"na yi fushi da dukkan taron jama'ar"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Allah ba zai ƙarfafa ɗayansu ba"
"Sun busa ƙaho don kiran mutane don yaƙi da abokan gaba"
Kalmar "takobi" nuna ga sojoji waɗanda ke kashe mutane ta amfani da takobi. AT: "akwai fada a waje."
Kalmar "cinye" kwatanci ne na "halakarwa gaba daya." AT: "kuma galibin mutanen da ke cikin birni zasu mutu saboda yunwa da rashin lafiya"
Ana maganar ta'addanci kamar sutura. AT: "kowa zai ga yadda suka firgita"
"a ranar da Yahweh ya aikata a kan fushinsa" ko "lokacin da Yahweh ya hukunta su"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "ba za su iya biyan yunwarsu ba" ko "har yanzu suna cikin yunwa koda bayan sun ci duk abin da suke da shi"
Waɗannan su ne maganar Yahweh game da Isra'ila.
Ana amfani da kalmar "hannu" don nuni ga sarrafawa. AT: "Zan ba da waɗannan gumakan a hannun mutanen da ba su sani ba" ko "Zan ba da waɗannan gumakan ga mutanen da ba su sani ba"
"Ba zan kula ba" ko "zan kau da kai" ko "Ba zan lura ba"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "ko'ina a ƙasar Allah yana hukunta mutane saboda sun kashe wasu da ƙarfi" ko kuma 2) "kotuna a ko'ina cikin ƙasar suna kashe mutane." Kalmar nan “jini” a nan tana wakiltar kisan kai da mutuwa.
Ana maganar gari kamar akwati ne, kuma ana magana da tashin hankali a matsayin abu wanda za'a iya saka shi a cikin akwati. Cikakken sunan "tashin hankali" ana iya fassara shi azaman aiki. AT: "tashin hankali ya kasance ko'ina a cikin birni" ko "mutane da yawa a cikin birni suna yin abin tashin hankali ga wasu"
"Zan sa manyan mutane a Isra'ila su daina alfahari da kansu"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "makiya za su ƙazantar da wuraren da suke yin sujada"
"Za su tambayi annabawa wane wahayi suka gani"
"Firistoci ba za su koyar da doka ba, kuma dattawa ba za su iya ba da shawara mai kyau ba." Wannan saboda Allah ba zai ba su hikima ba.
Kalmar "hannaye" alama ce ga mutane. AT: "Mutanen ƙasar za su ji tsoro don hannayensu su yi rawar jiki"
1Ana nan a shekara ta shida cikin wata na shida, a rana ta biyar ga watan, Ina zaune cikin gidana dattawan Yahuda kuma suna zaune a gabana, sai hannun Yahweh ya sake saukowa a kaina a wurin.2Sai na duba, sai ga alamar wani mai kama da bayyanuwar mutum. Daga bayyanuwar ƙugunsa zuwa ƙasa akwai wuta. Daga kuma ƙugunsa zuwa sama akwai bayyanuwar wani abu mai ƙyalli, kamar ƙarfe mai sheƙi.3Daga nan sai ya miƙa abu mai kama da hannu, ya ɗauke ni ta gashin kaina; Ruhun kuma ya ɗaga ni tsakanin duniya da sama, a kuma cikin wahayoyi daga wurin Allah, sai ya kawo ni Yerusalem, zuwa wurin shiga ƙofar arewa ta ciki, inda gunki mai cakuno babban kishi ke tsayawa.4Daga nan duba, ɗaukakar Allah na Isra'ila na wurin, bisa ga wahayin da na gani a sarari.5Daga nan sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ka ɗaga idanunka zuwa arewa." Sai na ɗaga idanuna zuwa arewa, daga arewacin ƙofar da ke bida wa zuwa bagadi, a ƙofar shigar, gunkin kishi ne.6Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ko ka ga abin da suke yi? Waɗannan sune haramtattun ayyuka masu girma da gidan Isra'ila ke yi da nufin su sani in tafi nesa da wurina mai tsarki. Amma za ka juya ka ga waɗansu haramtattun ayyukan mafi girma."7Daga nan sai ya kawo ni bakin ƙofar farfajiya, sai na duba, sai kuma ga rami a jikin bango.8Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ka yi gini cikin bangon nan" Sai na gina cikin bangon, sai ga wata ƙofa.9Daga nan sai ya ce mani, "Je ka ka ga haramtattun ayyukan muguntar da suke yi a nan."10Sai na shiga ciki na duba, kuma duba! Akwai kowanne abu mai rarrafe da ƙazantattun bisashe! Kowanne gunki na gidan Isra'ila an sasssaƙa siffarsa a jikin bangon kewaye ko'ina.11Dattawa saba'in na gidan Isra'ila suna wurin, Yãzaniya ɗan Shafan kuma na tsaye a tsakiyarsu. Suna tsaye a gaban siffofin, kowanne mutum na riƙe da kaskon ƙona turare a hannunsa yadda ƙanshin girgijen turaren kuma ya hau sama.12Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ko ka ga abin da dattawan gidan Isra'ila ke aikatawa a cikin duhu? Kowannesu na aikata wannan a cikin ɓoyayyen wurin ɗakin gunkinsa, gama sun ce, 'Yahweh ba ya ganin mu! Yahweh ya yi watsi da ƙasar."13Daga nan sai ya ce mani, "Ka sake juyawa ka ga waɗansu manyan haramtattun ayyuka da suke yi."14Gaba kuma sai ya kawo ni wajen ƙyauren ƙofar gidan Yahweh wadda ke gefen arewa, kuma duba! Mata na zaune suna makoki domin Tamuz.15Sai ya ce mani, "Ɗan mutum, ko ka ga wannan? Ka sake juyawa za ka ga manyan haramtattun ayyuka fiye da waɗannan."16Ya kawo ni cikin farfajiya ta cikin gidan Yahweh, duba kuma! A ƙofar shiga haikalin Yahweh tsakanin harabar da bagadi, akwai maza ashirin da biyar sun juyawa haikalin Yahweh baya fuskokinsu na fuskantar gabas, suna kuma yiwa rana sujada.17Sai ya ce mani, Ɗan mutum, ka ga wannan? Wannan ƙaramin abu ne ga gidan Yahuda, su yi waɗannan haramtattun ayyuka da suke yi a nan? Gama sun cika ƙasar da tashin hankali sun sake juyawa kuma sun cakune ni ga yin fushi, suna sanya reshe cikin hancinsu.18Ni ma zan yi aiki a cikinsu; Idanuna ba za su tausaya masu ba, ba kuwa zan raga masu ba. Koda za su yi kuka da babbar murya a kunnuwana, Ba zan ji su ba."
Ezekiyel ya ba da labarin wani wahayi da ya gani.
Ana amfani da wannan jumlar a nan don alamar farkon sabon ɓangaren labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
Wannan shine wata na shida a kalandar Ibraniyanci. Rana ta biyar tana kusa da farkon watan Satumba a kan kalandar yamma. AT: "rana ta biyar ga wata na shida"
Lokacin da karfe yayi zafi sosai, yakan haskaka da hasken rawaya ko lemu.
"tsakanin ƙasa da sama"
Kalmomin “a wahayin” suna nufin cewa wannan abin yana faruwa ne a cikin tunanin Ezekiyel. Jikinsa zai kasance a gidansa yayin da Allah ya nuna masa waɗannan abubuwa.
"gunkin da ke sa Allah ya kasance mai tsananin kishi"
"Ɗfan ɗan adam" ko "ɗan ɗan adam." Allah ya kira Ezekiyel wannan don ya nanata cewa Ezekiyel ɗan adam ne kawai. Allah madawwami ne kuma mai iko, amma mutane ba haka suke ba. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 2: 1. AT: "Mutum mai mutuwa" ko "Mutum"
Wannan karin magana yana nufin ya kalli wani abu. AT: "duba sama ... duba sama" ko "juya kan ka ka duba ... juya kai na duba"
"ƙofar da mutane zasu bi ta inda zasu iya zuwa bagadin"
Kila iya buƙatar bayyana wane tsakar gida. "farfajiyar haikalin"
"Sassaka a bangon kowane irin dabbobi masu rarrafe da dabbobin ƙyama." Maganar "abu mai rarrafe" na nufin kwari da sauran ƙananan dabbobi.
Sunayen maza
Allah yana umartar Ezekiyel ya duba abin da dattawan suke yi. AT: "ku kalli abin da dattawan gidan Isra'ila suke yi a cikin duhu."
"dakin da babu wanda zai ganshi yana bautar gunkinsa"
Wannan ƙofar arewa ta waje ce -- ba ɗaya take ba kamar yadda take a cikin Ezekiyel 8: 3.
"suna kallon gabas"
Allah ya yi amfani da wannan tambayar don ya nuna cewa daidai ne ya yi fushi da mutanen Yahuda. AT: "Ina daidai da in yi fushi a gidan Yahuda saboda waɗannan abubuwan banƙyama da suke yi a nan."
"A duk fadin kasar suna aikata abubuwa na tashin hankali ko" a duk fadin kasar suna yiwa juna fintinkau "
AT: "Duk da cewa suna kirana a gare ni da babbar murya"
1Sa'an nan sai ya yi kuka da babbar murya a kunnena, ya ce, "Bari matsara su taso zuwa birni, kowanne da makamin hallakarwarsa a hanunsa."2Daga nan duba! Mutane shida suka zo daga hanyar ƙofa ta bisa, wadda ke fuskantar arewa, kowanne mutum da makamin yankansa a hanunsa. Akwai mutum ɗaya a tsakiyarsu saye da tufafin linin a jikinsa da abin rubutu a gefensa. Suka shiga ciki suka tsaya wajen bagadi na tagulla.3Daga nan sai ɗaukakar Allah na Isra'ila ta hau daga wurin kerubim inda take a dã har zuwa bakin ƙofar gidan. Sai ya kira mutumin da ke saye da tufafun linin wanda yake da kayan rubuta a gefensa.4Yahweh ya ce masa, "Ka ratsa ta tsakiyar birnin - ta tsakiyar Yerusalem - ka sa shaida a goshin mutanen da ke nishi da tsaki game da dukkan haramtattun ayyukan da ake yi cikin tsakiyar birnin."5Daga nan na ji ya yi magana da sauran ya ce, "Ku ratsa birnin ku bi bayansa ku yi kisa. Kada ku bari idanunku su tausaya, kada kuma ku raga wa kowa.6Ko tsoho, ko saurayi, ko budurwa, ko ƙananan yara, ko mata. Ku kashe dukkan su! Amma kada ku kusanci kowanne mutum da ke da shaida a goshinsa. Ku fara daga wurina mai tsarki!" Sai suka fara da dattawa waɗanda ke a gaban gidan.7Sai ya ce masu, "Ku ƙazantar da gidan, ku cika harabunsa da matattu. Ku zarce gaba" Sai suka fita waje suka kai wa birnin hari.8Yayin da suke kai masa harin, sai na sami kaina ni kaɗai sai na faɗi a fuskata na yi kuka na ce, "Ah, Ubangiji Yahweh, za ka hallakar da dukkan sauran Isra'ila cikin hasalar fushin da kake zubawa kan Yerusalem?"9Sai ya ce mani, "Zunubin gidan Isra'ila da na Yahuda ya ƙasaita ƙwarai. Ƙasar cike take da jini kuma birnin cike yake da ayyukan ƙazanta, tun da suka ce, 'Yahweh ya manta da ƙasar,' kuma Yahweh ba ya gani!'10To daga nan, ni ma idanuna ba za su duba da tausayi ba, kuma ba zan raga masu ba. Maimakon haka, zan kawo masu duk alhakinsu a kansu."11Duba! Mutumin da ke saye da tufafin linin wanda ke da kayan rubutu a gefensa ya dawo. Ya kawo rahoto ya ce, "Na aiwatar da dukkan abin da ka umarta."
"Na ji shi ya kira"
makami don lalata mutane ko abubuwa
kayan aikin da marubuta ke rubutu da su
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) "daga saman halittu masu fukafukai huɗu" (Ezekiyel 1: 4) ko 2) daga tsakanin kerubim ɗin biyu a wuri mafi tsarki a cikin haikalin. Gwada fassara wannan a zahiri.
"munanan abubuwan da ake aikatawa a cikin birni" ko "abubuwan ƙyama da mutane ke aikatawa a cikin birni"
Kalmar "wasu" tana nufin masu tsaro (Ezekiyel 9: 1).
Ido wani magana ne na mutumin da ido yake. AT: "Kada ku da tausayi"
Allah yana ci gaba da magana da masu tsaron yana hukunta mutanen Isra'ila.
"Na sunkuyar da kaina ƙasa" ko "Na kwanta a ƙasa." Ezekiyel bai fadi da bazata ba. Ya gangara ƙasa don ya nuna girmamawa da tsoron Yahweh. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 1:27.
Ezekiyel yana roƙon Yahweh kada ya hallaka sauran. AT: "don Allah kar ku halakar da sauran Isra'ilawa a yayin isowar fushinku akan Yerusalem!"
Anan ana maganar "ƙasa" kamar dai akwati ne cike da jini. Anan “jini” ishara ce ta kisan kai. Kuma "birni" ana maganarsa kamar akwati ne kuma "ɓata gari" sune abubuwan da ke ciki. AT: "A duk faɗin ƙasar mutane suna kashe marasa laifi, kuma a duk faɗin garin mutane suna aikata mugunta"
Ido wani magana ne na mutumin da ido yake. AT: "Ba zan dube su da tausayi ba" ko kuma "Ba zan tausaya musu ba"
1Da na duba ta sararin da yake bisan kawunan kerubobin; wani abu ya bayyana a samansu kamar yakutu da bayyanuwa mai kamannin kursiyi.2Daga nan Yahweh ya yi magana da mutumin da ke saye da tufafin linin ya ce, "Jeka tsakaningargarorin da ke ƙarƙashin kerubobin, ka cika hannuwanka biyu da garwashin wuta mai zafi daga tsakanin kerubobin ka watsa su bisa birnin." Daga nan mutumin ya tafi ni yayin da nake kallo.3Kerubobin suna tsaya a gefen dama na gidan sa'ad da mutumin ya shiga ciki, sai girgije ya cika harabar da ke can ciki.4Ɗaukakar Yahweh ta taso daga kerubobin ta tsaya a ƙyauren gidan. ta cika gidan da girgijen, kuma harabar ta cika da hasken ɗaukakar Yahweh.5Aka kuwa ji ƙarar fukafukan kerubobin har can wajen harabar, kamar muryar Allah maɗaukaki sa'ad da yake magana.6Ana nan kuma, sa'ad da Allah ya umarce mutumin da ke saye da tufafin linin ya ce, "Ka ɗebi wuta daga tsakanin gargarorin da ke tsakanin kerubobin," mutumin ya je ciki ya tsaya a gefen gargare ɗaya.7Kerubim ɗaya ya miƙa hannunsa tsakanin kerubobin zuwa wutar da ke tsakanin kerubobin, ya ɗiba ya zuba a hannun wanda ke saye da tufafin linin. Mutumin ya karɓa ya tafi waje.8Na kuwa gani a kerubobin wani abu kamar hannun mutum a ƙarƙashin fukafukansu.9Saboda haka na duba, sai ga! gargarori huɗu a gefen kerubobin - gargare ɗaya a gefen kowanne kerubim guda - kuma fasalin gargarorin na kamar dutse mai daraja.10dukka huɗun fasalinsu dai-dai yake, kamar gargare na gittawa cikin wani gargaren.11Sa'ad da suke matsawa, suna tafiya a dukkan shiyyoyi huɗun. kuma ba tare da juyawa ga wata shiyyar ba, Maimakon haka, duk inda kan yake fuskanta, nan suke bin shi. Ba su kuwa juyawa ga wata shiyya sa'ad da suke tafiya.12Dukka jikinsu - haɗe da bayansu da hannuwansu da fukafukansu - na rufe da idanuwa, kuma idanuwan sun rufe gargarori huɗun dukka kewaye kuma.13Sa'ad da nake saurarawa, gargarorin suna kira, "guguwa."14Kowanne ɗayansu na da fuskoki huɗu; fuska ta fari ta Kerubim ce, fuska ta biyu ta mutum ce, fuska ta uku ta zaki ce, fuska ta huɗu kuma ta gaggafa ce15Daga nan kerubobin - waɗannan ne hallitu masu rai da na gani ta Kogin Keba - suka taso.16Duk sa'ad da Kerubobin suka matsa, gargarorin za su bi su gefensu, kuma duk sa'ad da kerubobin suka ɗaga fukafukansu su tashi daga ƙasa, gargarorin ba su juyewa. Suna dai tsaye a gefensu.17Sa'ad da kerubobin suka tsaya cik, gargarorin suma sai su tsaya cik, kuma idan suka tashi sama, gargarorin suma sai su tashi tare da su, gama ruhun halittar mai rai na cikin gargarorin.18Sa'an nan ɗaukakar Yahweh ta fita daga ƙyauren gidan ta tsaya a kan kerubobin.19Kerubobin suka ɗaga fukafukansu suka tashi daga ƙasa a fuskata sa'ad da suka fita, gargarorin kuma suka yi kamarsu a gefensu. Suka tsaya a bakin kofar shiga ta wajen gabas, ta gidan Yahweh, sai ɗaukakar Allah na Isra'ila ta zo gare su daga sama.20Waɗannan ne halittu masu rai dana gani a ƙarƙashin Allah na Isra'ila ta Kogin Keba, shi yasa na sani cewa su keruubobi ne!21Kowannen su na da fuskoki huɗu da fukafukai huɗu, da kamannin hannuwan mutum a ƙarƙashin fukafukansu,22kuma kamannin fuskokinsu na kama da wadda na gani a ruya a Kogin Keba, kuma kowannen su ya tafi gaba kai tsaye.
Ezekiyel ya ci gaba da ba da labarin wahayin da ya fara a cikin Ezekiyel 8: 1.
"wannan yayi kama da wani abu mai kama da kursiyi." Ezekiyel bai yarda ya faɗi tabbaci cewa ya yi kama da kursiyi ba.
mayafi mai ƙarfi, mai santsi da aka yi da shuka. Mutane da yawa suna sa shi a wuraren da suke da zafi. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 9: 2. AT: "santsi kyalle"
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 1:27.
ɗaukakar Yahweh kuwa ta cika
"Na ga kerubobin suna da wani abu kamar hannun mutum a ƙarƙashin fikafikansu"
Mai yiwuwa ma'anoni ga "kai" sune 1) wannan yana nufin halittu masu fuka-fukai. AT: "sun tafi duk inda fuskokin halittu masu fukafukai suke kallo" ko 2) wannan yana nufin keken gaba. AT: "sun bi duk hanyar da dabaran gaba ya bi"
"Kowane kerub yana da fuskoki huɗu" ko "Kowane kerub yana da fuska huɗu." Kowane taliki yana da fuska a gaba, yana da fuska a bayansa, yana da fuska a kowane gefen kansa. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 1: 4.
"gargarorin sun tsaya tare da kerubobin." AT: "gargarorin sun motsa tare da kerubim"
Zai yiwu ma'anoni su ne 1) Ezekiyel yana magana ne akan “halittu” na aya ta 15 kamar halitta ɗaya ce. AT: "ruhun talikan yana cikin ƙafafun" ko 2) Ezekiyel yana amfani da karin magana. AT: "ruhun rayuwa yana cikin ƙafafun" ko "ruhun mai rai yana cikin ƙafafun" ko kuma 3) ruhun da ke cikin talikan kuma a ƙafafun daidai yake. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 1:19. AT: "wannan ruhun da ya ba halittu rai shi ma ya ba ƙafafun rai"
"ya tafi sama da kerubim"
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 1:13.
1Sai Ruhun ya ɗago ni sama ya kawo ni ƙyauren gabas na gidan Yahweh, yana kuma fuskantar gabas, a bakin ƙofar akwai mutum ashirin da biyar. Na ga Yãzaniya ɗan Azzu da Felatiya ɗan Benayya shugabanin mutanen, a cikinsu.2Allah ya ce mani, "Ɗan mutum, waɗannan ne mutanen da ke ƙirkiro zunubai da kuma yin miyagun shirye-shirye a wannan birnin.3Suna cewa, 'Ba yanzu ne lokacin gina gidaje ba, wannan birnin shi ne tukunyar, kuma mu ne naman.'4Saboda haka ka yi annabci gãba da su. Ɗan mutum, ka yi annabci."5Sai Ruhun Yahweh ya sauko mani ya kuma ce mani, "Ka ce: Ga abin da Yahweh ya ce, "Gidan Isra'ila wannan shi ne abin da kuke cewa; gama na san abin da ke tafiya a zuciyarku.6Kun yawaita mutanen da kuka kashe a wannan birnin kuma kun cika karafku da su.7Saboda haka, Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Mutanen da kuka kashe, waɗanda kuka sa jikunansu a tsakiyar UYerusalem, su ne naman, kuma wannan birnin ne tukunyar. Amma za a fitar daku daga tsakiyar wannan birnin.8Kun ji tsoron takobi, saboda haka ina tahowa da takobi a kanku - wannan ne furcin Ubangiji Yahweh.9Zan fitar daku daga cikin birnin, in sa ku a hannun bãƙi, gama zan kawo hukunci a kanku.10Za ku faɗi ta takobi. Zan hukunta ku a cikin iyakar Isra'ila domin ku sani cewa Ni ne Yahweh.11Wannan Birnin ba zai zama tukunyar dahuwarku ba, ko ku zama naman cikinta ba. Zan hukunta ku a kan iyakar Isra'ila.12Sa'an nan za ku sani cewa Ni ne Yahweh, wanda kuka ƙi yin tafiya bisa ga tafarkinsa wanda kuma kuka ƙi aikata umarninsa. Maimakon haka, sai kuka aikata dokokin al'umman da ke kewaye daku."13Hakanan kuma sa'ada da nake annabci, Felatiya ɗan Benayya, ya rasu. Sai na faɗi fuskata a ƙasa na yi kuka da murya mai ƙarfi na ce, "Kash, ya Ubangiji Yahweh, za ka hallakar da ragowar Isra'ila ne kakaf?"14Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,15"Ɗan mutum, 'yan'uwanka! 'Yan'uwanka! Mutanen danginka da dukkan gidan Isra'ila! Dukkansu ne waɗanda a ka yi magana game da su ta wurin waɗanda ke zama cikin Yerusalem, 'Su na nesa da Yahweh! Wannan ƙasar an bada ita gare mu a matsayin mallakarmu.'16Saboda haka ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya ce haka: Koda shi ke na kai su nesa tsakanin al'ummai, kuma na warwatsar da su cikin ƙasahe, duk da haka na zama haikali a gare su na ɗan lokaci ƙaɗan cikin ƙasashen da suka tafi.'17Saboda haka ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya ce haka: Zan tattaro ku daga mutane daban-daban, in jera ku daga ƙasashen da kuka warwatse, sai in ba ku ƙasar Isra'ila.18Sa'an nan za su je wurin su cire dukkan abin banƙyama da dukkan ayyukan banƙyama daga wancan wurin.19Zan ba su zuciya ɗaya, kuma zan sa sabon ruhu a cikin su. Zan ɗauke zuciyar dutse daga jikinsu in ba su zuciyar tsoƙa,20domin su yi tafiya cikin tafarkina, za su kiyaye ka'idodina su kuma aikata su. Sa'an nan za su zama mutanena, Ni kuma in zama Allahnsu.21Amma ga waɗanda ke tafiya tare da sha'awar abin ƙyamarsu da taƙaicinsu, Zan kawo masu ayyukansu ga kawunansu - wannan ne furcin Ubangiji Yahweh."22Kerubobin suka ɗaga fukafukansu da gargarorinsu da ke a gefensu, ɗaukakar Allah na Isra'ila kuma ta kasance a can sama bisansu.23Sa'an nan ɗaukakar Yahweh ta fito daga cikin tsakiyar birnin ta kuma tsaya a tsauni ta gabashin birnin.24Ruhun ya ɗago ni ya kawo ni cikin Kaldiya, gun 'yan zaman ɓauta, a wahayi daga Ruhun Allah, kuma wahayin da na gani ya fito daga gare ni.25Sai na furtawa masu zaman bautar dukkan abubuwan Yahweh da na gani.
Ezekiyel ya ci gaba da ba da labarin wahayin da ya fara a cikin Ezekiyel 8: 1.
Duba yadda kuka fassara wannan jumlar a cikin Ezekiyel 8:16.
Mutanen suna magana ne game da kansu kamar masu yanke nama mai kyau ne kuma na birni kamar dai tukunya ce wacce ake ajiye naman a ciki ko dafa shi. Wani magana yana nuna cewa suna da mahimmanci kuma suna da aminci a cikin gari. AT: "Wannan birni kamar tukunya ne wanda zai kāre mu kamar yadda tukunya ke kare nama"
Yahweh ya ci gaba da magana da annabi Ezekiyel.
Ezekiyel yayi magana game da Ruhun Yahweh yana ba shi izini da ƙarfafa shi yin annabci kamar dai Ruhun Yahweh ya sauka a kansa. AT: "Ruhun Yahweh ya ba ni iko"
Yahweh yana magana akan mutanen da suka kashe kamar yankakku ne na nama da birni kamar tukunya ce wacce ake ajiye naman a ciki ko dafa shi. Duba yadda kuka fassara wannan maganar a cikin Ezekiyel 11: 3. AT: "Mutanen da kuka kashe ... suna kama da naman a cikin tukunya, kuma wannan birni kamar tukunya ne.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT "Amma zan fito da ku"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Isra’ila.
Kalmar "takobi" wani magana ne ga sojoji waɗanda ke kashe mutane ta amfani da takobi. AT: "Za su kashe ku da takubbansu" ko "Za ku mutu a yaƙi"
Anan kalmar "hannaye" suna wakiltar ƙarfi ko iko. AT: "sanya ku cikin ikon baƙi" ko "sa baƙin su kama ku"
Mutanen sun yi magana game da kansu kamar masu yanke nama ne mai kyau kuma na birni kamar dai tukunya ce da ake ajiye naman a ciki ko dafa shi. Yahweh yace wannan ba gaskiya bane. Duba yadda kuka fassara wannan kwatancin a cikin Ezekiyel 11: 3. AT: "Wannan birni ba kamar tukunya ba ne wanda zai kare ku kamar yadda tukunya ke kare nama"
"a cikin ƙasar Isra'ila"
Waɗannan sunanayen mutum ne.
"Na sunkuyar da kaina ƙasa" ko "Na kwanta a ƙasa." Ezekiyel bai fadi da bazata ba. Ya gangara ƙasa don ya nuna girmamawa da tsoron Yahweh.
Wannan karin magana ne da ake amfani da shi don gabatar da wani abu da Allah ya faɗa wa annabawansa ko mutanensa. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 3:16. AT: "Yahweh ya faɗi wannan saƙon" ko "Yahweh ya faɗi waɗannan kalmomin"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki.AT: "Mutanen da ke zaune a Yerusalem suna faɗi game da su duka"
Yahweh ya ba wannan saƙon ga Ezekiyel game da Isra'ilawa da suke zaman talala.
Yahweh yayi magana game da zama a tsakanin mutanen da ke cikin bauta kamar ya kasance tsattsarkan wuri ne a gare su. AT: "Na kasance tare da su" ko "Na kasance kamar wurin bautarsu"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Maimaitawar ta nanata tabbacin alkawarin Yahweh na dawo da bautar talala zuwa ƙasar Isra'ila. AT: "Zan dawo da ku daga duk al'umman duniya"
Yahweh yayi magana akan mutane masu taurin kai kamar suna da zuciyar dutse da kuma yin biyayya da yardan rai kamar suna da zuciya ta nama. Yana magana ne game da sa su zama masu biyayya da yardan rai kamar yana musanya waɗancan zukatan biyu. AT: "Zan sa su daina taurin kai kuma a maimakon haka zan sa su yi min biyayya da yardar rai"
Kowane ɗayan waɗannan jimlolin suna da ma'anoni iri ɗaya kuma suna bayyana mutane da yin biyayya ga abin da Yahweh ya umurce su da su yi. An maimaita su don girmamawa.
Kerubim da ɗaukakar Allah sun bar haikalin da birni.
Ezekiyel yayi maganar wahayin da ya ƙare kamar dai wahayin wani abu ne wanda ya taɓa shi kuma ya bar shi. AT: "wahayin da na gani ya ƙare"
1Maganar Yahweh ta zo mani, cewa,2"Ɗan mutum, kana zama a cikin gidan tayarwa, inda suna da idanuwan gani amma ba su gani; inda kuma suna da kunnuwan ji amma ba su ji. Saboda su gidan tayarwa ne.3Saboda haka kai ma, ɗan mutum, ka shirya kayanka domin zaman bauta, kuma ka tashi da rana a fuskarsu, domin zan sa kaje zaman bauta a fuskarsu daga wurin da kake zuwa wani wurin. Watakila za su fara gani, koda shi ke su gidan tayarwa ne4Za ka fitar da kayayyakinka na zaman bauta da rana a fuskarsu; jeka waje da yamma a fuskarsu a hanyar da kowa ke zuwa zaman bauta.5Ka huda rami a bango a fuskarsu, kuma ka fita ta wurin.6A fuskarsu, ka ɗauki kayayyakinka kan kafaɗarka, ka kawo su waje a cikin duhu. Ka rufe fuskarka, gama lallai ba za ka ga ƙasar ba, tunda na sa ka kamar alama ne ga gidan Isra'ila."7Sai na yi hakan, kamar dai yadda aka umarce ni. Na kawo kayan zaman bautata da rana, kuma da yamma na huda rami da hannu a bango. Na fitar da kayana waje a duhun, sai na sa su a kafaɗata na ɗaga sama a fuskarsu.8Sai maganar Yahweh ta zo mani da safe, cewa,9"Ɗan mutum, ko gidan Isra'ila, gidan tayarwar nan, ba su tambaya, 'me ka ke yi?'10Ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Wannan aikin annabcin ya shafe ɗan sarki a Yerusalem ne, da dukkan gidan Isra'ila wanda a cikinsa suke.'11Ka ce, 'Ni ne alama a gare ku. Kamar yadda na yi, haka za a yi masu; za su je zaman bauta da zaman talala.12Ɗan sarkin da ke a cikinsu zai ɗauki kayansa a kafaɗarsa da duhu, kuma ya fice ta bango. Za su huda bango su fita da kayansu. Zai rufe fuskarsa domin kar ya ga ƙasar da idanuwansa.13Zan shimfiɗa ragata a kansa kuma zai kamu a tarkona; sa'an nan zan kawo shi Babila, da ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan su ba. Zai mutu a can.14Ta kowacce shiyya kuma zan warwatsar da dukkan waɗanda ke kewaye da shi da za su taimaka masa da dukkan sojojinsa, kuma zan aikar da takobi biye da su.15Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Yahweh, idan na warwatsar da su cikin al'umma na kuma tarwatsar da su ko'ina a ƙasashe.16Amma zan bar kaɗan daga cikinsu daga takobin da yunwa da annoba, saboda su bada rohoton dukkan abin ƙyamar da ke cikin ƙasar inda na ɗauke su, domin su sani Ni ne Yahweh."'17Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,18"Ɗan mutum, ka ci gurasarka a giggice, ka kuma sha ruwanka da rawar jiki da damuwa.19Sa'an nan sai ka ce da mutanen ƙasar, ' Ubangiji Yahweh ya ce haka game da mazaunan Yerusalem, da ƙasar Isra'ila: Za su ci abincinsu da rawar jiki kuma su sha ruwa cikin fargaba, tun da za a washe ƙasar da dukkan abin da ke ciki saboda hargitsin dukkan waɗanda ke zaune a ciki.20Domin haka Biranen da ke da mazauna za su zama kufai, kuma ƙasar za ta zama kango; To za ku sani cewa Ni ne Yahweh."'"21Karo na biyu kuwa, maganar Yahweh ta zo mani, cewa,22"Ɗan mutum, Mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra'ila da ke cewa, 'Kwanakin na da tsawo, kuma dukka wahayin bai gudana ba'?23Saboda haka, ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya ce haka: Zan kawo ƙarshen wannan karin maganar, kuma mutanen Isra'ila ba za su ƙãra amfani da ita ba.' Ka ce masu, 'Kwanakin sun kusato sa'ad da dukkan wahayoyin za su cika.24Gama ba za ƙãra samun wahayoyin ƙarya ba ko dũba ta neman suna cikin gidan Isra'ila ba.25Gama Ni ne Yahweh! Nakan faɗa, kuma ina aikata abin da na faɗa. Ba za a ƙãra ɓata lokaci a kan batun ba. Gama zan faɗi wannan magana a kwanakinku, gidan tayarwa, kuma tabbas zan aiwatar da shi! - wannan ne Ubangiji Yahweh ke furtawa."'26Haka kuma maganar Yahweh ta zo mani, cewa,27"Ɗan mutum! Duba, gidan Isra'ila ya ce, 'Wahayoyin da yake gani na kwanaki da yawa ne daga yanzu, kuma yana annabcin lokutta masu nisa ne.'28Saboda haka ka ce da su, 'Ubangiji Yahweh ya ce: Maganganuna ba za su ƙãra yin jinkiri ba, amma maganar da na faɗa za ta cika - wannan ne furcin Ubangiji Yahweh.
Mutane ba sa iya fahimtar saƙon Yahweh da abin da yake yi ana maganarsu kamar mutane ba su iya gani da ji a zahiri.
"To, ga abin da zan gaya muku"
Mutane suna iya fahimtar saƙon Yahweh da abin da yake yi ana maganarsu kamar mutane suna iya gani.
Allah yana magana da Ezekiyel kuma yana kwatanta yadda yakamata yayi kwatancin.
A nan kalmar "alama" tana nufin wani abu da ke isar da gargaɗi na musamman ga waɗanda suka gani. Yahweh yayi magana akan Ezekiyel da ayyukansa kamar wannan gargaɗi ne. AT: "sun sanya ku zama masu gargadi"
Ezekiyel ya nuna wa Isra'ilawa ba da daɗewa ba za a tilasta musu bauta.
"Na huda rami ta bango da hannuna"
Kalmomin "a cikin wanene" yana nufin Yerusalem, yayin da "su" suna nufin "gidan Isra'ila." AT: "waɗanda ke Yerusalem"
Yahweh yayi magana akan bawa Kaldiyawa damar kama yarima kamar shi da kansa yake kama basarake a cikin tarkon da ya saka.
Yahweh yayi magana akan bawa Kaldiyawa damar kawo ɗan sarki zuwa Babila kamar dai shi da kansa ke kawo yariman can. AT: "Zan sa Kaldiyawa su kawo shi Babila"
Kalmar "takobi" na nufin ga sojojin abokan gaba waɗanda za su kawo hari da takubbansu. AT: "Zan aika da runduna don bin su da takuba"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya dai-dai. AT: "lokacin da na sa su rabu da juna kuma nake zaune a cikin al'ummu daban-daban"
AT: "yi rayuwarka ta yau da kullun da tsananin babban tsoro"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "garuruwan da mutane suka rayu za su kasance kufai"
Yahweh yayi wannan tambaya don tunatar da Ezekiyel wani abu da ya riga ya sani. Tambayar ita ce ta tsautawa ga mutanen da ke amfani da karin maganar. AT: "mutanen ƙasar Isra'ila suna da wannan karin maganar da ke cewa, 'Kwanakin sun yi tsawo, kuma kowane hangen nesa ya kasa.'"
Wannan jumlar tana nufin ranakun da za'a yiwa Isra'ila hukunci. AT: "Kwanan hukunci suna zuwa ba da daɗewa ba"
“Al’amarin” yana nufin abubuwan da Yahweh ya ce za su faru. AT: "Abin da na ce ba za a jinkirta shi ba" ko "Abin da na ce zai faru ba da daɗewa ba"
Waɗannan jimlolin sune hanyoyin da mutanen Isra’ila ke faɗakar da gargaɗin Ezekiyel ba zai faru ba a rayuwarsu amma zai faru a nan gaba.
1Bugu da ƙari, maganar Yahweh ta zo mani, cewa.2"Ɗan mutum, ka yi annabci gãba da annabawan da ke annabci a Isra'ila, kuma ka faɗa wa waɗanda ke annabci daga tsammace-tsammacensu, ' Ku saurari maganar Yahweh.3Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Kaiton wawayen annabawan da ke bin ruhun kansu, amma ba su ga komai ba!4Isra'ila, annabawanki sun zama kamar diloli a watsattsun gonaki.5Ba ku je wurin tsagogin bango da ke kewaye da gidan Isra'ila domin ku gyara shi ba, domin ku yi tsayayya a yaƙi a ranar Yahweh ba.6Mutanen na ganin wahayoyin ƙarya kuma su na yin annabcin ƙarya, waɗanda ke cewa, "Wannan da wancan ne furcin Yahweh." Yahweh bai aike su ba, amma ko kaɗan ba su bar sanya mutane begen saƙonninsu za su zama gaskiya ba.7Ba ku yin wahayin ƙarya da annabcin ƙarya, ku da ke cewa, "abu kaza da abu kaza ne furcin Yahweh" sa'ad da Ni kaina ban yi magana ba?8Saboda haka Ubangiji Yaweh ya faɗi wannan, 'Domin kun yi ƙarairayi a kan karɓar wahayi - Saboda haka Ubangiji Yahweh ya yi furcin gãba da ku:9Hannuna zai yi gãba da annabawa masu wahayoyin ƙarya da annabcin ƙarya. Ba za su kasance a taruwar jama'ata ba, ko a sa su a cikin lissafin gidan Isra'ila ba; Ba za su tafi ƙasar Isra'ila ba. Gama za ku san cewa Ni ne Ubangiji Yahweh!10Domin wannan, kuma saboda sun sa mutanena su kauce daga hanya da cewa, "Salama!" sa'ad da babu salama, suna gini a bangon da za su shafa farar ƙasa.'11Ka cewa waɗanda ke shafen bangon da farar ƙasar,' zai faɗo ƙasa; za a yi ruwan sama, kuma zan aiko da guguwar da za ta sa ya faɗi, da iska mai ƙarfi da za ta rushe bangon.12Duba, bangon zai faɗo. Waɗansu ba su ce maku, "Ina farar ƙasar da kuka shafa wa bangon ba?"13Saboda haka Ubangiji Yahweh ya ce: Zan kawo guguwar iska a fushina, kuma za a samu ambaliyar ruwan sama a hasalata! ƙurar fushina za ta hallaka shi kakaf.14Gama zan rushe bangon da kuka shafe da farar ƙasa, kuma zan ragargaza shi har ƙasa in bar ginshiƙan a fili. Domin ya faɗo, kuma ku hallaka a tsakiyarsa. Za ku kuwa sani cewa Ni ne Yahweh.15Gama cikin fushina zan hallakar da bangon da waɗanda ke shafa masa farar ƙasa.16wato annabawan Isra'ila da ke yin annabci a kan Yerusalem waɗanda kuma ke ganin wahayoyin salama dominta. Amma babu salama!- wannan furcin Ubangiji Yaweh ne."'17Saboda haka, ɗan mutum, ka sa fuskarka gãba da 'ya'ya mata na mutanenka da ke annabci daga nasu tunanin, kuma ka yi annabci gãba da su.18Ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Kaiton matayen da ke ɗinka layun dabo a dukkan ɓangarorin hannunsu suna kuma yin gyalulluka domin kawunansu da kowanne irin fasali, suna amfani da shi a farautar mutane. Za ku farauci mutanena amma ku ceci ranku?19Kun ɓãta ni a cikin mutanena domin a ba ku ɗan danƙin bali da gutsiren gurasa, ku kashe mutanen da bai dace su mutu ba, da kuma barin waɗanda bai dace su rayu ba su rayu, saboda karairayi da kuke yiwa mutanena da ke jinku.20Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ina gãba da dabo da layun da kuka yi aiki da su domin ku yiwa rayukan mutane tarko kamar tsuntsaye. Hakika zan yayyage su daga hannuwanku; kuma mutanen da kuka cafko kamar tsuntsaye - Zan sake su su tafi.21Zan yayyage gyalullukanku na tsafi in ceci mutanena daga hannunku, saboda ka da su ƙara faɗawa a tarkon hannuwanku. Za ku kuwa sani cewa Ni ne Yahweh.22Saboda kun karya zuciyar mutum mai adalci da ƙarairayi, koda yake Ni ban yi niyyar karya zuciyarsa ba, kuma domin kun ƙarfafa wa mugu gwiwa domin kar ya juyo daga hanyarsa ya ceci ransa -23to ba za ku ƙara ganin wahayoyin ƙarya ko ku ci gaba da yin annabcin ƙarya ba, gama Zan ceci mutanena daga hannunku. Za ku sani cewa Ni ne Yahweh,"'
"annabci kawai abubuwan da suke tunanin"
Anan kalmar “ruhu” tana wakiltar tunani da dabarun mutum. "Bi" a nan wani karin magana ne da ke nufin aikata abin da ra'ayinsu ya nuna musu. AT: "waɗanda suke aiki daidai da ra'ayinsu"
Kamar diloli masu neman abinci da mafaka a cikin kango biranen, annabawa suna amfani da halakar Yerusalem don amfanin kansu.
Kuna iya ba da cikakken bayanin nan. AT "tsayayya wa sojojin abokan gaba" ko "kare birni"
Tunda annabawan karya ba su karɓi saƙo da gaske daga Yahweh ba, abin da suke faɗi game da makomar ba gaskiya ba ne.
Anan kalmar “hannu” tana wakiltar ikon Yahweh. Cewa hannunsa zai kasance akan su kwatanci ne wanda ke nufin cewa zai azabtar da su da ƙarfinsa. AT: "Zan hukunta annabawa"
Wannan yana nufin cewa Yahweh ba zai ɗauki waɗannan annabawan ƙarya a matsayin wani ɓangare na Isra'ilawa ba.
A cikin waɗannan ayoyin, Yahweh yana magana ne game da amincin ƙarya da annabawa suka ba mutane ta wurin yin magana game da salama kamar annabawa sun gina katanga mara kyau kuma sun lulluɓe shi da farin fenti don ya yi kyau.
Kalmar "wannan" tana nufin annabawa masu ba da rahoton wahayin ƙarya ga mutane kuma suna yi musu ƙarya.
Yahweh yana magana akan annabawa suna yaudarar mutane kuma suna sa su suyi imani da ƙarya kamar dai annabawan sun ɓatar da mutane daga hanyar da ya kamata su bi. (Duba:
Yahweh yana nufin hukuncin da zai aiko wa mutane kamar hadari ne mai ƙarfi wanda ya rushe bangon.
Yahweh yana nufin hukuncin da zai aiko wa mutane kamar hadari ne mai ƙarfi wanda ya rushe bangon.
Kalmar "ta" tana nufin Yerusalem.
Anan "fuska" ƙira ce don kulawa ko kallo, kuma "saita fuskarka" tana wakiltar kallo. AT: "ku zura ido"
Wannan karin magana yana nufin mata waɗanda suke cikin rukunin mutane kamar Ezekiyel. AT: "matan Isra'ila" ko "matanku na gari"
Yahweh ya ci gaba da magana a kan annabawan annabawan ƙarya a Isra'ila.
Sha'ir hatsi ne da ake amfani da shi don yin burodi kuma kalmar "marmashi" ƙaramar gurasa ce. Dukansu jumlolin abinci ne kaɗan kuma ana amfani dasu don jaddada ƙaramar kuɗin da aka biya ga annabawa.
"yaga laya daga hannunka"
Anan kalmar "hannu" tana wakiltar ƙarfi ko iko. Yahweh yayi magana akan mutanen da ke cikin ikon waɗannan matan kamar matan sun kama su da hannayensu. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ba za ku ƙara tarko su kamar ganima a hannunku ba" ko "ba za ku ƙara sarrafa su da ƙarfinku ba"
Anan kalmar "zuciya" tana wakiltar mutum da motsin zuciyar sa. AT: "kashe zuciyar mai adalci"
1Waɗansu daga cikin dattawan Isra'ila suka zo wurina suka zauna a gabana.2Sa'an nan maganar Yahweh ta zo mani, cewa,3"Ɗan mutum waɗannan mazajen sun ɗauki gumakansu cikin zukatansu sun kuma sa tuntuɓen zunubansu a gaban fuskokinsu. Za su ma roƙe ni wani abu kuwa?4Saboda haka ka sanar da wannan gare suka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Duk mutumin gidan Isra'ila wanda ya ɗauki gumaka ya sa a zuciyarsa, ko ya sa tuntuɓen zunubansa a gaban fuskarsa, kuma ya zo gun Annabi - Ni, Yahweh, zan amsa masa bisa ga yawan gumakansa.5Zan yi wannan domin Zan iya ɗauke gidan Isra'ila daga cikin zukatansu da ke nesa da ni ta dalilin gumakansu.'6Saboda haka ka cewa gidan Isra'ila. 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Ku tuba ku juyo daga gumakanku! Ku juya fuskokinku baya daga dukkan haramtattun ayyukanku.7Domin duk wanda yake daga gidan Isra'ila da duk wanda ke cikin bãƙin da ke zaune a Isra'ila da suka rabu da ni, wanda ke ɗauke da gumaka cikin zuciyarsa ya sa abin tuntuɓe na zunubansa a furkarsa, kuma ya zo gun annabi ya roƙe ni - Ni, Yahweh, zan amsa masa da kaina.8Saboda haka zan sa fuskata gãba da mutumin nan in maida shi alama da karin magana, gama zan yanke shi daga tsakiyar mutanena, kuma za ku sani cewa Ni ne Yahweh.9Idan a ka ruɗi annabi ya faɗi sãƙo, daga nan Ni, Yahweh, zan ruɗi annabin nan; Zan miƙa hannuna gãba da shi kuma in hallaka shi daga tsakiyar mutanena Isra'ila.10Za su ɗauki laifofinsu; laifin annabi zai zama dai-dai da laifin wanda ke zuwa nema daga gare shi.11Saboda wannan, gidan Isra'ila ba zai ƙara bijirewa ba daga bi na ko su ƙazamtar da kansu ta wurin bin dukkan laifofinsu. Za su zama mutanena, Ni kuma zan zama Allahnsu - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne,"'12Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,13"Ɗan mutum, Idan ƙasa ta yi zunubi gãba da ni ta aikata laifi har Na fitar da hannuna gãba da ita na karya sandar gurasarta, kuma Na aiko yunwa a kanta kuma na datse mutum da dabba daga ƙasar;14to ko mutanen nan guda uku - Nuhu da Daniyel da Ayuba - suna cikin tsakiyar ƙasar, za su dai iya ceton ransu ne kawai ta ayyukansu na adalci - wannan furcin Yahweh ne.15Idan na aiko miyagun bisashe ta ƙasar na maida ita bakarariya saboda ta zama kufai inda ba mutum da zai iya wucewa saboda bisashen,16daga nan ko waɗannan mutum ukun kuma na ciki - Muddin ina raye, furcin Ubangiji Yahweh - ba za su iya su ceto ko da "ya'yansu maza ko mata ba; Rayukansu ƙadai za su iya cetowa, amma ƙasar za ta zama watsattsiya.17Ko idan na kawo takobi gãba da ƙasar na ce, 'Takobi, je ta cikin ƙasar ki datse mutum da dabba daga cikinta,18daga nan ko waɗannan mutane ukun suna tsakiyar ƙasar- muddin Ina raye, furcin Ubangiji Yahweh - ba za su iya su ceto ko da ma 'ya'yansu maza ko mata ba; rayukansu ƙaɗai za su iya cetowa.19Ko idan na aiko da annoba gãba da ƙasar nan kuma na zubo fushina gãba da ita ta wurin zubda jini, saboda in datse mutum da bisã,20daga nan ko da Nuhu da Daniyel da Ayuba na cikin ƙasar - muddin ina raye, furcin Ubangiji Yahweh - Ba za su iya su ceto ko da ma 'ya'yansu maza da mata ba; rayukansu ne kawai za su iya cetowa ta wurin ayyukan adalcinsu.21Gama Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Zan maida abubuwa su fi haka ɓaci tabbas ta wurin aikowa da hukuntaina - yunwa da takobi da namomin jeji, da annoba - gãba da Yerusalem domin in datse mutum da bisã daga cikinta.22Duba! duk da haka, Za a bar ragowa a cikinta, waɗanda suka rayu da za su fito da 'ya'ya maza da mata. Duba Za su fita zuwa wurinku, kuma za ku ga hanyoyinsu da ayyukansu sai ku ƙarfafa game da horon da Na aiko a Yerusalem, da a kan komai da na aiko gãba da ƙasar.23Waɗanda suka rayu za su ta'azantar da ke sa'ad da kika ga hanyoyinsu da ayyukansu, saboda ku san dukkan waɗannnan abubuwan da na yi gãba da ita, cewa ban yi su a banza ba! wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."
Yahweh yayi magana game da dattawan da suka ba da kansu ga bautar gumaka kamar dai dattawan sun "ɗauki gumakansu a cikin zukatansu." AT: "sun ɗauki ga gumaka"
Yahweh yayi magana akan gumakan da dattawa ke bautawa kamar dai sune tubalan da dattawa suka yi tuntuɓe a kansu, da kuma ƙuduri aniyar bautar gumakan kamar suna sanya waɗannan abubuwan tuntuɓe a gaban fuskokinsu. AT: "sun kuduri aniyar bautar abubuwan da ke haifar da mummunan aiki"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) gumaka wani abin tuntuɓe ne da ke kaiwa ga dattawa mugunta ko 2) bautar gumaka laifi ne da ke sa dattawa tuntuɓe.
Yahweh yayi magana akan mutanen da suka sadaukar da kansu ga bautar gumaka kamar sun dauki gumakan cikin zukatansu. Duba yadda kuka fassara wannan kwatancin a cikin Ezekiyel 14: 3. AT: "wanda ya keɓe kansa ga gumaka"
Yahweh yayi magana akan gumakan da mutane suke bautawa kamar su tubalan da mutane suka yi tuntuɓe akansu, da kuma ƙudurin bauta wa gumakan kamar suna sanya waɗannan abubuwan tuntuɓe a gaban fuskokinsu. Duba yadda kuka fassara wannan kwatancin a cikin Ezekiyel 14: 3. AT: "wanda ya yanke shawarar bauta wa abubuwan da ke haifar da aikata mugunta"
Anan kalmar "zukata" tana wakiltar tunani da soyayyar mutane. Yahweh yayi magana game da sa su sake ba da kai gare shi kamar dai zai kama zukatansu. AT: "Zan sa mutanen Isra'ila su sake sadaukar da kai gare ni"
Duk waɗannan jimloli guda biyu hanyoyi ne da za a gaya wa Isra'ilawa su daina bautar gumaka.
A nan kalmar "alama" tana nufin wani abu da ke isar da gargaɗi na musamman ga waɗanda suka gani. Kalmar karin magana tana nufin abin da mutane za su ce game da wannan alamar idan suka gan ta. AT: "Zan sanya mutumin ya zama abin gargaɗi da karin magana"
Hannun Allah yana nufin abin da yake yi. AT: "Zan yi aiki a kansa"
Wannan karin magana ne da ake amfani da shi don gabatar da wani abu da Allah ya faɗa wa annabawansa ko mutanensa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kawai sun iya ceton rayukansu"
Yahweh yana maganar kashe mutane da dabbobi kamar yana yankan su ne, kamar mutum zai sare reshe daga itace. AT: "ku kashe mutum da dabba"
Kalmar "ta" na nufin Yerusalem.
Yahweh ya ci gaba da magana da Ezekiyel game da horon Isra'ilawa.
Duk waɗannan kalmomin suna nuni ga abin da mutanen Isra'ila suka yi. AT: "yadda suke rayuwa" ko "abubuwan da suke yi"
1Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, yaya kuringar inabi ta fi kowanne itace mai rassa da ke kurmi kyau?3Mutane na ɗaukar katako daga kuringar inabi su yi wani abu da shi? Ko kuwa su yi maratayi daga gare ta su rataya wani abu a kai?4Duba! Idan aka jefa ta cikin wuta kuma idan wutar ta ƙone dukka sassa biyu na ƙarshenta da kuma na tsakiya, za a iya yin wani amfani?5Duba! Sa'ad da ta kai ƙarshe, ba za ta iya yin komai ba; tabbas, sa'ad da wutar ta ƙona ta, to ba za ta yi wani abin amfani ba.6Domin haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ba kamar itatuwan dazuzzuka ba, Na ba da kuringar inabi ta zama abin ƙonawa ga wuta; Kamar haka zan yi ga mazaunan Yerusalem.7Gama zan sa fuskata gãba da su. koda yake sun fito daga wutar, duk da haka wutar ba za ta cinye su ba; da haka za ku sani cewa Ni ne Yahweh, sa'ad da na sa fuskata gãba da su.8Sa'an nan zan maida ƙasar watsattsen kufai domin sun aikata zunubi - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."
Yahweh yayi wannan tambaya don tunatar da Ezekiyel wani abu da ya riga ya sani. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Itacen inabi bai fi kowane itacen da yake da rassa ba wanda ke cikin bishiyoyi a cikin daji."
Yahweh yayi wannan tambaya don tunatar da Ezekiyel wani abu da ya riga ya sani. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Mutane ba sa ɗaukar itace daga itacen inabi don yin komai."
Yahweh ya ci gaba da magana game da itacen inabi.
Yahweh yayi magana da Ezekiyel game da Isra'ilawa.
"sun ba da zunubi"
1Maganar Yahweh ta zo mani, cewa,2"Ɗan mutum, ka sanar da Yerusalem game da haramtattun ayyukanta,3ka kuma furta, 'Ubangiji Yahweh faɗi wannan ga Yerusalem: Farkonki da haihuwarki sun faru a ƙasar Kan'ana ne; Mahaifinki Ba'amore ne, mahaifiyarki Bahitiya ce.4A ranar haihuwarki, mahaifiyarki bata yanke cibiyarki ba, balle ta tsabtace ki a ruwa ko ta shafe ki da gishiri, ko ta rufe ki da tsumma.5Babu idon da ya tausaya maki ya yi wani abu daga cikin waɗannan domin ki, ya ji tausayinki. Aranar da aka haife ki, domin ƙin jininki, an jefa ki waje a fili.6Amma na bi ta wurinki, kuma na ga kina motsi cikin jininki; sai Na ce da ke a cikin jininki, "Ki rayu!" Na ce da ke a cikin jininki, "Ki rayu!"7Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yawaita kin kuma zama da girma, kika zama abin ƙauna sosai kuma kin kai ga sa kayan ado. Nonnanki sun tsaya tantsan-tantsan, kuma gashin kanki ya yi kauri, koda shi ke ki na tsirara tumɓur.8Na bi ta wurin da kike kuma, na kuma gan ki. Duba! lokacin ƙauna ya zo maki, sai na rufe ki da bargo na rufe tsiraicinki. sa'an nan na yi maki rantsuwa na kawo ki ga alƙawari - kika kuma zama tawa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.9Sai na wanke ki da ruwa, na kuma wanke ki daga jini, sai na shafe ki da mai.10Na suturta ki da ɗinkakken tufafi na sa maki takalman fãta a ƙafafunki. Na naɗe ki da linin mai kyau na rufe ki da silki.11Biye da haka na yi maki ado da sarƙoƙi masu daraja, sai na sa maki sarƙar hannu, da sarƙa kewaye da wuyanki.12Na sa zoben hanci a hancinki, da 'yan kunne a kunnuwanki, da kambi a kanki.13Saboda haka an yi maki ado da zinariya da azurfa, kuma an suturta ki da linin mai kyau da silki da ɗinkakkun kaya; kin ci gari mai kyau da zuma da mai, kuma kika zama kyakkyawa, sai kika zama sarauniya.14Shahararki ta kai ga al'ummai saboda kyaunki, gama cikakkiya ce a cikin darajar da na ba ki - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.15Amma kin dogara ga kyaunki, kuma kin yi kamar karuwa saboda shahararki; kin zubo ayyukan karuwancinki ga duk wanda ke wucewa, saboda kyaunki ya zama nasa.16Sa'an nan kika ɗauki tufafinki kuma da su kika yiwa kanki masujadai masu ado da launuka daban-daban, a wurin kuma kika yi kamar karuwa. Bai kamata hakan ya faru ba. ko irin wannan abin ya kasance.17Kin ɗauki kyawawan kayan adonki na zinariya da azurfa da na ba ki, sai kika yiwa kanki siffofin mazaje, sai ki ka yi da su kamar yadda karuwa ke yi.18Kika ɗauki tufafinki da a ka yi aikin ɗinki mai kyau kika rufe su, sai kika ajiye maina da turarena a gabansu.19Gurasata na ba ki - wanda aka yi da lallausan gari da maida zuma - kin ajiye su domin kamshi mai daɗi, gama abin da ya faru kenan - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.20Sa'an nan kuka ɗauki 'ya'yanku maza da mata da kuka haifa mani, kuka kuma yi hadaya da su ga siffofin domin su lanƙwame kamar abinci. Ayyukan karuwancinku ƙaramin abu ne?21Kun yanka 'ya'yana kuka sa su a cikin wutar.22A cikin dukkan abin ƙyamarku da ayyukan karuwancinku ba ku yi tunani a kan kwanakin kuruciyarku ba, a sa'ad da kuke tsirara tumɓur sa'ad da kuke birgima cikin jininku.23Kaito! Kaitonki! - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - saboda haka, a kan dukkan wannan muguntar,24kin gina wa kanki sãƙon tsafi a kowanne wurin taruwar jama'a.25Ki ka gina wurin tsafi a kan kowacce hanya kuma kin wulaƙanta kyaunki, gama kin bada kanki ga kowanne mai wucewa kuma kika ƙara yin ayyukan karuwanci.26Kika yi kamar karuwa tare da Masarawa, makwabtanki masu sha'awace-sha'awace, kika kuma aikata ayyukan karuwanci da yawa, ki na ta sani fushi.27Duba! Zan cake ki da hannuna in yanke abincinki. Zan miƙa ranki ga maƙiyanki, 'yan matan Filistiyawa, waɗanda suka ji kunyar halinki na lalata.28Kin yi kamar karuwa tare da Asiriyawa saboda ba ki ƙoshi ba. Ki ka yi kamar karuwa amma dai ba ki ƙoshi ba.29Kin ƙara aikata ayyukan karuwanci da yawa a ƙasar attajiran Kaldiya, kuma ko wannan ma bai ƙosar da ke ba.30Yaya ciwon zuciyarki yake - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - cewa za ki yi dukkan waɗannan abubuwan, ayyukan bankunya na karuwanci?31Kin gina wurin tsafinki a kan dukkan tituna kuma ki ka sa sãƙon tsafinki a dukkan wurin taruwar jama'a. Duk da haka ke ba kamar karuwa ba ce saboda kin ƙi karbar biya.32Ke mazinaciyar mace, kin amince da kwartaye a maimakon mijinki.33Mutane na biyan kowacce karuwa, amma ke kina bada ladarki ga dukkan masoyanki kina kuma ba su cin hanci su zo wurin ki daga ko'ina domin ayyukan karuwancinki.34Saboda haka akwai bambanci tsakaninki da waɗancan matayen, tun da ba mai zuwa wurinki ya sa ki kwana da shi, a maimakon haka kina biyan su. Babu mai biyan ki.35Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Yahweh.36Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Saboda kin zubo sha'awace-sha'awacenki waje kika kuma buɗe tsiraicinki ta wurin ayyukan karuwanci da dukkan masoyanki da dukkan ƙazaman gumakanki, kuma saboda jinin 'ya'yanki da kika miƙawa gumakanki,37saboda haka, Duba! Zan tara dukkan masoyanki da kika sadu da su, dukkan waanda kike so da waɗanda kike ƙi, kuma zan tara su gãba da ke a ko'ina. Zan fallasa tsiraicinki wurinsu domin su ga dukkan tsiraicinki.38Gama zan hukunta ki saboda zina da zubda jini, kuma zan kawo maki zubda jinin fushina da shauƙi.39Zan bada ke a hannunsu saboda su jefar da sãƙon tsafiinki ƙasa su kuma rurrushe wuraren tsafinki su kuma tuɓe maki tufafinki su ɗauki dukkan kayan adonki. Za su bar ki tsirara tumɓur.40Sa'an nan za su tara maki jama'a gãba da ke su jejjefeki da duwatsu, kuma su daddatsa ki da takkubansu.41Za su ƙone gidajenki su yi abubuwan hukuntawa da yawa a kanki a gaban mata da yawa, gama zan tsayar da karuwancinki, ba za ki kuma biya masoyanki ba.42Sa'an nan ne zan kwantar da fushina a kanki; fushina zai bar ki, gama zan gãmsu, kuma ba zan ƙara yin fushi ba.43Saboda ba ki tuna da kwanakin kuruciyarki ba kuma kin sa na girgiza da fushi saboda dukkan waɗannan abubuwan, Domin haka, Duba! Ni kaina zan aiko hukunci a kanki domin abin da kika yi - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne. Ba za ki ƙara karuwanci da dukkan sauran kazamtattun ayyukanki ba?44Duba! Duk mai faɗin karin magana game da ke zai ce, "Kamar yadda uwa take, haka ma 'yarta take."45Ke ɗiyar mahaifiyarki ce, wadda ta ƙi mijinta da 'ya'yanta, kuma ke 'yar'uwar 'yan'uwanki ne waɗanda suka ƙi mazajensu da 'ya'yansu. Mahaifiyarki Bahitiya ce, kuma mahaifinki Ba'amore ne.46Yãyarki Samariya ce 'ya'yanta mata kuma su ne ke zama a Arewa, ƙanwarki kuma ita ce wadda ke zama a kudu da ke, wato Sodom da 'ya'yanta mata.47Ba tafiya a hanyarsu da bin halayensu da ayyukansu kawai kika yi ba, amma a dukkan hanyoyinki kin zama fiye da yadda suke.48Da dawwamata - wannan furcin Yahweh ne - Yar'uwarki Sodom da 'ya'yanta mata, ba su yi yawan mugunta kamar yadda ke da 'ya'yanki mata suka yi ba.49Duba! Wannan ne zunubin 'yar'uwarki Sodom: ta na da kumbura kai a cikin wadataccen jin daɗi da zaman sangarcewa da rashin kulawa da komai. Ba ta ƙarfafa hannun talakawa da masu buƙata ba.50Ta zama mai kumbura kai da aikata ayyukan ƙyama a gabana, saboda haka na ɗauke su kamar yadda kuka gani.51Ko Samariya bata aikata rabin zunubanki ba; maimakon haka ma, kin yi ayyukan ƙyama da yawa fiye da yadda suka yi, kuma kin nuna cewa 'yan'uwanki sun fi ki kirki saboda dukkan abubuwan ƙyama da kika yi!52Ke musamman, kin nuna kunyar kanki; a wannan hanyar kin nuna cewa 'yan'uwanki sun fi ki kyau, saboda laifofin da kika aikata a dukkan hanyoyin banƙyaman nan. 'Yan'uwanki yanzu sun nuna alamar fin ki kyau. Ke musamman, kin nuna kunyar kanki, gama a wannan hanyar kin nuna cewa 'yan'uwanki sun fi ki kyau.53Gama zan komo da wadatarsu - wadatar Sodom da'ya'yanta da wadatar Samariya da 'ya'yanta; amma wadatarki zata kasance a cikinsu.54A game da waɗannan abubuwan kuwa za ki nuna kunyarki; za a wulaƙanta ki saboda dukkan abubuwan da kika yi, kuma a sa'an nan ne za ki zama mai ta'azantarwa a gare su.55Saboda haka 'yar'uwanki Sodom da 'ya'yanta mata za a komo da su kamar yarda suke a dã. Samariya kuma da 'ya'yanta mata za a komo masu da matsayinsu na dã.56Ba ki ambato 'yar'uwarki Sodom da bakin ki ba a kwanakin da kike fahariya.57kafin muguntarki ta bayyanu. Amma yanzu kin zama abar zargi ga 'ya'ya mata na Idom da kuma dukkan 'ya'ya mata na Filistiyawa kewaye da ita. Dukkan mutanen da ke kewaye na raina ki.58Za ki nuna kunyarki da aikin banƙyamarki! wannan furcin Yahweh ne!59Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Zan yi da ke yadda kika cancanta, ke da kika raina rantsuwarki ta wurin karya alƙawari.60Amma ni da kaina zan tuna da alƙawarin da na yi da ke a kwanakin kuruciyarki, kuma zan kafa madawamin alƙawari da ke.61Sa'an nan ne za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya a sa'ad da kika ƙarɓi yãyarki da ƙanwarki. Zan ba ki su a matsayin 'ya'yanki mata, amma ba saboda alƙawarinki ba62Ni da kaina zan ƙulla alƙawarina da ke, kuma za ki san cewa ni ne Yahweh.63Saboda waɗannan abubuwan, za ki tuna da komai ki kuma ji kunya, saboda haka ba za ki sake buɗe bakinki ki yi magana ba saboda kunya, sa'ad da na gafarce ki a kan dukkan abin da kika yi - wannan furcin Yahweh ne."'
A cikin wannan sura, Yahweh yayi magana game da Yerusalem kamar dai birni amarya ce mai cin amana. Ya bayyana girmanta tun daga yarinta har zuwa girmanta. Garin yana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna da ma'anoni iri ɗaya. Yahweh yana maganar lokacin da mutane suka kafa garin kamar dai shine asalin garin.
Yahweh ya ci gaba da magana game da Yerusalem kamar dai birni ne jariri. Garin yana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin. (Duba:
Anan kalmar "ido" tana wakiltar mutumin da ya gani. AT: "Babu wanda ya gan ku da ya tausaya muku"
"saboda iyayenku sun ƙi ku"
Yahweh ya ci gaba da magana game da Urushalima kamar dai birni ne jariri. Garin yana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin.
Anan ana maganar mace, wanda ke wakiltar Yerusalem, kamar ta zama mafi kyau a cikin duk adon lu'ulu'u, ma'ana, kamar dai ta zama mafi kyawun duka mata.
Yahweh ya ci gaba da magana game da Yerusalem kamar dai birni ne budurwa. Garin yana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin.
Wannan yana nufin cewa Yahweh yana ganin yarinyar ta isa aure.
Yahweh ya ci gaba da magana game da Yerusalem kamar dai birni ne budurwa. Garin yana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin.
"Na sanya maka kayan ado"
Yahweh ya ci gaba da magana game da Yerusalem kamar dai birni ne budurwa. Garin yana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin.
"kin sanya dogaro ga kyanki"
Yahweh yayi magana game da Yerusalem kamar dai birni mace ce marar aminci wacce ke kwanciya da wasu maza don amsar kuɗi.
Yahweh ya ci gaba da yin magana game da Yerusalem kamar dai garin ya zama matarsa marar aminci.
Yahweh ya ci gaba da yin magana game da Yerusalem kamar dai garin ya zama matarsa marar aminci.
Yahweh yayi wannan tambayar don ya nanata cewa matar tana yin kamar karuwancinta bai isa sosai ba don haka ta yanke shawarar sadaukar da yaranta kuma. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Dole ne ku yi tunanin cewa ayyukan karuwanci ƙaramin al'amari ne." ko "Bana tsammanin ayyukan karuwancinku ba ƙaramin al'amari bane."
Mai yiwuwa ma'anoni su ne cewa ta gina wani wuri inda 1) za ta iya bautar gumakanta ko 2) ta iya yin karuwancinta.
Yahweh ya ci gaba da yin magana game da Yerusalem kamar dai garin ya zama matarsa marar aminci.
Anan "hannu" yana wakiltar iko. AT: "Zan yi amfani da ƙarfina don buge ku"
Anan “rai” yana wakiltar mutum. AT: "Zan bashe ku"
Yahweh yayi tambaya mai ma'ana domin ya tsauta wa Yerusalem. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Dole zuciyarku ta kasance da rashin lafiya ... da za ku aikata duk waɗannan abubuwa, ayyukan karuwan mara kunya!"
Yahweh ya ci gaba da yin magana game da Yerusalem kamar dai garin ya zama matarsa marar aminci.
Yahweh ya ci gaba da yin magana game da Yerusalem kamar dai garin ya zama matarsa marar aminci.
Wannan yana nufin kashe yara a matsayin yanka ga gumaka.
Mai yiwuwa ma'anoni su ne: 1) wurin da ta bauta wa gumakanta ko 2) wurin da ta yi karuwancinta.
Yahweh ya ci gaba da yin magana game da Yerusalem kamar dai garin ya zama matarsa marar aminci. Ya yi maganar sojojin abokan gaba kamar masoyinta.
Kalmar "fushi"na nuni ga horon da Yahweh yake yi saboda yana fushi. Kalmomin guda biyu ma'anar abu ɗaya ne. AT: "Zan daina hukunta ku saboda ba zan ƙara yin fushi da ku ba"
AT: "Zan hukunta ku saboda abin da kuka aikata"
"wacce ta tsani mijinta"
Waɗannan sunayen birane ne.
Ana magana akan yadda mutum yake rayuwa kamar mutum yana tafiya akan hanya. AT: "Ba ku kawai kuka yi kamar su ba"
Yahweh ya bayyana Sodom a matsayin mace mai arziki wacce take da isasshen abinci kuma take rayuwa cikin tsaro.
Yahweh yayi amfani da wannan kalmar sau uku don jaddada cewa mugayen biranen Samariya da Sodom sun fi Yerusalem adalci.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan wulakanta ku"
Anan kalmar "baki" tana wakiltar mutumin da yayi magana. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Ba ku ma ambaci 'yar uwarku Saduma ba"
Wannan yana nufin Yerusalem azaman abin da mutane suke magana da mummunar magana a kansa.
Yerusalem ta karya alkawarin aurenta da Yahweh, wanda hakan ya nuna cewa ba ta damu da rantsuwar da ta yi masa ba. AT: "kin raina rantsuwar da kuka yi mani ta hanyar karya alkawarin da kuka yi da ni"
Yahweh ya ci gaba da yin magana game da Yerusalem kamar dai garin ya zama matarsa marar aminci. Garin yana wakiltar mutanen da suke zaune a wurin.
Wannan karin magana yana nufin tunawa. AT: "ku tuna komai"
Wannan yana nufin cewa Yerusalem za ta ji kunya sosai don yin magana.
1Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, faɗi kacici-kacici da kuma misali ga mutanen Isra'ila.3Ka ce, 'Ubangiji Yahweh ne ya faɗi wannan: Wani babban gaggafa mai manyan fikafikai da dogayen gasusuwan fikafikai da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ya je Lebanon ya kama saman kan itacen sida.4Ya karya kan tohonsa mafi tsawo ya ɗauko su zuwa ƙasar Kan'ana; ya shuka su a birnin fatake.5Sai kuma ya ɗauki wani iri na ƙasar ya dasa shi a wuri mai dausayi kusa da ruwa mai yawa kamar itacen warɗi.6Sai ya yi toho ya zama kuringa mai yaɗuwa har ƙasa. Rassansa suka tanƙwasa wajensa, saiwoyinsa suka kama ƙasa sosai. Domin haka ya zama kuringa ya yi rassa da toho.7Amma akwai wani babban gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Sai wannan kuringa ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen gaggafan, ta kuma miƙe rassanta zuwa wajensa tun daga inda aka dasa ta domin ya rika yi ma ta ban ruwa.8An dasa ta a wuri mai kyau da danshi inda akwai ruwa da yawa domin ta yi rassa ta kuma ba da 'ya'ya, ta zama kuringar inabi ta ƙwarai.'9Ka cewa mutanen, 'Ubangiji Yahweh ne ya faɗi wannan: Ko za ta wadatu? Ba za a iya cire ta a kuma ɗebe 'ya'yanta domin kada su yi yaushi, kuma dukkan ganyayenta masu kyau su yanƙwane ba? Babu wani abu ko mutane masu yawa da a ke buƙata da su cire ta daga jijiyoyinta.10To duba! bayan an sake dasa ta, za ta sake yin girma? Ba za ta yanƙwane ba idan iskar gabas ta hura ta? Babu shakka za ta yanƙwane ga baki ɗaya daga tushenta.'"11Sai maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,12"Ka yi magana da 'yan tawayen gidan, 'Ba ku san mene ne waɗannan abubuwa ke nufi ba? Duba! Sarkin Babila ya zo Yerusalem ya kuma tafi da sarkinta da yarimanta ya kai su zuwa gare shi Babila.13Sai ya ɗauki wani daga zuriyar sarauta, ya yi alƙawari da shi, ya kuma ɗauki rantsuwa da shi. Ya ɗauke mutane na ƙasar masu iko,14domin mulkin ya zama da rauni har ƙasar ta kasa ɗaga kanta. Ta wurin kiyayye alƙawarinsa ƙasar za ta tsira.15Amma sarkinYerusalem ya yi masa tawaye ta wurin aikawa da jakadai zuwa Masar domin a ba shi dawakai da sojoji. To, zai yi nasara? Wanda ya yi irin waɗannan abubuwa zai tsira? Idan ya karya alƙawari, zai iya tsira?16Da dawwamata -wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - babu shakka zai mutu a cikin ƙasar sarki wanda ya naɗa shi sarauta, sarkin da ya rena rantsuwarsa, wanda kuma ya karya alƙawarinsa. Zai mutu a tsakiyar Babila.17Fir'auna da sojojinsa masu ƙarfin yaƙi da kuma jama'arsa masu yawa domin yaƙi ba za su tsare shi ba a wannan yaƙin, sa'ad da Babilawa suka gina hasumiyoyi da kagarai don su kashe rayuka masu yawa.18Gama sarkin bai cika rantsuwar alƙawarinsa ba. Duba ya miƙa hannunsa ga yin alƙawari duk da haka ya aikata dukkan waɗannan abubuwa. Ba zai kuɓuta ba.19Domin haka ni Ubangiji Yahweh na faɗi wannan: Da dawwamata, ba rantsuwata da alƙawarina ya rena ya kuma karya ba? Saboda ha ka zan ɗora hukuncinsa a kansa!20Zan kafa masa tarko in kama shi, kuma za a kama shi a tarkon farautata. Sa'an nan zan kai shi Babila inda zan yi masa shari'a saboda cin amana da kuma tayawar da ya yi mani!21Dukkan 'yan gudun hijira cikin sojojinsa za a kashe su da takobi, sauran da suka ragu za a watsar da su ko'ina. A sa'an nan ne za su sani cewa Ni ne Yahweh; Na furta wannan zai faru."22Ubangjji Yahweh ya faɗi wannan, 'Saboda haka ni kaina zan cire toho a kan itacen sida mai tsawo, zan kuma sake dasa shi daga sashen jikin rassansa. Zan karye shi, ni da kaina kuma zan dasa shi a tsauni mai tsayi.23Zan dasa shi a kan tsaunukan Isra'ila domin ya fito da rassa, ya bada 'ya'ya, ya kuma zama itacen sida na gaske saboda kowanne tsuntsu mai fiffike ya zauna a ƙarƙashinsa. Za su yi sheƙa a cikin inuwar rassansa.24Sa'an nan dukkan itatuwan jeji za su sani cewa Ni ne Yahweh. Na kan kawo manyan itatuwa ƙasa sa'an nan in tada ƙananan itatuwa sama. Zan sa ɗanyen itace ya bushe in kuma sa busashen itace ya zama ɗanye. Ni ne Yahweh, Na furta wannan zai faru; na kuma yi shi.
Ezekiyel ya ba da saƙo da Allah ya ba shi.
"ba su wuyar warwarewa don tunani" ko "ba da labarin wannan a matsayin misali"
"ya dasa shi a garin da ke da fatake da yawa." Dan kasuwa shine mutumin da yake siyar da abubuwa.
"mikiya ta dasa iri a wurin da ake da ruwa da yawa"
"Sai iri ya fara girma ya zama shuka"
"Haka itacen inabin ya girma"
Yahweh yayi magana akan itacen inabi kamar tana iya yin halin mutum kuma da gangan ya juya saiwoyinsa zuwa ɗaya gaggafa don karɓar abinci daga gare ta. AT: "Tushen itacen inabi ya girma zuwa gaggafa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "daga wurin da gaggafa ta farko ta dasa ta domin ta sami ruwa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mikiya ta farko ta dasa inabi"
Yahweh yayi wannan a matsayin babbar tambaya don jaddada amsar mara kyau. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Ba zai ci gaba ba."
Yahweh yayi wannan tambaya ta lafazi don jaddada cewa lallai hakan zai faru. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Zai bushe lokacin da iskar gabas ta taɓa shi."
Yahweh yayi wannan a matsayin babbar tambaya domin bayar da amsar. Ana iya fassara tambayar a matsayin sanarwa. AT: "Wannan shine ma'anar waɗannan abubuwan."
Yahweh yayi magana game da sarkin Yerusalem wanda ya tayar wa sarkin Babila.
Yahweh yayi wannan tambaya mai mahimmanci don jaddada amsar mara kyau. Ana iya fassara wannan azaman bayani. AT: "Wanda ke yin waɗannan abubuwa ba zai tsere ba."
Yahweh yana magana game da sarkin Yerusalem.
Waɗannan jimlolin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna ƙarfafa yadda ƙarfin Fir'auna yake da ƙarfi.
Wannan yana nufin rike hannun wani a matsayin alamar abota da yarjejeniya. A nan yana wakiltar rantsuwar alkawarin da ya yi da sarkin Babila.
Yahweh yayi wannan babbar tambaya don jaddada amsar tabbatacciya. Ana iya fassara wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "rantsuwata ce cewa sarkin Kudus ya raina kuma alkawarina ya karya."
Kalmomin "kawo ... a kansa" yana nufin cewa zai dandana wannan hukuncin. Duba yadda kuka fassara wannan karin magana a cikin Ezekiyel 11:21. AT: "Zan sa shi shan hukuncinsa"
Yahweh ya ci gaba da misalin da ya faɗa a cikin Ezekiyel 17: 1 kuma yayi magana game da Yerusalem kamar dai reshe ne wanda ya shuka a kan duwatsun Isra’ila.
Yahweh yana magana akan bishiyoyi kamar dai mutane ne da zasu iya saninsa. Itatuwan suna wakiltar al'ummomi da mutanen da ke zaune a cikinsu.
1Maganar Yahweh ta sake zuwa gare ni, cewa,2"Me kuke nufi, ku da kuka yi amfani da wannan karin magana a kan ƙasar Isra'ila cewa, 'Mahaifa sun ci 'ya'yan inabi masu tsami, hakoran 'ya'yansu kuma sun dakushe'?3Da dawwamata - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - ba za a ƙara samun wani dalili da za ka sake amfani da wannan karin magana a Isra'ila ba.4Ga shi! Kowanne rai nawa ne - ran mahaifi duk da na ɗan, dukka nawa ne! Wanda ya yi zunubi shi zai mutu!5Me za a ce a kan mutum wanda yake shi adali ne yana kuma aikata shari'a da adalci--6idan ba ya cin abinci a kan tsaunuka ko ya sa idanunsa a kan allolin da ke gidan Isra'ila, bai kuma kwana da matar maƙwabcinsa ba, ko ya Kwana da mace a lokacin hailarta, wannn mutum adali ne?7Me za a ce a kan mutum wanda ba ya ƙuntatawa kowa, wanda yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa, wanda ba ya ƙwace amma ya kan bada abinci ga mayunwanci, yakan ba huntu tufa, wannan mutum adali ne?8Me za a ce da mutumin da ba ya bada bashin kuɗi da ruwa; ko tare da wani ƙari a kan abin da ya sayar? Haka yake ce da shi yana goyon bayan gaskiya a tsakanin masu gaskiya, yana kuma tabbatar da adalci a tsakanin mutane.9Amma idan mutumin yana tafiya cikin farillaina yana kuma bin ka'idodina da gaskiya, daga nan alƙawarin wannan mutum mai adalci shi ne: hakika zai rayu! - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.10Amma da a ce yana da ɗa wanda ya zama ɗan fashi mai kisankai yana kuma yin waɗannan abubuwa masu yawa kamar yadda a ka nuna su a nan,11koda mahaifinsa ba ya yin ɗaya daga waɗannan abubuwa, amma yana cin abinci a kan tsaunuka ya kuma kwana da matar maƙwabcinsa, me za a ce game da shi?12Wannan mutum yana cin zalin matalauta da masu buƙata, yana kuma yin ƙwace da fashi, ba ya mayar da abin da a ka jinginar masa, yana bautawa gumaka yana kuma aikata abubuwa masu banƙyama,13yana bada rancen kuɗi da ruwa, yana cin riba ta fitar hankali a kan abin da ya sayar, shin wannan mutum zai rayu? Babu shakka ba zai tsira ba! Lallai ne zai mutu kuma alhakin jininsa yana a kansa domin ya yi munanan abubuwa.14Amma idan akwai mutum da ya haifi ɗa, kuma ɗan nasa ya ga dukkan zunuban nan da mahaifinsa ya yi, koda ya gan su, amma shi bai yi waɗannan abubuwa ba.15Wannan ɗa bai ci abinci a kan tsaunuka ba, bai kuma sa idanunsa ga gumakan gidan Isra'ila ba, bai kwana da matar maƙwabcinsa ba, me za a ce game da shi?16Wannan ɗa bai ci zalin kowa ba, ko ya ƙarbi jingina, ko ya saci wasu abubuwa, amma a maimakon haka yana bada abincinsa ga mayunwaci, yana ba huntu tufafi.17Wannan ɗan ba ya zaluntar kowa ko ya bada bashi da ruwa ko kuma ya ci ƙazamar riba a kan bashin, amma yana bin ka'idodina, yana kuma tafiya bisa ga farillaina; wannan ɗa ba zai mutu ba saboda zunubin mahaifinsa: Lallai za ya rayu.18Mahaifinsa kuwa, da yake ya ƙuntatawa wasu ta wurin zaluntarsu, ya yiwa ɗan'uwansa ƙwace, ya kuma aikata abubuwa marasa kyau a cikin mutanensa - zai mutu saboda muguntarsa.19Amma kun ce, 'Me ya sa ɗa ba zai ɗauki laifin mahaifinsa ba?' Domin ɗan ya bi shari'a da adalci kuma ya bi dukkan umarnaina; ya yi su dai-dai. Babu shakka za ya rayu!20Shi wanda ya yi zunubi, shi ne wanda zai mutu. Ɗa ba zai ɗauki laifin mahaifinsa ba, haka nan mahaifi ba zai ɗauki laifin ɗansa ba. Adalcin wanda ya yi dai-dai ai nasa ne, muguntar azzalumi zata kasance a kansa.21Amma idan mugu ya juya daga dukkan zunubansa wanda ya aikata ya kiyaye umarnaina ya bi shari'a da adalci, lallai za ya rayu ba zai mutu ba.22Dukkan muguntar da ya aikata ba za a neme su a kansa ba. Zai rayu saboda adalcin da ya yi.23Ina murna da mutuwar mugu ne - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - ba juyowa daga muguwar hanyarsa ba domin ya rayu?24Amma idan adalin mutum ya bar yin adalcinsa, ya aikata haramtattun ayyuka kamar dukkan haramtattun ayyuka waɗanda wannan mugun mutum ya aikata, daga nan sai ya rayu? Dukkan adalcin da ya aikata ba za a tuna da su ba idan ya ci amanata da laifin da ya aikata. To zai mutu a cikin zunuban da ya aikata.25Amma kun ce, 'Hanyar Ubangiji ba dai-dai ba ce!' Ku ji ya ku gidan Isra'ila! Hanyata ba dai-dai ba ce? Ashe ba hanyarku ce ba dai-dai ba?26Sa'ad da mutum adali ya bar adalcinsa, ya kuwa aikata mugunta zai mutu saboda su, zai mutu a cikin muguntar da ya aikata.27Amma idan mugun mutum ya bar muguntar da ya yi ya zo ya aikata gaskiya da adalci, za ya rayu.28Domin ya gani kuma ya bar dukkan laifofin da ya aikata. Babu shakka za ya rayu, ba zai mutu ba.29Amma gidan Isra'ila suka ce, 'Hanyar Ubangiji ba dai-dai ba ce! Gidan Isra'ila yãyã hanyata ta zama ba dai-dai ba? Ai hanyarku ce ba dai-dai ba.30Saboda haka zan shar'anta kowanne mutum a cikinku gwargwadon ayyukansa, ya gidan Isra'ila! - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne. Ku tuba daga dukkan muguntarku domin kada su zamar maku dalilin hallaka.31Ku rabu da dukkan laifofin da kuka aikata; ku samo wa kanku sabuwar zuciya da sabon ruhu. Me ya sa za ku mutu, gidan Isra'ila?32Gama ba na murna da mutuwar wanda ke mutuwa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - saboda haka sai ku tuba domin ku rayu!"
Yahweh yayi wannan tambaya don tunatar da Ezekiyel wani abu da ya riga ya sani. Tambayar ita ce tsawatarwa ga mutanen da ke amfani da karin maganar. AT: "Mutanen ƙasar Isra'ila suna da wannan karin magana, iyaye suna cin innabi masu tsami, kuma haƙoran yara sun zama marasa haske."
Kalmar "duba" anan tana faɗakar da mu da mu kula da bayanan ban mamaki da ke biye.
Mutane galibi suna yin sujada da miƙa hadayu ga gumakan arna a kan duwatsu. Ana nuna cewa wannan mutumin bai shiga cikin waɗannan nau'ikan ayyukan tsafin arna ba. AT: "baya cin naman da aka yanka wa gumaka a kan tsaunuka"
"Ya mayar wa wanda ya ci bashi abin da bashin ya ba shi a matsayin bashi don lamunin"
Wannan yana nuni ne ga ayyukan zunubi da Yahweh ya ambata tun a cikin Ezekiyel 18:11-12.
Yahweh ya ci gaba da magana game da ɗan tashin hankali.
Anan kalmar “jini” tana wakiltar mutuwa. Don jini ya hau kan mutum magana ce wacce ke nufin mutumin ne ke da alhakin wannan mutuwar. AT: "zai zama sanadiyyar mutuwar kansa"
Mutane galibi suna yin sujada da miƙa hadayu ga gumakan arna a kan duwatsu. Ana nuna cewa wannan mutumin bai shiga cikin waɗannan nau'ikan ayyukan tsafin arna ba. Dubi yadda kuka fassara makamancin magana a cikin Ezekiyel 18: 6. AT: "Wannan ɗan ba ya cin naman da aka yanka wa gumaka a kan tsaunuka"
Kalmomin "ɗaga idanunsa" yana nufin duban wani abu. Dangane da gumaka, wannan isharar tana wakiltar bautar ko yin addu'a ga gumaka. Dubi yadda kuka fassara makamancin magana a cikin Ezekiyel 18: 6. AT: "baya bautar gumaka" ko "baya addu'a ga gumakan"
Yahweh ya ci gaba da magana game da ɗan da ba ya yin zunubi irin na mahaifinsa.
Yahweh yayi magana akan bin dokokinsa kamar cewa dokokinsa hanya ce da mutum yake tafiya a ciki. AT: "yana bin dokokina"
Yahweh yayi magana game da mahaifin ɗa wanda bai kiyaye dokar Allah ba.
Yahweh yayi magana akan mutum wanda ke da alhakin ko ya aikata laifi kamar dai laifin wani abu ne da mutum yake ɗauka. AT: "Me yasa ɗan bai ɗauki alhakin laifin mahaifinsa ba?" ko "Me yasa ɗan bai yi laifin laifin mahaifinsa ba?"
Don adalci ya tabbata a kan mutum magana ce da ke nufin mutumin yana da alhakin wannan adalcin. AT: "Wanda ya aikata dai-dai zai ɗauki alhakin adalcinsa"
Don mugunta ta hau kan mutum magana ce da ke nufin mutumin yana da alhakin wannan mugunta. AT: "mugu ne zai ɗauki alhakin muguntarsa"
Yahweh yana magana akan mugu wanda ya canza ya aikata abin da yake dai-dai.
"saboda adalci da ya aikata"
Yahweh yayi magana game da burinsa ga mugayen mutane
Yahweh yayi wannan tambaya ta zance domin a nuna akasin haka. AT: "Ba na matuƙar farin ciki da mutuwar mugaye ... amma ina matuƙar farin ciki idan ya juya baya daga hanyarsa don ya rayu."
Yahweh ya ba da misali na mutumin da ya juya daga adalci zuwa mugunta.
"zai mutu saboda zunuban"
Waɗannan jimlolin suna maimaita tunanin mutum ya mutu saboda zunubinsa don bayyana cewa laifinsa ne kuma laifin wani ne.
Yahweh yayi magana akan mutumin da yake tunani da fahimtar wani abu kamar mutum yana ganin sa. AT: "ya yi la'akari" ko "ya fahimta"
Yahweh ya ci gaba da koya wa Isra'ilawa dalilin da ya sa tafarkinsa yake da kyau.
Ayyuka ko halaye ana maganarsu kamar suna hanya ko hanyar da mutum zai bi. AT: "Yahweh baya aiki dai-dai ... Yaya ban yi adalci ba ... Ku ne ba ku yin adalci"
Anan kalmar "zuciya" tana wakiltar so da motsin rai kuma kalmar "ruhu" tana wakiltar tunani da halaye. Yahweh yayi magana akan mutanen da suke da sababbin motsin rai da tunani kamar suna yin sabuwar zuciya da ruhu don kansu. AT: "ku samo wa kanku sabbin motsin rai da sabuwar hanyar tunani"
1"Yanzu kai, sai ka yi makoki a kan shugabanin Isra'ila2ka ce, 'Wace ce mahaifiyarka? Zakanya, tana zaune tare da ɗan zaki; a cikin tsakiyar 'yan zakoki, ta yi renon 'ya'yanta.3Ita ce ta goyi ɗaya daga cikin 'ya'yanta ya zama ɗan zaki wanda ya koyi kamun nama, har ya cinye mutane.4Sai al'ummai suka ji labarinsa. Sai aka kama shi cikin tarkonsu, suka ja shi da ƙugiyoyi zuwa ƙasar Masar.5Daga nan ta ga cewa koda yake ta jira dawowarsa, sa begenta a kansa yanzu ya ƙare, sai ta ɗauki ɗaya daga cikin 'ya'yanta, ta goye shi ya zama sagari.6Wannan sagari yana ta kai da kawowa a cikin zakoki. Ya zama sagari yana kuma koyan kamun nama; ya cinye mutane.7Ya lalatar da kagarunsu ya kuma maida biranensu kufai. ƙasar da mazaunan cikinta an bar su saboda jin rurinsa8Amma al'ummai suka kafa masa tarko daga kowanne waje; suka baza masa tarunsu a kansa. Suka kama shi cikin tarkunansu.9Suka sa masa ƙugiyoyi, sa'an nan suka kawo shi ga sarkin Babila. Suka kawo shi cikin matsaran wurare domin kada a ƙara sake jin muryarsa a kan tsaunuka Isra'ila.10Mahaifiyarka tana kamar kuringar inabi da aka dasa a cikin jininka a gefen ruwa. Ta yi 'ya'ya da rassa da yawa saboda isasshen ruwa.11Tana da rassa masu ƙarfi da a ke amfani da su domin sandunan masu mulki, tsayinta zuwa sama da dukkan rassan, ta yi tsayi sosai daga nesa ana iya hangen ganyenta.12Amma aka tumɓuke kuringar inabin da fushi aka jefar da ita a ƙasa, iskar gabas ta busar da ita. Rassanta masu ƙarfi suka kakkarye suka bushe, wuta kuwa ta cinye su.13Yanzu an dasa ta a cikin jeji, cikin busasshiyar ƙasa mai ƙishi da fari.14Sai wuta ta fito daga manyan rassanta ta kuwa cinye 'ya'yanta, babu reshe mai ƙarfi a kanta, babu sandar da zan yi mulki.' Wannan makoki ne, kumaza a raira shi a matsayin makoki."
Yahweh ya gaya wa Ezekiyel ya yi magana da Isra'ilawa. Ya ba da labari inda al'ummar Isra'ila ta kasance zakanya kuma wasu sarakunan da suka gabata a cikin mulkin Yahuda 'ya'yanta ne.
Yahweh ya ci gaba da bayyana al’ummar Isra’ila a matsayin zaki, sarakunan mulkin Yahuda kuma kamar ’ya’yansu ne.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Mutane sun yi watsi da ƙasar da cikakkiyarta"
"daga lardunan da ke kewaye da ƙasar Isra'ila"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne cewa "jini" yana wakiltar 1) tashin hankalin sarakunan Yahuza waɗanda suka kashe mutane. AT: "itacen inabi da aka dasa ta hanyar tashin hankali" ko 2) Yalwar ruwan inabin Yahuza wanda ya zama alama ta wadata. AT: "itacen inabi da aka dasa a cikin wadatar ku"
Yahweh ya ci gaba da ba da labari inda al’ummar Isra’ila ta zama kurangar inabi.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh ya kakkarya rassanta masu ƙarfi kuma suka bushe" ko "Mutane suka karya reshenta masu ƙarfi kuma suka bushe"
Yahweh ya ci gaba da ba da labari inda al’ummar Isra’ila ta zama kurangar inabi.
1Ya zamana a kan shekara ta bakwai, a rana ta goma ga watan biyar, sai dattawan Isra'ila suka zo domin su yi roƙo a wurin Yahweh suka kuma zauna a gabana.2Daga nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,3"Ɗan mutum, ka faɗa wa dattawan Isra'ila ka ce da su, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Kun zo ku yi roƙo a wurina? Da dawwamata, ba za ku taɓa tuntuɓa ta ba! -wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'4Za ka shar'anta su? Za ka shar'anta, ɗan mutum? Bari su san haramtattun ayyukan da ubanninsu suka aikata.5Ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ne ya faɗi wannan: A ranar da na zaɓi Isra'ila na ta da hannuna na rantse wa zuriyar gidan Yakubu, na kuma bayyana kaina a gare su cikin ƙasar Masar, sa'ad da na ta da hannun rantsuwa a gare su. Na ce, "Ni ne Yahweh Allahnku"-6a wannan rana na ta da hannuna na rantsuwar alƙawari a gare su cewa zan fito da su daga ƙasar Masar zuwa cikin ƙasar dana zaɓa dominsu. Mai malalowa da madara da zuma; tana da abubuwa masu kyau da babu irinsu a dukkan ƙasashe.7Na ce da su, "Bari kowanne ɗayanku ya yi watsi da abubuwan banƙyama daga idanunsa, da gumakan Masar. Kada ku ƙazantar da kanku; Ni ne Yahweh Allahnku."8Amma sun yi mani tawaye, ba su da niyyar sauraro na. Kowanne mutum ya ƙi watsi da abubuwan banƙyama daga idanunsa ko ya rabu da gumakan Masar, sai na shirya zan zubo masu da fushina domin in cika hasalata a cikinsu a kuma tsakiyar ƙasar Masar.9Amma saboda sunana ban yi haka ba a idanun al'ummai da suke zama a cikinsu. Na sanar da kaina a gare su, a idanunsu, ta wurin fito da su daga ƙasar Masar.10Sai na fitar da su daga ƙasar Masar na kawo su cikin jeji.11Sa'an nan na ba su farillaina na sa su san ka'idodina a gare su, waɗanda idan mutum ya kiyaye su zai rayu.12Na kuma ba su Asabatai a matsayin alama tsakanina da su, domin kuma su sani cewa Ni ne Yahweh wanda ke tsarkake su.13Amma gidan Isra'ila suka tayar mani a cikn jeji. Suka ƙi su yi tafiya cikin farillaina; maimakon haka, sai suka ƙi ka'idodina, waɗanda ta wurinsu ne mutum zai rayu idan ya yi biyayya da su. Sun ɓata Asabataina ƙwarai, saboda haka na ce zan zubo masu da fushina a cikin jeji domin in ƙarar da su.14Amma sabili da sunana ban yi haka ba saboda kada a saɓi sunana a idanun al'ummai, waɗanda a kan idanunsu ne na fitar da su daga ƙasar Masar.15Sai na kuma tada hannuna na rantse masu a cikin jeji ba zan kai su cikin ƙasar da na ba su ba, ƙasar da ta ke cike da yalwar madara da zuma, wadda tafi kyau a cikin dukkan ƙasashe.16Nayi rantsuwa a kan wannan domin sun ƙi ka'idodina kuma sun ƙi yin tafiya cikin farillaina, sun ɓata Asabataina, gama zuciyarsu ta fi so ta bauta wa gumakai.17Amma na kawar da idanuna daga hallakasu ban kuma hallakar da su a cikin jeji ba.18Sai na ce da 'ya'yansu a jeji, "Kada ku yi tafiya a kan farillan ubanninku; ko ku kiyaye sharuɗɗansu ko ku ɓata kanku da gumakansu.19Ni ne Yahweh Allahnku, ku yi tafiya a kan farillaina, ku kuma kiyaye ka'idodina, ku yi biyayya da su.20Ku kiyaye Asabataina da tsarki domin su zama alama tsakanina da ku, domin ku sani cewa Ni ne Yahweh Allahnku."21Amma 'ya'yansu maza da mata suka tayar mani, ba su yi tafiya a cikin farillaina ko su kiyaye ka'idodina ba, ta haka idan mutum ya yi biyayya da su zai rayu. Sai kuma suka ɓata Asabataina, domin haka na yi tunani zan zubo masu da fushina a kansu in kuma huce fushina a kansu a jeji.22Amma na yi hakuri sabili da sunana, domin kada a saɓi sunana a gaban idanun al'ummai waɗanda a idanunsu ne na fito da Isra'ilawa.23Ni da kaina na ɗaga hannuna bisa na rantse masu a jeji, zan warwatsar da su cikin al'ummai in kuma raba su a sauran ƙasashe.24Na yi shawara zan yi wannan domin sun ƙi yin biyayya da ka'idodina, sun kuma ƙi bin farillaina, sun lalata Asabar ɗina. Idanuwansu na mamarin bauta wa gumakan kakanninsu.25Sai kuma na ba su farillai waɗanda ba su da kyau, da ka'idodi marasa amfani da ba za susa su rayu ba.26Na furtasu ƙazantattu ta wurin kyaututtukansu - sunyi hadayunsu na kowanne ɗan fãri daga mahaifa sunsa su ratsa ta cikin wuta - domin in cika su da fargaba su kuma sani cewa Ni ne Yahweh!"27Saboda haka, ɗan mutum, yi magana da gidan Israila ka ce da su, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: A wannan kuma ubanninku suka saɓe ni ta wurin rashin aminci a gare ni.28Sa'ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su, daga nan kuma dukkan sa'ad da suka hango wani tudu da itace mai ganye, sai su miƙa hadayunsu, suka tsokane ni ta wurin baye-bayensu, a wurin kuma suka ƙona turare mai ƙanshi da zuba baye-bayensu na sha.29Daga nan na ce da su, "Wanne wurin ne wannan da kuke miƙa baye-baye a can?" Domin haka aka kira sunan wurin Bama har zuwa wannan rana.'30Saboda haka ka cewa gidan Isra'ila, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Me ya sa kuka ƙazantar da kanku da hanyoyin ubanninku? To me ya sa kuke haka kamar karuwai, ku na neman abubuwan banƙyama?31Duk sa'ad da ku ke miƙa kyaututtukanku - kuma duk sa'ad da kuke sanya 'ya'yanku maza su bi ta cikin wuta - har ya zuwa wannan rana kuna ƙazantar da kanku ta wurin dukkan gumakanku. To me ya sa zan barku ku neme ni, gidan Isra'ila? Da dawwamata - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - ba zan bari ku neme ni ba.32Tunanin nan da kuke yi a zuciyarku ba zai faru ba. Kuka ce, "Bari mu zama kamar sauran al'ummai, kamar dangogin sauran ƙasashe waɗanda ke bauta wa katako da dutse."33Da dawwamata - wannan furcin Yahweh ne - tabbas zan yi mulki a bisan ku da hannu mai ƙarfi, da ɗagaggen damtse, da fushina zan zubo a kanku.34Zan fitar da ku daga sauran mutane zan kuma tattaro ku daga sauran ƙasashe inda aka warwatsar da ku. Zan yi wannan da ikona ta wurin fushina mai zafi.35Sa'an nan zan kawo ku cikin jejin mutane, a wurin ne zan yi maku shari'a fuska da fuska.36Kamar yadda na yi wa ubanninku shari'a a jeji a ƙasar Masar, haka nan kuma zan yi maku shari'a - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.37Zan sa ku wuce ta ƙarƙashin sandata, in kuma sa ku yi biyayya da abubuwan da alƙawari ya wajabta.38Zan fitar da 'yan tawaye daga cikinku da waɗanda ke yi mani laifi. Zan fito da su daga ƙasar da suke zaune kamar bãƙi, gama ba za su shiga ƙasar Isra'ila ba. Sa'an nan ne za ku sani cewa Ni ne Yahweh.39To ku, gidan Israila, Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: kowannen ku zai tafi wurin bautar gukinsa. Ku bauta ma sa tun da ya ke ba za ku saurare ni ba, amma ba za ku sake ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku.40Gama a kan dutsena mai tsarki, a bisa ƙwanƙolin dutsen Israila--wannan furcin Yahweh ne--dukkan gidan Israila za su bauta mani a ƙasar. Zan yi murna in bukaci hadayunku a wurin, da kuma nunar 'ya'yan farin gandunku na dukkan abubuwanku masu tsarki.41Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa'ad da na fito da ku daga cikin sauran mutane, na tattaro ku daga ƙasashen da aka warwatsar da ku. Zan nuna kaina mai tsarki a cikinku domin sauran al'ummai su gani.42Gama idan na kawo ku a ƙasar Isra'ila, a ƙasar da na ɗaga hannuna sama na rantse zan bada ita ga ubanninku, za ku sani cewa Ni ne Yahweh.43A nan za ku tuna da mugayen hanyoyinku da dukkan ayyukanku da kuka ɓata kanku da su, za ku ji ƙyamar kanku a idanunku saboda mugayen abubuwa da kuka aikata.44Za ku sani cewa Ni ne Yahweh sa'ad da na yi maku wannan saboda sunana, ba kuma saboda gurɓatattun ayyukanku ba, ya gidan Isra'ila - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'"45Sai maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa.46"Ɗan mutum, ka fuskanci ƙasashen kudu, ka yi maganar gãba da kudu; ka yi annabci a kan kurmin Negeb.47Ka cewa kurmin Negeb, 'Wannan furcin Yahweh ne - Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Duba, zan kunna wuta a cikinka. Za ta kuwa cinye kowanne ɗanyen itace da kowanne busashen itace da ke cikinta. Ba za a iya kashe harshen wutar ba, kowacce fuska daga kudu da arewa za su ƙone.48Gama dukkan masu rai za su sani cewa Ni ne Yahweh idan na sa wutar, ba kuma za a iya kashewa ba.49Sai na ce, "Ya Ubangiji Yahweh, suna cewa da ni, wannan ba maganar misalai kawai yake yi ba?'"
Ana amfani da wannan jumla don alamar farkon sabon ɓangaren labarin.
Ana iya kawo bayanin a bayyane. AT: "a shekara ta bakwai ta gudun hijira na Sarki Yehoiachin"
Yahweh yayi wannan tambayar don jaddada cewa dattawa bai kamata su tambaye shi ba. AT: "Bai kamata ku zo don tambayata ba."
Yahweh ya yiwa Ezekiyel wannan tambayar sau biyu don ya tabbatar wa annabin Ezekiyel na zartar da hukuncin. AT: "Shin kuna shirye ku yanke hukunci a kansu, ɗan mutum?"
"Itasa ce da yalwar madara da zuma ke gudana." Yahweh yayi magana akan ƙasar da kyau ga dabbobi da tsire-tsire kamar su madara da zuma daga waɗancan dabbobi da tsirrai suna .
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga dattawan Isra'ila.
Kalmar "su" tana nufin "zuriyar gidan Yakubu."
"ba zai yi mini biyayya ba"
A nan kalmar "su" tana nufin al'ummu. Karin magana "a idanunsu" na nufin kasancewa a wurin da mutane zasu iya gani. AT: "Na bayyana kansu gare su, a gabansu"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga dattawan Isra'ila.
Kalmar "su" tana nufin "zuriyar gidan Yakubu."
Anan kalmar "suna" tana wakiltar mutuncin Yahweh. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 20: 8. AT: "Na yi aiki ne saboda mutunci na"
Anan "ɗaga hannuna" aiki ne na alama wanda ke nuna zai aikata abin da ya rantse da gaske. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 20: 4. AT: "Ni ma da kaina na rantse da rantsuwa"
Anan kalmar "ido" tana wakiltar Yahweh. AT: "Na kiyaye su"
Yahweh yayi magana akan mutumin da yake biyayya da dokoki kamar dai ka'idodi hanyoyi ne tare da mutum yana tafiya. AT: "Kada ku yi biyayya da dokokin iyayenku"
Yahweh yayi magana akan mutumin da yake biyayya da dokoki kamar dai ka'idodi hanyoyi ne tare da mutum yana tafiya. AT: "A kiyaye" dokokin Yahweh dai-dai yake da "a bi su."
Yahweh yayi magana game da nuna fushinsa ta hanyar azabtar dasu kamar dai fushin nasa wani ruwa ne da ya zubo musu. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 20: 8. AT: "don yi musu hukunci a fushina"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 12:14. AT: "sa su rabu da juna su zauna a cikin al'ummu daban-daban"
A nan kalmar "idanu" tana wakiltar mutumin da ya kalli gumaka don bauta musu. AT: "Sun kasance suna ɗokin ganin kakanninsu gumaka."
Kalmomin dokoki a cikin wannan jumlar ba sa nufin dokar Allah. Allah ya basu damar yin rayuwa bisa ga dokokin mutane da hukunce-hukuncen da basu da kyau.
Yahweh yayi wannan tambaya domin ya tsauta wa mutane. AT: "Wannan ba wuri bane mai tsayi inda zaku kawo sadaka!"
Sunan "Bama" yana nufin "wuri mai tsayi," wurin bautar gumaka. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "mutane sun kira wurin Bama"
Yahweh yayi wannan tambaya don ya tsauta wa mutane. AT: "Kada ku ƙazantar da kanku ta hanyar yin abin da kakanninku suka yi."
Yahweh yayi wannan tambaya don ya tsauta wa mutane. AT: "Ba zan bari ku zo kusa da ni ba, gidan Isra'ila."
Kalmomin guda biyu suna wakiltar ƙarfi. AT: "da iko mai girma"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙon ga Isra'ila.
Wannan yana nufin aikin makiyayi yana kirga tumakinsa yayin da tumaki ke tafiya karkashin sandar sa. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) Yahweh zai ƙidaya mutanensa waɗanda ya tara daga cikin al'ummu don tabbatar da cewa duk suna nan. AT: "Zan ƙididdige ku a hankali kamar yadda makiyayi ya ƙidaya tumakinsa" ko 2) Yahweh zai duba kowane mutum yayin da suke wucewa ƙarƙashin sandar sa domin raba masu aminci da marasa aminci. AT: "Zan binciki ku a hankali kamar yadda makiyayi yakan binciki tumakinsa"
"yi min biyayya" ko "a kula da ni"
Yahweh yayi magana akan mafi kyawu a cikin duk abin da suka ba shi kamar suna "nunan fari." AT: "mafi kyawun gudummawarku"
Waɗannan kalmomin guda biyu suna nufin abu ɗaya kuma suna jaddada cewa Ubangiji zai dawo da mutanensa daga cikin duk al'umman da ya warwatsasu. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 20:34.
Anan "ɗaga hannuna" na nuna zai aikata abin da ya rantse da gaske. AT: "Na rantse da gaske"
Wannan karin magana ne da ake amfani da shi don gabatar da wani abu da Allah ya faɗa wa annabawansa ko mutanensa. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 3:16. AT: "Yahweh ya faɗi wannan saƙon" ko "Yahweh ya faɗi waɗannan kalmomin"
Yahwehi ya ci gaba da ba wa Ezekiyel saƙonsa a cikin kurmin Negev.
1Sai maganar Yahweh ta zo ga gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, ka fuskanci Yerusalem, ka yi maganar gãba da masujadarta; ka kuma yi annabci a kan ƙasar Isra'ila.3Ka ce da ƙasar Isra'ila, 'Yahweh ya faɗi wannan: Ina gãba da ita! Zan zare takobina daga cikin kubanta in datse adalin mutum da mugun mutum daga cikinta!4Da yake ni zan daddatse adalai da mugaye daga gare ki, takobina zata fito daga cikin kubenta gãba da dukkan mutane daga kudu da kuma arewa.5Dukkan mutane kuwa za su sani Ni, Yahweh, na zare takobina daga kubenta. Ba kuwa za a sake mayar da ita a kubenta ba!'6Kai kuma, ɗan mutum, sai ka yi nishi da ajiyar zuciya yayin da ƙugunka ya karye! cikin ɗacin rai kayi nishi a gaban idanunsu!7Idan har za su tambaye ka, 'Donme ya sa kake nishi?' Sai ka ce masu, 'Saboda labarin abin da ke zuwa, domin kowacce zuciya za ta narke, kuma kowanne hannu zai yi lakwas! Kowanne ruhu zai some, kuma kowace gwiwa zata malale kamar ruwa. Duba! Abin yana zuwa kuma zai kasance kamar haka! - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'"8Sai maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,9"Ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, 'Ubangiji ya faɗi haka: "Ka ce Takobi! Takobi! Za a wãsa ta sosai a kuma goggoge ta!10Za a wãsa ta domin a yi babban kisa, an goge ta domin ta yi walwal kamar walƙiya! Shin mũyi murna a kan sandar girma ta ɗana? Takobi mai zuwa na gãba da kowacce sanda!11Saboda haka za a bada takobin a goge ta, sa'an nan a cafke ta da hannu! Takobin an wãsa ta an kuma goge ta za a kuma bada ita a hannun wanda ke yin kisa!""'12Ɗan mutum ka yi kiran neman taimako da makoki! Gama takobi ta zo ta yi gãba da mutanena! Ta na gãba da dukkan shugabannin Isra'ila. An bada su ga takobi tare da mutanena. Saboda haka, ka buga cinyarka!13Gama akwai gwaji, amma idan sandar girman bata daɗe ba fa? - wannan furcin Yahweh ne.14Yanzu kai, ɗan mutum, ka yi annabci ka buga hannuwanka biyu tare, don takobi zata kai hari har sau uku! Takobi domin waɗanda za a yanka! Ita ce takobin da zata datse mutane da yawa, za a yi masu gunduwa-gunduwa a ko'ina!15Domin a narkar da zukatansu a kuma ruɓanya faduwarsu, na aika da takobi domin yanka a ƙofofinsu. Ah! An yi ta kamar walƙiya, an cafko ta domin yanka!16Ke, takobi! ki sara dama! ki kuma sara hagu! Ki kuma je duk inda kika juya fuskarki.17Gama ni ma zan buga hannuwana biyu, Sa'an nan kuma zan kwantar da fushina, Ni, Yahweh na furta haka.18Maganar Yahweh ta sake zuwa gare ni, cewa,19"Yanzu kai, ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu domin takobin sarkin Babila ta zo. Hanyoyin biyu kuwa za su fara a ƙasar, alama kuma za ta nuna ɗaya daga ckinsu da ke kaiwa zuwa birnin.20Ka kuma sa alamar ɗaya hanyar domin sojojin Babila da za su zo Rabba, birnin Ammonawa. Ka kuma sa ɗaya alamar ta kai sojoji Yahuda da kuma birnin Yerusalem, wadda aka katange.21Gama sarkin Babila zai tsaya a mararrabar hanyoyi, inda hanyar ta rabu biyu, domin ya yi tsãfi. Yana girgiza waɗansu kiɓau yana kuma neman bayani daga waɗansu gumaka zai kuma binciki hanta.22A hannun damarsa zai riƙe wani abun sihiri game da Yerusalem, zai kafa mata dundurusai, ya buɗe bakinsa domin ya bada umarnin yanka, a yi kururuwar yaƙi, a rurrushe ƙofofinta ya kuma gina mahaurai da gina hasumiyoyin sansani.23Zai kasance kamar abin banza ne a idanuwan waɗanda suke a Yerusalem, waɗanda suka rantse ga Babiloniyawa! Amma sarkin zai zarge su da karya yarjejeniyarsu domin mamaye su!24Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Saboda kun sa a tuna da laifinku, kuka kuma sa a bayyana kurakuranku, domin a ga zunubanku a dukkan ayyukanku - saboda kun yi haka za a kame ku a hannu.25Kai kuma, ƙazantacce da mugun shugaban Isra'ila, wanda ranar hukuncinsa ta zo, wanda kuma lokacin aikata laifofinsa ya zo karshe,26Ubangiji Yahweh ne ya faɗi haka zuwa gare ka: Ka cire rawani ka kuma cire kambi! Abubuwa ba za su sake zama dai-dai ba! A ɗaukaka marasa martaba a kuma ƙasƙantar da masu girmankai!27Kufai! Kufai! Zan maida ita kufai! ba za a komar da ita ba, har sai shi wanda aka sa ya zartar da hukunci ya zo.28To Kai, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan ga mutanen Ammonawa a kan zuwan kaskancinsu: Takobi! an zare takobi! An wãsa ta domin yanka domin ta lanƙwame, haka zata zama kamar walƙiya!29Annabawa kuma suna ganin holoƙan wahayoyi domin ku, sa'ad da suke yin bukukuwan addini domin su zo maku da karairayi, wannan takobin zata kwanta a wuyan mai mugunta wanda aka kusan kashewa, wanda ranar hukuncinsa ta zo wanda kuma lokacin zunubinsa ya kusa ƙarewa.30Maida takobi a cikin kubenta. A wurin da aka hallice ka, a cikin ƙasarka ta ainihi, zan hukunta ka!31Zan zubo da hasalata a kanka! Zan kunna wutar fushina gãba da kai in kuma sa ka a cikin hannun mugayen mutane masu dabarar hallakarwa!32Za ka zama abincin wuta! Jininka zai kasance a tsakiyar ƙasar. Ba za a tuna da kai ba, gama Ni, Yahweh na furta wannan!'"
Wannan umarni ne na zura ido ga Yerusalem a matsayin alama ta azabtar da mutanen wurin. AT: "ku zura wa Yerusalem" ko "ku kalli Yerusalem don mutanen da ke wurin su cutu"
Wannan yana magana ne game da Yahweh yana kashe waɗannan mutane kamar dai ya kashe su da takobinsa. AT: "Ina adawa da ku, kuma zai zama kamar na zare takobina daga cikin kubenta don in kashe adalai da miyagu a cikinku"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa zuwa ƙasar Isra'ila.
Wannan magana ne wanda ke nufin yankin zuwa arewa, da kudu, da duk wuraren da ke tsakanin. AT: "a kowane bangare" ko "ko'ina"
Wannan yana magana ne game da Yahweh yana kashe mutane kamar dai ya kashe su da takobinsa. AT: "kamar dai ni, Yahweh, na bugi mutane da takobina"
"Tare da tsananin baƙin ciki" ko "Tare da baƙin ciki mai girma"
Wannan yana magana ne game da "labarai" kamar dai mutum ne wanda zai zo musu ba da daɗewa ba. AT: "labaran da za su ji ba da daɗewa ba"
Wannan yana magana ne game da mutane suna jin tsoro, kamar dai zukatansu suna suma. Hakanan, wannan yana magana ne akan mutane suma a sakamakon tsoro. AT: "don kowa zai tsorata"
Wannan yana magana ne game da mutane suna firgita a cikin ruhinsu kamar dai ruhunsu zai kusan suma. AT: "Kowa zai kasance mai tsoro a cikin halayensa"
Wannan jumlar tana nuna cewa takobi a shirye yake don wani yayi amfani da shi. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yana da kaifi da gogewa"
Yahweh ya ci gaba da bayanin takobin Yahweh wanda yake kwatanci ne ga sojojin abokan gaba waɗanda Yahweh zai yi amfani da su don ya yaƙi Yerusalem.
Wannan tambayar tana jaddada cewa mutanen Isra’ila ba za su yi bikin ikon sarkinsu ba, saboda ba za ta iya tsayayya da “takobi” ba. AT: "Mutanen Yahuda ba za su yi murna game da sandar sarautar su ba." ko "bai kamata mu yi biki ba da karfin sandar sarkinmu."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "a shirye yake don wanda ya yi kisan ya yi amfani da shi"
Wannan yana magana ne game da takobin Yahweh wanda yake afkawa mutanensa kamar takobi kanta. AT: "Zan yi amfani da takobina don kashe mutanena! Zan kawo ta kan kowa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Takobi ne don yankan mutane"
Anan "faɗuwa" yana nufin mutanen da aka kashe a yaƙi. Wannan yana nufin za a sami adadi mafi yawa na mutanen da aka kashe. AT: "don kashe mutane da yawa daga cikinsu"
Anan Yahweh yana magana da waɗanda za su kawo wa mutanensa hari kamar za su ji shi kuma kamar takobin da za su yi amfani da shi wajen kai harin. Yana yin hakan ne don jaddada cewa shi ke da iko da abin da ke faruwa yayin harin. Kalmomin "duk inda fuskarka ta juya" kalma ce ta "duk inda kake son zuwa." AT: "Ina gaya wa masu kai hari da takuba"
Kalmar "takobi" wani magana ne ga sojoji waɗanda ke kashe mutane ta amfani da takobi. AT: "sojojin sarkin Babila" ko "sojojin Babila"
Waɗannan hasumiya ne na katako waɗanda sojojin Babila suka gina a kewayen Yerusalem don su sami damar harba kibiyoyi a bangon Yerusalem.
"Saboda ka tunatar da ni laifinka"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. "Hannun abokan gaba" yana wakiltar ikon magabci. AT: "maƙiyinka zai kama ka a hannunsa" ko "maƙiyanka za su kama ka kuma su kai ka bauta"
Wannan karin magana ne. AT: "wanda Yahweh zai azabtar yanzu"
"a lokacin da Yahweh zai kawo karshen mugunta"
Wannan yana magana ne game da wahayin ƙarya da marasa ma'ana kamar suna kwantena fanko. AT: "wahayin da ba gaskiya bane" ko "wahayi na karya"
Ana iya bayyana kalmar "halitta" azaman magana. AT: "A wurin da na halitta ku"
"Wutar za ta kone jikinku"
1Sai maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa2"Yanzu, kai ɗan mutum, za ka shar'anta? Za ka shar'anta birni mai jini? Kasa ta san dukkan ayyukanta na banƙyama.3Dole ne ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Wannan shi ne birnin da ke zubar da jini a tsakiyarsa domin lokacinsa ya zo; birnin da ya yi gumaka domin ya kazantar da kansa.4Ka zama mai laifi ta wurin jinin da ka zubar, ka ƙazantar da kanka ta wurin gumakan da ka yi. Domin ka jawo kwanakinka kusa, ƙarshen shekarunka kuma ya zo. Domin haka zan maida kai abin reni ga dukkan al'ummai, abin ba'a kuma a dukkan ƙasashe.5Da waɗanda ke kusa da waɗanda ke nesa da kai za su yi maka ba'a, kai ƙazantaccen birni - da aka sani a ko'ina cike da rudami.6Duba! Masu mulki na Isra'ila, kowannen su da ikonsa, ya zo wurin ka domin ya zubar da jini.7Sun rena ubanni da uwaye a cikin ka, kuma suka yiwa baƙi danniya a cikin tsakiyar ka.8Sun wulaƙanta marayu da gwauraye a cikinka ka rena abubuwana masu tsarki, ka tozarta Asabataina.9Masu yankan baya sun zo cikin ka domin su zubar da jini, kuma sun ci abinci a kan tsaunuka. Sun yi mugunta a tsakiyarka.10Mazaje sun buɗe tsiraicin mahaifinsu a cikin ka. Sun kuma tozarta mata masu haila a cikin ka a lokacin hailarsu.11Mutanen da suka yi aikin kazanta da matan makwabtansu, mutanen da suka sa surukansu cikin kunya da kazanta; mazajen da suka ɓata 'yan'uwansu mata - 'ya'ya matan ubanninsu - dukkan waɗannan suna cikin ka.12Waɗannan mutane sun karɓi toshi a cikin ka domin su zubar da jini. Ka karɓi kuɗinka da ruwa, kaci riba mai yawa, ka ɓata maƙwabtanka da danniya, ka mance da ni - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.13Duba! Da hannuna na bugi kazamar ribar da kaci, da kuma zubar da jinin da ke a tsakiyarka.14Zuciyarka zata tsaya, hannuwanka suyi ƙarfi a kwanakin da ni da kaina zan ɗauki mataki a kan ka? Ni Yahweh ni ne ke furta wannan, kuma zan aikata.15Zan watsar da kai cikin al'ummai in sa ka ɗaiɗaice cikin ƙasashe. Ta haka zan wanke ƙazantarka.16Ta haka za ka zama mai ƙazanta a cikin al'ummai. Sa'an nan za ka sani cewa Ni ne Ubangiji Yahweh."17Sai kuma maganar Yahweh ta zo gare ni cewa,18"Ɗan mutum, gidan Isra'ila sun zama a yamutse a gare ni. Dukkan su sun zama ragowar tagulla da tãma da ƙarfe da dalma a cikin tsakiyar ka. Za su zama kamar gurɓatacciyar azurfa a cikin kaskonka.19Saboda haka Ubangiji Yahweh ya ce, 'Saboda ku dukka kun zama kamar gauraye, duba, saboda haka na kusa tattara ku a cikin tsakiyar Yerusalem.20Kamar yadda mutane ke tara azurfa da tagulla da ƙarfe da tãma da dalma a maƙera su narke, su kuma hura wuta a kan su domin su narkar da su, to haka zan tattara ku cikin fushina da hasalata, zan kuma sa ku a wurin in narkar da ku.21Zan tattara ku in hura wutar hasalata a kanku, za ku kuma narke a cikin tsakiyarta.22Kamar yadda a ke narka azurfa a cikin tsakiyar maƙera, za ku narke a cikin ta, sa'an nan za ku sani cewa Ni, Yahweh na zubo da hasalata a kan ku.23Maganar Yahweh ta zo gare ni cewa,24"Ɗan mutum ka ce da ita ke ƙasa ce wadda ba a tsabtace ba. Ba ruwan sama a cikin ranar hasala!25Akwai haɗaɗɗiyar maƙida ta annabawanta a cikinta kamar zaki mai ruri yana yaga nama. Suna kashe rai su kwashi dukiya mai daraja, suka sa gwauraye su yi yawa a cikin ta!26Firistocinta suna yiwa shari'ata tayarwa, sun ɓata abubuwa masu tsarki. Ba su banbanta abu mai tsarki da lalatacce ba, bãsa koyar da banbanci tsakanin abu mai tsabta da marar tsabta. Sukan kawar da idanunsu daga ranakun Asabar ɗina, saboda haka suka tozarta ni a cikin su.27Hakiman da ke cikin ta kamar kerketai suke lokacin da suke yayyaga nama. Sukan kashe rai, su zubar da jini domin suci riba ta rashin gaskiya.28Annabawanta sun shafe su da farar ƙasa; suna ganin wahayoyin ƙarya suna kuma faɗa masu ƙarya. Sukan ce, "Ubangiji Yahweh ya faɗi haka" Sa'ad da Yahweh bai yi magana ba.29Mutanen ƙasar suna yin zalunci, suna karɓar toshi, suna yin fashi, suna wulaƙanta mabuƙata da masu talauci, suna ƙwarar bãƙo da rashin adalci.30Sai na nemi mutum ɗaya a cikin su wanda zai gina ganuwa, ya tsaya a gabana a cikin tsagar domin kada in hallaka ta, amma ban samu ba.31Saboda haka zan zuba fushin hasalata a kan su. Zan gama da da su da fushin hasalata in maida masu ayyukansu a kansu - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."
Wannan tambayar ta magana tana aiki a matsayin umarni. AT. "ɗan mutum, tafi ka yanke hukunci. Ka je ka yanke hukunci game da garin jini."
Kalmar "jini" wani magana ta kisan kai. AT: "garin da mutane da yawa ke kashe maƙwabtansu"
Yahweh ya ci gaba da magana ta bakin Ezekiyel ga mutanen Yerusalem.
Hotunan ranakun da ake kawowa kusa da shekaru masu zuwa ƙarshen maganganunsu dukka suna wakiltar ƙarshen mutuwa ko halaka. Ta wurin faɗi cewa Yerusalem ta share kwanakin ta don ƙarshe, Yahweh yana nuna cewa ba da daɗewa ba za a halaka Yerusalem saboda zunubin mutane. AT: "Saboda waɗannan abubuwan da kuka aikata, kuna gab da ƙarshen lokacinku" ko "Kuna kawo ƙarshen wanzuwar ku"
Yahweh yana magana game da shugaban Isra'ila a Yerusalem.
"aikata mugunta a tsakaninku"
Allah ya ci gaba da magana ta bakin Ezekiyel game da mugayen ayyukan da mutanen Yerusalem suka yi. Yana yi wa mutanen Yerusalem magana kamar suna birnin da kanta, da kuma na Yerusalem kamar mace. Kalmar "ku" koyaushe ta mata ce.
Wannan yana nufin cewa ɗa yana kwana da matar mahaifinsa. AT: "akwai maza da ke kwana da matar mahaifinsu"
Toin yi wa Yahweh biyayya kamar manta shi ne.
"Na girgiza ƙugu a kan" ko "Na tafa hannayena da." Wannan aikin alama ne wanda ke nuna fushi da rashin yarda. AT: "Na nuna fushina da rashin yarda da su" (Duba: figs:metaphor)
Yahweh yayi amfani da wannan tambaya ta zance don ya nanata yadda za su ji daɗi idan ya hukunta su. Ana iya rubuta wannan tambayar azaman sanarwa. AT: "Zuciyarku ba za ta iya tsayawa ba kuma hannayenku ba za su yi ƙarfi a ranakun da ni kaina zan yi ma'amala da ku ba."
Anan "al'ummai" suna nufin mutanen da suke zaune a waɗancan wurare. “Idon” yana wakiltar gani, kuma gani yana wakiltar tunani ko hukunci. AT: "Don haka al'umman za su dauke ku marasa tsarki"
Yahweh yana ci gaba da magana game da yadda mutane suka zama marasa amfani a gareshi kamar suna ƙura. AT: "Dukkansu ba su da daraja kamar abin da ya rage na tagulla da kwano, da baƙin ƙarfe da gubar da suka rage bayan an narkar da azurfa a tanderu"
Allah ya ci gaba da bayanin hukuncin da ya yi wa Isra’ilawa a Yerusalem kamar ƙarafa ce da yake narkewa kuma yana tsarkakewa a cikin tanda.
Ana amfani da ruwan sama a matsayin misali na ni'imar Allah. AT: "Babu albarka a ranar hasala"
Waɗannan jimlolin guda biyu ma'anar abu ɗaya ne kuma suna jaddada tashin hankali da yarima ke yi. AT: "Suna kashe mutane"
Yahweh ya kamanta shugabannin Yerusalem da bango da kuma kansa da runduna mai zuwa.
Wannan yana magana ne game da mutumin da zai ɗauki alhakin yin addu'a domin mutane kuma ya kai su ga tuba kamar dai mutumin zai gina bango ne don ya kāre mutane daga Yahweh. AT: "wani mutum daga cikinsu wanda zaiyi kamar ya gina bango"
Wannan yana maganar Yahweh yana azabtar da mutane kamar dai fushin sa wani ruwa ne da ya zubo musu. AT: "Zan hukunta mutane saboda fushin da na yi musu" ko "Zan hukunta mutane saboda fushin da nake yi da su"
1Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, akwai mata guda biyu, mahaifiyarsu kuma ɗaya.3Sun yi aikin karuwanci a Masar sa'ad da suke matasa. Sun yi aikin karuwanci a can. A can aka lagwaigwaita nonnansu, aka daƙuna kan nonnan budurcinsu.4Sunayensu su ne Ohola - ita ce babba - da Oholiba kuma ƙanwarta. Daga nan suka zama nawa suka haifi 'ya'ya maza da mata. Ga ma'anar sunayensu: Ohola tana nufin Samariya, Oholiba tana nufin Yerusalem.5Ohola ta yi karuwanci ko sa'ad da take tawa; ta yi sha'awar masoyanta, su Asiriyawa waɗanda suke da yawa a wurin.6Gwamna mai saye da shuɗi, da jami'ansa kyawawa majiya ƙarfi, da dukkan waɗanda ke a kan dawakai.7Ta bayar da kanta karuwa a gare su, da dukkan mahimman mazaje na Asiriya, ta ƙazantar da kanta da dukkan waɗanda ta yi sha'awar su - da dukkan gumakansu.8Gama ba ta bar halinta na karuwanci a Masar ba, sa'ad da suka kwana da ita lokacin da take yarinya, sa'ad da suke taɓa nonnanta na kuruciya, lokacin da suka fara zuba mata halinsu na lalata.9Saboda haka na miƙa ta a hannun masoyanta, a hannun Asiriyawa waɗanda ta yi sha'awar su.10Suka yi mata tsirara sun kwashe 'ya'yanta maza da mata, kuma suka kashe ta da kaifin takobi, ta zama abin kunya ga sauran mata, suka yi mata hukunci.11Oholiba 'yar'uwarta ta ga haka, amma ta yi sha'awa fiye da ita, ta yi aikin karuwanci fiye da 'yar'uwarta.12Ta yi sha'awar Asiriyawa da gwamnoni da jami'ai waɗanda suke sa kaya masu kyau, masu hawan dawaki. Dukkan su kyawawa ne kuma ƙarfafan mutane ne.13Na ga ta kazamtar da kanta. Dukkan su sun zama ɗaya.14Sai kuma ta ƙaru cikin karuwancinta, ta ga sifofin mazaje a kan ganuwa, waɗanda a ka zãna da siffar Kaldiyawa da jar kala,15suna ɗaure da ɗamara a gindinsu, da rawunna masu lilo a kansu. Dukkan su sun yi kama da jami'ai masu karusai, kamanninsu na 'ya'yan Babiloniyawa ne, waɗanda asalin ƙasarsu Kaldiya ce.16Da dai idanunta suka gan su, sai ta yi sha'awar su, sai ta aiki waɗansu wurin su a cikin Kaldiya.17Sai Babiloniyawa suka zo wurin ta, wurin gadon sha'awarta, suka kazantar da ita da lalatarsu. Abin da ta yi ya kazantar da ita, sai ta ɓatar da kama ta rabu da su.18Ta bayyana aikin karuwancinta ta nuna tsiraicinta, raina ya yi ƙyamar ta kamar yadda raina ya yi kyamar 'yar'uwarta.19Sa'an nan ta ƙara tunawa da aikin karuwanci, kamar yadda ta yi kwanakin ƙuruciyarta, sa'ad da ta zama kamar karuwa a cikin ƙasar Masar.20Ta yi sha'awar masoyanta waɗanda mazakuttarsu ke kamar na jakuna, waɗanda kuma maniyinsu kamar na dawaki ne.21Haka ki ka yi aikin kunya a lokacin ƙuruciyarki, sa'ad da Masarawa suka taɓa kan nonnanki suka lagwaigwaita nonnanki da ke tsaye.22Saboda haka, Oholiba, Ubangiji Yahweh ya faɗi haka, 'Duba! Zan sa mãsu ƙaunar ki su yi gãba da ke. Waɗanda kika gudu daga wurin su, za su taso maki daga kowanne sashi:23Babiloniyawa da dukkan Kaldiyawa da Fekod da Shoya da Koya da dukkan Asiriyawa tare da su da ƙarfafa da kyawawan mutane da gwamnoni da jami'ai, dukkan su jami'ai ne da mazaje masu muƙami, dukkan su suna kan dawakai.24Za su auko maki da kayan yaƙi, da karusai da kekuna da taron mutane da yawa. Za su ta da garkuwoyi manya da ƙanana da hulunan ƙarfe kewaye da ke ko'ina. Zan ba su zarafi su hore ki, za su hore ki da ayyukansu.25Gama zan sa kishin fushina a kan ki, za su lallasa ki da fushinsu. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka tsira kuma za su faɗi da kaifin takobi. Za su kwashe 'ya'yanki maza da mata, waɗanda suka tsira kuma wuta za ta cinye su.26Za su tuɓe kayanki su bar ki tsirara, su kwashe kayan adonki dukka.27Ta haka zan cire halinki na abin kunya da aikin karuwancinki daga ƙasar Masar. Ba za ki ƙara ɗaga idonki wajen su da marmarin ki gan su ba, ba za ki ƙara yin tunanin Masar ba.28Gama Ubangiji ya faɗi haka. Duba! zan bayar da ke a hannun waɗanda kika ƙi su, ki koma hannun waɗanda kika juyawa baya.29Za su azabtar da ke cikin zafin ƙiyayya, za su ɗauke dukkan kayayyakinki su bar ki huntuwa. Huntancinki na karuwanci zai bayyana, halinki na kunya da lalatarki za su bayyana.30Za a yi maki waɗannan abubuwa saboda aikinki na karuwanci, sha'awarki ta al'ummai wadda ta ƙazamtar da ke da gumakansu.31Kin yi tafiya cikin hanyar 'yar'uwarki, saboda haka zan sa ƙoƙon horona a cikin hannunki.'32Ubangiji Yahweh ya faɗi haka, 'Za ki sha ƙoƙon 'yar'uwarki mai faɗi da zurfi. Za ki zama abin dariya da abin ba'a - cikin wannan ƙoƙon akwai abubuwa da yawa.33Za ki cika da maye da baƙinciki, ƙoƙon fargaba da lalacewa; ƙoƙon 'yar'uwarki Samariya.34Za ki shanye shi dukka ki farfasa shi ki tsattsaga nononki da gutsattsarinsa. Gama na furta shi - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.35Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi haka, 'Saboda kin manta da ni kin jefar da ni bayanki, ke kuma za ki ɗauki alhakin halinki na kunya da lalata."36Yahweh ya ce da ni, "Ɗan mutum, za ka hukunta Ohola da Oholiba? To ka nuna masu ayyukansu na banƙyama,37tun da yake sun yi zina, tun da yake akwai jini a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu, sun sa 'ya'yansu cikin wuta, a matsayin abinci ga gumakansu.38Sa'an nan sun ci gaba da yi mani haka, sun ɓata gidana mai tsarki, sun tozarta Asabataina.39Gama sa'ad da suka yanka 'ya'yansu ga gumakansu, rannan kuma suka zo gidana mai tsarki suka ɓata shi! To duba! Wannan shi ne abin da suka yi a tsakiyar gidana.40Kin yi aike wurin mutanen da suka zo daga nesa, an aika manzanni - duba yanzu. To sun zo su waɗanda kika yi wanka domin su, kin yi wa idanunki kwalliya kin sa kayan adonki.41Can kika zauna a kan gado mai kyau wanda aka shirya teburi a gabansa inda kika ajiye turarena da maina.42To ga hayaniyar babban taro kewaye da ita; ciki akwai mutane iri-iri har da masu maye daga cikin jeji, sun sa sarƙoƙi a hannuwansu da kambuna kyawawa a kawunansu.43Sa'an nan na ce da ita, ita wadda ta tsofe a wurin karuwanci, 'Yanzu za su ƙazantu da zinarta, ita kuma da su.'44Suka je wurin ta suka kwana da ita kamar yadda mutum zai je wurin karuwa. Ta wannan hanya suka kwana da Ohola da Oholiba, kazantattun mata.45Amma mazaje masu adalci za su yi masu hukuncin mazinata, kuma za su yi masu hukunci na mãsu zubar da jini, saboda su mazinata ne kuma jini yana hannuwansu.46To Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: zan sa taron mutane su auko masu da ta'addanci su washe su.47Sa'an nan waɗannan mutane za su jejjefe su da duwatsu su daddatsu da takubbansu. Za su karkashe 'ya'yasu maza da mata, su ƙone gidajensu.48Gama zan cire halayen kunya daga ƙasar, in hori dukkan mataye domin kada su ƙara yin rayuwa kamar karuwai.49Haka za su sa maki halinki na kunya. Za ki ɗauki hakin zunubanki da gumakanki, ta haka za ki sani cewa Ni ne Ubangiji Yahweh."
Yahweh yayi magana akan yadda biranen Yerusalem da Samariya suka kasance marasa aminci a gareshi inda ya ambace su da karuwai biyu. Wannan kwatancin ya ci gaba ta hanyar Ezekiyel 23:34.
Wannan jimlar tana nufin abu ɗaya daidai da kalmar da ta gabata kuma tana ƙarfafa halayen lalata na 'yan matan biyu. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "a can ne maza ke shaawar nonon budurwa"
"Oholah tana wakiltar Samariya, kuma Oholiba tana wakiltar Yersalem." A wannan kwatancin ana maganar Samariya kamar tana Oholah kuma ana maganar Yerusalem kamar da Oholiba. Wannan yana magana ne akan yadda waɗannan biranen suka kasance marasa aminci ga Yahweh kamar suna matan rashin aminci.
Yahweh ya ci gaba da kwatancinsa inda yake magana game da biranen Yerusalem da Samariya kamar su karuwai biyu ne.
Kalmar "hannu" tana nufin iko. Kalmomin guda biyu suna da ma'ana ɗaya kuma kalmar ta biyu ta bayyana cewa "masoyanta" sun kasance "Asiriyawa." AT: "Na ba da ita ga masoyanta, Asiriyawa"
Wannan yana nufin yadda dukansu suka ƙazantu. AT: "Duk 'yan uwan matan sun zama marasa tsabta ta hanyar ayyukansu na karuwanci"
Yahweh ya ci gaba da kwatancinsa inda yake magana game da biranen Yahweh da Samariya kamar su karuwai biyu ne.
Wannan karin magana ne. AT: "don haka ta ƙi su"
AT: "ta tuna kuma ta aikata irin abubuwan da ta yi lokacin ƙuruciyarta"
Wannan yana kwatanta ƙarar mazan hayaki da na doki don nuna yadda muguwar sha'awar Oholiba ta kasance. Wannan karin gishiri ne saboda ba za su iya zama kamar na doki ba. AT:" wanda hayakin haifuwarsa yana da girma, kamar waɗannan na doki"
Waɗannan su ne kungiyoyin mutane a cikin Babila.
Ana amfani da waɗannan abubuwan kariya don komawa zuwa nau'ikan sojoji. AT: "Sojoji za su kawo muku hari a kowane bangare dauke da manyan garkuwa, kananan garkuwa, da hular kwano"
Wannan wata hanya ce da ake nufin mutum ya juya kansa ya kalli wani abu. Anan kallo yana wakiltar sha'awa. AT: "Ba za ku kallesu ba tare da kewa" ko kuma "Ba za ku so waɗannan abubuwan ba"
Anan "Masar" tana wakiltar abubuwan kunya da ta aikata a Masar. AT: "zaku yi tunani game da abubuwan da kuka yi a Masar ba" ko kuma "ba za ku ƙara tunanin abin da kuka yi a Masar ba kuma"
Wadannan kalmomin guda biyu suna nufin abu daya kuma suna nanata cewa za a gano ta kwata-kwata.
Wannan yana nuni ne ga hukuncin Oholiba da za a yi mata kamar ƙoƙon ruwan inabi. AT: "don haka zan sa a hukunta ku kamar yadda aka yiwa 'yar'uwar ku"
Anan Yahweh yayi maganar azaba kamar dai ƙoƙon ruwan inabi ne matar ta sha. AT: "Za ku sha ƙoƙon hukunci ɗaya da na 'yar uwarku"
Wannan jumlar bata faɗi abin da ke cikin ƙoƙon ba saboda an fahimta ta hanyar karantawa Ezekiyel 23:30. AT: "wannan kofin yana dauke da azaba mai yawa"
Wannan yana magana game da buguwa sosai kuma cike da baƙin ciki kamar maye da baƙin ciki abubuwa ne da suka cika jikinta. AT: "Za ku bugu sosai ku bugu da baƙin ciki"
Yahweh yayi magana akan Oholiba ta ƙi shi kamar wani abu ne da ta jefa a baya ta manta shi. AT: "sun ƙi ni"
Wannan karin magana ne. AT: "sun kashe mutane"
Jumlar "rana ɗaya" tana nufin maganar da ta gabata "ku tsarkake wurina." AT: "A ranar da suke tozarta haikalina, suna ɓata Asabar ɗina"
Waɗannan abubuwa ne da mace ke yi don sanya ta zama mafi kyau ga namiji.
Ana amfani da sautin taron don nuni ga taron mutane. AT: "Don haka akwai taron mutane masu hayaniya a kusa da ita"
Sun sadu da ita kamar yadda maza suke saduwa da karuwa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "don kamfanin su firgita su kuma su washe su"
Wannan karin magana ne. AT: "sa ku yarda da alhakin halayenku na kunya" ko "azabtar da ku saboda halin kunyarku"
"ku yarda da alhakin zunubanku tare da gumakanku." Wannan yana nuna cewa za a hukunta su saboda zunubansu. AT: "karɓar hukuncin zunubin ta hanyar bautar gumakanku"
1Maganar Yahweh ta zo gare ni a cikin shekara ta tara, a cikin wata na goma, a kan rana ta goma ga watan, cewa,2"Ɗan mutum, ka rubuta wa kanka sunan wannan rana, ranar nan ta yau, gama a dai-dai wannan ranar ne sarkin Babila ya ƙwace Yerusalem.3To sai ka yi magana da misali gãba da wannan gida mai tayarwa, a misali. Ka ce da su Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ɗora tukunyar girki. Ɗora ta ka zuba ruwa a cikin ta.4Ka tattara gutsattsarin abinci a cikin ta, kowanne yanka mai kyau - kamar su cinya da karfata - ka cika ta da ƙasusuwa zaɓaɓɓu.5A cikin garke ka ɗauki dabba zaɓaɓɓiya ka jera kasusuwan a ƙarƙashin ta. Ka sa ta tafasa ka dafa ƙasusuwan a cikin ta.6Saboda haka, Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Kaiton birni mai jini, tukunyar girki mai tsatsa kuma tsatsar ba za ta fita daga cikin ta ba. Ka ɗauki yanka bayan yanka daga cikin ta, amma kada ka jefa ƙuri'a kan ta.7Gama jininta yana cikin tsakiyarta, ta sa shi a kan dutse mai laushi; ba ta zubar da shi a ƙasa ta rufe shi da turɓaya ba,8ta kawo hasala dai-dai ta ɗaukar fansa. Na sa jininta a kan dutse mai laushi domin kada ya rufu.9Saboda haka, Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Kaiton birni mai jini. Zan ƙara sa itace da yawa.10Iza itacen ka sa wuta. Ka dafa naman ya dafu sosai ka gauraye da kayan yaji ka kuma bari kasusuwan su gashe.11Sa'an nan ka ɗora tukunyar a kan garwashi ba komai a ciki, domin ta yi zafi tagullarta ta rikiɗe, domin ƙazantar da ke cikinta ta narke, tsatsarta ta ƙone.12Ta zama gajiyayya saboda aiki, amma tsatsarta ba ta fita daga cikin ta da wuta ba.13Halinki na kunya yana cikin ƙazantarki. Saboda nayi ƙoƙari in tsabtace ki amma har yanzu ba ki tsabtatu daga ƙazantarki ba, ba za ki sake tsabtatuwa ba sai na ƙosar da fushina a kan ki.14Ni, Yahweh, na furta, kuma zan aikata. Ba zan janye ba, ba zan huta ba. Yadda hanyoyinki suke, yadda kuma ayyukanki suke, su za su hukunta ki! - Wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."15Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,16"Ɗan mutum! Duba zan ɗauke maka muradin idanunka daga gare ka da annoba, amma kada ka yi baƙinciki ko kuka, kada hawayenka su zubo.17Ka yi nishi a hankali. kada kayi jana'izar matattu. Ka ɗaura rawaninka a jikinka ka sa takalmanka a ƙafafunka, amma kada ka lulluɓe gashin bakinka, kada ka ci gurasar waɗanda ke makoki saboda sunyi rashin matayensu."18Domin haka na yiwa mutane magana da safe, da yamma kuma matata ta mutu. Da safe na yi abin da aka umarce ni in yi.19Mutanen suka tambaye ni, "Ba za ka gaya mana ma'anar waɗannan abubuwa ba, abubuwan da kake yi?"20To sai na ce da su, "Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,21'Ka ce da gidan Isra'ila, ga abin da Ubangiji Yahweh ya fadi: Duba! Zan ƙaskantar da gidana mai tsarki - girmankan ikonku da muradin idanunku, da marmarin ranku da na 'ya'yanku maza da mata da kuka baro, za su faɗi da kaifin takobi.22Sa'an nan za ku yi dai-dai yadda na yi: Ba za ku lulluɓe kanku ba, ba za kuci gurasar mazajen da ke yin makoki ba!23Maimakon haka rawunanku za su kasance a kan ku takalmanku kuma a ƙafafunku; ba za ku yi baƙinciki ka kuka ba, gama za ku narke cikin muguntarku, kowanne mutum zai yi nishi saboda ɗan'uwansa.24Domin haka Ezekiyal za ya zamar maku misali, yadda idan wannan abu ya zo za ku yi dukkan abin da ya yi. Sa'an nan za ku sani cewa Ni ne Ubangiji Yahweh."25"Amma kai ɗan mutum, ran da na ƙwace haikalinsu, wanda shi ne farincikinsu, da fahariyarsu da abin da suke gani suna jin daɗi - sa'ad da kuma na ɗauke 'ya'yansu maza da mata -26a wannan rana mai gudun hijira zai zo ya ba ka labari!27A wannan rana ne bakinka zai buɗe ga wannan mai gudun hijira za ka yi magana - ba za ka ƙara yin shiru ba. Za ka zama misali a gare su domin su sani cewa Ni ne Yahweh."
"ranar goma ga watan goma" ko "ran 10 ga watan 10." Wannan shi ne watan goma na kalandar Ibraniyanci. Rana ta goma tana kusa da farkon watan Janairu a kan kalandar yamma.
Sojojin Babila ana kiran shugaban su. AT: "sojojin sarkin Babila sun kewaye ta"
Wasu al'adun suna kara kasusuwa a wuta saboda sun fi wuta tsawo fiye da itace. Wannan yana nufin ƙasusuwan da suka rage bayan an sanya mafi kyau ƙasusuwa a cikin tukunya. AT: "sanya sauran kasusuwa a ƙarƙashin tukunya don hura wutar"
Yahweh ya ci gaba da kwatanta Yerusalem da tukunyar girki. AT: "kamar tukunyar girki ne"
Yin ƙuri'a hanya ce ta zaɓar waɗancan naman da za a fitar, amma saboda Yahweh yana so ya fitar da duka naman, babu buƙatar jefa ƙuri'a.
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Ezekiyel wani kwatanci game da tukunyar girki da ke wakiltar Yerusalem. Wannan kwatancin ya ci gaba ta hanyar Ezekiyel 24:14.
"ya sanya jinin a kan duwatsu mara haushi"
An nuna cewa tarin itace yana ƙarƙashin tukunyar girki wanda yake wakiltar Yerusalem. "Zan sanya tarin itacen a kan wutar da ke ƙarƙashinku mafi girma"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "ƙona ƙasusuwa"
Anan kalmar "ta" tana nufin tukunyar girki. Wannan itace tukunyar girki wacce ke misalta Yerusalem. AT: "Yerusalem ta gaji"
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Ezekiyel wani kwatanci game da tukunyar girki da ke wakiltar Yerusalem.
"nima ba zan huta daga azabtar da kai ba." Kalmar "shi" tana nufin Yahweh yana hukunta mutane.
Wannan yana nufin matar Ezekiyel. Yahweh yana nufin Ezekiyel ta ɓangaren jikinsa da yake amfani da su don ganin matarsa. AT: "matarka, wacce kuke matukar so, daga"
Waɗannan jimlolin suna nufin abu ɗaya kuma suna ƙarfafa cewa Ezekiyel ba zai yi kuka game da mutuwar matarsa ba. AT: "Kada ku yi baƙin ciki ko kuka"
Wannan ya bayyana haikalin da cewa ginin da mutane suke alfahari da shi. Wannan yana magana game da shi azaman "girman kai" maimakon asalin abin alfaharinsu. AT: "ginin da kuke alfahari da shi" ko "asalin girman ku"
Wannan yana nufin makiyansu da takubbansu. AT: "'ya'yanku maza da mata ... za a kashe su a yaƙi" ko "maƙiyanku za su kashe ɗiyanku maza da mata ... da takubbansu"
Anan "narkewa" kwatanci ne na ɓata rai da mutuwa. AT: "zaku zama sirara sosai kuma a hankali zaku mutu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Ezekiyel aka bashi fahimta da ikon magana ana wakilta bakinsa ana buɗewa. AT: "Zan buɗe bakinka" ko "za ku san abin da za ku ce" ko "Zan sa ku san abin da za ku ce"
A nan kalmar "alama" tana nufin wani abu da ke isar da gargaɗi na musamman ga waɗanda suka gani. Yahweh yayi magana akan Ezekiyel da ayyukansa kamar wannan gargaɗi ne. Duba yadda kuka fassara wannan kwatancin a cikin Ezekiyel 12: 6. AT: "Za ku zama gargaɗi a gare su"
1Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, ka sa fuskar ka gãba da mutanen Amon ka yi anabci gãba da su.3Ka ce da mutanen Amon, 'Ku ji maganar Yahweh. Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya faɗi: Saboda kun ce, "Aha!" a kan wurina mai tsarki sa'ad da aka ɓata shi, da kuma gãba da ƙasar Isra'ila sa'ad da ta zama kango, da kuma gidan Yahuda sa'ad da suka tafi bauta,4saboda haka, duba, zan bashe ku ga mutanen gabas su mallake ku. Za su kafa sansani gãba da ku su kafa rumfuna a cikin ku. Za su ci 'ya'yan itatuwanku su sha madararku.5Zan maida Rabba wurin kiwon raƙuma mutanen Amon kuma saura domin garkuna. Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Yahweh.6Gama Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Da yake kun tafa hannuwanku kun buga ƙafafunku kun yi farinciki da ƙiyayya a cikin ku gãba da ƙasar Isra'ila.7Saboda haka, duba! Zan buge ku da hannuna in bashe ku ganima ga al'ummai. Zan datse ku daga cikin mutane in sa ku lalace daga cikin al'ummai! Zan hallaka ku, kuma za ku sani cewa Ni ne Yahweh.'8Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan, 'Saboda Mowab da Siya sun ce, "Duba! Gidan Yahuda ya zama kamar kowacce al'umma."9Saboda haka, Duba! Zan buɗe magangarin Mowab in fara daga biranensa a kan iyaka - martabar Bet Yeshimot, Ba'al Miyon da Kiriyattayim -10domin mutanen gabas waɗanda ke gãba da mutanen Amon. Zan bayar da su a mallake su yadda ba za a ƙãra tunawa da mutanen ba a cikin al'ummai.11Haka zan yi hukunci a kan Mowab, za su kuma sani cewa Ni ne Yahweh.12Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan, 'Idom ta ɗauki fansa a kan gidan Yahuda kuma ba ta yi dai-dai ba da ta yi haka.13Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Zan bugi Idom da hannuna in hallaka kowanne mutum da kowacce dabba a can. Zan maida su kufai, yasasshen wuri tun daga Teman har zuwa Dedan. Za su faɗi da kaifin takobi.14Zan ɗora ramakona a kan Idom ta hannun mutanena Isra'ila, za su yi wa Idom bisa ga fushina da hasalata, kuma za su gane ramako na ne - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'15Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan, 'Tun da Filistiyawa sun ɗauki fansa da reni a cikin su, sun yi ƙoƙari su rushe Yahuda ba sau ɗaya ba.16To ga abin da Ubangiji Yahweh ya faɗi: Duba! Zan kai hannuna a kan Filistiyawa, zan datse Keretiyawa in hallaka waɗanda suka rage a gefen teku.17Gama zan ɗauki fansa a kan su da fushi mai zafi da horo, saboda su sani cewa Ni ne Yahweh, sa'ad da na ɗauki fansata a kan su."
Wannan umarni ne don a zura wa Ammonawa alama don azabtar da su. AT: "ku kalli mutanen Ammon" ko "ku kalli mutanen Ammon don cutar da su"
"yi annabci game da munanan abubuwan da zasu same su." Wannan yana nufin yin annabci game da mugayen abubuwa da za su aukar wa Ammonawa. Dubi yadda kuka fassara wata magana makamancin wannan a cikin Ezekiyel 4: 7.
Wannan yana magana ne game da sojojin abokan gaba da suka ci ƙasar Ammonawa suka mallaki ƙasar da duk abin da ke ciki kamar dai abokan gaba sun ƙwace mutanen Ammon a matsayin mallakarsu. Ba a nuna a nan cewa abokan gaba sun kame mutanen Ammon a matsayin bayi ba. AT: "Zan sa sojoji daga ƙasar da take gabashinku su zo su cinye ku"
"Za su kafa tanti kuma za su zauna a ƙasarku"
Anan kalmar "mutanen Ammon" tana nufin ƙasar da ta kasance ta Ammonawa. Hakanan, ana iya bayar da bayanan da aka fahimta a farkon wannan jumlar. AT: "Zan mayar da sauran ƙasar Ammon a filin filin garken tumaki"
"Zan mare ka da hannuna mai karfi." Anan Yahweh yayi maganar azabtar da mutane kamar dai yana bugun su da hannu. AT: "Zan hore ku"
Kalmar "ku" tana nufin mutanen Ammon amma kuma alama ce ta ƙasarsu da dukiyoyinsu. AT: "Zan ba wa magabta damar fatattakarsu su kwace ku, ƙasarku, da dukiyoyinku ganima"
Anan ana maganar garin Mowab tare da wakilin suna na "nasa." AT: "farawa daga biranenta"
Waɗannan sunayen wuraren ne.
Zan kuma aiko da wannan runduna guda daga mutanen gabas waɗanda suka yi yaƙi da Ammonawa.
Anan Yahweh yayi maganar azabtar da mutane kamar dai yana bugun su da hannu. Duba yadda kuka fassara makamancin wannan magana a cikin Ezekiyel 25: 6. AT: "Zan hukunta Idom"
Waɗannan su ne birane biyu a gefen iyakar Idom. Wannan yana nufin cewa Yahweh zai hallaka Idom dukka.
Anan “hannun” Isra’ilawa ne na sojojin Isra’ila. Yahweh yayi maganar ɗaukar fansa a kan mutanen Idom kamar ɗaukar fansa kamar mayafin da ya rufe su da shi. Ana iya fassara kalmar 'ramuwar gayya' tare da kalmar aikatau "don hukunci." AT: "Zan yi amfani da mutanena Isra'ila don hukunta mutanen Idom"
AT: "Za su nuna wa Idom fushina da fushina" ko "za su hukunta Idom bisa fushina da fushina kan mutanen Idom"
Kalmomin "daga cikin kansu" salon magana ne. ATa: "Filistiyawa sun ƙi Yahuda kuma sun yi ƙoƙari su ɗaukar fansa a kanta ta ƙarfinsu sau da yawa"
Anan ikon Yahweh yana wakiltar da "hannunsa." AT: "Zan juya hannuna mai iko kan Filistiyawa" ko "Zan juya babban iko na kan Filistiyawa"
Mutanen da suka rayu a garin Keret na Filistiya
1Ya zama a cikin wata na goma sha ɗaya, a kan rana ta fari ga watan, Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, saboda Taya ta ce, 'Aha! A kan Yerusalem, ƙofofin mutanen yanzu an ɓalle su! ta dawo wurina; zan cika saboda ta zama kango.'3Saboda haka, Ubangiji Yahweh ya faɗi haka, 'Duba! Ina gãba da ke Taya, zan taso da al'ummai da yawa a kan ki kamar yadda teku ya kan tada raƙuman ruwansa.4Za su rushe ganuwoyin Taya, su farfasa hasumiyoyinta. Zan share ƙurarta in sa ta zama kamar huntun dutse.5Za ta zama wurin da a ke shimfiɗa taru ya bushe a tsakiyar teku, tun da shi ke na furta - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - kuma za ta zama ganima ga al'ummai.6'Ya'yanta waɗanda suke cikin gona za a datse su da takobi; kuma za su sani cewa Ni ne Yahweh.'7Gama wannan shi ne abin da Yahweh ya faɗi: Duba, daga arewa zan kawo Nebukadnezza sarkin Babila, sarkin sarakuna gãba da Taya, da dawakai da karusai da masu hawan dawakai da mutane da yawa.8Za ya kashe 'ya'yanki mata a gona. Ya kafa sansani ya gina wuraren hawan ganuwarki ya tada garkuwoyi gãba da ke.9Zai sa mabugi ya bubbuge ganuwarki, ya rushe hasumiyoyinka da kayan aikinsa.10Dawakinsa za su yi yawa har ƙurar su za ta rufe ki. Ganuwarki za ta girgiza da ƙarar mahayan dawakai da kekunan yaƙi da karusai. Sa'ad da zai shiga ƙofofinki zai shiga kamar yadda mutane ke shiga birnin da aka rushe ganuwarsa.11Kofatun dawakinsa za su yi tafiya a cikin dukkan hanyoyinki. Zai kashe mutanenki da takobi, ginshiƙanki na dutse masu ƙarfi za su faɗi har ƙasa.12Za su kwashe dukiyarki da kayan cinikinki, za su farfasa ganuwarki su rushe gidajenki na jin daɗi. Duwatsunki da katakonki da ɓaragwazanki za su zubar da su a cikin ruwaye.13Zan tsayar da ƙarar waƙoƙinki. Ba za a ƙara jin ƙarar molayenki ba.14Zan maida ke huntun dutse, za ki zama wurin da za a shanya taru ya bushe. Ba za a sake gina ki ba, gama Ni, Ubangiji Yahweh na faɗi - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.15Ubangiji Yahweh ya faɗawa Taya haka, 'Tsibirai ba za su girgiza ba da ƙarar faɗuwarki, da nishin waɗanda aka yiwa rauni sa'ad da wannan kisa mai muni ya zo cikin ki?16Sa'an nan dukkan yarimai na bakin teku za su sauka daga mulkokinsu su tuɓe tufafinsu, su jefar da rigunansu masu aiki. Za su rufe kansu da rawar jiki, za su zauna a ƙasa suna rawar jiki kowanne lokaci, kuma za su yi nukura saboda ke.17Za su yi makoki a kanki su ce da ke, yaya haka, ke da kike wurin zaman masu tukin jirgin ruwa aka rushe ki. Sanannen birni mai ƙarfin gaske - yanzu ba shi a bakin teku. Su da suke zaune cikin ta suka baza labarin fargabarsu ga waɗanda ke zaune kusa da su.18Yanzu ƙasashen tudu sun girgiza da ranar faɗuwarki. Tsibirai na cikin teku sun firgita saboda kin rabu da wurin ki..19Gama Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Sa'ad da na mayar da ke kangon birni, kamar biranen da ba kowa. Sa'ad da na taso da zurfafa a kan ki, sa'ad da manyan ruwaye suka rufe ki,20sa'ad da zan saukar da ke wurin mutanen dã, kamar waɗanda suka gangara cikin rami; gama zansa ki zauna can ƙarƙashin ƙasa kamar irin kango na zamanin dã. Saboda haka ba za ki ƙara dawowa ki tsaya a cikin ƙasar masu rai ba.21Zan saukar maki da masifa, kuma ba za ki ƙara wanzuwa ba har abada. Sa'an nan za a neme ki, kuma ba za a ƙara samun ki ba - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."
Anan garin suna "Taya" da "Yerusalem" suna wakiltar mutanen waɗannan biranen. AT: "mutanen Taya sun faɗi game da mutanen Yerusalem"
Mutanen Taya suna amfani da waɗannan kalmomin don ambaton Yerusalem kamar dai ƙofar birni ce inda 'yan kasuwa daga al'umman da ke kewaye da ita suke wucewa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sojoji sun farfashe kofofin mutane"
A nan kalmar "al'ummai" tana nufin rundunoninsu. AT: "Zan tattara sojoji daga al'ummomi da yawa waɗanda za su yi yaƙi da ku kamar raƙuman ruwa a cikin raƙuman ruwa"
Yahweh yayi magana akan yadda zai sa Taya ta hallaka gaba ɗaya. AT: "Zan sa sojoji su rusa garin kwata-kwata, kuma ba za su bar komai a wurin ba"
Ana maganar birnin Taya a nan kamar mace. AT: "Taya za ta zama" ko "Zai zama"
Wani ɓangare na Taya tsibiri ne. Wannan furcin ishara ce ga sakamakon halakar Taya. AT: "tsibiri mara amfani da ake amfani da shi don bushe tarunan kifi" ko "tsibirin da babu kowa inda mutane ke shanya tarun kifinsu"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sojojin abokan gaba za su yanka tare da takuba ga 'ya'yanta mata waɗanda ke cikin filin"
Jimlar "sarkin sarakuna" take ne, ma'ana shi ne mafi girma a cikin sarakuna, sarkin da sauran sarakuna ke yi masa biyayya. AT: "Nebukadnezza sarkin Babila, sarki mafi girma"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "'ya'yanku mata" yana nufin' yan matan Taya waɗanda suke aiki a cikin gona ko kuma 2) "'ya'yanku mata" sunaye ne na garuruwa da ƙauyuka na kusa da ke babban yankin da ke tallafawa babban birnin Taya. Duba yadda kuka fassara makamancin magana a cikin Ezekiyel 26: 5. AT: "al'ummomin ɗiyar ku waɗanda ke kan babban yankin"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Wannan tambayar tana buƙatar amsa mai kyau kuma tana nanata sakamakon halakar Taya. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Tsibiran za su girgiza ... a tsakaninku."
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
1Kuma maganar Yahweh ta sake zuwa gare ni cewa,2"Yanzu kai, ɗan mutum, sai ka soma makoki game da Taya,3ka kuma cewa Taya, wadda take zama kurkusa da ƙofofin teku, masu kasuwancin mutane ne ga Tsibirai da yawa, Ubangiji Yahweh ya faɗa maki haka: Taya, Kin ce, 'Ni kammalalliya ce mai kyau.'4Iyakokinki suna cikin tsakiyar zuciyar tekuna; maginanki sun kamalla kyaunki;5Sun yi katakan ki da siferas daga Tsaunin Hamon; sun ɗauko sida daga Lebanon domin su yi maki sandar tukin jirgi.6Sun sarrafa sandar tukin jirginki da itace na Bashan; suka yi matakalar ki da katakan siferas daga Saifrus, suka kuma lulluɓe ta da hauren giwa.7Mayafanki mayafai masu ƙawa ne daga Masar da ke a matsayin tutarki; launin shuɗi da shunayya daga gaɓar Elisha a na amfani da su domin kare jirgin ruwanki.8Waɗanda suka zauna cikin Sidon da Abad su ne matuƙanki; masu hikima na Taya na cikin ki; su ne masu yi maki jagora.9Ƙwararru masana masu aikin hannu daga Baibilos sun gyarta tsagaggun wurarenki; dukkan jiragen teku da matuƙansu da ke cikin ki suna ɗaukar kayan fatauci domin kasuwanci.10Fãsha da Lidiya da kuma Libiya suna cikin rundunarki, mayaƙãnki sun rataye garkuwa da ƙwalƙwali a cikin ki; suka bayyana darajarki.11Mazajen Abad da Helek da ke cikin rundunarki sun zama katanga zagaye da ke, kuma mutanen Gammad su ne hasumiyoyinki. Sun rataye garkuwoyinsu a kan katangu zagaye da ke! Suka kammala kyaunki.12Tarshish abokiyar kasuwancinki ce saboda yawan wadatar dukiyarki ta sayarwa: da azurfa, da baƙin ƙarfe, da tãma, da dalma. Suka saya suka kuma sayar da kayayyakin ki!13Yaban da Tubal da kuma Meshek-sun sayar da bayi da kuma kayayyaki na tagulla. Suka sarrafa kayan fataucinki.14Bet Togama ta tanadi dawakai, da dawakan yaƙi da alfadarai a matsayin kayan fataucinki.15Mazajen Rodes suka zama yan kasuwarki a tsibirai masu yawa. Fatauci na cikin hannunki; suka kuma aiko maki ƙaho da hauren giwa da katakai masu ƙarfi a matsayin kyautai.16Aram babbar 'yar kasuwa ce da kayayyakin ki masu yawa; suka tanada koren dutse mai daraja da shunayya, kaya mai launuka, da yãdi mai kyau da tsakiya da sauran kayan ado a matsayin kayan fataucinki.17Yahuda da Isra'ila abokan kasuwancin ki ne. Suka tanada alkama daga Minit, waina da zuma, da mai, da ƙãro a matsayin kayan fataucinki.18Dimaskus dillaliyar dukkan kayayyakin da kika sarrafa ce, ta hamshaƙiyar dukiyarki, da kuma ruwan inabi na Helbon da ulun Zaha.19Dan da Yaban daga Izal suka yi maki fataucin ɗanyen ƙarfe da ɓawon ƙirya, da ƙansa-ƙansa. Wannan ya zama abin fatauci domin ki.20Dedan ce mai samar maki da mashinfiɗai na sirdin dawakai masu kyau.21Arebiya da dukkan shugabannin Keda suna ciniki da ke; sun samo maki 'yan raguna da raguna da awaki.22'Yan kasuwa na Sheba da Rama suka zo su sayar maki da kowanne irin kayan ƙamshi mafiya daraja da kowanne irin dutse mai daraja; suka yi safarar zinariya domin fataucinki.23Haran da Kane da Iden su ne abokan kasuwancinki, tare da Sheba da Ashu da kuma Kilmad.24Waɗannan su ne dillalanki waɗanda ke sayar da kayan ƙawa (kayayyaki masu daraja na sãƙaƙƙun kayan ãdo), da kuma cikin barguna masu zane iri-iri da sãƙaƙƙun kaya a cikin kasuwannin ki.25Jiragen ruwa na Tarshish su ne masu kawo maki kayayyakin fataucinki! Domin haka ki ka cika, aka loda maki kaya masu nauyi a tashoshin jiragen ruwanki.26Matuƙan jiragen ruwanki suka kawo ki ga manyan tekuna; iskar gabas ta karya ki a tsakiyar su.27Dukiyarki, da abin fataucinki da kuma kayan kasuwancinki; matuƙan jiragenki, da mãsassaƙa jiragen ruwa; abokan cinikinki da dukkan mayaƙan da ke cikin ki da dukkan ma'aikatan jiragenki- za su nutse cikin zurfin teku a ranar hallakarki.28Biranen kusa da teku za su yi rawar jiki da jin ƙarar kukan masu yin jagoran jiragen ruwanki;29Dukkan matuƙan jiragen za su sauko daga jiragensu; ma'aikata da majayan hanya za su sauka su tsaya kan ƙasa.30Sa'an nan za susã ki saurari muryarsu za su kuma yi kuka mai zafi; za su watsa ƙura a kawunansu. Za su kwanta suna birgima cikin toka.31Za su aske sumar kansu dominki su kuma ɗaure kansu da tsummokin makoki, kuma za su yi kuka mai zafi su kuma tãda murya ƙwarai.32Za su tãda muryarsu ta makoki mai zafi dominki su kuma furta kalamai na habaici a kanki, wane ne kamar Taya, wadda yanzu aka sa tayi shiru a tsakiyar teku?33A lokacin da fataucinki ya kai bakin teku, yana biyan buƙatar mutane masu yawa; kin azurtar da sarakunan duniya da dukiyarki da fataucinki!34Amma lokacin da teku ya ragargaza ki, ta zurfafan ruwaye, fataucinki da dukkan ma'aikatanki suka nutse!35Mazaunan tsibirai suka gan ki suka tsorata da ke, kuma sarakunansu suka yi rawar jiki mai ban razana! Fuskokinsu suka gigice!36Fatake suka yi maki tsãki, kin zama abin razana, kuma ba za a sake ganin ki ba har abada."
"wanene ke zaune a ƙofofin teku" ko "wanene ke zaune a ƙofar shiga teku"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
"gyara tsaga"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
"mutanen da suka yi yaƙi a yaƙe-yaƙenku" ko "kasancewa a matsayin mayaƙanku"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Wannan shine sunan yankin bakin teku wanda akafi sani da Iyonia.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Samun abubuwa a hannun anan mai yiwuwa kwatanci ne na ɗaukar waɗancan abubuwan ko samun su a cikin kayan su. AT: "Kun mallaki abubuwan da kuka siyar musu"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Jiragen ruwan Tarshish suna ɗauke da kayan kasuwancinku"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
"Kuka da bakin ciki"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Waɗannan maganganu ne na nuna baƙin ciki da makoki.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Taya.
Cikakken sunan "tsoro" za'a iya fassara shi ta amfani da sifa "razana." Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kun zama abin tsoro"
1Sai maganar Yahweh ta zo mani, cewa,2"Ɗan mutum, ka yi magana da shugaban Taya, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: zuciyarka tunƙaho! Kãce, 'Ni allah ne! zan zauna a cikin mazaunin alloli a tsakiyar tekuna!" koda shi ke kai mutum ne ba allah ba, ka maida zuciyarka kamar ta allah;3kana tunanin ka fi Daniyel hikima, kuma babu asirin da ke ba ka mamaki!4Ka maishe da kanka mawadaci da hikima da fasaha, ka kuma tara zinariya da azurfa cikin ma'ajin ka!5Ta wurin babbar hikima da kuma kasuwanci, ka ruɓanɓanya wadatarka, sai zuciyarka ta kumbura saboda dukiyarka.6Saboda haka, Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: domin ka maida zuciyarka kamar zuciyar allah,7Zan kawo bãƙi gãba da kai, Mazaje masu ban razana daga waɗansu al'ummai. Za su kawo takubba gãba da kyakkawar hikimarka, kuma za su wulaƙanta darajarka.8Za su tura ka cikin rami, kuma za ka mutu mutuwa irin ta masu mutuwa cikin tsakiyar tekuna.9Ka iya cewa, 'Ni allah ne' a fuskar mai kashe ka? Kai mutum ne ba Allah ba, kuma za ka zama a hannun wanda yake caccakar ka.10Za ka yi mutuwar marasa kaciya ta hannun bãƙi, gama na furta haka - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."11Maganar Yahweh ta sake zuwa gare ni karo na biyu, cewa,12"Ɗan mutum, ka tãda makoki domin sarkin Taya kace da shi, "Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: ka zama misalin kammala, cike da hikima da kammalanlen kyau.13Kana cikin Iden, lambun Allah. Kowanne dutse mai daraja ya rufeka; da rubi, da tofaz, da imeral, da kiraisolet, da oniks, da yasfa, da saffiya, da tokwayis, da beril. Tsare-tsarenka da haɗuwarka anyi su ne da zinariya. A ranar da aka hallice ka ne aka shirya su.14Na ajiye ka a bisa tsauni mai tsarki na Allah a matsayin kerubim da na shafe domin ya yi tsaron 'yan adam. Kana cikin tsakiyar dutse ma wuta inda ka yi yawo.15Kana da aminci a tafarkunka tun daga ranar da aka hallice ka har sai da aka sami rashin adalci cikin ka.16Ta wurin girman kasuwancinka ka cika da ta'addanci, domin haka ka yi zunubi. Saboda haka sai na jefar da kai daga tsaunin Allah, kamar wadda ya ƙazanta, kuma sai na hallakar da kai, kerubim mai tsaro, na kore ka daga cikin duwatsu masu wuta.17Zuciyarka ta cika da tunƙaho domin kyaunka; ka wofintar da hikimarka saboda darajarka. Na koro ka ƙasa. Na sanya ka a gaban sarakuna domin su gan ka.18Saboda zunubanka masu yawa da kuma rashin amincin kasuwancinka, ka ƙazantar da wurarenka masu tsarki. Domin haka na sa wuta ta fito daga gare ka; zata cinye ka. Zan maishe ka toka a fuskar dukkan waɗanda suke kallon ka.19Dukkan waɗanda suka san ka cikin mutanen za su girgiza kai; za su yi fargaba, kuma ba za a sake ganinka ba har abada."'20Sai maganar Yahweh ta zo mani, cewa,21"Ɗan mutum, ka sa fuskar ka gãba da Sidon ka kuma yi annabci gãba da ita.22Ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Duba! Ina gãba da ke, Sidon! Gama za a ɗaukaka Ni a tsakiyarki domin mutanenki su sani cewa Ni ne Yahweh a lokacin da zan zartar da adalci a cikin ki. Za a nuna ni mai tsarki cikin ki.23Zan aika da annoba cikin ki da jini cikin titunanki, kuma waɗanda aka kashe za su faɗi a tsakiyarki. A lokacin da takobin zata tashi gãba da ke ta ko'ina, sa'an nan za ki sani cewa Ni ne Yahweh.24Daga nan ba za a sami wata sarƙaƙiya da ƙaya mai azaba domin gidan Isra'ila ba daga dukkan waɗanda ke zagaye da ita waɗanda ke raina mutanenta ba, haka za su sani cewa Ni ne Ubangiji Yahweh!'25Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan, 'Lokacin da na tara gidan Isra'ila daga cikin mutane waɗanda aka tarwatsa su, kuma lokacin da na keɓe cikin su, domin al'ummai su gani, sa'an nan za su gina gidajensu a cikin ƙasar da zan ba bawana Yakubu.26Sa'an nan za su zauna lafiya cikin ta su kuma gina gidaje, su shuka gonakin inabi, su kuma zauna lafiya a lokacin da zan shar'anta dukkan waɗanda suka rena su yanzu daga dukkan kewaye; Da haka za su sani Ni ne Yahweh Allahnsu!"'
Anan “zuciya” tana wakiltar wasiyya ko tunanin mai mulkin Taya. AT: "Kuna da girman kai"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga mai mulkin Taya.
Ana iya fassara sunayen suna "hikima" da "fasaha" ta amfani da sifofin "masu hikima" da "ƙwarewa." AT: "Kun zama mawadata ta hanyar hikimarku da gwanintarku" ko "Kun zama mawadata ta hanyar hikima da fasaha"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga mai mulkin Taya.
Ana iya fassara sunayen mara kyau "kyakkyawa" da "hikima" ta amfani da sifa "kyakkyawa" da karin magana "da hikima." AT: "kyawawan kyawawan abubuwan da kuka yi masu hikima"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga mai mulkin Taya.
Wannan tambayar tana buƙatar amsar mara kyau don ƙarfafa ƙaryar lokacin da wanda ya ce shi allah ne mutane sun hallaka shi. Ana iya fassara shi azaman bayani. AT: "Ba za ku ce" ˜Na allah ne ™ ga fuskar wanda ya kashe ku ba!"
"raira waƙar makoki"
Ana iya fassara sunayen suna "hikima" da "kyakkyawa" ta amfani da sifofin "hikima" da "kyakkyawa." AT: "cikakke mai hikima kuma cikakke kyakkyawa"
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel saƙonsa ga sarki Taya.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "tun daga ranar da na halicce ku har sai da na sami rashin adalci a cikinku"
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel saƙonsa ga sarki Taya.
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel saƙonsa ga sarki Taya.
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 27:34.
"yi annabci game da munanan abubuwan da zasu faru." Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 4: 6.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Sidon.
"a cikin ƙasar"
1A cikin shekara ta tara, a watan goma a ran sha biyu ga wata, maganar Yahweh ta zo mani, cewa,2"Ɗan mutum, ka juya fuskar ka gãba da Fir'auna, sarkin Masar; ka yi annabci gãba da shi da kuma gãba da dukkan Masar.3Ka furta ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Duba! Ina gãba da kai, Fir'auna, sarkin Masar. Kai, babbar dabbar teku da ke ɓuya cikin tsakiyar kogi, da ke cewa, "Kogi nawa ne. Na yi shi domin kaina."4Gama zan sa ƙugiya a cikin bakinka, kuma kifaye na cikin Nilunka za su liƙe bisa ɓawonka; Zan tãda kai sama tare da dukkan kifayen kogin da suka manne wa ɓawonka.5Zan jefar da kai cikin hamada, kai da dukkan kifaye daga koginka. Zaka faɗi a buɗaɗɗen fili; ba za a tãra ka ko a tãda kai sama ba. Zan bada kai abinci ga hallitun ƙasa da kuma tsuntsayen sammai.6Sa'an nan dukkan mazaunan Masar za su sani cewa Ni ne Yahweh, domin sun zama sandar matsala ga gidan Isra'ila.7A lokacin da suka riƙe ku da hannunsu, kun karye kun kuma yage kafaɗarsu; da suka jingina a kanku, sai kuka karye, sai kuma kuka sa ƙafafunsu suka kasa tsayawa.8Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Duba! Zan kawo takobi gãba da kai. Zan datse mutum da dabba daga gare ka.9Sai ƙasar Masar ta zama yasasshiya da kuma kufai. Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Yahweh, domin dabbar teku ta ce, "Kogin nawa ne, gama ni na yi shi."10Domin haka, duba! Ina gãba da kai kuma ina gãba da koginka, don haka zan bayar da ƙasar Masar ga hallakarwa da lalacewa, kuma za ta zama lalatacciyar ƙasa daga Migdol zuwa Sãyin da kuma iyakokin Kush.11Babu ƙafafun mutum da za shi wuce ta cikin ta, kuma babu ƙafar naman jeji da za shi wuce cikin ta. Ba za a zauna cikin ta ba har shekaru arba'in.12Gama zan maida Masar ƙango a tsakiyar ƙasar da ba a zama cikin ta, kuma biranenta a tsakiyar lalatattun birane za su zama kufai har shekaru arba'in; sa'an nan zan tarwatsa Masar cikin al'ummai, in kuma watsa su cikin ƙasashe.13Gama Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: a ƙarshen shekara arba'in zan tara Masar daga cikin mutanen da aka watsar da su.14Zan dawo da abin da ke na Masar in kuma dawo da su zuwa ga yankin Fatros, zuwa ga ƙasar su ta asali. Sa'an nan za su zama masarauta marar muhimmanci a can.15Zata zama ƙasƙantacciyar masarauta cikin masarautu, kuma ba za a ɗaga ta sama ba cikin al'ummai. Zan ƙasƙantar da su domin kada su yi mulkin al'ummai.16Masarawa ba za su ƙara zama dalilin ƙarfin zuciya ga gidan Isra'ila ba. Maimakon haka, za su zama abin tunawa da zunubin da Isra'ila ta aikata a lokacin da suka juya ga Masar neman taimako. Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Ubangiji Yahweh."'17Sai ya zama a cikin shekara ta ashirin da bakwai a ranar farko ta watan ɗaya, maganar Yahweh ta zo mani, cewa,18"Ɗan mutum, Nebukadneza sarkin Babila ya shirya rundunarsa su yi aiki mai wuya gãba da Taya. Kowanne kai an murje shi har sai ya yi saiƙo, kuma kowacce kafaɗa ta gogu. Duk da haka shi da rundunarsa ba su karɓi lada daga wurin Taya domin aiki mai wuyar da ya yi gãba da ita ba.19Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: 'Duba! Ina bayar da Masar ga sarki Nebikadneza sarkin Babila, kuma zai kwashe dukiyarta, ya kwashe mallakarta, ya tafi da duk abin da ya iske a can; wannan zai zama ladar rundunarsa.20Na ba shi ƙasar Masar domin aikin da suka yi mani - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.21A wannan rana zan sa ƙaho ya taso domin gidan Isra'ila, kuma na sa ku yi magana a tsakiyarsu, domin su san cewa Ni ne Yahweh."
"a ranar goma sha biyu ga watan goma." Wannan shi ne watan goma na kalandar Ibraniyanci. Ranar goma sha biyu tana kusa da farkon watan Janairu a kan kalandar yamma.
"babbar halittar da ke rayuwa a cikin ruwa." Yahweh ya kira Fir'auna dodo wanda ke zaune a cikin ruwa. Da dodo mai yiwuwa kada ne.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Fir'auna, yana magana game da shi kamar shi dodo ne a cikin ruwa kuma mutanen Masar sun kasance kifi.
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel saƙonsa ga Fir'auna.
Saboda Masar ba ta taimaki Isra’ilawa ba, Isra’ilawa ba za su iya kāre kansu daga magabtansu ba, wato Babilawa. Allah yayi magana game da Isra'ilawa sun kasa kare kansu kamar kafafunsu ba su da ƙarfi. AT: "kun sanya su sun zama kamar mutanen da ƙafafunsu ba su da ƙarfi"
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel saƙonsa ga Fir'auna.
Anan “takobi” yana nufin sunan yaƙi, kuma “kawo takobi a kanku” kwatanci ne don sa rundunar abokan gaba su zo su yaƙi Masar. AT: "Zan sa makiyanku su zo su yi yaƙi da ku"
Wannan yana nufin dukkanin Masar. Inda wadannan wuraren suke ana iya bayyana su a sarari. AT: "a duk cikin Masar, daga Migdol a arewa zuwa Syene a kudu da iyakokin Masar da ke kudu"
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel saƙonsa ga Fir'auna.
Anan "ƙafar dabba" tana wakiltar dabbobi. AT: "hatta dabbar daji ba za ta ratsa ta ba"
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel saƙonsa ga Fir'auna.
Kalmar "arzikin Masar" kwatanci ne na mutanen Masar da aka ɗauke su zuwa wasu ƙasashe. AT: "Zan dawo da mutanen Masar"
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel saƙonsa ga Fir'auna.
Cikakken sunan "amintacce" za a iya fassara shi da kalmomin nan "aminci" ko "dogara." AT: "Gidan Isra'ila ba zai ƙara amincewa da Masarawa ba" ko "Gidan Isra'ila ba zai ƙara dogara ga Masarawa ba"
"a ranar farko ga watan farko." Wannan shine farkon watan kalandar Ibraniyanci. Ranar farko tana kusa da farkon watan Afirilu.
Kahon dabba yana wakiltar ƙarfin dabba, don haka ƙaho alama ce ta ƙarfin ƙarfi. Allah yayi maganar ƙarfafa Isra’ila kamar Isra’ila dabba ce, kuma zai sa ƙahon ta ya yi girma. AT: "Zan sa mutanen Isra'ila su yi ƙarfi"
1Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ku yi kururuwa, "Kaiton ranar mai zuwa."3Ranar ta kusa. Ranar ta gabato domin Yahweh. Za ta zama rana ce ta hadarai, lokaci na masifa ga al'ummai.4Sa'an nan takobi zata zo gãba da Masar, kuma za a yi ƙunci a cikin Kush a lokacin da mutanen da aka kashe suka fǎɗi a Masar - a lokacin da suka ɗauki dukiyarsu, da kuma lokacin da ginshiƙanta aka warwatsar.5Kush da Libiya, da kuma Lidiya, da dukkan Arebiya, tare da mutanen da ke na alƙawari - dukkan su za su fãɗi ta dalilin takobi.6Yahweh ya faɗi wannan: Waɗanda suka tsaya tare da Masar za su fǎɗi, kuma girman ƙarfin ta zai fǎɗi ƙasa. Daga Migdol zuwa Siyen sojojinsu za su fǎɗi da takobi - wannan furcin Yahweh ne.7Za su zama wofi a tsakiyar yasassun ƙasashen, kuma biranen su za su zama cikin dukkan rusassun biranen.8Sa'an nan za su san cewa Ni ne Yahweh, yayin da na cinna wuta cikin Masar, kuma lokacin da aka hallaka dukkan mataimakanta.9A wannan ranar 'yan saƙo za su fito daga gare ni cikin jirage su addabi tsararrar Kush, kuma za a yi azaba a cikin su a wannan rana ta azabar Masar. Duba! Tana zuwa.10Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Zan kawo ƙarshen taron jama'ar Masar ta hannun Nebukadneza, sarkin Babila.11Shi da rundunarsa tare, ta'addar al'ummai, za a hallakar da ƙasar; za su zare takobinsu gãba da Masar su kuma cika ƙasar da gawawwakin mutane.12Zan maishe da rafuffuka busassun ƙasa, zan kuma sayar da ƙasar cikin hannun mugayen mutane. Zan maishe da ƙasar da dukkan cikarta kufai ta hannun bãƙi- Ni, Yahweh, na yi magana.13Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: zan hallakar da gumaka, kuma zan kawo iyakar gumakan Memfis marasa amfani. Ba za a sake samun yarima cikin ƙasar Masar ba, kuma zan sa ta'adda a bisa ƙasar Masar.14Sa'an nan zan sa Fatros ta zama kufai in kuma cinna wuta a Zowan, kuma zan aiwatar da ayyukan shari'a a kan Tebes.15Gama zan zubo da fushi na a bisa Felusiyom, kangararren wuri na Masar, in kuma datse taron jama'ar Tebes.16Sa'an nan zan cinna wuta a Masar; Felusiyom za ta zama da azaba mai tsanani, Tebes za ta kakkarye, Memfis kuma za ta fuskanci magabta a kowacce rana.17Majiya ƙarfi cikin Heliyofolis da Bubastis za su fǎɗi ta takobi, kuma birninsu zai tafi bauta.18A Tafahes, rana za ta ƙi bada haskenta sa'ad da na karya karkiyar Masar a nan, za a ƙarar da alfarmar ikonta. Girgije zai rufe ta, kuma 'ya'yanta mata za su tafi bauta.19Zan aiwatar da ayyukan shara'a a Masar, domin su sani cewa Ni ne Yahweh.'"20Sai ya kasance a cikin shekara ta sha ɗaya, cikin wata na farko, a cikin kwana na bakwai na watan, da maganar Yahweh ta zo mani, cewa,21"Ɗan mutum, na karya hannun Fir'auna, sarkin Masar. Duba! Ba a rigaya an ɗaure masa ciwon ba, ko a shirya shi ya warke da bandeji, saboda ya yi ƙarfi ya kama takobi.22Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: 'Duba, ina gãba da Fir'auna, sarkin Masar. Gama zan karya hannunsa, da mai ƙarfin da wanda aka karye, kuma zan sa takobin ya fǎɗi daga hannunsa.23Sa'an nan zan tarwatsa su cikin Masar cikin al'ummai in kuma watsa su cikin ƙasashe.24Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babila in kuma ɗibiya takobina a cikin hannunsa domin in hallaka hannun Fir'auna. Zai yi nishi a gaban sarkin Babila da nishi kamar na mutum mai mutuwa.25Gama zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babila, amma hannun Fir'auna zai faɗi. Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Yahweh, a lokacin da zan sa takobina cikin hannuwan sarkin Babila; gama zai kai wa Masar farmaki da ita.26Don haka zan watsar da Masar cikin al'ummai In kuma tarwatsa su a cikin ƙasashe. Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Yahweh."'
Wannan kirari yana nuna tsoron da mutane zasu ji game da wata ranar da abubuwa masu ban tsoro da firgici zasu faru. AT: "Oh a waccan ranar" ko "Oh, abin da ranar tsoro za ta zo"
Gizagizai masu duhu suna wakiltar haɗari da tsoro. AT: "Zai zama kamar yini tare da gizagizai masu duhu" ko "Zai zama abin firgita kamar ranar da ke cikin gajimare mai duhu"
Cikakken sunan "ƙaddara" za a iya fassara shi da kalmar "munanan abubuwa za su faru." AT: "lokacin da mummunan abubuwa zasu faru ga al'ummomi"
Waɗannan su ne maganar Yahweh game da Masar.
Ana iya bayyana kalmar "baƙin ciki" ta la'akari da yadda mutane suke ji. AT: "mutanen Cush za su yi baƙin ciki ƙwarai" ko "mutanen Cush za su sha wuya"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "lokacin da maharan suka rusa harsashin ginin a Masar"
Kalmar "dukka" a nan gaba ɗaya ce. Yana nufin mutane da yawa zasu mutu.
"Sojojin kawayen Masar za su firgita yayin da aka bar su ba tare da komai ba sai kasashen da aka watsar"
Kasancewa cikin biranen da aka rusa yana wakiltar lalacewa kamar halakar biranen wasu ƙasashe. AT: "garuruwansu za su lalace kamar biranen wasu ƙasashe"
Anan "sanya wuta a Masar" yana wakiltar tura sojoji don kai hari Masar da kunna wuta. AT: "lokacin da na aike da sojoji don ƙona Masar da wuta"
Manzanni za su kawo labarin halaka Masar zuwa Kush, wanda labarin zai firgita shi.
Cikakken sunan "baƙin ciki" da "azaba" ana iya fassara tare da kalmomin "wahala" da "azabtarwa." AT: "Mutanen Kush suma zasu sha wuya lokacin da na hukunta Masar"
"Zan yi hakan ne saboda kada Masar ta kara samun mutane da yawa."
Anan “hannu” yana wakiltar ikon sojojin Nebukadneza. Nebukadneza ne zai kawo wannan hukunci.
Wannan ƙari ne don a nuna cewa Babiloniyawa za su kashe Masarawa da yawa. Da akwai matattun Masarawa da yawa da har za a ga gawawwakinsu sun rufe ƙasar Masar duka. AT: "kashe mutane da yawa har sai ya zama kamar gawawwaki suna ko'ina"
"Zan busar da kogunan Masar"
Yahweh zai ba wa Babiloniyawa iko a kan Masar kamar yadda mutumin da ya sayar da abu yake ba wanda ya saya shi ya mallaki abin. AT: "Zan ba da ikon mallakar ƙasar ga mugayen mutane"
"Zan hallakar da gumaka marasa amfani"
Anan "sanya ta'addanci akan ƙasa" yana wakiltar haifar da mutanen ƙasar su firgita ƙwarai. AT: "Zan sa mutanen Masar su ji tsoro"
Anan "zubo fushina" yana wakiltar hukunta mutane ne saboda tsananin fushinsa. AT: "Gama zan yi aiki da tsananin fushin Felusiyom" ko "Saboda na yi fushi sosai, zan hukunta Felusiyom mai tsanani"
Anan "yankewa" yana wakiltar kashe mutane. AT: "kashe adadi mai yawa na mutanen a Tebes"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "makiya za su fasa ganuwar da gineginen a cikin Tebes" ko "makiya za su ruguza Tebes"
Waɗannan su ne birane a arewacin Masar.
Anan "birane" suna wakiltar mutanen garuruwan. Cikakken sunan "kamammu" ana iya bayyana shi da mafi ƙarancin suna "kamammu" ko kuma kalmar aikatau "kama" AT: "mutanen garuruwansu za su kasance kamammu" ko "maƙiyansu za su kama mutanensu kuma su tafi da su"
Kalmar "karkiya" a nan tana nufin ikon Masar na zaluntar mutane. AT: "lokacin da na dakatar da Masar daga zaluntar mutane" ko "lokacin da na kawo karshen ikon Masar na zaluntar sauran al'ummomi"
Ana amfani da wannan jumlar a nan don alamar farkon sabon ɓangaren labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
Anan "hannu" yana wakiltar rundunar sarki mai ƙarfi.
"Zan fisge takobi daga hannun Fir'auna"
"Zan fisge takobi daga hannun Fir'auna"
"Zan sa hannayen sarkin Babila su yi ƙarfi"
Anan "makamai na Fir'auna" suna ne na sojojinsa, kuma "zai faɗi" yana nuna rauni. AT: "amma sojojin Fir'auna ba za su iya yin nasara a kan abokan gaba ba"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Duba yadda kuka fassara irin waɗannan jimloli a cikin Ezekiyel 20:23.
1Sai ya zama a cikin shekara ta sha ɗaya, a wata na uku, a rana ta farko ta watan, da maganar Yahweh ta zo mani, cewa,2"Ɗan mutum, ka ce da Fir'auna, sarkin Masar, da kuma ga taron jama'arsa da ke kewaye da shi, 'girman kujerarka, kama da wa kake?3Duba! Asiriya ta zama sida a cikin Lebanon da kyawawan rassa, ta na bada inuwa ga jejin, kuma doguwa ce, kuma rassanta suka zama ƙoƙuwar itace.4Ruwaye masu yawa suka sa tayi tsayi; zurfafan ruwaye suka sa tayi faɗi. Rafuka suka gangara dukka kewaye da sashenta, gama hanyoyinsu sun bi ta dukkan hanyoyi zuwa ga dukkan itatuwan fili.5Tsawonsa mai girma yafi sauran itatuwa da ke a filin, kuma rassanta sun zama da yawa; rassanta suka yi tsayi sabili da ruwaye masu yawa sa'ad da suke girma.6Kowanne tsuntsun sammai na zama cikin rassanta, haka kuma kowacce halita mai rai na cikin filin suna haifar 'ya'yansu a ƙarƙashin inuwarsa. Dukkan al'ummai masu yawa suna zama a ƙarƙashin inuwarsa.7Gama yana da kyau a cikin girmansa da kuma tsayi a rassansa, gama saiwarsa na cikin ruwaye masu yawa.8Sida na cikin gonar Allah ba su kai shi ba. A cikin itatuwan gora babu waɗanda suka kai rassansa, kuma itacen durumi bai kai shi rassa ba. Babu wani itace a cikin lambun Allah da ke kamar sa cikin kyaunsa.9Na yi shi da kyau da rassansa masu yawa kuma dukkan itatuwan Iden da ke cikin lambun Allah suka yi kishinsa.10Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Saboda yana da tsawo, kuma ya sa dogayen rassansa a tsakanin rassansa, ya ɗaukaka zuciyarsa sabili da tsawonsa.11Na rigaya na bayar da shi cikin hannuwan jarumi na al'ummai, ya yi masa dai-dai da muguntarsa. Na wurga shi waje.12Bãƙi waɗanda ke ta'addanci a dukkan al'ummai suka datse shi suka bar shi ya mutu. Rassansa suka fãɗi a kan tsaunuka da kuma dukkan kwari, rassansa suka kakkarye a cikin dukkan magudanun ruwaye na ƙasar. Sai dukkan al'ummai na duniya suka fito daga ƙarƙashin inuwarsa suka kuma tafi suka bar shi.13Dukkan tsuntsayen sararin sama suka sauka bisa tushen itacen da ya fãɗi, kuma kowacce dabba ta fili ta zo rassansa.14Wannan ya faru ne domin kada wata itaciyar ta tsiro kusa da ruwayen ta ɗaga ganyayesu zuwa ga itatuwa mafiya tsawo, kuma kada waɗansu itatuwa su yi girma gefen ruwayen su kai tsayinta. Dukkan su an sa sun mutu, a can ƙasa, a cikin 'ya'yan mutane, tare da waɗanda suka gangara cikin rami.15Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: A ranar da sida ya gangara zuwa Lahira na kawo makoki cikin duniya. Na rufe zurfafan ruwaye bisanta, na kuma tsayar da ruwayen teku. Na tsai da ruwaye masu girma, na kuma kawo makoki ga Lebanon dominsa. Saboda haka dukkan itatuwan saura suka yi makoki sabili da shi.16Na kawo rawar jiki ga al'ummai ta dalilin ƙarar faɗuwarsa, a lokacin da na wurga shi cikin lahira tare da waɗanda suka gangara zuwa cikin rami. Sai na ta'azantar da dukkan itatuwan da ke a Iden a cikin wuraren duniya a ƙasa. Waɗannan su ne da zaɓaɓɓu da kuma mafi kyaun itatuwa na Lebanon; itatuwan da suka sha ruwan.17Gama suma suka gangara tare da shi zuwa Lahira, zuwa ga waɗanda aka kashe da takobi. Waɗannan su ne ƙarfin hannunsa, waɗannan al'umman da suka zauna cikin inuwarsa.18Wacce itaciya ce dai-dai da ke a ɗaukaka da girma? Gama za a kawo ki ƙasa tare da itatuwan Iden zuwa ƙarkashin ƙasa a tsakanin marasa kaciya; za ka zauna tare da waɗanda aka kashe da takobi.' Wannan shi ne Fir'auna tare da dukkan taronsa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."
Ana amfani da wannan jumlar a nan don alamar farkon sabon ɓangaren labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
"a ranar farko ga wata na uku." Wannan shine wata na uku na kalandar Ibraniyanci. Wannan rana ta farko tana kusa da farkon watan Yuni akan kalandar yamma.
"Waye babba kamar kai?" Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don gabatar da sabon batun. Fir'auna yayi zaton cewa al'ummarsa ita ce mafi girma, amma Allah yana shirin magana game da wata babbar al'umma. AT: "Kuna tsammani babu wata ƙasa wacce ƙarfin ta ya kai na ƙarfin ƙasarku."
Waɗannan kalmomin Allah ne ga Fir'auna game da Asiriya. Allah yana ba da sakonsa a cikin hanyar misali game da babban itacen al'ul.
"Saboda itacen al'ul na da ruwa da yawa, ya yi tsayi sosai"
"ruwan da ke zurfin ƙasa ya sanya itacen al'ul ya yi girma ƙwarai da gaske"
Misalin Yahweh game da itacen al'ul ya ci gaba.
"Itacen al'ul ya fi kowane sauran itatuwa tsayi"
"Duk tsuntsayen da suke shawagi a sararin sama sun yi sheƙan a rassansa"
"Dukkanin manyan al'ummomi sun rayu a inuwar wannan itaciyar." Anan "kasashe" suna wakiltar mutanen da suke zaune a wurin. AT: "Mutanen daga duk al'ummomi sun rayu a ƙarƙashin inuwar waccan itaciyar"
Wannan wata hanya ce ta nufin "gonar Eden."
Yahweh yana gwada yawan rassa da bishiyoyi. AT: "Babu ɗayan bishiyar gora da take da rassa kamar itacen al'ul"
"Na yi itacen al'ul da kyau ta hanyar ba ta dogayen rassa masu yawa"
Misalin Yahweh game da itacen al'ul ya ci gaba.
Kalmar "hannu" tana wakiltar iko. AT: "Na sanya shi a cikin ikon al'umma mafi ƙarfi" ko "Na ba wa al'umma mafi ƙarfi iko a kanta"
"Na kori itacen al'ul daga ƙasar itacen al'ul domin itacen al'arshi ya munana"
Cikakken sunan "ta'addanci" ana iya bayyana shi da "tsoro." Kuma a nan “al’ummai” suna wakiltar mutanen ƙasashe. AT: "wanda ya sa mutanen duk al'ummu su ji tsoro"
"baƙi sun karya reshen itacen al'ul"
Misalin Yahweh game da itacen al'ul ya ci gaba.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Kuma zahirin kalmar "mutuwa" ana iya bayyana ta "mutu." AT: "Na yi shi ne don duk su mutu su zurfafa a ƙarƙashin ƙasa"
Kalmomin "sun gangara zuwa Sheol" na nufin "sun mutu." AT: "A ranar da itacen al'ul ya mutu" ko "A ranar da aka sare itacen al'ul ɗin"
Cikakken sunan "makoki" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "Na sa duniya ta yi makoki"
Cikakken sunan "makoki" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "Na sanya Lebanon ta yi makokin itacen al'ul"
Anan "jefa shi ƙasa zuwa lahira" wani karin magana ne wanda ke nufin kisa. "Ramin" yana nufin kabari; saboda ana zaton kabari shine hanyar shiga lahira, rami shima yana wakiltar waccan duniyar. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 31:14. AT: "lokacin da na kashe itacen al'ul kuma ya tafi lahira tare da duk wanda ya mutu"
Anan “takobi” yana wakiltar maƙiyan da suka yaƙe su. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda makiya suka kashe da takuba" ko "wanda ya mutu a yaƙi"
"Wanne daga cikin waɗannan bishiyoyi a cikin Eden yake da ɗaukaka kamar ku kuma ya girma kamar ku?" Allah ya yi wa Fir'auna wannan tambayar don ya nuna masa cewa misalin ya shafe shi da ƙasarsa. Zai iya farawa tare da "Don haka Fir'auna" ko " Don Masar" AT: "Babu ɗayan bishiyun a cikin Eden da yayi dai-dai da ɗaukaka da girma!"
AT: "inda zaka kasance tare da mutanen da ba a yi musu kaciya ba"
1Sa'an nan ya kasance a cikin wata na sha biyu ta shakara ta sha biyu, a rana ta farko ga watan, da maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, tãda makoki domin Fir'auna sarkin Masar; ka ce masa, 'Ka na kamar ɗan zaki a cikin al'ummai, amma ka zama kama da dodon ruwa na cikin teku; ka na dama ruwa, ka na dãma ruwaye da ƙafafunka ka kuma yamutsa ruwayensu.3Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Haka zan warwatsa tãruna bisan ka cikin mutane da yawa, kuma za su ɗaga ka cikin tãruna.4Zan yashe ka cikin ƙasar. Zan wurga ka cikin fili in kuma sa dukkan tsuntsayen sammai su zauna bisanka; yunwar dukkan dabbobi masu rai a duniya za su ƙoshi ta wurin ka.5Gama zan sa naman ka a bisa tsaunuka, zan kuma cika kwarurruka da gawarka cike da tsutsotsi.6Sa'an nan zan watsar da jininka a bisa tsaunuka, ruwayen ƙarƙarshin ƙasa za su cika da jininka.7Bayan na katse ka, Zan rufe sammai in kuma baƙantar da taurarinsu; Zan rufe rana da giza-gizai, wata kuma ba zai bada haskensa ba.8Dukkan haske masu haskakawa a sammai zan baƙanta su bisan ka, zan kuma sa duhu bisa ƙasarka - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.9Da haka zan tsoratar da zuciyar mutane da yawa a cikin ƙasashen da ba ka sani ba, a lokacin da na kawo rushewarka a tsakiyar al'ummai, cikin ƙasashen da ba ka sani ba.10Zan firgita mutane da yawa saboda kai; sarakunansu za su girgiza cikin tsoro saboda kai a lokacin da zan jujjuya takobina a gabansu. A kowacce sa'a kowa zai yi rawar jiki saboda kai, a ranar faɗuwar ka.11Gama Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Takobin sarkin Babila zai auko gãba da kai.12Zan sa taron jama'arka mutanenka su faɗi ta hannun takobin jarumi - kowanne jarumi ɗan ta'adda ne ga al'ummai. Waɗannan jarumawa za su lalatar da fahariyar Masar su kuma lalata dukkan tarurrukanka.13Gama zan lalatar da dukkan garkunan da ke a bakin magudanun ruwaye masu yawa; tafin ƙafar mutum ba zai ƙara dãma ruwan ba, ko kuma kofatun dabbobi su dãma su.14Sa'an nan zan kwantar da ruwansu in sa ƙogunansu su zubo kamar mai - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.15A sa'ad da na maida Masar yasasshiyar ƙasa, lokacin da aka maida ƙasar abin wofi sarai da dukkan cikarta, bayan na kai hari ga mazaunanta, za su san cewa Ni ne Yahweh.16Za a yi makoki; 'ya'ya mata na al'ummai za su yi makoki domin ta; za su yi makoki domin Masar, domin dukkan taruwar jama'arta za su yi makoki - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."'17Hakanan ya faru a cikin shekara ta sha biyu, a ranar sha biyar ga wata, da maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,18"Ɗan mutum, ka yi kuka domin taron jama'ar Masar ka kuma jawo su ƙasa - ita da 'ya'yanta mata masu daraja na al'ummai-- zuwa cikin ƙarƙashin ƙasa tare da sụ waɗanada suke gangarawa cikin rami.19'Ki na da kyau fiye da wani? Je ƙasa ki kwanta da marasa kachiya.'20Za su faɗi daga cikin waɗanda aka kashe da takobi. An zare takobin! An miƙa ki ga takobin; za su kama ta tare da taron jama'arta.21Mafi ƙarfi daga cikin jarumawa a Lahira zai yi magana game da Masar da kuma abokan amanarta. Sun gangaro zuwa nan! Za su kwanta tare da marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.'22Asiriya ta na can tare da dukkan jama'arta. Kaburburanta suna zagaye da ita; dukkansu an kashe su da takobi.23Su waɗanda kaburburansu na can cikin wuri mai zurfin rami su na can, da dukkan jama'arta. Kaburburanta sun zagaye dukkan waɗanda aka kashe, su da suka faɗi ta wurin takobi, su da suka jawo masifa a bisa ƙasar masu rai.24Ilam na wurin tare da dukkan taron. kaburburanta na zagaye da ita; dukkan su aka kashe su. Waɗanda suka faɗi ta wurin takobi, su da suka gangara ƙasa babu kaciya zuwa wurin zurfafa na iyakar ƙasa, su da suka kawo ta'addancin su bisa ƙasar masu rai kuma su waɗanda suke ɗauke da kunyarsu, tare da waɗanda suke gangarawa cikin rami.25Suka shirya wa Ilam makara da dukkan taron ta cikin tsakiyar waɗanda aka kashe; kaburburanta sun zagaye ta. Dukkan su marasa kaciya ne, an sha zararsu da takobi, domin sun kawo ta'addancinsu cikin ƙasar masu rai. Domin haka suna ɗauke da kunyarsu, tare da su waɗanda suke gangarawa zuwa cikin rami a tare da dukkan waɗanda aka kashe, waɗanda suke gangarawa zuwa cikin rami. Ilam na cikin dukkan waɗanda aka kashe.26Meshek, Tubal, da dukkan taron suna wurin! Kaburburansu na kewaye da su. Dukkansu marasa kaciya ne, aka kashe da takobi, domin sun kawo ta'addancinsu cikin ƙasar masu rai.27Ba su kwanta da jarumawan da suka faɗi na marasa kaciya waɗanda suka gangara zuwa Lahira da dukkan makamansu na yaƙi ba, kuma da dukkan makamansu ƙarƙashin kawunansu da kuma kurakuransu bisa ƙasusuwansu. Gama su ne 'yan ta'adda na jarumawa a cikin ƙasar masu rai.28To ke, Masar, za a kakkarya ki a cikin takiyar marasa kaciya! Za ki kwanta tare da waɗanda aka sare su da takobi.29Idom na wurin tare da sarkinta da kuma dukkan shugabanninta. An sanya su cikin ƙarfinsu tare da waɗanda aka kashe da takobi. Tare da marasa kaciya suka kwanta, tare da waɗanda suka gangara cikin rami.30Sarakunan arewa suna wurin - dukkansu da kuma dukkan Sidoniyawa waɗanda suka gangara ƙasa tare da waɗanda aka sare su. Suna da matuƙar karfi kuma suka sanya waɗansu jin tsoro, amma yanzu suna wurin cikin kunya, marasa kaciya tare da waɗanda aka sare da takobi. Sun ji kunyarsu, tare da waɗanda suke gangarawa cikin rami.31Fir'auna zai gani ya kuma karfafa game da dukkan taron jama'arsa waɗanda aka sare da takobi - Fir'auna tare da dukkan sojojinsa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.32Na sa shi a matsayin mai ban tsoro a cikin ƙasar masu rai, amma za a ajiye shi ƙasa a tsakiyar marasa kaciya, cikin waɗanda aka sare da takobi, Fir'auna da dukkan taron jama'arsa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."
Ana amfani da wannan jumlar a nan don alamar farkon sabon ɓangaren labarin. Idan yarenku yana da hanyar yin wannan, kuna iya la'akari da amfani da shi anan.
Masar ta fi sauran al'ummomi ƙarfi, kamar zaki ya fi sauran dabbobi ƙarfi.
Fir'auna mai iko ne, amma kawai ya haifar da matsala ga wasu, kamar wannan dodo a cikin ruwa.
An yi maganar azabar Allah ga Fir'auna kamar dai sarki shi ne dodon kogin da aka kama cikin raga. AT: "Don haka zan tara mutane da yawa in jefa taru a kanku"
"Zan bar ku marasa ƙarfi a ƙasar." Dodo da yake da tsoro da karfi lokacin da yake cikin ruwa ba zai iya yin komai ba yayin da aka barshi a busashhiyar ƙasa.
Ana iya sanya wannan cikin tsari mai aiki. AT: "Zan cika rafuka da jininka"
Abu ne gama gari magana game da rayuwar mutum kamar dai fitila ce da za a iya kashewa. AT: "Lokacin da na halakar da ku"
Yahweh yayi magana game da sanya taurari duhu kamar yana sanya murfin samaniya. AT: "Zan sanya komai a sama ya yi duhu"
Ana maganar ƙasar Masar, wanda sarki ke wakilta, kamar gini ne wanda yake rushewa. AT: "lokacin da al'ummomi suka ji labarin yadda na hallaka ku"
Anan "rawar jiki" wani aiki ne da mutane sukanyi yayin da suke cikin tsoro ƙwarai. AT: "Kowannensu zai ci gaba da girgiza saboda tsoronsa"
Tunanin faɗuwa yana wakiltar mutuwa. AT: "lokacin da na halakar da ku"
Anan “takobi” yana wakiltar sojoji. AT: "Sojojin sarkin Babila za su kawo muku hari"
Cikakken sunan "ta'addanci" ana iya bayyana shi azaman "firgita" ko "tsoro." AT: "Kowane jarumi yana tsoratar da al'ummomi" ko "kowane ɗayansu yana tsoratar da al'ummomi"
"a wuraren da ake da ruwa da yawa"
Mai iya yiwuwa su ne 1) "Zan sa ruwan ya huce" ko 2) "Zan sa ruwan ya zama mai tsabta." Idan babu wanda ya tursasa ruwan, sai datti ya sauka sai ruwan ya bayyana.
Anan ra'ayin kai hari yana wakiltar lalatawa. AT: "lokacin da na halakar da duk waɗanda ke rayuwa a cikin ta"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "matan wasu al'ummomi" ko 2) "mutanen wasu al'ummomi"
"ku yi kuka da ƙarfi saboda sojojin Masar"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne (1) "mutanen ƙasashe masu ƙarfi" ko (2) "sauran ƙasashe masu ƙarfi."
Ana iya sanya wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Na bai wa Masar takobi"
"Makiyanta za su kwace Masar da mutanenta"
Kalmar "takobi" ishara ce ga sojoji waɗanda ke amfani da takobi don kashe mutane. Ana iya sanya wannan a cikin tsari mai aiki. AT: "Sojoji sun yi amfani da takubba don kashe su duka"
Cikakken sunan "ta'addanci" ana iya bayyana shi da "tsoro." AT: "waɗanda, lokacin da suke raye, suka sa mutane cikin tsoro ƙwarai"
Yahweh ya ci gaba da yi wa Ezekiyel magana game da al'umman Lahira.
Wannan yayi kamanceceniya da sashin farko na ayar. AT: "Mutanen da suka mutu sun ba Ilam wurin da za su kwanta a tsakaninsu"
Ana faɗar da tsoro ga mutane kamar ana kawo musu abu ne. Cikakken sunan "ta'addanci" ana iya fassara shi da kalmar aikatau.AT: "sun firgita kowa a ƙasar masu rai"
Mayaƙan mugunta sun rufe jikinsu, kodayake mutum yana tsammanin garkuwar su zata lulluɓe su cikin mutuwa.
Anan "Idom" tana wakiltar dukkan mutanen Idom. AT: "Mutanen Edom suna cikin Lahira tare da sarakunansu da dukkan shugabanninsu"
"Yariman da suka mallaki al'ummomi a arewa"
Ana maganar kunya kamar abu ne wanda mutum zai iya kaiwa inda ya tafi. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 32:24. AT: "waɗanda ke jin kunya" ko "waɗanda yanzu aka wulakanta"
Ana iya bayyana bayyane wanda Fir'auna zai gani. AT: "Fir'auna zai ga duk mutanen da suka mutu daga sauran al'ummomi"
"Duk da cewa Fir'auna yana raye, na sanya shi ya firgita mutane"
1Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Dan mutum, ka faɗa wa mutanenka wannan; ka ce masu, 'Sa'ad da na kawo takobi gãba da wata ƙasa, sai mutanen wannan ƙasar suka ɗauki ɗaya da ga cikin su suka maishe shi mai tsaro domin su.3Zai riƙa duba idan takobi ya taso wa ƙasar sai ya busa ƙahonsa ya faɗakar da mutane!4Idan mutanen suka ji ƙarar ƙaho amma ba su yi lura ba, idan kuma takobi ya zo ya kashe su, to kowanne ɗayansu alhakin jininsa na kansa.5Idan wani ya ji ƙarar ƙaho amma ya ƙyale, alhakin jininsa na kansa; amma idan ya kula, zai ceci na sa ran.6Idan kuwa, mai tsaro ya ga takobi yana tasowa, amma bai busa ƙaho ba, sakamakon bai faɗakar da mutane ba, takobi ya zo ya ɗauki ran wani, wannan mutum ya mutu cikin zunbinsa, zan biɗi alhakin jininsa daga hannun mai tsaro.'7Yanzu kai da kanka, ɗan mutum! Na saka ka zama mai tsaron gidan Isra'ila; za ka ji maganganu daga bakina kayi gargaɗi a madadi na.8Idan na cewa mugun mutum, 'Kai mugu, hakika za ka mutu!' Amma idan ba ka faɗakar da wannan ba domin a gargaɗi mugu game da hanyarsa, mugun nan zai mutu cikin zunubinsa, amma zan biɗi alhakin jininsa a hannun ka!9Amma idan kai, ka gargaɗi mugu game da hanyarsa, domin ya juyo ya bar ta, idan bai juyo yabar hanyarsa ba, to zai fa mutu cikin zunubinsa, amma kai da kanka ka riga ka ceci ranka.10Saboda haka, ɗan mutum, ka cewa gidan Isra'ila, 'Kuna cewa haka, 'Kurakuranmu da zunubanmu suna kanmu, muna kuma ruɓewa a cikin su! Ƙaƙa za mu rayu?'"11Ka ce masu, 'Muddin ina raye - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - ba na farinciki da mutuwar mugu, domin idan mugu ya tuba daga hanyarsa, zai rayu! Ku Tuba! Ku Tuba daga mugayen hanyoyinku! Donme ne ne za ku mutu, gidan Isra'ila?'12Yanzu kai, ɗan mutum, ka cewa mutanenka, 'Ayyukan adalcin adali ba zai cece shi ba idan ya yi zunubi! Muguntar mugun mutum ba za ta sa shi ya hallaka ba, idan ya tuba daga zunubinsa! Domin mai adalci ba zai iya rayuwa ba saboda adalcinsa idan ya yi zunubi.13Idan na cewa adali, "Ba shakka za ka rayu!" idan kuwa ya dogara ga adalcinsa sa'an nan ya aikata rashin gaskiya, ba zan tuna da adalcinsa ba ko guda ɗaya. Zai mutu saboda muguntar da ya yi.14Idan na cewa mugu, "Ba shakka za ka mutu," amma kuma sai ya tuba daga zunubinsa ya aikata abin adalci da gaskiya -15idan ya mayar da ƙwacen da ya yi da sunan jingina, ko kuma ya mayar da abin da ya sata, kuma idan ya yi tafiya a cikin farillan rai ya dena yin laifi - ba shakka zai rayu. Ba zai mutu ba.16Ba za a kuma tuna masa da laifofinsa waɗanda ya aikata ba. Gama ya aikata gaskiya da adalci, saboda haka, zai rayu!17Amma mutanenka suka ce, "Hanyar Ubangiji ba dai-dai take ba!" alhali hanyoyinku ne ba dai-dai ba!18Sa'ad da adali ya juya daga adalcinsa ya yi zunubi, zai mutu cikinsa!19Sa'ad da mugu ya juya ya bar muguntarsa ya yi abin da ke gaskiya da adalci, zai rayu saboda waɗannan abubuwa!20Amma ku mutane kun ce, '"Hanyar Ubangiji ba dai-dai ba ce!" Zan shar'anta kowannenku bisa ga hanyarsa, gidan Isra'ila.'"21Wannan ya faru a shekara ta goma sha biyu, a rana ta biyar ga watan goma na bautar talalarmu, wani ɗan gudun hijira ya zo guna da ga Yerusalem ya ce, "An ci birnin!"22Hannun Yahweh yana bisana da maraice kafin ɗan gudun hijiran ya zo, bakina kuma ya rigaya ya buɗe kafin lokacin zuwansa da safe. Bakina kuwa ya buɗe; ban ƙara yin shuru ba!23Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,24"Ɗan mutum, waɗanda suke zaune cikin kango a ƙasar Isra'ila suna magana suna cewa, 'Ibrahim kaɗai ne ya gaji ƙasar, amma mu, muna da yawa! An riga an ba mu ƙasar a matsayin mallaka.'25Saboda haka ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi: Kuna cin nama da jini, kuna bautar gumakanku sa'an nan kuna zubda jinin mutane. Lallai sai kun mallaki ƙasar?26Kun kafa dogararku ga takubba, kunyi abubuwan banƙyama; kowannenku yana zina da matar maƙwabcinsa. Ya kamata ku mallaki ƙasar kenan?'27Za ka faɗa masu haka, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Muddin ina raye, 'hakika waɗanda ke kufai za a kashe su da takobi, zan kuma bada waɗanda ke jeji ga hallitu masu rai su zama abincinsu, waɗanda ke cikin kagaru da koguna annoba za ta kashe su.28Sa'an nan zan maida ƙasar kufai da kuma abin tsoro, ƙarfinta na taƙama zai ƙare, gama za a bar duwatsun Isra'ila, ba wanda zai ratsa ta cikinsu.'29Gama za su sani Ni ne Yahweh, sa'ad da na maida ƙasar kufai a lalace saboda dukkan abubuwan banƙyamar da suka aikata.30Yanzu kai, ɗan mutum - mutanenka suna faɗin abubuwa game da kai a jikin garu da ƙofofin gidaje, suna cewa junansu - kowanne mutum ga ɗan'uwansa, 'Bari mu je mu saurari maganar annabi wadda ta zo daga Yahweh!'31Mutanena za su zo wurinka, kamar yadda suka saba yi, za su zauna a gabanka su saurari maganganunka, amma ba za su yi biyayya da su ba. Maganganu masu kyau suna bakinsu, amma zukatansu na bin ƙazamar riba.32Gama kai kamar waƙa mai daɗi ne a gare su, ƙyakkyawar murya da a ke rairawa a kan garaya, lallai za su kasa kunne ga maganarka, amma ba ko ɗaya da zai yi biyayya da ita.33Saboda haka idan duk waɗannan sun faru - duba! haka kuwa zai faru! - sa'an nan ne za su sani annabi ya kasance a tsakanin su."
Kalmar "takobi" tana nufin sojojin abokan gaba da suka kawo hari. Hakanan, "ƙasa" tana nufin mutanen da suke zama a wurin. AT: "sojoji don afkawa mutanen kowane yanki"
Anan “jini” yana wakiltar mutuwa. Kalmomin "a kansa kansa" salon magana ne da ke nufin za a ɗora wa mutum alhakin. AT: "Laifin nasu ne idan suka mutu"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Isra'ilawa.
Anan "takobi" yana wakiltar rundunar abokan gaba. AT: "sojojin makiya sun zo sun kashe kowa"
"wannan mutum ya mutu saboda nasa zunubi"
"ku gargade su a matsayin wakili na" ko "ku musu gargadi daga wurina"
Mutum ba ya yin halin sa ta wata hanya ana maganarsa kamar yana juyawa da jiki ya koma kan turba. AT: "zai iya daina aikata munanan abubuwa, kuma idan bai daina aikata munanan abubuwa ba"
"zai kiyaye kanka da rai"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "a kanmu" ishara ce da ke nufin suna jin laifi don laifuffukansu da zunubansu ko 2) "a kanmu" wata alama ce da ke nufin sun fahimci cewa Yahweh yana azabtar da su saboda laifuffukansu da zunubansu.
Anan "hanya" tana wakiltar yadda mutum yake. AT: "idan mugu ya daina aikata munanan abubuwa"
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa ba ya son mutanen Isra'ila su mutu. AT: "Kada ku zaɓi mutuwa, gidan Isra'ila!"
Cikakken sunan "adalci" ana iya bayyana shi azaman sifa "dai-dai." An nuna cewa ba zasu sami tsira daga azabar Allah ba. AT: "Idan mutanen kirki suka fara yin zunubi, gaskiyar cewa sun yi abin da ya dace a da ba zai hana ni hukunta su ba"
"yana mayar da abin da ya sata" ko "yana biyan diyyar abin da ya sata"
Yin magana ko yin abu ta wata hanya ana maganarsa kamar yana tafiya. AT: "yana rayuwa ne bisa dokokin da ke ba da rai"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga Isra'ilawa.
"mutu saboda zunubansa"
"wani ya tsere daga Yerusalem ya zo wurina" Kaldiyawa sun halaka Yerusalem kuma suka kashe mutanen Yerusalem, amma wasu mutane kaɗan sun tsere.
Maganar "birni" tana nufin "Yerusalem." Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Babiloniyawa sun lalata Yerusalem"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "waɗancan rusassun gine-ginen" ko 2) "waɗancan biranen da aka rusa"
Bayyanar sunan "mallaka" za'a iya bayyana shi a matsayin "mallaka." AT: "domin mu mallake ta"
Yahweh ya ci gaba da magana da Ezekiyel game da mutanen da suke zaune a kango Isra'ila.
Ana nuna cewa suna cin jini ta hanyar cin naman wanda har yanzu yana da jini a ciki. Yahweh ya umarce su su zubar da jinin. AT: "Kuna cin nama tare da jini a ciki"
"ku kalli gumakanku" Wannan salon magana ne. AT: "kuna bautar gumakanku"
Anan “jini” yana wakiltar rayuwar mutum. Zubar da jini wani karin magana ne da ke nufin kisan kai. AT: "ku kashe mutane"
"annoba za ta kashe mutanen da ke zaune a kagara da kogo"
Kalmar "shi" tana nufin ƙasar, wanda ke nufin mutanen ƙasar. AT: "mutanen ƙasar ba za su ƙara yin alfahari ba cewa sun fi ƙarfi"
"ba wanda zai rage ya yi tafiya cikin ƙasa ko bisa duwatsu"
Cikakken sunan "abubuwan ƙyama" ana iya bayyana shi azaman "abubuwan da na ƙi." AT: "duk abubuwan da suka aikata na tsana"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Suna magana game da ƙaunata, amma zukatansu suna bin riba mara kyau" ko 2) "Suna magana ne game da abubuwan da suke sha'awa, kuma zukatansu suna bin riba mara kyau "
Anan "zukata" suna wakiltar sha'awa. AT: "a cikin zukatansu suna son samun ribar rashin adalci" ko "suna son samun abubuwa ta hanyoyin da ba na adalci ba"
Anan "ku" yana nufin Ezekiyel, kuma a nan yana wakiltar saƙon da yake faɗa. Wannan ya kwatanta saƙon Ezekiyel da kyakkyawar waƙa, wanda ke nufin mutane suna jin daɗin saurarensa, amma ba su ɗauka cewa saƙon nasa yana da muhimmanci sosai da za a yi masa biyayya ba. AT: "suna tsammanin kalmominku kamar waƙa ce mai kyau"
"da gaske ne na aiko ka annabi a gare su"
1Sai maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2"Ɗan mutum, ka yi annabci gãba da makiyayan Isra'ila. Yi annabci ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya cewa makiyaya: Kaiton makiyayan Isra'ila masu kiwon kansu. Bai kamata masu kiwo su tsare garke ba?3Kuna cin rabo mai tsoka kuna kuma sa tufafi na ulu. Kuna yanka masu ƙiba cikin garke. Baku yin kiwo ko kaɗan.4Ba ku ƙarfafa waɗanda ke da cututtuka ba, ko ku warkar da marasa lafiya. Waɗanda suka karye, ba ku ɗori su ba, waɗanda aka kora ba ku dawo da su ba ko ku nemo ɓatattu. Maimakon haka, kun mallaƙesu ƙarfi da yaji.5Sai suka warwatse saboda ba makiyayi, suka zama nama ga kowanne mai rai a jeji bayan an warwatsar da su.6Tumakina suka yi makuwa a kan duwatsu da tsaunuka, suka kuma warwatsu a dukkan faɗin duniya. Duk da haka ba wanda ya ke neman su.7Saboda haka, makiyaya, ku ji maganar Yahweh:8Da dawwamata - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - saboda tumakina sun zama ganima da abinci ga kowanne naman jeji, saboda rashin makiyayan kirki, kuma masu kiwon garkena ba su nemo tumakin ba, amma makiyayan sun kãre kansu, ba su yi kiwon garkena ba.9Saboda haka, makiyaya, ku ji maganar Yahweh:10Ubangiji Yahweh ya faɗi: Duba! Ina găba da masu kiwon tumakina, zan nemi tumaki na a hannunsu. Sa'an nan zan sallame su daga kiwon garkena; makiyayan ba za su ƙara kiwon kansu ba tunda zan ƙwace garkena daga bãkinsu, domin kada tumakina su ƙara zama abincinsu.11Gama Ubangiji Yahweh ya faɗi: Duba! Ni da kaina zan nemo garkena in kuma lura da su,12kamar yadda makiyayi yakan nemi tumakinsa da suka watse daga cikin garkensa. Haka zan nemo tumakina, zan kuma cecesu daga dukkan wuraren da aka warwatsa su a ranar hadari da duhu.13Sa'an nan zan fito da su daga cikin al'ummai; zan tattaro su daga ƙasashe dabam dabam in kawo su ƙasarsu. Zan saukar da su a wurin kiwo mai dausayi a gefen duwatsu na Isra'ila, a maɓugɓugai, a dukkan wuraren da mutane ke zaune a ƙasar.14Zan sa su a makiyaya mai kyau; manyan duwatsun Isra'ila za su zama wurin kiwonsu. Za su kwanta a wurin kiwo mai kyau, inda akwai ciyawa da yawa, za su yi kiwo a tsaunukan Isra'ila.15Ni da kai na zan yi kiwon garkena, Ni da kaina kuma zan sa su kwanta - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne -16Zan nemo ɓatattu in kuma dawo da waɗanda aka watsar da su. Zan ɗora karyayyun tumaki, in warkar da marasa lafiya amma masu ƙiba da ƙarfafa zan hallaka su. Zan yi kiwo da adalci.17Yanzu dai ku, garkena - ga abin da Ubangiji Yahweh ya faɗa - duba, zan shar'anta tsakanin tunkiya da tunkiya, tsakanin raguna da bunsurai.18Bai isa ba ku ci ciyawa mai ƙyau, sai kun tattake ragowar da ƙafafunku; ku kuma sha ruwa mai kyau, sai kuma kun gurɓata rafin dukka da ƙafafunku?19Dole ne tumakina suci abin da kuka tattake da ƙafafunku, su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku?20Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗa masu haka: Duba! Ni da kaina zan shar'anta tsakanin tumaki masu ƙiba da ramammu,21domin kun tunkuɗe su da kwankwasonku da kuma kafaɗunku, kun kuma tunkuɗe dukkan marasa ƙarfi da ƙahonninku har sai da kuka warwatsar da su daga ƙasar.22Zan ceci garkena ba za su ƙara zama ganima ba, zan shar'anta tsakanin tunkiya da tunkiya!23Zan ɗora makiyayi guda a bisansu, bawana Dauda. Shi zai yi kiwon su, zai ciyar da su, zai kuma zama makiyayinsu.24Gama Ni, Yahweh, zan zama Allahnsu, kuma bawana Dauda zai zama sarki a cikin su - Ni, Yahweh, na furta wannan.25Sa'an nan zan yi alƙawarin salama da su in fitar da mugayen dabbobi a ƙasar, domin su zauna lafiya a jeji su kuma yi barci lafiya a kurmi.26Zan kuma kawo albarku a bisan su da kuma wurare kewaye da tuddaina, domin zan aiko da ruwan sama a lokacinsa. Zai zama ruwan albarka.27Sa'an nan itatuwan saura za su bada 'ya'yansu, ƙasa za ta bada amfaninta. Tumakina za su zauna lafiya a ƙasarsu; sa'an nan ne za su sani cewa Ni ne Yahweh, sa'ad da zan karya gungumen kãrkiyarsu, in kuma cece su daga hannun waɗanda suka bautar da su.28Ba za su ƙara zama ganima ga al'ummai ba, mugayen namomin jeji a bisa ƙasa ba za su cinye su ba. Gama za su zauna lafiya, ba kuma wanda zai tsoratasu.29Gama zan ƙebe masu mazaunin salama domin kada a ƙara zama da yunwa a cikin ƙasar, al'ummai kuma ba za su kawo zargi a kansu ba.30Sa, an nan za su sani cewa Ni, Yahweh Allahnsu, ina tare da su. Su jama'ata ne, gidan Isra'ila - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.31Gama ku tumakina ne, garken makiyayata, mutanena, ni kuma Allahnku ne - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'"
A cikin sura ta 34, Yahweh yayi magana game da mutanen Isra’ila kamar su garken tumaki ne kuma shugabannin Isra’ilawa makiyaya ne waɗanda ya kamata su kula da garken amma ba su yi ba.
Ana magana da shugabannin Isra'ila kamar makiyaya ne. Ya kamata su kula da mutanensu kamar yadda makiyaya ke kula da garken su. AT: "shugabannin Isra'ila waɗanda suke kamar makiyaya"
Shugabannin da ke kula da kansu maimakon mutane ana maganarsu kamar suna kiwon kansu. AT: "suna ciyarwa da kulawa da kansu"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga shugabannin Isra'ila. Yahweh yana ci gaba da magana da Isra'ilawa kamar garken tumaki da shugabannin Isra'ila kamar makiyaya ne waɗanda ba su kula da garken ba.
AT: "tumakin da suka karye ƙashi" ko "tumakin da suka ji rauni"
"da karfi da kuma mugunta"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sai suka watse saboda ba su da makiyayi"
AT: "dukkan dabbobin daji za su iya kawo hari su cinye su"
"saboda ba su da makiyayi"
"babu wani makiyayi na da ya nemo garkena"
"Ina adawa da makiyaya"
Jumlar "buƙatar ... daga hannunsu" magana ce da ke nufin riƙe ko ɗaukar wani da alhakin wani abu. AT: "Zan ɗora musu alhakin duk munanan abubuwan da suke faruwa ga garkena" ko "Zan hukunta su game da duk munanan abubuwan da suka bari garkena ya faru da su"
"makiyaya ba za su ƙara ci tumaki da awakin garkena"
"a cikin gajimare da rana mai duhu." Ana maganar bala'i kamar ranar duhu ce. AT: "lokacin da mummunan bala'i ya same su"
"daga wuraren da suka zauna tare da sauran mutane"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga shugabannin Isra'ila. Yahweh ya ci gaba da magana game da Isra'ilawa kamar garken tumaki. Anan yayi maganar kansa a matsayin makiyayinsu wanda zai kula dasu.
"ƙasashe waɗanda suke da ciyawa da tsire-tsire masu yawa"
"kunsa zani a jikin duk wani karyayyen kashin tumaki" ko "kunsa wani kyalle a jikin raunin ragon"
"Zan yi hukunci tsakanin tunkiya daya da tunkiya"
Kalmar "kaina" ta nanata cewa Yahweh ne zai yi hukunci.
Maganar "saita" kalma ce da ke nufin haifar da mutum ya mallaki wani. AT: "Zan sanya makiyayi guda ya zama mai kula da tumakina da awakin"
Anan "Dauda" yana nufin zuriyar Dauda. AT: "zuriyar bawana Dauda"
"alƙawarin da ke kawo salama"
Wasu sabon juyi na suna fassara wannan da "Ni kuma zan mai da su da wuraren da ke kewaye da tsauni na su zama albarka."
"Wannan ruwan sama zai zama albarka"
Anan “al’ummai” suna wakiltar mutanen ƙasashe. Cikakken sunan "raini" ana iya bayyana shi azaman aiki. AT: "ba za su ƙara jin mutanen al'ummomi suna zagin su ba"
AT: "Ni, Yahweh Allahnsu, ina taimaka musu"
Ana iya bayyana wannan azaman jumla ɗaya. AT: "tare da su, kuma cewa su mutanena ne"
1Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2'Ɗan mutum, kasa fuskarka gãba da Tsauna Seyir ka yi annabci gãba da shi.3Ka ce masa, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi: Duba! Ina gãba da kai, Tsauni Seyir, kuma zan buge ka da hannuna in maishe ka kufai abin watsarwa.4Zan maida biranenka kufai, kai kuma da kanka za ka zama kango; sa'an nan za ka sani cewa Ni ne Yahweh.5Domin kullum kana ƙiyayya da mutanen Isra'ila, kuma domin ka bashesu a hannun takobi a lokacin ƙuncinsu, a lokacin da hukuncinsu yake da zafi.6Saboda haka, Muddin ina raye - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - zan shiryaka domin zubar da jini, alhakin jini zai bi ka! Tun da ba ka ƙi zubar da jini ba, alhakin jini zai bi ka.7Zan maida Tsaunin Seyir kufai gaba ɗaya sa'ad da na datse mai shiga cikinsa da mai fita.8Sa'an nan zan cika duwatsunsa da gawawwakinsa. Da tuddansa da kwarurukansa da dukkan rafuffukansa, waɗanda aka kashe da takobi za su fǎɗa.9Zan sa ka yi ta zama kufai. Ba za a zauna cikin biranenka ba, amma za ka sani cewa Ni ne Yahweh.10Ka ce, "Waɗannan al'ummai biyu da ƙasashen nan biyu za su zama nawa, zan kuma mallakesu," koda yake Yahweh yana tare da su.11muddin ina raye - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - zan sãka maka gwargwadon fushinka da gwargwadon kishi da ƙiyayyar da ka yiwa Isra'ila, kuma zan bayyana kaina gare su sa'ad da na shar'anta ka.12Sa'an nan za ka sani cewa Ni ne Yahweh. Na ji ɓatancin da ka yi gãba da duwatsun Isra'ila, sa'ad da ka ce, "An lalatar da su; an rigaya an ba mu su mu cinye."13Ka ɗaukaka kanka gãba da ni da abin da ka faɗa, ka yi maganganu da yawa gãba da ni; na kuma ji su dukka.14Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Zan maishe ka kufai, dukkan duniya za suyi murna.15Kamar yadda ka yi murna da gãdon mutanen Isra'ila saboda ta zama kufai, kai ma zan yi haka da kai. Za ka zama kufai, Tsaunin Seyir da dukkan Idom - dukkanta! Sa'an nan za ka sani cewa Ni ne Yahweh."'
Yahweh ya gaya wa Ezekiyel ya yi annabci. Ezekiyel zai yi magana da Tsauni Seyir, amma saƙon ga dukkan mutanen Idom ne.
Tsauni Seyir ya yi nisa, saboda haka Ezekiyel ba zai iya gani ba, amma Yahweh ya umurce shi ya dube ta wannan hanyar alama ce ta cutar mutanen da ke wurin. Dubi yadda kuka fassara wata magana makamancin wannan a cikin Ezekiyel 6: 2. AT: "juya zuwa Tsauni Seyir ka zura ido" ko "ka kalli Tsauni Seyir don mutanen da ke wurin su cutu"
Yahweh ya gaya wa Ezekiyel ya yi magana da Tsauni Seyir kamar zai ji shi. Sakon ga dukan mutanen Idom ne. AT: "Ku saurara, Tsauni Seyir, zan buge ku da hannuna in maishe ku kufai da kango saboda abin da mutanenku suka yi"
Wannan ya ci gaba da saƙon da Ezekiyel zai yi wa Tsauni Seyir. Sakon ga dukan mutanen Idom ne.
Mai yiwuwa ma'anar wannan sune 1) "kun bashe su ga abokan gabansu waɗanda suka kashe su da takuba" ko 2) "kun kashe su da takuba."
Anan "zubar da jini" yana nufin don kisa. AT: "Zan sauƙaƙa magabtanku su kashe yawancinku"
"kufai har abada." Wannan na iya zama ƙari don jaddada halakarwa.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Wannan na iya zama ƙari don girmamawa. AT: "Mutane ba za su zauna a cikin garuruwanku ba"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Zan hore ku saboda fushinku da kishinku" ko 2) "kamar yadda kuka yi wa Isra'ilawa fushi da hassada, haka zan yi muku da fushi da hassada."
Mutanen Tsauni Seyir da suka karɓi ƙasar Isra'ila suka yi amfani da ita wa kansu ana maganarsu kamar dabbobi ne da za su cinye duwatsun Isra'ila. AT: "suna nan don mu cinye"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "Zan mai da ƙasarku ta zama kango" ko 2) "Zan yi murna idan ƙasarku ta zama kufai" ko kuma 3) "Zan sa wasu mutane su yi farin ciki saboda halakar ku"
1Yanzu dai, ɗan mutum, ka yi annabci ga tsaunukan Isra'ila ka ce, "Tsaunukan Isra'ila, ku saurari maganar Yahweh.2Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Magabci ya ce a kanka, "Aha!" kuma "Daɗaɗɗun tuddai na dã sun zama mallakarmu.'"3Saboda haka ka yi annabci kace, Ubangiji Yahweh ya ce: Saboda an maishe ka kufai an kuma murƙushe ka ta kowacce fuska, ka zama abin mallaka ga sauran al'ummai; ka zama abin ɓatanci a leɓuna da harsuna, a kuma labaran mutane.4Saboda haka, Tsaunukan Isra'ila, ku kasa kunne ga maganar Ubangiji Yahweh: Ubangiji Yahweh ya faɗi haka ga tsaunuka, da tuddai, da rafuffuka da kwarurruka, da kufafan da ba kowa da yasassun biranen da aka washe su sun zama ganima da abin ba'a ga sauran al'umman da ke kewaye da su -5saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Hakika nayi magana cikn zafin fushina da hasalata gãba da sauran al'ummai, gãba da Idom da dukkan waɗanda suka ƙwace ƙasata suka maisheta mallakarsu, gãba da dukkan masu murna a zuciyarsu ko reni a ruhunsu, yadda suka ƙwace ƙasata domin su mallaki wuraren kiwo su zama nasu.'6Saboda haka, ka yi annabci a kan ƙasar Isra'ila ka cewa tsaunuka da kuma tuddai, da rafuffuka da kwarurruka, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Duba! A cikin fushina da hasalata nake furta wannan domin ka jure da zage-zagen al'ummai.7Saboda haka, Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Ni da kaina zan ɗaga hannuna in rantse cewa al'ummai da ke kewaye daku tabbas za su sha tasu kunyar.8Amma ku, tsaunuka Isra'ila, za ku yi rassa ku haifi 'ya'ya domin mutanena Isra'ila, domin bada daɗewa ba za su komo wurinku.9Ku duba, Ni naku ne, na yi maku tagomashi; za a huɗe ku a kuma shuke ku da iri.10Saboda haka zan ruɓanya maku yawan mutanenku, koda dukkan gidan Isra'ila ne. Birane za su kasance da mazauna, za a sake gina rusassun wurare.11Zan riɓaɓɓanya mutum da dabba a kanku ku tsaunuka saboda su ruɓaɓɓanya su hayayyafa. Sa'an nan Zan sa a zauna a cikin ku kamar yadda kuke dã, zan sa ku yalwata fiye da dã, domin ku sani cewa Ni ne Yahweh.12Zan kawo mutane, jama'ata Isra'ila, su tattaka ku. Za su mallakeku, za ku zama gãdonsu, ba za ku ƙara sa 'ya'yansu su mutu ba.13Ubangiji Yaweh ya faɗi haka: Saboda suna ce maku, "Ku na cinye mutane, kuna sa 'ya'yan al'ummarku suna mutuwa,"14saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ba, ba za ku ƙara sa al'ummarku ta yi makokin mutuwarsu ba. Wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.15Ba zan ƙara bari ku sake sauraren zage-zagen al'ummai ba, ba za ku ƙara jin kunyan mutane ba ko ku sa al'ummarku ta faɗi - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'"16Sa'an nan maganar Yahweh ta zo wuri na, cewa,17"Ɗan mutum, sa'ad da gidan Isra'ila suka gaji ƙasarsu, suka ƙazamtar da ita ta wurin hanyoyinsu da ayyukansu. Hanyoyinsu a gabana kamar ƙazantar hailar mace suke.18Saboda haka na zuba hasalata gãba da su, domin zubar da jini da suka yi a ƙasar da kuma ƙazantarsu ta wurin gumakansu.19Na warwatsa su cikin al'ummai; suka warwatsu cikin ƙasashe. Na hukunta su gwargwadon hanyoyinsu da ayyukansu.20Sai suka tafi cikin al'ummai, duk inda suka tafi, sai suka ɓata sunana mai tsarki sa'ad da mutane suka ce masu: 'Da gaske waɗannan mutanen Yahweh ne? Gama an fitar da su daga ƙasarsa.'21Amma ina da juyayi saboda sunana mai tsarki wanda gidan Isra'ila ya ƙazantar cikin al'ummai lokacin da suka tafi can.22Saboda haka ka cewa gidan Isra'ila, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: 'Ba saboda ku nake wannan ba, gidan Isra'ila, amma saboda sunana mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al'ummai dukkan inda kuka tafi.23Gama zan sa sunana mai girma ya zama da tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al'ummai - a tsakiyar al'ummai, kuka ɓata shi. Sa'an nan al'ummai za su sani cewa Ni ne Yahweh - wannan furcin Ubagiji Yahweh ne - sa'ad da za ku ga Ni mai tsarki ne.24Zan kwasoku daga cikin al'ummai, in tattaro ku daga kowacce ƙasa, zan kawo ku ƙasarku.25Sa'an nan zan yayyafa maku tsabtataccen ruwa domin ku tsarkaka daga dukkan ƙazantarku, zan kuma tsarkake ku daga gumakanku.26Zan ba ku sabuwar zuciya da sabon ruhu a cikinku, zan ɗauke zuciyar dutse daga cikinku. Gama zan ba ku zuciyar tsoka.27Zan sa Ruhuna a cikinku in sa ku kuyi tafiya a cikin farillaina da kiyaye umarnaina, domin ku yi su.28Sa'an nan za ku zauna a ƙasar da na ba kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuma in zama Allahnku.29Gama zan ceceku daga dukkan ƙazantarku. Zan sa hatsi ya yawaita. Ba zan ƙara nawaitaku da yunwa ba.30Zan yawaita 'ya'yan itatuwa da amfanin gona domin kada ku ƙara jin kunya a wurin al'ummai saboda yunwa.31Sa'an nan za ku yi tunani a kan mugayen hanyoyinku da ayyukanku masu banƙyama, za ku nuna naɗama a fuskokinku sabili da zunubanku da kuma mugayen ayyukanku.32Ba dominku nake yin wannan ba - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - yakamata ku san wannan. Saboda haka, ku kunyata ku ƙasƙanta, saboda hanyoyinku ku gidan Isra'ila.33Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: A ranar da na tsarkake ku daga dukkan kurakuranku, zan sa ku zauna a birane, ku kuma gina rusassun wurare.34Gama za ku noma ƙasa wadda take kufai a dã masu wucewa wurin ba za su gane ta ba.35Sa'an nan za su ce, "Wannan ƙasa wadda dă kufai ce yanzu ta zama kamar lambun Iden; rusassun birane da rusassun wurare waɗanda suka zama kufai an yi masu garu a na kuma zama a cikin su."36Sa'an nan sauran al'ummai da ke kewaye daku za su sani cewa Ni ne Yahweh, mai gina rusassun wurare da mai zaunar da mutane a yasassun wuri. Ni ne Yahweh. Ni na faɗi haka, zan kuma aiwatar da shi.37Ubangiji Yahweh ya faɗi: Gidan Isra'ila za su roƙe ni in yi masu haka, in riɓaɓɓanya su kamar garken mutane.38Kamar garken da aka keɓe domin hadayu, kamar garke a Yerusalem a lokacin bukukuwan idi, haka rusassun birane za su cika da ɗumbun mutane za su kuma sani cewa Ni ne Yahweh."'
Yahweh ya gaya wa Ezekiyel ya yi annabci. Ezekiyel zai yi magana da duwatsun Isra’ila, amma saƙon ga dukan Isra’ilawa ne.
Allah yana son Ezekiyel yayi magana da duwatsu kamar mutane. Saƙon ga mutanen Isra'ila ne.
Wannan yana nufin manyan duwatsu na Isra'ila. AT: "Tsoffin tsaunuka."
"saboda an kawo muku hari ta kowace fuska" ko "saboda makiyanku sun kawo muku hari ta kowace fuska"
"cewa makiya suka sata daga"
Wannan yana magana ne game da fushin Yahweh kamar wuta. Yahweh yana kaunar Isra'ila sosai, saboda haka yana da kishi da hasala lokacin da wasu al'umman suka yi masa ba'a. AT: "saboda tsananin kishi na" ko "saboda tsananin fushina"
Anan “zuciya” da “ruhu” suna wakiltar halayen mutum. Za'a iya bayyana ra'ayoyin samun farin ciki da ƙyama da kalmomin "farin ciki" da "raina." AT: "waɗanda suka raina mutanen Isra'ila kuma suka yi murna yayin da suka karɓi ƙasata"
"wasu al'ummomi sun zage ku" ko "wasu al'ummomin sun yi muku ba'a"
Anan "ɗaga hannuna" aiki ne na alama wanda ke nuna zai aikata abin da ya rantse da gaske. AT: "Na rantse da gaske"
Mutanen da suke fuskantar kunya ana maganarsu kamar zasu ɗauki kunyarsu. AT: "lalle mutane za su yi izgili ga al'umman da suka kewaye ku"
Anan "ku" yana nufin dutsen Isra'ila wanda anan yake wakiltar bishiyoyi akan dutsen da zasu bada 'ya'ya. AT: "bishiyoyinku za su yi girma suna ba da 'ya'ya"
"Zan tausaya muku"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Sannan mutane za su zauna a cikin birane kuma za su sake gina kango"
Ana nuna cewa a da yara sun mutu saboda rashin isasshen abinci a ƙasar. Yanzu ƙasar za ta samar da wadataccen abinci.
Wannan yana magana ne akan duwatsu kamar suna iya ji yayin da mutane suka zage su. AT: "Ba zan ƙara barin sauran al'ummomi su zage ku ba"
Gashi ana maganar kunya kamar dai duwatsu zasu iya daukar kunya. AT: "al'ummomin ba za su ƙara sanya ku jin kunya ba"
"ta hanyar yadda suka rayu da kuma abubuwan da suka aikata"
Wannan yana kwatankwacin yadda mutane sukayi da dabi'ar mace mai tsafta. Wannan yana nanata yadda ƙyamar halayensu suke ga Yahweh. AT: "Hanyoyinsu sun zama abin ƙyama a gare ni kamar rashin jinin al'ada na mace"
Ana maganar mutanen da suke bautar gumaka kamar gumakan sun ƙazantar da ƙasar da jiki. AT: "saboda sun ƙazantar da ƙasar da gumakansu"
Waɗannan jimlolin biyu suna nufin abu ɗaya daidai. Dubi yadda kuka fassara wata kalma makamancin wannan a cikin Ezekiyel 12:14. AT: "Na sa su rabu kuma suna zaune a cikin yankuna daban"
Anan “suna” yana wakiltar Yahweh da mutuncinsa. AT: "sun yi min ba'a"
"saboda ku" ko "domin ya taimake ku"
An yi magana game da gafarta wa mutane da kuma sa su daina yin zunubi kamar zai tsabtace su da ruwa. Kalmar "za a tsarkake ku" ana iya bayyana ta cikin sigar aiki. AT: "Zan tsarkake ku kamar ina yayyafa muku ruwa mai tsarkakakke, kuma zan sa ku daina bautar gumaka"
"duk abubuwan da suka sa ka kazanta"
Anan “zuciya” da “ruhu” suna wakiltar tunanin mutum, halaye, da motsin rai. Duba yadda kuka fassara "zuciya" da "ruhu" a cikin Ezekiyel 11:19.
Wannan yana magana ne game da mutane masu taurin kai kamar dai an yi zukatansu da dutse. Duba yadda kuka fassara "zuciyar dutse" a cikin Ezekiyel 11:19. AT: "zuciya mai tauri kamar dutse"
Mutanen da suke son bauta wa Yahweh ana maganarsu ne kamar suna da taushi kamar nama. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 11:19. AT: "zuciya mai taushi kamar nama"
Ana magana da mutumin da yake aikatawa ko yin abu ta wata hanya idan mutum ne yake tafiya. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 11:19. AT: "ba ku damar biyayya ga dokokina"
"Zan kira hatsi ya zo." Wannan jumlar tana gabatar da hatsi a matsayin bawan Yahweh. AT: "Zan sa hatsi ya kasance a ƙasar Isra'ila"
Ana magana akan Yahweh wanda ke haifar da yunwa a cikin ƙasa kamar ya sanya yunwa akan mutane. AT: "Ba zan ƙara haifar da yunwa ba" ko "Ba zan ƙara sa abinci ba"
"san wannan" ko "zaka iya tabbatar da wannan." Yahweh ya faɗi haka ne don ya nanata cewa ba don mutane suna da kirki ba ne zai sa su maido da su. Ana iya motsa wannan jimlar zuwa farkon ayar.
Kalmomin "kunya" da "ƙasƙantattu" suna da ma'anoni iri ɗaya. Tare suna jaddada tsananin abin kunyar. AT: "Don haka ku ji kunya ƙwarai"
"zaka noma kasar da ta lalace"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) "cewa abokan gaba suka wargaza" ko kuma 2) "wanda mutane ba su iya shiga ciki"
"dasa shuki a cikin kufai"
Yahweh yana sa mutane su yawaita da sauri kuma ana magana da sauri kamar garken tumaki. Tumaki suna ninkawa da sauri sosai. AT: "don sanya su yawaita kamar garken tumaki" ko "don sanya mutane yawaita da sauri kamar tumaki"
1Hannun Yahweh yana bisa na, ya fito da ni waje ta wurin Ruhun Yahweh kuma ya zaunar da ni a tsakiyar wani kwari; yana cike da ƙasusuwa.2Daga nan ya sani na bi ta tsakiyar su ina ta zagayawa, Duba! Da yawansu birjik suna cikin kwarin. Duba! Ga su busassu ƙayau.3Sai ya ce mani, "'Dan mutum, ƙasusuwan nan za su iya rayuwa kuma?" Sai na ce, "Ubangiji Yahweh, kai kaɗai ka sani."4Daga nan ya ce mani, "'Ka yi annabci a kan waɗannan ƙasusuwa ka ce masu, 'Busassun ƙasusuwa. Ku saurari maganar Yahweh.5Ubangiji Yahweh ya cewa ƙasusuwan nan: Duba! Zan sa numfashi a cikinku, za ku kuma rayu.6Zan sa jijiyoyi a jikkunanku in kuma sa tsoka. Zan rufe ku da fata in hura numfashi a cikinku domin ku rayu. Daga nan za ku sani cewa Ni ne Yahweh.'"7Sai na yi anabci kamar yadda ya umarce ni; da na ke anabcin, duba, sai wata ƙara ta fito, mai girgiza. Sai ƙasusuwan suka marmatso ga junansu - ƙashi ya haɗu da ƙashi a mahaɗinsu.8Da na duba, ai kuwa, sai ga jijiyoyi a kansu, tsoka kuma ta fito fata kuma ta rufe su. Amma ba numfashi a cikinsu tukuna.9Daga nan Yahweh ya ce mani, "Yi anabci a kan numfashi, yi anabci, ɗan mutum, ka ce da numfashi, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Numfashi, ka zo daga kusurwai huɗu, ka hura a kan waɗannan da aka kashe, domin su rayu.'"10Sai na yi anabci kamar yadda aka umarce ni; numfashi ya shiga cikinsu suka rayu. Daga nan suka miƙe a kan ƙafafunsu, babbar rundunar mayaƙa.11Daga nan Yahweh ya ce da ni, "Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwan gidan Isra'ila ne dukka. Duba! Suna cewa, 'Kasusuwanmu sun bushe, zuciyarmu ta karai. An datse mu.'12Saboda haka ka yi anabci ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Duba! Zan buɗe kabarbarunku in tashe ku daga cikinsu, ya ku mutane na. Zan dawo daku ƙasar Isra'ila.13nan za ku sani cewa Ni ne Yahweh, sa'ad da na buɗe kabarbarinku na tashe ku daga cikin su, mutane na.14Zan sa Ruhuna a cikin ku domin ku rayu, zan sa ku huta a ƙasarku sa'ad da kuka sani ni ne Yahweh. Ni na faɗa kuma zan aikata - wannan furcin Yahweh ne.'"15Sa'an nan maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,16"Yanzu dai, ɗan mutum, ka ɗauki sanda guda domin kanka ka yi rubutu a kan sa, 'Domin Yahuda da mutanen Isra'ila abokan tarayya.' Sa'an nan ka ɗauki wata sandar ka yi rubutu a kansa, 'Domin Yosef reshen Ifraim kuma domin dukkan mutanen Isra'ila, abokan tarayya.'17Haɗa biyun su zama sanda guda, domin su zama ɗaya a hannunka.18Sa'ad da mutanenka za su yi maka magana, su ce, 'Ba za ka gaya mana abin da kake nufi da waɗannan ba?'19sai ka ce masu, 'Ubangiji Yahweh ya ce: Duba! Ina ɗauke reshen Yosef da ke hannun Ifraim da kabilar Isra'ila abokan tarayyarsa domin in haɗa shi da Yahuda, domin su zama sanda guda, za su kuma zama ɗaya a hannuna.'20Ka riƙe sandunan da ka yi rubutu a kansu a hannunka a kan idanunsu.21Ka furta masu, Ubangiji Yahweh yafaɗi wannan: Duba! Ina gab da fitar da mutanen Isra'ila daga cikin al'ummai inda suka tafi. Zan tattaro su daga ƙasashen kewaye in kuma dawo da su ƙasarsu.22Zan tattaro su al'umma ɗaya a ƙasar, a kan tsaunukan Isra'ila, sarki guda ne zai yi sarauta bisansu dukka, ba za su ƙara zama al'umma biyu ba. Ba za a ƙara raba su zuwa masarautai biyu ba.23Daga nan ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumakansu ba, da abubuwansu na ban ƙyama, ko kowanne irin zunubansu ba. Gama zan cece su daga dukkan ayyukan rashin aminci waɗanda da su suka yi mani zunubi, zan kuma tsarkake su, domin su zama mutanena ni kuma in zama Allahnsu.24Bawana Dauda zai zama sarki bisansu. Domin su kasance da makiyayi ɗaya a bisansu dukka, za su yi tafiya bisa ga dokokina su kuma kiyaye farillaina su yi biyayya da su.25Za su zauna a ƙasar da na ba bawana Yakubu, inda ubanninku suka zauna. Za su zauna cikin ta har abada - da su, da 'ya'yansu, da jikokinsu, gama bawana Dauda zai zama sarkinsu har abada.26Zan kafa alƙawarin salama da su. Zai zama madawwamin alƙawari ne da su. Zan kafa su in ruɓanɓanya su, in kuma kafa wurina mai tsarki a tsakaninsu har abada.27Mazaunina zai kasance tare da su; zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena.28Daga nan al'ummai za su sani cewa Ni ne Yahweh da na ƙeɓe Isra'ila da bam, sa'ad da wurina mai tsarki yana cikinsu har abada.'"
Kalmar "hannu" ana amfani da ita don nuni ga ƙarfi ko aikin wani. Mutum tare da hannunsa akan wani mutum yana da iko akan wannan mutumin. Dubi yadda kuka fassara makamancin magana a cikin Ezekiyel 1: 3.. AT: "Yahweh ne yake iko da ni"
"a kowane bangare"
"Saurari saƙon Yahweh"
Kalmar suna "numfashi" za'a iya bayyana ta azaman kalmar "shaka." AT: "Zan sa ku numfasawa"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "kamar yadda Yahweh ya umarce ni da in yi magana"
Kalmar suna "numfashi" za'a iya bayyana ta azaman kalmar "numfashi." AT: "Amma ba su numfashi" ko "Amma ba su da rai"
"daga hanyoyi huɗu da iska za ta iya shiga ciki." Wannan karin magana ne. AT: "daga kowane bangare"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "waɗannan mutanen da abokan gaba da bala'i suka kashe"
Kalmar "gida" ishara ce ga dangin da ke zaune a gidan, a wannan yanayin Isra'ilawa, zuriyar Yakubu cikin shekaru da yawa. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 3: 1.
Waɗannan su ne maganar da Yahweh ya yi wa gidan Isra'ila.
"ku zauna lafiya a yankinku"
Anan "Don" yana nufin "wakilci." AT: "Wakiltar Yahuda" ko "Na Yahuda Ne"
Wannan yana nufin Isra’ilawan da ke zaune a masarautar kudanci ta Yahuda. AT: "duk kabilun Yahuda" ko "kabilun Isra'ila waɗanda suke wani ɓangare na mulkin Yahuda"
Yosef shi ne mahaifin Ifraim. Kabilar Ifraim suna zaune ne a masarautar arewacin Isra'ila. Anan ana amfani da sunaye don wakiltar duk masarautar arewa.
"don su zama sanda ɗaya"
"me sandunanku suke nufi" ko "me yasa kuke da sandunan nan"
"sandar Yusuf." Wannan yana wakiltar mulkin Isra'ila.
Kalmar "hannu" tana nufin iko. AT: "wannan yana cikin ikon Ifraim" ko "cewa kabilar Ifraim ke mulki"
"sandar Yahuda." Wannan yana wakiltar masarautar Yahuza.
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 5:11.
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 11:19.
Wannan yana magana ne game da sarki yana mulkin mutane kamar dai shi makiyayi ne mai jagorantar tumaki. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 34:22.
Wannan yana magana ne game da aiki ko yin abubuwa a wata hanya kamar dai mutum ne yake tafiya. AT: "zai rayu kamar yadda na umarta"
"alkawarin da ke kawo zaman lafiya." Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 34:25.
"tsattsarkan wuri mai tsarki" ko "tsattsarkan haikali na"
"wurin da nake zama"
1Maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,2Ɗan mutum, ka juya ka fuskanci Gog, ƙasar Magog, babban yariman Meshek da Tubal; ka kuma yi anabci gãba da shi.3Ka ce, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Duba! ina gãba da kai, Gog, babban yariman Meshek da Tubal.4Domin in juya ka in kuma sa maka ƙugiya a muƙamuƙinka; Zan fitar da kai da dukkan sojojinka, da dawakai, da mahaya dawakan, dukkansu sun sa kayan yaƙi sosai, babbar runduna da manyaan garkuwoyi da ƙananan garkuwoyi, dukkan su suna riƙe da takubba!5Fasiya, Kush, da Libiya suna tare da su, dukkan su da garkuwoyi da hulunan kwano!6Goma da dukkan rundunarta, da Bet Togama, daga arewa mafi nisa, da dukkan rundunarta! Mutane da yawa na tare da kai!7shiri!, ka shirya kanka da tawagarka da suka yi layi tare kai, ka zama kwamandansu.8Bayan waɗansu kwanaki da waɗansu za a kiraka, kuma bayan waɗansu shekaru za ka je wata ƙasa da ta farfaɗo daga takobi wadda kuma aka tattaro daga mutane masu yawa, tattare aka koma tsaunin Isra'ila wanda ya ci gaba da zama kango. Amma mutanen ƙasar za a fito da su daga mutanen, kuma za su zauna cikin tsaro, dukkan su!9Saboda za ka tashi sama kamar yadda hadari ke yi; za ka zama kamar girgijen da yake rufe ƙasar, da duk rundunar sojojinka, da sojoji masu yawa da ke tare da kai.10Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: zai kuma faru a wannan ranar da aka tsara wannan shiri a zuciyarka, kuma za ka ɓata mugayen shirye-shirye.'11Daga nan za ka ce, zan je can buɗaɗɗiyar ƙasa; zan je wurin mutane masu natsuwa da ke zama cikin tsaro, dukkan su da ke rayuwa a inda babu garu ko danga, inda babu ƙofofin birane.12Zan kwaso kayayyaki in saci ganima, domin in kawo hannuna gaba da kangayen da yanzu mutane suka fara zama, da kuma gaba da al'ummai waɗanda ke samun dabbobi da kayayyaki, waɗanda kuma ke zama a tsakiyar duniya.'13Sheba da Dedan, da 'yan kasuwar Tarshish haɗe da matasan mayaƙanta za su ce da kai, Kun zo ne domin ku kwashi ganima? Kun tattara sojoji ne domin ku kwashi ganima, domin ku kwashi azurfa da zinariya, ku kuma kwashi dabbobinsu da kayayyaki ku kuma kwashi garar ganimar yaƙi?'14Saboda haka, ɗan mutum ka yi anabci, ka ce da Gog, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: A wannan rana, lokacin da mutanena Isra'ila na zama cikin tsaro, ba za ku koyi wani abu ba game da su?15Za ku fito daga wurarenku a can arewa mafi nisa tare da babbar rundunar sojoji, dukkan su suna kan dawakai, babbar runduna, manyan mayaƙa.16Za ka kai hari ga mutanena Isra'ila kamar girgijen da ya rufe ƙasar. A kwanaki masu zuwa zan kawo ka gãba da ƙasata, domin ƙasashe su san ni a lokacin da na nuna kaina ta wurinka, Gog, ka zama da tsarki a idanunsu.17Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ba ku ba ne waɗanda na yi magana a kan ku a waɗancan kwanaki ta hannun bayina, annabawan Isra'ila, waɗanda suka yi anabci a nasu lokuttan game da shekarun da zan kawo ku gãba da su?18Haka zai faru a waɗancan kwanaki bayan Gog ya kai hari ƙasar Isra'ila - wannan furcin Yahweh ne - fushina zai yi ƙuna a cikin hasalata.19A cikin himmata da kuma cikin wutar fushina, na furta cewa za'a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra'ila.20Za su girgiza a gabana - da kifayen teku da tsuntsayen sama, da dabbobin saura, da dukkan dabbobi masu rarrafe a duniya, da kowanne mutum da ke a doron ƙasa. Za'a ragargaza duwatsu ɓallin zai faɗi, har sai kowacce kusurwa ta faɗi a kan duniya.21Zan kawo takobi a kansu a kan dukkan duwatsu -wannan shi ne furcin Ubangiji Yahweh - kowanne mutum zai juya takobinsa gãba da ɗan'uwansa.22Bayan wannan zan hukunta shi da annoba da jini; da kuma ambaliyar ruwa da aman duwatsu da tattatsin wuta zan saukar a kansa shi da rundunarsa da dukkan al'umman da ke kewaye da shi.23Domin zan nuna girmana da tsarkina zan kuma sa al'ummai da yawa su san ni, za su kuma sani cewa Ni ne Yahweh.'"
Wannan sunan shugaba ne ko sarki wanda yayi mulki a kasar Magog.
Ana nuna cewa Magog shine ƙasar da Gog yake mulkin sa. AT: "Gog wanda ke mulkin ƙasar Magog"
Wannan furcin ya bayyana sau biyu a cikin waɗannan ayoyin. Wasu sifofin zamani, suna fassara kalmar Ibraniyanci a matsayin "shugaban Rosh, Meshek, da Tubal." Wannan wani taken ne na Gog. AT: "wanene babban basaraken Meshek da Tubal"
Yahweh ya ci gaba da magana da Gog.
Anan "ƙugiya a cikin muƙamuƙin" yana wakiltar ikon Allah akan Gog. Mutane suna sanya ƙugiya a cikin bakin dabbobi domin su iya kai dabbobin duk inda suke so.
al'ummar da ta rayu a arewacin Bahar Maliya
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 27:14.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan kira ku ku zo don yaƙi"
"duk rundunonin ka da ka tattara kansu" ko "duk rundunonin ka da ka tara kansu"
"a wancan lokacin"
Anan "zuciya" tana nufin tunaninsa. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "zaku yi tunanin shirye-shirye"
Yahweh ya ci gaba da magana da Gog.
Yahweh yayi amfani da wannan tambaya don ya nanata cewa hakika Gog zai ji labarin mutanen da ke Isra'ila. AT: "A wannan rana, lokacin da mutanena Isra'ila ke zaune lafiya, za ku ji labarinsu."
Yahweh yayi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa shi ne ya kawo Gog zuwa ƙasar Isra’ila. AT: "Kai ne ... kawo maka su."
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Yahweh zai sa duwatsu su faɗi"
Yana iya zama da taimako canza tsarin wannan jumla. AT: "Zan yi ruwan sama mai yawa a kansa da ƙanƙarar duwatsu da ƙibiritu mai ƙuna a kansa"
1"Yanzu, kai ɗan mutum, ka yi annabci gãba da Gog ka ce, Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Duba! ina gãba da kai Gog, sarkin Meshek da Tubal.2Zan juya ka in bi da kai; Zan kawo ka daga can arewa in kawo ka tsaunukan Isra'ila.3A sa'an nan ne zan bugi bakanka daga hannunka na hagu in kuma sa kibiya ta faɗi daga hannunka na dama.4Za ka fãɗi ƙasa matacce a kan tsaunukan Isra'ila -kai da tawagar da ke tare da kai da kuma sojojin da ke tare da kai. Zan miƙa ka ga tsuntsayen sama da dabbobin dawa ka zama abincinsu.5Za ka faɗi ƙasa a saura, domin ni da kaina na furta haka - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.6Daga nan zan aika da wuta a kan Magog a kan kuma masu zama cikin tsaro a wurare masu nisa, za su kuma sani cewa Ni ne Yahweh.7Domin zan sa su san sunana mai tsarki a tsakiyar mutanena Isra'ila, kuma ba zan taɓa yadda sunana ya ɓaci ba; al'ummai za su sani cewa Ni ne Yahweh, mai Tsarki na Isra'ila.8Duba! Rana na zuwa, kuma za ta zo - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.9Masu zama a biranen Isra'ila za su fita za su mori makamai su kunna wuta su ƙone su - ƙananan garkuwoyi, da manyan garkuwoyi, da bakkuna, da kibau, da kwarin mashi; za su wuta da su har tsawon shekaru bakwai.10Ba za su tattara itatuwa daga saura ba ko su sassaro bishiyoyi daga dawa, tun da ya ke za su ƙona makamansu; za su ɗauka daga wurin waɗanda ke son su ɗauka daga gare su; za su baje waɗanda suka so su baje su - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."11Kuma zai zamana a wannan rana zan tanada wuri domin Gog - maƙabarta a Isra'ila, kwari ga waɗanda ke tafiya cikin gabashin kwarin teku. Zai toshe waɗanda ke son ƙetarewa su haye. A can za su binne Gog da dukkan mutane masu yawa da ke tare da shi. Za su kira shi kwarin Hamon Gog.12Har tsawon watanni bakwai gidan Isra'ila za su binne su domin su tsarkake ƙasar.13Domin dukkan mutanen ƙasar za su binne su; za su zama abin tunawa a gare su a lokacin da na sami ɗaukaka - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.14A sa'an nan ne za su keɓe mutanen da za su ci gaba da tafiya a cikin ƙasar, domin su sami waɗanda ke tafiya a ciki, amma waɗanda suka mutu gangar jukkunansu kuma na waje a ƙasar za su iya su binne su, domin su tsarkake ƙasar. A ƙarshen shekarun nan bakwai za su fara bincikensu.15A lokacin da mutanen nan ke tafiya a cikin ƙasar, bayan sun ga ƙashin mutum za su sa alama a gefenta, har sai masu haƙar kabari sun zo domin su binne su a kwarin Hamon Gog.16Za'a sami wani birni a can ta wurin sunan Hamona. A wannan hanya za su tsarkake ƙasar.17Yanzu a gare ka, ɗan mutum, Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ka faɗi wannan ga dukkan tsuntsayen sama da dukkan dabbobin daji, 'Ku taru wuri ɗaya ku zo. Ku tattaru daga ko'ina ku kewaye hadayar da ni kaina nake miƙawa a kan tsaunukan Isra'ila, domin ku ci gangar jiki ku kuma sha jini.18Za ku ci jikkunan mayaƙa ku kuma sha jinin shugabannin duniya; za su zama raguna, da 'yan raguna, da awaki. da bijimai, duk sun yi ƙiba a Bashan.19Daga nan za ku ci wadataccen kitse ku ci ku ƙoshi; ku kuma sha jini har sai kun bugu; wannan ita ce hadayar da zan yanka dominku.20A kan teburina za ku ƙoshi da dawakai, da karusai, da mayaƙi, da dukkan jaruman yaƙi - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.'21Zan sa ɗaukakata a cikin al'ummai, kuma dukkan al'ummai za su ga hukuncina da nayi da kuma hannuna da na sa nake gãba da su.22Gidan isra'ila za su sani cewa Ni ne Yahweh Allansu daga wannan rana zuwa gaba.23Al'ummai za su sani cewa gidan Isra'ila sun je bauta saboda laifofinsu wanda ta wurinsu suka bashe ni, domin haka na ɓoye fuskata daga gare su, na kuma miƙa su ga abokan gãbarsu domin a hallaka dukkan su da takobi.24Na yi masu gwargwadon ƙazantarsu da zunubansu, a lokacin da na kawar da fuskata daga gare su.25Saboda haka Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan; Yanzu zan komo da damar Yakubu, kuma zan ji tausayin dukkan gidan Is'raila, a lokocin da na yi haka da himmar sunana mai tsarki.26A lokacin za su sha kunyarsu a cikin dukkan cin amanar da suka bashe ni. Za su manta da duk wannan a lokacin da suka huta a cikin ƙasarsu cikin tsaro, inda ba wanda zai firgita su.27lokacin da na komo da su daga cikin jama'a na kuma tattaro su daga ƙasar maƙiyansu, zan nuna kaina a matsayin mai tsarki a idon al'ummai masu yawa.28Sa'an nan za su sani cewa Ni ne Yahweh Allahnsu, domin na aika su zuwa bauta a cikin al'ummai, amma zan sake tattara su a ƙasarsu. Ba zan rage ko ɗaya daga cikinsu ba a cikin al'ummai.29Ba zan sake ɓoye fuskata daga garesu ba a lokacin da na huro Ruhuna a kan gidan Isra'ila - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."
Yahweh ya ba wa Ezekiyel saƙonsa ga Gog.
Ana buga bakan Gog da kibiyoyin daga hannuwansa ana magana kamar Allah yana lalata ikon soja Gog.
Yahweh ya ba wa Ezekiyel saƙonsa ga Gog.
A nan amfani "sunana mai tsarki" yana nufin halin Yahweh. Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "Zan sa jama'ata, Isra'ila, su san cewa ni mai tsarki ne"
sandunan katako da aka yi amfani da su azaman makami
Wasu sabon juyi zamani sun fassara kalmar Ibraniyanci a nan "zuwa gabas zuwa teku."
"Kwarin Babban Sojojin Gog"
"binne sojojin Gog"
Yahweh ya ci gaba da gaya wa Ezekiyel abin da zai faru da Gog.
Wannan sunan yana nufin "Babban Sojoji."
"zuwa idi" ko "zuwa yanka." Yahweh yana nufin cewa zai ba tsuntsaye da dabbobi abinci mai kyau ba wai yana bauta musu ba.
Ana iya bayyana hakan ta hanyar aiki. AT: "duk sun yi kiba yayin kiwo a Bashan"
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel sako game da tsuntsaye da namomin jeji game da abin da za su yi da Gog.
Kalma "karusai" na nufin mutanen da suke cikin karusar. AT: "mutanen da suke hawan karusai"
Yahweh yana maganar ɗaukakarsa kamar zai sanya shi a tsakiyar al'umman da za su gan shi. AT: "Zan sa al'umman duniya su ga ɗaukana"
Duk waɗannan jimlolin suna nuni ne ga hukuncin da Yahweh zai yi wa Isra’ila kuma an maimaita su don ƙarfafawa. Ana iya haɗa su cikin jimla guda. AT: "yadda zan hukunta su"
Anan “fuska” na nuni ga taimako da kariyar Yahweh. AT: "Na daina kare su da kula da su"
Fassara "zai dawo da sa'a" kamar yadda yake a cikin Ezekiel 16:53. Koyaya, wasu juyii na zamani suna fassara kalmar Ibraiynanci anan kamar "zasu dawo da Yakubu daga bauta."
Anan "gani" shine wani magana don fahimta. AT: "kasashe da yawa zasu fahimci cewa ni mai tsarki ne saboda abinda nayi wa gidan Isra'ila"
Anan bada Ruhu magana ne akan "zubo" Ruhun. AT: "lokacin da na bayar da Ruhuna da karimci ga gidan Isra'ila"
1A cikin shekara ta ashirin da biyar ta bautar talalarmu a farkon shekara a rana ta goma ga wata, A shekara ta sha huɗu bayan an kame birnin a wannan dai ranar, hannun Yahweh na bisana ya kuma ɗauke ni zuwa can.2A cikin wahayai daga Allah sai ya kawo ni zuwa ƙasar Isra'ila. Ya kawo ni in huta a kan tsauni mai tsawo sosai; a ɓangaren kudu inda abin da ya bayyana ya zama gine-ginen birni.3Sai ya kawo ni can. Sai ga wani mutum! Bayyanuwarsa kamar bayyanuwar tagulla. Yana ɗauke da igiyar linin da sandar awo a hannunsa, sai ya tsaya a bakin ƙofar birnin. Mutumin ya ce da ni,4"Dan mutum, ka duba da idanunka ka kuma saurara da kunnuwanka, ka kuma maida hankali ga dukkan abin da nake bayyana maka, domin an kawo ka nan ne domin in bayyana maka su. Ka bada rahoton duk abin da za ka gani ga gidan Isra'ila."5Akwai katangar da ta kewaye haikali. Tsawon sandar awon a hannun mutumin kamu shida ne. Dukkan mizanan tsawonsu iri ɗaya. Sai ya auna katangar; ta kai kamu ɗaya da rabi na tsawon sandar awon.6Daga nan sai ya tafi ƙofar haikali da ke fuskantar gabas. Sai ya hau kan matakansa ya auna ginshiƙin ƙofar tsawonsa shi ne dai-dai tsawon sandar gwajin a zurfi.7Ɗakunan tsaron dukkan su kamun sandar awon ɗaya a tsawo kuma ɗaya ne a fãɗi; akwai tsawon kamu biyar a tsakanin kowanne ɗakuna biyu, kuma daga dankarin shirayin haikalin akwai kwararo mai tsayi da aka kafa ƙasa.8Sai ya auna kwararon ƙofar; faɗinsa ya kai kamu guda na sandar awon.9Ya auna kwararon ƙofar. Zurfinsa ya kai kamu guda na sandar awo. Madogaran ƙofofin sun kai kamu biyu a fãɗi. Wannan shi ne kwararon ƙofar da ke fuskantar haikali.10Akwai ɗakunan tsaro guda uku a kowacce kwana a ɓangaren gabas, kuma dukkan su suna da awo iri ɗaya ne, kuma katangar da ta raba su ita ma awo iri ɗaya ne.11Daga nan mutumin ya auna faɗin ƙofar shiga - aka sami kamu goma; kuma faɗin ƙofar shiga - ya kai kamu goma sha uku.12Sai ya auna katangar da ke iyaka da ɗakuna na gaba - tsayinta kamu guda ne. Aka auna ɗakunan kowannen su ya kai kamu shida a kowanne gefe.13Daga nan sai ya auna ƙofar shiga daga rufin ɗaya daga cikin ɗakin har zuwa ɗaki na gaba - aka sami kamu ashirin da biyar, daga ƙofar farko ta shiga ɗakin har ya zuwa ta biyun.14Daga nan ya auna katangar da ta bi ta tsakanin ɗakunan tsaron - tsawonsu ya kai kamu sittin; ya auna har ya zuwa kwararon ƙofar.15Mashigi daga ƙofar gaba har ya zuwa kwararon ƙofar ƙarshen kamu hamsin.16Akwai kullallun tagogi a kusa da ɗakunan da kuma kusa da madogaran da ke cikin dukkan ƙofofin da ke kewayen; hakannan kuma zaurukan. Akwai tagogin da ke kewaye a ciki, kuma kowanne ƙyaure an yi masa ado da itacen kwakwa.17Sai mutumin ya kawo ni harabar waje da haikalin. Duba, ga ɗakuna, akwai gefen hanya a harabar, da kuma ɗakuna sittin a gaban harabar, da ɗakuna talatin gaba da gefen hanyar.18Gefen hanyar ya bi ta gefen ƙofofin, kuma fasalinsu ɗaya ne da tsawon ƙofofin. Wannan shi ne gefen hanya mafi kwari.19Sai mutumin ya auna nisan daga gaban ƙaramar ƙofa zuwa gaban ƙofofi na ƙurya; kamu ɗari ne daga bangon gabas, haka kuma yake a bangon arewa.20Daga nan sai ya auna tsawo da fadin ƙofar da ke arewa a can cikin harabar waje21Akwai ɗakuna guda uku a kowanne gefe na ƙofar, ƙofar da kwararonta duk suma an auna su kamar yadda aka auna babbar ƙofar - tsawonta dukka kamu hamsin ne sai fadinta kuma kamu ashirin da biyar ne22Tagogin, da kwararon, da ɗakunan, da bishiyoyin dabinon da aka sa a ƙofar da ke fuskantar gabas. Taki bakwai su ne suka kai kwararonsa.23Akwai kuma wata ƙofar daga ciki wadda ke fuskantar arewa, kamar dai yadda akwai ƙofa a gabas; mutumin ya auna daga ƙofa ɗaya zuwa ƙofa ɗaya - ya sami kamu dari na nisa.24A gaba sai mutumin ya kawo ni ƙofar shiga ta kudu, kusurwarta da tsawonta suma ya auna su kamar yadda ya auna sauran ƙofofin.25Akwai tagogi da ke a kulle a kan hanyar ƙofar da kwararonta kamar dai irin na waccan ƙofar. Kofar kudu da kwararonta tsawonta kamu hamsin ne faɗinta kuma kamu ashirin da biyar ne.26Akwai kuma ƙofa zuwa can ƙuryar harabar daga bangon kudu tsawonta kamu ɗari ne.27Akwai matakai bakwai da ake hawa zuwa ƙofar da kwararonta akwai kuma itacen dabino da aka kewaye katangar da su a kowanne gefe.28Sai mutumin ya kawo ni ƙuryar harabar ta hanyar ƙofarsa ta kudu, wadda ke da awo irin na sauran ƙofofin.29da bangayen, da kwararon duk awonsu dai-dai ne da na sauran ƙofofin; kuma akwai tagogi a ko'ina a kwararon. ƙofar ciki da girmanta kamu hamsin ne na tsawo kuma faɗinta kamu ashirin da biyar ne.30Kuma akwai kwararo da suka kewaye katangar ta ta ciki a ko'ina; waɗannan ne ma su kamu ashirin da biyar a tsawo da kuma kamu biyar na faɗi.31Wannan kwararo ya fuskanci harabar waje da aka kewaye da sassaƙaƙƙun itatuwan dabino a bangonta kuma akwai matakai takwas da a ke takawa a hau samanta.32Daga nan sai mutumin ya kawo ni cikin haraba ta ƙurya ta bangon gabas ya kuma auna ƙofar, ita ma awonsu ɗaya da sauran ƙofofin.33Ɗakunansa, da bangayen, da kwararon suma an auna su kamar yadda aka auna sauran ƙofofin, kuma awonsu dai-dai, kuma akwai tagogi a kewaye a ko'ina. Ƙofar ciki da kwararonta an auna tsawonsu kamu hamsin, faɗinsu kuma kamu ashirin da biyar.34Kwararonta na fuskanci harabar waje; kuma tana da itatuwan dabino a kowanne gefe kewaye da matakai takwas na hawa bisansa.35A gaba sai mutumin ya kawo ni ƙofar arewa ya kuma auna ta; awonta dai-dai ne da sauran ƙofofin.36Ɗakunanta, da bangayenta, da kwararonta duk ɗaya suke da sauran ƙofofin, akwai kuma tagogi a kewaye a ko'ina. ƙofar shiga da kwararonta an auna kamu hamsin na tsawo, sai kamu ashirin da biyar na faɗi.37Kwararonta na fuskantar harabar waje; tana kuma da itatuwan dabino a kowacce kusurwarsa da kuma matakai takwas na hawa samansa.38Akwai ɗaki da ƙofa a kowanne gefe na hanyoyin shiga da ke ciki. Wannan ne wurin da suke ɗauraye baye-baye na ƙonawa.39Da tebura guda biyu a kowanne gefen kowanne kwararo, inda a ke yanka baikon ƙonawa a kai, haka kuma baiko na zunubi da kuma baiko na laifi.40Bangon harabar, da ya bi ta ƙofa zuwa arewa, akwai tebura guda biyu. Hakan nan a ɗaya gefen shi ma akwai tebura guda biyu a kwararon ƙofar.41Akwai kuma tebura guda huɗu a kowanne gefe wurin ƙofa; su na yanka dabbobi a kan teburan nan guda takwas.42Akwai kuma tebura huɗu na yakkakken dutse domin baye-baye na ƙonawa, tsawonsu kamu ɗaya da rabi, sanan faɗinsa rabin kamu ne, tsayinsa kuma kamu guda ne. A kansu suke ɗora kayayyakin da suke yanka baye-baye na ƙonawa da su.43Aka kakkafa matsirai guda biyu tsawonsu kamun hannu ne a kwararon kewaye da ko'ina, domin a dinga ƙyafe naman baye-bayen da za'a miƙa a kan teburan.44A waje da ƙofar ciki, a cikin harabar ciki, akwai ɗakuna na mawaƙa, ɗaya daga gefen arewa yana fuskantar kudu, ɗayan kuma daga gefen kudu yana fuskantar arewa.45Bayan haka sai mutumin ya ce da ni, "Wannan ɗakin da ke fuskantar kudu domin firistoci ne waɗanda ke kan aiki a cikin haikali.46Ɗakin da ke duban arewa na firistocin da ke kan aiki ne a bagadi. Waɗannan sune 'ya'yan Zadok da suka zuwa kusa da Yahweh domin su bauta masa; suna cikin 'ya'yan Lebi."47A gaba sai ya auna harabar - tsawo kamu dari faɗi kuma kamu ɗari ne, tare da bagadi a gaban gidan.48Sai mutumin ya ɗauko ni ya kawo ni kwararon gidan ya kuma auna madogaran ƙofofin - kaurinsu ya kai kamu biyar a kowanne gefe. Hanyar shiga ita kanta kuma sha huɗu ne a faɗi, kuma bangayen kowanne gefe faɗinsu kamu uku ne.49Tsawon kwararon ya kai kamu ashirin, kuma zurfinsa ya kai kamu sha ɗaya. Akwai matakai da suka nufe shi sama da lungunan da ke a kowanne gefen gini.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "Babiloniyawa sun kame birnin Yerusalem"
"Ya sanya ni ƙasa"
"Yahweh ya kawo ni wurin da yake da gine-gine"
"igiya da aka yi da lilin." Wannan kayan aiki ne don auna nisan nesa.
Wannan kayan aiki ne don auna guntun nisa.
AT: "gaba ɗaya a kewayen yankin haikalin"
"gaba ɗaya a kewayen yankin haikalin"
Waɗannan ɗakunan aka gina a ciki yayin ƙofar inda masu tsaron suke tsaron ƙofar.
"ɗakunan da ke kusa da juna kamu biyar ne a tsakaninsu" ko "akwai kamu biyar tsakanin ɗaki da ɗayan kusa da shi"
Wannan sutura ce a gaban ƙofar ko ƙofa tare da ginshiƙai ko posts don tallafi. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiel 8:16.
"Ya kasance sanda ɗaya faɗi"
"wurin da yake bakin ƙofar"
"tagogin yana kewaye da ciki"
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 10: 3.
AT: "kuma akwai dakuna 30 kewaye da daɓen"
"ƙofar da take gefen gabas na haikalin"
Ezekiel ya ci gaba da bayanin wahayin haikalin da na mutumin da ya yi kama da tagulla.
"yana da ma'aunai kamar ƙofofin arewa da na gabas"
"ƙofar falon yana fuskantar farfajiyar waje"
"kuma yana da zane-zane na dabino"
Mai yiwuwa ma'anar "su" sune 1) mutanen da ke kawo sadaka ko 2) firistocin da suka yanka dabbobin.
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "sun kashe hadayar ƙonawa" ko "sun kashe dabbobin da za su ƙona a matsayin hadaya"
Ana iya bayyana wannan ta hanyar aiki. AT: "za su ɗora naman hadayar a kan teburin"
"ɗakuna don mawaƙa." Koyaya, wasu juzu'an da na zamani suna karanta "ɗakuna" ne kawai ba tare da ambaton mawaƙa ba.
"waɗanda ke aiki a haikalin" ko "waɗanda ke da alhakin tsare haikalin"
"kuma bagaden ya kasance"
"ƙofofin gidan"
1Sai mutumin ya kawo ni cikin wuri mai tsarki na haikali, sai ya auna madogaran ƙofofin - faɗinsa kamu shida ne ta kowanne gefe.2faɗin hanyar ƙofar ya kai kamu goma; bagon a kowanne gefe ya kai kamu biyar a tsawo. Daga nan sai mutumin ya auna fasalin wuri mai tsarki - tsawonsa kamu arba'in da faɗinsa kamu ashirin.3Daga nan mutumin ya tafi ya shiga wuri mafi tsarki ya auna madogaran hanyar ƙofar - aka sami awo biyu, hanyar ƙofar kuma kamu shida ne faɗinsa. Bangayen ta kowanne gefe kamu bakwai ne a faɗi.4Daga nan sai ya auna tsawon ɗaki - awo ashirin ne. Faɗinsa kuma - kamu ashirin ne zuwa gaban sararin haikalin. Daga nan sai ya ce mani, "Wannan shi ne wuri mafi tsarki."5Sai mutumin ya auna bangon gidan - kaurinsa kamu shida ne. Faɗin kowanne gefen ɗaki kewaye da gidan kamu huɗu ne a faɗi.6Akwai ɗakuna a gefe bisa hawa ku, ɗaki ɗaya bisa ɗaya, akwai ɗakuna talatin a kowanne hawa. Akwai ginshiƙai kewaye da bangon gidan, domin su zama makarai na dukkan ɗakunan da ke gefe, domin babu makarin da aka sa a bangon gidan.7To ɗakunan gefen suka faɗaɗa suka kewaya suka nufi sama, domin gidan ya zama bene kan bene a kewaya; ɗakunan suna faɗaɗa yayin da gida ke yin sama, hawan benen ya hau zuwa mataki mafi bisa, ta cikin mataki na tsakiya.8Sa'an nan na ga sashen da aka ɗaga dukkan kewayen gidan, da harsashe domin ɗakunan gefe; an auna shi kamun tsayin sanda - wato awo shida.9Faɗin bangon ɗakunan gefe ta waje awo biyar ne. Akwai kuma wuri buɗaɗe a wajen waɗannan ɗakunan a masujada.10A ɗaya gefen na wannan buɗaɗɗen fili akwai ɗakunan firistoci da ke waje; wannan filin faɗinsa ya kai awo ashirin a dukkan kewayen masujadar.11Akwai ƙofofi a cikin ɗakunan gefe daga wani buɗaɗɗen filin -akwai kuma wata hanyar ƙofar daga bangon arewa, da kuma wata daga kudu. Faɗin wannan buɗɗaɗen fili dukka kamu biyar ne.12Ginin da ya fuskanci harabar daga yamma ya kai kamu saba'in a faɗi. Bangonsa kuma da aka auna ya kai kamu biyar a kauri a kewaye da ko'ina, tsawonsa kuma ya kai kamu tasa'in.13Daga nan sai mutumin ya auna masujadar - tsawonsa kamu ɗari ne. Ginin da ke ware, da bangonsa, da harabar duk suma an auna su tsawonsu kuma ya kai kamu ɗari.14Faɗin gaban harabar a gaban masujadar shi ma kamu ɗari ne.15Sai mutumin ya auna tsawon ginin da ke bayan masujadar, zuwa yammacinsa, da ɗakunan ajiya da ke a dukkan gefen - aka sami awo ɗari. Wuri mai tsarki da kwararon,16da bangayen ciki da tagogi da duk da ƙananan tagogi, da ɗakunan ajiya kewaye da dukkan hawa ukunnan, duk an ƙayata su da katako17A saman hanyar shiga zuwa masujada ta ciki da kuma filin da ke wurin shi ma duk an auna shi.18An yi masa ado da kerubim da itatuwan dabino a tsakanin kowanne kerubim da kerubim, kuma kowanne kerubim na da fuskoki biyu:19fuskar mutum na duban itacen dabino ta gefe ɗaya da kuma fuskar sagarin zaki da ke duban ɗaya gefen. Sun kewaye ko'ina na gidan,20Doga ƙasa har zuwa saman hanyar ƙofa, an kewaye shi da kerubim da kuma itatuwan dabino a dukkan bangon gidan21Madogaran ƙofar wuri mai tsarki an yi masu zagaye. Kammanninsu kamar kamannin22bagadin katako ne a gaban wuri mai tsarki, wanda bisansa kamu uku ne, tsawonsa kuma kamu biyu ne ta kowanne gefe. Madogaran kusurwa, da harsashen, da matokaranta, da katako aka yi su. Sai mutumin ya ce da ni, "Wannan shi ne teburin da ke tsaye a gaban Yahweh."23Akwai ƙofofi ruɓi biyu manne domin wuri mai tsarki da kuma wuri mafi tsarki.24Waɗannan ƙofofin suna da maƙalatun ƙofa guda biyu, maƙalatun ƙofa biyu domin kowacce ƙofa.25Aka sassaƙa a kansu - a kan ƙofofin wuri mai tsarki - kerubim ne da itatuwan dabino, kamar dai yadda aka yi wa bango ado, kuma an yi rufin katako a kan kwararon daga gaba.26Akwai kuma tagogi da itatuwan dabino a gefen kwararon waɗannan su ne ɗakunan da ke gefen gidan, suma kuma suna da rufi a sama.
Mutumin da ke wahayin Ezekiyel (Ezekiyel 40: 3) ya ci gaba da nuna wa Ezekiyel kewaye da haikalin.
"kamar faɗin wuri mai tsarki"
Fassara "sanda" kamar yadda yake a cikin Ezekiyel 40: 5.
"ɗakunan gefen firistoci waɗanda suke nesa da wuri mai tsarki"
"baranda"
"an yi kyau"
"wuri mai tsarki da wuri mafi tsarki duka suna da ƙofofi biyu"
"kamar yadda bangon kuma yana da zane-zanen kerubim da dabinai
1A gaba sai mutumin ya aike ni waje zuwa harabar ciki daga wajen arewa, sai ya kawo ni ɗakuna a gaban harabar waje da kumabangon waje daga kudu.2Waɗannan ɗakunan sun kai kamu ɗari a tsawonsa a gaba sai kuma kamu hamsin na faɗi.3Waɗansu daga cikin ɗakunan sun fuskanci harabar ciki nisansu daga masujadar ya kai kamu ashirin. Akwai ɗakuna hawa uku waɗanda ke sama suna duban ƙasa na waɗanda ke ƙasa da su, an kuma bubbuɗe masu ƙofofin da a ke bi. Waɗansu ɗakunan kuma suna duban haikalin.4Sararin wucewa kamu goma ne na faɗi da kuma kamu ɗari na tsawo su ne a gaban ɗakunan. Ƙofofin ɗakunan na duban arewa.5Amma ɗakunan taro na sama ƙanana ne daga nan ne a ke samun hanyar wucewa, ƙofofin suna da faɗi fiye da filin da ke a ƙasa da kuma tsakiyar matakai na ginin.6Domin ɗakunan taron da ke hawa na uku ba su da shingaye. Ba kamar harabar ba, da ke da shingaye. To benayen da ke can sama ƙanana ne in kwatanta da girman ɗakunan da ke ƙarƙas da kuma benaye na hawan tsakiya.7Bangon da ke waje ya bi ta kusa da harabar ciki, harabar da ke gaban ɗakunan. Wannan bangon ya kai kamu hamsin a tsayi.8Tsawon ɗakunan ya kai kamu hamsin, ɗakunan da ke fuskantar masujada kamunsu kamu ɗari ne a tsawo.9Akwai hanyar shiga ta ɗakunan da ke kwari da ke gefen gabas, da suka fito daga wajenharabar waje.10A gefen bangon harabar waje da ke gefen gabas da harabar waje, a gaban harabar ciki na masujada, akwai kuma waɗansu ɗakunan11da hanyar wucewa a gabansu. Suna kama da bayyanuwar ɗakunan a gefen arewa. Suna da tsawo da faɗi iri ɗaya kuma kasancewar iri ɗaya ne da jerin da ƙofofin.12A gefen kudu akwai ƙofofin zuwa cikin ɗakuna waɗanda suke dai-dai da da na gefeb arewa. Sararin wucewa daga ciki yana da ƙofa bisa kansa, kuma sararin wucewar ya buɗe zuwa cikin ɗakuna daban-daban. A gefen gabas akwai hanya da ke zuwa sararin wucewar a ƙarshe ɗaya.13Daga nan sai mutumin ya ce da ni, "Ɗakunan da ke arewa da kuma ɗakunan da ke kudu waɗanda ke a gaban harabar waje ɗakuna ne masu tsarki inda firistocin da ke aiki kusa da Yahweh za su iya cin abinci mafi tsarki. Za su ajiye abubuwa mafiya tsarki a can - baiko na abinci, da baiko na zunubi, dabaiko na laifi - domin wannan wuri mai tsarki.14Sa'ad da firistoci suka shiga can, ba za su fita daga wuri mai tsarki ba zuwa harabar waje, ba tare da sun ajiye tufafin da suea yin hidima da su ba, tun da ya ke waɗannan masu tsarki ne. To dole ne su sa waɗansu tufafin na da ban kafin su kusanci mutane."15Mutumin ya gama auna gida na ciki daga nan sai ya ɗauke ni zuwa waje zuwa ƙofar da ke duban gabas ya auna dukkan filayen da ke kewaye a can.16Ya auna gefen gabas da sandar awo - ya sami kamu ɗari biyar da sandar awon.17Ya auna gefen arewa - awo ɗari biyar da sandar awo.18Hakannan ya auna gefen kudu - awo ɗari biyar da sandar awo.19Ya kuma juya ya auna gefen yamma - awo ɗari biyar da sandar awo.20Ya auna sassan guda huɗu. Akwai bango a kewaye da shi tsawonsa kamu ɗari biyar, da kuma kamu ɗari biyar a faɗi, domin ya raba tsakanin wuri mai tsarki da kuma dandali.
"saboda akwai wurin da mutum zai iya tafiya tare da ɗakunan"
"karami daga dakuna"
"a farkonsa"
Wannan shi ne hatsi ko gari da mutane suka miƙa don nuna cewa suna godiya ga Allah.
Kalmar "ya" tana nufin mutumin da yayi kama da tagulla. (Duba: Ezekiel 40: 3)
"Gidan yana da katanga kewaye da shi"
1Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da ta buɗe zuwa gabas.2Duba! ɗaukakar Allah na Isra'ila na zuwa daga gabas; muryarsa kamar rurin ruwaye masu yawa, duniya kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.3Bisa ga bayyanuwar wahayin dana gani ne, bisa ga wahatin dana gani sa'ad da yazo domin ya lalatar da birnin, wahayoyin kuma sun yi kama da wahayin dana gani a Kogin Keba - sai na faɗi da fuskata.4Sai ɗaukakar Yahweh ta zo gidan daga ƙofar da ta buɗe zuwa gabas.5Sai Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin harabar ciki. Duba! ɗaukakar Yahweh ta cika gidan.6Mutumin na tsaye a gefena, sai na ji muryar wani mutumin da ban na magana da ni daga gidan.7Ya ce mani, "Ɗan mutum, wannan ne wurin kursiyina da kuma wurin sawayen ƙafafuna, inda zan zauna a tsakiyar mutanena Isra'ila har abada. Gidan Isra'ila ba za su ƙara rena sunana mai tsarki ba - su ko sarakunansu - da rashin amincinsu ko kuma da gawayen sarakunansu bisa dogayen wurarensu ba.8Ba za su sake rena sunana mai tsarki ba ta wurin kafa dankarin gidansu, da dankarin gidana ba, da kuma madogaran ƙofofinsu da madogaran ƙofofina ba, babu wani abu sai katanga kawai tsakanina da su. Suka rena sunana mai tsarki da ayyukansu na ƙazanta, sai na cinye su cikin fushina.9Yanzu bari su kawar da rashin amincinsu da gawarwakin sarakunansu daga gabana, daga nan in zauna a tsakiyarsu har abada.10Ɗan mutum, kai da kanka dole ka gaya wa gidan Isra'ila game da wannan gida domin su ji kunyar kurakuransu. Su yi tunani game da wannan kwatancin.11Gama idan suka ji kunyar abin da suka yi, dagaan sai ka bayyana masu zanen gidan, da dukkan abin da ya ƙunsa, da wanzuwarsa, da hanyoyin shiga cikinsa, dukkan dokoki da ka'idodinsa. Daga nan sai ka rubuta wannan a gaban idanunsu domin su kiyaye dukkan tsarinsa da dukkan dokokinsa, domin su yi biyayya da su.12Wannan ne ka'idar gidan: Daga ƙololuwar tudu zuwa dukkan kewayen kan iyakar da ta kewaye shi, za ya zama mafi tsarki. Duba! wannan ce ka'idar gidan.13Waɗannan ne za su zama gwaje-gwajen bagadin bisa ga kamu-kamun kuwa dai-dai kamun tafin hannu a tsawonsa. To ramin da ke kewaye da bagadin zurfinsa za ya zama kamu ɗaya, faɗin sama kamu ɗaya. Kan iyakar da ke kewaye da gefensa zaya zama taƙi daya. Wannan ne za ya zama ƙasan bagadin.14Daga ramin daɓen ƙasa zuwa hawa na farko na bagadin kamu biyu ne, hawa na farkon kansa faɗinsa kamu ɗaya ne. Daga ƙaramin hawan kuma zuwa babban hawan bagadin kamu huɗu ne, babban hawan kuma faɗinsa kamu ɗaya ne.15Murhun bagadin kuma domin baye-baye na ƙonawa bisansa kamu huɗu ne, akwai kuma ƙahonni huɗu da suka fuskanci sama a bisa murhun.16Tsawon murhun kamu sha biyu ne faɗinsa kuma kamu sha biyu ne, a kewaye.17Kan iyakarsa kuma tsawonsa kamu sha huɗu fadinsa kamu sha huɗu a fannoninsa huɗu, gefensa kuma rabin kamu a faɗi. Ramin kuwa faɗinsa kamu ɗaya ne a dukkan kewayen da matakalunsa na fuskantar gabas.18Daga nan sai ya ce mani, "Ɗan mutum, Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Waɗannan ne ka'idoji domin bagadi a ranar da aka yi su, domin ɗaga baikon ƙonawa a kansa, da kuma yayyafa jini a kansa.19Za ku bada maraƙi daga cikin garken shanu a matsayin baikon zunubi domin Lebiyawa firistoci waɗanda ke na zuriyar Zadok, waɗanda ke zuwa kusa da ni su yi mani bauta - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.20Sai ka ɗauki jinin ka sa a ƙahonnin huɗu na bagadin, da fannoni huɗu na hawan da kewayen gefen kuma; za ka tsaftace shi ka kuma yi kaffara domin sa.21Sai ka ɗauki maraƙin baikon zunubin ka ƙona a wurin da aka zaɓa a sashen harabar haikalin da ke waje da masujadar.22A rana ta biyu sai ka miƙa bunsuru marar aibi daga garken awaki a matsayin baikon zunubi; Firistocin za su tsaftace bagadin da shi kamar yadda suka tsaftace shi da maraƙin.23Idan kuka gama tsaftace shi, sai ku miƙa maraƙi marar aibi daga garken shanu da rago marar aibi daga garken tumaki.24Ku miƙa su a gaban Yahweh; Firistocin za su barbaɗa masu gishiri su ɗaga su sama a matsayin baikon ƙonawa ga Yahweh.25Dole ku shirya bunsuru a matsayin baikon zunubi kullum har kwanaki bakwai, Firistoci kuma dole su shirya maraƙi marar aibi daga garken shanu da rago marar aibi daga garken tumaki.26Dole su yi kaffara ta kwana bakwai domin bagadin su tsarkake shi, ta wannan hanya dole su keɓe shi.27Dole su kammala waɗannan kwanaki, a rana ta takwas kuma da nan gaba za ya kasance Firistocin za su shirya baye-baye na ƙonawa da baye-baye na salama a kan bagadin, kuma zan karɓe ku - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."
Wannan kawai yana nufin "ruwa mai yawa." Zai iya nufin babban kogi ko babban ambaliyar ruwa ko raƙuman ruwa da ke buguwa a teku. Duk waɗannan suna da ƙarfi sosai. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 1:24.
"duniya cike take da haske daga daukakarsa"
Mai yiwuwa ma'anoni su ne 1) jimla ta biyu da farawa da "bisa" ta bayyana ma'anar jimlar farko da ta fara da "bisa ga." AT: "Bisa ga kamannin wahayin da na gani lokacin da ya zo ya hallaka birnin" ko 2) kalma ta farko tana nufin wahayin da Ezekiyel ya gani na ɗaukakar Allah. AT: "Bayyanar wannan wahayin da na gani ya yi dai-dai da wahayin da na gani lokacin da ya zo don ya hallaka birnin"
Ana maganar gumakan da sarakunan mutane suke bautawa kamar gawawwaki ne saboda gumakan ba su da rai. AT: "gumakan da ba su da rai waɗanda sarakunansu ke bautawa"
Maganar "cinye" a nan na nufin "an hallakar da ita gaba ɗaya." AT: "gaba ɗaya halakar da su saboda na yi fushi"
Ana maganar gumakan da sarakunan mutane suke bautawa kamar gawawwaki ne saboda gumakan ba su da rai. AT: "gumakan da ba su da rai waɗanda sarakunansu ke bautawa"
Anan an ambaci Isra’ilawa da “idanunsu” don jaddada abin da suka gani. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 21: 6. AT: "a gabansu" ko "a gaban jama'ar Isra'ila"
"zai kiyaye ta juna"
"umarnin" ko "doka"
Kalmar "iyaka" wataƙila tana nufin bangon da ya zagaye haikalin.
"Waɗannan su ne auna ma'aunin bagaden."
Ƙahonniin sune sassan bagadin a kusurwa huɗu na bagadin waɗanda suka makale a kan sauran bagadin.
"Yahweh yace"
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 43:18.
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 43:18.
Bagadin da za su yi hadaya da bijimi da rago yana gaban ƙofar Haikalin, inda Yahweh yake zaune.
Wannan ana magana da Ezekiyel don haka kalmar "ku" ɗaya ce.
"za mu yi marhabin da ku"
1Sai mutumin ya dawo da ni ƙofar masujadar da ke fuskantar gabas; an rufe ta gam.2Yahweh ya ce mani, "An datse wannan ƙofar gam; ba za a buɗe ta ba. Babu wanda za ya bi ta cikin ta, gama Yahweh, Allah na Isra'ila, ya bi ta cikin ta, domin haka an rufe ta gam.3Shugaban Isra'ila za ya zauna a kai ya ci abinci a gaban Yahweh. Za ya shiga ta rumfar ƙofar ya kuma fita ta cikin ta."4Daga nan sai ya kawo ni ta hanyar ƙofar arewa da ke fuskantar gidan. Sai na gani na kuma duba, ga ɗaukakar Yahweh ta cika gadan Yahweh, sai na faɗi bisa fuskata.5Sai Yahweh ya ce mani, "Ɗan mutum, ka shirya zuciyarka ka kuma duba da idanunka ka saurara kuma da kunnuwanka dukkan abin da na ke furta maka. Ga dukkan farillai na gidan Yahweh da dukkan ka'idodin. Yi tunani game da ƙofofin shiga gidan dana fitarsa.6Sai ka faɗa wa kangararrun nan, gidan Isra'ila, 'Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Bari dukkan ayyukanku na ƙazanta su ishe ku, gidan Isra'ila -7Da kuka kawo baƙi marasa kaciyar zuciya da kaciyar jiki su kasance a Haikalina, suna rena gidana, yayin da kuke miƙa mani abinci, kitse da Jini - Kun karya alƙawarina da dukkan ayyukanku na ƙazanta.8Ba ku aiwatar da ayyukanku ba game da abubuwana masu tsarki, amma kuka zaɓi wasu suyi ayyukanku, kuka kuma sanyasu su lura da wurina maitsarki.9Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Ba bu wani baƙo, marar kaciyar zuciya da jiki, a cikin dukkan waɗanda ke zaune tare da mutanen Isra'ila, da za ya shiga wurina mai tsarki.10Amma Lebiyawa suka tafi nesa da ni - suka kauce daga gare ni, suka tafi ga gumakansu - amma za su biya domin zunubinsu.11Su bayi ne a haikalina, suna lura da ƙofofin gidan suna kuma yin bauta a cikin gidan suna kuma yanka baye-baye na ƙonawa da hadayun mutane, za su tsaya a gaban mutane su bauta masu.12Amma saboda sun miƙa hadayu ga gumakansu, sai suka zama abin sa tuntuɓe domin zunubi ga gidan Isra'ila. Saboda haka zan ɗaga hannuna in furta rantsuwa game da su - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - zasu ɗauki nauyin horonsu.13Ba za su zo kusa da ni ba su yi aikin firistoci ko kuma su kusanci abubuwana masu tsarki, abubuwa mafi tsarki ba. Maimako haka, za su ɗauki zarginsu da laifofinsu domin ayyukan ƙazanta da suka aiwatar.14Amma zan maishe su masu tsaron aikin cikin gidan, domin dukkan ayyukansa da dukkan abin da a ke yi a cikinsa.15Daga nan su Lebiyawa firistoci, su waɗannan 'ya'ya maza na Zadok waɗanda suka cika ayyukan masujadata sa'ad da mutanen Isra'ila suke bauɗewa daga gare ni - za su zo kusa da ni su yi mani sujada. Za su tsaya a gabana su miƙa mani kitse da jini - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.16Za su zo masujadata; za su kusanci teburina su yi mani sujada su kuma cika ayyukansu a gare ni.17Hakanan za ya kasance sa'ad da suka zo ƙofofin harabar ciki, dole su yi sutura da kayan linin, dole ne kuma ba za su zo cikin ƙofofin harabar ciki da gidansa ba a cikin suturar ulu.18Za su sa rawwunan linin a kawunansu da kuma bujen linin a kwankwasonsu. Ba za su yi sutura da kayan da za susa su yi zufa ba.19Idan suka fita zuwa harabar waje, zuwa harabar waje domin suje wurin mutanen, dole su tuɓe kayan da suka sa sa'ad da suke yin hidima; dole su tuɓe su su kuma ajiye su a cikin ɗaki mai tsarki, domin kada su maida sauran mutane masu tsarki ta wurin shafar suturarsu ta musamman.20Dole ne kuma ba za su aske kawunansu ba ko su bar gashinsu a rataye ba yana lilo, amma dole su yiwa gashin kawunansu saisaya.21Kada wani firist ya sha ruwan inabi idan za ya shiga harabar ciki,22ko kuma ya ɗaukarwa kansa gwauruwa ko bazawara a matsayin matar aure, sai dai budurwa kaɗai daga zuriyar gidan Isra'ila ko kuma gwauruwar da ta auri firist.23Gama za su koyawa mutanena bambanci tsakanin abu mai tsarki da abun reni; za su sanya su su san abu mai tsafta daga marar tsafta.24A wurin saɓani za su tsaya su yi hukunci da dokokina; dole su kasance masu adalci. Za su kiyaye shari'ata da farillaina a cikin kowanne buki, kuma su yi shagalin Asabataina masu tsarki.25Ba za su je ga wanda ya mutu ba domin su zama marasa tsarki, sai dai ko mahaifinsu ne ko mahaifiyarsu, ko ɗa ko ɗiya, ko ɗan'uwa ko 'yar'uwar da ba ta taɓa kwana da namiji ba; idan kuwa ba haka ba, za su zama marasa tsafta.26Bayan da firist ya zama marar tsafta, za su lissafa warewar tsawon kwana bakwai domin sa.27A ranar da za ya shiga wuri mai tsarki, a cikin harabar ciki domin ya yi bauta a wuri mai tsarki, dole ne ya kawo baikon zunubi domin kansa - wannan ne furcin Ubangiji Yahweh.28Wannan za ya zama gãdonsu: Ni ne gãdonsu, tilas kuma ba za ku ba su kaddara ba a Isra'ila; Ni ne zan zama kaddararsu!29Za su ci baye-baye na abinci, da baye-baye na zunubi, da kuma baye-baye na laifi, da kuma dukkan abin da aka keɓe domin Yahweh a Isra'ila, za ya zama nasu.30Mafi kyau na 'ya'yan fari na dukkan abubuwa da kuma dukkan baiko, kowanne abu daga dukkan baye-baye za ya zama na firistoci, za ku kuma bayar da mafi kyau na baye-bayen abincinku ga firistoci domin albarka ta sauka bisa gidanku.31Firistoci kuma ba za su ci wani mushe ba ko dabbar da naman daji ya yaga, ko tsuntsu ne ko bisa ne.
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "babu wanda zai buɗe shi"
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 3:12.
"Na sunkuyar da kaina ƙasa" ko "Na kwanta a ƙasa." Ezekiyel bai fadi da bazata ba. Ya gangara ƙasa don ya nuna girmamawa da tsoron Yahweh. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 1:27.
"kula" ko "tunani." Fassara kamar yadda kuka fassara "sanya zuciyarku a kan" a cikin Ezekiyel 40: 3.
"Ayyukanku masu banƙyama sun isa su isa gare ku" ko "Kun aikata ayyuka masu banƙyama da yawa"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙon Isra'ila ga Isra'ila.
"za su zama bayina a haikalina"
"Waɗannan Lebiyawa za su tsaya a gaban jama'a don su yi wa jama'a aiki"
"Ba zan yarda su matso ba." Yahweh ba ya son su zo wurinsa kamar yadda bawa ke zuwa wurin sarki don karɓar umarni, kamar yadda zuriyar Zadok za su yi (Ezekiyel 40:46).
"Zan ji kunya in sha azaba idan na hukunta su"
"waɗanda suke zuriyar Zadok kuma sun cika"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga mutanen Isra'ila game da zuriyar Zadok waɗanda suke aiki a matsayin firistoci.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga mutanen Isra'ila game da zuriyar Zadok waɗanda suke aiki a matsayin firistoci.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga mutanen Isra'ila game da zuriyar Zadok waɗanda suke aiki a matsayin firistoci.
"dole ne su kiyaye gashinsu da kyau"
"wanene zuriyar bani Isra'ila"
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga mutanen Isra'ila game da zuriyar Zadok waɗanda suke aiki a matsayin firistoci.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga mutanen Isra'ila game da zuriyar Zadok waɗanda suke aiki a matsayin firistoci.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙonsa ga mutanen Isra'ila game da zuriyar Zadok waɗanda suke aiki a matsayin firistoci.
"duk wata baiwa ko wacce iri ce daga dukkan kyaututtukan ka" ko "dukkan kyautai na kowane irin kyaututtukan ka"
Wannan kalmar tana nufin "domin zan albarkaci iyalanka da duk abin da yake naka."
1Idan kuka jefa ƙuri'u domin raba ƙasar a matsayin gãdo, dole ku bayar da baiko domin Yahweh; wannan baiko za ya zama fanni mai tsarki na ƙasar, kamu dubu ashirin da biyar a tsawonsa, faɗinsa kuma kamu dubu goma. Za ya zama mai tsarki, da dukkan lardin da ke kewaye da shi.2Daga wannan za a ɗibi wuri kamu ɗari biyar na tsawo da kamu ɗari biyar na faɗi a kusurwa huɗu kewaye da wuri mai tsarki, da kuma kewayen kan iyakarsa kamu hamsin a faɗinsa.3Daga wannan lardin za ka ɗibi wuri kamu dubu ashirin da biyar a tsawo da kamu dubu goma a faɗi; shi ne za ya zama masujada, wuri mafi tsarki.4Za ya zama wuri mai tsarki a ƙasar domin firistoci da ke yiwa Yahweh bauta, waɗanda ke zuwa kusa da Yahweh su bauta masa. Za ya zama wuri domin gidajensu da kuma lardi mai tsarki domin wuri mai tsarki.5Saboda haka za ya zama kamu dubu ashirin da biyar a tsawonsa da kamu dubu goma a faɗinsa, za ya kuma zama garurruka domin Lebiyawa da ke bauta a gidan.6Zaku keɓe lardi domin birnin, kamu dubu biyar a faɗi da kamu dubu ashirin da biyar a tsawo, wanda zaya zama a gaba da lardin da aka keɓe domin wuri maitsarki; wannan birni zaya zama na dukkan gidan Isra'ila.7Ƙasar shugaban zata kasance a ɓarayi biyu na lardin da aka keɓe domin wuri maitsarki da kuma birnin. Zaya zama a yamma da su da kuma gabas da su. Tsawonsa zaya zama dai-dai da tsawon ɗaya daga cikin wuraren da aka keɓe, daga yamma zuwa gabas.8Wannan ƙasa zata zama kaddarar shugaba a Isra'ila. Shugabannina ba zasu sake muzgunawa mutanenaba; Maimako, zasu bayar da ƙasar ga gidan Isra'ila, domin kabilunsu.9Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Ya isheku, shugabannin Isra'ila! Ku kawar da ta'addanci da rigima; kuyi hukunci da adalci! ku daina kawar da mutanena! - wannan ne furcin Ubangiji Yahweh.10Dole kuyi ma'aunai na gaskiya, da jarka ta gaskiya, da daro na gaskiya!11Awon jarkar da daron su zama ɗaya, saboda daro ɗaya ya zama kashi ɗaya cikin goma na durom; jarkar kuma ta zama kashi ɗaya cikin goma na durom. Ma'auninsu zaya zama dai-dai da durom.12Shekel zaya zama gerori ashirin; shekel sittin zaya zama maina a gare ku.13Wannan ne baikon da ya zama tilas ku gabatar: kashi shida na jarka domin kowanne durom na alkama, zaku kuma bayar da kashi shida na jarka domin kowanne durom na bãli.14Baikon ka'ida na mai zaya zama kashi goma na daro wanda ya ke durom ɗaya (wanda ya ke darurruka goma), ko kuma kowanne durom, tunda ya ke durom ɗinma darurruka goma ne.15Tunkiya ɗaya ko akuya ɗaya daga cikin garken kowanne dabbobi ɗari biyu daga shiyyoyin ruwa na Isra'ila za a yi amfani da su domin baikon ƙonawa da baikon salama ayi kaffara domin mutanen - wannan ne furcin Ubangiji Yahweh.16Dukkan mutanen ƙasar zasu bayar da wannan baiko ga shugaban Isra'ila.17Zaya zama aikin shugaban ya shirya dabbobin domin baye-baye na ƙonawa, da baye-baye na hatsi, da baye-baye na abin sha a lokacin shagulgula da bukukuwan sabon wata, da ranakun asabaci - dukkan kafaffun shagulgulan gidan Isra'ila. Zaya bayar domin baye-baye na zunubi, da baye-baye na hatsi, da baye-baye na ƙonawa, da baye-baye na salama domin kaffara a madadin gidan Isra'ila.18Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: A wata na farko, a rana ta farko ga watan, zaku ɗauki maraƙi marar cikas daga garke kuyi baikon zunubi domin masujadar.19Firist zaya ɗiba daga cikin jinin baikon zunubin sai ya sanya a dawakan ƙofar gidan da kuma kusurwa hudu na kan iyakar bagadin, da kuma dawakan ƙofar shiga harabar ciki.20Zakuyi wannan a rana ta bakwai na watan domin zunubin kowanne mutum da a kayi cikin kuskure ko jahilci; ta wannan hanya zakuyi kaffara domin haikalin.21A cikin wata na farko a rana ta sha huɗu ga watan, akwai shagali dominku, shagali na kwana bakwai. Za kuci gurasa marar gami.22A wannan rana, shugaban zaya shiryawa kansa da dukkan mutanen maraƙi a matsayin baikon zunubi.23A kwanaki bakwai na bukin, shugaban zaya shirya baiko na ƙonawa ga Yahweh: maraƙai bakwai da raguna bakwai marasa cikas kowacce rana har ranaku bakwai, da kuma bunsuru kowacce rana a matsayin baikon zunubi.24Daga nan shugaban za ya yi baikon abinci na jarka ɗaya domin kowanne maraƙi da kuma jarka ɗaya domin kowanne rago da gwajin mai domin kowacce jarka.25A cikin wata na bakwai a rana ta sha biyar ga watan, a wurin shagalin, shugaban za ya yi baye-baye cikin waɗannan kwanaki bakwai: baye-baye na zunubi, baye-baye na ƙonawa, baye-baye na abinci, da baye-baye na mai.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙon ga gidan Isra'ila.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙon ga gidan Isra'ila.
"wani yanki na ƙasar"
Ana iya fassara wannan ta hanyar aiki. AT: "wanda kuka bayar domin wuri mai tsarki"
An nuna cewa waɗannan sune iyakokin yamma da gabas na ƙasar Isra'ila. AT: "Daga iyakar yamma ta Isra'ila zuwa tekun ko "zuwa iyakar gabas a Kogin Yodan"
Wannan yankin rabon gādon ɗan sarki ne daga cikin Isra'ilawa.
"Kun aikata munanan abubuwa da yawa" ko "Kun daɗe kuna aikata mummunan aiki"
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel ga sarakunan Isra'ila.
"bangarorin Isra'ila da ke samun kyakkyawan ruwa"
bukukuwan da suke faruwa lokaci guda a kowace shekara ko wata ko mako
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel ga sarakunan Isra'ila.
"ga kowane mutum da ya yi zunubi ba tare da ma'ana ba ko kuma don bai san yana yin zunubi ba" ko "ga kowane mutum da ya yi zunubi bisa kuskure ko kuma don yanzu bai yi abin da ya dace ba"
Kalmar "ku" jam'i ne kuma tana nufin yarima da sauran mutanen gidan Isra'ila.
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel ga sarakunan Isra'ila.
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel ga sarakunan Isra'ila.
1Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: Ƙofar harabar ciki, da ke fuskantar gabas, za a rufe ta a cikin kwanaki shida na aiki, amma a ranar Asabaci za a buɗe ta, ranar sabon wata kuma za a buɗe ta.2Shugaban za ya shiga harabar waje ta hanyar ƙofar da rumfarta da ke waje, za ya kuma tsaya a dawakan ƙofa na ƙofar ciki yayin da firistocin ke shirya masa baikon ƙonawa da baikon salama. Daga nan sai ya yi sujada a dankarin ƙofar ciki sai ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da yamma.3Mutanen ƙasar kuma za suyi sujada a gaban Yahweh a wurin shiga wannan ƙofa a ranakun asabaci da sabobbin watanni.4Baikon ƙonawa da shugaban zaya miƙa ga Yahweh a ranar asabaci zaya zama 'yan tumaki shida marasa cikas da kuma rago ɗaya marar cikas.5Baikon hatsi tare da ragon zaya zama jarka ɗaya, baikon hatsin dana 'yan ragunan zaya bayar bisa ga ra'ayinsa, da kuma gwajin mai ga kowacce jarkar hatsin.6A ranar sabon wata tilas ne ya miƙa maraƙi marar cikas daga garke, 'yan tumaki shida, da rago marar cikas.7Tilas ya miƙa baikon hatsi na jarka ɗaya domin maraƙin da kuma jarka ɗaya domin ragon, da abin da ya yi niyyar bayar wa domin 'yan tumakin, da kuma gwajin mai ga kowacce jarkar hatsi.8Idan shugaban ya shiga ta hanyar ƙofar da rumfarta, tilas ya fita ta hakan.9Amma idan mutanen ƙasar suka zo gaban Yahweh a lokacin shagulgulan da aka kafa, duk wanda ya shiga ta ƙofar arewa domin ya yi sujada tilas ya fita ta ƙofar kudu; duk kuma wanda ya shiga ta ƙofar kudu tilas ya fita ta ƙofar arewa. Babu wanda za ya koma baya ta ƙofar da ya shiga, tilas ya miƙe ya fita ta gabansa.10Tilas shugaban ya kasance a tsakanin su; yayin da suke shiga, tilas ya shiga, yayin da suke fita, tilas ya fita.11A lokacin shagulgulan, baikon hatsin tilas ya zama jarkar hatsi ɗaya domin maraƙin da jarka ɗaya domin ragon, da kuma duk abin da ya yi niyyar bayarwa domin 'yan tumakin, da gwajin mai domin kowacce jarka.12Idan shugaban ya bayar da baikon yaddar rai, kodai baiko na ƙonawa ko baiko na salama ga Yahweh, za a buɗemashi ƙofar da ke fuskantar gabas. Zaya miƙa baikonsa na ƙonawa da baikonsa na salama kamar yadda ya ke yi a ranar asabaci. Daga nan tilas ya fita, bayan kuma daya fita sai a kulle ƙofar.13Bugu da ƙari, za ku bayar da ɗan rago marar cikas ɗan shekara ɗaya a matsayin baikon ƙonawa ga Yahweh kullum; za ku yi wannan safiya bayan safiya.14Za ku bayar da baikon hatsi tare da shi safiya bayan safiya, ka shi shida na garwar da kashi uku na gwajin mai domin a murtsike garin baikon hatsin ga Yahweh, bisa ga madawwamin farilla.15Za su shirya ɗan ragon, da baikon hatsin, da kuma mai safiya bayan safiya, baikon ƙonawa madawwami.16Ubangiji Yahweh ya faɗi wannan: idan shugaban ya bayar da kyauta ga ɗaya daga cikin 'ya'yansa maza, gãdonsa ne. Za ya zama kadarar 'ya'yansa maza, gãdo ne.17Amma idan ya bayar da kyauta daga gãdonsa ga ɗaya daga cikin bayinsa, za ya zama na bawannan har zuwa shekarar 'yantarwa, sai kuma a maida shi ga shugaban. Gãdonsa lallai za ya zama na 'ya'yansa maza ne.18Shugaban ba za ya ɗauke gãdon mutanen daga kadararsu ba; dole ya bayar ga 'ya'yansa maza daga kadararsa domin kada mutanena su warwatse, kowanne mutum daga kadararsa."'19Daga nan sai mutumin ya kawo ni ta hanyar shiga ɗakuna masu tsarki domin firistoci, masu fuskantar arewa duba kuma! Akwai wani wuri kuma zuwa yamma.20Ya ce mani, "Wannan ne wurin da tilas firistoci su dafa baikon laifofi da baikon zunubi inda kuma tilas su gasa baikon hatsi. Tilas kuma ba za su kawo baye-bayen ba zuwa harabar waje, domin mutanen za su zama keɓaɓɓu."21Daga nan ya kawo ni harabar waje ya bida ni na bi ta kusurwoyi huɗu na harabar, sai kuma na ga cewa a kowacce kusurwar harabar akwai wata harabar.22A kusurwoyi huɗu na harabar waje akwai waɗansu ƙananan harabai huɗu, kamu arba'in a tsawo da kamu talatin a faɗi. Dukkan harabobin huɗu gwajinsu ɗaya ne.23Akwai layin da aka yi da dutse kewaye da dukkan su huɗun, kuma murahun girki na ƙarƙashin dutsen.24Sai mutumin ya ce mani, "Waɗannan ne wuraren da bayin haikali za su dafa hadayun mutane."
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel ga sarakunan Isra'ila.
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 40:17.
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 43:22.
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel ga sarakunan Isra'ila.
Fassara kamar yadda kuka fassara "idodin da aka ƙaddara" a cikin Ezekiyel 36:37.
Yahweh ya ci gaba da ba wa Ezekiyel ga sarakunan Isra'ila.
"wanda zai jiƙa"
Wannan shine shekarar da bawa yake samun yanci. Wannan kuma ana kiranta "Shekarar 'Yanci."
"wanda ke da manyan hanyoyin shiga arewa"
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 10: 3.
1Sai mutumin ya maida ni baya hanyar shiga haikalin, sai ga ruwa na ɓulɓulowa daga ƙarƙashin dankarin haikalin gidan zuwa gabas - gama gaban haikalin na fuskantar gabas - kuma ruwan na ɓulɓulawa ɓangaren kudu na haikalin, zuwa dama da bagadin.2Sai ya fito da ni ta hanyar ƙofar arewa ya kuma bi da ni zagaye da ƙofar da ke fuskantar gabas, a nan ruwan yana ta malalawa daga wannan ƙofa zuwa kudu da ita.3Yayin da mutumin ke tafiya zuwa gabas, yana riƙe da magwaji a hannunsa; sai ya gwada kamu dubu ya kuma kawo ni ta cikin ruwan inda zurfinsa ya kai idon ƙafa.4Ya sake gwada kamu dubu ya kuma kawo ni ta cikin ruwan inda zurfinsa yakai gwiwa; ya sake gwada kamu dubu ya kuma kawo ni inda zurfin ruwan ya kai kwankwaso.5Sai ya sake gwada wani kamu dubu, amma ruwan ya zama kogi wanda bazan iya bi ta cikin ba gama ruwan ya taso sama zurfinsa kuma ya isa ayi iwo a ciki - ya zama kogin da ba a iya ƙetarewa.6Daga nan mutumin ya ce mani, "Ɗan mutum, ka ga wannan?" sai ya fito da ni waje ya kuma sa na tafi na koma baya ina tafiya ta gefen kogin.7Yayin da nake komawa baya sai na ga gefen kogin nada itatuwa da yawa a wannan gefe da kuma wancan gefe.8Mutumin ya ce mani, "Wannan ruwan na tafiya lardin gabas ne da ƙasa zuwa Araba; wannan ruwan yana gudu ne zuwa cikin tekun gishiri za ya kuma sabunta ta.9Za ya zama kuma duk wata halitta mai rai da ke iwo za ta kasance inda ruwan ya tafi; za ayi kifaye masu yawa, gama wannan ruwan za ya malala zuwa can. Za ya maida ruwan gishirin mai daɗi. Komai za ya rayu a duk inda ruwan ya je.10Daga nan za ya kasance masu kamun kifi na Engedi za su tsaya bakin ruwan, za a sami wurin shanya tarurrukan kamun kifin su bushe a En Egilayim. Za a sami kifaye daban-daban a Tekun Gishiri, kamar kifayen babbar teku domin tsananin yawansu.11Amma kududdufai da tafkunan Kogin Gishirin ba za a maida su masu daɗi ba; za su zama wurin samun gishiri.12Gefen wannan kogin a bakunansa, a gefensa biyu, itatuwa daban-daban masu bada abinci za su fito. Ganyayensu ba za su yi yaushi ba kuma ba za su taɓa dena bada 'ya'ya ba. Kowanne wata itatuwan za su bada 'ya'ya, saboda ruwa daga haikalin yana malalawa zuwa gare su. 'Ya'yansu za su zama domin abinci, ganyayensu kuma za su zama domin warkaswa.13Ubangiji Yahweh ya faɗi haka: Wannan ce hanyar da za ku raba ƙasar ga kabilu sha biyu na Isra'ila: Yosef za ya sami kaso biyu.14Za ku raba dai-dai abin da na ɗaga hannu na rantse wa ubanninku zan ba su. Wannan ƙasa za ta zo maku a matsayin gãdo.15Wannan ne za ya zama kan iyakar ƙasar a gefen arewa dagaBabbar Teku zuwa hanyar Hetlon, daga nan kuma zuwa Zedad.16Daga nan kan iyakar za ya tafi Berota, da Sibirayim, wadda ke tsakanin Damaskus da Hamat, daga nan kuma zuwa Haza Hattikon, wadda ke gefen kan iyakar Hauran.17Saboda haka kan iyakar za ya tafi daga teku zuwa Haza Enan kan iyaka da Damaskus da Hamat zuwa arewa. Wannan ne za ya zama ɓarayin arewa.18A gefen gabas, a tsakanin Hauran da Damaskus da kuma tsakanin Giliyad da ƙasar Isra'ila za ya zama Kogin Yodan. Tilas ka gwada daga kan iyaka zuwa tekun gabas; dukkan wannan za ya zama kan iyakar gabas.19Daga nan gefen kudu kan iyakar zai kama daga Tama zuwa ruwayen Meriba Kadesh, gulbin Masar zuwa BabbarTeku. Wannan zai zama kan iyakar gefen kudu.20Daga nan kan iyakar yamma za ya zama daga BabbarTeku zuwa inda ya tafi daura da Hamat. Wannan ne za ya zama gefen yamma.21Ta wannan hanyar za ku raba ƙasar a tsakaninku, domin kabilun Isra'ila.22Sai ku rarraba gãdon domin ku da kuma baƙin da ke zaune a tsakanin ku, su waɗanda suka haifi 'ya'ya a tsakanin ku, tare daku, kamar haihuwar 'yan asalin mutanen Isra'ila. Za ku jefa ƙuri'u domin gãdo a tsakanin kabilun Isra'ila.23Daga nan za ya zama cewa baƙo za ya kasance tare da kabilar da ke zaune tare da su. Tilas ku ba shi gãdo - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne."
Wannan shi ne gefen dama na bagadin lokacin da mutum ya dube shi yayin da suke fuskantar gabas, don haka yana gefen kudu na bagadin. AT: "a gefen kudu na bagadin"
kirtani ko igiya da mutane suke amfani da shi don auna nisan nesa
Yahweh yana umurtar Ezekiyel ya yi tunani game da abin da ya gani. Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 8:14. AT: "kuyi tunani game da wannan."
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 21: 6.
Wannan sunan babban maɓuɓɓugar ruwa a yamma da Tekun Gishiri.
wurare da ruwa mara ƙima da bishiyoyi da ciyawar da ke girma a cikin laka mai zurfi
Mutumin yana da kyan gani ga zuriyarsa. AT: "zuriyar Yosef za su sami yankuna biyu na ƙasa"
A wancan zamanin mutum zai daga hannunsa na dama ya nuna cewa ya fahimci cewa Allah zai yi masa azaba idan bai aikata abin da ya rantse zai yi ba.
Waɗannan su ne sunayen garuruwa.
Waɗannan su ne sunayen garuruwa. (Duba:
babban rafi mai girma a arewa maso gabashin yankin Sinai
Anan kalma "ku" na nufin mutane Isra'ila.
1Waɗannan ne sunayen kabilun. Kabilar Dan za su karɓi kaso ɗaya na ƙasar; Kan iyakarsu za ya tafi dai-dai da kan iyakar Isra'ila ta arewa ta hanyar Hetlon da Lebo Hamat. Kan iyakar za ya tafi har zuwa Hazar Enan ya kuma tafi kan iyaka da Damaskus zuwa arewa daga nan har zuwa Hamat. Kan iyakar Dan za ya tafi daga gabas har zuwa Babbar Teku.2Haɗe da kan iyakar Dan, daga gefen gabas zuwa yamma, Asha za ya sami kaso ɗaya.3Haɗe da kan iyakar Asha, daga gefen gabas zuwa yamma, Naftali za ya sami kaso ɗaya.4Haɗe da kan iyakar Naftali daga gefen gabas zuwa yamma, Manasse za ya sami kaso ɗaya.5Haɗe da kan iyakar Manasse daga gefen gabas zuwa yamma, Ifraim za ya sami kaso ɗaya.6Haɗe da kan iyakar Ifraim daga gefen gabas zuwa yamma, Ruben za ya sami kaso ɗaya.7Haɗe da kan iyakar Ruben daga gefen gabas zuwa yamma, Yahuda za ya sami kaso ɗaya.8Baikon ƙasa da zaku bayar za ya kasance daga kan iyakar Yahuda ya zarce daga gefen gabas zuwa gefen yamma; Faɗin ta za ya zama kamu dubu ashirin da biyar. Tsawonta kuma za ya zama dai-dai da kason kabila ɗaya daga gefen gabas zuwa gefen yamma, Haikalin kuma za ya kasance a tsakiyarsa.9Wannan ƙasa da za ku miƙa baiko ga Yahweh za ta zama kamu dubu ashirin da biyar a tsawo da kuma kamu dubu goma a fãɗi.10Waɗannan ne za su zama ayyukan kason wannan ƙasa mai tsarki: za a ɗeba wa firistoci ƙasar a gwada kamu dubu ashirin da biyar bisa gefen arewa; kamu dubu goma a fãɗi bisa gefen yamma; kamu dubu goma a fãɗi bisa gefen gabas; kamu dubu ashirin da biyar kuma bisa gefen kudu, tare da wuri mai tsarki na Yahweh a tsakiyarta.11Wannan za ya zama domin keɓewar firistoci zuriyar Zadok, waɗanda suka bauta mani da aminci ba su kuma kauce ba a lokacin da mutanen Isra'ila suka kauce, yadda Lebiyawa suka yi.12Baiko dominsu za ya kasance kason wannan ƙasa mafi tsarki, ya zarce zuwa kan iyakar Lebiyawa.13Ƙasar Lebiyawa da ke kan iyaka da ƙasar firistoci za ta kasance kamu dubu ashirin da biyar a tsawo da kamu dubu goma a fãɗi. Tsawon gabaɗaya na tsagawar ƙasar biyu za ya kasance kamu dubu ashirin da biyar da kuma kamu dubu ashirin a fãɗi.14Dole ba za su sai da ba ko su yi musanya da ita; 'Ya'yan fari na ƙasar Isra'ila dole ba za a taɓa ware su ba daga waɗannan karkasawar, gama dukkan ta mai tsarki ce ga Yahweh.15Sauran ƙasar, kamu dubu biyar a fãɗi da kamu dubu ashirin da biyar a tsawo, za ta zama abin amfanin birnin gabaɗaya, da gidajen, da saurar kiwo, birnin za ya kasance a tsakiya.16Waɗannan ne za su zama gwaje-gwajen birnin: Gefen arewa za ya zama kamu 4,500 a tsawo; gefen kudu za ya zama 4,500 a tsawo; gefen gabas za ya zama 4,500 a tsawo; gefen yamma za ya zama 4,500 a tsawo.17Za a fidda saura domin birnin wajen arewa, kamu 250 a zurfi; wajen kudu, kamu 250 a zurfi; wajen gabas, kamu 250 a zurfi; wajen yamma, kamu 250 a zurfi.18Sauran lardin domin baiko mai tasrki za ya zarce ya kai kamu dubu goma zuwa gabas da kamu dubu goma zuwa yamma. Za ta zarce har zuwa kan iyaka da baiko mai tsarki, amfanin ta kuma za ya zama abinci domin masu aiki cikin birnin.19Mutanen da ke aiki cikin birnin, mutanen da suka fito daga dukkan kabilun Isra'ila, za su noma wannan ƙasar.20Dukkan ƙasar baikon za a gwada kamu dubu ashirin da biyar da kamu dubu ashirin da biyar. Ta wannan hanyar za ku bada baikon mai tsarki da ƙasa, domin birnin.21Sauran ƙasar daga kowanne gefe na baiko mai tsarki da lardin birnin za ya zama domin shugaban. Tsagin ƙasar shugaban zuwa gabas za ta zarce ta kai kamu dubu ashirin da biyar daga kan iyakar baiko mai tsarki zuwa gabashin kan iyakar - tsagin nasa kuma daga yamma za ta zarce ta kai kamu dubu ashirin da biyar zuwa yammacin kan iyakar. Tsakiyar za ta zama baiko mai tsarki, wuri mai tsarki kuma na haikalin za ya kasance a tsakiyarta.22Ƙasar za ta zarce daga kadarar Lebiyawa da kuma lardin birnin da ke tsakiya zaya zama na shugaban; za ta kasance tsakanin kan iyakar Yahuda da kuma kan iyakar Benyamin - wannan ƙasa za ta zama ta shugaban.23Sauran kabilun kuwa, na su kashi-kashinsu ma za ya fara daga gefen gabashi zuwa gefen yamma. Benyamin za ya karɓi kaso ɗaya.24Haɗe da kan iyakar Benyamin daga gefen gabas zuwa yamma, Simiyon za ya sami kaso ɗaya.25Haɗeda kan iyakar Simiyon daga gefen gabas zuwa yamma, Issaka za ya sami kaso ɗaya.26Haɗe da kan iyakar Issaka daga gefen gabas zuwa yamma, Zebulun za ya sami kaso ɗaya.27Daga kudancin kan iyakar Zebulun, ya kamo daga gefen gabas zuwa yamma, za ya zama ƙasar Gad - kaso ɗaya.28Kan iyakar kudancin Gad za ya zarce daga Tama zuwa Meriba Kadesh da kuma nesa daga tafkin Masar, daga nan kuma zuwa babbar teku.29Wannan ce ƙasar da za ku jefa ƙuri'u; za ta zama gadon kabilun Isra'ila. Waɗannan ne za su zama rabonsu. Wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.30Waɗannan ne za su zama wuraren fita daga birnin: a gefen arewa, wanda za a gwada kamu 4,500 a tsawo,31za ya zama ƙofofi uku, waɗanda za a yi wa suna domin kabilun Isra'ila: ƙofa ɗaya domin Ruben, ƙofa ɗaya domin Yahuda, ƙofa ɗaya kuma domin Lebi.32A gefen gabas, wanda za a gwada kamu 4,500 a tsawo, za ya zama ƙofofi uku: ƙofa ɗaya domin Yusufu, ƙofa ɗaya domin Benyamin, ƙofa ɗaya kuma domin Dan.33A bangon kudu, wanda za a gwada kamu 4,500 a tsawo, za ya zama ƙofofi uku: ƙofa ɗaya domin Simiyon, ƙofa ɗaya domin Issaka, ƙofa ɗaya kuma domin Zebulun.34A gefen yamma, wanda za a gwada kamu 4,500 a tsawo, za ya zama ƙofofi uku: ƙofa ɗaya domin Gad, ƙofa ɗaya domin Asha, ƙofa ɗaya kuma domin Naftali.35Tazarar kewaye da birnin za ya zama kamu dubu sha takwas; daga ranar nan zuwa nan gaba, sunan birnin za ya zama "Yahweh yana wurin."
"yanki ɗaya wanda zaka raba"
Waɗannan su ne sunayen garuruwa.
Fassara kamar yadda kuka fassara "yanki ɗaya na ƙasa" a cikin Ezekiyel 48: 1.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙon ga Isra'ilawa
Wannan rabo kaɗan ne a cikin tsattsarkan yankin ƙasar, zai zama na firistoci ne, rabo mafi tsarki fiye da sauran tsattsarkan yankin.
"wannan ƙasar wanda shine nunan fari." Anan “nunan fari” mai yiwuwa yana nufin mafi kyawu a cikin duk sadakoki da aka keɓe don bayarwa ga Allah. Haka ake maganar ƙasar, kamar ƙasa da aka keɓe domin Yahweh.
"a matsayin wurin zama na gidaje kuma na sarari"
"abincin da ke tsirowa can"
"Za ku bayar da tsattsarkan hadaya da dukiyar birni"
Duba yadda kuka fassara wannan a cikin Ezekiyel 48:17.
Yahweh ya ci gaba da bai wa Ezekiyel saƙon ga Isra'ilawa.
1A cikin shekara ta uku ta mulkin Yehoyakim sarkin Yahuda, Nebukadnezza sarkin Babila ya zo Yerusalem ya kewaye birnin domin ya yanke dukkan abin da zai shigo cikinsa.2Ubangiji ya ba Nebukadnezza nasara akan Yehoyakim sarkin Yahuda, ya ba shi waɗansu keɓaɓun abubuwa daga gidan Allah. Ya kawo su cikin ƙasar Babila, zuwa gidan allahnsa, kuma ya sa keɓaɓun abubuwan a cikin ma'ajin allahnsa.3Sarkin ya yi magana da Ashfenaz, baban jami'insa, ya kawo waɗansu daga cikin mutanen Isra'ila, waɗanda su ke daga iyalin sarauta da kuma manyan mutane -4samari waɗanda ba su da cikas, kyawawa, ƙwararru a kowacce hikima, cike da ilimi da ganewa, waɗanda suka cancanci su yi aiki a fãdar sarki. Shi ne zai koya masu adabin mutanen Babila da harshensu.5Sarki ya ɗibar masu abinci daga abincinsa da ruwan inabi wanda ya ke sha. Za a horar da waɗannan samari har shekaru uku, bayan haka, za su yi wa sarki hidima.6A cikin su akwai Daniyel da Hananiya da Mishayel da Azariya, daga cikin mutanen Yahuda.7Babban jami'in ya ba su sunaye, Daniyel ya kira shi Beltishazza, ya kira Hananiya Shadrak, ya kira Mishayel, Meshak Azariya kuma ya kira shi Abednego.8Amma Daniyel ya yi niyya a ransa, cewa ba zai ɓata kansa da abincin sarki ba ko da ruwan inabin da ya ke sha. Sai ya roƙi alfarma daga wurin babban jami'in saboda ba ya so ya ɓata kansa.9Sai Allah ya ba Daniyel tagomashi da tausayi daga babban jami'in ta wurin girmamawar da da ya ke yi masa.10Babban jami'in ya ce da Daniyel, "Ina jin tsoro shugabana sarki. Ya bada ummurni akan abincin da za ku ci da abin shan da za ku sha. Me ya sa zai gan ku da rãma da samari abokanku? Sarki zai fille kaina saboda ku."11Sa'annan Daniyel ya yi magana da mai aikin da babban jami'in ya sa ya kula da su Daniyel, Hananiya, Meshayel da Azariya.12Ya ce, "Idan ka yarda ka gwada mu bayinka na kwana goma, ka riƙa ba mu kayan lambu mu ci da kuma ruwa mu sha.13Sa'annan ka gwada baiyanarmu da baiyanar samarin da ke cin abincin sarki, ka yi mana mu bayinka, bisa ga abin da ka gani."14Sai mai hidimar ya yarda ya yi haka, ya gwada su kwana goma.15A ƙarshen kwanaki goman sai baiyanarsu ta fi lafiya, kuma suka fi duk samarin da ke cin abincin sarki annuri.16Sai mai hidimar ya ɗauke abincinsu da ruwan inabinsu ya ba su kayan lambu kawai.17Waɗannan samari huɗu, Allah ya ba su ilimi da ganewa da fahimtar dukkan adabi da hikima, Daniyel kuma ya na iya gane kowanne irin wahayi da mafarkai.18Da lokacin da sarki ya bayar a kawo su wurinsa ya yi, sai babban mai hidimar ya kawo su ciki gaban Nebukadnezza.19Sarki ya yi magana da su, a cikin dukkan taron babu wanda za a iya kwatanta shi da Daniyel, Hananiya, Meshayel da Azariya. Suka tsaya a gaban sarki, a shirye su yi masa hidima.20A cikin kowacce tambaya ta hikima da ganewa da sarki ya tambaye su, ya tarar sun fi dukkan masu dũba da masu magana da kurwa waɗanda ke cikin dukkan mulkinsa har sau goma.21Daniyel ya zauna can har shekara ta fari ta Sairus.
Wannan na nufin Nebukadnezza da sojojin sa, ba Nebukadnezza kadai ba. AT: "Sojojin Nebukadnezza" ko kuma "Nebukadnezza sarkin Babila da sojojin sa"
"a hana mutane karbar duk wani abin da zai shigo"
Wannan na nufin Yehoyakim da sojojin sa, ba ga Yehoyakim kadai ba. AT: "dakaran Yehoyakim sarkin Yahuda"
Yehoyakim ya ba Nebukadnezza
Duk da cewa Nebukadnezza bai yi wadannan abubuwa shi kadai ba, zai zama da sauki mai karatu ya sansance wakilan sunan.
Anan "su" watakila na nufin Yehoyakim da sauran yan sarka, da kuma sauran abubuwa masu daraja
wannan wani nau'in ibada ne ga allolin sa
Wannan na nufin Nedukadnezza
Wannan ne shugaban ma'aikata.
Wannan shine kashin mutane masu martaba
Wadannan kalmomi biyu marasa kyau a haɗe na karfafa tunani mai tasiri. AT: "tare da shiga mai armashi"
Wannan karin magana ce. Wannan na nufin sun san abubuwa da yawa kuma zasu iya shirya wa da kuma amfani da bayanai.
Wannan babban gida ne ko gini inda sarki ke rayuwa
Ashfenaz ne zai koya masu
Ma'aikatan sarkin ke yin wannan aikin domin sa. AT: "Ma''aikatan Sarkin ne suka danƙa masu"
keɓaɓɓu, masu wuyar samu, abinci masu kyau da sarki ke ci
Za'a iya fadin wannan da gaba gadi. AT: "Ashfenaz ne zai koyas da wadannan matasan"
A cikin matasa daga Isra'ila
Wannan na nufin Ashfenaz wanda shi ne babban ma'aikacin sarki Nebukadnezza
Wadannan duk sunayen maza ne.
A nan "ransa" na nufin Daniyel da kansa. AT: "Daniyel yayi wa kansa zaɓi"
A "gurɓata" wani abu na nufin maishe shi mara tsarki. Wadansu daga cikin abubuwan ci da sha na Babiloniyawa zasu iya maishe da Daniyel mara tsarki bisa ga dokar Allah. Za'a iya fayyace wannan. AT: "maishe da kansa mara tsarki bisa ga dokar Allah"
Wannan na nufin keɓaɓɓu, masu wuyar samu, abubuwan ci masu kyau da sarki ke ci. Duba yadda aka fasara wannan a 1:1.
Shugaban yayi anfani da wannan tambaya ya bayyana abin da yake tunani zai faru. Zai iya zama furci. AT: "Ba ya so ya gan ku a rãme in an kwatanta da sauran abokanku."
Wannan habaici ne. AT: "Sarki zai iya fille kai na" ko kuma "Sarki zai kashe ni"
Daniyel ya bukaci mai shidimar ya duba idan shi da abokansa sun fi sauran rãma. AT: "ka gwada baiyanarmu ka gani ko ta fi tasu muni"
Duk wadannan wakilan sunan na nufin Daniyel, Hananiya, Meshayel, da Azariya
Wannan yana nufin zama da lafiya daga abin da ka ci
Za'a iya sauya kalmar domin bayyana boyayyan sunan "ilimi" da "ganewa" kamar aikatau "koyo" da "fahimta." AT: "Allah ya basu ikon koyo da fahintar a zahiri"
An ɗabbaƙa wannan ne don a nuna yadda suke a cikakken ilimi da ganewa.
Sarkin yayi magana da "samari hudun" (1:17).
Za'a iya fadin wannan da gaba gadi. AT: "Daniyel, Hananiya, Meshayel, da Azariya sun gamshe shi fiye da kowa a cikin dukan taron
Wadannan sunayen maza ne. Duba yadda aka fasara wadannan sunayen a 1:6
A nan "sau goma" an fifita shi ne wanda ke wakiltar inganci. AT:"fiye da kowa"
shekara ta fari da Sarki Sairus ya muki Babila
1A cikin shekara ta biyu ta mulkin Nebukadnezza, sai ya yi mafarkai. Hankalinsa ya tashi, bai iya yin barci ba.2Sarki ya umarta cewa masu dũba da masu cewa suna magana da kurwa su zo. Haka kuma ya kira masu sihiri da mutane masu hikima. Ya so su ba shi bayanin mafarkansa. Sai suka zo suka tsaya a gaban sarki.3Sarki ya ce da su, "Na yi mafarki, kuma raina ya ƙagara ya san ma'anar mafarkin."4Sai mutanen masu hikima suka yi wa sarki magana cikin harshen Aremiyanci, "Ranka ya dade ya sarki! Ka gaya mana mafarkin, bayinka kuwa za su baiyana maka ma'anarsa."5Sai sarki ya amsawa masu hikimar da cewa, "Wanann maganar a yanke take. Idan ba ku baiyana mani mafarkin da fassararsa ba, za a yayyaga jukkunanku a mayar da gidajenku kufai.6Amma idan kun baiyana mani mafarkin da ma'anarsa, za ku karɓi kyautai daga gare ni, da lada da ɗaukaka. To sai ku gaya mani mafarkin da ma'anarsa."7Suka sake amsawa suka ce, "Bari sarki ya gaya mana mafarkin, mu bayinsa mu kuwa za mu baiyana maka ma'anarsa."8Sai sarki ya amsa, "Tabbas na sani kuna bukatar ƙarin lokaci, saboda kun ga shawarata ta yi tsauri akan wannan abu.9Amma idan ba ku faɗa mani mafarkin ba, hukunci ɗaya ne a kanku. Kun shirya ku gaya mani ƙaryar da kuka shirya ku ka yarda a kanta da maganganu na ruɗi, har sai na canza shawarata. To ku gaya mani mafarkin, sa'annan zan sani za ku ba ni bayaninsa."10Masu hikima suka amsa wa sarki, "Ba wani mutum a duniya da zai iya biyan bukatar sarki. Ba wani babban sarki mai iko da ya taɓa bukatar irin wannan abu daga masu dũba, ko daga wani mai magana da kurwa, ko mutum mai hikima.11Abin da sarki ya ke bukata yana da wuya, ba wanda zai iya gaya wa sarki shi sai dai alloli, su kuma ba a cikin mutane suke zama ba."12Wannan ya sa sarki ya ji haushi ya hasala ƙwarai, ya bada ummurni a hallaka dukkan masu hikima na Babila.13Shela ta fita a kashe dukkan waɗanda aka sani su masu hikima ne. Saboda wannan doka, aka nemo Daniyel da abokansa domin a kashe su.14Sai Daniyel cikin ladabi da hikima ya amsa wa Ariyok shugaban masu tsaron sarki, wanda ya zo ya kashe dukkan waɗanda aka san masu hikima ne a cikin Babila.15Daniyel ya tambayi jami'in sarkin, "Me ya sa shelar sarki ta zo da sauri haka?" Ariyok ya gaya wa Daniyel abin da ya faru.16Sai Daniyel ya roƙi a ba shi lokaci ya zo wurin sarki domin ya kawo wa sarki fassara.17Sai Daniyel ya koma gida ya gaya wa su Hananiya, Meshayel da Azariya, abin da ya faru.18Ya roƙe su su nemi jinƙai daga Allah na sama akan wannan asiri domin kada a kashe su tare da sauran mutanen Babila waɗanda aka sani saboda da hikimarsu.19A wannan daren a ka baiyana wa Daniyel asirin a cikin ruya. Sa'annan Daniyel ya yabi Allah na sama20ya ce, "A yabi sunan Allah har abada abadin; gama hikima da iko nasa ne.21Shi ne mai canza lokatai da zamanai; ya kan cire sarakuna ya sa waɗansu sarakunan akan mulkokinsu. Ya kan ba da hikima da ilimi ga masu fahimta.22Yakan baiyana ɓoyayyun abubuwa masu zurfi gama shi ya san abin da ke cikin duhu, haske kuwa tare da shi ya ke zama.23Allah na ubannina, na gode maka na yabe ka saboda hikima da iko da ka ba ni. Yanzu ka sanar da ni abin da muka roƙe ka; ka kuma sa mun san abin da ya dami sarki."24Sai Daniyel ya shiga wurin Ariyok (wanda sarki ya sa ya kashe kowanne mai hikima a cikin Babila). Ya je ya ce masa, "Kada ka kashe masu hikima na cikin Babila. Ka kai ni wurin sarki zan nuna masa fassarar mafarkinsa."25Nan da nan kuwa Ariyok ya kawo Daniyel gaban sarki ya ce, "Na samo wani daga cikin 'yan bauta na Yahuda wanda zai baiyana wa sarki ma'anar mafarkinsa."26Sarki ya cewa Daniyel (wanda a ke kira Beltishazza), "Ko ka iya gaya mani mafarkin da na gani da ma'narsa?"27Daniyel ya amsa wa sarki ya ce, "Asirin da sarki ya tambaya game da shi masu hikima ba zasu iya baiyana shi ba, ko masu magana da kurwa da masu dũba, ko masana taurari.28Duk da haka, akwai Allah wanda ya ke zaune a cikin sammai, wanda ya ke baiyana asirai, kuma ya sanar da kai, ya sarki Nebukadnezza, abin da zai faru a cikin kwanaki masu zuwa. Wannan shi ne mafarkinka da ruyar ranka lokacin da ka ke kwance akan gadonka.29Amma kai, ya sarki, zace-zacenka sa'ada ka ke kan gadonka game da abubuwan da zasu faru nan gaba ne, kuma shi wanda ya ke baiyana asirai ya sanar da kai abin da ya kusa faruwa,30A gare ni ba a baiyana mani wannan asiri domin na fi kowanne mutum da ke rayuwa hikima ba. An baiyana mani asirin ne domin, kai, sarki ka gane ma'anar, domin kuma ka gane zurfin tunanin da ke cikin tunane-tunanenka da ke da zurfi a cikinka.31Sarki, ya dubi sama ya ga siffa mai girma. Wannan siffa mai girma da haske, ta tsaya a gabanka. Haskenta yana da ban tsoro.32Kan sifar an yi shi da zinariya mai kyau. Ƙirjinta da hannuwanta na azurfa ne. Tsakiyarta da cinyoyinta an yi su da tagulla,33ƙafafunta kuma an yi su da ƙarfe. Tafin sawunta kuma an yi su rabi da ƙarfe rabi da yumɓu.34Da ka duba sama, an saro wani dutse, ko da ya ke ba da hannun mutum ba ne, ya kuma bugi siffar ya farfasa ƙafafunta na ƙarfe da na yumɓu.35Sa'annan ƙarfen da yumɓun da baƙin ƙarfen da azurfar da zinariyar aka farfasa su gaba ɗaya suka zama kamar ɗan maraƙi a masussuka lokacin kaka. Iska ta kwashe su ba ta rage komai ba. Amma dutsen da ya faɗo ya farfasa siffar ya zama babban dutse ya cika duniya.36Wannan shi ne mafarkinka. Yanzu zamu gaya maka ma'anarsa.37Kai, sarki, kai ne sarkin sarakuna waɗanda Allah na sama ya ba su mulki, da iko da ƙarfi da martaba.38Ya bayar da wurin da mutane ke zaune a hannunka. Ya kuma bada dabbobi da tsuntsayen sama a cikin hannunka, ya sa ka yi mulki akan su dukka. Kai ne kan zinariya na siffar nan.39Bayanka, wani mulki zai taso wanda bai kai kamar ka ba, daga nan mulki na uku na baƙin ƙarfe zai yi mulkin dukkan duniya.40Mulki na huɗu zai zo, mai ƙarfi kamar ƙarfe, saboda ƙarfe ya farfasa kome ya lalata su. Zai farfasa duk waɗannan abubuwa ya lalata su.41Kamar yadda ka gani an yi tafin ƙafafun rabi da yumɓu rabi da ƙarfe, mulkin zai rabu kenan; wani sashi zai sami ƙarfi kamar ƙarfe, kamar yadda ka ga an gauraya ƙarfe da yumɓu mai taushi.42Kamar yadda aka yi yatsun ƙafafun rabi da ƙarfe, rabi da yumɓu, haka mulkin zai zama wani sashi da ƙarfi wani sashi da rauni.43Kamar yadda ka ga ƙarfe gauraye da yumɓu mai taushi, haka mutanen za su zama a gauraye; ba za su tsaya tare ba kamar yadda ƙarfe ba zai gaurayu da yumɓu ba.44A cikin kwanakin waɗannan sarakunan, Allah na sama zai tayar da wani mulkin da ba za a iya rushe shi ba, waɗansu mutane ba zasu iya cin nasara akan sa ba. Zai farfasa sauran mulkokin gutsu-gutsu ya kawo ƙarshensu, shi kuwa zai kasance har abada.45Kamar yadda ka ga an saro dutse daga babban dutse, amma ba da hannuwan mutum ba. Ya farfasa ƙarfen da baƙin ƙarfe da yumɓu da azurfa da zinariya gutsu-gutsu. Allah Mai Girma ya sanar da kai, ya sarki, abin da zai faru bayan wannan. Mafarkin gaskiya ne, wannan bayanin kuma tabbas ne."46Nebukadnezza sarki ya faɗi da fuskarsa a ƙasa a gaban Daniyel ya girmama shi; ya ba da ummurni a yi bayarwa dominsa a ba shi turare.47Sarkin ya cewa Daniyel, "Hakika Allahnka shi ne Allahn alloli, Ubangijin sarakuna, wanda ya ke baiyana asirai, gama ka iya ka baiyana wannan asiri."48Sai sarki ya sa Daniyel ya zama mai martaba sosai, ya ba shi kyautai da yawa na mamaki. Ya mai da shi mai mulki a bisa dukkan gundumar Babila. Daniyel ya zama babban gwamnan masu hikima na Babila.49Daniyel ya roƙi sarki, sarkin kuma ya naɗa Shadrak, Meshak da Abednego su zama masu gudanarwa a gundumar Babila. Amma Daniyel ya zauna a fãdar sarki.
"A shekara ta biyu" (Duba:|OrdinalNumbers)
"Nebukadnezza ya yi mafarkai"
A nan "Hankalinsa" na nufin tunanin sa. AT:"Hankalinsa ya tashi" (Duba:|Metonymy)
Damuwar sa ta hana shi barci. AT: "har bai iya yin barci ba"
"Sai Sarki ya kira masu dũba"
"Mutanen da suka mutu"
"suka shiga cikin fadar"
"suka tsaya a gaban"
A nan "raina" na nufin Sarkin da kan sa. AT: "Na ƙagara"
"tsaka-mai-wuya"
Wannan yarin da mutanen Babila soke yi. "Duba:
Mai yiwuwa mutanen sun fadi hakane don su nunawa sarkin suna yi masa biyayya. AT:"Sarki, muna da begen zaka dade!"
Mutanen sun kira kansu bayin sarkin su nuna mashi bangirma
A nan kalmar "mu" na nufin mutanen da sarki ke magana da su wanda kuma bai hada da sarkin ba.
Za'a iya baiyana wannan da gabagadi.AT:"Na riga na yanke abin da zan yi game da wannan batun"
Za'a iya baiyana wannan da gabagadi.AT:"Zan umarci sojoji na su yaiyaga jukunanku a kuma mayar da gidajen ku kufai"
Za'a iya baiyana wannan da gabagadi.AT:"Zan baku kyautai"
Mutane masu hikimar sun bayayya sarkin a fakaice a matsyin bangirma.
Zabin da ba za'a iya canza wa ba an baiyana shi a matsayin wani abu mai tasiri. AT:"kunga ba zan iya canza zabi na ba game da wannan"
"akwai hukunci ɗaya ne a kanku"
Wadannan kalmomi guda biyu na da kusan ma'ana daya kuma sun fifita cewa "karya da aka shirya don ruɗi."
wadannan kalmomi biyu na kusan magana akan abu daya ne tare da fifita girman ikon Sarki. AT:"mai iko"
An yi bayanin wannan da rarraunan harshe don a nuna tasirin sa. AT: "alloli ne kadai zasu iya fadawa sarki wannan"
Wadannan kalmomi biyu na iya zama da ma'ana daya da kuma fayyace matakin hasalar sa.AT:"hasala ƙwarai"
"dukkan mutanen da ke cikin Babila"
An fadi shelar ne kamar tana da rai da kuma kamar zata iya aiwatar da kanta. AT:"Saboda haka sai Sarkin ya bada umarni" ko kuma"Saboda haka sarki ya fitar da umarni"
Za'a iya furta wannan da gabagadi. AT:"a kashe dukkan waɗanda aka sani su masu hikima ne"
Za'a iya furta wannan da gabagadi. AT:"domin a kashe su"
Wadannan kalmomi guda biyu nada ma'ana iri daya da kuma fifita tasirin ladabin sa. AT: "ladabi da hattara wajen yanke hukunci"
Wannan sunan shugaban masu tsaron sarki ne
Wannan kungiyar mutanen ne wanda aikinsu shine tsare da kare lafiyar sarki.
"wanda sarki ya aika domin ya kashe"
Maiyiwuwa Daniyel ya je fada. AT:"Daniyel ya je fada" ko kuma"Daniyel yaje yayi magana da sarki"
"ya roki wani keɓaɓɓen lokaci domin ya gana da sarki"
Wannan na nufin gidan Daniyel
"game da umarnin sarki"
"Ya roke su su yi addu'a domin jinkai"
Za'a iya furtashi da gabagadi. AT:"domin kada sarki ya kashe su" ko kuma "domin kada matsaran sarkin su kashe su"
Za'a iya baiyana wannan da gabagadi.AT:"A wannan daren Allah ya baiyana asirin"
Wannan na nufin mafarkin sarki da ma'anar sa
A nan "sunan" na nufin Allah da kansa. AT:"A yabi Allah"
Wadannan ayoyi ma sun kunshi wani sashi na addu'ar Daniyel
"ya kan cire ikon sarakuna na mulki"
A nan zama a kan "mulki" na nufin shugabancin mulki. AT: "ya sa waɗansu sarakunan a kan mulkokinsu"
"haske na zuwa daga inda Allah yake"
Wannan aya ma wani sashi ne na addu'ar Daniyel. Ya daina bayyana Allah a fakaice ya koma a zahirance.
"Ka sanar da ni da abokaina abin da muka roƙeka"(UDB)
"Ka sheda mana abin da sarki ke bukatar sani"
Wannan ne sunan shugaban sojojin sarki. Duba yadda aka fasara wannan sunan a 2:14.
"masu hikima"
Wannan ne sunan da Babiloniyawa suka ba Daniyel. Duba yadda aka fasara wannan sunan a 1:6.
Za'a iya baiyana wannan da gabagadi. AT:"Wadanda suke da hikima, wadanda suke kikirarin iya magana da matattu, matsafa, da masana taurari baza su iya baiyana asirin abin da sarki ke tambaya ba"
Wannan jimlar na magana akan mafarkin sarki
Daniyel ya ci gaba da magana ga sarki
Wannan jimla na nufin Allah. AT:"Allah,wanda ke baiyana asirai" ko kuma "Allah, mai maida asirai su zama a baiyane"
Za'a iya baiyana wannan da gabagadi. AT:"Allah bai baiyana mani wannan asirin ba"
Za'a iya baiyana wannan da gabagadi. AT: "Ya baiyana mani asirin ne domin"
Wannan jimlar na amfani da kalmar "kai" a matsayin tunanin mutum. AT:"ka gane zurfin tunanin da ke cikin zace-zacen ka"
Daniyel ya ci gaba da yin magana ga sarki
"an yi shi da zinariya mai kyau" ko kuma "zinariya mai kyau"
"an yi su rabi da ƙarfe rabi da yumɓu" ko kuma "an yi su rabi ƙarfe rabi yumɓu"
Daniyel ya ci gaba da yin magana ga sarki
Za'a iya bayyana wannan da gabagadi idan an raba jimlar gida biyu. AT: "wani ya saro dutse daga tsauni, amma ba mutum bane ya saro shi. Dutsen"
Wannan jimla na kwatanta ɓalle-ɓallen siffar da kananun abubuwa marasa nauyi wanda iska kan dauke. AT: "kamar kananun busassun ciyayi da iska ke hurewa"
Za'a iya bayyana wannan da gabagadi. AT: "sun tafi duka"
"ya warwatsu cikin duniya duka"
Daniyel ya ci gaba da yin magana ga sarki
A nan "mu" na nufin Daniyel kawai. Zai iya yiwuwa yayi amfani da fiye da daya cikin ƙasƙanci don ya gujewa fariyar sanin mafarkin da Allah ya baiyana masa.
"babban sarki mai amfani" ko kuma "sarkin da ke mulkin sarakuna" (UDB)
Wadannan kalmomi na da ma'ana kusan ɗaya.
A nan "hanu" na nufin karfin iko. AT: "Ya bayar da wurin a hannunka"
Anyi amfani da wurin a wakilci mutanen da ke zama wurin. AT:"mutanen kasar"
A nan "hanu" na nufin iko. AT: "ya baka iko a kan dabbobin da ke filaye da kuma tsuntsayen sararin sama"
A nan anyi amfani da "sama" a matsayin sararin sama
A cikin mafarkin sarkin kan siffar na wakiltar sarkin. AT: "Kan zinariyar na nuna ka" ko kuma "kan zinariyar alamar ka ce da ikon ka"
Daniyel ya ci gaba da magana ga sarki.
A cikin mafarkin sarkin mulkin sa na zinariya ne don haka wani rarraunan mulki zai zama na azurfa. AT: "wani mulkin, wanda na azurfa ne, zai taso" ko kuma "wani mulki, wanda sashin azurfa na siffar ya wakilta, zai taso"
"daga nan mulki na uku, na baƙin ƙarfe ," ko "daga nan wani mulki, wanda sashin baƙin karfe ke wakilta a jikin siffar"
Daniyel ya ci gaba da magana ga sarki.
"Mulki na huɗu zai zo"
Anyi maganar Mulki na huɗun da zama da karfi kamar ƙarfe.
Wannan yaren na nufin mulki na hudun zai lalata ya kuma maye sauran mulkokin.
"wadancan mulkokin" (UDB)
Daniyel ya ci gaba da magana ga sarki
Nebukadnezza ya ga tafin ƙafafun rabi da yumɓu rabi da ƙarfe. Bai ga matakan da aka bi wajen yin kafafun ba.
Za'a iya fadin wannan da gabagadi. AT: "haɗe-haɗen yumɓu da karfe"
"ba zasu zauna a haɗe ba"
Daniyel ya ci gaba da magana ga sarki
A nan "waɗannan sarakunan" na nufin masu mulkin da sassan siffar ke nunawa
Za'a iya baiyana wannan da gabagadi. AT: "wanda ba mai iya lalatawa, wanda kuma ba mutanen da zasu yi nasara da shi"
Za'a iya bayyana wannan da gabagadi. AT: "wani ya saro dutse daga baban dutse, amma ba mutum ne ya saro shi ba"
wanda za'a iya dogara da shi kuma daidai ne
Wannan halin ya nuna sarkin na girmama Daniyel. AT: "ya faɗi da fuskarsa a ƙasa"
Za'a iya bayyana wannan da gabagadi. AT: " bayin sa sun yi hadaya da bayarwa turare domin Daniyel"
"Hakika Allahnka ne"
"ya fi dukan alloli, da kuma Ubangijin sarakuna" (UDB)
Fassara "wanda yake baiyana asirai" kamar yadda ya ke a 2:29.
"a baiyana asirin mafarkina"
"Sarki ya maishe da Daniyel mai mulki"
Wadannan sune sunayen Babiloniya na Yahudawa ukun nan wanda aka kawo su Babila tare da Daniyel. Duba yadda aka fassara wadannan sunaye a 1:6
1Nebukadnezza sarki ya yi siffa ta zinariya wadda tsawonta ƙafa tasa'in ne fadinta kuma ƙafa tara, ya ƙafa ta a Filin Dura wanda ke a gundumar Babila.2Sai Nebukadnezza ya aika da 'yan kai saƙo, a tattaro shugabanni, masu riƙe da sassa da yankuna da gundumomi da masu ba da shawara da masu ajjiya da masu shari'a da alƙalai da dukkan manyan jami'an gundumomi, su zo wurin ƙaddamar da siffar da ya kafa.3Sai shugabannin sassa da yankuna da gundumomi da masu bada shawara da masu ajjiya da masu shari'a da alƙalai da dukkan manyan jami'an gundumomi, suka tattaru domin ƙaddamar da siffar da Nebukadnezza ya kafa. Suka tsaya a gaban siffar.4Sa'annan aka yi shela mai ƙarfi, "An ummurce ku, ku mutane da al'ummai da harsuna,5a lokacin da ku ka ji ƙarar kahonni da sarewa da garaya da molo da caki da kuge da algaita da kowanne irin kayan kiɗa, sai ku faɗi warwas a gaban siffar zinariya wadda Nebukadnezza sarki ya kafa.6Duk wanda bai faɗi ya yi sujada ba, a wannan lokacin, za a jefa shi cikin tanderu mai ci da wuta."7To lokacin da dukkan mutane suka ji ƙarar ƙahonni da sarewa da garaya da molo da caki da kuge da algaita da kowanne irin kayan kiɗa, dukkan mutane da al'ummai da harsuna suka faɗi warwas a wurin siffar zinariya wadda Nebukadnezza sarki ya kafa.8To sai waɗansu Kaldiyawa suka zo suka kawo sãra akan Yahudawa.9Suka ce da Nebukadnezza sarki, "Ranka ya daɗe, ya sarki!10Kai sarki, kai ne ka ba da ummurni, dukkan wanda ya ji ƙarar ƙahonni da sarewa da garaya da molo da caki da kuge da algaita da kowanne irin kayan kiɗa, dole ya faɗi warwas a gaban siffar zinariya.11Duk wanda bai faɗi ya yi sujada ba, dole za a jefa shi cikin tanderu mai ci da wuta.12To akwai waɗansu Yahudawa da ka naɗa su lura da harkokin gundumar Babila; sunayensu kenan, Shadrak, Meshak da Abednego. Sarki, waɗannan mutane ba su damu da kai ba. Ba za su yi wa allolinka sujada ba, balle su bauta masu, ko kuma su faɗi warwas a gaban siffar zinariya wadda ka kafa."13Sai Nebukadnezza cike da fushi da hasala, ya ummurta a kawo su Shadrak, Meshak da Abednego a wurin sa. Sai aka kawo waɗannan mutane gaban sarki.14Nebukadnezza yace da su, "Ko kun yi shawara, ya Shadrak, Meshak da Abednego, ba za ku yi sujada ga allolina ba ko ku faɗi warwas a gaban siffar zinariya wadda na kafa ba?15Yanzu idan kuna shirye -lokacin da ku ka ji ƙarar ƙahonni da sarewa da giraya da caki da kuge da algaita da kowanne irin kayan kiɗa - ku faɗi warwas a gaban siffa wadda na kafa, ba komai. Amma idan ba za ku yi sujada ba, yanzun nan za a jefa ku cikin tanderu mai ci da wuta. Wanne allah ne zai iya kuɓutar da ku daga hannuna?"16Shadrak, Meshak da Abedinego suka amsa wa sarki, "Nebukadnezza, ba mu da bukata mu amsa maka a kan wannan magana.17Idan da wata amsa ita ce, Allahn da muke bauta wa zai iya tsare mu lafiya daga cikin tanderu mai ci da wuta, kuma zai kuɓutar da mu daga hannunka, ya sarki.18Amma idan ma ba haka ba, bari ka sani ya sarki, ba za mu bauta wa allolinka ba, kuma ba za mu faɗi warwas a gaban siffar zinariya wadda ka kafa ba."19Sai Nebukadnezza ya cika da hasala; yanayin fuskarsa ya canza game da Shadrak, Meshak da Abednego. Ya ba da ummurni a zuga tanderun har sau bakwai fiye da yadda aka saba zugawa.20Sa'annan ya ummurci waɗansu ƙarfafa cikin sojojinsa su ɗaure su Shedrak, Meshak da Abedinego, su jefa su cikin tanderun mai ci da wuta.21Aka ɗaure su saye da tufafinsu da alkyabbunsu da rawunansu da sauran kayan jikinsu, aka jefa su cikin tanderun mai ci.22Saboda ummurnin sarki ya yi tsauri kuma haka aka yi, tanderun ya yi zafi ƙwarai, harshen wuta ya kashe mutanen da suka ɗauki su Shedrak da Meshak da Abednego.23Waɗannan mutane uku, wato, Shedrak, Meshak da Abednego, suka faɗa a cikin tanderun mai ci da wuta a ɗaure.24Sai Nebukadnezza ya cika da mamaki, ya tashi da sauri. Ya tambayi mashawartansa, "Ba mutane uku mu ka jefa a ɗaure cikin wuta ba?" Suka amsa wa sarki suka ce, "Tabbas haka ne, ya sarki."25Ya amsa ya ce, "Na ga mutane huɗu ba a ɗaure ba suna yawo a cikin wutar, kuma ba abin da ya same su. Hasken na huɗun kamar na ɗan alloli."26Sai Nebukadnezza ya zo kusa da ƙofar tanderun mai ci da wuta ya yi kira, "Shedrak, Meshak, da Abednego bayin Allah Mafi Ɗaukaka, ku fito! Ku zo nan!" Sai su Shadrak, Meshak da Abednego suka fito daga cikin wutar.27Shugabannin sassa da yankuna da gundumomi da suka taru a wurin suka ga waɗannan mutane. Wuta ba ta ƙona jukkunansu ba; gashin kansu bai taɓu ba; kuma ba abin da ya sami tufafinsu; kuma babu ƙaurin wuta a jikinsu.28Nebukadnezza yace, "Bari mu yabi Allah na Shadrak, Meshak da Abednego wanda ya aiko ɗan saƙonsa ya ba bayinsa saƙo. Sun gaskata da shi lokacin da ba su bi dokata ba, sun ba da jikkunansu a maimakon su yi sujada ga wani allah ko su faɗi warwas a gabansa sai dai Allahnsu kaɗai.29Saboda haka na ba da ummurni ko dukkan mutane ko al'umma ko harshen da ya yi magana gãba da Allah na Shadrak, Meshak da Abednego dole za a yayyaga su a mai, da gidajensu juji saboda ba wani allah da zai iya yin ceto kamar wannan."30Sa'annan sarki ya ƙara wa su Shadrak, Meshak da Abednego girma a cikin gundumar Babila.
Yadda mutanen Nebukadnezza suka gina tare da kafa siffar ta wurin umarnin sa an baiyana shi kamar Nebukadnezza ya gina tare da kafa siffar. AT: "Nebukadnezza ya umarci mutanen sa suyi siffar zinariya...sun kafa ta"
"kusan tsawo mita 27 da faɗi kusan mita 3"
Wannan wani wuri ne a cikin yankin mulkin Babila.
Wadannan shugabanni ne wadanda ke da matakan iko akan sassa dabam-dabam
Wadannan maikata ne ke kula da harkokin kuɗi
A fassara wadannan kamar yadda ya ke a 3:1
Kamar yadda mutane Nebukadnezza suka kafa siffar an baiyana shi ne kamar Nebukadnezza ne ya gina ta. AT: "siffar da mutanen Nebukadnezza suka kafa"
Wannan mutumin zaɓaɓɓen dan saƙon sarki ne
Za'a iya baiyana wannan da gabagaɗi. "Sarkin ya umarce ka"
A nan "kasashe" da "harsuna" na nufin mutane daga kasashe masu magana da harsuna dabam-dabam. AT:"mutane daga kasashe masu magana da harsuna dabam-dabam"
Wadannan kayayyakin kiɗane daidai da caki. An siffanta su ne da kusurwowi uku suna kuma da tsarkiya huɗu
A nan "faɗi ƙasa" na nufin "rusunawa da sauri"
" faɗuwa ƙasa warwas da fuska kasa cikin yanayin sujada ga"
Za'a iya baiyana wannan da gabagaɗi. AT:"Sojojin zasu jefa duk wanda bai rusuna yayi wa siffar sujadaba a wannan lokacin da sukaji amon kayan kaɗe-kaɗe cikin tanderu mai ci da wuta"
A nan "faɗi ƙasa" na nufin "faɗuwa ƙasa warwas"
Wannan wani ɗaki ne da aka cika shi da wuta mai zafi.
A nan "dukan" na nufin dukan mutanen da suka kasance
A nan "al'umma" da "harsuna" na nufin muytane daga kasashe dabam-dabam da ke magana da harsuna dabam-dabam. Duba yadda aka fassara wannan a cikin 3:3. AT: "al'umma daga kasashe dabam-dabam masu magana da harsuna dabam-dabam"
Wadannan kayan kiɗe-kiɗe ne. Fassara wadannan kamar yadda ka yi a 3:3
A nan "kwanciya ƙasa" na nufin "faɗuwa ƙasa da sauri"
" faɗuwa ƙasa warwas da fuska kasa cikin yanayin sujada ga"
Kamar yadda mutane Nebukadnezza suka kafa siffar an baiyana shi ne kamar Nebukadnezza ne ya gina ta. AT: "siffar da mutanen Nebukadnezza suka kafa"
Anyi amfani da wannan kalmane domin a nimfasa game da cikakken labarin. A nan marubucin yayi magana kana wasu sabbin mutane a cikin labarin
Wannan hanyace da aka saba miƙa gaisuwa ga sarki
Wadannan kayan kaɗe-kaɗe ne. Fassara wannan kamar yadda kayi a 3:3
A nan "faɗi ƙasa" na nufin "faduwa ƙasa warwas"
" faɗuwa ƙasa warwas da fuska kasa cikin yanayin sujada ga"
Za'a iya baiyana wannan da gabagaɗi. AT: "An umarci sojoji su jefa cikin tanderun wuta mai ci duk wanda bai rusuna ƙasa ba yayi sujada"
A nan "faɗi ƙasa" na nufin "faduwa ƙasa warwas"
Wannan wani ɗaki ne da aka cika shi da wuta mai zafi. Fassara wannan kamar yadda da akayi a 3:6
"abubuwa" ko "harkokin yau da kullum"
Wadannan sune sunayen Babiloniya na Yahudawa ukun nan wanda aka kawo su Babila tare da Daniyel. Duba yadda aka fassara wadannan sunaye a 1:6
"kada a saurare ka"
" faɗuwa ƙasa warwas da fuska kasa cikin yanayin sujada ga"
Kamar yadda mutane Nebukadnezza suka kafa siffar an baiyana shi ne kamar Nebukadnezza ne ya gina ta. AT: "siffar da mutanen Nebukadnezza suka kafa"
Fushi da hasala Nebukadnezza sun kai matakin da yana baiyana su kamar sun cika shi. A nan "fushi" da "hasala" na da ma'ana kusan ɗaya kuma anyi amfani da su ne a baiyana matakin damuwar sarkin. AT: "matsananci fushi"
Wadannan sune sunayen Babiloniya na Yahudawa ukun nan wanda aka kawo su Babila tare da Daniyel. Duba yadda aka fassara wadannan sunaye a 1:6
A nan "shawara" na nufin zaɓi. Ka "yi zaɓi" habaici ne da ke nufin yin zaɓi na haƙika. AT:"Ka yi zaɓi na haƙika"
" faɗuwa ƙasa warwas da fuska kasa cikin yanayin sujada ga"
Kamar yadda mutane Nebukadnezza suka kafa siffar an baiyana shi ne kamar Nebukadnezza ne ya gina ta. AT: "siffar da mutanen Nebukadnezza suka kafa"
Wadannan kayan kaɗe-kaɗe ne. Fassara wannan kamar yadda kayi a 3:3
A nan "faɗi ƙasa" na nufin "faduwa ƙasa warwas"
" faɗuwa ƙasa warwas da fuska kasa cikin yanayin sujada ga"
"ba za'a sake samun matsala ba" ko "za ka zama da yancin tafiya"
Kamar yadda mutane Nebukadnezza suka kafa siffar an baiyana shi ne kamar Nebukadnezza ne ya gina ta. AT: "siffar da mutanen Nebukadnezza suka kafa"
Za'a iya baiyana wannan da gabagadi. AT: "Sojojina za su jefa ka cikin tanderun wuta nan take"
Wannan wani ɗaki ne da aka cika shi da wuta mai zafi. Fassara wannan kamar yadda da akayi a 3:6
Sarkin bai tsammaci ansa ba. Yana tsoratar da mutane ukun ne. AT: "Ba wani allah da zai iya yantar da ku daga iko na!"
A nan "hannuna" na nufin ikon iya azabtarwa. AT: "daga horo na"
Wannan wani ɗaki ne da aka cika shi da wuta mai zafi. Fassara wannan kamar yadda da akayi a 3:6
A nan "hannuna" na nufin ikon iya azabtarwa. AT: "daga horo na"
"Amma ya sarki, muna so ka sani cewa koda Allahn mu ba zai yantar da mu ba"
" faɗuwa ƙasa warwas da fuska kasa cikin yanayin sujada ga"
Kamar yadda mutane Nebukadnezza suka kafa siffar an baiyana shi ne kamar Nebukadnezza ne ya gina ta. AT: "siffar da mutanen ka suka kafa"
Sarkin ya cika da hasala har ya kai ana baiyana shi kamar an ƙure shi. AT: "Nebukadnezza ya zama da fusata kwarai"
A nan " zugawa sau bakwai fiye" habaici ne da ke nufin a maishe da wutar da zafi ainun. Za'a iya baiyana wannan da gabagaɗi. AT: "Ya umarci mutanen sa su zuga tanderun wutar fiye da yadda suka saba yi"
Rawani wani lulluɓi ne da ake yi a kai ta wurin naɗa tufafi
Wannan wani ɗaki ne da aka cika shi da wuta mai zafi. Fassara wannan kamar yadda da akayi a 3:6
Za'a iya baiyana wannan da gabagaɗi. AT: "Domin mutanen sun yi daidai yadda sarki ya umarta"
"mutane uku mu ka jefa a ɗaure cikin wuta ba,ko"
An yarda allolin na haske kamar walkiya. AT: "Hasken na huɗun kamar yadda ɗan alloli ke yi"
Wadannan shugabannai ne dake da iko akan yankuna dabam-dabam. Duba yadda aka fassara wannan a 3:1
Za'a iya baiyana wannan da gabagaɗi. AT: "gashin kansu bai taɓu ba"
"babbake kaɗan"
Za'a iya baiyana wannan da gabagaɗi. AT: "wutar bata ƙona tufafin su ba"
"basa ƙaurin wuta a jikinsu"
An bayyana kin bin umarnin sarki kamar an janye shi ne daga wurin su. AT: "sun bijirewa umarni na"
Wannan jimlar na nuna ra'ayin mutane ukun su mutu domin abin da suka gasganta da shi. AT:"sun yarda su mutu"
"faɗuwa ƙasa warwas da fuska kasa cikin yanayin sujada ga"
"duk wani allah sai dai Allahn su"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT"bayina za su yayyaga kowacce al'umma, kasa, ko yare...a kuma maishe da gidajensu juji"
A nan "al'ummai" da "harsuna" na nuna mutane daga kasashe dabam-dabam masu magana da harsuna dabam-dabam. Duba yadda aka fassara irin wannan jimlar a 3:3. AT: "ko wacce al'umma daga kowacce ƙasa, ko ko duk wanda suke magana da kowanne harshe da ke cewa"
"yin magana da bata nuna bangirma ga Allah"
"za'a yayyage jukkunan su"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Allahn su ne kadai zai iya ceto kamar haka"
1Sarki Nebukadnezza ya aika wannan umarni ga dukkan mutane da al'ummai, da harsuna waɗanda ke zaune a duniya: "Bari salamarku ta ƙaru.2Na ga ya yi kyau in faɗa maku akan waɗansu abubuwan alamu da al'ajabai da Maɗaukaki ya yi mani.3Ya ya girman alamunsa, kuma ya ya girman al'ajabansa! Sarautarsa har abada ce kuma mulkinsa daga zamani zuwa zamani ne."4Ni, Nebukadnezza ina zaune cike da murna a cikin gidana, ina nishaɗi a fãdata.5Sai na yi mafarki wanda ya sa na ji tsoro. lokacin da na ke kwance, kamanni da wahayin da na gani ya dami tunanina ƙwarai.6Saboda haka sai na ummarta a kirawo mani dukkan masu hikima na Babila don su yi mani fassarar mafarkin.7Sai masu sihiri da waɗanda ke cewa suna magana da matattu da masu hikima da masu duba suka zo. Na faɗa masu mafarkin, amma ba su iya fassara mani ba.8Sai daga baya Daniyel ya zo - wanda a kira Beltishazza wato irin sunan allahna, a gare shi kuwa akwai ruhun alloli tsarkaka-- na faɗa masa mafarkin.9Beltishazza, shugaban masu sihiri, na sani ruhun alloli tsarkaka yana cikinka kuma ba wani asirin da zai fi ƙarfin ganewarka. Ka faɗa mani mene ne na gani a mafarkina kuma me ya ke nufi.10Waɗannan su ne alamun da na gani a cikin tunanina lokacin da nake kwance akan gadona: Na duba, akwai wani itace a tsakiyar duniya, yana da tsayi ƙwarai da gaske.11Itacen ya yi girma ya zama mai ƙarfi. ƙwanƙolinsa ya kai sammai, kuma ana iya ganinsa har duk ƙarshen duniya.12Yana da ganyaye masu kyau, 'ya'yansa kuwa suna da yawa, a kansa kuma akwai abinci domin kowa. Namomin jeji suka sami inuwa a ƙarƙashinsa, tsuntsayen sama kuma suka zauna a rassansa. Dukkan masu rai suna ci daga gare shi.13A tunaninna da nake kwance akan gadona na ga wani tsattsarkan mai saƙo ya sauko daga sammai.14Sai ya yi magana da ƙarfi, ya ce, 'A sare itacen, a kuma daddatse rassansa, a zage ganyayensa kakaf, a kuma warwatsar da 'ya'yansa. Bari namomin jeji su yi gudu daga ƙarƙashinsa, tsutsaye kuma su tashi daga rassansa.15A bar kututturen da saiwoyinsa a cikin ƙasa, ɗaure da sarƙar baƙin ƙarfe da tagulla, a cikin tsakiyar ɗanyar ciyawar saura. A bar shi ya jiƙe da raɓa daga sammai. A bar shi ya zauna da namomi a cikin tsirai na ƙasa.16Bari tunaninsa ya canja daga tunanin mutum, a kuma ba shi tunanin irin na dabba zai zauna a wannan hali har shekaru bakwai.17Wannan ita ce shawara da hukuncin da ɗan saƙon ya faɗa. Shawarar da masu tsarki suka zartar don waɗanda ke da rai su sani Maɗaukaki ne ke sarautar mulkokin 'yan adam, ya kan kuma ba da ita ga wanda ya ga dama a maimakonsu, har ma da mutane masu tawali'u.'18Ni, sarki Nebukadnezza, na yi wannan mafarki. Yanzu kai, Beltishazza, ka faɗa mani ma'anarsa, domin dukkan masu hikima na cikin mulkina ba su iya faɗa mani ma'anar ba. Amma kai za ka iya yi, gama ruhun alloli tsakaka yana cikinka."19Sai Daniyel, wanda aka lakaba wa suna Beltishazza, ya tsaya zugum da ɗan daɗewa, tunaninsa ya ba shi tsoro. Sarki yace, "Beltishazza, kada ka bar mafarkin ko ma'anarsa ya ba ka tsoro." Beltishhazza ya amsa, "Ya shugabana, bari mafarkin ya zama domin waɗanda ke gãba da kai ne; bari ma'anarsa kuma ta zama ta masu gãba da kai.20Itacen nan da ka gani - wanda ya yi girma ya kuma yi ƙarfi, wanda ƙwanƙolinsa kuma ya kai sammai, har ma wanda za a iya ganinnsa daga ko'ina a duniya -21wanda ke da ganyaye masu kyau, wanda kuma har ya yi 'ya'ya jingim, don a cikinsa akwai abinci domin kowa, har ma namomin jeji sun sami inuwa a ƙarƙashinsa, wanda tsuntsaye sammai kuma suka zauna a kai -22wannan itacen kuwa kai ne, ya sarki, kai ne ka yi girma ka ƙasaita. Girmanka kuma ya kai har sammai, mulkinka kuma ya kai har iyakar duniya.23Kai, sarki, ka ga tsattsarkan ɗan saƙo na saukowa daga sama yana cewa, 'A sare itacen nan, a ragargaje shi, amma a bar kututturen da saiwoyinsa cikin ƙasa, a ɗaure da sarƙar ƙarfe da kuma tagulla, a tsakiyar ɗanyar ciyawar saura. A bar shi can ya jiƙe da raɓa daga sammai. Bari ya zauna tare da namomin jeji har shekaru bakwai.'24Wannan ita ce fassarar, sarki. Wannan hukunci ne na Maɗaukaki ya same ka, shugabana sarki.25Za a kore ka daga cikin mutane, zaka kuma zauna tare da namomin jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa, zaka jiƙe da raɓa daga sammai, har shekaru bakwai sun cika lokacin nan za ka sani Maɗaukaki ne ke sarautar mulkin 'yan adam, kuma ya kan ba da ita ga kowa yadda ya ga dama.26Kamar yadda aka ummarta a bar kututturen itace da saiwoyinsa, a wannan hanyar mulkinka zai dawo gare ka daga lokacin da ka san Mai sama ne ke mulki.27Saboda haka, ya sarki, bari shawarata ta sami karɓuwa gare ka. Ka daina zunubi, ka yi abin da ke da kyau. Ka juyo daga muguntarka ta wurin aikata alheri ga waɗanda ake wulaƙantawa, wataƙila za a ƙara maka tsawon kwanakinka da salama."28Dukkan waɗannan abubuwa sun kasance ga sarki Nebukadnezza.29Bayan wata goma sha biyu lokacin da ya ke tafiya akan benen fãdar Babila,30sai ya ce, "Ashe wannan ba ita ce babbar Babila ba, wadda ni da kaina na gina domin zama fãdar sarauta, don darajar ɗaukakata ba?"31Lokacin da kalmomi ke fita daga leɓunan sarki, sai ga murya daga sama: "Sarki Nebukadnezza, ana sanar da kai an ɗauke wannan mulkin daga gare ka.32Za a kuma kore ka daga cikin mutane, gidanka kuwa zai kasance tare da namomin jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa. Shekaru bakwai cur zasu wuce sa'an nan za ka gane Maɗaukaki ne ke mulkin mulkokin mutane, yana kuma ba da su ga wanda ya ga dama."33Wannan hukuncin akan Nebukadnezza ya tabbata nan take. An kore shi daga cikin mutane. Ya shiga cin ciyawa kamar sa, jikinsa kuwa ya jiƙe da raɓa daga sammai. Gashinsa kuma ya yi tsawo kamar gashin gaggafa, farotansa kuma suka yi tsawo kamar na shaho.34A ƙarshen kwanakin ni, Nebukadnezza, sai na ɗaga idanuna sama, hankalina ya komo gare ni. "Na ɗaukaka Maɗaukaki, na yi yabo na kuma ɗaukaka shi wanda ke rayayye har abada. Gama mulkinsa madawwamin mulki ne, sarautarsa kuwa daga dukkan zamanai zuwa zamanai ne.35Dukkan mazaunan duniya yana ɗaukan su kamar ba a bakin kome suke a gare shi ba; yakan yi yadda ya nufa a cikin rundunar sama da mazaunan duniya abin da ya yi masa dai-dai. Babu wanda zai iya hana wa ko ya ƙalubalance shi. Ba wanda zai ce da shi, 'Me ya sa ka yi wannan?"36A lokacin nan hankalina ya komo gare ni, an mayar mani da sarautata da darajar mulkina. 'Yan majalisata da fãdawana suka dawo da mutuncina. Aka maido ni kan gadon sarautata, har ma an darajanta ni fiye da dã.37Yanzu ni, Nebukadnezza, na ba da yabo da girma da ɗaukaka ga Sarkin samaniya, domin dukkan abubuwan da ya aikata masu kyau ne, al'amuransa kuma gaskiya ne. Ya kan ƙasƙantar da waɗanda ke da girmankai.
A wannan sura, Nebukadnezza ya sheda abin da Allah yayi masa. A aya ta 1-18, Nebukadnezza ya bayyana mafarkinsa a zahirance daga Allah. Aya 19-33 ta bayyana hukuncin Nebukadnezza. Aya 34-37 ta bayyana yadda ya maida martani ga Allah.
Wannan jimla na nuna dan saƙon sarkin a matsayin sarkin da kansa. AT:"Nebukadnezza ya aiki yan saƙon sa da"
A nan "al'ummai" da "harsuna" na nuna mutane daga kasashe dabam-dabam masu magana da harsuna dabam-dabam. Duba yadda aka fassara irin wannan jimlar a 3:3. AT: "ko wacce al'umma daga kowacce ƙasa, ko ko duk wanda suke magana da kowanne harshe da ke cewa"
Sarakuna kan fifita faɗin girman yadda masarautar su. Nebukadnezza yayi mulki kan kusan duk wuraren da aka sani a duniya a lokacin da aka rubuta wannan littafin. AT: "wadanda suke rayuwa a yankin mulki Babila"
Wannan gaisuwa ce da aka saba yi
Wadannan kalmomi na da ma'ana kusan iri ɗaya kuma suna nuna abubuwan banmamaki da Allah yayi.
Wadannan jimloli na da ma'ana ɗaya ana kuma amfani da su ne wajen nuna yadda girman al'ajibai da ma'ujjizan Allah suke.
Wadannan jimloli na da ma'ana ɗaya an kuma maimaita su ne don nuna yadda Allah yake mulki har abada
A aya ta 1-18, Nebukadnezza ya bayyana wahayin sa daga Allah.
Wadannan jimloli biyu sun yi hannun riga kuma suna da ma'ana iri ɗaya
Wadannan jimlolin na da kusa ma'ana daya.
Wadannan jimlolin na da kusa ma'ana daya.
Wadannan jimloli biyu sun yi hannun riga kuma suna da ma'ana iri ɗaya
"dukan masu hikima na Babila"
A aya ta 1-18, Nebukadnezza ya bayyana wahayin sa daga Allah.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"wanda na kira da suna Beltishazza"
Wannan shine sunan da Babiloniyawa suka baiwa Daniyel. Dubi yadda aka fassara wannan sunan a 1:6.
Nebukadnezza ya gamsu cewa ikon Daniyel ya fito ne daga allolin karya da Nebukadnezza ke bautawa.
Za'a iya bayyana haka.AT:"kana fahimtar ma'anar kowanne irin asiri"
A aya ta 1-18, Nebukadnezza ya bayyana wahayin sa daga Allah.
abubuwan da zaka iya gani
"yana da tsawo kwarai"
Wannan yarene da ke fifita tsayi da yadda itacen yake.AT:"Yayi kamar ƙwanƙolinsa ya kai sammai, kuma ana iya ganinsa har duk ƙarshen duniya"
"yana da 'ya'ya da yawa akan itacen"
"abinci ne ga mutane da dabbobi duka"
A aya ta 1-18, Nebukadnezza ya bayyana wahayin sa daga Allah.
Wannan na nufin ganin mafarki ko wahayi. AT:"Na gani a mafarki na"
za'a iya fahimtar cewa dan aike mai tsarki na magana ne ga fiye da mutum ɗaya. AT:"Yayi magana da karfi ga wasu mutane ya ce"
"namomin jeji su yi gudu daga ƙarƙashinsa, tsutsaye kuma su tashi daga rassansa"
A aya ta 1-18, Nebukadnezza ya bayyana wahayin sa daga Allah.
Dan saƙo mai tsarki a cikin wahayin ya ci gaba da sowa ga wadansu mutane
Wannan sashi ne na itace da ake bari bayan an sare itace
danshin da ake gani kan ƙasa da safe
Tun da itaciyar na wakiltar Nebukadnezza, wakilin sunan "na shi" da "shi" a aya ta 16 na nufin itace daya ne da ak yiwa laƙabi da "shi" a aya ta 15 AT: "Zuciyar mutum kan canza daga zuciyar mutum zuwa ta dabbba har tsawon lokacin shekara bakwai" (Duba:
A aya ta 1-18, Nebukadnezza ya bayyana wahayin sa daga Allah.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Masu tsarki ne suka yi wannan ƙudiri"
Wannan jimlar watakila na nufin mala'iku. AT:"Mala'iku masu tsarki"
"duk mai rayuwa" ko "kowa"
"bayaswa ga mulkokin"
Wannan shine sunan da Babiloniyawa suka ba Daniyel. Duba yadda aka fasara wannan sunan a cikin 1:6.
"kana iya fassara shi"
Nebukadnezza ya yarda cewa ikon Daniyel ya zo ne daga allolin karya da Nebukadnezza ke bautawa. Wannan ba daidai yake da "tsarkaka" a aya ta 17. Dubi yadda aka fassara wannan jimlar a cikin 4:7
A aya ta 19-33 an yi amfani da mafayyaciyar kalma a bayyana horon Nabudkanezza.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"wanda aka lakaba wa suna Beltishazza"
Fahimtar wahayin da Daniyel ya yi ne ya tada masa hankali. Za'a iya faiyace wannan. AT:"kada ka faɖi wani abu har na wani dan lokaci domin ya hassala matuka game da ma'anar mafarkin" UDB)
Daniyel na baiyana fatanshi na tsammanin mafarkin ba game da Nebukadnezza ba ne, duk da cewa ya gane cewa tabbas game da sarki ne
A aya ta 19-33 an yi amfani da mafayyaciyar kalma a bayyana horon Nabudkanezza.
Kalmomi da yawa a wannan surar na da kusan ma'ana daya kamar yadda ya ke a 4:10. Dubi yadda ka fasara wadannan ayoyin.
"barkatai"
"wannana itace na wakiltar ka, ya sarki"
Wadannan jimloli biyun na nufin abu iri daya.
Wannan jimla na amfani da kalmar "girma" a matsayin hanya ta cewa girman sarkin ya ƙasaita. AT:"girmanka ya ƙasaita"
Wadannan jimlolin na fifita abin da kowa a ko'ina ya sani kan girman yadda Nebukadnezza yake.
A aya ta 19-33 an yi amfani da mafayyaciyar kalma a bayyana horon Nabudkanezza.
Wannan aya na kusan daidai da 4:13 da 4:15. Duba yadda aka fassara wadannan ayoyin
Wannan sashi ne na itace da ake bari bayan an sare itace
"zagaye da ɗanyar ciyawar saura"
danshin da ake gani kan ƙasa da safe
A aya ta 19-33 an yi amfani da mafayyaciyar kalma a bayyana horon Nabudkanezza.
A aya ta 19-33 an yi amfani da mafayyaciyar kalma a bayyana horon Nabudkanezza.
"wanda ka ji"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Mutane zasu kore ka daga cikin su"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"zaka ci ciyawa"
A aya ta 19-33 an yi amfani da mafayyaciyar kalma a bayyana horon Nabudkanezza.
A nan "sama" na nufin allahn da ke zama sama. AT:"Allah na sama ne ke mulkin komai"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"ina roƙo bari shawarata ta sami karɓuwa gare ka"
A nan yi magana kan ƙin zunubi kamar guje masa. AT:"Ka gujewa zunubi"
Wannan na nufin mutanen da aka wulaƙanta.AT:"mutanen da akawulakanta"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Allah zai iya kara maka kanakin yalwarka"
A aya ta 19-33 an yi amfani da mafayyaciyar kalma a bayyana horon Nabudkanezza.
Bayanan dake cikin 4:28 a sake shirya su saboda haka za'a iya fahimtar ma'anar ta da sauki.
"wata 12"
Nebukadnezza yayi wannan tambaya domin ya fifita daukakar sa. Za'a iya fassara wannan a matsayin magana. AT:"Ashe wannan ba ita ce babbar Babila ba... don darajar ɗaukakata ba!"
"in nunawa mutane girmana da daukaka ta" (UDB)
A aya ta 19-33 an yi amfani da mafayyaciyar kalma a bayyana horon Nabudkanezza.
Wannan habaicin na nufin lokacin da sarkin ke kan magana.AT:" Lokacin da kalmomi ke fita daga leɓunan sarki"
"ya ji murya daga sama"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Sarki Nebukadnezza, an yi umarni a kan ka cewa baka da wani tasiri yanzu kan wannan mulkin"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Mutane zasu koreka daga wurin su"
"duk wanda ya zaɓa"
A aya ta 19-33 an yi amfani da mafayyaciyar kalma a bayyana horon Nabudkanezza.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Wannan hukuncin a kan Nebukadnezza ya tabbata nan take"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:" Mutane sun kore shi daga cikin su"
"farotansa kuma suka zama kamar na shaho"
A aya ta 34-37 Nebukadnezza yayi magana a zahiri ya nuna martanin sa ga Allah
Wannan na nufin shekaru bakwa a cikin 4:31
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:" hankalina ya komo gare ni" ko "na sake zama mai hankali"
Wadannan kalmomi biyu na nufin aiki ɗaya ne.
Wadannan jimloli na iya zama abu ɗaya an kuma yi amfani da su ne don fifita yadda mulkin Allah zai dauwama. AT:"Mulkin sa zai dauwama har abada"
A aya ta 34-37 Nebukadnezza yayi magana a zahiri ya nuna martanin sa ga Allah
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:" Ya kalli dukkan mazaunan duniya kamar ba a bakin kome suke a gare shi ba"
"Dukkan mutanen duniya"
"Mala'ikun sojojin sama" (UDB)
"abin da ya yi masa dai-dai" ko "duk abin da ya so yayi"
Zai zama da taimako a ƙara wasu bayanai. AT:"Ba wanda zai dakatar da shi abin abin da yayi niyar yi"
Wannan zai iya zama kamar zance a ɓoye.AT:" Babu mai tambayar shi abin da yake yi"
A aya ta 34-37 Nebukadnezza yayi magana a zahiri ya nuna martanin sa ga Allah
A nan an bayyana hankalin sa kamar zai iya dawowa da ikon kansa.AT:"Hankalina ya komo"
A nan an yi magana kan sarauta da daraja kamar zasu iya kafa kansu. AT:"an mayar mani da sarautata da darajar mulkina"
Wadannan kalmomi biyu na nuna girman daukakar Allah.
'"Yan majalisata da fadawa na sun sake neman taimakona"
A nan "kujerar mulki" na nufin ikon jagoranci.AT:"Na komo mulkina, na kuma ƙara samun daukaka"
Duka wadannan kalmomi ukun na nuna yadda yake daukaka Allah.
A wannan jimlar an yi amfani da "ke da" don nuna girmankai. AT:"masu girman kai"
1Sarki Belshazza ya yi babban liyafa domin manyan mutanensa, ya kuwa sha ruwan inabi a gaban dukkan su su dubu.2A lokacin da Belshazza ya kurɓi ruwan inabin, sai ya umarta a kawo tasoshi na zinariya da na azurfa waɗanda Nebukadnezza ubansa ya ɗauko daga cikin haikali a Yerusalem, daga waɗanda shi kansa, da manyan mutanensa da matansa da ƙwaraƙwaransa za su sha.3Barorinsa kuwa suka ɗauko waɗannan kayyayaki da aka kwaso su daga cikin haikali, gidan Allah, a Yerusalem. Sarki da manyan mutanensa da matansa da ƙwaraƙwarnsa suka sha a cikin su.4Sun sha ruwan inabin sun yabi allolinsu waɗanda aka yi da zinariya da azurfa da tagulla da baƙin ƙarfe da katako da kuma dutse.5A dai- dai wannan lokaci sai ga yatsun hannun mutum suka bayyana a gaban fitila da rubutu a kan shafen bangon fadar sarki. Sarki ya ga rabin hannun na rubutu.6Sai fuskar sarki ta turɓune, tunaninsa ya razanar da shi; gaɓoɓinsa kuwa suka saki, gwiwoyinsa suka soma bugun juna.7Sarki ya yi umarni da babbar murya a kawo masu cewa suna iya magana da matattu, da masu dabo da bokaye, da masu duba. Sarki ya ce da waɗannan da aka san su masu hikima ne a Babila, "Wanda duk ya bayyana wannan rubutu ya kuma faɗi ma'anarsa za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa. Zai zama da iko ya kuma zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar."8Sai dukkan waɗanda aka san masu hikima na sarki ne suka shigo, amma babu wanda ya iya karanta rubutun balle ya faɗa wa sarki ma'anarsa.9Sarki Belshazza kuwa ya firgita ƙwarai, fuskarsa ta turɓune. Fãdawansa kuma duk suka ruɗe.10Yanzu da sarauniya ta zo wurin babban liyafa domin abin da sarki da manyan fãdawansa suka ce. Sarauniya ta ce "Ran sarki, ya daɗe! Kada ka bar tunaninka ya sami damuwa. Kada kuma ka bar fuskarka ta turɓune.11Ai, akwai wani mutum a cikin mulkinka wanda ke da ruhun alloli tsarkaka. A kwanakin ubanka, an iske haske da fahimi da hikima da ganewa kamar na alloli a cikinsa. Sarki Nebukadnezza, ubanka sarki, ya naɗa shi shugaba na masu sihiri, da kuma shugaban masu magana da matattu, da bokaye da masu dũba.12Ya na da ruhu nagari, da ilimi da ganewa da fassarar mafarkai da bayyana ma'anar ka-cici-ka-cici, da warware al'amura masu wuya - waɗannan ƙwarewa aka sami wannan mutum wato Daniyel da su, wanda sarki ya lakaɓa wa suna Beltishazza. Yanzu sai ka kirawo Daniyel, shi kuwa zai faɗa maka ma'anar abin da aka rubuta."13Sai aka kawo Daniyel a gaban sarki. Sarki ya cewa Daniyel, "Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin waɗanda aka ɗauko a Yahuda, wanda ubana sarki ya kawo daga Yahuda.14Na ji labarinka, ruhun alloli tsarkaka na cikinka, haske da ganewa da mafificiyar hikima aka samu a cikinka tare.15Yanzun nan mutanen da aka san su da hikima da waɗanda ke magana da matattu an kawo su gabana don su karanta wannan rubutu su kuma yi mani fassara, amma sun kasa faɗar ma'anar rabutun.16Amma na ji kai kana iya fassara, ka kuma iya warware al'amura masu wuya. Yanzu idan fa ka iya karanta rubutun nan, har kuma ka iya faɗa mani ma'anarsa, za a sa maka rigar shunayya, a kuma sa maka sarƙar zinariya a wuyanka, za ka zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar."17Sai Daniyel ya amsa a gaban sarki, "Bar kyautarka don kanka, ka ba wani ladan. Duk da haka zan karanta rubutun a gare ka, ya sarki, zan kuma faɗa maka ma'anarsa.18Ya sarki, Allah Maɗaukaki ya ba Nebukadnezza ubanka sarauta, da girma, da daraja, da martaba.19Saboda girman da Allah ya ba shi, dukkan mutane, da al'ummai, da harsuna suka ji tsoronsa suna rawar jiki a gabansa. Ya kashe duk waɗanda ya ke so ya kashe, ya kuma bar waɗanda ya ke so ya bar su su rayu. Haka nan kuma ya kan ɗaukaka waɗanda ya ke so, ya kuma ƙasƙantar da waɗanda ya ga dama.20Amma sa'ad da zuciyarsa ta kumbura, ruhunsa kuma ya taurare don haka sai ya yi girmankai, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa.21Aka kore shi daga cikin mutane, aka ba shi hali irin na dabba, ya kuma zauna tare da jakunan jeji. Yana ta cin ciyawa kamar sã. Jikinsa ya jiƙe da raɓa daga sammai har zuwa lokacin da ya gane ashe Allah Maɗaukaki ne ke mulkin 'yan'adam, ya kan kuma ba da shi ga wanda ya ga dama.22Kai kuma ɗansa, Belshazza, ba ka ƙasƙantar da zuciyarka ba, duk da ka san wannan dukka,23Sai ka ɗaukaka kanka kana nuna wa Ubangiji na sama girmankai. Tun daga gidansa suka kawo maka waɗannan abubuwa kai da fãdawanka, da matanka da ƙwaraƙwaranka ku ka sha ruwan inabi daga ciki, kuna yabon gumakan da aka yi da zinariya da na azurfa da na tagulla da baƙin ƙarfe da itace da dutse - gumakan da ba sa gani, ba su ji, ko su gane kome. Ba ka girmama Allah wanda ya ke riƙe da numfashinka a hannunsa ba, wanda kuma ya san dukkan hanyoyinka.24Saboda haka ne Allah ya aiko da hannun da ya yi wannan rubutun.25Wannan shi ne rubutun da aka yi: 'Mene, Mene, Tekel, da Pharsin.'26Wannan ita ce ma'anar: 'Mene,' 'Allah ya sa kwanakin mulkinka sun ƙare.'27'Tekel' 'an auna ka a ma'auni, aka tarar ka kasa.'28'Peres,' 'an raba mulkinka, an kuma ba Mediyawa da Fashiyawa.'"29Sai Belshazza ya ba da umarni, suka sawa Daniyel rigar shunayya. Aka sa masa sarkar zinariya a wuyansa, sarki kuma ya yi shela a kansa cewa yanzu shi ne mai iko na uku cikin masu mulkin ƙasar.30A wannan dare aka kashe Belshazza, sarkin Babila,31Dariyos Bamediye ya karɓi mulkin ya na da shekaru sittin da biyu.
Wannan dan Nebukadnezza ne da ya zama sarki bayan ubansa.
" domin 1,000"
"ya sha ruwan inabi a wurin"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"tasoshin zinariya ko na azurfa da Isra'ilawa suka yi"
Wadannan wasu kofika da sauran abubuwa ne wanda ƙanƙantar su kan bari mutum ya riƙe ya kuma sha wani abu daga cikin su
Wannan jimlar na amfani da sunan Nebukadnezza a matsayin sojojin Sarki. AT:"sojojin da ubansa Nebukadnezza ya dauka"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"tasoshin zinariya da sojojin Nebukadnezza suka dauko daga haikali"
"wajen haikalin Allah." Jimlar "ɗakin Allah" ya bayyana mana abubuwa da yawa game da haikalin.
"yayin da suka yi haka" ko "Nan take" (UDB)
Siminti ko laka da ake sawa a bango ko sili don bashi fuska mai kyau idan ya bushe
"fuskar sarki ta turɓune" (UDB). Wannan ya farune saboda razanar sa.
"ƙafafun sa"
Wannan sakamako ne na matsananciyar razanar sa
Wannan na nufin masu cewa suna iya magana da matattu, da masu dabo da bokaye, da masu duba da masana taurari.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:" Zan bawa Wanda duk ya bayyana wannan rubutu ya kuma faɗi ma'anarsa za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa"
Ba kasafai ake samun rigar shunayya ba kuma akan keɓe ta domin masu mulkin sarauta. AT:"ya sa rigar sarauta"
"Zama na uku a cikin masu mulki"
Wannan dan Nebukadnezza ne da ya zama sarki bayan ubansa.
"fuskarsa ta turɓune kwarai." Fuskar sarki ta turɓune fiye da a cikin 5:5
"Rikicewa"
A wasu sabbin juyin suna danganta wannan da uwar sarauniya, wato, ga uwar sarauniya. Akan girmama uwar sarauniya kwarai a zamanin mulkin Babila na da can.
Yadda ake kai gaisuwa ga sarki
"Ba bukatar ka bar tunaninka ya sami damuwa"
Sarauniya ta gasganta cewa ikon Daniyel na zuwa ne daga allolin karya da Nebukadnezza ke bautawa. Duba yadda aka fassara wannan jimlar a 4:7
"Lokacin da ubanka ke mulki"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:" yana da haske da fahimi da hikima da ganewa kamar na alloli a cikinsa"
" Ubanka sarki, Sarki Nebukadnezza"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"wannan Daniyel dai, wanda sarki ya lakaɓa wa suna Beltishazza, ke da duk wadannan ƙwarewa"
"abin da aka rubuta kan bango." Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:" abin da hannu ya rubuta a bango"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Sai aka kawo Daniyel a gaban sarki" ko "Sai sojojin suka kawo Daniyel gaban sarki"
A jimlar farko "ubana" na matsayin dukan sojojin. AT:" wanda sojojin Ubana suka kawo daga Yahuda"
Belshazza ya gasganta cewa ikon Daniyel na zuwa ne daga allolin karya da Belshazza ya bautawa. Duba yadda aka fassara wannan jimlar a 4:7
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:" kana da haske da ganewa da mafificiyar hikima"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Yanzun nan mutanen da aka san su da .... sun zo gabana"
"bayyana mani"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:" zan baka rigar shunayya, da kuma sarƙar zinariya a wuyanka"
Ba kasafai ake samun rigar shunayya ba kuma a kan keɓe ta domin ma'aikatan sarauta. AT:"ado irin na sarauta"
"mai karfin iko na uku" Duba:
"bana ra'ayin kyautar ka, don haka"
An yi amfani da kalmar "dukkan" a nuna girman yawa. AT:" mutane masu ɗinbin yawa, daga ƙasashe dabam-dabam da harsuna,"
A nan "al'ummai" da "harsuna" na nufin mutane daga ƙasashe dabam-dabam masu magana harsuna dabam-dabam. Duba yadda aka fasara wannan a 3:3. AT:"mutane daga kasashe dabam masu magana da harsuna dabam"
Wadannan kalmomi biyun na nufin kusan abu daya kuma suna bayyana girman razana. AT:"suna matukar tsoron sa"
Wannan jimlar ba tana nufin Nebukadnezza da kansa ke kashe mutane ba amma wadanda ya ba umarni. AT:" Nebukadnezza ya umarcin sojojin sa su kashe duk wanda ya so ya kashe"
"ya kan ɗaukaka waɗanda yake so ya ɗaukaka"
Wadannan kalmomin nada ma'ana ɗaya.
"ya kuma ƙasƙantar da waɗanda ya ke so ya ƙasƙantar"
A nan "zuciyarsa" na nufin sarki da kansa. AT:"zuciyar sarki ta kumbura"
A nan "ruhu" na nufin sarkin da kansa. an bayyana taurin kansa kamar ya kangare. AT:"ruhunsa kuma ya taurare"
gabagaɗi kwarai
A nan "kujerar mulki" na nufin ikon sa na sarauta. Za'a iya bayyana shi da gabagaɗi. AT:" mutane suka dauke mulkinsa"
Za'a iya bayyana shi da gabagaɗi. AT:" Mutanen suka kore shi daga wurin su"
A nan "hali" na nufin tunani. AT:" yana tunani kamar yadda dabba keyi"
danshin ƙasa da ake gani da safe
"duk wanda ya zaɓa"
Wannan dan Nebukadnezza ne da ya zama sarki bayan ubansa. duba yadda aka rubuta wannan sunan a cikin 5:1
A nan "zuciya" na nufin Belshazza da kansa. AT:" ba ka ƙasƙantar da kanka ba"
An bayyana tayaswa ga Allah kamar yin tsayayya da shi.AT:"Ka yiwa Allah tawaye"
Me da ina "gidan sa" za'a iya bayyana wa.AT:"Daga hakalin sa a Yerusalem"
A nan "numfashi" na nufin rayuwa "hannu" kuma na nufin iko ko mulki. AT:"Allah wanda ke baku numfashi" ko "Allahn da ke da iko kan dukan rayuwar ka"
"dukan abin da kake yi"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"an rubuta wannan saƙo"
Za'a iya bayyana wanna da gabaga di. AT:" Wannana sune rubutun da hannu ya rubutawa"
Wadannan sune Kalmomin yaren Armeniyawa da aka rubuta bango. Ka rubuta wadannan da sautin harshenka.
"'Mene,' na nufin 'Allah ya ƙididdige"
"Tekel' na nufin 'an auna ka a ma'aun"
Peres,' 'na nufin mulkinka''
Wannan kalma ce dake ɗayanta "Pharsin" a cikin 2:25
Yiwuwar mulkin sarki ma'auni ne na gwada ƙwarjinin sa. AT:"Allah ya auna yiwuwar ka na zama sarki sai aka iske baka cancanta ba"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Allah ya raba mulkinka, an kuma ba Mediyawa da Fashiyawa.'''
Wannan dan Nebukadnezza ne da ya zama sarki bayan ubansa. duba yadda aka rubuta wannan sunan a cikin 5:1
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Za'a sa masa sarkar zinariya a wuyansa"
"mai iko na uku cikin masu mulkin ƙasar"
"ya zama mai mulki"
tsawon shekaru biyu-"lokacin da ya kai wajen shekaru 62"
1Ya gamshi Dariyos ya naɗa dagatai 120 a masarautar domin su yi mulkin dukkan masarautar.2Sama da su kuma ya naɗa manyan hakimai uku, Daniyel kuma na ɗaya daga cikin su. Waɗannan manyan hakimai an zaɓe su ne domin su riƙa duba ayyukan dagatan, domin kada sarki ya yi asara.3Daniyel ya yi fice daga cikin manyan hakiman da kuma dagatan saboda yana da nagartaccen ruhu. Sarki yana shirin ya sanya shi bisa dukkan masarautar.4Sai manyan hakiman da dagatan suka duba domin su sami kuskure a cikin aikin da Daniyel ya ke yiwa masarautar, amma ba su sami wata rashawa ko kasawa ba saboda shi mai aminci ne. Ba a sami wani kuskure ko watsi da aiki a cikinsa ba.5Sai waɗannan mutane suka ce, "Bamu sami wani dalilin da zamu yi ƙarar wannan Daniyel ɗin ba sai dai ko mu sami wa ni abin tsayayya da shi game da shari'ar Allahnsa."6Daga nan waɗannan hakimai da Dagatai suka kawo wani shiri a gaban sarki. Suka ce da shi, "Sarki Dariyos, ranka ya daɗe!7Dukkan manyan hakiman masarautar, da dagatan gudumomi, da dagatan lardi, da mashawarta, da gwamnoni sun yi shawara a tsakaninsu sun ɗauki mataki cewa kai, sarki, ka fito da doka kuma ka tilastata, yadda duk wanda ya yi wani roƙo ga wa ni allah ko mutum cikin kwana talatin, sai dai gare ka kaɗai, sarki, wannan mutum tilas a jefa shi cikin ramin zakuna.8Yanzu dai, sarki, ka fito da doka ka kuma sanya hannu a takardar yadda ba za a iya canza ta ba, kamar yadda aka umarta bisa ga shari'un Medeyawa da Fashiyawa, domin baza a iya sauya ta ba."9Sai sarki Dariyos ya sa hannu a takardar ya maida dokar ta zama shari'a.10Da Daniyel ya fahimci cewa an sanya hannu a takardar ta zama shari'a, sai ya tafi cikin gidansa (tagoginsa dai a buɗe suke a ɗakinsa na saman bene suna fuskantar Yerusalem), sai ya durƙusa bisa gwiwoyinsa, yadda ya saba sau uku a rana, ya yi addu'a ya kuma bada godiya a gaban Allahnsa, yadda ya ke yi a dã.11Daga nan waɗannan mutane waɗanda suka shirya makircin tare suka ga Daniyel yana yin roƙe-roƙe da neman taimako wurin Allah.12Sai suka zo wurin sarki suka yi masa magana game da dokarsa: Ashe ba ka kafa doka ba cewa duk wanda ya yi roƙo ga wani allah ko mutum a cikin kwanaki talatin, in ba gare ka kaɗai ba, ya sarki, tilas a jefa shi cikin ramin zakuna?" Sarkin ya amsa, "Al'amarin zaunannne ne, kamar yadda aka umarta bisa ga shari'ar Medeyawa da Fashiyawa; baza a iya sokewa ba."13Sai suka amsa wa sarki, "Wannan Daniyel ɗin, wanda ke ɗaya daga cikin 'yan bauta da daga Yahuda, bai kula da kai ba, sarki, ko dokar da ka sa hannu. Yana addu'a ga Allahnsa sau uku a rana."14Da sarkin ya ji haka, sai hankalinsa ya tashi sosai, sai ya ƙudura a ransa ya ceci Daniyel daga wannan hukunci. Ya yi ƙoƙari har zuwa faɗuwar rana ya ga ya ceci Daniyel.15Sai waɗannan mutane waɗanda suka shirya makircin suka tattaru tare da sarki suka ce masa, "Ka sani, sarki, cewa shari'a ce ta Medeyawa da Fashiyawa, cewa babu wata doka ko umarni da sarki ya fito da shi da za a iya canzawa."16Daga nan sarkin ya bada umarni, sai aka kawo Daniyel, aka kuma jefa shi cikin ramin zakunan. Sarkin ya cewa Daniyel, "Bari Allahnka, wanda ka ke bautawa babu fasawa, ya kuɓutar da kai."17Aka kawo dutse aka rufe ramin, sai sarkin ya hatimce shi da zobensa na sanya hannu da kuma zobunan sanya hannun 'yan, majalisarsa yadda babu wani abin da za a canza game da Daniyel.18Daga nan sarki ya koma fãdarsa ya yi azumi tsawon dare. Babu wani abin annashuwa da aka kawo a gabansa, barci kuma ya guje daga gare shi.19Da gari ya waye sarkin ya tashi da sauri ya tafi ramin zakunan.20Da ya matso kusa da ramin, ya yi kira ga Daniyel da muryar baƙinciki, "Daniyel, bawan Allah mai rai, ko Allahnka, wanda ka ke bautawa babu fasawa, ya iya cetonka daga zakunan?"21Daga nan Daniyel ya ce da sarki, "Ran sarki, ya daɗe!22Allahna ya aiko da manzonsa ya rufe bakunan zakunan, ba su kuma cutar da ni ba. Gama an same ni marar laifi a gabansa da kuma gabanka, sarki, ban kuma cutar da kai ba."23Daga nan sarki ya yi murna ƙwarai. Ya bada umarni a fito da Daniyel daga ramin. Sai aka ciro Daniyel daga ramin. Babu wani abin cutarwa da ya same shi, saboda ya dogara ga Allahnsa.24Sarkin ya bada umarni, sai aka kawo mutanen nan da suka zargi Daniyel aka kuma jefa su cikin ramin zakunan - dukka, da 'ya'yansu, da kuma matansu. Kafin su kai ƙasa, zakunan suka sha ƙarfinsu suka kakkarya ƙasusuwansu suka yi ragargaza su.25Sai Sarki Dariyos ya rubuta zuwa ga dukkan mutane, da al'ummai da kuma harsuna da ke zaune a cikin dukkan duniya: "Bari salama ta ƙaru gare ku.26Yanzu na kafa doka a dukkan mulkin masarautata mutane su yi rawar jiki su kuma ji tsoro a gaban Allahn Daniyel, gama shi ne Allah mai rai kuma ya dawwama har abada, sarautarsa kuwa ba za a rushe ba; mulkinsa kuwa za ya kasance har ƙarshe.27Yana kiyaye mu yana kuɓutar da mu, yana yin alamu da al'ajibai a sama da kuma duniya; Ya kiyaye Daniyel daga ƙarfin zakuna."28Daniyel kuwa ya wadata a zamanin mulkin Dariyos da mulkin Sairus bafashiye.
Abubuwan da suka faru a wannan babin sun kasance ne bayan yan fasiya sun mamaye Babiloniyawa lokacin Dariyus na Mede ya fara mulkin Babila
"sarki Dariyus ya yanke"
"dagatai ɗari da ashirin"
Kalmar "su" na nufin dagatai 120
"don kada a saci kayan sarki" ko "don kada wani ya zalunci sarki"
"ya fi duka" ko "ya fi kowa cancanta"
A nan "ruhu" na nufin Daniyel. Yana nuna tasirin sa. AT:"shi dabam yake"
"wanda babu kamar sa"
"a bashi iko akan" ko "a bashi damar kula da"
Sauran ma'aikatan suna kishin Daniyel. Za'a iya fifita wannan. AT:"sai sauran mayan maikatan da dagatan suka fara kishi. Saboda haka suka yita neman Daniyel da sheri a kowanne aikin da yake yi"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:" Ba a sami wani kuskure ko watsi da aiki a cikinsa ba"
kaucewa aiki
"yin korafi kan Daniyel"
"suka kawo wani shiri a gaban sarki"
Wannan hanya ce da aka saba miƙa gaisuwa
" har kwana 30"
"wanda ya kawo roƙo"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"sojojin ka zasu jifa wannan mutum cikin ramin zakoki"
A aya ta 8, shugabannin suka ci gaba da magana ga sarki
" bisa ga doka"
"ba za'a iya sauyawa ba"
"maishe da umarnin ya zama doka"
Yana da kyau labarin ya nuna cewa Daniyel ya fahimci sabuwar dokar kafin yayi addu'a ga Allah.
Wannan bayanin ne matashiyar sanin dalilin da abokan gabar Daniyel suka fahimci yana addu'a ga Allah. (Duba: writiing_background)
"miƙa godiya ga Allahnsa"
shiri na mugunta
Sun yi wannan tambaya ne don su tabbatar cewa sarki ya bada umarnin
"wanda ya gabatar da bukata"
Wannan zai iya zama ɗaki ko rami in ake ajiye zakuna. Dubi yadda aka fassara a cikin 6:6
"bisa ga doka"
Wannan ba haya ce ta bayyana Daniyel da bangirma ba. Sun yi haka ne da gangan don su kaucewa ba Daniyel martabar sa a matsayin shugaba.
"wanda ya yi hijira daga Yahuda"
Wannan habaicin na nuna bai kula da sarki ba. AT:"bai bi umarnin ka ba"
A nan "ra'ayi" na nufin tunaninsa. AT:"yana tunani matuƙa a kan yaya"
Wannan na nufin amfani da hankali, ba aiki na zahiri ba.
Za'a iya ƙara wani abu don ƙarin fahimta. AT:"na umarni...da za'a canza. Sai sun jefa Daniyel cikin kogon zakuna"
"sojojin sa suka je suka samo Daniyel"
Wannan zai iya zama ɗaki ko rami in ake ajiye zakuna. Dubi yadda aka fassara a cikin 6:6
Sarkin na nuna fatan sa na Allah ya ceci Daniyel
"cece ka daga zakoki"
Wannan zai iya zama ɗaki ko rami in ake ajiye zakuna. Dubi yadda aka fassara a cikin 6:6
Amfanin hatimin zoɓen sa a fili yake. Sarki da masu mulki kan danna zoɓen su cikin tawadar hatimi. AT:"Sarki ya danna zoɓen sa cikin tawada, shugabanni kan yi haka suma. Ba wanda ake tsammanin zai karya hatimin don ceton Daniyel"
"ba mai taimakon Daniyel"
Wannan hali ya nuna yadda sarki ya damu da Daniyel.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaiɗi. AT:"babu wanda zai nishaɗantar da shi"
An yi maganar barci kamar zai iya gudu daga wurin sarki. AT:"bai iya yin barci ba tsawon dukan daren"
Wannan zai iya zama ɗaki ko rami in ake ajiye zakuna. Dubi yadda aka fassara a cikin 6:6
Za'a iya bayyana wannan da gabagaiɗi. AT:"ya san bai yi laifin komai ba"
"ban kuma cutar da kai ba"
Wannan zai iya zama ɗaki ko rami in ake ajiye zakuna. Dubi yadda aka fassara a cikin 6:6
Za'a iya bayyana wannan da gabagaiɗi. AT:"ba su sami ko dan rauni tare da Daniyel ba"
Wannan zai iya zama ɗaki ko rami in ake ajiye zakuna. Dubi yadda aka fassara a cikin 6:6
Kafin su kai ƙasan ramin zakunan
"ragargaza ƙasusuwan su" (UDB)
A nan "al'ummai" da "harsuna" na nufin mutane daga kasashe dabam-dabam masu magana da harsuna dabam-dabam. Duba yadda aka fassara a 3:3. AT:"al'ummai daga ƙasashe dabam-dabam masu magana da harsuna dabam-dabam"
Sarki Dariyus ya rubuto saƙon sa ga dukan kasar sa wadda ke da girma. Ga abin da ta kunsa "dukan al'umma" don a nuna yadda girman yake, duk da cewa bai kunshi kowa a duniya ba. AT:"a mulkin sa"
Wannan hanya ce da ake gaisuwa da nuna fatan alheri a kowanne fannin rayuwa ga wani
Wannan ya ci gaba da bayyana sakon da Dariyus ya aika ga masarautar sa
Wadannan kalmomi biyu na nufin abu daya za kuma a iya haɗa su. AT:"rawar jiki da tsoro"
"Allahn da Daniyel ke wa sujada" (UDB)
Kalmomi biyun " Allah Mai Rai" da "dawwama" na bayyana abu ɗaya, Allah madawwami ne.
kalmomi biyun sun yi hannun riga , suna nuna yadda mulkin Allah zai dawwama. "
Za'a iya bayyana wannan da gabagaiɗi. AT:" babu mai iya rusa sarautarsa" ko "sarautarsa zata dawwama"
"zai yi mulki har abada"
"bai bar ƙarfafan zakunan nan su cutar da Daniyel ba"
Sairus bafashiye ne sarkin da yayi mulki bayan Dariyos
1A shekara ta farko ta Belshazza sarkin Babila, Daniyel ya yi mafarki da wahayoyi a ransa da ya ke kwance bisa gadonsa. Sai ya rubuta abin da ya gani a mafarkin. Ya rubuta al'amura mafi muhimmanci:2Daniyel ya bayyana cewa, "A cikin wahayina na dare sai na ga iskokin sama huɗu suna motsa babban teku.3Manyan dabbobi huɗu, kowanne ya sha daban da ɗayan, suka fito daga cikin tekun.4Ɗayan ya yi kama da zaki amma yana da fukafukai kamar gaggafa. lokacin da nake kallo, sai aka yage fukafukansa aka kuma ɗaga shi sama aka sa ya tsaya bisa ƙafafu biyu, kamar mutum.5Daga nan akwai dabba ta biyu, kamar damisa, a sunkuye kuma; tana da haƙarƙari uku a tsakiyar haƙoranta a cikin bakinta. Aka ce mata, 'Tashi ki lanƙwame mutane da yawa.'6Bayan wannan na sake dubawa. Akwai wata dabbar kuma, kamanninta kamar damisa. Bisa bayanta tana da fukafukai huɗu kamar fukafukan tsuntsu, tana kuma da kawuna huɗu. Aka ba ta ikon yin mulki.7Bayan wannan kuma na gani a wahayina na dare dabba ta huɗu, mai ban razana, da ban tsoro, kuma mai ƙarfi ƙwarai. Tana da babban haƙorin ƙarfe; tana haɗiyewa, tana karyawa rugu-rugu, tana kuma tattake abin da ya rage da ƙafafunta. Ta bambanta da sauran dabbobin, kuma tana da ƙahonni goma.8Yayin da nake yin la'akari da ƙahonnin, dana duba sai naga wani ƙaho ya fito daga cikinsu, ƙaramin ƙaho. Uku daga cikin ƙahonnin aka daga jijiyoyinsu. A wannan ƙaho na ga idanu kamar idanun mutum da kuma bakin da ke fahariya game da manyan abubuwa.9Da na duba, sai na ga an shirya kursiyoyi a waje ɗaya, sai Mai dogon zamani ya zauna. Suturarsa fari fat kamar ƙanƙara, gashin kansa kuwa kamar farin ulu. Kursiyinsa harsunan wuta ne, gargarensu kuwa suna ci da wuta.10Ƙoramar wuta na fitowa daga gabansa; miliyoyi na bauta masa, miliyan ɗari kuma na tsaye a gabansa. Ana zaman kotu, aka kuma buɗe litattafai.11Na ci gaba da dubawa saboda maganganun fankama da ƙahon ke furtawa. Ina kallo lokacin da aka kashe dabbar, aka lalatar da jikinta, aka kuma miƙa ta domin a ƙone ta.12Sauran dabbobin huɗu kuwa, ikonsu na yin mulki aka ɗauke shi, amma aka ƙarawa rayukansu tsawon kwanaki na wani lokaci.13A cikin wahayoyina na daren nan, sai na ga wani na zuwa da gizagizan sama kamar ɗan mutum; ya zo wurin Mai dogon zamani ya gabatar da kansa a gabansa.14Ikon yin mulki da ɗaukaka da ikon sarauta aka bayar a gare shi yadda dukkan mutane, da al'ummai, da harsuna zasu bauta masa. Ikonsa na mulki madawwamin iko ne da ba zai shuɗe ba, masarautarsa kuwa ba za a taɓa iya rusawa ba.15Ni kuwa, Daniyel, ruhuna ya damu a cikina, wahayoyin da na gani kuwa a cikin raina suka dame ni.16Sai na kusanci ɗaya daga cikin waɗanda ke tsaye a wurin na kuma tambaye shi ya nuna mani ma'anar waɗannan abubuwa.17Waɗannan manyan dabbobin, guda huɗu, sarakuna huɗu ne da zasu taso a duniya.18Amma tsarkakan mutanen Mafi Girma zasu karɓi masarautar, zasu kuma mallake ta har abada abadin.'19Sai kuma na so in ƙara sani game da dabbar nan ta huɗu - ta bambanta sosai da sauran kuma tana da ban razana da haƙoranta na ƙarfe da kofatun tagulla; tana cinyewa, tana karyawa rugu-rugu, ta kuma tattake abin da ya rage da ƙafafunta.20Na so in sami sani game da ƙahonnin goma da ke a kanta, game kuma da ƙahon ɗaya da ya tsiro, wanda kuma a gabansa ƙahonni uku suka faɗi. Na so in sami sani game da ƙahon da ke da idanu da kuma game da bakin da ke fahariyar manyan abubuwa wanda kuma ya ke ganin kamar ya fi abokan tarayyarsa girma.21Lokacin da nake kallo, sai wannan ƙaho ya yaƙi tsarkakan mutane yana kuma kayar da su22har sai da Mai dogon zamani ya zo, an kuma bayar da hukunci ga tsarkakan mutane na Mafi Girma. Daga nan lokaci ya zo inda tsarkakan mutanen suka karɓi sarautar.23Wannan ne abin da mutumin nan ya faɗa, 'Dabbar nan ta huɗu kuwa, zata kasance masarauta ta huɗu a duniya wadda zata sha bamban da dukkan sauran masarautun. Za ta cinye dukkan duniya, ta tattake ta ta kuma karya ta rugu-rugu.24Ƙahonnin goma kuwa, daga cikin wannan masarauta sarakuna goma ne za su taso, wani kuma zai taso bayan su. Zai sha bamban da waɗanda suka wuce, zai kuma yi nasara da sarakunan uku.25Zai furta maganganun tsayayya da Mafi Girma zai kuma tsananta wa tsarkaka mutanen Allah Mafi Girma. Zai yi ƙoƙarin canza shagulgula da kuma shari'a. Za a bayar da waɗannan abubuwa cikin hannunsa har shekara ɗaya, shekaru biyu, da kuma rabin shekaru.26Amma zaman kotu zai ci gaba, za a kuma ɗauke ikon sarautarsa domin a gama da shi a kuma lalatar da shi a ƙarshe.27Masarautar da mulkin, da kuma girman masarautun da ke ƙarƙashin dukkan sama, za a bayar ga mutane waɗanda ke tsarkakan mutanen Mafi Girma. Masarautarsa madawwamiyar masarauta ce, dukkan sauran masarautu kuma za su bauta masa su kuma yi masa biyayya.'28Ga ƙarshen al'amarin. Ni kuwa, Daniyel, tunane-tunanena sun motsa ni sosai fuskata kuwa ta canza kamanni. Amma na ajiye waɗannan abubuwa a gare ni."
Sura 7 da 8 ba a jere suke ba. Sun faru ne tun lokacin da Belshazza ke sarauta, kafin mulkin Dariyos da Sairus da akayi maganar su a sura 6
A cikin wahayin Daniyel, ya ga dabbobin dake ma'anar wasu batutuwa. Can gaba cikin wahayin wani yayi masa bayanin wadannan abubuwan. (Duba: writting_symlanguage)
Wannan sunan dan sarki Nebukadnezza ne, wanda ya gaje shi. Dubi yadda aka rubuta sunan a 5:1
Kalmomin "mafarki" da "wahayi" na nufin mafarkin da aka bayyana a wannan sura. AT:"wahayi lokacin da yake mafarki"
"iska daga ko'ina" or "gagarumar iska daga kowacce kusurwa" (UDB)
"juyawa sama" ko "tirniƙewa" ko "tada iska sama"
Wannan wata halitta ce dabbam ba kamar dabbobin da ke rayuwa ba. (Duba: writings_symlanguage|symbolic_Langauge)
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"wani ya yage fukafukansa aka kuma ɗaga shi sama aka sa ya tsaya bisa ƙafafu biyu, kamar mutum" (Duba:|Active_or_Passive)
A nan "zuciyar" na nufin tunani. Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"wani ya bata damar yin tunani kamar mutum" (Duba: da|Active_or_passive)
Wannan ba ainihin damisa bane, amma dabbace da ke kama da damisa. (Duba:|symbolic_Language)
Manyan ƙasusuwan ƙirji da suka haɗe da ƙashin baya
"wani ya faɗa" (Duba:|active_or_passive)
Wannan ba ainihin damisa bane, amma dabbace da ke kama da damisa.
fukafukai huɗu da kawuna huɗu alamu ne, amma ma'anar a duhu take.
"dabbar tana da kai hudu"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"wani ya bata yancin mulki"
wannan ma ba dabba ce a zahiri ba. wata irin halitta ce.
"tafiya kai da gurjewa"
Daniyel ya ci gaba da bayyana wahayin sa na dabbar nan ta huɗu da ya gani a 7:6
Masu fasara zasu iya rubuta wannan kamar haka: "ƙahonni alama ce ta karfi yana kuma nuna karfin shugabanni." Duba:
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"karamin ƙahon ya yayyaga uku daga cikin ƙahonnin farko"
A nan ƙaho na kirari, ta wurin yin amfani da bakin sa. AT:"ƙahon nada baki yana kuma fariya game da yin manyan abubuwa"
Yawancin abin da ke aya 9-14 yare ne mai hannun riga amma ma'anar su ɗaya. Saboda wannan dalili ne, Littafi Mai Tsarki juyin ULB da UDB suka yi su da tsarin waƙa.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"wani ya shirya kursiyoyi a wuri ɗaya"
Wannan sunan na Allah da ke ma'anar yana rayuwa dukan zamanai. AT:" Wanda ke rayuwa har abada" ko "wanda ke rayuwa koyaushe"
Wurin ya bayyana Allah kamar wanda ya zauna, da sutura da suma kamar mutum. Wannan ba yana nufin Allah kamar mu yake, amma yadda Daniyel ya ga Allah a wahayin ne.
Wannan habaici ne da ke nufin ya zauna. AT:" ya zauna a kan kursiya"
An kwatanta tufar sa da dusar kankara don a nuna fara ce sosai. AT:"tufafin sa fari fat ne"
An kwatanta sumar Allah kamar farin ulu. Ma'anonin zasu iya zama 1) tana da fari ƙwarai
"tsabtataccen ulu" ko ulun da aka wanke"
wannan na nuna kursiyin Allah da gargaren sa kamar an yi su da wuta. Kalmar"wuta" da "wuta maici" na ma'anar kusan abu ɗaya za kuma a iya fasara su ta hanya ɗaya.
Ba a fayyace dalilin da yasa aka danganta mulkin Allah da cewa yana da gargare. A zahiri kursiyi bashi da gargare, amma nassin ya nuna a fili cewa wannan kursiyin yana da wadansu gargare. A yi amfani da wata kalma domin "gargare" idan zai yiwu.
Daniyel ya ci gaba da bayyana wahayin sa na kursiyin sama tare da martanin dabbar na ta huɗu da ya gani ciki 7:6
Yawancin abin da ke aya 9-14 yare ne mai hannun riga amma ma'anar su ɗaya. Saboda wannan dalili ne, Littafi Mai Tsarki juyin ULB da UDB suka gabatar da su da tsarin waƙa.
Hanya mafi sauri da wuta ke saukowa da ga wurin Allah an bayyana shi kamar yadda ruwa ke ganagarawa a rafi. AT:"Ƙoramar wuta na fitowa daga gabansa kamar ruwa a rafi" UDB)
Kalmar"gabansa" na nufin Allah, mai Mulkin Zamanai daga 7:9
Wataƙila wannan na nufin masu ya maimakon kima. AT:"dubun dubbai" ko "mutane masu ɗunbin yawa"
Wataƙila wannan na nufin masu ya maimakon kima. AT:"goman dubbai sau goman dubbai" ko "mutanen da basu ƙirguwa"
Wannan na nufin Allah, mai shari'ar, na shirye ya binciki shaidun don yin hukunci.AT:" Mai shari'ar ya shirya don yin shari'a" ko "Mai shari'ar ya zauna"
Wadannan littattafai ne da ke kunshe da shedun da za'a yi amfani da su a kotu. AT:"sai aka buɗe littattafan shaidu"
Daniyel ya ci gaba da bayyana wahayin sa na kursiyin sama tare da martanin dabbar na ta huɗu da ya gani ciki 7:6
Za'a iya baiyana wannan da gabagaɗi. AT:"sai suka kashe dabbar nan ta huɗu, aka lalatar da jikinta, aka kuma miƙa ta domin a ƙone ta"
an kashe dabbar ne saboda mai shari'ar ya sameta da laifi. AT:"sun hukunta dabbar" ko "mai shari'ar ya bada umarni sai suka kashe dabbar"
Wannan na nufin dabbar nan ta huɗu dake da ƙahonni goma da kuma ƙahon da ke fahariya. AT:"dabba mai matuƙar razanarwa" ko "dabbar da ke dauke da ƙahon fahariya"
Zai iya zama a fayyace a ce "sauran dabbobi ukun"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"mai shari'ar ya karɓe ikon su na mulki" ko "ikon su na yin mulki ya ƙare"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"sun ci gaba da rayuwa har na wani lokaci" ko "mai shari'ar ya bar su da rai har na wani dan lokaci"
Yawancin abin da ke aya 9-14 yare ne mai hannun riga amma ma'anar su ɗaya. Saboda wannan dalili ne, Littafi Mai Tsarki juyin ULB da UDB suka yi su da tsarin waƙa.
Mutumin da Daniyel ya gani ba mutum bane a zahiri, amma yana da kamannin mutum. "A daren nan kuma na ga wani na zuwa kamar dan mutum, wato, yana da kamannin mutum"
"da gizagizan sararin sama"
Wannan na nufin Allah da zai dawwama. Duba yadda aka fassara wannan kan maganar a 7:9
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"suka gabatar da wannan ɗan mutum din ga Mai Dogon Zamanai" ko "ya tsaya gabansa"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Shi wanda ke kama da ɗan mutum ya karɓi ikon mulki, daukaka, ikon sarauta"
A nan ana nufin iko
A nan "al'ummai" da "harsuna"na nufin mutae dabam-dabam masu magana da harshe dabam-dabam. Duba yadda aka fassara wannan a 3:3. AT:"mutane daga al'ummai dabam-dabam masu magana da harsuna dabam-dabam"
Wadannan jimloli biyu na nufin abu ɗaya.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"yadda ba wanda zai taɓa iya rusawa ba"
Jimloli biyun nan sun nuna yadda Daniel ke ji. Na biyun yafi bada cikakken bayani game da na farkon, yana bayyana ɗacin zuciyarsa.
A nan "ruhuna" na nufin Daniyel da kansa. AT:"na damu sosai a cikin raina"
Wannan ɗaya daga cikin talikan da ke tsaye a gaban kursiyin Allah (UDB). Ma'anonin kan zama 1) Wadannan mala'iku ne, ruhohin da ke bautawa Allah 2) wadannan mutanene wanda suka mutu yanzu suke cikin sama.
"ya sheda mini" (UDB) ko "ya bayyana mini"
"abubuwan da na gani"
"Waɗannan manyan dabbobin huɗun"
"na wakiltar sarakuna huɗu"
A nan "taso a duniya" na nufin su mutane ne a zahiri.AT:" sarakuna huɗu wanda za su yi mulki a duniya"
"zasu mulke ta"
Wannan tabbacin na nuni cewa mulkin ba zai taɓa zuwa karshe ba.
"mai tsoratarwa"
"a tattake da murje"
"ƙahonnin goma da ke a kan dabba ta hudun"
"ya tsiro, da kuma game da ƙahonna ukun da suka faɗi a gaban sa" ko "ya tsiro, kuma game da ƙaho ukun da suka faɗi saboda shi"
A nan "faduwa" kalmace da ke nuna an lalata su. AT:"wanda ya lalata ƙahonni ukun"
"bakin ta ke fahariyar" ko "bakin sabon ƙahon, dake fahariya"
kahon mai idanu da baki ya zama kamar ya fi sauran
"wannan ƙaho na huɗu."wannan na nufin ƙahon da akayi bayani a 7:19
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"har sai Mai dogon zamani ya zo, ya bayar da hukunci"
Wannan yana nuna Allah madawwami ne. Duba yadda aka fasara wannan a 7:9
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"Allah ya bada mulkin sa ga tsarkakan sa"
Yawancin rubutun aya 23-27 an yi shi ne da harshe mai fayyace wa. Saboda wannan dalilin, juyin ULB ya bada su da tsarin waƙa.
Wannan ne mutumin da Daniyel ya tunkara a 7:15
"mutumin ya amsa"
"game da dabbar nan ta huɗu kuwa...game da Ƙahonnin goma kuwa" ko "yanzu, game da dabbar nan ta huɗu kuwa...yanzu, game da Ƙahonnin goma kuwa"
Ba wannan na nufin mulki na hudun zai lalata duniya ba, amma zai kai mata mummunan hari, mamaya, da lalata dukan sauran mulki a doran ƙasa.
za suyi mulki ɗaya bayan ɗaya. Za'a iya cewa. AT:"sarakuna goma zasu yi mulki a wannan mulki na huɗun, ɗaya bayan ɗaya" Duba:
Wannan ba cikin goman yake ba. Zai fi dacewa idan mun kira shi a matsayin "sarki na sha ɗaya." AT:"bayan nan sarki na sha ɗaya zai zama da iko"
"Zai sha bamban da sauran sarakuna goman"
zai kuma yi nasara da sarakunan uku daga cikin goman. Zai zama da armashi in mun ce sarakuna ukun na matsayin ƙahonni ukun da aka tunɓuke ne. AT:"zai yi nasara da sarakunan uku da ke matsayin ƙahonni ukun da aka tumɓuke" (UDB)
Mutumin da ke cikin wahayin Daniyel ya ci gaba da magana ga Daniyel
Yawancin bayanin da ke aya 23-27 yare ne mai bayyana wani abu. Saboda wannan dalili ne, Littafi Mai Tsarki juyin ULB da UDB suka yi su da tsarin waƙa.
Wannan na nuna sabon sarkin zai yi jayayya a fili tare da furta baƙaƙen maganganu a kan Mafi Girma.
Kalmar "Shi" da "sa" na nufin sabon sarkin, ba madaukaki ba
"tsarkakan Allah"
Dukan kalmomin na nufin dokar Musa. Shagulgula wani sashi ne mai amfani na addinin a Isra'ila a cikin Tsohon Alkawali.
A nan "hannunsa" na nufin ikon sa. Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Sabon sarkin zai kula da shagulgulan addini da shari'a"
Wannan na nufin "shekaru uku da rãbi" (UDB). Wannan ba hanyar da Isra'ilawa suka saba ƙidaya ba. Ka ƙokarta fassara wannan tare da adana wannan hanyar ƙirga. AT:"shekara ɗaya a tara da shekara biyu a tara da wata shida"
Wannan na nufin mai shari'ar na a shirye ya binciki shedu ya kuma zartas da hukunci. AT."mai shari'ar zai shara'anta" ko "mai shariar zai zauna"
"sauran yan kotun zasu ɗauke ikon sarautar daga sabon sarkin"
Wannan, anan, na nufin "iko". Duba yadda aka fassara wannan a 7:13
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"kuma a gama da lalatar da shi a karshe" ko "kuma a lalatar da ikon mulkin sa a karshe"
Mutumin da ke cikin wahayin Daniyel ya ci gaba da magana ga Daniyel
Yawancin bayanin da ke aya 23-27 yare ne mai bayyana wani abu. Saboda wannan dalili ne, Littafi Mai Tsarki juyin ULB da UDB suka yi su da tsarin waƙa.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"Allah zai bayar ga mutane mulkin da girman masarautar...ga mutane"
Wadannan kalmomin yawanci na nufin abu ɗaya kuma suna fifita cewa wannan zai shafi kowanne irin iko.
Mafayyacin suna "girman" za'a iya fassara shi da "girma". AT:"duk wani abu da ke da girma game da mulkin"
habaicin "doron ƙasa" na nufin dukan mulkokin cikin duniya"
"Mulkin Allah Maɗaukaki"
"mulkin da zai dawwama har abada" ko "mulkin da bazai ƙare ba"
Wannan na nufin ya gama bayyana wahayin. AT:"Wannan shine karshen bayanin abin da na gani a wahayin"
"fuskata tayi fari"
1A cikin shekara ta uku ta mulkin Sarki Belshazza, Ni, Daniyel, wahayi ya bayyana a gare ni (baya ga wanda ya bayyana a gare ni da farko).2A cikin wahayin na gani, yayin da nake dubawa, cewa ina cikin fãdar Susa a gundumar Ilam. Na gani a wahayi cewa ina bakin Rafin Ulai Kanal.3Na duba sama sai na ga rago a gabana mai ƙahonni biyu, yana tsaye bakin rafin. Ƙaho ɗaya ya fi ɗaya tsawo, amma wanda ya fi tsawon girmansa a hankali ne fiye da gajeren har ya zo ya zarce shi a tsawo.4Sai na ga ragon na bankawa yamma, daga nan arewa, daga nan kuma kudu; babu wata dabbar da ke iya tsayawa a gabansa. Babu waninsu da ke iya kuɓuto da wani daga hannunsa. Yana yin abin da ya ga dama, ya kuma zama babba.5Yayin da nake tunani game da wannan, sai na ga bunsuru ya fito daga yamma, wanda ya tafi cikin sararin dukkan duniya, yana gudu da sauri, ya yi kamar baya taɓa ƙasa. Bunsurun yana da babban ƙaho a tsakanin idanunsa.6Ya zo wurin ragon mai ƙahonni biyu - naga ragon yana tsayawa a bakin rafin - bunsurun kuwa ya ruga wurin ragon cikin matsanancin fushi.7Na ga bunsurun ya zo kusa da ragon. Yana cikin fushi sosai da ragon, sai kuma ya tunkuyi ragon ya ɓalle masa ƙahonnin biyu. Ragon kuwa bai da ƙarfin tsayawa a gabansa. Bunsurun ya fyaɗa shi ƙasa ya take shi. Babu wani da ke iya kuɓuto da ragon daga ikonsa.8Sai bunsurun ya zama mai girma sosai. Amma da ya zama mai ƙarfi, sai babban ƙahon ya ɓalle, a gurbinsa kuwa ƙahonni manya huɗu suka fito suka fuskanci kusurwoyin iskoki huɗu na sammai.9Daga kan ɗaya daga cikin su wani ƙahon ya tsiro, da farko dai ƙarami ne, amma ya zama babba sosai a kudu, a gabas, a kuma ƙasa mai kyau.10Ya yi girma sosai har ya shiga yaƙi da mayaƙan sama. Waɗansu daga cikin mayaƙan da waɗansu daga cikin taurarin aka watso su ƙasa cikin duniya, ya kuma tattake su.11Ya maida kansa ya zama da girma kamar shugaban mayaƙan. Ya ɗauke baiko na ƙonawa da aka saba yi, wurin haikalinsa kuma aka gurɓata shi.12Saboda tawaye za a miƙa mayaƙan ga ƙahon bunsurun, kuma za a tsai da baikon ƙonawa. Ƙahon zai watsar da gaskiya ƙasa, zai kuma yi nasara cikin dukkan abin da ya yi.13Sai na ji wani mai tsarki na magana wani kuma mai tsarkin na amsa masa, "Har yaushe waɗannan abubuwa za su kasance, wannan wahayin game da baikon ƙonawa, zunubin da ya kawo rusarwa, miƙawar haikalin, da kuma tattakawar mayaƙan sama?"14Ya ce mani, "Za su kasance har yamma-yamma da safiya-safiya 2,300. Bayan wannan za a maido da haikalin dai-dai."15Lokacin da ni, Daniyel, na ga wahayin, na yi ƙoƙari in fahimce shi. Sai ga wani ya tsaya a gabana mai kamannin mutum.16Sai na ji muryar mutum na kira daga tsakiyar bakin Rafin Ulai. Ya ce, "Jibra'il, ka taimaki mutumin nan ya fahimci wahayin."17Sai ya zo kusa da inda na tsaya. Da ya zo, sai na tsorata na rusuna ƙasa. Ya ce mani, "Ka fahimta, ɗan mutum, wahayin domin lokacin ƙarshe ne."18Da ya yi mani magana, sai na faɗa cikin barci mai nauyi da fuskata a ƙasa. Daga nan ya taɓa ni ya sa na miƙe a tsaye.19Ya ce, "Duba, zan nuna maka abin da zai faru daga bisani a lokacin hasala, saboda wahayin ya shafi zaɓaɓɓen lokacin ƙarshe.20Game da ragon da ka gani, wanda ke da ƙahonni biyu - sune sarakunan Mediya da Fashiya.21Bunsurun shi ne sarkin Girka. Babban ƙahon tsakanin idanunsa shi ne sarkin farko.22Game da ƙahon da ya ɓalle kuwa, wanda a gurabunsa huɗu kuma suka taso - masarautai huɗu ne za su taso daga al'ummarsa, amma bada babban ikonsa ba.23A ƙarshen lokacin waɗannan masarautai, lokacin da masu kurakurai suka ƙure iyakarsu, wani sarki marar sakin fuska, mai basira sosai, zai taso.24Ikonsa zai zama babba - amma ba da ikonsa ba. Zai zama da ban mamaki cikin abin da ya ke rusarwa; zai aikata ya kuma yi nasara. Zai lalatar da manyan mutane, mutane daga cikin tsarkakan.25Da dabararsa zai sa yaudara ta yi nasara a hannunsa. Zai zama babba a cikin tunaninsa. Kamar yadda aka zata zai lalatar da mutane da yawa. Zai kuma yi tsayayya da Sarkin sarakuna, za a kuma karya shi, amma ba da hannun mutum ba.26Wahayi game da yammaci da safiya da aka faɗa gaskiya ne. Amma ka rufe wahayin, gama yana magana ne akan kwanaki masu yawa nan gaba."27Daga nan ni, Daniyel, aka sha ƙarfina na kwanta da kasala har kwanaki da yawa. Daga nan na tashi, na kuma ci gaba da hidimomin sarki. Amma na razana game da wahayin, babu kuma wani wanda ya fahimce shi.
Sura 7 da 8 ba a jere suke ba. Sun faru ne tun lokacin da Belshazza ke sarauta, kafin mulkin Dariyos da Sairus da akayi maganar su a sura 6
A cikin wahayin Daniyel, ya ga wasu dabbobi da ke alamun wadansu abubuwa. Gaba a cikin wahayin wani ya bayyana ma'anar wadannan alamu.
"A shekara ta uku"
Wannan dan sarki Nebukadnezza ne wanda ya gaji sarautar ubansa. Duba yadda aka fassara wannan sunan a 5:1
Wannan matashiya ce da ke tunawa mai karatu cewa wannan wahayin Daniyel na biyu ne.AT:"wahayi ya sake bayyana a gare ni"
tsarewa da karewa
Wadannan sunayen wurare ne.
Kanal wata hanyar ruwa ce mara faɗi da mutum ke yi
rago mai ƙahonni biyu -Abin da aka saba gani ne rago da ƙahonni biyu. Wadannan ƙahonnin, na da ma'ana ta masamman.
"amma wanda ya fi tsawon girmansa a hankali ne fiye da gajeren har ya zo ya zarce shi a tsawo"
"Sai na ga ragon na hanzari" ko "Sai na ga ragon na gudu da sauri"
Raguna basu da hannu. A nan "hannunsa" na nufin karfin ragon. AT:"ya kuɓuto wani daga hannun sa" ko "a kubutar da wani daga ikon sa"
Jimlar "dukan duniya" na fifita ce ya zo ne daga nesa. AT:"daga wuri mai nisa cikin sararin ƙasa"
Bunsurai nada ƙaho biyu a gefen kansu. A bayyana wannan siffa. AT:"bunsurun nada babban ƙaho daya a tsakiyar kansa"
Wannan jimlar an sata ne a matsayin matashiya wajen bayyana wurin da ragon yake.
"kuma cikin matsanancin fushi"
a mutsike wani abu ta wurin tattake shi
"ragon daga bunsurun saboda ikon sa"
" bunsurun ya zama mai girma sosai da ƙarfi"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"wani abu ya ɓalle babban ƙahon"
A nan "kusurwoyin iskoki huɗu na sammai" habaici ne da ke nufin kusurwowi huɗu
"amma ya zama babba kwarai"
Wannan watakila na nufin ya fuskanci wannan wajen. Za'a iya bayyana wannan. AT:"ya karkata ga kudu, gabas, da kuma ƙasa mai kyau ta Isra'ila.
Wannan na nufin kasar Isra'ila.
A nan an bayyana ƙahon kamar mutum da zai yi yaƙi.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"ƙahon ya jefar da wasu dakarun da wasu taurarin ƙasa"
A nan an dauki ƙahon kamar mutum da ya tattake taurari da dakaru.
Daniyel ya ci gaba da bayyana wahayin sa na ƙaho
An kwatanta ƙahon da mutum"
wannan na nufin Allah da kansa, wanda shine shugaban dakarun mala'iku.
A nan "tsai da" na nufin ƙahon ya dena baikon. A nan "shi" na nufin Allah, mai runduna. AT:"ya dakatar da mutane daga yin baikon da suka saba"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"ya gurɓata haikalin sa"
ƙin gaskiya da adalci ne abin da aka bayyana halin ƙahon wanda kamar zai yar da gaskiya ƙasa. AT:"Kahon zai ƙi gaskiya"
"mala'iku"
"miƙa haikalin"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:" kahon na tattaka mayaƙan sama"
A nan "yamma-yamma da safiya-safiya" na nufin komai dake tsakani, wanda ke nufin dukan cikakkun kwanaki. AT:"yamma-yamma da safiya-safiya 2,300" ko "kwanaki 2,300"
"za a tsarkake haikalin tare da mai da shi dai-dai" (UDB)
A nan ana sansance mutum ta wajen muryarsa. AT:"muryar mutum na kira daga tsakiyar bakin Rafin Ulai"
Rafi wata hanyar ruwa ce da mutum ke yi. Dubi yadda aka fasara wannan suna a cikin 8:1
Wannan hanya ce ta sujada in da mutum zai kwanta ƙasa warwas.
"kwanakin karshe" ko "karshen duniya." Wannan ba yana nufin karshen lokaci ba, amma ga batutuwa da zasu faru nantake kafin karshen.
Wannan wani nau'in barci ne da mai yi zai yi kuma baya tashi da sauri
Wannan na nufin lokacin da Allah zai shara'anta. Za'a iya baiyana wannan a zahiri. AT:"lokacin da Allah zai yi shari'a da hasala"
"lokacin da duniya zata ƙare"
A wannan aya, mala'kan ya yi wa Daniyel bayani ma'anar abubuwan da ya gani a wahayin sa. Dabbobin da ƙahonnin a zahiri na wakiltar mutane masu mulki da masarautu.
" ƙahonni biyu -suna wakiltar"
Wasu ma'anoni sun kunshi 1) wannan na nufin sarakunan Mediya da Fashiya ko 2) ana alakanta sarakuna a matsayin wakilan Mediya da Fashiya. AT:"mulkin Mediya da Fashiya"
Wasu ma'anonin sun kunshi 1) wannan na nufin sarkin Giris ko 2) ana alakanta sarkin da sarkin Giris. AT:"mulkin Giris"
"Babban ƙahon tsakanin idanunsa na wakiltar"
A wannan aya, mala'kan ya yi wa Daniyel bayani ma'anar abubuwan da ya gani a wahayin sa. Dabbobin da ƙahonnin a zahiri na wakiltar mutane masu mulki da masarautu.
"wurin da babban ƙahon ya ɓalle, wasu huɗu kuma suka taso"
ƙahonni huɗun na wakiltar sabbin masarautu huɗu. AT:"suna wakiltar masarautu huɗu in da masarautar sarkin farko zata rarrabu"
"amma ba za su sami iko kamar yadda babban ƙahon ke wakiltar sarkin ba"
" A lokacin da wadannan masarautu ke tunƙarar ƙarshe"
"suka ƙure iyakarsu" ko "sun ƙare aikin su"
fuska-wannan na nufin wanda ke da rashin biyayya, ko mara ɗa'a.
A wannan aya, mala'kan ya yi wa Daniyel bayani ma'anar abubuwan da ya gani a wahayin sa. Dabbobin da ƙahonnin a zahiri na wakiltar mutane masu mulki da masarautu.
"wani dabam zai bashi ikon sa"
A nan an bayyana "yaudara" kamar mutum ne mai nasara. AT:" yaudara zata ƙaru"
A nan "hannu" na nufin mulkin sa. AT:"a karkasin ikon sa"
Wannan na nufin Allah
A nan "shi" na nufin iko. AT:"mulkin sa zai ƙare"
A nan "hannu" na nufin iko. Za'a iya fifita wannan. AT:"bada ikon mutum ba" ko "ta wurin ikon mai tsaki"
Mala'ikan ya cigaba da bishe da Daniyel game da wahayin da Daniyel ya gani.
Mala'ikan yayi magana kan wahayin kamar takardar da ake naɗewa da za'a iya rufewa da hatimi. Wannan kan hana kowa daga ganin abin da ke ciki har sai an karya hatimin. AT:"ka rufe tare da hatimce abin da ka rubuta game da wahayin" ko "kar ka faɗawa kowa game da wahayin yanzu"
"an sha ƙarfina na kwanta da kasala har kwanaki da yawa"
"na ci gaba da hidimomin da sarki ya sa ni"
"na razana da wahayin" ko "na riki ce saboda wahayin"
1Dariyos ɗan Ahazurus ne, daga zuriyar Medeyawa. Ahazurus ne aka naɗa sarki a dukkan ƙasar Babiloniyawa.2To a shekara ta farko ta mulkin Dariyos ni, Daniyel, ina binciken litattafai da ke ɗauke da maganar Yahweh, maganar da tazo wa Irmiya annabi. Sai na lura za ayi shekaru saba'in har watsarwar Yerusalem ta kai ƙarshe.3Sai na juya fuskata ga Ubangiji Allah, na biɗe shi cikin addu'a da roƙe-roƙe, tare da azumi, ina sanye da tsumma, ina zaune kuma cikin toka.4Nayi addu'a ga Yahweh Allahna, na kuma furta zunubanmu. Na ce, "Ina roƙon ka, Ubangiji - kai ne Allah Mai Girma Mai Ban mamaki - kai ne mai riƙe alƙawari kana kuma da aminci da ƙaunar masu ƙaunarka suna kuma kiyaye dokokinka.5Mun yi zunubi kuma mun yi abin da ba dai-dai ba. Mun aikata mugunta kuma mun kangare, mun kauce daga umarnanka da dokokinka.6Ba mu saurari bayinka annabawa ba waɗanda suka yi magana cikin sunanka ga sarakunanmu, da shugabanninmu, da ubanninmu, da kuma dukkan mutanen ƙasar.7A gare ka, Ubangiji, adalci ya tabbata. Ko da ya ke, a gare mu yau, kunya ce ta tabbata a fuskokinmu-ga mutanen Yahuda, da mazauna Yerusalem, da kuma dukkan mutanen Isra'ila. Wannan ya haɗa da waɗanda ke kusa da waɗanda ke nesa a cikin dukkan ƙasashen da ka warwatsa su. Wannan ya zama haka saboda babban tawayen da muka yi maka.8A gare mu, Yahweh, kunya a fuskokinmu ta tabbata-ga sarakunanmu, ga shugabanninmu, ga kuma ubanninmu - saboda mun yi maka zunubi.9Jinƙai da gafartawa sun tabbata ga Ubangiji Allahnmu, gama mun yi maka tawaye.10Ba mu yi biyayya ga muryar Yahweh Allahnmu ba ta wurin tafiya bisa ga shari'unsa waɗanda ya ba mu ta wurin bayinsa annabawa ba.11Dukkan Isra'ila sun karya shari'arka su ka juya gefe ɗaya, suka ƙi biyayya da muryarka. La'ana da rantsuwar da aka rubuta cikin shari'ar Musa, bawan Allah, an zubo ta a kanmu, gama mun yi masa zunubi.12Yahweh ya tabbatar da maganganun da ya furta game da mu da kuma masu mulki a kanmu, ta wurin kawo babban bala'i a kanmu. Gama a ƙarƙashin sama dukka babu wani abu da za a iya kwatantawa da abin da a kayi wa Yerusalem.13Kamar yadda aka rubuta a shari'ar Musa, duk wannan bala'i ya sauka akan mu duk da haka ba mu roƙi jinƙai ba daga wurin Yahweh Allahnmu ta wurin kaucewa daga laifuffukanmu da mai da hankali ga gaskiyarka.14Saboda haka Yahweh ya ajiye bala'i a shirye ya kuma kawo shi a kanmu, gama Yahweh Allahnmu mai adalci ne cikin dukkan abin da ya yi, duk da haka ba mu yi biyayya da muryarsa ba.15Yanzu, Ubangiji Allahnmu, ka fito da mutanenka daga ƙasar Masar da hannu mai iko, ka yi wa kanka sanannen suna, kamar yadda ya ke a yau. Amma duk da haka mun yi zunubi; mun yi abubuwan mugunta.16Ubangiji, domin dukkan ayyukanka na adalci, bari fushinka da hasalarka su kawu daga birninka Yerusalem, tsauninka mai tsarki. Saboda zunubanmu, saboda kuma laifuffukan ubanninmu, Yerusalem da mutanenka sun zama abin ba'a ga dukkan waɗanda ke kewaye da mu.17Yanzu, Allahnmu, ka saurari addu'ar bawanka da roƙe-roƙensa domin jinƙai; Ubangiji, ka sa fuskarka ta haskaka akan haikalinka da ya zama kufai.18Allahna, ka buɗe kunnuwanka ka saurara; ka buɗe idanunka ka duba. Mun wulaƙantu; kalli birnin da ake kira da sunanka. Ba muna roƙon taimakonka ba ne saboda adalcinmu, amma saboda jinƙanka mai girma.19Ubangiji, ka saurara! Ubangiji, ka gafarta! Ubangiji, ka kula ka ɗauki mataki! Saboda kai, kada ka yi jinkiri, Allahna, saboda birninka da kuma mutanenka ana kiran su da sunanka."20Yayin da na ke magana - ina addu'a da furta zunubina da zunubin mutanena Isra'ila, ina kuma gabatar da roƙe-roƙena a gaban Yahweh Allahna a madadin dutsen Allah mai tsarki -21yayin da nake addu'a, mutumin nan Jibra'il, wanda na gani a wahayin da farko, ya taso zuwa wurina da gaggawa, a lokacin hadayar maraice.22Ya ba ni fahimi ya kuma ce mani, "Daniyel, yanzu na zo in ba ka masaniya da fahimta.23Da ka fara roƙo domin jinƙai, an bayar da umarni na kuma zo in faɗa maka amsar, gama an ƙaunace ka sosai. Domin haka ka yi la'akari da wannan magana ka fahimci wahayin.24Bakwai-bakwai sau saba'in na shekaru aka zartar domin mutanenka da birninka mai tsarki domin a kawo ƙarshen laifofi a kuma kawo ƙarshen zunubi, a yi kaffara domin mugunta, a kuma kawo madawwamin adalci, a kuma aiwatar da wahayin da anabcin, a kuma keɓe wuri mafi tsarki.25Ka sani kuma ka fahimci cewa daga zartar da umarnin maidowa da sake ginin Yerusalem har ya zuwan shafaffen nan (wanda za ya zama shugaba), za a sami bakwai-bakwai sau bakwai da kuma bakwai sittin da biyu. Za a sake gina Yerusalem da tituna da ramin ganuwa, duk da cewa lokutan tsanani ne.26Bayan bakwai-bakwai sittin da biyu na shekaru, za a rugurguza shafaffen zai zama kuma zama ba komai. Mayaƙan shugaba mai zuwa za su rugurguza birnin da kuma wuri mai tsarki. Ƙarshen shi zai zo da ambaliya, za a kuma yi yaƙi har zuwa ƙarshe. An zartar da abubuwan ban ƙyama.27Zai tabbatar da alƙawari da mutane da yawa na bakwai ɗaya. A tsakiyar bakwai ɗin zai kawo ƙarshen hadaya da baiko. A tsakiyar haramtattun al'amura wani mai hallakarwa zai zo. Cikakkken ƙarshe da rusarwa aka zartar da za a zubo akan wanda ya kawo hallakarwar."
Sura 7 da 8 ba a daki-daki suke ba. Sun faru ne lokacin da Belshazza ke sarauta. Sura 9 yanzu ta koma kan abubuwan da suka faru a lokacin mulkin Dariyos wanda ya zama sarki ya sura 6
Wannan bayani matashiya ce game da ko waye Ahazurus. Littafi Mai Tsarki Juyin UDB ya saka wannan a cikin baka don mai karatu ya fahimta
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:" wanda aka naɗa sarki a dukkan ƙasar Babiloniyawa" ko "wanda ya mamaye Babiloniyawa"
"kan ƙasa" ko "kan mulki"
Wannan ne sunan Allah da ya bayyana wa mutanen sa a Littafin Tsohon Alkawari. Duba sashi fassara game da Yahweh domin yadda za'a iya fassara wannan.
"daga lokacin da aka lalata Yerusalem, zata zauna a matsayin kufai har shekaru 70"
Wannan na nufin babu wanda zai taimaka ko gina Yerusalem a wannan lokacin
A nan "fuskata" na nuna hakalin Daniel. AT:"Na mai da hankali na akan Allah Ubangiji" ko "Na mai da tunanina ga Ubangiji Allah"
Wadanda suke son su san Yahweh tare da gamsar da shi an bayyana su kamar masu biɗar Yahweh.
Wadannan halaye ne na nuna tuba da tausayi.
"Na nemi gafarar zunuban mu"
"Kana yin abin da ka faɗa a alkawarin ka, kuma kana kaunar masu"
Daniyel ya ci gaba da addu'a ga Ubangiji game da mutanen Isra'ila
Wadannan kalmomi biyu na bayyana abu ɗaya a hanya biyu mabanbanta don karin armashi.
Wadannan kalmomi biyu na bayyana abu ɗaya a hanya biyu mabanbanta don karin armashi.
Kalmomin nan "umarninka" da "dokokinka" na ma'ana kusan ɗaya kuma suna magana ka dukan doka
A nan "ba mu saurari" na nufin basu yi biyayya ga saƙon su ba. AT:"ba mu saurari bayinka annabawa"
A nan "suna" na nufin ikon Allah. AT:"magana da ikon ka" or "na yi magana a matsayin wakilin ka"
A nan "kasar" na nufin Isra'ila. AT:"mutanen Isra'ila"(UDB)
Daniyel ya ci gaba da yin addu'a ga Ubangiji game da mutanen Isra'ila.
An yi magana kan zama da adalci ne kamar "adalci" wani abu ne na Yahweh. Za'a iya bayyana wannan a matsayin aiki. AT:"Ubangiji, kayi daidai"
Zama da kunya an kwatanta shi kamar cewa "kunya" wani abu ne da ya shafi mutane. za'a iya duban wannan a matsayin aiki. AT:"amma gare mu, muna jin kunyar abin da muka yi-mu mutane"
Kalmar "mu" ta hada da Daniel da Isra'ilawa, amma banda Allah.
Wannan habaici na nufin kunyar su a fili take ga kowa.
"saboda mun yi maka zunubi ta wajen kunyatar da kai" ko "saboda rashin amincin mu gare ka" (UDB)
Daniyel ya ci gaba da yin addu'a ga Ubangiji game da mutanen Isra'ila.
Da wadannan abubuwa an yi magana kamar ya dangana ga Ubangiji. AT:"Jinƙai da gafartawa sun tabbata ga Ubangiji Allahnmu"
A nan "murya" na nufin umarni da Yahweh ya faɗa.AT:"Ba mu yi biyayya ga abin da Yahweh faɗa mana ba"
Kalmar "juyawa" na nufin Isra'ilawa sun ɗena biyayya ga dokar Ubangiji.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"da Musa ya rubuta a cikin doka"
Yawan la'ana da alkawari an yi magana kansu kamar an zuba ruwa. Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"ka zubo mana"
Daniyel ya ci gaba da yin addu'a ga Ubangiji game da mutanen Isra'ila.
Daniyel na bayyana yadda yake tausayawa Yerusalem matuƙa. Garuruwa da yawa an lalata su gaba ɗaya.
"ba abin da aka yi"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"abin da aka yi wa Yerusalem"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Kamar yadda Musa ya rubuta a shari'a"
A nan dakatar da mugayen ayyuka an bayyana shi kamar juyowa daga gare su. AT:"dakatar da mugayen al'amuranmu"
"Yahweh ya shirya wannan bala'i"
A nan "murya" na nufin abin da Yahweh ya umarta. AT:"ba mu yi biyayya da abin da ya ce muyi ba"
A nan "hannu mai iko" na zama kamar ƙarfi. AT:" da ƙarfi kwarai"
"ka sa mutane su san ƙarfin ikon ka, kamar yadda kake yi a yanzu"
Wadannan zantuttuka biyu na nufin kusan abu ɗaya kuma ana amfani da su tarene a nuna yadda rashin kyaun zunubi yake.
Daniyel da Isra'ila sunyi zunubi da abubuwan mugunta, amma "mun" bata kunshi Allah ba
Kalmomin "fushi" da "hasala" nada kusan ma'ana ɗaya kuma suna nuna yadda fushin Allah yake idan ya tabbatar da shi.
Wannan tsaunin zai iya zama da tsarki saboda haikalin Allah na wurin. AT:"tsaunin da haikalin ka mai tsarki yake"
A nan "mu" na nufin Daniyel da Isra'ila, amma ba Allah ba.
"abin reni"
Wannan ba yana nufin "wannan lokacin ba", amma hanya ce ta nuna cewa abu nagaba addu'ar Daniyel ce zata fara
Kalmar "bawanka" da "sa" anan na nufin Daniyel. Yayi magana da kansa a fakaice a matsayin bangirma ga Allah.
"neman jinkai"
Mai rubutun na magana akan Yahweh wajen nuna kamar fuskar Yahweh tana haske. AT:"kana yin alheri ga"
Wannan na nufin haikali a Yerusalem
"ka buɗe kunnuwanka ka" habaici ne da ke nufin ka saurara. Wadannan jimloli biyu na nufin abu ɗaya kuma suna nuna bukatar Daniyel na Allah ya ji addu'ar sa. AT:"ina roƙonka ka saurara"
" buɗe idanu" habaici ne da ke nufin gani. Wadannan jimloli biyu na nufin abu ɗaya kuma suna nuna bukatar Daniyel na Allah ya kasa kunne ga addu'ar sa. AT:"ka tuna da mu" ko "ka kula da mu"
A nan "sunanka" na nuna sujada. AT:"birnin ka ne" ko "naka ne"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"kayi wani abu da sauri"
"mutanena Isra'ila in da na fito"
Dutsen zai iya zama mai tsarki saboda haikalin. AT:"dutsen inda haikalin Allah mai tsarki yake"
Wannan mala'ikan nan ne Jibra'il da ya baiyana a siffar mutum a 8:15. AT:"Jibra'il, wanda ya bayyana a matsayin mutum"
Wannan zai iya zama wahayi na farko da Daniyel yayi yayin da yake tsaye.AT:"a wahayi na baya" ko "a cikin wahayin da na gani a baya" ko "a wahayin baya"
"ya taso zuwa wurina da sauri"
Mutanen Yahudawa kan yi hadaya ga Allah kowacce yamma kafin rana ta faɗi.
Kalmomin "masaniya" da "fahimta" nanufin abu ɗaya kuma sun bayyana yadda Jibra'il zai taimake Daniyel ya fahimci saƙon gaba ɗaya.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Allah ya bada umarnin"
A nan "magana" na nufin dukan saƙon. AT:"yi tunani akan wannan saƙon"
Wannan ya dangata da anabcin Irimiya a cikin 9:1
Bakwai biyu-Ba haka Isra'ilawa ke ƙirga ba. In zai yiwu, a fassara a hanyar da za'a kare amfani da lamba bakwai. AT:" shekaru saba'in sau bakwai...shekara bakwai sau bakwai... da kuma shekara sittin da biyu sau bakwai"
Allah yayi alkawarin yin abubuwan dake wannan aya ga mutanen da birni mai tsarki.
Kalmar "mutanenka" anan na nufin Daniyel. Mutanen kuma Isra'ilawa da kuma birni mai tsarki Yerusalem.
An maimai ta wannan abu ne don nuna tabbacin faruwar sa.
A nan "aiwatar" habaici ce da ke nufin cimma nasara. AT:"a aiwatar da wahayin"
Wadannan kalmomi na nufin abu ɗaya bisa ga yadda akayi amfani da su. Sun tabbatar wa Daniyel cewa wahayin Irimiya anabci ne.
An yi amfani da wadannan kalmomi ne domin a bayyana amfanin. AT:"dole ne ku fahimta" ko "dole ne ku sani"
Shafewa alama ce ta numa cewa an zaɓi wani. AT:"mutumin da Allah ya shafe" ko "mutumin da Allah ya zaɓa"
Bakwai biyu-idan aka haɗa su zai bada 69 na bakwai 70 da aka bayyana a aya 24
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Mutane zasu sake gina Yerusalem"
Rami ne mai zurfi da ake zagaye gini ko birni, yawancin lokuta da ruwa
"lokacin matsanancin bala'i"
bakwai biyu na-Ba haka Isra'ilawa ke ƙirga ba. in zai yiwu, a yi ƙokari a fassara a hanyar da ta adana amfani da bakwai. Duba yadda aka fassara wannan a 9:24. AT:"bakwai sau sittin da biyu"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"mutane za su rugurguza shafaffen zai zama ba komai"
Shafewa alama ce ta numa cewa an zaɓi wani. Dubi yadda aka fassara wannan maudu'i a 9:24 AT:"mutumin da Allah ya shafe" ko "mutumin da Allah ya zaɓa"
Wannan baƙon mai mulki ne, ba "wanda aka keɓe ba".AT:"baƙon mai mulki wanda zai zo" ko "mai ƙarfin mulki wanda zai zo"
sojojin zasu lalata birnin da gurin tsarki kamar yadda ambaliya ke lalata abubuwa".
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Allah ya umarci lalacewa ga birnin da haikalin" ko "Allah ya tabbatar cewa sojojin abokan gaba zasu lalata komai"
Wannan na nufin mai mulkin da zai zo ya lalatar da shafaffen.
A nan an yi amfani da "bakwai" ne a nuna lokacin shekaru bakwai. AT:"shkaru bakwai...rabin shekaru bakwai"
"hana" ko "tsaida"
Wadannan kalmomi na nufin abu ɗaya ne. Maimaicin don a nuna cewa mai mulkin zai hana kowanne irin baiko. AT:"kowanne irin baiko" ko "kowacce irin hadaya"
Wannan ka iya nufin kayan kariya da ke saman bangayen haikali, wanda ake kira "haramtattun al'amura" domin cike suke da gumaka. AT:"bangayen haikali da suke cike da haramtattun al'amura"
"mutum wanda ke hallakarwa"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Allah ya al'ƙawarta zai zubo Cikakkken ƙarshe da rusarwa"
Wadannan kalmomi kan zama da ma'ana ɗaya. Sun nuna a zahiri yadda rushewar zata kasance. AT:"cikakkiyar rushewa"
"mutumin da ya zama sanadin rushewar"
1A cikin shekara ta uku ta Sairus sarkin Fasiya, an bayyana wa Daniyel wani saƙo, wanda kuma ake kira Beltishazza. Wannan saƙon gaskiya ne. Game da babban yaƙi ne. Daniyel ya gane saƙon ya kuma sami fahimta daga wahayin2A cikin waɗannan kwanaki ni, Daniyel ina cikin makoki har sati uku.3Ban ci abincin da nake marmari ba, ban ci nama ba, ban sha ruwan inabi ba, ban kuma shafe kaina da mai ba har sai da mako uku ɗin suka cika.4A rana ta ashirin da huɗu ga watan fari, lokacin da nake bakin babban kogi (wato Tigris),5Sai Na duba sama sai ga mutum saye cikin linin, ƙugunsa na ɗaure da ɗammara na tsattsarkar zinariya daga Ufaz.6Jikinsa na kama da tofaz, fuskarsa tana kamar walƙiya. Idanunsa kamar fitilu na wuta, ƙafafunsa da hannuwan sa kamar gogagiyar tagulla. Muryar kalmominsa tana kama da muryar babban taro.7Ni, Daniyel, kaɗai na ga wahayin, gama mutanen da ke tare da ni ba su ga wahayin ba. Duk da haka, babban tsoro ya sauko masu, suka ruga don su ɓoye kansu.8Ni kaɗai aka bari sai na ga wannan babban wahayin. Babu sauran ƙarfi da ya rage a cikina; bayyanata mai haske ta juya ta za ma kallon lalatarwa, ba sauran ƙarfi da ya rage a cikina.9Daga nan sai na ji kalmominsa - da na ji su, sai na faɗi kan fuskata cikin barci mai nauyi da fuskata a ƙasa.10Sai hannu ya taɓa ni, ya sa jikina ya yi ta rawa a cikin gwiwoyina da dantsen hannuwana.11Mala'ika ya ce mani, "Daniyel, ƙaunataccen mutum na ƙwarai, Ka fahimci maganar da nake faɗa maka. Ka tashi tsaye, gama an aiko ni wurin ka." Sa'ad da ya faɗa mani wannan saƙon, na miƙe tsaye, ina rawar jiki.12Daga nan sai ya ce mani, "Kada ka ji tsoro, Daniyel. Tun ran da ka fara ƙwallafa ranka ka fahimta kuma ka ƙasƙantar da kanka gaban Allahnka, an ji maganganunka, nima na zo ne saboda maganganunka.13Sarkin mulkin Fasiya ya yi mani tsayayya, an ajiye ni a can tare da sarakunan Fasiya har kwanaki a shirin da ɗaya. Amma Makyal, ɗaya daga cikin manyan sarakuna, ya zo domin ya taimake ni.14Yanzu na zo in taimake ka fahimtar abin da zai faru da mutanenka a kwanakin ƙarshe. Gama wahayin domin kwanakin da ba su zo ba ne tukuna."15Lokacin da ya ke magana da ni yana morar waɗannan kalmomin, sai na juya fuskata wajen ƙasa ban iya yin magana ba.16Wani mai kama da 'ya'ya maza na mutum ya taɓa laɓunana; sai na buɗe bakina na yi magana da shi wanda ke tsaye a gabana. "Ya shugabana, I na cikin tsanani saboda wahayin nan; Ba ni da sauran ƙarfi.17Ni bawanka ne. Ta ya ya zan yi magana da shugabana? Gama ba ni da ƙarfi, kuma ba sauran numfashin da ya ragu a cikina."18Har yanzu sai shi mai bayyana irin ta mutum ya taɓa ni ya ƙarfafa ni.19Ya ce, "Kada ka ji tsoro, ƙaunataccen mutum na ƙwarai, Salama a gareka! Ka yi ƙarfin hali yanzu, ka yi ƙarfin hali!" Lokacin da ya ke magana da ni, Na sami ƙarfi, Na ce, "Bari shugabana ya yi magana, gama ka ƙarfafa ni."20Ya ce, "Ko ka san dalilin da ya sa na zo gare ka? Ba da jimawa zan dawo in yaƙi sarkin Fasiya. Idan na tafi, sarkin Girka zai zo.21Amma zan faɗa maka abin da a ka rubuta cikin Littafin Gaskiya. Ba wanda ya nuna kansa cewa yana da ƙarfi tare da ni gãba da su, sai Makyal sarkinku."
" Sekara ta 3 a mulkin Sairus sarkin Fasiya"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Allah ya bayyana wa Daniyel wani saƙo"
"fahimta"
Wadannan sun ƙunshi abubuwa masu tsada ko masu wuyar samu na ire-iren abinci. AT:"abincin kwalam"
"har sati uku suka cika"
Rana ta huɗu a watan farko-Wannan ne watan farko a kalandar Yahudawa. Rana ta ashirin da huɗu kusan tsakiyar watan Afirilu ce na kalandar mutanen Yamma.
"kuma ƙugunsa na ɗaure da ɗammara"
Ufaz wuri ne. Ba'a san katamaimai inda yake ba.
Jikin sa na haske da kalar shuɗi ko garin ɗorawa kamar anyi shi ne da tofaz. AT:"Jikinsa na kama da tofaz"
Dutse ne mai launin shuɗi ko ruwan ɗorawa, wanda ake kuma kira beril, Feridot, ko krissolin
Fuskar sa na haske kamar walƙiya. AT:"fuskarsa tana haske kamar walƙiya"
Idanunsa na haske kamar harshen wuta. AT:" Idanunsa kamar fitilu na wuta"
ƙafadunsa da hannuwan sa na haske kamar gogagiyar tagulla. AT:"ƙafafunsa da hannuwan sa kamar gogagiyar tagulla"
Muryar kalmominsa nada ƙara kamar mutane da yawa na magana da karfi
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. "Ni kaɗai aka bari sai na ga wannan "
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi." bayyanata mai haske ta juya ta za ma kallon lalatarwa"
Wannan misali ne na fuskar wani lokacin da yake da lafiya.AT:" bayyanata mai lafiya"
Wannan misali ne na fuskar wani lokacin da yake rashin lafiya. AT:"a yamitse"
Wannan ya nuna wani na magana a lokacin wahayin. AT:"sai na ji kalmominsa yana cewa"
Mai yiwuwa 1) Daniyel ya firgita da abin da ya gani har ya zabi ya kwanta ƙasa, inda ya sume ko 2) Daniyel ya suma sa'anan ya faɗi ta gaba a ƙasa"
A nan anyi afani da hannu ya wakilci mai shi, mai yiwuwa mutumin da Daniyel ya gani a 10:4 .AT:"Sai hannu ya taɓa ni"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"Daniyel wanda Allah ke kauna"
mai daraja da ake kauna
"ka ƙwallafa ranka ka fahimci wahayin"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"Allah ya ji maganganunka"
A nan wannan na nufin ruhun da ke iko da ƙasar mutane. AT:"ruhun sarki"
Wannan zai iya nufin sarakuna dabam-dabam da suka mulki daular Fasiya, kuma wadanda suka yi biyayya ga sarkin Fasiya.
"Makyal, ɗaya daga cikin manyan mala'iku" ko "Makyal, ɗaya daga cikin shugabannin mala'iku"
Mala'ikan ya ci gaba da magana da Daniel
"Na kalli ƙasa." Mai yiwuwa Daniyel yayi haka ne don ya nuna bangirma, ko don ya ji tsoro.
Wannan zai iya zama wanda ya gama magana da Daniyel. Ko da wasu juyin Sun nuna shi a matsayin wani mutum dabam. AT:' Wani mai kama da 'ya'ya maza na mutum"
Wannan bayanin na nuna mutum ne gabaɗaya.AT:"mai kama da 'ya'ya maza"
tsaka mai wuya
Daniyel ya yi wannan tambaya ne don ba zai iya magana da mala'ikan ba don su ba daidai suke ba. AT:"Ba zan iya amsa maka ba don ni bawa ne"
Wannan habaicin na nufin numfashi.AT:"ba zan iya numfashi ba" ko "da kyar nake numfashi" .
"shi mai kama da mutum"
Kalmomin "kayi karfin hali" an maimaita sune don fifita bayanin
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"kai wanda Allah ke kauna"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"na ƙarfafu"
A nan "sarkin" nanufin ruhun da ke mulki da tsare ƙasar mutane. Dubi yadda aka fassara irin wannan jimlar a 10:12.AT:"ruhun sarkin Fasiya"
Wannan ya nuna mala'ikan zai fadawa Daniyel game da wannan abu nan take, kafin ya tafi. AT:"amma da farko zan faɗa maka"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"abin da a ka rubuta cikin Littafin Gaskiya" ko "abin da wani ya rubuta a littafin gaskiya"
"wanda ya tabbatar cewa yana da ƙarfi"
"Ba wanda ya nuna kansa cewa yana da ƙarfi tare da ni gãba da su, sai Makyal sarkinku" ko "Makyal sarkinku ne kadai ya taimake ni gaba da su".
Kalmar "sarkinku" na nufin Daniyel da sauran mutanen Isra'ila. AT:"Makyal, sarkin mutanen ku"
"Makyal mala'ikan kare ku." Fassara "sarkin" idan kana nufin Makyal kamar yadda akayi a 10:12
1Cikin shekara ta fari ta Dariyos Bamedeya, ni da kaina na zo domin in goyi baya in kuma kãre Makyal.2Yanzu kuma zan bayyana maka gaskiya. Sarakuna uku zasu tashi daga cikin Fasiya na huɗun zai fi sauran wadata nesa. Yayin da ya sami iko ta wurin wadatarsa, zai zuga mutane su tayarwa mulkin Girka.3Sarki mai girma zai tashi wanda zai yi mulkin masarauta mai girma, zai kuma aikata bisa ga yadda ya so.4Sa'ad da ya tashi sama, mulkinsa zai karye za a raba su wajen iskoki huɗu na sama, amma ban da zuriyarsa, ba kuma zai zama da iko kamar lokacin da ya ke mulki ba. Gama za a tunɓuke mulkinsa a raba shi ga waɗansu ba ga zuriyarsa ba.5Sarkin kudu zai zama da ƙarfi, amma ɗaya daga cikin jarumawansa zai fi shi ƙarfi zai yi mulkin masarautarsa da babban iko.6Bayan 'yan shekaru idan lokaci ya yi, za su yi ƙawance. Ɗiyar sarkin kudu za ta zo wurin sarkin arewa domin tabbatar da yarjejiniyarsu. Amma ba za ta riƙe da ƙarfin hanunta ba shi kuwa ba zai tsaya ba ko 'ya'yansa. Za a yãshe ta - tare da waɗanda suka kawo ta, da mahaifinta, da shi wanda ya goyi bayanta a waɗancan kwanaki.7Amma reshe daga cikin sauyoyinta zai tashi a maimakonta. Zai kai wa rundunar hari ya shiga sansanin sarkin Arewa. Zai yaƙe su, kuma zai yi nasara da su.8Za ya ɗauke su ya kai su Masar bauta. allolinsu da siffofinsu na zubi tare da kyawawan kayansu na azurfa da na zinariya. Har waɗansu shekaru zai janye da ga sarkin Arewa.9Daga nan sarkin Arewa zai mamaye daular sarkin Kudu, amma zai janye ya koma ƙasarsa.10'Ya'yansa za su yi shiri su kuma tara babbar rundunar yaƙi. Za su ci gaba da zuwa su yi ambaliyar kowanne abu; za su ratsa ta duk hanyar zuwa kagararsa.11Daga nan sarkin Kudu zai ji haushi ƙwarai; zai je ya yi yaƙi da shi, wato sarkin Arewa. Sarkin Arewa zai tara manyan mayaƙa, amma za a bayar da rundunar a cikin hanunsa.12Za a kwashe rundunar, zuciyar sarkin kudu kuma za ta ɗaukaka, zai sa dubbun-dubbai su faɗi amma ba zai yi nasara ba.13Daga nan sarkin Arewa zai tãda wata rundunar, da suka fi ta fari girma. Bayan waɗansu shekaru, lallai sarkin Arewa zai zo da babbar runduna waɗanda sun tănaji kayayyaki masu yawa.14Cikin waɗancan lokatai da yawa za su ṭashi gãba da sarkin kudu. 'Yan tada zaune tsaye daga cikin mutanenka za su shirya kansu domin su cika wahayin, amma za su faɗi.15Sarkin Arewa zai zo, zai zuba ƙasa kewaye domin yin matakalu, ya kuma ci birni tare da sansanonin. Ko zaɓaɓɓun sojojinsu. Ba su da sauran karfin tsayawa.16Maimakon haka, shi wanda ya zo zai aikata bisa ga manufofinsa gãba da shi; Ba wanda zai tsaya cikin hanyarsa. Zai tsaya cikin ƙasa mai kyau, hallakarwa kuwa zata kasance cikin hanunsa.17Sarkin Arewa zai ƙudurta ya zo da dukkan ƙarfin mulkinsa, tare da shi kuma zai zama akwai yarjejeniya da sarkin Kudu. Zai ba shi 'ya mace ya aura domin ya lalata mulkin Kudu. Amma dabarar ba za ta taimake shi ba ba kuwa zai yi nasara ba.18Bayan wannan, sarkin Arewa zai maida hankali ga ƙasashen bakin teku zai kama da yawa daga cikin su. Amma wani Jarumi zai kawo ƙarshen girmankansa zai sa girmankansa ya koma kansa.19Sa'annan zai mai da hankalinsa ga sansanoni na ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe ya faɗi; ba za a ƙara ganinsa ba.20Amma wani zai tashi a madadinsa zai sa mai karɓar haraji ya ratsa saboda darajar mulkinsa. Amma cikin kwanaki masu zuwa za a karya shi, ba cikin fushi ko cikin yaƙi ba.21A maimakonsa kuma wani zai tashi mutum abin raini wanda mutane ba za su ba shi darajar sarauta ba; zai zo ba tsammani zai karɓi mulki ta wurin yaudara.22Za a share rundunar yaƙi kamar ambaliya a gabansa. Dukan su da rundunar yaƙi da shugaban alƙawari za a hallakar da su.23Daga lokacin da a ka yi ƙawance da shi, zai yi aikin yaudara; da kimanin mutane 'yan kaɗan zai yi ƙarfi.24Ba tare da gargaɗi ba zai zo cikin waɗansu lardunan da suka fi wadata, zai yi abin da mahaifinsa ko kakansa bai yi ba. Zai baza wa mabiyansa ganima, ganimar yaƙi, da dukiya. Zai shirya juyar da sansanoni, amma na ɗan lokaci ne.25Zai ta da ikonsa da zuciyarsa gãba da sarkin Kudu da babbar rundunar yaƙi. Sarkin Kudu kuma zai ja dagar yaƙi, da babbar rundunar yaƙi, ba zai iya tsayawa ba saboda waɗansu zasu shirya masa makirci.26Har su da suke cin abincisa mai kyau za su yi ƙoƙarin hallaka shi. Rundunarsa za'a share su kamar ambaliya, da yawan su zasu faɗi kisassu.27Dukansu sarakunan nan, da zukatansu da ke nufin mugunta gãba da juna, za su zauna a teburi ɗaya suna yiwa juna ƙarya, amma ba za ta zama da amfani ba. Gama matuƙa za ta zo a ƙayadadden lokaci.28Sa'an nan sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai yawa, ya sa zuciyarsa ta yi gãba da alƙawari mai tsarki. Zai aikata abin da ya so daga nan ya koma ƙasar sa.29A cikin sanyayyen lokaci zai sake dawowa gaba da Kudu. Amma a wannan lokacin ba zai zama kamar na farin ba.30Gama jiragen Kittim za su kawo masa hari, zai tsorata kuma ya koma baya. Zai ji haushin alƙawari mai tsarki, zai nuna amincewa ga waɗanda suka watsar da alƙawari mai tsarki.31Dakarunsa zasu tashi su tozartar da kagarun wuri mai tsarki. Zasu kawar da baikon ƙonawa na kullum, za kuma su kafa abin banƙyama da zai sa hallakarwa.32Gare su da suke aikata mugunta saɓanin alƙawari, zai yaudare su ya ɓata su. Amma mutanen da suka san Allahnsu zasu yi ƙarfi su kuma ɗauki mataki.33Su da ke da hikima cikin mutane zasu sa da yawa su fahimta. Amma zasu faɗi ta kaifin takobi da harshen wuta; zasu faɗi cikin bauta da yi masu fashi kwanaki da yawa.34Cikin faɗuwarsu, za a taimake su da taimako ƙanƙane. Cikin munafunci da yawa za su haɗa kai da su.35Daga cikin masu hikima waɗansu zasu faɗi domin a tace su, a wanke su, a tsarkake su, har kwanakin ƙarshe. Amma lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.36Sarki zai aikata bisa ga son ransa. zai ɗaukaka kansa ya maida kansa babba bisan kowanne allah. Zai faɗi abubuwan ban mamaki gãba da Allahn alloli, zai yi nasara har lokacin da fushi ya cika. Gama abin da aka wajabta zai faru.37Ba zai kula da allolin kakanninsa ba ko allahn da mata ke marmari. Ba zai kula da kowanne allah ba. Gama zai maida kansa babba a bisa kowannen su.38Maimakon waɗannan, zai girmama allahn ganuwoyi. Shi ne allahn da ubanninsa ba su sani ba zai girmama shi da zinariya da azurfa da duwatsu masu daraja da kyaututtuka masu amfani.39Zai kai hari ga ganuwoyi masu ƙarfi ta wurin taimakon baƙon allah. Ga duk wanda ya yarda da shi, zai ƙara mai ɗaukaka. Zai maishe su masu mulkin mutane da yawa. Zai raba masu ƙasa a matsayin lada.40A kwanakin ƙarshe kuma sarkin Kudu zai kai hari. Sarkin Arewa kuma zai tasar masa da karusan yaƙi da mahaya dawakai, da jirage da yawa. Zai shiga cikin ƙasashe, ya kwarara, ya ratsa.41Zai shiga cikin ƙasa mai kyau dubbun-dubban Isra'ilawa za su faɗi. Amma waɗannan zasu tsira daga hanunsa: Idom, Mowab da sauran mutanen Amon.42Zai ƙara miƙa hanunsa cikin ƙasashen; ƙasar Masar ba za ta tsira ba,43Zai sami iko bisa kan taskar zinariya da azurfa da kan dukkan wadatar Masar; Libiyawa da Kushawa zasu bi tafin sawayensa.44Amma labari daga gabas da arewa zai tsoratar da shi, zai fita da babbar hasala domin ya hallakar gaba ɗaya ya kuma keɓe da yawa domin hallaka.45Zai kafa rumfar fãdarsa tsakanin teku da kyakkyawan dutse mai tsarki. Zai kawo ƙarshen sa, ba kuwa mai taimakon sa.
A cikin Daniyel 11:1 zuwa 12:4, wanda ke magana da Daniyel a sura 10 ya sheda masa abin da ke rubuce a littafin gaskiya. Wannan kamar yadda ya faɗa yake cikin 10:20
Dariyos sarkin Medeya ne. "Shekara ta fari" na nufin shekarar fari da ya zama sarki. AT:"Cikin shekara ta fari ta Dariyos"
"Sarakuna uku zasu yi mulki cikin Fasiya"
"baya su sarki na huɗu zai hau kan karagar mulki wanda zai zama da dukiya fiye da sauran ukun kafin shi"
Ma'anar ta kunshi 1) karfin mulki 2)karfin soja
"zai zuga mutane su yi tunanin yin faɗa"
Mala'ikan ya ci gaba da magana ga Daniyel
Raɗin tada ko ɗaga wa akan yin amfani da shine ga wanda ya zama da karfi. AT:"Sarki mai girma zai tashi"
Ma'anar ta kunshi 1) girman daular sa zata zama gawurtaccen, ko 2)cewa sarkin zai mulki daular sa da babban iko.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"mulkinsa zai karye ya rabu" ko "mulkinsa zai karye ya rarrabe"
Fassara wannan kamar a 7:1
Batun rarrabawa na da tasiri a nan. AT:"amma ba za'a raba shi ba ga zuriyarsa" ko "amma ba za'a raba tsakanin zuriyarsa ba"
mulkin an yi bayanin sa kamar tsiro da wani ya lalata shi ta wurin tugeshi. Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"wani ikon zai tsige tare da lalatar da mulkin sa sai sauran da ba zuriyarsa ba zasu yi mulki"
Mala'ikan ya ci gaba da magana ga Daniyel
ɗaya daga cikin jarumawan sarkin kudanci zai zama sarkin arewaci
Sarkin kudu zai yi ƙawance da na arewa. Wannan ƙawance zai zama yarjejeniya da ake buƙatar kowa ya bi. AT:"Sarkin kudu da na arewa zasu yi alkawarin yin aiki tare."
Sarkin kudu zai bada ɗiyarsa aure ga sarkin arewa. Auren zai tabbatar da yarjejeniyar da ke tsakanin sarakuna biyun
A nan "kafaɗa" na matsayin iko.
Wannan ya nuna kamar maƙarƙashiyar kashe ta tare da wadanda sukayi yarjejeniyar. Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"za su manta da ita"
Mala'ikan ya ci gaba da magana ga Daniyel
An bayyana iyalin nan kamar itace. sauyoyi na matsayin kakanni, da rassanta kuma zuri'a. AT:"zuriyar kakannin ta" ko "ɗaya daga cikin zuriyar ta"
Kalmar "ta" na nufin yar sarkin kudu a cikin 11:5
Kalmar "shi" na nufin zuriyata, kuma a nan tana nufin sojojin sa. AT:"shi da sojojin sa zasu kai hari ga sarkin arewa"
A nan "su" na nufin sojojin abokan gaba. AT:"zai yaƙi sojojin abokan gaba"
Kalmar "shi" na nufin sarkin Arewa
Mala'ikan ya ci gaba da magana ga Daniyel
yayan sarkin Arewa
"tara mutane da yawa wanda zasuyi yaƙi a bakin daga"
Yadda dakarun zasu mamaye ƙasar zai zama kamar ambaliyar ruwa. AT:"zasu zama da yawa da zai sa su mamaye dukan ƙasar"
Mala'ikan ya ci gaba da magana ga Daniyel
"zai tara mayaƙa"
A nan "hannunsa" na nufin ikon sarkin kudu. AT:"sarkin zai sallama sojojin sa ga sarkin kudu"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"sarkin kudu zai kama sojojin na arewa"
"ɗaukaka na nufin yanayin zama da fariya.AT:"zai zama da fariya"
A nan faɗi na nufin mutuwa a bakin daga. AT:"dakarunsa zasu kashe dubban abokan gabar sa" ko "zai kashe da yawan dubban abokan gabarsa"
"dubbai da yawa"
Mala'ikan ya ci gaba da magana ga Daniyel
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"babbar runduna waɗanda sun tănaji kayayyaki masu yawa"
Mala'ikan ya ci gaba da magana ga Daniyel
A nan batun tashi na nufin tayaswa. AT:"mutane da yawa zasu yi wa sarki tawaye"
Wannan na nufin mutane masu tawaye.
A nan faɗuwa na nufin kasawa.AT:"ba zasu yi nasara ba"
Mala'ikan ya ci gaba da magana ga Daniyel
"Sarkin arewa" a nan na nufin sojoji a cikin dakarun sarki, wanda zai yi ainihin aikin matakalu" (Duba:|Metonymy)
A nan "sarkin arewa" ya haɗa da sojojin sa. AT:"dakarun sarkin arewa zasu zo" (Duba:|Metonymy)
Wannan ya kunshi shirya ƙasa yadda sojoji zasu iya hawa saman ganuwa domin kai hari. Sojoji da bayi zasu sa lallausar ƙasa a mazubi, su kai ta wurin da ya dace, sa'annan su juye domin a gina matakalar.
bangaye da wasu abubuwa da ake ginawa don kare birni daga dakaran abokan gada
A nan tsayawa na nufin damar yaƙi. AT:"ba wanda zai iya ci gaba da yaƙarsu" (Duba:|Metonymy)
"sarkin da yayi mamayar zai yi abin da ya ga dama ga ɗaya sarkin"
A nan tsayawa na nufin mulki. AT:"Sarkin zai fara mulki" (Duba:|Metonymy)
Wannan na nufin ƙasar Isra"ila. Dubi yadda aka fassara wannan a cikin 8:9
A nan "hallakarwa" na nufin ikon lalatarwa. Kuma, an yi maganar ikon hallakarwa kamar wani abu ne da wani zai riƙe a hannun sa. AT:"zai sami ikon lalata komai"
Mala'ikan ya ci gaba da magana ga Daniyel
"zaɓi" (Duba:|Idiom)
Wannan zai iya zama karfin soja. AT:"zai zo da karfin dakarun sa" (Duba: fig_metonymy)
Wannan wata hanya ce ta cewa "mace" (Duba:|Idiom)
"zai maishe da sarkin Arewa ya dena zaton dabarar sa"
"zai sa sarkin Arewa ya sha wuya saboda halin sa ga wasu"
"Sarkin Arewa zai mai da hankali"
Wannan hanya ce ta cewa zai mutu. Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"zai ɓace" ko "zai mutu" (Duba:|Idiom da|Active_or_passive)
Mala'ikan ya ci gaba da magana ga Daniyel
Tashi a wurin sarki na nufin zama sarki a madadin sarki na baya. AT:"wani mutumin zai zama sarkin Arewa a maimakon wancan sarki"
Mai karbar harajin zai ratsa ƙasar yana matsawa mutane su biya haraji. AT:"zai aiko wani ya sa mutane su biya haraji"
A nan "shi" na nufin sabon sarki. Karya shi na nufin mutuwa. AT:"sabon sarkin zai mutu"
Ma'anar ta kunshi 1) ba wanda yayi fushi da sarkin 2) sanadi da dalilin mutuwar sarkin an barshi a matsayin sirri.
Mutane zasu ƙi yarda da shi a matsayin sarki domin shi ba daga zuriyar sarauta yake ba. AT:"mutumin da mutane zasu raina ba kuma zasu bashi martabar sarki ba"
Sharewa na nufin lalatawa. AT:" dakarun sa zasu lalata sojoji masu girma kamar yadda ambaliyar ruwa ke lalata duk abin da ta samu" .
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"zai hallaka wannan dakarun da shugaban alƙawarin" .
Wannan jimlar na nufin mutumin da ya cika gurbin addini mai daraja da Allah ya bukata a alƙawarin sa, da na babban firis.
Bayani na gabaɗaya: Mala'ikan ya cigaba da magana ga Daniyel
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"lokacin da suran masu mulki suka yi yarjejeniyar salama da shi"
" Zai baza wa mabiyansa "
"abubuwa masu daraja da shi da dakaran sa suka dauko daga mutanen da suka yi nasarar yaƙar su"
Bayani na gabaɗaya: Mala'ikan ya cigaba da magana ga Daniyel
Ikonsa da zuciyarsa
Wannan na nufin gabagaɗi.
"da babbar rundunar yaƙi da zai shirya"
"zai yaƙe shi"
ba zai iya tsayawa na nufin an ci nasara akan sa.AT:"za'a yi nasara akan sarkin kudu" ko "za'a yi nasara akan dakarunsa"
A nan ana maganar masu bashi shawara. Abin da aka saba yi ne amintaccen mai ba sarki shawara ya ci abinci tare da shi. AT:"masu bada shawarar da sarki ya aminta da su"
A nan an yi magana kan matsananciyar nasara akan wasu dakarai kamar yadda ambaliya ke share duk abin da tayi karo da shi.AT:"abokin gabar zai yi nasara da dakarunsa" ko "abokin gabar sa zai yi nasarar lalata dakarunsa kamar yada ambaliya ke tafiya da duk abin da ta haɗu da shi a hanyar ta"
A nan "faduwa" habaici ce da ke nufin mutuwa a baƙin daga, saboda haka "faduwa" da "mutuwa" na da ma'ana kusan ɗaya. AT:"dakarunsa da yawa zasu mutu a filin daga"
A nan "zuciya" na nufin ƙudirin mutum. An yi maganar kudiri a nan kamar wani abu da wani zai ajiye a wani wuri. AT:"kowa na shirin mugunta ga ɗayan"
zama a teburi ɗaya na nufin magana da juna.
"amma maganganun su bazasu taimake su ba"
Wannan ya bayyana dalilin da yasa zaman su ba zai yi nasara. AT:"sakamakon ayyukan su zai zo ne kawai a lokacin da Allah ya shirya"
Wannan na nuna ra'ayin sarkin na yin tayaswa ga alƙawarin Allah a Isra'ila. Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"arziƙi. zai zaɓi yin tawaye ga alƙawari mai tsarki"
Wannan na nufin ra'ayin sarki.
Ra'ayin sarki na yin tawaye ga alƙawari mai tsarki na nuna ra'ayin sa na hana Isra'ilawa yin biyayya ga wannan alƙawarin. AT:"don ya hana Isra'ilawa yin biyayya ga alƙawari mai tsarki"
A nan "mai tsarki" na nuna alƙawarin Allah da Isra'ila. Ya nuna alƙawarin na buƙatar a girmama da yin biyayya gare shi domin daga Allah da kansa yake. AT:"alƙawarin Allah, wanda ake buƙatar duk Isra'ilawa su kiyaye"
Wannan na nufin sarkin zai yi wasu abubuwa a Isra'ila. AT:"zai yi abin da ya so a Isra'ila"
jiragen na nufin dakarun da zasu zo cikin su. AT:"dakaru zasu zo daga Kittim a cikin jirgin ruwa domin su yaƙi sojojin sa"
Wannan wani wuri ne a tsibirin sifris a Kogin Meditareniya.
"Zai ji haushi sosai"
"zai yi wani abu domin wasu" ko "zai taimaki wasu"
"Dakarunsa zasu bayyana" ko "dakarun sa zasu zo". Kalmar "sa" na nufin sarkin Arewa.
"wuri mai tsarkin da mutane ke neman mafaka"
kawar da baikon na nuna hana mutane su aikata haka. AT:"Zasu hana firis miƙa baikon ƙonawa na kullum"
Wannan na nufin gumakan da zasu maida haikali abin baƙyama, wato, wanda zai sa Allah ya bar haikalinsa. AT:"gumakan da zasu sa Allah ya bar haikali" ko "abubuwan banƙyama da zasu mai da haikali ya rasa tsarki"
"cikin mugunta su ƙi yin biyayya ga alƙawari"
"yaudare su don suyi mugunta"
A nan "sani" na nufin "yin aminci". AT:"wadanda suka yi aminci ga Allahn su"
"zasu tsaya daram su kuma ƙi su
A nan "faɗi" na nuna ɗanɗana tashin hankali iri-iri, har ma mutuwa da kanta.
Wannan na nufin mai hikima a cikin Isra'ilawa
A nan "takobi" na nufin filin daga. AT:"zasu mutu a filin daga".
A nan "haske" na nufin wuta. AT:"kuma ta wurin ƙonewa har mutuwa"
"maishe wa zuwa bauta"
Za'a iya cewa .AT:"abokan gabarsu zasu yi masu fashi"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"wasu zasu basu taimako dan ƙanƙane"
wannan na nuna wasu mutane zasu yaudari masu adalcin da sunan taimako, amma ba da gaske suke yi ba.
A nan "haɗa kansu" na nufin "kawo taimako".AT:"zai kawo agaji"
a nan "faɗuwa" na nuna tashin hankalin da zasu fuskanta iri-iri, harma ga mutuwa.
a nan "tsarkake" na nufin "da sakamako".AT:"da sakamakon tacewa da zata faru da su"
Wadannan ayyuka guda ukun an baiyana su kamar abubuwa ne. Duk da cewa, za'a iya daukar su haka. AT:"za'a tace su, tsarkake, da wankewa" ko " wahalar su zata tace, wanke, da tsarkake su"
Wahalar zata ci gaba har sai lokacin da Allah ya yanke karshen.
Wannan na nufin tace ƙarfe ta wurin narkas da shi a cikin wuta. Sa'adda Allah ya maishe da mutanen sa masu adalci gare shi, an ambace shi ne kamar su karfe ne da mai aik ke tsarkake su ta waje sa su cikin wuta.
Wannan na nufin maishe da mutane , wurare, ko wani abu daidai da amfanin Allah ta wurin ware su daga zunubi. Ya nuna zunubi kamar ƙazanta ce ta fili da za'a iya wanke wa.
Wannan batun na kusan daidai da tacewa, da aka yi magana da fari. Karfen da aka tace za'a iya ce wa an tsarkake shi.
"kwankin ƙarshe" ko "karshen duniya". Duba yadda aka fassara wannan a 8:15
A nan "ƙayyaɗaɗɗen lokaci" na nuna Allah ya shirya lokaci. Za'a iya cewa. AT:"Yahweh ya sa lokaci a nan gaba"
"sarkin zai yi abin da ya ga dama"
wannan na nufin sarkin Arewa
kalmar "daukaka kansa" da "ya maida kansa" na nufin abu ɗayakuma yana sarkin zai zama da fariya.
A nan wannan na nufin zama da fariya
A nan wannan na nufin tunanin zama da amfani da iko.
"abubuwan tada hankali" ko "abubuwan razana"
Jimlar ta nuna Allah na tara hukuncin sa har sai ya kai wani matsayi sa'annan ya yi wani abu. AT:"har sai Allah ya hasala kwarai game da shi" ko "har sai Allah ya cika da fushi kafin ya dauki mataki"
Wannan na nufin Allah ɗaya na gaskiya.AT:"Allah mai girma" ko "Allah ɗaya na gaskiya"
Wannan na nufin allan arna mai suna Tammuz
mai yiwuwa sarkin ya yarda cewa wadannan allolin ƙaryar zasu taimake shi ya yaƙi kariyar wasu mutane ya kare tashi. AT:"allahn da ke da ikon kariya"
kalmar "wadannan" na nufin allolin da aka faɗa a 11:36
Ma'anar ta kunshi 1) "zai ba da ƙasar ga masu bin sa a matsayin lada" ko 2) "zai sayar da ƙasar ga mabiyan sa"
"" a kwanaki na karshe" ko "karshen duniya". Duba yadda aka fassara a cikin 8:15
Wannan kalmar na nufin sarakunan da dakaran su. AT:" sarkin Kudu da dakarun sa...sarkin Arewa da dakaran sa"
an bayyana kai harin mai uwa da wabi kamar an yi ruwa da iska. AT:" zai kai masa hari kamar iskar hadari" ko " zai kai masa mummunan hari"
Idan dakaru su shiga gari, yana kamar anyi ambaliya. Duba yadda aka fasara wannan a 11:10.
Babu abin da zai dakatar da dakaran. AT:" zasu ratsa ta cikin ƙasar ba tare da wani ya tare su ba"
wannan na nufin ƙasar Isra'ila. Duba yadda aka fassara a cikin 8:9 da 11:15
A nan faɗuwa na nufin mutuwa. AT:"zai mutu"
A nan "hannu' na nufin iko. AT:"Amma waɗannan zasu tsira daga hanunsa" ko "amma ba zai iya lalatar da ƙasashen ba"
Har yanzu akan sarkin Arewa ake
a nan "hannu" na nufin iko da umarni. "Zai ƙara miƙa hanunsa ikon sa akan ƙasashe"
A nan batun na nufin ƙasashe da yawa ko ƙasashe
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"ƙasar Masar ba za ta tsira ba"
A nan "sawayensa" na nufin miƙa kai. AT:"Libiyawa da Kushawa zasu miƙa kai gareshi"
"mutanen Libiya da Itofiya." Libiya ƙasa ce a yammmacin Masar, da Itofiya kuma ƙasa ce a kudan cin Masar.
Har yanzu akan sarkin Arewa muka
Wannan mafaiyacin sunan "hasala" zamu iya bayyana shi da kalmar "fushi". za'a iya baiyana shi a fili cewa zai tafi da dakarun sa. AT:"zai fita da babbar hasala ya kuma fita " ko "zai zama da hasala ƙwarai ya kuma tafi da dakarun sa"
A nan wannan kudirin na nufin kaiwa abokan gaba hari
"domin ya hallakar da mutane dayawa"
Wannan na nufin rumfar fãdar sarki mai cike da kayan alatu da yake zama lokacin yaƙi tare da dakarunsa.
Wannan maiyiwuwa na nufin yankin da ke tsakanin kogin Meditareniya da haikalin dake Yerusalem.
Wannan na nufin tudan Yerusalem inda haikalin Allah yake. Duba yadda aka fasara makamanciyar jimlar a 9:15 da 9:20.
1"A wannan lokaci Makyal, babban yarima mai kare mutanenka, zai tashi. Za a yi kwanakin wahala irin waɗanda ba a taɓa yi ba tun da aka yi kowacce al'umma har ya zuwa lokacin nan. A lokacin nan za a ceci mutanenka, duk wanda aka iske sunansa a cikin littafi.2Da yawa waɗanda suke barci cikin turɓayar ƙasa za su tashi, waɗansu zuwa rai na har abada waɗansu kuma zu wa kunya da ƙasƙanci marar matuƙa.3Waɗanda suke da hikima zasu haskaka kamar walƙiya ta sararin sama, waɗanda suka juya mutane da yawa zuwa ga adalci za su haskaka kamar taurari har abada abadin.4Amma kai Daniyel, ka kulle maganganun nan; ka hatimce littafin har sai kwanakin ƙarshe. Da yawa zasu yi ta gudu nan da can, ilimi kuma zai ƙaru".5Sa'an nan, ni, Daniyel, na duba, akwai waɗansu biyu suna tsaye. Ɗaya yana tsaye a bakin kogi ɗaya kuma yana tsaye a bakin ƙetaren wancan kogin.6Ɗaya daga cikin su ya ce da mutumin da ke saye da linin, wanda ya ke kan magudanar kogin ya ce, "Har yaushe zai zama ƙarshen waɗannan al'amura na al'ajabi?"7Na ji mutumin da ke sanye da linin, wanda ya ke bisa magudanar kogin - ya ɗaga hanunsa na dama da na hagu sama ya yi rantsuwa ga shi wanda ya ke rayuwa har abada za a yi lokaci da lokatai, da rabin lokaci. Sa'ad da ikon mutane masu tsarki ya karye a ƙarshe, dukkan waɗannan al'amura zasu cika.8Na ji amma ban fahimta ba. Sai na tambaya, "Ya shugabana, ina mafitar waɗannan al'amura?"9Ya ce, "Tafi yi tafiyarka, Daniyel, gama an kulle maganganun nan an hatimce su har sai kwanakin ƙarshe.10Waɗansu da yawa zasu tsarkaka, tsabtattu, su zama tatattu, amma miyagu za su aikata mugunta. Babu wani a cikin mugaye da zai fahimta, amma masu hikima zasu fahimta.11Daga lokacin da aka kawar da baiko na ƙonawa aka kuma kafa abin ƙyama mai sa hallakarwa, za'a yi kwanaki 1,290.12Mai albarka ne shi wanda ya jira har ƙarshen kwanaki 1,335.13Dole ka yi tafiyarka har ƙarshen, kuma za ka huta. Za ka tashi a cikin wurin da aka keɓe maka, a ƙarshen kwanaki."
Mala'ikan da ya bayyana ga Daniyel a 10:4 ya ci gaba da magana
Makyal babban dan saƙo. A nan an bashi wani muƙami na "babban yarima".
A nan "tashi" habaici ne da ke nufin bayyana. AT:"Makyal... zai bayyana"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. Za ka iya bayyana shi cewa Allah zai ceci mutanen sa. AT:" Allah zai ceci mutanen sa"
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi."
Jimlar "barci cikin turɓayar ƙasa" wata hanya ce ta bayyana wadanda suka mutu. A nana "tashi" habaici ne da ke nufin sake dawowa da rai. AT:"wadanda suka mutu zasu sake rayuwa" (Duba: da"
Wannan na nufin mutanen Allah da zasu raba hikimar su da wadanda suke kewaye da su.
Wannan na nufin wadanda suke taimakon wadansu su gane sun rabu da Allah, kamar sun canza inda suka dosa. AT:"wadanda suke koyawa wasu yadda zasu yi rayuwar tsarki"
Wadannan mutanen an danganta su da taurari da ke haske. AT:"wadanda suka juya...zasu haskaka kamar taurari har abada abdin"
A nan "maganganun" na nufin littafin. AT:"ka kulle maganganun nan; ka hatimce littafin "
"kwanakin ƙarshe" ko "karshen duniya." Duba yadda aka fassara wannan a 8:15.
Mai yiwuwa wannan zai faru kafin "kwanakin karshe" lokacin da aka rufe littafin. Za'a iya fayyace wannan. AT:"kafin wannan ya faru, mutane da yawa zasu yi ta kai-komo nan da can, suna koyon abubuwa da yawa game da batutuwa masu dama"
Daniyel ya ci gaba da sheda abin da ya gani a wahayin da ya fara a 10:1.
"akwai waɗansu mala'iku biyu a tsaye"
Wannan na nufin mala'ikan da ya bayyana ga Daniyel a 10:4, ba daya daga cikin mala'ikun da ke tsaye a bakin kogin ba.
Mai yiyuwa ma'anonin su zama 1) mala'ikan da ke saye da linin na saman rafin, ko 2) mala'ikan na kan magudanar kogin
"Har yaushe waɗannan al'amura na al'ajabi zasu kai?" Wannan na nufin lokacin daga farko zuwa karshen al'amuran.
A lokacin da Mala'ikan yayi magana da Daniyel, ba wani daga cikin al'amuran wahayin da ya faru. Hakika wannan na nufin al'amuran da ke cikin 12:1, da wasu kuma na wahayin sura 11.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi.AT:"mutumin da ke sanye da tufafin linin" ko "mala'kan da ke sanye da tufafin linin"
Mai yiyuwa ma'anonin su zama 1) mala'ikan da ke saye da linin na saman rafin, ko 2) mala'ikan na kan magudanar kogin
"Allah, wanda zai dauwama har'abada"
Zai yi kyau a bar shi cikin rashin tabbas har sai an fara. Idan dole sai an fara daga farko, shekara uku da rabin mai yiwuwa zai fara da al'amuran 12:1
"shekara uku da rabi" (UDB). Wadannan "lokatai" an fahimci suna nufin shekaru. shekara ɗaya, da biyu da rabi wanda suka yi daidai da uku da rabi.
Za'a iya bayyana wannan da gabagaɗi. AT:"duk wadannan abubuwa da sun kasance"
A lokacin da mutumin da ke sanye da tufafin linin ya ke magana da Daniyel, babu ko daya daga cikin batutuwan wahayin da ya faru. Wannan na nufin batutuwan da ke cikin 12:1, da kuma batutuwan wahayin da ke sura 11
Daniyel ya bayyana mala'ikan da ke sanye da tufafin linin a matsayin "Shugaban sa" don nuna bangirma ga mala'ikan.
A lokacin da mutumin da ke sanye da tufafin linin ya ke magana da Daniyel, babu ko daya daga cikin batutuwan wahayin da ya faru. Wannan na nufin batutuwan da ke cikin 12:1, da kuma batutuwan wahayin da ke sura 11
Wahayin da aka ba Daniyel ba don a bayyana shi ba ne. An hatimce littafin babu kuwa wanda zai iya buɗe shi. AT:"idan zaka rufe ka kuma hatimce kalmomin da ka rubuta"
"kwanakin ƙarshe" ko "ƙarshen duniya." Duba yadda aka fassara a 8:15.
Mala'ikan da ke saye da tufafin linin ya ci gaba da yin magana ga Daniyel
Yahweh ne zai tsarkake. Wadannan kalmomi uku na nufin kusan abu ɗaya. AT:"Yahweh zai tsarkake, tsabtace ya kuma tace mutane da yawa"
tsarkakewa ta wurin cire duk wani abu da bai shafe su ba
Mugayen mutane zasu yi mugunta ko abubuwan zunubi
mugayen mutane baza su fahimci ilimin ruhaniya ba
Wannan na nufin masu hikima wajen yin biyyaya ga Yahweh zasu fahimta
Sarkin Arewa ne ya hana baiko a haikali. AT:"Sarkin Arewa ya kawar da baikon ƙonawa da aka saba yi ya fara mugayen ayyukan da suka maishe su abin ƙyama"
Wannan na nufin gunki da zai maishe da haikali abin ƙyama, wato, da zai sa Allah ya bar haikalin sa. Dubi yadda aka fassara wannan a 11:31. AT:" gunkin da zai sa Allah ya manta da haikali" ko " abin kyamar da zai mai da haikali mara tsarki"
A nan "kwanaki" na nufin wani lokaci. Yawancin lokuta akan kirashi kwanaki, zai iya nufin shekaru.
Mala'ikan da ke saye da tufafin linin ya ci gaba da yin magana ga Daniyel
"Mai albarka ne shi wanda ya jira" ko "Mai albarkane duk wanda ya jira"
"daure" ko "ya tsaya har matuƙa"
A nan "kwanaki" na nufin wani lokaci da aka fi kira kwanaki. Koda yake, zai iya zama shekaru.
"Daniyel, dole ka tafi". Wannan na nufin Daniyel ya ci gaba da rayuwa ya kuma bautawa sarkin har zuwa lokacin da aka ƙaiyade masa ya mutu.
Wannan hanya ce ta cewa "zaka mu".
Wannan na nufin tashin matattu na farko lokacin da mutane masu tsarki zasu tashi.
"urin da Allah ya keɓe maka"
1Wannan ita ce maganar Yahweh da ta zo wurin Hosiya ɗan Biri a kwanakin Uziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da kuma kwanakin Yerobowam ɗan Yoash, sarkin Isra'ila.2Sa'ad da Yahweh ya yi magana da fari ta wurin Hosiya, ya ce masa, "Jeka ka ɗaukar wa kanka mata wadda karuwa ce. Za ta sami 'ya'ya ta wurin karuwancinta. Domin ƙasar tana aikata matuƙar karuwanci ta wurin yashe da Yahweh."3Sai Hosiya ya tafi ya auro Gomar ɗiyar Diblayim, sai ta yi ciki ta haifa masa ɗa namiji.4Yahweh ya cewa Hosiya, "Ka kira sunansa Yeziril, gama a ɗan lokaci kaɗan zan hukunta gidan Yehu saboda ya zubda jini a Yeziril, zan kuma kawo ƙarshen mulkin gidan Isra'ila.5Wannan zai faru randa zan karya bakãr Isra'ila a Kwarin Yeziril."6Sai Gomar ta sake yin ciki ta haifi 'ya mace. Sai Yahweh yace wa Hosiya, "Ka raɗa mata suna Lo Ruhama, gama ba zan ƙara yi wa gidan Isra'ila jinƙai ba, har da zan gafarta masu.7Duk da haka zan yi wa gidan Yahuda jinƙai, zan cece su ni da kaina, Yahweh Allahnsu. Ba zan cece su da baka, da takobi, da yaƙi, da dawakai da mahayansu ba,"8Bayan da Gomar ta yaye Lo Ruhama, sai ta yi ciki ta haifi ɗa namiji kuma,9Sa'an nan Yahweh yace, "Ka raɗa masa suna, Lo Ammi, domin ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.10Duk da haka yawan mutanen Isra'ila za su zama kamar yashi a bakin teku, wanda ba za a iya aunawa ko ƙirgawa ba. Zai zamana inda aka ce masu, 'Ku ba mutanena ba ne, za a ce masu, "Ku mutanen Allah mai rai ne.'11Mutanen Yahuda da mutanen Isra'ila za su taru wuri ɗaya. Za su naɗa wa kansu shugaba ɗaya, za su haura su tafi daga ƙasar, gama ranar Yezril zata zama da girma.
Wannan maganar fasaha ce: "maganar da Yahweh, Allah, ya fada"
Wannan sunan wani mutum ne.
Al'amuran wannan littafin sun wakana a zamanin wadannan sarakan.
Wannan ne sunan Allah, wanda ya bayyana wa jama'arsa a Tsohon Alkawari. Dubi shafin fassarar Kalma a kan Yahweh game da yadda za a fassara wannan.
A nan "karuwanci" yana wakiltar rashin amincin mutanen ga Allah.
Wadannan sunayen mutane ne.
A nan "gida" yana nufin "iyali", hade da zuriyar Yehu.
Wannan furcin yana nufin masarautar Isra'ila.
A nan "baka" tana nufin karfin mayaka. "Karfin mayakan Isra'ila"
Wannan sunan yana nufin "babu jinkai". Mai fassara zai iya nuni da wannan ma'anar a matsayin sunan. A.T: "Babu Jinkai"
Wannan sunan yana nufin "babu jinkai". Mai fassara yana iya nuni da wannan ma'anar a matsayin sunan. AT: "Babu jinkai" Duba yadda ka fassara wannan a 1:6
Wannan sunan yana nufin "ba mutanana ba". Mai fassara yana iya nuni da wannan ma'anar a matsayin sunan. AT: "Ba mutanena ba"
Yahweh yana magana da Yusha'u.
Wannan yana jadda dumbin yawan Isra'ilawa.
Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "wadda babu wani da zai iya yin awo ko ya kididdige"
Ana iya fadin wannan kai tsaye. AT: "Inda Allah ya ce musu"
Mai yiwuwa wannan furcin yana nufin Yezrel, birnin nan inda sarakunan Isra'ila suka aikata laifuffuka, wadda kuma ya zama alamancin hukuncin Allah a kansu.
Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "Allah zai ce musu"
Za a iya fadin wannan kai tsaye: AT: "Allah zai tattara su tare"
Wannan furcin yana iya nufin kasar da jama'ar Isra'ila suka yi bauta (duba UDB).
Wannan yana nufin lokacin da Allah ya maido da jama'arsa kasar Isra'ila. Za a iya fadin cikakkiyar ma'anar wannan furcin kai tsaye.
1Ku cewa 'yan'uwanku maza, 'Mutanena!' ga 'yan'uwanku mata, 'An ji tausayin ku.'"2Ku kawo ƙarar mahaifiyarku, ku kawo ƙara, gama ita ba matata ba ce, ni kuma ba mijinta ba ne. Ta kawar da karuwancinta daga gare ta da halinta na zina daga tsakanin nonnanta.3Idan ba haka ba, zan maishe ta tsirara in nuna tsiraicinta kamar a ranar da aka haife ta. Zan maishe ta kamar hamada, kamar busasshiyar ƙasa, in sa ta mutu da ƙishiruwa.4Ba zan nuna jinƙai kan 'ya'yanta ba ko kaɗan, gama 'ya'yan fasikanci ne.5Domin uwarsu dăma karuwa ce, ita wadda ta ɗauki cikinsu ta yi abin kunya. Ta ce, "Zan bi masoyana, domin suna bani abincina, da ruwa, da ulu, da gyale, da mai da abin sha."6Sabo da haka zan gina shinge in tare hanyarta da ƙayayuwa. Zan gina katanga gãba da ita don kada ta gane hanyarta.7Zata bi masoyanta, amma ba za ta cim masu ba. Zata neme su, amma ba za ta same su ba. Sa'annan za ta ce, "Zan koma wurin mijina na farko, gama a dã ya fiye mani da yanzu."8Gama ba ta sani dama ni ne na ba ta hatsi ba, da sabon ruwan inabi da mai, na kuma yawaita ta da azurfa da zinariya, wanda suke amfani da shi ga Ba'al.9Saboda haka zan karɓe hatsinta da kaka, da sabon ruwan inabina a lokacin girbi. Zan karɓe uluna da gyaluluwana da aka mora don a rufe tsiraicinta.10Zan buɗe tsiraicinta a idanun masoyanta, ba wanda zai cece ta daga hannuna.11Zan sa dukkan shagulgulanta su ƙare - bukukuwanta, shagalin tsayawar sabon wata, Asabatai, da dukkan ayyanannun bukukuwa.12"Zan lalatar da kuringar inabinta da itatuwan ɓaurenta, da ta ce, "Waɗannan su ne ladar da masoyana suka bani.' Zan maishe su jeji, namun jeji kuma za su cinye su.13Zan hore ta domin ranakun bukukuwan Ba'aloli, lokacin da ta ƙona masu turare, sa'ad da ta yiwa kanta ado da zobba da duwatsu masu daraja, ta bi masoyanta ta manta da ni -- wannan shi ne furcin Yahweh."14Saboda haka zan lallashe ta in dawo da ita. Zan kai ta cikin jeji in yi mata tattausar magana.15Zan mayar mata da gonakin inabinta, Kwarin Akor zai zama kofar bege. Nan za ta amsa mani kamar kwanakin ƙuruciyarta, kamar ranar da ta fito daga ƙasar Masar.16"Zaya zamana a ranan nan - wannan furcin Yahweh ne - za ki kira ni, 'Mijina,' kuma ba za ki ƙara kira na 'Ba'al Nawa' ba.17Gama zan fitar da sunayen Ba'aloli daga bakinta, ba za a ƙara tunawa da sunayensu ba."18A ranan nan zan yi alƙawari domin su da namun jeji, da tsuntsayen sama, da masu rarrafe a ƙasa. Zan kori bakã, da takobi, da kuma yaƙi daga ƙasar, in sa ku zauna lafiya.19Zan yi alƙawari in zama mijinki har abada. Zan yi alƙawari in zama mijinki cikin gaskiya, da adalci, da alƙawarin aminci, da jinƙai.20Zan ɗaukar wa kaina alƙawarin aminci da ke, za ki kuma san Yahweh.21A ranar nan zan amsa - wannan furcin Yahweh ne - Zan amsa wa sammai, su kuma za su amsa wa ƙasa.22Ƙasa kuma za ta amsa wa hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai, za su amsa wa Yeziril.23Zan dasa ta domin kaina a ƙasar, zan nuna jinkai akan Lo Ruhama, Zan cewa Lo Ammi, 'Ke ce Ammi Attah,' sa'annan za su ce mani, 'Kai ne Allahnmu."'
Yahweh yana magana da Yusha'u.
Za a iya gabatar da wannan kalamin a matsayin magana. AT: "Ku jama'ata ne!"
Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "Yahweh ya nuna muku juyayi"
"nagarta" ko "jinkai"
Yahweh yana magana da Yusha'u.
Wannan korafi ne da wani ya kai game da wani a kotun shari'a.
A nan, "uwa" na nufin kasar Isra'ila.
Yahweh yana fadin cewa, Isra'ila, wacce a nan aka yi magana a kanta a matsayin mace, ta daina hidimarta ta macen aure ga Allah. Maimakon haka, sai Isra'ila ta juya daga binsa da kuma yi masa sujada.
Yahweh ba zai iya ci gaba da dangantaka da kasar Isra'ila kamar yadda miji zai yi da matarsa ba.
Macen aure da take mazinaciya, tana barin mijinta, ta kwana da wani maniji. Haka Isra'ila ta rika yi wa Yahweh.
Wannan misalin yana nuna cewa Isra'ila ta dogara ga gumaka ba Yahweh ba.
Yahweh ba zai ci gaba da kare Isra'ila da kuma yi mata tanadi ba, domin kasar ta juya daga gare Shi. A Isra'ila, hakkin maza ne, bisa doka, su tanadi tufafi domin matayensu. Kin yin haka alama ce cewa namiji yana kin matarsa. Za a iya kara bayyana cikakkiyar ma'anar wannan.
Yahweh zai maida Isra'ila ta yi kama da hamada, wadda yanki ne busasshe mara amfani.
A nan, "kishirwa" na nuni da bukatar sujada da dogaro ga Yahweh, ba gumaka ba, ko kuma Isra'ila ba za ta iya rayuwa a matsayin kasa ba.
Yahweh yana magana da Yusha'u
Isra'ilawa suna yi kamar su ba na Yaheh ba ne. kamar yadda iyayensu suka ki bauta wa Yahweh, haka suke yi.
zuriyar da ta gabata, wadda ta bi wadansu alloli, an dauke su karuwai, domin sun yi Yahweh rashin aminci.
A nan, "samarina" na nufin Ba'al da sauran allolin karya, wadanda Isra'ila ta zabi ta bauta wa a maimakon Yahweh. Jerin nan na muhimman kayayyaki ne da mutane suke bukata don rayuwa.
Yahweh yana magana da Yusha'u
Wannan nassin yana nuna cewa Yahweh zai hana mutanensa samun nasara da arziki, domin su ci gaba da bautar gumaka.
Isra'ila za ta koma wurin Yahweh ba domin kunar da take yi masa ba, amma domin bautarsu ta Ba'al ba ta gamsar da su ba.
Yahweh yana magana da Yusha'u.
Wannan yana iya nufin cewa girbin Isra'ila da garkenta ba za su yi kyau ba. Yahweh zai dauke albarkarsa daga Isra'ila, kuma zai rabu da jama'ar, su kasance cikin hatsarin hari.
Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "wadanda mutanen suka mora wajen sutura kansu".
Yahweh yana magana da Yusha'u.
Wannan yana nufin cewa Allah zai wulakanta jama'ar Isra'ila a gaban makwabtan kasashen. Duba yadda ka fassara wannan a 2:2.
Babu wanda zai yi yunkurin taimakon Isra'ila. A nan "hannu" yana nuni da ikon Allah na hukunci.
Yahweh yana magana da Yusha'u game da abin da zai yi wa Isra'ila.
Wannan yana nuni da ladan da Isra'ila ta samu daga bautar allolin karya ko Ba'al. Wannan nassi da aka dauko kai tsaye, anan iya fadin shi a fakaice. AT: "wadannan su ne hakkin da masoyanta suka ba ta".
Yahweh zai hallaka gonakin inabinta da 'ya'yan itatuwanta ta wurin barin wadansu itatuwa da ciyayi su yi girma a cikinsu.
"abin da Yahweh ya shaida" ko "abin da Yahweh ya rantse"
Yahweh yana magana game da Isra'ila.
"Ni, Yahweh, zan maido da ita zuwa wurina"
Yayin da Yahweh ya jagoranci Isra'ila daga Masar, zai kai Isra'ila Kwarin Akor, domin Isra'ila ta sake kafa begenta ga Yahweh. Kwarin Akor ne wurin da jama'ar Isra'ila suka jejjefi Achan har ya mutu, bisa ga umurnin Allah, domin Achan ya yi rashin biyayya da umurnin Allah. Za a bayyana cikakkiyar ma'anar wannan kai tsaye.
Yahweh yana begen cewa kasar Isra'ila za ta tuba, ta sake zabar ta bauta masa a matsayin Allahnta.
Wadansu sabobbin juyi sun fahimci kalmar Ibraniyanci a matsayin tana nufin "Za ta raira"
Wannan yana nuni da ranar da Isra'ila ta zabi ta bauta wa Yahweh Shi kadai.
"abin da Yahweh ya shaida" ko "abin da Yahweh ya rantse". Duba yadda ka fassara wannan a 2:12.
Wannan yana nufin jama'ar Isra'ila za su kaunaci Yahweh, su yi masa aminci, kamar yadda mace take yi wa mijinta.
"Ba'al" yana nufin "ubangida", kuma yana nuni da allahn karya da Kan'aniyawa suke bauta wa.
Isra'ilawa ba za su sake ambaton sunayen Ba'al da gumaka ba kuma.
Yahweh yana magana da Yusha'u game da abin da zai yi wa Isra'ila.
Ana morar wannan furcin don magana game da lokaci mai zuwa na maido da dangantaka tsaknin Isra'ila da Yahweh.
Sabon alkawarin Yahweh zai hada da zaman lafiya na dabbobi.
Yahweh zai nisanta magabtan Isra'ila daga gare su, ba za a sake yaki ba, jama'ar za su yi zaman lafiya.
Wannan furcin yana nuni da zaman lafiya.
Yahweh yana magana da Yusha'u game da abin da zai yi domin Isra'ila.
Yahweh zai zama kamar mijin, Isra'ila kuma za ta zama kamar matar Yahweh.
Yahweh zai yi aminci ga alkawarinsa da Isra'ila.
"amintaccen miji"
A nan "sani" yana nufin gane Yahweh a matsayin Allahnsu, da kuma yi masa aminci.
Yahweh yana magana da Yusha'u game da abin da zai yi domin Isra'ila.
"abin da Yahweh ya shaida" ko "Yahweh ya rantse". Duda yadda ka fassara wannan a 2:12.
Kasa za ta biya bukatar hatsi, sabon inabi, da man zaitun. Wadannan abubuwan za su biya bukatun Yezreyel kuma. Ana maganar kasar da wadannan abubuwan tamkar su mutane ne wadanda za su biya bukatun wadansu.
A nan, sunan wannan kwarin yana nufin dukkan jama'ar Isra'ila.
Yahweh yana magana da Yusha'u game da abin da zai yi domin Isra'ila.
Sa'adda Allah ya kiyaye jama'arsa lafiya, ya arzuta su a kasarsu kuma, ana maganrsu kamar amfanin gona. AT: "Zan kula da jama'ar Isra'ila kamar yadda manomi yake shuka kayayyakin gona ya kula da su" (UDB).
Wannan sunan yana nufin "ba jinkai". Mai fassara yana iya zaben ya nuna wannan ma'anar a matsayin sunan. Duba yadda ka fassara wannan a 1:6. AT: "Ba Jinkai"
Wannan sunan yana nufin "ba mutanena ba". Mai fassara zai iya morar wannan ma'anar a matsayin sunan. Duba yadda ka fassara wannan a 1:8. AT: "Ba Mutanena Ba"
Wannan sunan yana nufin "ku mutanena ne". Mai fassara yana iya morar wannan ma'anar a matsayin sunan. AT: "Ku Mutanena ne".
1Yahweh yace mani, "Jeka har wa yau, ka ƙaunaci wata mata wadda kaunatacciya ce ga mijinta, amma mazinaciya ce. Ka ƙaunaceta kamar yadda Ni, Yahweh, na ke ƙaunar mutanen Isra'ila, ko da yake sukan juya zuwa ga bin waɗansu alloli, suna ƙaunar wainar 'ya'yan itatuwa."2Sai na saye ta domin kaina a bakin azurfa sha biyar da hatsi tiya guda da rabin bali.3Na ce mata, "Dole ne ki zauna da ni kwanaki da yawa. Ba za ki zama karuwa ba, ko ki zama ta wani mijin ba. Haka nima kuma zan kasance a gare ki."4Gama mutanen Isra'ila za su kasance kwanaki da yawa ba sarki, ba kuma ɗan sarki, ba hadaya, ba bagadin dutse, ba falmara ko gumakan gida.5Daga baya mutanen Isra'ila za su juyo su nemi Yahweh Allahnsu da sarkinsu Dauda, kuma a kwanakin ƙarshe, za su zo da rawar jiki gaban Yahweh da alheransa.
Wannan yana nuni da 1:1. Yahweh yana sake fada wa Yusha'u kuma cewa ya kaunaci mazinaciyar mace.
Ta wurin kaunar mazinaciyar macen nan, Yusha'u zai zama misalin kaunar Yahweh domin Isra'ila.
Mutane suna cin wainar zabibi ko ta baure a lokutan bukukuwa, inda suke bautar allolin karya.
Wannan shi ne farashin sayen bawa.
"tsaba 15"
"buhun sha'ir biyu"
Kamar yadda Yusha'u ya zauna babu mata, don tana aikata zina, Isra'ila za su zauna babu sarki, babu bautar Allah, domin suna aikata zina.
A nan "nema" yana nufin suna rokon Allah ya karbe su da sujadarsu.
A nan "Dawuda" yana nuni da dukkan zuriyar Dawuda. AT: "wani zuriyar Dawuda ya zama sarkinsu"
A nan "kwanaki na karshe" yana nuni da wani lokaci a nan gaba. AT: "a nan gaba"
A nan "tsoro" yana nufin ban al'ajibi da tawali'u. AT: "za su komo wurin Yahweh su kaskantar da kansu, su girmama shi, su bidi albarkunsa".
1Ku ji maganar Yahweh, ku mutanen Isra'ila. Yahweh yana da ƙara game da mazaunan ƙasar, domin babu gaskiya ko alƙawarin aminci, babu sanin Allah a ƙasar.2Akwai la'antarwa, ƙarya, kisa, sata da zina. Mutanen sun zarce dukkan iyaka, ana zubda jini kan zubda jini.3Saboda haka ne ƙasar take bushewa, dukkan mazaunanta kuma suna yanƙwanewa; dabbobin jeji da tsuntsayen sama, har ma da kifayen dake a teku, ana kawar dasu.4Amma kada ka bari ko guda ɗaya ya kawo ƙara; kada ka bari wani ya zargi wani. Domin ku firistoci kune nake zargi.5Ku firistoci za ku yi tuntuɓe da rana, annabawa kuma za su yi tuntuɓe tare da ku da dare, zan kuma hallaka mahaifiyarku.6Ana hallaka mutanena saboda rashin ilimi. Saboda ku firistoci kun ƙi ilimi, nima zan ƙi ku zama firistocina. Domin kun manta da dokokina, ko da yake ni Allahnku ne, nima zan manta da 'ya'yanku.7Yadda firistocin suke ƙaruwa, haka ma zunuban da suke yi mani. Sukan misanya ɗaukakarsu da kunya.8Suna ci daga zunuban mutanena; suna da zarin mugunta da yawa.9Zai zama ɗaya saboda mutane da kuma firistoci: Zan hukunta su dukka saboda al'amuransu, zan saka masu saboda ayyukansu.10Za su ci amma ba zai ishe su ba; za su yi karuwanci, amma ba za su ƙaru ba, domin sun yi nisa da Yahweh.11Suna ƙaunar fasiƙanci, ruwan inabi, da sabon ruwan inabi, wanda yake ɗauke fahimtarsu.12Mutanena suna neman shawara daga gumakun itacensu, sandar tafiyarsu kuma na basu anabce - anabce. Domin tunanin fasiƙanci ya ɓadda su, sun aikata karuwanci maimakon su zama da aminci ga Allahnsu.13Suka miƙa hadayu a ƙwanƙolin duwatsu, suka ƙona turare bisa tuddai, ƙarƙashin rimaye, foflas da tsamiya, domin inuwar tana da daɗi. Sai 'ya'yanki mata suka yi lalata, surukanki mata kuma suka yi zina.14Bazan hori 'ya'yanki mata ba sa'ad da suka zaɓi suyi fasiƙanci, ko surukanki mata idan suka yi zina. Domin maza ma suna bada kansu ga karuwai, suna miƙa hadayu domin su yi lalata da keɓaɓɓun karuwai. Waɗannan mutane da basu da ganewa zan fyaɗa su ƙasa.15Koda yake Isra'ila kin yi zina, bari Yahuda ma kada ta yi saɓo. Ku mutane, kada ku tafi Gilgal, kada ku haye zuwa Bet Aben, kada kuma ku rantse kuna cewa, "Yahweh hakika mai rai ne."16Gama Isra'ila ta yi taurin kai, kamar karsana mai gardama. Ƙaƙa Yahweh zai kawosu makiyaya kamar 'yan tumaki wurin kiwo?17Ifraim ya haɗa kansa da gumaka; ku ƙyale shi.18Harma idan barasarsu ta ƙare, sukan ci gaba da zinarsu, masu mulkinsu suna amincewa da kunyarsu ƙwarai.19Iska za ta nannaɗe ta cikin fukafukanta; za su kuma ji kunya saboda hadayunsu.
Wannan surar ta fara da korafin Yahweh a kan Isra'ilawa marasa aminci.
Maganar Yahweh cewa mutanen Isra'ila sun yi masa zunubi, sun karya alkawarinsa, an yi ta kamar Yahweh yana yin kararsu a kotun shari'a.
Wannan kara ce da wani ya kai a kan wani a kotun shari'a. Duba yadda ka fassara wannan a 2:2.
A nan "iyaka" yana nufin sun keta dukkan abin da doka ta tanadar. AT: "mutanen sun karya doka ta kowace hanyar da za a iya tsammani".
A nan "zub da jini" yana nufin "kisa" wanda sau da yawa yakan zubar da jinin wanda aka kashe. AT: "kuna kisan kai bayan kisan kai" (UDB).
Wannan furcin yana nufin fari, sa'adda ruwa ya daina saukowa har lokaci mai tsawo.
kasancewa da kasala da mutuwa saboda cututtuka ko rashin abinci
Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "suna mutuwa".
Yahweh yana magana game da Isra'ila.
wata kara wadda wani ya kai game da wani a kotun shari'a
Kada kowa ya tuhumi wani game da wani abu, domin kowa yana da laifin wani abu.
A nan "tuntube" yana nufin rashin biyayya ga Allah ko ma daina dogara gare Shi.
A nan "mahaifiya" na nuni da kasar Isra'ila. Duba yadda ka fassara wannan a 2:2.
A 4:6 Yahweh yana magana da fristoci game da jama'ar Isra'ila. Amma a 4:7, yana magana game da firistocin, ba su ba. mai yiwuwa ne ga mai fassara ya bi misalin UDB, wanda ke nuna Yahweh yana magana da firistoci kuma a 4:7.
za a iya fadin wannan kai tsaye. A.T: "Jama'ata suna hallaka domin ku, firistoci, ba ku koyar da su sosai game da ni, yadda za su yi mini biyayya ba".
A nan, "sani" yana nufin sanin Allah.
Ma'anar tana iya zama 1) "daraja" kamance ne da ke wakiltar Yahweh, sa'annan "kunya" kamance ne mai wakilcin gumaka. A.T: "Sun daina yi mini sujada, Ni Allahnsu mai girma, yanzu suna bautar gumaka" ko 2) wadansu juyin Littafi Mai Tsarki sun fassara wannan zuwa "zan sake darajarsu da kunya". Wannan yana nufin Yahweh zai dauke abubuwan da firistoci suke darajantawa, ya sa firistocin su ji kunya.
Yahweh ya ci gaba da magana game da firistoci.
Sa'adda mutane suka yi zunubi, za su mika hadayu domin Allah ya gafarta musu. An ba wa firistoci daman cin wadannan hadayun. cin wadannan hadayun zunubin da firistoci suke yi shi ne aka bayyana kamar suna ciyar da kansu a zahiri da zunuban mutanen.
Firistoci suna so mutanen su kara zunubi domin mutanen za su kara yawan hadayun da firistocin za su ci.
"Mutanen da firistocin za su fuskanci hukunci iri daya"
"halayensu" ko "ayyukansu"
Yahweh yana magana game da Isra'ila.
"ba za su sami 'ya'ya ba"
Mutanen sun daina bauta da kuma bin Allah.
Mai fassara yana iya canza "Yahweh" zuwa "ni", domin Yahweh ne mai magana. Sake duba UDB.
Yahweh yana magana game da Isra'ila.
Jama'ar Isra'ila suna aikata lalata ta zina, suna buguwa da ruwan inabi. Ta wurin aikata wadannan ayyukan, sun manta da umurnan Yahweh. Ana maganar wadannan ayyukan a nan kamar sun zama wani wanda zai iya jama'ar fahimtar muhimmancin yi wa Yahweh biyayya.
Masu bautar gumaka suna amfani da sandunan tafiya don su taimake su sanin abin da zai faru nan gaba. A nan, ana maganar sandunan kamar mutane ne masu fadar anabci.
Bautar gumaka da kuma kwana da karuwai na haikali ya habaka marmari a zuciyar mutanen Isra'ila na yi wa Yahweh aikata zunubi kowane lokaci a wadannan hanyoyin. A nan, ana magana "ruhu" ko "tunani" kamar wani ne dabam wanda ya yaudari jama'ar su yi wa Yahweh rashin biyayya.
ya yaudare su sun aikata zunubi
Yahweh yana magana game da Isra'ila.
Mutanen su saba kafa gumaka a wadannan wuraren, wanda akan kira "manyan wurare" a Tsohon Alkawari.
Wadannan mata ne masu aikata jima'i da mzana da suka zo bautar wadansu gumaka. An dauki wannan a matsayin wata ibada ce ta bangirma ga allolin karyan nan.
Yahweh zai hallaka kasar Isra'ila domin ba su fahimci umurnan Allah ko su yi biyayya da su ba.
Yahweh yana magana game da Yahuza da Isra'ila.
Allah ya san yadda Isra'ila ta cika da zunubi, kuma ba ya so Yahuza ta aikata irin wannan sha'anin.
An yi wa mutanen Yahuza kashedi cewa, kada su tafi biranen Gilgal ko Bet-awen don bautar gumaka a wadannan wuraren. A da, Gilgal wuri ne inda ake yi wa Yahweh sujada, amma ya zama wurin bautar gumaka.
Wannan birni ne a kan iyaka tsakanin masarautar arewa ta Isra'ila da kabilar Bilyaminu a masaautar kudu.
An kwatanta Isra'ila da dan alfadari da ba ya yi wa ubangidansa biyayya.
Yahweh yana amfani da tambaya wajen jaddada cewa ba zai ci gaba da kula da |isra'ila ba, domin suna da taurin kai. An yi maganar yadda Yahweh ya daina kula da mutanensa kamar shi makiyayi ne wanda ba zai kula da tumakinsa a makiyaya ba, domin suna da taurin kai. A.T: "Yahweh ba zai zama makiyayin mutane masu tawaye ba" ko "Saboda haka, Yahweh ba zai ci gaba da kulawa da su ba".
A nan, Yahweh yana magana game da kansa kamar wani ne dabam. Za a iya fadin maganar kamar shi yake yin ta. A.T: "Yaya ni zan".
Yahweh yana magana game da Isra'ila.
A nan, "Ifraimu" yana nufin jama'ar masarautar arewacin Isra'ila. Sun zabi su bauta wa gumaka, maimakon Yahweh. Yahweh yana umurtar Yusha'u kada ya yi kokarin tsautar musu. Jama'ar Isra'ila ba za su saurara ba.
Shugabannin ba su jin kunyar abin da suke aikatawa sa'adda suke bautar gumaka suna juya wa Yahweh baya.
A nan, "iska" tana nufin hukuncin Allah da fushinsa a kan kasar Isra'ila. Yahweh zai kyale mayakan abokan gaba su yi nasara kan jama'ar Isra'ila, su dauke su bayi.
1Ku ji wannan ku firistoci! Ku natsu, gidan Isra'ila! Ku kasa kunne, gidan sarki! Domin hukunci na zuwa bisa kanku dukka. Kun zama tarko a Mizfa tarun da aka baza akan Tabor.2'Yan tawaye sun dage da hallakarwa, amma zan hukunta dukkansu.3Na san Ifraim, Isra'ila kuma ba a ɓoye take a gare ni ba. Ifraim yanzu kin zama kamar karuwa; Isra'ila ta ƙazantu.4Ayyukansu ba za su barsu su juyo ga Allah ba, domin tunanin zina yana cikinsu, ba su kuwa san Yahweh ba.5Girman kan Isra'ila yana shaida a kansu, saboda haka Isra'ila da Ifraim za suyi tuntuɓe cikin laifinsu. Yahuda ma zai yi tuntuɓe tare dasu.6Zasu tafi tare da garkunansu na tumaki dana shanu su biɗi Yahweh, amma baza su same shi ba, gama ya rigaya ya janye kansa daga gare su.7Sunyi rashin aminci ga Yahweh, domin sun haifi 'ya'yan haram. Yanzu bukukuwan sabon wata zai cinyesu dasu da gonakinsu.8Ku busa ƙaho a Gibiya, da kakaki a Rama. Ku tada kururuwar yaƙi a Bet Aben: 'Za mu bi ki Benyamin!'9Ifraim zata zama kango a ranar hukuncinta. Na yi shelar abin da zai faru lallai a cikin ƙabilar Isra'ila.10Shugabannin Yahuda suna kama da masu kawar da dutsen kan iyaka, zan zuba hasalata a kansu kamar ruwa.11An murƙushe Ifraim; an danne shi a shari'a domin da yardar rai ya bi gumaka.12Saboda haka zan zama kamar asu ga Ifraim, kuma kamar tsatsa ga gidan Yahuda.13Da Ifraim ya ga cutarsa, Yahuda ma ya ga rauninsa, sai Ifraim ya tafi Asiriya, Yahuda kuwa ya aiki jakadu wurin babban sarki. Amma bai iya warkar da mutanen ku ba, bai kuma iya warkar da raunukanku ba.14Saboda haka zan zama kamar zaki ga Ifraim, kuma kamar dan zaki ga gidan Yahuda. Ni, I, Ni' kaina zan kekketasu in yi tafiya ta; zan kwashe su; ba kuma wanda zai cecesu'15Zan tafi in koma wurina, har sai sun yarda su karɓi laifinsu su kuma biɗi fuskata, sai kuma sun biɗe ni da aniya cikin ƙuncinsu."
Yahweh yana magana game da Isra'ila.
Tarko da raga, duk ana amfani da su wajen kama dabba. A wannan yanayin, firistoci da gidan sarauta sun kirkiro dabarun nisanta jama'a daga Yahweh, yayinda suke yaudararsu zuwa ga bautar gumaka. Mizfa da Tbor wurare ne na bautar gumaka a kasar Isra'ila.
A nan "masu tawaye" yana nufin dukkan mutanen da suka juya wa Yahweh baya, sa'annan "zurfi cikin kisa" yana nufin zub da jinin mutane marasa laifi, ko yanka dabbobin da akan yi hadaya da su a bautar gumaka.
Mai fassara yana iya bayyana wannan a matsayin, "Ku masu tawaye", domin Allah yana magana ne da jama'a masu tawaye na Isra'ila.
Wadanus juyi na zamani sun fassara kalmar Ibraniyancin a matsayin mugunta.
Mai fassara yana iya bayyana wannan a matsayin "Zan hore ku duka".
Yahweh yana magana game da Isra'ila.
A nan, "Ifraimu" da "Isra'ila" duk suna nufin mutanen da suke zaune a masarautar arewa ta Isra'ila. A nan, Allah yana cewa ya san yadda suke da kuma abin da suke yi.
Ana gabatar da Ifraimu a matsayin karuwa, domin mutanen sun yi wa Allah rashin aminci, kamar yadda karuwa ba ta da aminci ga kowane mutum.
Wannan yana nufin suna da sha'awar yi wa Allah rashin aminci. Suna marmarin bautar gumaka.
Mai fassara zai iya bayyana wannan a matsayin "su komo wurina... ba san ni ba", ko "su juyo wurina... ba su san ni ba, Yahweh".
Isra'ila ta daina yi wa Yahweh biyayya a kowace hanya. Ba su dauki Yahweh a matsayin Allahnsu ba.
Yahweh yana magana game da Isra'ila.
Wannan yana bayyana "girman kai" a matsayin mutum wanda yake ba da shaida a kan mutanen Isra'ila a kotu. Halayyarsu ta girman kai ta nuna cewa suna da laifin daina yi wa Yahweh biyayya.
Masarutun nan biyu za su yi wa Allah rashin biyayya gaba daya saboda girman kansu da zunubinsu.
Ma'anar tana iya zama 1) wannan yana nufin cewa Isra'ilawa suna aure daga wadansu al'ummai, suna haifan yara tare da su, ko 2) wannan yana nufin iyayen Isra'ilawa sun ci amanr yahweh, kuma suna koya wa 'ya'yansu bautar gumaka.
Ya kamata mutanen Isra'ila su yi buki a lokacin sabuwar wata. A nan, kamar wannan maganar bayyana amaryara wata a matsayin muguwar dabbara da za ta cinye jama'a da gonakinsu. Amma, yana da wuya a fassara wannan maganar; juyi da yawa sun fassara ta ba a bayyane sosai ba. Amma, ma'anar dai gaba daya ita ce, hakika Allah zai hori jama'ar Isra'ila domin rashin amincin da suka yi masa.
Yahweh yana magana game da Isra'ila.
A nan, "kaho" da "kakaki" suna nufin abu daya. An ba da wannan dokar ga mutanen Gibiya da Rama don a jaddada cewa abokin gaba yana nan tafe.
Mai yiwuwa wannan roko ne cewa mayakan kabilar Bilyaminu za su jagoranci jama'a zuwa yakin. Amma sabobbin juyi sun yi kokarin fassara wannan maganar a hanyoyi da yawa.
Wanna ne birnin da ke kan iyaka tsakanin masarautar arewa ta Isra'ila da kabilar Bilyaminu a masarautar kudu. Duba yadda ka fassara wannan a 4:15.
"Zan yi wa kabilun Isra'ila abin da na yi shela"
Yahweh yana magana game da Yahuza da Isra'ila.
"Kawar da dutsen kan iyaka" yana nufin kawar da alamar da ta bambanta kan iyakar kasa, wanda laifi ne bisa ga dokar Isra'ila.
Fushin Yahweh a kan Yahuza zai zama kamar babbar magudanar ruwar da za ta hallaka su. A cikin nassi, akan yi maganar jin-zuci da halin da'a kamar suna da yanayin ruwa.
Za a iya fadin wannan kai tsaye. An yi wannan furcin sau biyu don a jaddada batun. A nan "Ifraimu" yana nufin mutanen masarautar arewaci ta Isra'ila. A.T: "Zan yi wa mutanen Isra'ila horo mai tsanani".
A nan, "bi" yana nuni da sujada.
Kalmar Ibraniyanci da aka fassara a nan a matsayin "gumaka", ba a tabbatar da ma'anarta ba, kuma sabobbin juyi sun fassara ta a hanyoyi da yawa.
Yahweh yana magana game da Yahuza da Isra'ila.
Asu a kan ulu da ruba a kan katako, duk suna da ta'adi. Yahweh zai hallaka duk kasashen biyu.
Wadannan kalmomi biyu, an fassara su a hanyoyi da yawa, domin ma'anar kalmar Ibraniyancin yana iya zama da fadi sosai ko kuma ma ba a tabbatar da ita ba.
Da Ifraimu (masarautar arewa ta Isra'ila) da Yahuza (masarautar kudu ta Isra'ila) sun gane cewa suna cikin hatsari.
Ifraimu da Yahuza sun roki taimako daga Assuriya, maimakon neman taimakon Yahweh. "Babban sarki" wani take ne na sarkin Assuriya.
A nan, "ba zai iya ba" yana nufin sarkin Assuriya.
Yahweh yana magana game da Yahuza da Isra'ila.
Yahweh zai faffari Ifraimu, ya kai mata hari kama zaki.
Yahweh zai yi Yahuza irin abin da ya yi wa Ifraimu. Yahweh yana nuna rashin jin dadinsa da dukkan masarautun arewa da kudu.
Yahweh yana jadda cewa shi ne zai kawo hukunci a kan dukkan mutanensa.
Kamar yadda zaki yage yayyage dabbar da yake ci, haka Yahweh zai yayyage mutanensa daga gidajensu da garuruwansu.
Yahweh zai rabu da mutanensa masu tawaye.
Su yi kokarin zuwa wurin Allah ta wurin sujada da hadaya. A.T: "su roke ni in maida hankalina a kansu".
1"Zo, mu koma gun Yahweh, gama ya yayyaga mu, amma zai warkar da mu; ya ji mana rauni, amma zai ɗaure mana raunukanmu.2Bayan kwana biyu, zai farkar da mu; zai tashemu a rana ta uku, zamu rayu kuma a gabansa.3Bari mu san Yahweh, bari mu ƙara nacewa mu san Yahweh. Zuwansa tabbataccene kamar wayewar gari. Zai zo wurinmu kamar ruwan sama, kamar ruwan ƙarshe mai jiƙa ƙasa.4Ifraim me zan yi da ke? Yahuda, me zan yi da ke? Amincinki kamar gajimaren safe ne, kamar raɓar da take kaɗewa da wuri.5Saboda haka na daddatse su ta wurin annabawansu, na kashesu da maganganun bakina. Umarninka kamar haske ne mai sheƙi.6Gama ina biɗar aminci ne ba hadaya ba, da kuma sanin Allah fiye da hadayun ƙonawa.7Kamar Adamu sun karya alƙawari; sun yi mani rashin aminci.8Giliyad birnin mugaye ne mai sawun jini.9Kamar yadda taron mafasa suke wa mutum kwanto haka ƙungiyar firistoci suke haɗa kai su yi kisa a hanya zuwa Shekem; sun aikata laifofi masu ban kunya.10A cikin gidan Isra'ila na ga mummunan abu; karuwancin Ifraim na nan, Isra'ila kuma ta ƙazantu.11Ke kuma, Yahuda, an ƙaddara miki girbi, sa'ad da zan mayar wa mutanena albarkunsu.
Jama'ar Isra'ila sun furta bukatarsu ta tuba.
Allah ya hori jama'ar Isra'ila domin sun masa rashin biyayya, sun bauta wa gumaka. (Duba: bayanai_iri daya)
Isra'ila ta yi imanin cewa Allah zai nuna musu jinkai sa'adda suka tuba, kuma zai kubutar da su daga masifunsu.
Wannan yana nui da takaitaccen lokaci. Isra'ila ta yi imanin cewa Allah zai gaggauta zuwa cetonsu daga abokan gabansu.
"kwana 2... rana ta 3"
A nan, "sani" ba sanin dokoki da halin Allah kadai yake nufi ba, amma kuma kasancewa da aminci gare shi. (Duba: UDB)
Yahweh zai zo ya taimaki jama'arsa kamar yadda tabbasa rana take tashi kowace safiya.
Yahweh yana magana.
Allah yana nuna cewa hakurinsa ta kawo karshe, kuma abin da ya rage kawai shi ne hukunci. A.T: "yana da wuya sanin abin da za a yi da ku!"
Ta wurin annabawansa, Yahweh ya yi shelar hallakarwa a kan kasar nan mai tawaye. Hallakarwar, wanda a nan aka kira "sassarewa", tabbasa ne kamar hukuncin.
A nan, Yusha'u yana magana da Allah. Mai yiwuwa yana nufin cewa sa'adda Allah ya yi shelar doka don wani ya mutu a matsayin hukunci, yana kama da ketowar walkiya mai bugu (duba UDB). Ko kuma, watakila yana nufin cewa dokokin Allah suna ba mutane damar sanin gaskiya, kamar yadda haske yakan haskaka abubuwa.
"Dokokin Yahweh"
Yahweh yana magana.
Wanna salon furci a harshen Ibraniyanci, a nan, yana nuna "fiye da", kamar yadda layi na biye ya nuna ("sanin Allah kuma fiye da hadayu na konawa"). A.T: "Gama aminci na fi so siye da hadaya".
Ma'anar tana iya zama 1) wannan yana nufin Adamu, mutum na farko, ko 2) wannan kamance ne mai nuni da mutanen da suke zaune a birnin Isra'ila da ake kira Adam. A.T: "Kamar mutanen da suke birnin Adam", ko 3) wannan yana nufin mutane gaba daya. Kalmar "Adam" tana nufin "mutum" ko "bil'adama. A.T: "Kamar dukkan bil'adama".
Yahweh yana magana.
Watakila "tabban jini" yana nufin mugayen mutane da ayyukansu na zub da jini.
Ba mu san abin da wannan yake nuni da shi ba. Ko dai , a zahiri, firistoci suna da laifin kai wa mutane hari a kan hanyarsu zuwa Shekem, wanda muhimmiyar cibiya ce ta addini da siyasa? Ko kuma annabin yana cewa firistocin sun "kashe" sani da bautar Yahweh? Ya fi kyau a fassara wanan furcin a bayyane sosai iyakar gwargwado.
Yahweh yana magana.
A nan, "karuwanci" yana nufin bautar allolin karya da Ifraimu take yi.
Isra'ila ta zama mara karbuwa a gun Allah saboda ayyukanta.
Za a iya fadin wannan kai tsaye. A.T: "Na tsai da ranar girbi dominku ku ma, Yahuza".
A nan, "girbi" yana nuni da hukuncin Allah na karshe a kan Isra'ila da Yahuza.
arziki da tsaro
1Duk lokacin da nake so in warkar da Isra'ila, sai zunuban Ifraim su bayyana, haka kuma mugayen ayyukan Samariya, domin suna shirya yaudara; ɓarawo ya kan shigo, mafasa kuwa su kai hari a titi.2Basu sani ba a zukatansu ina sane da dukkan mugayen ayyukansu. Yanzu ayyukansu sun kewayesu; suna nan a fuskata.3Da muguntarsu suke faranta wa sarki rai, hakimai kuma da ƙarairayi.4Dukkansu mazinata ne, kamar tanderun wuta da mai tuya ya dena zuga wutar daga lokacin kwaɓa curi zuwa lokacin sa gami.5A ranar sarki, hakimai suka sa wa kansu ciwo da ƙunar barasa. Ya miƙa hannunsa ga masu yin ba'a.6Da zuciya kamar tanderu suna ƙirƙiro dabarun ƙarya. Fushinsu; na ƙuna da dare, da safe yakan tashi kamar harshen wuta.7Duk suna da zafi kamar tanderu, suna kuma hallakar da masu mulkinsu. Dukkan sarakunansu sun faɗi; ba wanda yake kira na.8Ifraim ya na cuɗanya da al'umma. Ifraim waina ne mai faɗi da ba a juya shi ba.9Bãƙi sun cinye ƙarfinsa, amma bai sani ba. An yayyafa furfura a kansa, amma bai sani ba.10Girman kan Isra'ila na shaida gãba akansa a; duk da haka basu dawo ga Yahweh Allahnsu ba, basu kuma neme shi ba duk da waɗannan abubuwa.11Ifraim kamar kurciya yake, mara wayo, ba hankali, yana kiran Masar yana firiya zuwa Asiriya.12Sa'ad da suka tafi, zan baza ragata a kansu, zan jawo su ƙasa kamar tsutsayen sama. Zan hukunta su a tarayyarsu.13Kaiton su! Domin sun gudu daga gare ni. Hallaka tana zuwa kansu! Sun yi mani tawaye! Dã na cece su, amma sun yi mani ƙarya.14Basu yi mani kuka da dukkan zuciyarsu ba, amma a kan gadajensu suke rusa kuka. Suna taruwa domin hatsi da sabon ruwan inabi, sun juya daga gareni.15Ko da yake ni na koyar dasu na kuma ƙarfafa hannuwansu, amma yanzu suna ƙulla mani mugunta.16Sun dawo, amma ba su dawo wurina ba, Mafi Ɗaukaka. Suna kama da bakan da ya saki. Hakimansu za su fãɗi da kaifin takobi, saboda hasalar harshensu. Wannan zai jawo masu ba'a cikin kasar Masar.
Yahweh yana magana.
Sa Isra'ila ta yi biyayya da Allah kuma, su zama masu samun albarkunsa, an yi maganr kamar warkarwa ce.
Wadannan mutanen suna saye da sayarwa da rashin gaskiya.
Wannan kungiya ce ta mutane masu kai wa wadansu mutane hari babu dalili.
Mai yiwuwa ana maganar miyagun ayyukan mutanen a nan kamar wadansu mutane ne da suke shirye don su tuhume su da laifuffukansu.
"Ina ganinsu" yana nufin kasancewar Allah, ko kuma sanin Allah. "Shaidun", wato, miyagun ayyukan, suna a gaban Allah domin su kawo kararsu.
Yahweh yana magana. Nassin Ibraniyancin ba a bayyane yake sosai a wadansu wurare ba. Amma, mutane da yawa suna fassara shi a matsayin yana bayyana jami'an masarauta a amatsayin maciya amanar Allah, kuma suna shirin kashe sarki, sa'annan su aiwatar da shirye-shiryensu. Kamar wannan al'amarin ya faru fiye da sau daya. An ambaci wadannan laifuffukan kamar kwatanci ne na muguntar da kasar ta dulmuya kanta a cikin.
Mutanen sun aikata zina ta ruhaniya ta wurin bautar gumaka da cin amanar Yahweh. Mai yiwuwa ma suna cin amanar mazajensu ko maayensu ta wurin kwana da wadansu mutane.
Za a iya furta wannan kai tsaye. Wannan yana nufin mutanen suna da zafin sha'awar aikata mugunta. A.T: "kamar tandan da mai yin gurasa ya zafafa".
Wannan wani mataki ne na yin gurasa.
Mai yiwuwa wannan buki ne da sarki yake yi.
Watakila wannan yana nufin hadewa ko cudanya da wani. Yana iya nufin cewa sarkin yana hada kai da jami'ansa wajen yin ba'a kan abubuwa ko mutanen da bai kamat a ayi wa ba'a ba, har Allah kansa.
Ana bayyana makarkashiyar jami'an fadar sarki. Fushinsu ne ya ingiza su don su kashe sarkinsu.
Wannan yana nufin kamar yadda wuta take kuna a tanderu, mutanen nan suna da zafin kishin mugunta a cikinsu.
Kalmar "ci dare farai" tana nufin abin da ke kuna ba tare da harshen wuta ba. A.T: "fushinsu yana ta girma a hankali, a boye".
Ana maganar zafin fushinsu kamar wuta mai zafin gaske ne. A.T: "yakan zafafa kwarai".
Wannan yana kwatanta fushinsu da zafin da ke zuwa daga tanderu.
Kamar wannan yana nufin jami'an fadar sarki suna kashe sarakansu.
Yahweh yana magana.
Mai yiwuwa wannan nuni ne ga yunkurin da sarkin masarautar arewa ya yi na hada kawance da sauran al'ummai domin neman kariya daga hari.
Za a iya fadin wannan kai tsaye. A nan, "Ifraimu" tana nufin masarautar arewa ta Isra'ila. Kasar ba ta da karfi, kamar wainar da ba a juya a tanderu domin ta yi karfi ba. A.T: "Mutanen Ifraimu suna kama da wainar da babu wanda ya juya".
A nan, "furfura", tana wakilcin tsufa.
Amma, wannan "tsufa" hanya ce ta fadin cewa masarautar arewa ta rasa karfi a kai a kai, domin kasar ba ta sani cewa ta "tsufa" ba.
Yahweh yana magana.
Wannan yana bayyana "girmankai" kamar mutum wanda yake kai karar mutanen Isra'ila a kotu. Wannan yana nufin halinsu na girmankai ya nuna cewa suna da laifin rashin biyayya ga Yahweh.
A nan maganar rashin marmarin Isra'ila na neman Yahweh kamar ya bata ne, kuma ba su da niyyara neman shi. A.T: "ba su kuwa yi kokarin neman shi don ya maida hankalinsa a kansu ba".
A nan, "haka", tana nufin yadda Allah ya bar baki suka yi nasara a kansu, suka rage karfinsu.
An dauki kurciya a matsayin tsuntsu mara wayo.
Wadannan manyan kasashe ne masu karfi da Israila za ta iya neman taimakonsu.
Yahweh yana magana.
Wannan hanyar kama tsuntsu ce. Yahweh ya ci gaba da kwatanta jama'ar Isra'ila da kurciya. Sa'adda suka tafi wurin Masar ko Assuriya neman taimako, Yahweh zai hore su.
Yahweh yana maganar hanyar da zai hukunta Isra'ila kamar su tsuntsaye ne da zai kama da raga. A.T: "Zan farauce su kamar tsuntsaye" ko "Zan kama su kamar yadda mafarauci yakan kama tsuntsaye".
Wannan furcin ci gaba ne na kamancen tsuntsayen.
Yahweh yana magana.
Masu bautar gumaka sun saba cin abincin bukukuwa yayinda suke hutawa a kan kujeru ko gadaje.
A nan, ana maganar daina bauta wa Allah kamar juyawa daga gare shi. "suna daina yi mini sujada".
Mai yiwuwa wannan kamance yaki ne, inda ake maganar yadda Allah yake horar da Isra'ila domin ta kaunace shi ta yi masa biyayya kamar yana horara da mazajenta domin yaki.
Yahweh yana magana.
Wato, bakar da ba ta da igiya, ko wacce ba a tsuke ta ba.
A nan, "maganganunsu" yana nufin abin da jami'an suke fada. A.T: "domin suna zagi na" ko "domin suna la'anta ta".
"Wannan ne zai zama dalilin da Masar za ta yi wa Isra'ila ba'a da dariya".
1Ka sa ƙaho a leɓunanka! Gaggafa na zuwa bisa kan gidan Yahweh domin mutane sun karya alƙawarina sun kuma bijirewa dokokina.2Sun yi kuka gare ni, 'Ya Allahna, mu a Isra'ila mun san ka.'3Amma Isra'ila taƙi abin dake mai kyau, maƙiyi kuma zai tasar masa.4Sun naɗa sarakuna, amma ba dani ba, sun yi hakimai, amma bada sani na ba. Da zinariyar su da azurfa suka yi wa kansu gumakai, amma lallai za a datse su."5"An ƙi ɗan maraƙinki ya Samariya. Fushina yana ƙuna akan waɗannan mutane. Har yaushe zasu kasance cikin laifi?6Gama wannan gunki daga wurin Isra'ila ya fito; mutum ne yayi shi; ba Allah ba ne! Za a farfashe ɗanmaraƙin Samariya.7Gama mutane sun shuka iska sun girbe guguwa. Hatsin dake tsaye ba shi da tsaba; bai bada gari ba. Ko da ya nuna, bãƙi ne zasu cinye shi.8An haɗiye Isra'ila; yanzu sun kwanta tare da ƙasashe sai kace abin da ba shi da amfani.9Gama sun hau zuwa Asiriya kamar jakin jeji shi ka ɗai. Ifraim tayi hayar masoya domin kanta.10Ko da zasu yi hayar masoya daga cikin al'ummai, yanzu zan tara su. Zasu fara lalacewa, saboda danniyar sarkin sarakuna.11Saboda Ifraim ya ruɓanya bagadai domin miƙa baye-baye na zunubi, amma a maimakon haka sai suka zama bagadan aikata zunubi.12Ko da zan rubuta masu dokata sau dubu goma, zasu dube ta a matsayin baƙon abu a gare su.13Game da maganar hadayun baye-bayena, suna hadaya da nama su kuma ci. Amma ni, Yahweh, ban karɓe su ba. Yanzu zan tuna da muguntarsu in hukunta zunubansu. Za su koma Masar.14Isra'ila ya manta da ni, Mahaliccinsa, ya kuma gina masarautai. Yahuda ya gina garu masu yawa, amma zan aikar da wuta bisa biranen su; zai hallakar da kagara.
Yahweh yana magana game da zuwa mayakan Assuriya domin kai hari wa masarautar arewa.
Gaggafa, tsuntsu mai kama wadansu dabbobi, ana amfani da ita wajen wakilta abokan gaban Isra'ila. A.T: "Kamar yadda gaggafa take farautar sauran dabbobi, haka abokan gaban Isra'ila suke zuwa don su kama jama'ata".
A nan, "ta da" tana wakilcin "rashin biyayya", "ketawa".
"mun yi maka aminci"
Yahweh yana magana.
Za a iya fadin wannan kai tsaye. A.T: "amma sakamakon zai zama cewa zan hallaka mutanen".
Ma'anar tana iya zama 1) annabin ne yake magana a nan (duba UDB), ko 2) Yahweh yana magana. A.T: "Ni kaina na ki marakinku, Samariya".
Sarki Yerobowan na biyu na Isra'ila .
Akan yi maganan fushi kamar fushin wuta ne. A.T: "Ina fushi kwarai da mutanen nan".
Yahweh yana yin wannan tambayar don bayyana fushinsa game da rashin tsarkin mutanensa. "Ina fushi da wadannan mutanen domin ba su da marmarin zama marasa laifi".
Yahweh yana magana.
shuka iska shi ne aikin banza ko aikin da ke jawo lalacewa. Girbe guguwa kuwa shi ne fama da masifa daga ayyukan mutum.
A nan, "zangarniya" tana nufin bangaren hatsin da tsaba suke. Shukar da babu zangarniya ba ta da wani amfanin da za ta ba wa manomin. Haka nan kuma, ayyukan Isra'ila ba za su haifar da wani abin kirki ba.
Idan ma wani cikin ayyukan Isra'ila ya haifar da abin kirki, abokan gaban Isra'ila ne za su zo su kwace daga hannunsu.
Yahweh yana magana.
"Ciki" tana nufin an yi nasara a kansu, an kwashe su bauta. Za a iya fadin wannan kai tsaye. A.T: "Abokan gaban Isra'ila sun kwashi Isra'ilawa zuwa wata kasa".
Mutane sun san jakuna da taurinkai. Wannan yana nufin jama'ar Isra'ila sun ki su saurari Yahweh, amma sai suka tafi wurin mutanen Assuriya neman taimako.
Ana maganar kawancen Ifraimu da sauran kasashe kamar sun biya don su zama karuwai na Ifraimu. A.T: "Mutanen Ifraimu suna biyan wadansu kasashe domin su kare su" (UDB)
Wato, saboda sarkin Assuriya, wanda kuma akan kira "Babban Sarki", zai azabtar da jama'a.
Yahweh yana magana.
Wannan yana nufin cewa, Yahweh ya riga ya ba wa Isra'ila dokarsa ta wurin annabawa, ya kuma fada musu abin da yake bida daga gare su, sau da yawa.
"10,000"
Yahweh yana magana.
Saboda zunubansu, Allah zai aika mutanensa su zama bayi ga Masarawa.
1Isra'ila, kada ka yi farinciki, tare da murna kamar sauran mutane. Gama ka yi ta rashin aminci, ka yashe da Allahnka. Kana son biyan haƙƙoƙin karuwa a dukkan masussukai.2Amma masussuka da wurin matsewar inabi ba zasu ciyar da su ba; sabon ruwan inabi kuma zai ƙare.3Ba zasu ci gaba da zama a ƙasar Yahweh ba; maimakon haka, Ifraim zai koma Masar, wata rana zasu ci ƙazantaccen abinci a Asiriya.4Ba zasu zuba hadayun inabi ga Yahweh ba, ba kuma zasu zama abin karɓa gare shi ba. Hadayunsu zasu zama kamar abincin makoki: duk wanda ya ci shi zai ƙazantu. Domin abincinsu zai zama nasu ne kaɗai; ba zai zo cikin gidan Yahweh ba.5Me za ku yi a ranar da aka keɓe don taruwa, a ranar idi ta Yahweh?6Gama, duba, idan sun kubcewa hallaka, Masar zata tara su, Memfis kuma za ta bizne su, kayayyakin daraja na azurfa - abubuwa masu tsini zasu mallake su, ƙayayuwa kuma za su cika rumfunansu.7Kwanakin hukunci suna zuwa; kwanakin sakamako suna zuwa. Bari dukkan Isra'ila su san waɗannan abubuwa. Annabin wawa ne, masanin kuma taɓaɓɓe ne, saboda girman muguntarka da yawan zafin ranka.8Annabi mai tsaro ne domin Allahna akan Ifraim. Amma tarkon tsuntsu yana kan dukkan hanyoyinsa, rashin jituwa kuma na cikin gidan Allahnsa.9Sun ƙazantar da kansu ƙwarai kamar a cikin kwanakin Gibiya. Allah zai tuna da muguntarsu, zai kuma hukunta zunubansu.10Yahweh yace, "Lokacin da na samo Isra'ila, kamar samun 'ya'yan inabi ne a cikin jeji. Kamar nunan farin itacen ɓaure a lokacinsa, na samo ubanninku. Amma suka je wurin Ba'al Fiyo, suka kuma miƙa kansu ga wannan gunki abin kunya. Suka zama abin ƙyama kamar gunkin da suke ƙauna.11Amma ga Ifraim darajarsu zata tashi kamar tsuntsu. Ba mai haihuwa, ba mai juna biyu, ko mai daukar ciki.12Ko da yake sun goyi 'ya'ya, zan ɗauke su daga gare su ba wanda zai ragu. Kaiton su sa'ad da na juya daga gare su!13Na ga Ifraim, kamar Taya, an dasa ta a wuri mai dausayi, amma Ifraim zai kawo 'ya'yansa wurin wani wanda zai yayyanka su."14Ka ba su, Yahweh - me zaka ba su? Ka ba su mahaifa mai yin ɓari, da nonon da baya ba da madara.15"Saboda muguntarsu a Gilgal, a can ne na fara ƙinsu. Saboda mugayen ayyukansu, zan kore su daga cikin gidana. Bazan ƙara ƙaunarsu ba; dukkan shugabanninsu 'yan tawaye ne.16Ifraim na da cuta, sauyarsa kuma ta bushe; basu ba da 'ya'ya. Ko da zasu sami 'ya'ya, zan kashe ƙaunattatun 'ya'yansu."17Allahna zai ƙi su saboda ba suyi masa biyayya ba. Zasu zama masu kai wa da komowa cikin al'ummai.
Yusha'u, annabi, yana magana.
Wannan yana bayyana masussukar da wurin matsa ruwan inabi kamar su mutane ne da za su iya ciyar da wani. Wannan yana nufin cewa girbin ba zai zama da albarka ba sosai har hatsin da ke masussuka ya biya bukatar mutane, kuma ba zai samar da isasshen inabi domin a matsa isasshen ruwan inabi ba.
Wadannan wurare ne masu fadi, inda ba sussuka kadai ake yi ba, amma ana yin bukukuwan al'umma da na addini. Karuwai na haikali sukan zo domin su taimaki mazaje wajen bukin girbi da bukukuwan gumaka.
Ba za a sami isasshen inabin da zai samar da ruwan inabi ba.
Yusha'u, annabi, yana magana.
Wannan furcin yana nuna alamar cewa Yahweh ya ci gaba da ganin kasar Isra'ila a matsayin mallakarsa, ba mallakar Isra'ilawa ba.
Wannan abinci ne da ya kamata Isra'ilawa su ki ci domin zai kazantar da su a gaban Yahweh.
A nan, "abincin masu makoki" yana nufin abin da mutane suke ci sa'adda suke makoki, domin sun kazantu, kuma ba arbabbu ba ne a gaban Allah. Wannan yana nufin Yahweh zai dauki hadayun mutanensa su zama kazantattu, kuma ba zai karbe su ba.
Mutanen Isra'ila za su sami abincin ci, amma Yahweh ba zai karbi abincin a matsayin sadaka ba.
Ana maganar kazantaccen abincin kamar yana iya zuwa wurare da kansa. Hakika, mutane ne suke kai shi da kansu.
Yusha'u, annabi, yana magana.
Yusha'u yana amfani da wannan tambayar domin jaddada cewa mutanen ba za su ci gaba da yin idodinsu sa'adda abokan gabansu suka yi maishe su bayi ba. A.T: "Ba za ku iya bukin idin da Yahweh ya kayyade muku ba".
Duka wadannan biyu suna nufin abu daya.
A nan, "su" yana nufin mutanen Isra'ila ne. Za ka iya ci gaba da wannan maganar kamar wani ne yake magana da su. A.T: "idan kun tsira".
Masar da Memfis suna nufin mutanen da suke zaune a can. A.T: "mayakan Masar za su kama ku. Za ku mutu a can, kuma mutanen Memfis za su binne ku" (UDB)
Ana maganar kayuyuwan da ke girma a wuraren da Isra'ilawa suka adana azurfarsu kamar kayuyuwan mutane ne, abokan gaba, wadanda za su kwace abubuwan tamani na Isra'ilawa don kansu. A.T: "Kayuyuwa masu tsini za su yi girma a wuraren da suke adana dukiyarsu ta azurfa".
A nan, "kayuyuwa masu tsini" da "sarkakkiya" suna nufin abu daya. Girmar kayuyuwa da sarkakkiya tana wakiltan kasar da ta zama kango, kamar hamada.
A nan, "alfarwa", tana wakiltan gidajen Isra'ilwa.
Yusha'u, annabi, yana magana.
Yusha'u ya yi wadannan maganganu biyu iri daya domin jaddada cewa Yahweh zai hukunta jama'ar Isra'ila domin miyagun ayyukansu, nan ba da jimawa ba.
Wadannan kalamai suna nufin abu daya ne. Ma'anar tana iya zama 1) mutanen sun dauki annabawan a matsayin mahaukata, ko 2) annabawan sun haukace saboda zunuban da mutanen suka aikata.
A nan, "annabi" da "mutum mai ruhu" duk suna nufin mutumin da yake cewa yana karbar sakonni daga wurin Allah. Yana nufin cewa wadannan mutanen annabawan karya ne, kuma suna tunani ne kawai cewa suna karbar sakonni daga wurin Allah.
Kalmomin "yawan mugunta" da "yawan kiyayya" suna da ma'ana masu kama. Muguntar mutanen ta bayyana kanta cikin kiyayyarsu ga Yahweh da annabawansa.
Yusha'u, annabi, yana magana.
"Mai tsaro" yana tsaron wajen birninsa don ya ga ko hatsari yana zuwa. Kashedin da annabin yake yi wa mutanen sa'adda suke zunubi, kuma suna cikin hatsarin fuskantar hukuncin Allahnsa, ana magarsa a nan kamar shi ne mai tsaron birnin. A.T: "Annabin kamar mai tsaro ne na Allah bisa Ifraimu".
Wadansu juyin sun fassara wannan nassin kamar "Annabin, tare da Allahna, shi ne mai tsaron Ifraimu".
Wannan yana nufin annabwa gaba daya da Allah ya zaba. A.T: "Annabawan su ne" ko "Annabawan gaske su ne".
A nan, "Ifraimu", yana wakilcin dukkan jama'ar Isra'ila.
"Tarkon kama tsuntsu" ana amfani da shi wajen kama tsuntsu. Wannan yana nufin cewa mutanen Isra'ila suna yin duk abin da za su yi don dakatar da annabawan Allah: A.T: "mutanen suna dana masa tarko duk inda ya tafi" ko "mutanen suna yin duk abin da za su iya yi don su cutar da shi".
"Jama'ar Isra'ila sun yi zunubi, sun kazantu kamar yadda suka yi a Gibeya da dadewa". Mai yiwuwa wannan magana ce mai nuni da ayyukan bankyama na kabilar Bilyaminu da aka lissafta a Mahukunta 19-21.
Yahweh yana magana.
Wannan yana nufin sa'adda Yahweh ya fara dangantakarsa da farko da jama'ar Isra'ila ta wurin kiransu mutanensa na musamman.
Wadannan maganganu guda biyu suna jaddada yanayin da suke faranta ran mutum. Wannan yana nufin Yahweh ya ji dadi sosai sa'adda dangantakarsa da jama'ar Isra'ila ta fara.
Wannan sunan wani tudu ne a kasar Mowab inda ake yi wa allahn karyan nan, Ba'al, sujada.
Yahweh yana magana.
Jama'ar Ifraim, ko masarautar arewa, za ta rasa komai da ke sa sauran kasashe suna girmama su. Darajarsu za ta kare da wuri, kamar yadda tsuntsu yake tashi. A.T: "darajarsu za ta zama kamar tsuntsun da ya tashi daga gare su".
Sa'adda Allah ya daina taimakon masarautar arewa, zai zama kamar ya juya musu baya ne a zahiri.
Yusha'u, annabi, yana magana.
"Shuka" tana nufin kasancewa a wurin mai tsaro. A.T: "A da kasar Isra'ila tana da kyau kamar birnin Taya, kamar bishiyar da wani ya shuka a kasa mai danshi".
"'Ya'ya" su ne jama'ar wannan kasar. A.T: "amma jama'ar Isra'ila za su fitar da 'ya'yansu".
Yusha'u ya yi amfani da tambaya wajen jaddada cewa Yahweh yana so ya ba mutanensa abin da ya cancance su. A.T: "Wannan ne abin da na roke ka, Yahweh, ka ba su: ka ba su".
"Ba ya haihuwa" yana nufin cikin da ake baraswa, jaririn ya mutu. Yusha'u yana roko domin dukkan matayen Isra'ila su zama haka.
Yahweh yana magana.
Yahweh yanafurta cewa zai kori Isra'ila daga kasarsa, kasar Kan'ana.
masu yi wa sarki hidima
Yahweh yana magana a aya 16. Yusha'u ya fara magana a aya 17.
Yahweh yana maganan jama'ar Isra'ila kamar bishiya mai cuta, wadda ba ta ba da 'ya'ya, ana dab da sare ta. Wannan magana ce cewa mutane ba su da karfi, kuma nan ba da dadewa ba abokan gabansu za su zo su yi nasara a kansu.
1Isra'ila kuringa ce mai yabanya dake ba da 'ya'yansa. Gwargwadon yawan 'ya'yansa gwargwadon yawan gina bagadansa. Bisa ga albarkar ƙasarsa, yakan inganta ginshiƙansa.2Zuciyarsu da yaudara; yanzu dole su ɗauki laifinsu. Yahweh zai rushe bagadansu; zai lalatar da ginshiƙansu.3Sa'annan zasu ce, "Bamu da sarki, domin ba mu jin tsoron Yahweh, sarki kuma -- me zai yi mana?"4Maganganunsu na wofi ne, su kan ɗauki wa'adodi ta wurin rantsewa kan ƙarya. Domin wannan adalci ya tsuro kamar tsire - tsire masu dafi cikin gona.5Mazaunan Samariya zasu tsorata saboda 'yan'maruƙan Bet Aben. Mutanenta zasu yi makoki a kanta, kamar yadda mazinatan firistoci suka yi murna a kansu da darajarsu, amma yanzu ba su nan.6Za a kai su Asiriya a matsayin kyauta ga babban sarki. Za a kunyatar da Ifraim, Isra'ila kuma za ta ji kunya saboda gumakanta.7Za'a hallakar da sarkin Samariya, kamar sassaƙen itace a bisa ruwa.8Za a hallakar da wurin zaman mugunta. Wannan shi ne zunubin Isra'ila! Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya zasu fito bisa bagadansu. Mutane zasu cewa duwatsu, "Ku rufe mu!" tuddai kuma, "Ku faɗo mana!"9Isra'ila kayi zunubi tun kwanakin Gibiya; a can ka tsaya. Ko yaƙi ba zai iske 'ya'yan kurakurai a Gibiya ba?10A lokacin da na so, zan horar dasu. Al'ummai zasu taru su ɗaure su saboda laifofinsu.11Ifraim horarriyar karsana ce dake son sussukar hatsi, zan sa karkiya a bisa kyakkyawan wuyanta. Zan sa karkiya a wuyan Ifraim; Yahuda zai yi huɗa; Yakubu kuma zai ja garma da kansa.12Ku shuka wa kanku adalci, za ku girbi ɗiyan alƙawarin aminci. Kuyi kaftun saurar ƙasarku, gama lokaci ya yi da za a nemi Yahweh, har lokacin da zai zo ya zuba adalci a kanku.13Kun shuka mugunta; kun girbe rashin adalci. Kun ci 'ya'yan yaudara saboda kun dogara ga shirye-shiryenku da kuma yawan sojojinku.14Domin wannan hargitsin yaki zai tashi daga cikin mutanenku, za a kuma lalatar da dukkan garuruwanku masu kagara, zai za ma kamar yadda Shalman ya lalatar da Bet Arbel a ranar yaƙi, aka datse uwaye da 'ya'yansu gunduwa-gunduwa.15Haka zai faru dake, Betel, saboda muguntar ki mai yawa. Da wayewar gari za a datse sarkin Isra'ila gaba ɗaya."
Yusha'u yana magana game da Isra'ila.
Ana maganar Isra'ila kamar kuringar inabi mai bayar da 'ya'ya sosai. Akwai dan lokacin da mutanen suka arzuta, suka yi karfi.
Kunringar da ke ba da 'ya'ya fiye da yadda aka saba samu.
Dukka wadannan biyu suna nufin yadda wadatar mutanen take karuwa, suna kara karfi da arziki.
"Zuciya" tana nufin yanayinsu a ciki. "Suna da yaudara".
"Yanzu ne lokacin da Yahweh zai hore su saboda zunubansu".
Yusha'u yana magana game da Isra'ila.
Mutanen za su ce sarkinsu ba zai iya taimakonsu ba. A.T: "Ko da muna da sarki, ba zai iya taimakonmu ba".
A nan, "surutai" tana nufin karairayi. A.T: "Suna fadin karairayi".
Abin da mutanen suke kira hukunci a dokarsu da shari'arsu, ana maganarsa kamar shuka ce mai tsirowa. A.T: "Saboda haka shari'arsu ba ta adalci ba ce; sai dai, tana da illa".
Karairayinsu da rashin adalcinsu suna yaduwa ko'ina a kasarsu, suna cutar da kowa kamar shuka mai dafi.
Yusha'u yana magana game da Isra'ila.
Wannan ne birnin da ke kan iyaka tsakanin masarautar arewa ta Isra'ila da kabilar Bilyaminu a masarautar kudu. Duba yadda ka fassara wannan a 4:15.
Za a iya fadin wannan kai tsaye. A.T: "Assuriyawa za su tafi da su".
Za a iya fadin wannan kai tsaye. A.T: "Mutanen Isra'ila za su ji kunya domin sun bauta wa gumaka".
Juyi da yawa sun fassara wannan kalmar Ibraniyancin a matsayin "shawara", "shirye-shirye", ko "manufofi".
Za a iya fadin wannan kai tsaye. A.T: "Assuriyawa za su hallaka sarkin Samariya".
Wannan yana nufin sarkin Samariya zai rasa taimako kamar dan guntulen katakon da igiyoyin ruwa ke karkadawa gaba da baya.
Za a iya fadin wannan kai tsaye: A.T: "Assuriyawa za su hallaka masujadan tuddai na Isra'ila, inda mutanen suke aikata mugunta".
Mutane ba su saba yin magana da abubuwan ba su tunani ko jinsu ba. Mai fassara yana iya samu wata hanya dabam bayyana wannan nassin, idan yarensu bai ba da damar irin wannan furcin ba. A.T: "Mutanen za su ce, 'Da ma duwatsu su rufe mu!' kuma 'Muna fatar tuddai za su fado a kanmu!'".
Yahweh yana magana.
Watakila wannan yana nuni da miyagun ayyukan kabilar Bilyaminu da aka lissafta a Mahukunta 19-21. Duba yadda ka fassara wannan a 9:8.
Wannan nassin yana nufin cewa mutanen yanzu sun ci gaba da aikata irin ayyukan da kakanninsu suka yi a Gibeya. A.T: "kuma kuna tunani kamar yadda suka yi".
Yahweh ya mori tambaya domin jaddada cewa wadanda suke a Gibeya, wadanda suka aikata zunubi, tabbas za su yi fama da yaki. Kuma wannan yana maganar yadda mutanen za su yi fama da yaki sa'adda abokan gabansu suka zo kamar yakin mutum ne wanda zai kama su. A.T: "Tabbas, yaki zai abka wa wadanda suka aikata zunubi a Gibeya" ko "Hakika, abokan gaba za su kai hari kan wadanda suka aikata zunubi a Gibeya".
A nan, "'ya'ya" karin magana ce mai nufin "masu irin halin abu". A.T: "wadanda suke aikata zunubi" ko "masu mugunta".
Yahweh yana magana.
Wannan yana nuni da yawan zunuban Isra'ila.
Karsana tana jin dadin sussuka domin sukan yi ta yawo a sake ba tare da nauyin kaya ba. Yahweh yana nufin cewa ya bar jama'ar Isra'ila su sake su ji dadin rayuwa.
A nan, "karkiya" tana nufin shan wahala ko bauta. Yahweh ya yi jama'ar Isra'ila alheri, amma mutanen sun ci amanarsa. Saboda haka, zai hukunta su, ya korre su su zama bayi.
A nan, "Yahuza" tana nufin jama'ar masarautar kudu, "Yakubu" kuma tana nufin masarautar arewa. Wannan yana nufin Allah zai kawo lokutan wahala wa duka masarautu biyun.
abin da ake mora wajen baje kasa, a rufe iri bayan an yi noma.
Yahweh yana magana.
Ana maganar adalci da alkawarin aminci kamar hatsi ne da za a iya shukawa a girbe.
Sa'adda ba a yi "kaftun" kasa ba, to, ba ta kai a yi shuka a kanta ba. Yahweh yana nufin cewa yana so jama'ar Isra'ila su tuba, domin su fara yin abin da yake da kyau.
Ana mugunta da rashin adalci kamar hatsi ne da za a iya shukawa a girbe.
Ana maganar sakamakon yaudara kamar abinci ne da za a iya ci. A.T: "Yanzu kuna fama da sakamakon yaudarar juna".
Ana kwatanta yakin da ke zuwa da wani yaki da aka yi da dadewa a baya.
Wannan sunan sarkin da ya hallaka birnin Bet-arbel a wajejen shekara 740 BC. Mayakansa sun kashe mata da kananan yara a wannan harin.
Akwai yiwuwar wannan sunan wani birni ne na kabilar Naftali.
A nan, "Betel", tana wakiltan mutanen da suke zama a wurin, Annabin ya yi magana da mutanen Betel kamar suna nan a wurin suna sauraronsa.
1Lokacin da Isra'ila yake yaro na ƙaunace shi, na kuma kira ɗana daga cikin Masar.2Yawan kiran su, yawan gujewar su daga gare ni. Sun miƙa hadaya ga Ba'aloli, suka ƙona turare ga gumaka.3Duk da haka ni na koyawa Ifraim tafiya. Ni ne na ɗaga su da hannuwansu, duk da haka basu sani na kula dasu ba.4Na bishe su da linzamin mutune, da ragamar ƙauna. Na zama kamar mai kwance masu karkiya a muƙamuƙinsu, na sunkuya masu na ciyar dasu kuma.5Baza su koma ƙasar Masar ba? Ko Asiriya ba za suyi mulkinsu saboda sunƙi juyowa gare ni ba?6Takobi zai faɗa wa biranensu ya hallaka ƙarafan ƙofofinsu; zai hallaka su saboda shirye-shiryensu.7Mutanena sun ƙudurta juyawa daga gareni. Ko da sun yi kira ga Maɗaukaki, ba wanda zai taimake su.8Ta yaya zan iya rabuwa da kai, ya Ifraimu? Ta yaya zan mika ka, ya Isra'ila? Ƙaƙa zan maishe ka kamar Adma? Yaya zan maishe ka kamar Zeboyim? A gare ni zuciyata ta canza; dukkan jinƙaina ya harzuƙa.9Bazan tabbatar da zafin fushina ba; bazan hallakar da Ifraim ba. Gama Ni Allah ne ba mutum ba; Ni ne Mai Tsarki wanda ke tsakiyar ku, ba kuwa zan zo cikin hasala ba.10Zasu bi Yahweh; shi kuma zai yi ruri kamar zaki. Idan yayi ruri, 'ya'yansa za su zo suna rawar jiki daga yamma.11Zasu zo da rawar jiki kamar tsuntsu daga Masar, kamar kurciya daga ƙasar Asiriya. Zan maishe su su zauna a gidajensu - wannan furcin Yahweh ne.12Ifraim ya kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra'ila kuma da yaudara. Amma Yahuda har yanzu yana tare da ni, Allah, yana yi mani aminci, Mai Tsarkin nan."
Yahweh yana maganar kula da Isra'ila kamar yadda iyaye ke kula da 'ya'ya.
Allah yana magana game da jama'ar Isra'ila kamar sun zama karamin yaro. Yahweh yana nuni da lokacin da ya fara dangantakarsa da kasar.
"Dana" yana nufinmutanen Allah Uba. A.T: "Na fitar da dana daga Masar".
Za a iya fadin wannan kai tsaye. A.T: "Yawan kiran da nake yi musu su zama jama'ata, yawan kin da suke yi mini".
Yahweh yana magana game da yadda ya kula da Isra'ila.
Yahweh yana magana game da Isra'ila kamar karamin yaron da ya koya wa tafiya.
Wannan furcin ya ci gaba da nuna kamance. A.T: "na kula da su".
Yahweh ya kaunaci jama'arsa a hanyoyin su, a matsayin 'yan'adam, za su iya fahimta su darajanta.
Yahweh yana maganar kasar Isra'ila kamar dabba mai aiki sosai, wadda aka saukaka mata aikinta.
Wannan furcin yana ci gaba da bayanin kamacen da ake duban Isra'ila a matsayin karamin yaro. Yana iya nufin cewa Yahweh ya biya dukkan bukatunsu na jiki.
Yahweh yana magana game da Isra'ila.
Wannan tamnayar tana nufin cewa kasar Isra'ila za ta sake omawa bauta, kamar yadda suke da a Masa.
Kasar Isra'ila za ta zama baiwar Assuriya sanadiyar kin kasancewa da aminci ga Yahweh.
A nan, "takobi" yana wakilcin abokan gaban Isra'ila, wadanda za su hallaka biranen Isra'ila.
Kofofi suna tanadar da tsaro daga abokan gaba ga mazaunan birni, kuma sandunan suna rike kofofin da aka kulle. Hallaka sandunan yana nufin an kawar da tsaron jama'ar.
A nan Allah yana magana game da kansa kamar wani ne dabam yake ba da labarinsa. Za a iya fadin wannan daga mai maganar. A.T: "Ko da yake suna kira gare ni, Mafi Girma".
Yahweh ba zai bari wani ya taimaki Isra'ila ba, domin sun juya daga gare shi.
Yahweh yana magana game da Isra'ila.
Yahweh yana kaunar mutanen sosai, ba zai iya hallaka dungum ba. Za a iya fassara wadannan tambayoyin zuwa furci. A.T: "Ba zan yashe ki ba, ya Ifraimu. Ba zan mika ki ba, ya Isra'ila".
Yahweh yana kaunar mutanensa sosai, ba zai iya hallaka su dungum ba. Za a iya fassara tambayoyin nan kamar furci. A.T: "Ba na so in yi da ku kamar yadda na yi da Adma, ko in maishe ku kamar Zeboyim - wato, biranen da na hallaka tare da Saduma" (UDB)
Allah ba kamar mutane ba ne, wadanda sukan yi saurin daukan fansa.
A nan, "zuciya", tana wakilicin nufin Allah da shawarwarinsa.
Boyayyen suna na "hasala", za a iya fassara shi zuwa kalmar "fushi". A.T: "Ba zan zo wurinku, in yi fushi da ku ba" (UDB).
Yahweh yana magana game da lokacin da zai maido jama'arsa.
Anan maganar bauta da girmama Yahweh kamar bin shi ne (UDB).
Ana maganar yadda Yahweh zai sa mutanensa su iya komowa kasarsa kamar yana kiran mutanensa ne.
Za su dawo da wuri, kama yadda tsuntsu take komawa shekarta. "Rawan jiki" yana iya nufin bugun fukafukin tsutsu (Duba UDB). Yana iya nufin yadda mutanen suke cikin tawali'u da bangirma ga Allah.
"Abin da Yahweh ya fada" ko "abin da Yahweh rantse". Duba yadda ka fassara wannan a 2:12.
Yahweh yana magana game da Isra'ila da Yahuza.
Ana maganar ayyukna karairayi da munafunci kamar abubuwa ne da jama'ar masarautar arewa suka kewaye Yahweh da su.
Jama'ar masarautar arewa suna yi wa Allah biyayya, har yanzu. A nan, "tare da ni" yana wakilicin kasancewa tare da Allah. Amma, wadansu juyi suna da fassara dabam ta wannan mawuyacin nassin.
1Ifraim yana ci daga iska, ya na bin iskar gabas. Kullum yana yawaita ƙarairayi da ta'addanci. Sun yi alƙawari da Asiriya suna ɗaukar man zaitun zuwa Masar.2Yahweh kuma yana da ƙara gãba da Yahuda kuma zai hukunta Yakubu saboda abin da ya yi; zai sãka masa gwargwadon ayyukansa.3A cikin ciki Yakubu ya kama duddugen ɗan'uwansa, a cikin balagarsa kuma yayi kokowa da Allah.4Yayi kokowa da mala'ika kuma ya yi nasara. Ya yi kuka ya roƙi tagomashinsa. Ya sadu da Allah a Betel; a can Allah yayi magana da shi.5Wannan shi ne Yahweh, Allah Mai runduna; "Yahweh" shi ne sunansa da za a dinga kira6Domin wannan ka juyo wurin Allahnka. Ka kiyaye alƙawarin jinƙai da adalci, kana cigaba da sauraron Allahnka.7'Yan kasuwa na riƙe da ma'aunin algus a hannunsu; suna son yin algus.8Ifraim yace, "Hakika na zama mai arzaƙi sosai; na samarwa kaina dukiya. A cikin dukkan aikina ba za a sami laifi a ciki na ba, ko duk wani abin da zai zama zunubi."9"Ni ne Yahweh Allahnku tun daga ƙasar Masar. Zan kuma sa ku sake zama cikin rumfuna, kamar cikin kwanakin ayyanannen idi.10Na yi magana da annabawa, na kuma basu wahayi da yawa domin ku. Ta hannun annabawa kuma na ba da misalai."11Idan akwai mugunta a Giliyad, hakika mutane sun zama marasa amfani. A Gilgal sun yi hadayar bajimai; bagadansu zasu zama kamar tsibi -tsibin dutse a cikin gonaki.12Yakubu ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra'ila ya yi aiki domin ya sami mata; ya yi kiwon garkunan tumaki domin ya sami mata.13Yahweh ya fitar da Isra'ila daga Masar ta wurin annabi, ta hannun annabi kuma ya kula dasu.14Ifraim ya baƙanta wa Yahweh rai. Domin wannan Ubangijinsa zai bar jininsa a kansa, zai kuma sãka masa akan duk abin kunyarsa.
Yusha'u, annabi, yana magana.
A nan, "Ifraimu" tana wakiltar dukkan mutanen Isra'ila. Haka kuma, "iska" tana wakiltar wani abin da babu amfani ko mara jimawa. Ana maganar yadda jama'ar Isra'ila suke yin abubuwan da ba za su taimake su ba kamar suna cin iska ne.
Iskar gabas tana da zafi sosai, kuma tana yi wa kasa ta'adi. A nan, tana wakiltar duk abin da yake hallakarwa. Ana maganar yadda mutanen suke aikata abubuwan da za su hallakar da su kamar suna bin iskar gabas.
Mutanen Isra'ila sun aika man zaitun a matsayin kyauta zuwa ga sarkin Masar, don su shawo kansa ya taimake su.
Ana maganar yadda Yahweh yake fadin cewa jama'ar Yahuda sun yi masa zunubi, kuma sun karya alkawarinsa kamar Yahweh yana kararsu ne a kotu. Duba yadda ka fassara irin wannan kalmar a 4:1.
A nan, "Yahuza" da "Yakubu" duk suna wakiltar jama'ar Yahuza. A.T: "game da jama'ar Yahuza... hukunta su saboda abin da suka aikata... saka musu saboda ayyukansu".
Wannan korafi ne da wani ya kai game da wani a kotun shari'a. Duba yadda ka fassara wannan a 2:2.
Yusha'u, annabi, yana magana game da Yakubu, kakan Isra'ilawa.
Yakubu ya so ya dauki matsayin dan'uwansa na dan fari, saboda haka ya yi kokarin ya hana dan'uwansa ya fito da farko.
Yakubu ya yi fada da mala'ika don mala'ikan ya albarkace shi.
Yusha'u, annabi yana magana.
Za a iya fadin wannan kai tsaye. A nan, "suna" yana wakiltar dukkan halin Allah. A.T: "sunan da muke addu'a a cikin" ko "ta wurin sunansa muke yi masa sujada".
Wannan yana nufin yin biyayya da dokar Allah, da kuma yin abin da yake daidai.
Yusha'u, annabi, yana magana game da Isra'ila.
'Yan kasuwa suna amfani da ma'aunan da ba daidai ba wajen awon nauyin kudi ko kayayyakin da suke saya ko sayarwa.
'Yan kasuwa suna cutar kwastomominsu ta wurin fada musu karya da karbar kudi fiye da yadda ya kamata.
Wadannan maganganu biyu suna nufin abu daya, kuma suna nufin cewa mutanen Ifraimu sun dauki kansu masu arziki sosai.
Ana maganar zama mai dukiya ta wurin kasuwanci kamar samun dukiya. A.T: "Na tara kudi sosai".
Wadannan maganganu biyu suna nufin abu daya, kuma suna jaddada cewa jama'ar Ifraimu suna daukan kansu marasa laifi. Ana maganar sanin cewa wani ya yi zunubi kamar samun zunubi a cikin mutumin. A.T: "ba za su sami cewa na yi wani zunubi ba".
Yahweh yana magana da jama'ar Isra'ila.
Ma'anar tana iya zama 1) "Ni ne Yahweh Allahnku, wanda ya fito da kakanninku daga kasar Masar" ko 2) "Ni ne Allahnku tun kuna kasar Masar" ko 3) "Na zama Allahnku sa'adda kuke a kasar Masar".
Ma'ana tana iya zama 1) Yahweh yana barazanar korara jama'ar Isra'ila daga gidajensu, ya sa su zauna a alfarwai. Saboda haka, a nan "zauna cikin alfarwai" zai wakilci tafiya bauta, ko 2) alkawari ne cewa bayan bautarsu, jama'ar za su zauna a alfarwai kuma, kuma Yahweh zai kula da su kamar yadda ya yi sa'adda Isra'ilawa suka bar Masar. Saboda haka, a nan "zauna cikin alfarwai" zai wakilci komowa yadda al'amura suke sa'adda Yahweh ya kula da jama'arsa.
A nan, "hannu", yana wakiltan wanda yake aiwatar da aiki. A.T: "Ta wurin annabawa".
Yusha'u, annabi, yana magana.
Za a rusa bagaden da mutanen suka yin sujada, su zama tsibin duwatsu.
A nan, "Yakubu" da "Isra'ila" suna nufin mutum daya. Suna Yakubu ya zama Isra'ila daga baya.
Yusha'u, annabi, yana magana.
Wato, Musa
Fuhsin da jama'a suka jawo wa Yahweh yana da yawa kwarai.
A nan, "jini", yana magana game da laifin da masu kashe wadansu suka dora wa kansu. Allah ba zai gafarta zunubansu ba.
Ana maganar wannan ra'ayin wahal da wani sanadiyar ayyukansa kamar wadannan ayyukan kayayyakin mutumin ne da ake jefa masa kuma. AT: "zai sa ya sha wahalar ayyukansa na kunya".
1"Sa'ad da Ifraim ya yi magana, akwai razanarwa. Ya ɗaukaka kansa a Isra'ila, amma ya zama da laifi wajen bautar Ba'al, kuma ya mutu.2Yanzu, sai ƙara zunubi suke tayi, suna yiwa kansu sifofi na zubi daga azurfarsu, gumaka ne da masu hikima suka ƙera, dukkan su aikin gwanayen masu sana'a ne. Mutane suka ce masu, 'Waɗannan mutane masu miƙa hadaya sunyiwa 'yanmaruƙa sumba.'3Domin wannan zasu zama kamar gizagizan safe, kamar raɓa mai kaɗewa da sauri, kamar ƙai-ƙayi wanda iska ke hurewa daga masussuka, kamar hayaƙi daga cikin mafitarsa.4Amma ni ne Yahweh Allahnka tun daga ƙasar Masar, dole ka sani cewa ba bu wani Allah sai ni, dole kuma ka amince cewa banda ni babu wa ni mai ceto.5Na san ka a cikin jeji, cikin ƙasa mai tsananin fari.6Da kuka sami makiyaya, kun zama ƙosassu; amma bayan da kuka ƙoshi, kun ɗaukaka kanku. Saboda wannan dalili kuka manta da ni.7Zan zama kamar zaki a gare su; kamar damisa zan yi fako a kan hanya.8Zan faɗa masu kamar damisa da aka ƙwace mata 'ya'yanta, zan tsaga haƙarƙarin ƙirjin su, a can ne zan cinye su kamar zaki, kamar naman jeji zan yayyage su gunduwa-gunduwa.9Zan hallaka ku, ya Isra'ila; wanene zai iya taimakon ku?10Yanzu ina sarkinku, da za ya iya ceton ku daga cikin dukkan biranenku? Ina shugabanninku waɗanda kuka ce mani, 'Ka bamu sarki da hakimai'?11Na baku sarki cikin fushina, na kuma kawar da shi cikin hasalata.12Laifin Ifraim a ajiye yake; an kuma ajiye kurakuransa,13Zafin naƙudar haihuwa za ta afko masa, amma ɗa ne mara hikima, domin idan lokacin haihuwarsa ya yi, ba zai fita daga cikin mahaifa ba.14̀̀̀̀̀Zan cece su daga hannun Lahira? Zan cece su daga mutuwa? Mutuwa, ina, annobanki? Lahira, ina hallakarwarki? Babu sauran tausayi daga idanuna."15Koda Ifraim ya azurta cikin 'yan'uwansa, iskar gabas za ta zo; guguwar Yahweh za ta buga daga hamada. Maɓulɓular Ifraim za ta bushe, rijiyarsa ba zata ba da ruwa ba. Abokan gãbarsa zasu washe ɗakin ajiyar dukkan kayansa masu daraja.16Samariya za ta ji kunya, domin ta tayarwa Allahnta. Zasu faɗi ta kaifin takobi; ƙananan 'ya'yansu za a yayyankasu, matansu masu ciki za a farke su.
Yahweh yana magana.
Yusha'u ya mori kalmar "Ifraimu" don nuni da dukkan masarautar arewa, duk da cewa kuma sunan daya daga cikin kabilu goman ne. Kamar Yusha'u yana maganar wani lokaci ne da ya wuce da dadewa, sa'adda masarautar arewa take da karfi da daukaka, ba kamar yanzu ba.
A nan za a iya gane kalmar da babu, "a cikin al'ummai". Wadansu al'ummai sun wulakantu a gaban masarautar arewa. A.T: "mutane sun yi rawar jiki".
A nan, "daukaka", yana nufin mutum ya maida kansa muhimmi.
Sa'adda jama'ar Ifraimu suka shiga bautar Ba'al, sau suka raunana, abokan gabansu suka yi nasara a kansu. A nan, "mutu", tana nufin raunanar Isra'ila
A nan, "su" tana nufin kabilar Ifraimu da daukacin kasar Isra'ila, wadanda suke bin gurbin Ifraimu.
Cikin sujada ga gumaka akwai sumbatar siffofin 'yan maruka.
Wadannan furce-furcen suna bayyana cewa Isra'ila ba zai dade ba, kuma nan ba da jimawa ba za ta bata idan sun ci gaba da bautar gumaka, maimakon bin Yahweh.
Za a iya fadin wannan kai tsaye. A.T: "wadda iska take hurewa".
Yahweh yana maganar jama'arsa kamar sun zama garken tumakin da ya tara suna ta yawo a hamada. Ya ce ya mallake su a can a matsayin nasa.
Yahweh yana cewa jama'ar Ibraniyawa mutanensa ne na musamman, kuma ya kula da su a can.
An ci gaba da wannan misali na tumaki a wannan furcin.
A nan, "zuciya" tana wakiltan yadda gaba dayan mutum yake daga ciki. A.T: "sai kuka yi girmankai".
An yi maganar girmankai kamar fariya.
Yahweh yana magana.
Wadannan namun jeji ne masu kai hari da kashe sauran dabbobi. Yahweh ya ci gaba da fadin cewa zai hallaka mutanensa saboda zunubansu.
Ba a hada da kalmomin "zan abka" ba domin za a iya fahimtar su. A.T: "kamar yadda beyar zai kai wa dabbar da ta kwace 'ya'yanta hari".
Ba a hada da kalmomin "zan yayyage su" ba domin za a iya fahimta. A.T: "kamar yadda zaki zai yayyaga su".
Yahweh yana magana.
Yahweh yana amfani da tambaya wajen jaddada cewa babu wanda zai iya taimakon jama'ar Isra'ila. A.T: "babu wani wanda zai iya taimkon ku".
Yahweh yana yin wadannan tambayoyin domin ya fada wa Isra'ila cewa sa'adda suka yi masa tawaye, babu wani sarki ko shugaba da zai taimake su. Yahweh ne kadai zai iya ceton su daga hallaka.
Yahweh yana magana.
Wadannan kalamai biyu suna kama da juna, kuma ma'anar su daya ne.
Ana maganar zunubi da laifin masarautar arewa kamar kayayyaki neda za a iya ajiyewa da wata manufa.
A nan, Yahweh yana maganar wahalar da jama'ar Isra'ila za su fuskanta kamar nakudar haihuwa.
Yanzu Yahweh yana bayyana jama'ar Isra'ila a matsayin jaririn da uwar take haifa. Jaririn ba shi da wayo domin ba ya so a haife shi. Mutanen ba su so su tuba, su yi wa Yahweh biyayya.
Yahweh yana magana.
Yahweh yana morar wadannan tambayoyin don ya fada wa mutanen Isra'ila cewa ba zai cece su daga mutuwa ba. Tabbas zai hore su. A.T: "Hakika, ba zan cece su daga mutuwa ba, daga gangarawa zuwa Sheol/lahira".
Yahweh yana magana da "mutuwa" da Sheol/kabari" kamar su mutane ne. Yahweh yana morar tambayoyi wajen fadin cewa zai hallaka mutanen nan ba da jimawa ba. A.T: "Yanzu zan sauke annoba, in bari mutanen Isra'ila su mutu. Zan hallakar da su, in aika su Sheol/lahira".
Ana maganar samun juyayi kamar juyayin wani abu ne.
Ana maganar rashin tunanin samu juyayi kamar an boye juyayin yadda ba za a iya ganinsa ba. A.T: "Ba na juyayinsu".
Yusha'u, annabi, yana magana.
Kamar wannan furcin yana wakiltar kasashen da ke kewaye da masarautar arewa, musamman Yahuza, masarautar kudu.
Wata iska daga gabas tana da zafi da hallakarwa. A nan, tana nufin mayaka daga gabas, wadanda Yahweh zai aika domin su hallakar da jama'ar Isra'ila.
Yusha'u ya ci gaba da bayyana yadda Allah zai hirara da mutanen Isra'ila. A nan, ruwa yana wakiltar rai, wartsakewa, da karfi.
Wannan yana nuni da dukkan dukiyar jama'ar.
Yusha'u, annabi, yana magana.
A nan, "Samariya", tana nufin mutanen da ke a birnin Samariya wadanda suke da hakkin yi wa Allah tawaye.
Mutanen za su mutu.
A yaki.
Za a iya fadin wadannan kalaman kai tsaye. A.T: "aboan gaba za su fyade kananan yaransu a kasa, kuma za su bude cikin matansu masu cikin".
1Isra'ila, ka juyo wurin Yahweh Allahnka, gama ka faɗi saboda laifinka.2Ka ɗauki maganganun tare da kai ka juyo wurin Yahweh. Ka ce masa, "Ka kawar da dukkan laifinmu ka kuma karɓi abin da ke mai kyau, domin mu iya miƙa maka ɗiyan leɓunanmu.3Asiriya ba za su cece mu ba; ba za mu hau dawakai mu yi yaƙi ba. Ba kuwa zamu ƙara ce da aikin hannuwanmu, 'Ku ne allolinmu,' gama a cikinku marayu ke samun jinƙai."4"Zan warkar da bauɗewarsu; zan ƙaunacesu a yalwace, domin na kawar da fushina daga gare shi.5Zan zama kamar raɓa ga Isra'ila; zai yi fure kamar auduga, ya kuma kafu kamar itacen sida a Lebanon.6Rassansa zasu yaɗu waje; kyaunsa zai zama kamar itatuwan zaitun, ƙanshinsa kuma kamar itatuwan sida a Lebanon.7Mutanen da ke zaune ƙarƙashin inuwarsa zasu dawo; zasu farfaɗo kamar hatsi zasu yi fure kamar kuringar inabi. Shahararsa za ta zama kamar inabin Lebanon.8Ifraim, me zan yi kuma da gumaka? Zan amsa masa in lura da shi. Ni kamar itacen bakin rafi ne wanda kullum ganyayensa kore ne; daga wurina kuke samun 'ya'ya."9Wane ne mai hikima da zai fahimci waɗannan abubuwa? Wane ne ya fahimci waɗannan abubuwa domin ya san su? Gama hanyoyin Yahweh dai-dai suke, adali kuwa zaya yi tafiya cikinsu, amma masu tayarwa zasu faɗi a cikinsu.
Yusha'u, annabi, yana magana.
Ana maganar zunubi a nan kamar tana sa faduwa.
Mai yiwuwa wannan yana nufin kalmomin tuba da yabo. "Ku furta zunubanku".
Akan kira abin da mutum yake fada albarkar bakinsa. A.T: "kalmominmu da wakokinmu na yabo". Juyin zamani suna da wata fassara dabam ta wannan mawuyacin nassin.
Yusha'u yana magana.
"Hannuwa" tana nufin yadda mutane suke kera abubuwa. A.T: "ga gumakan da muka yi".
Watakila wannan furcin yana nufin dukkan kasar. Yana nuna dumbin jinkan Allah domin jama'arsa.
A nan, ana maganar yadda Allah ke nuna jinkai kamar wani abu ne da wani yake fuskanta, wadda jinkai ya samo.
Yahweh yana magana.
Ana maganar hana mutanen ridda daga Allah kamar warkar da su ne.
Ana maganar kasawar jama'ar su yi wa Allah biyayya kamar sun juya ne a zahiri daga gare shi.
Ana maganar Allah kamar shi raba ne da ke samar da danshin da ake bukata domin shuke-shuke, kuma ana maganar Isra'ila kamar mutum daya ne, kuma kamar shi shuka ne wanda zai yi fure.
An ci gaba da misalin Isra'ila a matsayin wata irar shuka, amma wannan karon a mastayin dogon itacen al'ul a Lebanon, inda aka sani da irin wadannan dogayen itatuwa.
Wannan nassin ya ci gaba da irin misalin nan.
Yahweh yana magana.
Mutanen Isra'ila za su sake rayuwa cikin kariyar Allah. Ana maganar Isra'ila kamar tana zama karkashin inuwarsa.
Ana maganar sabon arzikin Isra'ila kamat amfanin gona.
Kamar yadda ruwan inabin Lebanon ya yi suna, haka Isra'ila za ta yi suna. A.T: "Mutane ko'ina za su ji game da kasar Isra'ila".
Wannan nassin yana nuna cewa Allah zai hana jama'ar Isra'ila bautar gumaka kuma.
Fir itace ne wanda ganyayensa suke nan kore kowane lokaci cikin shekara. Wannan yana wakiltar Yahweh da albarkunsa bisa Isra'ila.
A nan, "'ya'ya", tana wakiltar kowane abu mai kyua da ke zuwa daga wurin Yahweh.
Yusha'u, annabi, yana magana.
Wannana annabin yana morar wadannan tambayoyin don ya fadi cewa mutane masu hikima za su fahimta, su saurari abin yake fada musu.
Ana maganar umurnan Yahweh kamar tafarkun da ake tafiya a ciki.
Ana maganar rashin biyayya ga Yahweh kamar yin tuntube yayinda ake tafiya.
1Wannan ita ce maganar Yahweh da ta zo ga Yowel ɗan Fetuwel.2Ku ji wannan ku dattawa, ku kuma kasa kunne dukkan ku mazauna ƙasar. Ko wannan ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin iyayenku?3Ku faɗa wa 'ya'yanku labarinsa, 'ya'yanku kuma su fada wa tsara mai zuwa.4Abin da bãbe ya rage fara ta ci; abin da da fara ta bari burdunnuwa ta ci; abin da burdunnuwa ta rage; ganzari ya cinye.5Ku mashaya, ku tashi, ku yi ta kuka! Ku yi ta baƙin ciki, ku dukkan mashayan ruwan inabi, don an datse inabinku mai zaƙi daga gare ku.6Don wata al'umma ta zo kan ƙasata, ƙaƙƙarfa mara ƙidayuwa. Haƙoransu haƙoran zãki ne, kuma suna da haƙoran zãkanya.7Sun mayar da kuringar inabina abar wofi. Sun yayyage dangar itacen ɓaurena, sun yayyage dangar sun watsar; rassan sun koɗe sun yi fari.8Ku yi makoki kamar amaryar da ke makokin mutuwar angonta.9An dena miƙa baikon hatsi da na abin sha daga gidan Yahweh. Firistoci, bayin Yahweh suna makoki.10Filaye sun bushe, ƙasa tana makoki saboda an hallakar da hatsi. Sabon ruwan inabi ya ƙare, mai ya kasa.11Ku manoma ku ji kunya, ku yi baƙinciki, hakan nan ku wuraren matse ruwan inabi, saboda alkama da sha'ir. Don abin da aka girbe ya lalace.12Inabi sun kaɗe, itatuwan ɓaure kuma sun bushe, itacen ruman, da kuma na dabino, da gawasa duk da sauran itatuwa sun bushe. Don farinciki ya ƙare daga cikin mutane13Ku firistoci ku sa tufafin makoki, ku firistoci ku yi bakin ciki, ku masu hidima a bagadi ku kwanta cikin tufafin makoki har safiya, ku bayin Allahna. Don an hana miƙa baikon hatsi da na abin sha daga gidan Allahnku.14Ku yi kira a yi azumi mai tsarki, ku kuma yi kira a yi tattaruwa mai tsarki. Ku tattara dattatawa da dukkan mazaunan ƙasar zuwa gidan Yahweh Allahnku, ku yi kuka ga Yahweh.15Kaito saboda ranar! Gama ranar Yahweh ta ƙarato. Tare da ita akwai hallakarwa daga Mai iko dukka.16Ba a ɗauke abinci daga gabanmu ba, an kuma ɗauke farinciki da fara'a daga gidan Allahnmu ba?17Iri ya lalace a kofensa, an wulaƙanta hatsi, an banzantar da wuraren ajiya don hatsi ya yanƙwane.18Yaya dabbobi ke nishi! Makiyayan dabbobi kuma ke shan wahala saboda ba wurin kiwo. Hakannan kuma garken tumaki na shan wahala.19Yahweh, ina kuka gare ka. Don wuta ta cinye makiyayar dake jeji, harshen wuta kuma ya ƙone bishiyoyin dake cikin filayen.20Har da dabbobin jeji suna yi maka kuka, don ƙoramun ruwa sun bushe, wuta kuma ta cinye makiyayar jeji.
Allah ya yi amfani da waka ya yi magana da mutanen Isra'ila ta wurin Yowel
"maganar da Yahweh Allah ya faɗi"
Wannan shine sunan Allah da ya bayyana wa mutanensa a cikin tsohon alkwali. Dubi juyinkalma shafi game da Yahweh don a san yadda za'a juya shi.
Shine mahaifin Joel
AT: "Wannan ba ya taɓa faruwa ko a ƙarnin ka ko na kakaninka ba
garken kwri kamar fari da ke firiya tare kuma su ci amfanin gona mai yawa
ma'anar su kenan: na farko na nufin fara da ta riƙa, kuma na iya firiya, na biyu fari masu yawa da ke firiya tare amma ba da sauki ba, na uku karamar fara da fikafikinta ba su isa na firiya ba, na hudu jaririyar fara da ba ta fara fit da fikafiki ba. Yi amfani da sunan da ke da saukin ganewa a yarenka.
Allah ya dokaci jama'ar Isarila game da zuwan rundunar fari.
idan yaren ku na da kalma ɗaya don bayana "kuka" da "makoki", sai ku haɗa layin ya zama guda ɗaya, kamar haka: "ku mutanen da kuke kaunar ruwan inabi sai ku yi sowa ta bakinciki."
cinciriɗon farin na kama da sojojin yaki
Farin na kama da kasa ko gari da ke zama mutum ɗaya. za ku iya kiran kasar kamar mutum ɗaya, ko ku kira farin "su," ko ku kira mayakan kamar mutum ɗaya.
waɗannan layi biyu na da ma'ana ɗaya. kwatancin hakoran farin da na zaki na nufin yadda suke ɓarnar amfanin gona sai ka ce n share ta.
Gonar Yahweh, gonar inabi, da bishiyar ɓaure
waɗanda suka ga kasar sun cika da matukar damuwa domin asarar da ta same ta.
Alla ya cigaba da magana da jama'ar Isarila
anan an ambata kasar kamar sai kace mutum ne. ko da shike wasu juyin sun fasara wannan surar da wata karin magana: "kasar na makoki."
Allah ya cigaba da magana da jama'ar Isarila
wata irin alkama mai nunna da sauri. Ana amfani da saɓar don a yi gurasa da shi
abu ya bushe har ya mutu
ira iran yaya bishaya wanda ana iya ci.
Allah ya yi magana da firistocin Isra'ila
Allah na gaya wa firistoci da su kaskantadda kan su, su yi kuka da ɓacin rai. AT: "Dukan firistoci sai ku yi makoki da kuka mai zafi ku kuma kaskantadda kanku tawurin yafa rigar sake dukan dare."
waɗannan sune baye bayen yau da kullum na haikali.
wato haikalin da ke Yerusalem
Wannan shine abinda Allah na bukatar firistoci su faɗa.
AT: "Mun ga karewar abincinmu, an kuma ăuke murna da farinciki daga gidan Allahnmu."
"daga garemu." Wannan na nufin dukan kasar Isarila.
Waɗannan kalmomi biyu na da ma'ana guda. Suna nufin babu wani abin farinciki kuma a haikali.
datti mai muni
Allah ya nuna wa firistoci yadda za su yi wa Isarila addu'a.
alamar sanani don zafin jiki
Waɗannan magana biyu na nufin sananin ɓarnar da ta shafi dukan kasar, wato gonakin da an shuka da waɗanda ba a shuka ba duka sun lalace.
kananar rafuffuka
1Ku hura ƙaho a Sihiyona, ku kuma kaɗa kararrawa a kan duwatsuna masu tsarki! Bari dukkan mazaunan ƙasar su gigice don tsoro, Don hakika ranar Yahweh tana tafe, hakika ta kusa.2Rana ce ta duhu baƙiƙƙirin, rana ce ta giza-gizai da baƙin duhu. Kamar yadda duhu ke rufe duwatsu, babbar rundunar sojoji tana kusantowa. Ba a taɓa samun soja kamarta ba, ba kuma za a sake samun kamar ta ba, Koma a bayan tsararraki da yawa.3Wuta na cinye duk abin da ke gabanta, bayanta kuma harshen wutar yana ƙuna. ƙasar ta zama kamar gonar Adnin a gabanta, amma a bayanta akwai jejin da ba komai. Ba kuma abin da zai tsira daga gare ta.4Bayyanuwar sojojin kamar ta dawakai ce, kuma su na gudu kamar mahayan dawakai.5Suna tsalle da ƙara kamar na masu karusa a kan duwatsu, kamar kuma ƙarar wutar da ke cin tarin yayi, kamar ta Sojoji masu iko dake shirye domin yaƙi.6A gabansu jama'a na cikin ƙunci, dukkan fuskokinsu kuma suka yi suwu.7Suna gudu kamar na jarumawa masu iko; suka hau katanga kamar sojoji; suna tafiya a jere kowanne dai-dai a kan sawu, basu kauce matsayinsu ba.8Ba wanda ya tunkuɗe wani a gefe, kowa yana tafiya a gefensa, suka kutsa ta cikin kariyar basu kuma kauce layi ba.9Suka ruga kan birnin, suna gudu a kan ganuwa, suka haura cikin gidaje, suka shiga ta tagogi kamar ɓarayi.10Duniya ta girgiza a gabansu, sammai kuma suka firgita, rana da wata sun duhunta, taurari kuma sun dena haskakawa.11Sai Yahweh ya tada muryarsa a gaban sojojinsa, don sojojinsa suna da yawa sosai, suna kuma da ƙarfi, waɗanda ke karɓar umarninsa. Don ranar Yahweh tana da girma da kuma ban tsoro sosai. Wa zai iya jure mata?12"Amma ko yanzu ma, "Yahweh yace, "Ku juyo wurina da dukkan zuciyarku. Ku yi azumi da kuka, da makoki."13Ku keta zuciyarku ba tufafinku kawai ba, ku komo wurin Yahweh Allahnku. Don shi mai alheri ne da jinƙai, marar saurin fushi kuma ya na cike da alƙawari mai aminci, kuma zai so ya kawar da aiwatar da hukunci.14Wa ya sani? Ko zai juyo ya ji tausayi, ya kuma sa masa albarka, da baiko na hatsi da na abin sha saboda Ubangiji Allahnku?15A hura ƙaho a Sihiyona, a kira ayi azumi mai tsarki, a kuma yi kira ayi tattaruwa mai tsarki.16A tattara jama'a don tattaruwa mai tsarki, a tattara dattawa, a tattara 'yan yara da jarirai masu shan nono. Sai anguna su fito daga ɗakunansu, amare kuma daga kagararsu ta amarcinsu.17Sai firistoci bayin Yahweh su yi kuka a tsakanin bagadi da shirayi. Sai su ce, "Ya Yahweh, ka ceci mutanenka, kada kuma ka mai da gãdonka abin ba a, har al'ummai su yi musu ba a. Me ya sa za su faɗa a cikin al'umai cewa, 'Ina Allahnsu?'"18Sai ya yi kishin ƙasarsa, ya kuma ji tausayin mutanensa.19Yahweh ya amsa wa mutanensa, "Duba zan aiko maku da hatsi, da sabon ruwan inabi, da mai. Zasu wadace ku, kuma ba zan ƙara mai da ku abin wulaƙanci ba a cikin al'ummai.20Zan kawar da maharan nan na arewa daga gare ku, kuma za ku kore su zuwa yasassun wurare. jagoran sojojinsu zai fuskanci gabashin teku. Bãshinta zai tashi, mumunan warinta kuma zai tashi.' Hakika, ya yi manyan abubuwa.21Ƙasa kada ki tsorata, ki yi murna da farinciki, domin Yahweh zai yi manyan abubuwa.22Kada ku ji tsoro, namomin jejin da ke cikin saura, gama tsire-tsiren dake cikin saura zasu tohu, itatuwa zasu bada 'ya'ya, kuma itacen ɓaure da na inabi za su bada "ya'yansu sosai.23Mutanen Sihiyona ku yi murna, kuma ku yi farinciki cikin Yahweh Allanhnku. Don zai baku ruwan sama da bazara ya kuma buɗe sakatun sama dominku, ruwan bazara da na koramunku kuma kamar dã.24Masussuka za ta cika da alkama, wurin matsar inabi kuma zai cika da sabon ruwan inabi da mai.25"Zan komo maku da shekarun da kuka yi asarar hatsinku wanda fãra ta cinye wato wannan farar mai hallakarwa da na aiko cikinku.26Za ku ci ku ƙoshi sosai, ku yabi sunan Yahweh Allahnku, wanda ya aikata abubuwan al'ajabi a cikinku, kuma ba zan taɓa sake kawo abin kunya akan mutane na ba.27Za ku san cewa ina cikin Isra'iila, kuma ni ne Yahweh Allahnku, kuma babu wani sai ni, kuma ba zan ƙara kawo kunya akan mutanena ba.28Bayan wannan kuma zan zubo da Ruhuna ga dukkan mutane, 'ya'yanku maza da mata za su yi anabci. Tsofaffinku zasu yi mafarkai, samarinku kuma zasu ga wahayi.29Kuma ga bayi da mata bayi, a waɗancan kwanaki zan zubo musu da Ruhuna.30Zan nuna al'ajabai a sama da kuma a duniya, jini, da wuta, da murtukewar hayaƙi.31Rana zata duhunta, wata kuma zai zama jini, kafin babbar ranar nan ta Ubangiji mai ban tsoro ta zo.32Zai zama kuma dukkan wanda ya yi kira ga sunan Yahweh zai tsira. Don a dutsen Sihiyona da kuma a cikin Yerusalem za a sami waɗanda suka tsira, kamar yadda Yahweh ya ce, da kuma cikin waɗanda suka rayu, wato waɗanda Yahweh ya kira.
Yowel ya cigaba da wakar ta da fara a sura ta farko.
Joel yana jaddada mahimmancin kiran Isarila wuri ɗaya don shirin masifar da ke zuwa.
kamominnan biyu, wato, "baka" da "duhu" suna da manufa daya, kuma suna jaddada girman duhun. dukan su biyu suna kwatanta masifa ko hukunci daga Allah. AT: "ranar da ke cike da duhu" ko kuma "ranar hukunci mai zafi."
wato bakar duhu ko kuma duhu irin ta yammaci
wannan maganar na da manufa iri daya kamar yadda take a baya. "gajimare" da "bakar duhu" na nufin hukuncin Allah. AT: "ranar da ke cike da duhu da kuma iskar gajimare."
AT: "babbar rundunar mayaka na saukowa daga duwatsu zuwa kasar. Sun bazu a kasar kamar hasken ranar safiya."
kalmominnan "babbar" da "runduna" suna da ma'ana kusar ɗaya, kuma suna jaddada karfin mayakan. A: "Babbar rundunar fari." (UDB) ko kuma "babbar rundunar mutane mayaka."
Misalin mayakan da ke zuwa, bisa ga Joel ta cigaba.
Gonar Eden tana da matukar kyau.
wannan kwatancin ɓarnar da wutar ta ke yi ne.
kwatancin ta cigaba tare da muryoyin mayaka masu dawakai.
doki dabba ce mai gudun gaske. Tana da kafafu hudu.
kan fara na kama da kan doki, kuma mayakan na da karfi da kuma sauri kamar doki.
mayakan suna da garaje, kamar yadda masu sukuwa ke dashi.
doki ta kan yi tsalle yayin da ta ke gudu sosai.
an kwatanta wannan da muryar fari masu yawa.
Joel ya cigaba da kwatanta rundunar farin da Yahweh ya aiko.
An kwatanta rundunar farin da asalin sojoji.
wato ganuwa kewaye the garuruwa.
bayanin fari a matsayin mayakan Yahweh ta cigaba.
A: sun ci galaɓa a kan sojojin da ke tsaron kasar.
farin sun yi matukar yawa har da kasa da tsarari sun girgiza, kuma dukan hallitun sararin sama basu ganuwa kuma.
Yahweh ya nuna ikon Allah da karfinsa bisa mayakan. AT: "Yahwe ke da iko"
a cikin wannan magana, dukan su biyu suna faɗin abu ɗaya. AT: "yana da muni sosai."
AT: "Babu wanda ke da karfin da zai tsira daga hukuncin Yahweh."
A: "Ku juyo daga barin zunubanku sai ku yi imani da ni tawurin mika kai."
yagan tufafi alamar kunya ne da tuɓa. "yaga zuciya" na nufin halin sahihiyar tuɓa daga zuciya ba da baki kaɗai ba.
bari
"Wata kila Yahweh zai juyo daga fushinsa... Allah."
ɗaki a gidan iyaye da amarya ta kan jira ranar bukin aurenta.
jama'a Isra'ila sune mutanen Allah na musamman.
AT: "Bai kamata wasu kasashe suce Allahn Isarila ya bashe da mutanensa ba."
"kasar isarila"
"Jama'ar Isra'ila"
"Kasa kunne ga abinda nake so in faɗa"
"abinda bai cancanji ban girma ba"
Allah ya cigaba da alkawarinsa ga Isarila
waɗannan fuskoki na daidai da yadda mazaunan Isarila ke gani.
"kaɗa ku ji tsoro, ku mazaunan kasar,"
bishiyoyi da ke da kyau don abinci zasu girma a kasar
farkon ruwar damina a farkon watan disamba da kuma ruwan damina na karshe a watan hudu da biyar
manyan abubuwa don zuɓa abu mai ruwa ruwa
"gonakin da kun lura da su matuka amma fari masu yawa sun cinye"
dubi yadda kun juwa waɗannan maganganu a 1:4.
Yahweh ya cigaba da alkawarin abubuwa masu kyau wa mutanensa Isra'ila.
Allah ya cigaba da alkawarin abubuwa masu kyau wa mutanensa Isra'ila
"Zan bayar a yalwace kamar yadda mutum na yafa ruwa."
"dukan mutane"
Yahweh ya cigaba da furta abubuwan da zai yi a nan gaba.
"jini" na misalin mutuwan mutane. A: "mutuwa, wuta da gajimare"
Anan, kalmar nan "jini" na nufin jan kala. zaku iya rubuta shi haka: A: "sai watan zai juya ya zama ja kamar jini"
a nan, kalmar "babba" na kara wa kalmar "matsifa" ma'ana." A: "babbar ranar ban razana."
Duka biyun na nufin wuri guda ne. AT: "bisa dutsen Sihiyona a Yerusalem."
AT: "wanda Yahweh ya kira zasu zama masu tsira."
waɗanda suka wanzu bayan yaki ko kuma babbar matsifa.
1A waɗannan kwanaki da lokatai, sa'ad da na komar da masu zaman talalar Yahuda da Yerusalem,2Zan tattara dukkan al'ummai in kuma kawo su kwarin Yehoshafat. A can zan yi masu shari'a, saboda jama'ata da abin gãdona Isra'ila, waɗanda suka warwatsar cikin al'ummai, saboda kuma sun raba ƙasata.3Sun kuma jefa ƙuri'a kan mutanena, sun sayar da yaro saboda da karuwa, sun kuma sayar da yarinya saboda ruwan inabi don su sha.4Yanzu don me kuke fushi da ni, ku Taya, da Sidon da dukkan yankin Filistiya? Ko za ku sãka mani? Ko da ma kun sãka mani nan da nan zan komo muku da ramuwarku a kanku.5Don kun ɗauke zinariyata da azurfata, kun kuma kawo kayayyakina masu daraja zuwa cikin masujadanku.6Kun sayar da mutanen Yahuda da na Yerusalem ga Girkawa, don ku cire su can nesa da ƙasarsu.7Duba, ina gab da in tayar da su, daga inda kuka sayar dasu, ku ne kuma za ku biya kuɗin fansa da kanku.8Zan sayar da 'ya'yanku maza da mata ta hannun mutanen Yahuda. Za su sayar da su ga Sabiyawa, ga al'umma mai nisa, Don Yahweh ne ya furta.9Yi wannan shela a cikin al'ummai, 'Ku shirya kanku domin yaƙi, ku horar da manyan mutane, ku bar su su zo kusa, ku bar dukkan jarumawan yaƙi su hauro nan.10Ku mayar da dumɓayen garemaninku takkuba, ku kuma mayar da wuƙaƙenku mãsu. Sai raunana su ce "muna da ƙarfi."11Ku yi sauri ku zo ku makusantan ƙasashe, ku tara kanku wuri ɗaya a can. Yahweh ya kawo ƙarshen mayaƙanku masu iko.'12Bari al'ummai su tada kansu tsaye su zo kwarin Yehoshafat. Don a can zan zauna don in yi wa dukkan al'umman da ke kewaye shari'a.13Ku ɗauki lauje don girbi ya nũna. Ku zo, ku mãtsi abin sha, don tulunan ruwan inabi sun cika. sun cika suna zuba, saboda muguntarsu tana da yawa sosai."14Akwai hayaniya, a cikin Kwarin Hukunci. Gama ranar Yahweh ta kusa a cikin Kwarin Hukunci.15Rana da wata sun zama baƙi, taurari kuma sun dena bada haskensu.16Yahweh zai yi ruri daga Sihiyona, ya kuma tada murya daga Yerusalem. Duniya da sammai za su girgiza, amma Yahweh zai zama mafaka ga mutanensa, da kuma kagara ga mutanen Isra'ila.17"Da haka za ku sani cewa ni ne Yahweh Allahnku wanda ke a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Daga nan Yerusalem zata tsarkaka, kuma ba wani sojan da zai ƙara ratsa ta.18A wannan rana kuma duwatsu zasu cika da ruwan inabi mai zaƙi, tuddai kuma za su kwararo da madara, dukkan ƙoramun Yahuda za su ɓulɓulo da ruwa, magudanu za su zo daga gidan Yahweh su jiƙe kwarin Shittim.19Masar zata zama yasasshiya, Idom kuma ta zama jejin da a ka yi watsi da shi, saboda tayarwar da a ka yi wa mutanen Yahuda, saboda an zubar da jinin marasa laifi a ƙasarsu.20Gama za a zauna a Yahuda har abada, Yerusalem kuma zata zama wurin zama na dukkan zamanai.21Zan yi ramuwar da ban yi ba tukuna a kan jininsu," don Yahweh yana zaune a Sihiyona.
Allah ya ci gaba da faɗin abubuwa masu zuwa
Kalmar "Duba" a nan ya kara mahimmanci ga magana na gaba.
maganar nan "a wancan lokaci" na nufin abu guda da maganar nan "a waɗancan kwanaki" ko kuma "a daidai wancan sa'a."
AT:"Idan na aiki waɗanda suka tafi bauta su dawo Yahuda da Yerusalem"
Waɗannan maganganu biyu sun nuna yadda Yahweh ke ɗaukan Isarila a matsayin mutanensa masu tamani. A: "mutanen isarila, wato waɗanda sun zama kayan gadona.
wannan misalin abin da suka yi ne, bai nuna da cewa sun yi shi wa wasu yara kayatattu ba. A: "sun yi abubuwa kamar sayar da yaro don su sadu da karuwa da sayar da yarinya don su sami ruwan inabi su sha."
Allah ya yi magana da mutanen kasashen da ke kewaye da Isarila
Allah yayi amfani da waɗannan kalmomi don ya tsauta wa Taya, da Sidon da Filistiya. AT: "ba ku da dama ku yi fushi da ni"
"Za ku yi ramako a kai na?" Allah ya yi amfani da wannan tambaya don ya sa mutanen su yi tunani game da abubuwan da suke yi. AT: "Ku na sammani za ku iya yin ramako a kai na"
a nan, kalmar na "Kai" na nufin mutumin. Ramakon da suke son so mayar a kan Yahweh, shi zai sa ya faru da su. AT: "Zan sa ku ku sha wahallar ramakon da kun yi kokarin sa mani"
"ramako" ko "sakaiyya"
Jama'ar Isra'ila zasu bar wuraren da suka zama bayi su kuma dawo kasar Isarila
A: "ba ka abinda ya kamanceka"
A: "ta karfin mutanen Yahuda" ko kuma "ta wurin mutanen Yahuda"
Mutanen Sabeya, wanda ana kiranta da Sheba. Mutanennan suna zama kudu da Isra'ila.
waɗannan magana guda biyu na nufin a shirya sojoji domin yaki.
"shirya mayaka domin ko ta kwana"
Maganganun nan biyu na da manufa ɗaya, wato su mayar da kayan aikin gona su zam kayan yaki.
abinda ake amfani da shi domin hudar kasa domin shirin shukin amfani
wukaken da ake amfani da su don yankan kananan ratsa da kuma girɓi
"Ku tattaro kanku domin shirin yaki."
A tsakiyar tsakon Yahweh zuwa ga abokan gaban Isra'ila, wannan magana zuwa ga Yahweh ne. Watakila ya zama haka ne don abokan gaban Isra'ila su ji tsoron mayakan Yahweh.
yahweh ya cigaba da magana da kasashen.
Kalmomin nan "kasashen" da kuma "kasashen da ke kewaye" na nufin kasashen da ke kewaye da Yahuda. Yahweh zai shar'antasu a gaɓar Yehoshafat domin abinda suka yi wa Yerusalem.
wasu daga ma'anar maganar nan sune 1) hari akan kasar da ke cike da zunibi na kama da girɓin inabi da kuma matsar ruwarsa, ko kuma 2) hanzarin hukunta kasashen da ke cike da zunubi na kama da hanzarin da ke cikin girbi da kuma matsar inabi.
doguwar tankwararrar wuka da ake amfani da ita don girbin hatsi.
"hatsin ya yi daidai na girɓi"
Yahweh na kwatanta kasashen da damin inabi a mamatsar inabi, wanda ke shirye domin a matsa. AT: "zo, tattaka kasashen, gama suna kama da inabin da ke cikin mamatsar inabi.
Yahweh na kwatanta muguntarsu da ruwan inabin da ke gangarowa daga mamatsa zuw mataranta. Mataran bata da girman da za ta dauki yawan mugunta da ke gangarowa a cikinsu.
ruɗani shine surutun da ke fitowa daga in da mutane dayawa suka taru. An maimaita kalmar don a nuna yawan surutun da ke fitowa daga mutanen.
an maimaita wannan magana don a nuuna da cewa lailai ne ta faru.
Maganarnan biyu na nunawa da cewa yahweh zai ta da murya mai karfi, mai kara daga Yerusalem. Idan yarenku na da kalma ɗaya ne kawai don misalta kalmar mgana da karfi, sai a mai da maganar ta zama guda ɗaya. A: "Yahweh zai ta da murya daga Yerusalem"
Wasu daga ma'anar maganarnan su ne 1) "yahwe zai yi ruri kamar zaki" ko kuma 2) "yahweh zai yi ruri kamar tsawa."
Rurin Yahweh na da karfi sosai har ya sa sama da kasa su girgiza.
dukan su na nufin Yahweh zaai tsare mutanensa. Maɓuya wuri ne mai karfi don ƙare mutane a lokacin yaki. A: "Yahweh zai zama mafaka mai karfi ga mutanensa"
Allah ya cigaba da magana akan ranar Ubangiji.
"ruwan inabi mai zaƙ zai ɖigo daga duwatsu." wannan magana ne kawai don a nuna da cewa kasar na da taki dayawa. A: "a bis duwastun za a sami gonar inabi mai yawa da zai bada yaya masu zaƙi
"madara zai gangara daga tuddai." A: "a bisa tuddai shanun ku da awakin ku zasu bada madara mai yawa."
"ruwa zai gangara zuw kowace rafi da ke Yahuda
"za a aiko ruwa zuwa kwarin Akasiya." "Shitim" suna wta wuri ne a gabas da Kogin Yodan. Tana nufin "bishiyar Akasiya."
A: "za'a rushe Masar, mutane zasu bar ta" ko kuma kasashen da ke gaɓa da ita zasu rushe ta, mutanen Masar kuma zasu bar kasarsu"
"Edom zata zama busasshiyar daji, mutane kuma ba zasu zauna a cikinta ba"
"domin kunci da tsanani da Masar da Edom suka nuna wa mutanen Yahuda"
"jinin marasa laifi" na nufin mutanen da su ka kashe ba dalili. A: "domin masar da Edom sun kashe marasa laifi a kasar mutanen Yahuda"
Yahweh ya ci gaba da magana game da ranar Ubangiji.
za a iya mai da maganar kamar haka: AT: "mutane zasu wanzu a kasa Yahuda har abada"
A: "daga tsara zuwa tsara, mutane zasu wanzu a kasar Yerusalem"
A: "zan hukunta magabatan da suka kashe jama'ar Isra'ila waɗanda basu sami hukunci ba
1Waɗannan sune abubuwa game da Isra'ila wanda Amos, ɗaya daga cikin makiyaya a Tekowa ya karɓa a wahayi. Ya karɓa waɗannan abubuwa a kwanakin da Azariya ke mulkin Yahuda, da kuma kwanakin Yerobowam ɗan Yehowash ke sarautar Israila, shekaru biyu kafin girgizar ƙasa.2Ya ce, "Yahweh zai yi ruri daga Sihiyona; zai yi tsawa da murya mai ƙarfi daga Yerusalem. Wuraren kiwo na makiyayan za su bushe; ƙwanƙolin Karmel zai yi yaushi."3Wannan shi ne abin da Yahweh yace: "Domin zunubai uku na Damasku, har don huɗu ma, Ba zan janye hukuncin ba, domin sun zalunci mutanen Gileyad da maƙamai na ƙarfe.4Zan aika da wuta a kan gidan Hazael, kuma za ta cinye kagarar Ben-hadad.5Zan karya makaran kyamran Damasku zan kuma kau da mutumin da ke rayuwa a Kwarin Aben, da kuma mutumin da yake rike da sandar girma a Bet Iden. Mutanen Aram za su tafi bauta a Kir," inji Yahweh.6Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na Gaza har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, domin su ne suka ɗauke kamammun mutane dukka, don su miƙa su ga mutanen Idom.7Zan aika da wuta akan garun Gaza, za ta kuma lakume kagarorinta.8Zan yanke mutumin da yake rayuwa a Ashdod da kuma mutumin da ya ke riƙe da sandar girma daga Ashkelon. Zan juya hannu na gãba da Ekron, kuma sauran Filistiyawa za su hallaka," inji Ubangiji Yahweh.9Wannan shi ne abin da Yahweh yace: "Domin zunubai uku na Taya, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, don sun miƙa dukkan mutanen zuwa Idom, kuma sun karya yarjejeniyar yan'uwantakarsu.10Zan aika da wuta akan garun Taya, kuma za ta ƙone kagarorinta."11Wannan shi ne abin da Yahweh yace, Domin zunubai uku na Idom, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, don ya farauci 'ɗan'uwansa da takobi ya kuma kawar da dukkan tausayi. Ya cigaba da fushi, fushinsa ya ɗore har abada.12Zan aika da wuta akan Teman, kuma za ta cinye fadodin Bozra."13Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na mutanen Ammon, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, don sun farke mata masu ciki na Gileyad, saboda su ƙara faɗaɗa yankinsu.14Zan kunna wuta a garun Rabba, kuma za ta cinye fadodin, tare da ihu a ranar yaƙi, tare da rugugin hadari a ranar guguwar.15Sarkinsu zai tafi zuwa bauta, tare da sauran jami'ansa," inji Yahweh.
Komai da Allah ya sa Amos ya fahimta ta wurin abin da Amos ya gani ko ya ji.
Wadannan bayanai biyu suna da ma'ana iri daya. Duka biyun suna jaddada cewa Yahweh yana magana da babbar murya yayinda yake shirin hukunta al'mmar.
kamar 1) zaki, ko 2) tsawa
Wannan ne sunan Allah, wanda ya bayyana wa mutanena a Tsohon Alkawari. Duba shafin fassara Kalma a kan Yahweh game da yadda za ka fassara wannan.
"Saboda yawan zunubai... saboda dumbin zunubai" ko "Saboda... sun yi zunubi sosai, sun yi zunubi fiye da yadda zan kyale"
AT: "Tabbas zan hukunta wadannan mutanen"
A nan "datse" yana nufin "hallaka" ko "kora".
Wadansu juyi na zamani sun fassara wannan a matsayin wannan mutumin da yake zaune a Bikat-aven.
Wadansu juyin zamani sun fassara wannan da ma'anar, "Mutanen da suke zama a Bikat-aven". Juyin da ke da "mutumin" sukan fassara wannan furcin da ma'anar sarki.
sunayen birane
dabam da Gonar Aiden
sarki ko hakimi
Duba yadda ka fassara wadannan kalmomin a 1:3.
A nan, "datse" yana nufin "hallaka" ko "kora".
Wadansu juyin zamani sun fassara wannan da ma'anar, "Mutanen da ke zama a Ashdod". Juyin da ke da "mutumin" sukan fassara wannan da ma'anar sarki.
Wadansu juyin zamani sun fassara wannan a matsayin mutumin da yake zama a Ashdod.
ko "Zan yi fada da Ekron"
Duba yadda ka fassara wadannan kalmomin a 1:3.
"yarjejeniyar da suka yi domin nuna wa juna 'yan'uwantaka"
Duba yadda ka fassara wannan a 1:3.
"fushinsa yana nan har yanzu"
Sunayen birane.
Duba yadda ka fassara wadannan kalmomin a 1:3.
"munanan abubuwa da yawa suna faruwa duka a lokaci guda"
kadawar iska iri biyu masu tsanani
wani irin hadarin da iska take jujjuyawa kamar zobe
1Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na Mowab, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, don ya ƙone ƙasusuwan sarkin Idom zuwa toka.2Zan aika da wuta akan Mowab, kuma za ta cinye kagarorin Keriyot. Mowab zai mutu a hargitsi, tare da sowa da kuma busa ƙaho.3Zan lalata mai shari'a a cikinta, zan kuma kashe dukkan 'ya'yan sarki tare da shi," inji Yahweh.4Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na Yahuda, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, domin sun ƙi dokar Yahweh kuma sun ƙi dokokinsa. Ƙarerayinsu sun jawo su yin tafiya ba dai dai ba, kamar yadda ubanninsu su ka yi tafiyar.5Zan aika da wuta akan Yahuda, kuma za ta cinye kagarorin Yerusalem."6Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na Isra'ila, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, domin sun sayar da salihai don azurfa da kuma masu bukata akan takalma.7Sun tattake kawunan talakawan kamar mutane na taka ƙura a ƙasa; suna ture matalauta a gefe. Mutum da ubansa su kwanta a wurin budurwa ɗaya kuma su na ɓata sunana mai tsarki.8Sun kwanta a gefen kowanne bagadi akan tufafin da aka bayar jingina don bashi, kuma a cikin gidajen Allahnsu sukan sha ruwan inabin waɗanda aka yi wa tãra.9Ga shi na hallakar da Ba'amore a gaban ku, dogaye masu tsawo kamar itatuwan sida; ya na da ƙarfin kamar rimaye. Ga shi na lalata 'ya'yan itatuwansa na sama da jijiyoyin ƙasa.10Kuma na fito da ku daga ƙasar Masar na kuma bi da ku a cikin daji shekaru arba'in, na kuma ba ku ƙasar Amoriyawa.11Na ta da annabawa daga cikin 'ya'yanku, waɗansu kuma daga cikin samarin sun zama Naziriyawa. Ko ba haka ba ne, ya ku mutanen Israila? Yahweh ne ya faɗa12Amma kun sa Naziriyawa shan ruwan inabi kun kuma umarci annabawa da kada su yi anabci.13Duba, zan ragargaza ku kamar yadda amalanke cike da hatsi yake ragargaza mutum.14Ko wani mai gudu ma ba zai tsere ba, mai ƙarfi ba zai ƙara wa kansa ƙarfi ba; ko mai iko ya ceci kansa.15Mai baka ba zai iya tsayawa ba; mai saurin gudu ba zai tsira ba; mahayin doki ba zai ceci kansa ba.16Ko ma sojojin da suka fi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan - wannan furcin Yahweh ne.
Duba yadda ka fassara wadannan kalmomin a 1:3.
abn da yakan rage sa'adda aka kona wuri da wadansu irin duwatsun ruwa.
Wannan sunna birni ko gari.
"Mutanen Mowab za su mutu"
Duba yadda ka fassara wadannan kalmomin a 1:3.
Wannan furcin a nan yana iya nufin "aloolin karya" ko "gumaka".
Anan maganar bautar gumaka kamar mutanen suna tafiya a bayan wadannan allolin karyan.
Duba yadda ka fassara wannan a 1:3.
jawo rauni ta wurin tattakewa da karfi a kai a kai
"sun ki su saurara sa'adda matalauta suka ce ana yi musu rashin adalci"
"suna da tsawo kamar itatuwa mafiya tsawo da ka sani, kuma da karfi kamar katako mafi karfi da ka sani"
Ka yi kokarin fassara wadannan kalmomin a hanya daya duk sa'adda suka bayyana a wannan littafin.
AT: "Saurara" ko "Maida hankali ga abin da zan fada muku".
"mai harbi da baka zai gudu"
"za a kama mai saurin gudu"
"mahayin dokin zai mutu"
Ma'ana tana iya zama 1) "gdud ba tare da makamansa ba", ko 2) "gudu ba tare da tufafi a jiki ba".
Fassara wadannan kalmomin kamar yadda ka yi a 2:11
1Ku saurari maganar da Yahweh ƙe faɗa akan ku, ku mutanen Isra'ila, akan dukkan iyalinku, na fito da ku daga ƙasar Masar. Ku kaɗai na zaɓa daga kowanne iyalai a duniya.2"Saboda haka zan hukunta ku don zunubanku."3Zan yiwu mutanen biyu su yi tafiya tare, ba tare da yarda ba?4Zai yiwu zaki yayi ruri a daji ba tare da ya sami kome ba? Zai yiwu ƙaramin zaki yayi gurnani a kogonsa idan bai kama kome ba?5Zai yiwu tsuntsu ya faɗi akan ƙasa idan ba a kafa masa tarko ba? Zai yiwu tarko ya zargu daga ƙasa idan bai kama wani abu ba?6Zai yiwu mutane su rasa firgita idan suka ji ƙarar ƙaho a birni? Zai yiwu wata masifa ta auko wa birnin amma Yahweh bai aiko ta ba?7Hakika Ubangiji Yahweh ba zai aikata komai ba ba tare da ya baiyana wa bayinsa annabawa ba.8Zaki yayi ruri wane ne ba zai ji tsoro ba? Ubangiji Yahweh yayi magana; wane ne ba zai yi anabci ba?9A yi shelar wannan a kagarar Ashdod da kuma kagarar ƙasar Masar; a ce, "Ku tara kanku akan duwatsun Samariya ku ga babban shashanci a cikinta, da kuma irin danniyar da ke cikinta.10Domin ba su san abin da ya ke dai dai ba - wannan furcin Yahweh ne. Sun cika da tashin hankali da barnar kagarorinsu."11Saboda haka, wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh yace, "Abokin gãba zai kewaye ƙasar. Zai nuna ƙarfinsa ya rushe kagarorinka."12Wannan ne abin da Yahweh yace: "Kamar yadda makiyayi ya kan ceci ƙafafu biyu kadai na tunkiya daga bakin zaki, ko gutsarin kunne, hakanan kuma ke ma daga cikin mutanen Isra'ila wanda yake zama cikin Samariya, a gefen taragon jirgi kaɗai ko a gefen gado."13Ku ji ku kuma shaida game da gidan Yakubu - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne, Allah mai runduna,14"A ranar da zan hukunta Isra'ila saboda zunubai, zan kuma hukunta bagadodin Betel. ƙahonin bagadi za su kakkarye su kuma fadi a ƙasa.15Zan lalata gidan hunturu tare da na bazara. Gidajen da aka yi da hauren giwa zasu lalace, babban gidan shi ma zai lalace, - wannan furcin Yahweh ne.
Wannan maganar Yahweh tana zuwa ga mutanen Isra'ila, dukkan iyalan Yahweh da aka fitar daga Masar.
Yahweh ya zabi Isra'ila daga cikin dukkan iyalan duniya.
Allah zai amsa wadannan tambayoyin a 3:7.
Allah zai amsa wannan tambaar a 3:7.
"Sai Ubangiji Yahweh ya fara bayyana... annabawa, kamin ya yi wani abu"
Fassara kalmomin an kamar yadda ka yi a 2:11.
wata kujera mai tabshi, wadda ke da girmar da za a iya kwanciya a kai
Wannan nassin a Ibraniyanci yana a wahalar fassara, kuma wadansu juyin zamani sun fassara shi dabam. Fassara UDB, wanda wadansu juyin zamani suka mora, yana amfani da kamance, kamar yadda mamallakin gida yake iya ceton kalilan cikin kayayyaki sa'adda gidansa ya kama da wuta.
Yi kokarin fassara wadannan kalmomin a hanya daya duk lokacin da suka bayyana a wannan littafin.
Wadanan suna kama da kahonnin bijimai da suke fita daga gefen da suka hadu a sama, kuma alamu ne na nuna yadda allahn yake da karfi.
"dukkan gidajen"
hakora da kahonnin manyan dabbobi
Fassara wannan kamar yadda ka yi a 2:11.
1Ku ji wannan maganar, ku shanun Bashan, ku na cikin dutsen Samariya, ku dake danne matalauta, ku dake hallaka mabukata, ku dake cewa da mazajenku, "Kawo mana abin sha."2Ubangiji Yahweh ya rantse da sunansa mai tsarki, "Ku duba, ranaku na zuwa akan ku da za a tafi da ku da ƙugiya, na ƙarshenku tare da fatsar kifi.3Za ku fita ta wurin da ya tsage a jikin garun birnin, kowannenku zai tafi ta cikin tsaguwar, za a jefar da ku waje wajen Harmon - wannan furcin Yahweh ne."4Ku tafi Betel ku yi zunubi, tafi Gilgal ku ƙara zunubi, ku kawo hadayarku kowacce safiya, zakkarku kowane kwanaki uku.5Ku mika gurasarku shaidar haɗayar godiya; ku yi shelar baikon yaddar rai, ku sanar da su, wannan dai dai ne, gare ku mutanen Isra'ila - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne.6Na ba ku tsabtatattun hakora a cikin dukkan biraninku da kuma ƙarancin gurasa a dukkan wurarenku. Duk da haka ba ku juyo gare ni ba - wannan furcin Yahweh ne.7Na kuma hana ruwan sama daga gare ku a lokacin da akwai sauran watanni uku a yi girbi. Na sa a yi ruwa a birni daya, kuma na sa ka da a yi ruwa a wani birnin. Ɗaya daga cikin sashen ƙasar an yi ruwa amma ɗaya sashen ba a yi ruwa ba ya bushe.8Birane biyu ko uku suna ƙishi har ma sun tafi neman ruwa a birnin, amma ba su ƙoshi ba. Amma duk da haka ba ku komo wurina ba - wannan furcin Yahweh ne.9Na sa ma ku ƙunci tare da darɓa da raɓa. Yawan lambunanku da gonakin inabinku da itatuwan ɓaurenku da itatuwan zaitun ɗinku fari sun laƙume su dukka. Duk da haka ba ku juyo gare ni ba - wannan furcin Yahweh ne.10Na aika ma ku da annoba irin wanda na aika wa Masar. Na kashe samarinku da takobi, an ɗauke dawakanku, an cika hancinku da ɗoyi. Amma duk da haka kun ki juyo wa gare ni - wannan furcin Yahweh ne.11Na hallakar da biraninku kamar yadda Allah ya hallakar da Saduma da Gwamrata. Kamar sandar da aka fizge daga wuta. Duk da haka ba ku juyo gare ni ba - wannan furcin Yahweh ne.12Domin haka zan yi wani abu mummuna a kanki, ya Isra'ila; shirya don ki sadu da Allahnki, Isra'ila!13Ku duba, wanda ya yi duwatsu ya kuma halicci iska, ya baiyana tunaninsa ga mutum, ya maida safiya duhu, ya auna wurare na Duniya. Yahweh, Allah mai runduna, shi ne sunansa."
Wadanan maganganu biyu suna da ma'ana kusan daya, kuma suna jaddada cewa abokin gaba zai kama mutanen kamar yadda mutane suke kama kifi. AT: "nasara a kan dukkanku, su tilasa muku ku tafi tare da su" ko "su sa ku a kan kugiyoyi kamar kifi, su tafi da ku".
wuraren da abokan gaba suka fasa ganuwar birni don su shiga
"za su jefar da ku zuwa wajejen Harmon" ko "abokan gabanku za su tilasa muku ku bar birnin ku nufi wajejen Harmon"
Wannan yana iya zama sunan wani wurin da ba mu sani ba. Ko kuma, yana iya nufin Dutsen Harmon, kuma wadansu juyi na zamani sun fassara shi a haka.
An yi amfani da wannan furcin don nuna cewa abubuwan da Allah ya fada za su faru hakika Fassara wadannan kalmomin kamar yadda ka yi a 2:11.
"Da yake kun ki ku tuba, hadayunku da kuke mikawa a Betel da Gilgal suna kara fusatar da ni ne kawai"
Idan yarenku yana da hanyar nuna cewa mutanen sun ki su gane cewa yin wadannan abubuwan ba zai taimake su ba, amma kuma ba za su daina yin su ba, to, za ka iya morar ta a nan.
Maimakon "kowace rana ta uku", wadansu juyi suna da "kowace shekara ta uku". Wannan haka ne domin ya kamata Isra'ilawa su kawo zakkarsu ga Alah sau daya kowace shekara uku.
Fassara wannan kamar yadda ka yi a 3:13.
"yunwa" ko "rashin abinci"
AT: "ba ku daina yi mini zunubi ba"
Fassara wadannan kalmomin kamar yadda ka yi a 2:11.
"Wadansu lokua nakan ba ku ruwan sama kadan, wani lokaci kuma in ba ku ya wuce kima"
cutar da busar da shuka ta kashe ta
wani abu mai girma a kan abubuwan da suka dade da danshi.
Fassara kalmomin nan kamar yadda ka yi a 4:6.
Fassara wadannan kalmomin kamar yadda ka yi a 2:11.
AT: "cika iska da doyin sansaninku" ko "ba za ku iya tsira daga doyin sansaninku ba".
wari mara kyau, musamman da matattun mutane
AT: "Na gaggauta fitar da ku daga cikin wuta kamar ku sanda mai konewa ne" ko "na bar ku kun dan kone kamin na gaggauta fitar da ku daga cikin wutar".
Fassara wadannan kalmomin yadda ka yi a 4:6.
Fassara wadannan kalmomn yadda ka yi a 2:11.
Yahweh yana fada wa jama'ar Isra'ila cewa, dole su shirya gamuwa da Allahnsu.
Yahweh, Allahn runduna, ya hallici duwatsu, ya kuma bayyana ufinsa ga bil'adama.
1Ku ji wannan maganar dana ɗauke ta kamar ta makoki da zan yi a kanku, gidan Israi'la.2Budurwa Isra'ila kin faɗi, ba za ki ƙara tashi ba, an yasheta a ƙasarta; ba wanda zai ta da ita.3Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Birnin da ya fita tare da dubu zai dawo da ɗari kaɗai, kuma wanda ya tafi da ɗari amma goma kaɗai za su rage na gidan Isra'ila."4Wannan shi ne abin da Yahweh ya ce da gidan Isra'ila: "Ku neme ni ku kuma tsira!5Kada ku nemi Betel; ko ku shiga Gilgal; ka da ku tafi Biyasheba. Gama babu shakka ita ma za ta tafi bauta, kuma Biyasheba za ta zama wofi.6Ku nemi Yahweh ku rayu, ko ya taso ma gidan Yosef kamar wuta. Zai kuwa laƙume, ba kuma wanda zai kashe ta a Betel.7Mutanen nan na juya adalci zuwa abu mai ɗaci kuma suna jefar da ayyukan adalci a ƙasa!"8Allah ya yi manyan taurari tare da haskensu; ya maida duhu haske; ya maida rana dare shi ne kuma ya kira ruwan teku; ya ƙwararo shi a fuskar duniya. Sunansa Yahweh ne!9Ya kawo hallaka a kan ƙarfafa don lalacewar ta kai kan kagarori.10Ku na ƙin duk wanda ya ƙwabe ku a ƙofar birnin, kuma tare da duk wanda zai faɗi gaskiya.11Domin kun matsa wa talakawa kuna ƙwace alkama daga gare su - koda yake kun gina gidajenku da dutse, ba za ku zauna a cikinsu ba. Kuna sha'awar gonakin inabinsu, kuma ba za ku sha ruwan inabin ba.12Domin na san yawan laifofinku, kuma da girman zunubanku - kuna wulakanta masu kirki, ku na karɓar rashawa ku na hanawa talakawa adalci a wurin shari'a.13Saboda haka mai hikima shiru yake a waɗanan lokatai, don mugun lokaci ne.14Ku nemi yin nagarta ba mugunta ba, saboda ku rayu. Don Yahweh, Allah mai runduna, ya kasance tare da ku, kamar yadda ku ka ce ya ke.15Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta, ku yi adalci a cikin majalisa. Watakila Yahweh, Allah mai runduna, zai yi wa sauran da su ka ragu na Yosef alheri.16Saboda haka wannan shi ne abin da Yahweh yace, Allah mai runduna, Ubangiji, "Za a yi kuka da kururuwa a kowanne wurin taruwa za su kuma ce a dukkan tituna, 'Kaito! Kaito!' Za su kira manoma su yi makoki kuma masu makokin su yi kuka mai zafi.17A cikin dukkan gonakin inabinku za a yi kuka da kururuwa, don zan wuce a tsakiyar ku," inji Yahweh.18Kaito ga ku dake marmarin zuwan ranar Yahweh! Me ya sa ku ke jiran ranar Yahweh?19Za ta zama baƙa bakikirin kuma babu haske, kamar wanda ya gujewa zaki ya fada a bakin damisa, ko kuwa kamar wanda ya komo gida ya sa hannunsa a bango, maciji kuma ya sare shi.20Ko ranar Yahweh za ta zama haske ne ba duhu ba? Almuru ne ba haske ba?21Na ki bukukuwanku ba na murna da tarurukanku.22Ko da ya ke kun kawo mani baikon ƙonawa da baikonku na hatsi ba zan karɓe su ba, ba kuma zan dubi tarurukan baye-bayenku na manyan dabbobinku ba.23Ku kawar mani da hargowar waƙoƙinku; ba zan saurari kaɗe-kaɗenku da bushe-bushenku ba.24Maimakon haka ku sa adalci ya kwararo kamar ruwa, adalci kuma ya zama kamar kogin da ba ya ƙafewa.25Gidan Isra'ila ko kun kawo mani hadaya da baye-baye a cikin jeji har shekaru ariba'in?26Duk da haka ku ka ɗauki siffofin Sakkut sarkinsu da Kaiwan, allolinku na taurari- gumakan da kuka yi wa kanku.27Saboda haka zan sa ku yi ƙaura gaba da Damaskus," inji Yahweh, wanda sunansa Allah mai runduna ne.
"mutanen Isra'ila sun yi mumunar mutuwa... za su ... suna... tashe su"
Wadannan jumla tana magana ne kan duk wani biranen da ya aika sojoji da yawa
"Ku zo wurina domin taimako"
"Betel za ta hallaka gaba daya". AT: "mutane za su zo su hallaka Betel kurmus"
"zai zama kamar wutar da take barkewa farat daya ta hallaka komai"
kiran miyagun ayyuka abubuwa masu kyau, da yi da abubuwan alherin kamar ba su da muhimmanci
ko "karkata shari'a" ko "aikata abin da ba daidai ba amma ku ce daidai ne"
ko "kuna yi da gaskiya kamar ba ta muhimmanci kamar kazanta"
kungiyar taurari
"zalunci matuka"
"ba ku barin mabukata su kawo kararrakinsu gun alkalai"
Wadanda ba su so mugayen mutane su cutar da su, ba za su yi magana game da miyagun ayyukansu ba.
ko "ku tabbatar cewa an aiwatar da adalci a wuraren shari'a a kofofin birni"
kuka mai karfi sosai
AT: "Bai kamata ku yi marmarin zuwan ranar Yahweh ba!"
"munanan abubuwa, ba masu kyau ba, za su abku a wanan ranar"
AT: "Hakika, ranar Yahweh za ta zma duhu, ba haske ba!" ko "munanan abubuwa, ba masu kyau ba, za su faru a ranar Yahweh!"
Kalmar "raina" tana jaddada tsananin kalmar "ki" ne. Tare duk kalmomin biyu suna jaddada tsananin kin da Yahweh yake yi wa bukukuwansu na addini. AT: "Na ki bukukuwansu sosai".
surutai masu cika kunne
AT: Mai yiwuwa 1) "Ban umurce ku ku kawo mini hadayu ba... Isra'ila!" ko 2) "Ba ni kuka kawo wa hadayu ba... Isra'ila!"
allolin kafirai
Ko "Kiyyun"
1Kaiton waɗanda ke zama sake a Sihiyona, da ke da kariya a tudun ƙasar Samariya, da ku da kuke sanannun mutane da suka fi na kowacce al'umma, ga waɗanda gidan Isra'ila ke zuwa don taimako!2Shugabaninku sun ce, "Mu je Kalne mu duba, daga wurin ku je Hamat, babban birnin, sa'an nan har zuwa Gat ta Filistiyawa. Sun fi mulkokinku biyu daraja ne? Ko kuwa, yankin ƙasarsu ya fi naku ne?"3Kaiton waɗanda suka kawar da ranar masifa suka kuma sa mulkin hargitsi ya zo kusa.4Suna kwance kan gadajen hauren giwa suna jin daɗin miƙe jiki a dogayen kujerunsu. Sun ci naman 'yan raguna daga garke da naman 'yan maruƙa daga turke.5Suna raira waƙokin wofi da giraya; kuna amfani da kayan aiki kamar Dauda.6Suna shan ruwan inabi daga manyan kwanoni sa'an nan su shafe jikinku da mai mafi kyau, amma ba su yin makoki saboda lalacewar Yosef.7To yanzu sune na fari da zasu tafi bauta, kuma bukukuwanku da shagulgulanku zasu wuce.8Ni, Ubangiji Yahweh na rantse da kai na - wannan furcin Ubangiji Yahweh, Allah mai runduna, na ƙi girman kan Yakubu; ba na son kagaransa. Saboda haka zan miƙa birnin da duk abin dake ciki.9Ko da zai zama mutane goma ne suka rage a gida ɗaya, zasu mutu dukka.10Sa'ad da dangin mamacin ya zo don ya ɗauki gawar mamatan -wanda zan ƙone su bayan ya fitar da gawarwaki daga gidan - sai yayi kira ga wanda ya ke a cikin gidan, ko akwai wani kuma a nan? Idan wannan mutum zai ce, "A'a." Sai ya ce, "Ka yi shuru, don ba za mu ambaci sunan Yahweh ba."11Duba, Yahweh zai ba da umarni, babban gida buge shi za a yi ya ragargaje, ƙaramin gida kuma ya rushe.12Dawakai sukan yi gudu a ƙonƙolin duwatsu? ko da wanda zai iya huɗa da shanu a can? Duk da haka ku ka mai da adalci dafi kuma ku ka mai da nagarta mugunta.13Ku da kuke murna akan Lo Dibar, wanda yace, "Ba mu ɗauke Karnaim ta wurin ƙarfinmu ba?"14Ku duba zan ta da wata al'umma ta yi gãba da ku, gidan Isra'ila -- wannan shi ne furcin Ubangiji Yahweh, Allah mai runduna. Zasu ƙuntata ma ku tun daga Lebo Hamat zuwa kwarin Araba."
zama cikin kwanciyar hankali, ba tare da damuwa cewa Allah zai hukunta su ba
AT: "Ba su masarautunku nan naku biyu ba".
"Yankin kasarsu bai kai naku girma ba" ko "Wadannan kasashen sun fi kankanta fiye da Yahuza da Samariya".
"aikata abubuwan da za su sa Allah ya kawo mugayen mutane su shar'anta ku"
"masarautar abokan gaba mai fitnar gaske"
A wannan lokacin Isra'ilawa sukan ci abinci yayinda suke zaune a kan tabarma ko wata kujera.
"gadaje masu hauren giwa a kansu, don su kaa musu kyau" ko "gadaje masu tsada"
hakora da kahonnin manyan dabbobi
"kwanciya kamar mutanen da ba su son yin aiki"
kujeru masu taushi sosai da za a iya kwanciya a kai
Ma'anar tana iya zama: 1) suna kirkiro sabobbin wakoki da hanyoyin kada kayan kida, ko 2) suna kirkiro sabobbin kayan kida.
kwanonin da ake amfani da su a hidimar haikali, suna da girma fiye da wanda mutum yakan yi amfani da su wajen cin abnci
"ba su bakin cikin su nuna kamar wani kaunatacce ya mutu"
Fassara wannan kamar yadda ka yi a 3:13.
"Na ki mutanen Isra'ila domin suna dogara da mafakarsu, ba ni ba, don ta kare su"
ganuwa da aka gina kewaye da birane don kare su daga mahara
Ma'anar wadannan kalmomin ba a bayyane suke ba. Tana iya zama: 1) "Dangin mamacin" shi ne wanda zai "fitar da gawar" ya "kone", kuma yana magana da wani wanda ya bye a gidan bayan an kashe mutum goma a iyalin gidan, ko 2) "Dangin mamacin" wanda "ya zo don ya fitar da gawar" wani ne dabam daga wanda "zai kone" gawar, kuma suna magana da juna a gidan: "dangin mamacin ya don ya dauki gawar tare da wanda zai kone gawar bayan an fitar da gawar daga gidan - idan yayinda suke cikin gidan, sai dan'uwan ya ce wa mai kone gawar, "Ko... kai?"
kona gawa
jikunan matattu
"Saurara" ko "Maida hankali ga abin da zan fada muku".
Wadannan maganganu biyu suna da ma'ana kusan iri daya. Bambanci tsakani "babban gida" da "karamin gida" yana nufin cewa anan maganar dukkan gidaje. Ma'ana tana iya zama: 1) Yahweh zai umurci wadansu su hallaka kowane gida, ko 2) Yahweh da kansa zai rushe kowane gida da kansa ta wurin ba da umurni.
AT: "abokin gaba zai rushe babban gidan, ya rugurguje shi"
Za ka iya morar kalma daya domin wadannan kalmomi biyun.
AT: "za a rushe karamin gidan kaca-kaca"
Amos ya mori tambayoyi biyu don jawo hankali ga tsautarwar da ta biyo baya.
Ba zai yiwu doki ya i sukuwa a kan duwatsu ba tare da jin rauni ba. Amosa ya mori wannan salon tambayar domin tsautar musu saboda ayyukansu.
Babu wanda yake huda a kan duwatsu. Amos yana morar wannan salon tambayar don ya tsautar musu saboda ayyukansu.
"Amma kun maida dokoki abin cutar jama'a"
"kuna horon wadanda suka aikata daidai"
Babu wanda ya san inda wadannan biranen suke a da.
AT: "saurara" ko "maida hankali ga abin da zam fada muku".
Fassara wannan kamar yadda ka yi a 3:13.
AT: "daga iyakokin arewar kasarku zuwa iyakokin kudu"
dan karamin rafi da ke gudana a lokacin damina kadai
1Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya nu na mani. Duba, ya sa fari sun yi cincirindo lokacin da aka fara yankan hatsi, duba lokacin girbin baya ne bayan an cire na sarki.2Bayan sun gama cinyen kowanne ɗanyen ganye a ƙasar, sai na ce, "Ubangiji Yahweh, idan ka yarda ka yi gafara, yaya Yakubu zai tsira? Don shi ƙarami ne ainun."3Yahweh kuwa ya dakatar da nufinsa. Ya ce, "Ba zai faru ba."4Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya nuna mani: Duba, Ubangiji Yahweh ya yi kira akan wuta ta shari'a. An busar da fili mai yawan gaske, ruwa mai zurfi a ƙarƙashin duniya an kuma lalata ƙasa.5Amma na ce, "Ubangiji Yahweh, idan ka yarda ka tsaya; Yaya Yakubu zai tsira? Don shi ƙarami ne."6Yahweh kuwa ya dakatar da wannan. "Wannan ma ba zai faru ba," inji Ubangiji Yahweh.7Wannan shi ne abin da aka nuna mani: Duba, Ubangiji ya tsaya gefen bango, yana rike da magwaji a hannunsa.8Yahweh yace da ni, "Amos, me ka gani? Sai na ce, "Magwaji." Sai Ubangiji yace, "Duba, zan sa magwaji a wurin mutanena Isra'ila. Ba zan sake barin su ba.9Wurare masu bisa na Ishaku za a lalace, wuraren sujada na Israila za su zama kufai, kuma zan yi gãba da gidan Yerobowam da takobi."10Sai Amaziya, firist na Betel, ya aika da saƙo zuwa Yerobowam sarkin Isra'ila: "Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a cikin gidan Isra'ila. Ƙasa ba za ta iya ɗaukan dukkan maganganunsa ba.11Wannan shi ne abin da Amos yace, 'Yerobowam zai mutu ta takobi, kuma babu shakka Isra'ila zai tafi bauta daga ƙasarsa.'"12Amaziya yace da Amos, "Mai gani, tafi da gudu. koma ƙasar Yahuda, a can za ka nemi gurasa ka ci ka kuma yi annabci.13Amma kada ka ƙara yin annabci a nan Betel don nan wurin yin sujadar sarki ne kuma gidan sarauta ne."14Sai Amos yace wa Amaziya, "Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi. Ni makiyayi ne, kuma mai lura da itatuwan ɓaure.15Amma Yahweh ya ɗauke ni daga kiwo sai ya ce da ni, 'Tafi, yi annabci ga mutanena Isra'ila.'16Yanzu ji maganar Yahweh. Ka ce; "Ka da ka yi annabci gãba da Isra'ila, kuma kada ka yi magana gãba da gidan Ishaku.'17Saboda haka ga abin da Yahweh yace, 'Matarka za ta zama karuwa a birni, za a karkashe 'ya'yanka maza da mata da takobi; ƙasarka za a gwada ta a kuma rarraba; kai kanka za ka mutu a cikin ƙasa marar tsarki, kuma babu shakka Isra'ila zai tafi bauta daga ƙasarsa.'"
Marubucin yana fada wa mai karatu cewa yana dab da fadin wani abin mamaki. Mai yiwuwa yarenka yana da hanyar yin wannan.
"Yakubu ba zai tsira ba!"
Marubucin yana fada wa mai karatu cewa wani abin mamaki yana dab da faruwa. Mai yiwuwa yarenka yana da hanyar yin wannan.
AT: "Hakika, Yakubu ba zai tsira ba!" ko "ina roko, ka fada wa Yakubu abin da zai yi don ya tsira!"
siriryar igiya mai wani dan abin nauyi a gefe daya, wadda ake mora a gini dan tabbatar da cewa bango yana a mike sama da kasa
jama'ar masarautar arewacin ta Isra'ila
Ma'ana tana iya zama: 1) Amaziya shi ne kadai firist a Betel, ko 2) Amaziya shi ne shugaban firstoci a Betel.
AT: "Amosa yana tsakiyar kasar Isra'ila, kuma yana shirin aikata miyagun ayyuka gare ka"
"Mai yiwuwa jama'ar su yarda da shi, sa'annan kuma su yi abubuwan da za su hallakar da kasar"
"ka ga ko za ka iya sa mutanen wancan wurin su biya ka saboda yin anabci"
Mai yiwuwa a nan wannan yana nufin "wanda yake kula da tumaki", da yake an kira shi "makiyayi" a 1:1.
A nan, wannan furcin yana nufin duk wata kasar waje, inda jama'ar ba karbabbu ba ne a gun Allah.
1Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya nuna mani. Duba, ga kwandon itacen ɓaure na kaka!2Ya ce, "Me ka gani, Amos?" Na ce "Kwandon itacen ɓaure na bazara." Sai Yahweh yace da ni, "ƙarshen mutanena Israila ya zo; Ba zan sake barin su ba.3Waƙoƙin haikali za su zama na makoki. A wannan rana -- wannan furcin Ubangiji Yahweh ne -- gawawwaki zasu yawaita, a ko'ina za a jefar dasu waje. Shuru!"4Ku saurari wannan, ku da ku ke tattake masu bukata ku na fitar da matalautan ƙasar.5Sun ce, yaushe ne sabon wata zai wuce, saboda ko ma sake sayar da amfanin? Yaushe ne Asabar za ta ƙare, ko ma sake sayar da alkama? Za mu rage girman ma'aunin mu kuma ƙara farashi, yayin da muke zalunci da ma'aunin ƙarya.6Wannan zai sa mu sayar da alkama mara kyau, mu saye talakawa da zinariya, kuma masu bukata da takalma."7Yahweh ya rigaya ya rantse ta wurin fahariyar Yakubu, "Babu shakka ba zan manta da kowanne aikinsu ba.8Shin ƙasar ba za ta girgiza a kan wannan ba, dukkan wanda ke cikinta zai yi baƙinciki? Dukkan ƙasar za ta hau ta sauka kamar Kogin Nilu, kuma za ta juya ta kuma sake dulmiyewa, kamar kogin Masar.9Za ya zama kuwa a wannan rana - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - zan mai da rana ta faɗi da tsakar rana, zan kuma sa duniya ta duhunta a rana kata.10Zan mai da bukukuwanku makoki kuma waƙoƙinku su zama makoki. Zan sa maku tufafin makoki, in kuma sa kowa ya aske kansa. Zan sa ku yi makoki kamar iyayen da suka rasa ɗan su tilo, kuma ranar mai daci ce har karshen ta.11Duba, ranaku na zuwa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - da zan aiko da yunwa a ƙasar, ba yunwa don gurasa ba, ko kishin ruwa, amma domin rashin samun sakon magana daga wurin Yahweh.12Zasu yi ta tangaɗi daga teku zuwa teku; zasu yi gudu daga arewa zuwa gabas suna neman sakon maganar Yahweh, amma ba kuma zasu samu ba.13A wannan rana kyawawan 'yan'mata da samari zasu faɗi saboda ƙishi.14Waɗanda suka yi rantsuwa da zunubin Samariya suka kuma ce, 'Muddin allahnku na raye, Dan,' 'Muddin hanyar zuwa Biyasheba nanan' -- za su faɗi kuma ba zasu ƙara tashi ba."
AT: "Saurara" ko "Maida hankali ga abin da zan fada maka"
Fassara wannan yadda ka yi a 3:13.
"a wurare da yawa"
Amos yana magana da wadanda suke "sayarwa" da "kasuwanci" (8:5).
Duba yadda ka fassara wannan a 2:7.
"Kowane lokaci suna tambayar lokacin da sabuwar wata za ta wuce domin su sayar da hanti kuma, da kuma lokacin da Asabar zai wuce domin su yi kasuwancin acca".
'Yan kasuwan za su yi amfani da ma'aunin zalunci da ke nuna kamar yawan ahtsin da suke awo ya fi yawan yadda yake a zahiri, sa'anna yawan kudin bai kai yadda ya yake ainihi ba.
AT: "mu sayi masu fatara da farashin takalma bi-shanu"
"Yahweh ya rantse da kansa, ya ce" ko "Yahweh, wanda Yakubu yake fahariya da shi ainun, ya rantse"
wani suna da ake kiran Kogin Nilu
Fassara wannan yadda ka yi a 3:13.
Fassara wannan kamar yadda ka yi a 3:13.
Wadansu za su yi tafiya a hankali su fadi a saukake, kamar mutumin da yake yunwa, wadansu kuma za su yi ta kai da komowa da sauri.
Ma'ana tana iya zama: 1) duba UDB, ko 2) "daga teku zuwa teku, daga arewa zuwa gabas, Za su yi ta kai da komowa suna neman maganar".
Ga mutumin da ke tsaye a Betel, wannan yana iya zama kewaye: Mataccen Teku (kudu) zuwa Bahar Maliya (yamma) zuwa arewa zuwa gabas.
rasa dukkan karfinsu
Mai yiwuwa wannan yana nuni da hanyoyin da matafiya za su bi ta Biyersheba domin su bauta wa gumaka a can.
1Na ga Ubangiji tsaye wajen bagadi, sai yace, "Bugi saman ginshiƙan don harsasan dukka su girgiza. Farfasa su gunduwa-gunduwa akan kowannen su, ni kuma zan kashe su da takobi. Babu ɗaya daga cikinsu da zai tsere.2Ko da za su nutse cikin Lahira, can hannu na zai kamo su. Ko da sun hau sama, zan sauko da su.3Ko da sun ɓuya a bisa kololuwar Karmel, can ma zan neme su in cafko su. Ko da sun ɓoye daga ganina a karkashin teku, can ma zan bada umarni ga maciji, shi kuma zai sare su.4Ko da sun tafi bauta ta hannun abokan gãbarsu, can ma zan bada umarni ga takobi, takobi kuwa za ya kashe su. Zan sa idanuna a kansu don azaba ba nagarta ba."5Ubangiji Yahweh mai runduna ya taɓa ƙasa har ta narke, dukkan waɗanda suke cikinta suna baƙinciki; dukkan abin da ke cikinta zasu tashi kamar Kogi, za ta kuma nutse kamar kogin Masar.6Shi ne ya gina matakansa a sammai, ya kafa maɓoyarsa a bisa duniya. Ya kira ruwan teku ya ƙwararo a bisa fuskar duniya, sunansa Yahweh ne.7"Ku ba kamar mutanen Kush ba ne gare ni, mutanen Isra'ila? - wannan furcin Yahweh ne. Ba na fito da Isra'ila daga ƙasar Masar da Filistiyawa daga Krit da Aramiyawa kuma daga Kir ba?8Duba, idanuwan Ubangiji Yahweh suna kan mulkin nan mai zunubi, kuma zan lalata su daga fuskar duniya, sai dai ba zan hallaka gidan Yakubu kakaf ba -wannan furcin Yahweh ne.9Duba, zan ba da umarni, zan kuma rairayi gidan Isra'ila a cikin al'ummai, kamar wanda yake tankaɗan hatsi, don kada a rage ko ɗan ƙaramin dutse ya faɗi a ƙasa.10Dukkan masu zunubi daga cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, waɗansu za su ce, 'Masifa ba za ta auko mana ko ta kusan ce mu ba!'11A wannan rana zan ta da rumfar Dauda wanda ta faɗi, zan toshe kafafe. Zan ta da lalatattun wurarenta, in kuma sake gina ta kamar kwanakin dă.12Ta haka zasu ci nasara ga waɗanda su ka ragu a Idom, da kuma dukkan al'ummai da suke kira da sunana - wannan furcin Yahweh ne - shi ne ya yi wannan.13Duba, kwanaki na zuwa - wannan furcin Yahweh ne - sa'ad da mai huɗa zai riga mai girbi, mai matse ruwa inabi kuma zai riga mai shuka iri nan da nan. Duwatsu zasu zubo da ruwan inabi mai zaƙi, dukkan tuddai kuma su kwararo da shi.14Zan dawo da mutanena Isra'ila daga bauta. Za su giggina biranensu da su ka rurrushe su kuma zauna a ciki, zasu dasa gonakin inabi su kuwa sha ruwan inabinsu, za su yi lambuna su kuma ci amfanin 'ya'yansu.15Zan dasa su a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumbuke su daga ƙasar da na ba su ba," inji Yahweh Allahnku.
Wannan yana iya nufin: 1) kakkarya bangarorin haikalin, ko 2) rusa saman ginshikan.
AT: "Ko da ina suka yi kokarin zuwa, ina can don in kama su".
wata muguwar dabbar teku da ba a sani ba, ba macijin Gonar Aidan ba, ba kuma macijin da aka sani ba
Idan yarenka yana da wata kalma da ku nufin mai magana yana so ya yi wa wadansu alheri amma kuma za a iya morar ta sa'adda mai magana yake so ya aikata abin cutarwa, za ka iya amfani da ita a nan.
kalmomin da ke tabbatar da cewa mai ji ya gane "domin cutarwa"
Mai yiwuwa wadannana ne matakalan da mutanen zamanin da suke tunanin cewa suna kaiwa fadar Allah a sama. Amma, wadansu juyin zamani suna ba da wata ma'ana ta kalmar Ibraniyancin kamar "fada" ko "dakuna". A nan, ami yiwuwa "matakalansa" wata hanyar cewa fadar Allah ce.
Wadansu juyi su fassara, "ya kafa ginshikansa bisa duniya", wato, ginshikan da duniya take zama a kai.
Fassara wadannan kalmomin yadda ka yi a 2:11.
Misalin a nan na hatsi ne yana ficewa ta rariya, sa'annan ana tsai da duwatsun. Wadansu juyi sun fassara "ko mafi kankantan dutse ma ba zai fadi ba" da manufar hatsi mai kyau din ba zai fadi ta cikin rariyar tare da abin da ba a so ba.
wata sakar wayoyi ko zare ce mai kananan ramummuka wadda kananan abubuwa ke shigewa ta ciki amma tana tsai da manayn abubuwa daga wucewa.
Bayan Yahweh ya hallaka masarautar Isra'ila, za ta zama kamar alfarwar da katakanta suka fadi, ganuwar da ta rugurguje, da kuma gidan da aka rushe.
ragowar ganuwar da ta fadi
abin da ya rage bayan an rusa gini
Ko dai abin da Isra'ila ba ta riga ta yi asara a kai ba a yankin, ko jama'ar Edom.
Mai rubutu yana fada wa mai karatu cewa zai fadi wani abin banmamaki. Mai yiwuwa yarenka yana da hanayar yin wannan.
Wadannan maganganu biyu suna da ma'ana kusan daya, kuma suna jaddada cewa kasar za ta ba da amfani sosai.
AT: "babu wanda zai sake tumbuke su daga kasar", "za su zauna a kasar har abada kamar itacen da jijiyoyinta suka yi zurfi cikin kasa"
tuge shuka da jijiyoyinta daga cikin kasa
1Wahayin Obadiya. Ubangiji Yahweh ya faɗi haka a kan Idom: Mun ji bayani daga wurin Yahweh cewa an aika da jakada a cikin al'ummai, da cewa, "Tashi tsaye! Bari mu tashi mu kai mata hari!"2Ga shi zan mayar dake 'yar ƙarama a cikin al'ummai, za a rena ki ƙwarai.3Girman kai na zuciyarki ya ruɗe ki, ke da ki ke zaune a can cikin kogunan dutse, cikin ƙayataccen gidanki; a cikin zuciyarki, kin ce, "Wane ne zai saukar da ni can ƙasa?"4Ko da zaki tashi sama kamar gaggafa, ko da zaki kai sheƙarki cikin taurari, zan sauko dake ƙasa, inji Yahweh.5Idan ɓarayi suka zo wurinki, idan 'yan fashi suka zo wurinki da daddare - dubi yadda za a maishe ki kufai! - ba za su saci abin da suke buƙata ba ne kawai? Idan masu tattara inabi suka zo, ba zasu rage kala ba?6Yadda aka bincike Isuwa, harma da abin da ya ɓoye dukka an bincike!7Dukkan mazajen da suka ƙulla amana da ke zasu kore ki har kan iyaka, mazajen da suke zaune lafiya da ke sun ruɗe ki, sun ci nasara a kan ki. Waɗanda suka ci abincinki sun ɗana maki tarko. Babu fahimta a cikinsa.8Yahweh yace a waccan rana, "Ba zan ce a hallaka ma su hikima daga cikin Idom ba, da masu ganewa daga cikin dutsen Isuwa ba?"9Jarumawanki zasu karaya, Teman, domin a datse kowanne mutum daga dutsen Isuwa ta wurin yankawa.10Saboda ta'addancin da aka yi wa ɗan'uwanki Yakubu, kunya za ta rufe ki, za a datse ki har abada.11A ranar da ki ka tsaya a ware ke kaɗai, a ranar da bãƙi suka kwashe dukiyarsa, bãƙi suka shiga ƙofofinsa, suka jefa ƙuri'a a kan Yerusalem, kema ki na kamar su.12Amma kada ki yi murna a cikin ranar ɗan'uwanki, a ranar da ya yi asara, kuma kada ki yi farinciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu; kada ki yi fahariya a ranar baƙincikinsu.13Kada ki shiga ƙofar mutanena a ranar masifarsu; kada ki yi murna a cikin ƙuncinsu a ranar bala'insu; kada ki washe dukiyarsu a ranar rushewarsu.14Kada ki tsaya a mararrabar hanyoyi, domin ki datse masu neman tsira da miƙa kuɓutattun mutanensa a ranar ƙuncinsu.15Gama ranar Yahweh ta kusa a kan dukkan al'ummai. Kamar yadda ki ka yi, haka za a yi maki, abin da kika yi zai dawo kanki.16Kamar yadda kika sha a kan dutsena mai tsarki, haka dukkan al'ummai za suyi ta sha. Za su sha su haɗiye su zama kamar basu taɓa kasancewa ba.17Amma a Dutsen Sihiyona za a sami waɗanda suka tsira, kuma zai zama da tsarki; gidan Yakubu kuma zasu mallaki mallakarsu.18Gidan Yakubu zai zama wuta, gidan Yosef kuma zai zama harshen wuta mai ci, gidan Isuwa kuma zai zama tattaka, za a ƙone su a hallakar da su. Ba wanda zai tsira daga gidan Isuwa, gama Yahweh ya faɗi."19Waɗanda suke daga Negeb zasu mallaki dutsen Isuwa, na Sefilah kuma za su mallake ƙasar Filistiyawa. Za su mallaki ƙasar Ifraim da ƙasar Samariya; shi kuma Benyamin zai mallaki Giliyad.20Masu zaman bauta na mutanen Isra'ila masu yawa zasu mallaki ƙasar Kan'ana har zuwa Zerefat. Masu zaman bauta na Yerusalem, waɗanda ke Sefarad zasu mallaki biranen Negeb.21Masu kuɓutarwa za su hau zuwa Dutsen Sihiyona za su yi mulki a ƙasar kan tudu ta Isuwa, mulkin kuma zai zama na Yahweh.
Wannan shine sunan Allah wadda ya bayana wa mutanensa a Tsohon Alƙawari.
AT: "Yahweh ya aiko da Jakada"
"Tashi saye". Ana amfani da wannan don a gaya wa mutane su shiirya.
AT: "kalla" ko "saurara" ko "kasa kunne ga abinda ina so in faɗa maku"
"jama'an wasu kasashe zasu ki ku"
Wannan shine taken littafin. AT: "Sakon Obadiya" ko "Annabcin Obadiya"
Chingabar ruyar da Obadiya ya gani game da Idom
Ubangiji yayi amfani da gababuwan jikin mutum domin ya bayyana girmankai da ke cike a cikin jama'an kasar Idom
"cikin tsaguwa na dutse".
"A gidan ka da aka gina a kan tudu"
Wannan tambayar ya nuna girmankan Idomawa da shike sun sammanci babu abinda zai taɓa su. AT: "Na tsira daga dukan hari na miyagu."
Waɗannan maganganu biyu suna nuna wa da cewa Idom tana gine a bisa tuddai fiye da sammani, wato an gina ta a bisa tuddai masu tsawo sosai.
Ana kwatanta girmankai da wuri mai tsawo, saukinkai kuma da wuri da ke kasa kasa. Ubangiji ya ce zai tsauko da Idom kasa, wato zai kaskantar da ita kenan. AT: "Zan kaskantar da ke"
Ubangiji ya cigaba da bayar da tsako wa Obadiya game da Edom
"ko kuma, Idan mafasa sun zo cikin dare"
masu satar kaya da karfi daga mutane
Yahweh ya yi wannan magana a tsakiyar jumla domin ya nuna da cewa hukuncin Idom abin razana ne. AT: "aiya, an hallaka ta kurmus."
AT: "Za su saci daidai da su ne kaɗai."
AT: "Aiya, magabta sun bincike Isuwa; sun nemi ɓoyayyiyar dukiyar sa."
bincike domin a saci abubuwa
Yahweh ya cigaba da bayar da tsakonsa wa Obadiya game da Idom.
Kalman nan "ku" na nufin kasar Idom kenan
"zan kore ku daga kasar su." Jama'a kasar Idom zasu yi kokarin neman mafaka a kasashen da suke dangantaka da su, amma waɗannan kasar ba zasu yadda jama'ar Idom su zauna a kasarsu ba.
"Idom ba zata fahimta ba."
Yahweh yace, "A ranar nan, lallai zan hallaka ... dutsen Isuwa."
Gwarzayen ki zasu ji tsoro
Sunar wata gari ne a cikin kasar Idom.
AT: "domin kaɗa a sami mutum ko ɗaya dutsen Isuwa, don magata sun kashe su duka.
Yawancin kasar Isuwa cike da duwatsu ne, wannan shine yadda ake kiran kasar Isuwa.
Yahweh ya cigaba da bai wa Obadiya tsako a kan Idom
AT: "danginka waɗanda sune zuriyar Yakubu."
"za ka cika da kunya kwarai"
AT: "ba zaka rayu ba daɗai."
"mutum ya tsaya ba tare da ya iya yin taimako ba"
mutane daga wasu kasashe
Kalmar "sa" na nufin "yakubu," wannan shine wata sunan da a ke kiran jama'ar Isarila
wannan magana na nufin "sun yi canki canki don su san wanene kayayyaki masu kyau da suka ɗeɓo daga Yerusalem zasu zama na sa."
"yananan kamar dama kuna ɗaya daga cikin bakinna."
Yahweh ya cigaba da bai wa Obadiya tsako game da Idom.
"kaɗa ku yi farinciki" ko "kaɗa ku ji dadi domin"
wannan shine yadda ake kiran jama'ar Ialila domin yakubu da Isuwa su yanuwane.
AT: "ranar hukunci" ko kuma "lokacin hukunsi."
"matsifa" ko kuma "damuwa"
"a ranar da magabatansu suka hallakasu."
"domin ita ce lokacin da suke shan wahalla."
dukan waɗannan juyi ne daga kalma guda ɗaya. Masu juyi su yi amfani da kalma daya domin juyin kalmomi guda ukun nan.
"domin mummunar abinda ya faru da su."
"kaɗa ku ɗauki dukiyrsu" ko "kɗa ku saci dukiyarsu."
wuri wanda hanyoyi biyu suka ketare juna
"a kashe jama'ar Isra'ila waɗanda suna kokarin tsira" ko "a kama waɗanda suke kokarin tsere." (UDB)
"kaɗa ka kwaso waɗanda ke da rai ka bai wa magabata.
Yahweh ya cigaba da bai wa Obadiya tsako don Idom
Ba da jimawa ba Yahweh zai nuna wa dukan kasashe da cewa shi ne Ubangiji
AT: "zan yi maka dai dai kamar yadda kuka yi wa shauran kasashe."
AT: "za ku sami sakamakon abubuwan da kuka yi."
Karmar nan "ku" na nufin jama'an Yahuda
Annabawa sun kwatanta mutanen da Yahweh ya horar da shan horo daga Yahweh. AT: "kamar yadda na horaceku."
Haka ake kiran Yerusalem
AT: "zan hukunta dukkan kasashe babu iyaka." Yahweh ya hukunta Yerusalem, amma ya dakanta domin kaɗa ya hallaka dukan mutanen. Duk da haka, zai hukunta sauran kasashe har sai sun kare.
Yahweh ya cigaba da bai wa Obadiya tsakonsa
Wanɗannan sune mutanen da suka wanzu bayan hukuncin Yahweh. AT: "tsira daga hukuncin Yahweh"
kalmar "ita" na nufin dutsen sihiyona
Yahweh ya kwatanta gidajen Yakubu da na Yosef da wuta domin zasu hallaka Isuwa kamar yadda wuta ke cinye yayi kurmus ba da ɓata lokaci ba.
"yayi" ko "kaikayi." wannan shine busasshiyar jikin amfanin gona wanda an rigaya an girbe hatsi daga jiki.
kalmar "su" na nufin gidan Yakubu da gidan Yosef ne.
kalmar "su" na nufin zuriyar Isuwa waɗanda sune kasar Idom.
"Ba ko mutum ɗaya daga gidan Isuwa da zai tsira."
"Zuriyar Benyamin" ko kuma "jama'an Benyamin"
"ɗumbin jama'ar Isra'ila da suke a kasar bauta
taruwar jam'a masu yawa
wannan sunar kasa na foneshiyawa da ke gaɓar tekun mediteraniya tsakanin Taya da Sidon
wannan sunan wuri ne da ba a iya gane ta ba
wannan na nufin shugabannin sujojin Isra'ila dabam dabam da Allah zai yi amfani da su domin su ci nasara a kan kasar Idom.
1Maganar Yahweh ta zo ga Yona ɗan Amittai, cewa,2"Ka tashi ka tafi Nineba, babban birnin nan, ka yi magana gãba da shi, saboda muguntarsa ta zo gare ni."3Amma Yona ya tashi ya gudu daga gaban Yahweh ya tafi Tarshish. Ya tafi Yofa ya sami jirgin da zai tafi Tarshish. Ya biya kuɗin tafiya Tarshish. Domin ya gudu daga fuskar Yahweh.4Amma sai Yahweh ya aika da babbar iska a kan teku wadda ta zama hadari mai ƙarfi ta sa jirgin ya yi ta kaɗawa kamar zai fashe.5Sai masu tuƙin jirgin su ka ji tsoro sosai mutanen suka yi ta addu'a kowanne ga allahnsa. Sai suka zubar da kayan da ke cikin jirgin a cikin teku domin su rage nauyin jirgin. Amma Yona yana can cikin ƙarshen jirgi yana barci mai nauyi.6Sai mai tuƙin jirgin ya zo ya same shi yace da shi, "Barci ka ke yi? Tashi! Ka kira ga allahnka! Ko allahnka zai ji ya cece mu daga hallaka."7Sai suka ce da junansu, "Ku zo mu jefa ƙuri'a mu gani ko wane ne ya sa muka shiga wannan masifa." Da suka jefa ƙuri'a sai ta faɗa kan Yona.8Sai suka ce da Yona, "In ka yarda ka gaya mana wane ne ya sa wannan masifa ta same mu. Mene ne aikinka, daga ina ka ke? Daga wacce ƙasa ka ke, kai ɗan wacce kabila ne?"9Yona yace da su, "Ni Ba'ibrane ne; kuma ina jin tsoron Yahweh, Allah na sama, wanda ya halitta sama da teku da busasshiyar ƙasa."10Sai mutanen suka ƙara jin tsoro suka ce da Yona, "Me ka yi kenan?" Sun sani cewa ya gudu ne daga wurin Yahweh, gama ya faɗa masu.11Sai suka ce da Yona, "Me za mu yi maka domin tekun ya kwanta?" Saboda tekun na ƙara yin hauka.12Sai Yona yace masu, "Ku ɗauke ni ku jefa cikin tekun. Tekun kuwa zai yi shiru domin ku, gama na sani saboda ni ne wannan babban hadari ya same ku."13Amma duk da haka, mutanen suka yi ta ƙoƙari domin su mallako jirgin ya dawo bakin gãɓa, amma suka kasa saboda tekun yana ta ƙara yi masu hauka.14Sai suka yi kuka ga Yahweh suka ce, "Mun roƙe ka, Yahweh, mun roƙe ka, kada ka bari mu hallaka saboda wannan mutum, ya Yahweh, kada ka ɗora alhakin mutuwarsa a kan mu, saboda kai Yahweh ka yi adalci ka kuma yi kamar yadda ya gamshe ka."15Sai suka ɗauki Yona suka jefa shi cikin teku sai tekun ya daina hauka.16Sai mutanen suka ji tsoron Yahweh ƙwarai da gaske. Suka miƙa hadayu ga Yahweh suka kuma yi alƙawura.17Yahweh kuwa ya shirya wani babban kifi don ya haɗiye Yona, Yona kuma ya kasance a cikin cikin kifi har yini uku da kwana uku.
Wannan karin magana ne da ke nufin cewa Yahweh ya yi magana. "Yahweh ya fadi sakonsa" (Duba: bayanai_karin magana)
A nan, "kalma" tana wakiltan sakon Yahweh. A.T: "sakon Yahweh" (Duba: bayanai_kamance)
Wannan ne ne sunan Allah wanda ya fada wa mutanensa a Tsohon Alƙawari. Ka duba shafin fassaraKalma game da yadda za a fassara wannan.
Wanna shi ne sunan uban Yona. (Duba: fassara_sunaye)
"Ka tafi muhimmin birnin nan na Nineba".
Wannan wata sananniyar hanya ce ta bayyana tafiya zuwa wuri mai nisa
"ka ja hankalin mutanen" (UDB). Allah yana magana ne a kan jama'ar birnin. (Duba: bayanai_kamance)
"Na sani suna ta aikata zunubi a kai a kai".
"ya tsrere daga Yahweh". "gudu" yana nuni da yadda Yunusa ya bar wurin da yake (Duba: bayanai_karin magana)
Yunusa yana kokarin tserewa daga wurin Yahweh. (Duba: bayanai_kamance)
"tashi zuwa Tarshish". Hanyar zuwa Tarshin akasin hanyar zuwa Nineba ce. Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "sai ya bi wata hanya dabam zuwa Tarshish". (Duba: bayanai_kai tsaye)
"Yona ya tafi Yafa".
"Jirgin ruwa" babban kwale-kwale ne wanda zai iya tafiya a kan teku, ya kuma dauki fasinjoji da yawa ko kaya masu nauyi.
"A can Yona ya biya kudin tafiyarsa".
"ya hau jirgin".
Kalmar "su" tana nuni da sauran mutanen da suke tafiya a jirgin.
Yunusa ya yi tsammanin cewa Yahweh ba ya a Tarshish. (Duba: bayanai_kamance)
Za a iya fadin wannan kai tsaye, wadanda suka ga kamar jirgin zai fashe. A.T: "Mutanen sun yi tsammani". (Duba: bayanai_kai tsaye)
Za a iya fadin wannan kai tsaye. A.T: "ya ruguje". (Duba: bayanai_kai tsaye/fakaice)
mutanen da suke aiki a jirgin
A nan, "allah", yana nufin allolin karya da gumakan da mutanen suke bauta wa.
"Mutanen sun yi ta jefar da kaya masu nauyi da ke cikin jirgin". An yi haka don a hana jirgin nutsewa.
Rage nauyin jirgin zai sa ya ci gaba da tsayuwa bisa ruwa sosai. A.T: "don taimaka wa jirgin ya tsaya a kan ruwan da kyau".
Yunusa ya yi wannan tun kamin iskar ta fara.
"daga ciki-cikin jirgin".
"ya riga ya kwanta yana barci" ko "yana kwance a can yana zurfin barci". Saboda wannan dalilin ne iskar ba ta tashe shi ba.
"Wanda yake shugaba a jirgin ya tafi wurin Yona yace".
"Me ya sa kake barci". Ya mori wannan salon tambayar domin ya tsautar wa Yona. AT: "Ka aina barci!" (Duba: bayanai_tambaya)
Wannan yana nufin yin wani aiki. A gun Yona, Shugaban yana fada masa cewa ya tashi, ya yi addu'a ga allahnsa domin su tsira. (Duba: bayanai_karin magana)
"Ka yi addu'a ga allahnka!" "Kira" suna nufin jan hankalin wani. (Duba: bayanai_karin magana)
Wannan dunkulallen bayanin cewa allahn Yona zai iya cetonsu, ana iya fadinsa kai tsaye. AT: "Watakila allahnka zai ji mu ya cece mu, don kada mu mutu" (Duba: bayanai_kai tsaye)
"Matukan jirgin suka ce wa juna"
"Ya kamata mu yi kuri'a don mu san wanda ya jawo mana wannan masifar". Mutanen sun yi imanin cewa alloli za su mori kuri'ar wajen nuna musu abin da suke so su sani. Wannan wata hanyar dabo ce.
Wannan yana nufin mumunar iskar.
"kuri'ar ta nuna cewa Yona ne yake da alhakin laifi"
"Sai mutanen da ke aiki a jirgin suka ce wa Yona"
"Wane ne ya jawo wannan mumunan abin da yake faruwa da mu?"
Kalmar "tsoro" tana nufin zurin bangrma da Yunusa yake da shi domin Allah.
Mutanen da ke a jirgin sun mori irin wannan salon tambayar don su nuna yadda suke fushi da Yona. AT: "Ka aikata mumunan abu". (Duba: bayanai_tambaya)
"Yona yana tserewa ne daga wurin Yahweh". Yona yana kokarin tsere wa Yahweh kamar Yahweh yana a kasar Isra'ila ne kawai. (Duba: bayanai_amance)
Za a iya fadin abin da ya fada musu kai tsaye. AT: "da yake ya riga ya fada musu 'Ina kokarin tserewa ne daga wurin Yahweh'". (Duba: bayanai_kamance)
"mutanen da ke cikin jirgin suka ce wa Yona" ko "matukan jirgin suka ce wa Yona"
"me za mu yi maka domin tekun ya natsu" (UDB)
Wannan ne dalilin da ya sa mutanen suka tambayi Yunusa abin da za su yi. Za a iya ganin dalilin kuma a farkon aya 11 a UDB.
"domin na sani wannan mugun hadarin laifina ne"
Mutanen ba su so su jefa Yona a cikin teku ba, saboda haka suka yi ta tuki da karfi kamar suna haka ruwan ne, don komo kasa. (Duba: bayanai_kai tsaye)
"hadarin yana ta karuwa, kuma rakuman ruwan suna ta girma"
Sakamakon yadda hadarn yake karuwa ne ya jawo abin da suka yi nan gaba. AT: "Da yake tekun yana ta kara bori" (Duba: bayanai_kai tsaye)
"mutanen suka yi addu'a ga Yahweh"
"Muna roko, kada ka kashe mu domin mun jawo mutuwar wannan mutumin" ko "Za mu jawo mutuar wannan mutmin. Amma, muna roko, kada ka kashe mu"
"kuma mua roko, kada kama mu da hakkin mutuwarsa" ko "kada ka dora mana laifi sa'adda wannan mutumin ya mutu". Marubucin yana maganar "laifi" kamar wani abu ne da za a iya dorawa a kan mutum. Yana nufin kama mutum da hakkin abin da ya aikata. (Duba: bayanai_kamance)
"tekun ya daina bori" ko "sai tekun ya natsu" (UDB)
"suka yi mamakin kwarai saboda ikon Yahweh"
Wadansu juyin sun saka wannan ayar a matsayin ayar farko ta sura 2. Za ka iya saka ayar bisa ga ainihin juyin da yarenka yake mora.
Akan mori wannan kalmar a Turanci domin gabatar da wani abon sashin labarin.
"ranaku uku da dare uku"
1Daga can cikin kifi sai Yona ya yi addu'a ga Yahweh Allahnsa.2Ya ce, "Na yi kira ga Yahweh game da ƙuncina ya kuwa amsa mani; daga can cikin Lahira na yi kuka na neman taimako! Ka ji muryata.3Ka jefa ni can cikin ƙarƙashin ƙasa, cikin zurfin tekuna, rigyawa da ambaliya, raƙuman ruwa sun bi ta kaina.4Na ce, 'An kore ni daga fuskarka; amma duk da haka zan sake duban haikalinka mai tsarki.'5Ruwaye sun sha kaina har zuwa wuyana; zurfi ya kewaye ni ta ko'ina, rigyawa ta sha kaina.6Na shiga ƙarƙashin duwatsu; duniya da makullanta sun rufe ni har abada. Amma duk da haka ka tsamo raina daga rami, Yahweh, Allahna!7Lokacin da raina ya sume a cikina, sai na tuna da Yahweh a cikin raina; sai addu'ata ta zo gare ka, a haikalinka mai tsarki.8Waɗanda suka juya ga alloli marasa amfani sukan ƙi amincinka zuwa gare su.9Amma ni zan miƙa maka hadaya da murya ta godiya, zan cikasa abin da na alƙawarta. Daga wurin Yahweh ceto yake zuwa!"10Sai Yahweh ya yi magana da kifin, sai kifin ya amayar da Yona a gãɓar tekun.
Wannan yana nufin "Yahweh, Allahn da yake bauta wa". Kalmar "Allahnsa" ba ta nufin cewa Yunusa ya mallaki Allah.
"Yona yace"
"Na yi addu'a ga Yahweh game da babbar wahalata". Duk da cewa Yona yana addu'a ga Yahweh ne, ya mori sunan Yahweh, ba "ka" ba. AT: "Yahweh, ina kira gare ka game da wahalata"
"Yahweh ya amsa mini" ko "ya taimake ni"
"daga tskiyar Sheol" ko "daga zurfafan Sheol". Ma'anar tana iya zama 1) Yona yana magana kamar kasancewa cikin cikin kifin shi ne kasancewa cikin Sheol, ko 2) Yona ya yi imanin cewa yana dab da mutuwa ya tafi Sheol, ko 3) Ya yi magana kamar ya riga ya mutu ya tafi can. (Duba: kamance)
Wannan ci gaban addu'ar da Yona ya fara ne a 2:1. A aya 4 Yona ya yi maganar wani abin da ya yi addu'a a kai kamin wannan addu'ar.
Wanan yana maganar girmar tekun da Yona yake ciki. (Duba: bayanai_iri daya)
"zuwa karkashin tekun"
"ruwan tekun sun rutsa ni"
Wadannan borin ruwa ne a bisa teku. (Duba: bayanai_tagwaye)
Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "Ka kore ni" ko "Ka sallame ni" (Duba: bayanai_kai tsaye/fakaice)
"daga gare ka". Sa'ad da Yona yace "wurinka", yana magana game da Yahweh gaba dayansa.
Yunusa yana begen cewa, duk da abin da yake fuskanta, zai ga haikalin. (Duba: bayanai_tambaya)
Wannan ci gaban addu'ar Yunusa ne, wada ya fara a 2:1.
"Ruwa" yana nufin teku.
Wadansu juyin sun fassara Ibraniyancin da nufin "raina". A wancan fassarar, ruwayen suna dab da dauke ran Yunusa.
"zurfin ruwan yana kewaye ni"
"ciyayin da ke girma a cikin teku"
Yona ya mori kamance wajen kwatanta kasa da kurkuku. AT: "kasa ta zama kamar kurkukun da ke dab da kulle ni har abada" (Duba: bayanai_kamance)
Yona yana maganar wurin matattu kamar rami ne. AT: "Amma ka ceci raina daga wurin matattu" ko "Amma ka cec ni daga wurin da matattun mutane suke" (Duba: bayanai_kamance)
A wadansu yarurrukan, ya fi daidai a sa wannan daga farkon maganar ko kuma bayana kalmai "kai".
Wanan ci gaban addu'ar Yona ne, wadda ya fara a 2:1.
Da yake Yona yana addu'a ga Yahweh ne, zai fi bayyanuwa a wadansu yarurruka idan an ce, "na yi tunani game da kai, Yahweh" ko "Yahweh, na yi tunani game da kai". (UDB)
Yona yana magana kamar addu'arsa za ta iya tafiya zuwa wurin Allah haikalinsa. AT: "sai kai, a tsattsarkar haikalinka, ka ji addu'ata" (Duba: bayanai_kamance)
"Mutanen da suke sa rai ga alloli marasa amfani"
"suna kin ka, kai wanda kake da aminci gare su"
Wannan ci gaban addu'ar Yona ne, wadda ya fara a 2:1.
Wannan furcin a Turanci yana nuna cewa akwai bambanci tsakanin mutanen da Yona ya gama magana a kansu da shi kansa. Suna maida hankalinsu a kan allolin banza, amma shi zai bauta wa Yahweh. AT: "Amma ni"
Wannan yana nufin cewa Yona zai gode wa Allah yayinda yake mika sadaka gare shi. Ba a bayyane yake ba sosai ko Yona yana shirin goda wa Allah ta wurin rairawa ne ko sowar farinciki.
Za a iya sake shirya kalmomin wannan furcin yadda boyayyen suna na "ceto" zai fito kamar kalmar "cetar". "Yahweh shi ne wanda yake cetar da mutane" (Duba: bayanai_boyayyunsunaye)
"a kasa" ko "a gabar teku"
1Maganar Yahweh ta zo wurin Yona karo na biyu, cewa,2"Ka tashi, ka tafi Nineba, babban birnin nan, ka yi shelar saƙon da na umarce ka ka bayar."3Sai Yona ya tashi, ya tafi Nineba ya yi biyayya da maganar Yahweh. Nineba dai birni ne babba, kuma tafiya ce ta kwana uku.4A yini guda Yona ya fara shiga birnin ya yi kira ya ce, "A cikin kwana arba'in za a rushe Nineba."5Mutanen Nineba suka gaskata Allah, suka yi shelar yin azumi. Dukkan su suka sanya tsummokara, daga manyansu har ya zuwa ƙananansu.6Nan da nan labari ya kai ga sarkin Nineba. Shi kuwa ya tashi daga kursiyinsa, ya tuɓe alkyabbarsa, ya rufe kansa da tsummokara, ya zauna cikin toka.7Sai ya aika ayi shelar cewa, "A cikin Nineba, bisa ga ikon sarki da majalisarsa, kada wani mutum ko dabba, ko garken shanu da tumaki, ko na awaki ya ɗanɗana wani abu. Kada su ci abinci ko su sha ruwa.8Amma sai mutum da dabba su rufa da tsummokara kuma su yi kuka mai ƙarfi zuwa ga Allah. Sai kowanne mutum ya juya daga hanyarsa ta mugunta da kuma ta'addancin dake cikin hannuwansa.9Wa ya sani? Ko Allah zai iya yin jinkiri kuma ya canza ra'ayinsa ya kuma juya daga fushinsa mai zafi domin kada mu hallaka."10Allah ya ga abin da suka yi, yadda suka juya daga hanyoyinsu na mugunta. Sai Allah ya canza ra'ayinsa game da hukuncin da ya ce zai zartar a kansu, bai kuma zartar da shi ba.
Wannan karin magana ne da ke nufin Yahweh ya yi magana. Duba yadda ka fassara wannan a 1:1. AT: "Yahweh ya fadi sakonsa" (Duba: bayanai_karin magana)
A nan, "kalma", tana wakiltar sakon Yahweh. AT: "sakon Yahweh" (Duba: bayanai_kamance)
"Ka tafi muhimmin birnin nan na Nineba"
Wannan yana nuni da barin wurin da mutum yake. (Duba: bayanai_karin magana)
"ka fada wa mutanen abin da na ce maka ka fada musu"
"Wannan karon, Yona ya yi biyayya da Yahweh, ya tafi Nineba"
"Sai Yona ya bar gabar tekun". "ya tashi" yana nuni da yadda Yona ya bar wurin da yake. (Duba: bayanai_karin magana)
An mori wannan kalmar a nan don nuna canji daga labarin zuwa bayani game da Nineba.
"birnin mai girmar tafiyar kwana uku". Dole mutum ya yi tafiyar kwana uku domin ya kewaya ko'ina a birnin. (Duba: bayanai_karin magana)
Ma'anar tana iya zama 1) "bayan Yona ya yi tafiyar yini guda, sai ya yi shela", ko 2) "yayinda Yona yake tafiya a rana ta farko, sai ya yi shela".
"bayana tafiyar yini guda". Tafiyar yini guda ita ce nsan da mutane suka yi tafiya a rana daya. AT: "Bayan Yona ya yi tafiya yini guda"
"ya shaida" ko "ya fada da babbar murya"
"kwana 40" (Duba: fassara_lambobi)
Za a iya fadin abin da ya sa mutane suke saka tsummoki a bayyane. AT: "Sun kuma saka kayan makoki domin su nuna nadamarsu saboda zunubin da suka yi" (UDB) (Duba: bayanai_kai tsaye)
"daga mafi tasiri zuwa mafi kankantan mutane" ko "hade da dukkan muhimman mutane da mutane marasa muhimmanci" (UDB)
"Sakon Yona"
"Ya tashi daga kursiyinsa" ko "Ya mike tsaye daga kursiynsa". Sarkin ya tashi daga kursiyinsa don ya nuna kaskancinsa.
Kursiyi kujera ne da sarki yake zama a kai. Yana nuna cewa shi sarki ne.
"Ya aika da sanarwar doka wadda ta ce" ko "Ya aika bayinsa su yi shela ga jama'ar Nineba"
"mashawarta" (UDB). Wadannan muhimman mutane ne wadanda suke taimaka wa sarki wajen mulkin birnin.
Wannan yana nuni da dabbobi iri biyu da mutane suke kula da su. AT: "shanu ko tumaki"
"Ba za su ci ko su sha wani abu ba". Dailin da ya sa ba za su ci ko su sha komai ba, ana iya bayyana shi sosai ta wurin kara "don su nuna cewa suna nadama saboda zunubansu". (Duba: bayanai_kai tsaye)
Wannan ci gaba ne na abin da sarkin ya fada wa mutanen Nineba.
"Bari dukan"
Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "bari mutane da dabbobi su saka tsummoki" ko "bari mutanen su sutura kansu da dabbobinsu da tsummoki" (Duba: bayanai_kai tsaye/fakaice)
Kalmar "dabbobi" tana nufin dabbobin da mutane suka mallaka.
"addu'a da gaske ga Allah". Abin da za su yi addu'a a kai, ana iya bayyaa shi kai tsaye AT: "ku yi kira da babbar murya ga Allah, ku roki jinkai" (Duba: bayanai_kai tsaye)
Wannan yana nufin "miyagun ayyukan da yake aiktawa"
Sarkin ya mori salon tambayar nan don ya sa mutane su yi tunani game da wani abin da mai yiwuwa suke gani ba zai yiwu ba, cewa idan za su daina zunubi, mai yiwuwa Allah ba zai kashe su ba. Za a iya fassara ta zuwa magana: "Ba mu sani ba". Ko kuma, ana iya fadin ta a matsayin kalam guda, a sa ta a magana ta gaba: "Kila". (Duba: bayanai_tambaya)
"Allah zai iya shawar yin wani abu dabam" ko "Mai yiwuwa Allah ba zai yi abin da ya ce zai i ba"
"kada mu mutu". A nan hallaka tana daidai da nutsewa ckin teku.
"Allah ya gane cewa sun daina aikata miyagun ayyuka"
Marubucin yana maganar yadda mutanen suka daina zunubi kamar sun juya bayansu ga wani abu ne. (Duba: bayanai_kamance)
"Allah ya sake tunaninsa game da hukuncin da ya ce zai yi musu" ko "Allah ya zabi cewa ba zai hukunta su ba kamar yadda ya ce zai yi ba" (Duba: bayanai_kamance)
Abin da Allah zai yi, ana iya bayyana shi kai tsaye, AT: "bai hukunta su ba" ko "bai hallaka su ba"
1Amma hakan bai yi wa Yona daɗi ba, sai ya ji haushi ƙwarai.2Saboda haka, Yona ya yi addu'a ga Yahweh ya ce, "Yahweh, ashe ba abin da na ce ba kenan tun ban baro ƙasata ba? Shi ya sa tun da farko na yi ƙoƙarin gudu zuwa Tarshish - domin na san kai Allah ne mai alheri, mai tausayi, mai jinkirin fushi, cike da aminci, ka kan kuma fasa aiko da bala'i.3Saboda haka yanzu, Yahweh, na roƙe ka, ka ɗauke raina daga gare ni, gama ya fiye mani in mutu, da in rayu."4Yahweh yace, "Ya dace da ka yi fushi haka?"5Sai Yona ya fita daga birnin ya zauna daga gabas da birnin. Can ya yi rumfa ya kuma zauna a ƙarƙashinta domin ya ga abin da zai faru da birnin.6Yahweh Allah ya shirya wata 'yar itaciya ya sa ta yi girma ta kere Yona, domin ta zama inuwa a saman kansa ta sauƙaƙa ƙuncinsa. Yona kuwa ya yi murna sosai sabo da wannan 'yar itaciyar.7Amma Allah ya shirya tsutsa da gari ya waye rana ta ɗaga. Tsutsar kuwa ta kawo hari ga 'yar itaciyar, ta cinye 'yar itaciyar, 'yar itaciyar kuma ta bushe.8Kashegari sa'ad da rana ta fito, Allah ya shirya wata iska daga gabas mai zafin gaske. Ranar kuwa, ta yi zafi matuƙa bisa Yona har ya some. Sai Yona ya gwammace ya mutu. Ya ce wa kansa, "Gara ma in mutu da in rayu."9Sai Allah yace wa Yona, "Ya dace da ka yi fushi game da 'yar'itaciyar? Sai Yona yace, "Ya dace da in yi fushi, har ma ga mutuwa."10Yahweh yace, "Ka ji tausayin 'yar itaciyar, wadda ba ka yi aiki a kai ba, ba ka kuma sa ta yi girma ba. 'Yar Itaciyar ta yi girma cikin dare ɗaya ta kuma mutu cikin dare ɗaya.11To ashe, Ni, ba zan tausayawa Nineba, wannan babban birni, wanda akwai fiye da mutane dubu ɗari da ashirin, da ba su san bambanci tsakanin hannunsu na dama da hannunsu na hagu ba, da kuma dabbobi masu yawan gaske?"
Kalmar "Ah" tana bayyana yadda Yunusa yake bakin ciki
Yona ya mori wannan salon tambayar domin ya nuna wa Allah fushinsa. Haka kuma, abin da Yunusa ya fada sa'adda yake gida, ana iya bayyana shi kai tsaye. AT: "Tun ina garinmu, na sani cewa idan na yi wa mutanen Nineba kashedi, za su tuba, kuma ba za ka hallaka su ba" (Duba: bayanai_tambaya da bayanai_kai tsaye)
Ma'anar tana iya zama 1) "Na yi kokarin hana faruwar wannan ta wurin tserewa zuwa Tarshish" ko 2) "Na gaggauta kokarin gudu zuwa Tarshish", ko 3) " Na yi iyakar kokarina don in tsere zuwa Tarshish".
"amintacce sosai" ko "kana kaunar mutane sosai" (UDB)
Wannan yana nufin, "ka ce za ka aiko da masifa a kan masu zunubi, amma kuma sai da fasa yin haka". AT: "ka fasa hukunta mutanen da suke aikata zunubi"
Za a iya bayyana dalilin Yona na son mutuwa kai tsaye. AT: "da yake ba za ka hallaka Nineba kamar yadda ka ce za ka yi ba, ina rokonka ka bar ni in mutu" (UDB) (Duba: bayanai_kai tsaye)
"Na gwammaci in mutu da in rayu" ko "da yake ina so in mutu, ba na so in zauna da rai"
Allah ya mori salon tambayar nan don ya tsautar wa Yunusa game da fushin da ya a kan abin da bai kamata ya yi fushi a kai ba. AT: "Fushinka bai cancanta ba". (Duba: bayanai_tambaya)
"ya bar birnin Nineba"
"abin da zai faru da birnin" (UDB). Yona yana so ya gani ko Allah zai hallaka birnin ko ba zai hallaka birnin ba.
"bisa kan Yona, don ya ji inuwa"
"ya kare Yona daga zafin rana"
"Allah ya aiko tsutsa" (UDB)
"Tsutsar ta ci shukar"
Shukar ta bushe ta mutu. AT: "shukar ta mutu"
Allah ya sa iska daga gabas ta buso kan Yona. In da iska tana nufin iska mai sanyi ko dumi kadai, to, kana iya gwada wannan. AT: "Allah ya aiko da wani zafi daga gabas zuwa wurin Yunusa" (Duba: bayanai_kai tsaye)
"rana ta yi zafi kwarai"
Watakila Yona ya fi jin zafin a kansa. AT: "a kan Yunusa".
"kasala ta kama shi" ko "ya rasa karfinsa"
"Na gwammaci in mutu da in rayu" ko "Da yake ina so in mutu, ba na so in rayu". Duba yadda ka fassara wannan a 4:1.
Allah yana kalubalantar Yona saboda fushin da ya ji cewa shukar ta mutu, amma kuma yana so Allah ya kashe mutanen Ninaba. AT: "Fushinka game da mutuwar shukar ba daidai ba ne". (Duba: bayanai_kamance)
Ana iya bayyana bayanin da ke boye kai tsaye. AT: "Ya kamata ka fidamuwa game da mutuwar mutanen Nineba fiye da mutuwar shukar". (Duba: bayanai_kai tsaye)
"Daidai ne in yi fushi. Yanzu na yi fushin da ya isa in mutu!" (UDB)
"Yahweh ya cewa Yona" (Duba: bayanai_kai tsaye)
Allah yana morar tambaya don jaddada cewa ya kamata ya nuna jinkai wa Nineba. AT: "Hakika, ya kamata in nuna jinkai ga Nineba, wannan muhimmin birnin... shanu". (Duba: bayanai_tambaya)
Wannan kuma yana iya zama farkon wata magana. AT: "Akwai fiye" ko "Yana da fiye"
Mutane 120,000 (Duba: fassara_lambobi)
Wannan yana iya zama hanyar cewa "ba za su iya fadin abin da yake daidai ko wanda ba daidai ba".
Marubucin yana nuni da zurfin tuban Nineba, har Yahweh ya lura da dabbobin a cikin sha'anin tuba. (Duba: rubutu_shifida)
1Wannan ita ce maganar Yahweh wadda ta zo wurin Mika, Bamorashtite a cikin kwanakin Yotam, da Ahaz, da Hezekiya, sarakunan Yahuda, abin da ya gani game da Samariya da Yerusalem.2Dukkan jama'a ku saurara, ke duniya ki saurara da dukan abin dake cikinki. Bari Ubangiji Yahweh ya zama shaida a kan ki daga haikalinsa mai tsarki.3Duba, Yahweh ya sauko daga kursiyinsa, zai bi ta wurare masu tudu a bisa ƙasa.4Duwatsu zasu narke a ƙarƙashinsa, kwarurruka kuma zasu farfashe kamar saƙar zuma a gaban wuta, kamar an zubar da ruwa a kan wuri mai tsauri.5Dukkan wannan saboda tawayen Yakubu ne, kuma saboda zunubin gidan Isra'ila ne. Mene ne dalilin tawayen Yakubu? Ba Samariya ba ce? Mene ne dalilin wurare masu tsawo na Yahuda? Ba Yerusalem ba ce?6"Zan maida Yahuda ta zama kamar kufai kawai kamar wurin dasa itatuwan inabi. Zan tura gininta na duwatsu cikin rami, zan kware harsasanta.7Za a farfasa sifofinta, dukkan kyaututtukanta za a ƙone su. Dukkan gumakanta zan rushe su. Gama daga wurin karuwancinta ta tattara su, zasu zama kamar abin da aka biya ta saboda karuwanci."8Domin wannan zan yi makoki in yi kuka, zan fita tsirara ba takalma; zan yi kuka kamar dila, zan yi makoki kamar mujiya.9Domin rauninta marar warkewa, domin ta zo Yahuda. Ta kawo ƙofar mutanena, wato Yerusalem.10Kada a yi maganar ta a Gat; kada a yi mata kuka. A Bet Lefra na yi birgima a ƙura.11Ki wuce ta mazaunan Shafir, a tsiraice cikin kunya. Mazauna Za'ana basu fito waje ba. Bet Ezel tana makoki saboda an ɗauke kariyarta.12Mutanen Marot suna da marmarin jin labari mai daɗi, saboda masifa daga Yahweh ta zo har ƙofofin Yerusalem.13Ku mutanen Lakish ku haɗa karusai na dawaki. Ke, Lakish, ke ce kika zama sanadin zunubin ɗiyar Sihiyona, saboda an sami kurakuran Isra'ila a cikinki.14To za ki bada kyauta ta ban kwana ga Morashet Gat; garin Akzib zai ba sarakunan Isra'ila kunya.15Zan sake kawo wanda zai mamaye ku, ku mazaunan Maresha, martabar Isra'ila zata dawo Adullam.16Ki aske kanki ki share gashinki saboda 'ya'yan da ki ke jin daɗin su. Ki sa kanki ya yi saiƙo kamar na gaggafa, domin 'ya'yanki za su tafi bauta daga wurinki.
"maganar da Yahweh ya fada"
Wannan ne suna Allah, wanda ya bayyana wa mutanensa a Tsohon Alaƙwari. Duba shafin fassaraKalma a kan Yahweh game da yadda za ka fassara wannan.
Wannan yana nufin shi daga Morashet ne, wanda gari ne a Yahuza.
"sa'ad da Yotam, Ahaz, da Hezekiya suke sarautar Yahuza"
AT: "wahayin da ya gani game da mutanen Samariya da Yerusalem"
Mika 1:2-7 yana game da hukuncin Allah a kan Samariya.
Wannan ne mafarin anabcin Mika. Duk wadannan maganganu biyu suna da ma'ana daya, kuma suna jaddada cewa dole kowa a duniya zai saurara. Mika ya yi magana kamar dukkan mutanen duniya suna a wurin suna sauraronsa.
AT: "zai hallakar da tsawawan wurare na duniya gaba daya, kamar yana tattake su da sawayensa"
Wannan yana nufin sa'ad da Allah zai zo don ya hallaka masujadun kafirai, babu abin da zai iya hana shi.
Wadannan kalaman suna nufin kusan abu daya, kuma suna jaddada cewa Yahweh yana daukan mataki saboda zunuban masarautun arewa da na kudu duka.
"Ubangiji zai zo ya shar'antar"
A nan "Yakubu" yana nufin masarautar arewa ta Isra'ila. Mika yana morar tambaya don jaddada cewa mutanen Samariya su ne dalilin da ya sa Allah zai shar'anta masarautar Isra'ila.
A nan "zan" yana nuni da Yahweh.
"Zan farfashe... zan kokkone"
A nan "gininta" yana nufin birnin Samariya.
Sau da yawa, bautan gumaka takan hada da kwana da karuwai a masujadai na kafirai.
Mika 1:8-16 yana magana game da hukuncin Allah a kan Yahuza.
A nan "zan" yana nufin Mika.
Wannan alama ce ta tsananin makoki da kunci.
Mafi yiwuwa, ba tsirara gaba daya Mika yake ba. Mai yiwuwa yana saye da bante.
Wadannan ne dabbobin da ka sani saboda karar kukarsu mai tsini. Kuma ana samunsu a kufai. AT: Za ku yi kuka da makoki kamar dabbobin dare"
A nan "ta" yana nufin birnin Samariya. Wannan yana nufin babu abin da zai haka mayakan abokan gaba da ke zuwa su hallaka jama'ar Isra'ila.
A nan "ya" yana nufin "raunin", wato, ga mayakan da Allah zai mora domin ya hori Samariya.
Mai yiwuwa ka so rubuta bayanin kasan shafi cewa, "Sunan wannan birnin yana nufin 'gidan kura'".
Mutanen da ke karkashin hukuncin Allah suna bayyana bakin cikinsu a wannan hanyar.
Don samun ma'anar sunayen kauyuka da garuuwa, za ka iya hada wannan bayanin a sashen bayanin kasan shafi.
Sunana wannan birnin yana kama da wanda ke da ma'anar "kyau". Ya bambanta da "tsiraici da kunya".
Mayakan abokan gaba sukan sa kamammunsu su yi tafiya tsirara zindir. Kuma, akwai kunya idan an zama mutanen da aka yi nasara a kansu.
Sunan wannan birnin yana nufin "fita". Suna tsoro sosai har ba za su iya fita su kai taimako ba.
Sunan wannan birnin yana nufin "gidan daukewa".
AT: "gama na dauke duk wani abin da zai iya kare su"
Sunana wannan birnin yana nufin "dacin rai".
"Masifa" muhimmiyar kalma ce a Mika da za a yi ta maimaitawa.
Akwai jujjuya kalma a nan, do Lakish yana kama da "zuwa ga karusai" a harshen Ibraniyanci. Mutanen suna shirya karusansu don gudu, ba yaki ba. Lakish ita ta biyu bayan Urushalima a muhimmanci a Yahuza.
"Diyar" birni tana nufin jama'ar birnin. Wani fassara kuma yana iya zama: "mutanen Sihiyona" ko "mutanen da ke zama a Sihiyona".
AT: "gama kun yi rashin biyayya kamar yadda jama'ar Isra'ila suka yi"
Mai yiwuwa ka so ka kara bayanin kasan shafi mai cewa, "Sunan nan 'Moreshet' yana nufin 'a tafi' kuma furcinsa yana kama da kalmar da ake mora don 'wacce ake tashi'". Kamar Moreshet ita ce budurwar da Assuriya ta dauka, kuma "kyautai na tafiya" su ne garan. Moreshet Gat ne kauyen Mika.
Za ka iya kara bayanin kasan shafi mai cewa, "Sunan wannan garin yana kara kusan daya da kalmar Ibraniyanci ta 'abin yaudara'".
A nan "zan" yana nufin Yahweh.
Za ka iya rubuta bayanin kasan shafi mai cewa, "Akwai jujjuya kalma a nan da sunan wannan kauyen da kalmar Ibraniyanci ta 'nasara'". An mori wannan kalmar a nasarar da Isra'ila ta yi kan Kan'ana; yanzu za a yi nasara kan Isra'ila. Mai yiwuwa wannan kauyen yana kusa da kauyen Mika na Moreshet Gat.
Wannan yana nufin birnin sarauta ta Filistiya.
Aske kai alamar makoki ne a gun Isra'ilawa.
1Kaiton masu shirya mugunta, ga waɗanda ke shirya mugunta a kan gadajensu. Idan gari ya waye sukan aikata ta domin suna da iko.2Sukan yi sha'awar gonaki su kuma ƙwace su; sukan yi sha'awar gidaje su kuma ƙwace su. Suna tsanantawa mutum da gidansa, da kuma abin gãdonsa.3Saboda haka Yahweh yace, "Duba, na kusa kawo bala'i ga wannan kabila, wadda ba zaku cire kanku daga ciki ba. Ba zaku yi tafiya da taƙama ba, gama zaya zama mugun lokaci.4A wannan rana abokan gãbarku zasu rera waƙa game da ku, zasu yi makoki da makoki mai zafi. Zasu yi waƙa, 'Mu Isra'ilawa mun hallaka sarai, Yahweh ya canza gundumar mutanena.' Ya ya zaya ɗauke shi daga wurina? Ya bayar da filayanmu ga maciya amana!"'5Saboda haka, ku masu arziki baza ku sami zuriyar da za a raba gundumominku a cikin taruwar mutanen Yahweh ba.6"Sun ce, "kada ka yi anabci." "Ba zasu yi anabcin waɗannan abubuwa ba; reni ba zaya zo ba."7Ko lallai za a iya faɗin gidan Yakubu, "Ko Ruhun Yahweh ya ji haushi ne?" Ko waɗannan su ne ainihin ayyukansa?" Ko kalmomina ba su yi wani aikin kirki ga kowa ba ne?8A makare mutanena suka tashi kamar abokan gãba. Kun tuɓe sutura, da riga, daga masu wucewa ba tare da tsarguwa ba, kamar sojoji suna dawowa daga yaƙi zuwa wurin da suke tsammani lafiyayye ne.9Kun kori matan mutanena daga gidajen da suke jin daɗi, kun ɗauke albarkuna daga wurin 'ya'yansu har abada.10Tashi ka tafi, nan ba wurin da za ka iya zama ba ne, saboda rashin tsafta; hallakakke ne sarai.11Idan wani ya zo da ruhun ƙarya ya yi ƙarya ya ce, "Zan yi maka anabci a kan ruwan inabi da abin sa maye," zasu ɗauke shi annabi domin wannan jama'a.12Tabbas, zan tattara dukkan ku, Yakubu. Tabbas zan tattara sauran mutanen Isra'ila. Zan kawo su kamar garken tumaki a cikin tsakiyar wurin kiwonsu. Saboda yawan mutanen za a ji ƙara mai ƙarfi.13Wanda ya fara ɓalle ƙofa shi ne zai yi masu jagora. Sun ɓalle ƙofa sun fita; sarkinsu zai wuce gabansu. Yahweh zai kasance a gabansu.
Yanzu a Mika 2:1-11, an kau da hankali daga hukuncin da za a yi wa garuruwan zuwa shugabanni a Isra'ila wadanda suke zaluntar matalauta, kuma ba su bin dokokin Allah.
"Wannan jama'a" tana nufin daukacin al'ummar Isra'ila, wadda masu arzikinta suke zaluntar matalauta. Hakkin zunuban shugabannin yana dawowa kan dukkan al'ummar.
Yahweh yana nufin hukuncinsa kamar nawaya a wuyarsu. Zai zama abin da zai kaskantar da girmankai masu arziki.
"za su yi kuka suna ihu"
Abokin gaba yana morar wata tambaya a wakarsu don bayyana mamakin da masu arzikin Isra'ila suka ji don Alah ya kwace kasarsu ya bayar da ita a ga wani dabam, kamar yadda su ma suka kwace kasar daga hannun matalauta. AT: "Ya karbe daga wurina"
Wadanda suka kwace gonaki daga matalauta ba za su sami gadon da suka hana wadansu ba.
Mika 2:6-11 yana magana game da annabawan ba su yi wa'azin da ya dace ba, wadanda suka ki Mika, da kuma karin hanyoyin da masu arziki suke zalunci da ikonsu.
"jama'ar Isra'ila sun ce"
"kada annabawa su yi anabci"
Mutanen sun mori tambayoyi don jaddada cewa suna da rashin fahimta, kuma ba su gaskata yarda cewa Allah zai hukunta su ba.
Mika yana morar wata tambaya don koyar da jama'ar. A.T: "Sakona yana da amfani ga wadanda suka kula da aikata abin da yake daidai".
A nan "na" yana nufin Yahweh.
Ma'ana tana iya zama: 1) Mika yana nufin mugayen mutanen suna sata riguna daga matalauta, amma da wuya yiwuwar haka, ko 2) Mika yana nufin masu ba da rance da ke rike tufafin matalautan da ke zuwa neman rancen kudi, su ba da rigar a matsayin tabbacin cewa za su biya bashin. Bisa ga dokar da ke a Fitowa, za su mayar da rigar kamin maraice, don tana iya zama ita ce kadai abin da talakan yake da shi na rufe sanyi da dare.
Yahweh ya ci gaba da magana da azzaluman masu arziki a Isra'ila.
Gaba daya dai, wannan yana nufin albarkun da Allah ya ba wa mutanensa. Yana iya nufin 1) zama mamallakan gonaki a Isra'ila, 2) albarka a nan gaba, ko 3) iyayen 'ya'yan, manoman da suke aiki tukuru domin kafa kasar.
AT: "Zan hallaka ta gaba daya"
AT: "za a dube ku"
Yahweh ya ci gaba da magana. A karshen wannan surar, Yahweh ya nuna kansa a matsayin makiyayi wanda yake kare mutanensa. Mai yiwuwa musamman yana magana ne da wadanda suke a Urushalima, wadanda suka dawo daga Assuriya.
Wannan misali ne na Sarki yana jagorantar jama'arsa daga birnin da aka kulle.
1Na ce, "Yanzu ku saurara, ku shugabannin Yakubu da masu mulki na gidan Isra'ila: Ashe ba dai-dai ba ne a gare ku ku fahimci adalci?2Ku da ke ƙin nagarta kuke kuma ƙaunar mugunta? Ku da ke yayyage fatarsu, da namansu daga ƙasusuwansu --3ku da ke cin naman mutanena, kun yage fatarsu, kun kakkarya ƙashinsu, kun daddatsa su gunduwa-gunduwa kamar naman da za a sa a tukunya, kamar nama domin dafawa.4Sa'an nan ku shugabanni zaku yi kuka ga Yahweh, shi kuwa ba zai amsa maku ba. Zai ɓoye fuskarsa daga gare ku, da yake kun yi aikin mugunta.5Yahweh ya faɗi haka, "Game da annanbawan da suke ɓatar da mutanena, idan wani ya basu wani abu su ci, sukan yi shelar 'Salama'. Amma ga waɗanda ba su sa komi a bakinsu ba, sai su fara yaƙi da su.6Saboda haka zai zama duhu a gare ku, babu ruya domin ku, zai zama duhu sosai har da ba zaku yi duba ba. Rana za ta faɗi a kan annabawa, yini zai yi masu duhu.7Masu duba zasu ji kunya, masu sihiri zasu rikice. Dukansu zasu rufe leɓunansu, domin babu amsa daga gare ni."8Amma ni ina cike da iko ta wurin Ruhun Yahweh, kuma ina cike da adalci da ƙarfi, don in furtawa Yakubu kuskurensa, Isra'ila kuma zunubinsa.9Yanzu ku ji wannan, ku shugabanni na gidan Yakubu, da masu mulki na gidan Isra'ila, ku da ke ƙyamar adalci, kuna wulaƙanta kowanne abu mai kyau.10Kun gina Sihiyona da jini, Yerusalem kuma da mugunta.11Shugabanninku suna hukunci da cin hanci, firistocinku suna koyarwa don a biya su, kuma annabawanku suna dubã saboda kuɗi. Duk da haka kun dogara ga Yahweh kun ce, "Ba Yahweh yana tare da mu ba? Ba masifa da za ta same mu."12Domin haka, saboda ku za a huɗe Sihiyona kamar gona, Yerusalem za ta zama juji, tudun haikali zai zama tsaunin daji.
Sura ta 3 tana maida hankali a kan malalatan shugabanni a Isra'ila.
A nan "na" yana nufin Mika.
Mika yana morar tambaya wajen tsautar wa shugabannin domin ba su kare mutane, ko ba su yi musu adalci.
Mika ya mori wannan mumunan misali na mahauci yana yayyanka naman dabba, don jaddada yadda Allah yake fushi da shugabannin saboda yadda suke yin keta ga wadanda ya kamata suna karewa.
Mika ya ci gaba da magana.
"kira da babbar murya ga Yahweh don taimako"
Wannan yana ufin Allah ba zai ji kukansu ba. Ba za su ji kukan matalauta ba, haka su ma Allah zai yi musu.
Mika ya ci gaba da furta hukunci a kan annabawab karya.
Yahwe yana cewa a 3:6, wadannan annabawan karya ba za su sake samun karbar Allah zuwa ga jama'ar Isra'ila ba. Wadansu lokuta annabawa sukan karbi sako daga Allah ta wurin wahayi, ko mafarkai da dare.
"Zan sa masu gani su ju kunya, kuma zan rikitar da masu duba"
"Ba za su sake magana ba kuma"
Wannan yana nufin Allah zai yi shiru matsayin wata hanyar yi musu horo.
"Ni" a nan yana nufin Mika, annabin gaskiya, yana bambanta kansa daga annabawan karya.
Ruhun Yahweh ya zabi ya ba wa Mika iko, shari'a, da karfin hali, a hanya ta musamman. A.T: "Ruhun Yahweh ya cika ni da iko, shari'a, da karfin hali" ko "Ruhun Yahweh ya ba ni iko, shari'a, da karfin hali"
Duk wadannan maganganu biyu suna nufin abu daya, kuma suna jaddada cewa duka mutanen masarautun arewa da na kudu sun yi zunubi.
Masu arziki suna gina wa kansu kyawawan gidaje, sau dayawa ta wurin zaluntar matalauta.
A nan, "jini" yana nufin kisankai.
Mika yana fadin maganar shugabannin da suke kuskuren tunanin cewa Yahweh ba zai hukunta su saboda ayyukan zunubansu ba. A nan, kalmar Ibraniyanci na "mugunta" daya ne da kalmar da ke nufin "masifa" a 2:3, wanda muhimmiyar kalma ce a littafin.
A nan, "ku" na nufin firistoci, annabwa, da shugabanni na ayar da ta gabata.
Mika yana nufin cewa za a hallaka Urushalima gaba daya. Babban birni mai yawan jama'a zai zama kufai, ya zama kamar gona ko kurmi.
Bayan an hallakar da ita, Urushalima za ta zama wurin noma. AT: "Wadansu za su nome Sihiyona kamar gona".
Har harabar haikali ma ba zai ta tsira ba. Shugabannin sun lalata ta, za kuma a hallaka ta.
1Amma zaya zama a rana ta ƙarshe dutsen gidan Yahweh zaya kafu a bisa sauran duwatsu. Zai ɗaukaka bisa sauran tuddai mutane kuma za su yi tururuwa wurinsa.2Al'ummai da yawa zasu ce, "Ku zo, mu je bisa dutsen Yahweh, zuwa gidan Allah na Yakubu. Zaya koya mana hanyoyinsa, kuma zamu yi tafiya cikin tafarkunsa." Gama daga Sihiyona shari'a zata fito, maganar Yahweh kuma daga Yerusalem.3Shi zaya hukunta tsakanin mutane da yawa, ya kuma yanke hukunci a kan mulkoki masu yawan gaske masu nisa kuma. Zasu maida takubbansu su zama garmuna mãsun su kuma su zama lauzuna. Wata al'umma baza ta ɗaga takobi gãba da wata al'umma ba, baza su ƙara koyar da yaƙi ba.4Maimakon haka kowanne mutum zai zauna ƙarƙashin kuringar inabinsa ko ƙarƙashin itacen ɓauransa. Ba wanda zai ƙara basu tsoro, gama bakin Yahweh mai runduna ne ya faɗi.5Gama dukkan mutane suna tafiya, kowanne ɗaya cikin sunan allahnsu. Amma mu zamu yi tafiya cikin sunan Yahweh Allahnmu har abada abadin6"A waccan ranar" - wannan furcin Yahweh ne - "Zan tattaro guragu da korarru, da waɗanda na tsanantawa.7Zan sa guragun su zama su ne saura, waɗanda a ka kora su zama al'umma mai ƙarfi, ni kuma Yahweh zan yi mulki a bisansu, a kan Dutsen Sihiyona daga yanzu da har abada.8Ke fa, hasumiya ta tsaron garke, tsaunin ɗiyar Sihiyona, mallakarki ta dã za ta dawo gare ki, da mulki na ɗiyar Yerusalem.9Yanzu, me yasa kuke ihu da ƙarfi haka? Babu sarki a cikinku ne? Mai shawararku ya mutu ne? Wannan shi ne yasa ciwo ya kama ku kamar mace mai naƙuda?10Ki zama da ciwo da naƙuda ta haifuwa, ke ɗiyar Sihiyona, kamar mace mai naƙuda. Gama yanzu ke zaki fita waje daga birnin, ki zauna a waje, kuma ki tafi Babila. A can za a kuɓutar da ke. A can Yahweh zaya kuɓutar da ke daga hannun abokan gãbarki.11Yanzu al'ummai da yawa sun taru gãba da ke; sun ce, 'Bari ta ƙazance; bari idanunmu su yi murna a kan Sihiyona'12Basu san tunanin Yahweh ba, basu gane shirye-shiryansa ba, gama ya tara su kamar dammai a masussuka.13Tashi ki yi shiƙa ɗiyar Sihiyona, gama zan maida ƙahonki ya zama ƙarfe, kofatanki kuma su zama jan ƙarfe. Zaku hallaka mutane da yawa kuma zaku miƙa dukiyarsu ta zilama ta zama ta Yahweh, mallakarsu kuma ga Ubangijin dukan duniya."
AT: "Yahweh zai kafa dutsen da aka gina haikalinsa a kai"
Wannan yana nufin cewa Dutsen Sihiyona zai zama mafi muhimmanci cikin dukkan duwatsu. Kuma yana iya nufin cewa wannan dutsen zai zama mafi tsawo a duniya, ba a yankin nan ba kawai.
AT: "za a girmama shi fiye da duk wani dutse"
Jama'ar al'ummai za su eika zuwa wurin dutsen Yahweh kamar ruwa ke gudana a kogi. Wannan yana nufin cewa mutane da yawa za su je. AT: "jama'r al'ummai za su kwararo kamar kogi zuwa wurinsa" ko "jama'ar al'ummai a su je wurinsa"
Da tudun da gidan, duk suna nufin haikalin da ke Yerusalem ne.
A nan, "tafarkunsa" da "hanyarsa" suna nufin abin da Allah yake so mutane su yi. Haka kuma, "tafiya" yana nufin za su yi biyayya da abin da ya fada.
A nan kalmomin "doka" da "magana" suna nufin abu daya. Al'immomin duniya za su ji dokar Allah a Yerusalem.
Garma wani karfe ne da mutane suke amfani da shi wajen haka kasa domin shuka iri.
Duka wadannan maganganu biyu suna nufin cewa za su maishe makaman yakinsu zuwa kayayyakin da za su mora don samar da abinci.
Ana amfani da wuakar aske itace wajen yanke rassa ko jikin itace domin ya fi ba da 'ya'ya.
Mika ya ci gaba da bayyana "kwanakin karshe" sa'ad da mutane za su koyi dokar Yahweh, su kuma yi biyayya shi.
Wannan misali ne na mutane suna zaman lafiya.
AT: "gama Yahweh Mai Runduna ya yi magana"
Wannan furcin yana nufin sujada da biyayya.
Yahweh yana bayyana "kwanakin karshe" sa'adda mutane za su koyi dokar Yahweh, su kuma yi biyayya da shi.
"a nan gaba"
"Zan tattara marasa karfi a gu daya"
"in kuma tattaro wadanda na tilasa wa suka gudu"
AT: "kuma wadanda na kora, zan maishe su al'umma mai karfi"
Yahweh yana amfani da wannan kalmar domin jaddada cewa ya kamata mutanen Urushalima su tsare, su kuma kiyaye dukkan sauran jama'ar Isra'ila.
"Diyar" birni tana nufin mutanen birnin. AT: "tuddan da jama'ar Sihiyona suke zama"
Wadansu juyi na zamani sun fassara wannan kalmar Ibraniyancin da nufin "wurin tsaro" ko "mafaka".
Mika yana yi wa mutanen ba'a, yana kokarin ya sa su yi tunani game da abin da ya sa Yahweh yake horar da su ta wannan hanyar. A.T: "Yanzu, kuna ihu da karfi".
Mika ya ci gaba da magana da mutanen cikin ba'a. Amsar wadannan tambayoyin ita ce a'a. Sarkin da mashawarcin suna nan a wurin, amma ba su da amfani da taimako. AT: "Saboda haka, me ya sa kuke kuka yanzu? Don ba ku da sarki ne? Ko dukkan masu hikimarku sun mutu ne? Kuna ta kuka da karfi kamar macen take haihuwa".
Mika ya mori misalin mace mai nakuda don jaddada kuncin bauta. Yana nufin cewa, ya kamata su su ji wahala domin Allah yana hukunta su ta wurin korar su daga Isra'ila. Da yawansu ba za su sake komowa gida ba kuma.
AT: "Daga can Yahweh zai cece ki"
Yerusalem za ta yi nasara kan abokan gabarta.
AT: "Bari mu rushe birnin Yerusalem, mu hallakar da jama'arta, don mu ji dadin faduwarta".
Wannan yana nufin Allah kuma yana shirin hukunta jama'ar al'ummai.
Yahweh yana nuna misalin masussuka. (Duba 4:11)
Allah zai mori jama'ar Sihiyona don horar da jama'ar al'ummai.
Yahweh yana kwatanta mutanen Sihiyona da bijimi mai karfi wanda zai sa jama'ar Isra'ila su yi karfi kuma, don su iya nasara da sauran al'ummai.
1Yanzu ku taru da shirin yaƙi, ɗiyan sojoji; sojoji sun yi sansani sun kewaye birni, zasu bugi alƙalin Isra'ila da sanda a kunci.2Amma ke Betlehem Ba'ifrata, ko da yake ke ƙanƙanuwa ce a cikin dangi Yahuda, wani daga cikinki zaya zo gare ni ya yi mulkin Isra'ila, wanda farkonsa tun daga lokacin dã ne, tun daga can farko.3Saboda haka zaya bashe su, har sai wadda ta ke naƙuda ta haifi ɗa, kuma sauran 'yan'uwansa su dawo wurin mutanen Isra'ila.4Zaya tashi ya yi kiwon mutanensa cikin ƙarfin Yahweh, a cikin darajar sunan Yahweh Allahnsa. Zasu kasance, sa'annan shi zaya zama babba har iyakar duniya.5Zaya zama salamarmu. Sa'ad da Asiriyawa suka shigo cikin ƙasarmu, sa'ad da suka yi gangami gãba da kagarunmu, sa'an nan zamu tashi gãba da su, makiyaya bakwai da shugabanni takwas a kan mutane.6Zasu kiwaci ƙasar Asiriya da takobi, ƙasar Nimrod kuma a cikin ƙofofinta. Zaya kuɓutar da mu daga Asiriyawa, sa'ad da suka shiga cikin ƙasarmu, sa'ad da suka yi gangami cikin iyakokinmu.7Waɗanda suka rage na wajen Yakubu zasu zama cikin tsakiyar mutane da yawa, kamar raɓa daga wurin Yahweh, kamar ruwa a kan ciyawa, wadda ba mutum take jira ba, ba kuma 'ya'yan mutane take jira ba.8Waɗanda suka rage na wajen Yakubu zasu zama a cikin al'ummai, cikin mutane da yawa, kamar zãki a cikin namomin jeji masu yawa, kamar ɗan zaki a cikin garken tumaki. Sa'ad da ya shiga cikinsu zai tattaka su, ya daddatsa su, ba wanda zaya cece su.9Za a ɗaga hannunka gãba da abokan gãbarka, zaya kuma hallaka su.10"Haka zaya kasance a wannan rana" - wannan furcin Yahweh ne -- "zan hallakar da dawakanka a gabanka in narkar da karusanka.11Zan hallakar da biranen ƙasarka in lalatar da wuraren ɓoyewarka dukka.12Zan hallakar da maita da ke wurinka, baza ka ƙara samun masu duba ba.13Zan hallakar da sassaƙaƙƙun sifofinka da ginshiƙai na duwatsu daga wurinka. Baza ka ƙara bautawa aikin hannuwanka ba.14Zan tumɓuke ginshiƙan Asherarka daga wurinka, kuma in hallakar da biranenka.15Zan ɗauki fansa cikin fushi da hasala a kan al'umman da basu saurara ba."
Za a bugi shigaban Isra'ila da sanda a kumatu.
Yahweh yana magana da mutanen wannan garin kamar suna wurin suna sauraro.
Wannan zai iya zama ko sunan wani yanki ne a inda Betlehem take ko kuma wani suna ne kuma na Betlehem ko yana bambanta wannan Betlehem da wata. Betlehem tana da nisan kusan mil shida kudu da Yerusalem. Garin Sarki Dauda kenan. Masu fassara suna kara wannan bayanin kasan shafin: "Sunan nan, 'Ifrata' yana nufin 'ba da amfanin 'ya'ya'".
Wannan yana nufin Allah zai yi manyan al'amra ta hannun dan karamin gari mara tasiri.
A nan "na" yana nufin Yahweh.
Wannan yana nufin mai mulkin zai zo daga zuriyar asali ta Sarki Dauda. Kalmomin "tun fil'azal" da "daga har abada" suna nufin abu daya ne, kuma suna jaddada dadewan wannan zuriyar a tarihi.
"Saboda haka Allah zai manta da jama'ar Isra'ila".
Wannan yana nufin lokacin da za a haifi mai mulkin, dan kankanin lokaci.
"sauran 'yan'uwansa Isra'ilawa". Wadannan su ne Isra'ilawa da suke bauta. A nan "'yan'uwansa" suna nuni da yaron da zai zama mai mulki.
Wadannan ayoyin sun ci gaba da bayyana mai mulkin daga Baitalami.
AT: "Zai jagoanci jama'arsa da karfin Yahweh".
AT: "cikin karfin ikon Yahweh Allahnsa"
A nan, "su" yana nufin mutanen Isra'ila. Ana nufar kalmar "Isra'ila" ko "Yerusalem".
Wannan yana nufin cewa, nan gaba dukkan mutane daga kowace al'umma za su girmama mai mulkin Yerusalem.
A nan "mu" yana nufin Mika da jama'ar Isra'ila. AT: "Zai zama mai kawo salama"
A nan "makiyaya" yana nufin "masu mulki". Haka kuma, za ka iya kara bayanin kasan shafi mai cewa, "Lambobin nan 'bakwai' da 'takwas', tare suna nufin cewa za a sami yawan shugabannin da za su biya bukata".
A nan ana maganar nasara a kan Asiriyawa kamar kula da garken tumaki.
Wannan wani suna ne na kasar Asiriya. Nimrod mafarauci ne, kuma shugaba a da. Masu fassara suna kara wannan bayanin kasan shafin: "Sunan 'Nimrod' yana nufin 'tawaye'".
Za a iya fahimtar wannan a matsayin "cikin kofofinta". Kofofin birni wurare ne da jama'a inda shugabanni sukan yanke muhimman shawarwari.
"Mai mulkin zai ceci"
Wannan yana jaddada cewa mutanen Yahuza za su zama al'umma mai wartsakewa, da albarka.
AT: "kuma za su yi jira ga Allah, su dogara gare shi"
Wadannan kalmomi biyu suna da ma'ana daya, kuma suna jaddada cewa "Ringin Yakubu" za su zauna a kasashe dabam-dabam masu yawa.
Wannan yana jadda cewa jama'ar Isra'ila za su sami iko da karfin hali yayinda suke bauta, don su hukunta, su hallaka abokan gabansu.
Wannan yana nufin wani lokaci da ba a sani ba a nan gaba, mai yiwuwa a lokacin bauta.
Mutanen Isra'ila suna mafani da dawaki da karusai a lokacin yaki ne kadai. Mai yiwuwa kuma ya shafi kawance da kasashen waje, garuruwan arna. Allah ba ya so mutanen su dogara ga kayan yakinsu don kare kansu fiye da yadda suke dogara gare shi.
Yahweh ya ci gaba da magana da jama'ar Isra'ila.
1Yanzu ji abin da Yahweh ya faɗi, "Ka tashi ka kai ƙararka ga duwatsu; bari tsaunuka su ji muryarka.2Ku ji ƙarar Yahweh, ku duwatsu, da ku ginshiƙan duniya masu juriya. Gama Yahweh yana da shari'a da mutanensa, zai yi faɗa da Isra'ila a kotu."3Mutanena, me na yi ma ku? Ta yaya na gajiyar da ku? Ku faɗi laifin da na yi!4Gama na fito da ku daga ƙasar Masar na kuɓutar da ku daga gidan bauta. Na aiki Musa da Haruna da Miriyam zuwa wurinku.5Mutanena, ku tuna abin da Balak sarkin Mowab ya ƙulla, da yadda Bala'am ɗan Biyo ya amsa masa sa'ad da kuke tafiya daga Shittim zuwa Gilgal, ta haka za ku san aikin adalci na Yahweh."6Me zan kawo gaban Yahweh, sa'ad da na durƙusa gaban Allah mai girma? Na zo da hadayu na ƙonawa, da ɗan maraƙi bana ɗaya?7Yahweh zai yi murna da dubban raguna, ko da dubban rafukan mai? Zan ba da ɗan farina saboda laifina, ɗiyan jikina domin zunubina?8Ya dai gaya maka, mutum, abin da ke mai kyau, abin da Yahweh ke nema daga wurinka: Aikin adalci, jinƙai da tafiya cikin tawali'u tare da Allahnka.9Yahweh, yana yin furci da muryarsa zuwa ga birnin - ko yanzu hikima ta san sunanka: "Ku saurari sandar, da wanda ya ajiye ta a wurin.10Akwai dukiya a gidajen masu mugunta wannan rashin aminci ne, mudun ƙarya abin ƙyama.11Ko zan lura da mutumin daya yi amfani da ma'auni mara kyau, da bahu wanda nauyinsa na cuta ne?12Masu arziki sun zama cike da ta'addanci, mazaunan sun faɗi ƙarairayi, kuma harshensu da bakinsu na cike da ruɗi.13Saboda haka na buge ku da ciwo mai zafi, na mai da ku kango saboda zunubanku.14Za ku ci ba za ku ƙoshi ba, yunwarku za ta zauna a cikinku, za ku ajiye kayayyaki amma ba za ku adana su ba, abin da kuka adana zan bayar ga takobi.15Za ku yi shuka amma ba za ku yi girbi ba; za ku sawo zaitun amma ba za ku shafe kanku da mai ba; za ku matse kuringar inabi amma ba za ku sha ruwan ba.16Farillan da Omri ya bayar an kiyaye su, haka kuma dukkan abin da gidan Ahab suka yi. Kun yi tafiya bisa ga shawararsu. To haka zan mai da birnin kango, mazauna ciki kuma abin ƙi, ku mazaunan za ku yi ta fama da ba'a a matsayinku na mutanena."
A 6:1-5, Mika yana morar misalin dakin shri'a. Yahweh yana magana a gaban shaidun, don su fadi abin da ya sa mutanen Isra'ila suka manta da Allah suka fara bauta wa gumaka.
Mika yana magana da wadannan abubuwan kamar su mutane ne. Mika yana amfani da duwatsu, tuddai, da tussan duniya a matsayin madawwamin shaida na halin bautar gumakar mutanen.
Wannan ci gaban tuhumar da Yahweh yake yi wa jama'ar Isra'ila ne. (Duba 6:1)
Allah yana amfani da tambayoyi don jaddada cewa shi Allah nagari ne, kuma babu abin da ya yi don hana mutanen bauta masa. AT: "Jama'ata, na nuna muku nagarta. Ban yi komai don in gajiyar da ku ba. Idan kuna tsammanin na yi haka, to, sai ku fada mini yanzu".
AT: "inda kuka zama bayi"
"ku yi tunani"
Wannan nuni ne ga wani al'amari a da, sa'ad da Sarki Balak ya kira Bala'am don ya la'anci jama'ar Isra'ila. Amma, Allah ya sa Bal'amu ya albarkaci jama'ar ne kawai.
Wannan ne sunan uban Bala'am.
Wannan suna wani wuri ne a Mowab.
"don ku tuna ko wane ne ni, da kuma abin da na yi dominku"
Mika yana morar tambayoyi wajen koya wa jama'ar Isra'ila game da ainihin abin da yake faranta zuciyar Allah. AT: "Hakika, ba ku tsammanin cewa za su iya faranta ran Allah ta wurin kawo masa dan maraki mai shekara daya, raguna 1,000, koguna 10,000 na mai, ko ma dan farinku a matsayin hadaya domin zunubanku".
Wadannan kalamai biyu suna nufin abu daya.
"Yahweh ya fada maka"
AT: "Yahweh yana yin shela ga jama'ar Yerusalem"
AT: "mai hikima zai ji tsoron Yahweh" ko "mai hikima zai yi biyayya da abin da yahweh ya fada"
A nan "sanda" tana nufin mayakan abokan gaban da Allah zai mora don horar da mutanensa.
Wannan yana nuni da abin awo da ake yin awon da ba daidai ba don mutum ya yaudari sauran jama'a, ya samar wa kansa karin kudi.
Yahweh yana morar tambaya wajen jaddada cewa mai lafi ne mutumin da ya yaudari wadansu don ya sami karin kudi. AT: "Hakika, zan kama mutum da laifi idan ya mori ma'aunin cuta da ma'aunin karya don ya cuci sauran mutane, ya kuma sama wa kansa karin kudi".
"Attajirai suna cutar matalauta"
Duk wadannan maganganu biyu suna nufin abu daya, kuma an hada su tare ne don jaddadawa. AT: "dukkanku makaryata ne". Ya kamata wannan ya soki zuciyar mai karatu.
Yahweh yana bayyana horon da zai yi wa jama'arsa kamar barin mayakan abokan gaba su kwashe duk abin da suka girmar, suka shirya, suka kuma adana wa kansu.
Yahweh ya ci gaba da magana da jama'ar Isra'ila.
"Kun yi abin da Omri ya Umurta"
Wadannan mutane biyu duk sarakuna ne na masarautar arewa ta Isra'ila. Allah ya dauki dukkansu biyu a matsayin mugaye.
"kun aikata miyagun abubuwan da Omri da Ahab suka fada wa jama'a su yi"
Wato, abin ba'a ta wurin yin tsaki.
1Kaito na! Gama a gare ni ya zama kamar an riga an gama girbi na kaka, har ma da kalar abin da ya rage na kuringar inabi a gonaki: Ba sauran 'ya'yan itatuwan da za a samu, babu nunar fari na 'ya'yan ɓaure waɗanda rai na ke so.2Babu sauran amintattun mutane a ƙasar, babu sauran na kirki a cikin dukkan 'yan adam. Dukkan su sun yi kwanto domin su zãbar da jini, kowanne ɗayansu yana farautar ɗan'uwansa da tãru.3Hannayensu sun iya yin ɓarna sosai: sarki yana nema a ba shi kuɗi, alƙali yana shirye ya karɓi cin hanci, ƙaƙƙarfan mutum yana gaya wa waɗansu abin da yake so ya samu. Haka suke rigima tare.4Mafi kyau a cikinsu kamar laka yake, mafi aminci a cikinsu yana kamar shingen ƙaya. Dãma masu tsaronmu sun yi magana a kan wannan rana, ranar da za a hore ku. Ranar ruɗewarsu ta zo.5Kada ka amince da kowanne maƙwabci, kada ka dogara ga kowanne aboki. Ka yi hankali da abin da za ka faɗi ko ma ga matar da ke kwance a kafaɗunka.6Gama ɗa yana rena ubansa, ɗiya kuma tana tayarwa uwatta, suruka tana tayarwa uwar mijinta. Abokan gabar mutum, mutanen gidansa ne.7Amma ni zan duba wajen Yahweh, zan jira ga Allah na cetona, Allahna zai ji ni.8Kada ka yi murna a kaina kai maƙiyina, ko na faɗi zan tashi. Sa'ad da na zauna cikin duhu, Yahweh zai zama haske a gare ni.9Saboda na yi wa Yahweh zunubi, zan jure da fushinsa har yayi mani shari'a, yayi mani hukunci. Zai kawo ni cikin haske, zan gan shi yana kuɓutar da ni cikin adalcinsa.10Sa'an nan maƙiyina zai gani, kunya za ta rufe wanda yake ce da ni, "Ina Yahweh Allahnka?" Idanuna zasu gan ta, za a tattake ta kamar taɓo a kan hanyoyi.11Ranar da za ka gina ganuwarka tana zuwa; a ranar nan za a faɗaɗa iyakokinka da nisa ƙwarai.12A ranar nan mutanenka zasu zo wurinka daga Asiriya da biranen Masar, daga Masar har zuwa babban Kogi, daga teku zuwa teku, daga dutse zuwa dutse.13Waɗancan ƙasashen za a watsar da su saboda mutanen da ke zaune, a wurin yanzu, saboda sakamakon ayyukansu.14Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garke abin gãdonka. Suna zaune su kaɗai a jeji, a tsakiyar fadama. Bari su yi kiwo a Bashan da Giliyad kamar kwanakin dã.15Kamar rana da ka fito daga kasar Masar, zan basu mamaki.16Al'ummai zasu gani su ji kunya a kan dukkan ikonsu. Zasu sa hannuwansu a bakinsu, kunnuwansu zasu toshe.17Zasu lashi ƙasa kamar macizai, kamar hallittun dake rarrafe a ƙasa. Zasu fito daga cikin kogunansu da tsoro, zasu zo wurinka da tsoro, Yahweh Allahnmu, kuma za su ji tsoro saboda kai.18Wane ne Allah kamar ka, kai da kake ɗauke zunubi, wanda yake ƙetare kurakuran mutanensa da suka rage, abin gãdonsa? Ba ka riƙe fushinka har abada, saboda kana ƙaunar ka nuna mana amincin alƙawarinka.19Za ka sake jin tausayinmu, kuma; za ka take muguntarmu a ƙarƙashin sawayenka. Za ka jefa dukkan zunubanmu cikin zurfin teku.20Za ka bada gaskiya ga Yakubu alƙawari da aminci kuma ga Ibrahim, kamar yadda ka rantsewa kakanninmu tun kwanakin dã.
Mika yana jaddada cewa babu mutane masu fadar gaskiya kuma, masu biyayya da Allah, a Isra'ila. AT: "Ni dai, jama'ar Isra'ila sun zama kamar gonar inabi bayan an gama girbi da kalace. Kuringan babu komai. Ba zan iya samun 'ya'ya ba kuma, amma ina marmarin cin nunannen baure".
Mika yana zugugutawa don ya nuna yadda yanayin ya yi muni. Yana jin cewa babu mutumin kirki da ya rage a Isra'ila.
Mika ya ci gaba da magana game da mutanen Isra'ila.
AT: "Mutanen suna da kirki kwarai"
Wannan yana nufin cewa, hatta mafi kyau cikin shugabannin Isra'ila suna cutarwa, kuma ba su da amfani.
A nan, "ku" yana nufin jama'ar Isra'ila. AT: "Annabawansu sun fada musu cewa Yahweh zai hukunta su"
Wannan yana iya nufin nasarar yaki a kansu. AT: "Yanzu ta zo, kuma ba za su fahimci abin da yake faruwa ba"
Mika ya ci gaba da magana da jama'ar Isra'ila.
Mika ya ci gaba da nuna cewa babu wani mai kirki, gaskiya, da biyayya ga Allah a cikin jama'ar Allah. A nan, yana jaddada cewa ba za su ma iya dogara da abokai ko dangi ba.
A nan "ni" yana nufin Mika.
Ba ga kansa kadai Mika yake magana ba. Yana nufin kada abokin gaba ya yi murna a kan abin da ke faruwa da jama'ar Isra'ila.
Mika yana nuni da masifar da ke zuwa ga jama'ar Isra'ila a matsayin "duhu". Yana nufin cewa, ko da Allah ya bar abokan gaba sun zo sun hallaka su yanzu, zai zo ya cece su nan gaba.
Ba ga kansa kadai Mika yake magana ba. Yana nufin dukkan jama'ar Isra'ila sun yi zunubi.
Wannan yana nuni da sa'ad da Allah zai yake cewa hukuncinsa a kan jama'ar ya isa. Sa'annan zai hori jama'ar wadancan kasashen da suka azabtar da jama'ar Isra'ila.
AT: "Zai zo ya cece mu daga hannun makiyanmu. Zai zama kamar kawo mutumin da yake cikin duhu zuwa wurin haske"
Ba ga kansa kadai Mika yake magana ba. Yanan nufin makiyin dukkan jama'ar Isra'ila.
Makiyin yana morar tambaya don yi wa jama'ar Isra'ila ba'a. AT: "Yahweh, Allahnku, ba zai iya taimakonku ba"
AT: "Ni" ko "Mu"
A nan "ta" yana nufin makiyan da suka azabtar da jama'ar Isra'ila.
AT: "za a tattake makiyansu a kasa"
A nan "garu" yana ufin ganuwar da ta kewaye biranensu, wadda ke tanadar da kariya da tsaro daga abokan gabansu.
AT: "Yahweh zai fadada iyakokin kasarka sosai" ko "Yahweh zai kara fadin masarautarka sosai"
AT: "Wadannan kasashen za su zama kango" ko "Babu wanda zai zauna a wadannan kasashen"
Mika yana addu'a ga Yahweh, yana rokonsa ya kare jama'arsa Isra'ila kuma. A nan "sanda" tana nufin shugabanci da jagorancin Allah, kamar yadda makiyayi yake amfani da sanda wajen bi da tumakinsa da kuma kare su.
Mika yana nufin cewa wadansu cikin mutanen suna zaune a wurinda kasar ba ta da amfani, kuma an yanke su daga sauran jama'a, ba za su iya samu kayayyakin da suke bukata a saukake ba.
Wadanan yankunan sun yi fice a matsayin kasa mai kyau don girmar da abinci. Saboda haka, Mika yana rokon karin fadadawa ta yankin, wanda aka rasa a da saboda abokan gaba sun mamaye.
Wannan yana iya nufin sa'adda Sulemanu yake sarki.
A nan "zan" yana nufin Yahweh.
Wannan yana nuna yadda suke mamaki, har ma ba za su iya yin wani abu ba. Duba UDB.
Duk maganganun nan biyu suna nufin abu daya. Za a wulakanta makiyan Allah gaba daya, za su zo wurinsa cikin fargaba don ganin al'amuran iko da yake yi.
Mika yana morar tambaya don jaddada cewa babu wani wanda yake aikata abin da Yahweh yake yi.
"cikin mu, zababbun jama'arka, wadanda suka tsira bayan hukuncinka"
A nan "ka" yana nufin Yahweh.
A nan "mu" yana nufin Mika da jama'ar Isra'ila.
Wannan yana nufin, Allah zai gafarta zunuban jama'ar gaba daya, kuma ba zai ci gaba da horon mutanen saboda su ba.
A nan, "Yakubu" da "Ibrahim", wadanda kakannin al'ummar Isra'ila ne, suna nufin jama'ar Isra'ila a yanzu.
Wannan yana nufin Ibrahim da yakubu, watakila ma da sauran da suke raye sa'adda Allah ya yi alƙawarinsa da Isra'ila.
1Furci game da Nineba. Littafin wahayin Nahum, mutumin Elkosh.2Yahweh Allah Mai kishi ne da sakayya; Yahweh mai sakayya ne da fushi mai zafi; Yahweh na ɗaukar fansa a kan abokan gãbarsa, kuma yana ci gaba da fushinsa a bisa maƙiyansa.3Yahweh na da jinkirin fushi da iko mai girma; ba zai ƙyale miyagu ba hukunci ba. Yahweh na shirya hanyarsa a cikin guguwa da hadari, gizagizai kuma ya maishe su ƙurar tafin sawayensa.4Yana tsauta wa teku ya kuma busar da ita; ya busar da dukkan koguna. Bashan ta yi rauni, haka kuma Karmel; furannin Lebanon sun yi yaushi.5Duwatsu suna girgiza a gabansa, tuddai kuma suna na narkewa; duniya tana rushewa a gabansa, hakika, dukkan duniya da mazaunanta.6Wane ne zai iya tsayawa a gaban hasalarsa? Wane ne zai iya tsayayya da zafin fushinsa? Hasalarsa na zubowa kamar wuta, kuma yana farfasa duwatsu.7Yahweh nagari ne, mafaka ne mai ƙarfi a ranar masifa; mai aminci ne kuma ga dukkan masu fakewa a cikinsa.8Amma zai hallakar da maƙiyansa kakaf da babbar ambaliya; zai kora su can cikin duhu.9Ku mutane mene ne ku ke shiryawa gãba da Yahweh? Zai kawo ƙarshensa dukka; Masifa ba za ta sake tasowa karo na biyu ba.10Gama zasu zama a harɗe kamar sarƙaƙiya; abin shansu zai gundure su; wuta zata cinye su sarai kamar busasshiyar ciyawa.11Wani ya tashi daga cikin ki, Nineba, wanda ya yi shirin mugunta game da Yahweh, wani wanda ya haɓaka aikin mugunta.12Ga abin da Yahweh ya faɗi, "Ko da suna cike da ƙarfinsu da kuma yawansu, duk da haka za a datse su; jama'arsu za su ƙare sarai. Amma kai, Yahuda; ko da ya ke na wahalshe ka, ba zan ƙara wahalsheka ba.13Yanzu zan karya karkiyar mutanen nan daga gare ka; Zan tsinke sarƙoƙinka."14Nineba, Yahweh ya ba da umarni game da ke; "Babu wata sauran zuriyar da za a kira ta da sunanki. Zan datse sassaƙaƙƙun gumaka da kuma gumakan ƙarfe daga gidajen allolinki. Zan haƙa kaburburanki, gama ke abin raini ce."15Duba, a bisa duwatsu, akwai sawayen wani mai kawo labarai masu daɗi, wanda ya ke shelar salama! Yahuda, yi murnar bukukuwanka, ka kuma cika wa'adodinka, gama mugu ba zai ƙara mamaye ka ba, don an datse shi sarai.
Nahum ya raira wakar kwatancin yadda za a hallaka Nineba.
"Sako daga Allah a kan kasar Nineba."
Mutumin kauyen Elkosh
Wannan shine suna Allah wanda ya bayana wa mutanen tsohon alkawali. dubi shafin translationWord game da Yahweh da kuma yadda zaa juya shi.
wannan na nufin, Yahweh zai sharanta ya kuma horata makiyansa idan sun ki yin biyayya.
karma yadda guguwa da haddirisuke mutsi, haka ne Yahweh ke tafiya da konsa. AT: "ya na zuwa da iko." .
kurar da kafafunsa ke bugawa.
Nahum ya cigaba da bayana ikon Yahweh bisa dukan duniya.
AT: "Duwatsu, tutdai, da duniya na razana a gabar Yawe"
kamar mutum wanda tsora ta kamashi
faɖuwa a kasa domin tsoro
Nahum ya yi magana game da ikon Yahweh
kwatancin yawan fushinsa ko kuma girmar fushinsa
AT: "Ya zuɓo fushinsa kamar wuta, ta kuma farfasa duwatsu."
wurin da aka gina domin mutane su ɓuya daga fuskar magabta
idan magabta suka afko. AT: "idan munanan abubuwa sun faru."
Nahum ya faɗă wa mutanen yadda Yawe zai hukunta su.
a sayar da abinda ake yi
AT: "Ba zai afko maku na biyu ba"
fuskanci matsaloli dayawa da zai hana su afko masu .
Yawe zai hallaka dukan Nineba
karfafa mutane su yi aikin mugunta
Yahweh yayi magana da Isra'ilawa game da Nineba
"Za'a kau da su" Yahweh ya yi amfani da misalin yadda ake jeme dabba don ya nuna yadda zai kau da Nineba, ko da shike su na da yawa. AT: "za'a hallakasu
AT: !yantatdasu daga bauta"
"yanka sarkar bautansu"
wani na kawo labari mai kyau
Nahum na magana da Nineba sai ka ce mutum ɗaya.
Nahum na maga sai ka ce ta rigaya ta faru
1Shi wanda zai daddatsa ku yana zuwa gãba da ku. Ku tsare ganuwar birnin, ku yi tsaron hanyoyi. Ku ƙarfafa kan ku, ku shirya sojojinku.2Don Yahweh zai dawo da darajar Yakubu, kamar darajar Isra'ila, ko da ya ke maharan sun washe su sun kuma ɓaɓɓata rassan kuringar inabinsu.3Garkuwoyin jarumawansa jajaye ne, kuma sojojinsa sun sa jajayen tufafi, ƙarafan karusansu na walƙiya tun ranar da a ka shirya su, kuma suna karkaɗa mãsunsu masu ƙotar katako a iska4Karusai na ta yin gudu a tituna suna kai wa suna kawowa a manyan tituna. Suna kama da harsunan wuta, kuma suna gudu kamar walƙiya.5Wanda zai daddatsa ku gutsu-gutsu ya kira jarumawansa, cikin tafiyarsu suna cin karo da juna, su na sauri don su kawo hari a kan ganuwar birnin. An shirya babbar garkuwa don ta kare masu kawo hari.6An buɗe ƙofofin bakin koguna ta ƙarfi da yaji, fadar kuma ta zama kufai.7An tuɓe wa Huzzab tufafinta an kuma tafi da ita; bayinta mata suna makoki kamar kurciyoyi, suna bugun ƙirjinsu.8Nineba ta zama kamar tafki mai maguda, tare da mutanenta suna gudu kamar ruwa mai kwarara. Waɗansu na ihu "ku tsaya, ku tsaya", amma ba wanda ya waiga baya.9Ku ɗauki ganimar azurfa, ƙu ɗauki ganimar zinariya don bata da iyaka, kan dukkan abubuwa kyawawa masu daraja na Nineba.10Nineba ta zama kango da kufai. Zuciyar kowa ta karaya, gwiwoyin kowa na gugar juna, kowa na cikin baƙinciki; fuskokinsu sun yanƙwane.11Yanzu kuma ina kógon zakokin, inda ake ciyar da 'ya'yan zăki, wurin da zãki da zãkanya ke tafiya da 'ya'yansu ba su tsoron komai?12Zãki ya yayyaga abin da ya kama don 'ya'yansa, ya murɗe abin da ya kamo wa zãkanyarsa, ya cika kógonsa da waɗanda ya kamo, ya cika raminsa da yagaggen mushen waɗanda ya yayyaga.13"Duba, ina gãba da ku - wannan furcin Yahweh mai runduna ne. Zan ƙone karusanku, a cikin hayaƙi, takobi kuma zai cinye ƙananan zakunanku. Zan datse ganima daga ƙasarku, kuma ba za a ƙara jin muryoyin masu kawo saƙonku ba."
Nahum ya cigaba da bayyana hallakarwa da za a yi wa Nineba.
an kwatanta kasar da gonar inabi. AT: "an tumbuke kasarku sai ka ce gonar inabi."
sojojin wanda zai kacancana Nineba kashi kashi. (2:1).
wata irin bishiyace wanda tana da kyau wajen kiran makamai.
masu hawan karusan sun yi mummunan gudu a hanyoyi.
wannan na nufin hasken da ke fitowa sa'ad da masu karusan ke fuskantar rana. (Dubi:
manufa: 1) "bada umurnin kiran shugabanninsa ko kuma, 2) tunanin shugabanninsa"
Wannan sunan saraniyar Asuriya ko kuma wata gunkin Asuriya. idan na nufin sarauniyar, ya zama kenan sojojin sun yage tufafinta don su kunyatarda ita. idan na nufin gunki, ya zama kenan sojojin sun sace duwatsu masu tsada da a ka rufe gunkin.
"barorinta matan na kuka da murya kamar na kurciya, yayinda suna makokin rashin masayinta.
abubuwan da aka kwashe da karfi, musamman lokacin yaki.
wannan na kwatanta misalin abu mai yawa. AT: a kwai shi dayawa
na nifin: 1) yalwar abubuwa masu kyau, ko kuma 2) wadatar abubuwa masu kyau.
dukan mutanen sun karaya
an kwatanta Nineva da kokon zakuna, domin a can ne makisa ke zama, su kuma kawo kayan da aka sace daga hannun waɗanda suka kashe.
zaki kan murɖa wuyar dabban da ya kama don ya hana shi numfashi.
wato "fahimci wannan"
"sojojinku zas yi mutuwar wulakanci"
wato samaranku masu kyau
kalmar "ganima" na nufin arzikinda Nineba ta kwashe daga wasu kasa. wannan na nufin Yahweh zai hallaka ikon sato arzikin wasu kasashe.
1Kaiton birni wanda ke cike da jini! Wanda ke cike da ƙarairayi da kayan sata; a kullum waɗanda aka ƙwara suna cikinsa.2Ƙarar bulala na cikinsa, da ƙarar karusan yaƙi da haniniyar dawakai da sukuwar karusai.3Akwai mahayan dawakai masu kawo hari, da walƙiyar takubba da ƙyallin mãsu da tarin gawaye da tsibin jukkuna. Gawarwaki ba su da iyaka; maharan sun yi tuntuɓe a kan su.4Wannan na faruwa ne saboda mummunar sha'awa ta ayyuka kyakkyawar karuwar, ƙwararriya a maita, mai sayar da al'ummai ta wurin karuwancinta, ta wurin ta kuma mutane na aikata maitanci.5"Duba, ina gãba da ke - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - Zan kware zanen ki in sa ki zama tsirara a gaban al'ummai, ki zama abin kunya ga masarautu.6Zan kawo ƙazanta a kan ki, in sa ki zama abin reni; zan mayar dake abin kallo.7Zai zama dukkan wanda ya dube ki zai koma da baya, ya ce 'Nineba ta rushe; wa zai yi kuka domin ta?' Ina zan sami wanda zai yi maki ta'aziya?"8Nineba, kin fi Tebes ne wadda aka gina ta kusa da Kogin Nilu, wadda ruwaye ke kewaye da ita, wadda kariyarta teku ne, wadda teku ta yi mata dajiya?9Kush da Masar ne ƙarfinta, kuma ba shi da iyaka; Fut da Libiya suka yi amana da ita.10Duk da haka an kwashe Tebes, ta tafi bauta; an fyaɗa 'ya'yanta a ƙasa a kan hanyoyi, abokan gabarta sun jefa ƙuru'u a kan manyan mutanenta, kuma an ɗaure ƙarfafan mutanenta da sarƙoƙi.11Ke ma za ki bugu, za ki yi ƙoƙarin ɓoyewa ki nemi mafaka daga abokan gãbarki.12Dukkan hasumiyoyinki zasu zama kamar itacen ɓauren da yake da 'ya'yan fari: idan an girjiza su, zasu faɗo a bakin mai cinyewa.13Duba, mutanen dake tare dake mata ne; ƙofofinki suna bude ga abokan gãbarki; wuta ta cinye makaranki.14Ki je ki ɗebo ruwa domin za a kewaye ki, ki ƙarawa kagarorinki ƙarfi, ki je wurin magina ki samo yunɓu ki yi tubula.15Wuta zata same ki a wurin, takobi zai hallaka ki. Zai cinye ki kamar yadda fãra ta kan cinye komi da komi. Ki maida kanki kamar 'ya'yan fãra, ki yi yawa kamar fãrin da suka yi ƙwari sosai.16Kin riɓanya abokan cinikayyarki da yawa kamar taurarin sammai; amma suna kamar 'ya'yan fãri sukan washe ƙasa su tashi.17'Ya'yan sarakunanki suna da yawa kamar fãrin da suka yi girma sosai, jarumawanki kuma na kamar fãrin da suka yi cincirindo a bango lokacin sanyi. Amma idan rana ta yi sai su tashi su tafi wurin da ba'a sani ba.18Sarkin Asiriya, masu tsaronka sun yi barci; masu mulkinka sun kwanta suna hutawa. Mutanenka sun warwatsu a kan duwatsu ba wanda za ya tattarosu.19Raunukanka ba zasu warke ba. Raunukanka sun yi zafi sosai. Dukkan wanda ya ji labarinka zai tafa hannu domin murna a kanka. Wane ne ya tserewa muguntarka ta ko yaushe?
Nahum ya cigaba da magana a kan Nineba kamar yadda ya fara a sura 1:1.
Sojojin Nineba sun kashe mutane dayawa. AT: "jinin mutane dayawa na bisa wannan kasar."
an maimaita domin a karfafa irin kisa da zai afko wa Nineba.
kamar yadda karuwa ke sayasda jikinta, da kuma yadda masu maitanci ke sayasda iliminsu, haka ne mutanen Nineba ke sayas da bayi don su sami kuɗi.
wannan na tamako don ya ja hankalin mai sauraro ga abinda za'a faɗa
AT: "babu wanta zai yi kuka da ita. Babu wanda zai ta'azantatda ita.
Nahum na magana da mutanen sai kace sne garin.
AT: "baku fi Tebes ba ..." Dubi:
tsohuwar cibiyar kasar Masa wanda Asiriyawa suka ci da yaki
dukansu biyu na nufin abu ɗaya ne. Dukansu na nufin kogin Nilu ne wanda ke kusa da garin har ya zama da wuya a afkar wa kasar.
garurukan da na da ganuwa kewaye da su don ya zama kariya daga magabta.
Nahum ya yi magana da mutanen Nineba kamar sai ka ce su ne kasar da kanta.
wannan cigaban kwatancin Nineba ne da Tebes daga sura 3:8. Maanar kuwa na iya zama: "Duk da haka" (UDB) ko kuma "bayan haka"
wannan shine tsohuwar cibiyar kasar Masar, wanda Asiriyawa suka cinye da yaki.
mayakan sun kashe kananan yara na kasar Tebes kamar sai kace ana farfasa kasko.
wato maida mutum bawa. AT: "zaman bayi"
Nahum ya yi magana da mutanen Nineba kamar sai ka ce su ne kasar da kanta.
ana iya juya kalmar nan kamar "madogara" wannan na nufin dukan kasar Nineba da kuma mulkin Asiriya.
Kasar Nineba zata yi saukin kwashewa kamar yadda ake sunkan yayan bishiya.
"Mutanenku basu da karfin tsare kansu ba."
wannan wata babbar gungume ne wanda ke tsare kowar gari ta ciki yadda magabata bazasu iya bude ta daga waje ba. Idan an kona wadannan gungumen, yana da wuya a kulle kofar birnin.
Nahum ya yi magana da mutanen Nineba kamar sai ka ce su ne kasar da kanta.
zata hallakar kamar yadda fari ke hallaka dukan abinda suka samu.
wato, wutar ko takobin
mayan fari - kun yawaita kamar manyar fari! Kun yawaita kamar kananan fari!. wadanan kalmomi suna fara managane.
wannan na nufin, zasu zama babbar birni cike da mutane masu yawa, zasu kuma hallaka kasashe.
Nahum ya yi magana da mutanen Nineba kamar sai ka ce su ne kasar da kanta.
kamar yadda take da wuya a kidaya taurarun sama, haka take da wuya kwarai a kiɗaya dillalen Nineva. AT: "Kuna dillalai fiye da abinda mutum zai iya kidayewa."
"masu kayan koli" ko kuma "masu saya da sayarwa"
ana amfani da wannan kalma wajen kiran shugabannin siyasa (UDB)
Ka yi amfani da kalmarnan wajen kiran shugabannin gwamnati ko kuma shugabannin sojoji. Dubi:
Anan, 'Makiyaya' na nufin shugabannin Asuriyawa.
AT: "Muguntarka na kullum ya raunana mutane da kasashe dayawa."
1Saƙon da annabi Habakuk ya karɓa,2"Yahweh, har yaushe zan yi kukan neman taimako, ba za ka ji ni ba? Na yi kuka gareka cikin 'husuma'! amma ba za ka cece ni ba.3Donme kake bari na in kalli mugunta, in kuma dubi rashin gaskiya? Hallaka da tashin hankali na gabana; akwai jayayya, kuma gardama ta taso.4Saboda haka shari'a ta yi rauni, adalci kuma bai ɗore ba ko da na ɗan lokaci. Domin muguye sun kewaye masu adalci; shi yasa shari'a ta karkace." Yahweh ya amsa wa Habakuk.5Ka dubi al'ummai ka bincike su; ka yi mamaki da al'ajibi! Domin lallai na kusa in yi wani abu a kwanakin ka da ba za ka gaskata ba idan an faɗa maka.6Ka duba! Na kusa ta da Kaldiyawa - waɗannan al'ummai - masu zafin rai da kuma garaje - zasu ratsa dukkan faɗin ƙasar, su ƙwace wurare da ba nasu ba.7Masu ban razana ne da kuma ban tsoro; hukunci da darajassu daga gare su suke fitowa.8Dawakansu sun fi damisa gudu, sun fi kyarketan maraice sauri. Dawakan su su na tattakawa, mahayansu sun zo daga nesa sosai - Su kan tashi kamar gaggafar da ke niyyar ci.9Duk sun zo domin husuma; rundunarsu sukan tafi kamar iskar hamada, sukan tara bayi kamar yashi.10Suna yi wa sarakuna ba'a, masu mulki kuma abin ba'a ne a gare su. Suna ma duk kagara dariya, domin sukan tula ƙasa su hau su washe su.11Sa'an nan iska za ta buga mugayen mutane ta wuce da sauri, waɗanda ƙarfinsu allahnsu ne." Habakuk ya sake tambayar Yahweh12"Kai ba tun fil'azal ka ke ba, Yahweh Allahna, Mai Tsarkin nan? Ba za mu mutu ba. Yahweh ya ƙaddara su ga hukunci, kai kuma, Dutse, ka kafa su domin gyara.13Idanuwanka masu tsarki ne ba za su duba mugunta ba, ba za ka kuma dubi mugun aiki da tagomashi ba; to don me kake duban masu cin amana da tagomashi? Don me ka yi shuru sa'ad da mugaye suke haɗiye waɗanda suka fi su adalci?14Ka maida mutane kamar kifi a teku, kamar abubuwa masu rarrafe da basu da shugaba.15Ya kan kawo su dukka da ƙugiyar kamun kifi; yakan ja mutane a tarun kifi su tara su a tãrunsu. Wannan ne ya sa suke murna suna sowa mai yawa.16Shi ya sa suke miƙa hadayu ga tarun kama kifinsu suna ƙona wa tarunsu turare, domin dabbobi masu ƙiba ne rabonsu, nama mai kitse ne abincinsu.17Saboda wannan ne zasu juye tarun kama kifinsu su ci gaba da yanka al'ummai, ba jin tausayi?"
waɗannan kalmomi sun bayyana surorin biyu na farko a littafinnan. ya yu ka fi son si a haha: "Wannan shine saƙon da Annabi Habakuk ya karɓa daga Allah."
wannan shine sunan Allah da shi da kanshi ya bayyana wa mutanen Tsoho Alƙawali. Dubi shafin translationWord game da Yawe domin karin bayani game da yadda ya kamata a juya shi.
AT: "Na jima ina ira domin taimako amma sai ka yi kamar ba ka ji na ba!"
Habakuk ya cigaba da addu'arsa ga Allah.
"faɗa tsakanin mutanen ya zama ruwan dare."
wannan na nufin, masu adalci na shan wahala domin 1) "mugaye suna da iko fiye da asu adalci" ko kuma 2) "mugaye sun fi masu adalci haɓaka."
AT: "mugunta ta yawaita maimakon adalci" ko kuma "rashi adalci na karuwa"
Yahweh ya asma addu'a Habakuk.
"Ka koyi abinda ke faruwa da shauwan kasashen
wannan zai iya zama: 1) koina a Yahuda ko kuma 2) ko ina a duniya.
karɓa da karfi ko kuma saci kayan wani
sojojin kaldiyawa. Allah zai tasar da kasar Kaldiya da sojojinta domin su kwace kasar Yahuda.
kalmar tsoro da razana na nufin abu ɗaya ne kuma na jaɗɗaɗa cewa sun sa mutane na tsoronsu kwarai da gaske. AT: "Sun sa tsoron a zuciyar jama'a."
dawakan sojojin Kaldiyawa
ana kwatanta dawakan Kaldiyawa da nyennyewar da take bin dabba domin ta kama, musamman da maraici a lokacinda suke cike da yunwa.
wato Kaldiyawa masu hawan dawakai
babbar dabba mai kama da kuliya
masu sukuwan na gudu sosai kamar yadda mikiya ke firiya.
Kaldiyawan na da yawan gaske, ba su iya kiɗuwa kamar yadda yana da wuya a kiɗaya kwayar yashi da iskar guguwa ke ɗauka. Ba shi kuwa yuwuwa a kiɗaya jama'ar da suke kamu domin bauta.
Yahweh ya cigaba da bayani game da sojojin Kaldiyawa.
An kwatanta Kaldiyawa da guguwa da ke busowa daga wuri zuwa wuri ba tare da ɓata lokaci ba.
Habakuk ya yi magana da Yahweh game da Kaldiyawa
AT: "Kai ne tun filazar, Yahweh Allahna, Mai Tsarki."
wato Kaldiyawa kenan
kariyar Isra'ila
"an tasar da su domin su kwaɓi Isra'ila"
Habakuk ya cigaba da magana da Yahweh game da Kaldiyawa
"wat Kaldiyawa, waɗanda babu mai yarda da su"
"hallaka" (UDB)
waɗannan magangan biyu na nufin abu ɗaya ne, wato Allah ya yadda Isarilawa su sa dibga a hannun Kaldiyawa kamar sai kace su ba wani abu mai daraja ba.
Habakuk ya cigaba da magana da Yahweh game da Kaldiyawa
kayan da ake amfani dasu domin kamun kifi
tarko don kamun kowan dabba mai rarrafe
AT: "dabbobi mafi kyau da kuma nama mafi kya suna suke raɓawa tsakaninsu."
wato raɓiya tsakanin jama'a
masunta na juya tarunsu domin iya wurga ta kuma.
1Zan tsaya wurin tsarona in kuma tsaya kan hasumiya, in duba da kyau in ji abin da dai zai faɗi mani da yadda zan amsa masa game da ƙarata.2Yahweh ya amsa mani ya ce, "Ka rubuta wannan ruyar, ka rubuta ta da kyau a kan alluna domin duk wanda ke karanta su ya gudu.3Domin ruyar lokacinta ya na gaba a ƙarshe lallai za ta cika ba zata fasa ba. Ko da ta yi jinkiri, ku jira. Tabbas zata zo ba za ta yi jinkiri ba.4Duba! Shi wanda sha'awace sha'awacensa ba dai-dai suke a cikinsa ba hurarra ne. Amma adali ta wurin bangaskiyarsa zai rayu.5Gama ruwan inabi abin yaudara ne ga mutum mai fahariya domin kada ya kiyaye, amma ya yawaita marmarinsa, kamar kabari, kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi. Ya kuma tattara wa kansa kowacce ƙasa ya kuma tattaro wa kansa dukkan mutane.6Ashe ko waɗannan ba zasu sa a ƙirƙiro masa maganganun reni da waƙa da zanbo suna cewa, 'Kaiton wanda yake ƙarawa kansa abin da ba nasa ba! Har yaushe zaka yi ta ƙara wa kanka nauyin al'ƙawuran da ka ɗauka?'7Masu cizonka ba zasu tashi farad ɗaya ba, su da ke tsoratar da kai sun farka? Za ka zama ganima a gare su.8Saboda ka washe mutane da yawa, dukkan sauran al'ummai za su washe ka. Saboda ka zubar da jinin mutane tare da tashin hankali a ƙasa, da birane da duk waɗanda ke zaune a cikinsu.9'Kaitonsa mai cin ƙazamar riba domin gidansa, yakan gina sheƙarsa a sama domin ya tsare kansa daga hanun mugunta.'10Ka jawo wa gidanka kunya ta wurin dạtse mutane da yawa, ka kuma yi wa kanka zunubi.11Gama daga cikin katanga duwatsu zasu tada murya, katako kuma daga cikin itatuwan jinka zai amsa masu,12'Kaiton wanda ya gina birni da jini, da wanda ya kafa gari da mugunta.'13Ashe ba daga Yahweh mai runduna ba ne mutane ke wahala domin su sami wuta, sauran ƙasashe kuma suna gajiyar da kansu domin abin wofi?14Har yanzu ƙasar zata cika da sanin darajar ɗaukakar Yahweh, kamar yadda ruwaye ke rufe teku.15'Kaiton wanda ke tilasta maƙwabcinsa ya sha, ka na nuna fushinka, kana kuwa sa su bugu, domin ka dubi tsiraicinsu.'16Maimakon ɗaukaka za ka cika da kunya. Yanzu lokacinka ne! Kai ma ka sha zaka kuma bayyana tsiraicinka. Ƙoƙon hannun dama na Yahweh zai juyo gare ka, kunya kuma zata rufe darajarka.17Tashin hankalin da aka yi wa Lebanon zai komo maka, hallakar dabbobi kuma zata tsoratar da kai. Domin ka zubar da jinin mutane, ka aikata tashin hankali gãba da ƙasa, da birane, da waɗanda ke zaune a cikinsu.18Ina amfanin sassaƙaƙƙiyar siffa a gare ka? Ko gare shi wanda ya sassaƙa ta, gunki na zubi, mai koyar da ƙarairayi; gama ya na sa dogararsa ga aikin hannuwansa sa'ad da ya ke yin waɗannan alloli bebaye.19'Kaiton wanda ke ce wa itace, 'Ka farka!' Ko ya ce wa beben dutse, 'Ka tashi!' Waɗannan abubuwa suna koyarwa ne? Duba, an dalaye su da zinariya da azurfa amma ba numfashi ko kaɗan a cikinsa.20Amma Yahweh yana cikin haikalinsa mai-tsarki! Ku yi shiru dukkan ƙasa a gabansa."
dukan su biy na nufin abu ɗaya ne, Kamar yadda sojoji ke sayuwa a bakin kofar gari suyi tsaro, hakanan Habakuk ke misalin sa da rayuwarsa.
AT: zan bar gunaguni in kuma yadda da Allah
Yahweh ya amsa Habakuk
dukansu biyu na nufin abu ɗaya. AT: "Ka rubuta dukan abinda Allah ke shirin faɗa maka a bisa allo"
an kerasu ne daga duwatsu ko kuma daga taɓo da ake amfani da shi domin ginin tukunya. da shi ne ake rubutu.
"Ba zai yi jinkiri ba," ko kuma "ba zai zo da hankali ba.
Yahweh ya cigaba da amsa Habakuk
kalmar "duba" na nufin jaddada magana akan abinda zai bi baya.
duka biyun na nufin abu ɗaya ne. "yana tattara kowane mutane daga kowane kasa"
Yahweh ya cigaba da amsa wa Habakuk. Ya yi magana da Kaldiyawa sai kace mutum ɗaya.
"Lokaci na zuwa da ba za ku iya karɓar alkawari ba kuma." Wannan na nufin: 1) Kaldiyawa na kama da ɓarayin da ke ɗauke da alƙawarin da suka sa mutane suyi na dole. 2) Yahweh na sane da abubuwan da Kaldiyawa suka sata, yana shirya lokacin da zai sa su dole su biya diyya.
abinda aka saci, ko kuma an karɓa da karfi.
Yahweh ya cigaba da amsa Habakuk, ya kira Kaldiyawa kamar sai ka ce mutum ɗaya ne.
"wanda yake aiki domin ya sami riɓar da ta shigo ta hanyar cuci domin iyalinsa.
wato ya gina ginasa a inda damuwa bazata same shi ba.
AT: mugayen mutane .
"da shike ka hallaka mutane da dama, iyalin ka zai cika da kunya"
Yahweh ya cigaba da amsa Habakuk. ya yi magana akan Kaldiyawa sai kace mutum ɗaya
dukansu biyu na nufin abu ɗaya. AT: "kashedi zuwa Kaldiyawa masu gina kasarsu da kaan da aka sata daga hannn mutanen da suka kashe."
Allah ya kawo sanadiyar hallakar dukiyar mutane. AT: Yahweh shi yakan sa abinda mutane suka tara ya salwance a bansa.
Yahweh ya cigaba da amsa Habakuk, yayi magana akan Kaldiyawa sai ka ce mutum ɗayane.
zuba dafinka a kan ruwansu
"da shike kuna neman ɗaukaka, Allah zai cika ku da kunya"
"kamar yadda Yahweh ya horanci wasu kasashe da ikonsa, hakanan sai horanceku da ikonsa"
"kowa zai ga tsirancinku, babu kuma wanda zai ga ɗaukakanku"
Allah ya cigaba da bayyana yadda zai hallaka Kaldiyawa
"idan dabbobi sun fara mutuwa zai sa ku ku razana"
kamar yadda masu gina tukunya suke yi, hakanan ake yi da azurfa a gina gumaka.
ana nufin sananda aka arke karfe domin gina wata abu.
wannan na nufin masu narke karafuna domin gina gumaka. Suna gina alloli na karya. Ta hakane suke karfafa koyarwar karya.
1Addu'ar annabi Habakuk a waƙance:2Yahweh na ji labarinka, kuma na tsorata. Yahweh, ka farfaɗo da aikinka a cikin waɗannan lokatai; a cikin waɗannan lokatai ka bayyana shi; ka tuna da yin tausayi cikin fushinka.3Allah ya zo daga Teman, kuma Mai Tsarki daga Dutsen Faran. Selah. Ɗaukakarsa ta rufe sammai, kuma duniya na cike da yabonsa.4Sheƙi biyu na hannunsa na haskakawa kamar walƙiya, inda ƙarfinsa yake a ɓoye.5Cuta mai hallakarwa ta tafi a gabansa, annoba kuma ta biyo sawunsa.6Ya tsaya ya auna duniya; ya duba kuma ya girgiza al'ummai. Harma daɗaɗɗun duwatsu suka rugurguje, madawwaman tsaunuka kuma suka rusuna ƙasa. Tafarkinsa madawwami ne.7Na ga runfunan Kushan cikin ƙunci, kuma bargunan runfunan cikin ƙasar Midiyan suna raurawa.8Yahweh ya fusata da kogunan ne? fushinka a kan kogunan ne, ko hasalarka kan teku ne, da ka yi sukuwa bisa dawakanka da karusanka masu nasara?9Kã fito da bãkanka a ɗane; kạ sa kibiyoyinka ga băkanka! Selah. Kạ raba duniya da koguna.10Duwatsu sun gan ka sun murɗe cikin zafi. Ambaliyar ruwa ta bi ta kansu; Teku mai zurfi ya yi ruri. Ya yi tsalle da raƙuman ruwansa.11Rana da wata suka tsaya cik can sama wurarensu masu nisa suka gudu daga hasken kibiyoyinka, daga kuma hasken walƙiyar sheƙin mashinka.12Ka tattaka duniya da zafin fushi. A cikin fushi ka sussuke al'ummai.13Ka fita domin ceton mutanenka, domin ceton zaɓaɓɓenka. Ka rugurguza kan gidan mai mugunta domin a kware shi daga ƙasa har zuwa wuyansa. Selah.14Da kibiyoyinsa ka soke kan mayaƙansa tun da sun taho kamar hadari domin su watsar da mu, marmarinsu kamar masu lanƙwame matalauta a ɓoyayyen wuri ne.15Ka yi tafiya zuwa ƙetaren teku da dawakanka, ka kuma tattara manyan ruwaye.16Na ji, kuma can cikin gaɓoɓina na yi rawar jiki! Da jin ƙarar leɓunana sun girgiza. Ruɓewa ta shigo cikin ƙasusuwana, a cikina ina rawar jiki yayin da nake jira shiru domin ranar ƙunci da zata zo a kan mutanen da suka mamayemu.17Koda itacen ɓaure bai yi toho ba kuma inabi bai ba da 'ya'ya ba; kuma itacen zaitun bai ba da amfani mai kyau ba kuma gonaki basu ba da abinci ba; koda a ce garke ya tsinke babu shanu a maɗauri, ga abin da zan yi.18Duk da haka, zan yi farinciki cikin Yahweh. Zan cika da murna saboda Allahn cetona.19Ubangiji Yahweh shi ne ƙarfina ya kuma maida sawayena kamar na barewa. Yana sa in tafi gaba bisa wurarena na ɗaukaka. - Ga shugaban mawaƙa, bisa kayan kaɗe-kaɗena masu tsarkiya.
wannan na nufin 1) na ji mutane na magane game da abinda kun yi ko kuma 2) na ji abinda kun faɗi.
"bada numfashi wa aikinka" ko kuma "yi abinda ka yi shi a da kuma"
"ka bayana aikinka"
A cikin littafi mai tsarki, kalmar "Allah" na nufin mahalicin sama da kasa. Allah ya bayana kanshi a matsayin Allah Uba, Allah Ɗa da kuma Allah Ruhu Mai Tsarki. Sunansa kuwa shine Yahweh. Allah na nan tun filazar, kuma zai rahu harabada abadin. Shine kaɗai Allah na gaskiya a dukan duniya da sama. Shi cikakkake ne, hikimarsa babu matuka, mai tsarki, mara aibi, mai adalci, mai jinkai, da kuma, mai kauna. Shi mai cika alƙawari ne. Ya hallaci mutane domin su yi masa sujada. kuma shi kaɗai ne za'a yi masa sujada. Allah ya bayana sunansa da cewa shine Yawe, ma'ana kuwa shine, "nine". Maganar Allah kuwa ta koyar mana game da allolin da basu da rai, waɗanda mutane ke bauta a cikin wautanci.
A cikin littafi mai tsarki, sau dayawa wannan kalmar na nufin Allah ne. A Tsohon Alƙawali, wannan lakabi na nufin mai tsarki na Isra'ila. A Sabon Alƙawali, akan kira Yesu da sunannan, mai tsarkinnan wani lokaci ana amfani da lakabinnan "mai tsarkinnan" don a yi magana akan maleku.
Habakuk ya cigaba da bayana ruyar da Yahweh ya nuna masa
"Duwatsun da ke nan tun fil'azar ... tutdan da zasu dawama har matukan zamani. Idan yaren ku ba shi da banbancin sunan dutse da na tudu, sai ka mai da su ab ɗaya.
domin yi wa Allah sujada. "sun faɗi rub da ciki"
Habakuk ya cigaba da bayyana ruyar da Yahweh ya nuna masa
an kwatanta tsoron da ya kama Midiyawa da Kushiyawa da bukkan da iska ke busa rumfarta.
wannan sunan wata kabila ce.
Kamar yadda mayaki ke hawan karusa domin yaki, haka kuma Yahweh ke zuwa domin fansar jama'arsa.
wannan kalma na nufin a "saya a yi binbini" ko kuma "a yi sowa ta yabo"
A lokacin da Allah ya raɓa duniya, duwatsu su yi motsi sai kace za su iya yin tawaye wa Allah su zauna a inda suka zaɓa.
wannan na nufin karar rakumin ruwa a bisa teku.
wannan na nufin ruwar ta karu.
Habakuk ya cigaba da magana game da ruyar da Yahweh ya nuna masa.
dalilin maganarnan shine, hasken kibiyar Yawe na da yawa sosai.
wato fushi a kan abinda bashi da kyau
wannan na iya nufin "kiristinku" amma anan na nufin "jama'arku ne"
"Kun hallaka shugaban mugaye"
an kwatanta yadda Kaldiyawa suka zo da iko da kuma garaje domin su hallaka Isarila da hadarin da ke haɗuwa farab ɗaya.
Habakuk ya kwatanta tsoronsa yayin da yake tunanin yadda Yahweh zai hukunta Kaldiyawa.
Wannan na kwatancin tsoron da ta zo ta dalilin tunanin abinda zasu faru nan gaba. Habakuk ya yi amfani da gababuwansa don ya kwatanta yadda dukan jikinsa ke da matsala.
babu abinci. waɗannan suna hanyoyin samun abinci a kasar Isra'ila
Habakuk ya yaɓi Yahweh
dukansu biyu na nufin abu ɗaya wato a cika da farinciki. idan yarenka na da wata lakamin suna da ke kwatanta farin ciki bayan nasara a wurin yaki sai a yi amfani da shi.
kafafu kamar na gaggafa na iya ba wa Habakuk karfin hawan saunuka masu tsawo. Wuraren da masifa ba zata iya samu shi ba. Yana nufin, Allah na ban zarafi don in sami mafaka mai kyau.
1Wannan maganar Yahweh ce da ta zo ga Zafaniya ɗan Kushi ɗan Gedaliya ɗan Amariya ɗan Hezekiya, a kwanakin Yosiya ɗan Amon, sarkin Yahuda.2"Zan hallakar da kome da kome daga doron duniya - wannan furcin Yahweh ne.3Zan hallakar da mutum da dabba; Zan hallakar da tsuntsayen sammai da kuma kifayen teku, rusasssun wurare tare da miyagu. Domin zan datse mutum daga sararin duniya - wannan furcin Yahweh ne.4Zan miƙa hannuna kan Yahuda da dukkan mazaunan Yerusalem. Zan datse kowanne ragowar Ba'al daga wannan wurin da kuma sunayen masu bautar gumaka daga cikin firistoci,5mutanen da a saman gidaje suke bautawa hallitun sammai, da mutanen da ke sujada da rantsuwa ga Yahweh amma kuma suna rantsuwa ta wurin sarkinsu.6Zan kuma datse waɗanda suka juye baya daga bin Yahweh, waɗanda basu neman Yahweh basu kuma neman bishewarsa."7Ku yi shiru a gaban Ubangiji Yahweh! Gama ranar Yahweh ta kusato; Yahweh ya shirya hadaya ya kuma keɓe baƙinsa.8"Zai zama kuma a ranar hadayar Yahweh, zan hori hakimai da 'ya'yan sarakuna, da duk wanda ke sanye da baƙin tufafi.9A ranan nan zan hukunta masu tsallake dankarin ƙofa, masu cika gidan shugabansu da ta'addanci da yaudara.10Haka zai zama a ranar nan - wannan furcin Yahweh ne - lallai za a ji kukan baƙinciki daga Kofar Kifi, da ƙarar kuka daga Gundumar Biyu, da gagarumar ƙarar farfashewa daga tuddai.11Kuyi kuka da ƙarfi, ku mazaunan Gundumar Kasuwa, gama za a rugurguje dukkan fatake; za a datse dukkan masu awon azurfa.12Zai zama a gabatowar lokacin nan ne zan binciki Yerusalem da fitilu in kuma hukunta mutanen da suka kafu a kan ruwan inabinsu suka ce a zuciyarsu, 'Yahweh ba zai yi kome ba, ko nagari ko mugu.'13Dukiyarsu zata zama ganima, kuma gidajensu za a maida su kufai da aka yi watsi da shi! Zasu gina gidaje amma baza su zauna a cikinsu ba, zasu dasa gargunan inabi amma baza su sha ruwansu ba.14Babbar ranar Yahweh ta yi kusa, tayi kuma kurkusa da sauri! Ƙarar ranar Yahweh zata zama kukan mayaƙi na ɓacin rai!15Ranar nan zata zama ranar tsananin fushi, ranar damuwa da baƙinciki, ranar baƙin hadari da rushewa, ranar duhu da baƙin ƙunci, ranar giza-gizai da baƙin duhu.16Zata zama ranar hura kakaoki da ƙararrawa gãba da ƙayatattun birane masu manya manyan wuraren ɓuya da ganuwoyi.17Gama zan kawo ƙunci ga mutane, saboda suyi tafiya kamar makafin mutane tunda sun yiwa Yahweh zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura, a kuma cire kayan cikinsu kamar kashin dabba.18A ranar hasalar Yahweh zinariyarsu ko azurfarsu ba zasu iya kuɓutar dasu ba. A cikin wutar kishinsa dukkan duniya zata hallaka, gama zai kawo cikakken mummunan ƙarshen dukkan mazaunan duniya."
"maganar da Yahweh, Allah, ya fada"
Wannan ne sunan Allah, wanda ya bayyana wa jama'arsa a Tsohon Alƙawari. Duba shafin fassaraKalma game da yadda za ka fassara wannan.
Wadannan kalmomin, Yahweh ne ya zuguguta su domin ya bayyana fushinsa a kan zunubin mutanen.
Ana maganar hallakarwa kamar datse wani abu ne daga jikin wurin da yake.
Mai yiwuwa "Milkom" wani suna ne na gunkin nan "Molek".
Wannan maganar tana nuna babban shirin Allah da kuma yadda yake morar abokan gaban jama'arsa domin ya cimma manufarsa.
wannan furcin yana nufin cewa Isra'ilawa sun sanya tufafin da suka yi kama da na baki don su nuna sha'awar al'adunsu, su kuma yi sujada ga allolin al'ummai.
"A ranar Yahweh"
wannan maganar nuni ce ga mutanen da suke bautar wani allah da ake kira Dagan. A.T: "duk wadanda suke bautar Dagan"
AT: "abin da Yahweh ya fada" ko "abin da Yahweh ya rantse"
Kofar Kifi tana daya daga cikin kofofin da ke a ganuwar birnin.
AT: "Makoki kwarai daga Lardi na Biyu". Lardi na Biyu wani sabon bangare ne na Yerusalem.
Wannan yana nufin tuddan da suka kewaye Yerusalem. AT: "daga tudan da ke kewaye da Yerusalem".
AT: "masu saye da sayar da kayayyaki, 'yan kasuwa, za a kashe su".
Babu wanda zai iya boyewa daga wurin Allah.
Suna jin sun tsira daga masifa.
Suna magana da tabbaci.
Maimaicin kalmar "gabato", tare da furcin "gabatowa da sauri" suna jaddada cewa ranar da Yahweh zai hukunta mutanen tana dab da abkuwa. AT: "tana kusa, kuma za ta iso nan ba da jimawa ba".
Wannan furcin yana jaddada yadda munin hukuncin Allah zai kasance. Kalmomin da aka mora suna tare domin nuna yanayin hallakarwa na wannan hukuncin karshe da Allah zai yi. Suna jaddada al'amarin.
Kalmomin "azaba" da "wahala" suna da ma'ana kusan daya, kuma suna jaddada tsananin wahalar mutanen. AT: "ranar da mutane za su sha mumunar azaba".
A nan, "tsawa" tana nufin hukuncin Allah. Kalmar "hallakarwa" tana bayyana munin wannan hukuncin.
Kalmomin "duhu" da "baki kirin" suna da ma'ana kusan iri daya, kuma suna jaddada tsananin duhun. Duka kalmomin suna nuni ne da lokacin masifa ko hukuncin Allah. AT: "ranar da ke cike da duhu" ko "ranar hukunci mai bantsoro".
wannan furcin yana da ma'ana iri daya da maganar da ta gabata, kuma yana jaddada ra'ayi daya. Kamar wancan furcin, "gizagizai" da "bakin duhu" suna nuni da hukuncin Allah. AT: "rana mai cike da gizagizai masu duhu da tsawa".
Kalmomin "kaho" da "kururuwar yaki" suna da ma'ana kusan iri daya a nan. Duk biyun hanyoyin kiran mayaka ne su shirya don yaki. AT: "ranar da mutane za su yi kururuwar yaki".
Wadannan kalamai biyu suna nufin wuraren tsaro na mayaka. AT: "birane masu kakkarfar garkuwa".
Wadannan kalamai uku suna nuni da kwatanci, don nuna yadda suke da kama.
Wannan yana nuni da ikon fushin Yahweh.
1Ku jero kanku tare ku taru, al'umma marar kunya -2kafin ranar aiwatar da dokokin kuma waccan ranar ta wuce kamar ƙaiƙayi, kafin zafin fushin hasalar Yahweh ta auko muku, kafin ranar hasalar Yahweh ta zo kanku.3Ku nemi Yahweh, ku mutane masu tawali'u da biyayya ga dokokinsa! ku nemi adalci Ku nemi tawali'u, ko wataƙila a yi maku kariya a ranar hasalar Yahweh.4Gama za a yashe da Gaza, kuma Ashkelon zata zama rusasshiya. Zasu kori Ashdod da rana, kuma zasu tunɓuke Ekron!5Kaiton mazaunan gaɓar teku, al'ummar Kiritiyawa! Yahweh ya yi magana gãba da ku, Kan'ana, ƙasar Filistiyawa. Zan hallakar dake har sai ba mazaunan da suka ragu.6Yankin gaɓar teku zai zama saurar makiyaya da makwantar dabbobi. Yankin gaɓar zai zama na ragowar mutanen gidan Yahuda, waɗanda zasu yi kiwon garkensu a wurin.7Da yamma mutanensu zasu kwanta a gidajen Ashkelon, gama Yahweh Allahnsu zai lura da su ya kuma mayar masu da mallakarsu.8Na ji cakunar Mowab da wulaƙancin mutanen Amon sa'ad da suke cakunar mutanena suna ci masu kan iyaka.9Don haka na rantse da kaina - wannan ne furcin Yahweh mai runduna, Allah na Isra'ila, - Mowab zai zama kamar Saduma, mutanen Amon kuma kamar Gomora; wurin ciyayi masu dafi da ramin gishiri da aka yi watsi da shi har abada. Amma ragowar mutanena zasu washe su, ragowar al'ummata kuma zasu mallake su."10Wannan zai faru da Mowab da Amon saboda girman kansu, tunda suka cakuni suka kuma yi ba'a ga mutanen Yahweh mai runduna.11Sa'an nan zasu ji tsoron Yahweh, don zai cakuni dukkan allolin duniya. Kowannensu zai yi masa sujada, kowanne daga wurinsa, daga kowacce gaɓar teku.12Ku Kushiyawa kuma za a soke ku da takobina,13Hannun Allah kuma zai kawo hari ga arewa ya hallaka Asiriya, don Nineba zata zama rusasshen wurin da aka watsar, busshiya kuma kamar hamada.14Sai garkuna su kasance kwance a nan, kowacce dabba ta kowacce al'umma, mujiyar hamada da mujiya mai tsuwwa ma zasu huta a samman ginshiƙanta. Za a yi waƙoƙin kira daga tagogi; Juji zai kasance a bakin ƙofofin; sassaƙaƙƙun ginshiƙanta na sidar za a bayyana su.15Wannan ne maɗaukakin birnin da ya zauna cikin rashin tsoro, da yace a zuciyarsa," Ni ne kuma ba wanda ya kai ni." To Yaya ya zama mafi muni, wurin da dabbobin jeji ke kwance ciki. Duk wanda ya wuce ta wurinsa zai yi tsaki ya kaɗa kai.
Wadannan kalmomi biyu suna nufin abu daya. Duka biyun suna jaddada umurnin don jama'a su tattaru tare domin tuba daga zunubansu. AT: "kutattara kanku tare".
Al'ummar ba ta nadamar zunubanta.
Kaikayi shi ne bangare mara amfani a jikin hatsi, wanda ake watsarwa, haka kuwa wannan ranar za ta wuce.
Annabin ya maimaita furcin kusan ta hanya daya don ya jaddada yadda hukuncin Yahweh zai yi muni, da kuma da ya kamata mutanen su tuba da shi.
Wannan yana nufin niyyar Allah ta aiwatar da hukunci.
Da gaggawa za tumbuke mutanen, a kawar da su gaba daya daga wadannan biranen.
AT: "har sai babu kowa a wurin"
Bangaren wannan ayra ba a bayyane yake sosai ba, kuma ana fassara shi a hanyoyi da yawa a juyin zamani.
Garken tumaki wani dan yanki ne da ake kewayewa da katanga domin a ajiye tumaki tare.
yana nufin yin barci a gado
"abin da Yahweh Mai Runduna ya fada" ko "abin Yahweh Mai Runduna ya rantse"
Sa'ad da aka hallaka gine-gine, suka fadi, ginshikan da ake mora don yin ado da karfafa ginin suka tsaya a a tsaye.
Rufin katakai dogayen katakai ne da ake mora wajen daure gini ya tsaya kam.
Tsaki kara ce ta fushi. Wannan furcin yana nuna tsananin fushin mutanen a kan Nineba.
1Kaiton ki birni mai tayarwa! Birni mai ta'addanci ya ƙazantu.2Bata saurari muryar Allah ba, ko ta karɓi gyara daga Yahweh. Bata dogara ga Yahweh ba kuma ba zata kusanci Allahnta ba.3Sarakunanta zakuna ne masu ruri a tsakiyarta. Alƙalanta kyarketan yamma ne da basa barin abin yin tuƙa da safe.4Annabawanta marasa biyayya ne masu cin amana. Firistocinta sun wulaƙanta abin da ke mai tsarki kuma sun yi ta'addanci ga shari'a.5Yahweh adali ne a cikinta. Ba zai yi kuskure ba. Daga safiya zuwa safiya zai aiwatar da adalci! Ba zai ɓoyu ba cikin haske, duk da haka mutane marasa adalci basu san kunya ba.6Na hallakar da al'ummai; an lalatar da kagarorinsu. Na mai da titunansu kufai, don kar kowa ya bi kan su. An hallakar da biranensu har babu mutumin dake zaune cikinsu.7Na ce, 'Hakika zaku ji tsoro na. Ku karɓi gyara don kada a datse ku daga gidajenku ta wurin dukkan abubuwan da na shirya in yi maku.' Amma suna ƙagara su fara kowacce safiya da lalata ayyukansu.8Saboda haka ku jira ni - wannan furcin Yahweh ne. Har sai ranar da zan tashi domin ƙwace wahalallun. Gama ƙudurina shi ne in tara al'ummai, in taro masarautu, in kuma zuba masu fushina-dukkan hasalata mai zafi; domin a cikin wutar kishina za a cinye dukkan duniya.9Amma zan bada leɓuna masu tsarki ga mutanen, a kira dukkan su cikin sunan Yahweh su bauta mani suna tsaye kafaɗa da kafaɗa.10Daga ƙetaren kogin Kush masu yi mani sujada - mutanena dake warwatse - zasu kawo baye-bayen dake nawa.11A ranan nan baza ku kunyata ba game da dukkan abubuwan da kuka yi mani. Tun da a wannan lokaci zan kawar da waɗanda suka yi bikin girman kanku daga cikinku, saboda kuma baza ku ƙara yin rashin hankali ba a bisa dutsena mai tsarki.12Amma zan bar ku ƙaskantattu matalautan mutane, zaku kuma fake a cikin sunan Yahweh.13Ragowar Isra'ila kuma baza su ƙara aikata rashin adalci ba ko su faɗi ƙarairayi ko kuma a sami yaudara a bakin su ba; saboda haka zasu yi kiwo su kwanta, babu kuma wanda zaya tsoratar dasu."14Yi waƙa 'ɗiyar Sihiyona! Yi ihu, Isra'ila. Yi murna da farinciki da dukkan zuciyarki, ɗiyar Yerusalem.15Yahweh ya ɗauke hukuncinki; Ya kori maƙiyanki! Yahweh shi ne sarkin Isra'ila a tsakiyarku. Baza ki ƙara jin tsoron mugunta ba!16A ranar nan zasu cewa Yerusalem, "Kada ki ji tsoro, Sihiyona. Kada ki bari hannuwanki suyi sanyi.17Yahweh Allahnku yana tsakiyarku, mai ƙarfin nan da zai cece ku. Zai ji daɗin ku da farinciki kuma zai yi shuru a kanku cikin ƙaunarsa. Zai yi murna a kanku kuma zai yi sowa ta farinciki a kanku,18Zan tattara waɗanda ke ɓacin, waɗanda baza su iya kasancewa a zaɓaɓɓun bukukuwa ba, domin haka baza ku ƙara jin kunya dominsa ba.19Duba, Ina gab da horon masu tsananta maku. A lokacin nan, zan ƙwato guragu in tattaro waɗanda aka watsar. Zan maishe su kamar yabo, zan musanya kunyarsu zuwa sanannu a dukkan duniya.20A lokacin nan zan bi daku; a lokacin nan zan tara ku tare. Zan sa dukkan al'umman duniya su girmama su kuma yabe ku, lokacin kuka gana dawo da ku," inji Yahweh.
Jama'ar Yerusalem ba su yi biyayya da abin da Allah da annabawasa suka koya musu ba.
Mutanen ba su marmarin yin sujada ga Allah ko su yi masa biyayya.
AT: "Shugabannin Yerusalem suna da keta".
AT: "Alkawalnta mugayen mutane ne wadanda suke karbe kayayyakin da ke na wadansu". Wannan ma kamance ne.
AT: "Annabawanta marasa biyayya ne, kuma suna cin amanar mutane".
AT: "adalcinsa a bayyane yake ga kowa"
Yahweh yana bayyana irin wannan ra'ayin a wurare dabam-dabam guda biyu, don ya jaddada hallakarwa ta duka da zai yi wa birnin.
Wannan yana nufin abin da Yahweh ya rantse.
"Zan tashi don in hallaka mai laifin"
Wadannan maganganu biyu suna nufin abu guda, kuma suna jaddada cewa Yahweh zai hukunta dukkan al'ummai.
Kalmomin "hasala" da "zafin fushi" suna da ma'ana kusan daya, kuma suna jaddada tsananin fushin Yahweh. AT: "tsananin fushina".
Za a iya bayyana wannan furcin kai tsaye. AT: "domin zafin fushina zai hallaka dukkan kasar"
Ana maganar fushi a nan kamar wuta ce da za ta iya kone abu.
Wannan wata hanya ce ta cewa Allah zai sa mutanen su fadi abin da yake daidai.
Mutanen za su zama da hadinkai cikin marmarinsu na bautar Allah, kamar yadda mutane sukan hadu sa'adda suka tsaya tare, kafadunsu suna taba juna.
AT: "babu wanda zai sami harshen yaudara a cikinsu" ko "ba za su yi yaudara ba".
Yahweh yana magana a kan mutanen Isra'ila kamar su garken tumaki ne da ke kiwo da kwanciya cikin tsaro.
"Wannan yana nufin dukkan mutanen da ke a Yerusalem".
Wannan yana nufin, kada ji sanyin jiki ko kasawa yadda za ki ji idan hannuwanki sun raunana.
Kamar wannan yana nufin tumakin da guragun tumaki da suke korarrau, wanda alama ce ta Isra'ilawan da suka sha wahala a kasar bauta.
Wannan yana nufin mutane ko dabbobin da ba za su iya tafiya ba.
Cikakkiyar ma'anar a nan ita ce "Zan sa su zama abin yabo", wato, "Zan sa wadansu su yabe su".
Wadannan maganganu biyu suna nufin kusan abu guda, kuma suna nufin cewa Yahweh zai dawo da jama'ar da ke bauta kasarsu. AT: "A wancan lokacin, zan tattara ku tare, in komo da ku gida".
1A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyos, a wata na shida, a rana ta fari ga watan, maganar Yahweh ta zo ta hannun annabi Haggai ga gwamnan Yahuda, wato Zerubabel ɗan Shiltiyel, da kuma babban firist Yoshuwa ɗan Yehozadak cewa2"Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Waɗannan mutanen na cewa, 'lokaci bai yi ba da za mu zo ko mu gina wa Yahweh gida.'"3Sai maganar Yahweh ta zo ta hannun annabi Haggai, cewa,4"Lokaci ya yi da za ku zauna a shiryayyun gidajenku, amma kuma wannan gidan na kwance a lalace?5To Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Ku lura da hanyoyinku!6Kun shuka iri da yawa amma kun girbi kaɗan, kun ci amma bai ishe ku ba, kun sha amma ba ku ƙoshi ba. Ku na sa tufafi amma ba ku ji ɗumi ba, kuma mai ƙarbar albashi yana ƙarba kawai ya sa shi cikin jakka mai hudoji!7Yahweh mai runduna ya faɗi haka: "Ku lura da hanyoyinku!8Ku hau bisa tudu, ku kawo katako ku gina mani gida, ta haka zan ji daɗi, kuma za a ɗaukaka ni!- in ji Yahweh."9"Kun nema da yawa amma duba kun kawo gida kaɗan, don na hure shi! Don me?" Yahweh mai runduna ya furta. "Saboda gidana na kwance a lalace, alhali kowanne ɗayan ku na aiki a nasa gidan.10Saboda haka sammai sun riƙe raɓa, ƙasa kuma ta riƙe amfaninta,11Ni na kawo ƒãri ga ƙasar kuma ga tuddai, ga ƙwayar hatsi, kuma ga sabon ruwan inabi, ga mai kuma ga girbin ƙasa, ga mutane da kuma ga dabbobi, kuma ga dukkan ayyukan hannuwanku!"12Sai Zarubabel ɗan Shaltiyel da babban firist Yoshuwa ɗan Yehozadak, tare da dukkan sauran mutanen, suka yi biyayya da muryar Yahweh Allahnsu da kuma kalmomin annabi Haggai, saboda Yahweh Allahnsu ya aiko shi kuma mutanen sun ji tsoron fuskar Yahweh.13Sai Haggai, mai kawo saƙon Yahweh, ya faɗi saƙon Yahweh zuwa ga mutanen ya ce, "Ina tare da ku! - wannan furcin Yahweh ne!"14Yahweh ya zuga ruhun gwamnan Yahuda, wato Zerubabel ɗan Shiltiyel, da kuma ruhun babban firist Yoshuwa ɗan Yehozadak, da kuma ruhun dukkan sauran mutanen, domin haka suka je su ka yi aiki a gidan Yahweh mai runduna, Allahnsu15a rana ta ashirin da hudu ta watan shida, a shekara ta biyu ta mulkin sarki Dariyos.
"shekara ta biyu na mulkin sarki Dariyos"
Dukansu sunayen mutane ne.
"a rana ta farko ga wat na shida." wannan shine wata na shidda ta watannin Yahudawa. Rana ta fari na kusa da tsakiyar wata na takwas ta watannin nasara. (Dubi: da translate _names)
"Yahweh ya yi maganarsa"
Wannan shine sunan Allah da ya bayyana wa mutanensa a Tsohon Alƙawari. Dubi shafin juyin kalma game da Yahweh da kuma yadda za'a juya shi.
Haggai shine ɗan tsako.
"Yahweh yayi maganarsa." Dubi yadda ka juya shi a 1:1.
kalmar "gida" a nan na nufin haikalin Allah ne.
A nan ba a ce, ko kuma a nufa da cewa buguwa abu ne mai kyau ba. Sai dai ana nufin babu isasshen ruwan inabi da zai kosar da mutane balle ya bugar.
AT: "kuɗin da kuke samu daga rabon aiki baya isa sayayyan ku."
Wannan ya nuna wani fanni ne da ake bukata domin ginan haikali.
AT: "abinda Yahweh Mai Runduna ya rigaya ya aiyatar"
A: "sarari"
AT: "hana ruwan sama"
rashin ruwa da ke hana amfani girma, yana kuma busar da ruwa da ake bukata domin shayar da dabbobi da kuma mutane a wannan haraɓa.
ruwan inabi shine yayan gireps, mai kuma shine man zaitun.
AT: "dukkan kokarin da ka rigaya ka yi!" kuma UDB
Dubi 1:1
AT: "abinda Yahweh ya aiyatar" ko kuma "abinda Yahweh ya faɗa."
kalmar saura na nufin jama'a da suke da rai bayan da suka dawo daga kasar bauta a Babila suka fara sake gina ganuwar Yerusalem.
rana ta hudu ga watan shida - wato kwana ashirin da uku kenan bayan da ya karɓi ruyan. Wannan shine wata na shidda bisa ga watannin Ibraniyawa. Rana ta ashirin da fudu na kusa da tsakiyar watan satumba bisa ga watannin nasara.
"shekara ta biyu ta mulkin sarki Dariyos"
1A wata na bakwai ranar ashirin da ɗaya a watan, maganar Yahweh ta zo ta hannun annabi Haggai, cewa,2"Yi magana da gwamnan Yahuda, Zerubabel ɗan Shiltiyel, da babban firist Yoshuwa ɗan Yehozadak, da dukkan mutane da aka rage. Ka ce,3"Wa ya rage a cikinku wanda ya ga wannan gida da darajarsa ta dã? Ya ya ku ka ganshi a yanzu? Shin kamar ba kome ya ke a idanunku ba?4Yanzu, sai ka yi ƙarfin hali, Zerubabel! - wannan furcin Yahweh ne, kai ma Yoshuwa ɗan Yehozadak babban firist sai ku yi ƙarfin hali, dukkan mutanen cikin ƙasar! - wannan furcin Yahweh ne, kuma ku yi aiki, domin ina tare da ku! - wannan furcin Yahweh mai runduna ne.5Wannan shi ne alƙawarin da na yi da ku sa'ad da kuka fito daga ƙasar Masar, kuma Ruhuna na tare da ku. Kada ku ji tsoro!6Domin Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: Ba da jimawa ba zan girgiza sammai da ƙasa, da teku da duk abin da ke a busarshiyar ƙasa!7Zan kuma girgiza kowacce al'umma, kuma kowacce al'umma za ta kawo abubuwa ma su daraja a gare ni, kuma zan cika wannan gidan da ɗaukaka, in ji Yahweh mai runduna.8Azurfa da zinariya nawa ne! - wannan furcin Yahweh mai runduna ne.9Ɗaukakar wannan gidan ta zama da girma a nan gaba fiye da farkonsa, inji Yahweh mai runduna, zan ba da salama ga wannan wuri! - wannan furcin Yahweh mai runduna ne."10A rana ta ashirin da hudu ga watan tara a shekara ta biyu ta Dariyos, maganar Yahweh ta zo ga annabi Haggai cewa,11"Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: A tambayi firistoci a kan shari'a, a ce,12"Idan mutum ya ɗauki nama da aka keɓe don Yahweh a rigarsa, sa'an nan ta taɓa gurasa, ko miya, ko ruwan inabi ko mai, ko kowanne irin abinci, ko wannan zai sa abin ya tsarkaka?" Firistoci suka amsa suka ce, "A'a."13Sai Haggai yace, "Idan wani wanda ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, daga cikin waɗannan, sun zama ƙazantattu? Sai firistoci suka amsa suka ce, "I sun ƙazantu.14Sai Haggai ya amsa yace, "Haka ya ke da mutane da al'umma da ke gabana! - wannan furcin Yahweh ne - haka ya ke game da dukkan abin da suke yi da hannuwansu. Da kuma abin da suke miƙawa a gare ni marar tsarki ne!15To yanzu, sai ku yi tunani a cikin lamirinku a kan abin da ya wuce har zuwa wannan rana. Kafin a ɗora dutse a kan dutse na haikalin Yahweh,16yaya ya ke? Lokacin da ku ka zo tarin da aka auna maku mudu ashirin na hatsi, sai aka iske mudu goma kaɗai; idan kuma kun zo wurin matsar ruwan inabi don a ɗebo mudu hamsin, sai aka tarar da mudu ashirin kawai.17Na aika maku da bala'i a aikin hannuwanku ta wurin darɓa da raɓa amma duk da haka ba ku komo wurina ba - wannan furcin Yahweh ne.18Lura tun daga wannan rana zuwa gaba, daga rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, tun daga ranar da aka aza harsashin ginin haikalin Yahweh. Ku lura da shi!19Akwai sauran iri a rumbun? Inabin da itacen ɓauren, da ruman, da itacen zaitun ba su bada amfani ba! Amma daga wannan rana zan albarkace ku!"20Sai maganar Yahweh ta zo a karo na biyu ga Haggai a rana ta ashirin da huɗu ga watan ya ce,21"Yi magana da gwamnan Yahuda, Zerubabel, ka ce, 'Zan girgiza sammai da ƙasa.22Zan kuma hamɓare kursiyin mulkoki in kuma lalata ƙarfin mulkokin al'ummai! Zan kuma hamɓare karusai da mahayansu; dawakai da mahayansu zasu faɗi ƙasa, kowanne saboda takobin ɗan'uwansa.23A wannan rana - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - Zan ɗauke ka, Zerubabel ɗan Shiltiyel, bawana - wannan furcin Yahweh ne. Zan mai da kai kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka!' - wannan furcin Yahweh mai runduna ne!"
Wannan shine wata na bakwai bisa ga watannin Ibraniyawa. Rana ta ashirin da ɗaya na kusa da tsakiyar watan oktoba bisa ga watannin nasara.
"Yahweh ya furta maganarsa." Dubi yadda ka juya shi a 1:1.
Dubi: 1:1
"Hakika ka ɗau ra'ayin ba shi da amfani ko kaɗan."
"Daga yanzu har gaba, ka karfafa,"
babbar tashin hankali.
maganar nan "azurfa da zinriya" na nufin kayayyakin da aka kawo a haikali.
Wannan shine wata ta tara bisa ga watannin Ibraniyawa. Rana ta ashirin da hudu na kusa da tsakiyar watan disamba bisa ga watannin nasara
"a cikin shekara ta biyu na mulkin Dariyos"
"Wannan shine gaskiya game da jama'ar Isra'ila" ko kuma "wannan kaidar yayi daidai da jama'ar Isra'ila"
ba'a san takamemen yaya mudu yake a da ba. .
ba'a san takamammen yadda mudu yake a da aba. .
"na la'anta zufarka da kuma dukan hatsinka."
Dubi yadda ka juya shi a cikin 2:10.
Amsar da yakamata shine "babu". wannan irin tambaya na kai ga bayyan abin da mai karatu ya rigaya ya sani.
Waɗannan suna bishiyoyin bada yaya da ke cikin kasar.
waɗannan sunayen mutane ne. (Dubi: 1:1)
Yahweh zai kawo rikicewa a duniyar su.
"dukkan duniya."
gomnatoci zasu wase cikin hargisi
AT:"gomnatin da sarki ke mulki"
AT: "takobin da ke hannun mayaki."
Dubi: 1:1
1A cikin wata na takwas na shekara ta biyu na mulkin Dariyos maganar Yahweh ta zo ga Zakariya ɗan Berekaya ɗan Iddo, annabi, yana cewa,2"Yahweh ya ji haushin ubanninku ƙwarai!3Ka faɗi masu, 'Yahweh mai runduna ya faɗi haka: ku juyo gare ni! - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - ni ma zan dawo gare ku, Yahweh mai runduna ya faɗa.4Kada ku zama kamar ubanninku waɗanda Annabawa suka yi wa shela a lokatan baya, suna cewa, "Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Ku juyo daga miyagun hanyoyinku da ayyukanku na mugunta!" Amma basu ji ba ko kuma su saurare ni - wannan ne furcin Yahweh.'5Ubanninku, ina suke? Ina Annabawan, suna nan ne har abada?6Amma maganganuna da dokokina da na umarci bayina Annabawa, ba sun zarce ubanninku ba? Sai suka tuba suka ce, 'Kamar yadda Yahweh mai runduna ya shirya ya yi mana abin da ya yi wa hanyoyinmu da ayyukanmu dai-dai, hakanan ya yi da mu.'"7A cikin rana ta ashirin da huɗu na watan sha ɗaya, wanda shi ne watan Shibat, cikin shekara ta biyu na mulkin Dariyos, maganar Yahweh tazo wurin Annabi Zakariya ɗan Berekaya ɗan Iddo, cewa,8"Da dare na gani, na duba kuma! ga mutum na sukuwa bisa jan doki, yana tsakiyar itatuwan cizaƙi dake cikin kwari; bayan shi kuma akwai dawakai da ja da jaja-jaja-ruwan ƙasa-ƙasa da kuma farare."9Na ce, "Ubangiji mene ne waɗannan?" Sai mala'ikan da ke magana da ni yace mani, "zan nuna maka ko mene ne waɗannan."10Sai mutumin dake tsaye tsakiyar itatuwan cizaƙi ya amsa yace, "Waɗannan su ne Yahweh ya aika su yi yawo cikin duniya duka."11Suna ba da amsa ga mala'ikan Yahweh wanda ke tsaye a tsakiyar itatuwan cizaƙi; suna ce masa, "Muna ta yawatawa cikin duniya dukka; duba, dukkan duniya na zaune tsit kuma cikin hutawa."12Sai mala'ikan Yahweh ya amsa yace, "Yahweh mai runduna, har yaushe ne ba za ka nuna tausayi ga Yerusalem ba da kuma biranen Yahuda da suka sha wahalar zafin fushi shekarun nan saba'in?"13Yahweh ya amsa wa mala'ikan da ya yi magana da shi, da kalmomi masu daɗi, kalmomin ta'aziya.14Sai mala'ikan dake magana da ni yace mani, "Ka yi kira ka ce, 'Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Ina kishi game da Yerusalem da Sihiyona da babban kishi!15Ina jin haushi ƙwarai game da al'umman dake zaune cikin hutu. Yayin da haushina kaɗan ne game da su, sai suka maida bala'in ya zama da tsanani.16Saboda haka Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: Na komo ga Yerusalem tare da jinkai. Za a sake gina gidana cikinta - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - kuma za a ja layin gwaji bisa Yerusalem!'17Ka sake kira, kuma, ka ce, 'Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Biranena zasu sake malala da nagarta, Yahweh kuma zai sake yi wa Sihiyona ta'aziya, zai kuma sake zaɓen Yerusalem.'"18Sai na ɗaga idanuna na ga ƙahonni huɗu!19Sai na yi magana da mala'ikan dake magana da ni, "Mene ne waɗannan?" Ya amsa mani, "Waɗannan ne ƙahonnin da suka warwatsa Yahuda, da Isra'ila, da Yerusalem."20Sai Yahweh ya nuna mani masassaƙa huɗu.21Na ce, "Me waɗannan mutanen suka zo yi?" Ya amsa, yace, "Waɗannan ne ƙahonnin da suka warwatsa Yahuda har ba mai iya ɗaga kansa. Amma waɗannan mutane sun zo ne su kore su, su kakkarya ƙahonnin al'ummai waɗanda suka ɗaga ƙahon tsayayya da ƙasar Yahuda domin watsar da ita."
Wannan ne wata na takwas a kalandar Ibraniyawa. Yana a wajejen karshen Oktoba da kuma farkon watan Nuwamba a kalantar kasashen Yamma.
"shekara ta biyu bayan Dariyos ya zama sarki"
"Yahweh ya fadi maganarsa"
Wannan ne sunan Allah, wanda ya bayyana wa jama'arsa a Tsohon Alƙawari. Duba shafin fassara Kalma a kan Yahweh game da yadda za ka fassara wannan.
Wadannan sunayen maza ne
"fushi kwarai da kakanninku"
Ana mora kalmar "komo" don nuni da wani sauyi. Yahweh yana fada wa jama'ar Isra'ila cewa su canza daga rashin yi masa biyayya zuwa yi masa biyayya.
Akan fassara wannan zuwa "Yahweh ya e" a UDB. Za ka iya fassara wannan bayanin a duk hanyar da ka ga ta fi dacewa a yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a cikin Zakariya.
Ta wurin cewa zai komo wurin jama'ar Isra'ila, Yahweh yana cewa al'amuran alheri za su faru domin yana taimakonsu. AT: "zan albarkace ku".
Duk wadannan maganganu biyu suna nufin cewa jama'ar Isra'ila sun ki su yi biyayya da umurnan Yahweh. AT: "Amma sun ki su saurari umurnaina".
Akan fassara wannan furcin zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara wannan bayanin a hanyar da fi dacewa da yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
An yi wadannan tambayoyi biyun don nuna gaskiyar cewa mutane suna mutuwa. AT: "Ubanninku sun mutu. Annabawan ma za su mutu".
An mori wannan tambayar don nuna wa jama'ar Isra'ila cewa, komai da Allah ya fada wa annabawansa su gargadi kakanninsu a kai, ya faru.
Duka wadannan biyun suna nufin abin da Allah ya fada wa annabawan.
Yahweh yana magana game da anabce-anabcensa kamar suna gudu ne don su shawo gaban kakannin jama'ar Isra'ila. Kalmar "tabbata a kan" tana nufin kurewa.
"halayyaramu da al'amuranmu"
Shebat ne watan goma sha daya a kalandar Ibraniyawa. Rana ta ashirin da hudu tana kusa da tsakiyar watan Febuari a kalandar Turawa.
"Yahweh ya fadi maganarsa". Duba yadda ka fassara wannan a 1:1.
wani irin karamin itace ne mai furenni masu kyaun launi
Kalmomin "wadannan" da "suka" suna nufin dawakin da ke cikin itatuwan ci-zaki.
ma'ana tana iya zama: 1) "suna tsaron dukkan duniya", ko 2) "suna yawo ko'ina a duniya".
Duba yadda ka fassara wannan a 1:7.
AT: "dukkan mutanen duniya suna zaman salama".
Wadannan kalamai biyu suna nuni da hutu ba tare da damuwa a kan wani abu ba.
Ma'ana tana iya zama: 1) "kana fushi da" (UDB), ko 2) "an ci mutunci"
Wadannan maganganun suna bayyana kalmomin da suke na alheri da ta'azantarwa. AT: "ta'azantar da ni".
AT: "Ina fushi kwarai da al'ummai da suke jin dadin zaman lafiya da tsaro".
AT: "na yi dan fushi ne kawai da mutanen Yahuda" (UDB)
Komowa Yerusalem yana nufin sake kula da jama'ar Isra'ila, kamar komowar sarki don ya fid da jama'arsa daga masifa.
AT: "Za a gina haikalina a cikin Yerusalem"
Akan fassara wannan furcin zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara wannan bayanin a hanyar da ta fi dacewa a yarenka. An mori wannan furci sau da yawa a Zakariya.
AT: "Za a yi nazarin awon Yerusalem kamin a sake gina ta"
Yahweh yana maganar abubuwan alherin da zai yi wa jama'ar Yerusalem kamar ruwa da zai iya cika biranen har ya malalo ta ganuwar. AT: "Biranen Isra'ila za su sake samun wadata"
AT: "Yahweh zai karfafa jama'ar Isra'ila"
Zakariya ya ci gaba da bayyana wahayinsa.
Wannan furcin yana nufin juya kanka don kallon sama.
Wadannan kahonnin suna wakiltar mayakan da suka kawo hari kan jama'ar Isra'ila. AT: "Wadannan kahonnin suna wakiltar al'ummai" (UDB).
Yahweh ya ci da bayyana wa Zakariya wahayinsa.
Masu wannan aikin suna kera abubuwa daga karfe. Ana misali da su wajen nuni da takuban mayaka.
Duba bayani a 1:18.
Wannan furcin yana bayyana wani wanda yake ya tsorata kwarai, ba zai iya kallon abin da ke tsorata shi ba. A.T: "babu mutumin da zai sami karfin hali"
"kori wadannan al'ummai"
"su yi nasara kan mayakan"
Wannan yana nufin busa kaho don ba da umurni ga mayaka.
1Daga nan na ɗaga idanuna sai na ga mutum da ma'auni a hannunsa.2Na ce, "Ina zaka?" Sai ya ce mani, "Domin in auna Yerusalem, a tantance faɗinta da tsawonta."3Sai mala'ikan da yake magana da ni ya yi tafiyar sa sai wa ni mala'ika kuma ya tafi domin ya same shi.4Mala'ikan na biyu yace masa, "Yi gudu ka yi magana da saurayin can; ka ce, 'Yerusalem zata zauna a buɗaɗɗiyar ƙasa saboda yawan mutane da dabbobi dake cikinta.5Gama ni - wannan furcin Yahweh ne - zan zama katangar wuta kewaye da ita, kuma zan zama ɗaukakar dake cikinta.6Tashi! Tashi! Ku gudu daga ƙasar arewa - wannan furcin Yahweh ne - gama na warwatsa ku kamar kusurwoyin iska huɗu a sasarin sama! - wannan furcin Yahweh ne.7Tashi! Ku tsere zuwa Sihiyona, ku da kuke zaune tare da ɗiyar Babila!'"8Gama bayan da Yahweh mai runduna ya darajantani ya kuma aike ni ga al'umman nan da suka washe ku - gama duk wanda ya taɓa ku, ya taɓa ƙwayar idon Allah! - bayan da Yahweh ya yi wannan, sai ya ce,9"Ni da kaina zan girgiza hannuna a bisansu, kuma za a washe su domin bayinsu. "Daga nan zaku sani Yahweh mai runduna ne ya aiko ni.10"Ki raira waƙa domin farinciki, ke ɗiyar Sihiyona, gama ni da kaina ina gaf da zuwa in kafa sansani a cikinki! - wannan ne furcin Yahweh."11Daga nan manyan al'ummai zasu haɗu da juna zuwa ga Yahweh a wannan rana. Ya faɗi, "Daga nan zaku zama mutanena; kuma zan kafa sansani a cikinku," daga nan kuma zaku sani Yahweh mai runduna ya aiko ni zuwa gare ku.12Gama Yahweh zai gãji Yahuda a matsayin mai 'yancin gãdonta cikin ƙasa mai tsarki kuma zaya sake zaɓen Yerusalem domin kansa.13Ku yi tsit, dukkanku masu rai, a gaban Yahweh, domin an zugo shi daga wurinsa mai tsarki!
Zakariya ya cigaba da bayyana wahayinsa.
AT: "Na duba sama"
Wata igiya mai wani tsawo, wanda ake mora wajen awon manyan abubuwa.
"Sai mutumin da ke rike da igiyar awon ya ce mini"
Wannan mala'ikan sabo ne, wanda ba a gani ba tukuna, sabda haka dole a gabatar da shi a matsayin sabon fitowa a bayanin. AT: "sai wani sabon mala'ika ya fita ya same shi"
"Mala'ika na biyun ya fada wa mala'ikan da ya yi magana da Zakariya 'Ka yi sauri' ka fada wa mai rike da igiyar awon"
Wannan yana nufin cewa ba za a kewaye Yerusalem da ganuwa ba.
Yahweh yana cewa zai kare Yerusalem, kuma yana kwatanta kariyarsa da ganuwar wuta.
Akan fassara wannan furcin zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Zakariya fassara wannan bayanin a hanyar da ta fi dacewa a yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
An maimaita wadannan kalmomin biyu, kuma suna nuna gaggawan sakon da ke biye. An more ta sau biyu domin sakon yana da matukar muhimmanci
Wannan yana nufin Babila.
Wannan yana nufin cewa jama'ar Isra'ila suna nesa da juna. Iskoki hudu suna nufin bangarori dabam-dabam na duniya
Wannan yana nufin babban birnin Babila
Zakariya yana fadin yadda Yahweh yake aikansa don ya shar'anta al'ummai da suka washe Yerusalem.
"sace kayayyaki daga Yerusalem bayan an kai mata hari"
Kalmar "taba" tana nufin irin tabin da ke cutarwa. AT: "gama duk wanda ya cutar da ku"
Kwayar ido tana nufin bangare da yake baki a ido, wanda ke sa mutum ya iya gani. Wannan muhimmin bangare ne, mai tasiri a jiki. An mori wannan furcin don bayyana cewa Yerusalem tana da matukar muhimmanci ga Allah, kuma aba ce da dole ya kare .
Wannan alama ce da ke nuna cewa Allah ya shirya hallaka wani abu. AT: "alamar cewa za a hallaka su"
An riga an hallaka biranensu, an bar su a bude domin mutanen su saci duk abin da suke so.
Wannan wani suna ne na Yerusalem, wanda ke nuni da birnin kamar diyar birnin samaniya ta Sihiyona
Kafa sansani da zama a ciki
AT: "al'ummai za su yi wa Yahweh biyayya"
"a wannan lokacin"
AT: "Yahweh zai maida Yahuza wurin zamansa a kasa mai tsarki"
Yahweh yana maganar dukkan halittu masu rai ta wurin kiransu jiki. Jiki abu da kowace halitta mai rai ke da ita.
Wannan furcin yana magana kan yadda aka sa Yahweh ya dauki mataki a kan duniya.
ya farka ko ya kara zama a fadake
1Sai Yahweh ya nuna mani Yoshuwa babban firist a tsaye a gaban mala'ikan Yahweh ga kuma Shaiɗan a tsaye a hannun damansa domin ya zarge shi da zunubi.2Mala'ikan Yahweh yace da Shaiɗan, "Bari Yahweh ya tsauta ma, Shaiɗan; bari Yahweh, wanda ya zaɓi Yerusalem, ya tsauta maka! Wannan ba reshe ba ne da aka ciro daga wuta?"3Yoshuwa dai na sanye da ƙazantattun tufafi yayin da yake tsaye a gaban mala'ikan.4Sai mala'ikan ya yi magana yace da waɗanda ke tsaye a gabansa, "Ku tuɓe ƙazantattun tufafin daga jikinsa." Sai yace da Yoshuwa, "Duba! na sa laifuffukanka su kawu daga gare ka kuma zan sanya maka kaya masu tsafta."5Sai yace, "Bari a sa rawani mai tsafta a bisa kansa!" Sai suka sa rawani mai tsafta a bisa kan Yoshuwa kuma suka sanya masa tufafi masu tsafta yayin da mala'ikan Yahweh ke tsaye tare dasu.6Daga nan sai mala'ikan Yahweh ya yi umarni mai juyayi ga Yoshuwa yace,7"Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: Idan za ka yi tafiya cikin hanyoyina, ka kuma kiyaye dokokina, to za ka yi mulkin gidana kuma ka yi tsaron harabaina, domin zan ba ka dama ka shiga ka fita a tsakiyar waɗannan dake tsayawa a gabana.8Ka saurara, Yoshuwa babban firist, kai da masu tarayya da kai dake zaune tare da kai! Domin waɗannan mutane alama ne, gama ni da kaina zan taso da bawana Reshen.9Yanzu ka duba dutsen da na sa a gaban Yoshuwa. Akwai idanu bakwai a kan wannan dutse ɗaya, kuma zan sassaƙa hatimi -wannan ne furcin Yahweh mai runduna - kuma zan cire zunubin daga wannan ƙasa a rana ɗaya.10A wannan rana - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - kowanne mutum zai gayyaci maƙwabcinsa ya zauna a gindin inabinsa da gindin itacen ɓaurensa."
Yahweh ya nuna wa Zakariya wahayin Yoshuwa babban firist
AT: "Yoshuwa kamar itacen da aka fizge daga cikin wuta ne"
Wani irin itacen ne da akan fisge shi daga wuta tun bai gama konewa ba. Wannan yana nufin Yoshuwa, wanda aka cece shi daga bauta a Babila, ya dawo Yerusalem.
A wannan wahayin, ana morar riguna masu dauda a matsayin alamar nuna halin zunubi.
A nan, riguna masu daraja alamar gaskiya ne.
wani dogon kyallen zani ne wanda ake nadewa a kai
"ya umurci Yoshuwa da matukar fadakarwa"
Tafiya a hanyoyi iri daya tana nufin aikata abubuwa iri daya.
AT: "idan kuwa ka tuna ka yi biyayya da umurnina"
"ka zama mai hakkin kula da harabobina"
Mala'ikan Yahweh ya cigaba da magana da Yoshuwa.
AT: "sauran firistocin da ke tare da kai"
Ya kamata a fassara taken "Reshe" kamar reshen itace. Yana nufin bawan Yahweh zai zo daga wurin Yahweh kamar yadda reshe yake fitowa daga itace.
Wato, bangarori bakwai
"sassaka"
kalmomin da akan rubuta a kan wani abu ko ake sassakawa a kan wani abu
Akan fassara wannan furcin zuwa "Yahweh ya fada" a UDB. Za ka iya fassara wannan bayanin a hanyar da ta fi dacewa a yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
AT: "A wannan lokacin" (UDB)
1Sai mala'ikan dake magana da ni ya juya ya farko da ni kamar mutumin dake farkarwa daga barci.2Ya ce da ni, "Me ka gani?" na ce, "Na ga mazaunin fitila da aka yi da zinariya baki ɗaya, da kwano a bisansa. Yana da fitilu bakwai a bisansa da kuma lagwanin fitilu bakwai a kan kowacce fitila.3Akwai itatuwan zaitun biyu a kowanne gefensa, ɗaya na gefen dama da kwanon ɗaya kuma na gefen hagu."4Sai na ƙara magana da mala'ikan dake magana da ni. Na ce, "Mene ne ma'anar waɗannan abubuwa ya shugabana?"5Mala'ikan dake magana da ni ya amsa yace da ni, "Baka san ma'anar waɗannan abubuwa ba?" Na ce, "A'a, ya shugabana."6Sai ya ce ma ni, "Wannan ce maganar Yahweh ga Zerubabel: Ba ta ƙarfi ba, ba ta iko ba amma ta Ruhuna, Yahweh mai runduna ya faɗa.7Kai wane ne, babban dutse? A gaban Zerubabel za ka zama sarari, zai kuma kawo dutsen dake sama tare da sowace - sowacen 'Alheri! Alheri a gare shi!'"8Maganar Yahweh tazo gare ni, cewa,9"Hannun Zerubabel ya ɗora harsashen ginin wannan gida hannunsa kuma zai kammala shi. Daga nan zaku sani Yahweh mai runduna ya aiko ni gare ku.10Wane ne ya rena ranar ƙananan abubuwa? Waɗannan mutane zasu yi farinciki kuma zasu ga dunƙulen dutsen a hannun Zerubabel. (Waɗannan fitilu bakwai idanun Yahweh ne dake dubawa ko ina cikin duniya)."11Daga nan na tambayi mala'ikan, "Mene ne waɗannan itatuwan zaitun biyu dake hagu da dama na mazaunin fitilar?"12Na sake tambayar shi kuma, "Mene ne waɗannan rassan zaitun biyu dake gefen bututun zinari biyu dake ɓulɓulo da mạn zinariya daga cikinsu?"13Sai ya ce ma ni, "Baka san ko mene ne waɗannan ba?" Na ce, "A'a, ya shugabana."14Sai ya ce, "Waɗannan 'ya'ya maza ne na sabon man zaitun dake tsaye a gaban Ubangijin dukkan duniya."
AT: "ya sa na kara zama a fadake, kamar mutumin da kak tashe shi daga barci"
bangarorin fitila da ake sa wuta
AT: "gefen hagu na kwanon"
A'a, Zakariya ya fada wa mala'ikan da ke magana da shi cewa bai gane ma'anar al'amuran da ke cikin wahayin ba
Mala'ikan da ke magana da Zakariya ya ci gaba da bayyana wahayin.
Ma'ana tana iya zama: 1) kalmomin "karfi" ko "iko" suna da ma'ana daya, kuma suna jaddada yawan karfin Zarubabel, ko 2) kalmar nan ta "karfi" tana nufin karfin yaki, sa'annan kalmar "iko" tana nufin hazikancin Zarubabel kansa. A.T: "Hakika, ba da karfinka ba" ko "Ba da karfin yaki ko naka ikon ba"
Yahweh ya yi wa dutsen nan wannan tambayar don ya nuna cewa ta wurin Ruhun Yahweh, ko dutse ma ba shi da karfin yin nasara a kan Zerubabel. AT: "Babban dutse, ko kai rarrauna ne idan an kwatanta ka da Zerubabel".
Dutsen kan kwankoli shi ne dutse na karshe da ake dorawa idan ana gina wani abu.
Mala'ikan da yake magana da Zakariya ya ci gaba da bayyana wahayin.
"Yahweh ya fadi kalmarsa". Duba yadda ka fassara wannan a 1:1.
Zerubabel ne mai kula da ginin haikalin. An kira girin "hannuwansa", duk da cewa ba lallai hannuwansa ne suka aza duwatsun ba.
Harsashi shi ne tushen gini, kuma bangaren farko a aikin gini. AT: "fara gini"
Ba a yi wannan tambayar don a sami amsa ba, amma don a fada wa mutanen kada su raina "ranar kananan abubuwa".
Wannan furcin take ne na lokacin da ake yin kananan ayyuka a kowace rana. Tare, wadannan kananan ayyukan sun gina haikalin. An kira gaba dayan lokacin ginin rana daya, duk da cewa ya dauki shekaru da yawa kamin a kammala.
wani dutse da akan hada da igiya. Ana morar wannan wajen gane ko bangon gini yana mike ko ya karkace.
Fitilu bakai din su ne alamun idanun Yahweh.
Kalmar "idanu" suna nufin Allah yana gani, domin ana amfani da idanu don gani.
"butoci biyu na zinariya"
"Ya kamata ka san ko mene ne wadannan, amma ba ka sani ba".
Hanyar waka ce ta cewa, "mutanen da aka kebe (wato, zababbu)".
Wannan furcin yana nui da bauta. AT: "bautar Ubangiji".
1Daga nan na juya na ɗaga idanuna, sai na gani, duba, ga littafi naɗaɗɗe na shawagi a sama!2Sai mala'ikan yace mani, "Me ka gani?" Na amsa, "Na ga littafi naɗaɗɗe na shawagi a sama, tsawonshi kamu ashirin fadinshi kamu goma."3Sai ya ce da ni, "Wannan ce la'anar dake yawo a fuskar dukkan ƙasar, za a datse kowanne ɓarawo bisa ga yadda ya faɗa a gefe ɗaya, dukkan wanda kuma ya yi rantsuwa da alƙawarin ƙarya za a datse shi bisa ga yadda ya faɗa a gefe ɗayan, bisa ga maganganunsu.4"Zan aika da ita - wannan shi ne furcin Yahweh mai runduna - saboda haka zata shiga gidan ɓarawo da gidan wanda ya yi rantsuwar ƙarya da sunana. Zata zauna a gidanshi ta cinye katakan da duwatsun."5Daga nan sai mala'ikan dake magana da ni ya fita ya ce mani, "Ɗaga idanunka ka ga abin dake tahowa!"6Sai na ce, "Mene ne?" Ya ce, "Wannan kwando ne dake ɗauke da garuwa dake zuwa. Wannan laifuffukansu ne cikin dukkan ƙasar."7Sai aka ɗauke murfin ƙarfen dake rufe da kwandon sai ga wata mace a cikinsa zaune!8Mala'ikan yace, "Wannan mugunta ce!" Sai ya sake jefa ta cikin kwandon, kuma ya sake rufe shi da murfin ƙarfen.9Na ɗaga idanuna sai na ga mata biyu na zuwa wurina, kuma iska na cikin fukafukansu - gama suna da fukafukai kamar fukafukan shamuwa. Suka ɗaga kwandon nan tsakanin duniya da sama.10Sai na ce da mala'ikan nan dake magana da ni, "Ina zasu kai kwandon?"11Ya ce da ni, "Zasu gina mashi haikali a ƙasar Shina, domin idan suka gama ginin haikalin, sai su ɗora kwandon a dai-dai wurinda suka shirya dominshi."
Kalmar "na" yana nufin Zakariya.
Wannan yana nufin kallon wani abu. Ya ce, "na daga idanuna" domin wannan ne bangaren jiki da mutum yake kallo da shi. AT: "duba"
Kalmai "sai" a nan yana nuna cewa Zakariya ya yi mamakin abin da ya gani.
Kamu ɗaya yana daidai da sentimita 46.
Mala'ikan ya ci gaba da magana da Zakariya.
"bisa ga abin da ke rubuce a kan littafin a gefe ɗaya"
"abin da ke rubuce a ɗaya gefen littafin"
Kalmar "kalmominsu" tana nufin abin da aka fada a rantsuwarsu. AT: "bisa ga abin da suka fada"
Kalmar "ita" tana nufin la'ana.
Akan fassara wannan furcin zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara wannan bayanin a hanyar da ta fi dacewa a yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
Wannan yana nufin iyalin mutum da dukkan mallakarsu.
"na mutumin da ya rantse"
katakon da ake gini da shi
Wannan furcin yana umurtar mutum ya yi kallo ta wurin magana game da idanunsa.
Wannan yana nufin marufi mai nauyi. Darma karfe ne mai nauyi.
A zahiri, mace ba za ta iya zama a cikin karamin kwando ba. Amma a wahayin Zakariya, ta iya zama a ciki. Sau da yawa, akan zuguguta girman abubuwa a wahayi. Kwandon da macen, duk alamu ne da ke wakiltar wadansu abubuwa.
Macen tana wakiltar mugunta. A.T: "Sunanta Mugunta ne"
Furcin nan yana bayyana yadda mata suke amfani da fukafukin mata har su tashi
Matan suna da fukafuki da suka yi kama da na shamuwa. Shamuwa babbar tsuntsu ne mai fukafuki mai fadin mita 2 zuwa 4.
An daga kwandon sama. An ce "tsakanin sama da kasa" don a jawo hankali a kansu, a nuna inda kwandon yake daga inda suke.
"Ia ne matan za su kai kwandon?"
"sa'ad da aka gama haikalin, za a ajiye kwandon a wurin da aka shirya masa"
1Sai na juya na hango karusai huɗu suna zuwa sun fito daga tsakanin duwatsu biyu; duwatsun nan biyu kuwa an yi su daga tagulla ne.2Karusa na farko dawakansa jajaye ne, karusa na biyu dawakansa baƙaƙe ne,3karusa na uku dawakansa farare ne, karusa na huɗu dawakansa dabbare - dabbaren ruwan toka ne.4Sai na amsa na ce da mala'ikan dake magana da ni, "Mene ne waɗannan, ya shugabana?"5Sai mala'ikan ya amsa yace ma ni, "Waɗannan su ne iskoki huɗu na sararin samaniya waɗanda ke fitowa daga wurin da suke tsayawa a gaban Ubangijin dukkan duniya.6Mai baƙaƙen dawakai na tafiya zuwa ƙasar arewa; fararen dawakan na tafiya zuwa ƙasar yamma; dawakai masu dabbare-dabbaren ruwan toka na tafiya zuwa ƙasar kudu."7Waɗannan dawakai masu ƙarfi suka tafi suka nemi su kewaye dukkan duniya, sai mala'ikan yace, "Ku tafi ku kewaye bisa duniya!" Sai suka tafi domin dukkan duniya.8Sai ya kira ni ya yi magana da ni ya ce, "Dubi waɗanda ke tafiya zuwa ƙasar arewa; zasu tausar da ruhuna game da ƙasar arewa."9Sai maganar Yahweh ta zo gare ni, cewa,10"Ka karɓi baiko daga 'yan gudun hijirar - daga Heldai, da Tobiya, da Yedaya - sai ka tafi dai-dai cikin wannan ranar ka kai cikin gidan Yosaya ɗan Zafaniya, wanda ya zo daga Babila.11Sai ka ɗauki azurfar da zinarin, sai ka yi rawani dasu ka ɗora bisa kan Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.12Ka yi magana da shi ka ce, 'Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: Wannan mutum, sunansa Reshe! Zai yi girma inda ya ke sa'an nan kuma ya gina haikalin Yahweh!13Shi ne wanda zai gina haikalin Yahweh sa'an nan ya ɗaga darajarsa; daga nan zai zauna ya yi mulki akan kursiyinsa. Zai zama firist a bisa kursiyinsa kuma fahimtar salama za ta kasance tsakanin su biyun.14Za a bayar da rawani ga Heldai, da Tobiya da Yedaya da Hen ɗan Zakariya a matsayin abin tunawa a cikin haikalin Yahweh.15Daga nan waɗanda ke daga nesa zasu zo su gina haikalin Yahweh, domin ku sani Yahweh mai runduna ne ya aiko ni zuwa gare ku; wannan zai faru idan da gaske kun saurari muryar Yahweh Allahnku!'"
Wannan yana nufin a dubi wani abu. AT: "duba"
AT: "duwatsu biyun tagulla ne"
Mala'ikan yana bayyana cewa karusan da dawakin alamu ne na iskoki hudu na sama.
Kalmar "iskoki" tana nufin kusurwoyi hudu: arewa, gabas, kudu, da yamma. Amma, waɗansu juyin zamani sun fassara wannan furcin Ibraniyancin da ma'anar "ruhohi hudu".
Waɗansu juyi na zamani sun fassara wannan furcin Ibraiyancin zuwa "fararen dawakan suna bin su".
"Duba bakaken dawakan"
"Yahweh ya fadi kalmarsa". Duba yadda ka fassara wanan a 1:1.
Wadannan sunayen maza ne.
AT: "a'an nan ka yi amfani da azurfa da zinariyar ka kera kambi"
Ba wannan ne mutumin da ya zama mataimakin Musa ba; wannan shi ne babban firist da ke a littafin Haggai.
A.T: "Yahweh ya fada wa mala'ikan ya yi magana da Zakariya ya ce"
Mala'ikan Yahweh ya ba da wannan suan ga sabon sarkin nan, Yoshuwa. Ka fassara wannan suna kamar yadda ka yi a 3:8.
Kalmar "girma" kalma ce mai nuna alamar reshen yana fara tohuwa. AT: "zai tohu"
Ma'ana tana iya zama: 1) "bunkasa darajar haikali", ko 2) "bunkasa darajar haikali, ya kuma sanya wa kansa darajar, kamar yadda mutum yakan sanya tufafi"
AT: "za a sami dayantaka a gurabensa na sarki da firist"
AT: "Zan saka kambi a haikalina"
Kalmar "Kambi" tana nuni da sarki a matsayin yadda sarki yake saka kambi.
Wannan furcin yana nuni da sarkin kuma a matsayin firist, kamar yadda firist yake hidima a haikali.
Duba yadda aka fassara wadannan sunayen a 6:9.
Waɗan juyi na zamani sun fassara wannan furcin zuwa "don tunawa da Hen, dan Zafaniya" ko "don tunawa da wanda yake nuna alheri, ɗan Zafaniya". Haka kuma, wadansu juyi na zamani sun fassara sunan "Hen" da ma'anar sunan "Yosiya".
Wannan yana nufin Isra'ilawan da suka rage a Babila.
Kalmar "ku" tana nufin jama'ar Isra'ila.
"ku saurara da gaske"
1Da sarki Dariyos ya yi mulki shekaru huɗu, a ranar huɗu ga watan Kisleb (wanda shi ne watan tara), maganar Yahweh ta zo ga Zakariya.2Mutanen Betel suka aika da Shareza da Regem Melek da kuma mazajensu domin su yi roƙo gaban fuskar Yahweh.3Suka yi magana da firistocin dake gidan Yahweh mai runduna da kuma annabawan; suka ce, "Ko zan yi makoki cikin watan biyar ta wurin yin azumi, kamar yadda na yi cikin shekarun nan masu yawa?"4Sai maganar Yahweh mai runduna ta zo gare ni, cewa,5"Yi magana da dukkan mutanen ƙasar da firistocin ka ce, 'Da kuka yi azumi da makoki watan biyar da watan bakwai cikin shekarun nan saba'in, da gaske ni kuka yi wa azumi?6Da kuka ci ku ka sha, ba don kanku ku ka ci kuka sha ba?7Waɗannan ba sune maganganun da Yahweh ya yi shela ba ta bakin annabawan dã, sa'ad da kuke zaune a Yerusalem da biranen kewaye cikin wadata kuma kuka yi zamanku a Negeb, da gefen tsaunukan yamma?'"8Maganar Yahweh ta zo wurin Zakariya, cewa,9"Yahweh mai runduna ya faɗi haka, 'Ku zartar da hukunci mai gaskiya, da amintaccen alƙawari, da kuma jinƙai. Bari kowanne mutum ya yi wa ɗan'uwansa haka.10Game da gwauruwa da maraya, da kuma baƙo, da matalauci-- kada ku ƙuntata masu, kada kuma wani ya shirya wani mugun abu game da ɗan'uwansa a cikin zuciyarsa.'11Amma suka ƙi maida hankali kuma suka ɗaga kafaɗunsu cikin taurinkai. Suka toshe kunnuwansu domin kada su ji.12Suka maida zukatansu taurara kamar dutse domin ka da su ji shari'a ko maganganun Yahweh mai runduna. Ya aika da saƙonnin nan ga mutanen ta wurin Ruhunsa a lokatan farko, ta bakin annabawa. Amma mutanen suka ƙi saurare, domin wannan Yahweh mai runduna ya ji haushin su ƙwarai.13Sai ya kasance da ya yi kira, basu saurara ba. Ta haka kuma," Yahweh mai runduna yace, "Zasu yi kira zuwa gare ni, amma ba zan saurare su ba.14Gama zan warwatsasu da guguwa cikin dukkan al'umman da basu taɓa gani ba, ƙasar za ta zama kufai bayansu. Gama ba wanda zai iya ratsawa ta cikin ƙasar ko ya dawo gareta tun da mutanen sun maida ƙasarsu ta farinciki zuwa watsartsiyar ƙasa."
AT: "a shekara ta hudu tun lokacin da Dariyus ya zama sarki"
"Kislev" shi ne wata na tara a kalandar Ibraniyawa. Rana ta hudu tana dab da karshen watan Nuwamba a kalandar Turawa.
"Yahweh ya fadi kalmarsa". Duba yadda ka fassara wannan a 1:1.
Wadannan sunayen maza ne.
Kalmar "suka" yana nufin Sharezer da Regem Melek.
Yahudawa sukan yi wa'azi a wani lokaci a watan biyar na kalandar Ibraniyawa, don wannan ne lokacin da Babilawa suka hallaka haikalin Yerusalem. wata na biyar yana a bangaren karshe na watan Yuli da bangaren farko na watan Agusta a kalandar Turawa.
AT: "a wata na biyar"
Yahudawa suka yi makoki a a wani lokaci a watan bakawai na kalandar Ibraniyawa, domin wannan ne bangaren watan da ragiwar Yahudawan da ke a Yerusalem suka tsere zuwa Masar bayan kisan gillar da aka yi wa Gedeliya, wanda sarkin Babila ya nada gwamnan Yahuza. Watan bakwai yana a karshen watan Stumba da farkon watan Oktoba na kalandar Turawa.
Mutanen Isra'ila sun yi bauta a Babila shekaru saba'in.
Wannan furcin yana nuni da lokacin da suke ci su sha a bukukuwan nuna girmamawa yadda Yahweh ya tanada musu.
An mori wannan tambayar don tuhumar mutanen Isra'ila da rashin girmama Yahweh sa'adda suke azumi. AT: "ba ku yi azumi don ku gimama ni ba"
An mori wannan tambayar don tuhumar jama'ar Isra'ila, wadanda ke murnar bukukuwa, da rashin girmama Allah da bukukuwansu. AT: "don kanku kuka ci, kuka sha"
Zakariya yana magana kan annabawan da ta wurin ambatan bangarorin jikinsu da suka fadi sakon Yahweh. AT: "Yahweh ya yi magana ta wurin annabawan da"
Za a iya rubuta wannan ambayar a matsayin magana. "Waɗannan ne daidai kalmomin nan... zuwa yamma".
"zauna a ciki"
Waɗannan ne kananan tuddai da suke dab da isowa duwatsun.
"Yahweh ya fadi kalmarsa". Duba yadda ka fassara wannan a 1:1.
Kalmar "wannan" tana nufin yadda mutum zai yi shari'a.
macen da mijinta ya mutu
dan da iyayensa suka mutu
wanda ya yi kaura daga kasarsa zuwa wata kasa dabam
"kada ku shirya aikata mugunta"
AT: "sun zama kamar shanun da suka ki a saka musu karkiya" ko "sun zama kamar shanun da suka ki biyayya"
"Sun rufe kunnuwansu"
AT: "Sun kudurta cewa za su ki sakonnin Yahweh"
AT: "ta wurin kalmomin annabawa"
AT: "zan tarwatsa su kamar yadda guguwa take tarwatsa ganyaye"
iska mai karfi mai jujuyawa yayinda take tafiya, tana warwatsa abubuwan da ke kan hanyarta
1Maganar Yahweh mai runduna ta zo gare ni cewa,2"Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: Ina kishi domin Sihiyona da kuma babban kishi da hasala mai zafi ƙwarai!3Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: Zan komo wurin Sihiyona in kuma zauna a tsakiyar Yerusalem, gama za a kira Yerusalem Birnin Gaskiya kuma dutsen Yahweh mai runduna za a ce da shi Dutse Mai Tsarki!4Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Tsofaffi maza da mata zasu ƙara kasancewa a titunan Yerusalem, kowannensu za shi buƙaci sanda a hannunsa domin yạ tsufa.5Titunan birnin zasu cika da matasa maza da mata, masu wasanni a cikinsu.6Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Idan wani al'amari ya zama mai wuya a ganin mutanen nan da suka rage, a wannan kwanaki, shi ma za shi zama abu mai wuya a idanuna? -- wannan furcin Yahweh ne.7Yahweh mai runduna ya faɗi wannan; Duba, Ina gaf da kuɓutar da mutanena daga ƙasashe na fitowar rana da na faɗuwar rana!8Gama zan dawo dasu, kuma zasu zauna a tsakiyar Yerusalem, haka zasu zama mutanena kuma, ni kuma zan zama Allahnsu cikin gaskiya da adalci!9Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Ku da kuka ci gaba da sauraron maganganuna daga bakin annabawa tun farkon kafa harsashen ginin wannan haikali, - wannan gida nawa, Yahweh mai runduna: Ku ƙarfafa hannayenku domin a gina haikalin.10Domin kamin wannan lokaci babu hatsin da aka tara daga wurin wani, babu wata riba domin mutum ko dabba, kuma ba a sami salama ba daga magabci ko ga mai shiga ko mai fita. Na maishe da kowanne mutum magabci ga makwabcinsa.11Amma yanzu baza shi kasance kamar kwanakin baya ba, zan zauna tare da mutanena waɗanda suka rage - wannan ne furcin Yahweh mai runduna.12Gama za a shuka irin salama; kuringa mai haurawa sama zata ba da 'ya'ya, duniya kuwa zata ba da amfanin ƙasa; sammai zasu ba da raɓarsu, gama zan sa sauran jama'ar da suka rage su gãji dukkan waɗannan abubuwa.13Kun zama misali na la'ana ga al'ummai, gidan Yahuda da na Isra'ila. Yanzu fa zan kuɓutar da ku da haka kuma zaku zama albarka. Kada ku ji tsoro; amma bari hannuwanku su ƙarfafa!14Gama Yahweh mai runduna ya faɗi wannan: kamar yadda na shirya yi maku lahani a lokacin da kakanninku suka cakuneni - Yahweh mai runduna ya fadi wannan - kuma bai fasa ba,15haka kuma zan yi shiri mai kyau a wannan kwanaki zuwa ga Yerusalem da kuma gidan Yahuda! Kada ku ji tsoro!16Ga abubuwan da dole ku aikata: ku faɗi gaskiya, kowanne mutum ga makwabcinsa. Ku yi shari'a da gaskiya, da adalci, da kuma salama a ƙofofinku.17Kada ku yi shirin aikata mugunta a cikin zuciyarku ga junanku, kuma kada ku ƙaunaci alƙawaran ƙarya -- gama waɗannan sune abubuwan da na ƙi! - wannan furcin Yahweh ne."18Sa'an nan maganar Yahweh mai runduna ta zo gareni, cewa,19"Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Azumi na watan huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai, da na watan goma, duk zasu zama lokatan farinciki, da jin daɗi, da bukukuwan murna na gidan Yahuda! Saboda haka ku ƙaunaci gaskiya da salama!20Yahweh mai runduna ya faɗi haka: Mutane zasu sake zuwa, harma da waɗanda suke zama a birane daban - daban.21Mazaunan birni ɗaya zasu je wani birnin su ce, "Mu yi sauri mu je mu yi roƙo a gaban fuskar Yahweh mu kuma nemi Yahweh mai runduna! Mu ma zamu tafi da kanmu.22Mutane dayawa da manyan al'umma zasu zo Yerusalem su nemi Yahweh mai runduna kuma su roƙi tagomashin Yahweh!23Yahweh mai runduna ya faɗi haka: A wannan kwanakin, maza goma daga kowanne harshe da kuma al'umma zasu kama haɓar rigarku su ce, "Bari mu tafi tare da ku, gama mun ji cewa Allah na tare da ku!"'
Yahweh Mai Ruduna ya ce mini
AT: "Na cika da fushi domin Sihiyona"
Wannan yana nufin Dutsen Sihiyona.
A nan "Tsattsarka" yana nufin "Na Yahweh".
"zama a cikin Yerusalem"
Zarafin tsufa alamar zaman lafiya da arziki ne.
Wuraren taruwar jama'a a birnin za su cika da jama'a, suna tafiyar da harkokinsu na yau da kullum.
"Idan ana ganin abu kamar mara yiwuwa"
AT: "jama'ar Yahuza da suka tsira"
Allah yana yin wannan tambayar don ya shawo kan jama'arsa su dogara ga alkawuransa. AT: "hakika, mai yiwuwa ne a gare ni!"
Akan fassara wannan furcin zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara wannan bayanin a hanyar da fi dacewa a yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
"zan ceci jama'ata ta Yahuda, wadanda suka tafi bauta"
AT: "sa'adda aka dora harsashen ginin haikalina" ko "sa'adda kuke gina harshashen gidana"
AT: "Ku yi aiki tukuru"
AT: "Tn kamin ku fara sake ginin haikalin"
AT: "babu hatsin da za a girba"
Babu amfani ga mutane ko dabbobinsu su nome kasa, gama ba su sami abinci daga gare ta ba.
"kamar a da"
AT: "Yanzu zan albarkaci jama'ar" ko "Yanzu zan yi wa jama'ar nan kirki"
AT: "Zan sa mutanen su yi zaman salama".
Akan fassara wannan furcin zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara wannan kalmar a hanyar da ta fi dacewa da yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
AT: "za a yi girbi mai kyau a gonaki"
Raba ita ce alamar yalwa. AT: "za a sami isasshen ruwan sama"
AT: "sami wadannan abubuwa duka a kowane lokaci"
AT: "Sa'ad da na hore ku, sauran al'ummai sun koyi abin da ke faruwa sa'ad da na la'anci mutum"
"jama'ar Yahuda da jama'ar Isra'ila"
AT: "ku yi aiki tukuru"
"hore ku"
"cakuni fushina"
"ban rage horon da na yi musu ba"
"Ku" yana nufin jama'ar Yahuza.
AT: "Ku fadi gaskiya ga kowane mutum"
AT: "Ku shar'anta rashin jituwa da adalci a majalisuku, don jama'a su yi zaman salama da juna"
AT: "kada ku yarda sa'adda mutane suka fadi karairayi a kararrakin kotu"
Akan fassara wannan furcin zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara wannan furcin a hanyar da ta fi dacewa a yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
"Ni" yana nufin Zakariya.
Yahudawa sukan yi makoki a wani lokaci a watan hudu na kalandar Ibraniyawa, domin wannan ne lokacin da Babiloniyawa suka fasa ganuwar Yerusalem. Wata na hudu yana a karshen watan Yuni da farkon watan Yuli a kalandar Turawa.
Duba yadda ka fassara wannan a 7:1.
Duba yadda ka fassara wannan a 7:4.
Yahudawa suna makoki a wai lokaci a watan goma na kalandar Ibraniyawa, domin wannan ne lokacin da Babiloniyawa suka fara yi wa Yerusalem kawanya. Watan goma yana karshen watan Disamba da farkon watan Janawari a kalandar Turawa.
"Mutane za su sake zuwa Yerusalem kuma"
"Mutane da yawa za su zo, hade da ama'a daga manyan kasashe"
"za su ja rigarku don kama hankalinku"
"Muna roko, baro mu yi tafiya zuwa Yerusalem tare da ku"
"Allah yana tare da ku, ya jama'a"
1Wannan furcin maganar Yahweh ne game da ƙasar Hadrak da Damaskus. Gama idanun Yahweh na bisan dukkan 'yan'adam, da kuma bisa dukkan kabilun Isra'ila.2Furcin nan kuma ya shafi Hamat wadda take maƙwabciya da Damaskus, ta kuma shafi Taya da Sidon, ko da shi ke suna da hikima ƙwarai.3Taya ta gina wa kanta mafaka mai karfi ta kuma lafta azurfa kamar ƙura da kuma tatacciyar zinariya kamar laƙa a bisa titunanta.4Duba! Ubangiji za ya kawar da ita ya kuma lallata karfinta na teku, da haka zata hallaka da wuta.5Ashkelon zata gani ta kuma ji tsoro! Gaza kuma zatayi rawar jiki ƙwarai! Ekron, begenta ba zai tabbata ba! Sarkin zaya hallaka daga Gaza, ba kuma za a sake zama cikin Ashkelon ba!6Baƙi zasu gina gidaje a Ashdod, zan kuma datse girman kan Filistiyawa.7Gama zan fitar da jininsu daga bakinsu, abubuwan banƙyamarsu kuma daga tsakiyar haƙoransu. Da haka zasu zama ragowa ga Allahnmu kamar zuriya a Yahuda, Ekron kuma zata zama kamar Yebusawa.8Zan kafa sansani kewaye da ƙasata gãba da sojojin maƙiya domin kada wani ya ratsa ta cikinta ko ya je ko ya dawo, domin ba bu mai tsanantawar da zai ƙara shigowa ta cikin ƙasata. Yanzu dai zan kula da ƙasata da idanuna!9Yi sowa da farinciki mai girma, ɗiyar Sihiyona! Yi sowa da murna, ɗiyar Yerusalem! Duba! Sarkinki na zuwa gare ki da adalci yana kuma kuɓutar dake. Mai tawali'u ne yana bisa kan jaki, a bisa kan ɗan jaki.10Daga nan zan datse karusa daga Ifraimu doki kuma daga Yerusalem, Za a kuma datse baka daga yaƙi; gama za ya yi maganar salama ga al'ummai, mulkinsa kuma za ya zama daga teku zuwa teku, kuma daga Ƙogi har zuwa ƙarshen duniya!11Amma ke, saboda jinin alƙawarina dake, zan fitar da 'yan sarƙarki daga ramin da babu ruwa.12Ku dawo cikin mafaka mai ƙarfi dukkan ku 'yan kurkukun bege! Ko yau ina shaida maku zan maido maku ruɓi biyu,13gama na lanƙwasa Yahuda kamar baka na. Na cika ƙwarina da Ifraimu. Na motso da 'ya'ya mazanki, Sihiyona, gãba da 'ya'ya mazanki, Giris, kuma na yi ki, Sihiyona, kamar takobin mayaƙi!14Yahweh za ya bayyana gare su, kuma kibiyoyinsa zasu harba kamar walƙiya! Gama Ubangijina Yahweh za ya busa ƙahon kuma za ya cigaba cikin hadari daga Teman.15Yahweh mai runduna zai kare su, zasu kuma haɗiyesu, su kuma ci nasara da duwatsun majaujawa. Sa'an nan zasu sha suna sowa kamar mutanen da suka bugu da ruwan inabi, zasu kuma cika da ruwan inabi kamar dãro, kamar kusurwoyin bagadi.16Yahweh Allahnsu zai cece su a wannan rana; zasu zama kamar garke mai ɗauke da mutanensa, gama zasu zama duwatsun kambi, wanda aka ɗaukaka bisa ƙasarsa.17Duba yadda zasu zama da kyau da kuma ban sha'awa! Samarin zasu yalwata kan hatsi, budurwan kuma bisa inabi mai zaƙi!
AT: "Wannan sakon Yahweh ne game da"
AT: "jama'ar kasar Hadrak da birnin Damaskus"
AT: "Gama Yahweh yana kallon kowane mutum". Amma, juyin zamani da yawa sun fassara wannan nassin zuwa "idanun bil'adama da na dukkan sauran kabilu suna a kan Yahweh".
AT: "mutanen kasar Hamat"
AT: "mutanen Taya da Sidon"
Mai yiwuwa ba da gaske Zakariya yake nufin cewa mutanen Hamat suna da hikima ba. AT: "ko da yake suna tsammani suna da hikima kwarai"
A nan, ana nuna birnin Taya kamar wata mace. AT: "gina kakkarfar mafaka" ko "gina doguwar ganuwa"
AT: "ta tara azurfa da zinariya kamar kurar kan titi"
AT: "Lura! Ubangiji zai karbe mallakar Taya"
AT: "zai kuma hallaka jiragen ruwan Taya, wadanda maza suke yaki da su a kan teku"
AT: "ta cinye birnin kurmus"
"za ta ga hallakarwar Taya"
AT: "Baki za su mamaye Ashdod, su zauna a wurin"
AT: "Zan sa Filistiyawa su daina fahariya da kansu kuma"
Wannan yana nufin nama da jin a cinkinsa, da kuma naman da ake mika wa gumaka. UDB ya bayyana wannan kai tsaye. AT: "Ba zan sake barinsu su ci nama da jini a cikinsa ba, kuma zan haramta musu cin abincin da aka mika wa gumaka"
Allah yana magana game da kansa kamar shi kungiyar mayaka ne. AT: "Zan kare kasata" (UDB).
Waɗannan maganganu biyu suna nufin abu daya, kuma suna jaddada umurnin a yi murna.
"Sihiyona" daya ce da "Yerusalem". Annabin yana maganar birnin kamar diya ce. Duba yadda ka fassara "ɗiyar Sihiyona" a 2:10.
Waɗannan kalamai biyu suna nufin abu daya, kuma suna maganar dabba daya ne. Jimla na biyu ya kara bayyana cewa wannan dan aholaki ne. AT: "a kan ɗan jaki"
AT: "hallak karusai na Isra'ila, waɗanda ake mora domin yaki"
AT: "dawakan yaki a Yerusalem"
A nan, baka yana wakiltan dukkan makaman yaki da ake yaki da su. AT: "za a hallaka dukkan makaman yaki"
A nan, aikin shelar salama yana wakiltan aikin wanzar da zaman lafiya. AT: "gama sarkinku zai kawo salama ga al'ummai"
"mulkinsa zai zama bisa dukkan duniya!"
A nan, "ke" yana nufin jama'ar Israila.
Wannan ramin yana nuni da bauta.
AT: "Ku komo kasarku, inda kuke da tsaro"
Wannan furcin yana nuni da Isra'ilawa da suke bauta, wadanda suke sa rai Allah zai cece su.
Ana maganar jama'ar Yahuza kamar su baka ne da Allah zai tafi yaki da ita. AT: "Zan mori jama'ar Yahuza in yaki mutanen Girka"
Ana maganar jama'ar Israimu, masarautar arewa, kamar su kibau ne da Allah zai harbi makiyansa. A cikin jakar kibau ake sojoji suke tara kibau.
Allah yana magana da mutanen kasashe biyu a lokaci guda.
Wannan bangaren anabcin ya ci gaba da kalmomin Yuhsa'u, maimakon kalmomin da Yahweh ya fada ta wurinsa.
Kalmar "su" tana nufin jama'ar Allah. AT: "jama'arsa za su gan shi a sararin samaniya" ko "zai zo wurin jama'arsa"
Isra'ila sukan dauki walkiya a matsayin kibiyar da Allah ya harba.
kahonnin na raguna ne. Mutanen sukan busa su don ba da alama a lokacin yaki da kuma wadansu bukukuwa.
Wadansu lokuta Isra'ilawa sukan yi tunanin Allah kamar yana tafiya a kan guguwa mai karfi, wacce ke zuwa daga kudu.
AT: "zai yi nasara gaba daya"
Isra'ilawa za su yi nasara kan mayakan da ke yaki da majajjawa. Wadannan mayakan suna wakiltan dukkan abokan gaban Isra'ila, ko da wane irin makamai suke dauke da su.
AT: "Za su yi ihu suna murnar nasararsu da babbar murya, kamar sun bugu".
Mai yiwuwa wannan yana nufin tasoshin da firistoci suke amfani da su wajen daukan jinin dabbobi zuwa bagade. AT: "za su cika da ruwan inabi kamar tasoshin da firistoci suke daukan jini zuwa bagade"
Bagadai suna da mikakkun kursuwoyi, inda jinin dabbobi ke taruwa. AT: "kamar yadda kusurwoyin bagade ke cika da jini"
Zakariya ya ci gaba da magana da jama'ar.
AT: "a kasarmu, za su yi kyau kamar lu'ulu'un kambi"
Samari za su ci abincin da suka samu daga girbin.
'Yan'mata za su ji dadin ruwan inabi. Wadannan maganganu a kna samari da 'yan'mata suna wakiltan daukacin jama'ar Isra'ila.
1Ku roƙi Yahweh ruwan sama a lokacin bazara -Yahweh shi ne mai yin hadarun-aradu -- kuma yana ba da ruwan sama ga kowa da kuma dukkan tsire tsiren gona.2Gama ƙarya kawai gumakan gãdo ke faɗi; masu sihiri kuma suna ƙirƙiro ƙarya; suna faɗin mafarkai na ruɗani su kuma yi ta'aziyar wofi, da haka suke yawo kamar tumaki suna shan azaba domin babu makiyayi.3Fushina na ƙuna akan makiyayan; sune bunsuran -- shugabannin -- waɗanda zan hora. Yahweh mai runduna za ya kuma lura da garkensa, gidan Yahuda, za ya mai dasu kamar dokin yaƙinsa a yaƙi!4Daga gare su dutsen kusurwar gini zaya fito; daga gare su turken rumfar za ya fito; bakan yaƙi za shi fito daga nan; daga can dukkan shugabanni zasu fito tare.5Zasu zama kamar jarumawa masu tattaka maƙiyansu a cikin laka a bisa titunansu a yaƙi; zasu ja dagar yaƙi, gama Yahweh na tare da su, zasu kuma kunyatar da mahayan dawakan yaƙi.6Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yosef; gama zan maido dasu in kuma nuna masu jinƙai. Ba za su yi kamar na yashe su ba, gama ni ne Yahweh Allahnsu, kuma zan amsa masu.7Daga nan Ifraim zaya zama kama da mayaƙi, zuciyarsu kuma zata yi farinciki kamar da inabi; 'Ya'yansu zasu gani su yi farinciki. Zuciyarsu zata yi farinciki a ciki na!8Zan yi masu busa in kuma tara su, gama zan kuɓutar dasu, kuma zasu zama da girma kamar yadda suke a dã!9Na shuka su cikin al'ummai amma zasu tuna da ni a ƙasashe masu ni sa, su da 'ya'yansu zasu rayu su kuma dawo gida.10Gama daga Asiriya zan tattara su in kuma maido dasu daga Masar. Zan dawo dasu ƙasar Giliyad da Lebanon har sai ba sauran wuri dominsu.11Zan bi ta cikin tekun azabarsu; Zan tsautawa igiyoyin tekun nan in kuma busar da dukkan zurfafun Nilu. Za a saukar da ƙasaitar Asiriya, sandar mulkin Masar kuma zata tafi daga Masarawa.12Zan ƙarfafa su a cikina, za su yi tafiya kuma cikin sunana - wannan furcin Yahweh ne.
Zakariya ya ci gaba da magana da mutanen.
"yake yin gizagizan hadari"
AT: "gumaka suna ba da sakonnin karya"
AT: "masu duba suna ganin wahayin karya"
AT: "masu duba suna karya game da mafarkasu don su yaudari jama'a"
AT: "mutanen ba su san hanyar da za su bi ba"
"Makiyaya" na wakiltan shugabannin jama'ar Allah. AT: "Fushina kan makiyayan jama'ar tana da zafi kwarai" ko "ina fushi kwarai da shugabannin jama'ata"
"Mazan awaki" na wakiltan azzaluman shugabanni.
AT: "zan kula da gidan Yahuza"
AT: "zan ba su karfin ikona na rashin tsoro"
"Dutsen kusurwa zai fito daga cikinsu". Ana maganar wanimuhimmin mai mulki kamar shi ne mafificin dutse na harsashen gini. AT: "Waɗansu cikin zuriyarsu za su zama muhimman masu mulki"
"turken alfarwa zai fito daga cikinsu". Ana maganar muhimman shugabanni kamar manyan turake ne su wadanda ke rike alfarwa kankam. AT: "shugabannin da za su rika kasara tare za su fito daga cikinsu"
"bakan yaki zai fito daga cikinsu". Ana maganar shugabannin mayaka kamar bakan da aake amfani da shi a yaki. AT: "shugabannin mayaka za su fito daga cikinsu"
AT: "Za su zama karfafa a yaki"
AT: "waɗanda suke nasara kan makiyansu gaba daya"
AT: "za su yi nasara bisa makiyansu da ke yakar su a kan doki"
AT: "Zan sa jama'ar Yahuda su yi karfi"
Wannan yana nufin jama'ar masarautar arewa ta Isra'ila.
AT: "kamar ban taba kinsu ba"
"Ifraim" a nan yana nufin masarautar arewa ta Isra'ila. AT: "Ifram zai yi karfi kwarai"
AT: "kuma za su yi murna kwarai da gaske"
"'Ya'yansu za su ga abin da ya faru, kuma za su yi murna saboda abin da Yahweh ya yi musu!"
Yafatowa tana nufin yin feduwa da kara mai tsini ta baki. Akan yi wannan don a ba da alama ga sauran jama'a, kamar yadda yake a nan.
Mutanen za su ci gaba da komawa Yahuza, har za ta cika da jama'a, a rasa wuri domin karin mutane su zauna a wurin.
Nassi yana yi maganar teku a matsayin alamar masifu da wahaloli da yawa.
AT: "Zan sa Kogin Nilu ya rasa dukkan ruwansa"
A nan, "martabar Asiriya" tana iya nufin mayakan Asiriya. AT: "Zan hallaka mayakan Asiriya masu fahariya".
AT: "kuma ikon Masar na mulkar sauran kasashe zai zo ga karshe"
Akan fassara wannan furcin zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara wannan bayanin a hanyar da ta fi dacewa a yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
1Ki buɗe ƙofofinki, Lebanon, don wuta ta cinye itatuwanki na sida!2Yi makoki, itatuwan siferes, gama itatuwan sida sun faɗi! Abin da yake ƙasaitacce ya lalace sarai! Yi makoki, ku rimaye na Bashan, gama babban kurmi dukka ya faɗi.3Makiyaya suna ta kururuwa, gama an lalatar da ɗaukakarsu! Muryar 'ya'yan zakuna na ruri, gama an lallatar da fahariyar Kogin Yodan!4Wannan ne abin da Yahweh Allahna ya faɗi: "Kamar makiyayi, mai kiwon garken da aka ƙaddara domin yanka!5(Su waɗanda suka sayesu suka yankasu kuma ba a yi masu horo ba, kuma waɗanda suka sayar da su sukace; "Mai albarka ne Yahweh! Na zama mai arziƙi! gama makiyayan dake yi wa masu garken aiki basu jin tausayinsu).6Gama ba zan ƙara jin tausayin mazaunan ƙasar ba! --- wannan furcin Yahweh ne. Duba! Ni da kaina ina gaf da bayar da kowanne mutum cikin hannun makwabcinsa da kuma cikin hannun sarkinsa, zasu kuma lallatar da ƙasar ba bu wanda zan kuɓutar daga hannunsu."7Don haka na zama makiyayin garken da aka ƙaddara domin yanka, ga masu cinikin tumaki. Na ɗauko sanduna biyu; ɗaya na kira ta "tagomashi" ɗayar kuma na kira ta "haɗin kai." da haka na yi kiwon garken.8A cikin wata ɗaya na hallaka makiyayan uku, gama hakurina ya gaza a kansu, haka su ma suka ƙi ni.9Sai na cewa masu garken, "Ba zan sake yi maku aikin makiyayi ba. Tumakin da ke mutuwa-- bari su mutu; tumakin da ke hallaka --- bari su hallaka. Bari tumakin dasu ka rage kowanne ya ci naman maƙwabcinsa."10Sai na ɗauki sandata "tagomashi" sai na karyata domin in karya alƙawarina da nayi da dukkan kabiluna.11A wannan ranar aka karya alƙawarin, masu cinikin tumaki da waɗanda ke kallona suka sani cewa Yahweh ya yi magana.12Na ce masu, "Idan kun ga ya dace ku biya ni ladata. Amma idan ba haka ba, kada kuyi." Sai suka auna mani ladata --- sulallan azurfa talatin.13Sai Yahweh yace dani, "Zuba azurfar cikin ma'aji, darajar farashin da aka kimantaka!" Sai na ɗauki sulallan azurfar talatin na zuba su cikin ma'aji a gidan Yahweh.14Sa'an nan na karya sandata ta biyu "Haɗin kai," domin a karya 'yan'uwantakar dake tsakanin Yahuda da Isra'ila.15Yahweh yace da ni, "Ka sake, ɗaukarwa kanka kayan aiki irin na wawan makiyayi,16gama duba, ina gaf da naɗa makiyayi a ƙasar. Ba za ya kula da tumakin dake hallaka ba. Ba za ya tafi neman ɓatattun tumaki ba, ko ya warkar da tumakin da suka gurgunce ba. Ba zaya ciyar da lafiyayyun tumakin ba, amma za ya cinye naman tumaki masu ƙiba, ya kuma saɓe ƙofatunsu.17Kaiton makiyayi mara amfani da ya yi watsi da garken! Bari takobi ta yi tsayayya da hannusa da kuma idonsa na dama! Bari hannunsa ya shanye idonsa na dama ya makance!"
Annabin yana magana da kasar Lebanon kamar ita mutum ne. AT: "Jama'ar Lebanon, ku shirya gama wuta za ta cinye itatuwanku na al'ul"
AT: "In da itatuwan mutane ne, za su yi kukan bakin ciki. Itatuwan kasharina suna tsaye su kadai domin an kone al'ul, kuma sun fadi".
AT: "In da itatuwan oak na Bashan mutanen ne, za su yi kuka, domin an sassare dazuzzukansu masu kauri".
AT: "Makiyaya suna kuka da karfi"
"Darajarsu" tana iya nufin arzikin ciyayin da makiyaya suke kai tumakinsu. AT: "gama an lalata ciyayinsu masu kyau".
AT: "domin an hallaka itatuwa da bishiyoyin wurin da suke zaune ta Kogin Yodan".
A nan, Yahweh ya fara ba da umurni ga Zakariya a hanyar misalin makiyayi da tumaki.
"jama'ar kasar"
Akan fassara wannan furcin zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara furcin a hanyar da ta fi dacewa da yarenka. An maimaita wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
AT: "zan sa kowane mutum ya zama a karkashin ikon wani"
AT: "cikin iko da rashin adalcin sarkinsa"
AT: "ba za su nuna wa jama'ar kasara tausayi ba"
AT: "amma ba zan ceci jama'ar Yahuza daga ikonsu ba"
An ci gaba da misalin makiyaya da tumaki.
"an nufi garken tumakin domin yanka"
Sanduna itatuwa ne da ke yin abubuwa dabam-dabam da su, hade da bi da tumaki. Sanduna suna iya samun lankwasa iri-ri a karshensu.
Juyi dabam-dabam sun fassara kalmar Ibraniyancin wannan nassin zuwa "alheri" da "kyau".
Wannan bayanin 'yan'uwantaka ne tsakanin bangarorin biyu na Isra'ila, masarautar arewa da masarautar kudu.
AT: "Ban iya jurewa kuma da masu tumakin da suka dauke ni aiki ba".
An ci gaba da misalin makiyaya da tumaki.
Annabin yana magana da kuma aiki a madadin Yahweh a nan.
AT: "ya fada musu sakon"
Giram 330 na azurfa. Shekel ɗaya yana da nauyin giram goma sha ɗaya.
An cigaba da misalin makiyaya da tumaki.
wurin ajiya a haikalin Yahweh
Wannan yana nufin farashin ya yi kadan da yawa a biya makiyayin da ke aikin Yahweh. Duba UDB, wanda ya cire akasin: "dan kankanin kudi".
tumaki masu lafiya, wadanda suka yi girma da kyau
mai yiwuwa a matsayin aikin keta
AT: "Ina misalin irin kunci da ke jiran wannan miyayi mara amfani!"
AT: "ji wa hannun damarsa rauni, da kuma huda idonsa na dama!"
"Takobi" a nan yana wakiltan abokan gaban da za su kai wa makiyayin hari.
karfinsa na fada
iyawarsa na gani yayinda yake fada.
1Wannan furcin maganar Yahweh game da Isra'ila - furcin Yahweh, shi wanda ya shimfiɗa sararin sammai ya kuma kafa harsashen duniya, wanda ya sa ruhun ɗan adam cikin mutum,2"Duba, ina gaf da sa Yerusalem ta zama kofi mai sa maƙwabtanta tangaɗi. Haka kuma za shi zama ga Yahuda a lokacin da aka yiwa Yerusalem sansani.3A wannan rana, Zan maida Yerusalem dutse mai nauyi domin dukkan mutane. Duk wanda ya yi ƙoƙarin ɗaga wannan dutse za ya ji wa kansa rauni mai tsanani, dukkan al'umman duniya kuma zasu tattaru yin gãba da wannan birni.4A ranan nan --- wannan ne furcin Yahweh --- zan bugi kowanne doki da firgita da kuma kowane mahayi da hauka. Zan dubi gidan Yahuda da tagomashi in kuma bugi kowanne dokin sojojin da makanta.5Daga nan shugabannin Yahuda zasu ce cikin zuciyarsu, 'Mazaunan Yerusalem sune ƙarfinmu saboda Yahweh mai runduna, Allahnsu.'6A wannan rana zan mai da shugabannin Yahuda kamar tukunyar wuta a tsakiyar itatuwa da kuma fitila mai ci balbal a cikin hatsin dake tsaye, gama zasu hallaka dukkan mazauna kewaye dasu dama da hagu. Yerusalem zata sãke zaunawa a wurinta."7Yahweh zai ceci rumfunan Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dauda da kuma na mazaunan Yerusalem su fi na sauran mazaunan Yahuda.8A wannan ranar Yahweh zaya zama kariyar mazaunan Yerusalem, kuma a wannan ranar, waɗanda basu da ƙarfi cikinsu zasu zama kamar Dauda, yayin da gidan Dauda zaya zama kamar Allah, kamar mala'ikan Yahweh a gabansu.9"A ranan nan da zan fara hallaka dukkan al'umman dasu ka yi tsayayya da Yerusalem.10Amma zan zubo da ruhun tausayi da na roƙo a bisa gidan Dauda da mazaunan Yerusalem, domin su dube ni, wanda suka soke. Zasu yi makoki domina, kamar wanda ke makoki domin tilon ɗansa; za su yi matuƙar makoki dominsa kamar waɗanda su ke makokin mutuwar ɗan fari.11A wannan ranar makokin cikin Yerusalem za shi zama kamar makokin da aka yi cikin Hadad Rimon cikin kwarin Megido.12Ƙasar zata yi makoki, kowacce zuriya daban da wasu zuriyoyin. Zuriyar gidan Dauda zata zama a ware matayensu kuma zasu zama a ware daga mazajen. Zuriya daga gidan Natan zasu zama a ware matayensu kuma zasu zama a ware da mazajen.13Zuriyar gidan Lebi zasu zama a ware, matayensu kuma a ware da mazajen. Zuriyar Shimeyawa zasu zama a ware matayensu kuma a ware daga mazajen.14Kowacce zuriya ta sauran zuriyar da suka ragu - kowacce zuriya zata zama a ware matayensu kuma zasu zama a ware daga mazajen."
Waɗannan ayoyin suna fara wani sashe ne da ke magana game da harin da ke zuwa Yerusalem, da kuma yadda Allah zai ceci birnin.
Akan fassara wannan zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara wannan bayanin a hanyar da ta fi dacewa a yarenka. An mori furcin sau da yawa a Zakariya.
"wand aya hallici sammai"
AT: "ya kirkiro dukkan duniya"
AT: "ya hallici ruhun mutum"
"kokon shan ruwa"
Wato, abin shan yana sa maye, kuma zai sa mayakan da suka kawo hari Yerusalem su bugu, su kasa yaki.
Wato, birnin Yerusalem. Al'ada ce a Ibraniyanci a yi maganar birni ko kasa kamar mace ce.
"abin da ba za a iya gusarwa ba"
Waɗannan ayoyin sun ci gaba da magana game da harin da ke zuwa kan Yerusalem, da kuma yadda Allah zai ceci birnin.
Wannan yana nufin ranar da mayaka za su abka wa Yerusalem.
Akan fassara wannan zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara furcin a hanyar da ta fi dacewa a yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
AT: "zan kare"
"jama'ar Yahuza"
Wannan yana nufin za su yi tunani, su ce wa kansu.
AT: "domin suna bautar Yahweh Mai Runduna"
"kamar tukunyar wuta a cikin tarin itatuwa ... hatsin da ya nuna yana tsaye a gona"
tukunyar wutar da mutanen zamanin da suke daukan garwashin wuta a ciki
sandar da ke ci da wuta a gefe daya, wadda ke haskakawa yayinda mutum ke tafiya, ko ta kai wuta wani wuri
"za su hallaka al'umman da ke kewaye"
Jama'ar Yerusalem za su sake zama a birninsu.
a nan, "alfarwai" suna wakiltar gidaje, kuma gidaje suna wakiltar mutanen da suke zaune cikinsu. AT: "jama'ar Yahuda".
Ma'ana tana iya zama: 1) zuriyar Dauda, ko 2) masu mulki.
Wannan mala'ika ne da Yahweh ya aika don ya kare jama'ar.
AT: "Zan ba wa jama'ar ruhun nuna jinkai ga wadansu, da kuma addu'a gare ni domin jinkai"
AT: "wanda suka suke shi ya mutu"
Hadad Rimmon yana iya zama wurin sarkin nan mai kirki, Yosiya, ya mutu da raunukan yaki, bayan yakin Magiddo. Kamar an kafa wata al'adar makoki a can domin mutuwarsa. Amma, wadansu mutane suna tunanin cewa hada Rimmon sunan allahnkarya ne wanda aka yi imanin cewa yana mutuwa kowace shekara, masu sujada sukan yi makoki a wannan bukin.
Wannan sunan wani fili ne a Isra'ila.
Wannan yana nufin dukkan mutanen da ke zaune a kasar Yahuda.
Zuriyar Dauda... da Natan... da Lebi.
1"A wannan rana za a buɗe wa gidan Dauda magudanar ruwa da kuma mazaunan Yerusalem, saboda zunubansu da rashin tsarkinsu.2A wannan ranar -- wannan furcin Yahweh mai runduna ne - cewa zan datse sunayen gumaka daga ƙasar don kada a ƙara tunawa dasu. Zan kuma sa dukkan annabawan ƙarya da ƙazamin ruhunsu su fita daga ƙasar.3Idan wani mutum ya ci gaba da yin annabci, mahaifinsa da mahaifiyarsa waɗanda suka haifeshi zasu ce masa, 'Ba za ka rayu ba, don kana ƙarya da sunan Yahweh! Sa'an nan mahaifinsa da mahaifiyarsa waɗanda suka haife shi zasu soke shi yayin da yake anabce-anabce.4A wannan ranar kowanne annabi zayaji kunyar wahayinsa yayinda yake gaf da yin annabci. Waɗannan annabawan ba zasu ƙara sanya rigar gashi ba don su ruɗi jama'a.5Gama kowanne zai ce, 'Ni ba annabi ba ne! Ni manomi ne, na fara aikin gona tun ina yaro!'6Amma wani zai ce masa, 'ina ka samo waɗannan raunukan a hannuwanka? shi kuwa za ya amsa, 'An yi mani rauni tare da waɗanda ke gidan abokaina."'7"Takobi! Motsa kanki gãba da makiyayina, mutumin da ya tsaya kusa da ni -- wannan furcin Yahweh ne - mai runduna. Bugi makiyayin, tumakin kuma zasu warwatse! Gama zan juya hannuna gãba da ƙasƙantattun.8Daga nan zaya kasance game da wannan a cikin dukkan ƙasar --- wannan furcin Yahweh ne --- kashi biyu cikin uku za a datse! Waɗannan mutane zasu hallaka; kashi ɗaya cikin uku kawai zaya rage a wurin.9Kashi ɗayan da ya rage zan bi dasu ta cikin wuta in tãcesu kamar yadda ake tãce azurfa; zan gwada su kamar yadda ake gwada zinariya. Zasu kira bisa sunana, ni kuwa zan amsa masu in ce, 'Waɗannan mutanena ne!' su kuma zasu ce, 'Yahweh ne Allahna!"'
Wurin da ruwa yake fitowa da kansa daga cikin kasa.
AT: "don wanke zunubinsu da rashin tsarkinsu"
Akan fassara wannan zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara shi a hanyar da ta fi dacewa a yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
AT; "kawar da bautar gumaka a daukacin kasar"
AT: "Zan kuma fitar da annabawan karya da kazanatattun ruhohinsu daga kasar"
Wannan furcin "wadanda suka haife shi" yana bayyana "ubansa da uwarsa" don nuna mamakin cewa iyayen mutum suna iya yi masa haka.
AT: "Lallai za ka mutu"
Soke shi ya mutu
Wannan yana nuni da annabawan karya, ba annabawan gaskiya na Yahweh ba.
"Riga" yana nufin babban rigar waje da ake yi da gashin dabbobi, wanda annabawa sukan sa.
Wato, "noma".
Waɗansu juyin zamani sun fassara nassin Ibraniyancin zuwa "wani mutum ya mallake ni tun ina dan saurayi", wato, ya saye shi a matsayin bawa.
AT: "Yaya ka sami wadannan raunukan a kirjinka?" Wannan yana nuni da wata al'adar annabawan karya inda suke ji wa kansu rauni a bukukuwansu.
Wato, zai amsa da karya.
AT: "Kai, Takobi! Ka farka". Wannan umurni ne daga Yahweh don a kai wa makiyayinsa hari, a kashe su.
Wannan yana nuni da wani sarki ko wani bawan Yahweh.
Akan fassara wannan furcin zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara wannan a hanyar da ta fi dacewa a yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
"garken" yana nufin jama'ar Isra'ila.
Watakila wannan yana nufin dukkan Israilawan da suke raunana, marasa karifa.
Akan fassara wannan furcin zuwa "Yahweh ya ce" a UDB. Za ka iya fassara furcin a hanyar da fi dacewa a yarenka. An mori wannan furcin sau da yawa a Zakariya.
Akan sa karfe ta cikin wuta don a tace shi a kara karfinsa. A nan, wannan furcin yana a matsayin kamance na kai mutanen cikin wahala domin su kara aminci ga Allah.
Tacewa yana nufin maida karafa masu daraja, kamar azurfa, su kara tatuwa. Karafa kamar azurfa da zinariya, akan gwada su don a san yadda tsabtarsu da karfinsu yake. Tacewa da gwadawa duka a nan kamance ne na kara maida mutanen masu aminci ga Allah.
1Duba! Ranar Yahweh na zuwa da za a raba ganimarku a tsakiyarku.2Gama zan tattara dukkan al'umma tsayayya da Yerusalem domin yaƙi kuma za a ci birnin. Za a warwashe gidajensu kuma za a yiwa matayensu fyaɗe. Rabin birnin za ya tafi zuwa bautar talala, amma ragowar mutanen ba za a datse su ba daga birnin.3Amma Yahweh zaya fita ya kuma jãdagar yaƙi da waɗannan al'ummai kamar yadda ya jãgadar yaƙi a ranar yaƙi.4A wannan rana tafin sawayensa zasu tsaya bisa Dutsen Zaitun, wanda yake gefen Yerusalem maso gabas. Za a raba Dutsen Zaitu kashi biyu tsakanin gabas da yamma ta kwari mai girma kuma sashe ɗaya na dutsen za shi janye zuwa arewa ɗaya sashen kuma za shi janye zuwa kudu.5Sa'an nan zaku tsere zuwa cikin kwarin tsakanin duwatsun Yahweh, domin kwarin dake tsakanin duwatsun za ya kai har Azel. Zaku yi ta gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzaya, sarkin Yahuda. Sa'an nan Yahweh Allahna za ya zo kuma dukkan tsarkaka zasu kasance tare dashi.6A wannan ranar da ba za a sami haske ba, babu sanyi ko ƙanƙara.7A wannan ranar, Yahweh kaɗai ya san ta, ba za a sake yin rana ko dare ba, gama maraice za ya zama lokacin haske.8A wannan rana ruwayen rai za su ɓulɓulo daga Yerusalem. Rabin ruwan za shi yi gudu zuwa tekun gabas rabin kuwa zuwa tekun yamma, damina da lokacin sanyi.9Yahweh zai zama sarki a bisa dukkan duniya. A wannan rana Yahweh kaɗai zai zama, Allah ɗaya, babu wani suna sai na sa.10Dukkan ƙasa za ta zama kamar Arabah, daga Geba har zuwa Rimon kudu da Yerusalem. Yerusalem zata ci gaba da haurawa bisa a mazamninta, daga Ƙofar Benyamin zuwa inda kofar ta ke a dã, zuwa Ƙofar Kusurwa, kuma zuwa Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsewar ruwan inabin sarki.11Mutane zasu zauna cikin Yerusalem kuma babu sauran hallaka da zata zo gare su daga wurin Allah. Yerusalem zata zauna cikin kariya.12Wannan ita ce annobar da Yahweh zai hari dukkan al'umman da suka tayarwa Yerusalem da yaƙi: Naman jikinsu zai ruɓe lokacin da suke a tsaye bisa sawayensu. Idanunsu zasu ruɓe cikin kwarminsu kuma harsunansu zasu ruɓe daga cikin bakunansu.13A wannan rana babban tsoro daga Yahweh za shi abko masu. Kowannensu zai kama hannun wani, kuma hannun wani zai ɗaga hannunsa domin tsayayya da hannun wani.14Yahuda kuma zai yi yaƙi da Yerusalem. Zasu tara dukiya daga al'umman dake zagaye dasu - zinariya, da azurfa da kuma kyawawan riguna tuli.15Annoba zata faɗo wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakai, da dukkan dabbobin da suke a sansaninsu zasu wahala da wannan annobar.16Za shi zama kuma dukkan waɗanda suka rage cikin ƙasashen da suka zo yaƙi da Yerusalem a maimako zasu zo kowacce shekara domin su yi wa sarki sujada, Yahweh mai runduna, sụ kuma kiyaye Idin Bukkoki.17Za shi zama kuma idan wani daga cikin al'umman duniya ya kasa zuwa Yerusalem don ya yi sujada ga sarki, Yahweh mai runduna, daga nan Yahweh kuma ba zai aiko masu da ruwan sama ba.18Idan al'ummar Masar basu je ba, to ba zasu sami ruwan sama ba. Annoba daga Yahweh zata abko wa duk mutanen dasu ka ƙi zuwa domin su yi Bikin Idin Bukkoki.19Wannan zai zama horon da za a yi wa Masar da kuma horo ga kowacce al'ummar da ba ta zo Yerusalem ta halarci Bikin Idin Bukkoki ba.20Amma a wannan ranar, ƙararrawar dawakai zasu ce, "ku keɓe ga Yahweh," kuma darurrukan da suke gidan Yahweh zasu zama kamar darurruka a gaban bagadi.21Gama kowacce tukunya a Yerusalem da Yahuda za a ƙeɓeta ga Yahweh mai runduna kuma duk wanda zai kawo hadaya zai ci daga cikinsu ya kuma tafasa a cikinsu. A wannan rana 'yan kasuwa ba zasu ƙara kasancewa a cikin gidan Yahweh mai runduna ba.
Wannan surar tana bayyana yakin karshe na birnin Yerusalem, da yadda Allah zai cece ta.
AT: "abokan gabanku za su kwashe dukkan mallakarki, su raba wa kansu yayinda kuke kallo"
AT: "Zan sa kasashe da yawa su kai wa Yerusalem hari"
AT: "abokan gabanku za su kyale ragowar jama'ar su zauna a birnin"
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da bayyana yakin karshe a kan birnin Yerusalem, da kuma yadda Allah zai cece ta.
AT: "kamar yadda ya yi yaki a da"
"Kafafunsa" na nufin Yahweh kansa.
Wannan sunan wani gari ne ko kauye gabas da Yerusalem.
Watakila wannan yana nufin mala'ikun Allah.
Wannan dai yana nufin ruwa mai gudu ko ruwa mai gudana, maimakon ruwa da taya cik a wuri daya.
Wannan yana nufin Mataccen Tekun, wanda yake gabas da Yerusalem.
Wannan yana nufin Tekun Baharmaliya
"za a sami Allah ɗaya, Yahweh, wanda za a bauta wa".
Waɗannan sunayen wurare ne.
Wannan yana nufin tudun da birnin Yerusalem yake bisa, kusan mita 760 bisa iyakar teku.
Waɗannan sunayen kofofi dabam-dabam ne a ganuwar Yerusalem.
Wanan yana nufin kakkarfar wuri a kariyar ganuwar birnin. Mai wani mutum ne mai Hananel ya gina wurin.
Mai yiwuwa wannan yana nufin wurin da ake yin ruwan inabi don gidan sarauta.
Waɗannan ayoyin suna ci gaba da bayyana yakin karshe a kan birnin Yerusalem da yadda Allah zai cece ta.
AT: "suna kewayawa"
Kowane mutum zai kai wa dan'uwansa hari.
Waɗansu juyin suna da, "Yahuda ma za ta yi yaki domin Yerusalem". Nassin Ibraniyanci ba a bayyane yake ba sosai.
AT: "Za su kwace mallakar"
"da yawan gaske"
AT: "waɗanda suka kai wa Yerusalem hari"
AT: "zai yi wa al'umman hukunci mai tsanani"
AT: "za su zama tsarkakakku kamar kwanonin da ake amfani da su a bagade"
Akan yi tukwane dabam-dabam da wadansu kayayyakin amfani musamman don a yi aiki da su a haikali wajen yin sujada ga Yahweh da kuma hadayu. An dauki wadannan kebabbau na musamman, ba za a more su domin wani abu dabam ba.
Al'ada ce 'yan kasuwa su rika sayar wa mutane abubuwan da suke bukata domin yin hadayar da ta dace ga Yahweh a haikalin. Waɗansu juyin sun fassara zuwa "Kan'aniyawa", domin nassin Ibraniyancin yana iya zama da tagwayen ma'ana: "'yan kasuwa" da "Kan'aniyawa".
1Furcin maganar Yahweh ga Isra'ila ta hannun Malakai.2"Na ƙaunace ku," inji Yahweh. Amma ku kun ce, "Ta yaya ka ƙaunace mu?"3"Ashe Isuwa ba ɗan'uwan Yakubu ba ne?" Yahweh ya furta. "Amma na ƙaunaci Yakubu, na ƙi Isuwa. Na maida tuddansa banza abin ƙi, kuma na maida gãdonsa muhallin diloli na daji."4Idan Idomawa suka ce, "An buge mu har ƙasa, amma za mu sake tashi," Yahweh mai runduna zai ce, "Zasu sake tashi kuma su gina, zan kuma sake rushewa. Wasu zasu kirasu, 'Ƙasar masu mugunta' kuma 'Mutanen da Yahweh ya la'anta har abada.'5Idanuwanku zasu ga wannan, kuma zaku ce, Yahweh mai girma ne har ma a gaban iyakokin Isra'ila.'"6Ɗa yana girmama ubansa, kuma bawa yana girmama ubangijinsa. Idan ni uba ne, ina ku ka girmama ni? Idan ni ubangijinku ne, me yasa ba ku ba ni daraja, inji Yahweh mai runduna ga ku firistoci, da ku ka rena sunana. "Amma kun ce ta yaya mu ka rena sunanka?'7Ta wurin miƙa ƙazantacciyar gurasa da kuke kawo wa bagadina. Amma kun ce, "Ta yaya mu ka ƙazantad da kai?"' Ta cewa teburin Yahweh marar daraja ne.8A lokacin da kuka miƙa hadayun makafin dabbobi ashe wannan ba mugunta ba ce? Duk lokacin da ku ka miƙa hadayun guragun dabbobi da marasa lafiya, wannan ba mugun abu ba ne? Kwa ba da wannan ga gwamnanku! Zai karɓa ko zaku sami tagomashi a wurinsa?" inji Yahweh mai runduna.9Yanzu kuna ta neman fuskar Allah, domin ya yi mana alheri. Amma Yahweh mai runduna yace da irin wannan baikon a hannunku, zaku sami tagomashinsa?10"Kash, ina ma da akwai wani daga cikinku wanda zai rufe ƙofofin haikali, don kada ku kunna wuta akan bagadina a banza! Domin ba na jin daɗinku," inji Yahweh mai runduna, "kuma ba zan karɓi kowanne baiko daga hannunku ba.11Daga fitowar rana har zuwa faɗuwarta sunana zai zama da girma a cikin al'ummai a dukkan wuraren da ake ƙona turare da kuma baye-baye masu tsabta da za a miƙa da sunana. Domin sunana zai zama da girma a cikin al'ummai," inji Yahweh mai runduna.12Amma kuna ɓata shi sa'ad da kuka ce teburi na Ubangiji ya ƙazance, kuma 'ya'yan itacensa da abincinsa abin reni ne.13Kun kuma ce, 'kai wannan abin gajiyarwa ne,' kuma kun wulaƙanta shi," inji Yahweh mai runduna. "kun kawo dabbar da naman daji ya kama ko gurguwa ko marar lafiya; kuma wannan ku ka kawo a matsayin hadayarku. Ko zan karɓi wannan daga hannunku? inji Yahweh.14"Bari mayaudari ya zama la'ananne wanda ke da dabba namiji a garkensa kuma ya yi wa'adi zai bayar da ita gare ni, amma duk da haka, Ni da na ke Ubangiji, ya kawo mani hadayar nakasashiya! Gama ni babban sarki ne," inji Yahweh mai runduna, "kuma za a girmama sunana a cikin al'ummai."
Za a iya furta wannan kamar magana. "Wannan shi ne shelar maganar Yahweh ga Isra'ila, wanda ya yi ta hannun Malakai"
Wannan shi ne sunan Allah, wana ya bayyana wa mutanensa a Tsohon Alƙawari. Duba shafin fassaraKalma game a kan Yahweh game da yadda za a fassara wannan.
A nan, "hannu", yana nufin aiki ko aikatawa. AT: "ta wurin ayyukan Malakai"
Wannan tambayar tana nuna cewa mutanen suna shakkar abin da Allah yake fada. Za a iya fadin wannan a matsayin magana. AT: "Ba ka nuna cewa kana kaunarmu ba".
Wannan tambayar, wadda amsar Yahweh ce don tuna wa jama'ar tarihin kasarsu, za a iya furta ta kuma kamar magana. AT: "Kun sani Isuwa dan'uwan Yakubu ne".
"Yahweh ya fadi wannan"
A nan, "kauna", tana nufin dangantakar biyayya tsakanin Yahweh da Yakubu, inda aka sami alkawari a tsakaninsu. Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "kamar yadda kuka sani, na mika kaina ga alƙawarin kaunar Yakubu".
A nan, wannan sunan, "Yakubu", ba ga Yakubu kadai yake nufi ba, amma dukkan zuriyarsa.
A nan, "ki", yana nufin cewa babu alkawari tsakanin Yahweh da Isuwa. Amma, ba ya nufin cewa Yahweh yana da wata kiyayya a zuciyarsa game da Isuwa.
Sunan nan, "Isuwa", ba yana nufin Isuwa ba kadai, amma dukkan zuriyarsa.
Wannan yana nufin kasar kan tudu ta Idom.
A Tsohon Alƙawari, kasancewar namomin jeji kamar diloli abu ne da akan mora do bayyana kasar da mutane suka zauna a ciki a da, amma suka watse suka bar ta, ta zama kango.
A nan, "gado", yana nufin yankin kasa ta zuriyar Isuwa, kasar Idom, wadda aka mamaye.
A nan, "Idom", tana nufin jama'ar Idom. AT: "Idan mutanen Idom sun ce".
A nan, "rurrushe", yana nufin "hallakawa". AT: "Zan hallaka".
A nan, "mugunta", tana nufin mugayen mutane ko miyagun ayyuka. AT: "kasar mugayen mutane".
A nan, "idanunku", tana nufin mutanen su kansu. AT: "Za ku ga wannan da kanku".
Yahweh yana tsautar wa firistoci ta wurin amfani da misalin tattaunawa, inda firistocin suke ikirarin cewa suna aikata kuma Yahweh yana fada musu cewa abin da suke ba daidai ba ne.
A nan, "sunana", yana nufin Yahweh kansa. AT: "kuna yi da ni kamar kun ki ni".
A nan, firistocin suna yin wata tambaya domin su nuna cewa ba su raina Yahweh ba a zahiri. Za a iya fadin wannan a matsayin magana. AT: "Zahiri, ba mu raina sunanka ba" ko "Ka fada mana yadda muka raina sunanka, domin ba mu tsammanin cewa mun yi hakan".
A nan, "kazantacciya" tana bayyana duk abin da bai cancanta a mika hadaya ga Allah ba.
A nan, firistoci suna tabaya don nuna cewa ba su kazantar da Yahweh ba. Za a iya fadin wannan a matsayin magana. AT: "Ba mu kasantar da kai ba" ko "Ka fada mana yadda muka kazantar da kai, gama ba mu tsammanin cewa mun yi hakan".
Wannan furcin yana nufin zagin Allah ta wurin mika masa hadayun da ba su cancanta ba.
Wannan yana nufin bagade.
Wannan ne amsar da Yahweh ya ba wa firistoci. Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "Kun kazantar da ni ta wurin cewa, 'Teburin Yahweh kazantacce ne'".
Abin da aka dauka mara daraja
A nan, Yahweh yana yin tambaya don fadin wani abu. Wannan maganar tana a matsayin tsautarwa ga mutanen. AT: "Kun sani sosai cewa mugunta ce a gare ku ku mika makauniyar dabba don hadaya!"
A nan, Yahweh yana yin tambaya don fadin wata magana. AT: "Kun sani kuma sosai cewa mugunta ce a gare ku ku mika gurguwar dabba, mara lafiya!"
A nan, Yahweh yana ba da umurni don bayyana wani musalin. AT: "Idan kun mika irin wannan wa mai mulkinku"
A nan, Yahweh yana yin wannan tambayar domin ya tsautar wa mutanen. AT: "Idan kun yi wadannan abubuwan, kun sani mai mulkinku ba zai amince da ku ba. Ba za ku sami tagomashi a wurinsa ba".
Fifita mutum yana nufin karbar mutumin da nuna masa tagomashi. AT: "zai karbe ku da tagomashi?" ko "zai yarda ya taimake ku?".
A bayar a matsayin kyauta don nuna bangirma.
Yanzu Malakai ba ya magana a madadin Allah. Yana magana kai tsaye da Isra'ilawa; yana sukar lamirinsu don tunaninsu cewa Allah zai nuna musu jinkai.
A nan, "fuska", tana nufin Allah da kuma kasancewarsa. AT: "kuna ta bidar Allah a gabansa"
A nan, Yahweh yana yin tambaya domin ya fadi kalmar tsautarwa. AT: "idan kun mika hadayu marasa karbuwa, hakika, Allah ba zai fifita ku ba".
A ibraniyanci an fassara wannan mawuyacin kalma a hanyoyi dabam-dabam a sabobbin juyi.
A na, "hannu", yana nufin yadda mutane suke kawo hadayu. AT: "wadda kuke kawowa"
Wannan yana bayyana zurfin muradi.
A nan, "hura wuta akan bagadena" yana nufin mika hadayu a kan bagaden Yahweh. AT: "domin kada ku hura wutar kona hadayun da ba zan karba ba".
A nan, "hannunku", yana nufin "ku". AT: "daga wurinku".
Wannan tagwayen kalamai suna nufin "ko'ina". Tana nan daidai da "cikin al'ummai" da "a kowane wuri".
A nan, "sunana", yana nufin "Ni". AT: "za a girmama ni a cikin al'ummai".
A nan, "sunana", yana nufin "martaba", "daraja".
Za a iya bayyana wannan kai tsaye. AT: "a wadannan kasashen, mutane za su kona turare su mika mini halaltattun hadayu, don su yi mini sujada".
A nan, "sunana", yana nufin Yahweh. AT: "gare ni".
Ma'anar tana iya zama 1) "naman da ake mika hadaya a kan bagade daga dabbobin da firistoci ke cin sauran gabobinsu" ko 2) "naman da ake mika hadaya a kan bagaden".
nuna tsananin raini ta wurin yin surutai ta hanci
A nan Yahweh yana yin tambaya don ya fadi kalmar tsautarwa. AT: "Hakika, bai kamata in karbi wannan daga gare ku ba".
A nan, "hannunku", yana nufin "ku". AT: "daga gare ku".
Za a iya furta wannan kai tsaye. AT: "mutane a sauran al'ummai za su girmama sunana"
A nan, "sunana", yana nufn Yahweh. AT: "za a girmama ni".
1Yanzu ku firistoci, wannan umurni domin ku ne.2"Idan ba zaku saurara ba, kuma in ba zaku yi niyya a zuciyarku ku bani girma ba," inji Yahweh mai runduna, "lallai zan aiko da la'ana zuwa gare ku, kuma zan la'anta albarkunku. Hakika, na la'antar da su, domin ba ku sa dokokina a zuciyarku ba.3Duba, ina shirin tsauta wa zuriyarku, kuma zan watsa kashin dabbobi a fuskokinku, wato kashin dabbobin bukukuwanku, kuma zan kore ku daga gare ni.4Za ku sani cewa ni na aiko da wannan umarni gare ku, kuma alƙawarina zai ci gaba da kasancewa tare da Lebi," inji Yahweh mai runduna.5Alƙawarina da shi na rai da salama ne, kuma ni na ba dasu gare shi; Na sa ya girmama ni, kuma ya ji tsoro na, kuma ya darajanta sunana.6Umurnin gaskiya ya kasance a bakinsa, kuma ba a sami ƙarya a leɓunansa ba. Ya yi tafiya da ni a cikin salama da daidaituwa kuma ya juyo da yawa ga tuba daga zunubi.7Domin ya kamata leɓunan firist su kasance da sani kuma mutane su nemi koyarwa daga bakinsa, domin shi ɗan saƙon Yahweh mai runduna ne.8Amma kun kauce daga hanyar gaskiya. Kun sa da yawa sun yi tuntuɓe game da koyarwar shari'a. Kun karya alƙawarin Lebiyawa," inji Yahweh mai runduna.9Haka ni ma na maishe ku marasa daraja kuma abin reni ga dukkan mutane, domin baku bi hanyoyina ba, maimakon haka kuka nuna son kai game da abin da aka umurta."10Ashe dukkanmu ba uba ɗaya muke ba? Ba Allah ɗaya ne ya hallicce mu ba? Me ya sa muka zama marasa aminci kowanne ga ɗan'uwansa, mu na ƙazantar da alƙawarin iyayenmu?11Yahuda ya kasance marar aminci. An aikata mummunan abu cikin Isra'ila da Yerusalem. Gama Yahuda ya ƙazantar da wuri mai tsarki na Yahweh da yake ƙauna, kuma ya aure 'yar baƙon allah.12Bari Yahweh ya datse irin wannan mutum daga alfarwar Yakubu, ko wane ne shi, ko da ma mai kawo hadaya ga Yahweh mai runduna ne.13Kuna kuma yin wannan: wato kuna rufe bagadin Yahweh da hawaye da kuka da ajiyar zuciya, domin ba ya kula da hadayunku ko karɓar su daga hannunku da tagomashi.14Amma ku ka ce "Don me ya ƙi?" Domin Yahweh shaida ne tsakaninka da matarka ta ƙuruciya, wadda ka yi mata rashin aminci, ko da yake abokiyar tarayyarka ce da matarka ta alƙawari.15Ba shi ne ya yi su ɗaya daga ruhunsa ba? To me yasa ya maishe ku ɗaya? Saboda ya na neman 'ya'ya daga Allah. Don haka ku lura da kanku a cikin ruhunku, kada ka zama marar aminci ga matarka ta ƙuruciya.16"Gama na ƙi kisan aure," inji Yahweh, Allah na Isra'ila, "da kuma wanda ya rufe tufafinsa da husuma," inji Yahweh mai runduna. "To sai ku yi lura da kanku cikin ruhu don kada ku zama marasa aminci."17Kun gajiyar da Yahweh da maganganunku. Amma kun ce "Ta yaya muka gajiyar da shi?" Ta cewa "Duk wanda ya yi mugunta managarci ne a idanun Yahweh, kuma yana jin daɗin su, ko "Ina Allah na adalci?"
Wannan yana nufin daukan wani abu da matukar muhimmanci. AT: "dauke shi da matukar muhimmanci".
Ana maganar bangirma kamar wani abu ne da za a iya mika wa mutum.
A nan, wannan furcin yana nufin Allah.
Ana maganar la'ana kamar wani abu ne da za a iya aikarwa a kan mutum. AT: "zan la'ance ku".
Wannan yana nufin daukan umurnin Allah da matukar muhimmanci. AT: "ba ku daukan umurnina da matukar muhimmanci".
A nan, "kashin dabbobi a fuskarku", tana nufin kunyatarwa. AT: "Hakika, zan jefa ku cikin kunya; za ta yi muni kamar watsa kashin dabbobi a fuskarku".
A nan, "bukukuwa", suna nufin dabbobin da firistoci suke mikawa hadaya a bukukuwa Isra'ilawa. Mai yiwuwa "kashin dabbar" tana nufin kashin da dabbobin suke yi dab kamin a yanka su don hadaya, da kuma kashin da ake samu a cikin dabbara sa'adda ake yayyaka namansu kamin a mika su hadaya. Ma'aikatan haikalai suka kai wannan kashin dabbar zuwa wani wuri a wajen haikalin, watakila ma a wajen Yerusalem.
Za a iya fassara wannan mawuyacin furcin a matsayin "kuma Allah zai tfi da ku tare da shi", wato, tare da kashin dabbobin. Wannan furcin yana ci gaba da misalin yanka dabbobi don hadaya, kuma za a iya fadinsa a kai tsaye. A.T: "kuma za a jefar da ku a kan tarin kashin dabbobin; Allah zai tabbatar cewa an dauke ku sa'adda ake cire dukkan kashin dabbobin".
Ma'anar wannan maganar tana iya zama 1) Allah zai hukunta firistocin da suka yi rashin aminci ta wurin kashe su, da kuma sa wa a dauke jikunansu a jefa a kan kashin dabbobin, ko 2) Allah zai hukunta firistoci marasa aminci a wata mumunar hanyar da zai zama kamar an kawar da gawawwakinsu tare da kashin dabbobin.
Yahweh yana maganar Lebi kamar shi daidai ne da zuriyarsa, wato, kabilar Lebi. AT: "domin alkawarina ya kasance tare da ku, zuriyar Lebi".
Yahweh yana magana da kabilar Lebi su mutum daya ne.
A nan, ana maganar sakamakon alkawarin da ake sa ran samu kamar alkawarin ne kansa. AT: "Manufar alkawarina da Lebi ita ce don firistoci su yi zaman wadata da salama".
Wannan furcin ya ci gaba da misalin nan, amma bai bayyana wani ra'ayi da aka nufa a nassin ba. AT: "Alƙawarina da shi kuma tsoro ne, ya kuwa ji tsorona" ko "Cikin alƙawarina da shi, na bukace shi ya ji tsorona, ya kuwa ji tsorona".
A nan, "sunana", yana nufin Allah kansa.
A nan, samun wani abu yana nufin akwai abin. AT: "babu karya".
A nan, "bakinsa" yana nufin iyawar mutum ta yin magana.
A nan, tafiya tana nufin rayuwa, tafiyar da rayuwar mutum a wata hanya ta musamman.
A nan, bayanin yana nuna halin da Lawi ya yi rayuwa. AT: "cikin salama da gaskiya".
A nan, ana maganar shawo kan mutane daga aikata zunubi kamar an juya su ne daga zunubi. AT: "ya shawo kan mutane da yawa su daina zunubi".
A na, ana maganar ilimi kamar wani abu ne da firist zai iya ajiyewa. A wannan nassin, maganar "kiyaye ilimi" tana nufin sadar da gaskiyar sani game da Allah.
A nan "lebuna" suna nufin iyawar mutum ta yin magana.
"marmarin samun umurni"
A nan, ana maganar ilimi kamar wani abu ne da mutane za su iya nema. AT: "neman firist don ya koyar da su da gaske".
A nan, "baki" yana nufin abin da mutum yake fada.
Ana maganar irin halin da ya kamata a nuna kamar madaidaiciyar hanyar da ya kamata a bi ne, sa'anna watsar da halayyara kirki kuma ana maganarta kamar juyawa daga wannan hanyar.
Ana maganar rashin biyayya ga Allah kamar tuntube.
Wannan furcin, "game da doka", yana bayyana yanayin "tuntuben". AT: "Kun sa mutane da yawa sun yi rashin biyayya ga doka".
Wannan maganar tana nufin yadda mutane suke sane da mugayen halayen firistoci.
A nan, "hanyoyi", tana nufin "nufi", da "halaye". Ana maganan wadannan hanyoyin kamar abubuwa ne da za a iya ajiyewa a kiyaye. AT: "bi nufina game da yadda ya kamata ku yi rayuwa".
"saukaka wa wadansu ka'aidar da ya kamata a bi don mutanen da kake so, sa'adda tsananta ka'idar da za a bi don mutanen da ba ka so".
A nan, ana maganar halin nuna wa wadansu mutane alfarma fiye da sauran kamar wani abu ne da za a iya nuna wa wadansu. AT: "sanar da mutane cewa kuna nuna wa wadansu alfarma fiye da sauran".
A na, annabi Malakai ya fara magana ga 'yan'uwasa Isra'ilawa.
Malakai ya yi wadannan tambayoyi don ya tunasar da 'yan'uwansa Isra'ilawa game da abin da suka riga suka sani. AT: "Dukkanku kun sani cewa dukkanmu ubanmu daya ne, cewa Allah ya hallici al'umma ta wurinmu" ko "Dukkanku kun sani cewa Allah ne uban dukkanmu Isra'ilawa, domin shi ne ya hada al'ummarmu".
An nfi wannan tambayar don ta bayyana wata magana. AT: "Hakika, Allah daya ne ya hallice mu".
Mai yiwuwa wannan yana nufin yadda Allah ya hada Ibraniyawa suka zama al'umma.
Malakai ya yi wannan tambayar domin ya tsauta wa 'yan'uwansa Isra'ilawa. Za a iya bayyana wannan tambayar a matsayin magana. A.T: "Bai kamata mu yi wa juna keta ba, ko mu raina alkawarin Allah ta wurin rashin biyayya da umurninsa, kamar yadda kuka yi".
A nan, "Yahuda", tana nufin mutanen da ke yankin Yahuda, kuma ana maganar yadda suka keta alkawarinsu da Yahweh kamar su mutum daya ne mai suna "Yahuzd". AT: "Mutanen Yahuda suna rashin aminci".
Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "Mutane suna aikata ayyukan assha a Isra'ila da Yerusalem".
A nan, "Yahuda" kuma tana nufin jama'ar Isra'ila. AT: "Gama jama'ar Yahuda sun kazantar da wuri mai tsarki na Yahweh".
An sake magana kan mutanen Yahuza kuma kamar mutum daya ne mai suna "Yahuda". A.T: "ya auro mata daga wadansu al'ummai, matan da suke bauta wa gumaka".
Akan yi maganar hallaka abu kamar kawar da shi daga wani abu. AT: "Bari Yahweh ya hallaka kowane mutum a alfarwar Yakubu wanda ..." ko "Bari Yahweh ya kashe duk wani a al'ummar Isra'ila wanda ..."
A nan "alfarwar Yakubu" tana nufin al'ummar Isra'ila.
A nan, "Yakubu" yana nufin dukkan Isra'ila, domin Yakubu yana daya daga cikin kakannin da Isra'ilawa suka samo asalin zuriyarsu.
Kamar wannan furcin yana nufin "kowane mutum".
Malakai ya ci gaba da magana da 'yan'uwansa Isra'ilawa.
Wannan wata hanyar zugugata yadda masu sujada sukan yi ta kuka sa'adda suke yin addu'ar neman taimako daga Yahweh. An nufi wannan maganar da bayyana rashin karbuwar sujadar karyar da suke yi a gun Yahweh.
Kalmomin "kuka" da "kururuwa" suna da ma'ana kusan daya, kuma suna nuna tsananin kuka. A.T: "da kuka mai zafi".
A nan, duba kallon kyauta yana nufin karbar ta da kuma nuna tagomashi ga wanda ya bayar.
Wannan yana nufin cewa, wadanda suke kuka a bagaden Yahweh sun mika masa hadayu.
A nan, "hannu" yana nufin mutumin da ya mika hadayar. AT: "daga gare ku".
Cikakkiyar maganar ita ce, "Me ya sa ba ya kallon hadayun ko ya karbe su da tagomashi daga hannunmu?" Waɗansu masu fassara za su iya morar wannan cikakken bayanin a juyinsu.
"matar da ka aura sa'ad da kake da kuruciya"
Wannan furcin yana a manufar cewa har yanzu matar tana nan da rai.
A nan, ana maganar shaida na yarjejeniya tsakanin mutum biyu kamar ana tsaye a tsakiyarsu don shida game da abin da suka hada yarjejeniya a kai, ko da rashin jituwa ta taso a tsakanin mutum biyun. An kuma nufi wannan maganar don tunsar wa mutane cewa Yahweh zai hukunta duk wani Ba'isra'ile wanda ya karya alkawarin auren.
Za a iya bayyana wannan tambayar a matsayin magana. AT: "Hakika, ya maishe mijin da matar daya, ya dayanta su da ruhunsa".
Wannan furcin yana nufin maida mijin da matar jiki daya. AT: "maishe mijin da matar jiki daya".
'Ya'yan da za su girmama Allah, su yi masa biyayya.
Wannan furcin yana nufin cewa Isra'ilawa da yawa sun saki matansu.
"ta wurin alƙawarin auren da kuka yarda a kai"
A nan, "kisan aure" yana nufin saki, sa'adda namiji ya kori matarsa, don ya kawo karshen aure da ita. AT: "Na ki sa'ad da mutum ya saki matarsa".
Mai yiwuwa wannan yana nufin duk mutumin da yake yi wa matarsa keta.
"Saboda haka, sai ku yi hattara, ku zama da aminci ga matanku".
Ana maganar Yahweh kamar halin mutum yana iya gajiyar da shi, amma Allah ba zai gaji da a jiki ko a zuci ba. Mai yiwuwa wannan maganar tana nufin cewa Yahweh ya ji fushi ko ya fusata. AT: "Kun yi wa Yahweh laifi".
An nufi wannan tambayar don musunta cewa mutanen sun aikata wani abin da ba daidai ba. Za a iya furta wannan a matsayin magana. AT: "Hakika, ba mu gajiyar da shi ba".
Cikakkiyar maganar ita ce, "Kun gajiyar da shi ta wurin cewa". Wannan ita ce amsar annabin ga wannan tambayar.
A ann, "a gaban Yahweh" yana nufin "ra'ayin Yahweh".
Firistoci suna yin wannan tambaar domin su nuna cewa ko dai Yahweh ba ya kula ko mutanen suna aikata mugunta ko a'a, ko kuma cewa ba ya hukunta masu aikata mugunta. AT: "Hakika, Allah ba ya hukunta masu mugayen mutane".
Allah da yake hukunta masu aikata mugunta cikin adalci.
1"Duba, na kusa aiko da manzona, kuma zai shirya mani hanya a gabana. Sa'an nan Ubangiji da kuke nema, zai zo haikalinsa ba zato. Manzon da aka alƙawarta, da kuke farinciki da shi, duba, zai zo," inji Yahweh mai runduna.2Amma wa zai jure ranar zuwansa? Wa zai iya tsayawa sa'ad da ya bayyana? Domin zai zama kamar wutar maƙera, kamar sabulun wanki.3Zai zama kamar mataci mai tace azurfa, zai tsarkake 'ya'yan Lebiyawa. Zai tace su kamar zinariya da azurfa, sa'an nan ne zasu kawo baikon adalci ga Yahweh.4Sa'an nan ne baikon Yahuda da na Yerusalem zai gamshi Yahweh, kamar a kwanakin dă, a shekarun baya.5"Sa'an nan zan zo gare ku domin hukunci. Nan da nan zan zama shaida gãba da masu sihiri, da mazinata, da masu shaidar zur, da masu zaluntar ma'aikata wajen albashinsu, da masu cutar gwauraye, da marayu, da masu korar baƙi, da marasa girmama ni," inji Yahweh mai runduna.6Domin ni Yahweh ban canza ba; saboda haka ne ku 'zuriyar Yakubu ba ku ƙare ba.7Tun daga zamanin ubanninku kun kauce daga bin farillaina ba ku kuma kiyaye su ba. Ku dawo gare ni, ni ma zan dawo gare ku," inji Yahweh mai runduna, "Amma kun ce, 'Ƙaƙa zamu dawo?'8Mutum zai iya yi wa Allah fashi? Duk da haka kuna yi mani fashi. Amma kun ce, 'Ta yaya muka yi maka fashi?' A zakkoki da baye-baye.9La'anannu ne ku da la'ana, domin kuna yi mani fashi, dukkan al'umma.10Ku kawo dukkan zakka a cikin ma'aji, domin a sami abinci a cikin gidana, ku gwada ni a wannan," inji Yahweh mai runduna, "idan ba zan buɗe maku tagogin sama, in zubo da albarku a kan ku, har ba wurin tara su.11Zan kwaɓi masu ɓarnata maku amfani domin su dena lalatar maku da amfanin ƙasarku. Gonakin inabinku ba zasu kakkaɓe 'ya'yansu ba, inji Yahweh mai runduna.12"Dukkan al'ummai zasu ce da ku masu albarka. Zaku zama ƙasa mai ban sha'awa," inji Yahweh mai runduna.13"Maganganunku a kaina suna da ƙarfi," inji Yahweh. "Amma kuka ce, 'Me muka ce a tsakaninmu gãba da kai?'14Kun ce, "Ba amfani a bauta wa Allah. Wacce riba ce muka samu da yin biyayya da dokokinsa ko kuma da tafiya rai ɓace a gaban Yahweh mai runduna?15Yanzu muna kiran masu girman kai masu albarka. Masu aikata mugunta bama azurta kaɗai suke ba, amma har ma suna gwada Allah su kuɓuta."'16Sai waɗanda ke jin tsoron Yahweh suka yi magana da junansu. Yahweh kuma ya ji su ya saurare su, sai aka rubuta littafin tunawa a gabansa game da waɗanda ke jin tsoron Yahweh masu girmama sunansa.17"Zasu zama nawa," inji Yahweh mai runduna, dukiyata mai tamani, a ranar da zan yi wannan. Zan yi masu jinƙai, kamar yadda uba ya kan yi wa ɗansa jinƙai wanda yake bauta masa.18Sa'an nan ne kuma zaku bambance tsakanin adalai da miyagu da tsakanin masu bauta wa Allah da marasa bauta masa.
Yahweh ya fara magana kuma da jama'ar Isra'ila a aya ɗaya, amma annabi Malaki ya fara magana a aya biyu.
"Sa ido" ko "Saurara" ko "Maida hankali ga abin da zan fada muku"
A nan, ana maganar shriya mutane domin marabtar Yahweh kamar ana gyara wata hanya don Yahweh ya yi tafiya a kai.
Waɗansu juyi na zamani sun fassara wannan da manufar cewa wadannan maganganu biyu suna nufin mutum daya. Sauran fassarorin zamani sun bar wannan tambayar babu cikakken bayani. Muna shawarta cewa fassarori su bar wannan batun a bude, kamar yadda yake a ULB da UDB.
Kusan dukkan juyi sun bar wannan maganar a bude. Amma masu fassara za su bukaci su bayyana sosai dangantakar da ke tsakanin "manzo" da "alƙawarin". UDB ya gabatar da "manzon" a matsayin wanda aka yi alƙawarta ta wurin alƙawarin da Yahweh ya yi da Isra'ila. Wani zabi kuma shi ne a gabatar da manzon a matsayin wanda zai tabbatar da alƙawarin ko ya yi shelar sabon alƙawarin.
Wannan salon tambayar tana nufin cewa babu wanda zai iya tayayya da Yahweh sa'ad da ya zo. Za a iya hada su cikin magana guda. AT: "Amma, babu wanda zai iya tsayayya da Yahweh sa'adda ya zo ya shar'anta su".
A nan, "rana" tana nufin "lokaci". AT: "lokacin da ya zo"
A nan tsayawa tana wakiltan tsayayya da hari ko tuhumar wani.
Wannan maganar ta ba da dalilin da ya sa babu wanda zai iya tsayayya da Allah sa'adda ya zo. Ikon Allah na hukunta mutanen da kuma hana su zunubi, ana maganarsa kamar ikon sabulu mai karfi na tsaftace tufafi, ko ikon wuta na narkar da abu. Waɗannan hanyoyi ne na cewa ikon Allah na yin waɗannan abubuwa ya wuce a yi tsayayya da shi.
Gafarta wa 'ya'yan Lebi da kuma shawo kansu don su daina zunubi, ana maganarsa kamar tace karfe. AT: "kuma zai tsautar da 'ya'yan Lebi, ya gafarta musu son su yi zunubi"
A nan, "'ya'ya" na nufin zuriya. Zuriyar maza na Lebi su ne firistoci da ma'aikata a haikali.
A nan, zama yana nufin aikin makeri, wanda yakan zauna domin ya tace zinariya ko azurfa. Yana kuma nufin aikin sarki, wanda yake zama domin ya yi wa mutane hukunci ya ba da doka.
A nan, ana maganar jawo hankalin mutanen don su daina zunubi kamar makeri ne yake kara tace zinariya da azurfa.
A nan, "suka dace" na nufin "hadayun da aka yi sanadiyar sahihin muradin yi wa Allah sujada". AT: "za su kawo hadayu karbabbu ga Yahweh domin su yi wa Yahweh sujada"
Malakai ya ci gaba da magana a aya hudu, amma Yahweh ya fara magana kuma a aya biyar.
A nan, "Yahuda" da "Yerusalem" suna nufin mutanen waɗannan wuraren. AT: "hadayun da mutanen Yahuda da Yerusalem suke kawowa"
Waɗannan kalamai biyu suna nufin kusan abu daya, kuma suna jaddada cewa a da hadayu suna karbuwa a gun Yahweh. AT: "kamar yadda yake a da can"
A nan, "shari'a" tana nufin aikin hukuntawa. AT: "Sa'annan zan zo wurinku domin in shar'anta ku"
"masu sa ma'aikacin da suka dauka ya sha wahala ta wurin kin biyansa kudin aikinsa"
Wato, tauye wa bako hakkinsa. Ana maganar tauye hakkokin mutane kamar wani yana korar su ne daga gare shi. Mai yiwuwa maganar tana nufin korar wani wanda ya zo don a maida abin da ba daidai ba ya zama daidai. AT: "hana wa bakin da ke zaune a Isra'ila hakkokin da ya kamata su samu"
Yahweh ya ci gaba da magana da jama'ar Isra'ila.
"ba ku hallaka ba"
Ana maganar rashin biyayya ga dokokin Allah kamar juyawa daga gare su ne. AT: "Kun yi rashin biyayya da dokokina tun zamanin kakanninku"
A nan, ana maganar kaunar juna da rike amanar juna kamar komowa ne ga juna. AT: "Ku kaunace ni, ku girmama ni, zan kuwa taimake a kowane lokaci"
Mutanen suna yin wannan tambayar don su nuna cewa ba su daina yi wa Allah biyayya ba. Za a iya fadin wannan a matsayin magana. AT: "Ba mu taba bjirewa daga gare ka ba, saboda haka kaka za mu dawo wurinka" ko "Ba mu taba kauce maka ba, don haka babu amfani ka yi mana magana cewa mu dawo wurinka"
Yahweh ya ci gaba da magana da jama'ar Isra'ila.
Wannan tambayar tana nufin cewa tunanin zambatar Allah mugunta ce kwarai. Za a iya fadin wannan kamar magana. AT: "Hakika, kada mutum ya zambaci Allah" ko "Kada wani ya zambace ni"
Wannan tambayar tana nuni da cewa mutanen ba su tsammanin cewa sun zambaci Allah. AT: "Hakika, ba mu zambace ba"
Wannan amsar daga Yahweh tana nuni da cikakkiyar amsa. AT: "Kun zambace ni ta wurin hana mini zakkarku da hadayunku"
Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "Hakika, na la'ance ku!"
A nan, "al'umma" tana nufin mutanen da Yahweh yake magana da su. AT: "dukkanku a daukacin al'ummar kuna yi mini zamba"
Yahweh ya ci gaba da magana da jama'ar Isra'ila.
"dukkan zakkar"
A nan, "dakin" yana nufin haikali. AT: "haikalina"
A nan, umurnin "ku gwada ni" yana nufin wani abin da mutane za su iya yi, kuma ya kamata su yi: "idan kun gwada ni". Za a iya raba wannan zuwa maganganu biyu kuma. AT: "Idan kun gwada ni ... zan bude muku taskokin sama" ko "Ya kamata ku gwada ni ... idan kuwa kun yi haka, zan bude taskokin sama"
A nan, cewa wa ku masu alarka ne yana nufin an albarkace su. AT: "Dukkan alummai za su sani cewa an albarkace ku"
Wannan furcin yana nufin mutane a dukkan al'ummai. AT: "Mutanen da ke a dukkan al'ummai"
A nan, "dadi" na nufin wani yanayin da mazaunan kasa suke farin cikin kasarsu.
Waɗannan ayoyin suna fara wani sabon sashe a cikin littafin. A nan, Yahweh yana magana ne da jama'ar Isra'ila.
A nan, "karfi" yana nufin "tsanani" ko "mugu". Kuma, "kalmominku" yana nufin "Abin da kuka fada". AT: "Abin da kuka fada game da ni yana mugu ne"
Mutanen suna wannan tambayar don su nuna cewa ba su fadi komai a kan Allah ba. Za a iya fadin wannan a matsayin magana. AT: "Ba mu fada wa juna komai a kanka ba".
Mutanen suna yin wannan tabayar a tsakaninsu da manufar wata magana. AT: "Babu amfani ma yadda muka kiyaye dokokinsa, muka yi tafiya cikin nadama a gaban Yahweh Mai Runduna".
A nan, "tafiya ta baci" tana nufin "nuna halin nadama", mai yiwuwa domin nuna bakin cikin zunubansu.
A nan, wannan furcin yana nufin Allah yana sane da wabin da mutanen suke aikatawa.
A nan a kira mutum "mai albarka" yana nufin an albarkace shi. AT: "muna cewa masu girman kai suna da albarka"
Za a iya fadin wannan kai tsaye. AT: "muna cewa masu girmankai suna jin dadi"
Wato, "sun tsira daga hukuncin Allah".
Watakila al'amarin da aka bayyana a nan ya faru bayan mutane maraa tsoron Allah a Isra'ila sun tuba daga zunubansu. (Duba UDB)
Wannan yana iya nufin 1) Isra'ilawa sun rubuta wani littafi domin su rika tuna abin da suka alkawarta, kuma suka lissafta sunayen wadanda suke tsoron Yahweh, ko 2) Yahweh ya sa sa wani a sama ya rubuta littafi da sunayen mutanen da suke tsoronsa.
Wannan furcin yana nufin kowane littafin da ke taimaka wa mutane su tuna muhimman abubuwa, kamar bukukuwa ko mutane da suka rayu a da.
A nan, "sunansa" yana nufin Allah kansa.
"Za su zama mutanena"
A nan, "mallaka" tana nufin abin da mutum ke da shi. Za a iya bayyana wannan maganar a aikace. AT: "za su zama mallakata gaba daya"
Wannan furcin yana nuni da lokacin da Yahweh zai yi shari'a ya hukunta Isra'ilawa masu tawaye, ya ba da nasara ga Isra'ilawa masu aminci.
"ga bamanci tsakanin" ko "bambanta tsakani"
1Duba rana na zuwa, mai ƙuna kamar tanderu, inda dukkan masu girman kai da masu aikata mugunta zasu zama tattaka. Ranar dake zuwa zata ƙone su, "inji Yahweh mai runduna, "Baza ta bar masu tushe ko reshe ba"2Amma a gare ku ku dake tsoron sunana, ranar adalci zata fito da warkarwa a fukafukanta. Zaku fita, ku yi ta tsalle kamar 'yan maruka a dangwali.3A wannan rana zaku tattake mugaye, zasu zama tattaka a ƙarƙashin sawayenku a ranar da zan aikata wannan", inji Yahweh mai runduna.4"Ku tuna da koyarwar bawana Musa wadda na ba shi a Horeb domin dukkan Isra'ila, farillai ne da dokoki.5Duba, zan aiko ma ku da annabi Iliya kafin babbar ranar nan mai tsoratar wa ta Yahweh.6Zai juyar da zuciyar ubanni zuwa wajen 'ya'ya, da zuciyar 'ya'ya zuwa ga ubanninsu, domin kada in kawo hari in hallakar da ƙasar ɗungum."
"sa ido" ko "saurara" ko "maida hankali kan abin da zan fada muku"
Ana maganar masifar da ke abkuwa a wannan lokacin kamar ranar kanta tana konewa. Akan yi maganar hukuncin Allah kamar wuta ne.
Fassara wadannan kalmomin kamar yadda ka yi a 3:13
Ana maganar wadannan mutane kamar za su zama busassun itatuwa da suka cancanci konewa kawai. A Littafi Mai Tsarki an saba maganar utane kamar su itatuwa ne ko shuke-shuke. AT: "dukkan masu girmankai da dukkan mugaye za su kone kamar busassun itatuwa"
A nan, "ranar" tana nufin al'amuran da za su faru a ranar nan. AT: "A ranar nan, zan kone su kurmus"
Wannan furcin ya ci gaba da magana kan mutanen kamar su shuke-shuke ne ko itatuwa. Saboda haka, hana saiwowi da rassa yana nufin an kashe su gaba daya. AT: "babu abin da zai rage"
A nan, "sunana" yana nufin Yahweh kansa.
Wannan yana iya nufin 1) Yahweh, wanda kuma adali ne, zai zo ya warkar da jama'arsa a wannan ranar, ko 2) a wannan ranar, Yahweh zai bayyana adalcin mutanensa, ya warkar da su.
Ma'anar tana iya zama 1) ana maganar warkar da wani kamar wani abu ne da rana take dauka tana kai wa mutane a fukafukinta, ko 2) warkarwar tana faruwa a karkashin fukafukin, wato, cikin tsaron da Allah yake ba wa mutanensa.
An aba, a yankin Gabashi a zamanin da, a yi maganar rana kamar tana da fukafuki wanda take tafiya da su a sararin sama. Ma'ana tana iya zama 1) ana maganar haske mai rayarwa wadda rana take bayarwa kamar fukafukinta ne, ko 2) ana cewa fukafukin suna kare mutanen Allah, don su ba su salama da tsaro.
A nan, ana maganan fansassun jama'ar Yahweh kamar sun zama 'yan marukan da aka sake daga garkensu, aka bar su su fita kiwo.
A nan, ana maganar nasarar mutanen Allah kamar suna tafiya ne a kan konannun gawawwakin abokan gabansu.
Ana maganar abokan gaban Isra'ila kamar sun kone sun zama toka. Duba: 4:1
Ana maganar abin da Allah ya koyar kamar abubuwa ne da Allah ya ba Musa.
A nan, "tuna" tana nufin "yi tunani a kai", alokaci daya kuma tana nufin "yi biyayya".
Wannan wani suna ne kuma na Sinai.
"yayinda dukkan jama'ar Isra'ila suke jira a gaban dutsen"
A nan, "dukkan Isra'ila" nuni ne ga dukkan mutanen da ke al'ummar Isra'ila.
Waɗannan ne dokokin da Allah ya ba Isra'ilawa don rayuwa a kowane lokaci.
Waɗannan zartarwar shari'a ne, waɗanda aka nufa da bayyana yadda dokoki suka shafi rayuwar yau da kullum.
A nan, ana maganar faruwar wannan ranar kamar tana zuwa. AT: "kamin babbar ranar nan mai banrazana ta Yahweh ta abku"
Wannan furcin yana nufin duk lokacin da Yahweh ya dauki tsauraran matakai.
A nan, ana maganar yadda za a canza tunanin mutane kamar ana juya zukatansu ne.
1Littafin asalin Yesu Almasihu Dan Dauda, Dan Ibrahim. 2Ibrahim shine mahaifin Ishaku, Ishaku shine mahaifin Yakubu, Yakubu shine mahaifin Yahuza da 'yan'uwansa. 3Yahuza shine mahaifin Farisa da Zera, ta wurin Tamar. Farisa kuma shine mahaifin Hasruna, Hasruna kuma shine mahaifin Aram.4Aram shine mahaifin Amminadab, Amminadab shine mahaifin Nashon, Nashon shine mahaifin Salmon. 5Salmon shine mahaifin Bo'aza ta wurin Rahab, Bo'aza shine mahaifin Obida ta wurin Rut. Obida shine mahaifin Yesse, 6Yesse shine mahaifin sarki Dauda. Sarki Dauda shine mahaifin Sulaimanu ta wurin matar Uriya.7Sulaimanu shine mahaifin Rehobo'am, Rehobo'am shine mahaifin Abija, Abija shine mahaifin Asa. 8Asa shine mahaifin Yehoshafat, Yehoshafat shine mahaifin Yoram, Yoram kuma shine mahaifin Uziya.9Uziya shine mahaifin Yotam, Yotam shine mahaifin Ahaz, Ahaz shine mahaifin Hezekiya. 10Hezekiya shine mahaifin Manassa, Manassa shine mahaifin Amon, sannan Amon shine mahaifin Yosiya. 11Yosiya shine mahaifin Yekoniya da 'yan'uwansa, dai dai locacin da aka kwashe su zuwa kasar Babila.12Bayan kwasar su zuwa kasar Babila, Yekoniya shine mahaifin Sheyaltiyel, Sheyaltiyel shine mahaifin Zarubabel. 13Zarubabel shine mahaifin Abihudu, Abihudu shine mahaifin Eliyakim, sannan Eliyakim shine mahaifin Azuru. 14Azuru shine mahaifin Saduku. Saduku shine mahaifin Akimu, sannan Akimu shine mahaifin Aliyudu15Aliyudu shine mahaifin Ali'azara, Ali'azara shine mahaifin Matana, sannan Matana shine mahaifin Yakubu. 16Yakubu shine mahaifin Yusufu maigidan Maryamu, wadda ta wurin ta ne aka haifi Yesu, wanda ake ce da shi Almasihu.17Tun daga Ibrahim zuwa Dauda, an yi tsara goma sha hudu ne, daga Dauda zuwa lokacin da aka kwashe su zuwa Babila, tsara goma sha hudu ne, sannan daga lokacin da aka kwashe su zuwa Babila zuwa Almasihu tsara goma sha hudu ne18Ga yadda haihuwar Yesu Almasihu ta kasance. Mahaifiyarsa, Maryamu, tana tashi da Yusufu, amma kafin su yi aure, sai aka same ta da juna biyu ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 19Mijinta, Yusufu, adalin mutum ne, amma ba ya so ya kunyatar da ita a sarari. Sai ya yi shawara ya sake ta a asirce.20Yana cikin tunanin wadannan al'amura, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gareshi a mafarki, ya ce masa, "Yusufu, dan Dauda, kada ka ji tsoron daukar Maryamu a matsayin matarka. Gama abinda ke cikinta, ta wurin Ruhu Mai Tsarki aka same shi. 21Za ta haifi Da, za ka kira sunansa Yesu, domin za ya ceci mutanensa daga zunubansu."22Duk wannan ya faru ne domin a cika abinda aka fada ta bakin annabin, cewa, 23"Duba, budurwa za ta sami juna biyu sannan za ta haifi da, za su kira sunansa Immanuel"-ma'ana, "Allah tare da mu."24Yusufu ya farka daga barci, ya yi kamar yadda mala'ikan Ubangiji ya umarce shi, sai ya dauke ta a matsayin matarsa. 25Amma Yusufu bai sadu da ita ba sai bayan da ta haifi da. Ya kira sunansa Yesu.
Marubucin ya fara da asalin Yesu domin ya nuna cewa Yesu daga zuriyar Sarki Dauda ne da kuma na Ibrahim. An cigaba da asalin har zuwa 1:1-17 .
Za a iya fassara wannan kamar cikakken zance. AT: "Wannan ita ce jerin sunayen kakanin Yesu Almasihu"
Akwai zuriya da yawa tsakanin Yesu, Dauda, da Ibrahim. Anan "ɗa" na nufin "ɗan zuriya". AT: "Yesu Almasihu, zuriyar Dauda, wanda shi zuriyar Ibrahim ne"
A wani lokacin ana amfani da kalmar "ɗan Dauda" kamar laƙani, amma a nan kamar ana amfani da shi a gano zuriyar Yesu.
Akwai hanyoyi dabam dabam da za a iya fassara wannan. A yadda ka fara fassara anan sai a ci gaba har karshen jerin sunayen kakanin Yesu. AT: "Ishaku ɗan Ibrahim"
A nan an riga an fahimci kalmar "shine". AT: "Ishaku shine mahaifin ... Yakubu shine mahaifin"
Wadannan sunayen maza ne.
A nan an riga an fahimci kalmar "shine". AT: "Feresa shine mahaifin ... Hesruna shine mahaifin"
A nan an riga an fahimci kalmar "shine". AT: "Aminadab shine mahaifin ... Nashon shine mahaifin"
Akwai hanyoyi dabam dabam da za a iya fassarar wannan. AT: "Salmon shine mahaifin Bo'aza, Uwar Bo'aza kuwa Rahab ce" ko kuma "Salmon da Rahab sune iyayen Bo'aza"
A nan an riga an fahimci kalmar "shine". AT: "Bo'aza shine mahaifin ... Obida shine mahaifin"
Akwai hanyoyi dabam dabam da za a iya fassarar wannan. AT:"Bo'aza shine mahaifin Obida, Uwar Obida kuma Rut ce" ko kuma "Bo'aza da Rut sune iyayen Obida"
A nan an riga an fahimci kalmar "shine". Akwai hanyoyi dabam dabam da za a iya fassarar wannan. AT: "Dauda shine mahaifin Sulaimanu, Uwar Sulaimanu kuwa matar Uriya ce" ko kuma "Dauda da matar Uriya sune iyayen Sulaimanu "
"gwauruwar Uriya." An haifi Sulaimanu bayar mutuwar Uriya.
A nan an riga an fahimci kamar "shine" a dukka maganar. AT: "Rehobo'am shine mahaifin Abija, Abija shine mahaifin Asa"
Wani lokaci ana fassara wannan haka "Amos"
ana iya amfani da wani kalma dabam da "kakani" idan ana amfani da wannan a nufin iyayen mahaifi ne kadai. AT: "Yosiya kakan Yekoniya ne"
lokacin da aka tilasta su tafiya zuwa Babila" ko kuma "lokacin da mutanen Babila suka Kwace yancin su a yaƙi, suka kuma sa su zama a Babila." idan harshe ku na bukatar a bayyana su wanene suke tafi Babila, za ku iya ce "Isra'ilawa" ko kuma "Isra'ilawan da suke zama a ƙasar Yahuza."
A nan wannan na nifin ƙasar Babila da al'ummar ta, ba birnin kawai ba.
yi amfani da kalmomin da ka mora a Matiyu 1:11.
Sheyaltiyel kakan Zarubabel ne.
Marubucin ya kumshi zuriyar Yesu, da ya fara cikin Matiyu 1:1.
Ana iya faɗin wannan cikin sifar aiki. AT: "Maryamu, wanda ta haifi Yesu"
Ana iya faɗin wannan cikin sifar aiki. AT: "wanda mutane ke kira Almasihu"
"14"
yi amfani da kalmomin da ka mora a Matiyu 1:11.
"Mahaifiyarsa, Maryamu, za ta auri Yusufu." Iyaye su ke shirya auren 'ya'yan su. AT: "Iyayen Maryamu, Mahaifiyar Yesu, sun yi alkawarin auren ta da Yusufu"
fassara wannan ta hanyar da zai nuna cewa ba a haifi Yesu ba a lokacin da Yusufu yake tashin Maryamu. AT: "ana tashin Maryamu, wanda za ta zama Uwar Yesu.
"kafin suyi aure." wannan na iya nufin kafin Maryamu da Yusufu su san juna. AT.: "kafin su san juna"
Ana iya bayyana wannan a sifar aiki. AT: "sai aka gane cewa za ta sami jariri" ko kuma "ya kassance cewa tana da juna biyu"
ikon Ruhu Mai Tsarki ya bata daman sami jariri kafin ta kwana da namiji.
Yusufu bai aure Maryamu ba tukunna, amma a sa'ada namiji da mace sun yi alkawarin aure ga juna, Yahudawa suna ganin su miji da mata, koda yake basu zama tare. AT: " Yusufu, wanda ke tsammani auren Maryamu" ko kuma "Yusufu"
"sokar da shirye shiryen auren su"
"Sa'ada Yusufu na tunani"
"zuwa ma sa a sa'ada Yusufu ke mafarki"
ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. "Ruhu Mai Tsarki ya sa ta kassance da juna biyu"
domin Allah ne ya aiki mala'ikan, shi yasa mala'ika ya san jaririn namiji ne.
"lalle za a ce da sunan sa" ko kuma "lalle za a sa masa suna." Wannan umurni ne.
mai fassara na iya kara matuni a kasa cewa "sunan 'Yesu' na nufin 'Ubangiji yana ceto.'"
wannan na nufin Yahudawa ne.
ba mala'ikan ne ke magana ba yanzu. Matiyu ne ke bayyana muhimmancin abin the mala'ikan ya ce.
ana iya ambata wannan cikin sifar aiki: AT: "abin da Ubangiji ya gaya wa annabin ya rubuta a zammanin da"
Akwai annabawa da yawa. Matiyu na magana game da annabi Ishaya ne. AT: "annabi Ishaya"
Anan Matiyu na ambata rubutun annabi Ishaya,
kula da kyau, domin abin da zan faɗa muhimmin gaskiyane: Budurwan"
Wannan sunan namiji ne.
Wannan baya cikin littafin Ishaya. Matiyu ne ke bayyana ma'anar sunan "Immanuwel." ana iya fassara wannan cikin wani jimla dabam. AT: "sunan na nufin 'Allah tare da mu.'"
Mala'ikan ya gaya wa Yusufu ya dauki Maryamu ta zama matarsa ya kuma kira sunan ɗan Yesu.
"ya aure Maryamu"
"jariri namiji" ko kuma "ɗan ta." tabata ce wa Yusufu bai fito a matsayin ainahin mahaifinsa ba.
"Yusufu ya sa sunan jaririn Yesu"
1Bayanda aka haifi Yesu a Baitalami ta kasar Yahudiya, a zamanin sarki Hirudus, sai ga wadansu masana daga gabas suka zo Urushalima, suna cewa, 2"Ina wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Mun ga tauraronsa a gabas mun kuma zo mu yi masa sujada." 3Da sarki Hirudus ya ji haka, sai ya damu kwarai, haka kuma dukan mutanen Urushalima.4Hirudus ya tara dukan manyan firistoci da marubuta na jama'a, ya tambaye su, "Ina za a haifi Almasihun?" 5Suka ce masa, "A Baitalami ne ta kasar Yahudiya, domin haka annabin ya rubuta, 6'Ke kuma, Baitalami, ta kasar Yahudiya, ba ke ce mafi kankanta ba a cikin shugabanin Yahudiya, domin daga cikin ki mai mulki zai fito wanda zai zama makiyayin jama'a ta Isra'ila.'"7Sai Hirudus ya kira masanan a asirce ya tambaye su aininhin lokacin da tauraron ya bayyana. 8Ya aike su Baitalami, ya ce, "Ku je ku binciko mani dan yaron da kyau. Idan kun same shi, ku kawo mani labari, don ni ma in je in yi masa sujada."9Bayan sun ji maganar sarkin, sai suka yi tafiyar su, ga shi kuwa, tauraron da suka gani a gabas yana tafe a gaban su, har ya zo ya tsaya bisa inda dan yaron nan yake. 10Da suka ga tauraron, sai suka yi matukar farin ciki.11Sai suka shiga gidan, suka ga dan yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka rusuna gabansa suka yi masa sujada. Sa'an nan suka kwance kayansu, suka mika masa kyautar su ta zinariya da lubban, da mur. 12Allah kuma ya gargade su a mafarki kada su koma wurin Hirudus, sai suka koma kasarsu ta wata hanya dabam.13Bayan sun tashi, sai ga wani mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki, ya ce, "Tashi, ka dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ka gudu zuwa kasar Masar, ka zauna a can sai na fada maka, don Hirudus yana shirin binciko dan yaron ya hallaka shi." 14A wannan dare fa Yusufu ya tashi ya dauki dan yaron da mahafiyarsa ya tafi Masar. 15Ya zauna a can har mutuwar Hirudus. Wannan kuwa domin a cika abin da Ubangiji ya fada ne ta bakin annabin, "Daga Masar na kirawo Da na."16Da Hirudus ya ga masanan nan sun shashantar da shi, sai ya hasala kwarai, ya aika a karkashe dukan 'yan yara maza da suke Baitalami da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa kasa, gwargwadon lokacin da ya tabbatar a gun masanan.17A lokacin ne aka cika fadar Annabi Irmiya, 18"An ji wata murya a Rama, tana kuka da bakin ciki mai zafi, Rahila ce take kuka saboda 'ya'yanta, kuma ta ki ta ta'azantu, domin ba su.19Sa'adda Hirudus ya mutu, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki a Masar ya ce, 20"Tashi ka dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ka tafi kasar Isra'ila, domin masu neman ran dan yaron sun mutu." 21Yusufu ya tashi, ya dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ya zo kasar Isra'ila.22Amma da ya ji Arkilayus ya gaji mahaifinsa Hirudus, yana mulkin kasar Yahudiya, sai ya ji tsoron isa can. Bayan da Allah ya yi masa gargadi a mafarki, sai ya ratse zuwa kasar Galili 23sai ya je ya zauna a wani gari da ake kira Nazarat. Wannan ya cika abin da aka fada ta bakin annabawa, cewa, za a kira shi Banazare.
A wannan aya an gabatar da sabon labari wanda aka cigaba har karshen ayan nan. Matiyu ya ba da labarin yunkurin Hiridus domin kisan sabon Sarkin Yahudawa.
"ƙasar Baitalami ta yankin Yahudiya"
"a lokacin da Hiridus ke sarki"
Ana nufin Hiridus mai girma ne
"masu Ilimin nazartan sararin sama daga gabas"
"daga wata ƙasa mai nesa a gabarcin Yahudiya
daga ilimin nazarin masanan, tauraron da suka gani na bayyana cewa an haife wanda zai zama sarki. Suna neman inda aka haife jaririn. AT: "Ina jariri da aka haifa wanda zai zama sarkin Yahudawa?"
ba su nufin cewa jaririn ne da tauraron. "tauraron da ya bayyana game da shi" ko kuma "tauraron da ke wakilce haifuwarsa"
"tasowa daga gabas" ko kuma "a lokacin da muke kasarmu"
AT: "suna da niyyar yi wa jaririn sujada a matsayin Ubangiji", ko kuma "suna so su daraja shi kamar sarkin wata ƙasa". Idan a harshen ku akwai wata hanyar bayyana wannan a yi amfani da shi.
" ya damu." Hiridus ya damu cewa wannan jaririn zai maye gurbinsa ta sarauta.
A nan "Urushalima na nufin mutanen ne. kuma "dukka" na nufin "da yawa." Matiyu ya yi magana haka domin ya nanata yadda mutane da yawa sun damu. AT: "Yawancin mutane da ke cikin Urushalima"
Cikin kasar Baitalami ta yanki Yahudiya
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "hakanan ne annabawa suka rubuta da dadewa"
Annabi Mika na magana da mutanen Baitalami kamar suna tare da shi a lokacin da yake magana amma ba haka ba. ana iya fassara "ba ke ce mafi kankanta ba" ta wani hanya. AT: ku mutanen Baitalami, ... kasar ku na cikin muhimman wurare a kasashen da ke Yahudiya"
Annabi Mika na magana game da wannan mai mulkin kamar wani makiyayi. wannan na nufin zai shugabanci, ya kuma kula da jama'an. AT: "wanda zai shugabanci jama'a ta Isra'ila kamar yadda makiyayi ke kiwon tumakinsa"
wannan na nufin Hiridus yayi magana da Masanan ba tare da sanin sauran mutane ba.
Za a iya fassara wannan ta wannan hanyan. AT: "Ya tambaye mazan, wani lokaci ne tauraron ya bayyana? Ya"
Yana nuna cewa Masanan sun faɗa masa lokacin da tauraron ya bayyana. AT: "wani lokaci ne tauraron ya bayyana. Masanan sun gaya wa Hiridus farkon bayyanuwar tauraron"
Wannan na nufin Yesu ne.
"bari in sani" ko kuma "gaya mani" ko "kawo mun rahoto"
dubi yadda aka fassara wannan cikin 2:2.
"Bayan Masanan"
"suka gani ya taso daga gabas" ko kuma " suka gani a kasar su"
"shirye su" ko kuma "jagorance su"
"tsaya bisa"
"wurin da dan jaririn ya ke zama"
zancen anan ya koma gidan da Yusufu, Maryamu, da Yesu suke zama.
"Masanan suka tafi"
AT: "Suka rusuna gabansa suka yi masa sujada" ko kuma "Suka rusuna da fuskansu a ƙasa." Sun yi haka ne domin su darajanta Yesu.
"taska" anan na nufin jakan da suke dauke da dukiyarsu a ciki. AT: "jaka ko akwatin da dukiyarsu ke dauke"
"daga baya kuma, Allah ya gargaɗe Masanan." Allah ya sani cewa Hiridus yana so ya yi lahani ga jaririn.
Ana iya fassara wannan haka. AT: a mafarki cewa, "kada ku koma wurin Sarki Hiridus, sai"
"Masanan sun tashi"
"ya zo wa Yusufu a lokacin da yake mafarki"
Allah na magana da Yusufu ne shi kadai.
ana iya bayyana wannan a sarari kamar haka. AT: har sai na faɗa maka cewa yayi kyau ka dawo"
A nan Allah ne ke magana. Malaika na magana a madadin Allah
ana nufin Yusufu, Maryamu, da Yesu ne suka kasance a Masar. AT: "suka kasance"
Hiridus baya mutu ba sai a 2:19. Wannan maganar na bayyana sawon kasancewarsu a Masar, amma ayan baya faɗa cewa Hiridus ya mutu a lokacin ba..
"na kira ɗa na daga Masar"
A littafin Yusha'u wannan na nufin dukka mutanen Isra'ila ne. Matiyu ya yi irin wannan maganar domin ya nuna gaskiyar cewa Yesu, Ɗan Allah ne. fassara wannan ta hanyar da zaya nuna cewa shine kadai ɗan ko kuma ɗan fari.
AT: "masanan sun kunyatar da shi ta wurin yin masa zamba"
Hiridus bai kashe yaran da hanunsa ba. AT: "Ya umurce sojoji su karkashe 'ya'ya maza" ko kuma " Ya aike sojoji wurin, su karkashe dukka 'ya'ya maza"
"shekaru biyu da wanda ba ya kai ba"
"a bisa lokacin"
ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: Wannan cikar" ko kuma "ayyukan Hiridus ya cika"
ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "abin da Ubangiji ya faɗa da dadewa ta wurin annabi Irimiya"
Matiyu na faɗin maganar annabi Irimiya.
ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "mutane suka ji murya" ko kuma "akwai wata ƙara mai ƙarfi"
Rahila ta yi rayuwa shekaru da yawa kafin wannan lokacin. wannan annabcin ya nuna Rahila, wanda ta mutu tana kuka domin zuriyarta.
ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "ba wanda ya iya ta'azantar da ita"
"domin ta rasa 'ya'yan kuma basu komo ba. Anan "an rasa" wata taushin hanyar cewa sun mutu ne. AT: "domin sun mutu"
Wannan alama ce ta fara fadan wani abu da ya faru cikin babban labari. ana iya samun mutane dabam da wanda suke abin da faru a baya. harshe ku na iya samun da yadda ake fadin wannan.
A nan "neman ran ɗan jaririn" hanyar nuna cewa suna so su kashe jaririn ne. AT: "wanda suke neman jaririn domin so kashe shi"
Wannan na nufin Sarki Hiridus da mashawarcinsa.
"Amma da Yusufu ya ji"
Wannan sunnan ɗan Hiridus ne.
"Yusufu ya ji tsoro"
ana iya faɗin wannan cikin sifar aiki. AT: "abin da Ubangiji ya faɗa da dadewa ta bakin annabawa"
"shi" anan na nufin Yesu. kafin lokacin zuwan Yesu annabawa sun ce da shi Mai ceto ko kuma Almasihu. AT: "mutuna za su ce Almasihu Banazare ne"
1A kwanakin nan Yahaya Mai baftisma ya zo, yana wa'azi a jejin Yahudiya yana cewa, 2"Ku tuba, domin mulkin sama ya kusa." 3Wannan shine wanda annabi Ishaya ya yi maganarsa, ya ce, "Muryar wani mai kira a jeji yana cewa, 'Ku shirya wa Ubangiji hanyarsa, ku daidaita tafarkunsa."4Yahaya kuwa yana sanye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma daure da damarar fata, abincinsa kuwa fara ne da zuman jeji. 5Sai mutanen Urushalima, da na dukan Yahudiya, da na duk kasashen bakin Kogin Urdun, suka yi ta zuwa wurin sa. 6Ya yi masu baftisma a Kogin Urdun, yayinda suke furta zunubansu.7Amma da ya ga Farisawa da Sadukiyawa da yawa, suna fitowa domin a yi masu baftisma, sai ya ce masu, "Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargade ku ku guje wa fushi mai zuwa? 8Ku ba da 'ya'ya da za su nuna tubanku. 9Kada kuwa ku dauka a ranku cewa, 'Ibrahim ne ubanmu.' Domin ina gaya maku, Allah yana da iko ya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin duwatsun nan.10Ko yanzu ma an sa gatari a gindin bishiyoyin. Saboda haka duk bishiyar da ba ta ba da 'ya'ya masu kyau ba, sai a sare ta a jefa a wuta. 11Na yi maku baftisma da ruwa, zuwa tuba. Amma mai zuwa baya na, ya fi ni girma, wanda ko takalmansa ma ban isa in dauka ba. Shi ne zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki, da kuma wuta. 12Kwaryar shikarsa na hannunsa, zai kuwa share masussukarsa sarai, ya tara alkamarsa ya sa a rumbunsa, amma zai kona buntun da wutar da ba za a iya kashewa ba."13Sai Yesu ya zo daga kasar Galili, ya je Kogin Urdun wurin Yahaya, domin ya yi masa baftisma. 14Amma Yahaya ya yi ta kokarin ya hana shi, yana cewa, "Ni da nake bukatar ka yi mani baftisma, ka zo gare ni?" 15Yesu ya amsa masa ya ce, "Bari ya zama haka a yanzu, domin a cika dukan adalci." Sai Yahaya ya yarje masa.16Bayan da aka yi masa baftisma, Yesu ya fito nan da nan daga cikin ruwan, sai kuma sammai suka bude masa. Ya ga Ruhun Allah yana saukowa kamar kurciya, ya sauko a kansa. 17Duba, wata murya daga sammai tana cewa, "Wannan shi ne kaunataccen Da na. Wanda ya gamshe ni sosai."
A Wannan sashin Matiyu ya fara ba da sabon labari game da hidimar bishara na Yahaya mai Baftisma. A aya Uku ta (3), Matiyu ya ambata maganar annabi Ishaya domin ya nuna cewa Yahaya mai Baftisma shine zabaɓen dan saƙon da zai shirya hidimar bisharar Yesu.
Wannan wasu shekaru ne bayan Yusufu ya bar Masar zuwa Nazarat. Wannan na yiyuwa kusa da lokacin da Yesu zai fara hidimar bishararsa. AT: " A bayan wasu lokaci" ko kuma "Bayan wasu shekaru"
Yahaya na magana da taro ne.
"mulkin sama" na nufin Allah na mulki kamar sarki. AT: "Allahnmu na sama zai nuna kansa a matsayin sarki bada jimawa ba"
ga wata hanyar faɗin wannan. AT: Gama annabi Ishaya yayi magana game da Yahaya mai Baftisma lokacin da ya ce"
Ana iya faɗin wannan cikin wata jimla kuma. AT: "An ji muryan wani na kira daga cikin jeji" ko kuma "Sun ji ƙarar wani da ke kira daga cikin jeji"
wannan jimlu biyun na nufin abu daya ne.
"Shirya hanyar Ubangiji"." Yin haka na nuna shirin jin sakon Ubangiji lokacin da ya zo. Mutane na yin haka tawurin tuba daga zunubansa. AT: "shirya domin jin sakon Ubangiji lokacin da ya zo" ko kuma "Tuba da kuma shiri domin zuwan Ubangiji"
A nan Matiyu na ba da wani muhimmin bayyani game da Yahaya mai Baftisma, shiyasa ya amfani da kalman "Yanzu kuwa" domin ya ba da wannan ƙarin hasken.
Irin wannan tufafi na ba da hoton cewa Yahaya mai Baftisma annabi ne kamar annabawan da, musamman annabi Iliya.
"Urushalima", "Yahudiya", da "kasashen da ke yankin" na nufin mutanen da ke cikin kasashen ne. kalman "dukka" na nuna cewa yawacin mutanen sun fito. AT: Sai mutane da yawa daga Urushalima, Yahudiya, da kasashen yankin"
Ana iya faɗin wannan ta wata hanya. AT: "Yahaya yayi masu Baftisma"
Wannan na nufin mutane daga Urushalima, Yahudiya, da kasashen da ke yankin kogin Urdu.
A nan " 'ya'ya" na nufin "yanayin halayya kamar." Macizai masu dafi na ba hoton miyagu ko mugunta. AT: "Ku mugayen macizai masu dafi! wa ya" ko kuma "Ku mugaye kamar macizai masu dafi! Wa ya"
Yahaya ya yi amfani da tambaya domin ya tsautawa farisawa da sadukiyawa wanda suna so ya yi masu baftisma domin su gujewa hukuncin Allah, amma ba su so su daina aikata zunubi. AT: "ba za ku iya guje wa fushin Allah haka ba." ko kuma "kada ku yi tunani cewa za ku gujewa fushin Allah wai domin na yi maku baftisma."
kalmar "fushi" na nufin hukuncin Allah domin fushinsa na zuwa kafin hukuncin. AT:"guje wa hukunci da ke zuwa " ko kuma "kuɓuta daga hukucin Allah a gare ku"
maganar "ba da 'ya'ya" na nufin halayyan mutum. AT: "Bari ayukkan ku su nuna cewa tũbanku na gaskiya ne"
"Ibrahim kakanmu ne" ko kuma "mu zuriyar Ibrahim ne." Shugabanin Yahudawa na tunani cewa Allah ba zai hukuntasu ba domin su zuriyar Ibrahim ne.
Wannan na kara karfin maganar da Yahaya zai yi.
Allah yana da iko ya wa Ibrahim zuriyar ta jiki daga duwatsun nan"
Yahaya mai Baftisma ya cigaba da tsautawa Farisawa da Sadukiyawa.
Wannan na nufin Allah na shirye ya hukunta masu zunubi. Za a iya bayana wannan ta wata hanya. AT: "Allah na shirye da gatarinsa ya sare duk itãcen da ta ke ba da mumunan 'ya'ya ya kuma kona ta" ko kuma "Kamar yadda mutum ke shirya gatarinsa domin ya sare itãcen da ke ba da 'ya'ya marasa kyau domin ya kone ta, haka Allah ke shirye domin ya hukunta ku sabili da zunubanku"
"nuna cewa an tũba"
Yesu shine mutumin da ke zuwa bayan Yahaya.
"yana da muhimmanci fiye da ni"
Ana kamanta baftisman da Yahaya ke yi da ruwa da kuma baftisma da ke zuwa na wuta. Wannan na nuna cewa baftisma Yahaya alama ce na tsaftace mutane daga zunuban su. Baftismar Ruhu mai Tsarki da wuta kuma shine ke da gaskiyar ikon wanke mutane daga zunubansu.
Wannan na kwatanta yadda Almasihu zai ware adalai da marasa adalci kamar yadda mutum ke ware alkama da ɓuntu. AT: "Almasihu na kamar mutumin da kwaryar shiƙarsa na hannunsa"
Anan "na hannunsa" na nufin mutum da ke shirye domin aiki. AT: "Almasihu na rike da Kwaryar shiƙarsa domin yana shirye"
Wannan kayan aikin sheke alkama ne domin a ware alkaman da ɓuntu. Ana jefa su sama amma alkaman na saukowa, sai iska ya kwaso ɓuntun zuwa wata gefe.
Almasihu na kamar mutumin da ke rike da Kwaryar shiƙarsa domin ya share masussukarsa.
"filinsa" ko kuma "filin ƙasa inda yake ware hatsin daga ɓutun"
Wannan na nuna yadda Allah zai ware adalai daga miyagu mutane. Adalai kuwa za su sama kamar yadda manomi ke tãra alkama a rumbu, sai Allah ya ƙone mutanen da ke kamar ɓuntu da wutan da ba za a iya kashewa ba.
AT: "ba za ta taba karewa ba"
AT: "don Yahaya ya iya masa baftisma"
Yahaya ya yi amfani da tambaya ya nuna mamakinsa game da buƙatan da Yesu ke yi. AT: " Kafini muhimmanci. baikamata in yi maka baftisma ba. Kai yakamata kayi mani baftisma."
A nan "mu" na nufin Yesu da Yahaya.
AT: "Bayan da Yahaya yi wa Yesu baftisma"
kalmar "gashi" anan na jan hankalimu zuwa ga sako mai ban mamaki da ke zuwa.
ga wata hanyar sa wannan. AT: "Yesu ya ga sama ta bude" ko kuma "Allah ya bude samai wa Yesu"
AT: "wannan magana na nufin cewa Ruhun na kamar kurciya or "Ruhun ya sauko akan Yesu a hankali kamar yadda kurciya ke yi.
"Yesu ya ji murya daga sama." Anan "murya" na nufin Allah ne ke magana. AT: "Allah ya yi magana daga sama"
Wannan muhimmin laƙani ne na Yesu da ke bayyana dangantakarsa da Allah.
1Sa'an nan Ruhu ya bi da Yesu zuwa cikin jeji, domin Ibilis ya gwada shi. 2Da ya yi azumi kwana arba'in dare da rana, daga baya yunwa ta kama shi. 3Sai mai jarabtar nan ya zo, ya ce masa, "Idan kai Dan Allah ne, ka umarci duwatsun nan su zama gurasa." 4Amma Yesu ya amsa ya ce masa, "A rubuce yake cewa, 'Ba da gurasa kadai mutum zai rayu ba, sai dai da kowace magana da ta ke fitowa daga wurin Allah.'"5Sa'an nan Ibilis ya kai shi tsattsarkan birni ya dora shi can kan kololuwar ginin haikali, 6ya ce masa, "In kai Dan Allah ne, to dira kasa. Domin a rubuce yake cewa, 'Zai ba mala'ikunsa umarni game da kai,' kuma, 'Za su daga ka da hannuwansu, domin kada ka yi tuntube da dutse.'"7Yesu ya ce masa, "kuma a rubuce yake, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'" 8Kuma, sai Ibilis ya kai shi kan wani dutse mai tsawo kwarai, ya nuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu. 9Ya ce masa, "Dukan wadannan zan baka idan ka rusuna ka yi mani sujada."10Sai Yesu ya ce masa, "Tafi daga nan, Shaidan! Domin a rubuce yake, 'Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kadai za ka bauta wa.'" 11Sa'an nan Ibilis ya rabu da shi, sai kuma mala'iku suka zo suka yi masa hidima.12To, da Yesu ya ji an kama Yahaya, sai ya tashi zuwa kasar Galili. 13Ya bar Nazarat, ya koma Kafarnahum da zama, can bakin tekun Galili, kan iyakar kasar Zabaluna da Naftali.14Wannan ya faru domin a cika fadar annabi Ishaya cewa, 15"Kasar Zabaluna da kasar Naftali, ta bakin teku, da hayin Kogin Urdun, Galili ta al'ummai! 16Mutane mazauna duhu suka ga babban haske, sannan ga wadanda ke zaune a yankin da inuwar mutuwa, haske ya keto masu."17Daga lokacin nan, Yesu ya fara wa'azi, yana cewa, "Ku tuba domin mulkin sama ya kusa."18Yana tafiya a bakin tekun Galili, sai ya ga wadansu 'yan'uwa biyu, Saminu da ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, suna jefa taru a teku, domin su masunta ne. 19Yesu ya ce masu, "Ku zo, ku biyo ni, zan mai da ku masuntan mutane." 20Nan da nan sai suka bar tarunsu, suka bi shi.21Da Yesu ya ci gaba da tafiya, sai ya ga wadansu mutum biyu, su kuma 'yan'uwa ne, Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya, suna cikin jirgi tare da mahaifinsu Zabadi, suna gyaran tarunsu. Sai ya kira su. 22Nan take suka bar mahaifinsu da jirgin, suka bi shi.23Yesu ya zazzaga dukan kasar Galili, yana koyarwa a majami'unsu, yana shelar bisharar mulkin, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiya a cikin mutane. 24Labarinsa ya bazu a cikin dukan kasar Suriya, kuma mutanen suka kakkawo masa dukan marasa lafiya, masu fama da cuta iri iri, da masu shan azaba, da kuma masu aljannu, da masu farfadiya, da shanyayyu. Yesu ya warkar da su. 25Taro masu yawa suka bi shi daga kasar Galili, da Dikafolis, da Urushalima, da kasar Yahudiya, har ma daga hayin Urdun.
A nan Matiyu ya fara ba da sabowar labari game da yadda Yesu yayi kwanaki arba'in a cikin jeji, anan ne Shaidan ya jarabce shi. a aya 4, Yesu ya tsuata wa Shaidan ta ruwaito magana a Maimaitawar Shariya.
AT: "Ruhun ya kai Yesu"
AT: "domin Iblis ya jarabci Yesu"
Wannan na nufin mutun ɗaya ne. Ya yiwu lalle ka yi amfani da dukka kalmomin domin fasara.
A magana game da Yesu ne.
"rana 40 da dare 40." Wannan na nufin sa'an lokaci 24. AT: "kwanaki 40"
Ya fi kyau a yi tsamanin cewa Shaidan ya san wai Yesu Ɗan Allah ne. Ya yiwu ana nufin 1) Wannan jaraba ne domin Yesu ya yi al'ajabi domin amfanin kansa. AT: "Domin kai Ɗan Allah ne, za ka iya umurci" ko 2) Wannan tuhuma ne ko zargi. AT: "ka hakikanta kai Ɗan Allah ne ta wurin umurtan"
Wannan muhimmin laƙani ne na Yesu ne da ke nuna dangantakar sa da Allah.
kana iya fasarar wannan ta wurin ruwaito maganar. AT: "ce da waɗannan duwatsun, 'Ku zama gurasa.'"
A nan "gurasa" na nufin kowani irin abinci. AT: "abinci"
AT: "Musa ya rubuto wannan a cikin nassosi tun da daɗewa"
Wannan na nuna cewa akwai wani abu game da ruwa da ya fi gurasa muhimminci.
Anan "magana" da "baki" na nufin abun da Allah ya ce. AT: "amma sai ta wurin sauraron dukka abun da Allah ya ce"
Ya fi kyau a yi tsamanin cewa Shaiɗan ya san wai Yesu Ɗan Allah ne. Ya yiwu ana nufin 1)Wannan jaraba ne domin Yesu ya yi al'ajabi domin amfanin kansa. AT: "Tun da shike da gaske kai Ɗan Allah ne, ka dira ƙasa" ko 2) Wannan tuhuma ne ko zargi. AT: "ka hakikanta gaskiyar cewa kai Ɗan Allah ne ta wurin dirowa da kanka ƙasa"
"bar kai da kanka ka dira zuwa ƙasa" ko "yi tsalle zuwa ƙasa"
AT: "gama ma rubucin ya rubuto a cikin nassosin" ko "domin nassosin ya ce"
"Allah zai umurce malai'ikunsa su lura da kai, kuma "Ana iya fasarar wannan ta wurin ruwaito magana. AT: "Allah zai ce da malai'ikunsa, "ku lura da shi", kuma"
" malai'ikunsa zasu riƙe ka"
An gane cewa Yesu na ruwaito nassi ne kuma. AT: Kuma, zan gaya maka abun da Musa ya rubuto a cikin nassosin"
Anan "ka" na nufin kowani mutum. AT: "kada wani ya gwada" ko "kar wani mutum ya gwada"
"daga nan, Iblis"
"Iblis ya ce wa Yesu"
"zan ba ka duk waɗannan abubuwan." majarabcin na jadada cewa zai bayar da "dukka waɗannan abubuwan," ba wai wasu ba.
"sa fuskar ka a ƙasa". An saba yin wannan domin nuna cewa mutum na sujada ne.
Wannan shine karshen sashin labari game da yadda Shaiɗan ya jarabce Yesu.
wannan umurni ne ga kowa da ke ji.
Kalmar "gashi" na jawo hankalin mu ne ga wani sabon bayani mai muhimmanci da ke zuwa.
Ana amfani da wannan kalma domin a dakatar da asalin labari da ake bayarwa. Matiyu ya fara bayar da wani sabon sashin labarin.
AT: "Tsarkin ya tsare Yahaya"
"Zabaluna da Naftali" sunayen zuriyar da suke zama a waɗannan yankuna ne shekaru da yawa da suka wuce kafin baƙi suka ɗauki iko akan ƙasar Isra'ila.
Wannan na nufin tafiyar Yesu zuwa Kafarnahum ya zauna.
AT: "Abun da Allah ya faɗa"
Waɗannan yankunan su na bayana wuri daya ne. Za a iya ambata waɗannan yankunan a cikin jimla. AT: "Cikin yankinZabaluna da Naftali ... cikin yankin Galili inda al'ummai ke zama, Mutanen da ke zama"
Wannan tekun Galili ne.
A nan "duhu" na nufin rashin sanin gaskiyar game da Allah. "haske" kuma na nufin gaskiyar maganar Allah da ke ceton mutane daga zunuban su.
Wannan na nufin abu daya ne da farkon sashin jimlar. Anan "waɗanda ke zaune a yankin, da inuwar mutuwa" ƙarin magane. yana nufin waɗanda basu san Allah ba. Waɗannan mutane na haɗari mutuwa da rabuwa da Allah har abada.
maganar "mulkin sama" na nufin shugabanci Allah a matsayin Tsarki. Wannan maganar na littafin Matiyu ne kadai. Dubi yadda aka fasara wannan a Matiyu 3:2. AT: "Allahnmu na cikin sama zai nuna kansa a matsayin Tsarki"
Ana iya bayana cikakiyar ma'anar wannan maganar a fili. AT: "jefan taru a cikin ruwa domin su kama kifi"
Yesu ya gayyato Saminu da Andrawus su biyo shi, su yi rayuwa da shi, su kuma kasance almajiransa. AT: "zama almajirai na"
Wannan ƙarin magana ne da ke nufin Saminu da Andrawus za su zama masu koyar da gaskiyar maganar Allah ga mutane, domin wasu ma su bi Yesu. AT: "Zan koyar da ku yadda za ku taro mutane wurina kamar yadda kuke taro kifi"
"Yesu ya kira Yahaya da Yakub." Wannan maganar na nufin cewa Yesu ya gayyace su, su biyo shi, su yi rayuwa da shi, su kuma zama almajiransa.
"nan da nan suka bar"
Yakamata ya zama a fili cewa wannan canjin rayuwa ne. Waɗannan mutanen baza su cigaba zama masunta ba, kuma za su bar kasuwanci iyalinsu su kuma bi Yesu dukka rayuwarsu.
"koyarwa a cikin majami'un Galilawa" ko "koyarwa a cikin majami'un waɗancan mutanen"
A nan "Mulki" na nufin shugabancin Allah a matsayin sarki. AT: "shelar bishara game da yadda Allah zai nuna kansa a matsayin tsarki"
kalmomin nan "cuta" da "ciwo" na da danganta sosai, amma a fasara su a matsayin kalmomi dabam dabam in ya yiwu. "cuta" shi ya ke sa mutum ya yi ciwo.
wannan rauni ne ko annoba ta jiki da ke samuwa daga cuta.
AT: "waɗanda suke karkashin mulkin aljannu"
Wannan na nufin kuwanene da ke da farfaɗiya a wurin, ba wai akwai wani da ake nufi ba na musammanda ke da farfaɗiya. AT: "waɗanda suke figar ruwa loto-loto" ko "waɗanda suke suma loto-loto da wanda baza a iya shawo kansa ba"
Wannan na nufin kuwanene da ke shanyayye a wurin, ba wai akwai wani da ake nufi ba na musamman da ke shanyayye. AT: "da kuma duk wanda ke shanyayye" ko "da waɗanda ba su iya tafiya ba"
Wannan sunan na nufin "garuruwa goma." Wannan sunan wani yanki ne kudu maso gabas da tekun Galili.
1Da Yesu ya ga taron jama'ar, sai ya hau saman dutse. Sa'adda ya zauna, almajiransa suka zo wurinsa. 2Ya bude bakinsa kuma ya koyar da su, yana cewa, 3"Albarka ta tabbata ga masu talauci a ruhu, domin mulkin sama nasu ne. 4Albarka ta tabbata ga masu makoki, domin za a ta'azantar da su.5Albarka ta tabbata ga masu tawali'u, domin za su gaji duniya. 6Albarka ta tabbata ga masu yunwa da kishin adalci, domin za a kosar da su. 7Albarka ta tabbata ga masu jinkai, domin za su samu jinkai. 8Albarka ta tabbata ga masu tsabtar zuciya, domin za su ga Allah.9Albarka ta tabbata ga masu kawo salama, domin za a ce da su 'ya'yan Allah. 10Albarka ta tabbata ga wadanda ake tsananta masu saboda adalci, domin mulkin sama nasu ne.11Masu albarka ne ku sa'adda mutane suka zage ku, suka kuma tsananta maku, ko kuwa suka zarge ku da dukan miyagun abubuwa iri iri na karya, saboda ni. 12Ku yi murna da matukar farin ciki, domin sakamakonku mai yawan gaske ne a sama. Ta haka ne mutane suka tsananta wa annabawa da suka yi rayuwa kafin ku.13Ku ne gishirin duniya, amma idan gishiri ya sane yaya za a mai da dandanonsa? Ba zai kara anfani ga komai ba, sai ko a zubar da shi, a tattake a karkashin kafafun mutane. 14Ku ne hasken duniya, birnin da ke kan tudu ba shi boyuwa.15Mutane ba za su kunna fitila su sa ta karkashin kwando ba, sai ko a dora ta a mazaunin ta, domin ta ba da haske ga kowa da ke gidan. 16Bari hasken ku ya haskaka gaban mutane yadda za su ga kyawawan ayyukanku su kuma yabi Ubanku da ke cikin sama.17Kada ku yi tsammanin na zo ne domin in rushe shari'a ko annabawa. Ban zo domin in rushe su ba, amma domin in cika su. 18Domin gaskiya ina gaya maku, har sama da kasa su shude, amma digo ko wasali daya ba za ya shude ba a cikin shari'ar, sai an cika dukan al'amura.19Saboda haka duk wanda ya karya mafi kankanta daga cikin dokokin nan ko kuwa ya koya wa wasu su yi haka, za a kira shi mafi kankanta a cikin mulkin sama. Amma dukan wanda ya kiyaye su ko kuwa ya koyar da su, za a kira shi mafi girma a cikin mulkin sama. 20Gama ina gaya maku cewa idan adalcin ku bai zarce adalcin marubuta da Farisawa ba, babu yadda za ku shiga mulkin sama.21Kun ji dai an ce wa mutanen da, 'Kada ka yi kisan kai,' kuma 'Duk wanda ya yi kisan kai yana cikin hatsarin hukunci.' 22Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da dan'uwansa, yana cikin hatsarin hukunci. Kuma duk wanda ya ce da dan'uwansa, 'Kai mutumin banza!' yana cikin hatsarin tsayawa gaban majalisa, kowa kuma ya ce da dan'uwan sa 'Kai wawa!' yana cikin hatsarin shiga wutar jahannama.23Saboda haka idan za ka yi baiko a bagadi sai ka tuna cewa dan'uwanka yana da damuwa da kai, 24ka bar baikon ka a gaban bagadin, ka yi tafiyarka. Da farko dai, ka sasanta da dan'uwanka kafin ka zo ka mika baikon.25Ka yi sulhu da mai karar ka tun kana hanyar zuwa gaban shari'a, domin kada mai karar ka ya mika ka ga alkali, alkali kuwa ya mika ka ga dogarai, za a kuwa jefa ka a kurkuku. 26Gaskiya ina gaya maka, ba za ka taba fita daga can ba sai ko ka biya dukan kudin da ya ke binka.27Kun dai ji an ce, 'Kada ka yi zina'. 28Amma ina gaya maku, duk wanda ya dubi mace, da muguwar sha'awa, ya riga ya yi zina da ita a zuciyarsa.29Idan idonka na dama zai sa ka tuntube, kwakule shi ka jefar daga gareka. Don gara daya daga cikin gabobinka ya halaka, da a jefa dukan jikin ka a jahannama. 30Ko kuwa idan hannunka na dama zai sa ka tuntube, ka yanke shi ka jefar daga gare ka. Domin gara daya daga cikin gabobin ka ya halaka, da a jefa dukan jikinka a jahannama.31An sake fada, 'Duk wanda ya kori matarsa, sai ya ba ta takaddar saki.' 32Amma ina gaya maku ko wa ya saki matarsa, idan ba a kan laifin lalata ba, ya mai da ita mazinaciya kenan. Kuma duk wanda ya aure ta bayan sakin, ya yi zina kenan.33Kun sake ji an ce wa wadan da suke a zamanin da, 'Kada ku yi rantsuwar karya, amma ku yi rantsuwar ku ga Ubangiji.' 34Amma ina gaya maku, kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama domin kursuyin Allah ne; 35ko kuwa da duniya, domin mazaunin kafafunsa ne, ko da Urushalima, domin birnin babban sarki ne.36Ko ma ace ku yi rantsuwa da kanku, domin ba za ku iya mai da gashin kanku baki ko fari ba. 37Amma bari maganarku ta zama 'I, I', ko kuwa 'A'a, a'a.' Duk abin da ya wuce wannan, daga mugun yake.38Kun dai ji an ce, "Ido a maimakon ido, hakori kuma a maimakon hakori.' 39Amma ina gaya maku, kada ku yi jayayya da wanda ke mugu, a maimakon haka, ko wa ya mare ku a kuncin dama, ku juya masa dayan ma.40Idan wani yana da niyyar kai kararku gaban shari'a saboda ya karbi rigarku, ku ba wannan mutumin mayafinku ma. 41Duk wanda ya tilasta ku ga tafiyar mil daya, ku je da shi biyu. 42Ku ba kowa da ya tambaye ku, kuma kada ku hana kowa da ke neman rance a wurinku.43Kun ji abin da aka fada, 'Za ka kaunaci makwabcin ka ka ki magabcin ka.' 44Amma ina gaya maku, ku kaunaci magabtan ku, ku yi addu'a domin masu tsananta maku, ku albarkaci wadanda suka la'ance ku, ku yi alheri ga wadanda suke kin ku, 45domin ku zama 'ya'yan Ubanku da ke cikin sama. Domin yakan sa rana ta haskaka wa mugu da mutumin kirki, kuma yakan aiko da ruwan sama ga adali da azzalumi.46Domin idan kuna kaunar wadanda suke kaunarku, wanne lada kuka samu? Ba haka masu karban haraji ma suke yi ba? 47Kuma in kun gaida 'yan'uwanku kadai, me kuke yi fiye da sauran? Ba hakanan al'ummai ma suke yi ba? 48Saboda haka, lalle ne ku zama cikakku, kamar yadda Ubanku na sama yake cikakke.
Wannan farkon sabuwar sashin labari ne da Yesu ya fara koyad da almajiran sa. Wannan sashin ya cigaba har zuwa karshen sura 7, an saba ce da wannan sashin huɗuba akan dutse.
Yesu ya fara bayana halayen mutane da suke da albarka a aya 3.
AT: "Yesu ya fara magana"
Kalmar "su" na nufin almajiransa.
Wannan na nufin wanda yake da tawali'u. AT: "waɗanda sun san bukatan su na Allah"
A nan "mulkin sama" na nufin Allah na mulki a matsayin sarki. A littafin Matiyu ne kadai aka ambata wannan. In ya yiwu, a sa "sama" a cikin fasara. AT: " gama Allah na sama zai zama tsarkin su"
Mai yiwuwa dalilin baƙin cikinsu su ne 1) yadda duniya ke cike da zunubi, ko 2) zunubansu, 3) mutuwar wani. kada a ba da takameme dalili nadămar, saidai harshan ku na bukatar wannan.
AT: "Allah zai sanyaya musu rai"
"mai kyakkyawan dabi'a" ko kuma "waɗanda basu dogara da karfin su"
"Allah zai ba su dukkan duniya"
Wannan na bayana mutanen da suke marmarin aikata abun da ke daidai. AT: "waɗanda suke marmarin aikata abun da ke daidai kamar yadda suke marmarin abinci da ruwan sha"
AT: "Allah zai cika muradinsu" ko "Allah zai gamsad da su"
"mutanen da zuciyar su na da tsarki." A nan "zuciya" na nufin asalin cikin mutum ko niyyar sa. AT: "waɗanda marmarin su kadai shine su bauta wa Allah"
A nan "ga" na nufin za su iya kasancewa tare da Allah. AT: Allah zai yardar musu su kasance tare da shi"
waɗannan mutane ne masu taimaka daidaita zaman salama tsakanin wasu.
AT: "gama Allah zai kira su 'ya'yan sa" ko "zasu kasance 'ya'yan Allah"
Ya fi kyau a fasara " 'ya'ya" yadda ake ce da yaran mutum a harshen ku.
AT: "mutane wanda ba a yi musu kirki ba"
"domin suna aikata abun da Allah ke so su yi"
A nan "mulkin sama" na nufin shugabancin Allah a matsayin sarki. Wannan maganar na littafin Matiyu ne kadai. In ya yiwu a sa kalmar "sama" a fassara. Duba yadda ku ka fassara wannan a 5:3. AT: "gama Allah na sama zai zama tsarkin su"
"faɗa kowace irin muguwar karya game da ku" ko "faɗin mumunar abubuwa game da ku da ba gaskiya ba"
"domin ku mabiya na ne" ko "domin kun gaskanta a gare ni"
"Murna" da "farin ciki matuƙa" na nufin kusan abu ɗaya. Yesu na so masu sauraron sa su kasance ba da murna kadai, in akwai abun da ya fi murna shi ya ke so su yi.
Mai yiwuwa ana nufi 1) kamar yadda gishiri ke sa abinci dadi, haka almajiran Yesu ke rinjayar mutane duniya domin su zama mutanen kirki. AT: " Kuna kamar gishiri ne ga mutanen duniya" ko 2) kamar yadda gishiri ke adana abinci haka almajiran Yesu ma suke kiyaye mutane daga ɓace wa. AT: "Kamar yadda gishiri ke a abinci, haka ku ke a duniya"
Mai yiwuwa ana nufi 1) "idan gishiri ya rasa ikon yin aikin sa na matsayin gishiri" ko 2) "in gishiri ya rasa ɗanɗano shi."
"yaya za a mayar da shi mai amfani kuma?" Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya koyad da almajiran sa. AT: "ba yadda za a iya amfani da shi kuma ba."
AT: "sai dai mutane su zubar da shi a kan yanya su kuma taka akai"
Wannan na nufi cewa mabiyen Yesu ke kawo saƙon gaskiyar maganar Allah ga mutane da basu san Allah ba. AT: "Ku na kamar haske ne ga mutanen duniya"
Da dare mutane na iya ganin hasken birnin na haskakawa. AT: "Da dare, ba mai iya ɓoye hasken da ke haskakawa a birnin da ke kan tudu" "Kowa na ganin hasken birnin da ke kan tudu"
"mutane ba su kunna fitila"
"sa fitilar a karkashin kwando." Wannan na nufi cewa wauta ne a kunna haske sa'anan a ɓoye ta domin kar mutane su ga hasken fitilar.
Wannan na nufin cewa ya kammata almajirin Yesu ya yi rayuwa ta hanyar da wasu zasu koyi game da gaskiyar Allah. AT: "Bari rayuwar ku ta zama kamar hasken da ke haskakawa ga mutane"
Zai fi kyau a fasara kalmar "Uba" yadda harshe ku ke kiran mahaifi.
Wannan na nufi abubuwan da annabawa suka rubuto a nassosin.
"Ina gaya muku gaskiya." Wannan maganar na nuna muhimmancin abun da Yesu zai faɗa nan gaba.
A nan "sama" da "ƙasa" na nufin duniya gaba daya. AT: "muddin duniya nan na nan"
ɗigo ne karamin haruffa na Yahudawa, wasali kuma wani dan alama da ke raba haruffa biyu. AT: "ba ko ɗigo ko wasali a haruffa ba"
AT: " dukka abubuwa sun faru" ko "Allah ya sa dukka abubuwa su auku"
"duk wanda ki biyayya" ko "duk wanda ya yi watsi"
"kowane daga waɗannan umurnai, ko mafi ƙanƙantan muhimmanci"
AT: "idan wani ... koyar wa wasu su yi haka, Allah zai ce da wannan mutum"
Wannnan magana "mulkin sama" na nufin sarautar Allah a matsayin sarki. A littafi Matiyu ne kadai aka faɗa wannan. In ya yiwu yi amfani da kalman "sama" a fasara ka. AT: "mafi ƙanƙanta a cikin mulkinsa na samaniya" ko "mafi ƙanƙancin muhimmanci a karkashin mulkin Allahnmu a sama"
"yi biyayya da dukka waɗannan umurnai, da kuma koyar wa wasu su yi haka"
mafi muhimmanci
Wannan na nuna muhimmancin abun da Yesu zai faɗa nan gaba.
AT: " cewa dole adalcinku ya fi ... malaman attaura domin ka shiga"
Ana iya faɗin wannan cikin sifar aiki. AT: "Allah ya ce wa mutane tun da daɗewa" ko "Musa ya ce wa kakaninku da daɗewa"
Anan "hukunci" na nufi alƙalin zai hukunta mutumin zuwa mutuwa. AT: "Alƙali zai hukunta duk wanda ya kashe wani mutum"
Wannan kalman na nufi kisan kai, ba kowani irin kisa ba.
Yesu ya yarda da maganar Allah, amma bai yarda da yadda malaman addini ke fasara maganar Allah. Kalmar "Ni" na bayyananniya. Wannan na nufin cewa abun da Yesu ke faɗi na na muhimmanci ɗaya da asalin umurnin da Allah ya bayar. Yi kokari fasara wannan maganar ta hanyar da zai nuna wannan bayyani.
Wannan na nufi ɗan'uwa mai bi, ba ɗan ciki ɗaya ba ko maƙwabci.
kamar wannan na ba da alamar cewa ba mutum ne alƙalin da Yesu ke nufi ba, amma Allah ne zai hukunta mutumin da ke fushi da ɗan'uwarsa.
Wannan zagi ga mutanen da ba su tunani da kyau. " wawa mutum" na kamar "mara ƙwaƙwalwa," "wofi" na ba da ra'ayin rashin biyyaya ga Allah.
Wannan na iya yiwuwa cewa ana nufi karamin majalisa ne ba babban majalisan firistoci na Urshalima ba.
Yesu na magana da jama'a game da abun da ya kamata su yi ko kar su yi a matsayinsu na mutane. An yi amfani da "ka" ko "naka", amma a wasu harshuna zai yiwu lalle a yi amfani da su a matsayin jam'i.
"bayar da sadakarka" ko "kawo sadakarka"
Wannan na nufin bagadin Allah a cikin haikali a Urshalima. AT: "ga Allah a kan bagadi a cikin haikali"
"a sa'ad da kana tsaye a bagadi ka tuna"
"wani mutum na fushi da kai domin wani abu da ka yi"
AT: "da farko ka samu salama da mutumin"
Yesu na magana da jama'a game da abun da ya kamata su yi ko kar su yi a matsayinsu na mutane. An yi amfani da "ka" ko "naka", amma a wasu harshuna zai yiwu lalle a yi amfani da su a matsayin jam'i.
Wannan na nufi mutum wanda ya zargi wani a kan aikata wani laifi. Ya kai mai laifin kotu domin ya dore masa laifi a wurin alƙali.
A nan "bashewa" na nufin bayar da yancin wani a hannun wani dabam. AT: "bar wa alƙali ya hukanta ka"
A nan "miƙa ka" na nufi bayar da yancin wani a hannun wani dabam. AT: "alƙali kuwa zai miƙa ka a wurin dogari"
mutum da ke da yancin ɗaukan umurnin alƙali
AT: "dogarin na iya jefa ka a cikin kurkuku"
"daga kurkuku"
AT: "wai Allah ce" ko "wai Musa ya ce"
Wannan kalmar na nufi aikata abu ko yin wani abu.
Wannan na nufin cewa mutumin da ya yi sha'awar mace na da alhakin laifin zina kamar mutum wanda ya aikata zinar kanta.
"kuma sha'awar ta" ko "kuma ya yi marmarin kwana da ita"
A nan "zuciya" na nufin tunanin mutum. AT: "cikin tunanin sa"
Yesu na magana da jama'a game da abun da ya kamata su yi ko kar su yi a matsayinsu na mutane. An yi amfani da "ka" ko "naka", amma a wasu harshuna zai yiwu lalle a yi amfani da su a matsayin jam'i.
A nan "ido" na nufin abun da mutum ke gani. "tuntuɓe" kuma na a matsayin "zunubi." AT: "in abun da ka ke gani na sa ka yi tuntuɓe" ko "in kana so ka yi zunubi domin abun da ka ke gani"
Wannan na nufin ido ko hannu mafi muhimmanci. Ya yiwu za a bukaci a fasara "dama" a matsayin "mafi inganci" ko "mafi karfi."
Wannan umurni ne da ke nufi mutum ya yi duk abun da ya ke bukata ya yi domin ya daina zunubi.
"cire shi a dole" ko "hallakar da shi." Idan ba a ambaci idon dama ba, za a bukaci a fasara wannan haka "hallakar da idanun ka." amma in an ambaci idanu, to ya yiwu a fasara shi "hallakar da su."
"kawar da shi"
"ka rasa ɗaya daga gaɓoɓin jikinka"
AT: "da Allah ya jefa dukka jikinka a gidan wuta"
hannun na a matsayin duk aikin da jikin mutum ke yi.
AT: "Allah ya kuma ce" ko "Musa ya kuma faɗa"
Wannan na nufin sakin mata.
"dole ya bayar"
mutumin da ya saki matarsa ba a hanyar da ta dace ba shi ne ya "mai da ita mazinaciya." A al'adu da yawa, ba damuwa ta sa ke aure, amma idan sakin ba a hanyar da ta dace ba to wannan auren zina ce.
AT: "bayan mai gidan ta ya sake ta" ko "sakakkiya matar"
"ku kuma" ko "ga wani misali. ku"
AT: "Allah ya faɗa wa mutanen zamanin da ya wuce" ko "Musa ya faɗa wa kakani tun da daɗewa"
"kada ka ɗauka alkawarin yin abu sa'an anan ka ki yi. Amaimako sai ka aikata abu da ka ɗau alkawari ga Ubangiji cewa za ka yi"
A nan Yesu na nufin cewa kada wanda suke ɗaukan alkawari ko faɗin gaskiya su rantse da wani abu. Wasu suna koyar cewa idan mutum ya rantse da Allah to wajibi ne ya cika, amma idan rantsuwar ga wani abu ne kamar samaniya ko ƙasa, to ba shi da wani illa sosai idan bai cika ba. Yesu na cewa rantsuwa da samaniya ko ƙasa ko Urshalima na da muhimminci ɗaya da rantsuwa da Allah, domin Allah ne ke da dukka abubuwa.
"kada ku ɗauki rantsuwa ko kadan" ko "kada ku rantse da kowani abu"
Domin Allah na mulki da ga sama. Yesu na maganar sama kamar sama kursiyi ne. AT: "da ga nan ne Allah ke mulki"
Wannan maganar na nufin cewa ƙasa ma na Allah ne. AT: "ta na kamar matashi ne da sarki ke sa ƙafarsa"
"domin ita ce birnin Allah, babban Sarki"
Yesu na magana da tarin mutane game da abun da yakamata su yi a matsayinsu na mutane. Duk wurin da wannan kalmar ya fito a matsayin mutum daya ne, amma za a iya fasara su a matsayin mutane dayawa.
Wannan na nufin ɗaukan alkawari. duba yadda aka fasara wannan a 5:34.
"Idan kana nufi I, ce I, idan kuma kana nufi a'a, ce a'a."
shariyar Musa ya yardar wa mutum ya yi lahani ga mutum ta hanyar da wancan mutumin ya cũtar da shi, amma ba fiye ba.
"mugun mutum" ko "wanda ke cũtar ka"
zagi ne a al'adar garin Yesu a mare mutum a kuncisa. Kamar yadda ido da hannu ke da muhimminci haka kunci dama ke da muhimminci, babbban zagi ne a mare mutum a kuncinsa.
mari da bayan hannu
"yardar masa ya mari ɗayan kuncin kuma"
Ana sa "tuguwa" a jiki ne, kamar riga mai nauyi. "mayafi" kuwa ya fi taguwa daraja, ana sa wannan akan taguwa ne domin dumi, kua akan yi amfani da shi kamar bargo wajen barci.
"ka kuma ba mutumin"
"Ko wanene." mahalin wannan maganar na nuna cewa ya na magana ne game da sojojin Roma.
Wannan na nufin takawa dubu, domin wannan ne iyakar tafiyar da sojan Roma ke da ikon tilasta wani ɗauka masa abu bisa ga doka. Idan ba a gane kalmar "mil" sosai ba, ana iya fasara wannan kamar "kilomita" ko "bisa nisa."
wannan na nufin ga wanda ya tilasta ka yin tafiya.
"yi tafiyar da ya tilasta maka, ka kuma kara wani mil." Idanba a gane kalmar "mil" ba, yi amfani da fasarar "kilomita biyu" ko kuma "hada nisar tafiyar sau biyu."
"kada ka hana ba da rance." AT: "rantar wa"
Anan ba wani makwabci ta musamman ne kalmar nan "makwabci" ke nufi ba, amma ko ma wani ɗan al'umma ko mutane. Waɗannan mutanen ne yawanci mutum yakan yi marmarin yin masu alheri ko a kalla ya yarda ya bi da su da kyau. AT: "'yangarinka" ko kuma "waɗanda suke mutanenka"
Ya fi kyau a fasara " 'ya'ya" a yadda harshe ku ke amfani da kalmar a kiran 'ya'yan wani mutum.
Wannan muhimmin laƙani ne na Allah.
Yesu yayi amfani da tambaya dommin ya koyad da mutanen cewa idan masoyansu kadai suke ƙauna, ai ba wani muhimmin abu ne da Allah zai saka musu ba. AT: "Gama in kuna ƙaunar iyakar wanɗanda ... ba ku samu ko wani lada ba."
Yahudawa na duban masu karɓar haraji a matsayin masu zunubi ƙwarai. Yesu yayi amfani da wannan tambaya ya tunashe su cewa ai ko masu karɓar haraji ma suna ƙaunar masoyansu.
Yesu yayi amfani da tambaya dommin ya koyad da mutanen cewa idan 'ya'uwansu kaɗai suke gayarwa, ai ba wani muhimmin abu ne da Allah zai saka musu akai ba. AT: "Idan 'ya'uwanku kaɗai kuke gayarwa, ba kuwa yin komai fiye da waɗansu."
Wannan hanyar nuna marmari ne domin lafiyar mai jin.
Yahudawa na duban al'ummai a matsayin masu zunubi sosai. Yesu ya yi tambaya ya tunashe su cewa ai al'ummai ma suna gai da 'yan'uwansu. AT: "ai ko al'ummai suna gai da mutanensu." Dubi:
1Ku yi hankali kada ku yi ayyukan adalcinku gaban mutane domin su ganku, idan kun yi haka, ba za ku sami sakamako a wurin Ubanku da yake sama ba. 2Saboda haka, in za ku yi sadaka, kada ku busa kaho yadda munafukai suke yi a majami'u da kuma akan tituna domin mutane su yabesu. Gaskiya ina gaya maku, sun samu ladansu.3Amma in za ku yi sadaka, kada hannunku na hagu ya san abin da hannunku na dama yake yi, 4domin sadakarku ta zama a asirce. Ubanku kuwa da yake ganin abin da ake yi a asirce, zai saka maku.5Sa'adda za ku yi addu'a kuma, kada ku zama kamar munafukai, domin sun cika son yin addu'a a tsaye a majami'unsu da kuma a gefen tituna, domin mutane su gansu. Gaskiya ina gaya maku, sun sami ladarsu kenan. 6Amma ku, idan za ku yi addu'a, sai ku shiga cikin daki. Ku rufe kofa, ku yi addu'a ga Ubanku wanda yake a asirce, Ubanku kuwa da ke ganin abin da ake yi a asirce, zai saka maku. 7Idan za ku yi addu'a, kada ku yi ta maimaici marar anfani, kamar yadda al'ummai suke yi, domin a tunanin su za a saurare su saboda yawan maganganunsu.8Domin haka, kada ku zama kamarsu, domin Ubanku ya san bukatar ku tun kafin ku roke shi. 9Saboda haka sai ku yi addu'a kamar haka: 'Ubanmu da ke sama, bari a tsarkake sunanka. 10Bari mulkinka shi zo. Bari nufinka ya yiwu a duniya kamar yadda ake yi a sama.11Ka ba mu yau abincinmu na kullum. 12Ka gafarta mana basussukanmu, kamar yadda mu ma muke gafarta ma wadanda muke bi bashi. 13Kuma kada ka kawo mu cikin jaraba, amma ka kubutar da mu daga Mugun.' 114Domin in kun yafe wa mutane laifuffukansu, Ubanku na Sama shima zai yafe maku. 15In kuwa ba ku yafe wa mutane laifuffukansu ba, Ubanku ma ba zai yafe muku laifuffukanku ba."16Haka kuma, in za ku yi azumi, kada ku zama da fuska kamar masu makoki yadda munafukai ke yi, domin sukan yankwane fuskokinsu, domin su bayyana ga mutane kamar suna azumi. Gaskiya, ina gaya maku, sun sami ladansu ke nan. 17Amma in kuna azumi, ku shafa mai a ka, ku kuma wanke fuska, 18don kada mutane su gane kuna azumi, sai dai Ubanku da yake a asirce. Kuma Ubanku da ke ganin abinda ke a asirce, zai saka maku."19"Kada ku tara wa kanku dukiya a duniya, inda asu da tsatsa ke batawa, inda barayi kuma ke fasawa su yi sata. 20Maimakon haka, ku tara wa kanku dukiya a sama, inda babu asu da tsatsa da za su bata, inda kuma ba barayi da za su fasa su yi sata. 21Domin inda dukiyar ka take, a nan zuciyar ka ma take.22Ido shi ne fitilar jiki. Saboda haka, idan idonka na da kyau, dukan jiki na cike da haske. 23Amma in idonka na da lahani, dukan jiki na cike da duhu. Saboda haka, in hasken da yake cikinka duhu ne, ina misalin yawan duhun! 24Ba mai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya, ko kuma ya amince wa dayan ya raina dayan. Ba dama ku bauta wa Allah da kuma dukiya.25Saboda haka ina gaya maku, kada ku damu a kan rayuwarku, game da abin da za ku ci, da abin da za ku sha- ko kuwa jikinku, abin da za ku yi tufafi da shi. Ashe rai bai fi abinci ba, jiki kuma bai fi tufafi ba? 26Ku dubi tsuntsayen da ke sararin sama. Ai, ba su shuka, balle girbi, ba su kuma tarawa a cikin rumbuna, amma Ubanku na Sama na ciyar da su. Ashe, ba ku fi su martaba ba?27Kuma wanene a cikinku, don damuwarsa, zai iya kara ko taki ga tsawon rayuwarsa? 28To, don me kuke damuwa a kan tufafi? Ku dubi furannin jeji, yadda suke girma. Ba su aiki, kuma ba su sakar kaya. 29Duk da haka ina gaya maku, ko Sulaimanu ma, cikin dukan daukakar sa bai yi ado kamar daya daga cikin wadannan ba.30Idan Allah yayi wa ciyawar jeji ado, wadda yau tana wanzuwa, gobe kuwa a jefa ta cikin murhu, ina misalin adon da za ya yi maku, ya ku masu karancin bangaskiya? 31Don haka kada ku damu, kuna cewa, 'Me za mu ci? ko, Me za mu sha?' ko kuwa, 'Wadanne tufafi za mu sa?'32Ai, al'ummai ma suna neman dukan irin wadannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa ya san kuna bukatarsu. 33Amma ku nemi mulkinsa da farko da adalcinsa, kuma dukan wadannan abubuwa za a baku. 34"Saboda haka kada ku damu don gobe, ai, gobe za ta damu da kanta. Kowace rana ta na cike da wahalarta".
Yesu ya ci da koyar da almajiransa a cikin wa'azinsa akan dutse, wadda ya fara a Matiyu 5:3. A wannan sashi, Yesu na magana game da "ayyukan adalci" na, sadaka, addu'a, da yin azumi.
Yesu na magana da taron jama'a game da abun da yakamata su yi a matsayinsu na mutane. Duk wurin da wannan kalmar ya fito a matsayin mutum daya ne, amma za a iya fasara su a matsayin mutane dayawa.
Wannan na nuna cewa waɗanda suka ga wannan mutumin za su girmama shi. AT: a gaban mutane domin su girmama ka akan abun da ka yi"
Wannan muhimmin laƙani ne na Allah.
Wannan maganar na nufin aikata abu da niyyar jawo hankalin mutane. AT: "kada ka jawo hankalin mutane a gare ka kamar wani mai busa ƙaho da ƙarfi a cikin jama'a"
"Ina faɗi muku gaskiya." Wannan maganar na nuna muhimmanci abun da Yesu zai faɗa nan gaba.
Wannan maganar na nufin "asiri gaba ɗaya." Kamar yadda yawanci loƙaci hannaye suna aiki tare, ɗayan hannun na sanin me ɗayan hannun ke yi, kada ma ka yarda mafi kusa da kai su sani a sa'ad da kana bayarwa ga matalauta.
AT: "kana iya bayar wa matalauta ba tare da sanin mutane ba"
Wannan na nuna cewa waɗanda suka gan su girmama su. AT: "domin mutane su gan su, su kuma girmama su"
"ka kebe wani wuri ka je" ko "ka je inda ka ke kai kadai"
Mai yiwuwa ana nufi 1)ba wanda ke iya ganin Allah. AT: " Uba, wanda baya ganuwa" ko 2) Allah na tare da mai yin addu'ar a kebeben wuri. AT: " Uban, wanda ke tare da ku a asirce"
"Ubanku zai ga abun da ku ke yi a asirce da"
Mai yiwuwa ana nufi 1) maimaitawar ba amfani. AT: "kada ku yi tsayuwar banza kuna ta maimaitawa" ko 2) kalmomin ko maganar ba su da ma'ana. AT: kada ku tsaya kuna ta maimaita kalmomi marasa ma'ana"
AT: "allolin karyarsu za su ji su"
Wannan shi ne farkon addu'ar, Yesu kuma ya na koyar wa mutanen yadda za su kira Allah.
Anan "sunanka" na nufi Allah da kansa. AT: "bari kowa ya daraja ka"
A nan "mulki" na nufi shugabancin Allah a matsayin tsarki. AT: "Bari mulkin ka akan kowa da komai ya cika"
AT: "Bari duk abun da zai faru a duniya ya zama bisa ga nufinka, kamar yadda komai a sama ke faruwa"
A nan "abinci" na nufin kowani irin abinci.
A nan laifi na nufi zunubi.
Wannan na nufin wanda suka yi mana laifi.
AT: kada ba kar wani abu ya jarabce mu" ko "kada ka bar wani abu ya sa mu sha'awar zunubi"
AT: "in su yi muku laifi ...in ku yi wa Allah laifi" ko "in sun illatar da ku ...in kun aikata abun da zai sa Ubanku fushi"
munafukai ba sa wanke fuskar su, ko tsefe gashi. Suna yin haka ne da niyyar jawo hanklin mutane a kansu domin a ga cewa suna azumi, sai a daraja su.
"sa mai a gashin ka." Anan "shafe" kai na nufi yadda aka saba lura da gashi. Bai shafe komai game da "Almasihu" "shafafen" ba. Yesu na nufi cewa mutane kar su canja ko da suna azumi ko ba sa yi.
"wanda ke ganin abun da ka ke yi a ɓoye."Dubi yadda aka fasara wannan a 6:6.
arziki, abubuwan da mutum ke ba da dukka daraja
"inda asu da tsatsa ke lalatar da dukiya"
karamin ƙwaro ne da ke ɓata tufafi
abune mai launin ruwar ƙasa da ke fitowa akan ƙarfe
Wannan maganar na nufin aikata abu mai kyau a duniya domin Allah ya ba ka lada a sama.
Wannan na kwatanta idanu masu lafiya da ke sa mutum gani, da kuma idanu ma masu lahani da ke sa makanta. Wannan na nufi lafiyar ruhaniya. Yayudawa na amfani da kalmar "mumunar ido" a nufin haɗama. Ma'anar ita ce idan mutum ya mika kai gaba ɗaya ga Allah, kuma yana duban abubuwa yadda Allah ke yi, to yana yin abun da ke daidai. Idan mutum na haɗama, to ya na aikata abun da ba dai dai ba.
Wannan maganar na nufin cewa ido ne ke sa mutum gani kamar yadda fitila na taimakon mutum kallo a duhu. AT: kamar fitila, ido na sa ku ganin abubuwa da kyau"
Ya yiwu zai fi a fasara wannan cikin jam'i, "Idanu."
Wannan ba ya nufin sihiri. Yahudawa sun saba amfani da wannan a nufi wanda ke da haɗama.
"idan abun da yakamata ya kawo haske ga jiki ka ke sa duhu, to jikinka na cikin duhu baki ɗaya"
dukka waɗannan maganar na nufin abu ɗaya ne. Suna jaddada cewa mutum ba zai iya so Allah ba ya kuma amince masa ba sanan kuma yaso kudi a lokaci ɗaya ba.
"ba za ka iya ƙaunar Allah da kudi a lokaci guda ba"
Wannan na nuna muhimmanci abun da Yesu zai faɗa a nan gaba.
Yesu na magana da taron jama'a game da abubuwan da yakamata a matsayin su na mutune su yi da wanda bai kamata su yi ba.
Yesu yayi amfani da tambaya don ya koyar da mutanen. AT: " A fili ya ke cewa rayuwa ya fi abun da kuke ci, jiki kuma ya fi abun da za ku sa." ko "A sarari ya ke, akwai abubuwa game da rayuwa fiye da abinci, kuma akwai abubuwa game da jiki da sun fi sa tufafi."
wurin ma'ajiyan abinci
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya koyar da mutanen. AT: "A fili ya ke, kun fi tsunsaye martaba."
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya koyar da mutanen. Anan "ƙara taƙi ɗaya ga tsawon rayuwarsa" na nufin ƙarin lokaci na zaman rayuwar mutum. AT: "Babu ko ɗayanku, ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara shekaru ga rayuwarsa. ba za ka iya ƙara ko minti ɗaya a rayuwarka ba! don haka kada ka damu game da abubuwan da ka ke bukata."
taƙi ɗaya auni ne kasa da rabin mita.
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya koyar wa mutanen. AT: "kada ku damu game da abun da zaku sa."
"dubi"
Yesu na magana game da tsire-tsire jeji kamar su mutane ne masu sa tufafi. Adon tsire-tsire jeji na nufi tsire-tsiren na da kyau da launin furanne.
wannann wani irin fure ne a jeji.
AT: "ba sa ado kamar yadda tsire-tsiren ke da kyau"
Yesu ya cigaba da magana game da tsire-tsire jeji kamar su mutane ne da ke sa tufafi. Adon tsire-tsiren jeji na nufin furanni masu kyau da launi da ke fitowa tsire-tsire.
Idan harshen ku na da sunan "ciyawa" dabam da "tsire-tsire jeji" da aka ambata a ayan baya, a yi amfani da shi anan.
Yahudawa a wacan zamani suna amfani da ciyawa a hura wutar dafa abinci. AT: "wani na jefa shi a cikin wuta" ko "wani na ƙona shi"
Yesu yayi amfani da tambaya ya koyar da mutane cewa Allah zai tanada musu abun da suke bukata. AT: "lalle ne ya tanada muku tufafi ... bangaskiya?
"ku da kuke da karamin bangaskiya." Yesu ya yi magana da mutanen haka domin suna ta da hankalin su game da tufafi, wannan ya nuna cewa suna da ƙaranci bangaskiya.
"domin dukka wannan"
A wannan jimla, "tufafi" na a matsayin mallakar dũkiya. AT: "Wani mallaka za mu samu"
"domin Al'ummai sun damu da abun da za su ci, su sha, da su kuma sa"
Yesu na nufin cewa Allah zai sa su samu duk abun da suke bukata.
A nan "mulki" na nufin shugabanci Allah a matsayin tsarki. AT: "ku dame kanku da bautar Allah, wanda shi ne tsarkin ku da kuma aikata abun da ke daidai"
AT: "Allah zai tanadar muku dukkan waɗannan abubuwa"
Yesu na managa game da "gobe" kamar wani mutum ne da zai iya damuwa. Yesu na nufin cewa mutum zai samu iyakar abubuwa da zai damu da su sa'ad da goben ta kai.
1Kada ku yi hukunci, domin ku ma kada a hukunta ku. Domin da irin hukuncin da ku kan hukunta da shi za a hukunta ku. 2Mudun da kukan auna, da shi za a auna maku.3Don me kake duban dan hakin da ke idon dan'uwanka, amma ba ka kula da gungumen da ke naka idon ba? 4Ko kuwa yaya za ka iya ce wa dan'uwanka, 'Bari in cire maka dan hakin da ke idon ka,' alhali ga gungume a cikin naka idon? 5Kai munafiki! Ka fara cire gungumen da ke idonka, sa'annan za ka iya gani sosai yadda za ka cire dan hakin da ke idon dan'uwanka.6Kada ku ba karnuka abin da ke tsattsarka. Kada kuma ku jefa wa aladu, lu'u lu'anku. Idan ba haka ba za su tattake su a karkashin sawunsu, su kuma juyo su kekketa ku.7Roka, kuma za a ba ku. Nema, kuma za ku samu. Kwankwasa kuma za a bude maku. 8Ai duk wanda ya roka, zai karba, kuma duk wanda ya nema zai samu, wanda ya kwankwasa kuma za a bude masa. 9Ko, kuwa wane mutum ne a cikin ku, dan sa zai roke shi gurasa, ya ba shi dutse? 10Ko kuwa in ya roke shi kifi, zai ba shi maciji?11Saboda haka, idan ku da ku ke miyagu, kun san yadda za ku ba da kyautai masu kyau ga 'ya'yanku, ina kimanin yadda Ubanku na sama zai ba da abubuwa masu kyau ga duk wadanda suke rokon sa? 12Saboda haka, duk abinda ku ke so mutane su yi maku, ku ma sai ku yi masu, domin wannan shi ne dukan shari'a da koyarwar annabawa.13Ku shiga ta matsattsiyar kofa, don kofar zuwa hallaka na da fadi, hanyar ta mai saukin bi ce, masu shiga ta cikin ta suna da yawa. 14Domin kofar zuwa rai matsattsiya ce, hanyar ta mai wuyar bi ce, masu samun ta kuwa kadan ne.15Ku kula da annabawan karya, wadanda su kan zo maku da siffar tumaki, amma a gaskiya kyarketai ne masu warwashewa. 16Za ku gane su ta irin "ya'yansu. Mutane na cirar inabi a jikin kaya, ko kuwa baure a jikin sarkakkiya? 17Haka kowanne itace mai kyau yakan haifi kyawawan 'ya'ya, amma mummunan itace kuwa yakan haifi munanan 'ya'ya.18Kyakkyawan itace ba zai taba haifar da munanan 'ya'ya ba, haka kuma mummunan itace ba zai taba haifar da kyawawan 'ya'ya ba. 19Duk itacen da ba ya ba da 'ya'ya masu kyau, sai a sare shi a jefa a wuta. 20Domin haka, ta irin 'ya'yansu za a gane su.21Ba duk mai ce mani, 'Ubangiji, Ubangiji,' ne, zai shiga mulkin sama ba, sai dai wanda ya yi nufin Ubana da yake cikin sama. 22A ranar nan da yawa za su ce mani, 'Ubangiji, Ubangiji,' ashe ba mu yi annabci da sunanka ba, ba mu fitar da aljanu da sunanka ba, ba mu kuma yi manyan ayyuka masu yawa da sunanka ba?' 23Sa'annan zan ce masu 'Ni ban taba saninku ba! Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta!'24Saboda haka, dukan wanda yake jin maganata, yake kuma aikata ta, za a kwatanta shi da mutum mai hikima, wanda ya gina gidan sa a bisa dutse. 25Da ruwa ya sauko, ambaliyar ruwa ta zo, iska ta taso ta buga gidan, amma bai fadi ba, domin an gina shi bisa dutse.26Amma duk wanda ya ji maganar nan tawa, bai aikata ta ba, za a misalta shi da wawan mutum da ya gina gidansa a kan rairayi. 27Ruwa ya sauko, ambaliyar ruwa ta zo, sai iska ta taso ta buga gidan. Sai kuma ya rushe, ya kuwa yi cikakkiyar ragargajewa."28Ya zama sa'adda Yesu ya gama fadin wadannan maganganu, sai taro suka yi mamakin koyarwarsa, 29Domin yana koya masu da iko, ba kamar marubuta ba.
Yesu ya cigaba da koyar da almajiran sa cikin huɗuban da ya fara a 5:3 akan Dutse.
Yesu na magana da taron jama'a game da abubuwan da yakamata a matsayin su na mutune su yi da wanda bai kamata su yi ba.
An nuna cewa "hukunci" anan na ba da ma'anar "mummunar kushewa" ko "ɗore laifi." AT: "kada ku yi wa mutane mummunar kushewa"
AT: "Allah ba zai yi muku mummunar kushewa ba"
tabbata cewa mai karatu ya gane maganar 7:2 na bisa abun da Yesu ya faɗa a 7:1.
AT: "Allah zai hukunta ku ta hanyar da kuka hukunta wasu"
Mai yiwuwa ana nufi 1) wannan ita ce yawan hukuncin da aka bayar ko 2) wannan shi ne ma'auni da ake amfani da shi wajen hukunci.
AT: "Allah zai auna muku"
Yesu ya yi amfani da tambaya ya tsautawa mutanen domin suna mai da hankali a zunubin wasu, ba sa kula da nasu zunubin. AT: kuna duban ... idon ɗan'uwa, amma ba ku lura da gungumen da yake a naku idon." ko "kada ku dubi ... idon ɗan'uwa, kuma kula da gungumen da yake naka idon."
Wannan na nufin ɗan laifi da ɗan'uwa maibi ya aikata mara muhimmanci.
"yayi" ko "sartse" ko "ɗan ƙura." Yi amfani da sunan ɗan karamin abu da ya saba fadi a idonun mutum.
duk inda aka yi amfani da kalmar "ɗan'uwa" a 7:3-5, ana nufin ɗan'uwa maibi ne ba ɗan'uwan haifuwa ko maƙwabci ba.
Wannan na nufin babban laifin da mutum a aikata. Gungume ba iya shigan idon mutum, Yesu ya yi amfani da wannan domin ya jaddada cewa mutum ya mayar da hankalinsa akan babban laifinsa kafin ya shiga harkar kananar laifofin wani.
sashi ne mafi girma a itacen da aka yanka
Yesu yayi amfani da wannan tambaya domin ya kalubalence mutane su sa hankalinsu a nasu zunuben kafin su sa hankalin su a zunuben wani. AT: "kada ka ce ... idon ka."
Yahudawa suna duban waɗannan dabobi da rashin tsabta, kuma Allah ya ce dasu kada su ci waɗannan dabobin. Suna a matsayin mugayen mutane wanda ba sa daraja tsarkakan abubuwa. Zai fi kyau a fasara waɗannan kalmomi yadda suke.
waɗannan suna kamar duwatsune ne masu daraja ko dusten ado. Suna a matsayin sanin Allah ko kuma kowani abu mai daraja.
"aladun kuwa su tattaka"
"karnukan kuwa su juyo su kyakketa"
Waɗannan na nufin addu'a ga Allah. A sifar aikatau, wannan jimlar na nuna cewa mu cigaba da addu'a har sai ya amsa. In a harshenku akwai kalmar da ke bayyana cigaba da yin abu akai-akai to ayi amfani da shi.
tambaye abu daga wurin wani, a wannan yanayi kuwa Allah ne
AT: "Allah zai baku abun da ku ke bukata"
neman wani, a wannan yanayi kuwa Allah ne
ƙwanƙwasa ƙofa rokone cikin kaskanci domin wadda yake cikin gida ya bude ƙofa. In ƙwanƙwasa ƙofa ba hanyar nuna kaskanci bane ko ma ba ayi a harshen ku, to ayi amfani da hanyar da mutane suke roƙa a buɗe musu ƙofa cikin kaskanci. AT: "gaya wa Allah kana so ya buɗe ƙofa"
AT: "Allah zai buɗe muku"
Yesu na amfani tambaya ya koyar da mutanen. AT: "Ba bu kowa a cikin ku ... dutse."
Wannan na nufi kowani irin abinci. AT: "abinci"
A fasara waɗannan sunaye yadda suke.
Yesu ya sake yin tambaya domin ya koyar da mutanen. A gane cewa har yanzu Yesu na magana game da Uba ne da ɗansa. AT: "Kuma ba bu ko ɗayan ku wanda in ɗansa ya roke shi kifi sai ya bashi maciji."
Yesu na amfani da tambaya ya koyar da the mutanen. AT: "ai lalle ne Ubanku na sama zai ba ... shi."
Wannan muhimmin laƙani ne na Allah.
kowace hanya kuke biɗar mutane su aikata muku"
Anan "attaura" da "annabawa" na nufin abun da Musa da annabawa suka rubuta. AT: "domin wannan shi ne Musa da annabawa suka koyar a cikin Nassi"
Wannan na ba da hoton masu tafiya akan hanya kuma suna shige wani kofa zuwa masarauta. wani masarautar na da saukin shiga, ɗayan na da wahalar shiga.
Ya yiwu zai bukaci a mayar da wannan zuwa ƙashen aya 14. "Saboda haka, ku shiga ta ƙunƙuntar ƙofa."
Mai yiwuwa ana nufi 1) "hanyar" na nufin in da za a bi zowa ƙofar masrautar, ko 2) "ƙofar" da "hanyar" duk na nufin ƙofar shiga masarautar.
Ana iya fasarar waɗannan sunayen da aikatau. AT: "zuwa wurin da mutane ke mutuwa ...zuwa wurin da mutane ke rayuwa"
"tsare kanku daga"
Wannan maganar na nufin cewa annabawan ƙarya na zuwa kamar masu gaskiya ne kuma suna so su taimake mutane, amma asilinsu miyagu ne kuma za su illatar da mutane.
Wannan na nufin ayyukan mutum. AT: "Kamar yadda akan gane itace ta irin 'ya'yan da take bayar, haka ma ta irin ayyukansu ake gane su annabawan ƙarya ne"
Yesu na amfani da tambaya ya koyar da mutanen. Yakamata mutanen su san amsa a'a ne. AT: "Mutane ba sa ciran ... kaya."
Yesu ya cigaba da misalta annabawa gaske ta wurin kyawawa ayyukansu da kalmominsu da 'ya'yan itace.
Yesu ya cigaba da misalta annabawa ƙarya ta wurin munanan ayyukansu da 'ya'yan itace.
Yesu ya cigaba da amfani da 'ya'yan itace a misalin annabawan ƙarya. Anan, yana faɗin iyakan abun da zai faru da munanan itace ne. Ana nufin cewa haka nan ma zai faru da annabawan ƙarya.
AT: "mutane na sare su kuma ƙona"
Kalmar "su" na iya zama annabawan ko itacen. Wannan na nuna cewa 'ya'yan itace da ayyukan annabawa ke bayyana ko su na da kyau ko babu. In ya yiwu, a fasara wannan ta hanyar da zai nuna cewa ana magana game da itace da annabawa.
A nan, "mulkin sama" na nufin sarautar Allah a matsayin tsarki. A littafin Matiyu ne kadai aka faɗi wannan maganar. in ya yiwu, a sa kalmar "sama" a fasarar, AT: "zai kasance tarw da Allah a sama a sa'ad da ya nuna kansa a matsayin tsarki"
"wanda yake aikata abun da Ubana na cikin sama yake so"
Yesu ya ce "ranar nan" domin ya san masu sauraronsa za zu gane yana magana game da ranar shariya. Za ka iya fasara shi haka "ranar shariya" inda masu karatu ba za su gane wace rana ne ba.
Mutanen suna amfani da tambaya domin su jaddada cewa sun aikata waɗannan abubuwa. AT: " mun yi annabci ... mun fitar da aljannu ... mun yi ayyukan al'ajabi masu girma da yawa."
Kalmar "mu" anan bai shafi Yesu a ciki ba.
ai yiwuwa ana nufi 1) "ta wurin ikon ka" ko "ta wurin karfin ka" ko 2) domin muna aikata abun da kake so mu aikata" ko 3) "domin mun roƙe ka ikon mu aikata su"
"al'ajibai"
Wannan na nufin mutumin baya tare da Yesu. AT: "Kai ba mabiyi na ba ne" ko "ba ni da wata harka da kai"
"Domin wannan"
A nan "kalmomi" na nufin abun da Yesu ya faɗa.
Yesu ya kwatanta masu jin maganarsa kamar mutumin da ya gina gidansa inda ba wanda zai iya hallakar.
Wannan dutse ne da shumfide a ƙasa, ba babban dutse mai tudu ba ko.
AT: "ya gina ta"
Yesu ya cigaba da kwatanci da yayi a ayan baya. Ya misalta waɗanda ba sa biyyaya da maganarsa da wawayen magina. Wawa ne kadai zai gina gida akan rairayi, inda ruwan sama, ambaliya, da iska na iya share wa.
Yi amfani da kalmar da akan kira a harshenku idan ana so a ce gida ya rushe.
Ruwar sama, da ambaliya, da kuma iskan sun hallakar da gidan gaba ɗaya.
Wannan maganar ya canja labarin daga koyar Yesu zuwa abun da ya faru na gaba. AT: "sa'adda" kon "bayan haka"
A fili ya ke cewa a 7:29 ba mamakin abun da Yesu ya koyar kadai suke yi ba amma har da yadda yake koyarwar ma. AT: "mamakin yadda yake koyarwa"
1Da Yesu ya sauko daga dutsen, sai taro masu yawa suka bi shi. 2Sai wani kuturu ya zo gunsa ya yi masa sujada, ya ce, "Ubangiji, in dai ka yarda, za ka iya tsarkake ni." 3Yesu ya mika hannunsa ya taba shi, ya ce, "Na yarda, ka tsarkaka." Nan da nan aka tsarkake shi daga kuturtarsa.4Yesu ya ce masa, 'Ka tabbata, ba ka gaya wa kowa komai ba. Sai dai ka je ka nuna kan ka ga firist, ka kuma bayar da baiko da Musa ya umarta domin shaida garesu?5Da Yesu ya shiga kafarnahum, sai wani hafsa ya zo gunsa ya roke shi, 6Ya ce, Ubangiji, bawana na kwance shanyayye a gida, yana shan azaba kwarai." 7Yesu ya ce masa, "Zan zo in warkar da shi."8Sai hafsan, ya ce, "Ubangiji, ban isa har ka zo gida na ba, amma sai ka yi magana kawai, bawana kuwa zai warke. 9Domin ni ma ina karkashin ikon wani ne, ina kuma da sojoji a karkashina, sai in ce wa wannan, 'je ka,' sai ya je, wani kuma in ce masa, 'zo,' sai ya zo, in ce wa bawa na, 'yi abu kaza,' sai ya yi," 10Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki, har ya ce wa mabiyansa, "Gaskiya, ina gaya maku, ko a cikin isra'ila ban taba samun bangaskiya mai karfi irin wannan ba.11Na gaya maku, da yawa za su zo daga gabas da yamma, su zauna cin abinci tare da Ibrahim da Ishaku, da Yakubu a cikin mulkin sama. 12Amma 'ya'yan mulkin kuwa sai a jefa su cikin matsanancin duhu. Can za su yi kuka da cizon hakora." 13Yesu ya ce wa hafsan, "Je ka! Bari ya zamar maka gwargwadon bangaskiyar da ka yi," A daidai wannan sa'a bawansa ya warke.14Da Yesu ya shiga gidan Btrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance da zazzabi. 15Yesu ya taba hannunta, zazzabin ya sake ta, ta kuma tashi ta fara yi masa hidima.16Da maraice ya yi, sai mutanen suka kakkawo wa Yesu masu aljanu da yawa. Da magana kawai ya fitar da aljanun, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya. 17Ta haka kuwa maganar annabi Ishaya ta samu cika cewa, "Shi da kansa ya debe rashin lafiyar mu, ya dauke cututtukan mu."18Sa'adda Yesu ya ga taro masu yawa kewaye da shi, sai ya ba da umarni su tafi su koma wancan hayi na tekun Galili. 19Sai wani marubuci ya zo ya ce masa, "Malam, zan bi ka duk inda za ka je." 20Yesu ya ce masa, "Yanyawa suna da ramukansu, tsuntsayen sama kuma da shekunan su, amma Dan mutum ba shi da wurin da zai kwanta."21Wani cikin almajiran ya ce masa, "Ubangiji, ka bar ni tukuna in je in binne mahaifina." 22Amma Yesu ya ce masa, "Bari matattu su binne matattunsu."23Da Yesu ya shiga jirgi, almajiransa suka bi shi. 24Sai ga wata babbar iska ta taso a tekun, har rakuman ruwa suka fara shan kan jirgin. Amma Yesu yana barci. 25Sai almajiran sa suka je suka tashe shi, suka ce, "Ubangiji, ka cece mu, za mu hallaka!"26Yesu ya ce masu, "Don me kuka firgita haka, ya ku masu karancin bangaskiya?" Sa'annan ya tashi, ya tsauta wa iskar da tekun. Sai wurin gaba daya ya yi tsit. 27Mutanen suka yi al'ajibi, suka ce, "Wanne irin mutum ne wannan, wanda har iska da teku ma suke masa biyayya?".28Da Yesu ya zo daga wancan hayin a kasar Garasinawa, mutane biyu masu al'janu suka fito suka same shi. Suna fitowa daga makabarta kuma suna da fada sosai, har ma ba mai iya bin ta wannan hanya. 29Sai suka kwala ihu suka ce, "Ina ruwanka da mu, kai dan Allah? Ka zo nan ne ka yi mana azaba tun kafin lokaci ya yi?"30To akwai wani garken aladu masu yawa na kiwo, babu nisa da su. 31Sai al'janun suka roki Yesu suka ce, "In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan." 32"Yesu ya ce masu, "To, ku je." Sai aljanun suka fita, suka shiga cikin aladun. Sai kuwa duk garken suka rugungunta ta gangaren, suka fada cikin tekun, suka hallaka a ruwa.33Mutanen masu kiwon aladun suka gudu, suka shiga gari, suka yi ta ba da labarin komai da komai, musamman abin da ya faru da masu al'janun. 34Sai duk jama'ar gari suka fito su sami Yesu. Da suka gan shi, suka roke shi ya bar kasarsu.
Wannan ne farkon sabon sashin labarin da ya kunsa labaran Yesu da ya warkad da mutane. Wannan kan magana ya cigaba har zuwa 9: 35.
"Bayan da Yesu ya sauko daga dutsen, taro masu yawa suka bi shi." Mai yiwuwa taron su na tare da mutanen da suke tare da shi a kan dutsen da kuma mutanen da ba sua tare da shi.
Kalmar "gani" na shirya mu ga sabon mutum a labarin. Harshenku na iya samin wata hanyar yin wannan.
"wani mutum da ke da kuturta" ko "wani mutum da ke da cuta"
Wannan alama ne na tawali'u da ladabi a gaban Yesu.
"idan ka na so." Kuturun ya san cewa Yesu ya na da ikon warkad da shi, amma bai san ko Yesu zai so ya taba shi ba.
A nan "tsarkake" na nufin warkewa da kuma iya yin rayuwa a cikin jama'a kuma. AT: "za ka iya warkad da ni" ko "don Allah ka warkad da ni"
Ta wurin fadan haka, Yesu ya warkad da mutumin.
"A wannan loƙacin aka tsarkake shi"
Sakamakon da Yesu ya ce "ka tsarkake" na nufin cewa mutumin ya warke. AT: "ya na da lafiya" ko "kuturtan ya bar shi" ko "kuturtan ya kare"
Wannan ya na nufin mutumin da Yesu ya warkad da shi.
"kada ka ce komai wa kowa" ko kada ka gaya wa wani cewa ni ne na warkad da kai"
Dokan Yahudawa ya bukaci mutumin ya nuna jikinsa da ya warke ga firist, wanda zai yarda mashi ya koma cikin gari, don ya yi zama da mutane.
Dokar Musa ya bukaci cewa duk wanda ya warke daga kuturta ya ba da baikon shaidan godiya ga firist. Mutane za su san cewa mutumin ya warke a loƙacin da firist ya karbi kyautan. A na tura kutare daga cikin gari, sai sun nuna cewa sun warke.
AT: 1) firistoci ko 2) dukka mutane ko 3) masu sokanan Yesu. Idan zai yiwu, yi amfani da wakilin suna da zai iya nufin kowane abu na wannan taron.
A nan sashin ya maso zuwa wani wuri da loƙaci dabam ya kuma faɗa game da yadda Yesu ya warkad da wani mutum.
A nan "shi" ya na nufin Yesu.
rashin iya motsi saboda cuta ko rashin motsi
"Yesu ya ce wa hafsan"
"Zan zo gidan ka in warkad da bawan ka"
Wannan ƙarin magana ne da na nufin cikin gidan. AT: "cikin gida na"
Anan "magana" na wakilcin umurni. AT: "ba da umurnin"
AT: "zai warke"
AT: "wanda ya na ƙarƙashin ikon wani dabam"
Zama a "ƙarƙashin" wani na nufin zama da ƙanƙancin muhimminci da kuma bin umurnin wani mai mafi muhimminci.
"Ina gaya maku gaskiyan." Wannan jumla na kara nanaci ga abin da Yesu ya faɗa.
Masu sauraran Yesu na iya yin tunani cewa Yahudawa a cikin Isra'ila, wadda sun ce su ne ''ya'yan Allah, za su sami babban bangaskiya fiye da kowa. Yesu ya na cewa ba daidai ba ne kuma bangaskiyar hafsan din ne ya fi.
A nan "ku" jam'i ce kuma ya na nufin "waɗanda suke bin shi" a cikin 8:10.
Yin amfani da "gabas" da "yamma" wata hanya ne na ce "ko ina." AT: "daga ko ina" ko "daga nesa a kowane jiha"
Mutane a wannan al'ada su na ƙwanciye sa'ad da su na cin abinci. Wannan jumla ya nuna cewa dukka waɗanda suke teburin yan iyali ne da abokai. Ana yawan maganan murna a cikin mulkin Allah kamar mutanen a wuri suna biki ne. AT: "zauna kamar iyali da abokai"
A nan "mulkin sama" na nufin mulkin Allah a matsayin sarki. An yi amfani da jumlar "mulkin sama" a cikin littafin Mata. In ya yiwu, bar "sama" a cikin juyinku. AT: "a lokacin da Allahn mu a sama ya nuna cewa shi sarki ne"
AT: "Allah zai jefar da 'ya'yan mulkin"
Jumlar " 'ya'yan" ƙarin magana ne da na nufin Yahudawa marasa bangaskiya na mulkin Yahudia. Akwai habaici anan domin za a jefar da "'ya'yan" a wuje sai a marabshe baki. AT: "waɗanda ya kamata sun yarda Allah ya yi mulki da su"
A nan "matsanancin duhu" ƙarin magana ne na wurin da Allah zai tura waɗanda sun ki shi. Wannan wuri ne da ya rabu daga Allah har abada. AT: "duhun wuri mai nesa daga Allah"
"cizon hakora" ayuka ne na alama, da na wakilcin tsananin bakin ciki da azaba. AT: "yin kuka da nuna tsananin azabarsu"
AT: "don haka zan yi maka"
AT: "Yesu ya warkad da bawan"
"a daidan loƙacin da Yesu ya ce zai warkad da bawan"
Mai yiwuwa almajiran su na tare da Yesu, abin duba a labarin na akan abin da Yesu ya faɗa da kuma yi, don haka za ku iya gabatar da almajiran idan ya kamata don hankali da ma'anar da ba daidai ba.
"mahaifiyar matar Bitrus"
Idan harshenku za su fahimci wannan ƙarin maganan da cewa zazzabi na iya tunani da kuma aikatuwa, za a iya juya wannan kamar "ta yi sauki" ko "Yesu ya warkad da ita."
"tashi daga gado"
Domin Yahudawa ba su yi tafiya ba ko su yi tafiya a ranar Asabar, "maraice" wannan na iya nufin bayan Asabar. Sun jira sai maraice don su kawo mutane wa Yesu. Ba sai kun ambaci Asabar ba sai dai ku yi hankali da ma'ana da ba daidai ba.
AT: "mutane dayawa da suke da aljanun" ko "mutane dayawa da aljanun su na mulki da su"
Anan "kalma" na matsayin umurni. AT: "Ya umurci aljanun su tafi"
AT: "Yesu ya cika annabcin da annabi Ishaya ya faɗa wa mutanen Israi'la"
Mata ya na faɗan abin da annabi Ishaya a faɗa. Waɗannan jumla biyu a takaice na nufin abu ɗaya kuma ya na nanata cewa ya warkad da dukka cututtukanmu. AT: "warkad da waɗanda suke da rashin lafiya"
An yi amfani da wannan kalma anan domin a sa alama a ainahin labarin. Anan Mata ya fara ba da sabon sashin labarin.
"ya gaya wa almajiransa"
Wannan na nufin bayan Yesu "ya ba da umarni" amma kafin ya shiga cikin kwalekwalen.
zuwa kowane wuri
Yesu ya amsa da wannan magana. Wannan na nufin cewa har dabban daji na da wurin hutawa.
Yanyawa dabba ne kaman karnuka. Suna cin tsuntsaye masu gida da kuma kananun dabbobi. Idan yanyawa ba sananne ne a garin ku ba, ku yi amfani da kalmar dabba kamar kare ko wani irin dabba mai fushi.
Yanyawa su na yin ramuka a kasa don su zauna a ciki. Yi amfani da kalma da ta dace a inda dabban da kun yi amfani a "yanyawa" suke zama.
Yesu ya na maganar kanshi.
Wannan na nufin wurin barci. AT: "ba wurin dake nasa da zai yi barci"
ba a bayyane ne ya ke ko mahaifin mutumin ya mutu kuma zai binne shi nan da nan ba, ko mutumin ya na so ya tsaya na dan tsawon loƙaci sai mahaifinshi ya mutu don ya iya binne shi. Ainahin maganan shi ne mutumin ya so ya yi wani abu dabam kafin ya bi Yesu.
Yesu ba ya nufin cewa matattu za su binne sauran matattu, "matattu." AT: 1) ƙarin magana ne ga waɗanda sun yi ƙusan mutuwa, ko 2) ƙarin magana ne na waɗanda ba su bin Yesu kuma matattu a ruhaniya. Ainahin maganan shi ne kada almajiri ya bar wani abu ya jinkirtad da shi daga bin Yesu.
"shiga kwalekwalan"
Yi ƙoƙari ku yi amfani da kalmomi ɗaya a "almajiri" da kuma "bi" da kuka yi amfani a cikin 8:21-22.
AT: "babbar hadari ta taso a tekun"
AT: "har rakuman ruwa suka sha kan jirgin"
AT: 1) da farko sun tashe Yesu sai suka ce, "Cece mu" ko 2) sa'adda sun ta da Yesu, su na cewa "Cece mu."
Zai yi kyau ku juya waɗannan tare. Mai yiwuwa almajiran su na nufin sun so Yesu ya cece su da kuma kansa daga nutsewa.
"za mu mutu"
Yesu ya na tsawta almajiransa da wannan tambaya mai zurfi. AT: "Kaɗa ku ji tsoro ... bangaskiya!" ko "Babu abin jin tsoro ... bangaskiya!"
"ku da kuke da karancin bangaskiya."Yesu ya yi wa almajiransa magana haka domin taraddadinsu akan hadarin ya nuna cewa suna da ƙarancin bangaskiya akanshi. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 6:30.
"Har iska da teku su na yi masa biyayya! Wanne irin mutum ne wannan?" Wannan tambaya ya nuna cewa almajiransa sun yi mamaki. AT: "Wannan mutum ba kamar kowane mutum ne da mun taba gani ba! Har iska da teku su na yi masa biyayya!
Ba abin mamaki ne mutum ko dabba ya yi biyayya ko rashin biyayya ba, amma abin mamaki ne iska da ruwa su yi biyayya. Wannan ƙarin magana ne da ke ƙwatanta abin halitta da na iya ji kamar mutane.
"ta hayin tekun Galili
An lakaɓa sunan kasar da sunar garin da ae kira da suna Gadara. (Dubi: Transalated names)
Aljannun da ke cikin waɗannan mutane biyu ɗin suna da zafi kwarai da gaske har da mutane kan guji ratsewa ta hanyar.
Aljannun sun yi amfani da tambaya amma sun haura wa Yesu kwarai da gaske. AT: "Kar ka damu da mu, ya "Ɗan Allah!"
wannan muhimmin laƙanin Yesu ne, wanda ya nuna dangantakarsa da Allah. (Dubi: duidelines_sonofgodprinciples)
A nan kuma, aljannun sun yi amfani da tambaya a cikin fushi. AT: "Kaɗa ka ketare dokar Allah tawurin tsananta mana kamin lokacin da Allah ya ayana mana!"
Ana nufin cewa al'janun sun san cewa Yesu zai fitar da su. AT: "Domin za ka fitar da mu"
Wannan dabam ne, ya na nufin al'janun kadai.
"Al'janun suka bar mutumin sai suka shiga cikin aladun"
"gangarawa da sauri"
"suka faɗi a cikin ruwan sun kuma nutse"
"kula da aladun"
AT: "abin da Yesu ya yi don ya taimake mutanen da al'janu sun mallaka"
Kalmar "gari" ƙarin magana ne na mutanen garin. Mai yiwuwa kalmar "duk" zuguici ne domin a nanata yadda mutane dayawa suka fito. Ba lallai ne kowane mutum ya fita ba.
"kasarsu"
1Yesu ya shiga jirgi ya haye ya je birninsa. 2Sai gashi, sun kawo masa wani mutum shanyayye kwance a tabarma. Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, "Da, ka yi farin ciki. An gafarta maka zunuban ka."3Sai wadansu marubuta suka ce a tsakaninsu, "Wannan mutum sabo yake yi." 4Yesu kuwa da yake ya san tunaninsu, yace, "Don me kuke mugun tunani a zuciyarku? 5Wanne ya fi sauki, a ce, 'An gafarta maka zunubanka,' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya'? 6Amma domin ku sani Dan mutum yana da ikon gafarta zunubai a duniya,..." Sai ya ce wa shanyayyen, "Tashi, ka dauki shimfidarka ka tafi gida."7Mutumin kuwa ya tashi ya tafi gida. 8Da taron suka ga haka sai suka yi mamaki, suka daukaka Allah, wanda ya ba mutane irin wannan iko. 9Da Yesu ya yi gaba, ya ga wani mutum mai suna Matiyu a zaune, yana aiki a wurin karbar haraji. Yace masa, "Ka biyo ni." Ya tashi ya bi shi.10Sa'adda kuma Yesu yake cin abinci a gida, sai ga masu karbar haraji da masu zunubi da yawa sun zo, sun zauna tare da shi da almajiransa. 11Da Farisawa suka ga haka, sai suka ce wa almajiransa, "Don me malamin ku ya ke ci tare da masu karbar haraji da masu zunubi?"12Amma da Yesu ya ji haka ya ce, "Ai, lafiyayyu ba ruwansu da likita, sai dai marasa lafiya. 13Sai ku fahimci ma'anar wannan tukuna, 'Ni kam, ina bukatar jinkai ba hadaya ba.' Ba domin in kira masu adalci su tuba na zo ba, sai dai masu zunubi.14Sai almajiran Yahaya suka zo wurinsa, suka ce, "Don me mu da Farisawa mu kan yi azumi a kai a kai, amma naka almajiran ba su yi?" 15Sai Yesu ya ce masu, "Masu hidimar buki za su yi bakin ciki tun ango yana tare da su? Ai, lokaci yana zuwa da za a dauke masu angon. A sa'annan ne fa za su yi azumi."16Babu mutumin da zai sa sabon kyalle a kan tsohuwar tufa, domin kyallen zai yage daga tufar, har ma yagewar ta fi ta da.17Mutane kuma ba su dura sabon ruwan inabi a tsofaffin salkuna. Idan sun yi haka, sai salkunan kuma su fashe inabin ya tsiyaye, sai salkunan su lalace. A maimakon haka, ana sa sabon inabi cikin sababbin salkuna, ta haka an tsirar da duka biyun kenan."18Yesu kuwa yana cikin yi masu magana sai ga wani shugaban jama'a ya zo ya yi masa sujada, ya ce, "Yanzun nan 'yata ta rasu, amma ka zo ka dora mata hannu, za ta rayu." 19Sai Yesu ya tashi ya bi shi tare da almajiransa.20Sai ga kuma wata mace wadda ta yi shakaru goma sha biyu tana zubar da jini sosai, ta rabo ta bayan Yesu, ta taba gezar mayafinsa. 21Domin ta ce a ran ta, "Ko da mayafinsa ma na taba, sai in warke." 22Sai Yesu ya juya, ya gan ta ya ce, '"Yata, ki karfafa. Bangaskiyarki ta warkar da ke." Nan take matar ta warke.23Da Yesu ya isa gidan shugaban jama'ar, ya kuma ga masu busar sarewa da taro suna ta hayaniya sosai. 24Sai ya ce, "Ku ba da wuri, ai, yarinyar ba matacciya take ba, barci ta ke yi." Sai suka yi masa dariyar raini.25Sa'adda aka fitar da taron waje, ya shiga ya kama hannunta, sai kuwa yarinyar ta shi. 26Labarin kuwa ya bazu a duk yankin.27Da Yesu ya yi gaba daga nan, sai wadansu makafi biyu suka bi shi, suna daga murya suna cewa, "Ya Dan Dauda, ka ji tausayinmu." 28Da Yesu ya shiga wani gida sai makafin suka zo gareshi. Yesu ya ce masu, "Kun gaskata ina da ikon yin haka?" Sai suka ce masa. "I, ya Ubangiji."29Sai Yesu ya taba idanunsu, ya ce, "Ya zama maku gwargwadon bangaskiyarku." 30Sai idanunsu suka bude. Amma Yesu ya umarce su kwarai, ya ce, "Kada fa kowa ya ji labarin nan." 31Amma suka tafi suka yi ta baza labarinsa a duk yankin.32Da makafin biyu suka tafi, sai aka kawo wa Yesu wani bebe mai aljani. 33Bayan da an fitar da aljanin, sai beben ya yi magana, taron kuwa suka yi mamaki, su ka ce, "Kai, ba a taba ganin irin wannan a cikin Isra'ila ba!" 34Amma sai Farisawa suka ce, "Ai, da ikon sarkin aljanu ya ke fitar da aljanu."35Sai Yesu ya zazzaga dukan garuruwa da kauyuka, yana koyarwa a majami'unsu, yana yin bisharar mulkin Allah, yana kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya. 36Amma da ya ga taro masu yawa sai ya ji tausayinsu, domin suna shan wahala kuma sun karaya. Suna nan kamar tumaki da babu makiyayi.37Sai ya ce wa almajiransa, "Girbin yana da yawa, amma ma'aikatan kadan ne. 38Saboda haka sai ku yi sauri ku roki Ubangijin girbin ya turo ma'aikata cikin girbinsa."
Matta ya komo zuwa ga maganan da ya fara a cikin 8:1, na Yesu da ya na warkad da mutane. Wannan ya fara ba da labarin Yesu da ya na warkad da shanyayyer mutum.
Ana nufin cewa almajiran su na tare da Yesu.
Mai yiwuwa wannan irin jirgin ne a Matta 8:23. Za ku iya ba da takamaiman wannan a inda ya kamata domin yin hankali da gardama.
"zuwa garin da ya na zama." Wannan na nufin Karfanahum.
Wannan ya ba da alama a farkon wani abu a babban labarin. Na iya ƙunshi mutane dabam dabam fiye da abin da ya faru a baya. Harshenku na iya samin wata hanyar nuna wannan.
"waɗansu mutane daga garin"
Wannan na nufin mazan kuma ya shafi bangaskiyar shanyayye mutumin .
Mutumin ba ainahin ɗan Allah ba ne. Yesu ya na yi masa magana da ladabi. Za a iya juya zuwa "Abokina" ko "ƙaramin mutum" ko kuma a cire idan zai kawo gardama.
AT: "Na gafarta maka zunuban ka"
AT: 1) kowanne na tunani wa kansa, ko 2) su na magana a sakaninsu.
Yesu ya na cewa zai iya yin abubuwan da marubatan su na tunani Allah ne kadai zai iya yi.
Yesu ya san abin da suke tunanin ko da ya wuce ikon ɗan Adam ko domin ya iya gani cewa suna magana da juna.
Yesu ya yi amfani da wannan tambaya domin ya ƙwabe marubutan.
Wannanmugunta ne da ba daidai ba, ba kuskure ba ne.
A nan "zuciya" na nufin hankalinsu ko tunaninsu.
Yesu ya yi amfani da wannan tambaya don ya sa marubuta su yi tunani game da abin da zai iya nuna cewa zai gafarta zunubai. AT: "Na ce 'An gafarta maka zunubanka.' Za ku iya tunani cewa ya na da wuya a ce 'Tashi ka yi tafiya,' domin tabacin cewa zan iya warkad da mutumin zai nuna ta wurin tashiwarsa ya yi tafiya." ko "Za ku iya tunani cewa mafi sauki ne a ce 'An gafarta maka zunubanka' da a ce 'Tashi ka yi tafiya."
Ana iya juya maganan a kaikace. AT: "wanne ne ya fi sauki, a ce wa wani cewa an gafarta masa zunubansa, ko a ce masa ya tashi ya yi tafiya?" ko "za ku iya tunani cewa mafi sauki ne a gaya wa wani cewa an gafarta masa zunubansa da ce masa ya tashi ya yi tafiya."
AT: "Na gafarta maka zunubanka"
"Zan nuna maku." "ku" jam'i ne.
Ba wai Yesu ya na haramta mutumin cewa ya tafi wani wuri ba ne. Ya na ba wa mutumin dama ya je gida.
"domin ya ba da"
Wannan na nufin irin iko da na furta gafartawar zunubi.
Wannan jumla ya sa alama a farkon sabon sashin labarin. Idan harshenku na wata hanyar yin haka, za ku iya amfani da shi anan.
"na tafiya"
Al'adan Ikilisiya ya ce Matiyu ne marubucin wannan bishara, amma littafin bai ba da dalilin canza wakilin sunaye daga "sa" da "Shi" zuwa "ni" ba.
"Yesu ya ce wa Matiyu"
"Matiyu ya tashi ya bi Yesu." Wannan na nufin cewa Matiyu ya zama almajirin Yesu.
Wannan abin ya faru a gidan Matiyu mai karban haraji.
Mai yiwuwa wannan gidan Matiyu ne, amma zai iya zama gidan Yesu ne. Ba da cikakken bayani don hankali da hargitsawa.
"Da Farisawa suka gan cewa Yesu ya na cin abinci tare da masu ƙarban haraji da mutane masu zunubi"
Farisawan sun yi amfani da wannan tambaya don su yi zargin abin da Yesu ya na yi.
A nan "haka" na nufin tambayan da Farisawan sun yi game da yadda Yesu ya na cin abinci da masu ƙarban haraji da masu zunubi.
Yesu ya amsa da magana. Ya na nufin cewa ya na cin abinci da irin waɗannan mutane domin ya zo don ya taimake masu zunubi ne.
"Mutane masu lafiya"
likita
An fahimci jumlar "na bukatan likita." AT: "mutane masu rashin lafiya na bukatan likita"
Yesu ya yi kusan magana daga nassin. AT: "Ku koya ma'anar abin da Allah ya ce a cikin nassin"
A nan "ku" jam'i ne kuma ya na nufin Farisawan.
Yesu ya na faɗan abin da annabi Hosiah ya rubuta a cikin nassi. Anan "Ina" na nufin Allah.
A nan "Na" na nufin Yesu.
Yesu ya na yin amfani da ƙarin magana. Ba ya tunanin cewa akwai mutanen da suke da adalci da ba su neman tuba. AT: "waɗanda su na tunanin cewa su masu adaci ne"
"shigaba da ci kullum"
Yesu ya yi amfani da tambaya don ya amsa almajiran Yahaya. Sun san cewa mutane ba su makoki da azumi a bukin aure. Yesu ya yi amfani da wannan magana don ya nuna cewa almajiransa ba su makoki domin ya na nan tare da su.
Wannan wata hanya ne na nuna loƙacin nan gaba. AT: "loƙacin na zuwa da" ko "wani rana"
AT: "angon ba zai iya kasance da su kuma ba" ko "wani zai ɗauke masu angon"
Mai yiwuwa Yesu ya na nufin mutuwarsa ne, amma kada a sa wannan a bayyane a wannan juyin. Zai yi kyau ku faɗa cewa angon ba zai kasance a wurin kuma ba don a tsare ƙarin maganan.
"Babu wani da na ɗinka sabon ƙyalle a kan tsohon tufa" ko "Mutane ba su ɗinka sabon ƙyalle kamar faci a kan tsohon tufa ba"
"tsohuwar ƙyalle ... ƙyalle"
In da wani zai wanke tufar, facin sabon kayan zai tauye, amma tsohon tufar ba zai tauye ba. Wannan zai yage facin daga tufar ya kuma bar babban rami.
"kyallen sabon kaya." Wannan kyalle ne da ana amfani don a rufe rami a tsohon tufa.
AT: "wannan zai sa yagewar mafi muni"
Yesu ya yi amfani da wani ƙarin magana don ya amsa almajiran Yahaya. Wannan na nufin abu ɗaya da ƙarin maganan a cikin 9:16.
"Ba wani da na ɗura" ko "Mutane ba su ɗura"
Wannan na nufin inabin da bai rigaya tashi ba. Idan ba a san inabi a yankin ku ba, ku yi amfani da kalmar 'ya'ya. AT: "ruwan inabi"
Wannan na nufin salkunan da sun yage domin an riga an yi amfani da su don ta da inabi.
Waɗannan jakuna ne da an yi shi daga fatan dabba.
AT: "kuma wannan zai ɓata salkunan ya kuma tsiyaye inabin"
Loƙacin da sabon inabin ya tashi ya kuma kumbura, fatan na yagewa domin ba za su iya miƙewa ba.
"sabon jakunan inabi." Wannan na nufin salkunan da ba a yi amfani da shi ba.
AT: "wannan zai ajiye salkunan da inabin"
Wannan na nufin amsa da Yesu ya ba wa almajiran Yahaya game da azumi.
Wannan hanya ne da mutum na nuna ladabi a al'adan Yahudawa.
Wannan ya nuna cewa shugaban Yahudawan ya gaskanta cewa Yesu na da ikon sa yarshi ta rayu kuma.
"Almajiran Yesu"
"wadda ta na jini" ko "wadda ta na yawan jini." Mai yiwuwa ta na jini daga mahaifarta ko loƙacin bai kai ba. Waɗansu al'adu na iya samin wata hanya mai kyau na kiran wannan yanayin.
"ma ɗaurinsa" ko "abin da ya sa"
Ta faɗa wa kanta wannan kafin ta taɓa mayafin Yesu. Wannan ya ba da dalilin da ta taɓa mayafin Yesu.
Bisa dokar Yahudawa, bai kamata ta taɓa kowa ba domin ta na yin jini. Ta taɓa mayafinsa domin ikon Yesu ya warkad da ita kuma
"Matan ta na bagen cewa za ta iya taɓa shi a ɓoye, amma Yesu"
Matan ba ainahin yar Yesu ba ne. Yesu ya na magana da ita da ladabi ne. Za a iya juya wannan kamar "ƙaramin mace" ko a cire idan zai zama da gardama.
"domin kin gaskanta da ni, zan warkad da ke"
AT: "Yesu ya warkad da ita a loƙacin"
Wannan yadda ana makokin wanin da ya mutu.
"mutane masu busar sarewa"
Yesu ya na magana da mutane dayawa, don haka ku yi amfani da umurni na jam'i idan harshenku na da shi.
Yesu ya na amfani da magana a cikin magana. Sanannen abu ne a zamanin Yesu a kira mataccen mutum wanda yake "barci." Amma anan matacciya yar za ta tashi, kamar dama ta na barci ne.
AT: "Bayan da Yesu ya fitar da taron waje" ko Bayan da iyalin suke fitar da mutanen waje"
"ta shi daga gado." Wannan ma'ana ɗaya ne a cikin 8:15.
"Mutanen dukka yankin su ji game da shi" ko "Mutanen da sun gan cewa yarinyar ta na da rai sun fara gaya wa kowa a cikin dukka garin"
Wannan na nufin cewa su na tafiya a bayan Yesu, ba lallai ne cewa sun zama almajiransa ba.
Ya na nufin cewa sun so Yesu ya warkad da su.
Yesu ba Ɗan Dauda na zahiri ba, do haka za a iya juya wannan kamar "Zuriyar Dauda." Ko da shike, "Ɗan Dauda" laƙabi ne wa Mai ceto, kuma mai yiwuwa mutanen su na kiran Yesu da wannan laƙabin.
Wannan zai iya zama gidan Yesu ko gidan a cikin 9:10.
Ba a rubuta cikkaken amsarsu ba, amma an gane. AT: "I, Ubangiji, mun gaskanta cewa za ka iya warkad da mu"
Ba a bayyane ne yake ko ya taba idanun maza biyun a loƙaci ɗaya ne ko ya yi amfani da hanunsa na dama don ya taba su ɗaya bayan ɗaya ba. Kamar yadda ana amfani da hanun hagu don ayuka mara tsarki a al'adan, mai yiwuwa ya yi amfani da hanun damansa ne. Ba a bayyane ne yake ko ya yi magana a yayin da yake taba su ba ko ya tabasu kafin ya yi masu magana ba.
AT: "Zan yi kamar yadda kun gaskanta" ko "Domin kun gaskanta, zan warkad da ku"
Wannan na nufin cewa sun iya gani. AT: "Allah ya warkad da idanunsu" ko "makafi biyun sun iya gani"
A nan "gan" na nufin "tabbaci." AT: "Ku tabbata cewa wani bai san game da wannan ba" ko "Kada ku faɗa wa wani cewa ni ne na warkad da ku"
"Mutane biyun ba su yi abin da Yesu ya gaya masu su yi ba. Su"
"gaya wa mutane dayawa game da abin da ya faru da su"
AT: "wani ya kawo beben mutum ... wa Yesu"
rashin iya magana
AT: "wanda na da aljani" ko "wanda aljani na iko da shi"
AT: "Bayan da Yesu ya fitar aljanin da ƙarfi" ko "Bayan da Yesu ya umurci aljanin ya tafi"
"beben ya ya fara yin magana" ko "mutumin da da shi bebe ne ya fara magana" ko "mutumin da yanzu ba bebe ba, ya yi magana"
"Mutanen sun yi mamaki"
AT: "Wannan bai taba faruwa ba" ko "Babu wanda ya taba yin abu irin wannan"
"ya na tilasa aljanun su tafi"
Wakilin suna "ya" na nufin Yesu.
Kalmar "dukka" zugwaigwaitawa ne da na nanata yawan garuruwa da Yesu ya je. Ba lalai ba ne ya je kowannensu ba. AT: "yawancin garuruwa "
"babban kauyuka ... kananun kauyuka" ko "babban birni ... kananun birni"
A nan "mulki" na nufin mulkin Allah kamar sarki. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 4:23.
"kowace irin cuta da rashin lafiya." Kalmomin "cuta" da "rashin lafiya" suna kusa amma za a iya juya su kamar kalmomi dabam dabam. "Cuta" abu ne da ke sa mutum rashin lafiya. "Rashin lafiya" rashin ƙarfin jiki ne ko rashin ɗadi daga samin cuta.
Wannan ƙarin magana na nufin ba su da shugaba da zai kula da su. AT: "Mutanen ba su da shugaba"
Yesu ya yi amfani da ƙarin magana don ya amsa abin da ya na gani. Yesu ya na nufin cewa akwai mutane dayawa da sun shirya su gaskanta da Allah amma mutane kaɗan ne akwai don su koya masu gaskiyar Allah.
"Akwai abinci da sun nuna don wani ya tara"
"ma'aikata"
"ku yi addu'a ga Allah, domin shi ne shugaban girbin"
1Yesu ya kira almajiransa goma sha biyu, ya kuma ba su ikon fitar da kazaman ruhohi, su warkar da kowacce irin cuta da rashin lafiya.2To yanzu ga sunayen manzanin nan goma sha biyu. Na farkon shine, Saminu, wanda ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, da Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya; 3Filibus, da Bartalamawus, da Toma da Matiyu mai karbar haraji da Yakubu dan Halfa, da Taddawus; 4Saminu Bakairawane, da kuma Yahuza Iskariyoti wanda ya bashe shi.5Sha biyun nan su ne Yesu ya aika, ya yi masu umarni ya ce, "Kada ku shiga wajen al'ummai, ko kuma kowane garin Samariyawa. 6Sai dai ku je wurin batattun tumaki na gidan Isra'ila. 7Sa'adda kuna tafiya, kuna wa'azi, kuna cewa, 'Mulkin Sama ya kusato'.8Ku warkar da marasa lafiya, ku tada matattu, ku tsarkake kutare, ku kuma fitar da aljanu. Kyauta kuka samu ku ma ku bayar kyauta. 9Kada ku rike zinariya, ko azurfa, ko tagulla a jakarku. 10Kada kuma ku dauki zabira a tafiyarku, ko taguwa biyu, ko takalma, ko sanda, don ma'aikaci ya cancanci abincin sa.11Kowanne birni, ko kauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a cikinsa, ku kuma zauna a wurin har lokacin da za ku tashi. 12In za ku shiga gida ku ce, salama a gareku. 13Idan gidan akwai dan salama, salamarku za ta ta tabbata a gare shi. Idan kuwa babu, salamarku za ta komo maku.14Ga wadanda su ka ki karbar ku ko sauraron ku, idan za ku fita garin ko gidan, sai ku karkade kurar kafafunku. 15Hakika, ina gaya maku, a ranar shari'a za a fi rangwanta wa kasar Saduma da ta Gwamrata a kan wannan birni.16"Duba, na aike ku kamar tumaki a tsakiyar kyarketai, don haka sai ku zama masu wayo kamar macizai, da kuma marasa barna kamar kurciyoyi. 17Ku yi hankali da mutane, don za su kai ku gaban majalisa, su kuma yi maku bulala a majami'unsu. 18Za su kuma kai ku gaban mahukunta da sarakuna saboda ni, domin ku bada shaida a gabansu, da kuma gaban al'ummai.19Idan har sun bada ku, kada ku damu da yadda za ku yi magana, ko kuwa abin da za ku fada, domin za a ba ku abin da za ku fada a lokacin. 20Domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhun Ubanku ne yake magana ta bakinku.21Dan'uwa zai ba da dan'uwansa a kashe shi, uba kuwa dansa. 'Ya'ya kuma za su tayarwa iyayensu, har su sa a kashe su. 22Kowa kuma zai ki ku saboda sunana. Amma duk wanda ya jure har karshe, zai tsira. 23In sun tsananta maku a wannan gari, ku gudu zuwa na gaba. Hakika ina gaya maku, kafin ku gama zazzaga dukan garuruwan Isra'ila, Dan Mutum zai zo.24Almajiri ba ya fin malaminsa, bawa kuma ba yafin ubangijinsa. 25Dai dai ne almajiri ya zama kamar malaminsa, bawa kuma kamar ubangijinsa. In har sun kira mai gida Ba'alzabuba, za su kuma bata mutanen gidansa!26Don haka kada kuji tsoron su, domin ba abin da yake boye da ba za a bayyana ba. 27Abin da nake fada maku a asirce, ku fada a sarari. Abin da kuma kuka ji a cikin rada, ku yi shelarsa daga kan soraye.28Kada ku ji tsoron masu kisan jikin mutum, amma ba sa iya kashe rai. Sai dai ku ji tsoron wannan da yake da ikon kashe jiki ya kuma jefa rai cikin jahannama. 29Ba 'yan tsuntsaye biyu ake sayarwa akan kobo ba? Ba ko daya a cikin su da zai fadi kasa ba tare da yardar Ubanku ba. 30Ai, ko da gashin kan ku ma duk a kidaye yake. 31Kada ku ji tsoro. Gama darajarku ta fi ta tsuntsaye masu yawa.32"Saboda haka duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, ni ma zan yi shaidar sa a gaban Ubana wanda ya ke cikin Sama. 33Amma duk wanda ya yi musun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi musun sanin sa a gaban Ubana da yake cikin Sama."34"Kada ku zaci na zo ne in kawo salama a duniya. Ban zo domin in kawo salama ba, sai dai takobi. 35Domin na zo ne in hada mutum da ubansa gaba, 'ya da uwatarta, mata da kuma surukarta. 36Zai zama na kuma magabtan mutum su ne mutanen gidansa.37Dukan wanda ya fi son mahaifinsa ko mahaifayarsa fiye da ni, bai cancanci zama nawa ba. Wanda kuma ya fi son dansa ko 'yarsa fiye da ni, bai cancanci zama nawa ba. 38Wanda kuma bai dauki gicciyensa ya biyo ni ba, bai cancanci zama nawa ba. 39Dukan mai son ya ceci ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa saboda ni, yana ceton sa ne.40"Wanda ya marabce ku, ya marabce ni ke nan. 41Wanda ya marabce ni kuwa, ya marabci wanda ya aiko ni. Wanda ya marabci annabi domin shi annabi ne, zai karbi lada kamar na annabi. Wanda kuma ya marabci mai adalci saboda shi mai adalci ne, zai sami lada kamar na mai adalci.42Kowa ya ba daya daga cikin 'yan kananan nan, ko da kofin ruwan sanyi ya sha, domin shi almajirina ne, hakika, Ina gaya maku, ba zai rasa ladarsa ba."
Wannan ya fara labarin da Yesu ya turo almajiransa goma sha biyu don su yi aiki.
"kirawo almajiransa goma sha biyu"
Ku tabata cewa wannan matanin ya bayyana cewa wannan iko 1) don fitar da kazaman ruhohi da kuma 2) don warkad da cuta da rashin lafiya.
"ya sa kazaman ruhohi su tafi"
"kowane irin cuta da kowane rashin lafiya." Kalmomin "cuta" da "rashin lafiya" su na kusa amma in ya yiwu a juya su kamar kalmomi biyu dabam dabam. "Rashin lafiya" rashin ƙarfin jiki ne ko wahala daga wani cuta.
Marubucin anan ya ba da sunayen manzane goma sha biyu a matsayin tushen bayanin.
An yi amfani da wannan kalma anan don a sa alama a ainahin labarin. Anan Matiyu ya ba da tushen bayani game da manzane goma sha biyu.
Wannan kungiya ɗaya ne da "almajirai goma sha biyu" a cikin 10:1.
Wannan farko ne bisa shiri ba a jeri ba.
AT: 1) "Bakairawane" laƙabi ne da na nuna cewa ya na cikin kungiyan mutane da sun so su ceci mutanen Yahudawa daga mulkin Romawa. AT: "mai kishin kasarsa" ƙwatanci ne da na nuna cewa shi bakairawane don Allah ya sami ɗaukaka.
"Matiyu, wanda da mai ƙarban haraji ne"
"wanda zai bashe Yesu"
"Yesu ya aika waɗannan mutane sha biyu" ko "waɗannan mutane sha biyun nan ne Yesu ya aiko":
Yesu ya aike su don wata dalili.
"Ya gaya masu abin da za su yi" ko "ya umurce su"
Wannan ƙarin magana ne da na ƙwatanta dukka al'umman Isra'ila da tumakin da sun bazu daga makiyayinsu.
Wannan na nufin al'umman Isra'ila. AT: "mutanen Isra'ila" ko "zuriyar Isra'ila"
A nan "kun" jam'i ne kuma na nufin manzane goma sha biyu.
Jumlar "Mulkin Sama" na nufin mulkin Allah kamar sarki. Wannan jumla na cikin littafin Matiyu ne kadai. Idan ya yiwu, yi amfani da kalmar "sama" a cikin juyinku. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 3:2. AT: "Allahn mu a sama ya yi kusa ya nuna kansa a matsayin sarki"
Waɗannan jam'i ne kuma na nufin manzane goma sha biyu.
Wannan ƙarin magana ne. AT: "sa matattu su rayu kuma"
Yesu bai bayyana abin da almajiran sun ƙarba ko za su bayar ba. Wasu harshen na iya bukaci wannan bayani a cikin jimlan. Anan "Kyauta" na nufin babu biya. AT: "A kyauta kuka ƙarba waɗannan abubuwa, ku bayar da su kyauta wa waɗansu" ko "Kun ƙarba waɗannan abubuwa ba tare da biya ba, don haka, ku ba wa waɗansu ba tare da sa su biya ba"
Waɗannan ƙarafuna ne da ake yin ƙerarren kuɗi. Wannan ƙarin magana ne na kuɗi, idan ba a san irin ƙarfen a garin ku ba, juya su kamar "kuɗi."
Wannan na nufin "ɗamara" ko "ɗamaran kuɗi" amma ya na iya nufin kowane abu da ana iya amfani da shi don ɗaukan kuɗi. Ɗamara wata dogon igiyan ƙyalle ne ko fata da an sa a ƙugu. Ya nan da faɗi da ana iya nadewa a kuma yi amfani don ɗaukan kuɗi.
Wannan na iya zama kowane irin jaka da ana ɗaukan kaya a tafiya, ko jakar da wani ke amfani da shi don ƙarban abinci ko kuɗi.
Yi amfani da irin kalma da kun yi amfani ma "taguwa" a cikin 5:40.
ma'aikaci
A nan "abinci" na nufin kowane abu da mutum na yi. AT: "abin da ya na bukata"
"Duk loƙacin da kun shiga birni ko ƙauye" ko "Loƙacin da kun shiga kowane birni ko ƙauye"
"babban ƙauye ... ƙaramin ƙauye" ko babban gari ... ƙaramin gari." Dubi yadda kun juya wannan a cikin 9:35.
A cikin 10:11-13 mutum da ya "dace" na nufin mutumin da ya yarda ya ƙarbi almajiran. Yesu ya ƙwatanta wannan mutum da wanda "bai dace ba," mutumin da ba ya ƙarban su almajiran.
Ana iya sa a bayyane cikakken ma'anar bayanin. AT: "ku zauna a cikin gidan wannan mutumin har sai kun bar garin ko ƙauyen"
Jumlar "yi masa gaisuwa" na nufin gai da gidan. Sanannen gaisuwa a waɗannan zamanin shi ne "salama a gareku!" Anan "gida" na wakilcin mutanen da suna zama a gidan. AT: "Sa'adda kun shiga cikin gidan, ku gai da mutanen da suke zama a ciki"
A nan "gida" na wakilcin waɗanda su na zama a cikin gidan. AT: "mutanen da suke zama a cikin wannan gidan sun ƙarbe ku da kyau" ko mutanen da suke wannan gidan sun nuna maku hali mai kyau"
Kalmar "shi" na nufin gidan, wadda na wakilcin mutanen da suke zama a cikin gidan. AT: "bari su ƙarbi salamarku" ko "bari su ƙarbi salamarku da kun gaishe su da shi"
Kalmar "bata" na nufin gidan. Anan "gida" na nufin mutanen da suke zama a cikin gidan. AT: "idan ba su ƙarbe ku da kyau ba" ko "idan ba su nuna maku hali mai kyau ba"
AT: 1) idan iyalin ba ta dace ba, Allah zai rike salama ko albarku daga wannan iyali ko 2) idan iyalin ba ta dace ba, yakamata manzanen su yi wani abu, kamar rokon Allah kada ya ƙarbi gaisuwar salamarsu. Idan harshenku na da irin ma'anar komar da gaisuwa, a yi amfani da shi anan.
"Idan babu mutane a cikin gidan ko birnin da za su ƙarbe ku ko saurara"
A nan "magana" na nufin abin da almajiran sun ce. AT: "saurare sakonku" ko "saurare abin da za ku ce"
Ku juya wannan kamar yadda kun yi a cikin 10:11.
"ku karkade kurar kafafunku sa'adda kun tafi." Wannan alama ne cewa Allah ya ki mutanen wannan gidan ko garin.
"Ina gaya maku gaskiyan." Wannan jumla ya kara bayani ga abin da Yesu ya faɗa a gaba.
"azaban zai yi sauki"
Wannan na nufin mutanen da suka yi zama a Saduma da Gwamrata. AT: "mutanen da sun yi zama a garurukan Saduma da Gwamrata"
Wannan na nufin mutanen cikin birnin da basu ƙarbi manzanin ko ji sakonsu ba. AT: "mutanen garin da basu ƙarbe ku ba"
Kalmar "Dubi" anan ya kara bayani a abin da ke a gaba. AT: "Ga, na aike" ko "Sauraro, aiko" ko "Ku yi hankali da abin da zan gaya maku. Na aiko"
Yesu ya na aikan su don wata dalili ta musamman.
Tumaki dabba ne da ba ya iya kariya kuma kyarketai sun ciki binsu. Yesu ya na bayyana cewa mutane na iya cutar da almajiran. AT: "kamar tumaki a cikin mutanen da suke kamar mugayen kyarketai" ko "kamar tumaki a cikin mutanen da su ke yi kamar yadda mugayen dabbobi suke yi"
Yesu ya na gaya wa almajiransa cewa dole ne su zama da hankali da rashin cuta a cikin mutane. Idan kwatanta almajiran da macizai ko kurciyoyi zai kawo rikicewa, Zai fi dama in kun fade shi tamka. AT: "aikata da fahimta da hankali, da kuma rashin laifi da kirki"
Za ku iya juya da "domin" don a nuna yadda waɗannan bayyanen sun shafi juna. AT: "Ku yi hankali da mutane domin za su"
"za su sa ku cikin ikon"
Shugabanin addini na wuri ɗaya ko dattibai wanda suke sadar da salama a cikin mutane
"duke ku da bulala"
AT: "za su kawoku" ko "za su jawoku"
"domin ku nawane" domin kun bi ni"
Jam'in "ku" na nufin "gwamna da sarakuna" ko Yahudawa masu kushewa.
"Idan mutane sun kai ku wa majalisa." "Mutanen" anan ɗaya ne da "mutanen" cikin 10:17.
"kada ku damu"
"yadda za ku yi magana ko abin da za ku ce." Ana iya hada ra'ayi biyun. "abin da za ku ce"
AT: "domin Ruhu mai Tsarki zai gaya maku abin da za ku fada"
Anan "loƙaci" na nufin "nan da nan." AT: "a wannan loƙacin"
Idan wajibi ne, Za a iya juya wannan kamar "Ruhun Allah Ubanku na samaniya" ko ana iya sa karin bayani don a bayyana cewa wannan na nufin Allah Ruhu mai Tsarki ba kuwa ruhun uba na duniya ba.
Wannan muhimmin laƙabi ne wa Allah.
"ta wurin ku"
"Wani ɗan'uwa zai ba da ɗan'uwansa ga mutuwa" ko "Yan'uwa za su ba da yan'uwansu ga mutuwa." Yesu ya yi maganar abin da zai faru sasai.
Ana iya bayyana kalmar "mutuwa." AT: "mika ɗan'uwa ga hukuma wanda za su ƙashe shi"
Ana iya fasara wannan kalmomin kamar ciƙaƙƙen jimla. AT: "Ubanni za su ba da 'ya'yansu ga mutuwa"
"yi tawaye"
AT: "sa a ƙashe su" ko "sa hukuma su ƙashe su"
AT: "Kowa zai tsane ku" ko "Dukka mutane za su tsane ku"
Wannan jam'i ne kuma ya na nufin almajirai goma sha biyun.
A nan "suna" na nufin dukkan mutum. AT: "saboda ni" ko "saboda kun gaskanta da ni"
"duk wanda ya tsaya da aminci"
Ba a bayyane ne yake ko "ƙarshen" na nufin loƙacin da mutum ya mutu, loƙacin da tsanantawan zai kare, ko ƙarshen zamani da Allah zai nuna kansa ma matsayin sarki. Ainahin maganan shi ne sun jure yanda ya kamata.
AT: "Allah zai ceci wannan mutumin"
A nan "wannan" ba ya nufin takamaiman gari. AT: "a gari ɗaya"
"gudu zuwa gari na gaba"
Yesu ya na magana game da kansa.
"isa"
Yesu ya na amfani da ƙarin magana ne anan domin ya koya wa almajiransa gaskiya ta musamman. Yesu ya na nanata cewa kaɗa almajiran su zaci mutane su yi masu da kyau fiye da yanda mutane suka yi wa Yesu.
"Almajiri na da mafi ƙanƙancin daraja fiye da ubangijinsa" ko "Malami na da mafi daraja fiye da almajirinsa"
"kuma bawa na da mafi ƙanƙancin daraja fiye da ubangijinsa" ko "kuma ubangiji na da mafi daraja fiye da bawarsa"
"Almajirin ya ji dadin zama kamar malaminsa"
In ya yiwu, za ku iya sa a bayyane yadda bawan ya zama kamar mallamin. AT: "san sosai kamar yadda mallamin ya sani"
In ya yiwu, za ku iya sa a bayyane yadda bawan ya zama kamar ubangijin. AT: "ya kamata bawan ya ji dadin zama da daraja kamar ubangijinsa"
Yesu ya na kuma nanata cewa tun da mutane sun wullakanta shi, almajiransa su yi zaci cewa mutane za su yi masu haka ko mafi muni.
"sunayen da ake kiran mutanen gidansa za su zama da mafi muni" ko "hakika za a kira mutanen gidansa da sunaye mafi muni"
"Tun da mutane sun kira"
Yesu ya na amfani da wannan ƙarin magana wa kansa.
Ana iya fasara wannan sunan kamar 1) "Beelzebul" ko 2) juya shi da ainahin ma'anarsa na "Shaidan."
Wannan ƙarin magana ne wa almajiran Yesu.
A nan "su" na nufin mutanen da su na wullakanta masubin Yesu.
Dukka waɗannan magana na nufin abu ɗaya ne. Zama da rufe ko ɓoye na wakilcin ajiye a asirce, kuma bayyana na wakilcin zama sananne. Yesu ya na nanata cewa Allah zai sa komai sananne. AT: "Allah zai bayyana abubuwan da mutane na ɓoyewa"
Dukka waɗannan magana na nufin abu ɗaya ne. Yesu ya na nanata cewa almajiran su gaya wa kowa abin da ya faɗa masu a asirce. AT: "Gaya wa mutane a haske abin da na faɗa maku a duhu, ku kuma yi shela akan soraye abin da kun ji a cikin kunnenku"
A nan "duhu" magana ne na "dare" wanda magana ne kuma na "asirce." Anan "haske" magana ne na "sarari." AT: "Abin da nake fada maku a asirce da dare, ku fada a sarari da haske"
Wannan wata hanya ne da na nufin raɗarwa. AT: "abin da na raɗar maku"
Sorayen inda Yesu na zama shimfiɗaɗɗe ne, kuma mutanen da su na da nisa na iya jin duk wanda ke magana da babban murya. Anan "soraye" na nufin wurin da dukka mutane na iya ji. AT: "yi magana da ƙarfi a sararin wuri domin kowa ya ji"
Wannan ba ya bambanta sakanin mutanen da ba su iya ƙashe rai da mutane da sun iya ƙashe rai ba. Babu mutum da zai iya ƙashe rai. AT: "Kada ku ji tsoron mutum. Za su iya ƙashe jikin, amma ba za su iya ƙashe rai ba"
Wannan na nufin sa mutuwa. Idan waɗannan kalmomin basu da kangado, za ku iya juya wannan kamar "ƙashe ka" ko "ƙashe wasu mutane."
sashin mutum da ana iya tabawa, da ke hamayya da jiki ko ruhu
Wannan na nufin lahanta mutane bayan sun mutu.
sashin mutum da ba a iya taba kuma na nan da rai har bayan jikin ya mutu
Za ku iya kara "domin" don ku bayyana dalilin da ya kamata mutane su ji tsoron Allah. AT: "Ji tsoron Allah domin na iya"
Yesu ya bayyana wannan magana kamar tambaya domin ya koyar da almajiransa. AT: "Yi tunani game da tsuntsaye. Su na da daraja kadan da ku na iya saya biyu a dan kobo kadan."
Waɗannan kananun, tsuntsaye masu cin ƙwaya. AT: "kananun tsuntsaye"
Ana juya wannan kamar ƙaramin kobo mai daraja da akawai a kasarku. Na nufin kobon ƙarfe da ya kai ɗayan-sha shida na ƙudin ma'aikaci na kwana ɗaya. AT: "ƙudi kadan sosai"
AT: "Ubanku ya san loƙacin da tsuntsu ɗaya yake mutuwa ya kuma faɗi a kasa"
AT: "Allah ya san yawan gashin dake kanku"
"ƙirga"
"Allah ya na daraja ku fiye da tsuntsaye masu yawa"
"duk wanda ya shaida ni ... Zan kuma shaida a gaban Ubana" ko "Idan wani ya shaida ni ... Zan kuma shaida a gaban Ubana"
"gaya wa waɗansu cewa shi almajiri na ne" ko "amince a gaban waɗansu mutane cewa ya na yi mani biyayya"
Za ku iya sa a bayyane bayanin da kun fahimta. AT: "Zan kuma amince a gaban Ubana wanda ya na cikin sama cewa wannan mutumin nawa ne"
"Ubana na samaniya"
"duk wanda ya musunta ni ... Zan kuwa musunta a gaban Ubana" ko "Idan wani ya musunta ni ... Zan kuwa musunta shi a gaban Ubana"
"musunta ga sauran mutane cewa ya na yi ma ni biyayya" ko "kin ya amince wa waɗansu cewa shi almajiri na ne"
Za ku iya sa a bayyane bayanin da kun fahimta. AT: "Zan musanta a gaban Ubana wanda na sama cewa wannan mutumin nawa ne"
"Kada ku zata" ko "Kada ku yi tunani"
Wannan na nufin mutanen da su na zama a duniya. AT: "ga mutanen duniya" ko "ga mutane"
Wannan na nufin rabawa, faɗa, da kisa a sakanin mutane.
"sa ... yi faɗa da"
" hada ɗa da ubansa gaba"
"mafi munin maƙiyan mutum"
"mutanen gidansa"
A nan "shi" na nufin kowane mutum. AT: "Waɗanda na ƙaunar ... bai cancanci" ko "Idan ku na ƙaunar ... ba ku cancanci"
Kalmar "ƙauna" a nan na nufin "ƙauna na 'yanwantaka" ko "ƙauna daga aboki." AT: "damu da" ko "ba da kai"
"ya cancanci ya zama nawa" ko "cancanci ya zama almajiri na"
"ɗauka gicciyensa ya biyo ni." Gicciyen na wakilcin azaba da mutuwa. Daukan gicciye na wakilcin yarda ka sha azaba ka kuma mutu. AT: "yi mun biyayya har ga azaba da mutuwa"
"ɗauka" ko "ɗauka da ɗauki"
Yesu ya yi amfani da ƙarin magana don ya koyar da almajiransa. AT: "Waɗanda sun so ransu za su rasa su. Amma waɗanda sun rasa ransu ... za su samu" ko "Idan kun sami ranku za ku rasa shi. Amma idan kun rasa ranku ... za ku same shi"
Wannan ƙarin magana ne na "ajiye" ko "ceci." AT: "na yin kokari ya ajiye" ko "na yin kokari ya cece"
Wannan ba ya nufin cewa mutumin zai mutu. Karin magana ne da na nufin cewa mutumin ba zai yi rayuwa ta ruhaniya da Allah ba. AT: "ba zai sami rayuwa ta gaskiya ba"
Wannan ba ya nufin mutuwa. Karin magana ne da na nufin mutum ya zaba cewa yin biyayya da Yesu ya fi muhimminci fiye da ransa. AT: "wanda ya hanakansa"
Wannan ƙarin magana na nufin cewa mutumin zai yi rayuwa ta ruhaniya da Allah. AT: "zai sami rai ta gaskiya"
Kalmar "Shi" na nufin kowanene. AT: "Duk wanda" ko "duk wanda ya" ko "Wanda ya"
Wannan na nufin ƙarban wani kamar bako.
Yesu ya na nufin cewa idan wani ya marabce ku, na nan kamar marabtan shi ne. AT: "Idan wani ya marabce ku, ya na nan kamar ya na marabta na ne"
Wannan na nufin duk loƙacin da wani ya marabci Yesu, Na nan kamar marabtan Allah ne. AT: "In wani ya marabce ni, na nan ne kamar ya na marabtan Allah Uba wanda ya aiko ni" ko "Idan wani ya marace ni, ya na nan kamar ya na marabtan Allah Uba wanda ya aiko ni"
A nan "shi" ba ya nufin mutumin da ke yin marabta. Ya na nufin mutumin da an yi masa maraba.
Wannan na nufin lada da Allah na ba wa annabin, ba lada da annabi ke ba wa wani mutum ba.
A nan "shi" ba ya nufin mutumin da ke yin marabta. Ya na nufin mutumin da an yi masa maraba.
Wannan na nufin lada da Allah na ba wa mai adalci, ba lada da mai adalci ke ba wa wani ba.
"Duk wanda ya bayar"
"daya daga cikin 'yan ƙanƙantan nan." Jumlar "ɗaya daga cikin waɗannan" na nufin ɗaya daga cikin almajiran Yesu.
"domin shi almajirina ne." Anan "shi" ba ya nufin wanda an ba shi amma ga mafi ƙanƙanci.
A nan "zai" da "sa" na nufin wanda an ba shi.
"Allah ba zai hana shi ba." wannan bai kunsa ƙwace dukiya ba. AT: "Allah zai ba shi"
1Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa gargadi, sai ya bar wannan wuri, ya tafi biranensu domin yayi koyorwa, da wa'azi. 2Da Yahaya mai baftisma ya ji daga kurkuku irin ayyukan da Yesu ke yi, sai ya aika sako ta wurin almajiransa. 3Ya ce masa. "Kai ne mai zuwa"? ko mu sa ido ga wani.4Yesu ya amsa ya ce masu, "Ku je ku gaya wa Yahaya abin da ku ka gani da abin da ku ka ji. 5Makafi suna samun ganin gari, guragu na tafiya, ana tsarkake kutare, kurame na jin magana kuma, ana tada matattu, mabukata kuma ana ba su bishara. 6Kuma mai albarka ne wanda baya tuntube sabili da ni.7Bayan wadannan sun tafi, sai Yesu ya fara wa jama'a jawabi game da Yahaya mai baftisma, yana cewa, "Me ake zuwa gani a jeji - ciyawa ce da iska ke busawa? 8Shin menene kuke zuwa gani a jeji - mutum mai sanye da tufafi masu laushi? Hakika, masu sa tufafi masu laushi suna zaune ne a fadar sarakuna.9Amma me ku ke zuwa gani, annabi? Hakika ina fada maku, fiye ma da annabi. 10Wannan shine wanda aka rubuta game da shi, 'Duba, ina aika manzona, wanda za ya tafi gabanka domin ya shirya maka hanya inda za ka bi'.11Ina gaya maku gaskiya, cikin wadanda mata suka haifa, babu mai girma kamar Yahaya mai baftisma. Amma mafi kankanta a mulkin sama ya fi shi girma. 12Tun daga kwanakin Yahaya mai baftisma zuwa yanzu, mulkin sama yana shan gwagwarmaya, masu husuma kuma su kan kwace shi da karfi.13Gama dukan annabawa da shari'a sun yi annabci har zuwa lokacin Yahaya. 14kuma in zaku karba, wannan shine Iliya wanda za ya zo. 15Wanda ke da kunnuwan ji, ya ji.16Da me zan kwatanta wannan zamani? Ya na kamar yara masu wasa a kasuwa, sun zauna suna kiran juna 17suna cewa mun busa maku sarewa baku yi rawa ba, mun yi makoki, baku yi kuka ba.18Gama Yahaya ya zo, baya cin gurasa ko shan ruwan inabi, sai aka ce, "Yana da aljannu". 19Dan mutum ya zo yana ci yana sha, sai aka ce, 'Duba, ga mai hadama, mashayi kuma, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!' Amma hikima, ta wurin aikin ta ake tabbatar da ita.20Sannan Yesu ya fara tsautawa biranen nan inda ya yi yawancin ayukansa, domin ba su tuba ba. 21"Kaiton ki Korasinu, kaiton ki Batsaida! In da an yi irin ayuka masu ban mamaki a Taya da Sidon! Yadda aka yi a cikinku, da tuni sun tuba suna sanye da tsumma da yafa toka. 22Amma zai zama da sauki a kan Taya da Sidon a ranar shari'a fiye da ku.23Ke kafarnahum, kina tsammani za a daukaka ki har zuwa sama? A'a za a saukar da ke kasa zuwa hades. Gama in da an yi irin al'ajiban da aka yi a cikin ki a Sodom, da tana nan har yanzu. 24Amma ina ce maku, za a saukaka wa Sodom a ranar shari'a fiye da ku."25A wannan lokaci Yesu ya ce, "Ina yabon ka, ya Uba, Ubangijin sama da kasa, domin ka boye wa masu hikima da fahimta wadannan abubuwa, ka bayyana wa marasa sani, kamar kananan yara. 26I, ya Uba gama wannan shine ya yi daidai a gare ka. 27An mallaka mani dukan abu daga wurin Ubana. Sannan babu wanda ya san Dan, sai Uban, babu kuma wanda ya san Uban, sai Dan, da duk wanda ya so ya bayyana masa.28Ku zo gare ni, dukanku masu wahala da fama da nauyin kaya, ni kuma zan ba ku hutawa. 29Ku dauki karkiya ta ku koya daga gare ni, gama ni mai tawali'u ne da saukin hali a zuciya, sannan zaku sami hutawa ga rayukanku. 30Gama karkiyata mai sauki ce, kaya na kuma ba shi da nauyi."
Wannan wani bangare ne daga cikin farkon labarin da Matiyu ya bayana yadda Yesu ya yi magana game da Yahaya Mai Baftisma ga almajiransa.
Wannan magana ya kai mu daga koyaswar Yesu zuwa ga abin da ya faru a gaba. AT: "Sa'anan kuma" " ko "Bayan haka"
"ya gama koyar" ko "ya gama bada umurnin"
Wannan na nufin mazanai goma sha biyun da Yesu ya zaɓa.
A nan "su" na nufin Yahudawa gabakiɗaya.
Wannan kalman alama ce ta kaucewa daga ainihin kan labarin. Anan Matiyu ya fara bada sabuwar gangaren labarin.
"Lokacin da Yahaya, wanda ke cikin kurkuku, ya ji game da" ko kuwa "Sa'ad da wani ya gaya wa Yahaya, wanda ke a kurkuku, game da." Kodashike, Matiyu bai gaya wa masu karatunsa cewa Sarki Hiridus ya kulle Yahaya a kurkuku ba, ainihin wanda ya rubuta masu suna sane da labarin sun kuma san ainihin zance anan. Matiyu zai kara yin bayani nan gaba game da Yahaya Mai Baftisma, saboda haka, zai fi kyau kada a bayana shi anan.
Yahaya Mai Baftisma ya aike almajiransa da sako zuwa ga Yesu.
"sa" na nufin Yesu.
"Kai ne wanda muke sa sammanin zuwansa." Wannan a wani hanya, na nufin Mai Ceto ko Almasihu.
"Mu yi sammanin wani dabam" Kalman nan "mu" na nufin dukkan Yahudawa ba almajiran Yahaya ba.
"gaya wa Yahaya"
AT: "Ina warkar da Kutare"
A nan a ta da na nufin a sa wanda ya mutu ya rayu kuma. AT: "Mutanen da suka mutu an sa su su rayu kuma" ko "Ina sa waɗanda suka mutu su rayu kuma" and idiom)
AT: "Ina gaya wa mutane mabukata"
Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yahaya Mai Baftisma.
Yesu ya yi amfani da tambaya don ya sa mutane su yi tunani ko wani irin mutum ne Yahaya Mai Baftisma. AT: "Haƙiƙa ba a zuwa jeji a ga ciyawa ...iska...!"
Ma'ana suna kamar haka 1) Yesu na nufin shuke-shuke da ke a Kogin Urdun ko 2) Yesu na amfani da wannan don ya na nufin wane irin mutum. AT: "mutum wanda ke iya canza ra'ayinsa, shi kuma kamar ciyawa ne da isake busawa nan da nan"
AT: "tafi cikin iska" ko "iska ke busawa"
Yesu ya yi amfani da tambaya don ya sa mutanen su yi tunani ko wani irin mutum ne Yahaya Mai Baftisma. AT: "Haƙiƙa ba ku zuwa jeji don ku ga mutum ...tufafin...!"
"Sanya tufafi masu tsada." Masu arziki na sa irin wannan tufafin.
Wannan kalman na kara nanata abin da ke biye. AT: "lalle"
"fădar sarakuna"
Yesu ya yi amfani da tambaya don ya sa mutane tunani ko wani irin mutum ne Yahaya Mai Baftisma. AT: "Amma kuwa kun tafi jeji don ku ga annabi!"
Ina gaya maku, hakika"
AT: "she ba annabi ne kawai ba" ko "yana da muhimmanci fiye annabi"
AT: "Wannan shine abin da annabi Malachi ya rubuta game da Yahaya Mai Baftisma tun dă"
kalman nan "na" na nufin Allah. Malachi ya ambata abin da Allah ya faɗa ne.
A nan "ka" na nuna cewa Allah na magana ne da Mai Ceton. AT: "ya zo a gabanka"
Wannan na nufin cewa manzon zai shirya mutane don su karɓi sakon Mai Ceton.
"gaskiya ina gaya maku." Wannan magana na kara nanata abin da Yesu ya faɗa a nan gaba.
Kodashike Adamu ba mace ce ta haife shi ba, amma wannan wata hanya ce na yin magana game da dukkan 'yan Adam. AT: "cikin dukkan mutane da suka taba rayuwa"
AT: "Yahaya Mai Baftisma ya fi kowa girma" ko "Yahaya Mai Baftisma shine mafi muhimanci"
A nan "Mulkin sama" na nufin mulkin Allah a matsayin Sarki. Maganan nan "mulkin sama" Matiyu ne kawai ya yi amfani da shi. In mai yiwuwa ne, to sai ku cigaba da amfani da "sama" a juyin ku. AT: "mafi kankanata a karƙashin mulkin Allahmu a cikin sama"
"ya fi Yahaya muhimanci"
Tun daga lokacin da Yahaya Mai Baftisma ya fara wa'azi sakonsa." Kalman nan "lokaci" mai yiwuwa na nufin watanni ko shekaru.
Akwai fasarar wannan aya daban dabam. UDB na ɗaukan cewa wasu mutane na so su yi amfani da mulkin Allah don son ransu, saboda da haka suna shirye su musguna wa sauran mutane don su cikata wannan. Wasu juyin suna ɗaukan cewa kira don shiga mulkin Allah ta zama cikin gaggawa, saboda haka lallai ne mutane su yi kowace abin da za su iya yi don su amsa wannan kira, su kuma guje wa gwaji ta cigaba da yin zunubi. Fasara ta uku shine cewa mutane masu kawo hargitsi na yi wa mutanen Allah lahani don haka suna koƙarin hana Allah mulki.
A nan "annabawa da shari'a" na nufin abubuwan da annabawa da Musa suka rubuta a nassi. AT: "Waɗannan sune abubuwan da annabawa da Musa suka yi annabcinsa tawurin nassosin har zuwa lokacin Yahaya Mai Baftisma"
"ku" na nufin taron mutane.
Kalman nan "shi" na nufin Yahaya Mai Baftisma. Ba wai wannan na nufin cewa Yahaya Mai Baftisma shine Iliya ba. Yesu yana nufin cewa Yahaya Mai Baftisma ya cika annabcin da aka yi game da "Iliya wanda zai zo" ko Iliya mai zuwa. AT: "sa'ad da annabi Malachi ya ce cewa Iliya zai dawo, yana magana ne game da Yahaya Mai Baftisma."
Wannan wata hanya ce da ake nufin kowane mutum da ke jin abin da Yesu ke faɗa. AT: "Duk wanda zai iya ji na"
A nan "kassa kunne" na nufin sa hankali ga abinda ake faɗa. AT: "kassa kunne ga abin da nake faɗa"
Yasu ya yi amfani da wannan tambaya don ya gabatar da kwatancinsa da mutane a lokacinsa da da kuma abin da 'ya'ya sa su ce a cikin kasuwa. AT: "Wannan shine kamanin wannan zamani"
"mutanen da ke rayuwa a yanzu" ko "waɗannan mutane" ko "ku mutanen wannan zamani"
Yesu ya yi amfani da wannan misălin don bayana irin mutanen da ke rayuwa a lokacinsa. Ya kwatanta su da 'ya'yan da ke koƙarin sa sauran 'ya'ya su yi wasa tare da su. Amma duk koƙarin da suka yi, sauran 'ya'yan ba za su haɗa kai da su ba. Yesu na nufin cewa ba lallai ne a ce in Allah ya aiko da wani kamar Yahaya Mai Baftisma, wanda ya yi rayuwa a jeji ya kuma yi azumi, ko wani kamar Yesu wanda ya yi murna a wurin biki da masu zunubi bai kuma yi azumi ba. Mutanen nan, musamman Farisiyawa da kuma shugabannen adini su taurare sun kuma ƙi su karɓi gaskiyar Allah.
wani babban wuri wanda mutane ke sayar da siyan abubuwa.
"mu" na nufin 'ya'ya da ke a kasuwa. Anan "ku" na nufin rukuni sauran 'ya'yan.
"amma ba ku yi rawa ba ga kiɗa ta murna ba"
Wannan na nufin cewa sin yi wakar baƙin ciki kamar wand mataye ke yi a wurin jana'iza.
"amma ba ku yi kuka tare da mu ba"
A nan "gurasa" na nufin abinci. Wannan ba ya nufin cewa Yahaya bai taba cin abince ba. Yana nufin cewa sau da dăma yana azumi, kuma a lokacin da ya ci abinci, bai ci abinci mai kyau ko mai tsada ba. AT: "Sau da dama yana azumi kuma ba ya shan barasa" ko "ba ya cin abinci mai kyau ba ya kuma shan ruwan inabi"
AT: sun ce wai yana da aljannu" ko "sun zargi shi cewa yana da aljannu"
Dukkan bayyanuwar kalman nan "su" na nufin mutane a wancan zamani musamman Farisiyawa da shugabannen adini.
Yesu yana nufin kansa. AT: "Ni, Ɗan Mutum na zo"
Wannan ya sha banbam da halin Yahaya. Wannan nufin ci fiye da sha fiye da yadda ya kamata. Yana nufin cewa Yesu ya yi biki ya kuma ci abinci mai kyau ya kuma sha daidai kamar sauran mutane.
AT: "sun ce wai shi mutum mai handama ne mashayi kuma ...masu zunubi." ko "sun zargi shi cewa yana ci yana kuma sha fiye da yadda ya kamata kuma shi... masu zunubi."
"shi mai handama ne" ko "a kodayaushe yana ci fiye da yadda ya kamata"
"bugagge" ko "ya cigaba da shan barasa so sai"
wannan wani karin magana ne da Yesu ya yi amfani da wannan a yanayin saboda mutanene da su ƙi shi da Yahaya su maras hikima ne. Yesu da Yahaya Mai Baftisma su masu hikima ne, kuma sakamakon ayyukansu ta tabbatar da ita.
A nan "hikima" an bayyana ta kamar mace da an tabbatar cewa ayyukan nagari ne. Yesu yana nufin cewa sakamakon ayyukan mutum mai hikima na nuna tabbacin cewa lallai shi mai hikima ne. AT: "sakamakom ayyukan mutum mai hikima yana ba da tabbacin cewa shi mai hikima ne"
Anan "biranen" na nufin mutanen da ke rayuwa a cikin ta. AT: "tsautawa mutane birane"
"gari"
"manya-manyan aiki" ko "aiki iko" ko "mu'ujizai"
Yesu ya yi magana kamar mutanen biranen Korasinu da Betsaida suna wurin kuma suna jin shi, amma ba sa ji
"Zai zama maki da muni." Anan "ki" na nufin birnin. In zai fi sauki a yi amfani da kalman nan "ku" a sa'ad da ake nufin mutane maimakon birni, to sai ku yi amfani da shi a juyin ku.
Sunayen waɗannan biranen na nufin mutanen da ke zama cikin waɗannan birane.
Yesu yana bayana wata yanayi ta musamman da zai iya faruwa a dă amma bai faru ba.
AT: "In da a ce na yi ayuka masu ban mamaki a tsakanin mutanen Taya da Sidon wanda na yi a tsakaninku"
A nan "ku" na nufin Korazinu da Betsaida. In ya fi sauki a harshenku, za ku iya yin amfani da "ku" a maɗaɗɗin birane biyun ko "ku" a maɗaɗɗin mutanen biranen.
"su" na nufin mutanen Taya da Sidon.
"da sun nuna cewa sun damu saboda zunubansu"
A nan "Taya da Sidon" na nufin mutanen da ke zama a wurin. AT: "Allah zai nuna jinkai ga mutanen da ke Taya da Sidon a ranar shari'a fiye da ku" ko "Allah zai yi muku hunkucin mai tsanani a ranar shari'a fiye da mutanen Taya da Sidon"
A nan iya bayana abin nufin anan a fili. AT: "fiye da ku domin ba ku tuba kun bada gasikiya a gare ni ba, kodashike kun ga mu'ujizan da na yi"
Yesu na magana da mutanen birnin Kafarnahum kamar suna jin shi, amma ba sa kuwa ji. Kalman nan "ke" na nufin Kafarnahum a gabaɗayan waɗannan ayoyi biyun.
In ya fi sauki ayi amfani da "ku" a sa'ad da ana nufin mutanen birnin, to za ku iya yi amfani da shi a juyin ku.
Sunayen waɗannan biranen na nufin mutane da ke zama a Kafarnahum da Saduma.
"kina tsammanin za a ɗauke ki zuwa sama?" Yesu ya yi tambayar ganganci don ya tsautawa matanen da ke Kafarnahum saboda girman kan su. AT: "ba za ki iya ɗauke kan ku zuwa sama ba!" ko "yabon da wasu ke yi miki ba za ta kai ki sama ba!" ko "Allah ba zai kai ki sama ba kamar yadda ki ke tunani zai yi!"
AT: "Allah zai kai ku zuwa Hades"
Yesu ya bayana wata misalin yanayin da dă zai iya aukuwa amma bai auku ba.
AT: "In da a ce na yi manyan ayuka a tsakanin mutanen Saduma irin wanda na yi a tsakanin ku"
Kalman nan "ta" na nufin birnin Saduma.
Wannan magana na kara nanata abin da Yesu ya faɗa a gaba.
A nan "ƙasar Saduma" na nufin mutane mutanen dake zama a wurin. AT: "Allah zai nuna jinkansa ga mutanen Saduma a ranar shari'a fiye da ku" ko "Allah zai yi maku hukunci mai tsanani fiye da mutanen Saduma a ranar shari'a"
Wannan lakabi mai muhimmanci ne na Allah.
"Ubangiji mai mulkin sama da duniya." "sama da duniya" na nufin dukkan mutane da abubuwan da ke cikin duniya gabakiɗaya. AT: "Ubangiji mai mulkin dukkan duniya"
Ma'anar kalmomin "waɗannan abubuwa." ba ya a fili. In harshen ku na bukatan bayana abin nufi, to wannan juyin zai zama mafi kyau a yi amfani da shi. AT: "ka ɓoye waɗannan gaskiyar ... ka bayyana su"
"ba ka sa waɗannan abubuwa su zama sanane ga." Wannan aikatau sabo ne da "bayyana"
AT: "ga mutanen masu hikima da fahimta"
Yesu ba ya tunanin cewa mutanen nan suna da hikima. AT: "mutanen da ke tunanin cewa suna da hikima da fahimta"
"sa su zama sananne." Kalman nan "su" na nufin "waɗannan abubuwa" a baya cikin wannan aya.
Yesu ya kwatanta mutane jãhilai da 'ya'ya kanana. Yesu ya nanata cewa mutane da yawa da suka gaskanta da shi ba a koyar da su da kyau ba ko kuwa ba sa tunanin kansu a matsayin masu hikima.
Maganan nan "a gare ka" na nufin yadda mutane ke duban wani abu. AT: "gama ka ga ya kyautu ka yi wannan"
AT: "Ubana ya mallaka mani dukkan kome" ko "Ubana ya mika mini dukkan kome
Ma'anar mai yiwuwa na kamar haka 1) Allah Uba ya bayyana dukkan abubuwa game da kansa da mulkinsa ga Yesu ko 2) Allah ya mika dukkan iko ga Yesu.
Wannan lakabi ne mai muhimmanci na Allah da ke bayana dangantakan Allah da Yesu.
"Uban kaɗai ne ya san Ɗan"
Kalman nan "san" anan na nufin fiye da idan sani wani. Yana nufin sani wani na kwarai saboda dangantaka ta musamman da shi.
Yesu na duban kansa a matsayin na uku.
Wannan lakabi ne mai muhimmanci na Yesu, Ɗan Allah.
"Ɗan kaɗai ya san Uban"
Yesu ya yi magana game da mutanen da sun raunana cikin koƙarinsu su yi biyayya ga dukkan dokoki kamar dokokin kaya ne mai nauyi kuma mutane da shan wahalan ɗaukansu. AT: "wanda ya raunana daga koƙarin" ko "waɗanda suka raunana daga koƙarin yi matuƙar biyayya da dokokin"
"Zan bar ku ku huta daga wahala da nauyi"
Yesu yana kiran mutane su zo su zama almajiransa da masubin sa.
A nan "tawali'u" da "saukin halin zuciya" a takaice na nufin abu ɗaya. Yesu ya haɗa su don ya nanata cewa shi zai yi kirki fiye da shugabannen adini. AT: "Ni mai saukin kai ne da kuma tawali'u" ko "Ni mai matuƙar saukin kai ne"
A nan "zuciya" na nufin cikin mutum. Maganan nan "saukin halin zuciya" na nufin "kaskanci" AT: "Kaskanci"
kalman "rayuka" na nufin mutum gabaɗaya. AT: "za ku sami hutawa" ko "za ku iya hutawa"
Duk waɗannan maganganu na nufin abu ɗaya. Yesu na nanata cewa ya fi sauki a yi masa biyayya fiye da shari'ar Yahudawa. AT: "Gama abin da na sa a kanku, za ku iya ɗauka wa domin ba shi da nauyi.
Kalman "ba shi da nauyi" anan dabam ne da nauyi ba kuma duhu.
1A wannan lokaci, Yesu ya tafi a ranar Asabaci, ya bi cikin gonar hatsi. Almajiransa na jin yunwa, sai suka fara zagar hatsi suna ci. 2Amma da Farisawa suka gan su, sai su ka ce wa Yesu. "Duba, almajiranka su na yin abin da doka ta haramta a ranar Asabaci."3Amma Yesu ya ce masu, "Baku karanta abin da Dauda ya yi ba, lokacin da ya ke jin yunwa, tare da mazan da ke tare da shi? 4Yadda ya shiga gidan Allah, ya ci gurasar alfarwa da doka ta hana shi ko mazan da ke tare da shi su ci, sai dai Firistoci ne kawai doka ta basu damar ci?5Sa'annan ba ku karanta cikin shari'a cewa, a ranar Asabaci, Firistoci da ke cikin haikali na sabawa ranar Asabaci, amma kamar ba su yi laifi ba? 6Amma ina tabbatar maku da cewa, wani wanda ya fi haikali girma yana nan.7In da kun san ma'anar wannan 'Na fi son jinkai fiye da hadaya,' da baku shari'anta wa marar laifi ba. 8Gama Dan mutum shine Ubangijin Asabaci."9Sa'annan Yesu ya bar wannan wuri, ya shiga majami'ar su. 10Sai ga wani mutum wanda hannun sa ya shanye, sai Farisawa suka tambayi Yesu, cewa, "Doka ta halarta a yi warkarwa a ranar Asabaci?" Domin su zarge shi a kan zunubi.11Yesu ya ce masu, "Wanene a cikin ku, wanda idan ya na da tunkiya guda, sa'annan tunkiyar nan ta fada a rami mai zurfi a ranar Asabaci ba zai kamo ta ya fitar da ita ba? 12Yaya za a kwatanta darajar mutum da tunkiya! Saboda haka ya halarta a yi alheri ranar Asabaci."13Sai Yesu ya ce wa mutumin nan "Mika hannun ka." Ya mike hannunsa, sai hannun nan ya dawo lafiyaye kamar dayan hannunsa. 14Amma Farisawa su ka fita waje su ka fara mugun shiri domin sa. Su na neman hanyar da za su kashe shi.15Da Yesu ya fahimci wannan, sai ya janye kan sa daga nan. Mutane da dama su ka bi shi, ya warkar da su duka. 16Ya dokace su da kada su bayyana shi ga kowa, 17domin ya zama gaskiyar abin da aka fada ta wurin annabi Ishaya, cewa,18"Dubi, bawa na zababbe; kaunatacce na, wanda ya ke faranta mani raina sosai. Zan sa Ruhu na bisan sa, za ya furta hukunci zuwa al'ummai.19Ba za ya yi jayayya ko tada murya ba, babu wanda za ya ji muryar sa a karabku. 20Ba zai karya kara da ya tankwashe ba; ba zai kashe fitilar da ta kusa mutuwa ba; sai ya kawo hukunci ga nasara. 21Sa'annan al'ummai za su dogara a ga sunansa.22Sa'annan wani mutum, makaho ne, kurma kuma, aljannu kuma na cikinsa, an kawo shi wurin Yesu. Ya warkar da shi, ya sami ganin gari ya kuma yi magana. 23Jama'a su ka yi mamaki kwarai, su na cewa, "Ko wannan ne Dan Dawuda?"24Amma da Farisawa su ka ji wannan al'ajibi, sai su ka ce, "Mutumin nan yana fitar da aljannu ta wurin Bahalzabuba sarkin aljannu ne." 25Amma Yesu ya san tunanin su, sai ya ce. "Duk mulkin da ya rabu gaba da kan sa, ba zaya tsaya ba, duk wani birni da ya rabu ba zai tsaya ba, ko gida da ya tsage, za ya rushe.26Idan Shaidan ya fitar da Shaidan, ya rabu gaba da kansa. Yaya mulkin sa za ya tsaya? 27Idan Ina fitar da aljannu da ikon Ba'alzabuba, ta wurin wa masu bin ku su ke fitar da su? Saboda haka, su za su shari'anta ku.28Amma idan ina fitar da aljannu da Ruhun Allah ne, hakika mulkin Allah ya zo gare ku. 29Kuma ta yaya mutum za ya shiga gidan mai karfi ya kwashe masa kaya ba tare da ya fara daure shi ba? Sa'annan ne za ya iya satar masa kaya daga gidansa. 30Wanda baya tare da ni yana gaba da ni ke nan, wanda kuma baya tarawa tare da ni, yana watsarwa ne.31Saboda haka ina ce maku, kowanne zunubi da sabo, za a gafarta wa mutum, amma sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta shi ba. 32Duk wanda yayi batanci ga Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma duk wanda yayi batanci game da Ruhu Mai Tsarki ba za a gafarta masa ba, a nan duniya da har abada.33Ko dai a mai da itace mai kyau 'ya'yansa kuma su yi kyau, ko a mai da itace marar kyau 'ya'yansa kuma marasa kyau, gama ana sanin itace ta wurin 'ya'yansa. 34Ku 'ya'yan macizai, tun da ku miyagu ne, yaya za ku iya fadin abubuwa nagari? Gama daga cikar zuciya baki ke magana. 35Mutumin kirki daga ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwa masu kyau, mugun mutum kuma daga mummunar ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwan mugunta.36Sa'annan ina ce maku a ranar shari'a, mutane za su bada lissafin abubuwan banza da su ka fadi. 37Gama ta wurin maganganun ku, za a 'yantar da ku, ta wurin maganganun ku kuma za a kashe ku."38Sa'annan wadansu Malaman Attaura, da Farisawa suka amsa suka ce wa Yesu, "Mallam, muna so mu ga wata alama daga gare ka."39Amma Yesu ya amsa ya ce masu, "Mugun zamani da mazinaciyar tsara, su na bukutar alama. Amma babu alamar da za a ba su, sai dai alamar annabi Yunusa. 40Gama yadda Yunusa ya yi kwana uku da dare uku a cikin babban kifi, haka ma Dan Mutum zaya yi kwana uku da dare uku a cikin zuciyar kasa.41Mutanen Nineba za su tsaya a ranar shari'a da wannan zamani sannan su kashe su. Domin sun tuba da suka ji wa'azin Yunusa, amma duba wanda ya fi Yunusa yana nan.42Sarauniyar Kudu za ta tashi da mutanen wannan zamani ta kuma kashe su. Ta zo daga karshen duniya domin ta ji hikimar Sulaimanu, kuma duba, wanda ya fi Sulaimanu yana nan.43Idan kazamin ruhu ya rabu da mutum, ya kan wuce ya nemi wuraren da ruwa yake domin ya huta, amma bai samu ba. 44Sai ya ce, 'zan koma gidana inda na fito'. Bayan ya dawo, sai ya tarar da gidan nan an share shi ya zama da tsabta. 45Sai ya koma ya kawo wadansu ruhohi guda bakwai, wadanda su ka fi shi mugunta, sa'annan dukan su su zo su zauna a nan. Sa'annan yanayin mutumin nan na karshe ya fi na farko muni. Haka zaya kasance ga wannan mugun zamani.46Sa'adda Yesu ya ke yi wa Jama'a jawabi, sai mahaifiyarsa da 'yan'uwansa su ka zo su ka tsaya a waje, suna neman su yi magana da shi. 47Sai wani ya ce masa, "Duba, mahaifiyarka da 'yan'uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai".48Amma Yesu ya amsa ya ce wa shi wanda ya gaya masa, "Wacece mahaifiyata? Kuma su wanene 'yan'uwana?" 49Sai ya mika hannu ya nuna almajiransa ya ce, "Duba, ga mahaifiyata da 'yan'uwana! 50Gama duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda ya ke cikin sama, shine dan'uwana, da 'yar'uwata da mahaifiyata."
Wannan farkon sashin labarin inda Matiyu ya bayana gãbã mutane domin aikin Yesu. Anan, Farisawa suna zargin almajiransa don suna tsine kwayar hatsi a ranar Asabar.
Wannan alama ce na sabuwar bangaren labarin. AT: "jim kaɗan"
wurin shukin hatsi. In ba a san alkama ba kuma kowa ya san "hatsi" to za ku iya amfani da "gonar tsire tsire da suke amfani da shi su yi gurasa"
Zagar hatsi a gonar wasu a ci ba a dubansa a matsayin sata. Tambayar ita ce ko mutum zai iya yin wannan abin da doka ta haramta a ranar Asabar.
"zagar wasu alkama suna ci" ko "zagar wasu hatsin suna ci"
Wannan na nufin saman alkama. Ta na rike hatsi da sun nuna ko iri.
Wannan ba ta nufin cewa dukkan Farisawan. AT: "wasu Farisiyawa"
Farisawan sun yi amfani da wannan kalman don su jawo hankalin mutane zuwa ga abin da almajiran suke yi.
Yesu ya amsa zargin da Farisiyawan.
"ga Farisawan"
Yesu ya yi amfani da tambaya don ya amsa zargin Farisawan. Yesu us kalubalance su su yi tunani game da ma'anar nassosin da suka karanta. AT: "Na san cewa kin karanta game da ... tare da shi"
ba bu haikali a zamanin sarki Dauda. AT: "alfarwa" ko "wurin yi wa Allah sujada"
Wannan gurasa ce mai tsarki da Firist ke ajiyewa a gaban Allah cikin alfarwa. AT: "gurasar da Firist ya ajiye a gaban Allah" ko "gurasa mai tsarki"
"mazan da ke tare da Dauda"
"amma, bisa ga doka, Firist zai iya ci"
Yesu ya yi amfani da tambaya don ya amsa zarginsa da Farisawa ke yi. Yesu ya kalubalance su, su yi tunani game da ma'anar abin da suka karanta a nassosin. AT: "Na tabbata kun karanta a cikin shariyar Musa cewa ... amma ba su da." ko "yakamata kun san cewa shariya ta koyar ... amma ba ku amince da laifinku."
"yi abin da za su iya yi a kowace ranar, a ranar Asabar"
"Allah ba zai hukunta su ba" ko "Allah ba ya duban su a matsayin masu laifi"
Wannan ya kara nanata abin da Yesu ya faɗa a gaba.
"wani wanda ya fi haikali muhimmanci." Yesu na nufin cewa shine wanda ya fi girma.
Yesu ya ɗauka daga nassi. AT: "Annabi Yusha'u ya rubuta wannan a dă: 'jinkai nake biɗa ba hadaya ba.' Da a ce kun fahimci ma'anar wannan, da baku shara'anta marasa laifi ba"
A cikin shariyar Musa, Allah ya umurci Isra'ilawa su mika hadaya. Wannan na nufin cewa Allah ya fi duban jinkai a matsayin mafi muhimmancin fiye da hadayu.
Kalman "nake" na nufin Allah.
AT: "waɗanda ba su da laifi"
Yesu na nufin kansa ne.
"mai mulkin Asabaci" ko "sa dokoki game da abin da mutane za su iya yi a ranar Asabar"
"Yesu ya bar gonar hatsin" ko "Sai yesu ya tafi"
Ma'ana mai yiwuwa 1) kalman nan "su" na nufin Yahudawan wannan gari. AT: "majami'an" ko 2) kalman nan "su" na nufin Farisawan da Yesu ya yi magana da su da sauran Yahudawan da suka zo garin. Kalman nan "su" baya nufin cewa majami'an na Farisawa ne. AT: "majami'an da suka shiga"
Kalman "sai ga" jawo hankalin mu zuwa ga sabon mutum a cikin labarin. Mai yiwuwa harshen ku na da wata hanyan yin wannan.
"mutum wanda hannunsa a gurgunce"
"Farisawan suna so su zargi Yesu a kan zunubi, sai suka tambaye shi, "ya kyautu a yi warkarwa a ranar Asabar?"
"Bisa ga shariyar Musa, a iya warkar da wani a ranar Asabar"
Ba wai kawai suna so su zarge Yesu a gaban mutane ba. Farisawan suna so Yesu ya ba su amsar da bai yi daidai da shariyar Musa ba don su kai shi gaban alkali nan kuma su dora masa laifin karye doka.
Yesu ya yi amfani da tambaya don ya bada amsa ga Farisawan. Ya kalubalance su su yi tunani game da irin aiki da suke yi a ranar Asabar. AT: "Kowannen ku, In a ce kuna da tunkiya ɗaya ... zai kama tinkiyan ya fitar da ita."
Maganan nan "yaya za a" na kara nanata maganan ne. AT: "Lallai hakika, mutum ya fi tunkiya daraja!" ko "Yi tunani game da muhimmancin mutum fiye da tunkiya"
"waɗanda suka yi ayuka nagari suna biyayya da dokar ranar Asabar"
AT: "Sai Yesu ya umurce mutumin ya mika hannunsa"
"mutumin da ke da shanyayyen hannu"
"Rike hannunka"
"Mutumin ya mika"
AT: "ya warke" ko "ya zama lafiyayye kuma"
"shiri su yi wa Yesu lahani"
"na tattauna yadda za su yi su kashe Yesu"
"Yesu na sane da abin da Farisiyawan na shirin yi , sai ya"
"bar wurin" ko "bar"
"kada ya gaya wa wani game da shi"
Maganan nan "domin ya zama gaskiyar" ana iya juya shi a farkon jimlar. AT: "kada ya sa wasu su san shi. wannan don a cika abin da"
AT: "Abin da Allah ya faɗa tun dă ta wurin annabi Ishaya"
"Duba" ko kassa kunne" ko "kassa kunne ga abin da zan faɗa maku"
Duk aukuwar wannan kalman na nufin Allah. Ishaya faɗi abin da Allah ya gaya masa.
"shi ƙaunatacce na ne, kuma ina farinciki da shi"
A nan "rai" na nufin mutum gabaɗayansa. AT: wanda nake farinciki da shi"
Hanyar da bawan Allah zai faɗa wa al'ummai cewa akwai hukunci. Ana iya bayana a fili cewa Allah shine wanda zai kawo hukunci, ana iya bayana "hukunci" a matsayin "abin da ke daidai." AT: "zai shaida wa al'ummai cewa Allah zai yi masu abin da ke daidai"
A nan rashin jin muryar na wakilcin rashin magana da karfi. AT: "ba zai yi magana da karfi ba"
Duk aukuwar waɗannnan kalmomin na nufin zaɓaɓɓen bawan Allah.
Wannan na nufin "a fili." AT: "a birane da garuruwa"
Duk magana biyu nan na nufin abu ɗaya. Suna kuma nanata cewa bawan Allah zai zama mai saukin kai da alheri. "karya kara da ya tanƙwashe" da "kusa mutuwa" na nufin mutane marasa karfin da an yi masu rauni. idan wannan na rikitar da ku, za ku iya juya zahirin ma'anan. AT: "zai yi kirki ga mutane marasa karfi, zai kuma zama mai saukin kai ga waɗanda aka yi wa rauni"
"tsiren da ya lalace"
"ba zai hana wata wuta ci ba"
Wannan na nufin fitilar da ta mutu an bar hayakin ne kaɗai.
Ana iya juya wanna cikin sabuwar jimla: "... Wannan shine abin da zai yi har"
Kai wani ga nasara na nufin a sa shi ya yi nasara. Sa hukunci ta yi nasara na nufin daidai abubuwa da sun lalace. AT: "ya na daidai kowane abu"
A nan "suna" na nufin mutum gabakiɗaya. AT: "cikin sa"
AT: "Sai wani ya kawo wa Yesu wani mutum wanda makaho ne kuma kurma ne domin aljannu na shugabncinsa"
"wani wanda baya gani bai iya magana ba kuma"
Dukkan mutanen da suka gan lokacin da Yesu ya warkar da mutumin sun yi mamaki ƙwarai da gaske"
Wannan lakabi ne na Almasihu ko Mai Ceto.
A nan na nufin "daga zuriyan"
Wannan na nufin al'ajibin na warkar da makaho, kurma, da mutum mai ajan.
AT: "Wannan mutum ya iya fid a ajan saboda shi bawan Ba'alzabul"
Farisiyawan sun ƙi kiran Yesu da sunansa don su nuna cewa sun ƙi.
"shugaban aljannu"
Yesu ya yi amfani da karin magana don ya amsa wa Farisiyawan. Maganganun nan biyu na nufin abu ɗaya ne. Sun nanata cewa zai zama da ma'ana ba Ba'alzabul ya yi amfani da ikonsa ya yi yaki da ajannu.
A nan "mulki" na nufin waɗanda ke zaman a mulkin. AT: "mulkin ba zai jima ba in har mutanen na yaki tsakaninsu"
A nan "birni" na nufin mutane dake zama a wurin, "gida" kuma na nufin iyali. "rabu" na nufin mutanen na fada da juna. AT: "yana rushe birni ko iyali in mutanen na fada da juna"
Yin amfani da Shaiɗan na biyun na nufin ajannu da ke bautawa Shaiɗan. AT: "Idan Shaiɗan ya găba da aljannunsa"
Duka biyun suna nufin mutum ɗaya.
Yesu ya yi amfani da tambaya don ya nuna wa Farisawan cewa abin da suke faɗi ba shi da ma'ana. AT: "Idan Shaiɗan ya rabu găba da kansa, mulkinsa ba zai tsaya ba!" ko "Idan Shaiɗan na yaki da aljannunsa, mulkinsa ba zai jima ba!"
Yesu ya yi amfani da wani tambaya don ya kalubalanci Farisawa. AT: "to sai ku ce masu bin ma na fitar da ajannu ta wurin ikon Ba'alzabul. Amma kun san cewa wannan ba gaskiya ba ne."
Yesu yana magana da Farisawan. Kalmomin nan "'ya'yan ku" na nufin masubinsu. Wannan wata hanya ce da aka saba amfani da ita sa'ad da ake nufin masubin malamai ko kuwa shugabanne. AT: "masubin ku"
"domin masubin ku na fitar da aljannu ta wurin ikon Allah, sun nuna cewa ba ku yi daidai game da ni ba."
A nan "idan" ba ta nufin cewa Yesu na shakkan yadda yake cire Aljannu. Anan Yesu ya yi amfani da kalman nan don ya gabatar da gaskiyar maganarsa. AT: "Amma domin ina"
"hakika mulkin Allah ya zo tsakanin ku." Anan "mulkin" na nufin mulkin Allah a matsayin sarki. AT: "wannan na nufin Allah ya kafa mulkinsa a tsakanin ku"
A nan "ku" na nufin mutanen Isra'ila
Yesu ya yi amfani da misali don ya cigaba da ba wa Farisawan amsa. Yesu na nufin cewa zai iya cire ajannu saboda ya fi Shaɗan Iko.
Yesu ya yi amfani da tambaya don ya koya wa Farisawan da kuma taron. AT: "Babu wanda zai iya shiga ... ba tare da ya fara ɗaure mutum mai karfin ba" ko "In wani yana so ya shiga ... dole ne ya fara ɗaure mutumin nan mai karfi."
"ba tare da ya fara mulkin mutum mai ƙarfin ba"
"Sa'annan zai yi sata" ko "to zai iya sata"
"wanda ba ya goyon baya na" ko "wanda ba ya aiki tare da ni"
"na hamayya da ni" ko "aiki găba da ni"
Yesu ya yi amfani da karin magana da ke nufin mutane na tattara garkin tumaki zuwa ga makiyayi ko kuwa suna sa su su yi nesa da makiyayin. Yesu yana nufin cewa mutum na koƙarin sa mutane su zama almajiran Yesu ko yana sa mutane su ƙi Yesu.
Yesu na magana ne da Farisiyawa, yana kuma koyawa taron.
AT: "Allah zai gafarta kowane zunubi da mutane suka yi da kowane mugun abu da sun faɗa" ko "Allah zai gafarta wa kowane mutum da ya yi zunubi ko faɗa mugun abubuwa"
AT: "Allah ba zai yafe wa mutumin da ya faɗi mugun abubuwa game da Ruhu Mai Tsarki ba"
Anan "kalma" na nufin abin da mutum ya faɗa. AT: "In wani mutum ya faɗi wani mugun abu game da Ɗan Mutum"
Yesu yana magana ne game da kansa.
AT: "Allah zai gafarta wa mutumin wannan"
AT: "Allah ba zai gafarta wa mutumin nan ba"
A nan "wannan duniya" da "wanda ke zuwa" na nufin rayuwa ta yanzu da nan gaba. AT: "a wannan rayuwa ko kuwa rayuwa a nan gaba" ko "yanzu ko har abada"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) "in kun sa itace ta yi kyau, to 'ya'yan ta ma sai ta yi kyau, un kuma kun sa itace ta zama mara kyau to 'ya'yanta ma sai ta zama mara kyau" ko 2) "in kun dubi itace a matsayin mai kyau, yana yiwuwa saboda 'ya'yan ta masu kyau ne, in kuwa kun dubi itace a matsayin mara kyau, to mai yiwuwa saboda 'ya'yan ta mara kyau ne." Wannan karin magana ne. Mutanen da za su yi amfani da gaskiyar ta don sani yadda za su san ko mutum nagari ne ko mugu.
"lafiyayye ... mai cuta"
"'ya'ya" anan na nufin ayyukan mutum. AT: "mutane suna sanin ko itace mai kyau ne ko mara kyau ta wurin duban 'ya'yan ta" ko "mutane sun san ko mutum nagari ne ko mugu ta wurin duban sakamakon ayyukan wannan mutum"
Anan "'ya'yan" na nufin " samu halayyan." Macizai anan na nufin macizai masu dafi kuma mugaye, macizai kuma na wakilkcin mugu. Dubi yadda kuka juya magana makamanci haka cikin [Matiyu 3:7]
Wannan na nufin Farisiyawa.
Yesu ya yi amfani da tambaya don ya sauta wa Farisiyawan. AT: "ba za ku iya faɗi abubuwa nagari ba." ko "kun iya faɗi miyagun abubuwa ne kawai."
A nan "zuciya" na nufin tunanin zuciyar mutum. Anan "baki" na nufin mutum gabakiɗayansa. AT: "abin da mutum ya faɗa da bakinsa na bayyana abin da ke zuciyarsa"
Yesu yana magana game da "zuciya" kamar wata bokiti ne da mutum ya cika ta da abubuwa masu kyau ko mummuna. Wannan magana ce da ke nufin abin da mutum ya faɗa na bayyana yadda mutumin yake. In kuna so ku iya amfani da wannan siffar, to ku dubi UDB. Kuna kuma iya juya zahirin ma'anan wannan. AT: "Mutum dake nagari zai yi maganan abubuwa masu kyau, mugun mutum kuwa zai yi maganan miyagun abubuwa"
"Allah zai tambaye mutane game da" ko "Lalle ne mutane su bayana wa Allah"
A nan "kalma" na nufin abin da wani ya faɗa. AT: "kowane abin cutaswa da suka faɗa"
AT: "Allah zai kuɓutar da ku ... Allah zai hukunta ka"
"muna buƙata"
Za ku iya bayyana a fili dalilin da ya sa suna so su ga alama. AT: "mu ga alama daga gare da ta tabbatar cewa abin da ka faɗa gaskiya ne"
Yesu na magana da mutanen zamaninsa. AT: "Ku muguwar zamani da mazinaciyar tsara wanda ke neman alama a gare ni ... za a ba ku"
A nan "mazinaciyar" na nufin mutanen da ba su da aminci a gaban Allah. AT: "tsara marasa aminci" ko "tsara marasa bin Allah"
Yesu ba zai nuna masu wata alama ba domin kodashike ya riga ya yi mu'ujiza masu yawa duk da haka sun ƙi su gaskanta da shi. AT: "ba zan ba ta wata alama ba" ko "Allah ba zai ba ku wata alama ba"
"sai dai irin alama da Allah ya ba wa annabi Yunusa"
A nan "kwana" da "dare" na nufin sa'a 24. AT: "kwanaki uku"
"'yan kasar Nineba"
"sa'ad da Allah zai shara'anta mutane"
Wannan na nufin mutane da ke rayuwa a lokacin da Yesu na wa'azi.
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) "kayas" anan na nufin zargi. AT: " za si kuma zargi wannan tsara" ko 2) Allah zai kayas da wannan tsara domin ba su tuba kamar yadda mutanen Nineba suka tuba ba. AT: "Allah kuma zai kayas da wannan tsara"
"duba." Wannan na nanata abin da Yesu ya faɗa a nan gaba.
"wani wanda ya fi muhimmanci"
Yesu na magana game da kansa.
Za ku iya bayana a fili abun da Yesu ke nufi a maganarsa. AT: "fiye da Yunusa na nan, duk da haka ba ku tuba ba, wannan ita ce dalilin da Allah zai kayar da ku"
Wannan na nufin Sarauniya Sheba. Sheba wata kasa ce a kudunci Isra'ila.
za ta tsaya a ranar shari'a"
Wannan na nufin mutanen da ke rayuwa a lokacin da Yesu ke wa'azi.
Dubi yadda ka juya magana makamancin haka cikin [Matiyu 12:41]. Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) "kayas" anan na nufin zargi. AT: " za si kuma zargi wannan tsara" ko 2) Allah zai kayas da wannan tsara domin ba su kassa kunne ga hikima kamar yadda Sarauniyar Kudu t ayi ba. AT: "Allah kuma zai kayas da wannan tsara"
A nan "karshen duniya" na nufin "nesa". AT: "Ta zo daga wuri mai nisa"
Wannan magana ta bayana dalilin da Sarauniyar Kudu ta kayas da mutane a zamanin Yesu. AT: "Gama ta zo"
Za ku iya bayana abin da maganar Yesu ke nufin a fili. AT: " fi Sulemanu yana nan, duk da haka ba ku kassa kunne ba. Shi ya sa Allah zai kayas da ku"
Yesu ya bada wannan misalin don ya yi wa mutane kashedi game da hasarin rashin bada gaskiya a gare shi.
"wuraren da sun bushe" ko "wuraren da mutane ba sa zama"
A nan "ba" na nufin hutu.
AT: "Don haka, baƙin aljan ya shirya ya koma gidan da ya fito"
Wannan wata karin magana ne na mutumin da baƙin aljan ke rayuwa a dă. AT: "wurin da na bari"
AT: "baƙin aljan ya tarar wani ya share gidan ya kuma addana ta"
A nan kuma "gida" na nufin mutum wanda baƙin aljan ke rayuwa a dă. Anan "share shi ya zama da tsabta" na nufin cewa ba wani wanda ke rayuwa a ciki. Yesu yana nufin cewa a sa'ad da baƙin aljan ya bar mutum, lalle ne mutumin ya gayaci Ruhu Mai Tsarki ya yi rayuwa cikin sa ko kuwa aljanun ya dawo.
Wannan na nufin cewa idan mutanen zamani Yesu ba su bada gaskiya a gare shi su kuma zama almajiransa ba, za su samu kansu a mummunan yanayi fiye da yanayin su na dă kafin ya zo.
Maryamu ce, Uwar Yesu a jiki.
Waɗannan mai yiwuwa wasu 'ya'ya ne da Maryamu ta haifa, amma yana iya yiwuwa wannan kalma "'yan'uwa" anan na nufin ɗan'uwa Yesu.
"so su yi magana"
AT: "Wani ya gaya wa Yesu cewa uwa tasa da 'yan'uwansa na waje kuma suna so su yi magana da shi"
Bayanin saƙon da mutumin ya gaya wa Yesu an fahimice ta filla-filla ba a kuwa maimiata ta anan ba. AT: "wanda ya gaya wa Yesu cewa uwa tasa da 'yan'uwansa sun so su yi magana da shi"
Yesu ya yi amfani da waɗannan tambayoyin don ya koyar mutanen. AT: "Zan gaya maku waɗanda suke uwa ta da 'yan'uwan na"
Wannan na nufin almajiran Yesu iyalin Yesu ne a ruhaniya. Wannan ya fi muhimmanci fiye da zama cikin iyalinsa a jiki.
...
Wannan lakabi ne ma muhimmancin na Allah.
Wannan na nufin cewa duk waɗanda ke biyayya ga Allah su 'yan iyali Yesu ne a ruhaniya. Wannan ya fi muhimmanci fiye da zama cikin iyalinsa a jiki.
1A waccan rana Yesu ya fito daga gida ya zauna a gefen teku. 2Taro mai yawan gaske kuwa suka kewaye shi, sai ya shiga cikin kwalekwale ya zauna. Dukan taron kuwa na tsaye a bakin tekun.3Sai Yesu ya fada masu abubuwa da yawa cikin misalai. Ya ce, "Wani mai shuka, ya tafi yayi shuka. 4Da yayi shukar, wadansu irin suka fadi a kan hanya, sai tsunsaye suka zo suka cinye su. 5Wadansu irin kuwa suka fadi a kan duwatsu, wurin da babu kasa. Nan da nan sai suka tsira, domin kasar babu zurfi. 6Amma da rana ta taso, sai suka yankwane domin ba su yi saiwa ba, suka kuwa bushe suka zube.7Wasu irin kuwa suka fada a cikin kayayuwa. Kayayuwan kuwa suka shake su. 8Wasu irin kuwa suka fada a wuri mai kyau suka ba da tsaba, wani ya ba da dari, wasu sitin, wasu kuma talatin. 9Duk mai kunnen ji, bari ya ji.10Almajiran suka zo suka ce ma Yesu, "Don me ka ke yi wa taron magana da misali?" 11Yesu ya amsa ya ce masu, "An baku 'yanci ku fahimci asiran mulkin sama, amma gare su ba a bayar ba. 12Domin wanda yake da shi, za a kara masa, zai kuma samu dayawan gaske. Amma duk wanda ba shi da shi, sai a dauke har ma abin da yake dashi.13Saboda haka na yi masu magana cikin misalai, amma ko da ya ke sun gani, duk da haka ba su gani ba. Kuma ko da yake sun ji, hakika ba su ji ba, balle ma su fahimta. 14A gare su ne annabcin Ishaya ya cika, wanda yake cewa, "Game da sauraro zaku saurara, amma ba za ku fahimta ba. Game da gani kuma za ku kalla, amma ba za ku gane ba.15Domin zuciyar mutanen nan ta duhunta, sun taurare ga saurare, kuma sun rufe idanunsu domin kada su gani da idanunsu, ko kuwa su ji da kunnuwansu, ko kuwa su fahimta da zukatansu, saboda su juyo kuma in warkar da su'.16Amma idanunku masu albarka ne, domin sun gani, haka ma kunnuwanku, domin sun ji. 17Hakika ina gaya muku, annabawa da mutane dayawa masu aldalci sun yi marmarin ganin abin da kuka gani, amma ba su sami ganin su ba. Sun yi marmarin jin abin da kuka ji, ba su kuwa ji su ba.18Ku saurari misalin nan na mai shuka. 19Idan wani ya ji maganar mulkin sama amma bai fahimce ta ba, sai mugun nan ya zo ya kwace abinda aka shuka a zuciyarsa. Wannan shine irin da aka shuka a kan hanya.20Shi wanda aka shuka akan duwatsu, shine wanda ya ji maganar ya kuma karbe ta da murna nan da nan. 21Duk da haka, bai yi karfi cikin ta ba kuma nan ba da dadaiwa ba. Da wahala da tsanani suka taso saboda maganar, sai ya yi tuntube nan da nan.22Shi wanda aka shuka a cikin kayayuwa wannan shine wanda ya ji maganar, amma dawainiyar duniya da kuma yaudarar dukiya suka shake maganar, sai ya kasa ba da 'ya'ya. 23Shi wanda aka shuka a kasa mai kyau, wannan shine wanda ya ji maganar, ya kuma fahimce ta. Wannan shine wanda ba da 'ya'ya da gaske; wadansu ribi dari, wadansu sittin, wasu kuma talatin."24Yesu ya sake ba su wani misali, yana cewa "Za a kwatanta mulkin sama da wani mutum wanda ya shuka iri mai kyau a gona. 25Amma da mutane suka yi barci, magabcin sa ya zo ya shuka ciyayi a cikin alkamar, ya kuwa yi tafiyarsa. 26Sa'adda suka yi toho suka kuma ba da tsaba, sai ciyayin suka bayyana.27Bayin mai gonar kuwa suka zo suka ce masa, maigida, ashe ba iri mai kyau ka shuka a gonarka ba? ya ya aka yi ta kasance da ciyayi? 28Ya ce masu, "Magabci ne ya yi wannan". Sai bayin suka ce masa, 'kana so mu je mu tuge su ne?'29Mai gonar ya ce, 'A'a, kada a garin tuge ciyayin, ku tuge tare da alkamar. 30Bari dukan su su girma tare har lokacin girbi, a lokacin girbin zan gaya wa masu girbin, "Ku tuge ciyayin da farko a daura su dami dami sai a kona su, amma a tara alkamar a kai rumbunana.'"31Sai Yesu ya sake yin magana da su cikin misalai, yana cewa "Za a kwatanta mulkin sama da kwayar mustad, wanda wani mutum ya shuka a lambunsa. 32Wannan iri shine mafi kankanta cikin dukan iri. Amma bayan ya yi girma, sai ya fi dukan ganyaye dake lambun. Ya zama itace, har ma tsuntsayen sama su yi sheka a rassansa."33Yesu ya sake fada masu wani misali. "Za a kwatanta mulkin sama da yisti da mace takan dauka ta kwaba gari da shi mudu uku har sai ya yi kumburi."34Duk wadannan abubuwa Yesu ya fada wa taron cikin misalai. Babu abinda ya fada masu da ba a cikin misali ba. 35Wannan ya kasance ne domin abinda annabin ya fada ya zama gaskiya, da ya ce, "Zan buda bakina da misali. In fadi abubuwan da ke boye tun daga halittar duniya."36Sai Yesu ya bar taron ya shiga cikin gida. Amajiransa suka zo wurin sa suka ce, "Ka fasarta mana misalan nan a kan ciyayin da ke gonar" 37Yesu ya amsa kuma ya ce, "Shi wanda ya shuka iri mai kyau Dan Mutum ne. 38Gonar kuwa duniya ce; iri mai kyau kuma sune 'ya'yan mulkin. Ciyayin kuma sune 'ya'yan mugun, 39magabcin da ya shuka su kuma shaidan ne. Girbin shine karshen duniya, kuma masu girbin sune mala'iku.40Saboda haka, kamar yadda aka tara ciyayin aka kona su da wuta, haka ma zai faru a karshen duniya. 41Dan Mutum zai aiki mala'ikunsa, kuma su tara dukan abubuwan da ke sa zunubi daga cikin mulkinsa, da kuma wadanda su ka yi aikin mugunta. 42Za su jefa su cikin korama ta wuta, inda za a yi kuka da cizon hakora. 43Sa'an nan ne mutane masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Bari mai kunnen ji, ya ji.44Mulkin sama kamar dukiya ce da ke boye a gona. Mutum ya samu sai ya boye ta, ya tafi cikin murna, ya sayar da mallakarsa kuma ya sayi filin. 45Haka ma za a kwatanta mulkin sama da wani attajiri mai neman Lu'ulu'ai masu daraja. 46Da ya sami lu'ulu'u daya mai darajar gaske, ya je ya sayar da dukan mallakarsa ya kuma saye shi.47Haka kuma, za a kwatanta mulkin sama da taru da aka jefa cikin teku, ya kuwa tara hallitu iri-iri. 48Da ya cika, sai masuntan suka jawo shi bakin tekun. Sai suka zauna suka tara kyawawan abubuwan a taska, amma munanan abubuwan, suka watsar da su.49Haka zai kasance a karshen duniya. Mala'iku za su zo su ware miyagu daga cikin masu adalci. 50Za su jefa su cikin korama ta wuta, inda za a yi kuka da cizon hakora.51Kun fahimci dukan wadannan abubuwa? Amajiran suka ce da shi, "I". 52Sai Yesu ya ce masu, "Saboda haka kowane malamin attaura da ya zama almajirin mulkin sama, yana kamar mutum mai gida wanda ya zaro tsoho da sobon abu daga taskarsa." 53Daga nan, sa'adda Yesu ya kammala ba da wadanan misalai, sai ya tafi ya bar wurin.54Sai Yesu ya shiga yankinsa ya koyar da mutane a masujadarsu. Saboda haka suka yi mamaki suna cewa, "Daga ina wannan mutumin ya sami hikimarsa da al'ajibai? 55Wannan mutumin ba dan masassakin nan ba ne? Ba kuma sunan mahaifiyarsa Maryamu ba? Ba Kuma 'yan'uwansa sune, Yakubu da Yusufu da Saminu da kuma Yahuza ba? 56Ba 'yan'uwansa mata na tare da mu ba? To daga ina wannan mutumin ya sami dukan wadannnan abubuwa?57Suka bata rai saboda shi. Amma Yesu ya ce masu, "Ai annabi bai rasa daraja sai dai ko a garinsa da kuma cikin iyalinsa. 58Kuma bai yi al'ajibai dayawa a can ba saboda rashin bangaskiyarsu.
Wannan farko ne a bangaren labarin wanda Yesu ya fara koya wa taron ta wurin amfani da misali game da mulkin sama.
Waɗannan sun faru ne a rana ɗaya da waɗanda ke a sura da ke a baya.
Ba a faɗa ko a gidan wa Yesu ke zama ba.
Na nufin cewa ya zauna don ya koyar da mutanen.
Na nufin cewa Yesu ya shiga cikin kwalekwale domin zai zama da sauki ya koyar mutanen.
Wannan mai yiwuwa wani kwalkwale da ke a bude, na itace kuma wanda ake kaman kifi.
Yesu ya bayana mulkin sama ta wurin ba da misali game da wani mutum da ke sukin iri.
...
"wa mutanen cikin taron"
"Kassa kunne." Wannan kalma na jan hankali zuwa ga abin da za a faɗa nan gaba. AT: "Kassa kunne ga abin da zan faɗa maku"
"manumi ya tafi gona don ya yafa iri"
"a yayinda manumin na cikin yafa iri"
Wabbab ba nufin "hanya" da ke gefen gonar. kasar ta yi tauri domin mutane suna tafiya a kai.
"cinye dukka irin"
Wannan wuri ne cike da duwatsu. kasa kuwa kaɗan ne a saman duwatsun.
"Irin nan da nan suka tsira suka yi girma"
AT: "rana ta sa shukin sun yankwane, sun yi zafin kuma"
"shukin ta bushe ta kuma mutu"
"faɗa cikin wurin da ƙaya ke girma"
"shaƙe sabbin da suka toho." Yi amfani da kalman da ke nuna yadda ciyayi ke hana tsire-tsire girma da kyau.
"bada iri da yawa" ko "bada 'ya'ya"
kalmomin nan "iri" "amfani" da "amfanin gona" an fahimce su ne daga magana da ke a baya. Ana iya bayana wannan a fili. AT: "wasu irin sun ba da amfani dari dari bisa ga yawan amfanin gona, wasu irin sun bada amfani sittin sittin bisa ga amfanin gona, wasu irin kuma sun bada talatin talin bisa ga yawan amfani"
"100 ... 60 ... 30"
Wannan wata hanya ce da ake nufin kowa da ke a wurin wanda ke jin abin da Yesu ke faɗa. Dubi yadda ka juya wannan cikin [Matiyu 11: 15] AT: "Duk wanda zai iya ji na"
A nan "kassa kunne" na nufin sa hankalin ga abin da ake faɗa. Dubi yadda ka juya wannan cikin [Matiyu 11: 15]. AT: "sa hankalin ga abin da nake faɗa"
Ana iya bayana abin nufin a fili. AT: "Allah ya ba ku 'yancin fahimtar asiran mulkin sama, amma Allah bai ba wa waɗannan mutane ba" ko "Allah ya sa ku ku iya fahimtar asiran mulkin sama, amma ba sa waɗannan mutane su fahimta ba"
Kalman nan "ku" na nufin almajiran.
A nan "mulkin sama" na nufin mulkin Allah. "mulkin sama" ta auku a littafin Matiyu ne kaɗai. In mai yiwuwa ne, ku yi iyakacin koƙarin ku ku juya shi yadda ta ke. AT: "asirai game da Allahnmu a cikin sama da mulkin sa"
"duk wand ke da fahimta" ko "duk wanda ya karɓi abin da na koyar"
AT: "Allah zai kara masa fahimta"
"duk wanda ba shi da fahimta" ko "duk wanda bai karɓi abin da na koyar ba"
AT: "Allah zai karɓi abin da yake da shi"
Duk aukuwar "su" na nufin mutanen taron.
Yesu ya nanata wa almajiransa cewa taron sun ƙi su fahimci gaskiyar Allah.
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) wannan na nufin sun ga abin da Yesu ya yi. AT: "ko da ya ke sun ga abin da na yi" ko 2) wannan na nufin sun iya gani. AT: "ko da ya ke sun iya ganin"
A nan "gani" na nufin fahimta. AT: "ba su fahimta ba"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) wannan na nufin cewa suna ji abin da Yesu ya koyar. AT: "Ko da ya ke sun ji abin da na faɗa" ko 2) wannan na nufin sun iya ji. AT: "ko da ya ke sun iya jin"
A nan "ji" na nufin kassa kunne da kyau. AT: "ba su kassa kunne da kyau ba" ko "ba su ba da hankalin su ba"
AT: "Suna cika abin da Allah ya faɗa tun dă ta wurin annabi Ishaya"
Wannan annabci ne daga annabi Ishaya da aka ambato game da rashin bada gaskiya na mutanen zamaninsa. Yesu ya yi amfani da wannan don ya bayana yadda taron da ke kassa kunne a gare shi suke. Wannan magana na nanata cewa mutanen sun ƙi sun fahimci gaskiyar Allah.
"Za ku ji abubuwa, amma ba za ku fahimce su ba." Za ka iya bayana a fili abin da mutanen za su ji. AT: "Za ku ji abin da Allah ya ce ta wurin annabawa amma ba za ku fahimci gaskiyar ma'anan ta ba"
Za ka iya bayana a fili abin da mutanen za su gani. AT: "za ku ga abin da Allah ya yi ta wurin annabawan, amma ba za ku fahimta ba"
Cikin 13:15 Allah ya kamanta mutane Isra'ila kamar suna da wata cuta ne cikin jiki da ke sa su su kăsa iya koya, gani, da ji. Allah yana so su zo gare shi don ya warkar da su. Wannan na bayana yanayi na ruhaniyan mutanen. Ta na nufin mutanen sun taurare sun kuma ƙi su sami fahimta daga gaskiyar Allah. In za su karɓi gaskiyar, to za su tuba, Allah kuma zai yafe masu, zai kuma marabce su a matsayin mutanensa. Idan ma'anan na a fili, to a yi amfani da karin magana cikin juyin ku.
Anan "zuciya" na nufin tunani. AT: "tunani waɗannan mutanen ba ta saurin koyo"
Su ba kurma ba ne a jiki. Anan "wuyan ji" na nufin sun ƙi su kassa kunne su koya gaskiyar Allah. AT: "sun ƙi su yi amfani da kunnuwan su su kassa kunne" (Dubi:
Ba su rufe idanun a zahiri ba. Wannan na nufin cewa su ƙi su fahimta. AT: " sun ƙi su yi amfani da idanun su don su gani"
"domin kada su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, ko kuwa su fahimta da zuciyarsu, kuma saboda haka su juyo kuma"
A nan "zukata" na nufin tunanin mutanen. AT: "fahimta daga tunanin su"
"juyo wurina" ko "tuba"
"in warkar da su." Wannan na nufin Allah zai warkar da su a cikin ruhaniya ta wurin yafe masu zunubansu ya kuma karɓe su a matsayin mutanen. AT: "in warkar da su kuma"
Maganganun na biyu na nufin abu ɗaya. Yesu ya nanata cewa sun faranta wa Allah rai domin sun bada gasikiya ga abin da Yesu ya faɗa da aikata.
A nan "idanu" na nufin mutum gabaɗayansa. AT: "Ku masu albarka ne domin idanun ku sun iya ganin"
Duk aukuwar wannan kalma na nufin almajiran ne.
A nan "kunnuwa" na nufin mutum gabaɗayansa. Za ka iya sa a fili zancen da aka fahimta anan. AT: "ku masu albarka ne domin kunnuwanku sun iya ji"
"Gaskiya ina gaya maku." Wannan na kara nanata abin da Yesu ya faɗa a nan gaba.
Kuna iya bayana abin da suka gani a fili. AT: "abubuwan da kun ga na yi"
Kuna iya bayana abin da suka ji a fili. AT: "abubuwan da ku ka ji na faɗa"
"sakon game da mulkin Allah a matsayin sarki"
Yesu ya yi magana game da Shaiɗan ya sa mutum ya manta abin da ya ji sai ka ce Shaiɗan tsuntsune da ke tsine iri daga ƙasa. AT: "Mugun ya sa shi ya manta da sakon da ya ji daidai kamar yadda tsuntsun ke tsine iri daga ƙasa"
Wanna na nufin Shaiɗan.
A yi ƙoƙari a yi amfani da kalman da ke nufin kwace wani abu daga wurin wani mai shi.
AT: "sakon da Allah ya shuka a zuciyarsa" ko "sakon da ya ji"
A nan "zuciya" na nufin tunanin mai sauraro.
"Wannan shine abin da irin da ya fadi a gegen hanya yake nufi" ko "Hanyar da an shuka irin na a maɗaɗɗin mutumin"
Maganan nan "abin da aka shuka" na nufin iri da ya făɗi. AT: "Irin da ya făɗi a duwastsu"
"Duwatsun da aka yi shuki na wakilcin" ko "Duwatsun da irin ya făɗi na wakilcin"
A misalin, irin na nufin maganar.
Wannan na nufin sakon Allah. AT: "sakon" ko "Koyaswar Allah"
An yi maganar gaskantawa da maganar kamar karɓan ta. AT: "gaskanta da farin ciki"
duk da haka jijiyoyin sa ba su yi nisa ba kuma suna jimawa na dan lokacin kaɗan ne. "Jijiya na nufin abin da ke sa mutum ya cigaba da bada gsakiya ga sakon Allah. AT: "Amma kamar shukin da jijiyoyin sa ba su yi nisa ba, yana jimawa na dan lokacin kaɗan ne"
A nan "tuntunɓe" na nufin ƙi gaskantawa. AT: "nan da nan ya faɗi" ko "nan da nan sai ya ƙi bada gaskiya ga sakon"
Wannan na nufin irin da an shuka ko kuwa ta faɗi. AT: "Irin da aka shuka" ko "Irin da ta faɗi"
"filin da akwai ƙaya, inda aka shuka irin"
"wannan na wakilcin mutumin"
Yesu yana magana game da dawainiyar duniya da jarabar dukiya a
"abubuwa da mutanen wannan duniya ke damuwa game da su"
Yesu ya yi bayani akan "dukiya" kamar dukiya mutum ne wanda zai iya yauɗarar wani. Wannan na nufin cewa mutane suna tunanin cewa samun kudi za ta sa su farin ciki, amma ba za ta sa su farin ciki ba. AT: "ƙaunar kuɗi"
An yi maganar mutmin kamar shi shuki. Rashin bada 'ya'ya na nufin rashin yin amfani. AT: "zama mara bada amfani" ko " ba ya yin abin da Allah yake so"
"Ƙasa mai kyau da aka shuka irin"
An yi maganar mutumin sai ka ce shuki. AT: "Kamar shuki da bata da cuta da ke bada amfanin gona, yana bada 'ya'ya"
Mangana nan "fiya da wanda aka shuka" an fahimce ta bisa ga waɗannan lambobin. Dubi yadda ka juya wannan cikin [Matiyu 13:8] AT: "Wasu mutane sun bada amfani fiye da abin da aka shuka sau 100 wasu sau 60, wasu kuma sau 30"
Kada a daidaita mulkin sama da mutum, amma sai dai mulkin sama na kamar yanayin da aka bayana a misalin.
A nan "mulkin sama" na nufin mulkin Allah a matsayin sarki. "An yi amfani da "mulkin sama" a Matiyu ne kaɗai. In mai yiwuwa ne, ku yi amfani da "sama" a juyin ku. AT: "Sa'ad da Allahnmu na sama ya bayana kansa a matsayin sarki, zai zama kamar"
"irin abinci mai kyau" ko "irin hatsi mai kyau." Mai yiwuwa masu sauraro suna tunanin cewa Yesu na magana game da alkama.
"magabcin sa ya zo gonar"
Waɗannan ciyayin suna kamar wata shuki ne da za a iya ci, a sa'ad da bai yi girma ba, amma hatsi su guba ce. AT: "iri mara kyau" ko "irin ciyayi"
Sa'ad da irin alkaman ta toho" ko "Sa'ad da shuki ta yi girma"
"bada tsaba" ko "bada tsaban alkama"
Sa'annan mutane za su iya ganin cewa lalle akwai ciyayi a gonar"
Wannan mutum ɖaya ne da wanda ya shuka iri mai kyau a gonarsa.
Barorin sun yi amfani da tambaya don su nanata yadda sun ji mamaki. AT: "ka shuka iri mai kyau a gonar ka!"
Mai yiwuwa mai gonar ya sa barorinsa ne sun shuka irin. AT: "ashe ba mu shuka"
"Mai gonar ya ce wa barorin"
Kalman nan "mu" na nufin barorin.
"Mai gonar ya ce wa barorinsa"
AT: "Zan gaya wa masu girbin su tara ciyayin da farko su ɗaure su dami dami su kona su, sai kuma su tara alkaman a cikin rumbu na"
ginin da ana iya amfani da shi a ajiye hatsi
wata ƙanƙanin iri da ke girma ya zama babbar itace
Ga masu sauraro na farko, iri mustad ita ce mafi ƙanƙanta cikin iri da suka sani.
"Amma bayan shukin ta girma"
"ta yi babba fiye da"
Itacen mustad na iya girma daga mita 2 zuwa 4 a tsayi.
"tsuntsaye"
Mulkin na kamar yisti, amma yaduwar mulkin na kamar yaduwar yisti.
Sai a ce "auwu mai yawa na gari" ko kuwa a yi amfani da kalman da ake amfani da shi a al'adan ku na auna gari mai yawa.
Abin nufin shine yisti da auwu uku na gari an yi kullun shi don a yi burodi.
Jimla biyun na nufin abu ɗaya. An haɗa su don a nanata cewa Yesu ya koyawa taron da misalai ne kaɗai.
Wannan na nufin abin da Yesu ya koyar da farko a [Matiyu 13:1]
"ba gaya masu komai ba sai dai ta wurin misalai." AT: "duk abin da ya koya masu ya faɗa cikin misalai ne"
AT: "Abinda Allah ya gaya wa ɗaya daga cikin annabawan ya rubuta tun dã zai zama gaskiya"
"sa'ad da annabin ya ce"
Wannan na nufin a yi magana. AT: "zan yi magana"
AT: "abubuwan da Allah ya ɓoye"
"tun daga farkon halittar duniya" ko "tun da Allah ya halici duniya"
"shiga cikin gida" ko "shiga cikin gidan da yake zama"
"Wanda ya shika iri mai kyau" ko "Mai shukin iri mai kyau"
Yesu na nufin shi da kansa.
Karin maganan nan "'ya'yan" na nufin waɗanda ke na mulkin ko suna da hali kamar na wani ko wani abu. AT: "mutanen da ke na mulkin"
A nan "mulki" na nufin Allah a matsayin sarki. AT: "na Allah"
Karin maganan nan "'ya'yan" na nufin waɗanda ke na mugun ko suna da hali kamar na wani ko wani abu. AT: "mutanen da ke na mugun"
"mugun wanda ya shuka ciyayi"
AT: "Saboda haka, kamar yadda mutane suna tara ciyayi su kona da wuta"
A nan Yesu na magana game da kansa. AT: "Ni Ɗan Mutum, zan aiko da mala'ikuna"
"waɗanda ba su bin doka" ko "mutane masu mugunta"
Wannan na nufin jahannama. In ba a san "korama" ba, to, ana iya amfani da "wuri mai zafi da ke da murfi " AT: "tafki ta wuta a ruruwa"
"Cizon haƙora" anan alama ce da ke wakilcin matuƙar bakinciki da wahala. Dubi yadda ka juya wannan cikin [Matiyu 8:12]. AT: "kuka suna nuna cewa lallai suna shan matuƙar wahala "
In ba a fahimci wannan a harshen ku ba, kana iya amfani da: "da saukin gani kamar rana."
Wannan lakani mai muhimmanci na Allah.
AT: "dukiya ce da wani ya ɓoye a gona"
abu mai daraja ko kuwa tarin abubuwa.
"rufe shi"
Abin nufin anan shine mutumin ya sayi filin don abin da aka ɓoye ya zama nasa.
Abin nufin shine mutumin da neman lu'ulu'ai masu daraja don ya saya.
mai ciniki ko 'yan sari wanda saya kaya yawanci lokatai dagar wurare masu nisa
"lu'ulu'ai" na da santsi, na da tauri, na walkiya kuma, fari ne ko kuma kamar dutsen ado mai haske wanda ke cikin teku ana kuma sayan shi da tsada kamar wani dutse mai daraja ko kuwa ana maida shi kamar kayan ado masu daraja. AT: "lu'ulu'ai mai tsabta" ko "lu'ulu'ai masu kyau"
Mulkin ba kamar tarun ba ne, amma mulkin na jawo kowane irin mutane kamar yadda taru ke kama kowane irin kifi.
AT: "kamar taru ne da masunta suka jefa a cikin teku"
"an wurga cikin teku"
"kama kowane iri kifi"
"jawo tarun suza bakin tekun" ko "jawo gaɓan teku"
"masu kyau"
"munanan kifin" ko "kifin da ba za a iya ci ba"
"za su fito" ko "za su fita" ko "za su zo daga sama"
AT: "mayagun mutane daga cikin mutane masu adalci"
"mala'iku za su jefa mugayen mutanen"
AT: "Yesu ya tambaya su ya ce in da sun fahimci duk wannan, sai suka ce sun fahimta."
A nan "mulkin sama" na nufin mulkin Allah a matsayin sarki. Maganan nan "mulkin sama" an yi amfani da shine a littafin Matthew ne kaɗai. In ma yiwuwa ne a yi "amfani" da juyinku. AT: "sun koyi gaskiya game da Allah na sama, wanda shine sarki" ko "ya mika kansa don Allah ya yi mulkinsa"
Yesu ya bada wani misali kuma. Ya kwatanta malaman attauran da sun san nassosin da Musa da annabawa sun rubuta kuma wanda sun karɓi koyaswar Yesu da magidanta wanda ya yi amfani da tsoho da kuma sabon taska.
Wannan magan na kai labarin daga koyaswar Yesu zuwa ga abin da ya faru nan gaba. AT: "Sai" ko "Bayan"
"birninsa." Wannan na nufin birnin Nazarat inda Yesu ya yi girma.
Kalman "su" na nufin mutanen yankin.
...
Mutanen sun gaskantan cewa Yesu shi kamar sauran mutane yake. Sun yi amfani da wannan tambayan don su nuna yadda suka ji mamaki cewa yana da hikima har ya iya yin aikin al'ajibi. AT: "Ta yaya mutum kamar wannan zai zama da hikima har ya yi manyan abin al'ajibi?" ko "Bakon abu ne cewa ya iya magana da hikima da kuma aikata abin al'ajibi!"
Taron sun yi amfani da wannan tambayar don su nuna cewa lalle sun san ko wanene Yesu, shi kuwa mutum na kamar mu. AT: "Shi ɗan masassaki ne. Mun san mahaifiyarsa Maryamu, da 'ya'uwansa Yakubu, Yusufu, Saminu da kuma Yahuza. Kuma duk 'yan'uwansa mata na tare da mu"
Masassaki mutum ne wanda ke yin abubuwa da katako ko dutse. In ba a san "masassaki" ba do za a iya amfani da "magina".
Taron sun yi amfani da wannan tambayan don su nuna fahimtarsu cewa lalle Yesu ya samin iyawarsa daga wanin wuri. Mai yiwuwa suna nuna shakkar su cewa ya sami wannan iya daga wurin Allah. AT: "Lalle iyawarsa na yin waɗannan abubuwa ya sami ta daga wani wuri!" ko "Ba mu san inda ya sami waɗannan iyawar ba!"
AT: "Mutanen garin Yesu sun yi fushi da shi" ko "Mutanen sun ƙi Yesu"
AT: "Annabi na samu daraja a ko'ina" ko "Mutane a ko'ina na daraja annabi"
"a yankin sa" ko "a garinsa"
"cikin gidansa"
"Yesu bai yi ala'jibai dayawa a garinsa ba"
1A lokacin nan ne, Hiridus mai mulki ya ji labarin Yesu. 2Ya ce wa barorinsa, "Wannan Yahaya mai baftisma ne; ya tashi daga matattu. Saboda haka wadannan ikoki na aiki a cikinsa".3Domin Hiridus ya kama Yahaya, ya daure shi, kuma ya jefa shi a kurkuku saboda Hirudiya, matar dan'uwansa Filibus. 4Ya ce masa, "Bai kamata ka dauke ta a matsayin matarka ba." 5Da Hirudus ya kashe shi, amma yana tsoron jama'a, domin sun dauke shi a matsayin annabi.6Amma da ranar bikin haihuwar Hirudus ta kewayo, diyar Hirudiya tayi rawa a lokacin har ta burge Hirudus. 7Sai ya yi mata alkawari har da rantsuwa cewa ta roki komenene ta ke so, zai ba ta.8Bayan ta amshi umurni daga wurin mahaifiyarta, ta ce, "Ka bani kan Yahaya mai baptisma a kan tire. 9Sarki ya husata da rokonta, amma domin rantsuwar da ya yi kuma domin mutanen da ke a wurin bukin tare da shi, sai ya umurta a yi haka.10Ya aika aka yanke kan Yahaya acikin kurkuku. 11Sai aka kawo kansa bisa tire, aka mika wa yarinyar, ta kuwa kai wa mahaifiyarta. 12Sai almajiransa suka zo, su ka dauki gawar su ka je su ka yi jana'iza. Bayan haka, su ka je su ka fada wa Yesu.13Sa'adda da Yesu ya ji haka, ya fita daga cikin kwale-kwale zuwa wani kebabben wuri. Da taron suka ji haka, suka bi shi da kafa daga biranen. 14Sai Yesu ya zo gabansu, ya kuma ga babban taron. Ya tausaya masu ya kuwa warkar da marasa lafiya dake cikinsu.15Da maraice ya yi, almajiransa su ka zo su ka ce masa, "Wannan wuri jeji ne, dare kuwa ya riga ya yi. Ka sallami taron domin su je cikin kauyukan nan, su sayo wa kansu abinci."16Amma Yesu ya ce masu, "Babu amfanin tafiyar su, ku basu abin da za su ci." 17Suka ce masa, "Muna da gurasa guda biyar da kifi biyu ne kawai." 18Yesu ya ce, "Ku kawo mani su."19Sai Yesu ya umarci taron su zauna akan ciyawa. Ya dauki gurasa biyar da kifi biyun. Ya dubi sama, ya sa albarka ya gutsuttsura ya kuma ba almajiran. Almajiran suka ba taron. 20Dukansu suka ci suka koshi. Sai suka dauki gutsattsarin gurasa da kifin, kwanduna goma sha biyu cike. 21Wadanda su ka ci kuwa kimanin maza dubu biyar ne, ban da mata da yara.22Nan take sai ya sa almajiran suka shiga kwale-kwalen su haye zuwa dayan gefen kafin shi, domin ya sallami taron. 23Bayan ya sallami taron sun tafi, sai ya haura kan dutse domin yayi addu'a. Da dare yayi, yana can shi kadai. 24Amma yanzu fa kwale-kwalen na tsakiyar tekun, kuma da wuyar sarrafawa saboda rakuman ruwa da iska na gaba da su.25Da asuba (wajen karfe uku na dare) Yesu ya nufo su yana tafiya akan teku. 26Da almajiran suka ganshi yana tafiya akan tekun, sai suka firgita suna cewa, "Fatalwa ce," suka yi kururuwa cikin tsoro. 27Amma Yesu yayi magana da su nan da nan yace, "Ku yi karfin hali! Ni ne! Kada ku ji tsoro."28Bitrus ya amsa masa cewa, "Ubangiji, idan kai ne, ka umarce ni in zo wurin ka bisa ruwan." 29Yesu yace, "Zo" Sai Bitrus ya fita daga jirgin yana tafiya akan ruwan zuwa wurin Yesu. 30Amma da Bitrus ya ga iska, sai ya tsorata. Yayin da ya fara nutsewa, sai ya tada murya ya ce, "Ubangiji, ka cece ni!"31Nan take Yesu ya mika hannunsa, ya kama Bitrus ya ce masa, "Kai mai karancin bangaskiya, meyasa ka yi shakka?" 32Bayan da Yesu da Bitrus suka shiga cikin kwale-kwalen, sai iska ta daina kadawa. 33Sai almajiran dake cikin kwale-kwalen su ka yi wa Yesu sujada suna cewa, "Hakika kai Dan Allah ne."34Da suka haye, sun iso kasar Janisarata. 35Da mutanen wurin suka gane Yesu, sai suka aika da sako zuwa dukan yankin, kuma suka kawo masa dukan marasa lafiya. 36Suka roke shi don su taba gezar rigarsa, kuma dukan wadanda suka taba shi sun warke.
Waɗannan ayoyi suna bayana yadda Hiridus ya yi, da ya ji labari game da Yesu. Wannan abun ya faru ne bayan wasu lokatai da suka wuce..
" A lokacin da suka wuce" ko "Da Yesu yake bishara a Galili"
"ya ji labari game da Yesu" ko "ya ji sunan da Yesu yayi"
"Hiridus ya ce"
Kalmomin nan "daga mattatu" na magana akan dukan mutanen da suka mutu na cikin karkashin kasa. Tashiwa daga mattatu na magana akan zama rayyeye kuma.
Wasu Yahudawa a lokacin can sun yadda cewa iɗan mutum ya dawo daga mattatu zai samu ikoki ya yi abubuwan al'ajibi.
A nan marubucin ya fara fada yadda Hiridus ya kashe Yahaya mai Baftisma. Waɗannan abubuwan sun faru a wasu lokatai kafin abun da ya faru a ayoyin da suka wuce.
Iɗan akawai bukata, za ka iya mika yadda abubuwan suka faru a 14:3-4, yadda take a UDB
Wannan na faɗi cewa Hiridus yayi haka ne, domin ya umurce wasu ne suyi mashi. AT: "Hiridus ya umurce sojojin sa su kamo Yahaya mai Baftisma, su ɗaure shi, su kuma jefa shi a kurkuku"
Filibus dan'uwan Hiridus ne. Hiridus ya ɗauki matar Filibus ta zama matar sa.
Iɗan ya zama dole, za'a iya fadin wannan maganan a wani juyi. AT: "Domin Yahaya ya fada wa Hiridus cewa bai kama Hiridus ya ɗauki Hirudiya a matsayin matar sa ba."
"Domin Yahaya ya cigaba da fada wa Hiridus"
Philibus yana nan a raye da Hiridus ya aure Hirudiya.
"Hiridus ya tsorata"
"sun ɗauka Yahaya"
AT: "a tsakanin baƙi da suka je bukin aihuwar"
AT: "Bayan da mahaifuwarta ta umurce ta"
"zuga" ko "gaya"
" 'yar Hirudiya ta ce wa Hiridus"
babban faranti
AT: " Roƙon da tayi ya saka Sarki bakin ciki sosai"
"Sarki Hiridus"
AT: "ya umurce mutanen sa su yi abin da ta faɗa"
AT: "wani ya kawo ƙansa a bisa tire, aka mika wa 'yarinyar"
Yi amfani da kalman wa 'ya, 'yarinya marasa aure.
"almajaren Yahaya"
"gangar jikin"
Za 'a iya bayyana ma'anar gabadaya a filli. AT: "almajaren Yahaya suka je suka kuma gaya wa Yesu abun da ya faru da Yahaya mai Baftisma"
An yi amfani da kalman nan domin a saka alamar burki acikin ainihin labarin. Anan, Mattiyu ya fara maganar sabuwar sashi a labarin.
"ji abun da ya faru da Yahaya mai Baftisma" ko "ji labari game da Yahaya"
"ya tafi" ko "ya bar wurin taron." Ana zaton cewa almajaren Yesu sun tafi tare da shi. AT: Yesu da almajarensa suka tafi"
"daga wancan wurin"
"Da taron suka ji inda Yesu ya je" ko "Da taron suka ji cewa ya tafi"
"taron jama'a" ko "babban taron jama'a"
Wannan na nufin cewa mutanen da suke cikin taron suna tafiya ne.
" Da Yesu ya je gaba, ya ga babban taro"
" almajaren Yesu suka je wurinsa"
"Ba llale ba ne mutanen da suke cikin taron"
Kalman nan "Ku" Jam'i ne, yana nufin almajaren ne.
"Almajaren suka ce wa Yesu"
Gurasa ɗunkulen ƙullu ne da aka shirya ta a wata tsifa aka kuma gasa ta.
"Ku kawo mini gurasan da kuma ƙifin"
"kwanta." Za ka iya yin amfani da wannan kalman tawurin nuna yadda mutanen kabilar ka suke cin abinci.
"Ya rike a hannayensa." Bai sato su ya yi ba.
" ya yage gurasar"
"gurasa" ko "gabadayar gurasar"
AT1): "Yayen da yake kallon sama" ko 2)"Bayan da ya kalla sama."
AT: "har sun koshi" ko "har suka daina jin yunwa"
"almajaren suka tattara" ko "wasu mutanen suka tattara"
"kwanduna 12 cike"
"Waɗanda suka ci gurasar da kuma ƙifin"
"maza 5,000"
"da Yesu ya gama ciyer da dukan mutanen, sai ya"
"har kurewar yammaci" ko "har guri tayi duhu"
"har ma almajaren basu iya tuka ƙwaleƙwalen ba saboda gaggarumin raƙumen ruwan"
Da asuba tsakanin ƙarfe uku na safiya da kuma rana. "dai kafin yammaci ta gabato"
"tafiya a bisa ruwa"
"suka ji tsoro sosai"
ruhun da ya rigaya ya bar gangan jikin mutum da ya mutu
"Bitrus ya amsa wa Yesu
Anan "gan iskan" na nufin yana sane da iskan. AT: "Da Bitrus ya ga iskan da ke koran raƙuman ruwan gaba da baya" ko "da ya gane karfin iskan"
"Kai da kake da ƙarancin bangaskiya." Yesu ya faɗa wa Bitrus haka domin Bitrus ya ji tsoro. AT: "Don me ka ke da ƙarancin bangaskiya haka!"
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya faɗa wa Bitrus kada yayi shakka. Za ka iya bayyana a fili dalilin da Bitrus zai yi shakka ba. AT: "bai kamata kayi shakka ba domin zan iya tsare ku daga nitsewa ba."
Wannan laƙabi ne mai muhinminci sosana Yesu da yake bayyana ɗangantakansa da Allah. (Dubi: )
"Da Yesu da kuma almajaren sa suka haye tekun"
Wannan ƙaramar gari ce da take...................................................................
"mazajen da suke wancan yankin suka aiko da sako"
"Mutane mara lafiya suka roƙe shi"
"tufafin sa" ko "abin da ya saka"
AT: "suka samu lafiya"
1Sai wadansu Farisawa da malamai suka zo wurin Yesu daga Urushalima. Su ka ce, 2"Meyasa almajiranka suke karya al'adar dattawa? Don ba su wanke hannayen su kafin su ci abinci." 3Yesu ya amsa masu ya ce, "Kuma don me ku ke karya dokar Allah saboda al'adunku?4Domin Allah ya ce, 'Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka; 'Shi wanda ya yi muguwar magana ga mahaifinsa ko mahaifiyarsa, lallai zai mutu. 5Amma kun ce, "Duk wanda ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, "Kowanne taimako da za ka samu daga gare ni yanzu baiko ne ga Allah,'" 6wannan mutum ba ya bukatar ya girmama mahaifinsa. Ta wannan hanya kun maida maganar Allah wofi saboda al'adunku.7Ku munafukai, daidai ne Ishaya ya yi annabci akan ku da ya ce, 8" Wadannan mutane girmama ni da baki kawai suke yi, amma zukatansu nesa suke da ni. 9Suna mani sujada a banza, domin suna koyar da dokokin mutane a matsayin rukunansu."10Sai ya kira taron mutane zuwa gare shi ya ce masu, "Ku saurara ku fahimta, 11ba abin da ke shiga baki ke kazantar da mutum ba. Sai dai, abin da ke fitowa daga baki, wannan shi ya ke kazantar da mutum."12Sai al'majiran suka zo suka ce masa, "Ka san Farisawa ba su ji dadi ba da suka ji maganan nan?" 13Yesu ya amsa ya ce, "Kowace shuka wadda ba Ubana na sama ya shuka ba za a tuge ta. 14Ku kyale su kawai, su makafin jagora ne. In makaho ya ja wa wani makaho gora dukan su za su fada rami."15Bitrus ya amsa ya ce wa Yesu, "Ka bayyana wannan misali a garemu," 16Yesu ya ce, "Ku ma har yanzu ba ku da fahimta? 17Ko baku gani ba duk abin da ke shiga baki zuwa ciki ta haka yake fita zuwa salga?18Amma abubuwan da ke fita daga baki suna fitowa ne daga zuciya. Su ne abubuwan da ke kazantar da mutum. 19Domin daga zuciya mugayen tunani suke fitowa, kisan kai, zina, fasikanci, sata, shaidar zur, da zage-zage. 20Wadannan su ne abubuwan da ke kazantar da mutum. Amma ci da rashin wanke hannu baya kazantar da mutum."21Sai Yesu ya tafi daga nan ya nufi yankin biranen Taya da Sidon. 22Sai wata mace Bakan'aniya ta zo daga wannan yanki. Ta daga murya ta ce," Ka yi mani jinkai, Ubangiji, Dan Dauda; 'yata tana cikin bakar azaba da aljani." 23Amma Yesu bai ce mata kome ba. Almajiransa suka zo suka roke shi, suna cewa, "Ka sallame ta, domin tana bin mu da ihu."24Amma Yesu ya amsa ya ce, "Ba a aike ni gun kowa ba sai dai ga batattun tumakin gidan Isra'ila." 25Amma ta zo ta durkusa a gabansa, tana cewa, "Ubangiji ka taimake ni." 26Ya amsa ya ce, "Ba daidai bane a dauki gurasar yara a jefa wa kananan karnuka.27Ta ce, "I, Ubangiji, amma ko kananan karnuka suna cin barbashin da ke fadowa daga teburin maigida." 28Sai Yesu ya amsa ya ce mata, "Mace, bangaskiyarki tana da girma. Bari ya zamar maki yadda ki ke so." 'Yarta ta warke a lokacin.29Yesu ya bar wurin ya tafi kusa da tekun Galili. Sai ya hau tudu ya zauna a can. 30Taro mai yawa suka zo gunsa. Suka kawo masa guragu, makafi, bebaye da nakasassun mutane da yawa, da wadansu marasa lafiya. Suka kawo su gaban Yesu, sai ya warkar da su. 31Don haka mutane da yawa suka yi mamaki a lokacin da suka ga bebaye suna magana, nakasassu sun warke, guragu suna tafiya, makafi suna gani. Sai suka daukaka Allah na Isra'ila.32Yesu ya kira almajiransa zuwa gun sa sai ya ce, "Ina jin tausayin taron, sun kasance tare da ni kwana uku ke nan kuma ba su da abin da za su ci. Bana so in sallame su ba tare da sun ci abinci ba, domin kada su suma a hanya." 33Almajiran suka ce masa, "A ina zamu sami isasshiyar gurasa a wannan wuri da babu kowa har ta ishi babban taron nan." 34Yesu ya ce masu, "Gurasa nawa ku ke da ita?" Suka ce, "Bakwai da 'yan kifi marasa yawa." 35Sai Yesu ya umarci taron su zauna a kasa.36Ya dauki gurasar nan bakwai da kifin, bayan ya yi godiya, ya kakkarya gurasar ya bada ita ga almajiran Sai almajiran suka ba taron. 37Jama'a duka suka ci suka koshi. Suka tattara gutsattsarin abincin da ya rage, kwando bakwai cike. 38Wadanda suka ci su dubu hudu ne maza, banda mata da yara. 39Sai Yesu ya sallami taron ya shiga cikin jirgin ruwa ya tafi yankin Magadan.
Wannan wurin ya canza zuwa abin da ya faru a sashin suran da suka wuce. Anan Yesu ya amsa game da mummunan ra'ayin farisawan.
Farisiyawa da kuma Mallamen attaura suna amfani da wannan tambayan don su zarge Yesu da almajaren sa. AT: "Almajaren ka ba suwa biyyaya ga dokokin da kaƙanen mu suka bamu."
Wannan ba iri ɗaya bane da dokan Musa. Wannan na kai mu zuwa ga koyaswan da suka zo daga baya da kuma fasarar doka da shugabanen addini suka bayas bayan Musa.
Wannan wankin, ba na hannaye kawai ba. Wannan na nufin bukin wanki bisa ga al'adun dattawa. AT: "basu wanke hannayen su tsap ba"
Yesu ya amsa da tambaya domin ya zargi abin da shugabanen addini suke yi. AT: " Kuma na gani cewa kun ki ku yi biyyaya ga umurnin Allah domin ku iya bin abin da kakannen ku suka koyas maku!"
Yesu ya cigaba da amsa wa farisawa
hakika mutanen za su halaka shi
AT: "Amma kuna koyas da cewa mutum bashi da bukata ya girmama iyayensa ta wurin basu abin da zai taimake su idan mutmin ya gaya wa iyayensa cewa ya riga ya bada shi a matsayin kyauta wa Allah"
Anan "ku" jam'i ne kuma na nufin Farisawa da mallaman attaura.
Ya nuna da cewa "ubansa" na nufi "iyensa." Wannan yana nufi da cewa shugabannen adini sun koyas da cewa mutum bashi da bukatan nuna girmamawa ga iyayensa ta wurin kulawa da su.
"kun mai da al'adunku mafi muhinminci fiye da umurnin Allah"
"Ishaya ya faɗi gaskiya game da ku a wannan anabcin"
Ana nufin cewa Ishaya ya na faɗin abin da Allah ya gaya mashi ne. AT: "da ya faɗa abin da Allah ya ce"
A nan "baki" na nufin magana ne. AT: "Waɗannan mutane sun faɗi abubuwa masu kyau game da ni"
Duk abubuwan da suka faru a maganan ya shafi Allah.
A nan "zuciya" na nufin tunani ko yadda mutum yake ji. Wannan maganan hanya ce da za'a iya cewa, da gaske ne mutane basu ba da kan su ga Allah ba. AT: "amma ba so na da gaske suke ba"
"Sujadarsu a banza ne gare ni" ko "Nuna wa suke yi wai suna mani sujada"
"dokan da mutane suka ƙera"
Yesu yana nanata muhinmincin abun yake ƙoƙarin faɗa. Za'a iya bayyana nufin bayanin nan a fili. AT: "Ku saurara da kyau ga abun da zan ce domin ku fahimce manufan ta"
Yesu yana kwatanta abin da mutum ke ci da abin da yake faɗi. Yesu na nufin cewa Allah ya fi kula da abin da mutum yake faɗi fiye da abin da yake ci.
AT: "Farisawan sun yi fushi da wannan kalman" Farisawan basu ji daɗi da wannan maganan ba"
Wannan ƙarin magana ne. Yesu yana nufin cewa Farisawan ba na Allah ba ne, saboda haka Allah zai cire su.
Wannan laƙani ne mai muhinminci sosai ga Allah wanda yake bayyana dangantakan saƙanin Allah da Yesu.
AT: "Uba na zai tuge ta" ko "zai tuge kasan" ko "zai cire"
Kalman nan "su" na nufin Farisawan ne.
Yesu yayi amfani da wata kalma domin ya yi bayani game da Farisawa. Yesu na nufin cewa Farisawan basu fahimce umurnin Allah ba ko kuma yadda zasu faranta masa rai.
"wa mu almajaren"
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya sauta wa almajaren domin basu fahimce misalin ba. Haka kuma, kalman nan "ku" ana nanata ta. Yesu ma bai yarda cewa almajaren basu fahimce shi ba. AT: "ina yanke buri na a gare ku almajare na, har yenzu baku fahimce abun da na koyas ba!"
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya sauta wa almajaren game da rashin fahimtan misalin sa. "haƙika kun fahimta ... zuwa salga"
"shiga zuwa ciki"
Wannan kalma ce mai ladabi da ake nufin inda mutane na binne mattacen gangan jiki.
Wannan na nufin abin da mutum yake faɗa. AT: "kalmomin da mutum yake faɗa"
A nan "zuciya" na nufin zuciyar mutum ko cikin mutum. AT: "daga cikin mutum" ko "daga zuciyar mutum"
aikata kisa ga mutum mara laifi
Bisa ga al'adun dattawan, da farko wannan na nufin mutum ya ci kafin bukin wanke hannun. AT: "ci kafin mutum ya wanke hannu"
Ana nufin cewa almajaren sun tafi tare da Yesu. AT: "Yesu da almajarensa sun bar wurin" (Dubi:
Kalman nan "Sai" na jawo hankalin mu zuwa sabon mutum a cikin labarin. Za ka iya nemi hanyar yin haka da harshen ka. AT: "Akwai wata mace Baƙan'aniya wanda ta zo"
"wata mace wanda ta zo daga wancan yankin mutanen da ake kiransu Baƙa'nai......... "Ƙasan Kan'anam ba ta nan a yanzu. Tana cikin taron mutanen da suka yi rayuwa kusa da garin Tyre da Sidon.
Kalman nan na nufin cewa tana roƙon Yesu ya warkas da 'yar ta"
Yesu ba ainihin ɗan Dauda ba ne, haka kuma za'a iya juya wannan a matsayin "Zuriyar Dauda." Haƙannan kuma "Ɗan Dauda" laƙabi ne na mai Ceto, mai yiwuwa matan ta kiran Yesu da laƙabin sa.
AT: "Aljani na mummunar mulki ga 'ya ta" ko "yata tana cikin bakar azaba da aljani."
Anan "kalma" na nufin abun da mutum ke faɗi ne. AT: "bai faɗi komai ba"
AT: "Allah bai aike ni gun kowa ba"
Wannan ƙarin magana ce da ta ke kwatanta gabadayar jihar Isra'ila da tumakin da ya raɓa hanya da makiyayinsa. AT: [10:6]
"Baƙa'aniyar macen ta zo"
Wannan ya nuna cewa matar ta ƙaskantar da kanta a gaban Yesu.
Yesu ya amsa wa matar da ƙarin magana. Tushin ma'anan nan shine ba daidai bane a ɗauki abun da ke na Ba-yahuɗe a ba wanda shi ba Ba-yahuɗe ba.
A nan "gurasa" na nufin abinci ne. AT: "abincin yara"
Yahudawa suna ɗaukan karnuka a matsayin kazamtattcen dabba ne. Anan amfani da hoton bayanin nan wa waɗanda su ba Yahudawa ba ne.
Amsar matar yayi iri ɗaya ne da kwatancin da Yesu yayi amfani da shi a ƙarin maganan da ya fada. Tana ma'anar waɗanda ba su Yahuɗawa ba su yi koƙarin su samu kiman abubuwa masu kyau da Yahudawa suna banza da ita.
AT: [Matta 15:26]
AT: "Zan yi"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "A daidai lokacin" ko "Nan da nan"
AT: "Yesu ya warkas da 'yar ta" ko " 'yarta ta warke"
"waɗanda ba suwa iya tafiya, waɗanda ba suwa iya gani, waɗanda ba suwa iya magana, da waɗanda hannayensu ko kafafunsu basuwa aiki"
Haka kuma wasu mara lifiya ko guragun mutane basu iya tashiwa ba, da abokanayen su suka kawo su a wurin Yesu, sun ajiye su a kasa a gaban shi. AT: "Taron suka ajiye mutane mara lafiyan a kasa a gaban Yesu"
AT: "guragun suka warke"
AT: "guragun mutane ... nakassasun mutane ... maƙafin mutane"
"ba tare da cin abinci ba domin zasu iya suma a hanya"
Almajaren suka yi amfani da tambaya don su fada cewa babu inda zasu samu abinci wa taron. AT: "Babu wuri kusa inda zamu iya samun isheshen gurasa wa irin wannan babban taron."
AT: "Gurasa guda bakwai da kuma kiman kananan ƙifaye"
Yi amfani da kalman kabilar ka domin nuna yadda mutane ke cin abinci a lokacin da babu tabur, ko ta wurin zama ko kwance.
" Yesu ya rike gurasa guda biyer da kuma ƙifin a hannayensa"
"ya yago gurasar"
"ya ba da gurasan da kuma ƙifin"
"almajaren suka tattara" ko "wasu mutane suka tattara"
"Mutanen da suka ci"
"maza 4,000"
"yankin"
Wasu lokaci ana kiran yankin " Magdala."
1Sai Farisawa da Sadukiyawa suka zo su gwada shi suka roke shi ya nuna masu alama daga sama. 2Amma ya amsa ya ce masu, "Lokacin da yamma ta yi, sai ku ce, 'Za a yi yanayi mai kyau, domin sama ta yi ja,'3Kuma da safe ku ce, 'Zai zama yanayi mara kyau a yau, domin sama ta yi ja ta kuma gama gari, kun san yadda za ku bayyana kammanin sararin sama, amma ba ku iya bayyana alamun lokaci ba. 4Mugun zamani, maciya amana suna neman alama, amma babu wata alama da za a nuna sai ta Yunusa." Daga nan sai Yesu ya tafi.5Almajiran suka zo daga wancan gefe, amma sun manta su dauki gurasa, 6Yesu ya ce masu, "Ku kula ku kuma mai da hankali da yisti na Farisawa da Sadukiyawa." 7Sai almajiran suka fara magana da junansu suka ce, "Ko saboda bamu kawo gurasa bane." 8Yesu yana sane da wannan sai ya ce, "Ku masu karancin bangaskiya, don me ku ke magana a tsakaninku cewa ko don bamu kawo gurasa bane?9Ba ku gane ko tuna da gurasa guda biyar da aka ciyar da mutum dubu biyar, kuma kwando nawa kuka tara ba? 10Ko gurasa bakwai ga mutum dubu hudu, da kuma kwanduna nawa kuka dauka ba?11Yaya kuka kasa fahimta cewa ba game da gurasa nake yi maku magana ba? Ku yi hankali ku kuma lura da yistin Farisawa da Sadukiyawa." 12Sa'annan suka fahimta cewa ba yana gaya masu su yi hankali da yistin da ke cikin gurasa ba ne, amma sai dai su yi lura da koyarwar Farisawa da Sadukiyawa.13A lokacin da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, ya tambayi almajiransa, cewa, "Wa mutane ke cewa Dan Mutum yake? 14Suka ce, "Wadansu suna cewa Yahaya mai baftisma; wadansu Iliya, saura suna cewa Irmiya, ko daya daga cikin annabawa." 15Ya ce masu, "Amma ku wa kuke ce da ni?" 16Sai Saminu Bitrus ya amsa ya ce, "Kai ne Almasihu, Dan Allah mai rai."17Yesu ya amsa ya ce masa, "Mai albarka ne kai, Saminu dan Yunusa, don ba nama da jini ba ne ya bayyana maka wannan, amma Ubana wanda ke cikin sama. 18Ina kuma gaya maka cewa kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikilisiya ta. Kofofin hades ba za su yi nasara da ita ba.19Zan ba ka mabudan mulkin sama. Duk abin da ka kulla a duniya zai zama abin da an kulla a cikin sama, kuma duk abinda ka warware a duniya a warware yake cikin sama," 20Sai Yesu ya umarci almajiransa kada su gaya wa kowa cewa shi ne Almasihu.21Daga lokacin nan Yesu ya fara gaya wa almajiransa cewa dole ne ya tafi Urushalima, ya sha wahala mai yawa a hannun dattawa, da manyan firistoci da malaman attaura, a kashe shi, a tashe shi zuwa rai a rana ta uku. 22Sai Bitrus ya kai shi a gefe ya tsauta masa, cewa, "Wannan ya yi nesa da kai, Ubangiji; wannan ba zai taba faruwa da kai ba." 23Amma Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, "Ka koma bayana, Shaidan! Kai sanadin tuntube ne gare ni, domin ba ka damuwa da abubuwan da suke na Allah, amma sai abubuwan mutane."24Sa'annan Yesu ya ce wa almajiransa, "Duk wanda yake so ya bi ni, lallai ne ya ki kansa, ya dauki gicciyensa, ya bi ni. 25Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi. Duk wanda ya rasa ransa domina zai same shi. 26Domin wace riba mutum zai samu in ya sami dukan duniya ya rasa ransa? Me mutum zai iya bayarwa a maimakon ransa?27Domin Dan Mutum zai zo ne cikin daukakar Ubansa tare da mala'ikunsa. Sa'annan ne zaya biya kowane mutum bisa ga ayyukansa. 28Gaskiya ina gaya maku, akwai wadansun ku da ke tsaye a nan, da ba za su dandana mutuwa ba sai sun ga Dan Mutum na zuwa cikin mulkinsa."
Wannan sashi ya fara da saduwar Yesu da Farisiyawa da kuma Malamen attaura.
A nan "gwadawa" ana amfani da shi tawurin mummunar nufi. AT: "ƙallubale shi" ko "so su sa masa tarko"
Za'a iya bayanin yanayin nan a fili. AT: "Idan sarari tayi jawur da yammaci" ko "Idan sarari tayi jawur a lokacin da rana take sauka"
Wannan na nufin haske, sauki da kuma yanayi mai kyau.
Idan rana ta na sauka, Yahudawa sun san cewa idan sarari ta canza zuwa ja, alama ce cewa washegari zata yi sauki ta kuma yi haske.
Yesu ya cigaba da amsar shi zuwa ga Farisiyawa da kuma Mallamen attaura.
Za'a iya bayanin yanayin nan a fili. AT: "Idan sararin ta yi ja da asuba" ko "Idan sarari ta yi ja alokacin da rana tana tashiwa"
"gizagizai, yanayin ta yi haɗari"
"ta yi ja da kuma gizagizai"
"Kun san yadda ake kallon sarari kun kuma gane wace irin yanayi ce za ku samu"
"amma baku gane yadda zaku dubi abin da yake faruwa yanzu kuma ku gane ma'anar ta ba"
"Yesu yana magana game da zamanin sa ne. AT: "Ku muguye zamani maciya amana ne, wanda kuke neman alamu daga ni ... da za a baku" [12:39]
A nan "maciya amana" magana ce da ake amfani wa mutanen da ba suwa abubuwan gaskiya ga Allah. [12:39] AT: "Zamani mara gaskiya" ko "Zamani marasa tsoron-allah"
Yesu ba zai ba su alamu ba domin, da shike ya rigaya ya yi abubuwan al'ajibai dayawa amma, sun ki su yarda da shi. AT: [12:39] "Ba zan nuna wata alama ba" ko "Allah ba zai nuna maku wata alama ba"
"saidai wancan alamar da aka ba wa annabi Yunusa." [12:39]
Za ka iya yin bayyana maganan nan yadda za a gane ta. AT: "wancan gefen tekun" ko "wancan gefe na tekun Galili"
A nan "yisti" magana ce da take nufin mugun shawara da kuma koyaswar ƙarya. Za a yi bayanin maganar nan gaba [16:12].
"shawara da junansu" ko "tunani game da abun"
"Ku masu ƙarancin bangaskiyan nan." Yesu yayi haka wa almajarensa domin tunanin da suke yi akan rashin kawo gurasa, ya nuna cewa suna da ƙarancin bangaskiya da cewa Yesu zai tanaɗa masu. [6:30]
Yesu yayi anfani da tambaya, ya kwaɓe almajarensa domin rashin fahimtar abin da ya faɗa. AT: "ban ji daɗi ba domin kun yi tunanin cewa kun manta ku kawo gurasa ne ya sa na yi magana game da yistin Farisiyawa da na Sadukiyawa."
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya kwaɓe almajiran. AT: "Haƙika, kun tuna ... kun tattara!"
" 5,000 ... 4,000"
"Ko kun tuna da gurasa bakwai ... kuka ɗauka ba? Yesu yayi anfani da tambaya domin ya kwaɓe almajaren. AT: "Haƙika kun tuna da gurasa bakawai ... da kuka ɗauka!"
Yesu yayi anfani da wannan tambaya domin ya kwaɓe almajaren. AT: "Da kun gane cewa ba gurasa nake magana akai ba."
Wannan nufin ga almajaren ne.
Ana amfani da kalman nan domin a nuna alamar birki cikin ainihin labarin ko kuwa a gabatar da sabon mutum cikin labarin. Anan Matiyu ya fara faɗa subuwar sashi a cikin labarin.
Yesu yana nufin ƙansa ne.
Wannan laƙaɓi ce mai muhinminci ne na Yesu da take nuna dangantakarsa da Allah.
A nan "rai" na kwatanta Allahn Isra'ila da dukkan allohlin ƙarya da kuma gumakai da mutane ke ɓauta wa. Allahn Isra'ila ne kadai yake raye, yana da iko kuma ya aikata.
"Saminu dan Yunusa"
A nan "nama da jini" na nufin mutum mai rai ne. AT: "mutum bai bayyana ba"
A nan "wannan" na nufin kalamun Bitrus ne, cewa Yesu shine Almasihu Ɗan Allah mai Rai.
AT: "amma Uba na wanda ke cikin sama ne ya bayyana maku wannan"
Wannan laƙani ce mai muhinminci ne na Yesu da take bayyana dangantaka sakanin Allah da kuma Yesu.
Wannan ya ƙara yin bayani akan abin da Yesu zai faɗa nan gaba.
"Ma'anar sunan Bitrus shine "dutse."
A nan "gina ikilisiya ta" wata irin magana ce da ake amfani domin a haɗa mutane da suka gaskanta da Yesu da jama'a. AT: 1) "wannan dutse" na nufin Bitrus ne, ko 2) "dutsen nan" na nufin gaskiya da Bitrus ya tashi fada a cikin [Matiyu 16:16]
Ana maganan "Hades" kamar gari ne da take kewaye da katanga da kofofi da take bambanta inda ake ajiye mattatu da kuma rayyayun mutane aciki da kuma waje. Anan "Hades" na nufin mutuwa ne, kuma "kofofin" na nufin ikon ta ne. AT: 1) "ikon mattatu ba za su yi nassara akan ikilisiya na ba" ko 2) "ikilisiya ta za ta yi nassara da ikon mattatu kamar yadda sojoji ke yin nassara da gari."
A nan "ka" na nufin Bitrus ne.
Mabuɗi abu ne da ake amfani a kulle ko a buɗe kofa. A nan suna walkilcin iko ne.
Wannan na nufin Mulkin Allah a matsayin Sarki. Kalman nan "mulkin sama" an yi anfani da shi kadai a littafin Matiyu. Idan zai yiwu, yi anfani da "sama" a fasarar ka.
Wannan maganan na nufin cewa Allah na sama zai amince da bin da Bitrus ya amince ko kuma ya ki amincewa a duniya.
AT: "Allah zai kulla ... Allah zai warware"
Yesu ya gaya masu na farko cewa ya kusan mutuwa. Zai kuma kara gaya masu bayan wannan na farkon. Bayan na farkon ne Bitrus ya kai yesu gefe.
A nan "hannu" na nufin iko. AT: "inda dattawa, manyan firistoci da malaman attaura zasu ba shi wahala"
A nan, a tasher zuwa rai kuma ƙarin magana ne da ya ke nufin saka wanda ya mutu ya zama rayyaye kuma. AT: Dattawa da manyan firistoci zasu kulla wa Yesu domin mutane su ƙashe shi. "mallaman attaura. Sai mutane zasu ƙashe shi, a rana ta uku zai zama rayayye kuma"
"Na uku" adadin jeranta siffa na "uku" ne."
"Bitrus ya yi wa Yesu magana yadda ba wanda zai iya jin su"
Wannan ƙarin magana ne da ke nufin "kada wannan ya faru." AT: "A' a" ko "Allah ya kiyaye wannan"
Yesu yana nufin Bitrus ya na yi kaman Shaidan domin Bitrus yana koƙarin hana Yesu cika nufin Allah game da abin da aka turo shi ya yi. AT: "Ka koma bayana, domin kana yi kaman Shaiɗan! kai sanadin tuntuɓe ne a gare ni" ko "Ka koma bayana, Shaiɗan! Na kira ka Shaiɗan domin kai sanaɗin tuntuɓe ne gare ni"
"Ka yi nesa da ni"
Bin Yesu anan na nufin zama ɗaya daga cikin almajarensa. AT: "zama almajiri na" ko "zama ɗaya daga cikin almajiri na"
"sai ya guje wa sha'awan jikinsa" ko "sai ya bar sha'awar jikinsa"
"ɗauka giciyensa, ya biyo ni." Giciyen na wakilce wahala da kuma mutuwa. Ɗaukan giciyen na nufin amincewa zaka sha wahala zaka kuma mutu. AT: "kuma yi biyyaya ga ni har ga wahala da kuma mutuwa" ko "sai kuma yayi biyyaya ga ni har ga wahala da kuma mutuwa"
Bin Yesu anan na nufin biyayya ga shi ne. AT: "ka kuma yi biyyaya ga ni"
"Ga duk wanda yake so"
Wannan bayanin na nufin cewa dolle ne mutumin zai mutu. Magana ne da yake ma'anan cewa mutumin zai duba yin biyayya ga Yesu a matsayi mafi muhinminci da rayuwarsa.
"domin ya gaskanta da ni" ko "akai na" ko "domina"
Wannan na nufin cewa mutumin zai fuskanci rayuwar ruhaniya da Allah. AT: "zai sami rai na gaskiya"
Yesu yayi anfani da tambaya domin ya koya wa almajarensa. AT: "ba zai kawo riba ga mutum ba ... ransa."
Kalmomin nan "dukan duniya" ƙãri ne ga babban arziki. AT: "idan ya samu duk abin da yake bukata"
"amma ya rasa ransa"
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya koya wa almajarensa. AT: "Babu abin da mutum zai iya bayarwa domin ya samu ransa."
A nan Yesu na nufin kansa ne a matsayin mutum uku. AT: "Ni, Ɗan Mutum ... Ubana ... Sai na"
"zai zo, zai zama da iko daya da Ubansa"
"mala'ikun zasu zauna tare da ni." AT: "mala'ikun Ubana zasu zauna tare da ni."
Wannan laƙani ne mai muhinminci da yake bayyana dangantaka sakanin Allah da Ɗan Mutum, Yesu.
"bisa ga abin da kowane mutum ya yi"
"Ina gaya maku gaskiya." Wannan kalmomin ƙari ce ga abin da Yesu ya fada a gaba.
Dukkan maganganun nan na nufin mala'ikun ne.
A nan "ɗandana" na nufin a fuskanta. AT: "ba za su fuskanci mutuwa ba" ko "ba zai mutu ba"
A nan "mulkinsa" na wakilcin sa a mastayin Sarki. AT: "sai dai sun ga Ɗan Mutum zuwa a kamanin Sarki" ko "sai dai sun ga shaiɗa cewa Ɗan Mutum Sarki ne"
1Bayan kwana shida Yesu ya dauki Bitrus da Yakubu, da Yahaya dan'uwansa, ya kai su kan wani dutse mai tsawo su kadai. 2Kamanninsa ya canja a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, kuma rigunansa suka yi kyalli fal.3Sai ga Musa da Iliya sun bayyana garesu suna magana da shi. 4Bitrus ya amsa ya ce wa Yesu, "Ubangiji, ya yi kyau da muke a wurin nan. In kana so, zan yi bukkoki uku daya dominka, daya domin Musa, daya domin Iliya."5Sa'adda yake cikin magana, sai, girgije mai haske ya rufe su, sai murya daga girgijen, tana cewa, "Wannan kaunattacen Dana ne, shi ne wanda yake faranta mani zuciya. Ku saurare shi." 6Da almajiran suka ji haka, suka fadi da fuskokinsu a kasa, saboda sun tsorata. 7Sai Yesu ya zo ya taba su ya ce, "Ku tashi, kada ku ji tsoro." 8Amma da suka daga kai ba su ga kowa ba sai Yesu kadai.9Yayin da suke saukowa daga dutsen, Yesu ya umarce su, ya ce, "Kada ku fadawa kowa wannan wahayin, sai Dan Mutum ya tashi daga matattu." 10Almajiransa suka tambaye shi, suka ce, "Don me marubuta ke cewa lallai ne Iliya ya fara zuwa?"11Yesu ya amsa ya ce, "Hakika, Iliya zai zo ya maido da dukan abubuwa. 12Amma ina gaya maku, Iliya ya riga ya zo, amma ba su gane shi ba. A maimakon haka, suka yi masa abin da suka ga dama. Ta irin wanan hanya, Dan Mutum kuma zai sha wuya a hannunsu. 13Sa'annan almajiransa suka fahimci cewa yana yi masu magana a kan Yahaya mai Baftisma ne.14Da suka iso wurin taron, wani mutum ya zo gunsa, ya durkusa a gaban sa, ya ce, 15"Ubangiji, ka ji tausayin yarona, domin yana da farfadiya, kuma yana shan wuya kwarai, domin sau da yawa yana fadawa cikin wuta ko ruwa. 16Na kawo shi wurin almajiran ka, amma ba su iya su warkar da shi ba."17Yesu ya amsa ya ce, "Marasa bangaskiya da karkataccen zamani, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe zan jure da ku? Ku kawo shi nan a wurina." 18Yesu ya tsauta masa, sai aljanin ya fita daga cikinsa. Yaron ya warke nan take.19Sai almajiran suka zo wurin Yesu a asirce suka ce, "Me ya sa muka kasa fitar da shi?" 20Yesu ya ce masu, "Saboda karancin bangaskiyarku. Domin hakika, ina gaya maku, in kuna da bangaskiya ko da kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan dutse, 'Matsa daga nan ka koma can,' zai kuwa matsa kuma ba abin da zai gagare ku. 21122Suna zaune a Galili, Yesu ya ce wa almajiransa, "Za a bada Dan Mutum ga hannun mutane. 23Kuma za su kashe shi, a rana ta uku zai tashi." Sai almajiransa suka yi bakin ciki kwarai.24Da suka iso Kafarnahum, mutane masu karbar haraji na rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, "Malaminku na ba da rabin shekel na haraji?" 25Sai ya ce, "I." Amma da Bitrus ya shiga cikin gida, Yesu ya fara magana da shi yace, "Menene tunaninka Saminu? Sarakunan duniya, daga wurin wa suke karbar haraji ko kudin fito? Daga talakawansu ko daga wurin baki?"26Sai Bitrus ya ce, "Daga wurin baki," Yesu ya ce masa, "Wato an dauke wa talakawansu biya kenan. 27Amma don kada mu sa masu karbar harajin su yi zunubi, ka je teku, ka jefa kugiya, ka cire kifin da ya fara zuwa. Idan ka bude bakinsa, za ka sami shekel. Ka dauke shi ka ba masu karbar harajin nawa da naka.
Wannan yana ba da farkon labarin canza kamanin Yesu kenan.
"Bitrus, Yahaya, da Yakubu ɗan'uwan Yahaya"
Da suka kalle shi, kamaninsa ya banbanta da yadda yake da.
AT: "bayyanuwarsa ya canza" ko kuma "bayyanuwarsa ya yi dabam"
"a idonsu" ko kuma "har sun iya ganinsa da kyau"
Waɗannan ƙãrin bayyani ne don a nanata irin hasken da bayyanuwar Yesu ya zama.
"kayakin jikinsa"
Wannan kalmar na jan hankalinmu ne zuwa ga abin mamaki da ya biyo baya.
Wato Bitrus, Yakubu, da Yahaya.
"da Yesu"
"cewa." Ba amsa tambaya Bitrus ke yi ba.
Babu wata taƙamammen bayani ko "mu" na nufin Bitrus, da Yakubu, da Yahaya ne kadai ko kuma idan yana nufin dukkan waɗanda ke wajen, a haɗe da Yesu, Iliya, da Musa. Idan za ku iya juya wannan don ya ba da dukkan ra'ayi biyun, to, sai ku yi hakan.
Wannan na iya nufin 1) wuraren da mutane za su iya zuwa don yin sujada ko kuma 2) wurare da mutane za su iya yi barci amma ba na dindindim ba.
"ya maimaye su"
A nan "murya" na nufin maganar da Allah ke yi. AT: "Sai Allah yayi magana da su daga girgijen"
"almajiran suka ji Allah na magana"
A nan "faɗi da fuskokinsu" karin magana ne. AT: "suka durkusa da fuskokinsu ƙasa"
Waɗannan abubuwan da suka biyo baya sun faru ne ba da jimawa ba bayan almajire ukun sun gan canjawar kamanin Yesu.
"Yayin da Yesu da almajiransa"
Yesu yana magana a kan shi da kansa ne.
Almajiran na magana ne game da wata sani na cewa Iliya zai dawo da rai ya kuma koma zuwa ga mutanen Isra'ila kafin Almasihu ya zo.
"yă sa abubuwa su yi daidai" ko kuma "yă shirya mutane domin marabtan Amasihu"
Wannan na ƙara nanata maganar Yesu da ke biyo baya ne.
Duk wuraren da waɗannan kalamun sun auku, sun iya nufin 1) shugabannin Yahudawa ko kuma 2) dukkan mutanen Yahudawa.
A nan "hannu" na nufin iko. AT: za su sa Ɗan Mutum yăsha wuya"
Yesu yana magana a kan shi da kansa ne.
Ana ɗaukan cewa mutumin yana so Yesu ya warkar da yaronsa ne. AT: "ka yi wa ɗa na jinkai ka warkar da shi"
Wato wani lokaci ya kan yi farfaɗiya. Hankalinsa ya kan fita, sai ya zama gagararre. AT: "yana da farfaɗiya"
"Wannan tsaran bata gaskanta da Allah ba kuma ba ta san abinda ke daidai da wanda ba daidai ba. Har"
Waɗannan tambayoyin suna nuna bakin cikin Yesu da mutanen. AT: "Na gaji da kasancewa tare da ku! Na gaji da rashin bangaskiyar ku da karkacewan ku!"
AT: "yaron ya sami warkaswa"
Wannan karin magana ne. AT: "nan da nan" ko kuma "a daidai lokacin"
A nan "mu" na nufin masu magana amma banda masu sauraro don haka, ba kowa da kowa bane.
"Me yasa ba mu iya fitar da aljannun daga jikin yaron ba?"
"Ina faɗa maku gaskiya." Wannan na ƙara nanata abin da Yesu zai faɗa ne.
Yesu yana kwatanta girrman kwayar mastad da iyakar bangankiyar da ake buƙata don a yi al'ajibi. Kwayar mastad karami ne sosai, amma yana girma ya zama wani babban bushiya. Yesus yana nufin cewa muna buƙatar bangaskiya kaɗan ne kawa mu iya yin babban al'ajibi.
AT: "za ku iya yin kowani abu"
Yesu da almajiransa suna zaune"
AT: "Wani zai ba da Ɗan mutum"
Yesu yana nufin shi kansa ne amma yan maganar kaman wani ne uku ne yake magan akai.
Kalmar "hannu" anan na nufin ikon da mutane ke moran hannun su su yi amfani da shi. AT: "ɗauke shi a sa shi a karkashi ikon mutane" ko kuma "ɗauke shi a ba da shi ga mutanen da za su yi da shi yadda suke so"
A nan "hannu" na nufin iko ko mulkin mutane"
"Uku" shi ne jerin kirge "uku"
Wato zai tashi daga matattu kenan. AT: Allah zai ta da shi kuma" ko kuma "Allah zai tashe shi da rai kuma"
Da Yesu da almajiransa"
Wannan harajjin ne mutanen Yahudawa ke biya don su tallafa wa haikalin da ke Urusahalima. AT: "haikalin haraji"
"wurin da Yesu ke zama"
Yesu yana wannan tambayan ne domin ya koya wa Saminu cewa, kada yă samu sanin don kansa kadai. AT: "Ka ji, Saminu. Mun san da cewa yayin da sarukuna sun karɓa haraji, suna karɓa ne daga wurin mutanen da ba 'yan gidansu ba"
Idan kun juya maganar a [17:25], kuna iya ba da wat hanya da za a iya juya ta anan. AT: "Da Bitrus ya ce, 'i, wannan gaskiya ne. Sarakuna suna karɓan haraji daga baƙi ne,' Yesu ya ce" ko kuma "Da Bitrus ya amince da maganar da Yesu ya yi, Yesu ya ce"
A zamanin yau, shugabanni sukan sa haraji wa nasu mazauna. Amma, a zamanin da, shigabanni suka sa haraji wa mutanen da su ci su da yaƙi ne ba mazaunan garinsu ba.
mutanen da mai mulki ko sarki ke mulki a bisansu
"Amma ba mu so mu sa masu karɓan haaji su yi fushi. Don haka, jeka"
Masu kaman kifi sukan ɗaura kugiyansu a ƙarshen igiya, sa'annan su jefa shi a ruwa don su kamo kifi.
"baƙin kifin"
kuɗi wanda ya isa ladan aiki na kwana huɗu
ka ɗauki kuɗin"
A nan "naka" na nufin Bitrus. Lalle ne kowanensu ya biya harajin rabin shekel. Don haka shekel ɗaya zai issa wa Yesu da Bitrus su biya harajinsu.
1Daidai wannan lokacin, almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, "Wanene mafi girma a mulkin sama?" 2Sai Yesu ya kira karamin yaro gunsa, ya sa shi a tsakaninsu, 3ya ce, "Hakika ina gaya maku, idan baku juya kun zama kamar kananan yara ba, babu yadda zaku shiga mulkin sama.4Saboda haka, duk wanda ya kaskantar da kansa kamar karamin yaron nan, shi ne mafi girma a mulkin sama. 5Duk wanda ya karbi karamin yaro a suna na, ya karbe ni. 6Amma duk wanda ya sa daya daga cikin 'yan yaran nan da suka gaskanta da ni zunubi, gwamma a rataya dutsen nika a wuyansa a jefa shi cikin zurfin teku.7Kaiton duniya saboda lokacin tuntube! Lallai ne wadannan lokuta su zo, amma kaiton mutumin da ta wurinsa ne wadannan lokutan za su zo! 8Idan hannunka ko kafarka ce za ta sa ka tuntube, ka yanke ta, ka yar daga gare ka. Zai fi maka kyau ka shiga rai da nakasa ko gurguntaka, da a jefa ka cikin madawwamiyar wuta tare da hannayenka ko kafafunka.9Idan idonka zai sa ka tuntube, ka kwakule shi, ka yar. Zai fi maka kyau ka shiga rai da ido daya, da a jefa ka cikin madawwamiyar wuta da idanu biyu.10Ku kula fa kada ku rena kananan nan. Domin koyaushe a sama, mala'ikunsu na duban fuskar Ubana da ke sama. 11112Menene tunaninku? Idan mutum na da tumaki dari, sa'annan daya ta bata, ashe ba zai bar tassa'in da tara a gefen tudu ya tafi neman wadda ta bata ba? 13In ya same ta, hakika ina gaya maku, farin cikinsa na samun dayan nan da ta bace, zai fi na tassa'in da taran nan da basu bata ba. 14Hakanan fa, ba nufin Ubanku dake sama ba ne da ya daga cikin wadannan kananan ya hallaka.15Idan dan'uwanka yayi maka laifi, fada masa tsakaninku, kai da shi kadai. Idan ya saurare ka, ka maido da dan'uwanka kenan. 16Amma in ya ki ya saurare ka, ka je da 'yan'uwa biyu ko uku su zama shaidu, don ta wurin shaidu biyu ko uku ake tabbatar da kowacce kalma.17In kuma ya ki ya saurare su, ka kai lamarin ga ikklisiya. Idan ya ki ya saurari ikklisiya, ka maishe shi ba'al'umme da mai karbar haraji.18Hakika ina gaya maku, duk abin da kuka daure a duniya, a daure yake a sama. Abin da kuka kwance kuma, a kwance yake a sama. 19Kuma ina gaya maku, idan mutum ku biyu zaku yarda akan duk abin da zaku roka, Ubana wanda ke a sama zai yi maku shi. 20Wurin da mutum biyu ko uku suka taru a cikin sunana, zan kasance tare da su."21Bitrus ya zo ya ce wa Yesu, "Ubangiji, sau nawa ne dan'uwana zai yi mani laifi in gafarta masa? Har sai ya kai sau bakwai?" 22Yesu ya amsa ya ce masa, "Ban gaya maka sau bakwai ba, amma bakwai din ma har sau saba'in.23Saboda haka, za a kwatanta mulkin sama da wani sarki da yake so ya lisafta dukiyarsa dake a hannun barorinsa. 24Da ya fara yin haka, sai aka kawo masa daya daga cikin barorinsa da yake binsa talanti dubu goma. 25Amma tunda ba shi da abin biya, ubangidansa ya bada umurni a sayar da shi, tare da matarsa da 'ya'yansa da duk mallakarsa, domin a biya.26Sai baran ya fadi kasa, ya rusuna a gaban ubangidansa ya ce, "Maigida, kayi mani hakuri, zan biya duk abin da na karba." 27Don haka ubangidansa yayi juyayi, sai ya ce, ya yafe bashin, a saki baran.28Amma bayan an saki wannan baran, ya je ya sami wani baran kamar sa da yake bi bashin dinari dari. Ya cafke shi, ya shake shi a wuya, ya ce, 'Ka biya bashin da nake bin ka.' 29Amma dan'uwansa bara ya roke shi ya ce, kayi mani hakuri, zan biya ka duk abinda na karba.'30Amma baran nan na farko ya ki. A maimakon haka, ya sa aka jefa dan'uwansa bara a kurkuku sai ya biya bashin nan. 31Da sauran barori suka ga abin da ya faru, suka damu kwarai. Sai suka je suka fada wa ubangidansu yadda abin ya faru duka.32Sai ubangidansa ya kirawo shi, ya ce masa, "Kai mugun bawa, na gafarta maka bashin nan duka, domin ka roke ni. 33Ashe, bai kamata kaima ka nuna jinkai ga dan'uwanka bara kamar yadda na nuna maka jinkai ba?'34Ubangidansa yayi fushi, ya danka shi ga masu azabtarwa, har sai ya gama biyan dukan bashin da ake binsa. 35Hakanan Ubana dake a sama zai yi maku, idan kowannenku bai gafarta wa dan'uwansa daga zuciya ba."
Wannan itace farkon labarin da ya maimaiye littafin Matta [18:35] inda Yesu yake koyarwa game da rayuwa a cikin mulkin sama. Anan, Yesu yana amfani ne da karamin Yaro a koyaswan shi ga almajiran.
"Wanene mafi muhimmanci" ko kuma "Wanene a cikinmu mafi muhimmanci"
Jimlar nan "mulkin ssama" na nufin sarautar Allah a matsayinsa na sarki. An yi amfani da wannan jimlar a littafin Matta ne kadai. In ya yiwu, ku bar "sama" a naku juyin. AT: "a mulkin Allah" ko kuma "yayin da Allahn mu na sama zai kafa mulkinsa a duniya"
"Ina gaya maku gaskiya." Wannan na kara nanata magan Yesu da ke biya baya ne.
AT: "sai kun canza ... kananan yara kamun ku shiga"
Yesu yana amfani ne da wannan karin magana ya koya wa almajiransa cewa kada su damu da zancen wanene mafi muhimmanci. Sai dai su damu da zancen wanene ke kaskatar da kansa kamar karamin yaro.
Jimlar nan "mulkin sama" na nufin sarautar Allah a matsayin sa na sarki. An yi amfani da wannan jimlar a littafin Matta ne kadai. In ya yiwu, ku bar "sama" a naku juyin. AT: "shiga mulkin Allah" ko kuma "zama da Allahn mu a sama yayin da ya kafa mulkinsa a nan duniya" (Dubi: )
Yesu ya cigaba da koya wa almajiransa muhimmancin zama da kaskanci kamar karamin yaro idan suna so su zama da girma a mulkin Allah.
"shi ne mafi muhimmanci" ko kuma "zai zama mafi muhimmanci"
A nan "suna na" na nufin mutum gabaɗaya. AT: "saboda ni" ko kuma "saboda shi almajiri na ne"
Yesu yana nufincewa daidai ne da marabtansa. AT: "Yayin da wani ... a suna na, yana daidai kamar yana marabta na ne" ko kuma "Yayin da wani ... a suna na, kamar yana marabta na ne"
AT: "in wani ya sa masa dutsen niƙa a wuyansa ya jefa shi cikin teku mai zurfi"
Wannan babban mulmulallen dutse ne, mai nauyi, da ake niƙa hatsi zuwa gari da ita. AT: "wata dutse mai nauyi"
A nan "duniya" na nufin mutane. AT: "mutanen duniya"
A nan "tuntuɓe" karin magana ne da ke nufin zunubi. AT: "abubuwan da ke sa mutane zunubi ... abubuwa za su zo da za su sa mutane su yi zunubi ... duk wanda ya sa wasu su yi zunubi"
Yesu ya yi wannan maganada karfi domin yă nanata cewa lallai ne mutane su yi komen da yakamata domin su kawas da zukatansu daga duk abinda ke sa su zunubi.
Yesu yana maganar mutane ne gabaɗaya. Zai fi ɗacewa harshenku ta juya wannan yadda za ta nuna cewa mutane masu yawa ne "ka" ɗin.
"cikin rai madawami"
AT: "da ka zama da hannayenka da kafafunka yayin da Allah ke jefa ka cikin madawwamiyar wuta"
Umarnin kwalkwale idon, wadda mai yiwuwa shi ne gabar jiki mafi muhimmanci, na iya zama kururuta magane ne kawai ga masu sauraronsa cewa su yi komai da yakamata domin su yi nesa da duk wani abu a rayuwarsu da ke sa su zunubi.
A nan "tuntuɓe" ƙarin magana ne da ke nufin zunubi. AT: "ke sa ka zunubi"
AT: "da ka kasance da idanuka biyu yayin da Allah ke jefa ka cikin madawwamiyar wuta"
"Ku yi hankali" ko kuma "Ku tabbatar cewa"
"kada ku ɗauki waɗannan kananan da rashin muhimmanci." AT: "ku ba waɗannan kananan nan girma"
Wannan na ƙara nanata maganar Yesu da ke biyo baya ne.
Malaman Yahudawa suna kayar da cewa mala'iku mafi muhimmanci ne kawai suna iya kasancewa a gaban Allah. Yesu kuma yana nufin cewa mala'iku mafi muhimmanci suna magana da Allah akan waɗannan kananan nan.
Wannan wata karain magana ne da ke nufin cewa suna gaban Allah. AT: "suna kusa da Ubana a kodayaushe" ko kuma "suna gaban Ubana a kodayaushe"
Wannan wata lakaɓi ne mai muhimmanci da ke bayyana ɗangartakan da ke tsakanin Allah da Yesu.
Yesu yana amfani da wannan tambayan ne domin ya jawo hankalin jama'a. AT: "Ku yi tunanin yadda mutane ke yin." ko kuma "Ku yi tunanin wannan"
...
Yesu yana amfani ne da misalai yă koya wa almajiransa.
"100 ... 99"
Yesu yana amfani ne da wannan tambayan ya koya wa almajiransa. AT: "zai riƙa barin ... băta ba"?
Ubanku da ke sama ba ya son ɗaya daga cikin waɗannan kananan nan ya mutu" ko kuma "Ubanku da ke sama ba ya son ko ɗaya daga cikin waɗannan kananan ya mutu"
Wannan wata lakaɓi ne mai muhimmanci na Allah.
Wato ɗan'uwanka a bin Allah kenan, ba wai na ciki ɗaya ba. AT: "ɗan'uwanka mai bi"
"ka sa ɗangartakanka da ɗan'uwanka ya yi kyau kenan kuma"
A nan "bãki" da "kalma" na nufin abinda mutum ya faɗa. AT: "don mutm biyu ko uku su tabbatar cewa abin nan da ka faɗa game da ɗan'uwanka gaskiya ne"
"In ɗan'uwanka mai bi ya ƙi yă saurare shaidun da suka zo tare da kai"
"taron masubi gabaɗaya"
"ka bi da shi kamar yadda za ka bi da Ba'alumme ko mai karɓar haraji." Wannan na nufin cewa a cire shi daga taron masubi.
...
Wannan wata karin magana ne da ke nufin cewa Allah na Sama zai amince da abinda almajiransa suka amince da shi ko sun haramta a duniya. Duba yadda kuka juya irin wannan jimlar a [16:19]
AT: "Allah zai ɗaure ... Allah zai kwance"
Wannan yana ƙara nanata maganar Yesu da zai biyo baya kenan.
Ana ɗaukan cewa Yesu na nufin "idan a kalla mutum biyu" ko kuma "in ku biyu ko fiye."
Wannan na nufin "ku biyu." AT: "ku ... ku"
Ana ɗaukan cewa Yesu na nufin "biyu ko fiye" ko kuma "a kalla mutum biyu"
"haɗu"
"sau 7"
Wannan na iya nufin 1) 70 sau 70" ko kuma 2) "sau 77." Idan amfani da lamba zai kawo rikicewa, kuna iya jya shi kamar "sau fiye da iya lisafin da kuka iya yi" ko kuma "lallai ne ku yi ta gafarta masa"
Wannan na gabatar da wata misali ne. Duba yadda kuka juya irin wannan gabatar da misalin a [13:24]
"barorinsa su biya bashin da ake binsu"
AT: "sai wani ya kawo ɗaya daga cikin barorin sarkin"
"talanti 10,000" ko kuma "kuɗi mai yawa da bawan ba zai iya biya ba"
AT: "saikin ya umarci barorinsa su sayar da mutumin ... domin a biya bashin da kuɗin da aka samu"
Wannan na nuna cewa baran ya zo gaban sarkin a wata hanya da ta fi nuna kaskanci.
"a gaban sarkin"
"ya ji tausayin baran"
"a bar shi ya tafi"
"dinari 100" ko kuma "ladan aikin kwana ɗari"
"Bara na farkon ya shaƙe ɗan'uwansa bara"
"ya cafke shi" jo kuma "ya riƙe shi"
Wannan na nuna cewa baran ya zo gaban sarkin a wata hanya da ta fi nuna kaskanci.Duba yadda kuka juya wannan a [18:26].
...
"bawa na farkon ya je ya sa aka jefa ɗan'uwansa bawa a kurkuku"
"sauran barorin"
"faɗa wa sarkin"
"Sai sarkin ya kirawo bara na farkon"
...
Sarkin yana amfani ne da wannan tambayan yana yi masa sawa. AT: "Ai da ka ...maka ...!"
"Sarkin"
"ya miƙa shi." Akwai sammani ko sarkin ne ya ɗauke bara na farin zuwa ga waɗanda za su azabce shi." AT: "ya umarci barorinsa su danka shi"
"ga waɗanda za su ba shi azaba"
AT: "da sarkin ke bin bara na farkon
Wannan wata laƙani ne mai muhimmanci da ke bayyana ɗangantakan da ke tsakanin Allah da Yesu.
Yesu yana magana ne da almajiransa, amma misalin sa yana koyar da gamammaiyar gaskiya da ya shafe dukkan masubi.
A nan "zuciya" na nufin tunanin da ke cikin mutum. Jimlar nan "daga zuciya" karin magana ne da ke nufin da "gaske." AT: "da gaske" ko kuma "gabaɗaya"
1Sai ya zama sa'adda Yesu ya gama wadannan maganganu, sai ya bar Galili ya zo kan iyakokin Yahudiya, ketaren kogin Urdun. 2Taro mai yawa suka bi shi, ya kuma warkar da su a wurin.3Farisawa suka zo wurinsa, suna gwada shi, suka ce masa, "Ya hallata bisa ga doka mutum ya saki matarsa don kowanne dalili?" 4Yesu ya amsa ya ce, "Baku karanta ba, cewa shi wanda ya yi su tun farko ya yi su miji da mace?5Shi wanda ya yi su kuma ya ce, "Saboda wannan dalilin, mutum zai rabu da mahaifinsa da mahaifiyarsa ya hade da matarsa, su biyun su zama jiki daya?" 6Su ba biyu ba ne kuma, amma jiki daya. Don haka, duk abin da Allah ya hada, kada wani ya raba."7Sai suka ce masa, "To me yasa Musa ya umarcemu mu bada takardar saki, mu kuma kore ta?" 8Sai ya ce masu, "Saboda taurin zuciyarku, shi yasa Musa ya yarda maku ku saki matanku, amma da farko ba haka yake ba. 9Ina gaya maku, duk wanda ya saki matarsa in ba saboda zina ba, ya kuma auri wata, yana zina kenan. Wanda kuma ya auri macen da aka saka, yana aikata zina."10Almajiran suka ce wa Yesu, "Idan haka yake game da mutum da matarsa, ba kyau ayi aure ba." 11Amma Yesu yace masu, "Ba kowa ne zai karbi wannan koyarwa ba, amma sai wadanda an yardar masu su karbe ta. 12Akwai wadanda aka haife su babanni. Akwai wadanda mutane ne suka maida su babanni. Sa'annan akwai wadanda sun mayar da kansu babanni saboda mulkin sama. Duk wanda zai iya karbar wannan koyarwa, ya karba."13Sai aka kawo masa yara kanana don ya dibiya hannuwansa akansu, yayi masu addu'a, amma almajiran suka kwabe su. 14Amma Yesu ya ce masu, "Ku bar yara kanana, kada ku hana su zuwa wuri na, domin mulkin sama na irinsu ne." 15Ya sa hannuwa akan su, sa'annan ya bar wurin.16Sai wani mutum ya zo wurin Yesu, ya ce, "Malam, wanne ayyuka nagari ne zan yi domin in sami rai madawwami?" 17Yesu ya ce masa, "Me yasa kake tambaya ta game da abin da ke nagari? Daya ne kawai ke nagari, amma idan kana so ka shiga cikin rai, ka kiyaye dokokin."18Mutumin ya ce masa, "Wadanne dokokin?" Yesu ya ce masa, "Kada kayi kisa, kada kayi zina, kada kayi sata, kada kayi shaidar zur, 19ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma ka kaunaci makwabcinka kamar kanka."20Saurayin nan ya ce masa, "Ai na kiyaye duk wadannan. Me nake bukata kuma?" 21Yesu ya ce masa, "Idan kana so ka zama cikakke, ka tafi ka sayar da mallakarka, ka kuma ba matalauta, zaka sami dukiya a sama. Sa'annan ka zo ka biyo ni." 22Amma da saurayin nan ya ji abin da Yesu ya fada, ya koma da bakin ciki, domin shi mai arziki ne kwarai.23Yesu ya ce wa almajiransa, "Hakika ina gaya maku, zai zama da wuya mai arziki ya shiga mulkin sama. 24Ina sake gaya maku, zai fi wa rakumi sauki ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah."25Da almajiran sun ji haka, suka yi mamaki kwarai da gaske, suka ce, "Wanene zai sami ceto?" 26Yesu ya dube su, ya ce, "A wurin mutane wannan ba zai yiwu ba, amma a wurin Allah, kome mai yiwuwa ne." 27Sai Bitrus ya amsa ya ce masa, "Duba, mun bar kome da kome mun bi ka. To me za mu samu?"28Yesu ya ce masu, "Hakika ina gaya maku, ku da kuka bi ni, a sabuwar haihuwa, lokacin da Dan Mutum ya zauna a kursiyin daukakarsa, ku ma zaku zauna a kursiyoyi goma sha biyu, kuna shari'anta kabilu goma sha biyu na Isra'ila.29Duk wanda ya bar gidaje, 'yan'uwa maza, 'yan'uwa mata, mahaifi, mahaifiya, 'ya'ya, ko gonaki, saboda sunana, zai sami ninkin su dari, ya kuma gaji rai madawwami. 30Amma dayawa dake farko yanzu, za su zama na karshe, dayawa dake karshe kuma, su zama na farko.
Wannan ita ce farkon wata sabuwar sashin labarin da ta biyo [22:46] da ke maganar hidimar Yesu a Yahudiya.
Wannan jimlar yana canza labarin daga koyarwar Yesu zawa abinda ya faru nan gaba. AT: "Da" ko kuma "Bayan da"
A nan "maganganu" na nufin koyarwan da Yesu ya yi daga [18:1]. AT: "ya gama koyar da waɗannan abubuwa"
"ya tafi daga" ko kuma "ya tashi daga"
Yesu Ya fara koyarwa akan aure da saki.
"suka zo wurin Yesu"
A nan "gwada" ba domin alheri ba. AT: "sai suka sokane shi ta wurin tambayansa" ko kuma "suna son su yi masa tarko ta hanyar yi masa tambaya"
Yesu yana amfani ne da wannan tambayan don yă tunashe Farisiyawan da abinda nassosin suka ce game da miji, mace, da kuma aure. AT: "Hakika kun karanta, cewa tun farko da Allah ya hallici mutane, ya hallice su miji da mace."
Wannan shi ne abinda Yesu yana sammanin Farisawa sun fahimta daga nassi. AT: "kuna haƙĩƙa kun sani cewa Allah ma ya faɗi cewa don wannan dalilin ... jiki"
Wannan sashin labarin daga littafin Farawa ne dame da Adamu da Hauwa'u. A wannan wurin, dalilin da namiji zai bar Ubansa da Uwatasa shi ne domin Allah ya hallici mace ta zama abokiyan tarayyan sa.
"ya zama kusa da matarsa" ko kuma "ya zauna da matarsa"
Wannan wata karin magana ne da ke nanata ɗayantakar mai gida da uwargida. AT: "za su zama kamar mutum ɗaya"
Wannan wata ƙarin magana ne da ke nanata ɗayantakar mai gida da uwargida. AT: "Don haka maigida da uwargida ba mutum biyu kuma ba, ammam suna kamar mutu m ɗaya ne"
"Farisiyawan sun ce wa Yesu"
"umarce mu Yahudawa"
Wannan wata takardar shaida ne da ke yanke raba aure bisa ga ka'ida.
Jimlar nan "taurin zuciya" ƙarin magana ne da ke nufin "taurin kai" AT: "Saboda taurin kan ku" ko kuma "Domin kuna da taurin kai"
Yesu yana magana da Farisawa ne, ammam Musa ya ba da wannan umarnin a shekaru da dama ne tun kakanninsu. Umarnin Musa ya shafe dukkan mutanen Yahudawa ne gabaɗaya.
Anan "farko" na nufin lokacin da Allah ya fara hallitan na miji da mace.
Wannan na kara nanata maganar Yesu da ya biyo baya ne.
Kuna iya kara haske a bayanin. AT: "auri wata mata"
Wasu rubuce-rubuce na dã basu haɗa waɗannan kalmomin ba.
AT: "waɗanda Allah ya bar su" ko kuma "waɗanda Allah ya izasu"
Kuna iya kara haske a wannan bayyani. AT: "Akwai dalilai daban daban da ya sa mutane basu aure. Ana misali, akawai maza da yawa da aka haife su babanni"
AT: "akawai waɗanda wasu mutane ne suka mayar da su babanni"
Wannan na iya nufin 1) mutanen da sun mayar da kansu babanni ta wurin cire gabansu" ko kuma 2) "mutanen da sun zaɓa su zama a rashin aure da kuma tsarkinsu a sashin jima'i
A nan "mulkin sama" na nufin sarautar Allah a matsayin sarki. Ana samun wannan jimlar a littafin Mata ne kawai. In ya yiwu, ku ba "sama" a juyin ku. AT: "don su fi iya bauta wa Allahn mu a sama"
"karɓa wannan koyarwa ... karɓe shi"
AT: "wasu mutane sun kawo wa Yesu yara kanana"
...
"kada ku hana su zuwa wurin na"
A nan "mulkin sama" na nufin sarautar Allah a matsayin sarki. Ana samun wannan jimlar a littafin Matta ne kadai. In Ya yiwu, sai ku bar "sama" a naku juyin. AT: "gama idan Allahn mu a sama ya kafa nasa sarautar a duniya, a bisa irin waɗannan" ko kuma "gama Allah yana barin irin waɗannan a cikin mulkinsa"
"na irin waɗanada su na kamar yara kanana ne." Wannan wata karin magana ne da ke nufin cewa waɗanda suna da kaskanci kamar yara kanana za su shiga mulkin Allah.
Wannan kalmar "ga shi" yana jan hankulan mu ne zuwa ga wani sabon mutum a labarin. Mai yiwuwa harshen ku ma da wata hanyar yin haka.
wato abinda ke gamsar Allah.
Yesu yana amfani da wannan tambayan gangancin ne domin ya ƙarfafa mutumin game da dalilinsa na tambayan Yesu game da abinda ke nagari. AT: "ka tambaye ni game da abinda ke nagari" ko kuma "Yi tunanin dalilin da ya sa ka yi mani tambaya akan abinda ke nagari"
"Allah ne kaway ke nagari gabakiɗaya"
"karba rai madawammi"
Mutanen Yahudawa sun gaskanta cewa makwabtansu ne kawai sauran Yahudawa. Yesu kuma yana faɗada wannan bayyani ya haɗa da dukkan mutane.
"idan kana marmari
AT: "waɗanda ke talakawa ne"
Jimlar nan "dukiya a sama" karin magana ne da ke nufin lada daga Allah. AT: "Allah zai baku lada daga sama"
"Ina gaya maku gaskiya." Wannan jimlar yana kara nanata maganar Yesu da zai biyo baya ne.
A nan "mulkin sama" na nufin sarautar Allah a matsayin sa na sarki. Ana samu wannan jimlar a littafin Matta ne kadai. In ya yiwu, ku bar "sama" a juyin ku. AT: "yă karɓa Allahnmu a sama a matsayin sarkinsu"
Yesu yana amfani ne da wannan kururtan ya kwatanta yadda ya ke da wuya wa mutum mai arziki yă shiga mulkin Allah.
ramin da ke kusa da ƙarshen allura, ta wurin da zaren ke bi
"almajiran suka yi mamaki." Ana ɗaukan cewa suka yi mamaki ne domin sun gaskanta cewa arziki alama ce cewa Allah ya amince da mutum.
Almajiran suna amfani ne da wannan tambayan don su nuna mamakinsu. AT: "To ai ba mutumin da Allah zai cetas!" ko kuma "To ai ba wanda zai samu rai madawammi!"
"mun bar duk dukiyoyiimu" ko kuma "mun yafe dukkan mallakarmu"
Wane abu nagari ne Allah zai bamu?
"a sabuwar lokaci." Wannan na nufin yayin da ya mai gyara dukkan kome. AT: a lokacin da Allah ya sa kome ya zama sabo"
Yesu na magana game da kansa ne.
Zama a kursiyinsa na nufin sarautar sa a matsayin sa na sarki. Kursiyinsa kuma ya zama da ɗaukaka na nufin sarautar sa ya zama da ɗaukaka. AT: "Yana zaune a kursiyinsa na ɗauka" ko kuma "yana sarauta da ɗaukaka a matsayin sarki"
A nan zama a kursiyoyi na nufin sarauta a matasyin sarakuna. Almajiran ba za su zama daidai da Yesu da shi ma ke bisa kursiyin ba. Za su karɓi iƙo daga wurinsa. AT: "zauna a matsayin sarakuna a bisa kursiyoyi 12"
A nan "kabilu" na nufin mutanen waɗannan kabilun. AT: "mutanen kabilu 12 na Isra'ila"
A nan "suna" na nufin mutumin gabaɗaya. AT: "saboda ni" ko kuma "domin ya gaskanta da ni"
"zai karɓa daga wurin Allah ninki 100 kamar iyakan nagargarin abubuwan da suka bari"
Wannan wata karin magana ne da ke nufin "Allah zai albarkace su da rai madawwami" ko kuma "Allah zi sa su rayu har abada."
A nan "farko" da "ƙarshe" na nufin matsayi ko muhimmancin mutane. Yesu yana banbanta matasyin mutane a yanzu da kuma matasyinsu a mulkin sama. AT: "Amma ma su yawa da sun na yi kamar suna da muhimmanci a yanzu za zama da mafi ƙanƙantan muhimmanci, kuma da yawa da suke yi kamar ba su da muhimmanci a yanzu za su zama da muhimmanci ƙwarai"
1Gama mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da asuba ya nemi 'yan kwadago da za su yi aiki a gonarsa. 2Bayan sun shirya kudin da zai biya ma'aikata kimanin dinari daya a kowanne yini, sai ya aike su gonarsa suyi aiki.3Misalin sa'a ta uku sai ya sake fita, sai ya ga wasu ma'aikata suna tsaye a bakin kasuwa, babu aiki. 4Sai ya ce masu, 'Kuzo kuyi aiki a gonar, duk abinda ya wajaba, zan ba ku,' Sai suka tafi su yi aikin.5Sai ya sake fita a sa'a ta shida ya kuma sake fita a sa'a ta tara, ya sake yin hakan din. 6Ya kuma sake yin haka a sa'a ta sha daya, da ya fita sai ya ga wasu a tsaye da ba sa yin kome. Sai ya ce masu, 'Me yasa kuke tsaye ba ku yin kome dukan yini?' 7Sai suka ce masa, 'Ai babu wanda ya dauke mu aiki, shi yasa.' Sai ya ce masu, 'ku ma, kuje cikin gonar.8Da yamma ta yi, sai mai gonar ya ce wa manajansa, 'Ka kira ma'aikatan nan ka biya su hakkin su, amma ka fara da wadanda suka zo a karshe, zuwa na farkon.' 9Sa'adda wadanda suka fara aiki da yamma suka zo, an biya su daidai yadda ake biya a yini. 10Da wadanda suka fara aiki tun safe suka zo, suna tsammani za a ba su fiye da wadanda sun zo daga baya, amma aka ba kowannensu dinari daya.11Da suka karbi hakkinsu, suka yi gunaguni game da mai gonar. 12Suka ce, 'Wadannan da suka zo a karshe, sa'a guda ce kadai suka yi aiki, amma ka ba su daidai da mu, mu da muka yi fama da aiki cikin zafin rana.'13Amma mai gonar ya amsa wa daya daga cikin su, ya ce, 'Aboki na, ban yi maku laifi ba. Ai mun shirya zan biya ku yadda ake biya a yini, ko ba haka ba? 14Ku karbi abin da ke na ku, ku tafi. Ganin dama ta ne, in ba wadannan da suka zo a karshe daidai da ku.15Ashe, ba daidai bane a gare ni, in yi abin da na ga dama da mallaka ta? Ko kishi ne kuke yi saboda kirki na?' 16Haka yake, na karshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na karshe." 117Da Yesu zai tafi Urushalima, ya dauki sha-biyun nan a gefe, yayin da suke tafiya, sai ya ce masu, 18"Ku duba fa, zamu tafi Urushalima, kuma za a bada Dan Mutum ga manyan firistoci da marubuta. Za su kuma yanke masa hukuncin kisa, 19za su kuma bada shi ga al'ummai don suyi masa ba'a, su bulale shi, su kuma gicciye shi. Amma a rana ta uku, za a tada shi."20Sai uwar 'ya'yan Zabadi ta zo wurin Yesu tare da 'ya'yanta. Ta rusuna a gabansa tana neman alfarma a wurinsa. 21Yesu ya ce mata, Me kike so in yi maki?" Sai ta ce masa, "Ina so ka ba 'ya'yana izinin zama a mulkinka, daya a hannun damanka, daya kuma a hannun hagunka.22Amma Yesu ya amsa, ya ce, "Baku san abin da kuke roko ba. Ko zaku iya sha daga cikin kokon da zan sha bada dadewa ba?" Sai suka ce masa, "Zamu iya." 23Sai ya ce masu, "In dai kokon nan da zan sha ne, lallai zaku sha. Amma, zama a hannun dama na da kuma hannun hagu na, ba ni ne mai bayarwa ba, amma na wadanda Uba na ya shirya domin su ne." 24Sa'anda sauran almajirai goma suka ji haka, sun yi bacin rai da 'yan'uwan nan biyu.25Amma Yesu ya kira su wurin sa, ya ce, "Kuna sane da cewa, sarakunan al'ummai suna gwada masu mulki, manyan-gari kuma na nuna masu iko. 26Ba zai kasance haka a tsakanin ku ba. A maimakon haka, duk wanda ke da marmari ya zama da girma a tsakanin ku, ya zama baran ku. 27Wanda kuma ke da marmari ya zama na farko a cikin ku, ya zama baran ku. 28Kamar dai yadda Dan mutum bai zo don a bauta masa ba, amma yayi bauta, ya kuma bada ransa fansa domin mutane dayawa."29Da suka fita daga Yariko, babban taro suka bi shi. 30Suka kuma ga makafi biyu zaune a bakin hanya. Da makafin suka ji cewa Yesu ne ke wucewa, sai suka tada murya suna cewa, "Ya Ubangiji, Dan Dauda, kayi mana jinkai." 31Amma jama'ar suka tsauta masu, suka ce suyi shiru. Duk da haka, makafin suka kara tada murya fiye da na da, suka ce, "Ya Ubangiji, Dan Dauda, kayi mana jinkai."32Sai Yesu ya tsaya cik, ya sa aka kira su, sai ya ce masu, "Me kuke so in yi maku?" 33Sai suka ce masa, Ya Ubangiji, muna so mu sami ganin gari." 34Sai Yesu yayi juyayi a cikin sa, ya taba idanunsu. Nan da nan, suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.
Yesu ya ba da misalin wani mai gona da ya ɗauki ma'aikata. Ya yi haka ne don ya ƙwatanta yadda Allah za sãka wa waɗanda suke 'yan mulkin sama.
Wannan itace farkon misalin. Duba yadda aka juya gabatarwar misalin a [13:24]
"Bayan da mai gonar ya yarda"
Kuɗin aikin kowane yini kenan a wancan lokacin. AT: "kuɗin yini ɗaya"
"sai ya aike su gonarsa su yi aiki"
"Mai gonar ya sãke fita"
Sa'a ta ukun shi ne misalin ƙarfe tara na safe.
"suna tsaye a bakin kasuwa ba su yin aikin kome" ko kuma "suna tsaye a bakin kasuwa ba aikin yi"
"wata babbar wuri ne, a tsarari kuma da mutane suna siya da sayar da abinci da sauran abubuwa.
"Sai mai gonar ya sake fita"
sa'a ta shida shi ne misalin tsakar rana. Sa'a ta tara shi ne misalin ƙarfe uku na rana.
Wato mai gonar ya sake zuwa bakin kasuwa ya ɗauke ma'aikata.
Wato a misalin ƙarfe biyar na yamma.
"ba su aikin kome" ko kuma "ba su da aiki"
Kuna iya kara hasken abinda ake nufi. AT: "fara da ma'ikatan da suka fara aiki a baya, sa'annan ma'aikatan da suka fara da ɗan lokaci, sai kuma a ƙarshe ma'aikatan da sun fara aiki tun farko" ko kuma "fara biyan ma'aikatan da na ɗauka a ƙarshe, sa'annan waɗanda na ɗauka a tsakar rana, sai kuma a ƙarshe na biya waɗanda na ɗauka da farko"
AT: "waɗanda mai gonar ya ɗake su aiki"
"Da ma'aikatan da suka yi aiki na tsawon lokaci mafi yawa suka karɓi"
"mai gonar innabi"
"ka biya su daidai kimanin kuɗin da ka biya mu"
Jimlar nan "fama cikin zafin rana" karin magana ne da ke nufin "aiki dukkan yini." AT: "mu da muka yi aiki dukkan yini, a lokaci mafi zafi ma"
"ɗaya daga cikin ma'aikatan da suka yi aiki na lokaci mafi yawa"
Ku yi amfani da kalmar da mutum zai yi amfani da shi idan yana magana da mutum da yake tsauta masa a hankali.
Mai gonar yana amfani ne da wannan tambayan don ya tsauta wa ma'aikatan da suna gunaguni. AT: "Ai mun riga mun shirya cewa zan biya ku dinari ɗaya ba."
Mai gonar yana amfani ne da wannan tambayan ya daidaita ma'aikatan da ke gunaguni. AT: "Ai zan iya yin duk abinda na ke so da mallaka ta"
Mai gonar yana amfani ne da wannan tambayan do ya tsauta wa ma'aikatan da suke gunaguni. AT: "Kada ku yi kishi sa'adda nake yin halin kirki ga sauran mutane."
A nan "farko" na nufin "ƙarshe" na nufin matsayin mutane ko kuma "muhimmanci. Yesu yana banbanta matsayin mutane a yanzu da kuma matsayin su a mulkin sama. Duba yadda kuka juya irin wannan jimlar a [19:30]. AT" Don haka, waɗanda suna kamar mara muhimmanci yanzu za su zama mafi muhimmanci, kuma waɗanda suke kamaar su ne mafi muhimmanci yanzu za su zama da kalilar muhimmanci"
Misalin ya kare a nan, Yesu kuma yana kan magana. AT: "Sai Yesu ya ce, 'haka yake, na ƙarshe za su zama na farko.'"
Urushalima yana bisa duwatsu ne, don haka mutane sukan haurowa sama ne zuwa wurin.
Yesu yana amfani ne da kalmar nan "Ku duba" don ya ce wa almajiransa, lallai ne su sa hankalinsu ga abinda zai faɗa masu.
A nan "mu" na nufin Yesu da almajiransa.
AT: "wani zai bada Ɗan mutum"
Yesu yana maganar kansa ne kamar wani mai saurara na uku ne. In ya zama lallai, kuna iya juya waɗannan zuwa mutum na fari.
"Babban firist ɗin da shugabannin shari'a za su yanke masa hukunci su bada shi ga al'ummai, sa'annan al'umman kuma za su ya wa Yesu ba'a.
"su zane shi" ko kuma "su yi masa duka da bulala"
"uku" na daidai bisa jerin kirge ne.
Kalmomin nan "a ta da shi" karin magana ne da ke nufin "zai rayu kuma." AT: "Allah za ta da shi" ko kuma "Allah zai ba shi rai kuma"
Wato Yakubu da Yahaya kenan.
Wato a matsayi mai girma, iƙo, da kuma daraja.
A nan "mulki" na nufin sarautar Yesu a matsaying sarki. AT: "yayin da kake sarki"
A nan "ku" na nufin uwar da 'ya'yan.
A nan "ku" na nufin 'ya'ya biyun. Kuma a yanzu dai Yesu yana magana da 'ya'ya biyun ne kawai.
A "sha kokon" ko kuma "sha daga kokon" karin magana ne da ke nufin a ɗanɗana azaba" AT: "sha azaban da zan sha"
"'Sai ya'yan Zabadi suka ce masa" ko kuma "Yakubu da Yahaya suka ce masa"
A "sha kokon" ko kuma "sha daga kokon" karin magana ne da ke nufin a ɗanɗana azaba." AT: "Lallai fa za ka sha azaba kamar yadda zan sha azaba"
Wato a matsayi mai girma, iƙo, da kuma daraja. Duba yadda kuka juya wannan a [20:21]
AT: "Ubana ne ya shirya waɗannan wuraren, kuma shi ne za ba wa duk waɗanda ya zaɓa"
Wannan wata lakani ce mai muhimmanci da ke bayyana ɗangartakar da ke tsakanin Allah da Yesu.
"suka ji abinda Yakubu da Yahaya suke tambayan Yesu"
Idan ya zama lallai, kuna iya kara bayanin dalilin bacin rai na almajirai goma. AT: "suna bacin rai da 'yan'uwan nan biyu domin kowannensu ma na son su zauna a wuri mai dararja kusa da Yesu"
"ya kira almajirai sha biyun"
"sarakunan al'ummai suna mulki a bisa mutanensu da ƙarfi"
"manyan gari a cikin al'ummai"
"suna mulkin mutanen"
"duk mai so" ko kuma "duk wanda ke marmari"
"yă zama farko"
Yesu yana maganar kansa ne kamar da wani na uku yake yi. Idan ya zama lallai, kuna iya juya wannan zuwa mutum na farko
AT: "bai zo don sauran mutane su bauta masa ba" ko kuma "ban zo don sauran mutane su bauta mini ba"
Kuna iya karin bayyanin abinda aka fahimta da wannan maganan. AT: "amma ya bauta wa mutane"
Ran Yesu "domin mutane" karin magana ne da ke nufin hukuncinsa don ya ceci mutane daga hukuncin zunubansu. AT: "ya ba da ransa a maimakon na mutane" ko kuma "ya da da ransa domin ya ceci mutane masu yawa"
Mutum yă ba da ransa karin magana ne da ke nufin mutum yă zaba ya mutu, sau da dama ana haka ne domin a ceci mutane. AT: "ya mutu"
...
Wato almajiran da Yesu kenan.
"suka bi Yesu"
Akan iya juya wannan zuwa "Sai, da wasu makafai biyu a zaune." Matta na jan hankalin mu ne zuwa ga sabobin mutane a labarin. Mai yiwuwa harshen ku na da wata hanya ta musamman na yin haka.
"Da suka ji"
"ke wuce kusa da su"
Yesu ba ɗan Dauda bisa ga jiki ba ne, don haka, anan iya juya wannan zuwa "Ɗan zuriyar Sarki Dauda." Ko da shike, "Ɗan Dauda" ma wata lakaɓi ce da Almasihu, kuma mai yiwuwa mutanen suna kiran shi ne da wannan lakaɓin.
"aka kira makafin"
...
Saboda tambayan da Yesu ya yi dama, muna fahimtar cewa suna furta abinda suke so ne. AT: "muna so ka buɗe idanun mu" ko kuma "muna so mu iya gani"
"cike da tausayi" ko kuma "ya ji tausayinsu"
1Yayinda Yesu da almajiransa suka kusato Urushalima sai suka zo Betafaji wajen dutsen zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa guda biyu, 2yace masu, "Ku shiga kauyen da yake gaban ku zaku iske wata jaka da aholaki tara da ita. Ku kwance su ku kawo mani su. 3Idan wani ya gaya maku wani abu game da haka, sai ku ce, 'Ubangiji ne yake bukatarsu,' mutumin kuwa zai aiko ku da su nan da nan."4Anyi wannan kuwa domin a cika annabcin anabin. Yace, 5"Ku cewa diyar Sihiyona, duba, ga sarkinki na zuwa wurin ki, mai tawali'u ne, kuma akan jaki wanda aholaki ne."6Sai almajiran suka tafi suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su. 7Suka kawo jakar da dan aholakin, suka sa tufafinsu akai, Yesu kuwa ya zauna akan tufafin. 8Yawancin jama'a kuwa suka baza tufafinsu akan hanya, wasu kuma suka yanko ganye daga bishiyoyi suka shimfida su a hanya.9Taron jama'a da suke gabansa da wadanda suke bayansa, suka ta da murya suna cewa, "Hossana ga dan Dauda! mai albarka ne shi wanda ke zuwa cikin sunan Ubangiji. Hossana ga Ubangiji!" 10Sa'adda Yesu ya shiga Urushalima sai doki ya cika birnin ana cewa, "Wanene wannan?" 11Sai jama'a suka amsa, "Wannan shine Yesu annabi, daga Nazaret ta Galili."12Sai Yesu ya shiga haikalin. Ya kori duk wadanda ke saye da sayarwa a cikin ikiilisiya. Ya birkice teburan masu canjin kudi da kujerun masu sayar da tantabaru. 13Ya ce masu, "A rubuce yake, 'Za a kira gidana gidan addu'a,' amma kun mayar dashi kogon 'yan fashi." 14Sai makafi da guragu suka zo wurin sa a haikalin, ya warkar da su.15Amma da manyan firistoci da malaman attaura suka ga abubuwan banmamaki da yayi, kuma sa'adda suka ji yara suna tada murya a cikin haikalin suna cewa, "Hossana ga dan Dauda," sai suka ji haushi. 16Suka ce masa, kana jin abinda wadannan mutanen ke fadi?" Yesu ya ce masu, "I! Amma ba ku taba karantawa ba, 'daga bakin jarirai da masu shan mama ka sa yabo'?" 17Sai Yesu ya bar su, ya fice daga birnin zuwa Betaniya ya kwana a wurin.18Washegari da safe yayin da yake komawa birnin, sai yaji yunwa. 19Da ya ga bishiyar baure a bakin hanya, sai yaje wurin amma bai sami kome ba sai dai ganye. Sai ya ce mata, "Kada ki kara yin 'ya'ya har abada." Sai nan take bishiyar bauren ta bushe.20Da almajiran suka ga haka, sai suka yi mamaki suka ce, "Kaka bishiyar bauren ta bushe nan da nan?" 21Yesu ya amsa yace masu, "Hakika ina ce maku, in dai kuna da bangaskiya ba ku yi shakka ba, ba abinda aka yi wa bauren nan kadai za kuyi ba har ma za ku cewa tsaunin nan, "Ka ciru ka fada teku,' sai kuwa haka ta kasance. 22Kome kuka roka cikin addu'a, in dai kun gaskanta, za ku samu."23Sa'adda Yesu ya shiga haikalin, sai manyan fristocin da shugabannin jama'a suka zo suka same shi yayin da yake koyarwa, suka ce, "Da wane iko kake yin wadannan abubuwa?" 24Yesu ya amsa yace masu, "Ni ma zan yi maku tambaya daya. In kun fada mani, ni ma zan fada maku ko da wane iko nake yin wadannan abubuwa.25Daga ina baftismar Yahaya ta fito, daga sama ko kuma daga mutune?" Sai suka yi shawara a tsakanin su, suka ce, "In munce, 'daga sama,' zai ce mana, 'don me bamu gaskanta dashi ba?' 26Amma in munce, ' daga mutune,' muna tsoron jama'a, saboda sun san Yahaya annabi ne." 27Sai suka amsa ma Yesu suka ce, "Bamu sani ba." Shi ma yace masu, "Nima bazan gaya maku ko da wane iko nake yin abubuwan nan ba.28Amma me kuke tunani? Wani mutum yana da 'ya'ya biyu. Ya je wurin na farkon yace, 'Da, je ka kayi aiki yau a cikin gona.' 29Yaron ya amsa yace, 'bazan yi ba,' amma daga baya ya canza tunaninsa ya tafi. 30Sai mutumin ya je wurin da na biyun ya fada masa abu guda. Wannan dan ya amsa ya ce, 'zanje, baba,' amma bai je ba.31Wanene a cikin 'ya'ya biyun nan yayi nufin ubansa?" Suka ce, "na farkon." Yesu ya ce masu, "Hakika ina gaya maku, masu karbar haraji da karuwai za su shiga mulkin Allah kafin ku. 32Gama Yahaya ya zo maku a hanyar adalci, amma ba ku gaskata da shi ba, a yayinda masu karbar haraji da karuwai suka gaskata da shi. Ku kuwa, bayan kun ga abin da ya faru, baku ma tuba daga baya ba don ku gaskata da shi.33Ku saurari wani misalin. Anyi wani mutum, mai gona. Yayi shuka a gonar, ya shinge ta, ya gina ramin matse inabi a cikin gonar, ya kuma gina wata hasumiyar tsaro, sai ya bada hayar gonar ga wadansu manoma. Sai ya tafi wata kasa. 34Da kakar inabi ta yi, sai ya aiki wadansu bayi su karbo masa amfanin gonar.35Amma manoman suka kama bayin, suka doddoki dayan, suka kashe dayan, suka jejjefe dayan da duwatsu. 36Sai mai gonar ya sake aika wadansu bayinsa da suka fi na farko, amma manoman suka yi masu kamar yadda suka yi wa sauran. 37Bayan wannnan, sai mai gonar ya aika da dansa wurin su yana cewa, 'za su yi wa dana biyayya.'38Amma da manoman suka ga dan, sai suka ce a tsakanin su, 'wannan shine magajin. Kuzo, mu kashe shi mu gaji gonar.' 39Sai suka dauke shi, suka jefar da shi daga cikin gonar, suka kashe shi.40To idan me gonar ya zo, me zai yiwa manoman? 41Suka ce masa, "Zai hallaka mugayen manoman nan ta hanya mai tsanani, zai kuma bada gonar haya ga wadansu manoman, mutanen da za su biya, lokacin da inabin ya nuna."42Yesu yace masu, "Baku taba karantawa a nassi ba," 'Dutsen da magina suka ki ya zama dutse mafi amfani. Wannan daga Ubangijine, kuma abin mamaki ne a idanunmu?'43Saboda haka ina gaya maku, za a karbe mulkin Allah daga wurin ku a ba wata al'umma da zata bada amfaninsa. 44Duk wanda ya fadi akan dutsen nan zai ragargaje. Amma duk wanda dutsen ya fadawa, zai nike."45Da manyan firistocin da farisawan suka ji wannan misalin, sai suka gane da su yake. 46Da suka nemi kama shi, sai suka ji tsoron taron, saboda mutanen sun dauke shi annabi.
Wannan ne mafarar labarin shigar Yesu a Urushalima. Anan ya ba wa almajiransa umurni game da abin da za su yi.
Wannan kawye ne da ke kusa da Urushalima.
AT: "jakin da wani ya ɗaura"
Za ku iya bayyana yadda an ɗaura jakin. AT: "a ɗaure a wurin, a kan itace"
ƙaramin jaki
A nan, marubucin ya faɗi abin da annabi Zechariah ya ce domin ya nuna cewa Yesu ya cika annabcin ta wurin hawan jaki zuwa Urushalima.
An yi amfani da wannan kalma anan domin a sa alama a ainahin labarin. Matthew ya bayyana yadda ayukan Yesu ya cika nassi.
AT: "wannan ya faru ne domin Yesu ya cika abin da Allah ya faɗa ta wurin annabi tun da daddewa"
Akwai annabawa dayawa. Matthew ya na maganar Zechariah ne. AT: "annabi Zechariah"
"diyar" garin na nufin mutanen garin. AT: "mutanen Sihiyona" ko "mutanen da su na zama a Sihiyona"
Wannan wani suna ne na Urushalima.
Jumlar "akan jaki, duƙushin jaki" na bayyana cewa jakin ƙaramin dabba ne. AT: "a kan ƙaramin jaki"
waɗannan tufa ne na waje.
Waɗannan hanyoyi ne na nuna girma ga Yesu sa'ad da ya na shigan Urushalima.
Wannan kalma na nufin "cece mu," amma ya na iya nufin "yabi Allah!"
Yesu ba ainahin ɗan Dauda ba ne, za a iya juya wannan kamar "ɗan zuriyar sarki Dauda." Ko da shike, "Ɗan Dauda" laƙani ne wa Mai ceto, mai yiwuwa taron su na kiran Yesu da wannan laƙanin.
A nan "a cikin sunan" na nufin "cikin iko" ko "kamar wakili." AT: "a cikin ikon Ubangiji" ko "kamar wakilin Ubangiji"
A nan "ma ɗaukaki" ya na nufin Allah da ke mulki daga sararin sama. AT: "Yabi Allah, wanda ya na cikin sama" ko "Yabo ga Allah"
A nan "garin" ya na nufin mutanen da suke zama a wurin. AT: "mutane dayawa daga garin sun yi ɗoki"
"murna"
Yesu bai shiga ainahin haikalin ba. Ya shiga ta fãdar haikalin.
Attajirai su na saya da sayar da dabbobi da waɗansu abubuwa da masu tafiye-tafiye sun saya don su mika hadaya da ta dace a haikalin.
"Yesu ya ce wa waɗanda su ke canza ƙudi da saya da sayar da abubuwa"
AT: "Annabawa sun rubuto tun da daddewa" ko "Allah ya faɗa da daddewa"
AT: "Gida na zai zama"
A nan "Na" ya na nufin Allah kuma "gida" na nufin haikali.
Wannan karin magana ne. AT: "wurin da mutane na addu'a"
Yesu ya yi amfani da ƙarin magana don ya tsawta wa mutanen don saya da sayar da abubuwa a cikin halkalin. AT: "kamar wurin da masu fashi suke ɓoye"
AT: "waɗanda su makafai ne da kuma waɗanda su guragu ne"
waɗanda su ke da ciwon ƙafa ko ƙafan da na sa tafiyawa wahala
"abubuwan banmamaki" ko "abin al'ajibi." Wannan ya na nufin warkaswa da Yesu ya yi wa makafi da guragu a cikin 21:14.
Ya na nufin cewa sun yi fushi domin ba su gaskanta cewa Yesu ne Almasihu ba kuma ba su son sauran mutanen su yabe shi. AT: "sun ji fushi sosai domin mutane su na yabon shi"
Manyan firistoci da malaman attaura suka yi wannan tambaya don su ƙwabe Yesu domin su na fushi da shi. AT: "Kada ka bar su sa faɗa waɗannan abubuwa game da kai!"
Yesu ya yi wannan tambaya domin ya tuna wa manyan firistoci da malaman attaura da abin da sun karanta a cikin nassi. AT: "I, Na ji su, amma ku tuna da abin da kun karanto a cikin nassi ... yabo."
Jumlar "daga bakin" na nufin magana. AT: "Ka sa ƙanannan 'ya'ya da masu shan mama su shirya don su yabi Allah"
" Yesu ya bar manyan firistoci da malaman attaura"
ya mutu ya kuma bushe
Almajiran su yi amfani da tambaya domin su nanata yadda suke mamaki. AT: "Mu na mamaki cewa bishiyar bauren ta bushe da sauri!"
"ya bushe ya kuma mutu"
"Ina gaya maku gaskiya." Wannan jimlar ya kara nanaci a abin da Yesu zai faɗa.
Yesu ya bayyana maganan don ya nanata cewa dole ne wannan bangaskiya ya zama na gaske. AT: "in kun gaskanta da gaskiya"
Za ku iya juya wannan magana kai tsaye. AT: "za ku iya ce wa wannan tsaunin nan ya tashi, ya jafa kansa a cikin teku"
AT: "zai faru"
Ya na nufin cewa Yesu bai shiga ainahin haikalin ba. Ya shiga fada a ta haikalin.
Wannan na nufin koyarswa da warkaswarYesu a cikin haikali. Mai yiwuwa ya na kuma nufin kora da Yesu ya yi wa masu saya da sayad a ranar da ta wuce.
"daga ina ne ya sami ikon yin wannan?
Wannan na da magana a cikin magana. za ku iya juya maganan. AT: "In mun ce mun gaskanta cewa yahaya ya karba ikonsa daga sama, Yesu zai tambaye dalilin da ba mu gaskanta da yahaya ba."
A nan "sama" na nufin Allah. AT: "daga Allah a sama"
Shugabanin addinai sun san cewa Yesu zai iya tsawta masu da wannan tambaya. AT: "Da kun gaskanta da Yahaya mai Baftisma"
Wannan magana ne cikin magana. Za ku iya juya maganan kai tsaye. AT: "Amma in mun faɗa cewa mun gaskanta Yahaya ya karba ikonsa daga mutane"
"muna tsoron abin da taron za su yi tunani ko su yi mana"
"sun gaskanta cewa Yahaya annabi ne"
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya tsokane shugabanin adini don su yi tunani da zurfi game da misalin da zai gaya masu. AT: "Faɗa mani game da abin da ku ke tunani a abin da zan gaya maku."
Wannan na nufin ɗan da ya sake duba tunaninsa ya kuma so ya aikata dabam daga yadda ya ce zai yi.
"Shugaban firistoci da dattawa su ka ce"
"Yesu ya ce wa shugaban firistoci da dattawa"
A nan "mulkin Allah" na nufin mulkin Allah kamar sarki. AT: "a loƙacin da Allah zai kafa mulkinsa a duniya, zai yarda ya albarkace masu karban haraji da karuwai ta wurin yin mulki da su kafin ya yarda ya yi maku wannan"
AT: 1) Allah zai karɓi masu karban haraji da karuwai ba da daddewa ba fiye da yadda zai karbi shugabanin Yahudawa, ko 2) Allah zai karbi masu karban haraji da karuwai a maimakon shugabanin addin yahudawa.
A nan "ku" ɗaya ne kuma ya na nufin dukka mutanen isra'ila ba shugabanin Yahudawa kadai ba. AT: "Yahaya ya zo wa mutanen isra'ila"
Wannan karin magana ne da na nufin cewa Yahaya ya nuna wa mutanen hanyar gaskiya da za su yi rayuwa. AT: "ya kuma gaya ma ku yadda Allah ya na so ku yi rayuwa"
A nan " ku" ɗaya ne kuma ya na nufin shugabanin Yahudawa.
"mutum da ke da dan dukiya"
"danga"
"gina rami a cikin gonan don matse inabi"
Mai shi ne ya ke da gonan, amma ya bar manoman su kula da shi. A loƙacin da inabin sun yi, za su ba wa mai shi sai su ajiye sauran.
Waɗannan mutane ne da sun san yadda ana kula da gona da kuma inabi.
"bayin mai gonan"
Matiyu bai bayyana wanda ya amsa Yesu ba. Idan ku na so ku ba da takamaiman mai sauraro, za ku iya juya ta kamar "Mutanen sun ce wa Yesu."
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya sa masu sauraransa su yi tunani da zurfi game da abin da wannan nassin na nufi. AT: "Yi tunanin abin da kun karanta ... idanu.?
Yesu ya na faɗa daga cikin zabura. Wannan magana ne da na nufin shugabanin Yahudawa, kamar masu gini, za su ki Yesu, amma Allah zai sa shi mafi muhimminci a cikin mulkinsa, kamar dutse mafi amfani a cikin gini.
AT: "ya zama dutse mafi amfani"
"Ubangiji ya sa wannan babban canji"
A nan "a idanunmu" na nufin gani. AT: "abin al'ajibi ne a gani"
Wannan na kara nanaci akan abin da Yesu zai ce.
A nan "ku" ɗaya ne. Yesu ya na magana da shugabanin addini da kuma mutanen Yahudawa ne a takaice.
A nan "mulkin Allah" ya na nufin mulkin Allah kamar sarki. AT: "Allah zai karbi mulkinsa daga wurin ku ya kuma ba wata al'umma" ko "Allah zai ki ku, Mutanen Yahudawa, kuma zai zama sarki ga mutane daga wasu al'ummai"
Ba bu wanda ya tabatar ko Yesu ya na nufin cewa Allah zai ba da mulkin wata rana ko kuwa ba zai ba da shi ba. Juyawarku ya ba da fahimta mai yiwuwa.
"amfanin" a nan magana ne na "sakamako." AT: "da na ba da sakamako masu kyau"
A nan, "wannan dutse" ɗaya ne a cikin 21:42. Wannan magana ne da na nufin cewa Almasihu zai hallakar da duk wanda ya yi masa tawaye. AT: "Dutsen zai ragargaje duk wanda ya faɗi akai"
A takaice wannan ya na nufin abu ɗaya ne a jumla da ta wuce. Magana ne da ya na nufin cewa Almasihu zai yi hukunci na ƙarshe kuma zai hallakar da duk wanda ya yi masa tawaye.
"misalan Yesu"
1Yesu ya sake yi masu magana da misalai, yace, 2"Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya wa dansa liyafar aure. 3Ya aiki bayinsa su kira wadanda aka gayyata su zo liyafar auren, amma suka ki zuwa.4Sai sarkin ya sake aiken wasu bayin, yace, "Ku gaya wa wadanda aka gayyata, "Duba, na shirya liyafata. An yanka bajimaina da kosassun 'yanmarukana, an gama shirya komai. Ku zo wurin bikin auren."5Amma mutanen ba su dauki sakon da mahimmanci ba kuma suka yi tafiyarsu. Wani ga gonarsa, wani ga kasuwancinsa. 6Sauran kuma suka kama bayin sarkin, suka wulakanta su, suka kuma kashe su. 7Amma sarkin ya ji haushi. Ya aika sojojinsa, ku kashe masu kisan kan nan, ku kuma kone birnin su.8Sai ya ce wa bayinsa, 'An gama shirya bikin, amma wadanda aka gayyata ba su cancanta ba. 9Saboda haka ku je bakin hanya ku gayyaci iyakar yawan mutanen da za ku samu zuwa bukin auren.' 10Bayin suka tafi hanya suka tattaro dukan mutanen da suka samu, da masu kyau da marassa kyau. Zauren auren kuwa ya cika makil da baki.11Amma da sarkin ya zo don ya ga bakin, sai ya ga wani wanda bai sa kayan aure ba. 12Sai sarkin ya ce masa, 'Aboki, ta yaya ka shigo nan ba tare da kayan aure ba?' Mutumin kuwa ya rasa ta cewa.13Sai sarkin ya ce wa bayinsa, 'Ku daure mutumin nan hannu da kafa, ku jefa shi cikin duhun, inda za ayi kuka da cizon hakora.' 14Gama mutane dayawa aka kira, amma kadan aka zaba."'15Sai Farisawan suka tafi suka shirya makirci akan yadda zasu kama shi ta maganarsa. 16Suka tura masa almajiransu, da Hirudiyawa. Suka ce ma Yesu, "Mallam, mun san kai mai gaskiya ne, kuma kana koyar da hanyar Ubangiji da gaskiya. Ba ka damu da ra'ayin kowa ba, kuma ba ka nuna bambanci a tsakanin mutane. 17To gaya mana, menene tunaninka? Ya halarta a biya haraji ga Kaisar ko a'a?"18Amma Yesu ya gane muguntarsu yace, "Don me kuke gwada ni, ku munafukai? 19Ku nuna mani sulen harajin." Sai suka kawo masa sulen.20Yesu yace masu, "Hoto da sunan wanene wadannan?" 21Suka ce masa, "Na Kaisar." Sai Yesu ya ce masu, "To ku ba Kaisar abubuwan dake na Kaisar, Allah kuma abubuwan dake na Allah." 22Da suka ji haka, suka yi mamaki. Sai suka bar shi suka tafi.23A ran nan sai wadansu Sadukiyawa, wadanda suka ce ba tashin matattu, suka zo wurinsa. Suka tambaye shi, 24cewa, "Mallam, Musa yace, 'Idan mutum ya mutu, bashi da 'ya'ya, dole dan'uwansa ya auri matarsa ya kuwa haifawa dan'uwansa 'ya'ya.25Akwai wasu 'yan'uwa bakwai. Na farkon yayi aure sai ya mutu. Da shike bai bar 'ya'ya ba. Ya bar wa dan'uwansa matarsa. 26Sai dan'uwansa na biyu shi ma yayi haka, haka kuma na ukun, har zuwa dan'uwan na bakwai. 27Bayan dukansu, sai matar ta mutu. 28To a tashin matattu, matar wa zata zama a cikin su bakwai din? Don duk sun aure ta."29Amma Yesu ya amsa yace masu, "Kun bata, domin ba ku san litattafai ko ikon Allah ba. 30Domin a tashin matattu basu aure, ba kuma a bada su aure. Maimaikon haka, suna kama da mala'ikun sama.31Amma game da tashin matattu, ba ku karanta abinda Allah ya fada maku ba, cewa, 32'Nine Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu'? Allah ba Allah na matattu bane, amma na rayayyu." 33Da taron suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.34Amma da Farisawan suka ji cewa Yesu ya kure Sadukiyawa, sai suka tattara kansu. 35Daya daga cikinsu, masanin shari'a, yayi masa tambaya, yana gwada shi- 36"Mallam, wace doka ce mafi girma a cikin shari'a?"37Yesu yace masa, "Ka kaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka.' 38Wannan itace babbar doka ta farko.39Doka ta biyu kuma kamar ta take- 'Ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.' 40Akan wadannan dokoki ne dukkan shari'a da annabawa suka rataya."41Yayin da Farisawa suke tattare wuri daya, Yesu yayi masu tambaya. 42Yace, "Me kuke tunani game da Almasihu? Shi dan wanene?" Suka ce masa, "Dan Dauda ne."43Yesu yace masu, "To ta yaya kuma Dauda cikin Ruhu ya kira shi Ubangiji, yana cewa, 44"Ubangiji ya cewa wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na mai da makiyanka matakin sawayenka."45Idan Dauda ya kira Almasihu 'Ubangiji,' ta yaya ya zama dan Dauda?" 46Ba wanda ya iya bashi amsa, ba kuma wanda ya kara yi masa tambayoyi tun daga wannan rana.
Yesu ya ba da labari game da bikin auren, don ya tsawata shugabanin addini da kuma nuna rashin gaskantawarsu.
"wa mutanen"
Wannan ne farkon labari. dubi yadda kun juya wannan a cikin 13:24.
AT: "mutanen da sarkin ya gayyato"
Ana iya bayyana wannan magana kai tsaye. AT: "bayin, umurta su su gaya wa waɗanda ya gayyato"
"Duba" ko "ji" ko" saurara abin da zan gaya ma ku"
Ya na nufin cewa an dafa dabbobin kuma su na nan a shirye don ci. AT: "Bayi na sun kashe sun kuma dafa bajimaina da kosassun 'yanmarukana"
"Bajimaina mafi kyau da kosassun 'yanmarukana don ci"
"Amma waɗannan baƙi da sarkin ya gayyata sun ki gayyatan"
Ya na nufin cewa sojojin sarkin sun ƙashe masu kisa.
AT: "waɗanda na gayyato"
"inda ainahin hanyoyin haye suke." Sarkin ya na aikan bayin zuwa wurin da za a iya samin mutane.
"mutane masu kyau da marassa kyau"
AT: "Bakin sun cika da zauren auren"
babban ɗaki
Sarkin ya yi amfani da wannan tambaya domin ya tsawata bakon? AT: "ba ka sa kayan da ta dace da aure ba. Bai kamata ka na nan ba."
"mutumin ya yi shiru"
"ɗaure shi don kada ya iya motsa hannunsa ko kafa"
A nan "cikin duhu" magana ne na wurin da Allah na tura waɗanda sun ki su. Wannan wuri ne da an ƙebe daga Allah har abada. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 8:12. AT: "duhun wuri da nisa daga Allah"
"cizon hakora" alama ne na yin abu, da na wakilcin bakin ciki mai tsanani da wahala. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 8:12. AT: "kuka da bayyana wahala mai tsanani"
AT: "Gama Allah ya gayyace mutane dayawa, amma ya zabi kadan"
Wannan ya nuna wucewa. Yesu ya kalmasa labarin zai kuma bayyana ma'anar labarin yanzu.
"yadda za su sa Yesu ya faɗa wani abin da ba daidai ba don su iya kama shi"
Almajiran Farisawa sun amince da biyan haraji ga shugabanin Yahudawa. Hirudiyawan sun amince da biyan haraji ga shugabanin Romawa. Ana nufin cewa Farisawa sun yarda cewa duk abin da Yesu ya ce, zai saba wa ɗaya daga cikin taron.
Waɗannan ma'aikata ne da masu bin sarki Hiradus na Yahudawa. Shi abuta ne da shugabanin Romawa.
"ba ka nuna bambancin girma ga kowa" ko "ba ku ɗaukan wani da mafi muhimminci fiye da wani dabam ba"
Mutane ba su biyan haraji kai tsaye wa kaisar ba amma ga wani mai karɓan harajinsa. AT: "a biya harajin da Kaisar ya umurta"
Yesu ya yi amfani da wannan tambaya domin ya tsawata waɗanda su na son su kama shi. AT: "Kada ku gwada ni, ku munafukai? ko "Na san cewa ku munafukai ku na so ku gwada ni ne!"
Wannan sulen Romawa ne da ya kai ƙudin aikin rana ɗaya.
Yesu ya yi amfani da wannan tambaya domin ya sa mutanen su yi tunani sosai game da abin da ya na faɗa. AT: "Faɗa mani hoto da sunan wanene ku ke gani a kan wannan sulen."
Za ku iya bayyana bayanin da an fahimta a cikin amsansu. AT: "Sulen na da hoto da sunar Kaisar a kai"
"abubuwan dake na Kaisar"
"abubuwan dake na Allah"
Shugabanin addini su na tambayan Yesu game da abin da Musa ya rubuto a cikin nissi. Idan harshenku bai yarda da magana a cikin magana ba, za a iya bayyana maganan kai tsaye. AT: "Mallam, Musa ya faɗa cewa idan mutum ya mutu"
Anan "sa" ya na nufin mutumin da ya mutu.
"Babban ... mai bin babban ... ɗayan babbab ... ƙaramin" ko "Babban ... babban ƙaramin ɗan'uwansa ... wannan babban ƙaramin ɗan'uwan ... ƙaramin"
"Bayan kowane ɗan'uwa ya mutu"
A nan Saducees sun matsa daga labari game da 'yan'uwa bakwai zuwa ainahin tambayansu.
"lokacin da matattu za su rayu kuma"
Ana nufin cewa Yesu ya na nufin sun bata da abin da su ke tunani game da tashin matattu. AT: "kun bata da tashin matattu"
"abin da Allah na iya yi"
"mutane ba za su yi aure ba"
AT: "mutane ba za su kuma ba da 'ya'yansu a aure ba"
A cikin 22:32, Yesu ya faɗa daga Fitowa don ya nuna cewa mutane na rayuwa kuma bayan mutuwa.
Yesu ya yi wannan tambaya domin ya tuna wa shugabanin addini game da abin da sun sani daga nassi. AT: "Na san cewa kun karanta, amma ba ku fahimci abin da ... Yakubu."
AT: "abinda Allah ya faɗa maku"
Za ku iya juya wannan magana kai tsaye. AT: "Allah, wanda ya ce wa Musa cewa shi ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu."
AT: "na matattun mutane, amma shi Allah na rayayyun mutane"
"gwani a shari'a." Wannan ba-Farasi ne da ke da fasahar shari'ar Musa.
An yi amfani da waɗannan jimloli biyu don a nuna "cikakke" ko "mai himma." A nan "zuciya" da "rai" magana ne na cikin mutum.
A nan "babban" da "farko" na nufin abu ɗaya. Su na nanata cewa wannan ne doka mafi muhimminci.
AT: 1) "akwai wani doka dake biye a muhimminci" ko 2) "akwai doka ta biyu da ke da muhimminci." haka kuma, Yesu ya na nufin waɗannan dokoki biyu su na da muhimminci fiye da dukka sauran dokoki.
Wannan ya na nufin kamar doka a cikin 22:37.
A nan "makwabcinka" ya na nufin fiye da waɗanda su ke zama kusa. Yesu ya na nufin dole ne mutum ya kaunace dukka mutane.
A nan jumlar "dukkan shari'a da annabawa" na nufin dukka nassi. AT: "Komai da Musa da annabawan sun rubuto a cikin nissi su na bisa waɗannan dokoki biyu"
A cikin waɗannan "ɗan" ya na nufin "zuriya."
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya sa shugabanin addini su yi zurfin tunani game da zabura da ya na sa ya faɗa. AT: "To, faɗa mani dalilin da Dauda a cikin Ruhu ya kira shi Ubangiji"
"Dauda, wanda Ruhu mai Tsarki ke ƙarfafa." Wannan na nufin Ruhu mai Tsarki ne na albarkaci abin da Dauda na faɗa.
A nan "shi" ya na nufin Almasihu, wanda shi ma zuriyar Dauda ce.
A nan "Ubangiji" ya na nufin Allah Uba.
A nan "Ubangiji" ya na nufin Almasihu. Kuma, "na" ya na nufin Dauda. Wannan Almasihun ya fi Dauda.
Zauna a "hannun damanan Allah" alama ne na karban babban ɗaukaka da iko daga Allah. AT: " zauna a wurin girma a gefena"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "sai na ci nasara da makiyanka" ko "sai na sa makiyanka su durkusa a gaban ka"
Yesu ya yi amfani da tambaya don ya sa shugabanin addini su yi zurfin tunani game da abin da ya na faɗa. AT: "Dauda ya na kiransa 'Almasihu,' don haka dole Almasihu zai fi zuriyar Dauda."
Dauda ya na kiran Yesu "Almasihu" domin Yesu ba zuriyan Dauda kadai ba, amma ya fi shi.
A nan "amsa" na nufin abin da mutane na na faɗa. AT: "ba shi amsan komai" ko "amsa shi"
Ana nufin cewa babu wanda ya yi masa irin tambayoyin da zai sa shi ya faɗa abin da bai dace ba don shugabanin addini su iya kama shi.
1Sai Yesu yayi wa taron da alamajiransa magana. 2Ya ce, "Marubuta da Farisawa suna zaune a mazaunin Musa. 3Don haka, duk abinda suka umarceku kuyi, kuyi wadannan abubuwa ku kuma kiyaye su. Amma kada kuyi koyi da ayyukansu, gama suna fadar abubuwa amma kuma ba su aikata su.4I, sukan daura kaya masu nauyi, masu wuyar dauka, daga nan su dauka su jibga wa mutane a kafada. Amma su kan su baza su mika danyatsa ba su dauka. 5Duk ayyukan su suna yi ne don mutane su gani, suna dinka aljihunan nassinsu da fadi, suna fadada iyakokin rigunansu.6Su na son mafifitan wuraren zama a gidan biki, da mafifitan wuraren zama a majami'u, 7da kuma gaisuwar musamman a wuraren kasuwanci, a kuma rika ce da su 'mallam.'8Amma ba sai an kira ku 'mallam, ba' domin malami daya kuke da shi, ku duka kuwa 'yan'uwan juna ne. 9Kada ku kira kowa 'Ubanku' a duniya, domin Uba daya ne ku ke da shi, kuma yana sama. 10Kada kuma a kira ku malamai, saboda malamin ku daya ne, shi ne Almasihu.11Amma wanda yake babba a cikin ku zaya zama bawanku. 12Duk wanda ya daukaka kansa za a kaskantar dashi. Duk wanda ya kaskantar da kansa kuma za a daukaka shi.13Amma kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Kun toshewa mutane kofar mulkin sama. Baku shiga ba, kuma ba ku bar wadanda suke so su sami shiga ba. 14kaiton ku marubuta da Farisawa, domin kuna hallaka gwauraya - 15Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Kuna tafiya ketaren tekuna da kasashe domin samun almajiri daya tak, in kwa kun samu kukan mai da shi biyunku danwuta.16Kaiton ku, makafin jagora, kuda kuke cewa, Kowa ya rantse da Haikali, ba komai. Amma duk wanda ya rantse da zinariyar Haikalin, rantsuwarsa ta daure shi.' 17Ku wawayen makafi! wanene yafi girma, zinariyar ko kuwa Haikalin da yake tsarkake zinariyar?18Kuma, 'Kowa ya rantse da bagadi, ba komai bane. Amma duk wanda ya rantse da baikon da aka dora a kai, sai rantsuwarsa ta kama shi.' 19Ku makafi! Wanene yafi girma, baikon ko kuwa bagadin da yake kebe baikon ga Allah?20Saboda haka, duk wanda ya rantse da bagadi, ya rantse da shi da duk abinda ke kansa. 21Kuma duk wanda ya rantse da Haikali ya rantse dashi da kuma wanda yake cikin sa. 22Kuma duk wanda ya rantse da sama, ya rantse da kursiyin Allah da kuma wanda yake zaune akai.23Kaiton ku Farisawa da marubuta, munafukai! Kukan fitar da zakkar doddoya, da karkashi, da lamsur, amma kun yar da al'amuran attaura mafi nauyi-, wato, hukunci, da jinkai da bangaskiya. Wadannan ne ya kamata kuyi, ba tare da kunyi watsi da sauran ba. 24Makafin jagora, ku kan burtsar da kwaro dan mitsil, amma kukan hadiye rakumi!25Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! kuna wanke bayan moda da kwano, amma aciki cike suke da zalunci da keta. 26Kai makahon Bafarise! Sai ka fara tsarkake cikin modar da kwanon domin bayansu ma su tsarkaka.27Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Kamar kaburburan da aka shafa wa farar kasa kuke, masu kyaun gani daga waje, daga ciki kuwa sai kasusuwan matattu da kazanta iri iri. 28Haka nan kuke a idanun mutane ku adalai ne, amma a ciki sai munafunci da mugun aiki.29Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Ku kan gina kaburburan annabawa, kuna kuma kawata kaburburan adalai. 30Kuna cewa, 'Da muna nan a zamanin Ubanninmu, da bamu basu goyon baya ba wajen zubar da jinin annabawa.' 31Domin haka kun shaida kanku ku ne 'ya'yan masu kisan annabawa.32Sai kuma kuka cika ma'aunin ubanninku! 33macizai, Ku 'ya'yan ganshekai, Yaya zaku tsere wa hukuncin Gidan wuta?34Saboda haka, duba, ina aiko maku da annabawa, da masu hikima da marubuta. Za ku kashe wadansun su kuma ku gicciye su. Zaku yiwa wasu bulala a majami'un ku, kuna bin su gari gari. 35Sakamakon hakan alhakin jinin dukkan adalai da aka zubar a duniya ya komo a kan ku, tun daga jinin Habila adali har ya zuwa na Zakariya dan Barakiya, wanda kuka kashe a tsakanin Haikali da bagadi. 36Hakika, Ina gaya maku, duk wannan zai auko wa mutanen wannan zamani.37Urushalima, Urushalima, keda kika kashe annabawa kika kuma jejjefi wadanda aka turo maki da duwatsu! Sau nawa ne naso in tattaro ki kamar yadda kaza take tattara 'yan tsakinta cikin fukafukanta, amma kin ki. 38Ga shi an bar maku gidan ku a yashe! 39Ina dai gaya maku, ba za ku kara gani na ba, sai ran da kuka ce, 'Albarka ta tabbata ga mai zuwa cikin sunan Ubangiji."'
Wannan farkon sabon sashin labarin da ta bi 25:46, inda Yesu ya koyar game da ceto da kuma hukunci na karshe. A nan ya fara da tsawata wa mutanen game da Marubuta da Farisawa.
A nan "zauna" na wakilcin ikon yin mulki da kuma yin hukunci. AT: "na da iko kamar Musa" ko "na da ikon faɗan abin da dokan Musa ke nufi"
"dukkan abubuwa ... yi su ku kuma kiyaye su" ko "komai ... yi ku kuma kiyaye"
A nan "ɗaura kaya masu nauyi ... jibga wa mutane a kafada" magana ne na shugabanin addini da su ke sa dokoki masu wuya da kuma sa mutane su yi biyayya ga su. Kuma "baza su motsa danyatsa" ƙarin magana ne da ke nufin cewa shugabanin addin ba za su taimake mutanen ba. AT: "su na sa ku yi biyayya ga dokoki masu yawa da ke da wuyan bi. Amma basu yin komai don su taimake mutanen a bin dokan"
AT: "Su na yin dukka ayukansu domin mutane su iya ganin abin da suke yi"
Dukka waɗannan abubuwa ne da Farisawa suke don su bayyana kamar su na girmama Allah fiye da waɗansu mutane.
ƙaramin akwatin fata da ke ɗauke da takarda da an rubuto nassi a kai
Farisawan sun yi alakwayi a ƙasan tufafinsu musamman don su nuna biyayyar su ga Allah.
Yesu ya cigaba da magana da taron da kuma almajiran game da su Farisawan.
Dukka waɗannan wurare ne da mutane masu daraja suke zama.
babban, fili inda mutane suke saya da sayar da abubuwa
AT: "don mutane su kira su 'Mallam."'
AT: "Amma ba sai kun yarda wani ya kira ku"
Duk aukuwar "ku" ɗaya ne kuma na nfuin duka masubin Yesu.
A nan "'yan'uwa" na nufin "'yan'uwa masubi"
Yesu ya na amfani da ƙarin magana domin ya faɗa wa masu sauraransa cewa kaɗa su yarda mutane masu daraja su fi daraja a wurinsu fiye da Allah. AT: "kaɗa ku kira wani a duniya Ubanku" ko "kaɗa ku faɗa cewa kowane mutum a duniya ubanku ne"
"Uba" anan muhimmin laƙabi ne wa Allah.
AT: "Kuma, kaɗa ku bar wani ya ƙira ku"
A lokacin da Yesu ya ce "Almasihu," ya na maganan kansa a cikin mutum na uku. AT: "Ni, Almasihun, ni ne malaminku"
"mutumin da ke mafi daraja a cikinku"
A nan "ku" na nufin masubin Yesu."
"daraja kansa"
AT: "Allah zai kaskanta"
AT: "Allah zai sa daraja" ko "Allah zai girmama"
"yadda zai zama da ban tsora a Dubi yadda kun juya wannan a cikin 11:21.
Yesu ya na maganar mulkin sama, wadda Allah ya na mulki akan mutane, kamar gida ne, kofa wadda farisawan suka toshe daga waje domin kada su ko wani dabam ya shiga gidan. Ana samin jumlar "mulkin sama" a cikin littafin matthew. In ya yiwu, Yi amfani da kalmar harshenku na "sama" a juyinku. AT: "kun sa shi yiwuwa wa mutane su shiga mulkin sama ... ba ku shiga ba ... kuma ba ku bar waɗanda suke so su sami shiga ba" ko "Kun hana mutane daga karban Allah, wadda yake zama a sama, sarki ... ba ku ƙarbe shi kamar sarki ba ... kuma kun sa shi mara yiwuwa wa waɗanda su ke so ƙarbe shi sarki su yi haka"
Wannan ƙarin magana ne da na nufin su na tifiyan wurare masu nisa. AT: "ku na tafiya mai nisa sosai"
"domin ya sa wani ya ƙarba addininka"
A nan "ɗan" ƙarin magana ne da na nufin "zama na." AT: "mutum da ya zama na wuta" ko "mutum da ya kamata ya je wuta"
Dubi rubutan ƙasa. Kalmar "cinye" magana ne da ke nufin kwace da ƙarfi. Ma'ana mai yiwuwa 1) "gidaje" na nufin gidajensu. AT: "ku na sace gidajen gomraye daga wurinsu" 2) "gidaje" magana ne na dukka mallakarsu. AT: "ku na sata dukka mallakar gomraye"
Shugabanin Yahudawan makafi ne a ruhaniya. Ko da shike sun ɗauki kansa kamar malamai, ba su iya gane gaskiyar Allah ba. Dubi yadda kun juya "jagora makafin" a cikin 15:14.
"ta haikali ba sai ya ɗauka rantuwarsa ba"
"ɗaure da rantsuwarsa." Jumlar "ɗaure da rantuwarsa" magana ne da na bukata a yi abin da ya ce zai yi a cikin rantsuwa. AT: "dole ne ya yi abin da ya ce zai yi"
Yesu ya yi amfani da wannan tambayan domin ya ƙwabe Farisawan domin sun ɗaukake zinariyar kamar ya fi haikalin daraja. AT: "Haikalin da ya mika zinariyar ga Allah ya fi daraja fiye da zinariya!"
"Haikalin da yake sa zinariyar ya zama na Allah kadai"
Ana iya sa a bayyana bayanin da an fahimta. AT: "Kun kuma ce"
"ba sai ya yi abin da ya rantse zai yi ba" ko "ba sai ya tsaya a kan rantsuwarsa ba"
Wannan dabba ne ko hatsi da mutum zai kawo wa Allah ta wurin sakawa a kan bagadin Allah.
Shugabanin Yahudawan makafi ne a ruhaniya. Ko da shike sun ɗauki kansa kamar malamai, ba su iya gane gaskiyar Allah ba.
Yesu ya yi amfani da wannan tambayan domin ya ƙwabe Farisawan don yadda suke yi da kyautan kamar ya fi daraja fiye da bagadin. AT: "Bagadin da ya na tsarkake kyautan ya fi kyautan!"
"bagadin da yake ba kyautan daraja ga Allah" "
"ta dukkan kyautanne da mutane sun saka a kai"
Duk waɗannan na nufin Allah Uban.
yadda zai zama da ban tsora ... munafukai! Dubi yadda kun juya wannan a cikin 11:21.
Waɗannan itce da iri ne da mutane na amfani don su sa abinci ya yi dadi.
"ba ku yi biyyaya"
"al'amuran mafi daraja"
"ya kamata kun yi biyyaya da waɗannan dokoki masu daraja"
AT: "tare da bin dokoki masu dan daraja"
Yesu ya yi amfani da wannan magana domin ya kwatanta Farisawan. Yesu ya na nufin cewa Farisawan ba su fahimci umurnin Allah ko yadda za su faranta mashi rai ba. Don haka, ba za su iya koya wa waɗansu yadda za su faranta wa Allah rai ba. Dubi yadda kun juya wannan magana a cikin 15:14.
Mai da hankali a bin ƙananan dokoki masu dan daraja da kuma ƙyale dokoki mafi daraja na nan kamar hwaka ne kamar mai da hankali don ƙada ku haɗiye ƙaramin dabba mai datti amma cin namam babban dabba. AT: "ku na nan kamar wawaye kamar mutum da ya na butsar da ƙwaro da ya faɗi a cikin ruwansa amma ya haɗiye rakumi"
Wannan na nufin juye ruwa a tuffafi don a cire ƙwaro daga ruwan sha.
ƙaramin ƙwaro mai tashi sama
Wannan magana ne da ke nufin cewa marubuta da Farisawan sun bayyana da tsarki a waje ga waɗansu, amma a a ciki kuwa mugaye ne.
"su na son abin da waɗansu ke da shi, kuma sun yi son kai"
Farisawan sun makanta a ruhaniya. Ko da shike sun ɗauki kansu kamar mallamai, ba su iya fahimtar gaskiyar Allah.
Wannan magana ne da na nufin cewa idan za su zama da tsarki a cikinsu sakamokan shi ne za su zama da tsarki a wajen.
Wannan magana ne da ke nufin cewa Farisawa da marubuta
"kaburburan da wani ya shafa wa farar kasa." Yahudawa su na shafa wa kaburbura farar kasa domin mutane su iya gani su kuma daina taɓasu. Taɓa kaburi zai sa mutum ya zama da kazanta.
AT: "na mutane masu adalci"
"a loƙacin kakaninmu"
"da bamu hadu da su ba"
A nan "jini" na nufin rai. Zub da jini na nufin ƙashe. AT: "ƙashe" ko "yin kisa"
A nan "'ya'ya" na nufin "zuriya."
Yesu ya yi amfani da wannan domin ya nuna cewa Farisawan za su cika mugayen ayukan da kakaninsu su ka fara a loƙacin da sun ƙashe annabawan. AT: "Kun kuma gama zunuban da kakaninku sun fara"
Shaidan macizai ne, kuma ganshekai macizai ne masu dafi. Mugaye ne kuma su kullum alamu ne na mugu. AT: "Ku na nan muguye da mugunta kamar macizai masu dafi"
A nan "'ya'ya" na nufin "samin halin." Dubi yadda kun juya jumla irin wannan a cikin 3: 7.
Yesu ya yi amfani da wannan tambaya don ƙwaba. "babu hanya da za ku tsere hukuncin gidan wuta!"
Ana magana wani loƙaci domin a nuna cewa wani zai yi wani abu nan ba da juma ba. AT: "Zan turo maku annabawa, masu hikima, da kuma marubuta"
Jumlar "A kan ku zai zo" ƙarin magana ne da ke nufin ƙarban hukunci. Zuba jini magana ne da na nufin ƙashe mutane, don haka "jinin adalci da an zuba a duniya" na wakilcin mutane masu adalci da an ƙashe su. AT: "Allah zai hukunta ku domin kisan dukka mutane masu adalci"
A nan kalmar "jini" na wakilcin ƙashen mutum. AT: "daga mai kisan ... zuwa mai kisan"
Habila ne farkon mai adalci wanda aka ƙashe shi, kuma Zakariya, wanda Yahudawa suka ƙashe shi a cikin haikali, ana zaton ku shi ne na ƙarshe. Waɗannan maza biyun su na wakilcin dukka mutane masu adalci da aka ƙashe.
Wannan Zakariya ba shi ne Uban Yahaya mai baftisma ba.
Yesu ba ya nufin cewa mutanen da ya ke magana da su ne suka ƙashe Zakariya. Ya na nufin kakaninsu ne su yi.
"Ina gaya maku gaskiyar." Wannan na kara nanaci a abin da Yesu zai faɗa nan gaba.
Yesu ya yi magana da mutanen Urushalima kamar su ne garin.
AT: "waɗanda Allah ya turo maki"
Yesu ya na magana da Urushalima kamar mace ne kuma mutanen 'ya'yanta ne. AT: "mutanen ki" ko "mazaunanki"
Wannan magana ne da ke nanata kaunar Yesu ga mutanen da kuma yadda ya so ya kula da su.
kaza na mace. Za ku iya juya da kowane tsuntsu da ke ƙare 'ya'yanta a cikin fiffikenta.
"Allah zai bar gidanku, kuma zai zama fanko"
AT: 1) "birnin Urushalima" ko 2) "haikalin."
Wannan na ƙara nanata abin da Yesu zai faɗa a gaba.
A nan "cikin sunan" ko "kamar wakili." Dubi yadda kun juya wannan a cikin 21:9. AT: "Mai albarka ne shi wanda ke zuwa a cikin ikon Ubangiji" ko "Shi wanda ke zuwa a matsayin wakilin Ubangiji zai zama da albarka"
1Yesu ya fita daga cikin haikalin ya kama hanyar sa. Almajiran sa suka zo suna nuna masa ginin haikali. 2Amma ya amsa masu yace, "kun ga dukkan wadannan abubuwan? Ina gaya maku gaskiya, ba ko dutse daya da za'a bari akan dan'uwansa wanda ba za'a rushe shi ba."3Yayin da ya zauna a kan dutsen zaitun, almajiran sa suka zo wurin sa a boye suka ce, "me zai zama alamar zuwanka da kuma na karshen duniya?" 4Yesu ya amsa yace dasu, "Ku kula kada wani yasa ku kauce." 5Gama da yawa za su zo da sunana. Za su ce, "ni ne almasihu," kuma za su sa da yawa su kauce.6Za ku ji labarin yake-yake da kuma shelar yake-yake. Ku kula kar ku tsorata, domin dole abubuwan nan su faru; amma karshen dai tukunna. 7Gama al'umma zata tayarwa al'umma, kuma mulki zai tayarwa mulki. Za'a yi yunwa da girgizar kasa a wurare dabam dabam. 8Amma dukkan wadannan farkon ciwon haihuwa ne kawai.9Bayan haka za'a bada ku ga tsanani a kuma kashe ku. Dukkan al'ummai za su tsane ku saboda sunana. 10Daga nan da yawa za su yi tuntube, kuma su ci amanar juna, su kuma tsani juna. 11Annabawan karya da yawa za su taso kuma susa da yawa su kauce.12Domin mugunta zata ribambanya, kaunar masu yawa zata yi sanyi. 13Amma duk wanda ya jure har karshe, zai sami ceto. 14Za'a yi wa'azin wannan bisharar mulkin a dukkan duniya don ya zama shaida akan dukkan al'ummai. Daganan karshen zai zo.15Don haka, idan kun ga abin kyama mai lalatarwa, wanda Annabi Daniyel ya yi maganar sa, Ya tsaya a wuri mai tsarki (bari mai karatu ya fahimta), 16bari wadanda ke yahudiya su gudu zuwa kan duwatsu, 17Bari wanda yake kan bene kada ya sauko don daukar wani abu a cikin gidansa, 18kuma wanda yake gona kar ya dawo gida domin daukar babbar rigarsa.19Amma kaito ga wadanda suke dauke da yaro, ko masu shayarwa a wannan kwanakin! 20Ku yi addu'a kada gudun ku ya zama lokacin hunturu, ko ranan asabaci. 21Domin za'ayi tsanani mai girma, wanda ba'a taba yin irin shi ba, tun farkon duniya har ya zuwa yau, a'a ba za ayi irin shi ba kuma. 22In ba don an rage kwanakin ba, da ba mahalukin da zai tsira. Amma albarkacin zababbun, za a rage kwanakin.23Sa'annan idan wani yace maku, duba, "ga Almasihu a nan!" ko, "ga Almasihu a can!" kar ku gaskata. 24Gama annabawan karya da almasihan karya za su zo suna nuna alamu da al'ajibai, don su yaudari masu yawa zuwa ga bata, in ya yiwuma har da zababbun. 25Kun gani, na gaya maku kafin lokacin ya zo.26Saboda haka, idan suka ce maku, "ga shi a jeji," kar ku je jejin. Ko, "ga shi a can cikin kuryar daki," kar ku gaskata. 27Yadda walkiya ke haskakawa daga gabas zuwa yamma, haka nan zuwan Dan mutum zai zama. 28Duk inda mushe yake, nan ungulai suke taruwa.29Amma nan da nan bayan kwanakin tsananin nan, rana za ta duhunta, wata kuma ba zai ba da haskensa ba, taurari kuma za su fado daga sama, ikokin sammai za su girgiza.30Sa'annan alamar Dan Mutum za ta bayyana a sararin sama, kuma dukkan kabilun duniya za su yi bakin ciki. Za su ga Dan Mutun na zuwa a gajimarai da iko da daukaka mai girma. 31Zai aiki mala'ikunsa, da karar kaho mai karfi, kuma za su tattara dukkan zababbu daga dukkan kusurwoyi hudu, daga karshen sararin sama har zuwa wani karshen.32Kuyi koyi da itacen baure. Da zaran reshen sa ya yi toho ya fara bada ganye, za ku sani bazara ta kusa. 33Haka kuma, idan kun ga dukkan wadannan abubuwa, ya kamata ku sani, Ya yi kusa, ya na bakin kofa.34Ina gaya maku gaskiya, wannan zamanin ba zai wuce ba, sai dukkan wadannan abubuwan sun faru. 35Sama da kasa za su shude, amma kalmomina ba za su shude ba.36Amma game da ranan nan ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai Uban kadai.37Kamar yadda kwanakin Nuhu suke, haka zai zama game da zuwan Dan Mutum. 38A wadannan kwankin kafin zuwan ruwan tsufana suna ci suna sha, suna aure suna aurarwa har ranar da Nuhu ya shiga jirgin, 39ba su san kome ba har ruwan ya zo ya cinye su_ haka ma zuwan Dan Mutun zai zama.40Sa'annan mutane biyu zasu kasance a gona za a dauke daya, a bar daya a baya. 41Mata biyu na nika a manika za a dauke daya, za a bar dayar. 42Don haka sai ku yi zaman tsaro, domin baku san ranar da Ubangijinku zai zo ba.43Amma ku san wannan, idan maigida ya san lokacin da barawo zai zo, zai zauna a shirye ba zai bar gidan sa har a balle a shiga ba. 44Don haka sai ku shirya, domin Dan Mutum zai zo a sa'ar da ba ku yi zato ba.45To wanene amintaccen bawannan mai hikima, wanda maigidan sa ya sa ya kula mar da gida, domin ya ba su abinci a kan lokaci? 46Mai albarka ne bawan, da mai gidan zai same shi a kan aikin sa a lokacin da ya dawo. 47Ina gaya maku gaskiya mai gidan zai dora shi a kan dukkan a binda yake da shi.48Amma idan mugun bawa ya ce a zuciyarsa, "maigida na ya yi jinkiri," 49sai ya fara dukan sauran barorin, ya yi ta ci da sha tare da mashaya, 50uban gidan bawan zai dawo a ranar da bawan bai zata ba, a lokacin da bai sani ba. 51Uban gidansa zai datsa shi biyu, karshen sa zai zama daidai da na munafukai, za a sashi inda a ke kuka da cizon hakora.
Yesu ya fara kwatanta abubuwan da zai faru kafin ya dawo kuma a zamanin ƙarshe.
Ya na nufin cewa Yesu da kansa ma ba ya cikin haikalin. Ya na cikin fadan haikalin.
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya sa almajiransa su yi tunani mai zurfi game da abin da zai gaya masu. AT: "Bari in gaya maku game da dukka waɗannan ginin."
"Na faɗa maku gaskiya." Wannan ya kara nanaci a abin da Yesu zai ce nan gaba.
Ya na nufin cewa makiya sojoji za su rushe duwatsun. AT: "loƙacin da makiya sojoji su ka zo, zo su rushe kowane dutse a cikin waɗannan gini"
Anan "zuwanka" na nufin loƙacin da Yesu zai zo a cikin iko, kafa mulkin Allah a duniya
A nan "sa ku kauce" magana ne na sa wani ya gaskanta da abin da ba gaskiya ba. AT: "Ku kula kada wani ya ruɗe ku ... kuma zai ruɗe mutane dayawa"
A nan "suna" na nufin "iko" ko "kamar wakilin" wani. AT: "da yawa za su amince cewa sun zo kamar wakili na" ko "da yawa za su ce su na yi mani magana"
AT: "Kaɗa ku bar wannan ya tsorata ku"
Dukka waɗannan na nufin abu ɗaya. Yesu ya na nanata cewa mutane a ko ina za su yi faɗa da juna.
Wannan na nufin zafin da mace ta ke ji kafin ta haife yaro. Wannan magana na nufin waɗannan yaƙe-yaƙe, yunwa, da girgizan kasa farkon abubuwan da zai kai ga ƙarshen duniya.
"mutane za su ba da ku ga masu iko, wadda za su za ku wahala a kuma ƙashe ku."
A nan "al'ummai" magana ne, da na nufin mutanen al'ummai. AT: "Mutane daga kowane al'umma za su tsane ku"
A nan "suna" na nufin cikakken mutum. AT: "domin kun gaskanta da ni"
"Taso" anan ƙarin magana ne na "zama tabbatacce." A: "zai zo"
A nan "sa ... ƙauce" magana ne na sa wani ya gaskanta da abin da ba gaskiya ba. AT: "kuma ruɗe mutane dayawa"
Za a iya fasara "rashin doka" da jumlar "rashin biyayya ga doka." AT: "rashin biyayya ga doka zai karu" ko "mutane za su ki bin dokan Allah da kuma fiye"
AT: 1) "mutane dayawa ba za su ƙaunaci sauran mutane ba" ko 2) "mutane dayawa ba za su ƙaunace Allah ba."
AT: "Allah zai cece mutumin da ya jure har ƙarshe"
"mutum da ya tsaya da aminci"
Ba a fahimci ko kalmar "ƙarshe" na nufin loƙacin da mutu ya mutu ko loƙacin da azaban ya kare ko ƙarshen zamani loƙacin da Allah zai nuna kansa a matsayin sarki. Ainahin maganan shi ne sun jure.
A nan "mulki" na nufin mulkin Allah kamar sarki. AT: "Mutane za su faɗa wannan sako game da mulkin Allah"
A nan, "alummai" na nufin mutane. AT: "dukka mutane a dukka wurare"
"ƙarshen duniya"
AT: "mara kunya wadda ya ƙazantad da abubuwan Allah, game da wadda Daniyel ya rubuto"
Ba Yesu ne na magana ba. Matthew ya ƙara wannan don ya shirya mai karatun da cewa Yesu ya na amfani da kalmomin da zai sa su yi tunani su kuma fasara.
Benen da Yesu ya yi zama na nan shimfiɗaɗɗe, kuma mutane na iya tsaya a kai.
Wannan wata hanya ne na ce "mata masu ciki."
"a wannan loƙacin"
"da ba sai kun gudu ba"
"loƙacin sanyi"
AT: "In Allah bai rage loƙacin wahalan ba, kowa zai mutu"
"mutane." Anan "mahaluki" hanya ne na ce dukka mutane.
AT: "Allah zai rage loƙacin wahalan"
"kada ku yarda da abubuwan karya da sun gaya maku"
A nan "yauɗare" magana ne na sa wani ya gaskanta wani abun da ba gaskiya ba. Ana iya juya wannan a jimloli biyu. AT: "don su ruɗi, in ya yiwu, har zababbun" ko "don su ruɗi mutane. In ya yiwu, za su ma ruɗi zababbun"
AT: "Idan wani ya ce faɗa maku cewa Almasihun na cikin jeji, kar"
AT: "Ko, idan wani ya gaya maku cewa Almasihun na cikin kuryar daka,"
"a cikin dakin ɓoye" ko "a cikin ɓoyeyyer wurare"
Wannan na nufin cewa Ɗan Mutum zai zo da sauri kuma za a iya ganin shi.
Yesu ya na maganar kansa a cikin na uku.
Mai yiwuwa wannan labari ne da mutanen zamanin Yesu sun fahimta. AT: 1) Loƙacin da Ɗan Mutum zai zo, kowa zai gan shi za su kuma san cewa ya zo, ko 2) duk inda matattun mutane a ruhaniya suke, annabawan karya za su kasance a wurin domin su gaya masu karya.
tsuntsaye da su ke cin jikin matattu ko matattun dabbobi
"sa'adda tsananin wannan loƙacin ya gama, ranan"
"loƙacin wahala"
AT: "Allah zai sa rana ta duhunta"
AT: "Allah zai girgiza abubuwa a cikin sarari da kuma saman sararin"
Yesu ya na maganar kansa a cikin na uku.
A nan "kabilu" na nufin mutane. AT: "dukka mutanen kabilun" ko "dukka mutane"
"Zai busa kaho ya kuma aiki mala'ikunsa" ko "zai sa mala'ika ya busa kahon, zai kuma aiki mala'ikunsa"
"mala'ikarsa za su tattara"
Waɗannan mutane ne da Ɗan Mutum ya zaba.
Dukka waɗannan na nufin abu ɗaya. Karin magana ne da ke nufin "daga koina." AT: "daga dukkan duniya"
Yesu ya na maganar kansa a cikin na uku. AT: "loƙacin zuwa na ya yi kusa"
"kusa da kofofin." Yesu ya yi amfani da misalin sarki ko mutum mai daraja da ke zuwa kusa da kofofin gari mai katanga. Magana ne da ke nufin loƙacin da Yesu zai shiga ba da daddewa ba.
A nan "wuce" hanya mai kyau ne a ce "mutu." AT: "wannan zamani ba za su mutu dukka ba"
AT: 1) "dukka mutane musa rai yau,"na nufin mutanen da suke rayayye a loƙacin da Yesu ya na magana, ko 2) "dukka mutane musa rai a loƙacin da waɗannan abubuwan da na faɗa maku ya faru." Yi kokari ku juya dukka don fasara ya iya yiwuwa.
"sai Allah ya sa dukka waɗannan abubuwa sun faru"
Kalmomin "sama" da "kasa" magana ne da ya kumshi komai da Allah ya hallita, musamman abubuwa da su na nan kamar dauwammamme. Yesu ya na ce wa kalmarsa, ba kamar waɗannan abubuwa ba, dauwammamme ne. AT: "Ko sama da kasa ma za su shude"
"ɓace"
A nan "kalmomi" na nufin abin da Yesu ya faɗa. AT: "abin da na faɗa zai zama gaskiya kulum"
A nan "rana" da "sa'a" na nufin daidan loƙacin da Ɗan Mutum zai dawo.
"ba ma Ɗan ba"
Wannan muhimmin laƙabi ne wa Yesu, Ɗan Allah.
Wannan muhimmin laƙabi ne wa Allah.
"A loƙacin da Ɗan Mutum zai zo, zai zama kamar loƙacin Nuhu."
Yesu ya na maganar kansa a na uku.
AT: " jirgin. Kuma mutanen ba su gane wani abu na faruwa ba"
AT: "ɗauke. haka ne zai zama a loƙacin da Ɗan Mutum zai zo"
Wannan ne loƙacin da Ɗan Mutum ya zo.
AT: 1)Ɗan Mutum zai ɗauki hanya ɗaya zuwa sama zai kuma bar ɗayan a duniya wa hukunci ko 2) mala'ikun za su ɗauki ɗaya don hukunci su kuma bar ɗayan wa albarka.
abin nika
"Domin abin da na faɗa gaskiya ne"
"yi hankali"
Yesu ya yi amfani da labarin maigida da bayi domin ya kwatanta wa almajiransa cewa su zauna a shirye domin zuwansa.
Yesu ya na faɗa cewa zai zo a loƙacin da mutane ba su zata ba, ba wai zai zo ya yi tsata ba.
"da ya tsare gidansa"
AT: "da bai bar wani ya shiga gidansa don ya saci abubuwa ba"
Yesu ya yi mafani da wannan tambaya domin ya sa almajiransa su yi tunani. AT: "To wanene amintaccen bawannan mai hikima wanda maigidansa ... lokaci."
"ba wa mutanen cikin gidan maigida abincinsu"
A nan "zuciya" na nufin hankali. AT: "na tunani a zuciyarsa"
AT: "Maigida ya ɗade da dawowa" ko "Maigida na ba zai dawo da sauri ba"
Dukka waɗannan maganganun na nufin abu ɗaya. Su na nanata cewa Uban gidan zai zo a loƙacin da bawan bai zata ba.
Wannan ƙarin magana ne da na nufin a sa mutum ya sha wuya sosai.
"sa shi da munafukai" ko "tura shi zuwa wurin da ana tura munafukai"
"cizon hakora" anan alama ne, da ke wakilcin wahala mai tsanani. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 8: 12. AT: "mutane za su yi kuka da cizon hakoransu saboda wahalarsu"
1Sa'annan mulkin sama zai zama kamar budurwai goma da suka dauki fitilunsu domin su taryi ango. 2Biyar daga cikin su masu hikima ne biyar kuma wawaye. 3Sa'adda wawayen budurwai suka dauki fitilunsu, ba su dauki karin mai ba. 4Amma budurwai masu hikimar suka dauki gorar mai tare da fitilunsu.5To da angon ya makara, dukkan su sai suka fara gyangyadi sai barci ya dauke su. 6Amma da tsakkar dare sai aka yi shela, 'Ga ango ya iso! Ku fito taryensa.7Sai dukka budurwan nan suka tashi suka gyaggyara fitilunsu. 8Wawayen su ka ce da masu hikimar, 'Ku sammana kadan daga manku gama fitilunmu su na mutuwa.' 9"Amma masu hikimar suka ce 'Tun da man ba zai ishe mu tare da ku ba, sai ku je gun ma su sayarwa ku sayo wa kanku.10Sa'adda suka tafi sayan man, sai angon ya shigo, kuma wadanda suke a shirye su ka shiga tare da shi bukin auren, sai aka rufe kofar. 11Bayan dan lokaci kadan sauran budurwan suka dawo suna cewa, 'Mai gida, mai gida, bude mana kofar.' 12Amma ya amsa ya ce, 'A gaskiya ina gaya maku, ni ban san ku ba.' 13Don haka sai ku lura, don baku san rana ko sa'a ba.14Domin yana kama da wani mutum da zai tafi wata kasa. Ya kira barorinsa ya ba su dukiyar sa. 15Ga wani ya ba shi talanti biyar, ga wani ya ba shi biyu, ga wani kuma ya ba shi talanti daya. kowa an bashi gwargwadon iyawarsa, sai wannan mutum ya yi tafiyar sa 16nan da nan sai wanda ya karbi talanti biyar ya sa nasa a jari, ya sami ribar wasu talanti biyar.17Haka ma wanda ya karbi talanti biyu ya sami ribar wasu biyu. 18Amma bawan da ya karbi talanti dayan ya yi tafiyar sa, ya haka rami, ya binne kudin mai gidansa.19To bayan tsawon lokaci sai ubangidan barorin nan ya dawo, domin yayi lissafin kudinsu. 20Bawan da ya karbi talanti biyar, ya kawo nasa da ribar wasu biyar. Yace, 'Maigida, ka bani talanti biyar, gashi na samo ribar karin talanti biyar.' 21Maigidansa yace masa, 'Madalla, bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abu kadan. Zan sa ka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'22Bawan da ya karbi talanti biyun, ya zo yace, 'Maigida, ka ba ni talanti biyu. Gashi kuwa na sami karin ribar wasu biyun.' 23Ubangidansa yace masa, 'Madalla, kai bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abubuwa kadan. Zan saka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'24Sai bawan da ya karbi talanti daya ya zo yace, 'Maigida, na san kai mai tsanani ne. Kana girbi inda baka yi shuka ba, kuma kana tattarawa inda ba ka watsa ba. 25Na ji tsoro, don haka sai na je na boye talantinka a rami. Duba, ga abinda yake naka.'26Amma ubangidansa ya amsa yace, kai mugu malalacin bawa, ka san cewa ni mai girbi ne inda ban shuka ba kuma ina tattarawa inda ban zuba ba. 27To da ba sai ka kai kudina a banki ba, da bayan na dawo da sai in karbi abina da riba.28Saboda haka ku kwace talantin daga gare shi ku baiwa mai talanti goman nan. 29Gama ga wanda yake da shi za'a kara masa har ma a yalwace za'a kara bashi. Amma ga wanda bashi da komai abinda ke nasa ma za'a kwace. 30Ku jefa wannan mugun bawan marar amfani, cikin duhu mai zurfi, inda ake kuka da cizon hakora.'31Sa'adda Dan mutum zai zo cikin daukakarsa da dukan Mala'iku tare da shi, sa'annan zai zauna kursiyinsa na daukaka. 32A gabansa za'a tattara dukkan al'ummai, zai rarraba mutanen daya'daya, kamar yadda makiyayi yake rarraba tumaki daga awaki. 33Zai sa tumakin a hannunsa na dama, amma awakin a hannunsa na hagu.34Sa'annan sarkin zai ce wa na hannun damarsa, 'Ku zo ku da Ubana ya albarkata, ku gaji mulkin da aka shirya maku kafin a kafa duniya. 35Gama na ji yunwa kuka bani abinci; Na ji kishi kuka bani ruwa; Na yi bakunci kun bani masauki; 36Na yi huntanci kuka tufasar dani; Na yi ciwo kuka kula dani; Ina kurkuku kuka ziyarceni.'37Sa'annan masu adalcin za su amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa muka baka abinci? Ko kana jin kishi muka baka ruwan sha? 38Kuma yaushe muka ganka kana bakunci har muka baka masauki? Ko kuma kana huntanci da muka tufatar da kai? 39Yaushe kuma muka ganka kana ciwo ko a kurkuku har muka ziyarce ka?' 40Sa'annan Sarkin zai amsa masu yace, 'Hakika Ina gaya maku, duk abinda kuka yi wa daya mafi kakanta daga cikin 'yan'uwana a nan ni kuka yi wa.'41Sa'annan zai cewa wadanda suke hannunsa na hagu, 'Ku rabu da ni, ku la'anannu, ku tafi cikin wutar jahannama da aka shirya wa Shaidan da aljannunsa, 42domin ina jin yunwa baku bani abinci ba; ina jin kishi ba ku bani ruwa ba; 43Ina bakunci amma baku bani masauki ba; ina huntanci, baku tufasar da ni ba; ina ciwo kuma ina kurkuku, baku kula da ni ba.'44Sa'annan suma zasu amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa, ko kishin ruwa, ko kana bakunci, ko kana huntanci, ko ciwo, kuma a kurkuku, da bamu yi maka hidima ba?' 45Sa'annan zai amsa ya ce masu, 'Ina gaya maku hakika abin da baku iya yiwa mafi karanta daga cikin wadannan ba, ba ku yi mani ba.' 46Wadannan kuwa zasu tafi cikin madawwamiyar azaba amma adalai zuwa rai madawwami."
Yesu ya ba da labarin budurwai masu hikima da wawaye don ya bayyana cewa almajiransa su shirya don dawowarsa.
A nan "mulkin sama" na nufin mulkin Allah kamar sarki. An yi amfani da jumlar "mulkin sama" a cikin Matthew ne kadai. In ya yiwu, yi amfani da "sama" a juyinku. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 13:24. AT: "Sa'ad da Allahn mu a sama ya nuna kansa sarki, zai zama kamar"
AT: 1) fitilu ko 2) jiniya da an yi su daga sa tufaffi a karshen itace da kuma jika tufaffun da mai.
"budurwai biyar"
"su na da mai na cikin fitilar su kadai"
An yi amfani da wannan kalma don a sa alama a ainahin labarin. Yesu anan ya fara faɗan sabon sashin labarin.
AT: "sa'ad da angon ya ɗauki tsawon lokaci kafin ya isa"
"gyangyadi ya ɗauke dukka budurwai goman"
"wani ya yi ihu"
"gyaggyara fitilinsu don ya ci da haske"
AT: "Wawayen budurwan su ka ce da budurwan masu hikimar"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "wutan cikin fitilunmu sun yi kusan mutuwa"
"wawayen budurwai biyar suka tafi"
AT: "zuwa sayan mai"
Wannan budurwan ne da suke da sauran mai.
AT: "bayin suka rufe kofan"
Ana iya sa wannan bayyani a bayyane. AT: "buɗe ma na kofa don mu iya shiga ciki"
"Ina gaya maku gaskiyan." Wannan na kara nanata a abin da mai gidan zai ce.
"Ban san wanene kai ba." wannan ne ƙarshen labarin.
A nan "rana" da "sa'a" na nufin abu ɗaya. Ana iya sa bayanin a bayyane. AT: "ba ku san ainahin lokacin da Ɗan Mutum zai dawo ba"
"mulkin Allah na nan kamar " (Dubi: Matthew 13:24)
"ya shirya tafiya" ko "ya kusan tafiya"
"ya sa su kula da dukiyarsa"
"dukiyar sa"
"talanti biyar na zinariya." Daina juya wannan zuwa kuɗin zamani. "Talanti" na zinariya ya kan kai kuɗin shekaru ashirin. Labarin ya na bayyana irin kuɗin biyar, biyu, da ɗaya da kuma babban dukiya da ke ciki. AT: "jaka biyar na zinariya" ko "jaka biyar na zinariya, kowanne ya kai kuɗin shekaru ashirin"
An fahimci kalmar "talanti" daga jumla da ta wuce. AT: "ga wani ya ba shi talanti biyu na zinariya ... ba da talanti ɗaya na zinariya" ko "ga wani ya ba shi jakan zinariya biyu ... ba da jakan zinariya ɗaya"
Ana iya bayyana wannan bayanin. AT: "bisa iyawar kowane bawa a bi da dukiya"
"daga cikin jarinsa, ya sami ribar talanti biyar"
"sami wani talanti biyu"
"na samo ribar karin talanti biyar"
"Talanti" ya kai ƙudin shekaru ashirin. Daina juya wannan zuwa kuɗin zamani. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 25:15.
"Ka yi koƙari" ko "Ka yi daidai." Al'adan ku na iya samin bayyyani da maigida (ko wani a mulki) zai yi amfani don ya nuna cewa ya amince da abin da bawansa (ko wani a karkashinsa) ya yi.
Jumlar "shiga cikin farincikin" ƙarin magana ne. Kuma, maigidan ya na naganar kansa ne a cikinsa na uku. AT: "Zo ku yi murna da ni"
"na sami ribar talenti biyu"
Kalmomin "girbi inda baka yi shuka ba" da "tattarawa inda ba ka watsa ba" na nufin abu ɗaya ne. Su na nufin manomin da yake tattara amfanin gona da waɗansu mutane sun shuka. Bawan ya yi amfani da wannan magana don ya yi zargin maigidan da ɗaukan abubuwan waɗansu.
"watsa iri." Wannan na nufin shuka iri ta wurin jefawa a hankali cike da hanu a cikin ƙasa.
"Duba, ga abinda da ke naka"
"Kai mugun bawa ne wadda ba ya so ya yi aiki. Ka san"
Kalmomin "girba inda ban shuka ba" ko " tattarawa inda ban zuba ba" na nufin abu ɗaya ne. Su na nufin manomin da ya ke tattara amfanin gona da mutanen da sun yi masa aiki sun shuka. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 25: 24, inda bawan ya yi amfani da waɗannan kalmomi biyu don ya yi zargin manomin. Mai karatun ya gane cewa manomin na amince cewa ya na tattara abin da waɗansu sun shuka amma ya na cewa daidai ne ya yi haka.
AT: " ƙarbi ƙudi na"
biya daga banki domin yin amfani da ƙudin mai gidan na dan loƙaci.
Mai gidan na magana da sauran bayin.
"Talanti" ya kai ƙudin shekaru ashirin. Daina juya wannan zuwa kuɗin zamani. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 25:15.
Ya na nufin cewa wanda ke da wani abu na amfani da shi da hikima. AT: "wanda ya na amfani da abin da ya na da shi da kyau"
AT: "Allah zai ba da fiye" ko "Zan ba da fiye"
"har fiye da"
Ya na nufin cewa mutumin na da wani abu amma ba ya amfani da shi da hikima. AT: "ga wanda ba ya amfani da abin da ya ke da shi da kyau"
AT: "Allah zai kwace" ko "Zan ƙwace"
Anan "duhu mai zurfi" magana ne na inda da Allah na tura waɗanda sun ki shi. Wannan wuri ne da ke rabe daga Allah har abada. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 8:12. AT: "wuri mai duhu mai nisa daga Allah"
"cizon hakora" anan alama ne, da ke wakilcin wahala da bakin ciki mai tsanani. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 8: 12. AT: "kuka da nuna tsananin wahalarsu"
Yesu ya na magana game da kansa a cikin mutum na uku.
AT: "Zai tattara dukka al'ummai a ganbansa"
"A gabansa"
A nan "al'ummai" na nufin mutane. AT: "dukka mutane daga kowane ƙasa"
Yesu ya yi amfani da ƙarin magana don ya kwatanta yadda zai raɓa mutanen.
Wannan magana ne da na nufin cewa Ɗan Mutum zai raɓa dukka mutane. Zai sa mutane masu adalci a hannun damarsa, ya kuma sa masu zunubi a hannan hagunsa.
A nan, "sarkin" wani laƙabi ne wa Ɗan Mutum. Yesu ya na nufin kansa a mutum na uku. AT: "Ni, sarki, ... hannun damana"
AT: "Zo, ku da Ubana ya albarkance ku"
Wannan muhimmin laƙabi ne wa Allah da ke kwatanta ɗangartaka tsakanin Allah da Yesu.
AT: "ku gaji mulkin da Allah ya shirya maku"
"tun da ya halittce duniya"
AT: "mutane masu adalci"
AT: "Ko yaushe mun gan ka na kishi ... Ko yaushe mun gan ka na tsirara"
Wannan wani laƙabi ne wa Ɗan Mutum. Yesu ya na magana game da kansa a mutum na uku.
"gaya wa waɗanda suke hannun hagunsa"
" ɗaya mafi daraja"
A nan " 'yan'uwa" na nufin kowai, na miji ko mace, da na biyyaya da sarkin. AT: " 'yan'uwana maza da mata anan" ko "waɗannan da su na nan kamar 'yan'uwana maza da mata"
"Na duba cewa kun yi mani"
"Sa'annan Sarkin zai." Yesu ya na maganar kansa a cikin mutum na uku"
"ku mutanen da Allah ya la'ananta"
AT: "wutar jahannama da Allah ya shirya"
masu taimakonsa
An fahimci kalmomin "ina" riga "tsirara." AT: "ina tsirara, baku tufasar da ni ba"
An fahimci kalmomin "ina" riga "ciwo." AT: " ina ciwo kuma ina kurkuku"
Wannan ne ƙarshen sashin labarin da ya fara a cikin 23
"waɗanda suke hagunsa za su amsa"
"wa mafi ƙaƙantan mutane na"
"Na duba cewa ba ku yi mani ba" ko "Ni ne wanda ba ku taimake ni ba"
"Sarkin zai turo waɗannan zuwa inda za su ƙarbi azaba da ba ya karewa"
AT: "amma sarkin zai turo adalai zuwa inda za su zauna har abada tare da Allah"
1Yayin da Yesu ya gama fadi masu wadannan maganganu, sai ya cewa almajiransa, 2"Kun sani sauran kwana biyu idin ketarewa ya zo, kuma za'a bada Dan mutum domin a gicciye shi.3Sa'annan manyan firistoci da dattawan jama'a suka taru a fadar babban firist, mai suna Kayafa. 4Suka shirya yadda zasu kama Yesu a boye su kuma kashe shi. 5Amma suna cewa, "Ba a lokacin idin ba, domin kada tarzoma ta tashi daga cikin mutane."6Sa'adda Yesu yake Baita'anya a gidan Saminu Kuturu, 7daidai lokacin da ya zauna a gefen teburin cin abinci, sai wata mata ta shigo da kwalbar mai, mai tsada, ta zuba wa Yesu a kansa. 8Amma da almajiransa suka ga haka, sai suka ji haushi suka ce, "Ina dalilin yin irin wannan asara? 9Ai da an sayar da wannan mai da kudi mai yawa a rabawa talakawa."10Amma da yake Yesu ya san tunaninsu, sai yace masu, "Don me kuke damun matar nan? Ta yi abu mai kyau domina. 11Kuna da talakawa tare da ku koyaushe, amma ni ba zan kasance da ku ba koyaushe.12Don a sa'adda ta zuba man nan a jikina, ta yi haka ne don jana'iza ta. 13Hakika Ina gaya maku, duk inda za ayi wannan bishara a dukan duniya, abin da matar nan tayi za'a rika ambatar da shi don tunawa da ita."14Sai daya daga cikin sha biyun, mai suna Yahuza Iskariyoti, ya tafi wurin manyan firistocin, 15yace, "Me kuke da niyyar bani idan na mika maku shi?" Suka auna masa azurfa talatin. 16Daga wannan lokacin yayi ta neman zarafi da zai bada shi a wurinsu.17To a rana ta fari na idin ketarewa almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, "Ina kake so mu shirya maka da zaka ci abincin idin ketarewa?" 18Yace, "Ku shiga cikin birnin zaku sami wani mutum sai kuce masa, 'Mallam yace, "lokaci na ya kusa. Zan ci idin ketarewa a gidanka, da almajiraina."'" 19Almajiran suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su, suka shirya abincin idin ketarewar.20Da yamma ta yi, sai ya zauna domin ya ci tare da almajiransa goma sha biyu. 21Sa'adda suke ci, yace, "Hakika ina gaya maku, daya daga cikin ku zai bada ni." 22Suka yi bakin ciki, suka fara tambayarsa daya bayan daya, "Na tabbata ba ni bane ko, Ubangiji?"23Sai ya amsa, "Wanda ke sa hannu tare da ni cikin kwano daya shi ne zai bada ni. 24Dan mutum zai tafi, kamar yadda aka rubuta akan sa. Amma kaiton mutumin da ta wurin sa za'a bada Dan mutum! Gwamma da ba'a haifi mutumin nan ba." 25Yahuza da zai bada shi yace, "Mallam ko ni ne?" Yace masa, "Ka fada da kanka."26Yayin da suke ci, sai Yesu ya dauki gurasa, ya sa albarka, ya karya. Ya ba almajiran yace, "Ku karba, ku ci, wannan jiki nane."27Sai ya dauki kokon yayi godiya, Ya ba su yace, "Ku sha, dukanku. 28"Gama wannan jinina ne na alkawari wanda aka zubar domin gafarar zunuban mutane da yawa. 29Amma ina gaya maku, ba zan kara shan ruwan inabin nan ba, sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a cikin mulkin Ubana."30Da suka raira waka, sai suka ka tafi dutsen zaitun. 31Sai Yesu yace masu, "Dukan ku zaku yi tuntube a wannan dare sabili da ni, gama a rubuce yake, "Zan bugi makiyayin, garken tumakin kuma za su watse.' 32Amma bayan an tashe ni, zan riga ku zuwa Galili."33Amma Bitrus yace masa, "Ko dama duka zasu fadi sabili da kai, ni kam bazan fadi ba." 34Yesu yace masa, "Hakika ina gaya maka, a wannan daren kafin carar zakara, za ka yi musun sani na sau uku." 35Bitrus yace masa, koda zan mutu tare da kai, bazan yi musunka ba." Sai sauran almajiran suma suka fadi haka.36Sa'anna Yesu ya tafi tare da su, wurin da ake kira Getsaimani sai yace wa almajiransa, "Ku zauna a nan ni kuma zan je gaba in yi addu'a." 37Ya dauki Bitrus da kuma 'ya'ya biyu na Zabadi tare da shi, sai ya fara damuwa da juyayi. 38Sai yace masu, "Raina na cikin damuwa sosai har ga mutuwa. Ku kasance anan kuna tsaro tare da ni."39Ya dan taka zuwa gaba kadan, sai ya fadi a fuskarsa, yayi addu'a. Yace, "Ya Ubana, in zai yiwu, bari kokon nan ya wuce ni. Duk da haka, ba nufina za'a bi ba, amma naka nufin." 40Ya koma wurin almajiran ya same su suna barci, sai ya cewa Bitrus, "Kai, ba zaku yi tsaro tare da ni ba koda sa'a daya? 41Ku yi tsaro kuma, kuyi addu'a domin kada ku fada cikin jaraba. Ruhu dai ya yarda amma, jiki ba karfi."42Sai ya koma karo na biyu yayi addu'a, Yace, "Ya Ubana, in wannan kokon ba zai wuce ba sai na sha shi, bari nufinka ya kasance." 43Ya sake dawowa, ya same su suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi. 44Sai ya sake barinsu ya tafi. Ya koma karo na uku yana addu'a yana fadin kalmomi iri daya.45Sai Yesu ya koma wurin almajiran yace masu, "Har yanzu barci kuke kuna hutawa? Duba, lokaci ya kusato, kuma an bada Dan mutum ga hannun masu zunubi. 46Ku tashi mu tafi. Duba, wanda zai badani ya kusato."47Sa'adda yana cikin magana Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya zo. Babban taro ya zo tare da shi daga wurin manyan firistoci da dattawan jama'a. Suna rike da takubba da kulake. 48To mutumin da zai bada Yesu ya rigaya ya basu alama, cewa, "Duk wanda na sumbata, shine. Ku kama shi."49Nan da nan ya kaiga Yesu ya ce, "Gaisuwa, Mallam!" sai ya sumbace shi. 50Yesu kuwa yace masa, "Aboki, kayi abin da ya kawo ka." Sai suka iso suka sa hannuwansu kan Yesu suka kama shi.51Nan take, daya daga cikin wadanda suke tare da Yesu ya mika hannunsa, ya zare takobinsa, ya sare wa bawan babban firist din kunne. 52Sai Yesu yace, masa, "Ka maida takobinka cikin kubensa, domin duk wadanda suka dauki takobi su ma ta wurin takobi za su hallaka. 53Ko kana tunanin ba zan iya kiran Ubana ba, ya kuma aiko da rundunar Mala'iku fiye da goma sha biyu? 54Amma to tayaya za'a cika nassi, cewa dole wannan ya faru?"55A wannan lokacin Yesu yace wa taron, "Kun zo da takubba da kulake ku kama ni kamar dan fashi? Ina zaune kowace rana a haikali ina koyarwa, amma baku kama ni ba. 56Amma duk wannan ya faru ne don a cika abinda annabawa suka rubuta." Bayan haka sai dukkan almajiran suka bar shi suka gudu.57Wadanda suka kama Yesu, suka kai shi wurin Kayafa babban firist, inda marubuta da duttawan jama'a suka taru. 58Amma Bitrus ya bi shi daga nesa, har zuwa farfajiyar babban firist din. Ya shiga ya zauna da masu tsaro domin ya ga abinda zai faru.59A wannan lokaci manyan firistoci da duk 'yan majalisar suka fara neman shaidar karya akan Yesu, domin su samu su kashe shi. 60Amma ba su samu ko daya ba, ko dayake an samu shaidun karya dayawa da suka gabata. Amma daga baya sai wasu su biyu suka fito 61sukace "Wannan mutum yace zan iya rushe haikalin Allah, in kuma gina shi cikin kwana uku.'"62Babban Firist din ya tashi tsaye yace masa, "Ba zaka ce komai ba? Wace irin shaida ce ake yi akanka?" 63Amma Yesu yayi shiru. Babban Firist ya ce, "Na umarce ka da sunan Allah mai rai, ka gaya mana ko kai Almasihu ne, Dan Allah." 64Yesu ya amsa masa, "Ka fada da bakin ka. Amma ina gaya maka, daga yanzu zaka ga Dan mutun na zaune a hannun dama na iko, ya na zuwa akan gizagizai na sama."65Sai babban firist din ya yayyaga rigarsa, yana cewa, "Yayi sabo! don me ku ke neman wata shaida kuma? Duba, yanzu kun ji sabon. 66Menene tunaninku?" Suka amsa sukace, "Ya cancanci mutuwa."67Sai suka tofa masa yawu a fuska, suka kuma yi masa duka, suka kuma mammare shi da tafin hannuwansu, 68sukace, "Ka yi mana anabci, kai Almasihu. Wanene wanda ya dokeka.69To Bitrus kuwa na zaune a farfajiyar, sai wata yarinya baiwa ta zo wurinsa tana cewa, "Kaima kana tare da Yesu na Galili." 70Amma ya yi musun haka a gaban su duka, yace, "Ban ma san abinda kike magana akai ba."71Da ya fita zuwa bakin kofa, nan ma wata yarinyar baiwa ta gan shi tace wa wadanda suke wurin, "Wannan mutumin ma yana tare da Yesu Banazare." 72Sai yayi musun haka kuma, har da rantsuwa, yace, "Ban san mutumin nan ba."73Bayan dan lokaci kadan wadanda suke a tsaye suka zo wurin Bitrus suka ce masa, "Hakika kai daya daga cikin su ne, gama harshen ka ya tonaka." 74Sai ya fara rantsuwa irin ta la'ana, yana cewa, "Ban san wannan mutumin ba," nan da nan zakara yayi cara. 75Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya fada, "Kafin carar zakara zaka yi musun sani na sau uku." Sai ya fita waje yayi kuka mai zafi."
Wannan ne farkon sabon sashin labari da ke faɗa labarin gicciyen Yesu, mutuwarsa, da kuma tashinsa. Anan ya gaya wa almajiransa yadda zai sha wahala ya kuma mutu.
"Bayan" ko "Sai, bayan." Wannan jumla ya canza labarin daga koyarwar Yesu zuwa abin da ya faru.
Wannan ya na nufin duk abin da Yesu ya koyar daga 24:3.
AT: "waɗansu mazaje za su kai Ɗan Mutum zawa wurin wasu mutanen da za su gicciye shi"
Yesu ya na maganar kansa a cikin mutum na uku.
Waɗannan ayoyin sun ba da tushin bayani game da shirin shugabannin Yahudawa don su kama Yesu su kuma ƙashe shi.
AT: "suka haɗu"
"Yesu a ɓoye"
Ana iya sa a bayyane abin da shugabannin ba su so su yi a lokacin idin. AT: "Kada mu ƙashe Yesu a lokacin idin"
Wannan idin ketarewa ne na kowane shekara.
An yi amfani da wannan kalma anan domin a sa alama a ainahin labarin. Anan Matiyu ya fara ba da sabon labari.
Ana nufin cewa wannan ne mutumin da Yesu ya warkar daga kuturta.
"Yesu ya na ƙwanciye a gefensa." Za ku iya yin amfani da kalmar harshen ku a zaman da mutane su ke yi a loƙacin da su na cin abinci.
"mace ta zo wurin Yesu"
Wannan ƙwalba ne mai tsada da an yi shi daga dutse mai laushi.
mai da ke da kamshi mai kyau
Matan ta yi wannan don ta girmama Yesu.
Almajiran sun yi wannan tambaya don fushinsu akan ayyukan matan. AT: "Wannan matan ta yi mumunan abu ta wurin yin asaran wannan mai!"
AT: "Da ta sayar da wannan da ƙudi mai yawa a kuma ba da ƙudin"
Ana iya bayyana "talakawa." AT: "wa mutane talakawa"
Yesu ya yi wannan tambaya don ya ƙwabe almajiransa. AT: "Kaɗa ku dame wannan matan!"
"ku" na nufin almajiran.
AT: "mutane talakawa"
"Ina gaya maku gaskiyan." Wannan ya kara nanata abin da Yesu ya faɗa ne.
AT: "duk inda mutane sun yi wannan wa'azin bishara"
AT: "za su tuna da abin da wannan matan ta yi za su kuma gaya wa wasu game da ita" ko "mutane za su tuna da abin da matan ta yi za su kuma gaya wa wasu game da ita"
"don in kawo maku Yesu"
Tun da waɗannan kalmomi ɗaya ne da waɗanda su na cikin annabcin Tsohon Alkawari, bar wannan a maimakon canzawa zuwa ƙudin zamani.
"guda talatin"
"don a mika shi masu"
Wannan na da magana a cikin magana. AT: "Ya faɗa wa almajiransa cewa su je cikin gari zuwa wurin wani mutum su kuma faɗa mashi cewa Mallam ya ce masa, 'Lokaci na ya kusa. Zan ci idin ketarewa a gidanka, da almajiraina."' ko "Ya gaya wa almajiransa su je cikin gari zuwa wurin wani mutum sai su faɗa mashi cewa lokacin Mallam ya yi kusa kuma zai ci idin ketarewa a gidan wannan mutumin tare da almajiraina."
AT: 1) "lokacin da na gaya maku" ko 2) "Lokacin da Allah ya shirya mani."
AT: 1) "ya yi kusa" ko 2) "ya zo."
"ci abincin idin ketarewa" ko "yi bikin idin ketarewa ta wurin cin abinci"
Yi amfani da kalman zama da mutane a al'adan ku ke amfani da shi a lokacin cin abinci.
"Na tabbata cewa ba ni bane, ni ne, Ubangiji?" Wannan na iya nufin 1) wannan tambayar ganganci ne da shike almajiran sun tabbata cewa ba za su ba da Yesu ba. AT: "Ubangiji, Ba zan taba ba da kai ba!" ko 2) wannan tambaya ne na gaskiya tun da mai yiwuwa maganar Yesu ya dame su.
A nan "tafi" wata hanya ne na nufin mutuwa. AT: "zai tafi mutuwarsa" ko "zai mutu"
AT: "kamar yadda annabawa sun rubuto game da shi a cikin nassi"
AT: "mutumin da ya ba da Ɗan mutum"
"Mallam, ni ne zan ba da kai?" Mai yiwuwa Yahuza ya na amfani da wata tambaya ne don ya musanta cewa shi ne wadda zai ba da Yesu. AT: "Mallam, hakika ba ni zan ba da kai ba"
Wannan ƙarin magana ne da Yesu na amafini da shi kuma yana nufin "i". AT: Ka na faɗin haka" ko "Ka na amincewa da haka"
Dubi yadda kun juya waɗannan kalmomi a 14:19.
Juya "ɗauki" kamar yadda kun yi a cikin 14:19.
A nan "koko" na nufin kokon da ke da ruwan inabin a cikinta.
"ya ba wa almajiransa"
"Sha ruwan inabi daga wannan kokon"
"Gama wannan ruwan inabin jini na ne"
"jinin da ya sa alkawarin yiwuwa"
AT: "zai fito daga jikina" ko "zai fito daga jikina loƙacin da na mutu"
Wannan na kara nanaci akan abin da Yesu zai faɗa.
Wannan karin magana ne. AT: "ruwan inabi"
A nan "mulki" na nufin mulkin Allah kamar sarki. AT: "a lokacin da Ubana ya ƙafa mulkinsa a duniya"
Wannan muhimmin laƙabi ne wa Allah da ke ƙwatanta ɗangartaka da ke tsakanin Allah da Yesu.
wakar yabo ga Allah
"bar ni"
AT: "gama annabi Zakariya ya rubuto da daɗewa a cikin nassin"
A nan "zan" na nufin Allah. Ana nufin cewa Allah zai sa ko zai bar mutane su yi wa Yesu illa, su kuma ƙashe shi.
Waɗannan karin magana ne da ke nufin Yesu da almajiransa.
AT: "za su watsar da garken tumakin" ko "garken tumakin za su gudu a kowane lungu"
A nan tashi ƙarin magana ne na sa wani da ya mutu ya rayu kuma. AT: "bayan Allah ya tashe ni" ko "bayan Allah ya sa na rayu kuma"
Zakaru sun saba cara a lokacin da rana ta fito, don haka mai yiwuwa masu sauraron sun fahimci waɗannan kalmomi akan karin magana ne na fitan rana. Ko da shike, ainahin carar zakara muhimmin sashi ne a labarin nan gaba, don haka ku bar kalmar "zakara" a juyin.
kaza na miji, tsuntsun da ke kira da ƙarfi a ta lokacin da rana ta fito
Wannan sanannen kalmar nasara ce na abin da zakara ya ke yi don ya yi babban kiransa.
"za ka faɗa sau uku cewa kai ba mai bi na ba ne"
"ya yi bakin ciki sosai"
Anan "rai" ya na nufin dukkan mutum. AT: "Ina bakin ciki sosai"
Wannan karin magana ne. AT: "kuma na ji kamar zan iya mutuwa"
Ya ƙwanta da da fuska a ƙasa don ya yi addu'a.
Wannan muhimmin laƙabi ne wa Allah da ke nuna ɗangartaka sakanin Allah da Yesu.
Yesu ya na maganar aikin da dole ne ya yi, tar da mutuwa a kan gicciye, kamar ruwa mai ɗaci da Allah ya umurce ci ya sha daga kokon. Kalmar "koko" muhimmin kalma ce a cikin Tsabon Alkawari, ku yi koƙari ku yi amfani da shi a juyin ku.
A nan "koko" magana ne da na wakilcin koko da abin cikin. Abin cikin kokon magana ne na wahala da Yesu zai sha. Yesu ya na rokan Uban da cewa idan zai yiwu ma shi kada ya mutu, ya kuma sha wahala da Yesu ya san zai faru ba da juma ba.
Za a iya bayyana wannan kamar jimla. AT: "Amma kada ku yi abin da ina so; a maimako, yi abin da ku na so"
Yesu ya na magana da Bitrus, amma "ku" ɗaya ne, ya na nufin Bitrus, Yakub, da kuma Yahaya.
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya ƙwabe Bitrus, Yakub da Yahaya. AT: "Ina mamaki da cewa ba ku iya zama da ni na sa'a ɗaya ba!"
A nan ana iya bayyana "jaraba." AT: "kada wani ya jarabce ku cikin zunubi"
A nan "ruhu" magana ne da ke matsayin begen mutum ya yi abu mai kyau. "Jiki" na matsayin sha'awar jikin mutum. Yesu ya na nufin cewa almajiran za su iya samin sha'awar yin abin da Allah na so, amma bas u da ƙarfi a mutuntaka kuma su na kasawa. (Dubi: and
"Yesu ya tafi"
"idan wannan ne hanya kadai da wannan zai wuce shi ne idan na sha shi." Yesu ya yi maganar aikin da ɗole zai yi kamar ruwa ne mai ɗaci da Allah ya umurce shi ya sha.
A nan "wannan" na nufin kokon da abin da ke ciki, magana ne na wahala, kamar a cikin 26:39.
"sai dai na sha daga shi" ko "sai dai na sha daga wannan kokon wahala." Anan "shi" na nufin kokon da abin da na cikinsa, magana ne na wahala, kamar a cikin 26:39.
AT: "bari abin da ka ke so ya faru" ko "yi abin da ka na so"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "su na jin barci"
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya ƙwabe almajiransa don yin barci. AT: "Ina mamaki da cewa har yanzu ku na barci da kuma hutawa!"
Wannan ƙarin magana ne. AT: "lokaci ya kai"
AT: "wani ya na bada Ɗan Mutum"
A nan "hannu" na nufin iko ko mulki. AT: "bada ga ikon masu zunubi" ko "bada domin masu zunubi su sami iko akansa"
"kasa kunne game da abin da zan gaya maku"
"Sa'adda Yesu ya na magana"
babban itce mai ƙarfi na buga mutane
A nan an yi amfani da "Yanzu" don a sa alama a ainahin labarin. Anan Matthew ya ba da tushen bayani game da Yahuza da kuma alama da ya shirya ya yi amfani don ya bada Yesu.
AT: "cewa duk wanda ya sumbuta shi ne wadda za su kama."
"Wanda na sumbata" ko "Mutumin da na sumbata"
Wannan amintacen hanya ne na gai da Mallam.
"Yahuza ya zo wurin Yesu"
"same shi da sumbata." Abokai masu hali za su sumbace juna a tsaurin ido, amma mai yiwuwa almajira zai sumbace mallaminsa a hannu don ya nuna ladabi. Ba bu wadda da ya san yadda Yahuza ya sumbace Yesu.
A nan "su" na nufin mutane masu takubba da kulake du su ka zo tare da Yahuza da shugabanin Yahudawa.
"riƙe Yesu, kuma kama shi"
Kalmar "Nan take" na sa mu ba da hankali akan bayani mai mamaki da ke biye.
Kalmar "takobi" magana ne na ƙashe wani da takobi. Ana iya sa a bayyane bayanin. AT: "wanda na ɗaukan takobi don ya ƙashe waɗansu" ko "wadda ya na so ya ƙashe waɗansu mutane"
"takobi za su mutu ta wurin takobin" ko "takobi-takobin ne wani zai ƙashe su"
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya tunawa mutumin da ke da takobin cewa Yesu zai iya hana waɗanda suke kama shi. AT: "Hakika ka san cewa zan iya kiran ... mala'uku"
A nan "ka" na nufin mutum mai takobin.
Kalmar "runduna" kalmace soja da ke nufin taron sojoji kusan dubu shida. Yesu na nufin cewa Allah zai turo da mala'iku dayawa don su iya hana waɗanda suke kama Yesu. Ainahin lambar mala'ikun ba su da muhimminci. AT: "fiye da ainahin babban taron mala'iku goma sha biyu"
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya bayyana dalilin da ya bar waɗannan mutane su kama shi. AT: "Amma idan ba yi ba, ba zan iya cika abin da Allah ya fada cewa dole ya faru a cikin nassi"
Yesu ya na amfani da wannan tambaya domin ya nuna mumunan ayukan masu kama shi. AT: "Kun san cewa ni ba mai fashi ba ne, ba daidai ba ne ku zo mani da takubba da kulake"
A nan nufin cewa Yesu ba ya cikin ainahin haikalin. Ya na ta farfajiyar haikalin.
AT: "Zan cika dukka abin da annabawa sun rubuto a cikin nassi"
Idan harshen ku na da kalma da na nufin sun bar shi a lokacin da ya kamata su kasance tare da shi, ku yi amfani da shi anan.
"Bitrus ya bi Yesu"
filli ne kusa da gidan babban firist
"Bitrus ya shiga ciki"
A nan "su" na nufin babban firistoci da membobin majalisa.
"iya samin dalilin ƙashe shi"
"maza biyu suka zo gaba" ko "shaiɗu biyu suka zo gaba"
Idan harshenku ba ta yarda da magana a cikin magana ba, za ku iya sake rubuta shi kamar magana ɗaya. AT: "Wannan mutum yace zai iya rushe ... kwanaki.'
"Wannan mutum Yesu ya ce"
"cikin kwana uku," kafin rana ta sauka sau uku, ba "bayan kwana uku ba," bayan rana ta sauka sau uku
Babban firist din ba ya tambayan Yesu game da abin da shaiɗun sun ce. Ya na tambayar Yesu don ya nuna cewa abin da shaidun sun ce ba daidai ba ne. AT: "Menene amsar ka game da abin da shaidun su na faɗa akanka?"
Wannan muhimmin laƙabi ne wa Allah da na ƙwatanta ɗangartaka sakanin Almasihu da Allah.
A nan "rai" na bambanta Allahn Isra'ila da allolin karya da gunki da mutane suke bauta. Allahn Isra'ila ne kadai na da rai kuma na da ikon aikatu. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 16:16.
Yesu ya na magana da babban firist da kuma sauran mutane a wurin.
AT: 1) jimlar "daga yanzu" magana ne da na nufin za su gan Ɗan Mutum a cikin ikonsa a wani lokaci gaba. ko 2) jumlar "daga yanzu" na nufin cewa daga lokacin shari'ar Yesu kuma nan gaba, Yesu ya na nuna kansa cewa shi ne Mai Ceto wadda na da iko da cin nasara.
A nan "Iko" magana ne da na wakilcin Allah. Zama a "hannun damar Allah" alama ne na karban babban daraja da iko daga Allah. AT: "a zaune a wurin daraja a gefen Allah mai iko dukka"
"zuwa duniya akan gizagizai na sama"
Yage tufafi alama ne na fushi da bakin ciki.
Dalilin da babban firist din ya kira maganar Yesu sabo shi ne wata kila ya fahimci kalmomin Yesu a cikin 26:64 da cewa shi daidai ne da Allah.
Babban firist ya yi amfani da wannan tambaya domin yă nanata cewa shi da membobin majalisa ba sau so su ji daga wasu shaiɗu. AT: "Ba mu so mu ji daga wani shaiɗu kuma ba!"
A nan "ku" na nufin mutanen majalisa.
AT: 1) Sai wasu mazajen" ko 2) "Sai sojojin."
An yi wannan kamar zagi ne.
A nan "yi mana anabci" na nufin faɗan ikon Allah. Ba ya nufin faɗan abin da zai faru a gaba.
Waɗanda suka buga Yesu ba su san cewa shi ne Almasihu ba. Sun kira shi haka don su yi masa ba'a.
Bitrus ya iya gane abin da yarinya baiwan ta na faɗa. Ya yi amfani da wannan kalmomi don ya musanta cewa ya na tare da Yesu.
"Loƙacin da Bitrus ya fita"
hanya a katangar farfajiyar
"faɗa wa mutanen da su na zaune a wurin"
"ya musanta kuma ta rantsuwa, 'Ban san mutumin ba!'"
"ɗaya daga cikin waɗanda suke tare da Yesu"
AT: "Za mu iya ce kai daga Galili domin ya na magan kamar ɗan Galili"
"ya kira rantsuwa a kansa"
Zakara tsuntsu ne da na kira da ƙarfi a lokacin da rana ta fito. A na kiran karan da zakara na yi "carar." Dubi yadda kun juya wannan a cikin 26:34.
AT: "Bitrus ya tuna cewa Yesu ya faɗa ma shi cewa kafin zakara ya yi cara, zai musanta shi sau uku"
1Da gari ya waye, duk manyan firistoci da dattawan jama'a suka shirya yadda zasu kulla makirci domin su kashe shi. 2Suka daure shi, suka mika shi ga gwamna Bilatus.3Sa'adda Yahuza, wanda ya bashe shi, ya ga an zartarwa Yesu hukuncin kisa, ya nemi tuba ya kuma mayar da azurfar talatin ga manyan firistocin da dattawan, 4yace, "Na yi zunubi ta wurin cin amanar mara laifi." Amma sukace, "Ina ruwan mu? Ka ji da shi da kanka?" 5Sai ya jefar da kwandalolin azurfar a kasa cikin haikalin ya kuma bar su, ya tafi ya rataye kansa.6Sai babban firist ya dauki kwandalolin azurfar ya ce, "Ba daidai bane bisa ga shari'a musa wannan cikin ma'aji, saboda kudin jini ne." 7Sai suka tattauna al'amarin a tsakanin su, kudin kuma suka sayi filin maginin tukwane domin makabatar baki. 8Dalilin wannan ne ake kiran wurin, "Filin jini" har yau.9Sai abin da aka fada ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa, "Suka dauki tsabar azurfa talatin na farashin da mutanen Isra'ila suka sa a kansa, 10suka bayar domin sayen filin mai tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni."11Sai Yesu ya tsaya a gaban gwamna, gwamna ya kuma tambaye shi, "Kai sarkin Yahudawa ne?" Yesu ya amsa, "Haka ka fada." 12Amma da manyan firistocin da dattawan suka zarge shi, bai ce komai ba. 13Sai Bilatus yace masa, "Baka ji dukan zarge-zargen da ake yi maka ba?" 14Amma bai ce masa ko kalma guda ba, sai gwamna yayi matukar mamaki.15To lokacin bikin idi, al'adar gwamna ne ya saki mutum guda wanda jama'a suka zaba. 16A wannan lokacin suna da wani sanannen dan kurkuku mai suna Barabbas.17To da suka tattaru, sai Bilatus yace masu, "Wa kuke so a sakar maku? Barabbas, ko Yesu wanda ake kira Almasihu?" 18Saboda ya san sun kawo shi ne domin kishi. 19Da yake zaune a kujerar shari'a, matarsa ta aika masa cewa, "Ka fita sha'anin mutumin nan marar laifi. Saboda na sha wahala sosai a yau cikin mafarki saboda shi."20A lokacin nan manyan firistoci da dattawa suka rinjayi ra'ayin jama'a suce a sakar masu da Barabbas, a kashe Yesu. 21Sai gwamna ya tambayesu, "Wa kuke so a sakar maku?" Sukace, "Barabbas." 22Bilatus yace masu, "Me zan yi da Yesu wanda ake kira Almasihu?" Sai duka suka amsa, "A gicciye shi."23Sai yace, "Don me, wane laifi ya aikata?" Amma suka amsa da babbar murya, "A gicciye shi" 24Amma da Bilatus ya ga ba zai iya komai ba don hargitsi zai iya barkewa, ya dauki ruwa ya wanke hannuwansa a gaban jama'a, yace, "Ba ni da laifi ga jinin mutumin nan marar laifi. Ku yi abin da kuka ga dama."25Duka mutanen sukace, "Bari jininsa ya kasance a kan mu da 'ya'yan mu." 26Sai ya sakar masu da Barabbas amma yayi wa Yesu bulala ya mika shi garesu domin su gicciye shi.27Sai sojojin gwamna suka dauki Yesu zuwa farfajiya suka kuma tara dukan rundunar sojoji. 28Suka yi masa tumbur sa'annan suka sa masa jar alkyabba. 29Sai suka yi masa rawanin kaya suka sa a kansa, suka kuma bashi sanda a hannunsa na dama. Suka rusuna a gabansa suna masa ba'a, suna cewa, "Ranka ya dade, Sarkin Yahudawa!"30Suka kuma tofa masa yawu, suka kwace sandar suka buga masa a ka. 31Bayan sun gama masa ba'a, suka cire masa alkyabbar suka sa masa kayansa, suka jagorance shi zuwa wurin da za a gicciye shi.32Da suka fito waje, sai suka iske wani Bakurame mai suna Saminu, wanda suka tilasta ya tafi tare dasu domin ya dauki gicciyen. 33Suka iso wani wuri da ake kira Golgotta, wanda ke nufin,"Wurin kwalluwa." 34Suka bashi ruwan inabi da aka gauraya da wani abu mai daci. Amma da ya 'dan-'dana shi sai ya ki sha.35Bayan da suka gicciye shi, suka kada kuri'a a kan rigarsa. 36Suka kuma zauna suna kallonsa. 37A sama da kansa suka sa abinda ake tuhumarsa da ita a rubuce, "Wannan shine sarkin Yahudawa."38An gicciye shi da 'yanfashi guda biyu, daya ta damansa dayan kuma ta hagunsa. 39Wadanda suke wucewa suna zaginsa, suna girgiza kai, 40suna kuma cewa, "Kai da kace zaka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku, ka ceci kanka mana! In dai kai Dan Allah ne, ka sauko daga gicciyen!"41Ta haka ma manyan firistocin suka rika yi masa ba'a, tare da marubuta da shugabannin, suna cewa, 42"Ya ceci wasu amma ya kasa ceton kansa. Shi ne sarkin Isra'ila. Ya sauko mana daga kan gicciyen, sai mu ba da gaskiya gareshi.43Tun da ya yarda da Allah. Bari Allahn ya cece shi mana, saboda yace, "Ni dan Allah ne." 44Hakan nan ma 'yanfashin guda biyu da aka gicciye su tare suka zage shi.45To tun da tsakar rana sai duhu ya rufe kasar gaba daya har karfe uku na yamma. 46Wajen karfe uku, Yesu ya tada murya mai karfi yace, "Eli, Eli lama sabaktani?" wanda ke nufin, "Allahna, Allahna, don me ka yashe ni?" 47Da wadanda suke tsaye kusa suka ji haka, sai sukace, "Yana kiran Iliya."48Nan take wani ya ruga da gudu ya dauki soso ya tsoma cikin ruwan inabi mai tsami ya soka kan sandar kara ya mika masa ya sha. 49Sai sauran sukace, "Rabu da shi mu gani ko Iliya zai zo ya cece shi." 50Sai Yesu ya ta da murya mai karfi yayi kuka sai ya saki ruhunsa.51Sai labullen haikali ya yage gida biyu daga sama zuwa kasa. Kasa kuma ta girgiza, duwatsu suka farfashe. 52Kaburbura suka bude, tsarkaka kuwa wadanda suke barci da yawa suka tashi. 53Suka fito daga kaburbura bayan tashinsa, suka shiga birni mai tsarki suka bayyana ga mutane da yawa.54Da hafsan sojan da wadanda suke kallon Yesu suka ga girgizar kasar da abinda ya faru, suka ji tsoro kwarai sukace, "Hakika wannan Dan Allah ne" 55Mata dayawa da suka bi Yesu daga Galili domin su lura da shi suka tsaya suna kallo daga nesa. 56A cikin su akwai Maryamu Magadaliya, Maryamu uwar Yesu da Yusufu, da uwar 'ya'yan Zabadi.57Da yamma sai wani attajiri mutumin Armatiya ya zo, mai suna Yusufu wanda shi ma almajirin Yesu ne. 58Ya je wurin Bilatus ya roka a bashi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a bashi.59Yusufu ya dauki jikin, ya rufe shi da likafani mai tsabta, 60sai ya sa shi a cikin sabon kabarinsa da ya sassaka cikin dutse. Sai ya mirgina babban dutse a bakin kofar kabarin ya tafi. 61Maryamu Magadaliya da dayan Maryamun suna nan zaune akasin kabarin.62Washegari, wato bayan ranar Shiri, Sai manyan firistoci da Farisawa suka taru tare da Bilatus. 63Sukace, "Mai gida, mun tuna lokacin da mayaudarin nan yake da rai, yace, "Bayan kwana uku zan tashi." 64Saboda haka, ka bada umarni a tsare kabarin na kwana uku. In ba haka ba almajiransa zasu zo su sace shi, kuma su ce wa mutane, "Ya tashi daga mattatu." Kuma yaudarar karshe zata fi ta farko muni."65Bilatus yace masu, "Ku dauki masu tsaro. Kuyi tsaro iyakar karfin ku." 66Sai suka tafi suka tsare kabarin, suka hatimce dutsen, suka sa masu tsaro.
Wannan ne farkon labarin shari'ar Yesu a gaban Bilatus.
An yi amfani da wannan kalma domin a sa alamar fashi a ainahin labarin. Anan Matiyu ya fara faɗan sabon labari.
Shugabanin Yahudawa suna shirya yadda za su iya sa shugabannin Romawa su ƙashe Yesu.
Wannan abin ya faru a bayan shari'ar Yesu a gaban majalisar shugabannin adinin Yahudawa, amma ba mu san ko ya faru kafin shari'a ko lokacin shari'ar Yesu a gaban Bilatus ba.
Idan harshenku na da wata hanyar nuna cewa an fara sabon labari, za ku so ku iya amfani da shi a nan.
AT: "cewa shugabannin Yahudawa sun hukunta Yesu"
Wannan ne ƙudin da firistoci suka ba wa Yahuza don ya bashe Yesu. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 26:15.
Wannan ƙarin magana ne da na nufin mutuwar mai mara laifi. AT: "mutumin da bai cancanci mutuwa ba"
Shugabannin Yahudawa sun yi amfani da wannan tambaya domin su nanata cewa ba su damu da abin da Yahuza ya faɗa ba. AT: "Wannan ba damuwar mu bane!" ko "Wannan damuwar ku ne!"
AT: 1) ya jefar da kandalolin azurfar a cikin farfajiyar haikalin, ko 2) ya na tsaye a cikin farfajiyar haikalin, sai ya jefar da kwandalolin azurfar a cikin haikalin.
"Shari'ar mu ba ta yarda mana mu sa wannan"
"sa wannan azurfa"
Wannan ne wurin da sun ajiye ƙudin ne da suke amfani da shi don su tanada abubuwan da ake bukata a haikali da kuma firistoci.
Wannan karin magana ne da na nufin ƙudin da an biya mutumin da ya taimaka a ƙashen wani. AT: "ƙudin da an biya don mutum yă mutu"
Wannan fili ne da aka saya domin a binne baki da suka mutu a cikin Urushalima.
AT: "mutane suke kiran wannan filin"
Wannan na nufin har lokacin da Matiyu ya na rubuta wannan littafi.
AT: "Wannan ya cika abin da annabi Irimiya ya faɗa"
AT: "farashin da mutanen Isra'ila suka sa a kansa"
Wannan na nufin waɗanda su na cikin mutanen Isra'ila wadda sun biya don a ƙashe Yesu. AT: "waɗansu mutanen Isra'ila" ko "shugabanin Isra'ila"
A nan "ni" na nufin Irmiya.
"Bilatus"
Wannan na iya nufin 1) ta wurin faɗin haka, Yesu ya na nufin cewa shi ne Sarkin Yahudawa. AT : "I, kamar yadda ka faɗa, haka ne" ko "I, haka ne yadda ka ce" ko 2) ta faɗin haka, Yesu ya na faɗin cewa Bilatus, ba Yesu ba, ne na kiran sa Sarkin Yahudawa. AT: "Kai da kanka ne ka faɗi haka"
AT: "Amma lokacin da manyan firistocin da dattawan suka zarge shi"
Bilatus ya yi wannan tambaya domin ya na mamaki da yadda Yesu ya yi shiru. AT: "Ina mamakin cewa ba ka amsa waɗannan mutanen da sun yi zargin ka da yin abubuwan da ba daidai ba!"
"bai ce ko kalma ɗaya ba; wannan ya ba wa gwamna mamaki sosai." Wannan wata hanyar nanaci ne na faɗa cewa Yesu ya yi shiru.
Wannan ne bikin idin ketarewa.
AT: "ɗan kurkuku wadda jama'a za su zaba"
"akwai wani sanannen ɗan kurkuku"
sananne a yin mugun abu
AT: "taron sun tattaru"
AT: "wanda wasu mutane ke kira Almasihu"
"shugabannin Yahudawa sun kawo masa Yesu." Sun yi wannan domin Bilatus ya hukunta Yesu.
"Da Bilatus yake zaune"
"zaune a kujerar mai shari'a." Wannan ne wurin da mai shari'a zai zauna a yayin da ya na yanke hukunci.
" aika sako"
"na damu sosai yau"
An yi amfani da "yanzu" a nan don a sa alama a ainahin labarin. Matiyu ya ba da tushen bayani game da dalilin da ya sa taron suka zabi Barabbas.
AT: "sa sojojin Romawa su ƙashe Yesu"
"tambaye taron"
AT: "wanda waɗansu mutane suke kira Almasihu"
"Yesu ya aikata"
"taron suka amsa da babbar murya"
Bilatus ya yi wannan domin ya nuna cewa ba shi da hakin mutuwar Yesu.
A nan "jini" na nufin mutuwar wani. AT: "mattatu"
"wannan hakinku ne"
A nan "jini" magana ne da na matsayin mutuwar mutum. Jumlar "kasance a kan mu da 'ya'yan mu" ƙarin magana ne da na nufin cewa sun amince da hakin abin da na faruwa. AT: "I! Mu da zuriyarmu mun ɗauki hakin zartadda shi"
"Sai Bilatus ya sakar masu da Barabbas"
Ana nufin cewa Bilatus ya umurci sojojin don su bulali Yesu. Mika Yesu domin a gicciye shi ƙarin magana ne na sa sojojinsa su gicciye Yesu. AT: "ya umurci sojojinsa don su bulali Yesu su kuma gicciye shi" (Dubi: and )
"bulali Yesu"
"taron sojoji"
"cire tufafinsa"
jar walƙiya
"rawanin da an yi daga reshen kaya" ko "rawanin da an yi daga reshe masu kaya"
Sun ba Yesu sanda ya rike don ya wakilci sandar sarauta da sarki ke rikewa. Sun yi haka don su yi wa Yesu ba'a.
Su na faɗa haka domin su yi wa Yesu ba'a. Su na kiran Yesu Sarkin Yahudawa," amma ba su gaskanta cewa shi sarki ba ne. Kuma abin da suna faɗa gaskiya ne.
"Mun girmamaka" ko "Bari ka yi rayuwar tsawon lokaci"
"da yawunsu, sojojin suka tofa wa Yesu yawu"
Wannan na nufin Yesu da sojojin sun fita daga garin. AT: "Sa'adda suka fito daga Urushalima"
"sojojin sun gan wani mutum"
"wanda sojojin suka tilasta ya tafi tare dasu domin ya ɗauki gicciyen Yesu"
AT: "wuri da mutane na kira Golgotta"
AT: "shi ruwan inabi da suka gauraya da wani abu mai ɗaci"
ruwan 'yarani mai ɗaci da jiki na amfani da shi a narkewar abinci
Waɗannan tufafi ne da Yesu na sakawa.
"rubutaccen bayani na dalilin da aka gacciye shi"
AT: "Sojojin suka gicciye 'yan fashi biyu tare da Yesu"
Sun yi haka ne don su yi wa Yesu ba'a.
Ba su gaskanta cewa Yesu Ɗan Allah ba ne, sun so ya nuna har idan gaskiya ne. AT: "Idan kai ne Ɗan Allah, ka nuna ta wurin saukowa daga gicciyen"
Wannan muhimmin laƙabi ne wa Almasihu da ke nuna ɗangartakarsa da Allah.
AT: ) Shugabannin Yahudawa ba su gaskanta cewa Yesu ya ceci wasu ba ko ma zai iya ceton kansa ba, ko 2) sun gaskanta cewa ya ceci wasu amma suna dariyarsa domin bai iya ceton kansa yanzu ba.
Shugabannin na yi wa Yesu ba'a. Sun kira shi "Sarkin Isra'ila," amma ba su gaskanta cewa shi sarki ba ne. AT: "Ya faɗa cewa shi ne Sarkin Isra'ila"
AT: "Don Yesu ya faɗa cewa shi ne Ɗan Allah."
Ɗan Allah Wannan muhimmin laƙabi ne wa Yesu da ke ƙwatanta dangartakarsa da Allah.
AT: "'yan fashin da sojojin suka gicciye su tare da Yesu"
"daga rana ... na sa'a uku" ko "daga ƙarfe sha biyu na tsakar dare ... sai ƙarfe uku na rana"
Kalmar "duhu" mai zuzzurfar ma'ana ne. AT:
"Yesu ya yi ihu"
Waɗannan ne kalmomin da Yesu ya yi kira a cikin harshensa. Masu juyi su na kan bar waɗannan kalmomin a yadda suke.
AT: 1) ɗaya daga cikin sojojin ko 2) ɗaya daga cikin masu kallo.
Wannan wani abu ne da ake samunta a teku, ana kuma amfani da shi don a daga a kuma riƙe abu ruwa-ruwa. Ana iya matse waɗannan abubuwa ruwa-ruwan.
"mika wa Yesu"
A nan "ruhu" na nufin abin da na ba da rai wa mutum. Wannan jimlar wata hanya ne na cewa Yesu ya mutu. AT: "ya mutu, ya ba da ruhunsa wa Allah" ko "ya ja numfashinsa na ƙarshe"
Kalmar "gashi" anan ya shiryamu mu ne mu ba da hankali ga bayani na mamaki da na biye.
AT: "labullen haikali ya yage gida biyu" ko "Allah ya sa labullen haikali ya yage gida biyu"
AT: "Allah ya buɗe kaburburan ya tashi da tsarkakun mutane dayawa da suka mutu"
Tashi anan ƙarin magana ne na sa mutum da ya mutu ya kuma rayu. AT: "Allah ya sa rai a tsarkakun mutane da suka yi barci"
Wannan wata hanya ce na ce mutuwa. AT: "mutu"
Jerin abubuwa da suka faru ba su a bayane. Bayan girgizan ƙasa a lokacin da Yesu ya mutu kaburbura kuma suka buɗe 1) tsarkakun mutanen suka rayu kuma, sai kuma, Yesu ya rayu kuma, tsarkakun mutanen suka shiga Urushalima, inda mutane dayawa suka gan su, ko 2) Yesu ya rayu kuma, sai kuma tsarkakun sun rayu, sun kuma shiga cikin garin, inda mutane dayawa sun gan su.
"waɗanda suke tsaron Yesu." Wannan na nufin sojojin da ke tsaron Yesu tare da jarumin. AT: "sojojin tare da shi wanda suke tsaron Yesu"
"mahaifiyar Yakub da Yahaya" ko "matar Zabadi"
Wannan sunan wata gari ne a Isra'ila.
AT: " Sai Bilatus ya umarci sojojin su ba wa Yusufu jikin Yesu"
tufafi mai kyau da kuma tsada
Ana nufin cewa Yusufu na da ma'aikata da sun yanka kabarin a cikin dutsen.
Mai yiwuwa Yusufu na da waɗansu mutane a wurin da sun taimake shi mirgina dutsen.
"a ƙetare daga kabarin"
Wannan rana ce da mutane na sa komai a shirye domin Asabar.
"sadu da Bilatus"
"lokacin da Yesu, mayaudarin, yake da rai"
Wannan na da magana a cikin magana. AT: "ya ce bayan kwana uku zai tashi kuma."
AT: "umurce sojojinka su tsare kabarin"
"almajiransa zasu iya zuwa su sace jikin shi"
AT: "almajiransa zasu iya ... ce wa mutane ya tashi daga mattatu, kuma"
Daga dukka waɗanda sun mutu. Wannan magana ya nuna dukka mattatu a cikin duniya. Tashi daga sakaninsu na nufin zama rayeyye kuma.
AT: "kuma idan sun yaudare mutane ta faɗa cewa, zai zama da muni fiye da yadda ya yaudare mutane a da lokacin da ya ce shi ne Almasihu"
Wannan ya ƙunshi sojoji huɗu zuwa sha shida na Romawa.
Wannan na iya nufin 1) suka sa igiya a kewaye da dutsen sun kuma haɗa shi da bangon dutsen a dukka gafen kofan kabarin ko 2) sun sa hatimi a sakanin dutsen da bangon.
"gayawa sojojin su tsaya a inda za su iya hana mutane daga yin karambani da kabari"
1Da daddare ranar Asabaci, rana ta fari ga mako ta fara gabatowa, Maryamu Magadaliya da daya Maryamun suka zo don su ziyarci kabarin. 2Sai aka yi girgizar kasa mai karfi, saboda mala'ikan Ubangiji ya sauko daga sama ya kuma murgine dutsen ya zauna a kai.3Kamanninsa kamar walkiya, tufafinsa kuma fari fat kamar suno. 4Masu tsaron suka razana don tsoro suka zama kamar matattun mutane.5Mala'ikan ya yi wa matan magana cewa, "Kada ku ji tsoro, nasan kuna neman Yesu wanda aka gicciye. 6Baya nan, amma ya tashi kamar yadda ya fada. Ku zo ku ga wurin da aka kwantar da shi. 7Ku hanzarta ku gaya wa almajiransa, 'Ya tashi daga matattu. Duba, ya tafi Galili, can zaku same shi.' Gashi ni kuwa na fada maku."8Matan suka yi hanzari suka bar kabarin da tsoro da murna, suka ruga domin su sanar wa almajiransa. 9Sai ga Yesu ya tare su, yace masu, "A gaishe ku." Sai matan suka kama kafar sa, suka kuma yi masa sujada. 10Sai Yesu yace masu, "Kada ku ji tsoro. Ku je ku fada wa 'yan'uwana su je Galili. Can zasu ganni."11Sa'adda matan suke tafiya, sai wadansu masu tsaro suka shiga gari suka fada wa Shugabanin Firistoci dukan abin da ya faru. 12Firistocin suka hadu da dattawa suka tattauna al'amarin, sai suka bada kudi masu yawa ga sojojin 13Sukace masu, "Ku gaya wa sauran cewa, "Almajiran Yesu sun zo da daddare sun sace gangar jikinsa lokacin da muke barci."14Idan wannan rahoto ya isa wurin gwamna, za mu lallashe shi mu ja hankalinsa mu raba ku da damuwa." 15Sai sojojin suka karbi kudin suka yi abinda aka umarcesu. Wannan rahoto ya bazu a tsakanin Yahudawa, ya ci gaba har zuwa yau.16Amma almajiran sha daya suka tafi Galili, kan dutsen da Yesu ya umarcesu. 17Da suka gan shi, suka yi masa sujada, amma wadansu suka yi shakka.18Yesu ya zo wurin su ya yi masu magana, yace, "Dukan iko dake sama da kasa an ba ni. 19Sai kuje ku almajirantar da dukan al'ummai. Kuna yi masu baftisma cikin sunan Uba da na Da da na Ruhu Mai Tsarki.20Ku koya masu su kiyaye dukan abin da na umarce ku. Duba, ni kuma kullum ina tare da ku har karshen zamani."
Wannan ya fara labarin tashiwar Yesu daga matattu.
"Da Asabar ya wuce, daidai haurowar rana da safe ran Lahadi"
An yi amfani da wannan kalma anan ne don a sa alama a ainahin labarin. Anan Matiyu ya fara maganar wata sabuwar sashin labarin kenan.
"ɗayan matan mai suna Maryamu." Wannan Maryamu uwar Yakubu da Yusufu. (Dubi: [Matthew 27:56])
Kalmar "ku ga" a nan yana sa mu mu sa hankali ne ga bayanin ban mamaki da ke biye. Harshenku na iya samun wata hanyar yin haka.
AT: 1) girgizan kasan ya faru domin mala'ikan ya sauko ya kuma murgine dutsen ko 2) dukka abubuwannan ya faru a lokaci ɗaya.
wata girgizan ƙasa mai ƙarfi
"Bayanuwar mala'ikan"
Wannan magana ne da ke nanata yadda hasken kamannin mala'ikan yake. AT: "na da haske kamar walkiya"
Wannan magana ne da ke nanata yadda tufafin mala'ikan yake da fari da kuma haske. AT: "tufafinsa fari ne sosai, kamar suno"
Wannan magana ne da ke nufin cewa sojojin sun faɗi kuma ba su motsa ba. AT: "sun faɗi a ƙasa sun kuma kwanta kamar matattun mutane"
"Maryamu Magadaliya da kuma wata mata mai suna Maryamu"
AT: "wanda mutane da sojoji suka gicciye" ko "wanda suka gicciye"
Wannan magana ne a cikin magana. AT: "gaya wa almajiransa cewa ya tashi daga matattu kuma Yesu ya tafi Galili inda za ku gan shi."
"Ya rayu kuma"
Daga cikin dukka waɗanda sun mutu. Wannan magana ya kwatanta dukka matattu a cikin karkashin duniya. Tashi a cikinsu na nufin rayuwa kuma.
A nan "ku" ɗaya. Ya na nufin matan da almajiran.
Anan "ku" na nufin matan.
Wannan gaisuwa ne irin ta yau da kullum, kamar "barka" a turanci.
"durkusa da gwiwarsu suka kuma kama kafarsa"
Wannan na nufin almajiran Yesu.
"daidaita shiri a sakaninsu." Firistoci da dattawa sun yarda su ba sojoji kuɗin.
AT: "Gaya wa waɗansu cewa almajiran Yesu sun zo ... lokacin da kuke barci"
"Idan gwamna ya ji cewa kuna barci ne lokacin da almajiran Yesu sun ɗauke jikinsa"
"Bilatus" 27:2
"kad ku damu. Za mu ɗauke shi don ka da ya hukunta ku."
AT: "yi abin da firistoci sun ce masu su yi"
"Yahudawa dayawa sun ji wannan rahoto sun kuma cigaba da faɗa wa waɗansu har zuwa yau"
Wannan na nufin lokacin da Matthew ya rubuto littafin.
AT: 1) sukka yi wa Yesu sujada ko da shike waɗansu sun yi shakka, ko 2) waɗansu sun yi wa Yesu sujada, amma waɗansu ba su yi masa sujada ba domin sun yi shakka.
Ana iya bayyana abin da almajiran sun yi shakka. AT: "waɗansu sun yi shakka cewa shi ne Yesu kuma wai ya rayu kuma"
AT: "Ubana ya ba ni dukkan iko"
An yi amfani da "sama" da "ƙasa" anan don a bayyana kowa da komai a cikin sama da ƙasa.
A nan "al'ummai" na nufin mutane. AT: "na dukkan mutanen duniya"
A nan "suna" ya na nufin iko. AT: "ta wurin ikon"
Waɗannan muhimmin laƙabi ne da ke kwatanta ɗangantaka sakanin Allah da Yesu.
"Duba" ko "ji" ko "ba da hankulanku ga abin da zan gaya maku"
"sai ƙarshen zamani" ko "sai ƙarshen duniya"
1Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah. 2kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya. 3Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.4Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai. 5Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu. 6Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.7Yana wa'azi, ya ce "akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba. 8Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki".9Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun. 10Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya. 11Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, "Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai".12Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji. 13Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.14Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah. 15Yana cewa, "Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara".16Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne. 17Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane". 18Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.19Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa. 20Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.21Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu. 22Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.23A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi. 24Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah". 25Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, "Ka yi shiru ka fita daga cikinsa". 26Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.27Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!" 28Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.29Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya. 30Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita. 31Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.32Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu. 33Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa. 34ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.35Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua. 36Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi. 37Suka sa me shi, sai su ka ce masa, "kowa yana nemanka".38Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan". 39Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.40Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, "in ka yarda kana iya warkar da ni. 41Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa "Na yarda. Ka sarkaka". 42Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.43Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi. 44Ya ce masa "ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.45Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.
littafin Markus ta fara the anabcin annabi Ishaya game da zuwan Yahaya mai baftisma, wanda ya yi wa Yesu baftisma.
Wannan laƙani ne mai mahimanci na Yesu.
Wannan karin magana ce wanda ke nufin "a gabanku"
A nan, kalman nan "ka"
Wannan na nufin mai sakon.
Yin haka na nufin shirya mutane domin zuwan Ubangiji. AT: "zai shirya mutanen domin zuwanka"
Wannan za a iya bayyanata a jimla kamar haka. AT: "an ji muryar wani na kira a jeji" ko kuwa "Sun ji karar wani na kira a jeji"
wadannan maganganu suna nufin abu daya ne.
"sa hanyar Ubangiji ta shiryu." yin haka na madadin yin shiri domin sakon Ubangiji in ta zo. mutane na yi haka tawurin tuba daga zunubansu. AT: "shirya domin sakon Ubangiji a sa'ada ta zo" ko kuwa "Tuba da kuma shiri domin zuwan ubangiji"
Ku tabbatar cewa masu karatu sun fahimci cewa Yahaya ne mai saƙon da anabi Ishaya ya yi maganarsa a ayan da ta rigaya.
Kalmomin nan "dukan kasar" misalin ne ta mutanen da ke zama a kasar da kuma wanda ake nufin mafi yawan mutane, ba kowane mutum ba. AT: "Mutane daga Yahudiya da Urushelima"
Sun yi wannan a lokaci ɗaya be. An yi wa mutanen baftisma domin sun tuba daga zunubansu. AT: A sa'ada suka tuba da zunubansu, Yahaya ya yi musu baftisma a Kogin Urdun"
Fara da zuma irin abinci biyu ne da Yahaya saba ci a sa'anda ya ke jeji. Wannan bai nuna cewa Yahaya ya cin waɗannan abinci a sa'ada yana yi wa mutanen baftisma ba.
"Yahaya ya shaida"
Yahaya ya kwatanta kansa da bawa don ya nuna yadda girman Yesu yake. AT: "ban isa in kaskantarciyar aikin cire takalminsa ba" (Dubi: )
A lwancan oƙacin da Yesu ke cikin duniya, mutane sun cika sa takalma wanda aka yi da fata suna kuma ɗaure ƙafafunsu da igiyar fata.
"sunƙuya"
Wannan na kwatanta baftisman Yahaya da ruwa da kuma baftisma mai zuwan nan gaba da Ruhu Mai Tsarki. Wannan na nufin cewa baftisman Yahaya alama ce ta share zunuban mutane. Baftisma ta wurin Ruhu Mai Tsarki lallai zai wanke mutane daga zunubansu. In ya yiwu, yi amfani da kalma ɗaya ta "baftisma" anan kamar yadda kun yi amfani da shi ga "Yahaya mai baftisma" don kwatanci tsakanin biyun.
Wannan alama ce na farkon wani abu da ya faru a labarin.
AT: "Yahaya ya yi masa baftisma"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) wannan wa salon magana ne, wato Ruhun ya sako bisa Yesu kamar tsuntsu dake saukowa daga sarari zuwa kasa ko kuwa 2) Ruhun daidai kamar kurciya ya sauko bisa Yesu.
Wannan na wakilcin Allah na magana. Wani loƙaci mutane na ƙin kiran sunan Allah domin suna girmama shi. AT: "Allah ya yi magana daga sama"
Wannan lakabi ne mai muhimmanci na Yesu. Uban ya kira Yesu "ƙaunatacciyar ɗa" sa saboda madawammiyar ƙaunarsa gare shi.
Bayan Baftisman Yesu, yana cikin jeje kwanaki arba'in, ya kuma tafi Galilee don ya koyar ya kuma kira almajiransa.
"tilasta Yesu ya fita zuwa"
"Ya zauna a jeji"
"kwanaki 40"
"Yana tsakanin"
"bayan an sa Yahaya a kurkuku." AT: "bayan su kama Yahaya"
"gayawa mutane da yawa game da bisharar"
"Yanzu ne lokacin"
"Lokaci ya kusa da Allah zai fara mulki mutanensa"
"Yesu ya ga Siman da Andarawas"
A nan iya bayyana ma'anar wannan magana a fili. AT: "jefa taru cikin ruwa don su kama kifi"
"Ku bi ni" ko kuwa "Ku zo tare da ni"
Wannan na nufin cewa Siman Andarawas za su koya wa mutane gaskiyar saƙon Allah don wasu ma su bi Yesu. AT: "Zan koya muku yadda za ku tara mutane zuwa gare ni kamar yadda kuna tara kifi"
Ana iy tsammani cewa jirgin na Yakubu da Yahaya ne. AT: "cikin jirginsu"
"gyaran taruna"
Zai zama da taimako sosai in ab faɗa dalilin da ya sa Yesu ya kira Yakubu da Yahaya. AT: "kira su su zo gare shi"
"bayin da ke yi musu aiki"
Yakubu da Yahaya sun tafi tare da Yesu.
"shiga Kafarnahum"
Ra'ayin "koyarwa" ana iya bayana ta a fili in ana magana game da "wani wanda ke da iko" da kuma "marubutan." AT: "domin yana koyar da su kamar yadda wanda ke da ikon ke koyarwa ba kamar yadda marubutan ke koywarwa ba"
Aljanu sun yi wannan tambaya da ma'anan cewa ba bu wata dalilin da Yesu zai shiga tsakani su kuma suna so ya bar su. AT: "Yesu Banazare, ka bar mu! Babu wata dalilin da zai sa ka shiga tsakanin mu."
Ajanun sun yi wannan tambaya don su cewa Yesu kada ya yi musu lahani. AT: "Kada ka hallaka mu!"
A nan kalman nan "shi na nufin mutumin nan mai aljanin.
Aljan ne ke kuka ba mutumin ba.
Mutanen sun yi amfani da tambayoyi biyu don su nuna mamakin su. Ana iya bayana tambayoyin kamar maganar motsin rai. AT: "suka cewa juna, "wannan da mamaki! Ya bada sabuwar koyarwa kuma ya yi magana da iko! ... suka kuma yi masa biyayya!'"
Kalman nan "ya" na nufin Yesu.
Kalman nan "yanzu" na gabatar da surukuwar Siman a labarin da kuma ƙarin haske ga labari game da ita.
"sa ta ta tashi tseye" ko kuwa "ya sa ta ta iya saukowa daga gado"
Ana iya nuna wa a fili wanda ya warkar da ita. AT: " Yesu ya warkar da ita daga zazzaɓi"
Ana nufin cewa an ba su abinci. AT: "ta ba su abinci da ruwan sha"
Kalman nan "duk" zuguiguci ne da ke nanata gaggaruman lisafin mutanen da suka zo. AT: "yawanci wanda ke rashin lafiya ko kuwa masu aljan"
Kalman nan "birni" na nufin mutanen da ke birnin. A nan kalman nan "dukka" mai yiwuwa na nanata cewa yawancin mutane daga birnin sun taru. AT: "Mutane da yawa daga birnin sun taru a bakin ƙofar"
"wurin da zai iya zama shi kaɗai"
A nan "shi" na nufin Siman. Waɗanda suke tare da shi kuma sune Andarawas, Yakub, Yahaya, mayiwuwa da wasu mutane.
Kalman nan "kowa" zuguiguci ne da ke nanata cewa mutane da yawa suna neman Yesu. AT: "Mutane da yawa suna neman ka"
"Ya kamata mu je wasu wurare." A nan Yesu ya yi amfani da kalman nan "mu" don yana nufin kansa da kuma Siman, Andarawas, Yakub da Yahaya.
Kalman nan "gama dukkan" zuguiguci ne aka yi amfani da ita don a nanata cewa Yesu ya tafi wurare da yawa lokacin da yake aikinsa. AT: "Ya tafi wurare da yawa a ƙasar Galili"
"Wani kuturu ya zo wurin Yesu, ya durƙusa yana roƙon Yesu yana cewa"
Cikin jimla ta farko, kalman nan "a tsarkake ni", an fahimce ta saboda jimla ta biyu ne. AT: "In ka yarda ka tsarkake ni, to, za ka iya tsarkake ni"
"so" ko kuwa "muradi"
A lokacin littafi Mai Tsarki, mutum da ke da wani cuta da ta shafi fata, ana dubansa mara tsarki, sai ya warke gabakiɗaya . AT: "za ka iya warkar da ni"
A nan kalman nan "ya yi" na nufin a ji tausayi game da bukatan wani. AT: "Da tausayi domin sa, Yesu" ko kuwa "Yesu ya ji tausayi domin mutumin, sai ya"
Zai yi taimako in an ambata abin da Yesu ya yarda ya yi. AT: "Na yarda in tsarkake ka"
"Ka tabbata ba ka gaya wa kowa kome ba"
Yesu ya ce wa mutumin ya nuna kansa ga firist domin firist ya duba fatansa ko kuturtan ya barshi da gaske. An bukaci wannan cikin dokar Musa, mutum ya kai kansa gaban firist in an tsarkake shi.
Kalman nan "kanka" na wakilcin fatan kuturun. AT: "Nuna fatanka"
Zai fi kyau a yi amfani da "su" in mai yiwuwa ne a harshen ku. Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) "shaida ga firist" ko kuwa 2) "shaida ga mutanen."
Kalman nan "ya" na nufin mutumin da Yesu ya warkar.
A nan "yada labarin a ko'ina" na nufin cewa ya yi shaida wa mutane a wurare daban dabam game da abin da ya faru. AT: "fara gaya wa mutane a wurare da yawa game da abin da Yesu ya yi"
Mutumin ya yada labarin har ya kai
Wannan ita ce sakamakon yada labarin da mutumin ya yi so sai. Anan "sarari" na nufin "a fili."Yesu bai ba iya shigan farin ba domin mutane da yawa sun taru a gefensa. AT; "cewa Yesu bai iya shigar a fili ba" ko kuwa "cewa Yesu bai iya shigar garin ta hanyar da mutane za su iya ganinsa ba"
"wuraren kaɗaici" ko kuwa "wuraren da babu kowa"
Kalman nan "ko'ina" an yi amfani da ita don a nanata cewa mutane daga wurare da yawa ne suka zo. AT: "daga dukkan yankin"
1Da ya dawo Kafarnahum bayan yan kwanaki kadan, aka ji cewa yana gida. 2Da yawa suka taru a can, ba wuri har kofa, sai Yesu ya yi masu magana.3Sai wadansu mutane su ka zo wurinsa dauke da wuni mutum shanyayye, mutane hudu na dauke da shi. 4Lokacin da ba su iya zuwa kusa da shi ba domin yawan jama'a, sai su ka daye jinkar dakin daidai da inda ya ke. Bayan da suka huda ramin suka saukar da gado wanda shanyayyen ke kwance a kai.5Da ganin bangaskiyarsu, Yesu ya ce wa shanyayyen mutumin, "Da, an gafarta maka zunuban ka". 6Amma wadansu marubuta da ke zaune a nan, suka yi tunani aransu. 7Yaya wannan mutum zai yi magana haka? Ya yi sabo! wa ke iya gafarta zunubi "sai Allah kadai?"8Nan da nan Yesu ya sani a ruhunsa, abinda suke tunani a tsakaninsu. Ya ce masu, "Me ya sa kuke tunanin wannan a zuciyarku? 9Me yafi sauki a cewa shanyayyen mutumin, 'An gafarta maka zunuban ka' ko kwa a ce masa, 'tashi, ka dauki shinfidarka, ka yi tafiyarka'?10Amma domin ku san cewa Dan mutum na da ikon gafarta zunubi a duniya, ya ce wa shanyayyen, 11"Na ce maka, tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidan ka." 12Sai nan da nan ya tashi ya dauki tabarmarsa, ya fita gidan a gabansu, dukansu su ka yi mamaki, su ka girmama Allah, "suka ce ba mu taba ganin abu irin wannan ba."13Ya sake fita gefen tafki, dukan taron jama'a suka zo wurinsa, sai ya koya masu. 14Sa'adda ya na wucewa, ya ga Levi dan Halfa yana zaune a wurin karbar haraji, sai ya ce masa, "Ka biyo ni." Ya tashi, ya bi shi.15Sa'adda Yesu ya shiga gidan Levi yana cin abinci, masu karbar haraji da masu zunubi da yawa su ka zo wurinsa da almajiransa, jama'a masu yawan gaske suka ka bi shi. 16Da Marubuta wadanda su ke Farisawa, sun ga cewa Yesu na cin abinci da masu zunubi da masu karbar haraji, sai su ka ce wa almajiransa, "Me ya sa ya ke ci da masu karbar haraji da mutane masu zunubi?"17Da Yesu ya ji wannan ya ce masu, "Mutane wadanda ke da lafiya a jiki ba su bukatar likita; sai dai ko marasa lafiya ke bukatarsa. Ban zo domin in kira mutane masu a dalci ba, amma mutane masu zunubi."18Almajiran Yahaya da Farisawa suna azumi, sai wadansu mutane suka zo suka ce, "Don me almajiran Yahaya da almajiran Farisawa na azumi amma na ka almajiran ba su yi?" 19Sai Yesu yace masu, "Abokan ango, za su yi azumi sa'adda ango yake tare da su? muddin suna tare da ango ba za su yi azumi ba.20Amma kwanaki za su zo da za a dauki angon daga gare su, a wadancan kwanakin ne, za su yi azumi. 21Babu wanda zai dinka sabuwar riga ya hada ta da tsohuwar riga, sai rigar ta yage, kuma ta yi mummunar yagewa.22Babu wanda zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsohuwar salka, ai sai salkar ta fashe kuma ruwan inabin ya zube. duka biyu ruwan inabin da salkar arasa su. A maimakon haka, sai ka sanya sabon ruwan inabi cikin sabuwar salka."23A ranar asabar Yesu ya tafi cikin gonakin hatsi, sai almajiransa su ka fara zagar hatsi, 24Sai Farisawa su ka ce masa, "Duba, don me suke yin abin da bai dace a yi ranar Asabar ba?"25Yace masu, Ba ku karanta ba abinda Dauda ya yi sa'adda yake jin yunwa, shi da mutanen da ke tare da shi? 26Yadda ya shiga gidan Ubangiji, sa'adda Abiyata ya ke babban firist, ya ci gurasa da ke ta firist wadda bai dace wani ya ci ba sai Firistoci. Har kuma ya ba wadanda ke tare da shi?"27Yesu yace, "Asabar an yi ta don mutum ne, ba a yi mutum don Asabar ba. 28Saboda haka, Dan Mutum Ubangiji ne, har da na Asabar."
Bayan wa'azinsa da kuma warkar da mutane da Yesu ya yi a yankin kasar Galili, ya koma kafarnahum inda ya warkar da wani shanyayye mutum ya kuma yafe masa zunubansa.
AT: "Mutanen da da ke a wurin sun ji cewa yana zama a gida"
Kalman nan "a wurin" na nufin in da Yesu ke zama a kafarnahum. AT: "Mutane da yawa sun taru a wurin" ko kuwa "Mutane da yawa sun zo gidan"
Wannan na nufi babu wurin a cikin gidan. AT: "har babu ɗaki domin su a ciki"
"Yesu ya yi wa'azin saƙon zuwa a gare su"
"su huɗu suna ɗauke da shi." Mai yiwuwa akwai mutane fiye da huɗu cikin mutanen da suka kawo mutumin wurin Yesu.
"na kawo mutumin wanda ba iya tafiya ba ko kuwa bai iya amfani da hannayensa ba"
"kăsa zuwa kusa da inda Yesu yake"
Gidajen da Yesu ya zauna na da shimfiɗaɗɗen rufi da aka yi da yumɓu aka kuma rufe da fale-falen abu. Ana iya bayana a fili yadda ake yin rami a rufi ko kuwa ana iya bayana ta ga yadda kowa zai gane ya harshen ku. AT: "suka cire fale-falen abin da aka sa a saman rufi daidai in da Yesu yake. Bayan sun tona rufin yumɓun, sai suka sauƙar" ko kuwa "sun yi rami cikin rufin daidai ta inda Yesu yake, sai suka suaƙar da
"da ganin bangaskiyar mutanen." Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) cewa mutanen da suka ɗauke shanyeyyen mutumin ne kawai ke da bangaskiya. ko 2) cewa shanyeyyen mutumin da mutanen da suka kawo shi wurin Yesu, dukkan su su na da bangaskiya.
Kalman nan "Ɗa" a nan na nuna cewa Yesu ya kula da shi kamar yadda uba ke kula da ɗa. AT: "Ɗa na"
In mai yiwuwa ne a juya wannan yadda zai nuna cewa Yesu bai faɗi wanda ya yafe zunuban mutumin ba. AT: "zunubanka sun tafi" ko kuwa "ba ka bukatan ka biya domin zunubanka na" ko kuwa "ba a lisafta zunubanka a kanka ba"
A nan "zuciyarsu" na nufin tunanin mutane. AT: "suna tunani da kansu"
Marubutan sun yi amfani da wannan tambayar don su nuna fushin su cewa Yesu ya ce "An gafarta maka zunubanka" AT" "Bai kamata wannan mutum ya yi magana haka ba!"
Marubuta sun yi amfani da wannan tambayar cewa dashike Allah ne kaɗai ke iya yafe zunubai, to ba kamata Yesu ya ce "An yafe maka zunubanka" ba. AT: " Allah ne kaɗai ke da iya yafe zunubai!"
"cikin ransa" ko kuwa "a cikinsa"
Kowane malamin attaura na tunani da kansa; ba su magana ga juna.
Yesu ya yi amfani da wannan tambayar don ya gaya wa malaman attauran cewa abin nana da suke tunani ba daidai ba ne. AT: "Abin da kuke tunani ba daidai ba ne." ko kuwa "Kada ku yi tunanin cewa ina saɓo"
Kalman nan "zuciya" na nufin tunaninsu da kuma sha'awace sha'awacensu. AT: "wannan a cikin ku" ko "waɗannan abubuwa"
Yesu ya yi amfani da wannan tambayar don ya sa malaman attauran tuna game da abin da zai tabbatar cewa lallai zai iya yafe zunubai ko ba zai iya ba. AT: "Na dai cewa wa shanyeyyen mutumin, 'An yafe maka zunubanka.' Mai yiwuwa kuna tunanin cewa yana da wuya a ce 'Tashi, ɗauki gadonka ka yi tafiya,' saboda tabbacin cewa zan iya ko ba zan iya warkar da shi, ba za a nuna ta tawurin tashinsa ya yi tafiya ko kuwa bai tashi ya yi tafiya ba." ko kuwa "Mai yiwuwa kuna tunanin cewa ya fi sauƙi a ce ma shanyeyyen mutumin 'An yafe maka zunubanka' fiye da a ce 'Tashi, ɗauki gadonka ka yi tafiya.'"
"Amma don ku sani." Kalman nan "ku" na nufin marubutan da kuma taron jama'an.
Yesu ya dubi kansa a matsayin "Ɗan Mutum." AT: "cewa ni Ɗan Mutum ne kuma ina da iko"
"a sa'ad da dukkan mutanen ke kallo"
Wannan tekun Galilli ne wanda ake kiran ta tafkin Janisarata.
"mutanen sun je in da ya ke"
Halfa uban Lawi ne.
"gidan Lawi"
Farisiyawan sun yi amfani da jimlar nan "mutane masu zunubi" don suna nufi mutanen da ba sa bin doka kamar yadda Farisiyawan na nuna su yi.
Ma'ana mai yiwuwa na kamar haka 1) "don akwai masu karɓar haraji masu yawan gaske da mutane masu zunubi wanda suka bi shi" ko kuwa 2)"gama Yesu yana da almajirai masu yawa sun kuma bi shi."
Malaman attauran da Farisiyawan sun yi wannan tambayar don su nuna cewa ba su yarda da kirkin da Yesu ya nuna ba. Ana iya sa wannan cikin magana. AT: "Bai kamata ya ci da masu zunubi da masu karɓar haraji ba!"
"ya ce wa malaman attauran"
Yesu ya yi amfani da wannan karin magana game da mutane marasa lafiya da likita don ya koya musu cewa mutanen da sun san cewa suna cike da zunubi sun gane cewa suna bukatan Yesu.
"lafiyayyu"
Yesu na tsammanin masu sauraronsa su fahimci cewa ya zo ne domin waɗanda ke bukatan taimako. AT: "Na zo domin mutanen da sun fahimci cewa su masu zunubi ne, ba domin mutane da sun gaskanta cewa su masu adalci ne ba"
Kalmomin nan "na zo in kira", an fahimci ta ne daga maganar da ke kafin wannan. AT: "amma na zo domin in kira mutane masu zunubi"
Wannan maganganu biyun na nufin ƙungiyan mutane ɗaya ne, amma an tabbatar da na biyun. Duka biyun na nufin mabiyan ɗarikar Farisiyawan, amma ba su mayar da hankali ga shugabannen Farisiyawan ba. AT: "almajiran Farisiyawan na azumi ... almajiran Farisiyawan"
"Wasu mutane." Zai fi kyau in an juya wannan magana ba tare da an tantance wanene waɗanan mutanen ba. Idan a harshen ku lallai ne a tantance, to ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) waɗannan mutanen ba sa cikin almajiran Yahaya ko kuwa almajiran Farisiyawa ba ko kuwa 2) waɗannan mutanen na cikin almajiran Yahaya.
"zo sun ce wa Yesu"
Yesu ya yi amfani da wannan tambayar don ya tunashe mutanen abin da sun riga sun sani don kuma ya karfafa su yi amfani da ita da shi da almajiransa. AT: "Abokan ango, ba sa azumi a sa'ad da ango na tare da su. Maimakon haka suna shagali da taya shi murna."
AT: "angon zai tafi"
Kalman nan "su" na nufin abokan ango.
Ɗinkin riga a kan tsohuwar tufa na sa ramin tsohuwar tufan ta zama mafi ɓaci in gutsuren sabon rigan bai tauye ba. Sabon rigar da tsohon tufan duk za su ɓaci.
"Babu mutum." Wannan maganar na nufin dukkan mutane, ba mazaje kawai ba.
"ruwan 'ya'yan itacen inabi." Wannan na nufin ruwan inabi da bai riga ya tashi ba. Inda ba a san inabi a yanki ku ba to a yi amfani da kalman da kowa ya sani na ruwan 'ya'yan itace.
Wannan na nufin salkunan da aka yi amfani da su sau da dama.
Waɗanan jakuna ne da aka yi da fatan dabba. Ana iya kiran su "jakunan inabi" ko "jakunan fata."
Sabuwar inabi na buduwa a sa'ad da yake tashiwa, saboda da haka zai sa tsohon salkunan fata ta yage.
"zai ɓaci"
"sabon salkuna" ko "sabuwar jakunan fata." Wannan na nufin salkunan fatan da ba taba amfani da ita ba.
zagar hatsi cikin gonakin wasu, kuma cin wannan ba a duban ta kamar sata. Tambayar ita ce ko daidai be bisa ga doka a yi wannan ranar Asabar.
Almajiran na zagar kan hatsi don su ci sabar, ko kwayar da ke cikin su. Ana iya sa wannan cikin kalma don nuna ma'anar gabaki ɗaya. AT: "zagar hatsi suna kuma cin kwayar"
"kan" saman tsiren alkama wanda ke kamar ciyawa mai tsayi. Kan na rike hatsi ko iri tsiren da ta balaga.
Farisiyawa sun yi wa Yesu tambaya don su kayar da shi. Ana iya juya wannan kamar magana. AT: "Duba! Su na karya dokar Yahudawa game da ranar Asabar."
"Duba wannan" ko "Kassa kunne." Wannan kalma ne da an yi amfani da shi don kama hankalin wani don a nuna musu wani abu. In akwai wata kalm a harshen ku da ake amfani da ita don a jawo hankalin mutu, to ana iya amfani da ita anan.
Yesu ya yi wannan tambayar don ya tunashe malaman attauran da Farisiyawa wani abin da Dauda ya yi a ranar Asabar.Tambayar ta yi dogo sosai, don haka ana iya raba shi zuwa jimla biyu.
Ana iya faɗin wannan kamar umurni. AT: "Ku Tuna abin da kin karanta game da abin da Dauda ... shi."
Yesu na nufin karanta game da Dauda cikin Tsohon Alkawari. Wannan ana iya juya shi ta wurin nuna ainihin zancen a fili. AT: "karanta cikin nassosin abin da Dauda"
A nan iya bayana wannan a matsayin furuci dabam da aya 25. AT: "Ya shiga gida Allah ... waɗanda ke tare da shi."
Kalman "ya" na nufin Dauda.
Wannan na nufin gurasa shabiyun wanda aka ajiye kan taburin zinariya wanda ke cikin alfarwa ko ginin haikali, hadaya ga Allah lokacin Tsohuwar Alkawari.
Yesu ya bayana a fili dalilin da Allah ya yi Asabar. AT: "Allah ya yi Asabar don mutum"
"mutum" ko "mutane" ko kuwa "bukatun mutane." Wannan kalma na nufin mazaje da mataye dukka.
Kalmomin nan "aka yi" an fahimci ta daga maganar da ke a baya. Ana iya sake faɗin ta ana. AT: "ba a yi mutum domin Asabar ba" ko kuwa "Allah bai yi mutum domin Asabar ba"
1Sai kuma ya sake tafiya cikin Majami'a sai ga wani Mutum mai shanyayyen hannu. 2Wadansu mutane suna kallonsa sosai, su gani ko zai warkar da shi a ranar Asabar. don su zarge shi.3Yesu ya ce wa mai shanyayyen hanun " Ka tashi ka tsaya a tsakiyar kowa." 4Sai ya ce wa mutane, "Ya dace a yi abu mai kyau aranar Asabar ko a yi mugunta; a ceci rai, ko a yi kisa? "Amma suka yi shiru.5Sai ya dube su cikin fushi, yana bakin ciki da taurin zuciyar su, ya ce wa mutumin ka mikar da hanunka, sai ya mikar da hanunsa Yesu kuwa ya warkar da shi. 6Sai Farisiyawa suka fita da sauri zuwa wurin mutanen Hirudus suka shirya yadda za su kashe shi.7Sai Yesu da almajiransa, suka tafi bakin teku. sai mutane dayawa suka bi shi, daga Galili da Yahudiya 8Daga Urushalima da Edom gaba da Urdun da kewayan Taya da Sidon, da baban taro, ya ji abinda yake yi. suka zo wurinsa.9Ya tambayi almajiransa su shirya masa karamin jirgin ruwa domin yawan mutane, domin kada su murkushe shi. 10Ya warkar da mutane da yawa, yadda duk wadanda suke da cuttutuka suna kokari su taba shi.11Duk sa'adda kazaman ruhohin suka ganshi, sai su durkusa a gabansa su yi ihu da karfi su ce, kai Dan Allah ne." 12Ya umarce su da karfi kada su sa a san shi.13Ya hau saman dutsen, ya kira wadanda yake bukar su, su zo wurinsa. 14Ya zabi guda goma sha biyu (ya kira su manzanni). Wadanda zasu kasance tare da shi, ya kuma aike su, su yi wa, azi, 15Ya kuma basu Ikon fitar da aljanu. 16Ya zabi guda goma sha biyu wato Saminu kuma yaba shi suna Bitrus.17Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan-uwan Yakubu wanda ya basu sunan Buwanarjis watau 'ya'yan tsawa, 18da Andarawus da Filibus da Bartalamawus da Matta da Toma da Yakubu dan Halfa, da Taddawus da Saminu Ba-kananiye, 19da Yahuza Iskariyoti wanda zai bashe shi.20Sa'adda ya shiga gida, Taron kuwa ya sake haduwa, har ya hana su cin abinci, 21Da iyalansa suka ji haka, sai suka fito sun kamo shi, saboda sun ce, "Ai, baya cikin hankalinsa " 22Marubutan da suka zo daga Urushalima suka ce "Ai Ba'alzabuba ne ya hau shi, da ikon sarkin aljannu kuma yake fitar da aljannu."23Yesu ya kirawo su wurinsa ya ce da su cikin misalai, "Yaya shaidan zai iya fitar da shaidan? 24idan mulki ya rabu gida biyu ba zai tsayawa ba. 25Haka in gida ya rabu kashi biyu, gaba da kansa bai zai tsaya ba.26Shaidan kuma in ya tayar wa kansa ya rabu, ba zai iya tsayawa ba, gama karshen sa ya zo kenan. 27Amma ba mai iya shiga gidan kakkarfan mutum ya kwace kayansa, ba tare da ya fara daure kakkarfan mutumin ba, sa'an nan kuma ya kwashe kayan gidansa.28Hakika, ina gaya maku, dukan zunuban da mutane suka yi za a gafarta masu, da kowane irin sabon da suka furta, 29amma fa duk wanda yayi sabon Ruhun Mai Tsarki baza a gafarta masa ba ko kadan, ya zama mai zunubi har abada." 30"Yesu ya fadi wadannan abubuwa domin suna cewa yana da ba kazamin ruhu,"31Sa'an nan uwatasa, da "Yan'uwansa suka zo suna tsaye a waje. sai suka aika masa, suna kuma umurtar sa ya zo. 32Taro kuwa na zaune kewaye da shi, sai suka yi magana da shi da cewa, ga uwarka da yan-uwanka suna nan a waje, suna nemanka."33Ya amsa masu, "Dacewa su wanene uwa-ta da "yan'uwa na?"34Sai ya waiwayi wadanda suke zaune kewaye da shi, yace, "Ga uwa-ta da yan-uwana anan! 35Gama duk wanda ke yin abin da Allah yake so, shine dan'uwana da yar, uwata, da kuma uwa-ta."
Yesu ya wakar da wani mutum ranar Asabar a cikin majami'a ya kuma nuna yadda ya ji game da abin da Farisiyawa sun yi da umurni game da Asabar. Farisiyawan da mutanen Hirudus su fara shirin yadda za su kashe Yesu.
"wani mutum wanda gurgu ne a hannu"
"Wasu mutane na kallonsa Yesu sosai, su gani ko zai warkar da mutumin wanda ke da shanyayyen hannu"
Wasu Farisiyawa." Nan gaba, cikin [Markus: 3:6] waɗannan mutanen an gane su Farisiyawa ne.
Ida Yesu ya warkar da mutumin a ranar, Farisiyawan za su zarge shi cewa ya karya doka ta wurin yin aiki ranar Asabar. AT: "domin su iya zarginsa cewa bai yi daidai ba" ko "domin su iya zarginsa cewa ya karya dokan"
"a tsakiyar wannan taron jama'a"
Yesu ya faɗi wannan domin ya kalubalance su. Ya na so su amince cewa ya halatta a warkar da mutane ranar Asabar.
Waɗannan magana biyun suna da ma'ana kusan iri ɗaya, sai dai na biyun matsananci ne sosai.
Mai yiwuwa zai yi taimako in an nanata "ya halatta" kamar ita ce tambayar da Yesu ya yi kuma a wata hanya. AT: "ya halatta a cece rai ko a yi kisa"
Wannan na nufi rai na wannan jiki. Ya na kuma nufin mutum. AT: "wani daga mutuwa" ko "ran wani"
"Amma sun ki su amsa masa"
"Yesu ya dube kewaye"
"ya yi fushi sosai"
Wannan ya bayyana yadda Farisiyawa ba sa shirye su ji tausayin mutum mai shanyayyen hannu da tausayi. AT: "domin ba sa shirye su ji tausayin mutumin"
"Mika hannunka"
AT: "Yesu ya komar masa da hannunsa lafiyayye" ko "Yesu ya sa hannunsa ya zama daidai yadda yake a dă"
"fara yin dabara"
Wannan suna ne na yau da kullum na wata kungiyan siyasa da ke goyon bayan Hirudus Antibas.
"yadda za su kashe Yesu"
Wannan na nufin Tekun Galili.
Wannan yankin ne wanda a baya an san ta da suna Edom, wanda ya kunshi rabin lardin kudacin Yahudiya.
Wannan na nufin al'ajiban da Yesu ke yi. AT: "babbar abin al'ajiban da Yesu ke yi"
"zo wurin da Yesu yake"
Aya 9 ta faɗi abin da Yesu ya ce wa almajiransa su yi saboda gaggaruman taron mutane da ke kewaye da shi. Aya 10 ta faɗi dalilin da ya sa gagaruman tarons suna kewaye da Yesu. Bayanin da ke a waɗannan ayoyi sake kasa su don a bayana labarun daidai yadda sun faru, kamar yadda yake cikin UDB.
A sa'ad da gaggaruman taron na kara matsowa kusa da Yesu, yana cikin hatsarin da za su iya murkushe shi. Ba da saninsu za su murkushe shi ba. Amma domin dai kawai akwai mutane da yawa.
"Yesu ya gaya wa almajiransa"
Wannan ta gaya mana dalilin da ya sa mutane masu yawa suna kewaye da Yesu har sai da ya yi tunani cewa za su murkushe shi. AT: "Gama, saboda Yesu ya warkar da mutane da yawa, duk waɗanda ... taba shi"
Kalman nan "yawa" na nufin gaggaruman mutanen da Yesu ya warkar da su. AT: "Gama ya wakr da mutane da yawa"
Sun yi wannan ne saboda sun gaskanta cewa in sun taba Yesu za su warke. A nan iya bayana wannan a fili. AT: " dukkan mutane marasa lafiya sun nace zuwa suna kokarin sun taɓa shi domin su warke"
"gan Yesu"
A nan "su" na nufin aljannun. Sune suke sa mutanen da suka shige su su yi waɗannan abubuwa. Anan iya bayana wannan a fili. AT: "Sun sa mutanen da suka shige su su fãɗi kasa a gaban shi, su yi kuka a gare shi"
Aljannun ba su fãɗi a gaban Yesu saboda suna kaunar shi ba ko suna so su yi masa sujada ba. Sun fãɗi a gabansa domin sun ji tsoronsa ne.
Yesu yana da iko a kan aljannun domin shi "Ɗan Allah" ne.
Wannan laƙani ne mai muhimmanci na Yesu.
"Yesu ya umurce aljannun"
"kada su bayana ko shi wanene"
"don su kasance tare da shi, shi kuma zai aike su, su yi wa'azi sakon"
Marubucin ya fara lisafta sunayen manzane goma sha biyun. Saminu shi ne na farko da aka ambata.
Maganan nan "wanda" na nufin Yakubu ɗan Zabadi da ɗan'uwansa Yahaya.
Yesu ya kira su da wannan suna domin suna kamar tsawa ne. AT: "suna Buwanarjis, wanda ke nufin mutane da ke kamar tsawa" ko "suna Buwarnarjis, wanda ke nufin mutanen tsawa"
Wannan sunan na miji ne.
"wanda zai bãshe da Yesu" Kalman nan "wanda" na nufin Yahuda Iskariyoti.
"Sai Yesu ya tafi gidan da yake zama."
Kalman nan "gurasa" na wakilcin abinci. AT: "Yesu da almajiransa ba su iya cin abinci ba ko kaɗan" ko "ba su iya cin komai ba"
'Yan iyalinsa sun shiga cikin gidan don su kama shi su sha shi dole ya je gida tare da su.
Ma'ana mai yiwuwa na kalman nan "su" na kamar haka 1) danginsa ko 2) wasu mutane da cikin taron.
iyalin Yesu sun yi amfani da wannan karin magana don su bayana yadda suke tunani yake yi. AT: "haukace"
"Ta wurin ikon Ba'alzabul, wanda shine sarkin aljannu, Yesu ke fid da aljannu"
"Yesu ya kira mutanen wurinsa"
Yesu ya yi wannan tambaya don ya amsa maganar malaman attaura da cewa yana fid da aljan ta wurin ikon Ba'alzabul. AT: "Shaiɗan ba zai iya fid da kansa ba!" ko "Shaiɗan baya gãba da mugayen ruhohinsa!"
Kalman nan "mulkin" na nufin mutane da ke wannan mulkin. AT: "Idan mutanen da ke zama cikin mulki sun rabu suna gãba da juna"
Wannan na nufin cewa mutane ba za su haɗu kuma ba kuma za su faɗi. AT: "ba zai iya jimrewa ba" ko "zai faɗi"
Wannan na nufin mutane da ke zama a gidan. AT: "iyali"
Kalman nan "kansa" na nufin Shaiɗan, yana kuma nufin mugayen ruhohi. AT: "Idan Shaiɗan da mugayen ruhohinsa suna faɗa da juna." ko "Idan Shaiɗan da mugayen ruhohinsa na gãba da juna kuma sun rabu"
Wannan na nufin cewa zai fãɗi kuma ba zai jimre ba. AT: "ba zai haɗu ba" ko "ba zai jima ba kuma ta zo ga ƙarshe kenan" ko "zai fãɗi kuma ta zo ga ƙarshe kenan"
a sata kayan mutum da kuma mallaka
Wannan na nuna cewa maganar da za a iya mai muhimmanci ne kuma gaskiya ne.
"waɗanda mutum ne ya haifa." Wannan na nanata cewa 'yan adam ne. AT: "mutane"
magana
"mutane suna cewa"
Wannan karin magana da ke nufin aljan ya yi mulkin wani. AT: "na da baƙin aljani"
"Sai uwar Yesu da 'yan'uwansa suka zo"
"Sun aiki wani a ciki ya gaya masa da cewa suna a waje kuma suna so ya zo wurin su"
"na tambaya game da kai"
Yesu ya yi amfani da wannan tambaya don ya koya wa mutanen. AT: "Zan gaya maki ko wanene uwata da 'yan'uwana"
"waɗanda ke aikata ... sune"
Wannan na nufin almajirans Yesu sune iyalinsa na ruhaniya. Wannan ya fi muhimmanci fiye da zama cikin iyalinsa na jiki. AT: "wannan mutum shi kamar ɗan'uwana, da 'yar'uwata, ko uwa a gare ni"
1Ya kuma fara koyarwa a bakin teku. Akwai babban taro kewaye da shi, sai ya shiga cikin jirgin ruwa a cikin tekun, ya kuwa zauna. Duk taron kuwa na kan tudu a bakin tekun. 2Ya koya masu abubuwa da yawa da misalai, a cikin koyawarsa ya ce masu,3"ku saurara! wani mai shuka ya tafi shuka. 4Yana cikin yafa iri, sai wadansu iri suka fadi a kan hanya, tsuntsaye kuma suka zo suka tsince su. 5Wadansu kuma suka fadi a kan dutse inda ba kasa dayawa. Nan da nan kuwa suka tsiro saboda rashin zurfin kasa.6Da rana fa ta daga, sai suka yankwane da yake ba su da saiwa sosai, sai suka bushe. 7Wadansu kuma suka fadi cikin kayayuwa su ka yi girma sai kayayuwan suka shake su, ba su yi tsaba ba.8Wadansu kuma suka fadi a kasa mai kyau, suka yi yabanya, suka yi tsaba, suka yi girma, wadansu ribi talattin wadansu sittin, wadansu kuma dari". 9Sai ya ce, Duk mai kunnen ji, ya ji,"10Sa'adda Yesu yake shi kadai, wadanda suke kusa dashi tare da sha biyun suka tambaye shi ma'anar misalan. 11Sai ya ce masu, "ku an yardar maku, ku san asirin mulkin Allah, amma ga wadanda ba su cikinku, komai sai a cikin Misalai, 12don gani da ido sun gani, amma ba su gane ba. ji kuma, sun ji, amma ba su fahimta ba, don kada su juyo a gafarta masu,"13Ya ce masu, "Ashe, ba ku fahimci wannan misalin ba? yaushe za ku fahimci sauran? 14Mai shukan nan fa maganar Allah yake shukawa. 15Wadanda suka fadi a hanyar kuwa, su ne kwatancin wadanda. a aka shuka mganar a zuciyarsu, Da suka ji, nan da nan sai shaidan ya zo ya dauke Maganar da aka shuka a zuciyarsu.16Haka kuma wadanda aka shuka a wuri mai duwatsu, sune wadanda da zarar sun ji Maganar sai su karba da farin ciki. 17Su kuwa basu da tushe, ba su da karfi, idan kunci ko tsanani ya zo saboda kalmar, nan da nan sai su yi tuntube.18Wadansu kuma su ne kwatacin wadanda suka fadi cikin kayayuwa, sune wadanda suka ji Maganar, 19amma abubuwan duniya, da rudin dukiya da kuma kwadayin wadansu abubuwa, sukan shiga su shake Maganar, har ta zama marar amfani. 20Wadanda aka shuka a kasa mai kyau kuwa, sune kwatancin wadanda suke jin Maganar, su karba, su kuma yin amfani da ita wadansu ribi talatin, wadansu sittin, wadansu dari."21ya ce masu, "Shin, ana kawo fitila a cikin gida don a rufe ta da kwando ko a ajiye ta a karkashin gado? ku kan kawo ta ne don ku dora ta a kan madorinta. 22Ba abin da yake boye, da baza a sani ba ko kuma ba abinda ke asirce da bazaya bayyana a fili ba. 23Bari mai kunnen ji, ya ji!"24Sai ya ce masu, ku mai da hankali a kan abin da kuka ji, Mudun da ka auna, da shi za a auna maka, har ma a kara maka. 25Domin mai abu akan karawa, marar abu kuma za a karba daga wurinsa a kuma karawa mai shi."26Sai ya ce, "Mulkin Allah kamar mutum yake mai yafa iri a kasa. 27A kwana a tashi har irin ya tsiro, ya girma bai kuwa san ta yaya aka yi ba. 28Kasa da kanta, takan ba da amfani, tsiro shine ne na farko, 29Sai kai, sa'anan sai kwaya mai kwari. Sa, adda amfani ya nuna, sai ya sa lauje ya yanke nan da nan, wato kaka ta yi kenan."30Ya kuma ce, "Da me za mu kwatanta Mulki Allah? ko kuwa da wane misali za mu misalta shi? 31Kamar kwayar zarra yake wadda, in an shuka ta, ko da yake ita ce mafi kankanta cikin kwayoyi a duniya. 32Duk da haka in an shuka ta, sai ta yi girma fiye da duk sauran ita-tuwan da ke a jeji tayi manyan rassa, har tsuntsaye su iya yin sheka arassanta."33Da misalai da yawa, irin wadannan ya yi masu Magana, dadai gwargwadon ganewarsu, 34ba ya fada masu kome sai da misali, amma a kebe, yakan bayyana wa almajiransa dukan abu.35A ranan nan da yama ta yi yace masu "Mu haye wancan ketaren." 36Sai suka bar taron, suka tafi tare da shi acikin cikin jirgin. wadansu jirage kuma na tare da shi. 37Sai babban hadari da iska mai karfi ya taso, rakuman ruwa kuma na ta girgizawa cikin jirgin, har jirgin ya cika.38Yesu kuwa na daga karshen bayan jirgin a kan kujera, yana barci, sai suka tashe shi, suka ce masa "Malam za mu hallaka ba ka kula ba?" 39Sai ya farka, ya tsawata wa Iskar. Ya kuma ce wa ruwan tekun, "Ka natsu! ka yi shiru!" Sai Iskar ta kwanta, wurin duk ya yi shiru.40Ya ce masu, "Don me kuka firgita haka? Har yanzu baku da bangaskiya ne?" 41Sai suka tsorata kwarai suka ce wa juna, "wanene wannan kuma, wanda har Iska da teku ma suke yi masa biyayya?"
A sa'ada Yesu ya koya masu daga cikin jirgin ruwa a bakin teku, ya basu misalin kasa.
Wannan Tekun Galili ne.
"Ku saurara! Wani manomi"
An yia maganar dukkan irin da manomin ya shuka kamar iri guda ɗaya ne. "irin ... waɗansu ... tsince su ... Wasu iri ... ba su sami ... suka tsiro ... ba su sami"
"A sa'ad da ya wasa iri a ƙasa." A al'adu daban-dabam mutane suna da hanyoyin shukin iri daban-dabam. A wannan misalin an shuka iri ta wurin wasa wa a ginar da aka shirya.
"irin da aka shuka a gonar da ke da duwasu sun fara girma da sauri"
Wannan na nufin datti da ke kasa wanda za a iya shuka iri.
Wannan na nufin shukin da basu kosa ba. AT: "ta yankwane shukin da basu kosa ba"
"domin shuki ba ta da saiwa sosai, sai suka bushe"
A nan an yi magana game da duk irin da manomin ya shuka kamar iri guda ɗaya ne. Dubi yadda ka juya wannan cikin [Markus 4:3]. "Wasu iri ... suka shake su ... ba su bada amfani ba"
Yawan tsaban da shukin ta bayar an kwatanta shi da iri guda da ya yi girma. AT: "Waɗansu shukin sun bada amfani fiye da irin da mutumin ya shuka sau talatin, waɗansu iiri sun bada tsaba sau sittin, waɗansu kuma sun bada amfanin tsaba sau dari"
"30 ... 60 ... 100." Za a iya rubuta waɗannan cikin adadi.
Wannan wata hanya ce da ake nufin duk wanda ke wurin wanda kuma na jin abin da Yesu yake faɗa. AT: "Kowa wanda zai iya ji na" ko "Duk wanda zai iya ji na"
A nan kalman nan "ji" na nufin saurara. AT: "yă saurara da kyau" ko "lalle ne ya suarari abin da ina faɗa da kyau"
Ba wai wannan na nufin cewa Yesu yana nan gabaɗaya shi kaɗai ba; maimakon haka, abin nufi shine, lokacin da taron sun tafi, Yesu kuma na tare da sha biyun da wasu masubinsa.
AT: "Allah ya ba ku" ko "Na ba ku"
"amma waɗanda ba sa cikin ku." Wannan na nufin dukkan mutanen da ba sa cikin sha-biyun ko sauran masubi Yesu na kusa.
Ana iya faɗin cewa Yesu ya ba wa mutanen misalai. AT: "Kowane abin da na faɗa, na yi shi cikin misali"
Ana ɗaukan cewa Yesu yana magana game da mutane suna ganin abubuwan da ya nuna masu suna kuma jin abin da ya gaya masu. AT: "sa'ad da suna ganin abin da nake yi ... sa'ad da suna jin abin da nake faɗa
Yesu yana magana game da fahimtar mutane ga abin da suka gani kamar a zahiri suna gani ne. AT: "sun gani ba su kuma gane ba"
"juyo wurin Allah." Anan "juyo" na nufin "tuba," AT: "za su tuba"
"Sai Yesu ya ce wa almajiransa"
Yesu ya yi amfani da waɗannan tambayoyi don ya nuna fushin sa cewa almajiransa ba su fahimci misalinsa ba. AT: "Idan ba ku iya fahimtar wannan misalin ba, yi tunani game da zai yi maku wahala ku fahimci sauran misalen."
"Manomi wanda ya shuka irinsa na wakilcin"
"maganar" na nufin saƙon Allah. Bada sakon na nufin koyar da ita. AT: "wanda yake koyawa mutane saƙon Allah"
"wasu mutane suna kamar iri da suka faɗi a gefen hanya" ko "wasu mutane suna kamar hanyan da wasu iri suka faɗi"
"tafarki"
A nan "ta" na nufin "maganan" ko "saƙon Allah"
"wasu kuma suna kamar irin." Yesu ya fara bayana yadda wasu mutane suna kamar iri da ta faɗi a kan ƙasa ma duwatsu.
Wannan kwatanci ne da shuki da jijiyoyin sa ba su yi zurfi ba. Wannan na nufin cewa mutanen sun yi murna sa'ada suka karɓi magana, amma basu dukufa ga maganar ba. AT: "suna kuma kamar shuki da ba shi da jijiya"
Wannan na nanata rashin zurfin jijiyoyin.
A wannan misali, "jimre" na nufin "bada gaskiya." AT: "cigaba cikin bangaskiyarsu"
Zai zama da taimako in an bayana cewa kunci na zuwa domin mutane sun bada gaskiya ga saƙon Allah. AT: "kunci ko tsanani na zuwa domin sun bada gaskiya ga saƙon Allah"
A wannan misalin, "tuntuɓe" na nufin "sun daina bada gaskiya ba saƙon Allah"
Yesu ya fara bayana yadda wasu mutane suke kamar iri da ya faɗi cikin ƙaya. AT: "wasu mutane kuma suna kamar irin da aka shuka cikin ƙaya"
"damuwoyin wannan rayuwa" ko "damuwan rayuwan yanzu"
"sha'awace sha'awacen dukiya"
Sa'anda Yesu ya cigaba da magana game da mutane wanda suke kamar irin da ta fadi cikin ƙaya, ya bayana ainihin mecece sha'awace sha'awace da damuwo'in ke yi wa kalmar a rayuwansu. AT: "sun shiga sun shake saƙon Allah cikin rayuwar su kamar yadda ƙaya ke shake shuki"
"maganan ba ta bada amfani gona a cikinsu ba"
Yesu ya fara bayana cewa wasu mutanen suna kamar iri da aka shuka a ƙasa mai kyau. AT: "kamar iri da aka shuka a ƙasa mai kyau"
Wannan na nufin tsaba da aka shukin ta bada amfanin ta. AT: " wasu sun yi tsaba talatin, wasu tsaba sittin, wasu kuma tsaba ɗari" ko "wasu sun bada tsaba fiye da abinda aka shuka sau 30, wasu sun bada tsaba fiye da abin da aka shuka sau 60, wasu kuma sun bada tsaba fiye da abin da aka shuka sau 100"
"Yesu ya cewa taron"
A nan iya rubuta wannan tambaya kamar ba tambaya ba. AT: "Haƙika ba a kawo fitila cikin gida don a rufe ta da kwando, ko a ajiye ta a ƙarƙashin gado!"
AT: "Gama duka abin da yake a ɓoye za a bayyana shi, kuma kowane abin da ke a asirce za a bayyana a fili"
"babu wani abin da ke a ɓoye ... babu wani abin da ke a asirce" Maganganu biyun nan na nufin abu ɗaya. Yesu yana nanata cewa kowane abu da ke a asirce za ta zama sanannen.
Dubi yadda ka juya wannan cikin [Markus 4:9]
"Yesu ya ce wa taron"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) Yesu yana magana game auwu da kuma bayarwa a yalwace ga wasu ko 2) wannan na nufin Yesu yana magana game da "fahimta" sai ka ce "auwu."
AT: "Allah zai auna maka, zai kuma kara maka"
AT: "Allah zai kara masa ... Allah zai karɓe" ko "Allah zai kara masa ...Allah zai karɓe daga wurinsa"
Yesu ya kwatanta mulkin Allah da manomi wand aya shika irinsa. AT: "kamar manomin da ya shuka irinsa"
Wannan abu ne da mutumin ya saba yi. AT: "Yana barci kowane dare, yana kuma tashiwa kowane rana" ko "Yana barci kowane dare ya kuma tashi kashegari"
"ya tashi da rana" ko "ya fara aiki da rana"
"kodashike mutumin bai san ya aka yi irin ya toho ya kuma yi girma ba"
kara ko toho
kan kara ko bangare shuke da ke rike 'ya'yan
A nan "lauje" na nufin manomin ko mutanen da manomin ya aike su girbin hatsin. AT: "nan da nan ya tafi gonar da lauje do ya yi girbin hatsi" ko "nan da nan ya aiki mutane da lauje zuwa cikin gonar su yi girbin hatsin"
wani wuka da ke a lanƙwashe ko wani kugiya mai kaifi da ana amfani da ita a girbe hatsi
A nan maganan nan "ta yi" na nufin hatsin ta yi don girbi. AT: "domin hatsi ta yi domin girbi"
Yesu ya yi wannan tambaya domin masu karatun su yi tunani game macece mulkin Allah. AT: "Da wannan misalin zan iya kwatanta mulkin sama."
AT: "sa'ad da wani ya shuka ta"
An bayana bishiyan mustad kamar an sa rassan tayi manya. AT: "da manyan rassa"
"Magana" anan na nufin "saƙon Allah." Kalman nan "su" na nufin taron. AT: "ya koyawa masu sakon Allah"
"kuma ida sun iya fahimtar wasu, sai ya cigaba da gaya masu"
Wannan na nufin cewa ba ya tare da taron, amma almajiransa suna tare da shi.
A nan "kowane abu" daɗaɗawa ne. Ya bayana masu duk misalinsa. AT: "Ya bayana masu duk misalinsa"
"wancan ƙetaren Tekun Galili" ko "wancan ƙetaren takun"
A nan "taso" na nufin "fara." AT: "sai babban hadari mai iska ya fara"
Zai yi taimako in an bayana cewa jirgin yana cika da ruwa. AT: "jirgin na hatsarin cika da ruwa"
A nan "kansa" na nanata cewa Yesu shi kaɗai ya kasan jirgin. AT: "Yesu kansa na nan shi kaɗai"
Wannan ita ce bayan jirgin. "bayan jirgin"
Kalman nan "su" na nufin almajiransa. Kwatanta zance dake kusan ɗaya da wanda ke a aya 39, "Ya tashi." "Ya" na nufin Yesu.
Almajiran sun yi wannan tambaya don su nuna soron su. A nan iya rubuta wannan tambaya a matsayin magana. AT: "ya kamata ka jawo hankalin ka ga abin da yake faruwa; mun kusa mu mutu dukkan mu!"
Kalman nan "mu" na nufin almajiran da Yesu kansa.
Waɗannan maganganu biyun suna nan kusan iri ɗaya ne kuma suna nanata abin da Yesu ya son iska da tekun su yi.
"an sami matuƙar kwantawar iska a tekun"
Yesu ya yi waɗannan tambayoyi don ya jawo hankalin almajiransa su duba dalilin da ya sa suka firgita a sa'ad da yake tare da su. AT: "Bai kamata ku ji tsoro ba. kuna bukatan ku sami bangaskiya sosai."
Almajiran sun yi wannan tamaya cikin mamaki saboda abin da Yesu ya yi. AT: "Wannan mutum ba kamar sauran mutane bane; har iska da teku sun yi masa biyayya!"
1Da su ka zo daya ketaren tekun, wanda ya ke cikin yankin Garasinawa. 2Sa'adda Yesu ya sauko daga cikin jirgin ruwan sai wani mutum mai aljanu ya fito daga cikin kaburbura ya tarbe shi.3Mutumin yana zama a cikin kaburbura. An daure shi da sarkoki da mari 4An daure shi da sarkoki da mari sau da yawa, amma ya tsuntsunke sarkoki da marin. har ma ba wanda zai iya daure shi kuma.5Dare da rana a cikin kabarbarun da duwatsu mutumin ya na ihu ya na yaiyage jikinsa da duwatsu masu kaifi. 6Sa'adda ya hango Yesu daga nesa, sai ya tarbi Yesu ya durkusa a gabansa.7Ya tada muryarsa da karfi ya ce, ina ruwa na da kai? Yesu Dan Allah Madaukaki Ina rokon ka da sunan Allah kada ka bani wahala, 8Gama Yesu ya ce masa kai aljani ka fito daga cikinsa."9Ya tambaye shi, "Yaya sunanka? Ya ce suna na tari gama muna da yawa. 10Ya yi ta rokonsa kada ya raba su da wannan yankin kasar.11Akwai babban garken aladu a wurin suna kiwo a gindin tsauni. 12Sai suka roke shi ya bar su su shiga cikin wadannan aladun. 13Shi kuma ya yardar masu. Aljanun suka fita suka shiga cikin aladun su kimanin dubu biyu. Aladun dubu biyu suka gangaro daga gindin tsaunin suka fada cikin ruwa.14Mutanen da ke kiwon aladun su ka shiga cikin gari da kewaye suka bada labarin abin da ya faru. Mutane da yawa suka je su ga abin da ya faru 15Sai suka zo wurin Yesu suka ga mutumin mai aljanun a zaune, cikin hankalinsa, saye da tufafi, sai suka tsorata.16Wadanda suka zo su ka ga abin da ya faru da mutumin mai aljanun, suka je suka fada wa mutane abin da suka gani game da aladun. 17Mutanen suka roke shi ya fita daga yankin kasarsu.18Shi mutumin da aljanu ke iko da shi, sa'adda ya ga Yesu zai shiga cikin jirgin ruwa ya tafi, ya roki Yesu da ya bi shi. 19Amma Yesu bai yarda masa ba. Ya ce masa ka tafi gidanku, wurin mutanenka ka gaya ma su alherin da Ubangiji ya yi maka. 20Mutumin ya shiga cikin Dikafolis yana shaidar babban abin da Yesu ya yi masa, dukansu suka cika da mamaki.21Sa'adda Yesu ya sake ketaren kogin zuwa daya gefen, acikin jirgin, sai taron jama'a suka keweye shi, a gefen tekun. 22Sai wani daya daga cikin shugabannin Majami'a mai suna Yayirus, ya zo, wurinsa sa'adda ya ganshi ya durkusa a gabansa. 23Ya yi ta rokonsa, yana cewa, "Diya ta ba ta da lafiya har ma ta kusa mutuwa. Ina rokonka mu je gida na ka dora ma ta hannu domin ta warke. ta rayu." 24Sai ya tafi tare da shi, babban taro suka biyo shi har ma suna matse shi.25Akwai wata mace wadda ta ke zubar jini ta kai tsawon shekara goma sha biyu. 26Ta sha wahala kwarai da gaske ta je wurin likitoci da yawa ta kashe kudi sosai, amma ba ta warke ba abin ma sai karuwa ya ke yi. 27Ta ji labarin Yesu. Sai ta biyo bayansa yana tafiya cikin taro, ta taba habar rigarsa.28Domin ta ce "Idan dai na taba ko da habar rigarsa zan warke." 29Da dai ta taba shi sai zubar jinin ta ta tsaya, ta ji a jikin ta ta warke, daga damuwarta.30Nan da nan, Yesu ya ji iko ya fita daga gare shi sai ya ce "wanene ya taba rigata?" 31Almajiransa suka ce, "a cikin wannan taron mutane da yawa ka ce wanene ya taba ni?" 32Amma Yesu ya waiga ya ga ko wanene ya taba shi.33Matar ta san abin da ya faru sai ta zo cikin tsoro da rawar jiki ta durkusa a gaban Yesu ta fada masa gaskiya. 34Sai ya ce da ita, "Diya bangaskiyarki ta warkar da ke, ki tafi lafiya kin sami warkewa daga cutarki".35Sa'adda ya ke magana da ita sai ga mutane daga gidan shugaban majami'a suka ce "Diyarka ta mutu me ya sa za ka dami malam?"36Amma sa'adda Yesu ya ji abin da suka ce, sai ya ce da shugaban majami'ar, "kada ka ji tsoro ka ba da gaskiya kawai." 37Bai bari kowa ya kasance tare da shi ba sai Bitrus da Yakubu da Yahaya dan'uwan Yakubu. 38Suka zo gidan shugaban majami'ar ya ga mutane suna bakin ciki, suna kuka sosai.39Sa'adda ya shiga gidan ya ce da mutane "Me ya sa kuke damuwa da kuka?" Yarinyar ba ta mutu ba barci ta ke yi. 40Sai su kayi masa dariya. Amma ya fitar da su waje su duka. Ya kira baban yarinyar da mamar ta da wadansu da ke tare da shi su ka shiga wurin da yarinyar ta ke.41Ya kama hannun yarinyar ya ce da ita "Tilatha koum" wato yarinya na ce ki tashi" 42Nan da nan yarinyar ta tashi ta yi tafiya (gama shekarun ta sun kai goma sha biyu). Nan da nan mutanen suka yi mamaki kwarai da gaske. 43Ya ummurce su da gaske kada kowa ya sani. Ya ce da su su ba ta abinci ta ci.
Bayan Yesu ya kwantar da iska, ya wakar da wani mutum da ke da aljannu, amma Garasinawan ba su yi murna domin ya yi warkarwa ba, saboda haka sun roƙe Yesu ya tafi.
Kalman nan "Su" na nufin Yesu da Almajiransa.
Wannan na nufin Tekun Galili.
Wannan suna na nufi mutanen da zama cikin Garasa.
Wannan karin magana ne da ke nufin cewa baƙin ajan na "mulki" ko "ya haukatar da shi". AT: "baƙin aljan na mulkinsa" ko "baƙin aljan ya haukatar da shi"
AT: "Mutane sun ɗaure shi da sarkoki sau da yawa"
AT: "ya tsintsinke sarkokinsa"
karafuna da mutan sukan kewa hannu da kafafun ɗan sarka su kuma haɗa shi da sarka da kuma wani abu da ba ya motsi don kada fursunan ya yi motsi
Mutumin na da ƙarfi har ma ba wanda zai iya ɗaure shi. AT: "Ya na da ƙarfi sosai har ma ba wanda ke da ƙarfin ɗaure shi"
"mulke shi"
Sa'ad da aljan ya mallake mutumin, so da dama aljan zai sa mutumin ya yi munanan abubuwa da zai hallakas da shi, wato abu kamar, yaiyanke kansa.
Da ganin Yesu, mai yiwuwa Yesu na koƙarin fitawa da jigin ruwa kenan.
Wannan na nufin cewa ya durkusa a gaban Yesu don ya girmama ya kuma daraja shi, ba ya na masa sujada ba.
Bayanin da ke waɗannan ayoyi biyun ana iya săke shirya shi don a iya ba da labarin daidai yadda ya faru, kamar yadda yake a UDB.
"Baƙin aljanin ya tada murya"
Baƙin aljanin ya yi wannan tambayar don ya ji tsoro ne. AT: "Rabu da ni, Yesu, Ɗan Allah Maɗaukaki! Babu wata dalili da zai sa ka sami sabani da ni."
Yesu na da ikon ba wa baƙin aljanin azăba.
Wannan lakani ne mai muhimmanci na Yesu.
A nan baƙin aljanin na ransuwa da Allah a sa'ada yana roƙo Yesu. Dubi yadda ake irin wannan roƙo a harshen ku. AT: "a gaban Allah ina roƙon ka" ko "na rantse da sunan Allah, ina roƙon ka"
"Sai Yesu ya tambaye baƙin ajan"
Ɗaya daga ciki aljanun na magana a maɗaɗɗin sauran. Ya yi magana game da su sai ka ce su rundunan, rundunar sojojin Romawa da ke kusan sojoji 6,000. AT: "Sai aljan ya ce masa, 'ka kira mu rundunan, domin dayawan mu muna cikin mutumin nan."
"bakin aljanun sun roke Yesu"
Zai iya zama da taimako in an bayana a fili abin da Yesu ya bar su su yi. AT: "Yesu ya bar baƙin aljanun su yi abin da suka roƙa"
"aladun suka ruga a guje"
Ka na iya raba wannan zuwa jimla daban dabam: "zuwa cikin teku. Aladun kusan dubu biyu ne, sun kuma hallaka a cikin tekun"
"aladu kusan 2,000"
Ana iya bayana a fili cewa mutanen sun ba da rohoto abin da ya faru ga mutanen da ke cikin gari da kewaye. AT: "ga mutanen cikin gari da kewaye"
Wannan sunan aljanun da dã suna cikin mutumin. Dubi yadda ka juya wannan cikin [Markus 5:9].
Wannan na nufin cewa yana tunani da kyau. AT: "hankalinsa daidai" ko "tunani da kyau"
Kalman nan "su" na nufin mutanen da suka je su ga abin da ya faru.
"Mutanen da sun ga abin da ya faru"
Kodashike a yanzu mutumin ba shi da aljan, akan bayana shi a haka. AT: "mutumin da dã ke da aljan"
Ana iya bayana a fili abin da Yesu bai ba shi daman yi ba. AT: "Amma bai bar mutumin ya bi su ba"
Wannan suna wani yanki ne da ke nufin Birane Goma. Ya na a kudu-gabacin Tekun Galili.
Zai zama da taimakon in an bayana dalilin da ya sa mutanen suka yi mamaki. AT: "dukkan mutanen da suka ji abin da mutumin ya faɗa sun yi mamaki"
Zai zama da amfani in an kara bayani a wannan magana. AT: "ɗayan bangaren teku"
"a bakin tekun" ko "gaɓar teku"
Wannan sunan mutum.
"sai Yesu ya tafi tare da Yayirus." Almajiran Yesu ma sun tafi tare da shi. AT: "Sai Yesu da Almajiran sun tafi tare da Yayirus"
"Sa hannu" na nufin annabi ko malami ya sa hannunsa a kan wani, yana kuma warkar da shi ko sa masa albarka. A wannan al'amari, Yayiru yana tambayar Yesu ya warkar da 'yarsa.
AT: "ya kuma warkar da ita da sa ta ta rayu"
Wannan na nufin sun taru kewaye da Yesu sun matse kansu don su yi kusa da Yesu.
"yanzu" na bada alaman cewa an gabatar da wannan macen a labarin. Dubi yadda kuna gabatar da abon mutum cikin labarin a harshen ku.
Macen ba ta da wani ciwon da ke a buɗe; maimakon haka, hailar ta bai tsaya ba. Mai yiwuwa harshen ku na da wata hanya mai da'a da ana iya faɗin wannan yanayi.
"tsawon shekara 12"
"rashin lafiyar sai karuwa ya ke yi" ko "zub da jinin sai karuwa ya ke yi"
Ta ji labari game da Yesu yadda ya warkar da mutane. AT: "cewa Yesu ya warkar da mutane"
rigar da ake sa a waje ko kwat
AT: "zai warkar da ni" ko "ikonsa za ta warkar da ni"
AT: "cutar ya bar ta" ko "ta sami lafiya"
Sa'ad da macen ta taɓa Yesu, Yesu ya ji ikon warkar da ita.Yesu kansa bai rasa ikonsa na warkar da mutane ba sa'ad da ya warkar da ita. AT: "cewa ikonsa na warkarwa ya warkar da macen"
Wannan na nufin sun taru kewa da Yesu, sun matse junansu don su yi kusa da Yesu. Dubi yadda ka juya wannan cikin [Markus 5: 24]
"durkusa a gabansa." Ta durkusa a gaban Yesu a matsayin girmamawa da mika kai.
Maganan nan "gaskiyar gabakiɗaya" na nufin yadda ta taɓa shi har ta warke. AT: "faɗa masa gaskiyar gabakiɗaya game da yadda ta taɓa shi"
Yesu ya yi amfani da wannan kalma don yana duban macen a matsayin maibi.
"bangaskiyar ki a ciki na"
"Sa'ad da Yesu ke magana"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) waɗannan mutane sun zo daga gidan Yayirus ko 2) Yayiru ya riga ya umurce waɗannan mutane su zo su ga Yesu ko 3) mutumin da ke shugaban majami'a a sa'ad da Yayiru ba ya nan, shine ya turo waɗannan mutane.
"shugaban majamia" shine Yayirus.
"majami'a, cewa wa Yayirus"
AT: "Ba shi da amfani a dame malamin kuma." ko "Ba ku bukata ku dame malamin kuma."
Wannan na nufin Yesu.
In lallei ne, to ana iya faɗin abin da Yesu yake umurtan Jarus ga bada gaskiya ga shi. AT: "Ka dai gaskanta cewa zan ta da 'yar ka"
Cikin waɗannan ayoyi kalman nan "Ya" na nufin Yesu.
"ya bi shi ba." Zai zama da taimakon in an faɗa wurin da za suna koƙarin zuwa. AT: "ya bi shi zuwa gida Shugaban majami'a"
"Yesu ya cewa mutenen da suke kuka"
Yesu ya yi wannan tambaya don ya taimake su su ga reashin bangaskiyarsu. AT: "Wannan ba lokacin damuwa da kuka ba ne."
Yesu ya yi amfani da kalman da an saba amfani da ita na barci, haka kuma sai a yi amfani da shi a juyin. Ya kamata masu karatun su fahimta cewa mutanen da ke sauraron Yesu sun yi masa dariya domin ba su san bambanci tsakanin mutumin da ya mutu da wanda ya ke barci ba, suna kuma tunanin cewa shi bai sani ba.
"ya fitar da sauran mutanen da ke cikin gidan zuwa waje"
Wannan na nufin Bitrus, Yakub da Yahaya.
Zai zama da taimakon in an bayana inda yarinyar take. AT: "shiga cikin ɗakin da yarinyar take kwanciye"
Wannan jimlar da harshe Yahudanci ne, wanda Yesu ya yi magana da karamar yarinyar cikin harshen ta. Ku rubuta waɗannan kalmomin kamar yadda yake da haruffan ku.
"shakarun ta 12 ne"
AT: "Ya umurce su da gaske, 'kada kowa ya san game da wannan!' Sa'annan" ko "Ya umurce da gaske, 'Kada ku gaya wa kowa game da abin da na yi!' Sa'annan"
"Ya ba su umurni da gaske"
AT: "Sai ya ce masu, 'Bata abinci ta ci"
1Ya bar su ya zo garinsu, almajiransa su ka biyo shi. 2Sa'adda ranar Asabar tazo ya shiga cikin masujada ya yi koyarwa. Mutane da yawa da su ka ji koyarwarsa su ka yi mamaki, suka ce daga ina ya sami irin wannan koyarwar? Wacce irin hikima ce Allah ya ba shi haka? Wadanne irin ayyukan al'ajibi ya ke yi da hannuwansa? 3Wannan ba kafintan nan ba ne dan Maryamu, dan'uwan Yakubu da Yosi da Yahuza da Saminu? Ba ga 'yan'uwan sa 'yan mata mu na tare da su ba? Ba su ji dadi ba a ransu saboda Yesu.4Yesu ya ce, "Annabi ba ya rasa daraja sai a gidansa da garinsa da cikin danginsa." 5Bai iya yin wani aikin al'ajibi a wurin ba sai dai mutane kadan marasa lafiya ya dorawa hannu ya warkar da su. 6Rashin bangaskiyarsu ya ba shi mamaki. Sai ya tafi cikin kauyuka na kewaye da su ya yi ta koyarwa.7Ya kira almajiransa su goma sha biyu, ya aike su biyu-biyu, ya ba su iko a kan aljanu, 8ya dokace su kada su dauki komai tare da su domin wannan tafiya, sai dai sanda kadai. Kada su dauki abinci ko jaka ko kudi a cikin aljihunsu, 9sai dai su sa takalmi kadai, kada su sa taguwa biyu a jikinsu.10Ya ce da su, idan ku ka shiga wani gida sai ku zauna a gidan har lokacin da za ku tashi. 11Idan ku ka je wani gari aka ki karbar ku, ku karkabe kurar da ke kafufunku ta zama shaida kan mutanen garin.12Sai suka tafi suka yi ta shela ga mutane cewa su tuba daga zunubansu. 13Sun fitar da aljanu da yawa, suka shafawa mutane da yawa mai suka warkar da su.14Sarki Hirudus ya ji wannan, gama sunan Yesu ya zama sananne a wurin kowa da kowa. Wadansu suna cewa Yahaya mai yin baftisma ne ya tashi daga matattu shi ya sa ake yin wadannan ayyukan al'ajibi ta wurinsa. 15Wadansu kuma suna cewa, "Iliya," Har yanzu wadansu suna cewa daya "daga cikin annabawa ne na da can."16Sa'adda Hirudus ya ji wannan sai ya ce, "Yahaya wanda na fillewa kai shine ya tashi." 17Saboda Hirudus ne ya sa aka kama Yahaya aka kulle shi a kurkuku saboda Hirodiya( matar Filibus dan'uwansa), domin ya aure ta.18Saboda Yahaya ya gaya wa Hirudus cewa bai halarta ya auri matar dan'uwansa ba. 19Sai ita Hirodiya ta yi kudurin ta kashe Yahaya amma bai yiwu ba. 20Domin Hirudus yana jin tsoron Yahaya, domin ya sani shi mai adalci ce, mai tsarki kuma. Domin haka Hirudus bai so wani abu ya faru da Yahaya ba, amma ya kan fusata idan ya ji wa'azin yahaya. Duk da haka da fari ciki yakan saurare shi.21Amma sai dama ta samu inda Hirodiya za ta iya yin abin da ta ke so ta yi. A lokacin kewayowar ranar haihuwar sa, sai Hirudus ya shirya liyafa domin manyan da ke aiki tare da shi a cikin gwamnatin sa, da shugabannin da ke cikin Galili. 22Diyar Hirodiya ta zo ta yi masu rawa, rawarta kuwa tagamshi Hirudus da bakinsa. Sarki ya ce da yarinyar, "ki tambayi duk abin da ki ke so ni kuwa zan ba ki shi".23Ya rantse mata da cewa"Ko menene ki ka ce ki na so, ko da rabin mulkina ne" 24Sai ta fita ta je ta tambayi mamarta, "me zan ce ya bani?" Sai ta ce kan Yahaya Mai Yin Baftisma. 25Sai ta dawo da sauri cikin dakin taro wurin sarki ta ce da shi, "Ina so ka ba ni kan Yahaya Mai Yin Baftisma a cikin tire."26Sarki ya damu kwarai, amma saboda ya yi alkawari ga kuma ofisoshinsa, ba dama ya ce a'a. 27Sai sarki ya aiki wani soja ya ba shi ummurni ya je ya kawo kan Yahaya. Sojan ya je ya fillo kan sa daga cikin kurkuku. 28Ya kawo kan a cikin tire ya ba yarinyar, yarinyar kuma ta kai wa mamarta. 29Da almajiran su ka ji labari, suka zo suka dauki gawarsa suka rufe a cikin kabari.30Almajiran suka zo wurin Yesu, suka fada masa dukkan abin da suka yi da abin da suka koyar. 31Sai ya ce da su "ku je cikin kebabben wuri domin ku huta kadan," domin mutane suna ta kaiwa da komowa, ba su sami damar hutawa ba balle su ci abinci 32Sai suka tafi kebabben wuri a cikin jirgin ruwa su kadai.33Amma mutane da yawa sun gansu suna tafiya sun kuma gane su, sai suka fito daga cikin dukan garuruwa da gudu har su ka kai wurin kafin su zo. 34Sa'adda suka zo bakin gaba Yesu ya ga taron mutane da yawa sai ya ji tausayinsu domin sun yi kamar tumakin da ba da mai kiwo. Sai ya cigaba da koya masu abubuwa da yawa.35Sa'adda yamma ta yi, almajiran sa suka zo suka ce da shi, "wurinnan kebabben wuri ne kuma ga lokaci ya tafi. 36Ka sallami mutanen nan domin su shiga cikin garuruwa da kauyuka da ke kusa domin su sayi abin da zasu ci.37Amma sai ya ba su amsa ya ce,"Ku ku basu abinci su ci mana". Sai suka ce da shi, "ma iya zuwa mu sawo gurasa ta sule dari biyu mu basu su ci?" 38Sai ya ce dasu, "Dunkulen gurasa guda nawa kuke dasu? Kuje ku gani." Dasuka gano sai suka ce da shi, dunkule biyar ne da kifi guda biyu."39Sai ya ba da umarni mutanen su dukka su zauna a kan danyar ciyawa. 40Suka zauna kungiya kungiya wadansu su dari wadansu hamsin. 41Sai ya dauki dunkulen gurasa guda biyar da kifi guda biyu, ya ta da kansa sama, yasa albarka, ya kakkarya dunkulen gurasan, ya ba almajiran domin su rabawa taron jama'a duka.42Dukansu suka ci suka koshi. 43Suka tattara gutsattsarin gurasar suka cika kwanduna guda goma sha biyu da gutsattsarin da kuma gutsattsarin kifin. 44Mutanen da suka ci gurasar sun kai mutum dubu biyar.45Nan da nan ya ce almajiran sa su hau jirgin ruwa su yi gaba kafin ya zo, su je Baitsaida. Shi kuma ya tsaya domin ya sallami taron mutanen. 46Bayan da suka tafi shi kuma ya hau kan dutse domin ya yi addu'a. 47Har yamma ta yi jirgin ruwan ya na tsakiyar rafi shi kuma yana kan tudu shi kadai.48Ya gansu suna wahala gama iska ta hana su tafiya. Wajan karfe hudu na asuba sai ya tawo wurin su yana tafiya a kan ruwa, yana so ya wuce gaban su. 49Sa'adda suka gan shi ya na tafiya a kan ruwa suka yi tsammani fatalwa ce, suka yi ihu, 50gama su duka sun gan shi, tsoro ya kama su. Sai nan da nan ya yi magana dasu ya ce, "Ku karfafa ni ne! kada ku ji tsoro!"51Ya shiga cikin jirgin ruwan tare dasu, sai iska ta dena bugawa. Sai suka yi mamaki kwarai. 52Gama basu gane batun dunkulen ba. Maimakon haka, sai zukatansu suka taurare.53Sa'adda suka haye su zo kasar Janisarita suka sa wa jirgin sarka. 54Su na fitowa daga cikin jirgin kenan, mutane suka gane cewa Yesu ne. 55Mutane suka ruga cikin yankin su, suka kawo marasa lafiya a bisa shinfidun su zuwa wurinsa, dukan inda suka ji yana zuwa.56Ko ina ya shiga birni da kauye, ko a cikin kasar sukan kawo marasa lafiya a kasuwanni suna rokonsa su taba ko da habar rigarsa, dukan wadanda suka taba kuwa suka warke.
Yesu ya komo garinsa, inda ba a karɓarsa.
Wannan na nufin garin Nazarat, inda Yesu ya yi girma da inda iyalinsa suke zama. Wannan ba ya nufin cewa yana da nasa fili a wurin.
AT: "Macece wannan hikima da ya samu?"
Wannan magana na nanata cewa Yesu kansa yana yin abin al'ajibin. AT: "wanda shi kansa ya yi"
Waɗannan tambayoyin ana iya rubuta su cikin jimlar da ba tambaya ba. AT: "Wannan kafinta ne kawai! Mun san shi da iyalinsa. Mun san uwa tasa Maryamu. Mun san 'yan'uwansa Yakubu, Yosi, Yahuza da kuma Saminu. 'yan'uwansa mata kuma suna tare da mu."
"wa taron"
AT: "Ana daraja Annabi a koyaushe, sai" ko "Wurin da ba a daraja annabi shine"
Annabi da malami na iya sa hannu a kan mutane don ya warkar da su ko albarkace su. Wannan yanayi, Yesu yana warkar da mutane ne.
Umurnin Yesu a aya 8 da 9, ana iya sake kasafa shi ta wurin raba abin da ya gaya wa almajiransa su yi daga abin da ya ce masu kada su yi, kamar yadda yake a UDB.
A nan kalman nan "kira" na nufin cewa ya urmuce sha biyun su zo wurinsa.
"2 da 2" ko "cikin biyu"
A nan "gurasa" na nufin abinci. AT: "ba abinci"
A wancan al'ada, mazaje na ɗauka kuɗi su ajiye a cikin damararsu. AT: "ba kuɗi a cikin jakunan kuɗinsu" ko "ba kuɗi"
"Yesu ya cewa sha biyun"
A nan "zauna" na nufin komowa zuwa gidan ko wani ranar don su ci su kuma yi barci a wurin. AT: "ku ci, ku kuma kwanta a wannan gida har sai lokacin da za ku bar wannan wuri"
"ta zama shaidan a kansu." Zai zama da taimako a bayana yadda wannan ya zama shaida a gare su. "ta zama shaida a gare su. Tawurin yin haka, za ku shaidi cewa ba su marabce ku ba"
Kalman nan "su" na nufin sha biyun, ban da Yesu. Zai zama da taimako kuma a bayana cewa sun tafi garuruwa daban dabam. AT: "Sun shiga garuruwa daban dabam"
A nan "juyo daga" na nufin a daina yi wani abu. AT: "bar yin zunubi" ko "tuba daga zunubansu"
Zai iya zama da taimako a faɗa cewa sun fitar da aljanu daga cikin mutane. AT: "Sun fid da aljanu da yawa daga cikin mutane"
Kalman nan "wannan" na nufin dukkan abin da Yesi da almajiransa sun yi ta yi a garuruwa daban dabam, duk da fid da aljannu da kuma warkar da mutane.
Wasu suna cewa Yesu, shine Yahaya Mai Baftisma. Wannan ana iya bayana shi a fili. AT: "Waɗansu suna cewa, "Shine Yahaya Mai Baftisma ne wanda aka"
"Tashi daga mattattu" anan wata karin magana ne na "sa mutum ya rayu kuma." AT: "Ana tashe Yahaya Mai Baftisma kuma" ko "Allah ya sa Yahaya Mai Baftisma ya rayu kuma"
Zai zama da taimakon in an bayana cewa wasu mutane suna tunanin cewa shine Iliya. AT: "Waɗansu sun ce, 'Iliya ne wanda Allah ya yi alkawari zai aika kuma.'"
A nan Hirudus ya yi amfani da kalman nan "na" don yana nufin kansa ne. Kalman nan "na" na nufin sojijin Hirudus. AT: "wanda na umurci sojoji na su fille kansa"
AT: "yana raye kuma"
AT: "Hirudus ya aiki sojojinsa su kama Yahaya su kulle shi a kurkuku"
"umurta a"
"ta dalili Hirodiya"
"matar ɗan'uwansa Filibus." Filibus ɗan'uwan Hirudus ba ɗaya ne da Filibus wanda an ambata cikin littafin Ayukan Manzani ko Filibus ɗaya daga cikin almajiran sha biyu na Yesu.
"domin Hirudus ya aure ta"
Hirodiya shine kan maganan wannan magana "ta" na nufin cewa ta na so wani ya kashe Yahaya. AT: "ta na so wani ya kashe shi amma ba ta iya kashe shi ba"
Waɗannan magana biyu ana iya haɗa don ya nuna a fili dalilin da ya sa Hirudus yana jin tsoron Yahaya. AT: "domin Hirudus yana jin tsoron Yahaya domin ya sani"
"Hirudus ya sani cewa Yahaya mutum ne mai adalci"
yakan saurare Yahaya"
A nan kalman nan "ya" na nufin Hirudus, yana kuma na nufin bawansa wanda ya bada umurni a shirya liyafa. AT: "ya shirya liyafa domin manyan ma'aikatansa ... Galili" ko "ya gayaci manyan ma'aikatansa ... Galili ci su kuma yi murna tare da shi"
wata abinci ta musamman ko liyafa
Kalman nan "kanta" an yi amfani da ita don nanata cewa yana da muhimmanci cewa 'yar Hirudiya ne wanda ta yi rawa a lokacin liyafa.
"shigo cikin dakin"
"zan ba ki har rabin abin da nake da shi da mulkina, in kin roƙa"
"fita daga dakin"
"kan katako" ko "a kan babban kwano da aka yi da itace"
Ana iya bayana abin da ke cikin alkawarin, da kuma dangantaka tsakanin alkawarin da bakin da sun zo liyafa, a fili. AT: "domin baƙin sun ji ya yi alkawarin cewa zai ba ta kowane abin da ta roƙa"
"a kan tire"
"Sa'ad da almajiran Yahaya"
wurin da ba kowa
Wannan na nufin cewa mutane suna zuwa wurin manzanin su kuma koma.
Kalman nan "su" na nufin manzanen.
A nan kalman nan "su" na nufin manzanen da Yesu.
"mutanen sun ga Yesu da manzanen suna tafiya"
Mutanen suna tafiya a kafa, wannan kuwa ya zama da bambanci da tafiyar almajiran a kwalekwale.
"Yesu ya ga gaggaruman taro"
Yesu ya kwatanta mutane da tumakin da sun rikice a sa'ad da ba su da makiyayi da ke shugabantansu.
Wannan na nufin can da yamma. AT: "Sa'adda yamma ya fara yi" ko "Can da rana"
"Amma Yesu ya amsa ya cewa almajiransa"
Almajiran sun yi wannan tambaya don su bayana cewa babu wata hanya da za su iya sayan abinci da zai ishe taron. AT: "Ba za mu iya sayan gurasa wanda zai isa ciyad da wannan taron ba, ko muna da denari ɗari biyu!"
"denari 200." Mufuradin wannan kalman "denari" shine "denarus." Denarus guda kuɗi ne na azurfa wanda Romawa ke amfani da shi a wancan lokaci don biyan hakin ma'aikata a rana ɗaya.
dunƙulallen gurasa da aka yi.
Ku bayana ciyawan da kalman kalan da ake amfani da shi a harshen ku na ciyawa mai kyau, wanda maiyiwuwa ba kore ba.
Wannan na nufin mutane da ke kowane kungiya. AT: "mutane kunsan hamsin a wasu kungiya, wasu kuma mutane kusan ɗari wa wasu kungiyan"
Wannan na nufin cewa ya daga kansa ya dubi cikin sama, wanda ake kamata shi da inda Allah yake.
"ya albarkaci" ko "ya mika godiya"
"ya raba kifi biyun don kowa ya samu"
Ma'ana ma yiwuwa na kamar haka 1) "Almajiran sun tattara" ko 2) "Mutanen sun tattara."
"gursarin gurasar sun cika kwanduna goma sha biyu"
"kwanduna 12"
"maza 5,000"
Ba a lisafta yawan mata da 'ya'ya ba. Idan ba za a iya fahimtar cewa ba a ambata yawan mata da 'ya'ya ba, to za a oya bayana a fili. AT: "mutum dubu biyar sun ci gurasan. Ba ma kirga mata da yara ba"
Wannan na nufin Tekun Galili. Anan iya bayana wanna a fili. AT: "zuwa wata bangaren Teku Galili" (Dubi: gs_ellipsis)
Wannan gari ne a arewacin Tekun Galili.
"Sa'ad da mutanen sun tafi"
Wannan lokaci ne tsakanin 3 a.m.
ruhu matatcen mutum ko kuwa wasu irin ruhu
Waɗannan jimla biyun suna da ma'ana kusan iri ɗaya, suna kuma nanata cewa almajiran ba sa bukatan su ji tsoroI. In ta zama wajibi, ana iya haɗa su su zama ɗaya. AT: "Kada ku ji tsoro!"
In kuna bukatan ku bayana a fili abin da ya sa su mamaki za ku iya yi. AT: "Sun yi mamakin abin da ya yi"
A nan maganan nan "gurasan" na nufin sa'ad da Yesu ya ninka dunƙunlen gurasa. AT: "abin da ake nufi da cewa Yesu ya ninka gurasan" ko "abin da ake nufin sa'ada Yesu ya sa dunkulen gurasa ta karu ta yi yawa"
Taurin zuciya na nufin kin ji don a fahimta. AT: "sun taurare zuciyar har sun kãsa fahimta"
Wannan sunan yankin arewa maso yammacin Tekun Galili.
Zai zama da taimako in an bayana dalili da ya sa sun ruga zuwa cikin yankin. AT: "sun ruga zuwa cikin yankin don ya gayawa sauran mutane cewa Yesu yana wurin"
Kalman nan "su" na nufin mutane sun gane Yesu, ba almajiran ba.
Wannan magana na nufin mutane. AT: "mutane marasa lafiya"
"Duk inda Yesu ya shiga"
A nan "su" na nufin mutanen. Ba ya nufin almajiran Yesu.
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) "Marasa lafiyan sun roƙe shi" ko 2) Mutanen sun roƙe shi."
Kalman nan "su" na nufin marasa lafiyan.
"bakin tufafinsa" ko "gefen rigarsa"
"dukkan waɗanda"
1Farisawa suka taru wurin Yesu tare da wadansu marubuta wadda suka zo daga Urushalima.2Sun ga cewa wasu daga cikin almajiransa sun ci gurasa da hannuwa marasa tsabta, wato, basu wanke hannu ba, 3(Domin Farisawa da dukan Yahudawa ba su cin abinci sai dole sun wanke hannu da kyau domin suna kiyaye al'adun dattawa. 4Idan Farisawa suka dawo daga kasuwa, wajibi ne su yi wanka kamin su ci abinci. Akwai sauran al'adun da suke kiyayewa, kamar wanke moda, tukwane, da wasu santula na dalma, har da dakin cin abinci.)5Farisawa da Marubuta suka tambaye Yesu, "Don me almajiran ka basu kiyaye al'adun dattawa, domin suna cin abinci ba tare da sun wanke hannu ba?"6Amma ya amsa masu cewa, "Ishaya ya yi anabci akan ku masu bautan ganin ido, da ya rubuta cewa 'wadanan mutane suna girmama ni a baka amma zuciyar su tana nesa da ni. 7Sujadar wofi suke mani suna koyar da ka'idodi na mutane a matsayin rukunansu'".8Kun watsar da dokar Allah sai kuka rungumi al'adun mutane. 9Sai yace masu, kun yi nasara wurin kau da dokokin Allah domin ku kiyaye al'adun ku na mutane. 10Koda shike Musa ya rubuta cewa, "ka girmama Ubanka da Uwarka", kuma, "duk wanda ya zagi Ubansa ko Uwatasa, ya cancanci mutuwa nan take".11Amma kun ce, 'idan mutum ya ce wa iyayensa, "duk taimakon da ya cacanci ku samu daga guna ya zama kebabbe (wato, 'na mika wa Allah)"'. 12Sabo da haka, kun ba shi izini kada ya yi wa Ubansa ko Uwatasa wani abu. 13Kuna mayar da dokan Allah abin banza, sabili da al'adun ku da kuka mika masu. Wannan, da wasu abubuwa kamar haka kuke yi."14Ya kara kiran taron jama'ar yace masu, "ku kasa kunne gareni, kuma ku gane. 15Babu wani abu daga wajen mutum da zai iya gurbatar da shi har idan ya shiga cikinsa. Amma, abinda ya fita daga cikinsa shike gurbatar da shi" 16Bari mai kunnen ji, ya ji.17Da Yesu ya bar taron jama'ar, ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi ma'anar wannan misali. 18Sai Yesu yace, 'ashe baku da ganewa? ko baku sani cewa abin da ya shiga cikin mutum daga waje ba zai iya gurbatar da shi ba, 19domin ba zai iya kai wa cikin zuciyarsa ba, sai dai ya shiga cikin sa ya kuma fita a matsayin bayan gari a salga". Da wannan magana, Yesu ya mayar da dukan abinci ya zama da tsabta.20Ya ce, abinda ke cikin mutum shike gurbatar da shi 21Domin daga cikin mutum, kuma daga cikin zuciyarsa ne, mugun tunani, lalata, sata, kisa, 22zina, kwadayi, mugunta, hai'inci, mugun guri, kishi, zargi, girmankai, wawanci. 23Duk wadannan miyagun abubuwa suna fitowa ne daga cikin mutum, kuma suke gurbatar da shi."24Ya tashi daga nan ya tafi shiyyar Sur da Sida. Ya shiga wani gida don baya son wani ya sani cewa yana nan, amma bai iya boyuwa ba. 25Amma nan da nan wata mace, wadda diyarta ke da mugun ruhu-wannan mace kuwa ta ji game da Yesu sai ta zo ta durkusa a gabansa. 26Matar yar kasar Girka ce, kuma asalinta daga Fonishiya take. Ta roke shi da ya fitar da mugun ruhun nan daga diyarta.27Sai ya ce mata, "Bari a ciyar da 'ya'ya tukuna. Domin bai kamata a dauki abincin yaya a ba karnuka ba". 28Sai ta amsa masa cewa, "I, Ubangiji, Karnukan ma sukan ci abincin da ke fadowa daga teburin 'ya'yan."29Ya ce mata, "domin kin fadi haka, kina iya ki tafi domin aljani ya fita daga diyarki." 30Ta koma gida sai ta iske diyarta na kwance akan gado, aljanin ya fice daga jikinta.31Ya sake fita daga shiyar Sur, ya biyo ta Sidon, har zuwa tekun Galili a shiyar Dikafolis. 32Sun kawo masa wani kurma, kuma bebe ne shi, suna rokansa ya dora hanuwansa a bisansa.33Sai ya jawo shi daga taron jama'ar, zuwa gefe, sai ya sa hanunsa a kunuwan beben bayan ya tufa yawunsa, sannan ya taba harshensa. 34Ya dubi sama, ya ja numfashi ya ce masa, "Ifatha", wato, "bude!" 35Nan da nan ya mayar masa da jinsa. abinda ya daure harshensa ya sake shi, sai ya fara magana da kyau.36Ya umarce su da kada su gaya wa wani. Amma duk da umarnin da yake basu, suna ta shaida shi ko'ina. 37kuma suna ta mamaki cewa, "Yayi kowanne abu da kyau, har ya sa kurame suna jin magana, da kuma bebaye na magana."
Yesu ya kwaɓe Farisiyawa da kuma mallaman attaura.
"taru a wurin Yesu"
A aya ta 3 da 4, marubucin ya ba da shahararen bayani game da al'adu na wankin Farisawan domin ya nuna dalilin da ya sa Farisawan suka damu da cewa almajaren Yesu basu wanke hannayen su kafin su fara cin abinci ba. Za a iya kara juya wannan bayanin domin a samu ganewa me kyau, kamar yadda take a UDB.
"Farisawan da mallamen attauran suka gani"
Kalman nan "basu wanke hannu ba" ya yi bayanin dalilin rashin tsabtan hannayen almajaren. AT: "cewa, da hannayen da basu wanke ba" ko "cewa, basu wanke hannayen su ba"
Dattawan Yahudawan shugabane ne a wurin su, kuma su Mahukunta ne ga mutanen.
"butan dalma" ko "tukunyan karfe"
"benci" ko "gado." A wancan lokacin, Yahudawan zasu jingina a kai iɗan suna cin abinci.
"kiyaye" kalma ce na yin "biyayya." Farisawan da mallaman attaturan sun yi tambayan nan domin su tsokane ikon Yesu. AT: "Almajaren ka sun rashin biyayya ga ala'dun dattawan mu! Su wanke hannayen su ta wurin anfani da hanyan al'adun mu."
Wannan kalma ce da take nufin abinci gabadaya. AT: "abinci"
A nan "baki" kalma ce na magana. AT: "ta wurin abin da suka ce"
A nan "zuciya" ya nufin shauƙi ko tunanin mutum. Wannan hanya ce da take cewa mutane basu ba da lokacin su da gaske ga Allah ba. "amma ba su ƙaunace ni da gaske ba"
"Sujadar wofi suke mani" ko "A banza suka bauta mani"
ki yin biyayya
"rike da ƙarfi" ko "kadai kuka ajiye"
Yesu ya yi anfani da kalman nan domin ya kwaɓe masu jin sa domin sun rabu da Umurnin Allah. AT: "Ku na tunanin kun yi adalci ta wurin kau da dokokin Allah domin ku iya kiyaye al'adun ku, ko kadan, abun da kuka yi ba shi da kyau"
"Kamar yadda kuka yi fasaha ta wurin kin"
"duk wanda ya zagi"
"lalle a kashe shi"
" AT: "Lallei ne hukuma ta zartadda kisa ga wanda ya zagi ubansa ko uwarsa"
Al'adan mallaman attaura sun zartadda da cewa da zaran an yi kautan kuɗi ko wani abu wa haikali, ba za a yi anfani da su wa waɗansu abubuwa ba.
"keɓaɓɓe" kalmar Yahudawa ne da yake nufin abubuwan da mutane suka yi alkawali cewa zasu mika wa Allah. AT: "kauta ce ga Allah" ko "na Allah ne"
Kalman nan ya ba da ma'anan kalman Yahudawan nan "keɓaɓɓe." AT: "Na rigaya na mika wa Allah"
Ta wurin yin haka, Farisawan suna hana mutane tanaɗa wa iyaye, iɗan suka mika wa Allah abun da suka yarda zasu mika masa.
abin da aka share ko aka manta da shi
"wasu abubuwan da kuke yi suna nan ƙamar haka ne"
"Yesu ya kira"
Kalman nan "Kasa kunne" da kuma "gane" suna kama. Yesu yayi anfani da su domin ya nanata wa masu jin sa cewa su kassa kunne ga abin da yake faɗi.
Zai zama da taimako a faɗa masu abin da Yesu yake so su gane. AT: "ku gane abin da nake so kokarin in gaya maku"
Yesu yana magana akan abin da mutum yake ci ne. Wannan ya bambanta da "abin da yake fita daga mutum." "babu wanu abu daga wajen mutu da zai iya ci"
Wannan na nufin abin da mutum yake yi ne ko kuma yana faɗa. Wannan ya bambanta da "abin da yake wajen mutum da yake kai ciki." AT: "abin da yake fitowa da cikin mutum ne yake faɗa ko ya aikata"
Ana anfani da wannan kalman anan domin a nuna alamar dakatawa a cikin ainihin labarin. Yanzu Yesu ya yi nesa da jama'a, a wani gida tare da almajarensa.
Yesu yayi anfani da tambayan nan domin ya nuna rashin jin daɗin sa cewa basu gane ba. AT: "Bayan abubuwan da na fada, na kuma aikata, ina gani kaman kun gane."
A nan "zuciya" kalma ce da take nuna cikin mutum ko zukatar sa. Anan Yesu na nufin cewa abinci bashi da anfani ga hallin mutum. AT: " ba zai taba shiga cikin zukatar s ba"
Yesu yayi anfani da tambayan nan domin ya koya wa almajaren sa abin da yakamata da daɗewa su sani. AT: "abin da ya shisga ... salga."
A nan "shi" na nufin abin da yake shigo cikin mutum; abin da mutum yake ci kenan.
Zai iya zama da taimako a bayyana ma'anan kalman nan a fili. AT: "duƙan abinci ya zama da tsabta, na ma'anan cewa mutum zai iya cin kowane abinci ba tare da Allah ya sabtace mai ci din ba"
"Yesu ya ce"
"abinda ke gubatar da mutum, shi ke a cikin sa"
rashin ƙame kai ga sha'awa
A nan kalman "cikin" na bayyana zuciyar mutum. AT: "na fitowa daga cikin zuciyar mutum" ko "na fitowa daga cikin tunanin mutum"
A nan "zuciya" kalma ce da yake nuna cikin zukatar mutum. AT: "daga cikin mutum ne, mugun tunani ke fitowa" ko "daga zukata ne, mugun tunani ke ftiowa"
Wannan ƙarin magana ne wande yake nufin ta kamu da mugun ruhu. AT: "kamu da mugun ruhu"
"durkusa." Wannan ayukan ba da girma ne da kuma mika kai.
Kalman nan "Yanzu" na nuna alamar dakatawa a cikin ainihin labarin, wannan maganan kuma na bamu shahararen bayani game da matan.
Wannan suna ne na inda matar ta fito. An haife ta ne a Phoenician yankin Syria.
A nan Yesu yana magana akan Yahudawa kaman su 'ya'ya ne, Al'ummai kuma kaman ƙarnuka ne. AT: "Bari a fara ciyar da 'ya'yan Isra'ila tukuna. Domin ba daidai bane a dauki gurasar 'ya'ya a ba wa Al'ummai, wanda suke kaman karnuka"
AT: "Lalle ne mu fara ciyes da 'ya'ya Isra'ila tukuna"
Wannan na nufin kananan karnuka wanda ake ajiyewa a matsayin abin wasa.
Yesu na nufin cewa ba dalilin ta saya ta tambaye shi cewa ya taimaki 'yar ta. Zai yi mata. AT: "za ki iya tafiya yanzu" ko "za ki iya tafiya gida da salama"
Yesu ya saka mugun ruhun ya ar jikin diyar matar. AT: "Na saka mugun ruhun ya bar jikin 'yar ki"
"bar jihar Sur"
AT:1) "a jihar" Da Yesu yake tekun a jihar Dikafolis ko 2) "ta jihar" da Yesu ya bi ta jihar Dikafolis domin ya iso tekun.
Wannan sunan wata jiha ce da take ma'anar Gariruwa Goma. Ana samun ta ne a ..................Galili
"Sai mutane suka kawo"
"wanda ba ya ji"
Annabai da mallamai suna saka hannuwan su akan mutane domin su wanrkas da su ko kuma su saka masu albarka. A wannan hali, mutane na roƙon Yesu ya warkas da wani mutum. AT: "sun roƙe Yesu ya saka hannun sa akan mutumin domin ya warkas da shi"
"Yesu ya dauki mutumin"
Yesu yana saka yatsosinsa a kunnen mutumin.
Yesu ya tofa wa mutumin yau, ya kuma taba harshen sa.
Zai iya zama da taimako a fadi cewa Yesu ya tofa yau a yatsosin sa ne. AT: "bayan da ya tofad da yau a yatsosin sa"
Wannan yana nufin cewa ya daga idanunsa zuwa sama, wanda ake zatto inda Allah yake.
A nan marubucin na nufin kalman da kalmar Aramaic. rubuta wannan kalma da sifar rubutu na ƙabilar ka. .........
Wannan na nufin cewa yayi nishi ko ya ja dogon numfashi da za a iya ji. Mai yiwuwa yana nuna tausayi d Yesu yake nuna wa mutum.
"faɗa wa mtumin"
Wannan na nufin cewa ya fara ji. AT: "kunnuwansa sun buɗu sai ya fara ji" ko "ya fara ji"
AT: "Yesu ya dauke abin da yake tsare harshen sa daga magana" ko "Yesu ya kwance harshen sa"
Wannan na nufin shi yake ba su umurni kada su fada wa kowa game da abin da yayi. AT: "duk da umarnin da yake basu kada su fada wa kowa"
"suna ta shaida shi ko'ina" ko "a yalwace"
"suka yi mamaki sosai" ko "suka yi mamaki kwarai" ko "suka yi mamaki gaba da kima"
Wannan na nufin mutane ne. AT: "kurmaye ... bebbe mutane" ko "mutanen da baswa iya ji ... mutanen da baswa iya magana"
1A kwanakin nan, akwai wani gagaruman taron mutane, kuma basu da abincin ci. Yesu ya kirawo almajiransa yace masu, 2"Ina tausayin taron mutanen nan domin kwana uku kenan suna nan tare da ni babu abinci. 3Idan na salame su su koma gidajensu ba tare da sun ci abinci ba, za su galabaita a hanya domin gidajensu na da nisa." 4Almajiransa suka amsa masa cewa, "A ina za mu iya samu gurasa a wannan jeji da zai ishi wadannan mutane haka?"5Ya tambaye su, "gurasa nawa kuke da su?" Sai suka ce, "Bakwai." 6Ya umarci mutanen da su zauna. Ya dauki gurasar bakwai, bayan da ya yi godiya, ya kakarya gurasar, sa'annan ya umarci almajiransa da su raba wa mutanen. Su kuwa suka raba masu.7Suna kuma da kananan kifaye kadan. Bayan da ya yi godiya akan su, ya umurci almajiran su rabawa mutanen. 8Sun ci sun koshi. Suka tattara ragowar, har sun cika kwanduna bakwai. 9Akwai maza kimanin dubu hudu a wurin. Yesu ya sallame su. 10Nan take, ya shiga jirgin ruwa da almajiransa zuwa shiyyar Dalmanuta.11Sai Farisawa suka zo suka fara gardama da shi. Suna nema ya nuna masu alama daga sama, domin su gwada shi. 12Ya ja numfashi a ruhunsa yana cewa, "Don me wannan tsarar tana neman alama. Hakika ina gaya maku, babu wata alama da za a ba wannan tsarar." 13Sai ya bar su ya sake shiga jirgin zuwa hayin tafkin.14A lokacin nan, almajiransa sun manta su dauki gurasa. Domin gurasa daya ce tak a garesu cikin jirgin ruwan. 15Ya gargade su, "ku yi hattara da yisti na Farisawa da Yisti na Hirudus."16Almajiran suka fara tattaunawa a tsakaninsu, "Saboda ba mu da gurasa ne." 17Yesu yana sane da wannan, sa'annan ya ce masu, "Don me kuke tattaunawa akan rashin gurasa? Har yanzu baku gane ba? Har yanzu ba ku da sane? Ko zuciyar ku ta duhunta ne?"18Kuna da idanu, ba ku gani? Kuna da kunnuwa, ba ku ji? Ba ku tuna ba? 19Da na kakkarya gurasar a cikin mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka samu ragowa? Suka ce masa, "Goma sha biyu."20Kuma da na kakarya gurasa bakwai a cikin mutane dubu hudu, kwanduna nawa kuka dauka cike da ragowar? Suka ce masa, "bakwai." 21Ya ce masu, "har yanzu baku gane ba?"22Sun zo Baitsaida. Mutanen wurin suka kawo masa wani makaho, sai suka roke shi ya taba shi. 23Yesu ya rike hanun makahon, ya jagorance shi zuwa bayan kauyen. Da ya tofa yawunsa a idon mutumin, kuma ya dora hanunsa akan mutumin, sai ya tambaye shi "kana ganin wani abu kuwa?"24Ya daga ido sai ya ce, "ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa." 25Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau. 26Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, "kada ka shiga cikin garin"27Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, "Shin wanene mutane ke ce da ni?" 28Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, "Iliya". wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa".29Ya tambaye su, "Amma me ku ke ce da ni?" Bitrus ya ce, "Kai ne Almasihu." 30Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.31Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu. 32Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.33Amma Yesu ya juya ya dubi almajiransa sa'annan ya tsautawa Bitrus yana cewa, "Ka koma bayana Shaidan, domin kana kula da abubuwan mutane ne kawai, ba na Allah ba." 34Sai ya kira taron jama'ar da almajiransa a wuri daya, ya ce masu, "Duk wanda yake so ya bini, dole ne ya musunci kansa, ya dauki giciyensa ya biyo ni.35Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi, amma duk wadda ya rasa ransa domina da kuma bishara zai cece shi. 36Me zai amfani mutum idan ya sami dukan duniya sannan ya rasa ransa. 37Me mutum zai bayar amaimakon ransa?38Duk wanda ke jin kunyata ko maganata a wannan mazinaciyar tsara mai zunubi, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa a lokacin da ya dawo cikin daukakar Ubansa da Malaiku masu tsarki."
Babban taron jama'an mutane da suke tare da Yesu suna jin yunwa. Yesu ya ciyes da su da gurasa biyer da kiman kifaye kafin shi da almajarensa suka shiga jirgi domin su je wani guri.
Ana anfani da wannan kalman domin a gabatar da sabon abu a cikin labarin.
"kwana uku kenan mutanen nan suna tare da ni, amma basu samu komai sun ci ba"
AT: 1) zahiri, " za su iya rasa hankulan su nan da nan" ko 2) misalin mangana "za su iya rasa ƙarfin su."
Almajaren suna mamaki cewa Yesu yana tsamanin cewa zasu sami ishashen abinci. AT: "Wannan wurin yayi shuru harma babu wurin da zamu samu ishashen gurasa da zai kosher da mutane!"
Gurasa dunkulen kunle ce da aka shirya ta a wata sifa sai a gasa shi.
"Yesu ta ya tambaye almajarensa"
Za a iya rubuta wannan kai saye a nassin. "Yesu ya umurci jama'an, 'Zauna a kasa'"
Yi anfani da kalmar kabilar ku domin nuna yadda mutane gargajiya suke cin abinci idan babu tabur, ko ta zama ko kwanciya.
Kalman nan "su" ana nufin Yesu da almajaren sa ne.
"Yesu ya yi godiya akan ƙifin"
"Mutanen suka ci"
"Almajaren suka tara"
Wannan na nufin raguwar ƙifi da gurasar bayan da mutane suka ci. AT: "raguwar gurasa da kuma ƙifin, wanda suka cika kwanduna baƙwai"
Zai zama da taimako a bayyana lokacin da ya sallame su. AT: " Bayan da suka ci, Yesu ya sallame su"
Zai zama da taimako a bayyana yadda suka kai Dalmanuta. AT: "suka yi ta yawo a tekun Galili a yankin Dalmanuta"
Wannan sunan wuri ne a kusa da arewa - kuɗu na tekun Galili.
"Suka tambaye shi akan"
Suna neman alama da zai tabbatar masu cewa iko Yesu daga Allah ne. 1) Kalman nan "sama" kalma ce da ke nufin Allah. AT: "alama daga Allah" ko 2) kalman nan "sama" na nufin sarari. AT: "alama daga sarari"
Farisiyawan sun yi kokari su gwada Yesu domin ya nuna masu ko shi daga Allah ne. AT: "ya tabbatar masu cewa Allah ne ya turo shi"
Wannan na nufin ya yi gardama ko ya ja numfashi da zurfi da mutane zasu iya ji. Mai yiwuwa ya nuna bacin ransa kwarai da Farisiyawan domin sunki su yarda da shi AT: [7:4]
"cikin sa"
Yesu yana masu faɗa. AT: "Kada wannan zamanin su nema alama"
A lokacin da Yesu yayi magana game da "wannan zamani," ya nufin mutane da suke rayuwa a lokacin ne. A wurin Farisiyawan ma an haɗa da su. AT: "ku da mutanen zamanin nan"
AT: "ba zan nuna alama ba"
Almajaren Yesu sun tafi tare da shi. Za a iya bayyana wasu bayanin a fili. AT: "ya bar su, ya shiga jirgin tare da almajaren sa"
Wannan ya yi bayanin tekun Galilin, wanda za a iya bayyana a fili. AT: a ɗayan gefe na tekun"
Ana amfani da wannan kalma domin a nuna alamar dakatawa a cikin ainhin labarin. Anan marubucin na ba da shahararen bayani game mantuwar da almajaren su ka yi su kawo gurasar.
Kalma mara amfanin nan "kar ya fi" ana anfani da shi a nuna kalilar yawan gurasar da suke da shi. AT: "gurasa ɗaya kawai"
Waɗanan kala
A nan Yesu yana magana da almajarensa a hanyan da zasu gane ne. Yesu yana kwatanta koyaswan Farisawa da kuma Hiridus game da yistin.
Za'a iya bayanin yanayin nan a fili. AT: "Idan sararin ta yi ja da asuba" ko "Idan sarari ta yi ja alokacin da rana tana tashiwa"
"Kun san yadda ake kallon sarari kun kuma gane wace irin yanayi ce za ku samu"
"Yesu yana magana game dazamanin sa ne. AT: "Ku muguye zamani maciya amana ne, wanda kuke neman alamu daga ni ... da za a baku" [12:39]
"saidai wancan alamar da aka ba wa annabi Yunusa."
A nan "yisti" magana ce da take nufin mugun shawara da kuma koyeswar ƙarya. Za a yi bayanin maganar nan gaba [16:12].
A nan "idanu" na nufin iko. AT: "inda dattawa, manyan firistoci da malaman attaura zasu ba shi wahala"
Wannan ƙarin magana ne da ke nufin "kada wannan ya faru." AT: "A' a" ko "Allah ya kiyaye wannan"
"sai ya guje wa sha'awan jikinsa" ko "sai ya bar sha'awar jikinsa"
Wannan na nufin mutane 4,000 da suka Yesu ya ciyes. AT: "mutane 4,000"
"Ina gaya maku gaskiya." Wannan kalmomin ƙari ce ga abin da Yesu ya fada a gaba.
Dukkan maganganun nan na nufin mala'ikun ne.
Wata gari ce wanda take kusa da Galili. [6:45]
Idan ya zama dole, za'a iya faɗin wannan maganan a wani juyi. AT: "Domin Yahaya ya faɗa wa Hiridus cewa bai kama Hiridus ya ɗauki Hirudiya a matsayin matar sa ba."
AT: "Bayan da mahaifuwarta ta umurce ta"
"Mutumin ya kalle sama"
A nan marubucin ya fara faɗa yadda Hiridus ya kashe Yahaya mai Baftisma. Waɗannan abubuwan sun faru a wasu lokatai kafin abun da ya faru a ayoyin da suka wuce.
"Sai Yesu ya kuma"
Idon akwai bukata, za ka iya mika yadda abubuwan suka faru a 14:3-4, yadda take a UDB
"Suka amsa shi, suna cewa"
Almajarensa suka amsa shi suka ce ga abin da mutane na cewa game da kai. AT: "Wasu sun ce kai Yahaya mai Baftisma ne"
Suka ce kai ne Yahaya mai Baftisma.
Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa cewa shi Almasihu ne. AT: Yesu ya umurce su, kada ku gaya wa kowa cewa ni Almasihu ne'"
Wannan lakani ne mai muhinminci na Yesu.
Wannan na faɗi cewa Hiridus yayi haka ne, domin ya umurce wasu ne suyi mashi. AT: "Hiridus ya umurce sojojin sa su kamo Yahaya mai Baftisma, su ɗaure shi, su kuma jefa shi a kurkuku"
Filibus dan'uwan Hiridus ne. Hiridus ya ɗauki matar Filibus ta zama matar sa.
AT: "a tsakanin baƙi da suka je bukin aihuwar"
AT: "Bayan da mahaifuwarta ta umurce ta"
"Ka yi nesa da ni"
Bin Yesu a nan na nufin zama ɗaya daga ciikin almajeren sa, AT: "zama almajerina " zama ɗaya daga ciikin almajerina"
AT: " Rokon da tayi ya saka Sarki bakin ciki sosai"
AT: "ya umurce mutanen sa su yi abin da ta faɗa"
"Ga duk wanda yake so"
Wannan na nnufin rayuwa ta jiki da na ruhaniya.
"domina da kuma bishara." Yesu yana magana game da mutanen da suka rasa ransu domin sun bi shi da kuma bisharar sa. AT: "domin ya bi ni ya kuma yi wa waɗansu bishara"
AT: "Idan ma mutum ya samu dukan duniya, ba riɓa bane idan ya rasa ransa."
AT: "idan ya samu dukkan duniya ya kuma rasa ransa"
Kalman nan "dikkan duniya" wannan magana ne da yake nuna arziki. AT: ya samu dukkan abin da yake bukata"
A rasa abu ko a bar wani ya kwashe ta.
AT: "Babu wani abu da mutum zai iya bayar a maimakon rayuwar sa" ko "Ba wanda zai bayar da komai a maimakon rayuwar sa."
A kabilar ka "bayarwa" na bukatar wani ya karbi abin da aka ba shi "Me mutum zai ba wa Allah"
"kunya ta da sako ta"
Yesu yayi magana game da wannan zamanin kamar "mazinaci ne," na nufin cewa ba suwa yin gaskiya cikin dagartakar su da Allah. AT: "a wannan zamanin mutane da suka yi zina suna kuma yin zunubi wa Allah" ko "a wannan zamani da mutane ba su da gaskiya suna kuma yin zunubi ga Allah"
"a lokacin da ya dawo"
Idon Yesu ya dawo, zai samu ɗaukaka daya da Ubansa.
"tare da mala'iku masu tsarki"
1Sai ya ce masu, "Hakika, ina gaya maku, akwai wasun ku anan da ba za su mutu ba, sai sun ga mulkin Allah ya bayyana da iko." 2Bayan kwana shida Yesu ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kadai. Sai kamaninsa ya sake a gabansu.3Sai tufafinsa ya zama fari fat, yadda ba mai rinin da zai iya rininsa haka a duniya.4Sai Iliya da Musa suka bayyana gare su, suna magana da Yesu. 5Sai Bitrus ya amsa ya ce, malam, bari mu da muke anan mu kafa bukka uku, daya ta ka, daya ta Musa, da ta Iliya, 6Ya rasa abin da zai fada ne, don sun tsorota kwarai.)7Sai ga wani gajimare ya zo ya rufe su, aka kuma ji wata murya daga gajimaren, "ta ce Wannan shine kaunataccen Dana, Ku saurare shi. 8Nan take da suka duba, ba su ga kowa ba, sai Yesu shi kadai.9Suna cikin gangarowa daga dutsen, sai ya kwabe su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan da Dan Mutum ya tashi daga mattatu. 10Sai suka bar zancen a tsakaninsu, amma suka tamabayi junansu "mene ne tashin matattu" ke nufi.11Suka tambaye shi yaya malaman attaura suka ce Iliya zai fara zuwa?" 12Ya ce masu, laile ne Iliya ya fara zuwa ya raya dukan abubuwan. Don me a ka rubuta cewa Dan Mutum, zai sha wuya iri iri a kuma ki shi? 13Amma ina gaya muku Iliya ya riga, ya zo, amma sun yi masa abin da suke so su yi kamar yadda littatafai suka yi magana a kansa."14Sa'adda suka dawo wurin sauran almajiran, suka ga taron jama'a masu yawa suna ta muhawara tare da manyan malaman attaura. 15Da ganin sa, sai dukan taron yayi mamaki kwarai da gaske, suka dungumo wurinsa a guje, suna gaishe shi. 16Ya tambayi almajiransa, "Wacce muhawara ce kuke yi da su?"17Daya daga cikin taron ya amsa masa"malam, ga shi na kawo maka dana don yana da beben aljani. 18Duk lokacin da ya tasar masa yakan buga shi har kasa, na kuma yi wa almajiranka magana su fitar sun kasa. 19Ya amsa masu ya ce ya ku mutanen zamaninnan marasa bangaskiya, har yaushe zan kasance tare da ku ina jimrewa? ku dai kawo mini shi.20Sai suka kawo masa yaron. Da ruhun ya ga Yesu, nan da nan ya buge yaron jikinsa na rawa. Sai yaron ya fadi yana ta birgima, bakinsa yana kumfa. 21Yesu ya tambayi mahaifin yaron, Tun yaushe wannan abu ya same shi? Mahaifin yaron ya ce tun yana karami. 22Ya kuwa sha jefa shi a ruwa da wuta, don ya halakar da shi. Idan zaka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimakemu.23Yesu ya ce masa, "In zan iya? Ai dukan abu mai yiwuwa ne, ga duk wanda ya gaskata. 24Nan da nan mahaifin yaron ya daga murya ya ce, Na ba da gaskiya. A kore mini rashin bangaskiyata. 25Da Yesu ya ga taron na dungumowa a guje, sai ya tsawata wa bakin aljanin ya ce masa, "kai, beben aljani na umarce ka, ka fita daga wannan yaron kar ka sake shigar sa.26Sai wannan aljanin ya daga murya ya fita ya rabu da wannan yaron. Sai yaro ya zama kamar mattacce, sai sauran mutanen suka ce, "Ai, yaron ya mutu. 27Yesu ya kama hannunsa, ya daga shi, sai yaron ya mike tsaye.28Da Yesu ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi a kadaice, me ya sa muka kasa fitar da shi?" 29Ya ce masu, "Ai, irin wannan ba ya fita sai da addu'a."30Sai suka ratsa cikin Galili, amma ba ya son kowa ya san inda suke. 31Da yake koyar da almajiransa, ya ce masu lokaci na zuwa da za'a ba da Dan mutum a hannun mutane, za su kuwa kashe shi, sa'adda aka kashe shi kuma, bayan kwana uku zai tashi. 32Amma fa ba su fahimci maganar ba, suna kuma jin tsoron tambayarsa.33Sai suka zo kafarnahum. A lokacin da ya ke cikin gida, ya tambayi Al'majiransa, Menene ku ke magana a kansa a hanya? 34Amma suka yi shiru. don suna gardama da junansu akan hanya, a kan wane ne mafi girma. 35Sai ya zauna, ya kira al'majiransa goma sha biyu, yace masu duk wanda ya ke so ya zama na fari, dole ya kankantar da kansa, sa'annan ya bautawa sauran duka.36Sai ya dauko karamin yaro a hannunsa ya sa shi a tsakiyarsu. Ya rumgome shi a kafadarsa ya ce masu. 37Dukan wanda ya karbi dan karamin yaron nan a cikin sunana ni ya karba, kuma dukan wanda ya karbi wani, ni ya karba, bai kuma karbeni ni kadai ba, duk da wanda ya aiko ni."38Sai Yahaya ya ce masa, Malam mun ga wani yana fitar da aljanu da sunanka mun yi kokari mu hana shi domin ba ya tare da mu. 39Sai Yesu ya ce masu ku kyale shi domin babu wanda zai yi irin wannan babban aikin, sa'annan ya fadi wasu maganganu mara sa kyau a kanmu.40Duk wanda ba ya gaba da mu, na mu ne. 41Duk wanda ya ba ku ruwa ku sha domin kuna na Almasihu, gaskiya nake fada maku ba za ya rasa ladansa ba.42Amma duk wanda ya sa kananan nan tuntube, ya fi kyau a rataya masa dutsen nika a jefa shi a cikin teku. 43Idan har hannun ka zai sa ka yi tuntube, zai fi kyau ka yanke shi. Domin zai fi kyau ka shiga aljanna da hannu daya da ka shiga jahannama da hannu biyu. 44(Inda tsutsotsi basu mutuwa, wutar kuma bata mutuwa).45Idan kafarka za ta sa ka yi tuntube, ka yanke ta ka yar. Zai fi kyau ka shiga aljanna da kafa daya da ka shiga jahannama da kafa biyu. 46(Inda tsutsotsi basu mutuwa, wutar kuma bata mutuwa).47Idan idonka zai sa ka yi tuntube, ka kwakule shi ka yar, domin gwamma ka shiga mulkin Allah da ido daya, da a jefa ka cikin wuta da idanu biyu. 48Inda tsutsotsi basu mutuwa, wutar kuma bata mutuwa.49Domin da wuta za a tsarkake kowa. 50Gishiri yana da kyau, amma idan ya rasa zakinsa, ta ya ya za ka sa shi yayi zaki kuma? Ku kasance da zaki, kuma ku yi zaman lafiya da kowa.
Yesu yana magana da mutane kuma almajaren sa suna ta kokarin bin sa. Bayan kwana ta shida, Yesu ya tafi tudu tare da almajarensa guda uku, inda watarana kamanin sa zai canza ba da daɗewa ba zuwa yanda zai zama a mulkin Allah.
"Yesu ya ce wa almajarensa"
Mulkin Allah da ke zuwa na nuna Allah da kansa a matsayin sarki. AT: "Yesu ya bayyana kansa a matsayin sarki da matukar iko"
Marubucin ya yi amfani da kalmar aiki ne anan "da kansu" domin ya nanata cewa da Yesu, da Bitrus, daYakubu, da Yahaya da kansu ne suka hau tudun.
Da suka kalle shi, kamanin sa ya canza dabam kamar yadda yake da farko.
AT: "Kamanin sa ya canza" ko "kamanin sa ya zama dabam"
"a gaban su" ko "domin su gan shi a fili"
"da haske." Tufafin Yesu yayi haske sosai har yana fitar da haske.
sosai ko fiye da take
AT: "yadda ba mai rinin da zai iya rininsa haka a duniya"
Za iya zama da taimako a fadi ko wanene mutanen nan suke. AT: "annabi guda biyu da suka yi rayuwa a tun zamanin da suka wuce, Iliya da Musa suka bayyana"
"Bitru ya ce wa Yesu." Kalman nan "amsa" an yi amfani da shi domin a gabatar da Bitrus cikin labarin. Bitrus bai amsa tambaya ba.
Kalman nan "mu" ba tabatar ba ko yana nufin Bitrus, ko Yakubu, da Yahaya ba ne, ko yana nufin duk wanda suke wurin wanda ya shafi Yesu, Iliya da Musa...
dan bukka da aka gyara domin a zauna ko a yi barci
Maganan nan ya ba da shahararen bayani game da Bitrus, Yakubu da kuma Yahaya.
"sun tsorata kwarai" ko "sun ji tsoro sosai"
"ya bayana ya rufe"
A nan "murya ta fito daga" kalma ce da take nuna wani na magana. Za a iya kuma bayana a filli wa ya yi maganan. AT: "Sai wani ya yi magana daga gajimaren" ko "Sai Allah ya yi magana daga gajimaren"
Allah Uba y nuna kaunar sa wa "kaunataccen Ɗan sa" Ɗan Allah.
Wannan lakaɓi ce mai muhinminci na Yesu. Ɗan Allah.
A nan "suka" na nufin Bitrus, Yakubu da kuma Yahaya ne.
Wannan na nufin cewa ya na basu izini su faɗa wa mutane abin da suka gani bayan da ya tashi daga mattatu.
"tashi daga cikin mattatu ... a tashi daga cikin mattatu." Wannan na magana game da zama rayayye kuma. Maganan nan "mattatu" na nufin "mattatun mutane" kuma magana ce na mutuwa. AT: "tashi daga mattatu ... tashiwa daga mattartu"
A nan "suka bar zancen a tsakaninsu" karin magana ne da yake nufin basu faɗa wa kowa ba abin da suka gani. AT: "Sai basu faɗa wa kowa ba abin da suka gani"
"Kalman nan "su" na nufin Bitrus, Yakubu da kuma Yahaha.
Anabci ya faɗi cewa Iliya zai sake zuwa daga sama. Sai Mai ceto, wanda shine Ɗan Mutum, zai zo domin yayi mulki. Almajaren suka rikice cewa ta yaya Ɗan Mutum zai mutu ya kuma tashi. AT: "don me malaman attaura suka ce Iliya zai fara zuwa kafin Mai ceton ya zo? "Dubi:
Bayan da faɗa haka, Yesu ya tabbatar da cewa Iliya zai fara zuwa.
Yesu yayi amfani da tambayan nan domin ya tunashe almajarensa cewa littafin ya koyas da cewa Ɗan Mutum zai sha wahala kafin a kashe shi. AT: "amma ina son ku duba abin da aka rubuta game da Ɗan Mutum.mlittafin ya faɗa cewa zai sha wahala sosai a kuma ki shi."
AT: "mutane zasu ki shi"
Zai zama da taimako a faɗi abiin da mutane suka yi wa Iliya. AT "dattawan mu sun yi mashi mugunta, kamar yadda suke so su yi"
Yesu, Bitrus, Yakubu da Yahaya sun dawo wurin sauran almajaren wanda basu tafi tare da su zuwa tuɗun ba.
"Yesu da almajaren nan guda uku sun ga babban taro kewaye da sauran almajaren"
Mallaman attaura suna musu da sauran almajaren da basu tafi tare da Yesu ba.
Zai zama da amfani a faɗi dalilin da suka yi mamaki. AT: "suka yi mamaki cewa Yesu ya zo"
Wannan na nufin aljani ya shige yaron. "Yana da aljani" ko "aljani ya shige shi"
ɗaukar ruwa daga baki, ko figar ruwa yan kan iya saka damuwa wa mutum ta wurin numfashi ko haɗiye abu. Wannan na saka farin kumfa ya fita daga baki. Idan harshen ka tana da wata hanyar bayyana wannan, ka yi amfani da ita. "kunfa ya fito daga bakin sa"
"ya kan zama da ƙauri" ko "jikin sa ya zama da ƙauri"
Wannan na nufin almajaren basu iya fitad aljanin daga yaron ba. AT: "basu iya fitad da shi daga jikin sa ba"
Kodashike, uban yaron ne ya tambaye Yesu, Yesu ya amsa wa dukkan jama'an"
" ku zamaninnan marasa bangaskiya." Yesu ya kira taron haka, da ya fara amsa masu.
Yesu yayi amfani da tambayoyin nan domin ya nuna damuwar sa. Tambayoyin nan suna da amsa iri daya. AT: "Na zama da damuwa kwarai domin rashin bangaskiyar ka!" ko "Rashin bangaskiyar ku ya ishe ni! Na rasa har yaushe ne zan hakkura da ku."
"jimre da ku" ko "hakkuri da ku"
"Kawo mani yaron"
Wannan na nufin aljani AT: [Markus 9:17]
Wannan yanayi ne da yake saka mutum ya rasa iko ga jikin sa, kuma jikin sa na kaɗewa da ƙarfi.
"Tun yana karamin yaro." AT: "Haka yake tun yana karamin yaro"
"ji tausayi"
Yesu ya sake maimaita abin da mutumin ya faɗa masa. AT: "Ka ce mani "Idan zan iya'?" ko "Don me ka ce 'Idan zan iya'?"
"Allah kan iya yin komai ga duk mutumin da ya ba da gaskiya gare shi"
"ga mutumin" ko "ma kowa"
Wannan na nufi ba da gaskiya ga Allah. AT: "ba da gaskiya ga Allah"
Mutumin na rokon Yesu ya taiake shi ƙoran rashi bangaskiyar shi ya kuma inganta bangaskiyar sa. AT: "Ka taimake ni idan ban gaskanta ba" ko "Ka taimake ni in samu bangaskiya"
Wannan na nufin mutanen suna zuwa inda Yesu yake a guje kuma taron na karuwa sosai.
Kalman nan "bebbe" da kuma "kurma" za a iya bayyana ta. AT: "Kai aljani, kai da kake hana yaron yin magana da kuma ji"
"aljanin ya daga murya"
"ya girgiza yaron da ƙarfi"
Wannan na nufin cewa aljani ya fita daga yaron. AT: "fita daga yaron"
An kwatanta fuskar yaron da mattatcen mutum. AT: "Yaron ya yi kaman ya mutu" ko "Yaron ya yi kama da mattacen mutum"
AT: [9:26]
Wannan na nufin Yesu ya kama hannun yaron da hannuwansa. AT: "ya kama yaron a hannu"
"ya taimake shi ya mike sama"
Wannan na nufin su kadai ne.
"fitar da aljanin." Wannan na nufin fitar da aljanin daga jikin yaron. AT: "fitar da aljanin daga jikin yaron"
Kalman nan "ba ya" da kuma "sai da" kalmomi mara amfani ne. zai fi kyau ayi amfani da kalmomi masu amfani a wasu harshen. AT: "sai ta wurin addu'a ne kawai za a iya fitad da su"
Wannan ya fasara aljanin. AT: "Irin wannan aljanin"
"Yesu da almajaren sa sun bar wancan yankin"
"suka bi ta" ko "suka wuce ta"
Yesu yana koyar da almajarensa a asirce, a nesa da jama'a. AT: "da yake koyar da almajaren sa a asirce"
AT: "Wani zai ba da Ɗan Mutum"
A nan Yesu yana kansa ne a matsayin Ɗan Mutum. Wannan laƙani ne mai muhinminci na Yesu. "Ni. Ɗan Mutum,"
A nan "hannu" kalma ce na iko na mutane. AT: "zuwa ga ikon mutane" ko "saboda mutane su iya samun iko a akan sa"
AT: "Bayan da aka kashe shi, kwana ta uku kuma ta wuce, ya"
Suna jin tsoro su tambaye Yesu mai nufin Maganar sa. AT: "suna jin tsoro sun tambaye shi mai yake nufi"
"suka iso." Kalman nan "su" na nufin Yesu da almajaren sa ne.
"kuna magana da junan ku ne"
Sun yi shiru domin suna kunyan faɗa wa Yesu abin da suke magana akai. AT: "sun yi shiru domin sun ji kunya"
A nan "mafi girma" na nufin "mai girma" a sakanin almajaren ne. AT: "wanene mafi girma a sakanin su"
A nan, kalmomin nan "farko" do "karshe" ƙishiyar junan su ne. Yesu yayi magana game da zama "mafi girman" kaman na "farkon ne" sai kuma "mara muhinminci" kaman na "karshen ne." AT: " idan akwai wanda yake son Allah ya duba shi a matsayin babba a sakanin su, sai ya mayar da kansa mara muhinminci a duka"
"a dukka mutane ... a dukkan mutane"
" a cikin su." Kalman nan "su" na nufin jama'a ne.
Wannan na nufin ya ɗauko yaron ya kuma ajiye shi a cinyar sa.
"irin yaron nan"
Wannan na nufin a yi abu domin kaunar Yesu. AT: "domin yana ƙauna ta" ko "domina"
Wannan nufin Allah ne, wanda ya turo shi zuwa duniya. AT: "Allah, da ya turo ni"
"Yahaya ya ce wa Yesu"
"korar aljani." Wannan na nufin cire aljani daga jikin mutane. AT: "fitar da aljani daga jikin mutane"
A nan "suna" ya shafe ikon Yesu da karfin sa. AT: "tawurin ikon sunan ka" ko "tawurin karfin sunan ka"
Wannan na nufin ba ya tare da almajaren. AT: "ba ya cikin mu" ko "ba ya tafiya tare da mu"
"ba ya gaba da mu"
AT: "yana kokarin yin nasara da mu ke"
Yesu yana magana akan ba wa wani ruwa, misali ne da yadda mutum ɗaya zai taimaki ɗan'uwan sa. Wannan magana ne na taimakon juna ta kowace hanya.
A wasu harshe, zai zama da tamako a yi amfani da kalmomi masu amfani. AT: "hakika, zai ƙarbi"
babbar, mulmulin dutse da ake yin amfani a niƙa kwayar hatsi zuwa gari
A nan "hannu"magana ne da yake nuna yin sha'awa ne da zai saka ka yin zunubi da hannun ka" AT: "Idan kana son ka yi zunubi da wani hannun ka"
"ka zama dungu sai ka shiga rai" ko "ka zama dungu kafin ka shiga rai"
A nan magana game da mutuwa sa'annan a fara rayuwan har'abada kammar shigar rai ne. AT: "ka shiga rai na har'abada" ko "ka mutu sa'annan ka fara rayuwa na har'anada"
Rasa wani gaba na jiki domin an cire ta ko ta wurin jin ciwo. Anan na nufin rasa hannu ne. AT: "ba hannu" ko "hannun da babu"
"inda ba za a iya kashe wutan ba"
A nan kalman nan "kafa" magana ne da yake nuna yin sha'awa ne da zai saka ka yin zunubi da ƙafafun ka, kamar inda bai kamata ka je ba. AT: "Idan kana son ka yi zunubi da wani ƙafafun ka"
"ka zama gurgu sa'a nan ka shiga rayuwa" ko "ka zama gurgu kafin ka shiga rai"
"rashin iya tafiya da kyau." A nan na nufin rashin iya tafiya domin babu wani ƙafa. AT: "babu ƙafa" ko "babu wani ƙafa"
AT: "da Allah ya wurga ka cikin wuta"
A nan kalmar "ido" 1) kalma ce da yake saka mutum sha'awar zunubi na kallo. AT: "Idan kana so ka yi wani abun zunubi ta wurin kallo, ka ƙwaƙule idanun ka" ko 2) sha'awar yin zunubi domin abin da ka kalla. AT" Idan kana so ka yi zunubi domin abin da ka kalla, ka ƙwaƙule idanun ka"
Wannan na nufin kamanin jikin mutum idan ya mutu. Mutum ba ya ɗaukan jikin sa tare da shi zuwa aljanna. AT: "ka shiga zuwa mulkin Allah bayan da ka yi rayuwa a duniya da ido ɗaya da ka yi rayuwa a duniya da idanu biyu"
AT: "da Allah ya wurga ka cikin wuta"
AT: "inda tsutsotsi masu cin mutane basu mutuwa"
AT: "Allah zai tsarkake kowa da wuta" ko "Kamar yadda wuta na tsarkake haɗaya, Allah zai tarkake kowa tawurin barin su su sha wuya"
A nan "wuta" magana ce na shan wuya, kuma saka wa mutane gishiri kalma ce na tsarkakewa. Hakannan "za a tsarkake su da wuta" magana ce na tsarkakewa ta wurin shan wuya. AT: "za a mayad da shi da tsabta cikin wutar mai wahala" ko "za a sha wuya domin a tsarkake a matsayin hadaya shine tsarkakewa da gishiri"
"zakinsa"
AT: "ba za ka iya samu ɗanɗanon ta kuma ba"
"ɗanɗanon kuma ba"
Yesu yana magana akan yi wa juna abubuwa masu kyau kamar abubuwa masu kyau gishiri ne da mutane ke gada. AT: Ku yi wa kowa kirki, kamar gishiri da yake kara ɗanɗano wa abinci"
1Yesu ya bar wannan wurin, ya tafi yankin Yahudiya, wajen hayin kogin Urdun. Sai jama'a suka je wurinsa. Ya ci gaba da koya masu, kamar yadda ya zama al'adarsa. 2Sai Farisawa su ka zo wurinsa, su ka ce, "dai dai ne mutum ya saki matarsa?" Wannan tambaya sun yi ta ne domin su gwada shi. 3Ya amsa ya ce, menene Musa ya umarce ku? 4Suka ce, "Musa ya yarda mutum ya rubuta takardar saki ga matarsa, ya sallameta ta fita."5"Domin taurin zuciyarku ne ya rubuta maku wannan dokar," Yesu ya ce masu. 6Amman tun daga farkon halitta, 'Allah ya halicci namiji da ta mata.'7Domin wannan dalilin ne mutum zai rabu mahaifinsa da mahaifiyarsa ya mannewa matarsa. 8Su biyu kuwa sun zama jiki daya, ba biyu ba, 9Saboda haka abinda Allah ya hada kada mutum ya raba."10Lokacin da suke cikin gida, sai almajiransa suka sake tambayarsa akan wannan magana. 11Ya ce da su. Dukan wanda ya saki matarsa ya kuma auro wata matar yayi zina da ita kenan. 12Haka nan duk matar da ta saki mijinta ta auri wani ta yi zina da shi kenan."13Mutane suka kawo masa 'ya'yansu kanana don ya taba su, sai almajiransa suka kwabe su. 14Da Yesu ya gani, ya ji haushi, ya ce masu. Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su domin mulkin Allah na irinsu ne.15Gaskiya na ke fada maku duk mutumin da bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, babu shakka ba zai shiga mulkin Allah ba. 16Sai ya rungume su ya sa masu albarka.17Lokacin da ya fara tafiya, sai wani mutum ya rugo wurinsa, ya durkusa a gabansa. Ya tambaye shi, yace ya "Malam managarci, me zan yi domin in sami rai na har abada?" 18Amma Yesu ya ce masa. Don me ka ke kira na managarci? Babu wani managarci sai dai Allah kadai. 19Kasan dokokin. Kada ka yi kisan kai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar zur, kada ka yi zamba, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka."20Sai mutumin ya ce masa Malam ai na kiyayye duk wadannan abubuwa tun ina yaro. 21Yesu ya dube shi duban kauna ya ce masa. Abu daya ka rasa. Shi ne ka je ka sayar da duk mallakarka ka ba mabukata, za ka sami wadata a sama. Sa'annan ka zo ka bi ni. 22Da ya ji haka sai ransa ya baci, ya tafi yana bakin ciki, don shi mai arziki ne kwarai.23Yesu ya dubi almajiransa ya ce. "Yana da wuya masu arziki su shiga mulkin Allah!" 24Almajiransa suka yi mamakin maganarsa. Sai Yesu ce masu, ya ku ya'ya'na yana da wuya kamar me a shiga mulkin Allah. 25Zai zama da sauki ga rakumi yabi ta kafar allura da mai arziki ya shiga mulkin Allah.26Sai suka cika da mamaki sosai, su kace wa juna, "to idan haka ne wanene zai iya tsira kenan?" 27Yesu ya dube su ya ce masu. Ga mutane a bu ne mai wuyar gaske, amma a wurin Allah komai yiwuwa ne. 28Bitrus ya ce masa, "to gashi mu mun bar kome, mun bika".29Yesu ya ce. Gaskiya na ke fada maku, babu wanda zai bar gidansa, da yan'uwansa maza da mata, da mahaifiya ko mahaifi, ko 'ya'ya ko gona, saboda da ni da kuma bishara, 30sa'annan ya rasa samun nikinsu dari a zamanin yanzu, na gidaje, da yan'uwa mata da maza' da iyaye mata da 'ya'ya da gonaki, game da tsanani, a duniya mai zuw kuma ya sami rai madawwami. 31Da yawa wadanda suke na farko za su koma na karshe, na karshe kuma za su zama na farko.32Suna tafiya Urushalima, Yesu kuwa na gabansu. Almajiransa sun yi mamaki, mutane da ke biye da su kuwa sun tsorata. Yesu kuwa ya sake kebe sha biyun nan, ya fara fada masu abin da zai same shi. 33"Kun ga, za mu Urushalima za a bada Dan mutum ga manyan Firistoci da malan Attaura, za su kuma yi masa hukuncin kisa su kuma bada shi ga al'ummai. 34Za su yi masa ba a, su tofa masa yau, su yi masa bulala, su kashe shi, bayan kwana uku kuwa zai tashi."35Yakubu da Yahaya, 'ya'yan Zabadi, suka zo wurin sa, suka ce, "Malam muna so kayi mana duk abin da mu ka roke ka" 36Ya ce masu. "Me ku ke so in yi maku?" 37Suka ce, "ka yardar mana, a ranar daukakarka, mu zauna daya a damanka, daya kuma a hagunka."38Yesu ya ce masu. "Ba ku san abinda ku ke roka ba. Kwa iya sha daga kokon da zan sha? Ko kuma za a yi maku baftismar da za a yi mani?" 39Suka fada masa, "Zamu iya." Yesu ya ce masu, "kokon da zan sha, da shi zaku sha, baftismar da za ayi mani kuma da ita za a yi maku." 40Amma zama a damata, ko a haguna, ba na wa ba ne da zan bayar, ai na wadanda a ka shiryawa ne."41Da sauran almajiran nan goma suka ji, suka fara jin haushin Yakubu da Yahaya. 42Yesu kuma ya kira su wurinsa ya ce masu, "kun sani wadanda aka san su da mulkin al'ummai sukan nuna masu iko, hakimansu kuma sukan gasa masu iko.43Amma ba haka zai kasance a tsakaninku ba. Duk wanda ya ke son zama babba a cikinku, lalle ne ya zama baranku. 44Duk wanda ya ke so ya shugabance ku lalle ne ya zama bawan kowa. 45Saboda haka ne Dan mutum ya zo ba domin a bauta masa ba, sai dai domin shi yayi bautar, ya kuma ba da ransa fansa saboda da mutane da yawa."46Sa'adda suka iso Yariko, yana fita daga Yariko kenan, shi da almajiransa, da wani babban taro, sai ga wani makaho mai bara, mai suna Bartimawas dan Timawas yana zaune a gefen hanya. 47Da ya ji Yesu Banazare ne, ya fara daga murya yana cewa, "Ya Yesu, Dan Dauda, kaji tausayina" 48Mutane da yawa suka kwabe shi, cewa yayi shiru. Sai ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, Ya Dan Dauda ka yi mani jinkai, ka ji tausayina!"49Yesu ya tsaya ya ce, ku kirawo shi. Su kuwa suka kirawo makahon suka ce masa. "Albishrinka, ta so! Yana kiranka." 50Makahon ya yar da mayafinsa, ya zaburo wurin Yesu.51Yesu ya tambaye shi, ya ce, "me ka ke so in yi maka?" Makahon ya ce, "Malam in sami gani." 52Yesu ya ce masa. "Yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai." Nan take idanunsa suka bude, ya bi Yesu, suka tafi tare.
Bayan da Yesu da almajiransa sunka bar Kafarnahum, Yesu ya tunashe Farisiyawan da kuma almajiransa, abin da Allah ke bukata a cikin aire da kuma kashe aure.
Almajiran Yesu suna cikin tafi tare da shi. Suna koƙarin barin Kafarnahum. AT: "Yesu da almajiransa sun bar Kafarnahum"
"zuwa kasar da ke wajen hayin Kogin Urdun" ko "zuwa gabacin Kogin Urdun"
Kalman nan "su" na nufin taron.
"zama al'adarsa" ko "ya saba yi"
Musa ya ba wa kakaninsu doka wanda yakamata su bi. AT: "Me Musa ya umuce kakaninku game da wannan"
Wannan wata takardar da ta bayana cewa macen ba matan shi bane kuma.
A wasu harsuna, mai magana ba ya katse maganar da aka ruwaito don a faɗa ko wa yake magana. Maimakon haka su kan faɗi wanda ke magana da farko ko a karshe maganar da aka ruwaita. AT: "Yesu ya ce masu, 'domin ... wannan dokar. Amma"
Tun da, Musa ya rubuta wannan dokar ga Yahudawa da zuriyarsu saboda sun taurare zukatansu. Yahudawan a lokacin Yesu su ma sun taurare zukatansu, saboda haka Yesu haɗa da su ta wurin yin amfani da kalman"ku." AT: "domin kakaninku da ku duk kuna da taurin zuciya shi ya sa ya rubuta wannan dokar"
A nan "zukatan" na nufin cikin mutum ko runaninsa. Maganan nan "taurare zukatan" na nufin "taurin kai." AT: "taurin kanku"
Yesu ya ruwaito wannan daga abin da Allah ya faɗa cikin littafin Farawa.
"Allah ya halicci mutane"
Yesu ya cigaba da ruwaito da abin da Allah ya faɗa a cikin littafin Farawa.
"Saboda haka" ko "saboda wannan"
"haɗuwa da mata tasa"
Wannan na misalta ɗayantakan su a matsayin miji da mata. AT: "mutane biyun suna kamar mutum ɗaya" ko "yanzu kam su ba biyu bane amma tare sun zama jiki ɗaya"
Maganan nan "abin da Allah ya haɗa" na nufin masu aure. AT: "Saboda haka, dashike Allah ya haɗa miji da mace, to, kada wani ya raba"
"Sa'adda Yesu da almajiransa suke"
Almajiran Yesu suna magana da shi a ɓoye. AT: "suke su kaɗai a cikin gidan"
Kalman nan "wannan" na nufin magnan da Yesu ya yi da Farisiyawan game da kashe aure.
"kowa"
A nan "ita" na nufin macen da ya aure ta da farko.
A wannan yanayi ta yi zina ga mijinta na dă. AT: "ta yi zina ga shi" ko "ta yi zina ga mutum na farkon"
"Mutane suna kawo." Wannan abin da ya faru nan gaba a labarin ne.
Wannan na nufin cewa Yesu zai taɓa su da hannunsa ya sa masu albarka. AT: "don ya taɓa su da hannunsa ya kuma sa masu albarka. ko "ya sa hannunsa a kansu ya albarkace su"
"sauta wa mutane"
Kalman nan "su" na nufin almajiran suna kwaɓen mutane wanda suke kawo 'ya'yan wurin Yesu.
"ya yi fushi"
Waɗannan maganganu biyu suna da ma'ana kusan iri ɗaya, an maimaita ta don nanaci. A wasu harsuna ba abune mai yiwuwa ba a nanata wannan a wanta hanya. AT: "Ku tabbata kun bar 'ya'ya kanana su zo wurina"
A wasu harsuna ba abune mai yiwuwa ba a yi amfani da magana da ke bada tabbaci. AT: "bar"
Mulkin ba mutane ne, na nufin mulkin har da su ma. AT: "mulkin Allah na haɗe da mutane kamar su" ko "domin mutane kamarsu sune kaɗai ke na mulkin Allah"
"duk wanda bai karɓi ... yaro, babu shakka ba zai shiga ba
Yesu ya kwatanta yadda ta zama tilas mutane su karɓi mulkin Allah da yadda kananan yara sun karɓi ta. AT: "daidai kamar yadda yaro zai yi"
"ba zai yi na'am da Allah a matsayin sarki ba"
Kalman nan "ta" na nufin mulkin Allah.
"ya rungume yara"
A nan mutumin ya yi maganar "karɓi" sai kace "gădo." Wannan na nanata muhimmancin karɓar. Haka kuma, "găji" anan ba ta nufin cewa dole wani ya mutu tukuna. AT: "karɓi rai madawwami"
Yesu ya yi wannan tambayar don ya tunashe mutumin cewa ba wani mutum da ke nagari kamar yadda Allah yake. AT: "Ba ka fahimci abin da kake faɗi ba a sa'adda ka kirani managarci."
"managarci. Allah kaɗai shine managarci"
"kada ka yi wa wani shaidar zur" ko "kada ka yi ƙarya game da wani a kotu"
"Akwai abu ɗaya da ka rasa." A nan "rasa" na nufin bukatan yin wani abu. AT: "Abu ɗaya kana bukata ka yi" ko "Akwai abu ɗaya da ba ka yi ba"
A nan kalman nan "ita" na nufin abubuwan da ya sayar. Wannan na nufin kuɗin da ya karɓa a sa'ad da ya sayar da su. AT: "ba da kuɗin ga matalauta"
Wannan na nufn mutane matalauta. AT: "mutane matalauta"
arziki, abubuwa masu daraja
"na da abubuwa masu yawa"
"Yana da matuƙar wahala"
"Yesu ya ce wa almajiransa kuma"
"'ya'yana, yana da." Yesu yana koya masu daidai kamar yadda uba zai koyawa 'ya'yansa. AT: "Abokaina, yana da"
"yana da matuƙar wuya"
Yesu ya yi amfani da wannan don ya nanata yadda yake da matuƙar wahala mutane masu arziki su shiga mulkin Allah.
Wannan na maganar yanayi da ba zai taba yiwuwa ba. In ba za ku iya bayana wanna a harshenku ba, to, to ana iya rubuta shi a matsayin misali. AT: "zai zama da sauki rãƙumi"
"ramin allura." wannan na nufin wata karamar rami a ƙarshen alluran dinki wanda zare ka wuce ta ciki.
"Almajiran sun yi"
AT: "In haka ne, to ba wanda zai tsira!"
Ana iya bayana abin da aka fahimta. AT: "Ba shi yiwuwa mutane su cece kansu, amma Allah zai iya ceton su"
A nan kalman nan "duba" an yi amfani da ita don a jawo hankali ga kalmomin da ke zuwa nan gaba. Abu makamancin haka ana iya bayana shi a wata hanya. AT: "Mun bar kowane abu, mun bi ka"
bar kowane abu a baya"
AT: "duk wanda ya bar ... zai sami"
"ko fili" ko "ko gonar da ke nasa"
"sabili da ni" ko "don ni"
"don shelar bishara"
"wannan rayuwa" ko "wannan zamani"
Daidai kamar jeri abubuwan da ke cikin aya 29, wannan na bayana iyali gabakiɗaya. Kalman nan "uba" ba a ambata shi a aya 30 ba , amma wannan bai canza ma'anar ba.
Ana iya sake rubuta wannan domin zance da ke wannan suna "tsanani" a bayana shi cikin aikatau "tsanantawa." Saboda jimlar ta yi tsayi kuma da wuyar fahimta, maganan nan"zai sami" ana iya maimaita shi. AT: "kuma ko mutane sun tsananta masu, a duniyan nan mai zuwa, za su sami rai madawwami"
"a duniyan da ke nan gaba" ko "a nan gaba"
A nan kalmomin nan "farko" da "ƙarshe" sun sha bam-bam da juna. Yesu yana magana game da zama "muhimmanci" a matsayin "farko" da kuma zama "marasa muhimmanci" a matsayin "ƙarshe." AT: "da ke da muhimmanci za su zama marasa muhimmanci, waɗanda basu da muhimmanci za su zama masu muhimmanci"
Maganan nan "na ƙarshe" na nufin mutanen da ke na "ƙarshe." Kuma, ana iya sa kalman aikatau da an fahimce ta a wannan magana. AT: "waɗanda ke ƙarshe za su zama farko"
"Yesu da almajiransa suna tafiya kan yanyan ... Yesu kuma na can gaban almajiransa"
"waɗanda ke biye da su." Wasu mutane suna tafiya biye da Yesu da almajiransa.
"Duba" ko "kassa kunne" ko "sa hankalin ku ga abin da zan gaya maku"
Yesu na magana game da kansa. Ana iya bayana wannan a fili. AT: "Ni, Ɗan Mutum, za a"
AT: "wani zai bashe Ɗan Mutum ga" ko "za su mika Ɗan Mutum ga"
kalman nan "su" na nufin firistoci da malaman attaura.
"sa shi karƙashin mulkin Al'ummai"
"Mutane za su yi masa ba'a"
"kashe shi"
Wannan na nufin tashiwa daga mattattu. AT: "zai tashi daga mattattu"
Waɗannan kalmomi na nufin Yakub da Yahaya ne kawai.
"sa'adda an ɗaukaka ka." Maganan nan "cikin ɗaukakarka" na nufin sa'adda an ɗaukaka Yesu a kuma yi mulki bisa mulkinsa. AT: "sa'adda kana mulki a bisa mulkin ka"
"Ba ku fahimci"
A nan "koko" na nufin wahalar da Yesu za sha. An yi maganar shan wahala sau da dama kamar sha daga ƙoƙo. AT: "sha ƙoƙon wahala da zan sha" ko "sha daga cikin ƙoƙon wahala da zan sha daga ciki"
A nan "baftisma" da kuma yin baftisma na wakilcin wahala. Kamar yadda ruwa ke rufe mutum a lokacin baftisma, wahala za ta shafe Yesu. AT: "jimre baftismar wahalar da zan sha"
Amsawarsu ta wannan hanya na nufin cewa sun za su iya sha da cikin ƙoƙon ɗaya su kuma jimre baftisma ɗayan.
"ku ma za ku sha"
"Amma ba ni bane zan bar mutane su zauna a hannu dama na ko kuwa hagu na"
"Amma waɗannan wurare ga waɗanda aka shirya wa ne." Kalman nan "ta" na nufin wurare a hannun damansa da hagunsa.
AT: "Allah ya shiya ta" ko "Allah ya shirya su"
Kalman nan "wannan" na nufin Yakub da Yahaya suna roƙo su zaun a hannun dama da hagun Yesu.
"Yesu ya kira almajiransa"
Ma'ana mai yiwuwa na kamar haka 1) mutane a takaice na duban waɗanda mutane a matsayin masu mulkin al'ummai. AT: "waɗanda mutane ke duba a matsayin masu mulkin Al'ummai" ko 2) Al'ummai na duban waɗannan mutane a matsayin masu mulkinsu. AT: "waɗanda Al'ummai na tunanin cewa sune masu mulkinsu"
mulki ko iko bisa
"nuna masu iko." Wannan na nufin cewa suna nuna ko amfani da ikonsu a yadda bai kamata ba.
Wannan na kai ga aya da ke a baya game da masu mulkin Al'ummai. Anan iya bayana wannan a fili. AT: "Amma kada ku zama kamar su"
"a girmama shi"
Wannan na nufin zama mafi muhimmanci. AT: "zama mafi muhimmanci"
AT: "Gama Ɗan Mutum bai zo don ya sa mutane su bauta masa ba"
"mutane su bauta masa ba, amma ya bauta wa mutane"
"gama mutane dayawa"
"makaho mai bara mai suna Bartimawas ɗan Timawas." Bartimawas shien sunan mutumin. Timawas kuma sunan mahaifinsa ne.
Bartimawas ya ji mutane suna cewa Yesu ne. AT: "Sa'adda ya ji mutane suna cewa ai Yesu ne"
An kira Yesu Ɗan Dauda saboda shi daga zuriyar Sarki Dauda ne. AT: "Kai da kake Mai Ceto daga zuriyar Sarki Dauda"
"Mutane da ya sun sauta"
"sosai"
AT: "umurci sauran su kira shi" ko "umurce su, 'ku kira shi ya zo nan.'"
Kalman nan "su" na nufin taron.
"Ka karfafa" ko "Kada ka firgita"
"Yesu yana kiranka"
"ya zabura"
"makahon ya amsa"
"in iya gani"
An rubuta wannan magana haka don a nanata bangaskiyar mutumin. Yesu ya warkar da mutumin don ya gaskanta cewa Yesu zai iya warkar da shi. Anan iya bayana wannan a fili. AT: "Ina warkar da kai don ka bada gaskiya a gare ni"
"ya bi Yesu"
1Da suka kusa Urushalima, kusa da Betafaji, da Betanya, wajen dutsen zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa biyu 2ya ce masu, "ku shiga kauyen can kusa da mu. Da zarar kun shiga za ku ga aholaki a daure, wanda ba a taba hawa ba. Ku kwance shi, ku kawo mani. 3In wani ya ce maku, "Don me kuke haka? ku ce, 'Ubangiji ne yake bukatarsa, zai kuma komo da shi nan da nan."'4Sai suka tafi, suka tadda aholakin a daure a kofar gida a bakin hanya, suka kwance shi. 5sai wadanda suke tsaye a gun suka ce masu, "Don me kuke kwance aholakin nan? 6Suka fada masu abinda Yesu yace, sai suka kyale su suka tafi.7Almajiran nan biyu suka kawo wa Yesu aholakin, suka shimfida mayafansu a kai, sai ya hau. 8Sai mutane da yawa suka shimfida mayafansu a hanya, wadansu kuma suka baza ganyen da suka yanko daga filayen. 9Wadanda suke gaba da shi da wadanda ke bin bayansa suka yi sowa suna cewa, "Hosanna! Albarka ta tabbata ga mai zuwa cikin sunan Ubangiji. 10Albarka ta tabbata ga mulkin nan mai zuwa na Ubanmu Dawuda! Dukaka a cikin sama!"11San nan Yesu ya shiga Urushalima, ya shiga Haikalin. Sai ya dudduba komai, da magariba ta yi, ya fita ya tafi Betanya tare da goma sha biyu nan. 12Kashe gari, suka tashi daga Betanya, sai ya ji yunwa.13Da ya hango itacen baure mai ganye daga nesa sai ya je ya ga ko za sami 'ya'ya. Da ya iso wurinsa bai ga komai ba sai ganye, don ba lokacin 'ya'yan baure ba ne.14Sai ya ce wa bauren, "Kada kowa ya kara cin "ya'yanka har abada!" Almajiransa kuwa sun ji maganar.15Suka iso Urushalima, da shigar su, ya kori masu saye da sayarwa, ya watsar da taburan 'yan canjin kudi, da kujerun masu sayar da tantabaru. 16Ya hana kowa ya dauki wani abu da za a i ya sayarwa a cikin haikalin.17Sai ya koyar da su cewa, "Ashe ba rubuce yake ba, "Za a kira gidana gidan addu'a na dukan al'ummai? Amma ku kun mayar da shi kogon yan fashi". 18Da mayan Faristoci da marubutan attaura suka ji maganar da ya yi, sai suka nami hanyar da za su kashe shi. Amma suka ji tsoronsa domin dukkan taron na mamakin koyarwarsa. 19Kowace yamma kuma, sukan fita gari.20Da safe suna wucewa, sai suka ga bauren nan ya bushe. 21Bitrus kuwa ya tuna ya ce "Malam, dubi! Baurenan da ka la'anta ya bushe."22Yesu ya amsa masu ya ce, "ku gaskata da Allah." 23Hakika, ina gaya maku, duk wanda ya ce wa dutsen nan tashi ka fada cikin tekun', bai kuwa yi shakka a zuciyarsa ba, amma ya gaskata haka kuwa zai faru, haka kuwa Allah zai yi.24Saboda haka ina dai gaya maku, komai kuka yi addu'a kuka roka, ku gaskata cewa samamme ne, zai kuma zama naku. 25Duk sa'add da kuke addu'a ku gafarta wa wadanda suka yi maku laifi, domin Ubanku shima zai gafarta maku naku laifi." 26(Amma in baku gafartawa mutane laifofinsu ba, Ubanku ma da ke sama ba zai gafarta maku ba.)27Da suka sake dawowa Urushalima. Yasu na tafiya cikin haikali, sai manyan firistoci, da marubuta, da dattawa suka zo wurinsa, 28suka ce masa, "Da wanne iko kake yin wadanan abubuwa? Ko kuwa wa ya ba ka ikon yinsu?"29Sai Yesu ya ce masu, "Zan yi maku wata tambaya. ku ba ni amsa, ni kuwa zan gaya maku ko da wanne iko ne nake yin wadannan abubuwan. 30Baftismar da Yahaya yayi, daga sama take ko kuwa daga mutum take? ku bani amsa".31Sai suka yi mahuwara da juna, suka ce, "in kuwa muka ce, 'daga sama take,' za ya ce, "To, don me ba ku gaskata shi ba? 32In kuwa muka ce, "amma in muka ce ta mutum ce zasu jejjefemu domi suna jin tsoron jama'a, don duk kowa ya tabbata, cewa Yahaya annabi ne. 33Sai suka amsa wa Yesu suka ce, "Ba mu sani ba" Yesu ya ce masu, "Haka ni kuma ba zan fada muku ko da wanne iko nake yin abubuwan nan ba."
"Sa'ad da Yesu da almajiransa sun yi kusa da Urushalima, sun shiga Betafaji da Betanya kusa da Dutsen Zaitun" Sun zo Betafaji da Betanya cikin yankin Urushalima.
Wannan sunan kauye ne.
"gaba da mu"
Wannan na nufin karamin jaki da zai iya ɗaukan mutum.
AT: "wanda ba wanda ya taba hawa"
Za a iya rubuta abin da kalman nan "wannan" ke nufin. AT: "Me ya sa kuke kunce, da kuma tafiya da aholakin"
"bukatar ta"
Yesu zai mayar da ita bayan ya gama amfani da ita. AT: "zai mayar da ita da wuri a lokacin da baya bukatan shi"
"Almajiran biyun sun tafi"
Wannan na nufin karamin jaki da zai iya ɗaukan mutum. Dubi yadda ka juya wannan cikin [Mark 11:2].
"Sun amsa"
"kamar yadda Yesu ya ce masu su amsa." Wannan na nufin yadda Yesu ya gaya masu amsa tambayar mutanen game da ɗaukan aholakin.
Wannan na nufin cewa sun bar su su cigaba da yin abin da suke yi. AT: "bar su su tafi da jakin"
"shimfiɗa mayafinsu a bayan ta don Yesu ya iya hawa." Ya fi sauki a tuka aholaki ko doki a sa'ad da akwai bargo ko wani abu makamancinsa a bayan. A wannan yanayi, almajiran sun shimfiɗa mayafinsu a kan ta.
"riga" ko "tufafi"
Al'ada ce a shimfiɗa mayafi a kan hanya daidai gaban mutane masu muhimmanci don a daraja su. Za a iya bayana wannan a fili. AT: "Mutane da yawa sun shimfiɗa mayafinsu
Al'ada ce a shimfiɗa ganyayen dabino a hanya gaban mutane masu muhimmancin don a martaba su. AT: "wasu suka baza ganyayen a da suka yanka daga fili, a kan hanya, don su martaba su"
"wanda suka bi bayansa"
Wannan kalma na nufin "Ka cece mu," amma mutane sun yi iihun kira da farinci a sa'adda suke so su yi wa Allah yabo. Za ku iya juya ta bisa ga yadda aka yi amfani da kalman, ko kuwa ku rubuta "Hosanna" ta wurin yin amfani da harshen ku bayana kalma. AT: "Yabi Allah"
Wannan na nufin Yesu. Ana iya bayana wannan a fili. AT: "Albarka ta tabbata a gare ka, kai wanda"
Wannan na nufin ikon Ubangiji. AT: "ikon Ubangiji"
"Albarka ta tabbata ga mulkin ubanmu Dauda." Wannan na nufin zuwan Yesu ya yi mulkin a matsayin sarki. AT: "Albarka ta tabbata ga zuwan mulkin ka" ko "Bari Allah ya albarkace ka a sa'adda kake mulkin ka mai zuwa"
"Allah ya albarkace"
A nan ana duban zuriyan Dauda da za su yi mulki kamar Dauda ne da kansa. AT: "na mafi girma cikin zuriyar ubanmu Dauda" ko "wanda mafi girma cikin zuriyar Dauda zai yi mulki"
Ma'ana mai yiwuwa 1) "Yabo ga Allah na sama" ko 2) "Bari wanda suke cikin sama su yi sowa su ce 'Hosanna'."
AT: "sama" ko "sama"
"saboda can da rana"
"shi da almajiransa goma sha biyun sun bar Urushalima sun tafi Betanya"
"sa'adda suke komowa zuwa Urushalima daga Betanya"
Wannan ya faru ne a sa'adda Yesu da almajiransa suna tafiya zuwa Urushalima.
"ko akwai wani 'ya'ya a"
Wannan na nufin cewa bai sami wani ɓaure. AT: "ya sami ganyaye ne kawai babu ɓaure a itacen"
"lokaci na shekara"
Yesu yana magana da itacen ɓaure ya kuma la'anta ta. Ya yi magana da itacen don almajiransa su ji shi.
"Ya yi magana da itacen"
Kalman nan "ta" na nufin cewa Yesu yana magana da itacen ɓauren.
"Yesu da almajiransa sun zo"
Yesu yana korin waɗannan mutane daga cikin haikali. Ana iya rubuta wannan a fili. AT: "ya fara fid da masu sayarwa da saya daga haikalin"
"mutanen da ke siya da sayarwa"
Allah ya faɗa a cikin maganarsa tawurin annabi Ishaya, cewa, haikalinsa zai zama gidan addu'a ga dukkan alummai.
Yesu ya sautawa shugabannen Yahudawan don sun yi amfani da haikalin ta hanyar da bai dace ba. AT: "An rubuta cikin nassosin cewa Allah ya ce, 'Ina so a kira gida na gidan da al'umma dukka za su yi addu'a."
Yesu ya kwatanta mutanen da 'yan fashi, haikali kuma da kogon 'yan fashi. AT: "Amma ku kamar 'yan fashi ne wanda suka maishe gida kogon 'yan fashi"
"kogon da 'yan fashi ke ɓoyewa"
"suna neman hanyar"
"da yammaci"
"Yesu da almajiransa sun bar birnin"
"suna tafiya a kan hanya"
Ka juya wannan magana yadda zai bayana da cewa itacen ya mutu. AT: "itacen ɓauren ya yi yaushi har zuwa jijiyoyin sa sai ya mutu"
"bushe"
Zai zama da taimako a bayana abin da Bitrus ya tuna. AT: "Bitrus ya tuna abin da Yesu ya faɗa wa itacen ɓauren"
"Yesu ya amsa wa almajiransa"
"Ina gaya maku gaskiya." Wannan magana na nanata abin da Yesu ya faɗa nan gaba.
"in wani ya ce"
A nan "zuciya" na nufin tunanin mutumin da kuma rayuwarsa na ciki. AT: "hakika in ya bada gaskiya a zuciyarsa" ko "in bai yi shakka ba amma ya bada gaskiya"
"Allah zai sa abin ya faru"
"Don haka ina gaya maku"
An fahimta cewa wannan zai faru saboda Allah zai tanada abin da kuka roƙa. Ana iya bayana wannan a fili. AT: "Allah zai ba ku"
Al'ada ce a yahudanci a tsaya a tsaye sa'adda ana addu'a ga Allah. AT: "Sa'adda kuke addu'a"
"kowane ƙiyayya da kuke da shi game da wani." Anan kalman nan "kowane" na nufin kowane ƙiyayya da kuke da shi game da wani do ya yi maku laifi ko wani fushi da kuke da shi game da wani.
"Yesu da almajiransa sun zo"
Wannan na nufin cewa Yesu yana tafiya a cikin haikalin; ba wai yana koƙarin shiga haikalin ba.
Kalman nan "su" na nufin firistocin, malaman attaura da kuma shugabanin jama'a.
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) Duk waɗannan tambayoyin suna da ma'ana iri ɗaya, an kuma yi su don a yi tambaya mai karfi game da ikon Yesu, saboda haka za a iya haɗa su. AT: "Wa ya ba ka ikon aikata waɗannan abubuwa?" 2) Tambayoyi biyu ne daban dabam, na farko na tambaya game da yanayin ikon, na biyun kuma na game da wanda ya ba shi ikon.
Kalmomin nan "waɗannan abubuwa" na nufin kife tabur na masu sayarwa da cikin haikali da Yesu ya yi, da kuma maganarsa da ke gãba da abinda firistocin da malaman attaura suke tunani. AT: "abubuwa kamar waɗanda ka yi anan jiya"
"ku ba ni amsa"
"baftismar da Yahaya ke yi"
"an ba shi ikon daga sama ne ko daga wurin mutane"
A nan "sama" na nufin Allah. AT: "daga Allah"
"daga mutane"
Wannan na nufin inda baftisman Yahaya ya fito.
Kalman nan "shi" na nufin Yahaya mai baftisma.
Wannan na nufin inda baftismar Yahaya ya fito.
Shugabannin addinin suna nufin cewa za su sha wahala daga wurin mutane in sun bada wannan amsar. AT: "Amma in mun ce 'daga mutum,' wannan ba zai zama da kyau ba." ko "Amma ba ma so mu ce, daga mutum ne."
Marubucin, Markus, ya bayana dalilin da ya sa shigabannin addinin ba sa son su ce cewa baftismar Yahaya daga mutum ne. Anan iya bayana wannan a fili. "Suka ce wa junansu don suna tsoron mutanen" ko "Ba sa so su ce cewa Baftismar Yahaya daga mutum ne domin suna tsoron mutane"
Wannan na nufin baftismar Yahaya. Abin da aka fahimta anan ana iya bayana shi. AT: "Ba mu san inda baftismar Yahaya ya fito ba"
1Sai Yesu ya fara koyar da su da misalai. "Wani mutum ne ya yi gonar inabi ya shingen ta, ya haka ramin matse inabin, ya kuwa gina hasumayar tsaro. Ya ba wandansu manoma jinginar gonar, sa'an nan ya tafi wata kasa mai nisa. 2Da lokaci ya yi, sai ya aika masu wani bawansa domin ya karbi wadansu daga cikin amfanin gonar. 3Amma manoman suka kama shi, suka yin masa duka, suka kore shi hannu banza.4Ya sake aikar wani bawan. Shi kuma suka raunata shi aka, suka wulakanta shi. 5Ya sake aiken wani. Shi kam, suka kashe shi. Haka fa aka yi ta yi da wadansu da yawa, sun dodoki wadansu, suka kuma kashe wadansu.6Yanzu dai yana da sauran daya tak, shine kaunatacen dansa. Daga karshe ya aike shi wurinsu, yana cewa, ai za su bashi girma. 7Amma manoman nan suka ce wa juna, "ai, wannan shine magajinsa, 'ku zo mu kashe shi, gadon ya zama namu."8Sai suka kamo shi, suka kashe shi, suka jefar da shi bayan shinge. 9To, me mai gonar inabin zai yi? Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba wadansu gonar.10Ashe, ba ku karanta wannan nassi ba? cewa, ' Dutsen da magina suka ki, shi ne ya zama mafi mahmimanci. 11Wannan daga Ubangiji ne, kuma ya yi dai dai a idanunmu."' 12Sai suka nemi su kama shi, don sun lura a kansu ne ya yi masalin, amma suka ji tsoron jama'a. Don haka suka kyele shi, suka tafi.13Suka aika masa da wadansu farisiyawa da Heridiyawa, don su sa masa tarko da kalamai cikin maganarsa. 14Da suka zo, suka ce masa, "Malam, gaskiya kana koyar da maganar Allah sosai, ba ka nuna bambanci tsakani mutane, sai koyar da tafarkin Allah kake yi sosai. "Shin, mu biya haraji ga Kaisar, ko a a?" 15AmmaYesu ya gane munafuncinsu, ya ce masu, "Don me kuke gwada ni? ku kawo mani dinarin in gani."16Suka kawowa Yesu daya. Ya ce masu, "Kamar waye da kuma rubutun wanene? suka ce masa, "Na Kaisar ne." 17Yesu ya ce, "to, ku ba Kaisar abinda yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah. Sai suka yi mamakinsa kwarai.18Sai Sadukiyawa suka zo wurinsa, su dake cewa babu tashin matattu. Suka tambaya shi suka ce, 19"Malam, Musa dai ya rubuta mana, cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, ya bar matarsa ba da, lallai ne dan'uwan mutumin ya auri matar, ya haifa wa dan'uwansa 'ya'ya.'20To an yi wadansu 'yan'uwa maza guda bakwai, na farko ya yi aure, ya mutu bai bar 'ya'ya ba. 21Na biyu kuma ya aure ta, shi ma ya mutu, ba 'ya'ya. Na ukun ma haka. 22Haka dai duk bakwai din, ba wanda ya bar 'ya'ya. A karshe kuma ita matar ta mutu. 23To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu? Don duk bakwai din nan sun aure ta".24Sai Yesu ya ce, "Ba saboda wannan dalili ne kuka yi kuskure ba, wato don ba ku san littafin ba, kuma ba ku san ikon Allah ba? 25Domin in an tashin daga matattu, ba a aure, ba a auraswa, amma sun zama kamar malaiku a sama.26Amma game da mattattun da suka tashi, ashe, ba ku taba karantawa a littafin Musa ba, yadda Allah ya ce masa? "Ni ne Allah na Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu'? 27Ai, shi ba Allahn mattatu bane, amma na rayyayu ne. Hakika kun yi kuskure ".28Sai wani malamin attuara ya zo ya ji suna muhawara da juna. Da dai ya ga Yesu yana ba su kyakkyawar amsa, sai ya tambaye shi, "Wanne Umarni ne mafi girma dukka?" 29Yesu ya amsa yace, "mafi girma shine, 'ku saurara ya Isra'ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji daya ne. 30Sai ka kaunaci Ubangiji Allah da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka da dukkan tunaninka, da dukkan karfinka. 31ta biyu itace, 'ka kaunaci makwabcinka kamar kanka, Ba wata doka da ta fi wadannan."32Sai malamin attaura ya ce masa, "Hakika gaskiyarka malam, Allah daya ne, ba kuma wani sai shi. 33A kaunace shi kuma da dukkan zuciya, da dukkan hankali, da dukkan karfi, a kuma kaunaci makwabci kamar kanka, ai ya fi dukkan hadayu na konawa." 34Da Yesu ya ga ya yi masa magana da hikima, sai ya ce masa, "Ba ka nesa da mulkin Allah." Bayan wannan kuma ba wanda ya sake tambayarsa wani abu.35Yesu ya amsa a lokacin da yake koyarwa a Haikali, ya ce "Yaya malaman attaura suke ce wa Kristi dan Dauda ne? 36Domin Dauda kansa, ta ikon Ruhu Mai Tsarki ya ce, "Ubangiji ya ce wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na kaskantar da makiyanka'. 37Dauda da kansa ya kira shi 'Ubangiji; To, ta yaya ya Almasihu zai zama Dan Dauda?" Babban taron jama'ar suka saurare shi da murna.38A koyarwa sa Yasu ya ce, "ku yi hankali da malaman attaura, masu son yawo da manyan riguna, suna so a gaishesu a kasuwa, 39da kuma son wuraren zama masu daraja a haikali, da wurin bukukuwa. 40Sun kuma kwace gidajen gwauraye, da yin doguwar addu'a, don mutane su gani. Wadanan mutanen zasu sami hukunci mai tsanani."41Sai ya zauna a gaban akwatin baiko a Haikalin, yana duban yadda jama'a suke zuba kudi a ciki. 42Wadansu masu arziki da yawa suna zuba kudi masu tsoka. Sai gwauruwa mara abin hanu ta saka anini biyu a ciki akwatin baikon.43Ya kira almajiransa, ya ce masu, "Hakika, ina gaya maku, abinda gwauruwa nan ta saka a akwatin baikon nan ya fi na sauran dukka. 44Su duk sun bayar daga yalwa tasu ne, ita kuwa daga cikin rashinta ta bada duk abinda take da shi."
Yesu ya yi wannan misalin saboda firistoci da malaman attaura da kuma shugabannin jama'a.
Kalman "su" a nan na nufin firistoci da malaman attaura da kuma shugabannin jama'a wanda Yesu ke magana da su a sura da ke a baya.
Ya sa abin toshe hanya kewaye da ita. zai iya zama kananan itatuwa da aka jera, shinge ko kuwa shingen da aka yi da duwatsu.
Wannan na nufin cewa ya sassaka rami a kan dutse wanda zai zama kasan wurin matse inabin wand da za a yi amfani da shi don tare ruwan 'ya'yan itacen inabin da aka matse. AT: "ramin da aka sassaka a dutse don matse inabi. ko "ya yi wata rami don tara ruwan inabi daga wurin matse inabi"
Har yanzu gonar na mai shi ne, amma ya ba bar manoman su lura da ita. A sa'anda inabin ya nuna, suna bukatan su ba wa mai gonar wasu sai su ajiya sauran.
Wanna na nufin lokacin girbi. Anan iya bayana wannan a fili. AT: "Sa'anda lokaci ya yi na girbin inabin"
"Amma manoman sun kama bawan"
Wannan na nufin cewa ba su ba shi wani 'ya'yan itacen ba. AT: "babu wani inabi"
"mai gonar ya aika wa manoman"
Ana iya rubuta wannan a fili. AT: "sun yi masa duka a kai, sun ji masa ciwo kwarai da gaske"
Waɗannan maganganu na nufin sauran barorin. AT: "aikan wani bawan ... waɗansu barorin"
Wannan na nufin barorin da mai gonar ya aika. Maganan nan "haka suka yi" na nufin cewa an wulakanta. Ana iya rubuta wannan a fili. AT: "Sun kuma wulakanta waɗansu barori wanda ya aika"
Na nufin cewa wannan ɗan mai gonar ne. AT: "ƙaunataccen ɗansa"
Wannan na nufin magaji mai gonar, wato wanda zai gaji gonar bayan mutuwar mahaifinsa. AT: "magajin mai gonar"
'Yan hayan na duban gonar a matsayin "gãdon." AT: "wannan gonar"
"Manoman suka kamo ɗan"
Yesu ya yi tambaya sai kuma ya bada amsan don ya koya wa mutanen. Ana iya rubuta tambayan ba a matsayin tambaya ba. AT: "Saboda haka ina gaya maku abin da mai gonar zai yi."
Yesu ya gama bada misalin, yanzu kuwa yana tambayan mutanen abin da suke tunani zai faru nan gaba.
kashe
Kalman nan "waɗansu" na nufin waɗansu manoma wanda za su lura da gonar. AT: "zai bada gonar ga manoma don su lura da ita"
Ana rubuta wannan nassi tun dã a cikin maganar Allah.
Yesu ya tunashe mutanen game da wata nassi cikin Littafi Mai Tsarki. Ya yi amfani da tambaya don ya sauta masu. AT: "Hakiƙa ba ku karanta wannan Nassi ba." ko "Ya kamata ku tuna da wannan Nassi."
AT: "Ubangiji ya maishe shi mafificin dutsen gini"
"Ubangiji ne ya yi wannan"
A nan "a idanunmu" na maɗaɗɗin gani, wanda ke nufin ra'ayin mutane. AT: "mun gani, mu kuma yi tunanin cewa ta yi daidai" ko "muna tunanin cewa abun ban mamaki ne"
"Su" na nufin firisitocin da malaman attaura da shugabannin jama'a. Waɗannan kungiya za a iya dubansu a matsayin "shugabannen Yahudawa."
"so"
Sun ji tsoron abin taron za su yi masu in sun kama Yesu. Ana iya bayana wannan a fili. AT: "amma sun ji tsoron abin da taron za su yi masu in sun kama shi:
"zarge su"
"Sai shugabannen Yahudawan suka aiki"
Wannan suna ce na jami'yan siyasa da ta yi goyon bayan Hiridus Antibas.
A nan marubucin ya bayana zambar da ake yi wa Yesu a matsayin "sa masa tarko." AT: "zambace shi"
A nan "su" na nufin waɗanda aka aika daga cikin Farisiyawan da mutanen Hiridus.
Wannan na nufin cewa Yesu ba damu ba. AT: "Ba ka damu da ra'ayin mutane ba" ko "ba ka damu da samun tagomashi a wurin mutane ba"
Riya suke yi. Anan iya bayana wannan a fili. AT: "Yesu ya san cewa ba so suke su san abin da Allah yana so su yi ba"
Yesu ya sautawa shugabannen Yahudawan don zambarsa suke koƙarin yi. AT: "Na san da cewa kuna so ku sa ni in faɗi wani abu da ba daidai ba don ku zarge ni."
Wannan kuɖin ya kai hakin ma'akaci na rana ɗaya.
Farisiyawan da Hiridiyawan sun kawo dinari ɗaya"
"hoto da suna"
A nan "Kaisar" na nufin kamaninsa da rubutunsa. AT: "Suka ce, 'Kamanin Kaisar da rubutunsa'"
Yesu yana koyar da cewa mutanensa su girmama gwamnati ta wurin biyan haraji. Anan iya bayana wannan a fili ta wurin canza sunan Kaisar zuwa gwamnatin Roma. AT: "Ba wa gwamnatin Roma abubuwan da ke na gwamnatin Roma"
Ana iya sa aikatau da aka fahimta . AT: "kuma ba wa Allah"
Sun yi mamakin abin da Yesu ya faɗa. Ana iya bayana wannan a fili. AT: "Sun yi mamakinsa da kuma abin da ya faɗa"
Wannan maganan ya bayana ko su wanene Sadukiyawa. Anan iya rubuta wannan a fili. AT: "wanda sun ce babu tashiwa daga cikin matattu"
Sadukiyawan suna ruwaita abin da Musa ya rubuta a attauran. Ana iya rubuta abin da musa ya rubuta kamar haka. AT: "Musa ya rubuta mana cewa ida ɗan'uwan mutum ya mutu"
"rubuto wa Yahudawa." Sadukiyawa wata kungiya ne na Yahudawa. Anan sun yi amfani da kalman nan "mu" don suna nufin kansu ne da kuma sauran Yahudawa.
"mutumin ya auri matar ɗan'uwansa"
"haifa wa ɗan'uwansa ɗa." Za a dubi ɗan farin mutumin a matsayin ɗan ɗan'uwan da ya mutu, zuriyar ɗan kuma za a dube su a matsayin zuriyar ɗan'uwan da ya mutu. Ana iya bayana wannan a fili. AT: "haifi ɗa wanda za a dube shi a matsayin ɗan ɗan'uwan da ya mutu"
Sadukiyawan sun yi magana game da yanayin da bai faru ba domin suna son Yesu ya faɗa masu abin da yake tunani daidai ne ko ba daidai ba. AT: "A misali akwai 'yan'uwa maza bakwai"
Waɗannan lambobin na nufin kowane ɗan'uwan kuma ana iya bayana shi a hakan. AT: "ɗan'uwan na farko ... ɗan'uwan na biyu ... ɗan'uwa na biyu"
Wannan na nufin dukka 'yan'uwan. AT: "'yan'uwa bakwain"
"na farkon ya aure matan ... na biyun ya aure ta." An yi maganar auren mace kamar an "ɗauke" ta.
Zai zama da taimako a bayana abin nufin da "haka kuma". AT: "ɗan'uwa na ukun ya aure ta kamar yadda ɗan'uwansa ya yi, sai shi ma ya mutu bai bar 'ya'ya ba"
Kowane daga cikin 'yan'uwan ya aure matan sai ya mutu kafin ya sami 'ya'ya da ita. Anan iya bayana wannan a fili. AT: "A ƙarshe dukka 'yan'uwa bakwai din sun aure wannan macen ɗaya bayan ɗaya, amma ba wanda ya sami 'ya'ya da ita, kuma ɗaya bayan ɗaya suka mutu"
Sadukiyawan suna gwada Yesu tawurin yin masa wannan tambayan. Idan masu karatunka za fahimci wannan a matsayin roƙo domin bayani, to ana iya rubuta wannan a matsayin magana. AT: "To, gaya mana ko matar wa za ta zama a ranar tashin matattu, a sa'adda sun tashi kuma."
Yesu ya sauta wa Sadukiyawan domin sun yi kuskure game da shari'ar Allah. Anan iya bayana wannan cikin magana. AT: "Kun yi kuskure domin ... ikon Allah."
Wannan na nufin cewa ba su fahimci abin da aka rubuta a cikin Nassosin Tsohon Alkawari ba.
"yadda Allah ke da iko"
A nan kalman nan "su" na nufin 'yan'uwan da macen da cikin misalin.
Tashiwa daga barci wata karin magana ne da ke nufin sake rayuwa kuma bayana an mutu.
Daga cikin duk waɗanda suka mutu. Wannan na bayana dukkan mutane da suka mutu a ƙarkashin ƙasa. Tashi daga cikin su na nufin sake rayuwa kuma.
"ba sa aure, kuma ba sa auraswa"
AT: "kuma ba wanda auras da su"
Wannan na nufin inda Allah ya ke.
AT: "wanda sun tashi" ko "wanda sun tashi don su rayu kuma"
"littafin da Musa ya rubuta"
Wannan na nufin bangaren Littafin Musa da ta yi bayani game da sa'adda Allah ya yi magana da Musa daga cikin jeji dake konewa amma bata kone ba. AT: "nassin game da jeji me konewa" ko "kalmomi game da jeji mai konewa"
Wannan na nufin kananan itace, wanda bai kai bishiya ba.
"game da sa'adda Allah ya yi wa Musa magana"
Wannan na nufin cewa Ibrahim da Ishaku da kuma Yakubu sun yi wa Allah sujada. Waɗannan mutane sun mutu, amma a ruhuniya suna a raye kuma suna yi wa Allah sujada.
A nan "mattattu" na nufin mutanen da suka mutu, "rayayyu" kuma na nufin mutanen da ke raye. Haka kuma, kalman nan "Allahn" ana iya bayana shi a fili cikin magana na biyu. AT: "ba Allah mattattun mutane ba, amma Allahn rayayyun mutane"
Wannan mutane ne wanda ke raye cikin jiki da kuma ruhaniya a haɗe.
Zai zama da taimakon a bayana abin da sun yin kuskure game da shi. AT: "In kun ce cewa mattattu ba za su rayu kuma ba, hakika kun yi kuskire"
"matuƙar kuskure" ko "ba daidai ba kwarai"
"Malamin attauran ya tambaye Yesu"
"Mafi muhimmanci" na nufin umurni mafi muhimmanci. AT: "umurni mafi muhimmanci dukka ... umurni mafi muhimmanci ta ce"
"Kassa kunne ya Isra'ila! Ubangiji Allahmu, Ubangiji ɗaya ne"
A nan "zuciya" da "rai" na nufin cikin mutum. Waɗannan maganganu huɗun na nufin "gabakiɗaya" ko "da naciya."
Yesu ya yi amfani da wannan don ya kwatantan yadda ya kyautu mutane su ƙaunaci juna da ƙuana iri ɗaya kamar yadda suke ƙaunar kansu. AT: "ƙaunaci makwabcinka kamar yadda kake ƙaunar kanka"
A nan kalman nan "waɗannan" na nufin dokoki biyun da Yesu ya gayawa mutanen.
"Amsa mai kyau, Malam" ko "Magana mai kyau, Malam"
Wannan na nufin cewa akwai Allah ɗaya ne kawai. AT: "Allah ɗaya ne kawai"
Kalman nan "Allah" an fahimce shi daga magana da ke a baya. AT: "babu wani Allah"
A nan "ziciya na nufin tunanin, ji ko kuwa cikin mutumin. Waɗanna maganganu uku an yi amfani da su tare ne kuma suna nufin "gabakiɗaya" ko "da naciya."
Wannan na kwatantan yadda ya kamata mutane su ƙaunaci juna da irin ƙaunar sa suke yi wa kansu. AT: "a ƙaunaci makwabci kamar yadda kake ƙaunar kanka"
Wannan na nufin cewa wani abu ya fi wani muhimmanci. A wannan yanayi, waɗannan dokoki biyun sun fi faranta wa Allah rai fiye da haɗayu. Anan iya bayana wannan a fili. AT: "ya fi muhimmanci fiye da" ko "ya fi faranta wan Allah rai fiye da"
A nan Yesu ya yi magana game da mutumin da ya shirya ya mika kansa ga Allah a matsayin sarki kamar yin kusa da mulkin Allah, sai ka ce wani wuri ne da ana gani. AT: "Kun yi kusa ku mika kanku ga Allah a matsayin sarki"
AT: "duk sun ji tsoro"
Bayan dan lokacin kaɗan, Yesu ya shi haikali. Wannan ba ya cikin hiran da ke a baya. AT: "Bayan haka, sa'anda Yesu yana koyaswa a cikin haikali, ya ce wa mutanen"
Yesu ya yi amfani da wannan tambaya don ya sa mutanen su yi zurfin tunani game da Zaburan da zai ruwaita. AT: "Dubi dalilin da ya sa malaman attaura sun ce Almasihu shi Ɗan Dauda ne."
"zuriyan Dauda"
Kalman nan "kansa" na nufin Dauda, an yi amfani da
Wannan na nufin cewa Ruhu Mai Tsarki ya iza shi. Wato, Ruhu Mai Tsarki ya shugabance Dauda cikin abin da ya făɗa. AT: "Ruhu Mai Tsarki ya iza shi"
A nan Dauda ya kira Allah "Ubangiji", ya kira Almasihu kuma "Ubangijina." Anan iya bayana wannan a fili. AT: "faɗa game da Almasihun, 'Ubangiji Allah ya ce wa Ubangijina"
Yesu ya ruwaita daga ckin Zabura. Anan Allah na magana da Almasihu ne. Zama a "hannun daman Allah" alama ce na samun martaba da iko daga Allah. AT: "zauna a wuri mai daraja tare da ni"
A wannan da aka ambata, Allah ya yi magana game da cin nasara ga abokn găba kamar ɗora ka a kansu. AT: " har sai na yi nasara da makiyin ka gabakiɗaya"
A nan kalman nan "shi" na nufin Almasihu.
AT: "to dubi yadda Almasihu zai iya zama daga zuriyar Dauda"
Sunan nan "gaisuwa" za a bayana shi da aikatau nan "gaishe." Waɗannan gaisuwar na nufin cewa mutanen sun martaba malaman attaura. AT: "a gaishe su da martaba a cikin kasuwa" ko "mutane su gaishe su da martaba a cikin kasuwa"
A nan Yesu ya bayana magudi da malaman attaura ke yi wa gwamraye da sata gidajen su a matsayin "kwace" gidajensu. AT: "sun kuma yi wa gwamraye magudi don su sata gidajensu"
Kalman nan "gwamraye" da "gidaje" na nufin mutanen da ba su samu mai taimakon ba, da kuma mallakar masu muhimmanci na mutumin. AT: "kowane abu daga wurin mutanen da basu da mai taimako"
AT: "Hakiƙa Allah za hukunta su da hukunci mai tsanani" ko "Hakiƙa Allah zai yi masu hukunci mai tsanani"
Kalman nan "tsanani" na nufin kwatanci. Anan kwatanci an yi shi ne da sauran mutane wanda aka hunkunta. AT: "za a yi masu hukunci fiye da sauran mutane"
Wannan akwatin da kowa zai iya amfani da shi akan sa baikon haikali a ciki.
"kananan tsabar kuɗi biyu." Waɗannan sune tsabar kuɗi masu daraja da akwai.
"farashin ta kaɗan ne." Farashin dinari kaɗan ne. A juya "dinari" da sunan kuɗi mai karami farashin a harshenku in kuna da wanda farashin ta kaɗan.
"Yesu ya kira"
Wannan na nuna cewa maganar da ya bi baya gaskiya ne kuma na da muhimmanci. Dubi yadda ka juya wannan cikin [Markus 3: 28]
"na dukka sauran mutanen da suka sa kuɗi a ciki"
yawan dukiya, yawan abubuwa masu daraja
"rashin" ko "kaɗan da take da shi"
"rayu da shi"
1da Yesu ke fita daga Haikalin, sai daya daga cikin almajirnsa ya ce masa "malam, dubi kyawawan duwatsunnan da kyawawan gine-ginnenan!" 2Ya ce masa, ka ga wadannan kyawawan gine- ginen? babu wani dutsen da za a bar shi akan dan'uwansa, da ba za a rushe shi ba."3Yana zaune a kan dutsen zaitun wanda yake kusa da Haikali, sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawus suka tambaye shi a asirce, suka ce. 4Gaya mana yaushe za a yi wadannan abubuwa? mecece zata zama alamar faruwar wadanna abubuwa da zasu faru?"5Yesu ya ce masu, "ku kula, kada kowa ya rudeku. 6Da yawa za su zo da sunana, suna cewa nine shi, har su bad da mutane da yawa.7In kuka ji labarin yake- yake, da jita-jitarsu kada ku damu, wannan zai faru, amma karshen duniya bai gabato ba. 8Al'umma za ta tasarwa al'umma, mulki ya tasarwa mulki. Za a yi girgizar kasa awurare dabam-dabam, da kuma yunwa, amma fa dukkan wadanna abubuwan mafarin azaba ne.9Amma, ku zauna a fadake. Don za su kai ku gaban majalisa. za a yi maku duka a cikin majami'u. Su kuma kai ku gaban masu mulki da sarakuna, saboda sunana, domin ku ba da shaida a gare su. 10Amma lallai sai an fara yi wa dukkan al, ummai bishara.11Sa'ad da suka kai ku gaban shari'a suka mika ku, kada ku damu a wannan lokacin, za a baku abin da zaku fada, Amma duk abin da aka yi muku a wannn lokacin, shi za ku fada, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu mai tsarki ne. 12Dan'uwa zai bada dan'uwarsa akashe shi, uba kuwa dansa. Yara kuma zasu tayar wa iyayensu har su sa akashe su. 13Za a ki ku saboda sunana, amma duk wanda ya jumre har karshe zai cetu.14Sa'adda kuka ga an kafa mummunan aikin sabo mai ban kyama a wurin da bai kamata ba (bari mai karatu ya fahimta), to, bari wadanda suke kasar Yahudiya, su gudu zuwa dutse. 15Wanda yake tudu kuma kada ya sauko ya shiga gida garin daukar wani abu. 16Wanda yake gona kuma kada ya koma garin daukar mayafinsa.17Amma, kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokacin. 18Ku yi addu, a kada abin ya faru da damina. 19A lokacin za ayi wata matsanaciyar wahala, wadda bata taba faruwa ba, tun farkon halittar da Allah ya yi har zuwa yau, ba kuwa za a taba yi ba har abada. 20In da ba ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba Dan adam din zai tsira. Amma saboda zabbabunan da ya zaba, ya rage kwanakin.21To, in wani ya ce maku, kun ga Almasihu nan!' ko, 'kun gan shi can, kada ku gaskata. 22Gama almasihan karya, da annabawan karya zasu bayyana kuma, zasu yi abubuwan al'ajibai masu ban mamaki. 23Amma ku zauna a fadake, Na dai fada maku wadannan abubuwan kafin lokacin.24Amma, bayan matsanaciyar wahalannan, rana zata duhunta, wata kuma ba zai bada haske ba. 25Taurari za su fado daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama. 26Sa' annan zasu ga Dan mutum na zuwa a cikin gajimare, da iko mai girma da daukaka. 27Zai aiko da mala'ikunsa su tattaro zabbabunsa daga kusuwoyi hudu na duniya(watau Gabas da Yamma, kudu da Arewa) har zuwa karshen sama.28"Ku yi koyi da itacen baure. Da zarar rassansa sun fara taushi yana kuma fitar da toho, kun san damina ta yi kusa ke nan. 29Sa'adda kuka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku dai sani ya kusato, a bakin kofa ma ya ke.30Hakika ina gaya maku, zamanin nan ba zai shude ba sai dukan abubuwan nan sun faru. 31Sararin sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba. 32Amma wannan rana ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai dai Uban kadai.33Ku kula, ku zauna a fadake, kuna addu'a don baku san ranar da lokacin zai yi ba. 34Kamar yadda mutum mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta bayinsa kan gidansa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai gadi ya zauna a fadake.35To, ku zauna a fadake don ba ku san lokacin da maigidan zai zo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne. 36Kada ya zo ba zato, ya samu kuna barci. 37Abinda na gaya maku, ina gaya wa kowa, shine ku zauna a fadake!"
Sa'adda sun bar haikalin, Yesu ya gaya wa almajiransa game da abin da zai faru da kyawawan haikalin da Hiridus ya gina a nan gaba.
Su "duwatsun" na nufin duwatsun da an yi su gine-ginnen da su. AT: "kyawawan gine-ginnen da kyawawan duwatsun da an yi da"
An yi amfani da wannan tambaya domin a jawo hankali ga gine- ginen. AT: "Dubi wannan gine- ginen! Babu wani ɗutsen" ko "Kun gan waɗannan gine- ginen masu girma yanzu, Amma babu wani dutsen"
Ana nufin cewa makiyan sojoji za su rushe duwatsun. AT: "babu wani dutsen da zai kasance a kan ɗan'uwansa, don makiyan sojoji za su zo su rushe waɗannan gine- ginen"
Yesu ya gaya masu abin da zai faru nan gaba, a cikin amsan tambayoyin almajran game da rushewan haikalin da abin da zai faru.
Ana iya bayyana cewa Yesu da almajiransa sun yi tafiya zuwa Dutsen Zaitun. AT: "Bayan da sun isa Dutsen Zaitun, da yake akasi da haikalin, Yesu ya zauna. Sai Bitrus"
lokacin da suke su kadai
Wannan na nufin abin da Yesu ya ce zai faru da dutsunan haikalin. AT: "waddannan abubuwan sun faru da gine- ginen haikalin ... ya yi kusan faruwa da gine- ginen haikalin"
"da dukka wadannan abubuwa"
"wa almajiransa"
A nan "ruɗu misaline na canza wa wani ra'ayi ya yarda da abin da ba gaskiya bane. AT: "ruɗe ka ... za su ruɗe mutane dayawa" (Dubi: [[rc://*/ta//man/translate/figs-metaphor]])
AT: 1)" riya iko na" ko 2) "cewa Allah ya aiko su."
"Ni ne Almasihun"
"ji game da yake-yake da labarin yake-yake." AT: 1) "ji karan yake-yake a krukusa da labarin yake-yake da nisa" ko 2) "ji game da yake-yaken da sun fara kai ruhotu game da yake-yake da sun yi kusan faruwa"
"amma ba karshen ba ne" ko "amma karshen ba za ta faru ba sai anjuma" ko "amma karshen zai zama anjuma"
Mai yiwuwa wannan na nufin karshen duniya.
Wannan ƙarin magana na nufin yin faɗa da juna. AT: "za ta yi faɗa da juna"
An fahimci kalmomin "za ta tasarwa" daga jumla da ta wuce. AT: "mulki za ta tasarwa mulk" ko "mutanen wani mulki za su yi faɗa da mutanen wani mulki"
Yesu ya yi maganar waɗannan abubuwa kamar farkon azabar haifuwa domin mafi matsanancin abubuwa za su faru bayan su. AT: "Waɗannan abubuwa zasu zama kamar azaba na farko da mace take sha a loƙacin da ta yi kusan haifuwa"
"Ku shirya da abin da mutane za su
"ɗauke ku a sa ku cikin mulkin majalisa"
AT: "mutane za su yi maku duka"
Wannan na nufin hukunta ku. AT: "Za a sharanta ku a gaban" ko Za a sharanta a kuma hukunta ku ta wurin"
"saboda ni" ko "bisa labari na"
Wannan na nufin za su shaida game da Yesu. AT: "ku kuma shaida masu game da ni" ko "za ku kuma gaya masu game da ni"
Yesu ya na magana game da abubuwan da ɗole za su faru kafin karshen ya zo. AT: "Amma ɗole sai an fara yi wa dukkan al'ummai bishara kafin karshen ya zo"
Wannan anan na nufin sa mutane a ikon hukuma. AT: "kai ku gaban hukuma"
An fahimci kalmomin "zai yi magana" a jumla da ta wuce. AT: "amma Ruhu mai Tsarki zai yi magana ta wurinku"
"Wani ɗan'uwa zai sa wani ɗan'uwa cikin ikon mutanen da za su kashe shi" ko "Yan'uwane za su sa yan'uwanensu cikin ikon mutanen da za su kashe su." Wannan zai faru da sosai wa mutane dayawa. Yesu ba ya maganan mutum ɗaya da ɗan'uwansa.
Wannan na nufin 'yan'uwa mata da maza. AT: "Mutane ... yan'uwani"
An fahimci kalmomin "zai mika wa mutuwa" daga jumla da ta wuce. Wannan na nufin cewa waɗansu ubanne za su bashe yaransu, kuma wannan bashewan zai sa a kashe yaransun. AT: "ubanne za su ba da yaransu ga mutuwa" ko "ubanne za su bashe yaransu, mika su don a kashea su"
Wannan na nufin cewa yara za su yi hamayya da iyayensu su kuma bashe su. AT: "Yara za su yi hamayya da iyayensu"
Wannan na nufin cewa hukuma za su hukunta iyayen ga mutuwa. AT: "sa hukuma su hukunta iyayen ga mutuwa" ko "hukuman za su kashe iyayen"
AT: "Kowa zai ki ku"
Yesu ya yi amfani da "sunana" don ya na nufin kansa. AT: "saboda ni" ko "saboda kun gaskanta da ni"
AT: "duk wanda ya jumre har karshe, Allah zai ceci wannan mutum" ko "Allah zai ceci duk wanda ya jumre har karshe"
A nan "jumre" na wakilcin cingaba da aminci da Allah ko a wahala. AT: "duk wanda ya sha wahala ya kuma saya har karshe da aminci ga Allah"
AT: 1) "har ga karshen rayuwarsa" ko 2) har ga karshen loƙacin wahala"
Wannan jumla na daga littafin Daniel. Ya kamata masu saurarans
Masu sauraron Yesu na iya gani cewa wannan na nufin haikali ne. AT: "na tsaye a cikin haikalin, inda bai kamata ya tsaya ba"
Wannan ba Yesu ba ne ke magana. Matiyu ya kara wannan domin ya sami hankalin masu karatun, domin su ji wannan gargadi. AT: "bari duk wanda ya na karanta wannan ya kasa kunne ga wannan gargadin"
Kan tudu da Yesu ya yi zama na nan shimfiɗaɗɗe, kuma mutane na iya sayawa akansu.
Wannan na nufin koma zuwa gidansa. AT: "kada ya koma gidansa"
"ɗaukar mayafinsa"
Wannan wata hanya ne na ce wani na da juna biyu. AT: "na da ciki"
"Ku yi addu'a wannan kwanakin" ko "Ku yi addu'a waɗannan abubuwa"
"loƙacin sanyi" ko "sanyi, loƙacin damin." Wannan na nufin loƙacin da ke da sanyi kuma babu dadi da kuma wuyan tafiya.
"ba za a sake samin mafi yawa kuma ba." Wannan ya nuna irin muni da wuya da azaban zai zama. Ba a taba yin irin azaba mai muni kamar irin wannan ba.
"ba za a sake samin mafi yawa kuma ba" ko "kuma bayan azaban, ba za a sake wani azaba kamar haka ba"
"ya rage loƙacin." Zai yi kyau a takaita wane "kwanakin" ne ana nufi. AT: "ya rage kwanakin wahala" ko "ya rage loƙacin wahala"
Kalmar "Ɗan Adam" na nufin mutane, kuma "tsira" na nufin ceton jiki. AT: "babu wanda zai tsira" ko "kowa zai mutu"
"don a taimake zabbabun"
Jumlar "waɗanda ya zaba" na nufin abu ɗaya da "zabbabun." An nanata cewa Allah ya zabi waɗannan mutanen.
"mutanen da suke ce su Almasihu ne"
"begen a ruɗe" ko "niyar ruɗe"
Jumlar "har zabbabun" na nufin cewa Almasihan karya da annabawan karya za su so su ruɗe mutane, amma ba za su san ko za su iya rudin zabbabun ba. AT: "don a ruɗe mutane, a kuma rude zabbabun, in ya yiwu"
"mutanen da Allah ya zaba"
"ku zauna da shiri"
Yesu ya gaya masu waɗannan abubuwa domin ya ƙwabe su. AT: "Na dai faɗa maku waɗannan abubuwa kafin loƙaci don in ƙwabe ku"
AT: "rana zata zama da duhu"
An yi maganar wata anan kamar na da rai kuma na iya ba wa wani abu. AT: "watan ba za ta haskaka ba" ko "watan za ta yi duhu"
Wannan ba ya nufin cewa za su fado kasa ba amma za su faɗi daga inda suke. AT: "tauraron za su fadi daga inda suke a sararin sama"
AT: "za a kuma girgiza ikon da suke a sararin sama" ko "Allah zai girgiza ikon da suke a sararin sama"
"abubuwa masu iko a cikin sammai." AT: 1) "wannan na nufin rana, wata, da tauraro ko 2) wannan na nufin ruhuhi masu iko.
"sararin sama"
"Sai mutane za su gan"
"da iko da ɗaukaka"
Kalmar "zai" na nufin Allah kuma ƙarin magana ne wa mala'ikunsa, don su ne waɗanda za su tara zabbabun. AT: "za su tara" ko "mala'ikunsa za su tara"
An yi maganar dukka duniya kamar "kusuwoyi hudu," wanda na nufin jihohi: Gabas, Yamma, kudu da Arewa" ko "dukka yankin duniya"
An ba da waɗannan matsananci biyun don a nanata cewa za a tara zabbabun daga dukka duniya. AT: "daga kowane wuri a duniya"
Jumlar "reshe" na nufin reshen itacen bauren. AT: "reshensa sun fara taushi su na kuma fitar da ganyensu"
"kore da laushi"
An yi maganar itacen baure anan kamar ya na da rai kuma na iya sa ganyensa su yi girma. AT: "ganyensa sun fara tohowa"
sashin shekara mai dumi ko loƙacin shuki
Wannan na nufin loƙacin azaba. AT: "waɗannan abubuwa da na ƙwatanta"
"Ɗan Mutumin ya yi kusa"
Wannan ƙarin magana na nufin cewa ya yi kusa kuma yi kusan zuwa, na nufin mai tafiya ya yi kusan isan kofan garin. AT: "kuma ya yi kusa"
Wannan ya nuna cewa magana da ke biye na da muhimminci. Dubi yanda kun juya wanna a cikin 3:28.
Wannan hanya ne mai kyau na magana game da mutum da ke mutuwa. AT: "ba zan mutu ba" ko "ba zai kare ba"
Jumlar "waɗannan abubuwan" na nufin lokacin azaba.
An ba da matsananci biyu domin a bayyana dukka sarari, tare da rana,wata, tauraro, da tauraro masu kewayan rana da dukkan kasan. AT: "Sararin, da kasan, da komai a cikinsu"
"daina kasance." Wannan jumla anan na nufin karshen duniya.
Yesu ya yi maganar rasa ikon magana kamar abu ne da ba zai taba mutuwa ba. AT: "maganata ba za su taba rasa ikonsa ba"
Wannan na nufin loƙacin da Ɗan Mutum zai dawo. AT: "wannan rana ko sa'a da Ɗan Mutum zai dawo" ko "ranar ko sa'a da zan dawo"
Waɗannan kalmomin sun nuna waɗansun da ba su san loƙacin da Ɗan Mutum zai dawo ba, dabam ne daga Uban, wanda ya sani. AT: "ba wanda ya san-ko mala'ikun a sama ko Ɗan-amma Uban" ko "ko mala'ikun a sama ko Ɗan sun sani; ba wanda ya sani sadai Uban"
A nan "sama" na nufin wurin da Allah yake zama.
Zai yi kyau ku fasara "Uba" da irin kalma da harshenku na amfani a kirin uba na mutuntaka. Wannan kuma ƙarin magana ne da na bayyana cewa Uban ya san loƙacin da Dan zai dawo. AT: "amma Uban ne kadai ya sani"
Za a iya bayyana da kyau abin da "loƙacin" na nufi anan. AT: "loƙacin da dukka abubuwan nan zasu faru"
"gaya wa kowanne aikin da zai yi"
"zai iya dawo da yamma"
Zakaran tsuntsu ne da na "cara" da sammako ta wurin kira mai karfi.
A nan Yesu ya yi maganar rashin zama da shiri kamar "barci." AT: "same ku da rashin shirin dawowarsa"
1Idin Ketarewa da bukin gurasa mara yisti sauran kwana biyu kenan, sai shugabanin firistoci da malaman attaura suka nemi yadda zasu kama Yesu a asirce domin su kashe shi. 2Suna cewa amma "Ba a lokacin idin ba, domin kada su haddasa hargitsi a tsakanin mutane".3Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana shirin liyafa kenan sai ga wata mace dauke da kwalbar turare mai tamanin kwarai, ta shafa masa a kansa. 4wasu dake tare da Yesu suka husata, suna kwalbarta da cewa 5"Ai wannan turare ne mai tsada, ina laifin a sayar a raba wa talakawa kudin? ina dalilin wannan almubazaranci?6Sai Yesu yace masu "Ku kyaleta, don me kuke tsauta mata, 7ai Idan kuna da niyyar taimakon talakawa ko matalauta, suna nan tare da ku ko a yaushe amma ni bazan kasance da ku kullum ba. 8Macen nan tayi aiki nagari domin shirya jikina ga jana'iza. 9hakika, Ina gaya maku, duk inda za'a yi bishara a duniya baza a mance da matan nan da hidimar da ta tayi mini ba."10Da jin haka sai Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin manzannin ya ruga zuwa wurin baban firist domin ya bashe shi a garesu, 11Da mayan firistoci suka ji haka suka yi murna matuka tare da alkawarin kudi ga Yahuza, shi kuwa sai ya fara neman zarafin da zai mika Yesu a gare su.12A ranar farko ta bukin gurasa marar yisti da kuma hadayar ragon Idin ketarewa, almajiransa suka ce masa "Ina zamu shirya liyafar domin idin ketarewa? 13Ya aiki biyu daga cikin almajiransa da cewa "Ku shiga cikin birnin, zaku tarar da wani mutum dauke da tullun ruwa. 14Duk gidan da ya shiga ku bishi, sai ku cewa mai gidan, malam yace "ina bukatar masauki domin hidimar idin ketarewa tare da almajiraina?"'15Zai kuwa nuna maku babban bene gyararre. Sai ku yi mana shiri a can." 16Da shigar almajiran cikin birnin, sai kome ya kasance yadda ya fada, su kuwa suka yi shirye shiryen idin ketarewar.17Da maraice ta yi, sai ya tare da sha biyun. 18Yayin da suke zazzaune a teburin suna cin abincin, sai Yesu ya ce "Hakika ina gaya maku wani da ke ci tare da ni a nan zai bashe ni". 19Sai suka damu suka tambaye shi daya bayan daya suna cewa "Hakika bani bane ko?"20Yesu ya amsa masu da cewa "Daya daga cikin sha biyu ne, wanda ke sa hannu tare da ni yanzu cikin tasar". 21Dan Mutum zai tafi ne yadda nassi ya umarta game da shi amma kaiton wanda zai bashe shi! "zai, fiye masa, dama ba a haife shi ba".22Lokacin da suke cin abincin, Yesu ya dauki gurasa ya sa albarka, ya gutsuttsura ta, sai ya basu yana cewa "Wannan jikinana ne". 23Ya kuma dauki koko, yayi godiya, ya basu, su kuwa suka sha daga kokon. 24Ya ce "Wannan jinina ne na alkawari da an zubar ga yawancin mutane". 25Hakika, bazan kara sha daga wannan ruwan inabi ba sai a ranar da zan sha sabo cikin mulkin Allah."26Bayan sun raira wakar yabo ga Allah, sai suka tafi wurin dutsen zaitun. 27Yesu ya ce masu dukkan ku zaku yi tuntube harma ku fadi saboda ni gama rubuce take cewa "Zan buge makiyayin, tumakin kuwa za su watse;28Amma bayan tashina, zai yi gaba in riga ku zuwa Galili. 29Bitrus ya ce masa "ko dukkansu sun fadi, faufau banda ni".30Yesu yace masa "Hakika ina gaya maka, cikin wannan dare kafin carar zakara ta biyu zaka yi musun sani na sau uku". 31Amma Bitrus ya sake cewa "Koda za'a kasheni tare da kai ba zan yi musun sanin ka ba". Dukkan su kuwa suka yi wannan Alkawari.32Suka isa wani wuri da ake kira Getsamani, sai Yesu ya ce wa almajiransa "Ku dakata anan domin zan je inyi addu'a". 33Sai ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya. Ya fara jin wahala mutuka tare da damuwa kwarai. 34Sai ya ce masu "Raina na shan wahala harma kamar in mutu. Ku dakata a nan, ku zauna a fadake".35Da Yesu yayi gaba kadan, sai ya fadi kasa yayi addu'a yana cewa idan mai yiwuwa ne "A dauke masa wannan sa'a daga gare shi. 36Ya ce "Ya Abba Uba, kome mai yuwane gare ka, ka dauke mini kokon wahalan nan, duk da haka ba nufina ba sai dai naka".37Da komowarsa ya same su suna barci, sai ya ce wa Bitrus, Siman barci kake? Ashe, ba za ka iya zama a fadake ko da sa'a daya ba? 38Ku zauna a fadake, kuyi addu'a kada ku fada cikin jaraba. Lalle ruhu na da niyya amma jiki raunana ne. 39Sai ya sake komawa, yayi addu'a, yana maimaita kalmominsa na farko.40Har wa yau kuma ya sake dawowa, ya same su suna barci don barci ya cika masu idanu kwarai, sun kuwa kasa ce masa kome. 41Ya sake komowa karo na uku yace masu "har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka! Lokaci yayi, an bada Dan Mutum ga masu zunubi". 42Ku tashi mutafi kun ga, ga mai bashe ni nan ya kusato."43Nan da nan, kafin ya rufe baki sai ga Yahuza, daya daga cikin sha biyun da taron jama'a rike da takkuba da kulake. Manyan firistoci da malaman attaura da shugabanni suka turo su. 44Mai bashe shi din nan ya riga ya kulla da su cewa "Wanda zan yi wa sumba shine mutumin, ku kama shi ku tafi da shi a tsare. 45Da isowarsa kuwa, sai ya zo wurin Yesu ya ce "Ya malam!". Sai ya sumbace shi. 46Su kuwa suka kama shi, suka tafi da shi.47Amma daya daga cikin na tsaye ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya yanke masa kunne. 48Sai Yesu ya ce "kun fito kamar masu kama yan fashi da takkuba da kulake, domin ku kama ni? 49Lokacin da nake koyarwa a Haikali, kowace rana da ku, baku kama ni ba. Amma anyi haka ne domin a cika abinda Nassi ya fada." 50Daga nan duk wadanda suke tare da Yesu suka yashe shi, suka tsere.51Wani saurayi, daga shi sai mayafi ya bi shi, suka kai masa cafka. 52Shi kuwa ya bar masu mayafin ya gudu tsirara.53Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. a can suka tara dattawa duk da manyan firistoci da shugabanni da marubuta, suka taru a wurinsa. 54Bitrus kuwa ya bi shi daga nesa har cikin gidan babban firist. Ya zauna tare da dogaran Haikalin, yana jin dumin wuta.55Sai, manyan firistoci da duk 'yan majalisa Yahudawa suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi. Amma basu samu ba. 56Da yawa kuma suka yi masa shaidar Zur (Karya), amma bakin su bai zama daya ba.57Sai wadansu kuma suka taso suka yi masa shaidar zur (karya) suka ce. 58"Mun ji ya ce, wai zai rushe haikalin nan da mutane suka gina, ya sake gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba". 59Duk da haka, sai shaidar tasu bata zo daya ba.60Sai babban firist ya mike a tsakanin su, ya tambayi Yesu yace "Ba ka da wata amsa game da shaidar da mutanen nan suke yi a kanka? 61Amma yayi shiru abinsa, bai ce kome ba. Sai babban firist din ya sake tambayarsa "To, ashe kai ne Allmasihu Dan Madaukaki? 62Yesu ya ce "Nine. Za ku kuwa ga Dan Mutum zaune dama ga mai iko, yana kuma zuwa cikin gajimare".63Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa yace "Wacce shaida kuma zamu nema? 64Kun dai ji sabon da yayi! Me kuka gani? Duk suka yanke masa hukunci akan ya cancanci kisa. 65Wadansu ma suka fara tottofa masa yau, suka daure masa idanu, suka bubbuge shi suna cewa "Yi annabci" Dogaran kuma suka yi ta marinsa.66Bitrus kuwa na kasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo. 67Da ta ga Bitrus na jin dumi, ta yi masa kallon gaske ta ce "Kaima ai tare kake da banazaren nan Yesu". 68Amma ya musa ya ce "Ni ban ma san abinda kike fada ba balle in fahimta". Sai ya fito zaure. Sai zakara yayi cara.69Sai baranyar ta ganshi, ta sake ce wa wadanda ke tsaitsaye a wurin, "Wannan ma daya daga cikinsu ne". 70Amma ya sake musawa, jim kadan sai na tsaitsayen suka ce wa Bitrus "Lalle kai ma dayansu ne don ba Galile ne kai".71Sai ya fara la'anta kansa yana ta rantsuwa yana ce wa "Ban ma san mutumin nan da kuke fada ba". 72Nan da nan sai zakara ya yi cara ta biyu, Bitrus kuwa ya tuna da maganar Yesu a gare shi cewa "Kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sani na sau uku". Da ya tuno haka, sai ya fashe da kuka.
Kwana biyu kafin idin ketarewa, shugabanin firistoci da malaman attaura suna yin shiri a boye don su kashe Yesu.
ba tare da mutuane su gane ba
Kalmar "su" na nufin shugabanin firistoci da malaman attaura.
Wannan na nufin ba su kama Yesu a loƙacin idin ba. AT: "Kada mu yi a loƙacin idin"
Dama wannan mutumin na da kuturta amma yanzu babu. Wannan mutum dabam ne da Saminu Bitrus da kuma Saminu Zilot.
A al'adan Yesu, loƙacin da mutane sun taru don cin abinci, su na kwanciye da gefensu, jinginar da kansu akan pillo a gefen tuburin.
Wannan ƙwalba ne da an yi shi daga alabaster. Alabaster wata kore-farin dutse mai sada. AT: "kyaukyauwar farin ƙwalba"
"da ya ƙunsa turare mai tsada da ake kira nard." Nard na da tsada, kuma mai ne da kamshi da ana amfani don yin turare.
"a kan Yesu"
Sun yi wannan tambaya domin su nuna cewa sun ki yadda matan ta na zuba turaren akan Yesu. AT: "Abin tsoro ne cewa ta na batar da turaren!"
Markus na so ya nuna wa masu karatunsa cewa waɗanda suke a loƙacin sun damu da ƙudi. AT: "Da mun sayad da wannan turaren" ko "Da ta sayad da wannan turaren"
"dinari ɗari uku." Dinari sulen azurfa ne na Roma.
Jumlar "talakawa"na nufin mutane masu talauci. Wannan na nufin ba da ƙudin wa talakawa daga sayad da turare. AT: "a ba wa talakawa ƙudin"
Yesu ya tsauta wa mutanen don maganganu akan abin da matannan ta yi. AT: "Kar ku dame ta!"
Wannan na nufin mutane masu talauci. AT: "talakawa"
Wannan na nuna cewa magana da na biye gaskiya ne kuma ya na da muhimminci. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 3:28.
AT: " duk inda masubi na sun yi bishara"
"za a kuma yi shilar hidimar da matan nan ta tayi"
Yahuza bai rigaya bashe Yesu ba, ya je ya yi shiri da su. AT: "don ya shirya da su cewa zai ba su Yesu"
"kowa masu Yesu don su iya kama shi"
Zai yi kyau ku bayyana abin da mayan firistoci sun ji. AT: "Da mayan firistoci suka ji abin da ya ke da niyar yin masu"
A ranar farko ta bukin gurasa marar yisti, al'ada ne a yi hadayar rago. AT: "da loƙacin da al'adan su ya kai na yin hadayar ragon idin ketarewa"
"ɗauke da babban tullu cike da ruwa"
AT: "Malamman mu su na so su san inda masuakin yake, inda zai iya cin abincin idin ketarewa tare da almajiransa."
dakin baki
A nan "ketarewa" na nufin abincin idin ketarewa. AT: "ci abincin idin ketarewa"
Za su shirya abinci wa Yesu da almajiransa don su ci. AT: "Shirya mana abincin a can"
"Almajirai biyun suka tafi"
"kamar yadda Yesu ya faɗa"
Zai yi kyau ku faɗa inda sun zo. AT: "ya zo gidan da sha biyun"
A al'adan Yesu, loƙacin da mutane sun taru don cin abinci, su na kwanciye da gefensu, su kuma jinginar da kansu akan pillo a gefen tuburin.
Wannan na nufin cewa almajiran sun tambaye juna "ɗaya bayan ɗaya."
AT: 1) wannan tambaya ne da almajiran sun zata amsan ya zama babu ko 2) wannan tambaya ne da bai bukaci amsa ba. AT: "Hakika ba ni ne zan bashe ka ba!"
"Shi ne ɗaya daga cikin sha biyun, wanda yanzu"
A al'adan Yesu, mutane na yawan cin gurasa, tsomawa a cikin tasar miya ko mai da an hada da ganyen itace.
A nan Yesu ya na nufin annabcin nassi game da mutuwarsa. Idan ku na da wata hanya mai kyau na magana akan mutuwa a harshenku, ku yi amfani da shi. AT: "Gama Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda nassi ya ce"
AT: "wanda ya bashe da Ɗan Mutum"
Wannan shimfiɗaɗɗer gurasa marar yisti. wanda an ci a abincin ketarewa.
Wannan na nufin cewa ya gutsuttsura gurasa wa mutanen su ci. AT: "ya gutsuttsura ta"
"Karba wannan gurasa. Jikina ne." Ko da shike yawanci sun fahimci wannan da cewa gurasa alama ne na jikin Yesu kuma ba ainahin jiki ba ne, zai yi kyau a fasara wannan magana a zahiri.
A nan "koko" ƙarin magana ne na ruwan inabi. AT: "Ya ɗauki kokon ruwan inabi"
Alkawarin na gafarta zunubai ne. Ana iya sa wannan a bayyane. AT: "Wannan jinina ne da ya tabbatar da alkawarin, jinin da an zub da domin yawancin su iya samin gafarar zunubai"
"Wannan ruwan inabin jinina ne." Ko da shike yawanci sun fahimci wannan da cewa ruwan inabin alama ne na jinin Yesu kuma ba ainahin jini ba ne, zai yi kyau a fasara wannan magana a zahiri.
"ruwan inabi." Wannan kwatanci ne na ce ruwan inabi.
AT: ) "kuma" ko 2) "a wata sabuwar hanya"
Wakar yabo wata irin waka ce. Al'ada ne masu su yi wakar zabura ta Tsohon Alkawari.
"Yesu ya ce wa almajiransa"
Wannan ƙarin magana ne da na nufin bari. AT: "bar ni"
"Ƙashe." "Zan" na nufin Allah.
AT: "Zan watsar da tumakin"
Wannan ƙarin magana na nufin cewa Allah zai sa Yesu ya tashi kuma bayan ya mutu. AT: "Allah ya ta da ni daga mattatu" ko "Allah ya sa ni rayuwa kuma"
"Zan tafi kafinku"
Ana iya bayyana "Ba zan" kamar "Ba zan faɗi ba." Jumlar "zai faɗi ba"na ɗauke da ma'ana mai yaƙini. AT: "ko da dukkansu sun bar ku, Zan zauna da ku"
Zakara tsutsu ne da na kirari
sau biyu
"za ka ce ba ka san ni ba"
"ko da ɗole ne in mutu"
Wannan na nufin cewa dukka almajiran su faɗa abin da Bitrus ya ce.
Kalmar "sun" na nufin Yesu da almajiransa.
cike da baƙin ciki
Kalmar "kwarai" na nufin Yesu ya damu sosai a rainsa. AT: "damuwa mai tsanani"
Yesu ya yi maganar kansa kamar "rain sa." AT: "Zan"
Yesu ya na zuguiguitawa domin ya na jin wuya da baƙin ciki har ya na ji kamar zai mutu, ko da shike ya san cewa ba zai mutu ba sai rana ya tashi.
Almajiran za su zauna a fadake sa'adda Yesu na addu'a. Wannan ba ya nufin cewa yakamata su kali Yesu sa'adda ya na addu'a.
Wannan na nufin cewa idan Allah zai bari ya faru. AT: "Idan Allah zai bari"
A nan "sa'an" na nufin loƙacin wahalar Yesu, yanzu da anjuma a lambun. AT: "ba sai ya yi wannan wahala ba"
kalma ne da 'ya'yan Yahudawa ke amfani da shi a yin magana da ubansu. Tun da ya na biye da "Uba," zai yi kyau a fasara wannan kalma.
Wannan muhimmin laƙabi ne wa Allah.
Yesu ya yi maganar wahala da zai sha kamar koko ne.
Yesu ya na rokon Allah ya yi abin da ya ke so a yi ba kuma abin da Yesu ya na so ba. AT: "Amma kada ka yi abin da nake so, yi abin da kake so"
Kalmar "su" na nufin Bitrus, Yakub da Yahaya.
Yesu ya ƙwabe Siman Bitrus domin barci. AT: "Siman, Kana barci bayan na gaya maka ka zauna a fadake. Ba ka iya zama a fadake ko na dan sa'a ɗaya ba."
Yesu ya yi maganar faɗi cikin jaraba kamar shigan cikin bayyananniyar wuri. AT: "kada a jarabta ku"
Yesu ya ƙwabe Siman Bitrus da cewa ba shi da ƙarfin yin abin da yake so ya yi a ƙarfinsa. AT: "Ka na da niyya a ruhunka, amma ka na raunana sosai a yin abin da ka ke so ka yi" ko "Ka na so ka yi abin da na ce, amma ka raunana"
Wannan na nufin kamani biyu na Bitrus. "Ruhun" shi ne bege na ciki. "Jikin" shi ne iyawa da ƙarfi na mutuntaka.
"maimaita addu'an da ya yi"
A nan marubucin ya yi maganar wuya da mutum mai jin barci ya ke ji a barin idannunsa a buɗe kamar "idannu masu nauyi." AT: "don sun ji barci sosai sun kasa barin idannunsu a buɗe"
Yesu ya je ya yi addu'a kuma. Sai ya kuma sau uku. AT: "Sai ya je ya yi addu'a kuma. Ya komo karo na uku"
Yesu ya ƙwabe almajiransa don rashin zama da fadake da kuma yin addu'a. AT: "Ku na nan ku na barci da hutawa!"
Loƙacin wahala da bada Yesu ya yi kusan faruwa.
"saurara!"
Yesu ya ƙwabe almajiransa cewa mai bashe shi ya yi kusa da su. AT: "Ni, Ɗan Mutum, an bashe ni"
Aya arba'in da hudu ya ba da tushen bayani game da yadda Yahuza ya shirya da shugabanin Yahudawa don ya bashe Yesu.
Wannan na nufin Yahuza.
A nan "ne" na nufin mutumin da Yahuza zai nuna. AT: "shi ne wanda ku ke so"
"Yahuza ya sumbace shi"
Waɗannan jumloli biyun na da ma'ana iri ɗaya don nanata cewa sun kama Yesu. AT: "rarume da kuma kama Yesu" ko "kama shi"
"wanda na tsaye a kusa"
Yesu ya na tsauta wa taron. AT: "abin ba'a ne cewa kun zo nan don ku kama ni da takkuba da kulake kamar na zama mai fashi!"
"Amma wannan ya faru domin"
Wannan ya na nufin almajiran.
kayan da an yi daga abin da ake tufkewa.
AT: "da ya yafa akansa"
"Da mutanen suka kama wannan mutumin"
Sa'adda mutumin ya na kokarin guduwa, sauran na iya kama kayansa, da kokarin hana shi.
Ana iya sakewa domin fahimta. "Dukka manyan firistoci, dattawa, da kuma marubuta sun taru a can"
An yi amfani da wannan kalma anan domin a sa alama a labarin sa'adda marubucin ya fara gaya mana game da Bitrus.
Sa'adda Bitrus ya bi Yesu, ya tsaya a fadar babban firist. AT: "kuma ya tafi da nisa har fadar babban firist"
Bitrus ya zauna tare da dogaran da suke aiki a fadan. AT: "ya zauna a cikin fadan tare da dogaran"
Basu ba ne za su kashe Yesu; maimakon haka, za su sa wani ya aikata. AT: "za su iya sa a kashe Yesu" ko "za su iya sa wani ya kashe Yesu"
Basu sami wani shaida akan Yesu da za su iya hukunta shi su kuma kashe shi ba. AT: "Amma basu samu wani shaida wanda za su iya hukunta shi ba"
A nan an kwatanta yin shaidar zur kamar abu ne da ana iya gani da wani na iya ɗauke. AT: "sun zarge shi ta wurin yin masa shaidar zur"
AT: "amma shaidarsu ya bambanta da juna"
"Mun ji Yesu ya ce." Kalmar "mun" na nufin mutanen da suna kawo shaidar zur akan Yesu, bai hada da mutanen da suke magana ba.
A nan "hannaye" na nufin mutane. AT: "da mutane sun yi ... ba tare da taimakon mutum ba" ko "da mutane sun gina ... ba tare da taimakon mutum ba"
"a cikin kwana uku." Wannan na nufin cewa za a gina haikalin a cikin kwana uku.
An fahimci kalmar "haikali" a jumla da ta wuce. AT: " zai gina wani haikali"
"bambanta da juna."
Yesu ya tashi a tsakiyar jama'a masu fushi don ya yi masu magana. Fasara wannan don ya nuna wanda ya na nan a loƙacin da Yesu ya tashi yin magana. AT: "mike a tsakanin manyan firistoci, marubuta, da dattawa"
Babban firist din bai tambayi Yesu akan bayanin game da abin da shaidun suka ce ba. Ya na tambayan Yesu don ya nuna cewa abin da shaidun sun ce ba daidai ba ne. AT: "Ba za ka amsa ba? Menene ka ce a amsa game da shaidan da waɗannan mutanen ke fada akan ka?"
A nan an kira Allah "Madaukaki." Zai fi kyau a fasara "Ɗan" da irin kalma da harshenku za su yi amfani a kiran "ɗan" uban mutum. AT: "Ɗan Maɗaukaki" ko "Ɗan Allah"
AT: 1) don amsa tambayar babban firist da kuma 2) don ya kira kansa "Nine," wanda shi ne yake abin da Allah ya kira kansa a cikin Tsohon Alkawari.
A nan "iko" ƙarin magana ne da na wakilcin Allah. Zama a "hannun damar Allah" alama ne na karban babban ɗaukaka da iko daga Allah. AT: "ya na zaune a wurin girma a gefen Allah mai iko dukka"
An ƙwatanta gajimaren a nan kamar su na rakiyar Yesu a dawowarsa. AT: "Indan ya soko a gajimaren a sararin sama"
Babban firist din ya kyakketa tufafinsa don ya nuna fushinsa da ƙyamarsa a abin da Yesu ya ce. AT: " kyakketa tufafinsa a cikin fushi"
AT: "Ba lallai ne muna son mutane kuma wanda za su shaida akan wannan mutum ba!"
Wannan na nufin abin da Yesu ya ce, wanda babban firist ya kira sabo. AT: "Kun dai ji sabon da ya ce"
Waɗannan jumlolin na nufin mutanen cikin taron.
Sun rufe masa idanunsa da ƙyalle ko abin ɗaure ido, don kada ya iya gani. AT: "don a rufe masa idanunsa da abin ɗaure ido"
Sun yi mashi ba'a, da ce masa ya yi annabcin wanda yake buga shi. AT: "Yi annabcin wanda ya buga ka"
mazajen da suke tsaron gidan gumna
"a waje a filin gida"
Baranyar yanmatan su na aiki wa babban firist. AT: "wata baranyar wanda su na yi wa babban firist aiki"
Wannan na nufin amince cewa wani abu ba gaskiya ba ne. Wannan lamarin, Bitrus na faɗa cewa abin da baranyar ta faɗa game da shi ba gaskiya ba ne"
Dukka "sani" da "gane" na da ma'ana iri ɗaya anan. An nanata ma'anar domin a nuna abin da Bitrus na ce. AT: "Ban gane abin da kike magana akai ba"
Wannan ne baranyar da ta nuna Bitrus a farko.
Mutanen suna nuna cewa Bitrus ɗaya ne daga cikin almajiran Yesu. AT: "ɗaya daga cikin almajiran Yesu" ko "ɗaya daga cikin waɗanda suke tare da wannan mutumin da an kama"
Idan ɗole ne ya kamata ku ba da sunan mutumin da ya la'anta wani a harshenku, ku ce Allah. AT: "ce don Allah ya la'anta shi"
Zakara tsuntsu ne da ke kira da samako. Karar da yake yi ne "cara."
"Biyu" lamba ne.
Wannan ƙarin magana na nufin cewa ya cika da damuwa ya kuma rasa ikon shaukinsa. AT: "ya cika da bakin ciki" ko "ya rasa ikon shaukinsa"
1Da sassafe, sai manyan firistoci suka hadu da dattawa da manyan malamai, da majalisa suka daure Yesu, suka sa shi gaba suka mika shi ga Bilatus. 2Bilatus ya tambaye shi, kaine sarkin Yahudawa? ya amsa ya ce "haka ka ce" 3Sai manyan firistochi suka kawo zargi iri iri a kan Yesu.4Bilatus ya sake tambayarsa, ba ka da abin cewa? ka lura da yawan zargi da ake yi maka. 5Amma Yesu baya sake yi masa magana ba. wannan ya ba shi mamaki.6A lokacin idi, Bilatus ya kan sakar masu da dan bursuna wanda jama'a suka bukaci a saka, 7A cikin gidan yari, in da aka tsare wadansu yan tawaye, da masu kisan kai, akwai wani mai kisan kai, ana ce da shi Barrabbas. 8Sai Jama'a suka zo wurin Bilatus ya yi masu kamar yadda ya saba yi.9Bilatus ya amsa masu ya ce, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa? 10Yayi wannan domin ya sani cewa Firistoci sun bada shi ne domin suna kishin sa, 11Sai Firistochi suka zuga jama'a, sai suka yi kuwwa suna cewa, a sakar masu Barrabbas amaimakon Yesu.12Bilatus ya sake yi masu tambaya "Yaya zan yi da Sarkin Yahudawa?" 13sai suka amsa da kuwwa" a "giciye shi!"14Bilatus ya ce masu menene laifinsa sai suka kara ihu, "a giciye shi." 15Bilatus don yana son ya farantawa jama'a zuciya sai ya sakar masu da Barrabbas sai ya yi wa Yesu bulala, sannan ya mika shi a giciye shi.16Sojoji suka kai shi cikin kagara, suka tara rundunan soja, 17Suka sa masa tufafin shulaiya suka nada masa rawanin kaya, 18Suna masa kirari na ba'a suna cewa, "A gaida sarkin Yahudawa!"19Sai suka buge shi a kai da kulki suka kuma tofa masa yau a fuska, suka kuma durkusa suna yi masa sujadar ba'a. 20Bayan sun gama yi masa ba'a sai suka cire masa tufafin shunnaiya, sai suka maida masa tasa tufafinsa, sai suka fitar dashi don su giciye shi. 21Suna cikin tafiya sai suka hadu da wani, mai suna Saminu Bakairawani (wato uban Alizanda da Rufus); suka tillasta shi ya dauki gijiyen Yesu.22Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira Golgota (wato kokon kai) 23Suka bashi ruwan inabi hade da mur, amma ya ki ya sha. 24Sai suka giciye shi, suka kuma raba tufafinsa suka kuma jefa kuri'a domin kowanne soja ya sami rabonsa.25A sa'a ta uku aka giciye shi. 26Sai aka rubuta alamar zargi da take cewa "Ga Sarkin Yahudawa" 27Suka kuma giciye shi tare da wadansu yan fashi guda biyu. 28Daya a hannun damansa daya a hannun hagunsa. Domin a cika abinda nassi ya fada.29suke wucewa suna zaginsa suna kada kai suna cewa, "Aha! kai da zaka rushe haikali ka kuma gina shi cikin kwana uku, 30ka ceci kanka mana, ka sauka daga giciye!"31Haka ma manyan firistoci da malamai, suka yi masa ba'a suna cewa "Ya ceci wadansu amma bai iya ceci kansa ba" 32Bari Almasihu Sarkin Yahudawa ya sauka daga giciye. Domin mu gaskata shi, sai wadanda aka giciye shi tare dasu, suma suka yi masa ba'a.33sa'a ta shida zuwa sa'a ta tara, duhu ya rufe ko'ina, 34A sa'a ta tara, Yesu ya tada murya da karfi ya ce Eloi, Eloi lamathsabathani?" Ma'ana Ya Allahna Ya Allahna, me ya sa ka yashe ni?" 35Wasu daga cikin na tsaye, da suka ji shi, sai suka ce, "Duba, yana kiran Iliya."36Sai wani ya hanzarta, ya dauki soso ya tsoma a ruwan inabi mai tsami, ya soka agora ya mika masa don yasha. Mutumin yace bari mu gani ko Iliya zai zo ya saukar da shi. 37Sai Yesu yayi kuka da babban murya da karfi sannan ya rasu. 38Sai labulen haikalin ya rabu kashi biyu daga sama har kasa.39Sa'adda da jarumin sojan da ke tsaye yana fuskantar Yesu ya ga yadda ya mutum, Sai ya ce "hakika, wannan mutum Dan Allah ne." 40Akwai kuma mata wadanda ke dubawa daga nesa. Daga cikinsu akwai Maryamu Magadala, da Maryamu( Uwar Yakubu da Yusufu) da Salome.41Wadannan matan sune suka bishi sa'adda da yake Galilee suna yi masa hidima. Da wadansu mata da yawa suka zo Urushalima tare da shi.42Da maraice an shiga shirye shirye domin kashe gari asabbaci ce. 43Sai Yusufu daga garin Arimatiya ya zo, mutumin kirki, mai girma kuma dan majalisar dattawa, mai sauraron mulkin Allah, da gaba gadi ya tafi wurin Bilatus ya bukaci a bashi jikin Yesu. 44Bilatus ya yi mamakin mutuwar Yesu cikin lokaci kadan, sai ya kira jarumin ya tabbattar koYesu ya mutu.45Bayan ya tabbattar daga wurin jarumin soja cewa Yesu ya mutu, sai ya bada jikin ga Yusufu. 46Yusufu ya sayo likafani. ya saukar da shi daga giciye, ya kawo likafanin nan ya lulube jikin Yesu dashi. Ya kai shi kabarin da aka sassaka da dutse, wadda ya shirya shi domin kansa. Ya kawo dutse ya rufe bakin kabarin da shi. 47Maryamu Magadaliya da Maryamu Uwar Yusufu sun ga wurin da aka yi jana'izar Yesu.
Da manyan firistoci, da shugabanni, da malaman Attaura, da dukkan 'yan majalisa suka Yesu wurin Bilatus, sai suka zarge shi da aikata munanan abubuwa. Da Bilatus ya tambaya ko karan da suka kawo gaskiya ne, Yesu bai amsa shi ba.
Sun umurta a ɗaure yesu, amma yana iya zama cewa masu tsaro ne suka ɗaure shi suka sa shi gaba. AT: "suka umarta a ɗaure Yesu, sa'annan aka yi gaba da shi" ko kuma "suka umarce masu tsaron su ɗaura Yesu, sa'annan suke sa shi gaba"
Suka sa aka kai Yesu ga Bilatus, sa'annan suka bar shi yă bi da Yesu.
Wannan na iya nufin 1) ta wurin faɗin haka, Yesu yana cewa Bilatus ne ke ce da shi Sarkin Yahudawa ba Yesu ba. AT: "Ai kai da kanka ne ke ce haka" ko kuma 2) ta wurin faɗin haka, Yesu na nufin cewa shi ne Sarkin Yahudawa. AT: "I, yadda ka faɗa, Ni ne" ko kuma "I, haka ne yadda ka faɗa"
"suna zargen Yesu da laifuffuka iri iri" ko kuma "suna cewa Yesu ya aikata munanan abubuwa masu yawa"
"Bilatus ya sake tambayar Yesu kuma"
AT: "Kana da abin faɗi"
"Duba" ko kuma "ka Saurara" ko kuma "Ka mai da hankali ga abinda za faɗa maka"
Bilatus ya yi mamaki cewa Yesu bai tanka shi ko ma ya kare kansa ba.
A nan amfani ne da wannan kalmar don a nuna kaucewa daga ainihin labarin yayin da marubucin yana ba da tarihin al'adan Bilatus na saka wani ɗan kurkuku a bukukkuwa da kuma game da Barrabas.
"A wancan lokacin akwai wani mutum mai suna Barrabbas, yana kurkuku tare da wasu mutane. Sun yi kisankai yayin da suka yi tawaye da gwamnatin Roma"
Wato sakie ɗan kukuku a bukukkuwa. AT: "ya sake masu wani ɗan kurkuku kamar yadda ya saba yi"
Wannan na ba da tarihin dalilin da yasa aka ɗanka Yesu wa Bilatus.
Suna kishin Yesu, mai yiwuwa domin da yawa a cikinsu suna binsa suna kuma zama almajiransa. AT: "manyan firistocin suna kishin Yesu. Shi yasa suna" ko kuma "manyan firistocin suna kishin farin jini da Yesu ke da shi ne a cikin mutane. Shi ya sa suna"
AT: "ta da hankulan jama'a" ko kuma "suka rinjaye jama'a"
Sun roƙa a sake masu barrabbas a maimakon Yesu. AT: "a sakar a maimakon Yesu"
Bilatus yana tambayan abinda zai yi idan ya sake masu Barrabbas. Ana iya kara haske a wannan, AT: "Idan na sake maku Barrabbas, me zan yi da Sarkin Yahudawa"
"Bilatus ya ce wa taron"
"ya sa taron su jo daɗi ta wurin yin abinda shi yake son su yi"
Sojojin Bilatus ne sun bulale Yesu, ba Bilatus dai da kansa ba.
"duka." A "bulale" mutum na nufin a yi wa mutum duka mai za i da sumagiya.
Bilatus ya umarci sojoji su tafi da Yesu don su giciye shi. AT: "ya ce wa sojojin su tafi da Yesu su giciye shi"
A nan ne sojojin Roma da ke Urushalima su ke zama, kuma gwamna ma yakan zama anan ne idan yana Urushalima. AT: "fadar rundunan sojoji da ke bariki" ko kuma "kagarar gidan gwamna"
"iyakar sojojin da ke wurin gabaɗaya"
shulaiya kala ce da 'yan sarauta ke sakawa. Sojojin ba su yarda cewa Yesu sarki ba ne. Sun saka masa waɗannan tufafun ne domin su yi masa ba'a domin akwai masu cewa shi ne sarkin Yahudawa.
"rawani da aka yi da rasan ƙaya"
Akan yin irin wannan gaisuwar da hannu a sama ne musamman domin a kaishe Sarkin Roma. Sojojin basu gaskata cewa Yesu sarkin Yahudawa bane. A maimakon haka, suna faɗin haka ne domin su yi masa ba'a'.
"sanda" ko kuma "itace"
Mutumin da ya durkusa ya lankwasa guiwar sa, ana iya cewa duk wanda ya durkusa ya lankwasa guiwarsa kenan." AT: "durkusawa" ko " durkusa"
Dokan Roma ya ba wa sojoin Roma izini su tilasta duk mutumin da suka samu a hanya ya ɗauki masu kaya. A wannan hali, sun tilasta Saminu yă ɗauki giciyen Yesu.
"daga bayan garin"
Wannan na ba da tarihin mutumin da sojojin sun tilasta shi ya ɗauki giciyen
Waɗannan sunayen mutane ne maza.
Wannan sunan wani wuri ne.
"wurin koƙon kai" ko kuma "wurin koƙon." Wannan shi ne sunan wurin. Ba wai yana nufin cewa akwai su koƙon kai da yawa a wurin ba.
koƙon kai shi ne ƙwaƙwalwan kai, ko kuma kan da babu soka ko nama a jikinta.
Zai zama da taimako idan an yi bayani cewa mur wata mai ce mai rage zafi. AT: "ruwa inabi a haɗe za wata magani mai suna mur" ko kuma "ruwan inabi a haɗe da magani mai rage zafi da ake kira mur"
"uku" anan yana daidai jerin kirge. Wannan na nufin ƙarfe tara na safe. AT: "a ƙarfe tara na safe"
Sojojin sun manna wata alama a jikin jiciyen a bisa Yesu. AT: "Sun manna a giciyen a sama da kan Yesu wata alama da ke"
"laifin da suke zargin sa"
Ana iya kara haske a wannan. AT: "ɗaya a bisa giciye a hannun damansa sannan ɗaya kuma a bisa giciye a hannun hagu"
Wannan alama ce da ke nuna cewa mutane ke yi don su nuna cewa basu amice da Yesu ba.
Wannan alama ce na ba'a. Ku yi amfani da daidai yadda ake yin ba'a a harshen ku.
Mutanen suna tunashe Yesu da abinda ya anabta zai yi ne dama. AT: "kai da ka ce za ka rushe haikali ka ka sake gina shi a kwana uku"
Wato yadda mutanen da ke tare da Yesu ma suna masa ba'a.
"suna faɗin maganganun ba'a a kan Yesu a junansu"
Shugabannin basu gaskata cewa Yesu shi ne Almasihu, Sarkin Isra'ila. AT: "Yana ce da kansa Almasihu da kuma Sarkin Isra'ila. To ya sauka" ko kuma "Idan shi ne Almasihu na gaskiya da Sarkin Isra'ila kuma, sai yă sauka"
Wato a gaskata da Yesu. AT: "gaskata shi"
suka zazzage shi.
Wato tsakar rana kenan ko kuma 12 p.m.
A nan Marubucin yana bayanin yadda wuri yake yin duhu ne kamar wani kaɗi ne da ke masowa a bisa ƙasar. AT: "ƙasar gabaɗaya ya zama baki"
Wato ƙarfe uku na rana kenan. AT: "A ƙarfe uku na rana kenan. ko kuma "a sakar yini kenan"
Waɗannan kalamun Yahudnci ne da ake iya ɗauko so zuwa harshenke yadda muryar su suka fito anan.
"ma'ana"
Ana iya fada a fili cewa basu fahimci abinda Yesu ke cewa ba. AT: "Wasu da ke tsaye a wurin sun ji kalamunsa, amma basu fahimci abinda yake cewa ba"
"ruwan inabi mai tsami da gaske"
"sanda."
"ya ba wa Yesu." Mutumin nan ya daga sandar sama ne domin Yesu ya samu yă iya shan ruwan inabin daga soson. AT: "ya riƙe shi sama wa Yesu"
Markus yana nuna cewa Allah ne da kansa ya raɓa labulen haikalin. AT: "Allah ya raɓa labulen haikalin kashi biyu"
Wannan shi ne jarumin da ya kula da sojojin da suka giciye Yesu.
Anan "fuskanta" wata karin magana ne da ke nufin a kalli mutum. AT: "ya tsaya a gaban Yesu"
"yadda Yesu ya mutu"
Wannan wata lakaɓi ne mai muhimmanci na Yesu.
"suna kallo daga nesa"
A nan iya rubuta wannan a baka ba.
kanin Yakubu Ana ce da wannan "kani" mai yiwuwa domin a banbanta shi da wani mutum mai kuma mai suna Yakubu ne.
Wannan Yosis ba shi ne kanin Yesu ba. Duba yadda kun juya wannan a [Markus 6:3]
Salome sunan mace ce.
" Waɗannna matan sun bi Yesu, sa'ad da Yesu yake galili ... da shi zuwa Urushalima." Wannan shi ne ɗan tarihi game da matan da suke kallon yadda a ka giciye shi daga nesa.
Urushalima na sama da kowani gari a Isra'ila, shi yasa mutane sun saba cewa suna haurowa zuwa Urushalima da kuma saukowa.
A nan ana maganar yamma kama wani abu ne da ke iya sa wa a wani wuri. AT: "yamma ya yi" ko kuma "yamma ne ko"
Jimlar nan "ya zo" na nufin Zuwan Yusufu zuw wurin Bilatus, wadda aka yi bayaninsa bayan tarihin da aka bayar, amma ana maganar zuwansa ne domin a nanata, ya kuma taimaka a gabatar da labarin. Ana iya samun wata hanya daban na yin haka a harshenku. AT: "Yusugu ɗan garin Arimatiya, mutum ne mai girma"
Yusufu shi ne sunan mutumin, Arimatiya shi ne sunan inda ya fito.
Wannan shi ne tarihin Ysusfu.
"ya tafi inda Bilatus yake"
Kuna iya karin bayani cewa yana bukatan jikin Yesu ne domin ya bizne shi. AT: "ya bukaci izinin ɗaukan jikin Yesu ne domin ya bizne shi"
Bilatus ya ji mutane suna cewa Yesu ya mutu. Wannan ya ba shi mamaki, don haka, ya tambayi jarumin ko hakan gaskiya ne. AT: "Bilatu ya yi mamaki da ya ji cewa Yesu ya riga ya mutu, don haka, ya kira jarumin"
"sai ya ba wa Yusufu Izini ya tafi da jikin Yesu.
likafini wani yadi ne da aka yi shi daga zaren wani itace. Duba yaka kuka juya wannan a [Markus 14:51]
Kuna iya bayani cewa Yesufu ya nema wasu mutane su taya shi daukan jikin Yesu da ya saukar da shi daga giciye, ya shirya shi domin ya sa shi a kabari, ya kuma rufe kabarin. AT: "Sai shi da wasu mutane sun saukar da shi ... Sun kawo dutsen sun rufe"
AT: "kabarin da wani ya sassaka da sutse
"babban dutse da aka fafe aka sa a gaban"
AT: "inda Yusufu da sauran suka binne jikin Yesu"
1Bayan ranar assabaci, Maryamu Magadaliya da Maryamu uwar Yakubu da Salomi, suka sayo man shafawa mai kamshi domin shafe jikin Yesu saboda jana'iza. 2Da safiyar ranar farko ta mako sai suka tafi kabarin a dai dai fitowar rana.3Suna magana a tsakaninsu suna cewa, wanene zai gangarar da dutsen da aka rufe bakin kabarin da shi?" 4Da suka daga ido, sai suka ga an riga an gangarar da dutsen, domin yana da girma.5Da suka shiga cikin kabarin sai ga wani saurayi saye da farar tufa, yana zaune a hannun dama, suna mamaki. 6Sai ya ce masu, "Kada ku ji tsoro. Kuna neman Yesu banazare, wanda aka giciye. Ya tashi! Baya nan. Ku duba wurin da aka kwantar dashi. 7Sai ku je, ku gaya wa almajiransa da Bitrus cewa ya rigaya ya yi gabanku zuwa Galili. A can zaku ganshi, kamar yadda ya fada maku."8Suka fita daga cikin kabarin da gudu suna rawar jiki da mamaki, ba su cewa kowa komai ba domin suna jin tsoro.9Da safiyar ranar farko ta mako ya fara bayyana kansa ga Maryamu Magadaliya wadda ya kori aljannu guda bakwai daga cikinta. 10Sai ta tafi ta shaida wadanda suke tare da shi suke makoki da kuka. 11Sai suka ji cewa ya tashi kuma ta ganshi, amma basu gaskata ba.12Bayan wadannan al'amura ya bayana kansa ta wata siffa ga mutum biyu sa'ilin da suke tafiya akan hanya. 13Sai suka tafi suka gaya wa sauran almajiransa, duk da haka basu gaskata ba.14Bayan wani lokaci, Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa su goma sha daya, ya tsauta masu saboda rashin gaskatawa da taurin zuciya, bayansun ji daga wadanda suka ganshi bayan ya tashi daga matattu. 15Sai ya umarcesu cewa "Ku tafi cikin duniya ku yi bishara ga dukan halitta. 16Wanda ya ba da gaskiya aka kuma yi masa baftisma, zaya sami ceto, wanda baya bada gaskiya ba za ya hallaka.17Wadannan alamu za su kasance da wadanda suka gaskata; a cikin sunana, za su fidda aljannu, za su yi magana da sabbin harsuna. 18Za su dauki macizai da hannayesu, idan sun sha guba ba ta cutar dasu ba, za su dibiya hannayensu ga marasa lafiya, za su sami warkaswa."19Bayan Ubangiji ya gama magana da su, sai aka dauke shi zuwa sama in da zai zauna a hannun dama na Allah. 20Almajiransa kuma suka tafi ko'ina suna sheilar bishara. Ubangiji kuma yayi aiki tare da su, yana tabbatar da kalma ta wurin ayukan al'ajiba tare da su.
A rana ta farko na mako, sa matan suka yi sammako domin su shafe jikin Yesu da man kamshi. Sun yi mamaki ƙwarai da sukn ga wani saurayi yana faɗi masu cewa Yesu yana da rai, amma sun ji tsoro kuma basu gaya wa kowa hakan ba.
Wato, bayan Asabar, rana ta bakwai na mako, ta kare sa'annan rana ta farko ta fara.
AT: "wani ya riga ya gangarar da dutsen"
Mala'ikan yana magana ne da tabbaci cewa yesu ya tashi daga matattu. AT: "Allah ya ta da shi daga matattu!" ko kuma "Ya ta da kansa daga matattu!"
"ranar Lahadi"
"Sai suka ji Maryamu Magadaliya tana cewa"
"su biyun" sun gan Yesu, amma ya yi daban da yadda yake dama.
mutum biyu "waɗanda ke tare da shi" ([Markus 16:10])
Sauran almajiran basu gaskata da abinda mutum biyun da ke ke tafiya cikin ƙasar ke cewa ba.
Waɗannan su ne manzanni goma sha ɗaya da suka rage bayan da Yahuza ya bar su.
Wannan misali ne na cin abinci, wanna haye ne na kullum wanɗa mutane suke cin abinci. AT: "suna cin abinci"
A al'adan Yesu, mutane suka taru ne a waje ɗaya lokacin cin abinci.
Yesu yana sauta wa almajiransa ne domin basu gaskanta da shi ba. A juya wannan karin maganar yadda za a fahimci cewa almajiran basu gaskata da Yesu ba ne. AT: "ƙi gaskatawa"
A nan "duniya" karin magana ne da ke nufin mutanen da ke cikin duniya. AT: "Ku je duk wurin da akwai mutane"
Wannan ƙari ne a maganar kuma ya na nufin mutane a ko'ina. AT: "kowa da kowa gabakiɗaya"
Kalmar nan "wanda" na nufin ko ma wa. AT: "Allah za cece dukkan mutanen da sun ba da gaskiya sun kuma yarda a ku yi masu baftisma"
Kalmar nan "wanda" na nufin ko ma wa. AT: "Allah zai hallaka dukkan mutanen da basu ba da gaskiya ba"
Markus yana maganar mu'ajizai kamar su mutane ne da ke tafiya tare da masubi. AT: "Mutanen da ke kallon waɗannan sun gaskata za su ga waɗannan abubuwan suna faruwa, za su kuma sani cewa Ina tare da masubi"
Wannan na iya nufi 1) Yesu yana ba da jerin abubuwa: "A cikin suna na za su yi abubuwa kamar haka: Za su" 2) Yesu yana ba da daidai jerin abubuwa: "Ga abubuwan da za su yi a cikin sunana: Za su."
A nan "suna" yana haɗe ne da Iko ko kuma karfin ikon Yesu. Duba yadda kuka juya "a cikin sunar ka" a [Markus 9:38]. AT: "Ta wurin ikon sunana" ko kuma "Ta wurin karfin ikon sunana"
AT: "Allah ya ɗauke shi zuwa sama, ya kuma zaunar da shi"
A zauna a "hannun dama na Allah" alama ce na samun wata babban girma da iƙo daga gun Allah. AT: "zaune a wuri mai girma a gefen Allah"
Wanna karin magana na nufin yana nuna cewa jawabin su gaskiya. AT: "yaya nuna cewa jawabin nan da suke yi gaskiya"
1Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu, 2kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon. 3Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas. 4Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.5A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne. 6Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji. 7Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.8Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa. 9Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare. 10Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.11A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren. 12Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi. 13Amma mala'ikan ya ce masa, "Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.14Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa. 15Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.16Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu. 17Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa."18Zakariya ya ce wa mala'ikan, "Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa." 19Mala'ikan ya amsa ya ce masa, "Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi. 20Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin."21Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali. 22Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana. 23Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.24Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce, 25"Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a."26A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat, 27zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu. 28Ya zo wurin ta ya ce, "A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke. 29Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.30Mala'ikan ya ce mata, "Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah. 31Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'. 32Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda. 33Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka."34Maryamu ta ce wa mala'ikan, "Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?" 35Mala'ikan ya amsa ya ce mata, "Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.36Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya. 37Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah." 38Maryamu ta ce, "To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka." Sai mala'ikan ya bar ta.39Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya. 40Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu. 41Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.42Ta daga murya, ta ce, "Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki. 43Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni? 44Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna. 45Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.46Maryamu ta ce, "Zuciyata ta yabi Ubangiji, 47kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na."48Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka. 49Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.50Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi. 51Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.52Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu. 53Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.54Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai 55(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada."56Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta. 57Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji. 58Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita59Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa "Zakariya" kamar sunan ubansa, 60amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, "A'a, za a kira shi Yahaya." 61Suka ce mata, "Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna."62Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna. 63Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, "Sunansa Yahaya." Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.64Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah. 65Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya. 66Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, "To me wannan yaro zai zama ne?" Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.67Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa, 68"Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su."69Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa, 70kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. 71Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.72Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki, 73rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim. 74Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba, 75a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.76I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa, 77domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.78Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu, 79domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.80Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
Luka ya bayyana dalilin rubutunsa zuwa ga Tiyofilas
"game da abubuwan da suka faru a tsakaninmu" ko "game da taronne da suka faru a tsakaninmu"
Ba wanda yake da tabbataciyar sani game da wayeTiyafilas. Idan shi maibine, kalman nan "mu" a a nan ya hada da shi kenan, amma idan shi ba maibi bane to kalman "mu" baya shafe shi ba.
"mashaidi" mutun ne wanda ya ga faruwan wani abu, bawan kalmar mutun ne da ke bautar Allah ta wurin gaya wa mutane sakon Allah. Za ka iya sa shi a bayyane yanda suka zama bayi na kalmar. AT: "ganin abin da ya faru da kuma bautawa Allah ta wurin shela wa mutane sakon sa"
Kalmar nan "kalma" na nufin hadden sako da ya kunshi kalmomi da yawa. AT: "bayin sako" ko "bayin sakon Allah"
"bincike da kula." Luka yayi binciken ainihin abin da ya faru cikin kula. Mai yiwuwa ya yi magana da mutane dabam-dabam wadanda sun ga abin da ya faru domin ya tabbatar cewa abin da ya rubuta game da al'amarin daidai ne.
Luka ya fadi haka domin ya ba Tiyofilas girma da martaba. Wannan na iya nufin cewa Tiyofilas muhimmin mutum ne a gwamnati. A wannan sashi, ku yi amfani da yadda ana martaba mutane dake da baban matsayi a al'adarku. Wasu mutane sun fi' son su sa gaisuwan da farko su ce, "Zuwa ga...Tiyofilas."
"mai daraja" ko "mai girma"
Ma'anar wannan suna shine "abokin Allah." Yana iya zama kwatancin halin wannan mutumin ne, ko kuwa sunan sa ne na ainihi. Yawancin fasara na anfani da shi a matsayin suna ne.
Mala'ikar yayi anabcin game da aihuwar Yohanna.
Wannan jimla "A lokacin da" ana mora don nuna sabon abu da ya faru. AT: A lokacin da Sarki Hirudus ke mulki akan Yahudiya"
"akwai wani musamman" ko "akwai wani." Wannan hanya ce da ake gabatar da sabon abu a cikin labari. Dubi yadda ana bayyana shi a harshen ka .
A nan an gane da cewa wannan na nufin firistoci ne. AT: "yankin fristocin" ko " kungiyar fristocin"
"wanda suka zo daga zuriyar Abaija." Abaija daga kaƙanin wadannan kungiyan fristocin ne, sa'anan dukkan su daga zuriyar Haruna ne, wanda shine fristi na farko daga Isra'ila.
"Matarsa daga zuriyar Haruna ne." Wannan ya nuna ita da Zakariya daga jerin zuriyar fristoci ne. AT: "Matarsa ma daga zuriyar Haruna ne" ko "Zakariya da Alisabatu matarsa duk daga zuriyar Haruna ne"
"daga zuriyar Haruna"
"a gaban Allah" ko "a ra'ayin Allah"
"dukkan ummurnai da Ubangiji ya bukata"
Wannan kalma ya nuna cewa abin da ke biye anan ya sha bam-bam da abin da ake tsamani. Mutane sunyi tsamani cewa idan sun yi abin da ke daidai, Allah zai barsu su sami 'ya'ya. Ko da shike wadannan ma'aurata sun yi abin da ke daidai, amma basu samu ya'ya ba.
Wanan jimla an mora a masayin alamar canji a labarin daga baya bayanai zuwa ga yan takara.
Ya nuni da cewa Zakariya dă yana haikalin Allah kuma yana nuna cewa wadannan hidimar firist yana bangarin sujada ga Allah.
"da ya kai ga lokacin kungiyarsu" ko "da lokacin kungiyarsu ya kai suyi bauta"
Wannan jumla ta bamu bayanai akan aikin firist.
" hanyar al'ada" ko " hanyar su ta kullum"
Kuri,a anan na nuna alaman dutse da aka wurgo, ko da aka mirgino zuwa kasa domin ya taimake su daidaitawa akan abu. Firistocin sun yaɗɗa da cewa Allah ya jagorance dayawa domin ya nuna masu wane firist ne yake so su zaba.
yakamata firistocin su kona turare karbbaɓe masu kamshi ga Allah kowace assuba da yammanci a bagadi na musamman a cikin haikali.
"Lambar mutane dayawa" ko "Mutane da yawa"
A nan ana nufi filin na kewaye da haikalin. AT: "wajen ginin haikalin" ko " wajen filin haikalin"
"a lokacin da aka shirya." Ba tabbaci cewa wannan safiya ce ko yammaci lokaci domin bayaswa na tiraren wuta.
Wannan kalma tana nuna alamar farkon labarin.
"sa'an nan ya zo mashi" ko " yana tare da Zakariya." A nan ana faɗi cewa mala'ikan na tare da Zakariya, ba wahayi bane kawai.
Wa'inan jimloli biyu na nufin abu daya ne, yana nanata yadda tsoro ya shiga Zakariya.
"sa'adda Zakariya ya gan mala'ikan." Zakariya ya tsorota domin bayannuwar mala'ikan akwai bansoro. Bai aikata laifin komai ba, sa bo da haka bai ji tsoron mala'ikar da kuma hukunci da zai yi masa ba.
An bayyana tsoro anan kaman abin da ya faɗawa ko ya fi-karfin Zakariya.
"Daina gin tsoro na" ko " bai kamata kaji tsoro na ba"
wannan ya nuna cewa Allah zai ba wa Zakariya abin da ya roka. AT: "Allah ya amsa adu'ar ka, kuma zai baka abin da ka roka"
"haifa da maka" ko "haifa maka da"
"Wannan saboda. zai zama mai girma" Zakariya da kuma "sauran" ma'anar su daya ne kuma ana za su yi farin ciki domin Yohanna zai zama "mai girma a gaban Ubangiji." Karshen aya 15 ya gaya yanda Allah ya na so Yohanna ya rayu.
Waddannan kalamai "murna" da kuma "farin ciki" biyun suna ma'anan abu daya kuma ana anfani da shi domin jaddada yanda girmam murnan zai zama. AT: "za ka sami farin ciki sosai" ko "zaka sami farin ciki"
"domin haifuwarsa"
"zai zama mutumin kirki ga Ubangiji" ko "Allah zai maishe shi mutumin kirki"
Za'a iya fadi wannan a kuzarin yanayi. AT: "Ruhu Mai Tsarki zai iza shi" ko " Ruhu Mai Tsarki zai jagorance shi" Ka tabbata bai yi kama da abin da mugun ruhu zai iya yiwa mutum ba.
"tun da yake cikin cikin uwata sa" ko "tun kafin a haife sa"
Idan ya yi kaman ba lisaffa Zakariya a cikin bayanin ba, ana iya fasarar wannan kalman kaman " dayawa cikin ku zuriyar Isra'ila ne" ko " dayawa cikin ku mutanen Allah, na Isra'ila ne." Idan an yi wannan canji, tabatar cewa "Allah su" za a canja ta zuwa " naku (jam'i) Allah."
"su juya" ko "juyo"
Zai yi gaba ya sanar wa mutane cewa Ubangiji zai bayyana a'garesu.
A nan "Fuskar" kalma ce da take nuna hallarar Ubangiji. Wasu lokatai ba a gaya wannan fasarar. AT: "a gaban."
"da ruhu daya da iko da Iliya yake da shi." Kalmar nan "ruhu" wanan ya shafi ko Ruhu Mai Tsarki na Allah ko halayen Iliya kokwa hanyar tunanin sa. Tabatar da cewa kalmar "ruhu" bai ya nufin fatalwa ko mugun ruhu.
"a lallashe ubanni su kuma damu da ya'yansu" ko "'hanyar mayar da dangantakar ubanni da ya'yansu".
Ana magana akan Zuciyan kaman abu ne da za a iya juya shi a wani hanya daban. Wanan na nufin canjin halayen wani zuwa ga abu.
"'tafiya" na nuna hanyar da mutun zai aikata a zaman rayuwarsa. AT: " marasa biyayya zai aikata" ko "marasa biyayya zai zama"
" mutane da basu biyayya"
Ba ambata yadda zasu yi shirin ba. Ana iya karin wannan tabbataccen bayanen. AT: " yin shirin aminche da sakon Ubangiji" ko "yin shirin biyayya na Ubangiji"
"Ta yaya zan san tabbaci da cewa abin da ka fadi zai faru? "A nan,"sani" na ma'anan; kayi koyi da kwarewa, ana shawara ko Zakariya na tambaya na alamar shaida. AT: Abinda za ka iya yi don tabatar mani da cewa wannan zai faru.
An fadi wannan tsaustauci zuwa ga Zakariya. A gaban Jibra'ilu, zuwa kai tsaye daga Allah, ya zama ishashen shaida donmin Zakariya.
"wanda ke bautawa"
Za iya kokarin fadi wannan kamar haka. AT: "Allah ya aiko ni in gaya maka labari"
Kalmar nan "gashi" yana son mu kula da bayanai masu ban-mamaki da ke biye.
Wadannan abu biyu din na ma'anan abi daya ne, ana kuma maimaitasu domin a nanata cikawan zama beben sa. AT: "cikaken ba za ka iya magana ba" ko " ba za ka iya magana ba ko kadan"
"baka gaskanta da abin da na ce ba"
"a lokcin da aka shirya"
Wannan ya nuna alamar canji a labarin, daga abun da ya faru a ciki zuwa wajen haikalin. AT: "cikin lolacin" ko " a lokacin da mala'ikan da Zakariya suna magana".
Watakila wadannan ababai sun faru a lokaci daya ne, kuma alamun Zakariya sun taimake mutane su gane cewa, ya ga wahayi. Zai iya zama abin taimako ga jama'ar ka, domin canjin yaɗɗa za a nuna, AT: "Ya cigaba da yi masu alamu, baya magana. Sun kuwa gane da cewa ya ga wahayi yayen da yake cikin haikali"
A kwatance na farko ya nuna cewa Jibri'lu ya zo gun Zakariya cikin haikali.
Wnnan kalman ya kai labarin zuwa ga lokacin da Zakariya, ya gama bauta.
Zakariya bai zamna a Urshalima ba, inda haikalin yake. Ya komo garinsa.
Wannan kalman "kwanakin nan" ya komar da mu zuwa lokacin da Zakariya na bauta a haikali. Yana yuwa a baiyana wannan kalman a fili. AT: "Bayan da Zakariya ya komo gida daga haikalin da yake bauta"
"matar Zakariya"
"bata bar gidan ta ba" ko " ta zamna ita kadai, a ciki"
Wannan kalman, ya komo damu zuwa asalin labarin da Allah ya bar ta tayi ciki
Wannan bayyani mai kyau ne. Ta yi murna sosai da abin da Ubangiji yayi mata.
"dube ni" kalma ne da yake ma'anan "a bi da" ko "a magance." AT " "ya ɗauke ni mai kirki" ko " ya ji tausayi na"
Wannan ya nuna kunya da ta ji domin bata iya ta samu ya'ya ba.
Mala'ika Jibrilu ya sanar wa Maryamu da cewa za ta zama Uwar wanda shi ne Ɗan Allah.
"a cikin wata na shidda da juna biyu na Alisabbatu." Yana yuwa wajibi ne a fadi wannan a fili idon zai zama rude ga wata ta shidda na shekarar.
Anna iya bayyana wannan cikin aiki. AT: "Allah ya gaya wa mala'ika Jibrilu ya je"
"Shi yare daya ne da Dauda" ko "Shi daga zuriyar Sarki Dauda ne" (UDB)
"rantsuwa" ko "alkawarin yin aure." Iyayen Maryamu sun mika kai domin ta aure Yusufu.
Wannan ya gabatar da Maryamu kaman sabuwar hali ce a labarin.
"Mala'ikan ya zo wa Maryamu"
Wannan yaɗɗa aka saba gaisuwar ne. Yana Ma'anan "Farin ciki" ko "Yi murna."
"ke da kin samu alheri mai yawa!" ko "ke da kin samu kirki na musamman!"
"da ke" kalma ne da yake nuna goyon baya da karbuwa. AT: " Ubangiji yana farin ciki da ke"
Maryamu ta gano wadannan kalamai dabam dabam, amma bata gane dalilin da mala'ikan ya mata wannan gaisuwa na ban mammaki ba.
Mala'ikan ba ya son Maryamu ta ji tsoron bayyanuwar sa, domin Allah ya aiko shi da sako mai kyau.
Kalman "a sami tagomashi" na ma'anan ka zama karbaɓɓe ta wurin wani. Ana iya canza wannan magana domin a nuna Allah kamar mai aikin. AT: "'Allah ya yanke shawarar baki alherin sa" ko "Allah na nuna maki kirkin sa."
Maryamu ta haifi "Ɗa" wanda za a kira shi" Ɗan Allah Madaukaki" (UDB). Yesu mutum ne ɗa haifaffe ta wurim macen mutum, shi kuma Ɗan Allah ne. Waddanan ambataccen labari na niman fasara da hankali sosai.
Ma'anna mai yiyuwa sune 1) " mutane, zasu ce da shi" or 2) "Allah zai ce da shi"
Wannan lakabi mai muhimminci ne na Allah, Ɗa na Allah.
Kursiyin na wakiltan izini sarkin ga mulkin. AT: "ba shi izinin ya yi mulki kamar sarki, kamar yadda kakkanen shi Dauda ya yi"
Mumunar kalman nan "mara iyaka" na nanata cigabawar sa na har'abada. Za a iya faɗe ta da kalma mai kyau. AT: "mulkinsa bashi da iyaka"
Maryamu bata gane yaɗɗa zai iya faruwa ba, bata kuwa yi shakkan zai iya faruwa ba. AT: "Ta yaya haka zai yiwu?"
Maryamu ta yi amfani da kalma mai ladabi, ta nuna bata sami kanta a ayukan jama'i ba. AT: "Ni budurwa ce."
Wannan hanyoyi da Maryamu ta ɗauka, zai fara da zuwan Ruhu Mai-tsarki gare ta.
"zai wuce" ko "zai faru da"
Allah ne "iko" Maryamu ta yi juna biyu da hanyar allahntakan sa duk da cewa i'ta budurwa ce. tabbatar wannan baya nufin saduwar jiki ko juma'i-wannan, abin al'ajibi ne.
"zai rufe ki kamar inuwa"
"Ɗa mai tsarki" ko "jariri mai tsarki"
Ma'anna mai yiwuwa sune 1) "jama'a zasu ce da shi" ko 2) "Allah zai ce da shi"
Duk da cewa Maryamu uwar Yesu mutumce, Allah ya
Wannan lakabi mai muhimminci ne ga Yesu.
Wannan magana na nanata bayanai masu muhimminci akan Alisabatu.
Idan ka na bukatar bayyana dangataka na musamman, mai yiwuwa Alisabatu innan Maryamu ce ko babban inna ta ce.
"ta samu juna biyu da ɗa, duk da cewa ta rigiya ta tsufa sosai" ko "duk da cewa ta tsufa, ta samu juna biyu kuma ta haifi ɗa."tabbar cewa ba a sa Maryamu da Alisabatu sun samu juna biyu a tsufan su ba.
"a watta na shida da juna biyun ta"
"Domin" ko "Wannan na nuna"
Wannan musu mai baki biyu, za a iya bayyana shi a sifar tabbaci. AT: "Wannan na nuna cewa Allah na iya yin kowace abu." Juna biyu na Alisabatu' tabbaci ne da cewa Allah ya iya yin kowace abu-da kuma ba wa Maryamu damar yin juna biyu ba tare da saduwa da mutum ba.
Maryamu ta yi amfani da kalma daya da Mala'ikan don ta nanata muhimmincin abin da ta yi ta wurin yanke shawar mika kai ga Ubangiji.
Zabi kalmar da ya nuna tayi kaskanci da biyyaya ga Ubangiji. Bata yi fahariyar zama bawar Ubangiji ba.
"Bari ya faru da ni" Maryamu na maganar yardawar ta akan abubuwan da zasu faru, da cewa abubuwan da mala'ikan ya gaya mata na hanyar faruwa.
Maryamu ta ziyarce yar'uwar ta Alisabatu wannda zata haifi Yohanna.
Wannan kalman na ma'anan bata tashi kadai ba, amma "tayi shiri." AT: "ta fara" ko "ta yi shiri"
"yanki mai duwastu" ko "yankin duwatsu na Isra'ila"
Ana nufin cewa Maryamu ta gama tafiyar ta kamin ta shigo gidan Zakariya. Za a iya fadi wannan a tsarari. AT "sa'adda ta iso, ta shigo"
Ana amfani da wannan kalma, a nuna sabuwar abin da ta faru a wannan sashi na labarin.
"a cikin Alisabatu"
"motsa a farat ɗaya"
Wadannan kalmomi biyu na ma'anan abu daya ne, kuma za'a iya amfani da ita a nanata farin cikin Alisabatu. Za iya hadda wadannan abu biyun zuwa kalma daya. AT: "faɗa da ƙarfi."
Wannan kalman na ma'anan"ta kara daga muryan ta"
Kalman "cikin mata" na ma'annan "fiye da kowace mace"
An yi magana akan ɗan Maryamu kamar itacen da ke haifa ya'ya. AT: "jaririn cikin ki" ko "jaririn da zaki haifa."
Alisabatu bata nima bayani ba. Tana nuna mamaki da murna da tayi sa'adda uwar Ubangiji ta zo wurin ta. "Abin banmamaki ne uwar Ubangiji ta ziyarce ni!"
Ana nufi Maryamu. "ke, uwar Ubangijina." (UDB)
Wannan kalma na jawo hankalin mu zuwa ga magana na ban-mamaki da Alisabatu ta yi.
"motsa farat daya da farin ciki" ko "juya da karfi domin yana murna sosai"
"mai albarkace ke da kika gaskanta" ko "domin kin gaskanta, za kiyi farin ciki"
"wadannan ababain zasu faru" ko "wadannan ababain zasu cika"
Za a iya bayyana wannan a wani yanayi. AT: "sakon da Ubangiji ya bata" ko "abubuwan da Ubangiji ya gaya mata"
Maryamu ta fara wakar yabo ga Ubangiji maiceton ta.
Maryamu ta yi amfani da kalman a wani yanayi da ta fadi abu daya zuwa kashi biyu kuma a hanyoyi dabam dabam. A fasara wadannan kalma ko kalmomi da su na da ma'anna iri daya zuwa hanyonyi dabam dabam.
Da "zuciya" da kuma "ruhu" yana nufin ruhaniyan mutum. Maryamu tana fadi cewa sujadarta na zuwa daga ciki cikin zuciyar ta ne.
"ta yi farin ciki sosai akan" ko "tayi murna sosai akan"
"Allah, wanda ya cece ni" ko "Allahn da ya cece ni"
"Domin ya"
"Dubi da idon tausayi" ko "kula da"
"talauci." iyalin Maryamu basu da arziki.
Wannan kalman na jawo hankalin mu zuwa ga bayyanainda ke biye.
"yanzu da kuma nan gaba"
"mutanen dukkan zamani"
"Allah, mai iko" (UDB)
A nan "sunan"na nufin dukkan tsifar Allah. AT: "shi"
"Jinkan Allah"
"daga tsara zuwa tsara mai zuwa" ko "cikin dukkan zamani" ko "ga mutannen kowace locaki"
A nan "hannuwansa" kalma ne da yake nuna ikon Allah. AT: "na nuna cewa yana da iko sosai"
"an kore su zuwa hanyoyi dabam dabam"
Wannan kalman na nufin zurfin tunanin su. AT: "tunani a cikin rayuwarsu"
Kursiyi kujera ce da mai mulki na zama, kuma alama ne na ikon sa. Idon an saukar da magada daga kujerar sa, ya nuna bashi da iko yayi sarauta. AT: "Ya dauke iko daga hannun magada" ko "Ya mier da mai mulki ya daina mulki"
Bambanci sakanin wadannan abubuwa dabam dabam din a bayyana shi a fili a cikin fasarar idon zai yiwu.
"'talauci." Iyalin Maryamu basu da arziki.
A hoton kalman nan, muhimman mutane suna gaban da kalilan muhimmanci. AT: "muhimman mutane ya mayad da su kaskantatun mutane" ko "ya bayar da martaba wa mutane da wadansu basu martaba ba"
Bambanci sakanin ayuka dabam dabam dinnan na niman bayyani cikin fili idon zai yiwu.
Ma'anna mai yiwuwa 1) " a ba wa mayuwanta abubuwa masu kyau su ci" ko 2) "ba wa mai nema abubuwa masu kyau."
"Ubangiji ya yi taimako"
Idon mai karatu ya rikice da mutum mai suna Isra'ila, za a iya fasarar shi kamar "bawar sa, jiha na Isra'ila" ko "Isra'ila, bawar sa."
"domin a"
Allah baya mantuwa. Lokacin da Allah "ya tuna," kalma ne da yake ma'annan Allah ya aikata alkawalin sa na farko.
"kamar yadda yayi wa kakkanen mu alkawali zai cika." Wannan kalma ya ba da shahareren bayani akan alkawalin Allah zuwa Ibrahim. AT: "domin yayi alkawalin jinkai wa kakkanenmu" (Dubi:
"Zuriyar Ibrahim"
"Maryamu ta koma gidanta(Maryamu)" ko "Maryamu ta koma gidanta na ainihi"
"haifi jaririn ta"
"Makwabta da 'yan'uwan Alisabatu"
"yana yi mata kirki"
"Alokacin da jaririn na kwana ta takwas" ko "A rana ta takwas bayan haifuwar jaririn"
Wannan biki ne da ake yi kullum, in da mutum daya ke yiwa jariri kaciya da kuma aboƙansa su kan yi murna tare da iyalin. AT: "domin bikin kaciyar jaririn"
"Da zasu ba shi suna" ko "Sun so su ba shi sunar." Wannan ainahin al'adar su ne.
"sunan ubansa"
"da wancan suna" ko "da irin sunan"
Wannan na nufin mutane wadanda su na nan a buki na kaciyan.
"motsi." Kokwa Zakariya bai iya ji ba da kuma yin magana, kokwa mutanen suna zaton cewa shi kurma ne.
"ga uban jaririn"
"wane suna ne Zakariya ya so a ba wa jaririn"
"Mai yiwuwa zai zama da taimako a fadi yadda Zakariya " yi tambaya,"da yake bai iya magana ba. AT: "Ubansa ya yi amfani da hanuwarsa ya nuna wa mutane ya son su ba shi allon rubutu"
"abin rubutu"
"mamaki sosai" ko "ji mamaki"
Hotunan kalamai biyun nan ya nanata tare yadda Zakariya ya yi magana nan da nan.
Ana iya bayyana wannan kalman cikin sifar aiki. AT: "Allah ya bude bakinsa da kuma sake harshensa"
Dukan wadanda suke zama kewaye da Zakariya da Alisabatu sun ji tsoro." Zai iya zama da taimako a bayyana a filli dalilin firgitar su. AT: "Dukan wadanda suke zama kewaye da su suna tsoron Allah wanda ya yi wa Zakariya wannan"
Wannan baya nufin makwaptan su na kusa kawai ba amma zuwa ga dukan wadanda suke zama a yankin.
Kalman "su" a nan na nufin ababai da suka faru.
Sashen nan "wanna labarin ya bazu" misali mutane ne da ke magana game da su. AT: "Dukan wanna zancen mutane ne suka yi maganarsu a cikin dukan dukan kasar duwtsun Yahudiya" ko "Mutanea dukan kasar duwatsun Yahudiya sun yi maga a kan wanna zancen"
"Dukan waɗanda su ji wanna zancen"
Ana maganar tunani a kai a kai a kan abubuwa sa suka rigaya su ka faru kamar sa waɗanna abuwa ne da sauki a zuciyarsu. AT: "tunani a hankali game da wanna zancen" ko "tunani da yawa game da abubuwan da suka faru"
"zuciya. su ka tambaya"
"Wane irin mutum mai girma ne wannan jaririn zai zama?" Yana kuma yiwuwa wannan tambayan yakamata ya zama bayani na mamakin su akan abin da suka ji game da jaririn. AT: "Wane mutum mai girma ne wannan yaro zai zama!"
Kalman "hannun Ubangiji" yana nufin ikon Ubangiji. "Ikon Ubangiji na tare da shi" ko "Ubangiji yayi aiki cikinsa da iko"
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya"
Mahaifin Yohana
Dubi yadda aka saba gabatar da hanyoyi dake kai tsaye a kabilar ku. AT: "anabci, ya ce" ko "anabci, kuma ga abin da ya fadi"
"Isra'ila" anan na nufin jihar Isra'ila. Dagantaka tsakanin Allah da Irsra'ila ana iya bayyana shi akan hannya. AT "Allahn da yayi mulkin Isra'ila" ko "Allahn da Isra'ila suke masa sujada"
"Mutanen Allah"
kahon dabba alamar ikon sa ne ya tsare kansa. An yi magana akan Maiceto anan kaman shi ne kaho da yake da iko ya cece Isra'ila. AT: "Wanda yana da iko ya cece mu"
"gidan" Dauda anan na wakilin iyalinsa, takamaimain zuriyar sa. AT: "cikin iyalin bawansa Dauda" ko "wanda shi daga zuriyan bawansa Dauda"
"kamar yadda Allah ya fada"
Maganar Allah ta wurin annabawansa na kwatanta cewa Allah na sa annabawan su faɗi abin da yake so su fada. Za'a iya bayyana ikon Allah. "ya sa annabawan sa tsarkaka su ce"
Za a iya bayyana "cece" da "ceto" ko "ceta." AT: "da daɗewa). Za ya cece mu daga magabtan mu"
Wadannan kalamu biyu na nufin abu ɗaya da aka sake nanata wa don nuna yadda magabtan su suna gaba dasu sosai.
Kalman "hannu" na nuna ikon da miagun mutane ke amfani akan mutanen Allah. "iko" ko "iko."
"a nuna jinkai zuwa ga" ko "su yi ayuka bisa ga jinkansa zuwa ga"
A nan kalman nan "tuna" na nufin a miƙa kai ko cika wani abu.
Wadannan kalamai biyu suna nufin abu daya ne. Su na sake bayyana muhimmancin alkawalin Allah wa Ibrahim.
"ya zama mai yiwuwa garemu"
zai iya zama da taimako a canja yanayin wadannan kalaman. AT: "cewa zamu bauta masa ba tare da tsoro ba bayan ya cece mu daga ikon miyagu."
a nan "hannu" na nufin ikon mutum. Za 'a iya fadin wannan a fili. AT: "daga ikon miƙiyan mu"
Wannan na nufin tsoron maƙiyan su. AT: "ba tare da jin tsoron maƙiyan mu ba"
Za a iya ƙara fadin wannan. Ma'ana mai yuwuwa sune 1) za mu mu bauta wa Alla a tsarkar da adallun hanyoyi. AT: "yin abuwan tarki da adalci" ko 2) za mu zama masu tsarki da adalci. AT: "zama da tsarki da adalci"
Wannan kalma ne da ke nufin "a halararsa"
Zakariya ya yi amfani da wannan kalma domin ya soma wa yaronsa magana. Kana iya samun hanya mai kama da wannan magana 'a kabilar ka.
Mutane zasu gane cewa shi annabi ne. Ana iya fadi wannan cikin sifar aiki. AT: "mutane zasu sani cewa kai annabi ne"
"wanda ke bauta wa Madaukaki." Wannan na nufin Allah: "wanda ke wa Allah Madaukaki Magana."
Wannan na nufin cewa yahayya zai shirya mutane su ji, su kuma gaskanta saƙon Ubangiji.
"bada ilimi" na nufin koyarwa. za a iya yin bayanin "ceto" da "gafartawa" kamar "ceta" da "gafara." AT: "ya koya wa mutanen sa ceto ta wurin gafaran zunubansu" ko "ya koya wa mutanen sa yadda Allah yake ceton mutanen sa ta wurin gafaran zunubansu" (Dubi:
Zai zama da taimako a fadi cewa jinkan Allah na taimakon mutane. AT: "domin Allah mai tausayi da jinkai ga mu"
Haske a nan kalma ce da ake amfani da ita akai akai a yi magana akan abi daya kaman abu dabam dabam ne wa gaskiya. A nan, ruhaniya na gaskiya Mai-ceto zai tanada an yi magana akai kaman hasken rana dake haskaka duniya ne.
"ba da ilimi ga" ko "ba da haske ta ruhaniya ga"
Duhu anan kalma ce da ake amfani da ita a yi magana akan abi daya kaman abu dabam dabam ne na rashin ruhaniya na gaske. Anan, mutane da basu da ruhaniya na gaskiya ana magana akan su kaman suna zama cikin duhu ne. AT: "mutanen da basu san gaskiya ba"
Wadannan kalamai biyu suna aiki tare domin su nanata zurfin ayuka na duhun mutane kafin Allah ya nuna masu jinkai.
Inuwan na wakilcin abin da na hanyar faruwa akai akai. A nan, na nufin kusance mutuwa. AT: " waddanda suna hanyar mutuwa"
A nan "kiyayewa" na nufin loyarwa, da "hanyar salama" ya ɗauki matsayin dukan cikin mutum. AT: "koya mana yadda za mu yi zama tare da Allah"
"zama ƙosasshe cikin ruhaniya" ko "karfafa a zumuntarsa da Allah"
"zauna wa cikin jeji." Luka bai fadi ko a shekara nawa Yohana ya fara zama cikin jeji ba.
Wannan bai nuna alamar wurin tsayawa ba. Yohana ya chigaba yin rayuwa cikin jeji har bayan da ya fara wa'azi wa jama'a a fili.
"da ya fara wa'azi cikin jama'a a fili"
Anyi amfani da wannan anan a matsayin "lokaci" ko "lokaci da abu ya faru."
1Ananan cikin kwanakin, sai Kaisar Augustas ya yi shela ya umarta a kidaya dukan mutane da ke zaune a cikin duniya. 2Wannan itace kidaya ta farko da aka yi lokacin da Kiriniyus yake mulkin Suriya. 3Sabili da haka, kowa ya koma garinsa domin a yi masa rijista domin kidayan.4Yusufu kuma ya tashi ya bar birnin Nazarat zuwa garin Baitalami da ke Yahudiya, wanda ake kuma kira birnin Dauda, domin shi daga zuriyar iyalin Dauda ne. 5Ya je can ya yi rijista tare da Maryamu, wadda yake tashi tana kuma da juna biyu.6Ya zama sa'adda suke can, lokaci ya yi da za ta haifi danta. 7Ta haifi da, dan farinta kuwa, ta nade shi da kyau da 'yan tsummoki. Ta sa shi cikin wani kwami na dabbobi, gama babu daki dominsu a masaukin.8A cikin wannan yankin, akwai makiyaya wadanda suke zama a sarari suna tsaron garken tumakinsu da dare. 9Nan da nan, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare su, daukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, sai suka figita kwarai.10Sai mala'ikan ya ce masu, "Kada ku ji tsoro, domin na kawo maku labari mai dadi da zai kawo murna da yawa ga dukan mutane. 11Yau an haifi maku mai ceto a cikin birnin Dauda! Shine Almasihu Ubangiji! 12Wannan itace alama da za a ba ku. Za ku ga dan jariri nade cikin 'yan tsummoki kwance cikin kwamin dabbobi."13Nan take, sai ga babban taro daga sama tare da mala'ikan suna yabon Allah, suna cewa, 14"Daukaka ga Allah daga bisa, bari salama ta kasance a duniya tsakanin mutanen da ya ke jin dadinsu."15Ya zama sa'adda mala'iku suka bar su zuwa cikin sama, sai makiyayan su ka ce wa junansu, "Bari mu je Baitalami mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya nuna mana." 16Su ka yi hamzari suka tafi can sun iske Maryamu da Yusufu, suka ga jaririn kuwa kwance a cikin kwamin dabbobin.17Bayan da sun ga wannan, suka gaya wa mutane abinda aka gaya masu game da wannan yaro. 18Dukan wadanda su ka ji, su ka yi mamaki kwarai game da abin da makiyayan su ka gaya masu. 19Amma ita Maryamu ta ci gaba da tunani akan wadanan abubuwa da ta ji, tana tunani mai zurfi a cikin zuciyarta. 20Makiyayan suka koma suna ta daukaka da yabon Allah domin dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, dadai da yadda aka gaya masu.21Da ya kai kwana takwas, lokacin da za a yi wa jaririn kaciya, sai aka rada masa suna Yesu, sunan da mala'ikan ya bashi kamin a yi cikinsa.22Da kwanakin tsarkakewar su ya wuce bisa ga shari'ar Musa, Yusufu da Maryamu suka kawo shi cikin haikali a Urushalima dominsu mika shi ga Ubangiji. 23Kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, "Za a kira duk da na fari kebabbe ga Ubangiji." 24Suka kuma zo su mika hadaya bisa ga yadda aka fada a shari'ar Ubangiji, "Kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu."25Ga shi akwai wani mutum a Ushalima mai suna Siman. Wannan mutum adali ne kuma mai ibada. Yana jiran mai ta'aziyar Isra'ila, kuma Ruhu Mai-sarki na bisansa. 26An kuma bayyana masa ta wurin Ruhu Mai-tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kristi na Ubangiji.27Wata rana Siman ya zo cikin haikali ta wurin jagorar Ruhu Mai-tsarki. Da iyayen suka kawo yaron ciki, wato Yesu, domin su cika sharudan da shari'ar ke bukata, 28sai Siman ya karbe shi cikin hanuwansa, ya yabi Allah ya ce, 29"Yanzu bari bawanka ya tafi da salama, Ubangiji, bisa ga kalmarka.30Domin idanuna sun ga cetonka, 31wanda ka shirya a gaban dukan mutane: 32Haske ne na wahayi ga al'ummai, kuma daukakar mutanenka Isra'ila."33Mahaifin yaron da Mahaifiyarsa, sun yi mamaki kwarai domin abubuwan da aka fada akansa. 34Sai Siman ya albarkace su ya ce wa uwatasa Maryamu, "Ki ji da kyau, wannan yaro zai zama sanadiyar faduwa da tashin mutane dayawa a Isra'ila, kuma alama wadda ake kushen ta. 35Kuma takobi zai tsaga zuciyar ki yadda tunanin mutane za ya bayyana."36Wata annabiya mai suna Annatu ta na nan wurin. Ita diyar Fanuyila ce daga kabilar Ashiru. Ta riga ta manyanta a shekaru sosai. Ta kasance da maigidanta shekaru bakwai bayan auren ta, 37sannan ta yi zama gwambranci na shekaru tamanin da hudu. Ba ta taba barin haikali ba, tana ci gaba da yi wa Ubangiji sujada, dare da rana. 38A dadai lokacin nan, ta hau zuwa wurinsu ta fara yi wa Allah godiya. Ta gaya wa dukan wadanda ke jiran fansar Urushalima.39Da su ka gama komai da aka bukace su suyi bisa ga tafarkin shari'ar Ubangiji, sai suka koma Galili, zuwa birninsu, Nazarat. 40Yaron kuma ya yi girma ya zama da karfi, yana karuwa da hikima, alherin Ubangiji kuma yana kansa.41Iyayensa sukan tafi Urushalima kowacce shekara domin idin ketarewa. 42Da yana shekara goma sha biyu, suka sake haurawa daidai lokacin idin a al'adance. 43Bayan da sun cika dukan kwanakin idin, sun fara dawowa gida. Amma dan yaron Yesu ya jinkirta ya zauna a Urushalima, kuma iyayensa basu sani ba. 44Suna tsammani yana tare da sauran mutane da suke tafiya tare, sai suka yi tafiya na kwana daya. Suka fara neman sa a cikin danginsu da abokansu.45Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima suna cigiyar sa a can. 46Ya zama bayan kwanaki uku, su ka same shi a cikin haikali, yana zama a tsakiyar malamai, yana sauraron su yana kuma yi masu tambayoyi. 47Dukan wadanda suka ji shi suna ta mamakin fahimtar sa da amsoshin sa.48Da suka gan shi, suka yi mamaki kwarai. Mahaifiyarsa ta ce masa, "Da na, don me ka yi mana haka? Ka ji, mahaifinka da ni muna ta neman ka rai a bace." 49Ya ce masu, "Don me kuke nema na? Ba ku sani cewa dole in kasance a gidan Ubana ba?" 50Amma ba su gane abin da yake nufi da kalmomin nan ba.51Sa'annan ya koma gida tare da su zuwa Nazarat yana kuma masu biyayya. Mahaifiayarsa kuma ta ajiye dukan wadannan abubuwa a zuciyarta tana yin tunani akansu. 52Amma Yesu ya ci gaba da hikima da girma, ya kuma karu da tagomashi wurin Allah da mutane.
Wannan ya ba da shaharenren labari domin nuna dalilin da ya sa Maryamu da Yusufu su ka tafi lokacin a haifuar Yesu.
Wannan kalma na nuna alamar sabuwar sashin labarin.
Ana amfani da wannan kalma domin nuna cewa wannan ne labari na farko. Idan kabilar ka tana da hanyar fara labari, kana iya amfani da wannan. Wasu suran basu haɗ da kalman nan ba.
"Sarki Augustas" ko "Daula Augustas." Augustas shine daula na farko a kasan Romawa.
Mai yiwuwa mesinjojin ne suka dauka wannan umurni a ƙasan gabadaya. AT: "umurce masinjojin da shela"
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "cewa su rubuta sunayen dukan mutane dake duniya" ko "su ƙirga dukan mutane da ke duniya, sukuma rubuta sunayen su"
"a sashin duniya da gwamnatin Romawa ne ke mulki" ko "a kasan da daulan Roma ne ke mulki"
An zabi Kiriniyus ne ya zama gwamnan Syria.
"kowa da kowa suka soma tafiya" ko "kowa na tafiya"
Wannan na nufin garin da kaƙƙanen mutane suka yi rayuwa. Mai yiwuwa mutane sunyi rayuwa a gari dabam dabam. AT: "garin da kaƙƙanen mu sunyi rayuwa"
"a samu sunayensu a rubuce cikin rijistan" ko "domin a saka su cikin ainihin kirgen.
A nan ana gabatar da Yusufu kaman sabon mutum ne a labarin.
Wannan shahareren bayani ne akan muhinmincin Baitalami. Ko da yake karamar gari ce, a năn aka haifi Sarki Dauda, kuma anyi anabci cewa a năn za'a haifi Mai Ceto. AT: "wanda ake kira birnin Sarki Dauda"
"domin Yusufu ɗan zuriyar Dauda ne"
Wannan na nufin ya je gaban hukumomin su domin su iya hada kirgen da shi. Nemi kalman da gwamnatin suna amfani da shi domin kirgen.
Maryamu tayi tafiyan da Yusufu daga Nazarat. Mai yiwuwa mataye ma na biyan harajin. Haka kuma Maryamu na bukacin tafiya domin ayi mata rijista.
"budurwarsa" or "wanda aka masa alkawalin ta." Bisa ga dokan su ana ganin budurrwa da saurayi da sukayi alkawali ma'aurata ne. Amma da babu saduwa ta jiki a saƙaninsu.
Wannan yayi magana akan haifuwar Yesu da kuma sanarwa daga mala'iku zuwa ga makiyayin tumakin.
Wannan kalma na nuna alamar abin da zai faru năn gaba cikin labari.
"sa'adda Maryamu da Yusufu suna Baitalami"
"lokaci ya yi da zata haifi danta"
Wannan hanya na kulum ne daa uwa tana kare dakuma kula da jinjirin ta a wancan al'ada. AT: "nade bargo mai kauri kewaye da shi" ko "nade shi cikin bargo mai dadi"
Wannan wani irin kwali ne kokwa tsaiko da mutane ke saka hatara kokwa abinci dabam dabam wa dabbobi suci. Mai yiwuwa ya kan zama da tsabta da kuma kila ya samu abu mai laushi da kuma busheshe kamar hatara a ciki da ke kama da matashin fata domin jinjirin. Sau da yawa akan ajiye dabbobi kusa da gidaje domin kiyayewa da kuma ciyad da su da sauki. Maryamu da Yusufu sun zamna cikin daki da ake amfani wa dabbobi.
"babu wuri zama dominsu a cikin dakin baki." Wannan zai iya yiwuwa domin mutane dayawa sun je Maitalami domin rijista. Luka ya kara wannan kaman shahareren bayani ne.
"Sai mala'ika daga Ubangiji" ko "Sain mala'ika wanda yama Ubangiji bauta"
"bayyana wa makiyayin tumakai"
Tushin haske mai walkiya daukakar Ubangiji ne, wanda ya bayyana a lokaci daya da mala'ikan.
"daina jin tsoro"
"da zai saka dukan mutane murna sosai"
Wasu sun gane wannan a nufin ga mutanen Yahudawa ne. Wasu kuma sun gane ta a masayin dukan mutane ne.
Wannan na nufin Baitalami ne.
Akan iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "Allah zai baku wannan alama" ko "za ku gan wannan alama daga Allah"
"tabbaci." Kokwa wannan zai iya zama alama domin a tabbatar da cewa abin da mala'ikan ke fadi gaskiya ne, ko zai iya zama alaman da zai taimake makiyayin tumakin su gane da jinjirin.
Wannan hanya na kulum ne daa uwa tana kare dakuma kula da jinjirin ta a wancan al'ada. AT: "nade bargo mai kauri kewaye da shi" ko "nade shi cikin bargo mai dadi"
Wannan wani irin kwali ne kokwa tsaiko da mutane ke saka hatara kokwa abinci dabam dabam wa dabbobi suci.
Kalman nan "runduna sama" zai iya nuna cewa zahiri wannan runduna mala'iku ne, ko zai iya zama karin magana a kan shiryayyen kungiyar mala'iku. AT: "babban Kungiyar mala'iku daga sama"
"suna yabon Allah"
Ma'ana mai yiwuwa sune 1) "Ba da girma ga Allah mafi ɗaukaka" ko 2) "Ba da girma mafi ɗaukaka ga Allah."
"bari mutane dake duniya wadanda Allah ke jin dadinsu su sami salama"
Ana amfani da wannan kalma domin nuna sabon abin da zai faru cikin labarin akan abin da makiyayan sunyi bayan tafiyan mala'ikun.
"daga makiyayan"
"wa junansu"
Tun da makiyayin yayi maganan akan kowani dayan, harsunan/yaranruka da suna da shi a wannan fanni sai suyi anfani da shi anan.
"Bari mu" (UDB)
Wannan nufin zuwa ga haifuwar jinjirin ne, amma ba bayyanuwar mala'ikun ba.
Wannan wani irin kwali ne kokwa tsaiko da mutane ke saka hatara kokwa abinci dabam dabam wa dabbobi suci.
Akan iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "abin da mala'iku suka gaya wa makiyayan"
"jinjirin"
Akan iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "abin da makiyayan suka gaya masu"
Ajiya wani abu ne mafi anfani ko ɗaraja. Maryamu ta gane abin da aka sanar da ita game da ɗanta yana da ɗaraja kwarai. AT: "tunawa da su a hankali" ko "tunawa da su a farinciki"
"makiyayam sun coma wurin tumakinsu"
Wadannan suna da kamani sosai da kuma nanata yadda suka yi murna aka abin da Allah yayi. AT: "magana akai dakuma yabon girman Allah"
Wannan kalma na nuna wucewar lokaci kafin wannan sobuwar abin.
"a kwana ta takwas bayan haifuwarsa" ko "yana kwana ta takwas"
Yusufu da Maryamu sun rada masa sunarsa.
Akan iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "sunan da mala'ikan ya kira shi"
wannan yana nuna wucewar lokaci kafin sabon taron
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "lambar kwanaki da Allah ke bukata"
"domin su zama da tsabta." Zaku iya bayyana aikin Allah. AT: "domin Allah ya sake yadda su zama masu sabta'
"A mika shi wurin Ubangiji" ko "su mika shi gaban Ubangiji." wannan wani biki ne don tabbatar da da'awar Allah game da ɗan fari a 'ya'ya maza.
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "Kamar yadda Musa ya rubuta" ko "Sunyi haka domin musa ya rubuta"
"bude mahaifa" kalmar alama ce da yake nufin ga jinjiri na fari da ya fito daga cikin ciki. Wannan nufin duk da dabbobi da kuma mutane ne. AT: "Dukan 'ya'ya na fari wanda na maza ne" ko "Dukan ɗa na fari"
"abin da dokar Ubangiji ya kuma ce." Wannan wani guri dabam ne cikin dokan. Na nufin dukan ɗa na fari, ko ɗa na fari ko ba ɗa na fari ba.
Kalman nan "ga ma" na faɗakar da mu zuwa wani sabon mutum a cikin labarin. Mai yiwuwa kabilar ka na da hanyar yin wannan.
Ana iya bayyana waɗanan kalmomi karmar aiki. AT: "ya aikata abin da yake faranta wa Allah rai, ya kuma yi biyyaya ga dokokinsa"
Wannan na nuna ta'aziyar Isra'ila sa'adda Mai ceto ya bayyana. AT: wanda zai ta'azantar da Isra'ila"
"Ruhu Mai Tsarki na tare da shi." Allah na tare da shi a hanya ta musamman, ya nuna mashi hanya, ya kuma bashi hikima dakuma cikin rayuwarsa.
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "Ruhu Mai Tsarki ya riga ya nuna masa" ko "Ruhu Mai Tsarki ya riga ya fadi masa"
"sai ya ga Ubangiji Mai ceto kafin ya mutu"
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki: "Kamar yadda Ruhu Mai Tsarki ya bi da"
Wasu kabilu zasu iya ce "ya je"
"cikin ginin haikalin." Firistoci ne kawai suna iya shigan ginin haikalin.
"Iyayen Yesu"
"ka'idar shari'ar Allah"
"Ni bawanka ne, bari in tafi da salama." Saminu yana nufin kansane.
Kalma ce da ake amfani da ita a ma'anan "mutuwa"
"kamar yadda ka ce" ko "domin ka fada, zan kuma yi"
Kalmomin nan na nufin, " na gani da kaina" ko "ni, da kaina, na gani"
Wannan kalman na nufin mutumin da zai kawo ceto - Yesu da yake jinjiri - wanda Saminu ke rike da shi. AT: "Mai ceto wanda ka turo" ko " wanda ka tura ya yi ceto"
Ya dangantaka ga yanda ka yi fasarar kalman da ya wuce, za'a iya canja wannan zuwa "wanda ka."
"wanda ka shirya" ko " ka sa ya faru"
Wannan na nufin cewa yaron zai taimake mutane su fahimci nufin Allah.
zai iya zama wajibi ne a faɗi abin da za'a bayyana. AT: "da zai bayyana gaskiyar Allah"
"zai zama dalilin da daukakar mutanen ka na Isra'ila zai zo"
Ana iya bayyana wannan cikin siffar aiki. AT: "abubuwan da Saminu ya fadi game da shi"
"ya fadi waMaryamu, Uwar jaririn ." Tabbatar da cewa bai yi kamman Maryamune Uwar Saminu ba.
Kalmomin nan "fadiwa" da kuma "tashiwa" ya bayyana juyewa daga hanyar Allah dakuma zuwa kusa da Allah. AT: "wannan jariri zai saka mutane dayawa a Isra'ila su fadi daga hanyar Allah ko su zo kusa da Allah"
"zai kuma zama sako daga Allah wanda mutane dayawa zasu ki"
Wannan karin maga ya bayyana surfin bakin cikin da Maryamu zata ji. AT: "Bakin cikin ki zai iya zama kaman takobin da ya tsaga ziciyar ki"
"zukata" na nufin zuwa ga mutane ne. AT: "tunannin zukata dayawa zasu bayyana"
Wannan na gabatar da sabon mutum cikin labarin.
"Fanuyila" sunan mutum na miji ne.
"shekaru 7
"bayan da ta aure shi"
Ma'ana mai yiwuwa sune 1) Ta yi zaman gwamranci na shekaru tamanin da hudu ko 2) ita gwamrurace harna shekaru tamanin da hudu.
zai iya yuwa karin bayyani ne kame da yawan lokaci da ta shafe a haikali ya iya nuna bata bari ba. AT: "ko da yaushe a haikali" ko "sau da yawa a haikali"
"ta wurin kin abinci na lokatai dayawa da kuma ta wurin adu'oi sosai"
"kusance su" ko "je wurin Yusufu da Maryamu"
A nan, anyi anfani da kalman nan "fansa" don a nufi mutumim da zai yi shi. AT: "wanda zai fanshe Urushalima" ko "mutumin da zai kawo albarkun Allah da kuma tagomashi zuwa ga Urushalima"
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "da sheri'ar Ubangiji ke bukata suyi"
Wannan kalma na nufin sunyi rayuwa cikin Nazarat. Yi tabbacin cewa bai yi kaman sune da birnin ba.
"karuwa da hikima sosai" ko "koyon abin da ke hikima"
"Allah ya albarkace shi" ko "Allah na tare da shi a hanya ta musamman"
Wannan shahareren bayyani ne.
"iyayen Yesu"
Urushalima na fiye da kusan kowane wuri a Isra'ila, haka kuma ba wani abu bane Isra'ilawa suyi maganan zuwa Urushalima.
"a daidai lokacin" ko "yadda suke yi a kowace shekara"
"Lokacin da murnan bikin idin ya wuce gabadaya" ko "Bayan murnan bikin idin na dukan kwanakin"
Wannan wani suna ne kuma domin idin ketarewa, da shike bai haɗa da cin abincin biki ba.
"Suna tunanin"
"suka yi tafiyan kwana daya" ko "suka kuma yi yadda mutane ke tafiya a kwana daya"
Wannan na nufin a filin kewaye da haikalin. Firistocin ne kawai ake bari acikin haikalin. AT: "a kewayen haikalin" ko "a haikalin"
Wannan baya nufin daidai tsakiyar ba ne. ya na nufin "tsakanin" ko "tare da" ko "kewaye da."
"malamen addini" ko "wanda suke koyas wa mutane game Allah"
Basu iya gane yadda yaron shekara goma shabiyu wanda bashi da illimi na addini zai iya bada amsa sosai haka ba.
"yawan ganewarsa" ko "cewa yana da ganewa sosai game da Allah"
"yawan amsoshi masu kyau da ya basu" ko "cewa ya amsa tambayoyin su da kyau"
"Lokacin da Maryamu da Yusufu suka same Yesu"
Wanan ba kaikaitacce tsautawa bane domin bai tafi tare da su ba garin comowa gida. AT: "bai kamata da ka yi wannan ba!"
Sau dayawa, akan yi amfani da wannan kalma domin nuna farkon sabuwar abu ko abu mai muhinminci. Ana iya amfani da shi domin nuna inda aikin ƙan fara. Idan kabilar ka tana da kalman da ake amfani da ita ta wannan hanya, yi tunanin ko alhali, za iya amfani da ita anan.
Yesu yayi amfani da tambayoyi guda biyu don ya tsauta wa iyayensa da lafazi mai taushi, ya kuma faɗa masu da cewa manufar zuwarsa a duhunce yake garesu. AT: "Bai kamata ku damu da ni ba."
Yesu yayi amfani da wannan tambaya na biyu domin yayi kokarin faɗa masu cewa yakamata iyayensa su sani game da nufin, wanda Ubansa ya turo shi.
A shekara ta 12, Yesu, Ɗan Allah, ya gane cewa Allah ne Assalin Ubansa
Ma'ana mai yiwuwa sune 1) "a gidan Ubana" ko 2) "game da aikin Ubana." ko dai, lokacin da Yesu yace "Ubana" yana nufin Allah ne. Idan yana nufin "gida ne," wato yana nufin haikalin ne. Idan yana nufin "aiki ne," yana nufin aikin da Ubangiji ya bashi ya yi. Amma, da yake aya na gaban ya fada cewa iyayensa basu gane abinda yake gaya masu ba, zai zama da kyau in ba yi bayyanin sa sosai ba.
"Yesu ya koma gida tare da Maryamu da Yususfu"
"masu biyayya" ko "yana masu biyayya kullum"
A nan "zuciya" na nufin "zuciyar mutum" ko tunanin mutum. AT: "tayi tunani cikin natsuwa game da dukan waddanan ababubuwa.
"ya zama da karfi da kuma hikima." Waddanan na nufin girma cikin hankali da kuma jiki.
Wannan na nufin girma ta jiki a kuma ruhaniya. Ana iya bayyana wannan dabam-dabam. AT: Ubaniji ya albarkace shi sosai, kuma mutane sun so shi sosai."
1A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya, 2kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.3Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.4Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, "Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!5Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada, 6kuma dukan mutane za su ga ceton Allah."7Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, "Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?8Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.9Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta."10Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, "To me za mu yi?" 11Ya amsa ya ce masu, "Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan."12Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, "Malam, me za mu yi?" 13Ya ce masu, "Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku."14Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, "To, mu fa? Yaya za mu yi?" Ya ce masu, "Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku."15Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu. 16Yahaya ya amsa ya ce masu duka, "Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.17Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.18Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara. 19Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi. 20Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.21Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude, 22kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, "Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka."23Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli, 24dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,25dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya, 26dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,27dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri, 28dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er, 29dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,30dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima, 31dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda, 32dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,33dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda, 34dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor, 35dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,36dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek, 37dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana, 38dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.
Kamar yadda annabi Ishaya ya fadi, Yohana ya fara shelar bisharar salama ga mutane.
Wadannan ayoyi suna bada shahareren bayyani don fadin abin da ke faruwa alokacin da dan'uwan Yesu ya fara bishararsa.
"Lokacin da Tibarius Kaisar yayi mulki har na tsawon shekaru goma sha biyar"
Wadannan sunayen maza ne.
Wadannan sunayen yankin kasashe ne.
"A lokacin da Hanana da Kayafa suke bauta tare a matsayin manyan firistoci." Hananiya ne babban firistin a lokacin, kuma Yahudawa suka chigaba da yarda (shaida) da shi a matsayinsa har bayan da Romawa suka naɗa sirikin sa, Kayafa, ya gaje shi a matsayin babban firistin.
"Allah ya fadi kalmar sa"
Kalmomin nan "baftisma" da kuma "tuba" ana iya fade su kamar aiki. AT: "sai kuma yayi wa'azi cewa ayi wa mutanen baftisma domin nuna cewa suna tuba"
Kalman nan "gafara" ana iya bayyana shi kaman aiki. AT: "domin a yafe masu zunubensu" ko "domin Allah ya yafe zunubensu." Zasu tuba domin Allah ya yafe zunubensu.
waddannan kalmonin na bayyana kalmomi daga annabi Ishaya. AT: "haka ya faru kaman yadda annabi Ishaya ya rubuta cikin littafinsa da ke dauke da kalmonin sa" ko "Yohana ya cika saƙon da annabi Ishaya ya rubuta cikin littafin sa"
Ana iya fadin wannan a matsayin magana. AT: "An ji muryar wanda ke kira daga cikin jeji" ko "Sun ji karar muryar wani da ke kira cikin jeji"
umurnin farko na bayani ko na ƙara bayani ga na farkon ne.
"Shirya hanya domin Ubangiji." Yin haka na wakiltcin yin shiri domin jin sakon Ubangiji alokacin da zai zo. Mutane na yin haka ta wurin tuba daga zunuben su. AT: "Yi shirin jin sakon Ubangiji alokacin da zai zo" ko "Ku tuba ku kuma yi shiri domin Ubangiji ya zo"
"hanyar" ko "hanyar
Idan mutane na shirya hanya domin zuwan mutum mai muhinmminci, suna yanke inda yayi tudu su kuma cika inda yayi kasa domin hanyar ya zama da lebur. Wannan sashin magana ya fara a ayan da wuce.
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "Zasu cika duk inda yayi kasa a hanyar"
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "zasu yi lebur na kowanne dutse" da "kuma kwanne tudu" ko " zasu cire kowanne wuri da ke da tudu a hanyar"
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "koyi yadda Allah ke ceton mutane daga zunubi"
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "domin Yohana ya masu baftisma"
A nan "yaya" na nufin zama da kwatancin. " AT: "Mugayen macizai na da dafi da hatsari sosai kuma ana kwatanta su da mugunta. AT: ku macizai masu dafi" ko "Kuna da mugunta, kamar macizai masu dafi
Bai yi zato za su bashi amsa ba. Yohana ya gargade jama'an domin suna so ya masu baftisma don kada Allah ya hukuntasu, amma, ba suwa son su daina yin zunubi. AT: "Ba zaku iya guje wa fushin Allah ta haka ba" ko "Ba zaku iya tsira daga fushin Allah ta wurin don yin baftisma ba kawai"
Kalman "fushi" ana amfani da shi domin nufin hukuncin Allah domin fushinsa ya riga shi. AT: "daga hukuncin da Allah zai aiko" ko "daga fushin Allah wanda yake shirin aikatawa"
A wannan kalman, ana kwatanta halayen mutane da 'ya'yan itace. Kamar yadda ake zacin itace ya ba da 'ya'ya wanda zai dace da ita, wanda yace ya tuba, ana zacin yayi rayuwan adalci. AT: "ba da irin 'ya'ya da zai nuna kun tuba" ko "yi abubuwa masu kyau da zai nuna kun juyo daga zunuben ku"
"cewa a tsakaninku" ko "tunani"
"Ibrahim kaƙan mu ne" ko "Mu zuriyar Ibrahim ne." Idan ba samu haske a dalilin da suka ce haka ba, zaku kuma iya karin asalin nufin bayyanin: "domin kada Allah ya hukunta mu"
Wannan kalma na ma'anan "hallita wa Ibrahim 'ya'ya" ko "sa mutane su zama zuriyar Ibrahim"
Watakila, Yohana na nufin ainihin duwatsu da suke hanyar Kogin Urdun
Gatari da yake a wurin domin yanke gindin itatuwa kalma ce da ake amfani domin hukunci da yake shirin farawa. Ana iya bayyana shi cikin sifar aiki. AT: "Allah kaman mutum ne da ya rigaya ya saka gatari a gindin itatuwan"
"wuta" Kalma ce da ake amfani domin hukunci. AT: "ya sare duk itacen da ba ta ba da 'ya'ya masu kyau zuwa kasa"
"tambaye shi, da cewa" ko "tambayan Yohana"
"amsa masu, yana cewa" ko "amsa masu" ko "ya ce"
"raba raguwar abinci kamar yadda kuka raba raguwar abin shan." Wannan na nufin koma wa bada abinci wa mabuƙata. AT: "ba da abinci wa wanda ba shi da komai"
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "domin Yohana ya yi masu baftisma"
"Kada ku tambayi kuɗi kuma" ko "kada ku yi neman ̀kuma." Masu karban haraji suna karban ƙudi fiye da yadda ya kamata. Su daina yin haka.
Wannan zancen na nufin masu karɓar haraji sukan karɓi ikonsu daga Roma ne. AT: "Fiye da abinda Romawa suka umurcesu su karɓa."
"Mu kuma fa sojoji, me za mu yi?" Kalman bai shafe Yohana ba" "da mu" da kuma "mu." Sojojin sun yi zaton cewa Yohana ya rigaya ya faɗa wa jama'a da kuma masu karɓan haraji abin da yakamata su yi ba da son me a matsayin sojoji za su yi ba.
kamar sojojin su na zargin karya game da mutane domin su samu kuɗi. Ana iya bayyana wannan da ƙarara. AT: "don haka kuma, kada ku wa wani zargin ƙarya domin ku samu ƙudi a wurin su" ko "kada ku ce mutum mara laifi ya ƙetare doka"
"Ku dogara ga albashinku"
"domin mutanen." Wannan na nufin mutanen ne suka zo gurin John.
kowa bai tabbata me zai yi tunani game da Yohana ba; sun tambayi kan su 'Ko shi ne Christi?' ko "ba wande ya tabbata abinda za yi tunani game da Yohana domin su na tunani ko ko zai iya zama shi ne Christi."
Amsar Yohana game da zuwan mutum mai muhinmincin na nufi cewa ba Yohana bane Christi. Zai iya zama da mahimmanci ka faɗa wa masu sauraronka. AT: "Yohana ya bayyana masu cewa ba shi bane ba Chiristi"
"Ina yin baftisma da ruwa" ko "Ina yin baftisma ta wurin amfani da ruwa"
"ban isa ba harma na kwance maballin takalmansa." Kwance maballin takalman aiki ne na bawa. Yohana yana faɗa cewa shi wanda ke zuwa mai muhinmici ne sosai, harma ni, Yohana, ban isa in zama bawansa ba.
Wannan kalma na zahirin kwatanta baftisma da ake yi da ruwa da baftisma na Ruhu da ke kawo su kusa da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
A nan, kalman nan "wuta" na iya nufin 1) hukunci ko 2) tsarki. Ya fi a bar shi a matsayin "wuta"
ya riƙe da ƙwaryar shiƙa domin yana shirye." Yohana na magana a kan zuwan Kristi domin sheri'a kaman shi manomi ne wanda yana shirye ya raba kwayan alkama daga dusan. AT: "Yana rike da kwayar shikar domin yana shirye" ko "Yana shirye ya yi hukunci kamar manomi wanda yana shirye"
Wannan kayan aiki ne da ake amfani domin busa alkama a iska, domin a raba kwayan alkaman da dusan. Ainihin kwayar na fadiwa zuwa ƙasa, sai kuma isca na hura dusa mara amfani. Yana nan kusa iri daya da abin shiƙa
Masussuƙan wuri ne da ake tara alkama domin shirin sussuƙa. A "share" ƙasan na nufin a gama tara kwayar. AT: "a gama tare kwayar"
Alkaman ne ya dace a ajiye a dakin ajiya bayan girbi.
ƙaiƙayin bashi da amfani 'a komai, sai, mutane na kona shi.
"Da gargadi masu karfi"
Hiridus, Mugu ne, amma ba sarki bane. Yana da ƙarancin ikon yin mulki a yankin ƙasar Galili.
"domin Hiridus ya auri matar dan'uwansa Hiruduya." Wannan mumunan abi ne domin dan'uwan Hiridus na nan da rai. Ana iya bayyana wannan a haske. AT: "domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, tun lokacin da dan'uansa yana da rai"
"ya gaya wa sojojinsa su saka Yohana a kurkuku"
Wannan kalman na alamar sonbon abin da zai faru na farko a cikin labarin. Idan kabilar ka tana da hanyar yin haka, za ka iya amfani da shi a nan.
"da Yohana ya yiwa dukan mutane baftisma." Kalman "dukan mutane" na nufin mutane da suna nan tare da Yohana.
Ana iya bayyana wannan cikin siffar aiki. AT: "Yohana ya yiwa Yesu ma baftisma"
"sararin sama ya bude" ko "sararin sama ya zama a bude." wannan na nufin yadda sararin sama ta yi haske, ko da shike ba a gane haskenta ba. wataƙila ya na nufin wani rami ya buɗe a sararin sama.
"a siffa ta jiki Ruhu Mai Tsarki ya sauko kamar kurciya a kan Yesu"
A nan "murya ta fito daga sama" wakiltar mutanen duniya masu jin Allah a sama yan magana. za a iya cewa Allah yayi magana da Yesus. AT: "murya daga sama ta ce" ko "Alla yati magana da Yesus daga sama, cewa"
Wannan baban sunane wa Yesu, ɗan Allah.
Ana amfani da wannan kalma don nuna alamar canji daga labarin zuwa shahareren bayyanen game da shekarun Yesu da ƙaƙanensa.
"Shekara 30"
"an yi tunanin cewa shi ɗan Yusufu ne" ko "mutane su yi tsammanin cewa shi ɗan Yusufu ne"
Ka lura da yadda mutane kan lisafta kakaninsu a yareka. Sai kayi amfani da yadda aka saɓa.
Wannan ne cigabawan sunaye na ƙakanen Yesu. Yi amfani da siffa iri daya da ka yi amfani da shi a ayoyin da suka wuce.
Wannan ne cigabawan sunaye na ƙakanen Yesu. Yi amfani da siffa iri daya da ka yi amfani da shi a ayoyin da suka wuce.
Wannan ne cigabawan sunaye na ƙakanen Yesu. Yi amfani da siffa iri daya da ka yi amfani da shi a ayoyin da suka wuce.
Wannan ne cigabawan sunaye na ƙakanen Yesu. Yi amfani da siffa iri daya da ka yi amfani da shi a ayoyin da suka wuce.
Wannan cigaba ne na lisafin kakanen Yesu. Yi amfani da irin sifan da aka yi aiki da shi a ayoyin da suka wuce.
"Adamu, hallitar Allah" ko "Adamu, wanda ya zo daga Allah" ko "Adamu, ɗan Allah, zamu iya ce, na Allah"
1Sai Yesu, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga kogin Urdun, sai Ruhu Mai Tsarki ya bishe shi zuwa cikin jeji 2kwana arba'in, shaidan kuma ya jarabce shi. A kwanakin nan, bai ci abinci ba, kuma yunwa ta kama shi bayan karshen lokacin.3Shaidan ya ce masa, "Idan kai Dan Allah ne, ka umarci wannan dutse ya zama gurasa." 4Yesu ya amsa masa, "A rubuce yake, 'Ba da gurasa kadai Mutum zai rayu ba.'"5Sai shaidan ya kai shi zuwa wani tudu mai tsawo, ya kuma nuna masa dukan mulkokin duniyan nan a dan lokaci. 6Shaidan ya ce masa, "Zan ba ka iko ka yi mulkin dukan wadannan, da dukan daukakarsu. Zan yi haka domin an ba ni su duka in yi mulkinsu, kuma ina da yanci in ba dukan wanda na ga dama. 7Saboda da haka, idan ka rusuna ka yi mani sujada, dukansu za su zama naka."8Amma Yesu ya amsa ya ce masa, "A rubuce yake, 'Dole ne Ubangiji Allahnka za ka yi wa sujada, shi kadai kuma za ka bauta wa."9Sai shaidan ya kai Yesu Urushalima, ya tsayadda shi a bisan kololuwar haikali, kuma ya ce masa, "Idan kai Dan Allah ne, ka jefas da kanka kasa daga nan. 10Domin a rubuce yake, 'Zai ba mala'ikunsa umarni su kiyaye ka, su kuma tsare ka,' 11kuma, 'Za su daga ka sama a hannunsu, don kada ka yi tuntube a kan dutse."12Yesu ya amsa masa cewa, "An fadi, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'" 13Da shaidan ya gama yi wa Yesu gwaji, sai ya kyale shi sai wani lokaci.14Sai Yesu ya koma Galili cike da ikon Ruhu, kuma labarinsa ya bazu cikin dukan wuraren dake wannan yankin. 15Ya yi ta koyarwa a cikin majami'unsu, sai kowa na ta yabon sa.16Wata rana ya zo Nazarat, birnin da aka rene shi. Kamar yadda ya saba yi, ya shiga cikin majami'a a nan ranar Asabaci, ya kuma tashi tsaye domin ya karanta Nassi. 17An mika masa littafin anabi Ishaya, ya bude littafin ya kuma ga inda an rubuta,18"Ruhun Ubangiji yana kai na, domin ya shafe ni in yi wa'azin Bishara ga matalauta. Ya aike ni in yi shelar yanci ga daurarru, da kuma budewar idanu ga makafi, in 'yantar da wadanda su ke cikin kunci, 19in kuma yi shelar shekarar tagomashi na Ubangiji."20Sai ya rufe littafin, ya mai da shi ga ma'aikacin majami'ar, sai ya zauna. Dukan wadanda suke cikin majami'ar suka zura Idanuwansu a kansa. 21Sai ya fara masu magana, "Yau wannan Nassi ya cika a kunuwanku." 22Dukan wadanda ke wurin sun shaida abin da ya fadi kuma dukansu sun yi ta mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suna cewa, "Wannan ai dan Yusufu ne kawai, ko ba haka ba?"23Yesu ya ce masu, "Lallai za ku fada mani wannan karin magana, 'Likita, ka warkar da kanka. Duk abin da mun ji wai ka yi a Kafarnahum, ka yi shi a nan garinka ma.'" 24Ya sake cewa, "Hakika na fada maku, annabi baya samun karbuwa a garinsa.25Amma na gaya maku gaskiya akwai gwauraye da yawa cikin Isra'ila a zamanin Iliya, lokacin da an rufe sammai shekaru uku da rabi babu ruwa, lokacin da anyi gagarumar yunwa a duk fadin kasar. 26Amma ba a aiki Iliya zuwa wurin waninsu ba, sai wurin gwauruwa da ke a Zarifat can kusa da Sidon. 27Akwai kutare da yawa kuma a Isa'ila a zamanin anabi Elisha, amma babu wanda aka warkar sai dai Na'aman mutumin Suriya kadai.28Dukan mutanen da ke cikin majami'a suka fusata kwarai sa'adda suka ji wadannan zantattuka. 29Suka tashi suka tura shi zuwa wajen birnin, suka kai shi bakin dutsen da aka gina garinsu a kai dominsu jefar da shi kasa. 30Amma ya ratsa tsakaninsu ya yi gabansa.31Sannan ya gangara zuwa Kafarnahum, wani birni a Galili. Wata Asabaci yana koya wa mutane a cikin majami'a. 32Sun yi mamaki kwarai da koyarwan sa, domin maganarsa na da iko.33A wannan lokacin akwai wani mutum a cikin majami'a mai kazamin ruhu, sai ya yi kara da babbar murya, 34"Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo domin ka hallaka mu ne? Na san ko kai wanene! Kai ne Mai Tsarki na Allah!"35Yesu ya tsauta wa aljanin yana cewa, "Yi shiru ka fita daga cikinsa!" Da aljanin ya jefar da mutumin kasa a tsakiyarsu, ya fita daga cikinsa ba tare da yi masa rauni ba. 36Dukan mutanen suka yi mamaki, kuma suna ta zancen wannan abu a tsakaninsu. Sun ce, "Wanda irin maganganu kenan? Ya umarce kazaman ruhohin da karfi da iko kuma sun fita." 37Saboda da haka, an fara yada labarinsa zuwa dukan kewayen yankin.38Sai Yesu ya bar majami'ar ya shiga gidan Siman. A wannan lokacin, surukar Siman tana fama da zazzabi mai zafi, sai suka roke shi dominta. 39Sai ya tsaya a kanta, ya tsautawa zazzabin, kuma ya rabu da ita. Nan take, ta tashi ta fara yi masu hidima.40Da faduwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan wadanda suke ciwo da cuttuttuka dabam dabam. Ya dora masu hannuwansa ya warkar da su. 41Aljanu kuma sun fita daga wadasunsu da dama, suna kuka cewa, "Kai ne Dan Allah!" Yesu ya tsauta wa aljannun ya kuma hana su magana, domin sun sani cewa shine Almasihu.42Da safiya ta yi, ya kebe kansa zuwa wani wurin da babu kowa. Jama'a da dama suna neman sa suka zo inda yake. Sun yi kokari su hana shi barin su. 43Amma ya ce masu, "Dole in yi bisharar Allah a wasu birane da dama, domin dalilin da aka aiko ni nan kenan." 44Sai ya ci gaba da wa'azi cikin majami'u dukan fadin Yahudiya.
Yesu ys yi azumi na kwana arba'in, sai sheɗan ya hadu da shi ya su ya ringaye ya y zunubi.
Bayan da Yahaya ya yi wa Yesu baftisma.
AT: "ruhu ya bishe shi"
juye mafi yawa sun ce gwajin gaba ɗaya na kwanaki arba'in ne. UDB ya fada, "da ya ke agun, shaiɗan ya cegaba da gwada shi" don a bayya na shi.
"kwanaki 40"
AT: "kuma zaka iya bayyana shi shaiɗan ya gwada shi ya yi. ATL "shaiɗan ya yi ya rinjaye shi domin kada ya yi wa Allah biyyaya"
Wannan kalmar "ya" na nufin Yesu.
Shaidan ya tsokani Yesu ya yi wannan aikin al'ajibin domin ya tabbatas da cewa shi ɗan Allah ne "ɗan Allah"
shaidan ko ya reke dutse a hannun sa ko kuwa ya na nuna wata dutse kusa.
Yesu ya ki tsokanan shaidan ya nuna ba shakka a amsar sa.zai zama da taimako ka faɗi wannan ba shakka ga masu sauraro, kamar yadda UDB ya yi. AT: "Yesu ya amsa, 'A'a, ba zan yi haka ba domin a rubuce yake ... kadai."
Wannan maganar daga rubutun Musa ne a tsohowar alkawari. AT: "Musa ya rubuta a cikin littafi"
Wannan kalmar "gurasa" na nufin aabinci gaki ɗaya. abinci kamar yadda Allah ya hada, da kanta, bai isa ya ceci mutum ba. Yesu ya faɗi littafi ya ce abin da ya sa ba zai juya dutsen ya zama gurasa ba. AT: "Mutane ba za su rayu da gurasa kadai ba" ko "ba abinci ne kadai yake sa mutum ya rayu ba" ko "Allah ya ce akwai abubuwa mafi muhimmanci fiye da abinci"
ya kai Yesu wani tudu.
"cikin ƙaramin" ko "nan da nan"
Ma'ana mai yuwa da suke "su" na nufin 1) iko da mai girma na mulkin ko 2) mulkin. AT: "Allah ya bani su"
Wannan sashin biyun sun yi kusa. Za'a iya hada su. AT: "idan ka rusuna ka yi mani sujada
"Zan baka dukkan wannan mulkin, da girmam su"
"ya amsa masa" ko "amsa masa"
Yesu ya na faɗan umurni daga littafi ya faɗa abin da ya sa ba zai bauta wa shadan ba.
Wannan na nufin mutanen da suke tsohowa alkawari wanda suka karbi dokar allah. za ka iya amfani da siffar mafuradi na 'ku' domin kowanne mutum ya yi biyayya da shi, ko ka yi amfani da siffar jam'i na 'ku' domin dukkan mutanen su yi biyayya da shi. (Dubi:
Wannan kalmar "shi" na nufin Ubangiji Allah.
Wannan lungu ne na jinkan haikalin. Idan wani ya faɗi daga wurin, za su ji ciwo sosai ko su mutu.
Wannan masayi ne mafi muhimmanci wa Allah.
"yi tsalle zuwa ƙasa"
Shaidan ya nuna da cewa faɗin sa daga zabura na nufin Yesu ba zai ji ciwo ba idan shi aɗn Allah ne. Wannan za'a iya faɗan ta ba shakka, kamar yadda UDB ya yi. AT: "Ba za ka j ciwo ba, domin a rubuce yake"
"Shi" na nufin Allah. shaidan ya faɗa daga zabura domin ya rinjayi Yesu ya yi tsalle daga ginin.
Yesu ya faɗa wa shaidan abin da ya zai yi abin da ya ce ya yi ba. ƙin yin bun na a bayyane. AT: "A'a, ba zan yi hakan ba, domin an faɗa"
Ma'ana mai yuwa 1) Kada Yesu ya gwada Allah da yin tsalle daga saman haikalin, ko 2) kada shaidan ya gwada Yesu cewa shi ɗan Allah ne. yana da kyau a juya ayan yadda aka faɗe ta da ka so ka bayana ma'anar sa.
"sai ranar aukowar babban abu"
Wannan arin bai nuna da cewa shaidan ya ci nasara a gwajin da ya yi wa Yesu ba - Yesu ya ƙi yarda da kowanne ƙoƙari. AT: "Ya gama gwadawa ya ringayi Yesu ya yi zunubi"
Wannan ya fara sabuwar abu a labarin.
"sai ruhun yana ba shi iko." Allah ya na tare da Yesu a wata hanya na musamman, sa shi ya yi abubuwa da mutane ba za su iya yi kullum ba.
"Mutane sun baza labari akak Yesu" ko "mutanesun gaya wa wasu game dea Yesu" ko "ilmi akan sa aka faɗa daga mutum zuwa wani mutum." Wadanda suka ji Yesu sun gay wa wasu mutane game da shi, sai kuma wadannan mutane suka gaya wa wasu mutane game da shi sosai.
Wannan na nufin filaye ko wurare kewaye da Galili.
"kowa ya faɗa manyan abubuwa game da shi" ko "dukkan mutanen su yi magana akan sa a hanya mai kyau"
"Wurin da iyayan sa suka rene shi" ko "in da ya zauna lokacin da yake yaro" ko "in da ya yi girma"
"kamar yadda yake yi kowanne Asabaci. "al'adar yi ne na kullayomi ya je majami'a a ranar Asabar.
AT: "Wani ya ba shi littafin annabi Ishaya"
Wannan na nufintakar dan Ishaya wanda aka rubuta a littafi. Ishaya ya rubuta kalmomin tun da daɗewa, sai wani dabam ya kofa a littafi.
"wuri a littafin da wadannan kalmamomin." Wannan bayanin ya cigaba har zuwa aya ba biye.
"Ruhu mai tsaki yana tare da ni a hanya na musamman." sa'anda wani ya faɗi haka, yana yin riya cewa yana maganar kalmomin Allah.
A tsohowar alkawari, main bikin al'ada aka zuba a kan mutum sa'anda aka ba su ƙarfi ko iko su yi wani aiki na musamman. Yesu ya yi amfani da wannan misalin ya yi nufin ruhu mai tsarki fara akan shi ya shirya shi domn aikin sa. AT: "ruhu mai tsarki yana kai na ya
"matalautan mutane"
"gaya wa mutane wadanda suke ɗaurarru da cewa za su iya tafiya" ko "a sake ɗaurarrun yaki"
"ba wa makafai idanu" ko "sa makafai iya gani kuma"
"a sake wadanda aka wulakantasu"
"gaya wa kowa da cewa Allah ya shirya ya yi wamutanen sa albarka" ko "ayi shaila cewa wannan shekaran ne Allah zai nuna wa alheri"
A na kulle littafi ta wurin naɗewa kamar bututu domin ya tsare rubutun ciki ta.
Wannan na nufin masu aiki a cikin haikalin wanda suke kawo su kuma aijiye da hankali da grimama littafin dauke da littafin kirista
Wannan ƙarin na nufin "juya ɗon mudube shi" ko "muna kallonsa da gangan"
Yesu ya na cewa shi yana cika wannan anabcin da aikin sa da maganar sa a waccan lokaci. AT: "I na cika abinda aya ta faɗa yanzu da kuke jina"
Wannan karin na nufin "sa'anda kuke jina"
"mamaki game da abubuwan alheri da yake faɗawa." A nan "alheri" mai yuwa na nufin 1) yadda yake da kyau ko yadda maganar Yesu ke rinjayer, ko 2) Yesu ya yi magana akan alherin Allah.
Mutane suna tunanin cewa Yusufu na uban Yesu. Yusufu ba shugaban addini bane, suna mamakin yadda yaron sa ya yi wa'azi yadda ya yi. AT: "Wannan ɗan Yusufu ne kawai!" ko "uban sa Yusufu ne kawai!"
Nazarat gari ne inda Yesu ya yi girma.
"ba shakka" ko "babu shakka da cewa"
Idan wani ya ce yana warkar da cutan da shi da kansa yakeda shi, ba dalili sai dai a yarda da cewa lallai shi likitane. Mutane zasu yi wa Yesu wannan ƙarin magana su ce za su yarda shi annabi ne idan ya yi abin da suke ji ya yi a wasu wurare.
Mutanen Nazarat ba su yarda ba. Yesu annabi bane domin ƙaramin masayin sa ɗan Yusufu. baza su yarda ba sai sun gan shi ya na yin ayukan al'ajibi.
"ba shakka da gaskiye ne."Wannan bayani ne mai ƙarfi game da abin da ya biyu baya.
Yesu ya yi magana na baki ɗaya damin ya kwaɓi mutanen. ya na nufin cewa sun ki su yarda da shalar ayukan al'ajibin sa a Kafarnahum. suna tunanin cewa su riga su san komai game da shi.
"garin sa" ko "ɗan ƙasar" ko "garin da ya yi girma"
"Na gay amaku gaskiyan." Yesu ya yi amfani da wannan sasjin domin ya yi nauyin muhimmanci, gaskiya, da daidai bayanin da ya biyu baya.
Gwamraye mataye ne wanda mazajen su sun mutu.
Mutanen da Yesu yake yi masu magana sun sani da cewa Iliya ɗaya daga cikin annabawan Allah ne. Idan mai ƙaratun ka bai san wannan ba, zaka iya bayana wannan kamar yadda yake a UDB. AT: "sa'anda Iliya yake yin ananbaci a Isar'ila"
Wannan misali ne. an ga hoton sama kamar rufin ɗaki wanda ya kullu, sabo da haka ba ruwa da zai faɗi daga ita. AT: "sa'anda babu ruwan da ya faɗɩ daga sama" ko "sa'an da babu ruwa gaba ɗaya"
an yi rashin abinci mai nauyi." yunwa doguwar lokaci ne sa'anda baroro bata haifu abinci sosai wa mutane ba.
Mutanen dake zama a Zarifat al'umai ne, ba Yahudawa ba. Wadannan mutanen da suke sauraran Yesu sun gane da cewa mutanen Zarifat ba Yahudawa bane. AT: "zuwa ga ba al'umar gwamruwa da take zama a Zarifat"
Mutumin Suriya mutum ne daga Suriya. Mutanen Suriya al'umai ne, ba Yahudawa ba. AT: "Na'aman ba al'ume daga Suriya"
Mutanen Nazarat suka ji haushi sosai cewa Yesu ya fsɗi littafi inda Yesu ya taimaki al'umai a maimakon Yahudawa.
"suka sa shi da arfi ya bar garin" ko "bangaje shi zuwa wajen garin"
"baki bakin"
"ta tsakanin taron" ko "tsakanin mutanen da suke so su kashi shi."
"ya tafi abunsa" ko "ya tafi a hanyar sa" Yesu ya tafi anda ya yi shiri ya je a maimakon inda mutanen su ke sa shi dole ya ji.
Sa'anan Yesu." Wannan ya nuna sabuwar abu.
Wannan sashin "gangara" an yi amfani da shi a nan domin Kafarnahum ya yi ƙasa da Nazarat.
"Kafarnahum, wani birni ne a Galili"
babban mamaki, ya ji babban mamaki
"ya yi magana kamar wanda yake da iko" ko "kalmomin sa yana da babban ƙarfi"
Wannan sashin an yi amfani da shi anan domin a s alamar gabatar da wani sabuwar hali a labarin; a wannan yanayi, mutum mai aljanu.
"wanda yake da kazamin ruhu" ko "wanda mugayen ruhohi suke aiki da shi"
"ya yi ihu da arfi"
Wannan amsa mai ƙari ne wanda ke nufin: "mai muke da shi iri ɗaya?" ko "Wanne dama kake da shi na damun mu?"
Wannan tambayn za'a iya rubutashi kamar bayani. AT: "Me kai, Yesu Banazarat, za ka yi da mu!" ko "baka da dama na damun mu, Yesu Banazarat!"
"Yesu ya yiwa aljanun tsawa. yana cewa" ko "Yesu ya ce wa al'janun da tsanani"
Ya umurci al'janun su daina iko da mutumin. AT: "ku bar shi" ko kada ku zauna a ciki mutumin kuma"
Mutanen suna furta yadda suke da mamaki da cewa Yesu ya na da iko ya umurci aljanu su bar mutum. Wannan za'a iya rubuta shi kamar bayani. AT: "Wannan kalmomin ban mamaki ne!" ko "Kalmomin sa abin mamaki ne!"
"Ya na da iko da ƙarfi ya umarce ƙazamen ruhohin"
Wannan magana ne akan abin da ya faru bayan labari da ya sa da abin da ya auko da cikin labarin da kanta.
"rihoton Yesu ya yaduwa" ko "mutane sun fara yada labari game da Yesu"
Wannan ya gabatar da sabuwar abu.
"Maman matar Siman"
Wanna ƙari ne da yake nufin " tana fama da"
"fata mai zafi ... zafi" ko "fata mai zafi ... ya tsautawa zazzabin"
Wannan na nufin sun tambaye Yesu ya warkar da ita daga zazzabin. AT: " tambaye Yesu ya warkar da ita daga zazzabin" ko "tambaye Yesu ya warkar da zazzabin ta"
Wannan kalmar "sai" ya nuna da cewa ya yi wannan sabo da mutanen sun roke shi a madadin surkuwan Siman.
"je gunta ya jingina da ita"
"ya yi wa zazabin magana mai tsanani, kuma ya rabu da ita" ko "ya umurce zazabin kuma ya bar ta, kuma ya yi." Zai zama da taimako ka faɖa abin da ya gaya wa zazabin ya yi. AT: "ya umurce fatan ta ya zama da sanyi, kuma ya yi" ko "ya umurce ciwon ta ya bar ta, kuma ya yi"
A nan wannan na nufin ta fara yin abinci wa Yesu da sauran mutanen dake gidan.
"ya sa hanunsa akan" ko "taba"
Ya nuna da cewa Yesu ya aljanu su bar mutanen dake da aljanu AT: "Yesu ya kuma sa aljanu su fito da ƙarfi"
Wannan na nufin abu ɗaya, kuma mai yuwa ya na nufin tsoro ko kuka ko hayshi. wasu masu juyin sun yi amfani da ajili ɗaya. AT: "iho" ko " ko kururuwa"
"ya yi magana mai ƙarfi wa aljanun"
"bai bar su ba"
"Da rana ya tashi" ko "Da ya faɗi"
"wurin hadama" ko "wurin da ba mutane"
"zuwa ga mutane da dama a wasu birane"
AT: "Wannan shine dalilin da Allah ya aiko ni"
Tunda Yesu ya na Galili, kalmar nan "Yahudiya" na nufin yankin da Yahudawa suke zaune a waccan lokacin gabaɗaya. AT: "inda aYahudawa suke zaune"
1Ya zama sa'adda mutane sun taru a wurin Yesu suna sauraron maganar Allah, yana kuma yana tsaye a bakin tabkin Janisarata. 2Ya ga jiragen ruwa biyu tsaye a bakin tabkin. Masu kamun kifin kuwa sun fita daga cikin jiragen suna wanke tarunsu. 3Yesu ya shiga daya daga cikn jiragen wanda shike na Bitrus ne, sai ya umarce shi ya dan zakuda da jirgin daga bakin tabkin kadan zuwa cikin ruwa. Sai ya zauna ya kuma koya wa mutane daga cikin jirgin.4Da ya gama magana, ya ce wa Siman, "Zakuda jirgin zuwa wuri mai zurfi sa'annan ka zuba tarunka domin kamu." 5Siman ya amsa ya ce, "Ubangiji, mun yi aiki dukan dare bamu kama komai ba, amma bisa ga maganarka, zan jefa tarun." 6Da sun yi haka, suka kama kifaye da yawan gaske, har tarunsu suna yagewa. 7Sai suka roki abokan aikinsu da ke a dayan jirgin su zo su taimake su. Suka zo sun cika jiragen biyu da kifaye, har suka fara nutsewa.8Amma Siman Bitrus, da ya ga haka, ya russuna a gaban Yesu, yana cewa, "Ka rabu da ni Ubangiji, gama ni mai zunubi ne." 9Domin ya yi mamaki, da dukan wadanda suke tare da shi, sabili da yawan kifaye da suka kama. 10Wannan ya hada da Yakubu da Yahaya 'ya'yan Zabadi abokan aikin Siman. Sai Yesu ya ce wa Siman, "Kada ka ji tsoro, domin daga yanzu, za ka kama mutane." 11Da sun kawo jiragensu waje kan kasa, suka bar komai suka kuma bi shi.12Sa'adda yana daya daga cikin biranen, wani mutum dauke da kuturta yana nan wurin. Da ya ga Yesu, ya fadi bisa fuskarsa kasa yana rokansa, yana cewa, "Ubangji, idan ka yarda, za ka iya tsarkake ni." 13Yesu ya mika hanunsa ya taba shi, yana cewa, "Na yarda. Ka tsarkaka." Sai nan da nan, kuturtar ta rabu da shi.14Ya umarce shi kada ya gaya wa kowa, amma ya ce ma sa, "Tafi ka nuna kanka ga firist sa'annan ka mika hadaya domin tsarkakewarka, kamar yadda Musa ya umarta, a matsayin shaida a garesu."15Amma labarinsa ya bazu nesa, taron mutane da yawa kuma suka zo wurinsa domin su ji shi, su kuma samu warkarwa daga cututtukansu. 16Amma ya kan janye zuwa wuraren da babu kowa ya yi addu'a.17Ya zama daya a cikin kwanakin da yake koyarwa, akwai Farisawa da malaman attaura da ke zaune a wurin wandanda suka zo daga kauyukan da suke kewaye da Galili da Yahudiya da kuma birnin Urushalima. Ikon Ubangiji yana tare da shi domin warkarwa.18A lokacin nan, wasu mutane suka zo dauke da wani mutum shanyayye a kan tabarma, suka kuma nemi yadda za su shigar da shi ciki, su kwantar da shi a gaban Yesu. 19Ba su iya samun hanyar da za su shigar da shi ba saboda taron, sai suka hau saman gidan, suka saukar da shi daga rufin, a kan tabarman sa, zuwa tsakiyar mutanen, dai dai a gaban Yesu.20Da ya ga bangaskiyarsu, Yesu ya ce, "Maigida, an gafarta zunubanka." 21Marubuta da Farisawa suka fara sukar wannan, suna cewa, "Wanene wannan da ke sabo? Wa zai iya gafarta zunubi, idan ba Allah kadai ba?"22Amma da Yesu ya fahimci abin da suke tunani, sai ya amsa ya ce masu, "Don me kuke sukar wannan a zuciyarku? 23Wanne ne ya fi sauki a ce, 'An yafe zunubanka' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya?" 24Amma domin ku sani cewa Dan Mutum yana da yancin gafarta zunubai a duniya, na ce maka, 'Tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidanka.'"25Nan take, ya tashi a gabansu ya dauki tabarma da yake kwance; sai ya koma gidansa, yana daukaka Allah. 26Kowa yana ta mamaki kuma suka daukaka Allah. Suna cike da tsoro, suna cewa, "Yau mun ga abubuwan al'ajibi."27Bayan wadannan abubuwa sun faru, Yesu ya fito daga can sai ya ga wani mai karban haraji mai suna Lawi yana zama a wurin karban haraji. Ya ce masa, "Ka biyo ni." 28Sai Lawi ya bar komai, ya tashi, ya bi shi.29Lawi kuma ya shirya gagarumar liyafa a gidansa, kuma akwai masu karban haraji da yawa a nan, da wasu mutane da ke zama a gaban teburin liyafar suna cin abinci tare da su. 30Amma Farisawa da Marubuta suka fara korafi ga almajiransa, suna cewa, "Don menene kuna ci da sha tare da masu karban haraji da mutane masu zunubi?" 31Yesu ya amsa masu, "Masu lafiya basu bukatar likita, wadanda ke marasa lafiya kadai ke bukatar likita. 32Ban zo domin kiran masu adalci ba, amma na zo ne domin kiran masu zunubi zuwa ga tuba."33Sun ce masa, "Almajiran Yahaya sukan yi azumi da addu'a, kuma almajiran Farisawa ma sukan yi haka. Amma almajiranka suna ci suna sha?" 34Yesu ya ce masu, "Akwai wanda zai sa abokan ango su yi azumi, a lokacin da shi ango yana tare da su? 35Amma kwanaki na zuwa wadanda za a dauke ango daga wurinsu, a kwanakin za su yi azumi."36Sai Yesu ya sake fada masu wani misali. "Babu wanda zai yage kyalle daga sabuwar tufa, ya kuma yi amfani da ita ya dinka tsohuwar tufa. Idan ya yi hakannan, zai yage sabuwar tufar, kuma kyallen daga sabuwar tufar ba zai dace da kyallen tsohuwar tufar ba.37Kuma, babu mutum da zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsofafin salkuna. Idan ya yi haka, sabon ruwan inabin zai fasa salkunan, kuma ruwan inabin din zai zube, salkunan kuma za su lallace. 38Amma dole ne a sa sabon ruwan inabi a sabobin salkuna. 39Babu wanda zai yi marmarin sabon ruwan inabi bayan da ya sha tsohon, gama zai ce, "Tsohon ya fi sabon."
Yesu ya yi wa'azi daga daga cikin jirgin ruwan Siman da ake kira Bitrus a bakin tabkin Janisarata.
Wannan sashin an yi amfani da shi a nan domin a sa alama a sabuwar abin da ya auko a labarin. Idan yaren tana da wata hanyar yin haka, zai ku yi amfani da shi a nan.
Ma'ana mai yuwa 1) "sauraron maganar da Allah yake so su ji" 2) "sauraron sakon Yesu game da Allah"
Wannan kalmar ya na nufin tabkin Galili. Galili ya na yanman cin tebkin, ƙasa Janisarata yana gefen gabas, sabo da haka ana kira da dukkan sunan. Wasu juyin turanci suna ne daidai na jikin ruwa, tabkin Janisarata."
Suna wanke tarusu fifayen su domin su yi amfani da su su kama kifi.
"jirgin ruwan Bitrus"
"ya ce ma Siman ya matsar da jirgin ruwan nesa da ɠaban tekun"
Zama, zama matsayi na al'ada ga malami.
"ya koya wa mutane sa'anda ya zauna a jirgin ruwa." Yesu ya na jirgin ruwa nisa kaɗan daga tukun kuma yana magana da mutanen wanda suke a ɠaban tekun.
"da Yesu ya gama koya wa mutanen"
"domin ka gaya mini in yi haka"
Suna nesa da tekun su yi kira, sai suka yi motsi jiki mai nuna abin da yake zuciya, mai yuwa t awurin ƙamumin ruwa da hannayen su.
"kwalekwalen ya fara nutsewa." dalilin za'a iya faɗa ba shakka. AT: "kwalekwalen ya fara nutsewa domin domin kifin ya yi nauyi"
Ma'ana mai yuwa 1) "ya russuna a gaban Yesu" ko 2)durkusa a tafin Yesu" 3) bai faɗi ba da gangan ba . ya yi haka kamar alaman tawali'u da ban girma wa Yesu.
Wannan kalmar a nan "mutum" na nufin "gimshiƙeƙƙen namiji" ba kuma gada ɗaya "mutanen."
"kifaye masu yawa"
"abokin hurɗar Siman a kasuwancin kifi"
an yi aiki da hoton kama kifi a nan kamar misali na tara mutane su bi Almasihu. AT: "zaku kama mutane" ko "zaku tara mini mutane" ko "zaku kawu mini mutane su zama al'majerai na"
Wannan sashin ya sa alaman sabuwar abu a labarin.
"mutum da kuturta ya rufe shi." Wannan ya gabatar da sabuwar hali a labarin.
A nan "fadi bisa fuskarsa" ƙari ne da yake nufin ya durkusa ƙasa. AT: " ya daukusa ya taba ƙasa da fuskar sa" ko "ya durkusa a ƙasa"
"idan ka na so"
An gane da cewa ya na so Yesu ya warkar da shi. AT: "Dan Allah ka tsarkakeni, domin zaka iya"
Wannan na nufin tsarkake nz al'ada, amma an gane bai da tsarkake domin kuturta tan sa. AT: "warkar da ni daga kuturta na domin in zama da tsarki ... in warke"
"ba shi da kuturka kuma"
Wannan za'a iya juya shi kamar magana na kai tsaye: kada ka gaya wa kowa" Wannan tambayan na nuna cewa za'a iya baiyana shi
Dokan ya buƙatar mutum ya yi hadaya na musamman bayan da ya warke. wannan ya bar mutumin ya zama tsarkakke, kuma ya sami damar sake sa kai ga harkokin addini na al'ada.
"kamar hujja na warkas su warka"
Ma'ana mai yuwa 1) "zuwa ga firist" ko 2) "zuwa ga mutane."
"labari game da Yesu." Wannan zai iya zama ko "rehoto game da Yesu ya warkar da mutumin daga kuturka" ko "rehoto Yesu ya warkar da mutane."
" labarinsa ya bazu nesa zuwa gaba." AT: "mutane sun cigaba da bada labarin shi a wasu wurare"
"wuraren da ba kowa" ko "wuraren da ba wasu mutane"
Wadannan ne mutanen da suke labarin. mai yuwa yaren ku suna da hanyar nuna cewa wadannan sabobin mutane ne.
gammon barci ko gado ko gadon daukar mara lafiya
"ba zai iya masar da kansa ba"
A wasu yaren mai yuwa zai zama na halita aa sake wannan umurnin. AT: "Amma domin taron mutanen, ba za su iya samun hanyar da za su iya shigar da shi ciki ba. Sai"
Yana da sauƙin ganewa da cewa dalilin da ya sa basu iya shiga ba shi ne taron ya yi babba har babu ɗaki domin su.
Gidaje yana da kitan jinka, kuma wasu gidajen suna da matakala ko mataki a waje domin ya zama masu d asauki su hau sama. AT: "sun hau saman kitan jinkan gidan"
"daidai a gaban Yesu" ko "nan da nan a gaban Yesu"
An gane da cewa sun bada gaskiya Yesu zai warkar da shanyyayen mutumin. AT: "Da Yesu ya gane cewa sun ba da gaskiya cewa zai warkar da mutumin, ya ce masu"
Wannan kalma ne nagaba ɗaya da mutane suke amfani da shi sa'anda suke magana da mutum wanda basu san sunar sa ba. ba rashin ladabi bane, kuma bai nuna wani ba da girma na musamman ba.wasu yaren mai yuwa za su iya aiki da kalma kaman "aboki" ko "laƙabin girma."
AT: "an yafe maka" ko "Na yafe maka zunubinka"
"tattauna wannan" ko "yi tunani akak wannan." Abin da suka yi tambayan za'a iya faɗa. AT: "sun yi magana akan ko Yesu yana da iko ya yafe zunubai"
Wannan tambayan ya nuna yadda suka yi mamaki da haushi game da abin da Yesu ya faɗa. Wannan za'a iya rubuta shi kamar bayani. AT: "Wannan mutumin yana sabo ga Allah!" ko "Yana sabo ga Allah da faɗan haka!"
Wannan ya nuna da cewa idan mutum ya ce yana gafarta zunubi yana cewa shi Allah ne. Wannan za'a iya rubuta kamar bayani mai sauƙin ganewa. AT: "zai iya gafarta zunubi, idan ba Allah kadai !" ko "Allah ne kadai wanda zai iya yafe zunubi!"
Wannan sashin ya nuna da cewa suna tunani mai shuru, sai Yesu ya gana maimakon ya ji abin da suke tunani.
Wannan za'a iya rubuta shi kamar bayani. AT: "Kada ku yi gardama da wannna a zuciyar ku." ko "Kada ku yi shakka da cewa ina da iko in gafarta zunubi."
A nan "zuciya" misali ne na hankalin mutane ko cikin mutum.
Yesu ya yi amfani da tambaya ya sa marubutan su yi tunani akan abin da zai hakikanta ko zai iya ko ba zai iya yafe zunubia ba. AT: "Na faɗa ne kawai 'An yafe maka zunuban ka.' Zaku yi tunani da cewa yana da wuya a faɗa 'Ta shi ka yi tafiya,' domin hakikantan cewa zan warkar da mutumin zai nuna idan ya tashi ya yi tafiya ko in bai tashi ba." ko "Zaku yi tunani da cewa ya na da sauƙi a ce 'An yafe maka zunuban ka' da a ce Tashi ka yi tafiya."
Ilan maganar da ba 'a yi ba shi na abu ɗaya "ya na da saui a ce domin ba wanda ya san abin da ya faru," amma ɗayan aun shi ne "da wuya a faɗa domin kowa zai san abin da ya faru." mutane ba za su san in a yafe wa mutum zunubia ba, amma duk za su sani idan an warkar da shi ya tashi ya yi tafiya.
Yesu ya na magana da Farisawa da marubutan. Wannan kalmar "kai" jam'i ne.
Yesu yana nufin kansa.
Yesu ya na faɗan wannan wa shanyyeyen mutumin. Wannan kalmae "kai" mafuradi ne.
"a take ya tashi" ko "nan da nan ya tashi"
Zai zama da taimako ka faɗa ba shakka da cewa ya warke. AT: "mutumin ya warke!ya tashi"
"tsoro sosai" ko cike da fargaba"
"abubuwan ban mamaki" ko "sabobin abubuwa"
sashin "wadannan abubuwa" na nufin abin da ya faru a ayoyin ɗaya wuce. Wannan ya nu na sabuwar abu.
"dubi mai karban haraji da kulawa" ko dubi mai karban haraji a hankali"
ka "bini" wani ya zama al'majerin mutumin. AT: "ka zama al'majeri na" ko "zo, ka bini a masayin malamin ka"
"ya bar aikin sa a masayin mai karban haraji"
"a gidan Lawi"
Hanyar cin abincin Gareka a biki shi ne a kwanta a gado a madogari kanka sama da hanun hagu akan wasu filo. AT: "cin abinc tare" ko "cin abinci akan taburin"
"wa al'majeren Yesu"
Farisawa da marubutan suka yi wannan tambayan su nuna rashin yardan su da almajeren Yesu da cewa suna cin abinci da masu zunubi. AT: "Kada ku ci abinci da masu zunubi!"
Farisawa da marubutan sun yarda da cewa mutanen addini su raba kansu da masu zunubi. Wannan kalmar "ku" jam'i ne.
Yesu ya yi amfani da ƙarin magana ya fara gaya masu ya kira masu zunubi su tuba kamar yadda likita suke kiran marasa lafiya su warke.
likita
za ka iya kara abin da aka cire. AT: "marasa lafiya kadai suke nemam likita"
Wasu mutane suna tunanin cewa suna da adalci. Yesu ya yi nufin su kamar yadda suke tunani ko da shike ya sani cewa ba su da adalci. AT: "mutanen da suke tunanin cewa suna da adalci"
"Shugabanen adinin sun cewa Yesu"
Yesu ya yi amfani da wannan tambayan domin ya sa su su yi tunani game da yanayin da sun sani. Wannan za'a iya rubuta shi kamar bayani. AT: "Akwai wanda zai sa abokan ango su yi azumi, a lokacin da shi ango yana tare da su"
"baki" ko "abokai" Wannan abokai ne wadanda suke yi murna da wanda yake yin aure.
Azumi alamar bakin ciki ne. shugabanen adini sun gane da cewa abakan ango ba za su yi azumi ba sa'anda angon yana tare da su.
"kusa" ko "wata rana"
Yesy ya na kwatanta kan sa da angon, al'majeren kuma abokan angon. juyawa ya bayana shi idan ya zama dole.
Yesu ya gaya wa Farisawa da marubutan labari wadanda suke gidan lawi.
babu wanda zai girbe ... yi amfani ... shi ... shi" ko "mutane kada su yage ... yi amfani ... su... su"
gyara
Wannan bayanin yana yin da ba'a gani ba ya rega ya bayana dalilin da mutum ba zai gyara rega a waccan hamyar ba.
"ba zai hadu ba" ko "ba zai zam daidai ba kamar"
"ruwan inabi." Wannan ya na nufin ruwan inabi da bai tashi.
Wadannan jaka ne da aka yi da fatar dabba. Za'a iya kiran su "jakar ruwar inabi" ko "jakar da aka yi da fata."
sa'anda sabuwar ruwan inabin ya tashi kuma ya karu. zai fashe tsohowar fatar domin ba za su iya mikewa kuma ba. ma su sauraron Yesu sun gane bayanin game da ruwan inabi da ya tashi kuma ya karu.
AT: "ruwan inabin zai zuba daga cikin jakan"
"sabon fatar ruwan inabin" ko sabuwar jakan ruwan inabin." Wannan na nufin sabon fatar ruwan inabin, da ba'a yi aiki da shi ba.
Wannan misalin ya haɗa tsohowar koyas su wan shugabanen addinin akan sabuwar koyasuwan Yesu. maganar shi ne mutanen da suka saba da tsohowar kayasuwan ba su yarda su ji sabuwar kayasuwan da Yesu ya na koyarwa.
"ruwan inabi da ya tashi"
Zai zama da taimako ka kara: kuma baya so ya gwada sabuwar ruwan inabi"
1Ana nan wata Asabaci Yesu yana ratsawa cikin gonar hatsi, almajiransa kuma na karyar zangarkun hatsin, suna murtsukawa a hanayensu suna ci. 2Amma wasu daga cikin Farisawa suka ce, "Saboda me kuke yin abin da bai halatta a yi a ranar Asabaci ba?"3Yesu ya amsa masu, ya ce, "Ba ku karanta abin da Dauda ya yi a lokacin da yake jin yunwa ba, shi da mutanen da ke tare da shi? 4Ya je cikin gidan Allah, ya dauki gurasar alfarwa ya kuma ci daga ciki, ya kuma ba mazajen da ke tare da shi su ci, ko da shike ya halarta ga Firistoci ne kadai su ci." 5Sai ya ce masu, "Dan Mutum shi ne Ubangijin asabaci."6Ya kasance a wata ranar Asabaci ya shiga cikin majami'a ya kuma koya wa mutane a can. Wani mutum na can wurin wanda hannun damansa ya shanye. 7Marubuta da Farisawa na kallonsa su ga ko zai warkar da wani a ranar Asabaci, domin su samu dalilin zarginsa da yin abin da bai cancanta ba. 8Amma ya san abin da suke tunani, sai ya ce wa mai shanyeyen hannun, "Tashi, ka tsaya a nan tsakiyar jama'a." Sai mutumin ya tashi ya tsaya a nan.9Yesu ya ce masu, "Ina tambayar ku, ya halatta a ranar Asabaci a yi nagarta ko mugunta, a ceci rai ko a hallaka shi? 10Sai ya dube su duka, ya kuma ce wa mutumin, "Mika hannunka." Ya yi haka, sai hannunsa ya koma lafiyayye. 11Amma suka fusata kwarai, suka yi shawara da junansu game da abin da za su yi da Yesu.12Ya zama a kwanakin nan, ya hawo bisan dutse domin ya yi addu'a. Ya ci gaba dukan dare yana addua'a ga Allah. 13Da safiya ta yi, ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya kuma zabi goma sha biyu daga cikinsu, wadanda ya kira su "Manzanni."14Sunayen Manzannin sune Siman (wanda ya kuma kira Bitrus) da dan'uwansa, Andrawus, Yakubu, Yahaya, Filibus, Bartalamawus, 15Matta, Toma, Yakubu dan Halfa, Siman, wanda ake kira Zaloti, Yahuda dan Yakubu, 16da Yahuda dan Iskariyoti, wanda ya zama maci amana.17Sai Yesu ya gangaro daga dutsen tare da su, suka kuma tsaya a sarari. Almajiransa da yawa na nan a wurin, tare da mutane da yawa daga Yahudiya da Urushalima, da kuma bakin tekun Taya da Sidon. 18Sun zo domin su ji shi, da kuma su sami warkarwa daga dukan cututukansu. Mutane waddan da ke fama da kazaman ruhohi ma sun sami warkarwa. 19Dukan taron jama'ar suna kokarin su taba shi domin ikon warkarwa yana fitowa daga wurinsa, ya kuma warkar da su duka.20Sai ya dubi almajiransa ya ce, "Masu albarka ne ku matalauta, gama Mulkin Allah naku ne. 21Masu albarka ne ku masu yunwa yanzu, domin za a kosar da ku. Masu albarka ne ku masu kuka a yanzu, domin za ku yi dariya.22Masu albarka ne ku idan mutane sun ki ku, suka nuna maku wariya suna mai da sunayen ku na mugunta, domin Dan Mutum. 23Za ku yi farin ciki a ranan nan kuna tsalle domin murna, domin hakika za ku samu lada mai girma a sama, domin haka kakannin-kakannin su suka yi wa annabawa.24Amma kaitonku mawadata! Domin kun rigaya kun samu ta'aziyar ku. 25Kaitonku kosassu a yanzu! Domin za ku ji yunwa nan gaba. Kaitonku masu dariya yanzu! Domin za ku yi makoki kuna kuka nan gaba.26Kaiton ku idan kowadanne mutane suna yabon ku! Domin haka kakannin-kakanninsu suka yi wa annabawan karya.27Amma ina ce maku ku masu saurare na, ku kaunaci magabtanku, ku kuma aikata nagarta ga wadanda suke kinku. 28Ku albarkaci masu zaginku, ku kuma yi addu'a ga wadanda suke wulakanta ku.29Wanda ya mare ku a wannan kunci, ku juya masa dayan. Idan wani ya dauki mayafinka, kada ka hana masa taguwarka. 30Ku bayar ga duk wanda ya roke ku. Idan wani ya dauki wani abu da ke naku, kada ku bidi ya mayar da shi.31Duk abin da kake so mutane su yi maka, ka yi masu hakan nan. 32Idan ka kaunaci masoyan ka ne kadai, me wannan zai amfane ka? Ko masu zunubi ma na kaunar masoyan su. 33Idan kuna nuna alheri ga wadan da ke maku alheri kadai, menene ladan ku a nan? Ko masu zunubi ma na yin hakan nan. 34Idan kun ba da rancen abubuwa ga mutanen da kuna sa zuciya zasu mayar maku ne kadai, menene ribar ku a nan? Ko masu zunubi suna ba masu zunubi rance, suna kuma sa zuciya a mayar masu dadai gwargwado.35Amma ku kaunaci magabtan ku, ku kuma nuna masu alheri. Ku basu rance, kada ku sa zuciya a maido maku, kuma sakamakon ku zai zama da girma. Za ku zama yayan Mafifici, domin shi da kansa yana nuna jinkai ga marasa godiya da miyagun mutane. 36Ku zama masu jinkai, domin Ubanku mai jinkai ne.37Kada ku shari'anta, kuma ba za a shari'anta ku ba. Kada ku kayar, ku ma ba za a kashe ku ba. Ku yafe wa wasu, kuma za a yafe maku.38Ku bayar ga wasu, ku ma za a ba ku da yawa. Magwaji dankararre, girgizajje har ya cika yana zuba, za su zuba har cinyarku. Domin duk ma'aunin da ku ka yi amfani da shi, da shi za a auna maku.39Sai ya sake basu wani misali, "Makaho yana iya yi wa makaho jagora? Idan ya yi haka, dukansu biyu za su fada cikin rami, ko ba haka ba? 40Almajiri baya fin Malaminsa, amma duk wanda ya samu horo sosai zai zama kamar malaminsa.41Don me kake duba dan hakin da ke a idon dan'uwanka, amma ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba? 42Don me za ka ce wa dan'uwanka, 'Dan'uwa, bari in cire dan hakin da ke a idonka', bayan kai da kanka ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen da ke a idonka, sa'annan za ka gani da kyau yadda zaka cire hakin da ke a idon dan'uwanka.43Domin babu itace mai kyau da ke haifar rubabbun 'ya'ya, ko rubabben itace da zai haifi kyawawan 'ya'ya. 44Domin ana iya sanin ko wani itace ta wurin 'ya'yan da yake bayarwa. Domin mutane basu kan tsinki 'ya'yan baure a jikin kaya, ko kuwa su dibi inabi daga jikin sarkakkiya.45Mutumin kirki, daga wadatar zuciyarsa ya kan ba da yaya masu kyau, kuma mugu daga cikin muguwar ajiyar zuciyarsa yake aikata mugunta. Domin daga cikar zuciyarsa ne bakinsa yakan yi magana.46Don me kuke ce da ni, 'Ubangiji, Ubangiji', amma ba ku yin biyayya da magana ta? 47Duk wanda ya zo wurina ya ji kalmomina ya kuma yi biyayya da su, zan gaya maku yadda yake. 48Yana kama da mutum da ke gina gida, wanda ya haka da zurfi zuwa cikin kasa ya kuma gina harshashin gidan sa a kan dutse. Da rigyawa ta zo, sai ruwa ya buga gidan, amma bai iya girgiza shi ba, domin an gina shi da kyau.49Amma duk mutumin da ya ji kalmomina ya kuma ki biyayya da su, yana kamar mutum wanda ya gina gidansa a kan kasa, babu harshashi. Amma da ambaliyan ruwa ta buga gidan, nan take ya rushe, ragargajewar gidan kuma da girma take.
sa'anda Yesu da al'majeren sa suke tafiya a gonar hatse, wasu Farisawa sun fara tambayan al'majeren game da abin da suke yi a ranar Asabaci, Wamda a dakar Allah an keɓe shi wa Allah.
Wannan kalmar "kai" anan jam;i ne, kuma ya na nufin al'majerensa.
Wannan sashin an yi amfani da shi anan domin a sa alama a sabuwar abin da ya auko a labarin. Idan yaren ku na da wata hanya na yin haka za ku iya amfani da shi anan.
a A wannan yana yi, akwai babbar gona wanda mutane suka wasa irin alkama domin ya yi girma.
Wannan shi ne sashi mafi sama na shukar hatsi, wanda shi ne irin babbar ciyawan. Ya rike nunannen, irin shukar mai ciyuwa.
Suna yin haka domin su raba irin hatsin. Wannan za'a iya bayyana shi ba shakka. AT: "Suna murtsukawa a hanayensu domin su raba hatsin daga ƙaiƙayin"
Sun yi wannan tambayan domin su zaigi al'majeren cewa suna ƙarya doka. za'a iya rubuta shi kamar bayyani. AT: "tsinan hatsi ranar Asabaci gana gaba da dokar Allah!"
Farisawan dubi karamin aikin murtsukawa a hanu ciki da hatsi aikin da ba na doka ba. Wannan za'a iya bayyana shi ba shakka. AT: "yin aiki"
Yesu ya kwaɓe Farisawan domin sun ki su koya daga lattafi. Wannan za' iya rubuta kamar bayyani. AT: "ku koya da ga abin da kuka karanta ... shi!" ko "ba shakka kun karanta ... shi!"
"gurasa mai tsarki" ko "gurasan da aka mika wa Allah"
Yesu ya na nufin kansa. Wannan za'a iya bayyana: AT: "Ni, Dan Mutum"
sunar "Ubangiji" anan ya yi nauyin bisa Asabaci. AT: "yana da iko ya yarda wa mutane abi da za su yi a ranar Asabaci!"
Wannan sashin an yi amfai da shi anan domin a sa alama akan sabuwar abin da ya aukoa labarin.
Wanna ya gabatar da sabuwar hali a labarin.
hanun mutumin ya bace a wata hanya da ba zai iya mikar da shi ba. mai yuwa ya lankwashekusan dunkulallen, ya zama karami da tamoji.
"suna kallon Yesu a hankali"
"domin suna so su samu"
"a gaban jama'a." Yesu yana so mutumin ta tsaya a wurin da jama'ar zasu gan shi.
"ma Farisawan"
Yesu ya yi tambaya domin ya sa farisawan su yarda da cewa ya yi daidai ya warkar a ranar Asabaci.niyar tambaya ba domin a ba shi amsa bane: ya sasu su yarda ne cewa duk sun sani gaskiya ne a maimakon ya sami bayyani. ko da shike Yesu ya ce, Na tambaye ku," saboda haka wannan tambayan ba kamar sauran tambayan da ba su bukatar amsa bane wanda suna so a juya su kamar bayyani. a juya su kamar tambaya. :
"ka taimaki wani ko ka hallakar da wani"
"rike hannun ka waje" ko "Mika hannun ka"
warke
Wannan sashin an yi amfani da shi anan domin a sa alama a sabuwar abin da ya auko a labarin.
"a kusa da lokacin" ko "bada daɗewa ba bayan" ko wata rana kusa da"
"Yesu ya je waje"
da safiya ta yi" ko "rana ta gaba"
"ya zabi al'majerensa goma sha biyu"
"wanda ya zamar da su manzanni" ko ka kuma sai ya zaɓe su su zama manzanni"
Luka ya rubuta tsarin sunayen manzannin. UDb ya yi amfani da wannan kalmar ya gabatar da tsarin.
"dan'uwan, Siman"
Ma'ana mai yuwa 1) "Zaloti suna ne wanda ya nuna da cewa ya na cikin sashin kungiyan da suka so su saki mutanen Yahudawa daga mulkin Romawa. AT: "yan kishin ƙasa" ko "yan ƙasar" ko 2) "Zaloti kwatancen da ya nuna cewa ya na da himma wa Allah ya sami daraja. AT: "mai so na kwaria"
Zai zama dole ka bayyana me "cin amana" yake nufi a wannan mahallin. AT: "ba she abokin sa" ko "ba da abokin sa ga makiyan sa" (yawanci a maimakon kuɗi a biya) ko "bijirar abokin sa ga hadari game da gaya wa makiyan game da shia"
"da sha biyun da ya zaba" ko "da al'majeren sa gama sha biyu"
AT: "Yesu ya warkar da su"
AT: "Yesu ya kuma warkar da mutane wanda suke fama da kazaman huhohi"
"mugun ruhohi ke damum su" ko "sarrafa da mugayen ruhohi"
"ya na da iko ya warkar da mutane" ko "yana amfani da ikon sa ya warkar da mutane"
Wannan sashin an maimaita shi sau uku. kowanni lokaci,ya nuna da cewa Allah ya bawa yarda ga wasu mutane ko yana yin su na da kyau ko mai yaƙani.
"Kumatalauta ku karɓe yardar Allah2 ko "Ku d akuke matalauta amfane"
Yaren da basu da kalma na mulkin za su iya cewa, "Allah ne mulkin ka" ko "domin Allah ne mai mulkin ka."
"mulkin Allah naku ne." Wannan zai iya zama 1) "ku na mulkin Allag ne2 ko 2) "za ku sami iko a mulkin Allah."
"za ku yi dariya da farinciki" ko "za ku zama masu murna"
"ki ku"
"domin kun hada kai da Dan Mutum" ko "domin su ki Dan Mutum"
"sa'anda suka yi wadannan abubuwan" ko "sa'anda ya faru"
Wannan ƙarin na nufin "yi marna sosai"
"babban biya" ko "kyautuna masu kyau"
"yada zai zama maku" Wannan sashin ya sake maimaitawa sau uku. kashiyar Allah ya sa maku albarka ne." kowanne lokaci, ya nuna da cewa hushin Allah ya na kanku daidai, ko da cewa wani abu mai kyau ko mumuna na jeran ku.
"yadda zai zama maku ku masu kuɗi" ko "damuwa zai zu maku ku masu kuɗi"
"abin da zai yi na ku ta'aziyar" ko "abin da zai biya maku bukata" ko abin da zai saku murna"
wanda cikin su ya cika yanzu" ko " wanda sun ci sosai"
"Wanda suke murna yanzu"
Anan "mutane" an yi amfani da su ma'ana danginsu hada da dukkan mutane. AT: "sa'anda kowanne mutum ya yi magana" ko "sa'anda kowa ya yi magana"
"kakannin-kakanninsu sun yi magana da kyau game da annabawan karya"
Yesu yanzu ya fara yi wa dukkan taron magana,a maimakon al'majerensa kadai.
kowanne umurnin ya ka mata acigsbs da bi,bana lokaci daya ba.
Wannan bai yi nu fin cewa su kaunaci magabtan su kadai ba ba abokan su ba. Wannan za'a iya bayyana. AT: kaunaci magabtan ku, ba abokan ku kwai ba"
Wannan sashi biyun na nufin abu ɗaya, kuma tare yake yin nauyin aya.
Allah ne wanda zai yi albarku. Wannan za'a iya bayyana. AT: "tambayi Allal ya albarkaci wadanda"
"wadanda suka zage ku akidar"
"wadanda suka wulakanta ku akidar"
"Idan wani ya buga ku"
"a gefen fuskan ku"
Zai zama da taimakoa ce ma harin zai yi wamutumin. AT: "juya fuskar ka saboda yamare ka a ɗayangefen kuncinkuma"
"kada ka hana shi daga dauka"
Idan kowa ya tambaye ka abun, ka ba shi"
"kadaku nemi ya bayar" ko "kada ku bukata ya bayar"
A wasu yareuka zai iya zama na halita a juya wannan umurnin. AT: "Duk abin da kake so mutane su yi maka, ka yi masu hakan nan" ko "yi wa mutane yadda ka ke so a yi maka"
"wani lada za ka karba?" ko "wani yaba za ka masu don yin haka?" baza ka barbi wani lada don yin haka ba." ko "Allah ba zai baka lada don yin haka ba."
Dokan Musa ya umurci Yahudawa kada su karbi riba akan kuɗin rancen da kuka ba wa juna.
kada ku sa zuciya a maido maku
"kada ku sa zuciya mutumin ya maido maku abin da kuka ba shi" ko "kada ku sa zuciya mutumin ya baku komai"
" za ku karbe babban sakamako" ko "zaku karbe biya mai kyau" ko "zaku sami kyau ta masu kyau sabo da shi"
Zai fi kyau ka juya" 'ya'yan" da kalma iri ɗaya yarenku zasu iya nufin cewa yaron mutum ne ko ɗa.
ya zama na cewa kalmar nan "ya'ya" jam'i ne domin kada a rikice da sunar Yesu "Dan Mafifici."
"mutanen da ba su yi masa godiya ba kuma mugaye ne"
Wannnan na nufin Allah. zai fi kyau a juya "Uba" da kalaman da yaren ku suke anfani da shi ga uban mutum.
"Kada ku shari'anta mutane" ko "kada ku zargi mutane mummunan"
"domin sakama kon ku"
Yesu bai fada wanda ba za'a shari'anta ba. Ma'ana mai yuwa 1) "Allah ba zai shari'anta ka ba" ko 2) "ba wanda zai shari'anta ka"
"Kada ku hukunta mutane"
Yesu bai fada wanda ba za'a hukunta ba. Ma'ana mai yuwa 1) "Allah ba zai hukunta ka ba" ko 2) "ba wanda zai hukunta ka"
Yesu bai fada wanda zai yafe ba. Ma'ana mai yuwa 1) "Allah zai yafe ku" ko 2) "mutane za su yafe maku"
Yesu bai fada asalin wanda zai bayar ba. Ma'ana mai yuwa 1) "wani zai baka" ko 2) "Allah zai baka"
Yesu ya yi magana ko a kak Allah ko mutane suna bayar karaminci kamar yana magana akan mai say da sayar da karimi hatsi. AT: "Allah zai zuba maku a cinyar ku karimi iya yawan kuɗi- dankararre girgizajje har ya cika yana zuba" ko "Kamar mai say da sayar da karimi hatsi wanda ya dankare hatsin ya girgizajje su tare kuma ya hatsi sosai hay rana zuba, za'a baku karaminci"
"babban kuɗi"
Yesu bai fada asalin wanda zai auna maka ba. Ma'ana mai yuwa 1 ) "za'a auna maku" ko "Allah zai auna maku"
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya sa mutanen su yi tunani wani abun da sun riga sun sani. Wannan za'a iya rubu ta kamar bayyani. AT: "dukka mun sani da cewa makaho ba zai iya yi wa makaho jagora ba."
Mutum wanda baya gani "makaho" misali ne na mutum wanda ba'a taba koya masa ba kamar al'majeri.
wasu yaren za su so, "Idan wani ya yi."wanna abu mara ma'ana ne wanda zai ba mutum dariya yana yin da ba zai iya faru ba.
Wannan za'a iya rubuta shi kamar bayyana. AT: "dukkan su zasu fadi a rami"
"Almajiri baya fin Malaminsa." Ma'ana mai yuwa 1) " Al'majeri ba ya yin ilimi fiya ea malaminsa" ko 2) "Al'majeri ba shi da iko mafi yawa fiye da malaminsa."
"kowani al'majeri wanda aka horas da shi da kyau" ko "kowani al'majeri wanda malaminsa ya koya masa"
Yesu ya yi amfani da tanbaya domin ya tsokane mutanen su kasa kunne ga zunuban su kamin su kasa kunne ga ga zunuban wasu. AT: "gungume da ke idanun ku."
Wannan misali na nufin mutane laifi mara muhimmanci na yan'uwa masubi.
"ɗigo" ko "tsage" ko "kura da ƙadan." yi amfani da ƙaramin abu da yawanci ya ke faɗiwa a idanuwan mutane.
Anan "dan'uwa" na nufin yan'uwa masubi Yahudawa ko yan'uwa masubi a cikin Yesu.
Wannan masalin ne na laifin mutum mafi muhimmanci. gungume ba na zahiri ba ne ya shiga idon mutum. Yesu ya yi furci domin ya yi nauyin mutum ya kasa kunne ga laifin sa mai muhimmanci kamin jiwa laifin wasu mutane mara muhimmanci.
"azara" ko "katako"
Yesu ya yi amfani da ya yi amfani da tambaya domin ya tsokane mutane su kasa kunne ga zunuban su kamin su kasa kunne ga zunubin wasu. AT: "Kada ka ce ... ido."?
Wannan domin babu." Wannan ya nuna da cewa abin da ya biyo baya dalili ne domi kada mu sharanta dan 'uwar mu.
"lafiyayen itace"
'ya'yan da suka bace ko mara kyau ko mara amfani
Mutane suna gane irin itace da 'ya'yan da take haifa. AT: "mutane suna gane irin itacen" ko "mutane suna gane itacen"
shuke ko ƙaramin itace mai ƙaya
inabi ko ƙaramin itace da yake da ƙayoyi
Wannan kalmar "kirki" anan na nufin adalci ko na halin kirki.
Kalmar nan "mutum" anan na nufin mutum, ma miji ko ta mace. AT: "mutumin kirki"
A nan tunanin mutum na kirki ana maganar sa kamar wadatar da aka yi ajiyar ta a zuciyar mutum, da "zuciya" misali ne na cikin ran mutum. AT: "abubuwa masu kyau da ya ajeye a cikinsa" ko "abubuwan da ya daraja mai yawa"
Haifar abin da ke da kyau misali ne na yin abin da ke da kyau. AT: "yi abin da ke da kyau"
A nan tunanin muguntar mutum an yi maganar sa kamar abubuwar mugunta ne aka ajiye a zucuyar mutum , kuma "zuciyarsa" misali ne na cikin ran mutum. AT: "abubuwar mugun ta da ya ajiye a cikin sa" ko "abubuwar mugun ta da ya daraja sosa"
A nan "zuciyz" misali ne na ran mutum ko cikin rai. sashin nan "bakinsa" misali ne na mutum gaba ɗaya. AT: "abin da yake tunani a zuciyar sa yana safar abin da bakin sa ya ke faɗa" ko "mutum zai yi magana da ƙarfi abin da ya daraja a cikin sa"
Maimaitawan wannan kalmar ya nuna da cewa yawanci suna kiran Yesu "Ubangiji."
Mai yuwa zai zama da kyau ba shakka a sake umurnin wannan bayanin. AT: "zan gaya maku yadda yake wanda ya ji magana na ya yi umurni da su"
tona tushin gidan sa da nisa sosai ya kai tushin a kan dutse." wasu al'adun ba su gane yin gini akan gadon dutse, kuma za su so su yi amfani da wata hoto domin wata tushi mai daɗi.
sashin gida da ya hada shi da ƙasa. Mutane a lokacin Yesu su na tuna zuwa cikin ƙasa zuwa kan dutse mai ƙaure sia su fara gini a kak dutse mai ƙaure. dutsen shi nn tushin.
gadom dutse." Wannan babab, dutse mai ƙarfi wanda yana ƙarƙashin ƙasa.
"ruwa mai gudu" ko "rafi"
"rushe akan"
Ma'ana mai yuwa 1) "ya sa shi girgiza" ko "rushe shi."
AT: "domin mutumin ya gina shi da kyau"
"Amma" nuna bambanci mai ƙarfi zuwa ga mutumin da aka yi maganar sa a baya wanda ya gina gidan da tushi.
Wa su al'adun ba su sani da cewa gida mai tushi ya fi ƙarfi. ƙarin bayani zai zama da taimako. aT: "amma bai tuna ƙasa da farko ya gina tushin"
faɗi ƙasa ko zo rabe
"waccan gidan ya rushe gaba ɗaya"
1Bayan da Yesu ya gama fadar dukan abubuwan da zai fadi a jin kunnen dukan mutanen, sai ya shiga Kafarnahum.2Bawan wani jarumi, wanda yake kauna, ba shi da lafiya har ma ya kusa mutuwa. 3Amma da ya ji labarin Yesu, jarumin ya aiki wadansu dattawan Yahudawa, ya ce a roki Yesu ya zo ya ceci bawansa daga mutuwa. 4Sa'adda su ka zo kusa da Yesu, su ka roke shi da gaske, cewa, "Wannan ya isa ka yi masa haka, 5saboda shi mai kaunar kasar mu ne, kuma shi ne ya gina mana majami'a.6Sai Yesu ya tafi tare da su. Amma sa'adda ya zo kusa da gidan mutumin, jarumin ya aiki abokansa su ka ce da shi, "Ubangiji kada ka damu domin ni ban isa ka zo gida na ba. 7Shi ya sa na ga ban isa in zo wurinka ba, ka yi magana kadai bawa na kuwa zai warke. 8Gama ni ma mutum ne mai iko, ina da sojoji karkashina. Ina iya cewa da wannan, 'Ka je' sai ya tafi, in kuma ce da wani 'ka zo' sai ya zo, in kuma ce da bawa na, 'Yi kaza,' sai ya yi."9Sa'adda Yesu ya ji haka, ya yi mamakin mutumin, ya juya wajen taron da su ke biye da shi, ya ce, "Na gaya maku, ko a cikin Isra'ila ban sami wani mai bangaskiya irin wannan ba" 10Daga nan wadanda a ka aika, suka dawo gida suka tarar da bawan cikin koshin lafiya.11Wani lokaci bayan wannan, ya zama Yesu yana tafiya wani gari da ake kira Na'im. Almajiransa su na tare da shi, da kuma taron mutane masu yawa. 12Sa'adda ya kusa da kofar garin, sai ga wani matacce ana dauke da shi. Kuma shi kadai ne da a wurin mahaifiyarsa. Ita kuwa gwauruwa ce, mutane da dama daga cikin gari suna tare da ita. 13Da ganin ta, sai Ubangiji ya cika da tausayi a game da ita ya ce da ita, "Kada ki yi kuka." 14Sai ya zo ya taba makarar, sai masu dauke da shi su ka tsaya. Ya ce 'Saurayi na ce ma ka ka tashi." 15Sai mataccen ya tashi ya fara yin magana. Sai Yesu ya ba mahaifiyar danta.16Sai tsoro ya kama su duka. Su ka kama yabon Allah, su na cewa, "An ta da wani annabi mai girma a cikinmu" kuma "Allah ya dubi mutanensa." 17Wannan labari na Yesu, ya ba zu a cikin dukan Yahudiya da yankuna da su ke kewaye.18Almajiran Yahaya suka gaya masa dukan wadannan abubuwa. 19Sai Yahaya ya kira biyu daga cikin almajiransa, ya aike su wurin Ubangiji, suka ce da shi, "Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?" 20Sa'adda suka zo kusa da Yesu, sai mutanen suka ce, "Yahaya Mai Baftisma, ya aiko mu, mu tambaya, "Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?"21A cikin wannan lokaci, ya warkar da mutane da yawa daga cututtuka da matsaloli da miyagun ruhohi. Makafi da yawa sun sami ganin gari. 22Yesu, ya amsa ya ce masu, "Bayan kun tafi, ku ba Yohanna rahoton abin da ku ka ji da abin da ku ka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana kuma tsarkake kutare. Kurame suna ji, ana tayar da matattu, ana gaya wa matalauta labari mai dadi. 23Mai albarka ne mutumin da ya tsaya a kan ba da gaskiya gare ni saboda ayukan da na ke yi."24Bayan da mutanen da Yahaya ya aiko suka tafi, Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yahaya. "Me ku ka tafi ku gani a cikin hamada, ciyawa wadda iska ta ke girgizawa? 25Amma me ku ka tafi domin ku gani, mutum mai saye da tufafi masu taushi? Duba mutanen da su ke saye da tufafi masu daraja, kuma suna rayuwa cikin jin dadi suna fadar sarakuna. 26Amma me ku ka tafi domin ku gani, annabi ne? I, ina gaya ma ku, ya ma fi annabi.27Wannan shine wanda aka rubuta a kansa, "Duba, ina aika manzo na a gabanka, wanda za ya shirya maka hanya a gabanka. 28Ina gaya maku, a cikin wadanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka, wanda ya fi kankanta a mulkin Allah, ya fi shi girma.29Sa'anda dukan mutane suka ji haka, har da ma su karbar haraji, suka shaida Allah mai adalci ne. Su na cikin wadanda Yahaya ya yi wa baftisma. 30Amma Farisawa da wadanda su ke kwararru a cikin shari'ar Yahudawa, wadanda ba shi ne ya yi masu baftisma ba, suka yi watsi da hikimar Allah don kansu.31Sa'annan Yesu ya ce, "Da me zan kamanta mutanen wannan zamani? Da me suka yi kama? 32Suna kama da yaran da suke wasa a kasuwa, wadanda suke magana da junansu suna cewa, "Mun yi maku busa, ba ku yi rawa ba. Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba."33Haka, Yahaya ya zo, bai ci gurasa ba, bai sha ruwan inabi ba, amma ku ka ce, 'Aljani ne yake mulkinsa. 34Dan Mutum, ya zo, yana ci, yana sha, amma, kuka ki shi, kuna cewa dubi mutum mai hadama, mai shan ruwan inabi da yawa, abokin masu karbar haraji da masu zunubi! 35Amma hikimar Allah tana shaidar dukan 'yayanta."36Wata rana wani Bafarise, ya roki Yesu ya je ya ci abinci tare da shi. Bayan da Yesu ya shiga gidan Bafarisen, ya zauna a teburi domin ya ci abinci. 37Sai ga wata mace mai zunubi, ta fito daga cikin birni. Sa'anda ta ji labari Yesu yana gidan Bafarisen, domin ya ci abinci. Ta dauki tandun mai na alabastar mai kamshi. 38Ta tsaya kusa da Yesu tana kuka. Ta fara jika kafafunsa da hawayenta, tana shafe kafafunsa da gashin kanta. Tana yi wa kafafunsa sumba, tana shafe su da turare.39Sa'anda Bafarisen da ya gaiyaci Yesu, ya ga haka, sai ya yi tunani a cikin ransa, da cewa, "In da wannan mutum annabi ne, da ya gane ko wacce irin mace ce, wannan da take taba shi, ita mai zunubi ce." 40Yesu ya amsa ya ce masa, "Siman, ina so in gaya maka wani abu." Ya ce, "malam sai ka fadi!"41Yesu ya ce, "wani mutum mai ba da bashi yana bin wadansu mutane su biyu kudi, yana bin dayan sule dari, dayan kuma yana bin sa sule hamsin. 42Da yake ba su da kudin da za su iya biyan sa, sai ya yafe masu, su duka biyu. A cikin su biyu, wanne ne zai fi nuna kauna ga wannan mutum?" 43Siman ya amsa ya ce, "Ina tsammani wanda ya yafe wa kudi da yawa." Yesu ya amsa ya ce masa, "Ka shari'anta dai dai."44Yesu ya juya wajen matar, ya ce da Siman, "Ka ga matan nan. Na shiga gidanka. Ba ka ba ni ruwa domin kafafuna ba, amma ita ta ba ni, da hawayenta ta wanke kafafuna, ta kuma shafe su da gashin kanta. 45Kai ba ka yi ma ni sumba ba, amma ita ta yi, tun sa'adda na shigo nan ba ta dena sumbatar kafafuna ba.46Kai ba ka shafe kai na da mai ba, amma ita ta shafe kafafuna da turare. 47Saboda haka, ita wadda ta ke da zunubi da yawa ta bayar da mai yawa, ta kuma nuna kauna mai yawa. Amma shi wanda aka gafarta wa kadan, ya kuma nuna kauna kadan."48Daga nan sai ya ce mata, "An gafarta zunubanki." 49Wadanda su ke a nan zaune tare da shi suka fara magana da junansu, "Wanene wannan wanda har yake gafarta zunubai? 50Sai Yesu ya ce da matar, "Bangaskiyarki ta cece ki. Ki tafi da salama."
Yesu ta shiga Kafarnahum inda ya warkar da bawa na shakaru dari.
ƙarin "a jin" ya yi nauyin da cewa ya na son su su ji abin da zai faɗa. AT: "ga mutanen da suki jin sa" ko "ga mutanen da su ke gun" ko ga mutanen su ji"
Wannan ya fara sabuwar abnu a labarin
"wanda jarumin yake daraja" ko "wanda yake grimamawa"
"ya yi masa rok" ko "roke shi"
"jarimin ya isa"
"mutanen mu." Wanna na nufin mutanen Yahudawa.
"tafi tare"
Yare na ƙasa za ' iya mai da. AT: "kusa da gidan"
Jarumin ya mai da ladabi yana magana da Yesu. AT: "kada ka dami kanka da zuwa gida na" ko "Ba na so in dameka"
Wannan sashin ƙari ne da yake nufin "shigo gida na." Idan yaren ku na da ƙari da yake nufin "shigo gida na," ti tunani ko yana da kyau a yi amfani da shi anan. ̇
Bawan ya gane da cewa Yesu zai iya warkar da bawan da magana kawai. Anan "kalma" na nufin umurni. AT: "ka bada umurni kawai"
Kalmar da aka juya anankamar "bawa"an saba juya ta kamar "yaro." zai nuna da cewa bawan karamin yaro ne ko nuna ƙaunar jarumin mi shi.
"I na da wani fiye da ni wanda dole in yi biyayya dashi"
"a karka shin iko na"
Kalmar da aka juya anan kamar "bawa" na hali kalma ne na bawa.
"ya yi mamakin jarumin"
Yesu ya faɗi wannanya yi nauyin abin mamakin da yake so ya faɗa musu.
Ma'ana shi ne Yesu yana tsammani mutanen Yahudawa su samu irin wannan bangaskiya, amma basu da shi. Ba ya tsammanin al'umai su samu irin wannan bangaskiya. duk da haka wannan mutum ya na da shi. mai yuwa za ka iya kara irin wannan labarin. AT: "Ban sami wani dan Isa'ilawa wanda ya gaskanta da ni kamar yadda wannan ba al'ume ya yi!"
An gane da cewa wadannan sune mutanen da jarumin ya yi aika. AT: "mutanen da hafsa Roma ya aika wa Yesu"
Yesu ya ji ƙasar Na'im, Inda ya warkar da wani mutum da ya mutu.
sunsr birnin
Wannan kalmar "gama" ya fahimtar da mu da mu da gabatar da mu ga wani mattacan mutum a labari. Mai yuwa Yaren ku suna da wani iri hanyan yin haka. AT: "akwai wani mutum wanda"
AT: "mutanen su na daukan mutanen da suka mutu zuwa wajen garin"
"dauka waje. shi ne ɗa a wurin mahaifiyarsa, kuwa ita gwauruwa ce. kokuwa taro dayawa." wannan bayani ne na ƙasa game da mutun wanda ya mutu da mahaifiyarsa.
matan da maigidan ta ya mutu kuma ba ta yi aure ba
"ya ji tausa yin ta"
"ya tafi gaba" ko "ya kusata da mutumin da ya mutu"
Wannan gadon daukan mara lafiya ko gado da ake amfani da shi a dauke jiki zuwa wurin biso. Bai zama wani abun da aka binne jikin ba. wasu masu juyan mai yuwa suna da kadan na kullum "anna'ashi" ko "gadon jana'izan."
Yesu ya faɗa wannan domin ya yi nauyin da cewa ya kamata wannan mutum ya yi umurni da shi. saurare ni! tashi"
mutumin har yanzu a mace yake; yanzu ya na da rai. zai zama da kyau ka bayana wannan. AT: "mutumin da ya mutu"
"dukak su sun ciki da tsoro." AT: "sun cika da tsoro sosai"
Suna nufin Yesu ba wa wani annabin da ba 'a gane shi ba." anan ƙari ne "na saka zama." AT: "Allah ya sa wani a cikin mu ya zama annabi" da
Wannan ƙarin na nufin "kula ga"
"Wannan labarin" na nufin abun da mutane suke faɗa a aya 16. AT: "Mutanen sun baza rehoton game da Yesu" ko "Mutane sun gaya wannan rehoton game da Yesu"
"Wannan rehoton" ko "Wannan labarin"
Wannan ya gabatar da sabuwar abu a labarin.
"gaya wa Yahaya"
"dukkan wadannan abubuwan da Yesu yake yi"
Wannan bayanin za'a iya rubuta domin a sa ya zama fɗi daidai guda ɗaya. AT: "mutanen sun ce Yahaya mai baftisma ya aike su gun sa su yi tambaya, 'Kai ne wanda kake zuwa, ko mu sa ido ga wani?"' ko "mutaanen sun ce, 'Yahaya mai baftis ma ya aike mu gun ka mu yi tambaya cewa kai ne kake zuwa ko mu sa ido ga wani'"
"ko mujire wani" ko "ko mu tsammaci wani dabam"
"A waccan lokacin"
Zai zama da taimako to a sake faɗan warkasuwan. AT: "ya warkar da su daga miyagun ruhohi" ko "sabo da haka ya warkar da mutane daga miyagun ruhohi"
"ya gaya wa dan aikan Yahaya" ko "ya gaya wa mai aikan Yahaya"
"gaya wa Yahaya"
"mutanen da suka mutu suna raye kuma"
"matalauta mutane"
AT: "Allah zai albarkace mutumin da ya daina bada gaskiya da ni saboda ayukana"
"Mutanen da basu yarda ... masu albarkane" ko "Duk wanda bai ... mai albarkane" ko "Duk wadda bai yarda ba ...mai albarkane." Wannan ba tabbatatcen mutum bane.
Wannan mara yaƙani yana nufin "cigaba da yarda da ni koda"
"bada gaskiya gaba ɗaya"
Wannan ana sammanin amsa mara yaƙani. ka je waje ka gan ciyawa wadda iska ta ke girgizawa? A'a!" za'a iya rubuta shi kamar bayani/ AT: "ba shakka ba ka je waje ka gan ciyawa wadda iska ta ke girgizawa!"
Ma'ana mai yuwa 1) mutumin da yana iya sake hankalin sa, ko 2) mutumin da yana magana dayawa amma baya faɗan abin mai muhimmanci, kamar yadda ciyawa yana cikasaura da makamancinsa da amon motsinsu idan iska ya hura su.
Wannan ma yana sammanin amsa mara yaƙani, tunda Yahaya ya sa tufafi mara kyau. "ka je waje ka ga mutumin da ya sa tufafi masu taushi? A'a!" Wannan za'a iya rubuta shi kamar bayani. AT: "kai ba shakka baka je waje ka ga mutumin da ya sa tufafi masu taushi!"
Wannan na nufin tufafi masu tsada. tufafi na kullum ba su da kyau. AT: "sa tufafi masu tsada"
fada na da babbane, gida mai tsada da sarki yake zama a ciki.
Wannan ya kai ga amsa mai yaƙani. ka je waje ka gan annabi? a ai ka yi!" Wannan za'a iya rubuta shi kamar bayani. AT: "Amma ainihi ka je waje ka ga annabi!"
Yesu ya faɗa haka domin ya yi nauyin muhimmancin abin da zai faɗa na biye.
Wannan sashin ya nuna da cewa gaskiya Yahaya annabi ne, amma ya ma fi annabi. AT: "ba annabi kawai ba" ko "ya ma fi muhimmanci da annabin kullum"
"Da cewa annabi shi ne wanda annabi suka rubuta a kan sa" ko "Yahaya shi ne wanda annabawa suka rubu ta akan sa tun da daɗewa"
A wannan ayan, Yesu yana faɗin annabi Malachi kuma yana cewa Yahaya shi ne dan aika wanda annbi Malachi ya yi magana.
Wannan ƙarin ya na nufin "a gabanka" ko "yav tafi a gabanka"
Wannan kalmar "naka" mafuradi ne domin Allah yana magana akan Mai ceto a faɗin.
"a cikin wadanda mata suka haifa." Wannanmisali ne da ya ke nufin dukkan mutane. AT: "a dukkan mutanen da suka taba rayuwa"
"Yahaya ya fi girma"
Wannan yana nufin duk wanda ya sashin mulkin da Allah zai kafa.
Wannan ruhaniyan mutane a mulkin Allah zai fi na mutane kamin a kafa mulkin. AT: "yana da ruhaniya sosai fiye da Yahaya"
Wannan ayan za'a iya rubuta domin ya zama mai sauki. AT: "Sa'anda dukkan mutanen da Yahaya ya yi masu baftisma, har da masu karban haraje , sun je haka, sun shaida da cewa Allah mai adalcine"
"sun ce da cewa Allah ya nuna kansa mai adalci" ko "sun shaida da cewa Allah ya yi aikin Adalci"
AT: "domin sun bar Yahaya ya yi masu baftisma" KO "domin Yahaya ya yi masu baftisma"
"suka ƙi abin da Yesu yana so su yi" ko "suka so su yi rashin biyyaya da abin da Allah ya gaya masu su yi"
AT: "ba su bar Yahaya yayi masu baftisma ba" ko "sun ƙi baftismam Yahaya"
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya gabatar da kwatantawa. za'a iya rubuta su kamar bayani. AT: "Wannan shi ne abin da na kwatanta wannan zamanin da shi, kuma suna kamar me."
Wannan hanya biyu ne na faɗan cewa wannan kwatanci ne.
mutanen da suke zama sa'anda Yesu yana magana.
Wadannan kalmomin sune farkon kwatancin Yesu. ya cewa mutanen suna kamar yara wanda basu gamsuwa da yadda wasu yara suke aikatawa".
babban budaɗen fili da mutane suke zuwa su sayar da kaya
"amma ba ku yi rawa wakar ba"
"amma ba ku yi kuka da mu ba"
Ma'an mai yuwa 1) "azumi koyaushe" ko 2) "ba su cin abin ci kullum."
Yesu ya na faɗan abin da mutane suka ce game da Yahaya. wannan za'a iya faaɗ ba da faɗi daidai ba. AT: "kun ce yana da aljanu." ko "kun yi masa shari cewa ya na da aljanu."
Yesu yana sammanin mutanen su gane da cewa yana nufin kansa, AT: "Ni, Ɗan Mutum"
Wannan za'a iya juya kamar daidai faɗi. AT: "kuncu shi mutum mai handama ne da kuma ma shayi ... zunubi." ko "kun yi masa shere da cewa yana ci yana sha da yawa kuma ya na zama ... zunubi."
"shi mai cin zari ne" ko "ya cigaba da cin abin ci"
"mai sha" ko "ya cigaba da shan barasa"
Wannan ƙarin magana ne da Yesu ya yi a yanayin, mai yuwa ya koya wa masu hikima da cewa da ba su ƙi su aƙrbi Yesu da Yahaya.
Alamar farawa a sabuwar sashin labarin kuma ya gabatar da Bafarise a cikin labarin.
"ya zauna a tebur don abinci." aladane hutun cin abincin dare kamar haka wa mutane su ci suna kwance da daɗi kewaye da tebur.
Kalmar "gama" ya ba mu saurin fahimtan wani sabon mutum a labarin. mai yuwa yaren ku na da wata hanyar yin haka.
"wa yake zaman zunubi" ko "wa yake da sunan zaman rayuwan zunubi." mai yuwa karuwa ce.
"tulun da aka yi da duwatsu mai taushi." alabastar farin dutse ne mai taushi. mutane su na ajiya abubuwa masu kyau a tulun alabastar.
"da mai mai kamshi a cikin." mai din yana da wata abu abu a cikin ta daya ke sa ta yi kamshi mai kyau. mutane suna sha fa akan su ko su yayafa a tufafin su domin su yi kamshi mai kyau.
"da gashin ta"
"wasa turarea kan su"
"ya cewa kansa"
Bafarise ya yi tunani da cewa Yesu ba annabi bana domin yana barin masu zunubi su taba shi. AT: "A bayyane Yesu ba annabi bana, domin annabi zai sani wannan matan da take taba shi mai zunubi ce"
Siman ya yi tunani da cewa annabi ba zai taba barin mai zunubi ya taba shi ba. Wannan sashin tunanin sa za'a iya bayana shi ba shakka. AT: "da cewa ita mai zunubi ne, kuma ba zai barta ta ba shi ba"
Wannan sunan Bafarisen ne wanda ya gayaci Yesu zuwa gidan sa. Wannan ba Siman Bitrus bane.
"mutane biyu sun karba bashin kuɗi a wurin wani mai bada bashin"
"kwana 500' hakin." "dinari jam'i dinari ne." dinari ƙarreran kuɗin azurfa ne.
"dayan mai bashin ya reke masa dinari hamsin" ko "hakin kwana 50"
"ya yafe masu bashin su" ko "ya share masu bashin"
Siman yana hankali game da amsan sa. AT: "mai yuwa"
"ka yi daidai"
Yesu ya sa hankalin Siman ya koma gun matar ta juyawa wajen ta.
hakin mai gida ne ya bawa baƙi ruwa da tawul domin su wanke ƙafafun su sai su dushar bayan da su yi tafiya a hanya mai kura.
Yesu ya yi amfani da sashin sau biyu domin ya hada rashin ladabin Siman da masanancin aikin godiyar zuciya.
Matan ta yi amfani da hawayenta a maimakon ruwa.
Matn ta yi amfani da gashin kanta a masayin tawul.
Mai gida mai kyau a aladar zai gaishe baƙi da sumba a ƙunci ba. Siman bai yi haka ba.
"ta cigaba da yin sumbantar ƙafafuwana"
Matar ya yi sumbatar ƙafan Yesu a maimakon ƙuncin sa a masayin masanancin nuna tawali'u.
Yesu ya cigaba da hada rashin kyaun liyafar Siman da aikin matar.
"sa mai a kai na." Wannan aladane na marabtan bako mai daraja. AT: "marabtana da shafa mini mai a kai na"
Matar ta daraja Yesu sosai da yin haka. ta kwatanta tawali'u da shafe ƙafafun sa a maimakon kansa.
AT: "Allah ya yafe zunuban ta masu yawa"
ƙuanar ta shaida ce da cewa an yafe zunuban ta. Wasu yaren suna neman abu na " ƙauna" a faɗa. AT: "gama tana ƙaunar wanda ya yafe mata zunuban ta sosai" ko "gana tana son Allah sosai"
"duk wanda aka yafe masa abubuwa kadan." A wannan jumlan Yesu ya faɗa ƙa'da na gaba ɗaya. yadda da ya na sammanin Siman ya gane da cewa ya nuna wa Yesu ƙauna kadan.
"Sai ya ce wa matar"
"An yafe miki." AT: "Na yafe zunubanki"
"zaune tare kewaye da tebur" ko "cin abinci tare"
Shugabanen adini sun sani da cewa Allah ne kadai yake gafrta zunubi kuma basu yarda da cewa Yesu Allah ne ba. Wannan tambayan mai yuwa domin a yi zargi ne. AT: "Wannan mutumi ya na tunanin shi wanene? Allah ne kadai yake gafrta zunubi!" ko Me ya sa wannan mutumin ya na yi kamar shi Allah ne, wanda shi kadai ne yake gafarta zunubi?"
"Domin bangaskiyarki, kin sami ceto." tsamo isimi "bangaskiya" za'a iya faɗan ta kamar aiki. AT: "Domin kin bangaskiya, kin sami ceto"
Wannan hanya ce na ce sai anjema da bayar da albarka a lokaci ɗaya. AT: "sa'anda kin tafi, kada ki damu kuma" ko "bari Allah ya baki salama sa'anda kin tafi"
1Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah, 2mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta, 3da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.4Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali. 5"Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye. 6Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.7Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba. 8Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari." Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, "Duk mai kunnen ji, bari ya ji."9Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin. 10ya ce da su, "Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba."11To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah. 12Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira. 13Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.14Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba. 15Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.16Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.17Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba. 18Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke."19Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a. 20Sai wani ya gaya masa, "Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka." 21Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, "Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita."22Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, "Ina so mu je dayan ketaren tafkin." Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin. 23Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.24Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, "Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!" Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit. 25Daga nan sai ya ce da su, "Ina bangaskiyar ku?" Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, "Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?"26Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili. 27Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.28Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, "Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!" 29Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.30Sa'annan Yesu ya tambaye shi, "Yaya sunanka?" Sai ya ba da amsa, "Suna na dubbai." Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum. 31Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi.32Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu. 33Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.34Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen. 35Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.36Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi. 37Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.38Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, "Ka barni in tafi tare da kai!" Amma Yesu ya sallame shi cewa, 39"Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka." Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.40Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa. 41Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa, 42saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.43Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita. 44Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.45Yesu ya ce, "Wanene ya taba ni?" Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, "Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai." 46Amma Yesu ya ce, "Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina."47Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke. 48Sai ya ce da ita, "Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama."49Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, "Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam." 50Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, "Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu."51Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta. 52Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, "Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!" 53Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.54Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, "Yarinya, na ce ki tashi!" 55Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci. 56Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.
Wannan ayan ya ba da labari na ƙasa game da Yesu yana koyasuwa sa'anda yake tafiya.
Wannan sashin an yi amfani da shi a nan domin a sa alama a sabuwar sashin labarin.
AT: "wadanda Yesu ya warkar da su daga aljanu da cututtuka iri iri"
Uku da ga cikin maatan aka lissafa: Maryamu, Yuwana, da Suzanatu.
AT: "Maryamu wanda mutane suke kira Magadaliya ... wanda Yesu ya cire aljanu bakwai daga cikin"
Yuwana, matar Kuza kuma kuza wakilin Hirudus, "Yuwana, matar wakilin Hirudus, kuza"
"sun taimaki Yesu da almajerensa da kuɗi"
"zuwa gun Yesu"
"Wani mai shuki ya fita ya wasa iri a gona" ko "Wani manomi ya je gona ya warwasa iri a gona"
"wasu irin sun faɗi" ko "wasu irin ya faɗi"
AT: "mutane suka yi tafiya a kan shi" ko "mutane suka yi tafiya akai"
Wannan ƙarin za'a iya juya shi da sauki kamar "tsuntsaye" ko "tsuntsaye suka faɗi ƙasa kuma" a ajiye hankalin "sararin sama."
"ya bushi sosai" ko "suka bushi sosai." Abin da ya saza'a iya faɗan ta. AT: "ƙasan ya bushi sosai"
Yesu ya gama gaya wa taron misali.
ƙayan shukin ya dauki dukkan abin da zai sa shi girma, ruwa, hasken rana,sabo da haka shukin manomin ba zai yi girma da kyau ba.
"girmar da girbi" ko "girmar da iri iri sosai"
Wannan na nufin sau dari fiye da abin da aka shuka.
Zai iya zama na halita ga wasu yaren su yiamfani da mutum na biyu: "kai da kake da kunnene ji, ka ji"
Ma'ana mai yuwa 1) "kowani ɗaya" tun da kowa yana da kunne ko 2) "duk wanda zai iya ganewa" wanda yake nufin wanda yana so ya saurari Allah.
"sai ya ji da kyau" ko "ya nasu ya ji abin da na faɗa"
AT: "Allah ya ba ku damar gane ... Allah" ko " Allah ya sa ku ku gane ... Allah"
Wannan gaskiya na da aka boye, Amma yanzu Yesu yana bayana masu.
"wa wasu mutane." Wannan na nufin mutanene da suka ki koyasuwan Yesu kuma sun ki su bishi.
"ko da sun gani, ba za su gane ba." Wannan faɗi ne daga annabi Ishaya. Wasu yaren za su so su faɗa manufan wannan fi'ilin. AT: "koda shike suna ganin aabubuwa,ba za su gane su ba" ko "ko da sun gan abu na faruwa, ba za su gane abin da suke nufi ba"
"ko da sun ii, ba za su gane ba." Wannan faɗi ne daga annabi Ishaya. Wasu yaren za su so su faɗa manufan wannan fi'ilin. AT: "koda sun ji umurni, ba za su gane gaskiyan ba"
"Irin saƙone da Allah"
Wannan irin da suka faɗi tare a kan hanya sune wadanda." Yesu ya faɗa abin da ya faru da irin kamar ya ruwaita da mutane. AT: "Irin da suka faɗi akan hanya na nufin mutane" ko "a misalin iri da suka faɗi akan hanya sune mutane"
Yesu ya yi magana akan irin ya na nuna wani abu game da mutane kamar irin mutane ne AT: "nuna abin da ya faru da mutane"
A nan "zuciya" misali ne na hankalin mutane ko na ciki mutum. AT: "shedan ya zo ya dauke magana Allah daga cikin zuciyanansu"
A wannan misalin ne wannan tsuntsun ne ya ƙwace irin. yi ƙoƙi ka yi amfani da kalma a yaren ku da zai ajiye hotan wannan.
tunda wannan manufan shaidan, za'a iya juya shi kamar: AT: "domin shiadan ya yi tunani, domin kada su bada gaskiya su tsira,' ko" kada ya zama sun yarda da Allah sun tsira."
"Irin da suka faɗia kan duwatsu sune wadanda."Yesu ya faɗa abin da ya faru da irin kamar ya ruwaita da mutane. AT: "Wannan irin da suka faɗi akan duwatsu na nufin mutane" ko "A misalin irin da suka faɗi akan duwatsu na nufin mutane"
"dueasun ƙasa"
"sa'anda suka ji wahala"
Wannan ƙarin na nufin "sun daina bada gaskiya" ko "sun daina bin Yesu"
"Irin da suka fada cikin kayayuwa, na nufin mutanen" ko " A misalin irin da suka faɗi a kayayuwa na nufin"
AT: "kula, da arziki dajin dadin wannan rayuwa ya ware su"
abubuwan da mutane suka damu a kai
"abubuwan wannan rayuwa da mutane suke jindadin"
Wannan misalin na nufin yadda iri ya ke yanka wuta da abin da ya ke sa su girma daga shukin kuma ya hana su girma. AT: "kamar yadda ciyawa yake hana shuki girma, da kila da arziki da jin dadin wannan rayuwa ya na hana wadannan mutane daga girma"
"ba su haifan 'ya'yan da suka nuna." nunannae 'ya'ya misali ne na kyawawan ayuka. AT: "sabo da haka kamar yadda shuki ba ta haifan nunannen 'ya'ya,ba su yin kuawawan ayuka"
"irin da suka fada a kan ƙasa mai kyau na nudin mutane" ko "A misalin irin da suka fada a kan ƙasa mai kyau na nudin mutane"
"jin wannan saƙon"
A nan "zuciyz" misali ne na tunanin mutum ko niyya. AT: "da gaskiye da bege mai kyau"
"haifan 'ya'ya da hakurin jimrewa" ko "haifan 'ya'ya da ƙokrin cingaba." 'ya'ya misali ne na ayuka masu kyau. AT: "kamar yadda shuki masu kyau suke haifan 'ya'ya masu kyau,suna haifan ayuka masu da jumriya"
Wannan ya sa alaman farawa na wata misali
AT: " duk abin da ya ke rufe za a bayyana ta"
Wannan abin da ba mai yaƙani ba za'a iya rubu ta shi kamar bayani mai yaƙani. AT: " duk wani abu da ya ke asirance za'a san shi kuma zai bayyana a hhaske"
Mai saukin gana wa ne a mahallin da Yesu yana magana game da ganewa da bada gaskiya. Wannan za'a iya faɗa ba shakka domin a sake siffa mai ƙoƙari. AT: "duk wanda ya gane za'a sake ganer da shi" ko "Allah zai sa wanda suka yarda da gaskiya su sake yarda soasi"
Mai saukin gana wa ne a mahallin da Yesu yana magana game da ganewa da bada gaskiya. Wannan za'a iya faɗa ba shakka domin a sake siffa mai ƙoƙari. AT: "Amma duk wanda ba shi da ganewa zai rasa ganewa da yake tunani yana da shi" ko Allah zai sa duk wanda ba su yarda da gaskiya ba kada su gane ko kaɗan da suke tunani sun gane"
Wadannana ƙannen Yesu ne- sauran yaran Maryamu da Yusufu wanda aka haife su bayab Yesu. Tunda Uban Yesu Allah ne, sanannun rabin yan'uwansa ne. Wannan bayyani ba a juya shi kullum.
AT: "mutane suka gaya masa" ko "wani ya gaya masa"
"kuma suna so su ganka"
Wannan misalin ya kwatanta da cewa mutanen da suke zuwa gun Yesu suna da muhimmaci masa feye da iyalin sa. AT: "Wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita sune kamar mahaifiyata da 'yan'uwana ne"
"maganar da Allah ya faɗa"
Wannan tafkin janisarata ce wanda ake kira tekun Galili.
Wannan kwatancin ya na nufin cewa sun fara tafiya a ketaren tafkin ƙyallen kwalekwale.
"sa'anda suke tafiya"
"fara barci"
"iska mai ƙarfi ya fara" ko "iska mai ƙarfi nan da nan ya fara busawa"
Iska mai ƙarfin ya sa raƙumin ruwa ya yi yawa har ya tira ruwa a gefen jirgin. AT: "iskan ya sa raƙumin ruwa mai ƙarfi da ya fara ya cika jirgin su da ruwa"
magana nan da nan wa
"raƙumin ruwa mai ƙarfi"
"iskan da raƙumin ruwan su tsaya" ko "sun tsaya tsit"
Yesu ya kwaɓi su mara tsanani domin ba su gaskak ta da shi ya kula da su ba. Wannan za'a iya rubu ta shi kamar jumla. AT: "ku sami bangaskiya" ko "ku yarda da ni!"
"Wani irin mutum ne wannan ... yi biyayya da shi?" Wannan tambayan ya furcin ya nuna motse mai tsanani da rikicewa bisa yadda Yesu ya yi mulki da iskan.
Wannan za'a iya juya shi kamar jumla: "Toh wanene wannan mutuimn? ya umurta ... yi biyayya da shi!"
Garasinawa inda mutane birnin suke kira jarasa.
"a ɗayan gefen tafkin Galili"
"wani mutum daga birnin jarasa"
mutumin yana da aljanu; ba birnin bane yake da aljanu. AT: "wani mutum daga birnin, kuma wannan mutumin yana da aljanu"
"wanda aljanu suke mulki da shi" ko "wanda aljanu na mulki da shi"
Wannan labari ne na ƙasa game da muyumin.
"bai sa tufafi ba"
Wannan wurare ne inda mutane suke sa mattatu, mai yuwa kogon dutse ko karamin gini da mutane za su iya amfani da shi kamar tsari.
"Sa'anda mutumin da yake da aljanu ya ga Yesu"
"yi ihu" ko "ya yi kururuwa"
ya kwanta a ƙasa a gaban Yesu." bai faɗi da hadari ba.
"ya ce da ƙarfi" ko "ya yi ihu"
Wannan ƙarin yana nufin "don me kake damuna?"
Wannan suna mai muhimmanci ne ga Allah.
"sau da dama ya yi mulkin mutumin" ko "sau da dama ya shige shi." Wannan ya faɗa abin da aljanun ya yi wa muyumin kamai Yesu ya hadu da shi.
AT: "ko da shike mutanen sun daura shi da sarka da mari kuma sun tsare shi"
AT: "aljanun za su sa shi ya tafi"
Juya wannan kalmar da ya ke nufin lambar sojoji dayawako mutane. wasu masu juyin suka ce "runudnar yaƙi." AT: "bataliya" ko "sashin rundunar sojoji"
"suka yi ta rokon Yesu"
Wannan ya bada labari na ƙasa ya gabatara da aladu.
"suna kusa suna ci ciyawa a kak tsauni"
Kalmar " sai" an yi amfani da shi anan domin a bayyana dalilin da aljanun su ka fito waje daga cikin mutumin domin Yesu ya ce masu su je cikin aladu.
gudu da sauri
"garkin ... suka nutse." ba wanda ya sa aladun su nutse tunda su ke cikin ruwa.
"sun gan mutumin wanda aljanu suka bar shi"
"mai hankali" ko "yana yin hali na kullum"
"zaune a ƙafafu" a nan ƙari ne da yake nufin "zaune da tawali'u kusa" ko "zaune a gaba AT: "zaune a gaban Yesu"
Zai zama da taimako ka bayyana da cewa sun jin tsoron Yesu. AT: "suna jin tsoron Yesu"
"wandanda suka gan abin da ya faru"
AT: "Yesu ya warka da mutumin da aljanu suka yi iko da shi" ko "Yesu ya warkar da mutumin wanda aljanu sun yi mulki da shi"
"waccan filin Garasinawa" ko "filin da inda mutanen Garasinawa suke zama"
AT: "sun fara ji tsoro sosai"
wurin zaman za'a iya faɗa. AT: "suka koma ketaren tafkin"
Abin da ya auko a wannan ayan ya faru kamin Yesu ya bar jirgin. zai zama da taimako ka faɗe shi ba shakka daga farko. AT: "Kamin Yesu da almajeren sa su bar mutumin" ko "Kamin Yesu da almajeren sa su shirya ƙyallen da aka rataya a kwalekwalen, mutumin"
"gidanka" ko "iyalin ka"
"gaya masu komai game da abin da Allah ya yi maka"
"taron suka gaishe shi da murna"
"ɗaya daga cikin shugabannin majami'a na wuri ɗaya" ko "shugaban mutanen wanda sun hadu a cikin majami'a"
Ma'ana mai yuwa 1)"ya runsuna a ƙafafun Yesu" 2)"ya kwanta a ƙasa aƙafafun Yesu."Yayirus ya rusuna da kansa a ƙasa bai faɗi da hadari ba. ya yi haka a alamar tawali'u da bada girma wa Yesu.
"ta kusa mutuwa"
Wasu masu juyin za su ce Yesu ya yarda da farko ya tafi da Yayirus. AT: "sai Yesu ya yarda ya je da shi. da yana kan hanya"
"tarom sun matsu kewaye da Yesu"
Wannan ya gabatar da sabuwar hali a labarin.
"tana da zuban jini." mai yuwa tana zubar da jini daga mahiafa ko da ba lokacin haka ba. wasu aladun suna da wata hanya mai sauki na nufin wannan yana yin.
AT: "amma ba wanda zai warkar da ita"
"ta taba geza rigansa." Mutanen YahudawaMai yuwa wannan shi ne abin da ta tabba. suna sa tunku a habar rigunar su kamar kayan biki kamar yadda aka umurta a dokan Allah. Mai yuwa wannan shi ne abin da ta tabba.
ba faɗan haka, Biturus ya na nuna da cewa kowa zai iya taba Yesu. Wannan bayanin za ka iya bayyana shi in ya zama dole. AT: "akwai taron mutane dayawa kewaye da kai da suna ta taruwa kewaye da kai kowa a cikin su zai iya tabaka"
Zai zama da taimako ka bambanta wannan da sanin ta "tabawa" daga tabawa hadari daga taron. AT: "Wani ya tabani da sanin sa"
Yesu bai rasa ƙarfi ba ko ya zama mara ƙarfi, amma ikon sa ya warkar da matan. AT: "Na sani da cewa ikon warkar wa ya fita daga jikina" ko " Na ji iko na ya warkar da ni"
"da cewa ba za ta iya boye asirin abin da ta yi ba." Zai zama da taimako a faɗa abin da ta yi. AT: "da cewa ba za ta iya baye asirin abin da ta yi ba da cewa ita ne ta taba Yesu"
"ta zo wurin sa ciki da tsoro
"dukkan mutanen na gani"
"Wannan hanya ne mai na kirki na magana da mata. mai yuwa yaren ku na da wata hanya na faɗan wannan kirkin.
"domin bangaskiyar ki, kin warke." tsamo isimi "bangaskiya" za'a iya faɗan ta kamar aiki . AT: "domin kin yarda, kin warke"
Wannan ƙarin hanya ne na faɗan, "sai anjima" da kuma bada albar ka a lokaci ɗaya. AT: " sa'an da ka tafi , kada ka damu kuma " ko "bari Allah ya baka salama sa;anda ka tafi"
"Yana cikin magana da wata mata"
Wannan na nufin yayirus. (Dubi: Luka 8:41)
Wannan bayanin ya nuna da cewa Yesu ba zai iya yin komai yanzu ya ceci yarin yan yanzu da ta mutu.
Wannan na nufin Yesu.
"zata sami lafiya" ko "za ta rayu kuma"
"Sa'anda suka zo gidan." Yesu ya tafi da Yayirus. wasu almajeren Yesu suma sun tafi.
Wannan za'a iya faɗa da yaƙani. AT: "Yesu ya bar Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta su shi ga gidan da shi"
Wannan na nufin Yyirus.
Wannan hanya ce na nuna bakin ciki a waccan aladan. AT: "dukka mutanen da suke wurin suna nuna bakin cikisu su na kuka da ƙarfi yarin yarta mutu"
"suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar"
"Yesu ya kama hanun yarinyar"
"ruhun ta ya dawo jikin ta ." Yhudawa sun gane da cewa rai sakamakon ruhu ne ya dawo cikin mutum. AT: "Ta fara nunfashi kuma" ko Ta dawo da rai kuma" ko "Tana raye kuma"
Wannan za'a iya faɗa dabam da ban. AT: "kada sun gaya wa kowa"
1Ya kira almajiransa goma sha biyu, ya ba su iko su fitar da kowanne irin aljani, su kuma warkar da cututtuka daga mutane. 2Ya aike su, su yi wa'azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.3Ya ce masu, "Kada ku dauki komi tare da ku domin wannan tafiya. Kada ku dauki sanda, ko jakar matafiyi, ko gurasa, ko kudi - Kada ma ku dauki taguwa biyu. 4Dukan gidan da ku ka shiga, ku zauna a gidan har zuwa lokacin da za ku tafi daga wannan yankin.5Dukan wadanda ba su marabce ku ba, sa'adda ku ke barin wannan gari, ku karkabe kurar kafufunku a matsayin shaida a kansu." 6Daga nan sai almajiran suka tafi zuwa cikin kauyuka, suka yi ta shelar bishara, su na warkar da mutane a ko'ina.7Ana nan Hirudus, mai mulki, ya ji labarin dukan abubuwan da su ke faruwa. Ya yi mamaki saboda wadansu mutane suna cewa Yahaya mai yin Baftisma ne ya sake dawowa da ransa. 8Wadansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sake bayyana, wadansu kuma suna cewa daya daga cikin annabawa na da can ne ya sake bayyana da rai. 9Hirudus ya ce, "Ba zai yiwu Yahaya ne ba, domin na datse masa kai. To, wanene wannan da ni ke jin wadannan abubuwa a kansa?" Daga nan sai ya cigaba da neman hanyar da zai ga Yesu.10Sa'adda manzannin suka dawo daga tafiyarsu, suka gaya wa Yesu dukan abubuwan da suka yi. Daga nan sai ya dauke su domin su tafi tare da shi zuwa garin Baitsaida. 11Amma sa'adda taron suka ji inda Yesu ya tafi, sai suka bi shi can. Ya marabce su ya yi masu jawabi a kan mulkin Allah, kuma ya warkar da wadanda su ke bukatar warkarwa.12Da yake yamma ta fara yi, sai almajiransa goma sha biyu suka zo suka ce da shi, "Idan ka yarda ka sallami wannan babban taron mutane dominsu shiga cikin kauyuka, da ke kewaye da gonaki, dominsu sami abinci da wuraren da za su kwana, da yake mu na nan a wurin da ba kowa." 13Amma sai ya ce da su, "Ku ba su abin da za su ci." Suka amsa masa, "Dukan abin da muke da shi shine, 'Yan dunkulen gurasa biyar da 'yan kifaye guda biyu, ba za mu iya zuwa mu sawo abincin da zai ishi mutanen nan su duka ba." 14Mutanen da suke wurin sun kai kimanin mazaje dubu biyar. Sai Yesu ya ce da almajiran, "Ku ce da mutanen su zauna kungiya-kungiya, mutane hamsin a kowacce kungiya."15Sai almajiran suka yi haka, dukan mutanen suka zauna. 16Ya dauki dunkulen gurasan guda biyar, da kifin guda biyu, yana dubawa zuwa sama ya albakarce su, sa'annan ya gutsuttsura, ya ba almajiran domin su rarraba wa mutane. 17Dukansu suka ci kowa ya koshi. Daga nan almajiran suka tattara sauran abin da ya rage, har kwanduna goma sha biyu suka cika!18Wata rana Yesu yana yin addu'a shi kadai, sai almajiransa suka zo sai ya tambaye su, "Wa mutane suke cewa da ni?" 19Suka amsa, "Wadansu suna cewa, Yahaya mai yin Baftisma, wadansu suna cewa kai annabi Iliya ne, har yanzu wadansu suna cewa kai wani cikin annabawa na da can ne ya dawo da rai."20Ya tambaye su, "Ku fa? Wa kuke cewa da ni?" Bitrus ya amsa, "Kai Almasihu ne wanda ya zo daga wurin Allah." 21Sai Yesu ya gargade su da karfi, kada su gayawa kowa haka tukuna. 22Sa'annan ya ce, "Dan Mutum dole ya sha wahalar abubuwa da yawa; dattawa za su ki shi da manyan fristoci da marubuta, sa'annan za a kashe shi. Bayan kwana uku, za a tashe shi da rai."23Sai ya ce da su duka, "Dukan wanda ya ke so ya biyo ni, dole ne ya yi musun kansa, ya dauki gicciyen sa kulluyomin, ya biyo ni. 24Dukan wanda yake so ya ceci ransa, za ya rasa shi, amma dukan wanda ya ba da ransa domina, za ya cece shi. 25Wacce riba mutum zai samu idan ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa?26Dukan wanda yake jin kunya ta da magana ta, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa, sa'adda ya dawo cikin darajarsa da darajar Uba da ta mala'iku masu tsarki. 27Amma ina gaya maku wannan tabbas, wadansu cikinku da ke nan tsaye, ba za su mutu ba sai sun ga mulkin Allah."28Kwana takwas bayan Yesu ya fadi wadannan kalmomi, sai ya dauki Bitrus da Yahaya da Yakubu, ya hau kan dutse domin ya yi addu'a a can. 29Sa'anda ya ke yin addu'a sai yanayin fuskar sa ya canza sosai, tufafinsa kuma suka yi sheki da haske kamar walkiya.30Nan da nan sai ga mutane biyu suna magana da shi, wato Musa da Iliya. 31Suka bayyana da daraja kewaye da su, suka yi magana da Yesu a kan tafiyarsa wadda za ta zo ba da dadewa ba a cikin Urushalima.32Bitrus da almajiran da suke tare da shi barci mai nauyi ya dauke su. Sa'adda suka farka sai su suka ga daukakar Yesu; kuma suka ga mutanen su biyu da ke tsaye tare da shi. 33Sa'adda Musa da Iliya suke shirin su bar wurin Yesu, sai Bitrus ya ce, "Ya shugaba, ya yi kyau da muke a nan. Zai yi kyau mu yi runfuna uku, daya dominka, daya domin Musa, daya kuma domin Iliya." Amma hakika bai san abin da ya ke fadi ba.34Sa'adda yake fadin haka sai wani girgije ya zo ya rufe su. Sai suka ji tsoro sa'adda girgijen ya kewaye su. 35Sai ga wata murya daga cikin girgijen tana cewa, "Wannan Dana ne wanda na zaba, ku ji shi." 36Sa'adda muryar ta gama magana, Yesu yana nan shi kadai. Suka yi shiru ba su iya cewa kome ba a kan abin da suka gani a kwanakin nan.37Washe gari, da suka sauko daga kan dutsen, sai taron mutane da yawa suka zo wurinsa. 38Nan da nan, wani mutum daga cikin taron mutanen ya yi magana da karfi, "Mallam, kayi wani abu dominka taimaki da na, shi kadai ne gare ni. 39Mugun ruhu ya kan hau kansa, ya sa shi ya yi ta magowa. Ya kan girjiza shi da karfi ya sa bakinsa ya yi ta kumfa. Da kyar ya ke rabuwa da shi, kuma ya kan ji masa ciwo ba kadan ba bayan da ya bar shi. 40Na roki almajiran ka su umurci mugun ruhun ya fita daga cikinsa, amma ba su iya ba!"41Yesu, ya amsa, ya ce, "Ku karkatattun tsara marasa bangaskiya, har yaushe zan zauna da ku ina jimrewa da ku? "Kawo yaronka anan." 42Sa'adda yaron yake zuwa, sai mugun ruhun ya fyada yaron a kasa, ya jijjiga shi sosai. Amma Yesu ya tsauta wa mugun ruhun, ya warkar da yaron. Sa'annan ya mika yaron wurin mahaifinsa.43Dukansu suka yi mamaki da girman ikon Allah. Amma sa'anda suke ta yin mamaki a kan dukan al'ajiban da ya yi, ya ce da almajiransa, 44"Ku saurara da kyau a kan abin da zan gaya maku, ba da dadewa ba za a bada Dan Mutum ga mutane." 45Amma almajiran ba su gane abin da yake nufi da haka ba, an hana su fahimta, domin kada su gane abin da ya ke nufi tukuna, kuma suna jin tsoron su tambaye shi.46Wani lokaci, almajiran suka fara gardama a tsakaninsu game da wanene za ya zama mafi girma a cikinsu. 47Amma Yesu ya san abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya kawo dan karamin yaro ya tsaya a kusa da shi, 48sai ya ce da su, "Idan wani ya karbi dan karamin yaro kamar wannan saboda ni, dai dai yake da ya karbe ni. Idan kuma wani ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni kenan. Wanda yake mafi kankanta a cikinku, shi ne mafi mahimmanci."49Yahaya ya amsa yace, "Ya shugaba, mun ga wani mutum yana ba miyagun ruhohi umarni su fita daga cikin mutane da sunanka. Sai muka ce da shi ya dena yin haka saboda baya tare da mu." 50Amma Yesu ya ce, "Kada ku hana shi yin haka, domin dukan wanda ba ya gaba da ku, yana tare da ku."51Sa'adda rana ta kusato da zai hawo zuwa sama, ya kudurta sosai zai tafi Urushalima. 52Ya aiki wadansu manzanni su shirya wuri dominsa kafin ya zo. Suka shiga wani kauye a cikin kauyen Samariya domin su shirya masa wuri a can. 53Amma mutanen can ba su karbe shi ba tun da ya ke Urushalima zai tafi.54Sa'adda biyu daga cikin almajiransa, wato Yakubu da Yahaya suka ga haka, suka ce, "Ubangiji, kana so mu umarci wuta ta sauko daga sama, ta hallaka su?" 55Amma, ya juya ya tsauta masu. 56Sai suka tafi wani kauye dabam.57Da suna cikin tafiya a kan hanya, sai wani mutum ya ce da shi, "Zan bi ka dukan inda za ka tafi." 58Yesu ya amsa masa, "Dila suna da ramuka a kasa inda za su shiga, tsuntsaye kuma suna da sheka, amma Dan Mutum ba shi da inda zai kwanta."59Yesu, ya ce da wani mutumin kuma, "Ka biyo ni." Amma mutumin ya ce, "Ubangiji, ka bari in koma gida in bizine mahaifina tukuna." 60Amma Yesu ya ce masa, "Ka bar matattu su bizine matattunsu; amma kai ka tafi ka yi wa mutane shelar mulkin Allah a ko'ina."61Wani kuma ya ce, "Ubangiji zan tafi tare da kai, amma bari in je gida inyi ban kwana da mutanena tukuna." 62Yesu ya ce da shi, "Dukan wanda ya fara huda a gonarsa idan ya dubi baya, bai isa ya shiga mulkin Allah ba."
Yesu ya tunashe al'majerensa kada su dogara akan kuɗi da abubuwan su, ku basu ƙarfi, ku kuma aike su zuwa wurare dabam daban.
Wannan ajilin guda biyuan yi amfani da su tare domin a nuna da cewa dukkan goma sha biyun suna da dama da kuma za su yia warkar da mutane. juya wannan sashin da haɗin kalmar da ya hada dukkan ra'ayin.
Ma'ana mai yuwa1) "kowanne aljani" ko 2) "kowanne irin aljani."
rashin lafiya
"ya aiki su wurare dayawa" ko "gaya masu su je"
"Yesu ya gaya wa goma sha biyun." Zai zama da taimako ka tada cewa ya faru kamim ya aiki su . AT: "Kamim su tafi, Yesu ya ce masu"
"Kada ku dauki komi tare da ku" ko "Kada ku kawo komai tare da ku"
"domin yar tafiyan ku" ko "sa'anda ku ka yi tafiya." Kada su dauki komai a duk tafiyan su, da suke tafiya daga kauye zuwa kauye, har sai sun zo gun Yesu.
babbar sandada mutane suke amfani da shi domin su daidaita saanda suke hauwa ko tafiya akan ƙasa wanda ba bai ɗaya bane,da kuma tsaro ga masu faaɗwa
jakar tafiya da ake daukan abin da ake so don tafiya
An yi amfani da wannan a nan domin shaida na "abinci." gaba ɗaya
"Dukan gidan da kuka shiga"
"tsaya a wurin" ko "ku zauna a gidan na dan lokaci kamar baki"
"zuwa lokacin da za ku bar garin" ko "zuwa ran da zaku bar wurin"
"A nan ga abin da za ku yi a garin in da mutane basu karbe kuba: sa'anda za ku tafi"
ku "karkabe kurar kafufunku" kwatanci ne na ƙi mai ƙarfi a waccan al'adar. Ya nuna da cewa basu son ku kurar garin nan ya ragu a sun su.
"sum bar wurin da Yesu yake"
"warkar a ko'ina da suka je"
Wannan ayan ya tura bayani ciki game da Hirudus.
Wannan sashin ya sa fashi a labarin. A nan Luka ya bada bayani na ƙasa game da Hirudus.
Wannan na nufin Hirudus Antifas, wanda ya ke mulkin ɗaya bisa hudu na Isra'ila.
ba'a iya ganewa ba, rekice
AT: "wadansu mutane suna cewa"
Wannan kalmar "ce" an gane shi a sashin da ya wuce. AT: "kuma suna cewa daya daga cikin annabawa na da can ne ya sake bayyana da rai"
Hirudus yana tsammanin cewa ba zai yu Yahaya ya tashi daga mattatu ba. Wannan za'a iya bayana ba shakka. AT: "Ba zai zama Yahaya ba domin Na datse masa kai. sabo da haka wanene wannan mutum"
Sojojin Hirudus su suka yanke hukuncin kisan. AT: "Na umurci sojoji na su datse kan Yahaya"
"manzannin sun dawo inda Yesu yake"
Wannan uana nufin warka suwa da koyarwa da suka yi sa'anda suka tafi biranen.
Wannan sunar birni ne.
"ranar ya kusan karewa" ko kusan karewan ranar"
dunƙulen gurasa dunƙulen ƙullun gurasa ne da aka siffa kuma an gasa.
Idan "sai dai" yana da wuya a gane a yeren ku, zaka iya yin sabuwar jumla. "kifaye guda biyu. domin a ciyar da wannan mutanen, sai dai mum je mu siya abinci"
"kimanin mazaje 5,000." Wannan lambar bai hada da yara da mataye ba wadanda mai yuwa suna nan.
"ku gaya masu su zauna"
"50 kowacce"
"Wannan" na nufin abin da Yesu ya ce su yi Luka 9:14. sun gaya wa mutanen su zauna akungiya kimanin mutane hamsin.
"Yesu ya dauki dunƙulen gurasan guda biyar"
Wannan na nufin kallon sama, zuwa sararin sama. Yahudawa sun yarda da cewa ana samun sama a sararin sa.
Wannan na nufin dunƙulen gurasan guda biyar da kifi guda biyu.
"ya raba wa" ko "ya băwa"
Wannan ƙarin ya na nufin sun ci abinci sosai har ba su jin yunwa. AT: "sun samu sosai kamar yadda suke bukata su ci"
AT: "al'majeren suka tara abin da ya rage" ko "al'majeren suka kwashe sauran abin da ya rage"
Wannan sashin an yi amfani da shi a nan domin a sa alama akan sabuwar abi da ya auko.
"yana yin addu'a shi kadai." al'majeren suna tare da Yesu, amma yana addu'a shikadai asirace da kansa.
Zai zama da taimako ka sakr faɗan sashin wannan tambayan a nan. AT: "Wasu sun ce kai ne Yahaya mai yin Baftisma"
Zai zama da taimako ka ganar da yadda wannan tambayan yadda ya hadu da tambayar Yesu. AT: "da cewa kai ɗaya daga cikin annabawa na da can ne ya dawo da rai"
"ya dawo da rai"
"Yesu ya ce wa al'majeran sa"
"kada su gayawa kowa" ko "da cewa kada su gaya wa kowa." Wannan za'a iya faaɗ kamar daidai faɗi. AT: "Kada ku gaya wa kowa."
"Mutaneza su sa Ɗan Mutum ya sha babar wahala"
Yesu yana nufin kansa. AT: "Ni, Ɗan Mutum ... kuma zan"
AT: "dattawa za su ki shi da manyan fristoci da marubuta"
AT: "za su kashe shi"
"kwana uku bayan da ya mutu" ko "a rana ta uku bayan mutuwarsa"
"zai tashi da rai kuma." AT: "Allag zai ... sa shi ya zama da rai kuma" ko "zai rayu kuma"
"Yesu ya ce "
Wannan na nufin al'majeren da suke tare sa Yesu.
"biyo ni" biyo Yesu ya na nufin zama ɗaya daga cikin al'majeren sa. AT: "zama al'majeri na" ko "zama ɗaya daga cikin al'majeria na"
"dole ba zai băwa sa'awar sa ba" ko "dole ya ki sa'awar sa"
"dauki gicciyen sa kulluyomin, ya biyo ni." giciyen na nufin wahala da mutuwa. dakar giciyen na nufin ya yarda zai sha wahala kuma ya mutu. AT: "zai yi biyayya dani kowace rana ko a ajilin wahala da mutuwa"
Bin Yesu a nan ya na nufin yin biyayya da shi. AT: "biyyaya da ni"
Amsar wannan tambayan shi ne bai da kyau. AT: "ba zai amfane wani ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa."
"ya sami komai a duniya"
"rasa kansa ko bada ransa"
"abin da na ce" ko "abin da na koyad"
AT: "Dan Mutum ma zai ji kunyarsa"
Yesu yana magana game da kansa. AT: "Ni, Dan Mutum ... sa'adda Na dawo"
Wannan suna ne mai muhimman ci wa Allah.
Yesu ya yi amfani da wannan sashin ya yi nauyin mumanci abin da ya ke so ya faɗana biye.
"wadansun ku dake tsaye a nan ba za su ɗanɗana mutuwa ba"
Yesu yana magana game da mutanen da yake magana akai. AT: "kamin ku gani"
Wannan ra'ayin " ba ... har sai" za'a iya furta da mai yaƙani da "kamim." AT: "za su ga mulkin Allah kamin su mutu" ko "za ka gan mulkin Allah kamin ka mutu"
Wannan ƙarin na nufin "mutuwa"
Wannan na nufin abin da Yesu ya gaya wa al'majeren a ayoyin da ya wuce.
Wannan kalmar "dubi" a nan ya samu saurin fahimta mu kula da bayanin ban mamakin da ya biyo baya. AT: "ba zato"
Wannan sashin ya ba da bayani game da yadda Musa da Iliya suke. Wasu yaren za su juya shi kamar sharaɗi dabam daban. AT: "kuma sun bayyana cikin daraj" ko "suna walkiya da haske"
"tafiyarsa" ko Yadda Yesu zai bar wannan duniyan nan." Wannan hanya ce mai ladabi na magana game da mutuwar sa. AT: "mutuwar sa"
Wannan kalmar an yi amfani da shi a nan domin a sa alaman fashi a asalin labarin. A nan Luka ya ba da labari akan Bitrus, Yakubu da Yahaya.
Wannan ƙarin na nufin "barci sosai"
Wannan na nufin hasky mai walƙiya ya ƙewaye su. AT: "sun ga haske mai walƙiya yana zuwa daga gun Yesu" ko "sun ga wuta mai haske ya fitowa daga gun Yesu"
Wannan yana nufin Musa da Iliya.
"Da Musa da Iliya suke barin wurin"
mai sauƙi, maficin wuri wanda za'a iya zama ko barci
"Wa'anda Bitrus yana faɗan wannan abubuwan"
cikakku al'majeren ba su ji tsoron gajimarai. Wannansashin ya nuna da cewa wani iri tsoro da ba na kullum ba ya ƙama su da gajimarin. AT: "suka ji tsoro"
Wannan za'a bayana a ajili da gakimarai ya yi. AT: "gajimaran ya zagaya su"
An gane da cewa muryan zai zama na Allah ne kawai. AT: "Allah ya yi magana da su a gajimaran"
Wannan suna ne mai muhimmanci wa Yesu, Ɗan Allah.
AT: "wanda Ni na zaba" ko "Na zabe shi"
Wannan bayanin ya faɗi abin da ya faru bayan labarin a sakamakon abin da ya auko a labarin da kanta.
Sashi na farko ya na nufin amsawar su nan da nan, na biyu kuma ya na nufin abin da suka yi a kwanakin da ya biyu.
Kalmar nan "gama" ya samu fahimtar sabuwar mutum a labarin. mai yuwa yaren ku na da wata hanyar yin haka Turaci sun yi amfani da "Akwai wani mutum a cikin taron wanda"
Saahin nan "kun ga" ya gabatar mana da mugun ruhu a labarin mutumin. mai yuwa yaren ku na da wata hanyar yin haka. AT: "Wannan mugun ruhu na da ya"
"kumfa ya fito daga bakinsa." Sa'anda mutum yana da waso, za su samu munfashi biyu ko haɗeyewa. Wannan ya na sa farin kumfa ya taru a bakin sa.
"Yesu ya amsa da cewa"
Yesu ya cewa taron da suka taru, ba wa al'majeren sa ba.
"tsara marasa kirki"
A nan "ku" jam'i ne. Yesu ya yi amfani da wannan tambayan ya bayyana bakin cikin sa da cewa mutanen ba shu gaskanta ba. Za'aiya rubuta su kamar bayani. AT: "na daɗe da ku, amma ba ku gaskanta ba. ina mamaki har yaushe zan zauna da ku ina jimrewa da ku."
A nan "na ka" mafuraɗi ne. Yesu ya na magana ne da uban wanda ya yi masa magana.
Yesu ya yi aiki al'ajibi, amma taron sun gane da cewa Allah mai iko wannan warkasuwa.
"komai da Yesu yake yi"
Wannan ƙari ne da yake nufin su kasa kunne. AT: "ku saurara ku tuna" ko "Kada ku manta da wannan"
Wannan za'a iya faɗan ta da shiraɗ mai yaƙani. A nan "hannaye" na nufin ƙarfin yin mulki. AT: "za a bada Ɗan Mutum a sa shi a iko mutane"
AT: "Allah ya boye masu ma'anar"
"tsakaninsu al'majeren"
A nan "zuciyz" misali ne na hankalin. AT: "sani dalilin a zuciyarsu" ko "sani abin da suke tunani"
Wannan na nufin mutum da ya yin abu kamar wakilin Yesu. AT: "domi na"
"Allah, wanda ya aike ni"
"wadanda Allah ya dauke su mafi mahimmanci"
"A amsawa Yahaya ya ce" ko "Yahaya ya amsa wa Yesu." Yahaya yana amsawa ga abin da Yesu ya ce akan zama mafi girma. bawai yana amsa tambayan bane.
Yahaya ya yi maganar kansa amma ba Yesu ba, sabo da haka "mu" a nan banda shi
Wannan na nufin mutum yana magana da iko da ƙarfi Yesu.
AT: " kubar shi ya cigaba"
Wasu yare na zamanin yanzu faɗi da yake nufin abu ɗaya. AT: "idan mutum bai hana ka aiki ba, kamar yana taya kane" ko "idan wani baya aikin gaba da kai, yana aiki tare da kai"
"Sa'adda rana ta kusato da zai hawo zuwa sama" ko "Sa'anda lokaci ya yi kusa da zai tafi sama"
Wannan ƙrin na nufin ya "ya kudurta sosai." AT: "ya shiya hankalin sa" ko "ya kudurta"
Wannan na nufin su shirya domin zuwansa gun, mai yuwa wurin magana, wurin zama, da abinci.
"ba su so ya zauna"
Samariyawa da Yahudawa su ƙi juna sosai. sabo da haka Samariyawa ba za su taimaki Yesu ba a tafiyar sa zuwa Urushalima, hed-kwatan Yahudawa.
"gani da cewa Samariyawan ba su ƙarbi Yesu ba"
Yakubu da Yahaya suka bada shawara a wannan hanyar shariyar domisun sani haka ne annabi Iliyay asharanta mutanen da suka ƙi Allah.
"Yesu ya juya ya tsauta wa Yakubu da Yahaya." Yesu bai huƙunta Samariyawan kamar yadda almajeren sa suke sammani ba.
Wannan ba ɗaya daga cikin almajeren ba.
Yesu ya amsa ƙairn maganar domin ya koya wa mutumin zama almajerin Yesu. Yesu ya nuna da cewa idan mutum ya bi shi, mutumin shi ma ba zai sami gida ba. AT: "Dila suna da ramuka ... ba shi da inda zai kwanta. sabo da haka kada ka yi sammani cewa za ka sami gida"
Wannan babbobin ƙasa ne kama da ƙararnuka. suna kwana a kogon ko a ramia ƙasa.
"tsuntsaye da suke firiya a iska"
Yesu yana magana a kansa a mutum na uku. AT: "Ni, Dan Mutum, yana ... inda zai kwana"
"ba inda zai huta da kansa " ko "ba inda zai yi barci." Yesu ya kwatanta ya yi nauyin cewa bai da asalil gida kuma mutane basu gayatan sa kullum ya zauna da su.
Ba'a gane ba ko mahaifin mutumin ya mutu kuma zai bizine shi nan da nan, ko mutumin zai daɗe na dan lokaci har sia uban sa ya mutu sai ya bizine shi asalin ajilin shi ne mutumin ya na so ya yi wani abu ne kamin ya bi aYesu.
"kamin in yi haka, bari in koma"
Asalin nufin Yesu bawai mattatu mutane su bizine mattatu mutane bane. Ma'ana mai yuwa na mattatu shi ne 1)misali ne na wadanda su kusa su mutu, ko 2)misali ne na wadan da sunki su bi Yesu kuma sun mutu a ruhaniyance. asalin maganar shi ne kada al'majeri ya bar wani abu ya hana shi bin Yesu.
Wannan na nufin wanda suka mutu gaba ɗaya. AT: "matattun mutane"
"Zan haɗu da ku a masayin almajeri" ko "Ina shiye in bika"
kamin in yi haka, bari in yi ban kwana da mutanena gida na tukuna"
Yesu ya amsa masu da ƙarin magana ya koya wa mutuminda yana so ya zama al'majerin sa. Yesu ya na nufin cewa mutum bai isa ya shi ga mulkin Allah ba idan ya damu da mutane dake a baya a maimakon bin Yesu.
A nan "ya sa hannun sa akan" wani abu ƙari ne na da yake nufin mutum ya fara yin wani abu. AT: "Ba wanda ya fara ɦuda a gonarsa"
Duk wanda ya juya baya sa'anda ya ke ɦudaba zai iya jagoran hudan in da ya ke so ya je ba. waccan mutumin dole ya nasu ya na kallon gabadomin ya yi huɗa da kyau.
"amfani ga mulkin Allah" ko "da cewa da mulkin Allah"
1Bayan wadannan abubuwa, Ubangiji ya sake nada wadansu saba'in ya aike su biyu biyu, domin su tafi kowanne birni da wurin da yake niyyan zuwa. 2Ya ce da su, "Girbin yana da yawa, amma ma'aikatan sun yi kadan. Saboda haka kuyi addu'a sosai ga Ubangijin girbin, domin ya aiko da ma'aikata cikin gonarsa.3Ku tafi, duba na aike ku kamar 'yan raguna cikin kyarkyetai. 4Kada ku dauki jakan kudi, ko jakar matafiyi, ko takalma, kada ku gai da kowa a kan hanya.5Dukan gidan da ku ka shiga, ku fara cewa, 'Bari salama ta kasance a wannan gida.' 6Idan akwai mutum mai salama a gidan, salamar ku za ta kasance a kansa, amma idan babu, salamar ku za ta dawo wurinku. 7Ku zauna a wannan gidan, ku ci ku sha abin da suka tanada maku. Gama ma'aikaci ya wajibci ladansa. Kada ku bi gida gida.8Dukan birnin da ku ka shiga kuma sun karbe ku, ku ci abin da suka sa a gabanku. 9Ku warkar da marasa lafiyar da ke wurin. Ku ce da su, 'Mulkin Allah ya zo kusa da ku.'10Amma dukan birnin da ku ka shiga, idan ba su karbe ku ba, ku tafi cikin titunansu, ku ce, 11'Ko kurar birninku da ta like a kafafunmu, mun karkabe maku ita a matsayin shaida a kanku! Amma ku sani mulkin Allah ya zo kusa da ku.' 12Na gaya maku, a ranar shari'a Saduma za ta fi wannan birni samun sauki.13Kaiton ki, Korasinu! Kaiton ki, Baitsaida! Ayyuka masu girma da aka yi a cikinku, da an yi su a cikin Taya da Sidon, da sun tuba tuntuni a zaune cikin toka da tufafin makoki. 14Amma a ranar shari'a Taya da Sidon za su fi ku samun sauki. 15Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani har zuwa sama za a daukaka ki? Babu, za a gangarar dake har zuwa hadas.16Wanda ya saurare ku ya saurare ni, wanda ya ki ku, ya ki ni, kuma wanda ya ki ni, ya ki wanda ya aiko ni."17Su saba'in din suka dawo da murna, suna cewa, "Ubangiji, har ma aljanu suna yi mana biyayya, a cikin sunanka." 18Sai Yesu ya ce masu, "Na ga Shaidan yana fadowa daga sama kamar walkiya. 19Duba, na ba ku iko ku taka macizai da kunamai, da kuma kan dukan ikon magabci, kuma ba zai iya yin illa a gareku ba ko kadan. 20Amma duk da haka kada ku yi murna a kan wannan kadai cewa ruhohi suna yi maku biyayya, amma ku yi murna domin an rubuta sunayenku a cikin sama."21Cikin wannan lokacin, ya yi farin ciki kwarai cikin Ruhu Mai Tsarki, ya ce, "Na ba ka girma, ya Uba, Ubangijin sama da kasa. Domin ka rufe wadannan abubuwa daga masu hikima da ganewa, ka bayyana su ga wadanda ba koyayyu ba ne, kamar kananan yara. I, Uba gama haka ne ya gamshe ka."22Dukan abu, Ubana ya damka su gare ni, kuma babu wanda ya san Dan, sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Dan. Sai kuma wanda Dan ya yi niyyar ya bayyana Uban a gareshi."23Ya juya wajen almajiran, ya ce da su a kadaice, "Masu albarka ne su wadanda suka ga abin da kuke gani. 24Na fada maku, annabawa da yawa, da sarakuna da yawa sun so da sun ga abubuwan da kuke gani, amma ba su gani ba. Kuma sun so da sun ji abubuwan da kuke ji, amma ba su ji su ba."25Sai ga wani malamin shari'ar Yahudawa, ya zo ya gwada shi da cewa, "Malam, me zan yi domin in gaji rai na har abada?" 26Sai Yesu ya ce masa, "Yaya kake karanta abin da aka rubuta cikin shari'a?" 27Ya amsa ya ce,"Dole ne ka kaunaci Ubangiji Allah da dukan zuciyarka, da dukan ranka da dukan karfinka, da dukan lamirinka. Ka kuma kaunaci makwabcinka kamar kanka." 28Yesu ya ce ma sa, "Ka amsa daidai, idan ka yi haka za ka rayu."29Amma, malamin ya na so ya 'yantar da kansa, sai ya ce da Yesu, "To, wanene makwabcina?" 30Ya amsa ya ce, "Wani mutum yana tafiya daga Urushalima za shi Yariko. Sai ya fada hannun mafasa, suka tube shi, suka kwace dukan abin da ya ke da shi, suka yi masa duka, suka bar shi kamar matacce.31Ya zama sai ga wani firist ya na bin wannan hanya, da ya gan shi sai ya bi ta gefe daya ya wuce. 32Haka kuma sai ga wani Balawi, sa'adda ya zo wurin, ya gan shi sai ya bi ta wani gefe ya wuce shi.33Amma wani Basamariye, ya na tafiya sa'adda ya zo wurin da mutumin yake, sa'adda ya ga mutumin sai tausayi ya kama shi. 34Ya zo inda mutumin yake, ya daure masa raunukan da aka ji masa, yana shafa masu mai da ruwan inabi. Ya dora shi a kan dabbarsa ya kawo shi wurin kwana, ya kula da shi 35Washegari ya kawo dinari biyu, ya ba mai wurin kwanan ya ce 'Ka kula da shi, idan ma ka kashe fiye da haka, idan na dawo zan biya ka.'36A cikinsu ukun nan, wanene kake tsammani makwabcin wannan mutum da ya fada hannun 'yan fashi?" 37Sai malamin ya ce, "Wannan da ya nuna masa jinkai" Sai Yesu yace masa, "Ka je kai ma ka yi haka."38Sa'adda suke tafiya, sai ya shiga cikin wani kauye, sai wata mata mai suna Marta ta marabce shi a gidanta. 39Tana da 'yar'uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a kafafun Ubangiji tana jin abin da yake fadi.40Amma ita Marta ta na ta kokari ta shirya abinci. Sai ta zo wurin Yesu ta ce, "Ubangiji, ba ka damu ba 'yar'uwata ta bar ni ina ta yin aiki ni kadai? Ka ce da ita ta taya ni." 41Amma Ubangiji ya amsa ya ce da ita, "Marta, Marta, kin damu a kan abubuwa da yawa, 42amma abu daya ne ya zama dole. Maryamu ta zabi abu mafi kyau, wanda ba za a iya kwace mata ba."
Yesu ya aiki feye da saba'in agaba da shi. mutane saba'in dinnan sun dawo da murna, sai Yesu ya amsa da yabo ga ubansa na sama.
wannan kalman anyi amfani da ita anan domin ya nuna alamar sabon labarin da ya auko.
" saba'in"wasu juyin sun ce "saba'in da- biyu" ko "72." za ku iya kara bayanin da ya fada haka.
"ya iaki su a kungiya biyu" ko "ya aiki su da mutane biyu a kowace kungiya"
Ya fada abin yadda yake kafin mutumin ya fita waje. AT: "ya fada masu" ko "kamin su fitawaje ya fada ma su"
akwai babban baroro, amma ma'aikatan kadan nae sukawa shi ciki." Yesu na nufin akwai mutane daya wa da suke so su shiga mulkin sama, amma babu a'lmagiren da zasu taimake mutanen.
"ku tafi biranan" ko "ku tafi gun mutanen"
kyarkyetai suna harin tumakin domin su kashe su. wannan na misalin cewa akwai wadan su mutane wadda suki kokara su kashe a'lmajiran wadda Allah zai aike su. za'a iya chire sunayen wasu dabbobi. AT: "idan na aike ku,mutane zasuso su lahane ku, kamar yadda kyarkyetai suke harin tumaki"
"Kada ku dauki jaka jakan tafiya ko takalma"
"kada ku gaida kowa akan hanya. " Allah yana nauyin dacewa su tafi da sauri zuwa biarnan suyi aikin sa.bawai su zama marasa ladabi ba.
wannan duka biyu gaisuwa ne da salama. Anan "gida" na nufin wadda suke zama a gida. AT: bari mutanen da suke wannan gida su sami salama"
"mutumin salama." wannan shi ne mutum mai son salama da Allah da kuma mutane.
Anan "salama" ana kwatanta salama kamar abu mai rai wadda zai iya zaba inda zaya zauna. AT: "zai sami salaman da ka albarka ce shi dashi"
Zai iya sake dukan kalman mai fatan alhari. AT: idan babu mutun mai salama" ko idan mai gidan ba mai son salama bane"
Anan "salama" ana kwatanta tane kamar abu mai rai wadda zaya iya za ban wurin da zai zauna. AT: "zaku sami wancen salamar" ko "ba zai sami salama can da ka a'lbarkace shi da shi ba "
Bawai Yesu yana nufin su zauna a wancan gidan dukan rana ba,amma suyi barci a gida daya wadda suke. AT: "cigaba da yin barci a wannan gida"
wannan shine babban wata muhimmin da Yesu yayi amfani da shi wa mutanen da ya aika. tun da zasu koyar su kuma warkar da mutane, mutanen kuwa zasu basu abinci da wurin kwaciya.
tafiya daga gida zuwa guda na nufin zuwa gidaje daban daban. zai iya za ma da ciwa yana tafiya yayi dare a gidaje daban daban. "kada ka je kayi barci kowace dare a gidaje daban daban"
" idan sun karbe ku"
za'a iya bayyana shi wa wata sifa. AT: "ci kowace irin abincin da suka baku"
wannan na nufin mutane marasa lafiya gabaki daya. AT: "mutane marasa lafiya"
wannan kalman "mulkin" za'a iya bayyana ta kamar fi'ili "shekarun sarauta" ko "mulki" ma'ana mai yuwa 1) mulkin Allah ya kusan farawa. AT: "Allah ya kusa ya fara mulki kamar sarki" ko 2) ayukan mulkin Allah suna faruwa kewaye daku. AT: "Abin shaida cewa Allah yana mulki na kewaye daku"
"idan mutanen garin sun ki ku"
wannan alamar aikatawa cewa sun ki karban mutanen garin. AT: "kamar yadda kuka ki mu, muma mun kiku sosai. muma mun ki kurar birninku da ta like a kafafunmu
tunda yesu yana aikan mutanen a kungiya biyu, zai zama mutane biyu ne na fadin wannan. yare dayake da sifa biyu "mu" zasu yi afani da ita.
wannan kalman "Amma kusan wannan" yana gabatar da gargadi. yana nufin "koda shike kun ki mu, bai canja damar cewa mulkin Allah ya kusan zuwaba!"
wannan kalman "mulkin" fadan ta da fi'ili "shekarun mulki" ko "mulkin" dubi yadda aka juya magana irinta acikin [luka 10:8]
Yakubu ya na fadin wannan wa mutane 70 da zai aiki su. Ya fada hakana domin ya nuna cewa ya na so ya fada wata abu mai muhimin amfani
wannan a'lamjiren yaka mata su ga na cewa wannan ya nufin ranan shari'a na karshe ga masu zunubi.
"Allah ba zai yiwa saduma shari'a mai tsanani feye da wannan brinin." AT: Allah zai yiwa mutanin brinin shari'a mai tsanani feye da mutanen saduma"
Yakubu yayi magana akan mutanen biranen Kaiton da Baisaida kamar suna jins, amma basu ji.
Yakubu yana bayyana yanayin da ya kama ta ya faru a baya amma bai faru ba. AT: "Idan wani ya yi aikin alajibi wa mutanen Taya da Sidon da na yi maku"
"mugayen mutanen da suka zauna awurin da sun nuna cewa sun tuba da kuskuren zunuban su a zaune"
"sa tufafin makoki da zama cikin toka"
Zai zama da fatan alheri a fade she ba shaka dalilin shari'an su. AT: "amma baku tuba ku yarda da ni ba koda sheke kunga aikin al'ajibin da na yi, allah zai yi maku shari'a mafi tsanani fiye da mutanen Taya Sidon"
"a ranan karshe ran da Allah zai sharanta kowa"
Yesu yayi magana yanzu da mutanen brinin Kafarnahum kamar suna jinsa, amma basu ji.
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya kwabe mutanen Kafarnahum game da griman kansu. AT: "ba shaka baza ku ji sama ba" ko "Alllah bazai daukaka kuba!"
wannan furcin na nufin "daukaka mai grima"
Za'a iya bayyana ta a wata sifa. AT: za ku gangara kasan hadas"
wannan kwatanci za'a iya fadin ta ba shaka kamar tamka. AT: "Idan wani ya ji ku, kamar suna ji na ne"
wannan kwatanci za'a iya fadin ta ba shaka kamar tamka. AT: "Idan wani ya kiku, kamar ya kina ne"
wannan kwatanci za'a iya fadin ta ba shaka kamar tamka. AT: "Idan wani ya kini, kamar yana kin wadda ya aiko ni ne"
wannan na nufin Allah Uban, wanda Yesu ya aza domin aikinan na susamman "Allah wanda ya aikoni"
wasu yarurukan zasu iya fa da cewa saba'in daidai ne sun fita da farko kamar yadda UDB yayi. wannan sanarwan ba'a bayyane yake ba amma za'a iya bayyana shi.
Anan "suna" na nufin karfi da ikon Yesu.
Yesu yayi amfani da tamka ya kwatanta yadda Allah yana yin nasara da shaitan yadda walkiya yana bugawa idan almajiren sana yin wa'azi a garuruwa.
"Na baku iko ku rugurguje karfin magabci" ko "Na baku iko ku ci nasara akan magabci." magabcin she ne shaitan.
"kada kuyi murna kawai domin ruhun yayi biyayya maku" za'a iya fadanta a wata sifa mai yaƙani. AT: " yi murna domin sunan ku na rubuce a sama ko da sheke kuyi murna domin ruhun yana biyayya daku"
wannan za'a iya bayana ta a wata sifa. AT: "Allah ya rubuta sunayen ku a cikin sama" ko "sunayen ku na cikin mutanen magadan mulkin sama"
wannan muhinmin shaida nena Allah.
"sama" da "kasa" na nufin ka mai da yake kasan ce AT: "Maigidan kowa da komai a sama da kasa"
wannan na nufin koyasuwan Yesu wadda suka wuce akan ikon almajirai.zai fi kyau a ce "wadannan abubuwa" da mai karatu ya gane ma'anar.
wannan kalman "hikima" da "fahimta" siffs ce ta wajen sunaye da ake nufin mutane da suke da nau'i. domin Allah ya boye masu gaskiya wadan nan mutane kuwa basu da hikima da fahimta,koda sheke suna tunanin cewa sunada shi. AT: daga mutanen da suke tunani cewa suna da hikima da fahimta "
wannan na nufin waddan da basu da ilmi sosai amma suna so su karbi koyasuwan Yesu haka kuma kananan yara suna so suji wadda da suka yarda da su. AT: "mutanen da suki da ilmi kadan, amma wanda yaji Allah kamar yadda yara suke yi"
"gama ya gamshe ku kuyi wannan"
wannan za'a iya bayayyana shsi a wata siffa. AT: "Ubana ya mika mini komai a hanuna"
Wannan shaida ne wanda ya kwatanta dagantaka Allah da Yesu.
wannan kalmar da aka juya ta kamar "sani" sabawa da mutun da kansa. Allah Uban yasan Yesu a wannan hanyan.
Yesu na nufin kansa a masayin mutum na uku.
wannan na nufin cewa Uban ne kawai ya san ɗan.
wannan kalman an juya ta kamar "sani" sabawa da mutumda kansa. Yesu yasan Allah Ubansa a wannan hanya.
wannan na nufin cewa ɗan ne kawai ya san wanene Uban.
"duk wanda ɗan ya so yanuna mishi Uban"
wannan kalman "asirance" ya nuna da cewa she kadai ne da almajiren sa. AT: anjima da ya gan shi da almajiren sa ne kawai, ya juya gunsu ya ce"
wannan mai yuwa ya na nufin ayuka masu kyau da aikin al'ajibi da Yesu ya ke yi. AT: "yadda yake da kyau ga wadanda suke ganin abubuwan da nake yi"
wannan nufin cewa Yesu baya yin wadan nan abubuwa tukunna. AT: " amma domin ba na yin su tukunna"
wannan mai yuwa na nufin koyassuwan Yesu. AT: "wadan nan abubuwa da kuke ji ina faɗa"
wannan na nufin cewa Yesu ba ya yin koyassuwa. AT: "amma baku jin su domin ban farayin koyassuwa ba tukunna"
Yesu ya amsa da labari wa malamin yahudawan wanda yake so ya gwada Yesu.
wannan ya sa mu saurin fahintan wata sabuwar abu da sabuwar mutum a cikin labarin.
"tsokana Yesu"
yesu baya neman labari.yayi amfani da tambayan domin ya koya wa malamin yahudawan. AT: "gaya mini abin da Musa ya rubuta acikin shari'a kuma mene ne ma;anarsa a tunanin ka."
wannan za'a iya tambaya a wata siffa. AT: " Me Musa ya rubuta a cikin shar'a?"
"Me kuka karata a ciki?" ko "Me ka fahinta kace?"
wannan mutum yana faɗin abin da Musa ya rubuta a shari'a.
Anan "zuciya" da "ranka" na nufin cikin ran mutum. wannan sashe guda hudun ana aiki da su ma'ana "gabaɗaya" ko "mai himmanci"
wannan tamka za'a iya faɗan ta ba shaka. AT: "kaunaci makwabcin ka sosai kamar kanka"
Amma malamin yana so ya yantar da kansa, sai ya ce" ko "Amma yana so ya bayyna kamar a'dali malamin ya ce"
Yesu ya amsa wa mutumin da wata misali. AT: "A amshe, Yesu ya bashe labarin"
Mutumin ya na so ya sani wadda ake so ya kaunaci. AT: "Wazan duba ya zama makwobci na in kuma soshe kamar kaina?" ko "wani mutane ne makwobci ci na da zan so su?"
wannan ya kawo sabuwar hali a cikin misalin.
"Mafasa suka zagayashe, wa" ko "wasu mafasa suka hareshe. su"
"karɓi dukan abin da ya ke dashi" ko "sata duk abubuwa shi"
wannan na nufin "kusan mutuwa"
wannan ba abun da mutum ya shriya bana.
wannan nannaga yana gabatar da sabuwar mutum a labarin, amma bai ambatasi da sunaba.
"da firist ya gan mutumin da ya jiciwo." Firist mutumin adini ne sosai, masu sauraron suna samanin cewa zai taimaki wanda ya ji ciwo. amma da bai yi ba, wannan magana za'a iya fadan ta kamar "amma da ya gan shi" a kira karsashi akan abin da ba a sammani.
ya nuna da cewa bai taimaki mutumin ba. AT: "bai taimaki mutumin da ya ji ciwo ba amma ya bi ta gefen hanya ya wuce" Dubi:
Balawin ya yi aiki a haikali. yaka mata ya taimaki ɗan'uwansa mutumin bayahude. tunda bai yi ba,zai iya zama da taimako a cewai. AT: Balawi ...ta wani gefe amma bai tai makeshi ba"
wannan ya gabatar da sabuwar mutum a labarin amma bai ambaci sunan saba. mum sani da cewa shi daga samariya ne.
Yahudawa suka raina Basamariye kuma suna tunanin cewa ba zai taimaki mutumni Yahudawan da ya ji ciwo ba.
"ya tausayamasa"
ya ka mata ya zuba masa mai da ruwan inabin da farko. "AT: ya sa masa mai da ruwan inabin akan ciwon sai ya ƙunsa masa da riga"
ya yi amfani da ruwan inabin ya share masa ciwon, mai kuma domin ya hana wata harbi. wannan za' iya fadan ta kamar. AT: zuba mai da ruwan inabi domin ya taimaka su warke"
"akan dabarsa ya kintsa." wannan dabane wadda ya ke amfani ya dauki kaya mai nauyi. maiyuwa jakine.
ladan aiki na kwana biyu." "dinari jam'i nw na dinariya."
mai ajiyan ƙaramar ɗaki" ko " mutumni mai lura da ƙaramai ɗakin"
wannan za; iya rubuta shi kamar tambayoyi guda biyu. AT: "meka ke tunani? wa kake sammani acikin ukun nan makwabci... 'yanfashi?"
"nuna kansa ya zama shi ne makwabci na gaskiye"
"ga mutumin wadda 'yanfashi suka hara"
zai iya zama da taimako ka bada labari da ya wa. AT: "a hanya daya,kaje ka taimaki duk wanda za ka iya"
"sa'adda Yesu da almajiren sa suke tafiya"
wannan ya gabatar da wata kauye a wata sabuwar wuri amma bai ambace sunan ta ba.
wannan ya gabatar da marta a masayin sabuwar hali, yaren ku zai iya samun wata hanya na gabatar da sabobin mutane.
wannan wurin zamane na ba da grima kullum ga mutanen da suke da ilmi a wancen zamani. AT: " zauna a kasa kusa da Yesu"
wannan na nufin komai da Yesu ya faɗ da yake gidansu Marta. AT: ji koyasu wan Yesu"
"hidimomi sosai" ko "hidima kuma"
Marta ta yi ƙara da cewa Uangiji ya bar Maryamu ta zauna tana sauraron sa kuma ga aiki sosai da zata yi. ta ba wa Ubangiji grima sosai sai ta yi amfani da bai damu da amsa ba domin ta zamar da ƙaran sa mai ladabi. AT: "kamar ba ka damu ba ... ni kadai."
Yesu ya nanata sunan Marta domin nauyi AT: "Masoyiya Marta" ko "Ke Marta"
Yesu ya nuna banbancin abun da Maryamu tana yi da kuma wanda Marta tana yi.zai za ma da taimako a mayar da shi a bun da ba sai an bayana ba. AT: "abun da ya za ma dale shine a saurari koyasuwa na" ko "Sauraron koyasuwana yafi shirya abinci"
Ma'ana mai yuwa 1) "Bazan kwace wannan daman daga wurin ta ba" ko 2) baza ta rasa abin da ta samu daga saurarona ba"
1Wani lokaci, Yesu yana yin addu'a a wani wuri, sai daya daga cikin almajiransa yace da shi, "Ubangiji, ka koya mana yin addu'a kamar yadda Yahaya ya koya wa almajiransa."2Yesu ya ce ma su, "Sa'anda ku ke yin addu'a ku ce, 'Uba a tsarkake sunanka. Mulkin ka ya zo.3Ka ba mu abin da za mu ci a kowacce rana. 4Gafarta mana zunubanmu, kamar yadda muke gafarta ma wadanda suke mana laifi. Kada ka kai mu cikin jaraba.'"5Yesu ya ce masu, "Wanene a cikinku idan yana da aboki, za ya je wurinsa da tsakar dare ya ce masa, "Aboki, ka ba ni rancen dunkulen gurasa guda uku, 6da ya ke wani abokina ya iso yanzu daga tafiya, kuma ba ni da abin da zan ba shi ya ci,' 7Sai wanda yake ciki, ya amsa, ya ce, 'Kada ka dame ni. Na riga na rufe kofa ta, kuma ni da yarana mun riga mun kwanta. Ba zan iya tashi in ba ka gurasa ba.' 8Na fada maku, ko da bai tashi ya ba ka gurasar ba, a matsayin abokinsa, ba ka ji kunya ba, ka nace da rokonsa, za ya tashi ya ba ka dukan yawan gurasar da kake bukata.9Ni kuma ina ce maku, ku roka za a ba ku; ku nema za ku samu; ku kwankwasa za a bude maku. 10Domin dukan wanda yake roko ya na karba; dukan wanda ya ke nema kuma yana samu; kuma wanda yake kwankwasawa, za a bude masa.11Wanne uba ne a cikinku, idan dansa ya tambaye shi kifi, zai ba shi maciji a maimakon kifi? 12Ko kuwa idan ya tambaye shi kwai, za ya ba shi kunama? 13To, da yake ku da kuke masu mugunta kun san ku ba 'yanyan ku abu mai kyau. Yaya fa ga Ubanku wanda yake cikin sama, za ya ba da Ruhu Mai Tsarki ga wadanda suka roke shi?"14Wani lokaci, Yesu yana fitar da wani beben aljani. Sa'adda aljanin ya fita, sai mutumin da yake bebe ya yi magana. Sai taron mutanen suka yi mamaki! 15Amma, wadansu daga cikin mutanen suka ce, "Da ikon Ba'alzabuba sarkin aljanu ne yake fitar da aljanu."16Wadansu suka gwada shi, suka nemi ya nuna masu wata alama daga sama. 17Amma Yesu da yake ya san tunaninsu, ya ce da su, "Dukan mulkin da ya rabu biyu, gaba da kansa, ya rushe kenan, kuma idan gida ya rabu biyu, gaba da kansa za ya fadi.18Idan Shaidan ya rabu biyu gaba da kansa, ta yaya mulkinsa zai iya tsayawa? Gama kun ce ina fitar da aljanu ta wurin Ba'alzabuba. 19Idan ni na fitar da aljanu ta wurin Ba'alzabuba, ta wurin wa wadanda suke bin ku suke fitar da aljanu? Saboda haka, su ne zasu zama masu yi maku shari'a. 20Amma idan daga wurin Allah na ke fitar da aljanu, to, ya zama ke nan mulkin Allah ya zo wurinku.21Idan mutum mai karfi, mai kayan fada ya tsare gidansa, kayansa za su tsira. 22Amma idan wani mutum wanda ya fi shi karfi ya zo ya ci nasara a kansa, zai dauke kayan fadan daga wurin mutumin, kuma ya kwashe kayansa. 23Wanda ba ya tare da ni, gaba da ni ya ke yi, kuma wanda ba ya tattarawa tare da ni, watsarwa yake yi.24Idan kazamin ruhu ya fita daga cikin mutum, ya kan bi ta wurin busassun wurare yana neman wurin da zai huta. Idan bai samu ba sai ya ce, 'Bari in koma gidana inda na baro. 25Sa'adda ya dawo, ya tarar an share gidan, an kuma gyara shi tsaf. 26Sai ya je ya dauko wadansu aljanu guda bakwai wadanda su ka fi shi mugunta, su zo su zauna a wurin. Sai karshen mutumin nan ya fi farkonsa muni."27Ya zama, lokacin da ya ke fadin wadannan abubuwa, wata mace ta tada muryarta a cikin taron mutanen ta ce da shi, "Mai albarka ne cikin da ya haife ka, da maman da ka sha." 28Sai shi kuma ya ce, "Masu albarka ne wadanda suke jin maganar Allah suke yin biyayya da ita."29Lokacin da mutane suke kara taruwa, sai ya fara cewa, "Wannan tsara, muguwar tsara ce. Ta na neman alama, Ko da yake ba wata alamar da za a bata sai irin ta Yunusa. 30Domin kamar yadda Yunusa ya zama alama ga mutanen Neneba, haka kuma Dan Mutum za ya zama alama ga wannan tsara.31Sarauniyar Kudu, za ta tsaya ta yi shari'a da mutanen wannan tsara, kuma za ta kashe su, gama ta zo daga wuri mai nisa domin ta saurari hikimar Sulaimanu. Kuma ga wani wanda ya fi Sulaimanu a nan.32Mutanen Neneba, za su tsaya shari'a da matanen wannan tsara, kuma za su kashe su. Gama sun ji wa'azin Yunusa sun tuba. Kuma ga wani wanda ya fi Yunusa a nan.33Ba wanda zai kunna fitila ya boye ta, ko kuwa ya sa ta a karkashin kasko, amma zai sa ta a mazaunin ta domin dukan wanda ya shiga dakin ya ga haske. 34Idon ku shine fitilar jikinku. Idan idonku yana gani sosai, jikinku zai cika da haske. Amma idan idonku ba ya gani sosai, jikinku zai cika da duhu. 35Ku yi hankali fa, domin kada hasken da ya ke wurinku ya zama duhu. 36Idan dukan jikinku yana cike da haske, babu duhu ko kadan, to sai dukan jikinku ya zama kamar fitilar da take bada haskenta a bisanku."37Sa'adda ya gama jawabi, sai wani Bafarise ya ce da shi ya zo gidansa ya ci abinci, sai Yesu ya shiga ya zauna. 38Sai Bafarisen ya yi mamaki da ganin bai wanke hannu kafin ya ci abinci ba.39Amma sai Ubangiji ya ce da shi, "Ku Farisawa kuna tsabtace bayan kofi da bangaji, amma cikin yana cike da kazamta da mugunta. 40Ku mutane marasa tunani, wanda ya yi wajen, ba shine ya yi cikin ba? 41Ku bayar da abin da ke ciki ga matalauta, kuma dukan abu zai zamar maku da tsafta.42Amma kaitonku Farisawa, gama kuna karbar zakka da daddoya da karkashi da kowanne irin ganye na lambu, amma kun watsar da adalci da kaunar Allah. Dole ne a yi adalci, a kaunaci Allah, a yi sauran abubuwan kuma.43Kaitonku Farisawa, domin kuna so a ba ku wuraren zama masu kyau a cikin masujadai, a kuma yi maku gaisuwar bangirma a cikin kasuwanni. 44Kaiton ku, gama kuna kama da kabarbarun da ba yi masu shaida ba, mutane kuwa suna tafiya akansu ba tare da saninsu ba."45Wani malami a cikin shari'ar Yahudawa ya amsa masa ya ce, "Malam, abin da ka ce ya bata mana rai mu ma." 46Sai Yesu ya ce, "Kaitonku malaman shari'a! Gama kun dora wa mutane kaya mai nauyi wanda ya fi karfinsu dauka. Amma ku, ko da dan yatsa ba ku taba kayan ba.47Kaiton ku, gama kuna gina abubuwan tunawa a kabuburan annabawa, alhali kuwa kakanni-kakanninku ne suka kashe su. 48Ya zama kenan kuna sane da ayyukan kakanni-kakanninku, domin sune suka kashe annabawan da kuke tunawa da su.49Saboda wannan daliline hikimar Allah ta ce, "Zan aika manzanni da annabawa a wurinsu, kuma za su tsananta masu har ma za su kashe wadansu daga cikinsu.' 50Wannan tsarar, za ta dauki alhakin jinin dukan annabawan da aka kashe tun kafuwar duniya. 51Tun daga jinin Habila, har zuwa jinin Zakariya wanda aka kashe tsakanin bagadi da wuri mai tsarki. I, na gaya ma ku za a nemi hakin su a wurin wannan tsarar52Kaitonku malaman shari'a na Yahudawa, domin kun dauke mabudin sani, ku da kanku ba ku shiga ba, kuma kun hana masu shiga su shiga."53Bayan da Yesu ya bar nan wurin, Marubuta da Farisawa suka yi gaba da shi, suka yi jayayya da shi a kan abubuwa da yawa, 54suna kokari su kafa masa tarko domin su kama shi a cikin kalmomin da yake fadi.
wannan wata farkon sashi na a labarin. Yesu ya koya wa almajiren sa yadda za su yi addu'a.
wannan sashen maganan anyi amfani da ita anan domin a nuna wata sabuwar sashi na labarin. idan yaren ku tana da wata hanyan yi haka, za'a iya amfani da ita anan.
zai yiya zama kace Yesu ya gama addu;a kamin almajiren sa suka yi tambaya. AT: "da cewa Yesu yana addu'a a wani wuri. sa'an da ya gama addu'a daya daga "
"Yesu ya cewa almajiren sa"
Yesu yana umurtan almajiren sa su ɗaukaka sunan Allah Uba da kiran sa kamar "Uba" sa'an da suke addu'a. wannan masayine mai muhimmaci wa Allah.
" ka sa kowa ya ɗaukaka sunan ka." "Suna ya na nufin dukan mutum. AT: bari dukan jama'a su ɗaukaka ka"
Aikin Allah yayi mulki akan kowa anyi magana kamar Allah da kansa. AT: "bari ka zo kayi mulki a kan kowa"
Yesu ya cigaba da koya wa almajirensa yadda za su yi addu'a.
wannan wajibi na, amma za'a iya juya shi kamar roko, ba kamar dokoki ba. zai iya da amfani a kara wani bau kamar "in ka yarda" domin kusa a gane. AT: "in ka yarda ka bamu ... inka yar da ka yafe mana ...in ka yarda kada ka kaimu"
gurasa abinci ne mara sada wadda mutane suke ci kullum.anyi amfani da ita anan a masayin abinci na gaba daya. AT: "abincin da muke bukata kowane rana"
"Kayafe mana zunuban da muke yi maka" ko "kayafe mana zunuban mu"
"tunda muma muna yafewa"
"wanda ya yi mana zunubi" ko "wanda yayi mana abin da ba kyau"
wannan za;a iya faɗan ta a siffa mai yaƙani. AT: "kadau ke mu daga wurin jaraba"
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya koya wa almajiren sa. AT: "Misali wdaya a cikin ku yana da ...ya sa a gaban shi.' " ko "Misali kana da ... Bin da za ka sa a gaban shi.' "
"bari in ranci gurasa uku" ko "kaba ni garasa uku zan biya anjima" Mai gidan bashi da wani abincin da zai ba wa bakon.
Ana amfani da gurasa amasayin abinci na gaba ɗaya. AT: dayawa suna ɗafa abinci domin a ci" ko "ɗayawa suna ɗafa abinci domin mutum ya ci"
wannan na nufin bakon ya zo da gidan sa can da nisa. AT: "yana tafiya sai ya shiga gida na"
"akwai abincin da ya yi a ba shi"
"Ba ji dadin tashiwa ba "
Yesu ya wa almajiren sa magana. wannan kalma "kai" jam'i ne.
Yesu yana magana da almajiren sa kamar su ne suke tambayan gurasan. AT: " ka bashi gurasan ka domin shi ne ... nasa... shi shi ke bukata"
wannan sashin za'a iya ba da lada a fid da isimi "nacewa." AT: " domin ka nace da rashin kunya" ko "domin cigaba da tambaya shi"
Yesu ya ba da wannan umurnin domin ya karkafa almajiren sa su cigaba da addu'a. wasu yaren za su nemi wasu labarai da wannan fi'ili. ku yi amfani da siffa "ku" da ya dace da wannan mahilli. AT: ci gaba da tambayan abin da kake so ... ci gaba da neman abin da kake sa daga Allah ...neme shi ... ci gaba da kwankwasa kofan"
wannan za'a iya fadan ta a wata siffa. AT: "Allah zai ba ka shi" ko "za ka same shi"
Kwankwasa kofa shi ne ka buga na ɗanlokaci domin mutumin da ya ke ciki ya sani cewa ka na tsaye a bakin kofar. za'a iya juya ta kamar yadda mutani al'adun ku suke nuna cewa sun iso, kamar "fito waj" ko "tari" ko "tafi" anan an nufin cewa mutum ya ci gaba da addu'a sai Allah ya amsa.
wannan za'a iya fadan ta a wata siffa. AT: Allah za ya buɗe maka kofar" ko "Allah za ya karɓe ka ciki"
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya koyar da almajiren sa. za'a iya rubu ta shi kamar bayani. AT: "Ba wani uba ... kifi"
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya koyar da almajiren sa. za'a iya rubu ta shi kamar bayani. AT: "Kuma baza ka iya ba shi kunama ba idan ya tambayi kwai"
Kunama yana kama da gizogizo, amma ya na da wutsiya da ƙari mia dafi. idan ba a san kunama ba a inda kake, za ka iya juya shi kamar "gizogizo mai dafi" ko "gizogizo mai ƙari"
"tunda ku mugaye kun sani" ko ko dashi ke kuna da zunubi, kun sani"
"yaya tabbacin ka ceaw Uban ka da ke cikin sama zai ba ka Ruhu mai Tsarki ... shi? Yesu kuma ya yi amfani da tambaya domin ya koyar da almajiren sa. za'a iya rubu ta shi kamar bayani. AT: "kana da tabbacin cewa Uban ka da ke sama zai baka Ruhu mai Tsarki ... shi."
Mai wallafa ya yi amfani da wannan kalman domin ya sa lamba a farkon sabuwa abin da ya auko.
zai za da amfani a kara wa ta bayani. AT: "Yesu yana fitar da aljini a cikin wani mutum" ko "Yesu yana sa aljani ya bar mutum"
Aljani ya na da karfi ya hana mutane magana. AT: " aljani ya sa mutumin kar ya yi magana"
zai za da taimako a kara wata labari fiye da kima. AT: " Da aljani ya fita daga cikin mutumin" ko "da aljani ya bar mutumin"
"mutumin da bai iya yin magana ba yayi magana"
"Ya na fitar da aljani da ikon Ba'alzabuba, sarkin aljanu"
"Wasu mutane sun gwada Yesu," Suna so ya hakikanta cewa ikon sa daga Allah ne.
suka tambaya shi ya bada wata alama daga sama" ko "suna neman ya ba su wata alama daga sama." Hakan ne suke so ya hakekance da cewa ikon sa daga Allah ne.
"mulkin" a nan an nufin mutane a ciki. wannan za'a fadan ta a wata siffa. AT: "idan mutanen mulki sun yi fada a tsakaninsu, za su hallakar da mulkin"
A nan "gida" na nufin iyali. AT: idan mutanen iyali suna faɗa da juna, zasu rusa iyalin su"
"faɗuwa kasa da rushewa."wannan sifar gidan rushe wa na nufin hallakan iyalin idan su na faɗa da juna.
"sheɗan" a nan na nufin aljanu wanda suke bin sheɗan da sheɗan da kansa. AT: "Idan sheɗan da membobin sa suna faɗa da junan su"
Yesu yayi amfani da tambayan domin ya koya wa mutane. wannan za'a iya juya ta kamar bayani. AT: Idan shaiɗan ... da mulkin sa ba za su dawama ba." ko "Idan sheɗan ... da mulkin sa zai rabu."
Domin kun ce da karfin Ba'alzabuba nake sa aljanu su bar mutane." Mahawaran sa mai zuwa za'a iya faɗan ta kamar baro-baro: AT: "Domin kun ce da karfin Ba'alzabuba nake sa aljanu su bar mutane. wannan na nufin cewa sheɗan ya rabu gaba da kan sa"
Idan ni ... da ikon wa masubin ka suke sa aljanu sa fita da karfi su bar mutane?" Yesu yayi amfani da tambaya domin ya koya wa mutane. ma'anar tambayan Yesu za'a iya bayyana. AT: "Idan ni ... toh za mu iya yarda da cawa masubin ka suma suna fitar da aljanu da ikon Ba'alzabuba. amma baku yarda da cewa gaskiya ne."
"masubin ka wadda suke fitar da aljanu da ikon Allah zasu sharanta ku domin kun ce ina fitar da aljanu da ikon Ba'alzabuba"
"Yatsa Allah" na nufin ikon Allah.
"wannan ya nuna cewa mulkin Allah ya zo gun ku"
wannan na magana akan Yesu yadda ya yaki sheɗan da dukkan aljanu sa kamar Yesu mutum mai karfi ne wanda ya kwashe abin mutum mai karfi.
"cire kayan faɗan mutumin da kariyansa"
"ba wanda zai sata abun"
"saci kayan sa" ko dauki ko mai da yake so"
wannan na nufin kowane mutum ko kugiyan mutane. "Wanda ba nawa bane gaba yake dani, wanda kuma baya taya ni tarawa watsarwa yake yi" ko "wandanda basu tare dani gaba suke dani wadan da kuwa basu taya ni tarawa watsarwa suke yi"
"wanda baya tallaba mini" ko "wanda ba ya aiki da ni"
"aikin gaba dani"
Yesu na nufin tara almajiren da suke bin sa. Wannan za'a iya fadin ta baro baro. AT: "duk wanda ba ya sa mutanesu guna ya na sa mutane su guje ni"
Wannan na nufin "wurin da ba'a feya zuwa" wurin da ruhun mugaye ke yawo.
"Idan ruhun bai sami hutawa a wurin ba"
wannan na nufin mutum wanda da yake raye. AT: "mutum wanda ni na ke a raye"
Wannan misalin ya yi magana akan mutum kamar shi gida ne wanda aka share tsaf an kuma sa komai a inda ya kamata. na nufin cewa gidan ba komai. wannan za'a iya bayana ta a wata siffa da labarin a bayyane. AT: "neman mutum kamar gidan da wanda mutum ya share ya kuma shriya ya sa komai a ida ya kamata, amma ya bari ba komai" ko "neman mutumin kamar gidan da aka share an gyara amma ba komai"
Wannan kalman" farko" na nufin yanayi mutum lokacin da ya na da ruhu mara kyau kamin ya barshi. AT: "muni fiye da yanayin ɗanekamin ruhun ya barshi"
Wannan sashin maganar anyi amfani da ita a nan damin a nuna abu mai muhimmanci a labarin da ya auko. idan yarenku suna da wata hanyan yin haka,zaku iya amfani da shi anan.
Wannan karin maganar na nufin " yi magana da karfi feye da amon taron"
Wannan sashin jikin matan an nufim mace gaba daya. AT: "Yana da kyau ga macen da ta haife ka ta kuma shayar da kai a maman ta" ko "Yaya murnan macen da ta haife ka ta kuma shayar da kai a mamanta zai zama"
"Zai iya zama mafe kyau ga wadansu"
"ji sakon da Allah ya fada"
"Da mutane suna karuwa a taron" ko "Da taron suna kara grima"
A nan "zamani" ana nufin mutanen da ke cikin ta. AT: "Mutanen dake zama a wancen lokacin mugayen mutane ne. suna nema... ma su" ko Mutanen da ke zama a wannan lokacin mugayen mutane ne. kuna nema... ma ku"
Wannan labarin akan wace irin alama take nema za'a iya bayyana ta. AT: "suna so in yi wata aikin al'ajibi da zai zama shaida cewa na zo daga Allah"
Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: " Allah ba zai ba ta wa alama ba"
"meya faru da Yunana" ko "aikin al'ajibin da Allah ya yi wa Yunana"
wannan na nufin cewa Yesu zai zama alaman daga Allah wa Yahudawan wancan ranan daidai yadda Yunana ya zama alama daga Allah wa mutanen Nineba
Yesu yana magana akan sa.
"wannan mutanen da suke zama ayau"
wannan na nufin Sarauniyar Sheba. Sheba wata mulki na kudun cin israi'la.
"zai tashi tsaye ta yi shari'a wa mutanen wannan zamani"
Wannan karin magana na nufin cewa ta zo daga wuri mai nisa. AT: ta zo da wuri mai nisa sosai" ko "ta zo daga wuri mai nisa"
Yesu yana magana akak sa. AT: Ni, wanda na fi Sulemanu, ina nan"
Yesu yana magana akak sa. AT: Ni, na fi Sulemanu"
zai zama da taimako ka bayyana cewa wannan na nufin tsohon brinin Neniba. AT: "mutanen da ssuka zauna a tsohon brinin"
wannan ya kumshe maza da mata. AT: " mutanen"
"mutanen wannan zamani"
"domin mutanen Nineba sun tuba"
Yesu ya na magana akak sa. zai zama da taimako a bayyana cewa ba su saurare shi ba. AT: "ko da shike na fi Yunana, amma baku tuba ba"
"boye shi ko ya sa ta a karkashin kwando"
Fahimtatciyar batun da fi'ili a cikin kashi za iya samarma. AT: amma mutum ya sa shi a mazaunin ta" ko " mutumin ya sa shi a kan tebur"
a sashin wannan misalin, abin da suka gan yesu ke yi ya ba su ganewa kamar yadda ido ke bada gani wa jiki. AT: "idon ka kamar fitilar jikine"
Ido misali ne na gani.
jiki shine dukan rayuwan mutum.
A nan "ido" na misalin gani. AT: "Idan gani ka na da kyau" ko "idan kana gani da kyau"
Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "haske zai cika dukan jikin ku" ko "za ka iya gann kowace irin abu da kyau"
A nan "ido" na misalin gani. AT: " Idan ba ka gani da kyau" ko " kana talauci a gani"
"ba za ka iya gani ba"
"ka tabbata cewa abin da kake tunani haske ne ba duhu ba" ko "ka tabbata cewa ka san abin ka haske ka kuma tabbata cewa ka san abin dake duhu"
Yesu ya faɗi gaskiyar kuma kamar tamka. yayi maganar mutane da suki ciki da gaskiya kamar fitilar da hasken sa ya haskaka.
Marubucin yayi amfani da wannan kalman domin ya sa alama a sabuwar abin da ya auko.
wannan na nufin gidan Farisawa.
Wannan al'adane na cin abincin shakatawa kamar dina wa mutane su ci suna kwance da daɗi kewaye da tebur. za ka iya juya shi da kalma da yaren ka suke amfani da shi yadda mutane ke yi idan suna cin abin ci. AT: "zauna a tebur"
Farisawan suna da doka wanda sai mutane sun wanke hannayen su kamin su zama da tsabta kamar masu biki a ga ban Allah.AT: "wanke hannayen ka" ko "wanke hannayen ka kamin ka za ma sa tsabta"
wankin bayan ganga sashi ne na al'adun al'adar yin Farisawa ne
wannan sashin misali ne bambanci ne na dubawa a hankali yadda suke wanke bayan kwanuka da yarda suke watsar da yanayin su na ciki.
wannan furcin zai iya zama maza ko mata, ko da shike Farisawa da Yesu yake magana da su maza ne.
Yesu ya yi amfani da tambayan domin ya kwaɓi Farisawan da rashin ganawar su cewa abin da ke zuciyar su al'amrin Allah. wannan za'a iya juya shi kamar bayyani. AT: "wanda yayi cikin shine ya yi wajen"
wannan na nufin abin da za su dinga yi da kwapina su da tasaar su. AT: "Ku ba wa talakoki abin da ke ciki" ko "ko zama masu bayarwa"
"za ku zama da tsabta gaba daya" ko "za ku zama da tsabta ciki da waje"
"kuna bawa Allah daya daga cikin goma na'ana'a da yin nadama da wasu ganye daga cikin lambun ku. "Yesu ya na bada misali ya da Farisawan suke ba da zakkan abin da suka samu.
wannan ganyayene. mutane suna saganyayen kadan ne a cikin abincin su domin ya ba shi dandano. idan mutanen basu san na;ana'a da yin nadama ba,sai ku yi amfani da sunan ganye da suka sani ko gabadayan furci kamar "ganye"
ma'ana mai yuwa 1) " kowace irin kayan lambu" 2) " kowace irin ganyen lambu" ko 3) "kowace irin shukin lambu."
"son Allah" ko "kauna ga Allah." Allah shine kauna.
"babu kasawa" yi nauyin da cewa wannan yaka mata a dinga yi.wannan za'a iya bayanata kamar mai yaƙani. AT: "ka kuma yi duk sauran abubuwa masu kyau"
" kujera mafi kyau"
"kuna so mutane su gaishe ku da daraja"
Farisawan suna kama da kabarbarun da ba alama domin kuna da kyau kamar masu biki, amma kuna sa mutane kewaye da ku su zama mara tsabta.
Wannan kabarbarun ramuka ne a ƙasa ida ake binne mattce. ba su da farin dutsen da mutane suki sawa akan kabarbarun domin souran su gan su.
Idan yahudawan suna tafi ya akan kabarin, za su zama marasa tsabta. wannan kabarbarun marasa alama neke sasu su yi haka.wannan za'a iya fadan ta da kyau. AT: "da rashin sani kuma yana sasu su zama marasa tsabta"
Wannan ya gabatar dawani sabuwar hali a labarin.
maganar Yesu game da Farisawa mai yuwa ta shafe malaman ataura ta Yahudawa.
Yesu ya bayyana cewa yayi niya ya hukunta aikin malaman ataura da Farisawa.
"kun sa wa mutane damuwa mai nauyi wanda baza su iya daukawa ba." Yesu ya yi magana akan wani game da sa wa mutane doka kamar ya basu kaya ne mai nauyi su dauka. AT: "kun dame mutane da ba su dokoki daya wa su bi"
Ma'ana masu yuwa 1) " ku yi komai duka ku taimaki mutanen daukan kayan" 2) "yi dukan kokari ku dauki kayan da kan ku."
Yesu ya kwaɓi Farisawan da malaman shari'an. sun sani game da kisan annabawan, amma basu hukunta su kakan kakanninsu domin kashe su. AT: "Toh amma sun yi ƙarar su, kun tabbata ku kuma yarda"
wannan yana nufin maganar da aka yi a baya da cewa malamin atauran suna damin mutane da dokoki.
"hikima" an yiwa kamar zai iya yi wa Allah magana. AT: "Allah cikin hikimar sa ya ce" ko " Allah cikin hikima yace"
"Zan aika annabawa da manzannai wa mutane na. "Allah ya bayyana kafin da cewa zai aika annabawa da manzanai wa kakan kakar Yahudawa maso sauraron wanda Yesu yake yi masu magana.
"mutane na za su tsananta su kuma kashe wasu annabawa da manzanai."Allah ya bayyana kafin da cewa kakan kakar Yahudawa maso sauraron wanda Yesu yake yi masu magana za su tsananta su kuma kashe wasu annabawa da manzanai.
Mutanen da Yesu yake yi masu magana za'a rike su alhakin ƙashe annabawan da suka yi da kakan kakanin nasu. AT: "saba da haka Allah zai rike tsaran alhakin dukan mutuwar annabawab da mutane suka ƙashe"
"jinin" ... zubar" na nufin jinin da ya zuba da aka ƙashe su. AT: "kisan kai da aka yi wa annabawa"
Wannan yana yuwa fada na a tsohon alkawari wada ya kwaɓi mutanen isra'ilawa akan bautar gumaka. wannan ba uban yahaya mai baftisma bane
Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "wanda mutane suka kashe"
Yesu ya yi maganan gaskiyar Allah kamar gida ne wanda malaman sunki su shiga sun kuma ha wasu samun makullin su shiga suma. Allah, sun kuma hana wasu sani shi kuma.
Wannan misalin na nufin samun hanya na shigan gida ko dakin ajiya
"kai da kanka ba ka shiga ka sami sani ba"
"Sa'an da Yesu ya bar gidan Farisawa"
marubata da Farisawa basu yi jayayya doimn su kare ra'ayinsu ba, amma domin su yiwa Yesu tarko cewa ya karya dokan Allah.
wannan na nufin suna so su fadi wani abu wanda ba daidai ba su yi masa shari.
1Da jimawa kadan, bayan da mutane da yawa suka taru kwarai har suna tattaka junansu. Sai ya fara yin magana da almajiransa. "Ku yi lura da yisti na Farisawa, wanda shine manufunci.2Amma ba abin da ke rufe wanda ba za a tone ba, ba kuma abin da ke boye wanda ba za a sani ba. 3Saboda haka ba abin da za ku fadi a asirce wanda ba za a ji shi a cikin sarari ba. Abin da ku ka fadi da rada cikin lungu, za a yi shelarsa a ko'ina.4Ina gaya maku abokaina, kada ku ji tsoron wanda da za su kashe jiki. Bayan haka kuma ba abin da za su iya yi. 5Bari in gargade ku a kan wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron shi wanda bayan ya kashe zai iya jefa ku cikin jahannama. I, ina ce maku ku ji tsoronsa.6Ba a kan sayar da 'yan tsuntsaye biyar a kan anini biyu ba? Duk da haka, Allah ba zai manta da ko daya daga cikinsu ba. 7Har ma gashin da ke kan ku ya san yawan su. Kada ku ji tsoro, ku kun fi tsuntsaye daraja a wurinsa.8Ina gaya maku, dukan wanda za ya shaida ni a gaban mutane, Dan Mutum kuma za ya shaida shi a gaban mala'kun Allah. 9Kuma dukan wanda ya ki ni a gaban mutane, za a ki shi a gaban mala'ikun Allah. 10Dukan wanda ya yi magana gaba da Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma shi wanda ya yi sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.11Idan suka kawo ku gaban majami'a, ko gaban masu shari'a, ko gaban masu iko, kada ku damu da abin da za ku fada domin ku kare kanku. Ko kuwa abin da za ku ce. 12Gama Ruhu Mai Tsarki zai koya maku abin da za ku fadi a wannan lokaci."13Sai wani a cikin taron ya ce masa, "Malam, ka yi wa dan'uwana magana ya raba gado da ni 14Yesu ya ce masa, "Kai, wanene ya sa ni in zama alkali, ko matsakanci a kanku?" 15Sai kuma ya ce masu, "Ku yi lura kada ku zama masu hadama, gama ba abin da mutum ya mallaka ne ya fi mahimmanci a cikin rayuwar sa ba."16Sa'annan Yesu ya fada masu wani misali, ya ce, "Gonar wani mutum ta bada amfani sosai, 17ya yi tunani, ya ce, 'Me zan yi, domin ba ni da wurin da zan iya ajjiye amfanin gonata?' 18Sai ya ce, na san abin da zan yi. Zan rushe rumbuna na in gina wadansu manya-manya, a nan zan ajjiye hatsi na da dukan abubuwa. 19Sai in ce da raina, "Ya raina, kana da abu da yawa da aka ajjiye dominka, sai ka huta, ka ci, ka sha, ka yi murna."20Amma sai Allah ya ce da shi, 'Wawan mutum, a cikin daren nan ana son ranka daga wurinka. Kayan da ka tara ka shirya wa kanka, na wa za su zama?' 21Haka wanda ya tara wa kansa dukiya yake, idan ba shi da dukiya a wurin Allah."22Yesu, ya ce da almajiransa, "Saboda haka ina cewa da ku, kada ku damu da rayuwarku, wato, abin da za ku ci, ko abin da za ku sa a jikinku. 23Gama rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.24Ku dubi hankaki wadanda ba sa yin shuka, ba sa yin girbi. Ba su da rumbuna ko dakunan ajjiya, amma Allah ya na ciyar da su. Ku fa kun fi tsuntsaye daraja! 25Wanene a cikinku ta wurin sha'awarsa za ya iya karawa kansa kwanaki? 26Idan ba ku iya yi wa kanku dan karamin abu ba, me ya sa za ku damu da sauran abubuwa?27Ku dubi furanni a daji - yadda suke yin girma. Ba su kan yi aiki ba, ba su kan yi kadi ba. Ina gaya maku, ko Sulaimanu, a cikin darajarsa, bai sa tufafin da suka fi nasu kyau ba. 28Idan Allah ya sa wa ciyawa tufafi masu kyau haka, wadda yau tana nan, gobe kuma a sa ta a wuta, ta yaya zai kasa sa maku tufafi, ku masu kankantar bangaskiya!29Kada ku damu da abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kuma kada ku yi alhini. 30Gama dukan al'umman duniya suna neman wadannan abubuwa, kuma Ubanku ya san kuna bukatar wada nan abubuwan.31Amma ku bidi mulkinsa, wadannan abubuwa kuma za a kara maku su. 32Kada ku ji tsoro, ku 'yan kanana, domin da murna Ubanku zai ba ku mulkin.33Ku sayar da abin da ku ke da shi ku ba matalauta. Kuyi wa kanku jakukkuna wadanda ba za su lalace ba, ku yi ajjiya cikin sama inda abin ba ya karewa, inda barayi ba za su iya zuwa ba, kwari kuma ba za su iya lalatawa ba. 34Domin inda dukiyarka take, can zuciyarka za ta kasance kuma.35Ku rage tsawon tufafinku, ku yi dammara, ya zama fitilarku tana ci koyaushe, 36ku kuma zama kamar wadanda suke jiran mai gidansu ya dawo daga gidan buki, domin duk sa'adda ya zo ya kwankwasa kofa, nan da nan za su bude masa.37Masu albarka ne wadannan bayi, wadanda ubangijinsu za ya tarar suna jiran dawowar sa. Gaskiya ni ke gaya ma ku, zai yi dammara yasa su zazzauna ya ba su abinci shi da kansa. 38Ko da ubangijinsu ya zo da dare, ko da tsakar dare, ya tarar da su a shirye suna jiransa. Masu albarka ne wadannan bayi.39Kuma ku san wannan, da mai gida ya san lokacin da barawo zai zo, ba zai bari a fasa masa gida a shiga ba. 40Sai ku zauna da shiri fa domin ba ku san lokacin da Dan Mutum zai dawo ba."41Sai Bitrus ya ce masa, "Ubangiji, mu ka ke fadawa wannan misali, ko ga kowa da kowa ne?" 42Sai Ubangiji ya ce, "Wanne shugaba ne, mai aminci, mai hikima kuma wanda ubangijinsa za ya damka bayinsa a hannunsa, domin ya kula da su, ya ba su abincinsu a kan lokaci? 43Mai albarka ne wannan bawa, wanda ubangijinsa za ya tarar da shi yana yin abin da aka sa shi ya yi. 44Hakika, ina gaya maku, zai danka dukan malakarsa a gareshi.45Amma idan wannan bawa, ya ce a cikin zuciyarsa, 'Ubangiji na yayi jinkirin dawowa,' sai ya fara dukan bayin, maza da mata abokan bautarsa, ya ci ya sha, ya bugu, 46ubangijin bawan nan zai dawo a lokacin da bawan bai sa tsammani ba, kuma a cikin lokacin da bai sani ba, ya daddatsa shi gunduwa-gunduwa, ya kuma hada shi da marasa aminci.47Bawan nan, ya san halin ubagijinsa, amma bai shirya yayi abin da ubangijinsa yake so ba. Zai sha duka da bulala da yawa. 48Amma shi wanda bai sani ba, kuma yayi abin da ba daidai ba, ba zai sha duka da bulala da yawa ba. Dukan wanda aka ba abu da yawa, za a kuma nemi abu da yawa daga wurinsa. Kuma ga wanda aka ba abu da yawa amana, za a nemi abu mafi yawa daga gareshi.49Na zo domin in sa wuta a duniya, na so da ta riga ta kama. 50Amma ni, ina da baftisma wadda za a yi mani baftisma da ita, kuma na kagara, da an riga an yi ta!51Kuna zaton na zo duniya domin in kawo salama? Na ce maku a'a, amma tsattsaguwa. 52Daga yanzu za a sami mutane biyar a cikin gida daya, kuma za su rarrabu, mutane uku suna gaba da biyu, biyun kuma suna gaba da ukun. 53Da da mahaifi za su yi gaba da juna, dan zai yi gaba da mahaifinsa. Mahaifiya za ta yi gaba da diyarta, diya kuma gaba da mahafiyarta; uwar miji za ta yi gaba da matar danta, matar da kuma gaba da uwar mijinta."54Yesu, ya kuma gaya wa taron, "Da kun ga hadari ya taso daga yamma, nan da nan sai ku ce za a yi ruwa, haka kuwa ya kan zama. 55Idan iska tana busowa daga kudu sai ku ce za a yi zafi mai tsanani, haka kuwa ya kan faru. 56Munafukai, kun iya fasarta yanayin kasa da sama, amma baku iya fasarta abin da yake faruwa yanzu ba?57Me ya sa ba ku iya gane abin da zai tamake ku? 58Idan kuna tafiya wurin shari'a da abokin husumarka, ka yi kokari ku daidaita tun a kan hanya domin kada ya kai ka wurin mai shari'a. Domin kada mai shari'a ya mika ka ga mai tsaron kurkuku, shi kuwa mai tsaron kurkuku ba zai nuna maka sani a cikin kurkuku ba. 59Na gaya maka, ba za ka iya fitowa ba sai ka biya dukan kudin da a ke binka?
Yesu ya fara koya wa almajiren sa a gaban mutane dubu.
Wannan yana yuwa alokacin da marubucin da farisawan suke neman hanya su yiwa Yesu tarko.marubucin ya yi amfani da wannan domin ya sa alama a sabuwar abin da ta auko.
Wannan labarin baya ne awnda yake fadan saitin labarin.
"taro mai yawa sosai"
Wannan yana yuwa an ari ayi nauyi saboda mutane suna ma'il kusa da juna kuma zasu iya taka juna" ko "suna taka junan su a kafa"
"Yesu ya fara magana wa almajiren sai ya ce masu"
Kamar yadda yisti yake bazuwa a dukan kullun dun kulen burodi, nasu munafurcin ya na bazuwa a cikin al;umma. AT: " Ka tsare kan ka game da munafurcin Farisawan, wanda ke kama da yisti" ko "Kayi hankali kada ka zama kamar munafurcin Farisawan. halin muguntar su ya na shafan kowa kamar yanda yisti ya shafan kullun dun ulen burodi"
Wannan kalman "Amma" ya hada aya da ayan da ya wuce a baya akan munafurcin Farisawan.
"komai da yake a ɓoye zai bayyanu, "Wannan za'a iya bayyana shi a wata siffa. AT: "mutane za su san abin da mutani suka yi a boye"
Wannan na nufin abu daya ne yadda ya ke a farkon sashin bayanin domin a yi nauya gaskiyan ta. za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: mutane zasu san kowanni abu da wasu suka boye"
A nan "duhu" misali ne na "dare" wanda yana misalin "asirce . da "haske" wato misalin "rana" wanda shi ne misalin "abayyane. wannan saahin "za'a ji" za'a iya bayyana a wata siffa . AT: duk abin da ka fada asirce da dare, mutane za zasu ji ta da hasken rana"
wanna za'a iyabayyana ta a wata siffa. AT: "raɗa wa wani mutun"
"a dakin kulle" wannan na nufin magana asirce. " "asirce" ko "ɓoye"
"za'a yi iho da karfe" wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: " mutane za su yi shelar"
gidaje a Isra'ilasuna da kitan jinka, mutane sukan je su tsaya a sama su. idan zai janye hakalin mai karatu yayi tunanin yadda mutum zai je ya hau saman gida, toh sai a juya she da furcin gaba daya kamar "a wuri mafi tsaho domin kowa ya ji"
Yesu ya yi magana da al'majeren sa su daina wannan maganar su koma wata sabuwa, a wannan magana sai su yi magana akan rashin jin tsoro.
"baza su iya yin wata lahani ba"
wannan shashin "wanda" na nufin Allah. wannan za'a iya bada lada. AT: "ji tsoron Allah wanda, bayan ...yana da iko" ko "ji tsoron Allah, domin bayan ... yana da iko"
"bayan da ya kashe ka"
wannan bayani ce gaba daya akan ikon Allah ya sharanta mutane. baya nufin cewa wannan zai faru ne da al'majiren sa. AT: "yana da iko ya jefa mutane a cikin gidan wuta "
Yesu ya yi amfani da tambaya ya koya wa al'majiren sa. AT: "kun sani da cewa yan tsunsaye biyar akan sayar anini biyu."
kankananan tsuntsaye masu cin iri
wannan za'a iya bayaana ta a wata siffa da siffa mai yaƙini. AT: "Allah ba ya manta da ko dayan su" ko "Allah yana sane da kowa ce tsuntsaye"
wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: " Allah ya sani gashi nawa ne akan ka"
dalilin tsoron ba a fada ba. ma'ana mai yuwa 1) "Kada ka ji tsoron abin da zai faru da kai" ko 2) "sabada haka kada ka ji tsoron mutane cewa za su ji maka ciwo."
"Kuna da daraja sosai a gun Allah feye da tsuntsaye"
Yesu yayi magana da masu sauraron sa cewa suko ma wata magana su yi magana akan shaidawa.
menene shaidawaza'a iya faɗan ta ba shakka. AT: "duk wanda ya gaya wa wani cewa shi al'majiri na ne" ko "duk wanda ya yarda agaban mutane cewa yana biyayya da ni"
Yesu yana mai da kansa. AT: "Ni ɗan mutum"
"wanda ya musan ce ni a gaban mutane. "menene musu za'a iya fadan ta ba shakka. AT: duk wanda ya ki ya yarda da cewa shi al'majiri na ne" ko "ko ya ki ya cewa ya na beyayya da ni, shi"
"za'a ki shi." wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "ɗan mutum zai yi musun sa" ko " Ni zanyi musu cewa shi ba al'majiri na bane"
"Duk wanda yayi maganan da babu kyau akan ɗan mutum"
"za'a yafe masa."wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "Allah zai yafe masa wancan"
"maganar mugunta akan Ruhu Mai Tsarki"
wannan za' a iya furta da siffan fi'ili. AT: "amma shi...Allah ba zai yafe masa ba" ko "amma shi Allah zai dube shi da laifi harabada"
Ba'a fada wa ya kawo su ga shari'a ba.
"a cikin majami'a a yi maku tambayoyi a gaban shugabanan adini"
zai iya zama na tilas ka hada wanan ya za ma bayani. AT: "wasu mutane wanda suke da karfi a cikin ƙasa"
"a wan can lokaci" ko sa'a nan"
A wata al'ada, gado yana zuwa daga uba musamman in ya mutu. zaka iya ka bayyana cewa uban mai maganar ya mutu. AT: karaba gadon da ni tun da ubana ya mutu"
ma'ana mai yuwa 1)wannan wata hanya ce mai sauki na magana da bako ko 2)Yesu ya kwaɓe mutumin. yaren ku kila tana da wata hanya da suki magana da mutane kamar haka. wasu mutane basu juya wannan gaba daya.
Yesu yayi amfani da tambayan domin ya kwaɓe mutumin. wasu yaren zasu yi amfani da siffar jam'i "ku" ko "kai." AT: Ni ba alkali ko komatsakacin ku bane."
Wannan kalman "su" anan mai yuwa tana nufin dukan taron jama'a ne. AT: " sai Yesu ya cewa taron"
"ku kare kanku daga kowace irin handama." AT: "kada ku bar kanku ku so kawace irin abu" ko "kada ku bar sha'awancen kuna samun abubuwa ya yi mulki akan ku"
wannan tabbataccen labari ne na kowa. baya nufin takamaiman mutum. wasu yaren suna da hanyan furta wannan .
"abu nawane yake da su" ko "arziki nawa ne ya ke da su"
Yesu ya cigaba da koyasuwan sa da ba da almara.
Mai yuwa Yesu yana magana da dukan taron jama'a ne
"girman da gribi mai kyau"
wannan tambayan ya nuna yadda mutum yake tunani wa kansa.AT: "ban san abin da zanyi ba, domin bani da wani wuri babba da zan iya ajiye amfanin gonata!"
gini wanda manomi suke ajiya amfanin gana idan suka gribe
mallaka
zan ce wa kaina ,inada shi ... shekaru. huta... murna." ko "zan gaya wa kai na inada shi ... shekaru, domin in huta ... murna."
"Rai" yana nufi rayuwan mutum. AT: "za ka muyu yau da dare" ko "za dauki ran ka daga wurin ka yau da dare"
wa zai reki abin da ka tara?" ko "wa zai samu abin da ka shirya?" Allah ya yi amfani da tambaya domin ya sa mutum ya sani cewa ba zai reke wadannan abubuwan kuma ba. AT: "abubuwan da ka shirya zai zama na wani"
"tara abubuwa masu daraja a sama"
bai yi amfani da lokacin ko da dukiyan sa akan abubuwa masu amfani a wurin Allah ba
"domin wanan dalilin" ko "domin abin da wannan labarin ya koyas"
"sabo da rayuwan ka da abin da zaka ci" ko "sabo da samin abincisosai domin ka rayu"
"sabo da jikin ka, abin da za ka sa" ko "sabo da samun kaya da za ka sa a jikin ka"
wannan labari ne na daraja ga kowa. AT: "rayuwa yana da amfani sosai fiye da abincin da muke ci"
"jikin ka ya na da amfani sosai fiye da kayan da kake sawa"
Wannan na nufin kowanne1) hankaka, irin tsuntsu wanda take cin musamman hatsi, ko 2) hankaki, wata irin tsuntsu wanda take cin naman mataccen dabbobi. Masu sauraron Yesu suna daukan hankaki marasa amfani domin Yahudawa basu cin irin wannan tsuntsayen.
wannan warare ne wanda ake ajiye abinci.
Wannan maganar motsin rai ne, ba tambaya ba ne. Yesu yanuna nauyi akan yadda mutane su ke da daraja ga Allah fiye da tsuntsaye.
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya koya wa al'majiren sa . AT: bawa ni a cikin ku da zai iya karawa kansa kwanaki da zama mai radɗaɗi!"
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya koya wa al'majiren sa. AT: "Tunda baza ku iya yi wa kanku karamin abu ba, kada kudamu da sauran abubuwan."
"Yi tuntni yadda furanni suke grima"
furanni fure ne kyau da suke grima a daji.idan yarenku ba su da kalma wa lily.za ka iya yin iaki da wata fure mai kamar ta ko ka juya ta kamar "furanni"
tsarin da ake yin zare ko yadi na riga ana kiran ta "kadi."zai zama da taimako ka bayyana. AT: ba su yun zare domin su yi riga" ko "kuma ba su yin zare"
"sulemanu, wanda ya ke da dukiya mai grima" ko "sulemanu, wanda ya ke sa kaya masu kyau"
"Idan Allah ya sawa ciyayin gona reguna kamar haka, kuma shi" ko "Idan Allah ya ba wa ciyayin gana reguna mau kyaukamar haka, kuma shi." ana maganar Allah ya sa ciyayin sunyi kyau kamar Allah ya sa masu reguna ne masu kyau. AT: "Aian Allah ya sa ciyayin gonar sunyi kyau kamar haka, kuma shi"
Wannan za'a iya bayyana ta a watasiffa. AT: "wani yajefa shi cikin wuta"
wannan magana ce ba tambaya ba ne. Yesu yayi nauyi cewa zai hakika zai lura da mutane feye da yadda ya ke yi wa ciyawa. wannan za'a iya bayyana ssshi ba shakka. AT: "hakika zai sa mana kaya mafi kyau"
"kada ku damu akan abin da za ku ci ko za ku sha" ko "kada ku damu sosai da abun da za ku ci ko sha"
A nan "kashashen"tana nufin "marasa bangaskiya." AT: "dukka mutanen wasu kashassshe" ko " dukka marasabi na duniya"
wannan suna ci mai muhimmanci ga Allah.
"sa zuciya ga mulkin Allah" ko " sa bege ga mulkin Allah"
"wadannan abubuwa kuma za'a kara maka" "wadannan abubuwa" na nufin abinci riguna. wannan za'a iya bayyana shi a wata siffa. AT: "Allah kuwa zai ba ka wadan nan abubuwa"
Yesu yana kiran al'majiren sa garki. graki tarone na raguna ko akuyoyi wanda makiyayi yake lura da su kamar yadda makeyayi ya ke lura da tumakin sa, haka ne Allah ya ke lura da al'majiren sa. AT: "karamin kungiya" ko "tsada kungiya"
zai zama da taimako a fada abin da suka karba. AT: "ku bawa talakokin mutane kudin da kuka karba daga sayarwa"
Jakukkuna da ajiya a sama abu daya ne. duk suna nufin albarkan Allah a sama.
wannan shi ne albarkan ba wa ta;akoki. AT: "ta haka zaka yi wa kanka"
"jakan kuɗi wanda ba za a sami rami a kai ba"
"wanda ba zai kare ba " ko "mara ƙanƙnata"
"barayi ba za su zo kusa ba"
"asu ba su batarwa"
asu karamin ƙwaro ne wanda yake cin rami a kaya. za ka iya amfani da wata ƙwaro kamar tururuwa ko gara.
"zuciyar ka yana gun da ka ajiye arzikin ka"
A nan "zuciya" na nufin tunanin mutum.
Mutane suna sa rigunar tsarauta mai filawa. su na yin dama ra da shi domin su ɗage sa'anda su ke tafiya. AT: "Yi damara da regunar ku domin ku yi shirin bauta" ko "ka shirya domin bauta"
Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "ya zama fitilarku tana ci"
yesu ya umurce al'majiren sa su shirya domin sa haka kuma su zama kamar yaron gida wanda yake a shirye domin zuwan maigidan sa.
"dawo gida daga bukin aure"
Wannan na nufin kofan maigidan aikin yaron gidan ne ya buɗe masa kofa.
"yadda ya ke da kyau wa"
"wadan da maigidan ya same su a shirye su na giran dawa wan sa" ko "wanda suke a shirye lokacin da ya zo"
domin yaron gidan amintacce ne kuma yana a shirye ya bauta wa maigidan sa, mai gidan kuma zai basu lada ta wurin yi masu bauta.
tsakar dare wato daga karfe 9:00 pm da tsakar dare. AT: "tsakar dare" ko "kafin tsakar dare"
agogo na uku wato daga karfe 3:00am. AT: "ko idan ya zo da lati a cikin dare"
"san yaushe"
Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "da bai bar barawo ya fasa ma sa gidan sa ba"
Abin da ke kama kaɗai da barawo da kuma ɗan mutum shine mutane basu san lokacin da ko dayan su zai zo ba, ya ka mata su zauna a shiri.
"ba su san a wani lokaci ba ne"
Yesu yan amagana a kan sane. AT: Ni ɗan mutum zan zo"
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya amsa wa Bitrusba ta hanya kusakusa ba. ya sammanin wadanda su na so su za amintaccen manaja su gane da cewa wanan misalin akan su ne. AT: "Na fada na kowa ne wandanda ... daidai lokaci"
Yesu ya ba da wani misali yadda yaron gida zai zama da aminci sa'anda ya na jeran maigida.
"wanda ubangiji sa zai damka masa sauan yaran gidan a hanunsa"
"Yadda yake da kyau ga yaron gidan"
"idan ubangijin sa ya same shi ya na yin wancan aikin idan ya dawo"
Wannan furcin yana mufin ku lura kuna kulawa ma musamman da abin da zan fada.
"zai sa shi bisa udkan malakarsa"
Wannan nanufin yarao gidan wanda ubangijin sa ya damka masa sauran yaran gidan.
Anan " zuciya" misali hankali ne na mutum ko cikin zucicyar mutum. AT: " yi tunani wa kansa"
"maigida na ba zai dawo yan zu ba"
Kalman nan da aka juya anan "yaran gida namiji da namace" akan juyan su kamar "maza" da "mata" ya nuna da cewa yaran gidan kananane ko suna kaunar maigidan su.
Wannan kalman "rana" da "lokaci"
Ma'ana mai yuwa 1) wannan zuguiguita ne wa maigidan ya yi ma'amala da matsanancin horon yaron gidan, ko 2) wannan ya kwatanta yanayin da yaron gidan zaifalle kan a kuma binne shi kamar horo.
Wannan za'a iya juya ta a wata isffa mai yakani. AT: "Amma ga yaron gidan da ya san ra'ayin ubanjigin sa kuma bai shirya ya yi yadda ya kamata, maigidan zai yi masa bulala da yawa"
"abin da maigidan sa yake so ya yi ...shi"
dukkan yaren gidan an yi masu horo, amma wanan sashin ya nuna dukyaron gidan da ya ki ya yi beyyaya da maigidan sa za'a yi ma sa horo sosai fiye da tsoran yaran gidan.
Wanan za'a iya bayana ta a wata siffa. AT: "za'a nemi sosai ga duk wannan da ya karba sosai" ko "maigidan zai nemi sosai ga duk wanna da aka bashi dayawa"
Wanan za'a iya bayana ta a wata siffa. AT: "mai gidan zai tambaya fiye da dayen ... da yawa" ko "maigidan za' nemi fiye da dayan ... da yawa"
Wanan za'a iya bayana ta a wata siffa. AT: "duk wanda maigidan ya ba shi dukiya da yawa ya lura da su" ko "duk wanda maigidan ya ba shi abin da zai yi"
"Na zo in jefa wuta akan duniya" ko "Na zo in sa wa duniya wuta." Ma'ana mai yuwa1) Yesu ya zo domin ya sharan ta mutanen duniya ko 2) Yesu ya zo domin ya tsakake masubi ko 3) Yesu ya zo domin ya kawo rabuwa tsakanin mutane.
Wannan magana ya nuna nauyin yadda yake so ya faru.AT:"na so sosai da ya kama" ko "na so da ta riga ta kama"
Anan " baftisma" ya na nufin yadda Yesu zai sha wahala. kamar yadda ruwa ya ke rufemutum sa'anda ake yi ma sa batisma, tadda wahala za ta rufe Yesu. AT: "Dole na in sha wahala ta hanyan batisma mai ban tsoro" ko "Dole ne wahala ta rufe ni a masayin mutum yin batisma kuma ruwa ta rufe"
Kalman "amma" anyi aiki da shi ya nuna cewa a zai iya jefa wuta a duniya ba sai ba yan da ya ga ma batisman sa.
Wannan furcin nauyin yadda ya sha wahala. AT: " Na sha wahala mai ban tsoro kuma zai zama haka sai na gama wannan batisma na shan wahala"
Yesu ya yi tanbaya domin ya nuna masu cewa ya zo ya gyara abin da su ke yi da mara kyau. zaku iya kawo kalman "Na zo" da aka cire a bayani na biyu. AT: "Kuna sammanin na zo in ba da zaman lafiya ne a duniya, amma na gaya ma ku ban kawo ba. amma na zo in kawo rabuwa"
"abokan gaba" ko "saɓani"
Wannan misalin irin rabuwan da za'a samu ne a cikin iyali.
zai zama da taimako ka fada cewa wannan na nufin mutane. AT: "za'a sami mutane biyar a gida daya"
"yi wa hamayya ... yi wa hamayya ... yi wa hamayya ... yi wa hamayya ... yi wa hamayya ... yi wa hamayya ... yi wa hamayya ... yi wa hamayya ..."
Wannan yanayi na kullum ya nufin ruwa na zuwa a isra'ila.
"Ruwa na zuwa" ko "za'a yi ruwa"
Wannan yanayi na kullum ya na nufin cewa zafin yanayi na zuwa a isra'ila
"duniya da sararin sama"
Yesu ya yi amfani da tambaya ya ƙwabe taron. Yesu ya yi amfani da tanbayan domin ya fursuna su. za'a iya juya ta kamar bayani. AT: "ku san yadda za ku bayyana wannan lokacin
Yesu ya yi amfani da tanbaya domin ya ƙwabe taron. za'a iya juya ta kamar bayani. AT: "Ku dakan ku iya gane abin da ke mai kyau. "
"a na ku yin"
Yesu ya yi amfani da yanayin munafurci domin ya koyar da taron. tsini sa she ne su tsida shawara a abubuwan da za su iya tsi da shawara ba sai sun je kotu jama'a ba. Wannan za'a iya sake fadan ta domin ya zama mai sauƙin ganawa ba zai iya faruwa ba. AT: "Amma in za ku je ... kudi kaɗan"
tunanin Yesu ya na magana da taron, yanayin da ya ke bayana abu ne wanda mutum zai je ya yi tunani akai shi kadai. a wasu yaren kalmanan "ku" zai zama mafuradi.
"shriya sha'anin da abokin gaban ka"
Wannan na nufin majistare, amma ajilin anan ƙayyadadde ne da yi wa kurari.
"bai dauke ku ba"
"duka kudin da abokin gaban ka ke so"
1A lokacin, wadansu mutane suka gaya masa game da galilawa wadanda Bilatus ya gauraye jininsu da hadayunsu. 2Sai Yesu ya amsa masu yace "Kuna tsammani wadannan Galilawa sun fi duk sauran Galilawan zunubi ne, da suka sha azaba haka? 3A'a, ina gaya maku. In ba ku tuba ba, dukanku za ku halaka kamarsu.4Ko kuwa mutane goma sha takwas din nan da suna Siluwam wadanda hasumiya ta fado a kansu ta kashe su, kuna tsamani sun fi duk sauran mutanen Urushalima laifi ne? 5Ina gaya maku ba haka bane. Amma duk wanda ya ki tuba, dukanku za su hallaka"6Yesu ya fada wannan misali, "Wani mutum yana da baure wanda ya shuka a garkar inabinsa sai ya zo neman 'ya'yan itacen amma bai samu ba. 7Sai mutumin ya ce wa mai kula da garkar, "ka ga, shekara uku kenan nake zuwa neman 'ya'yan wannan baure, amma ban samu ba. A sare shi. Yaya za a bar shi ya tsare wurin a banza?8Sai mai lura da garkar ya amsa yace, 'Ka dan ba shi lokaci kadan in yi masa kaftu in zuba masa taki. 9In yayi 'ya'ya shekara mai zuwa to, amma in bai yi 'ya'ya ba sai a sare shi!"'10Wata rana Yesu yana koyarwa a wata majami' a ran Asabaci. 11Sai, ga wata mace a wurin shekarunta goma sha takwas tana da mugun ruhu, duk ta tankware, ba ta iya mikewa.12Da Yesu ya gan ta, sai ya kira ta ya ce mata, an warkar da ke daga wannan cuta." 13Sai Yesu ya dora hannunsa a kanta, nan da nan sai ta mike a tsaye ta fara daukaka Allah. 14Amma shugaban majami'a yayi fushi domin Yesu yayi warkarwa a ranar Asabaci. Sai shugaban ya amsa yace wa jama'a, "Akwai ranaku shida da ya kamata a yi aiki. Ku zo domin a warkar da ku amma ba ranar Asabaci ba."15Amma Ubangiji ya amsa masa ya ce, "Munafukai! Ashe kowannenku ba ya kwance Jakinsa ko Sa daga turkensa ya kai shi banruwa ran Asabaci? 16Ashe wannan 'yar gidan Ibrahim, wanda shaidan ya daure ta shekara goma sha takwas, wato ba za a iya kwance ta a ranar Asabaci kenan ba?17Da ya fada wadannan abubuwa, dukansu da suka yi adawa da shi suka kunyata, duk taron kuwa suka yi ta farin ciki da abubuwa masu daraja da yayi.18Sai Yesu ya ce, "Yaya za a misalta mulkin Allah, kuma da me zan kwatanta shi? 19Yananan kamar kwayar mastad, wanda wani mutum ya dauka ya jefa ta a lambunsa, ta kuma yi girma ta zama gagarumin itace, har tsuntsaye suka yi shekarsu a rassanta."20Ya sake cewa, "Da me zan kwatanta mulkin Allah? 21Yana kamar yisti wanda wata mace ta dauka ta cuda da mudu uku na garin alkama don ya kumburar da shi."22Yesu ya ziyarci kowanne birni da kauye, a hanyar sa ta zuwa Urushalima yana koyar da su. 23Sai wani ya ce masa, "Ubangiji, wadanda za su sami ceto kadan ne?" Sai ya ce masu, 24"Ku yi kokari ku shiga ta matsatsiyar kofa, domin na ce maku, mutane dayawa za su nemi shiga amma ba za su iya shiga ba.25In dai maigida ya riga ya tashi ya rufe kofa, sannan za ku tsaya a waje kuna kwankwasa kofar kuna cewa, 'Ubangiji, Ubangiji, bari mu shiga ciki'. Sai ya amsa yace maku, 'Ni ban san ku ba ko daga ina ku ka fito.' 26Sannan za ku ce, 'Mun ci mun sha a gabanka, ka kuma yi koyarwa a kan titunanmu.' 27Amma zai amsa ya ce, "Ina gaya maku, ban san ko daga ina ku ka fito ba, ku tafi daga wurina, dukanku masu aikata mugunta!'28Za a yi kuka da cizon hakora a lokacin da kun ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu da dukan annabawa a mulkin Allah amma ku-za a jefar da ku waje. 29Za su zo daga gabas, yamma, kudu, da arewa, za su ci a teburin abinci a mulkin Allah. 30Ku san da wannan, na karshe za su zama na farko, na farko kuma za su zama na karshe."31Nan take, wadansu farisiyawa suka zo suka ce masa, "Ka tafi daga nan domin Hirudus yana so ya kashe ka." 32Yesu ya ce, "Ku tafi ku gaya wa dilan nan cewa, 'Duba, na fitar da aljanu, ina warkarwa yau da gobe, kuma a rana ta uku kuwa zan gama aiki na.' 33Ko da kaka, dole ne in ci gaba da tafiyata yau, da gobe, da kuma jibi, don bai dace a kashe annabi nesa da Urushalima ba.34Urushalima, Urushalima masu kisan annabawa, masu jifan wadanda aka aiko gare ku. Sau nawa ne ina so in tattara 'ya'yanki kamar yadda kaza take tattara 'ya'yanta a cikin fukafukanta, amma ba ki so wannan ba. 35Duba, an yashe gidanki. Ina kwa gaya maku ba za ku kara ganina ba sai ran da kuka ce, 'Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji.'"
Yesu ya cigaba da magana a gaban taron. wasu mutane a cikin taron sun yi masa tambaya sai ya fara amsa masu. wannan ya cigaba da labarin da yake luka 12: 1.
wannan shashin ya hada abin da ya auko zuwa ga karshen aya 12, da Yesu ya na kayar da taron jama'an.
a nan "jini" yana nufin mutuwan Galilawa. mai yuwa an kashe su ne sa'anda su ke hadayan su. wannan za'a iya bayyana kamar yadda ya ke a cikin UDB.
Galilawa sunfi yin zunubi ne ... hamya? A'a, na gaya maku." ko "wannan ya nuna maku cewa Galilawa sun fi yin zunubi ... hanya? A'a, na gaya maku."Yesu ya yi amfani da tambaya ingiza gane wa mutanen. AT: "ka na tunanin cewa wannan mutanen Galilawa sun fi yin zunubi ... hanya, amm basu yi" ko "kada ka yi tunanin cewa mutanen galilawa sun fi yin zunubi ... hanya"
Anan "NA gaya maku" nauyin." AT: ba shakka ba su yin zunubi" ko "ka yi kuskure ka yi tunani cewa wahalar su ne yake nina cewa sun fi yin zunubi"
"dukan ku kuma za ku mutu a wanna hanya" za su gan sakamakon sa, ba wai cewa za su mutu a irin wannan hali.
mutu
Koyasuwan Yesu na biyu akan mutane da suka sha wahala. AT: "koka duba waɗancan" ko "yi tunani akan waɗancan"
"mutane 18"
Wannan sunan wuri na a c.
"shin wannan ya hakikanta maku cewa su suka fi yin zunubi ... Urushalima? A'a, na ce." Yesu ya yi tambaya domin ya tsokani ganawan mutanen. AT: "kuna tunanin cewa sun fi yin zunubi ... Urushalima, amma na ce ba su bane" ko "Na ce kada kuyi tunanin cewa sufi yin zunubi ... Urushalima
Taron sun dauka ce wa sun mutu a cikin wannan yanayi mai ban tsoro domin ƙwarai sun fi yin zunubi. Wannan zai iya zama a bayane. AT: "sun mutu domin su suka fi yin zunubi mzfi muni"
"wasu mutane." Wannan kalman anan ajili ne na gaba daya na mutum.
A nan "Na ce a'a" nauyin "A'a." zai zama da taimako a fadi tsini Yesu ba shakka. AT: " Na tabbata cewa basu mutu ba domin su fi yin zunubi" ko "b daidai bane ka yi tunanin cewa wahalar su ya nuna su fi yin zunubi"
Yesu ya fara gaya wa taron misali domin ya bayyana maganar sa na karshe, " Amma in ba ku tuba ba, sukan ku za ku hallaka."
Mai garkar inabin yana da wani mutum wanda ya shuka bishiya a garkar inabin.
Mutumin ya amfani da tanbaya ya yi nauyin da cewa itacen banzane sai ya cewa gadina ya tsare shi. AT: "Kada ka bar shi ya ɓata ƙasa abanza."
"Kada ka yi komai wa itacen" ko " Kada ka tsare shi"
"sa masa taki a ƙasa." taki kashain babboni ne. mutane sukan sa shi a ƙasa domin ya sa ƙasa da itace su yi kyau don shuki. AT: " Sa ma sa taki"
zai za da taimako ka fada abin da zai faru. AT: "Idan ya na da 'ya'ya shakara mai zuw, sai mu bar shi ya cigaba da grima"
bawan yana ba da na shi shawaran; ba doka ya ke bayar wa ga mai sh ba. AT: "ka gaya mini in tsare shi" ko "Zan tsare shi"
mai wallafa ya yi amfani da wannan kalman domin ya nuna farkon abin da ya auko.
" a rana Asabaci" wasu yare za su ce " Asabaci" domin ba mu san wace rana ce Asabaci ba.
Wannan kalma "ga" anan ya nuna mana wani sabon mutu a labarin.
"shekara 18"
"mugun ruhu da ya sa ta mara ƙarfi"
"Mata, an warkar da ke daga cutan ki." Wannan za'a iya bayyana shi a siffar fi'ili: AT: "Mata, na warkar da ke daga rashin ƙarfi"
" Ya taɓa ta"
Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "sai ta mike"
"da haushi sosai"
"ce" ko amsa"
Wanna za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "Bari wani ya warkar da ki cikin wannan kwanaki shida"
"a rana Asabaci." Wasu yaren za su ce "Asabaci" domin ba mu san wata rana ce Asabaci ba.
"Ubangiji ya amsa wa mahukuncin ikilisiyan"
Yesu ya yi magana nan da nan da mahukuncin ikilisiyar, amma ajm'i ya hada da sauran mahukuntan adini kuma, Wannan za'a iya bayyana. AT: "kai da sauran mahukuntan adinin manafukai ne"
Yesu ya yi amfani da tanbaya domin ya sa su su yi tunani akan abin da sun riga sun sani. AT: "kowannenku ba ya kwance Jakinsa ko Sa daga turkensa ya kai shi banruwa ran Asabaci."
Wadan nan dabbobi ne wanda mutane suke lura da su ta wurin basu ruwa.
" a rana Asabaci" wasu yare za su ce " Asabaci" domin ba mu san wace rana ce Asabaci ba.
Wannan kari ne wanda take nufin, "zuriyar Ibarhim"
Yesu ya kwatanta ya da mutane suke daura dabbobi da yadda shaiɗan ya ƙuntata matan da wannan cuta. AT: "wandab shaiɗan ya ajiye naƙasasshe da ciwon ta" ko "wanda shaiɗan ya daure da wannan cuta"
"dogon shekar. 18." Wannan kalmar "dogo" anan na nuna nauyin shekara goma sha takwas doguwan lokaci ne wa matan ta sha wahala. wasu yaren zasu iya samun yadda za su yi nauyin akan wannan.
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya gaya wa mahukuntan ikilisiya cewa basu yi daidai ba. Yesu ya yi magana akan cutan matan kamar igiya ne ya daure ta. Wanna za'a iya juya ta kamar bayani mai ƙoƙari. AT: "ya na da kyau a kunce ta daga wannan daurin ciwon ... rana."
"Da Yesu ya faɗa wadannan abubuwa"
"abin ban mamakin da Yesu yake yi"
Yesu ya yi amfani da tambaya biyu domin ya gabatar da abin da ya ke so ya koyar. AT: "Zan gaya maku yadda mulkin Allah yake ... da me zan kwatanta da shi."
Asalin wannan tambayan daya ne da wanda ya rigaya. wasu yaren zasu yi amfani da dukan tambayan biyu wasu kuma zasu yi da daya.
Yesu ya kwatanta mulkin kamar kwayar mastad. AT: "Mulkin Allah kamar kwayar mastad ce"
kwayar mastad karamin iri ne wanda yake grima ya zama babban tushi. Idan wannan irin ba'a santa ba, wannan shashin za'a iya juya ta da sunan wata iri mai kamar ta ko karamin iri."
"shuka ta cikin lambu."mutane suna shuka wata iri ta gun jefa su domin su warwasu a cikin lambun.
Wannan kalmar "babba" magana ne da ta nuna bambancin itacen da karamin iri. AT: "karamin babban itace"
"tsuntsayan sararin sama." AT: "tsuntsayen da suke tashi sama" ko " tsuntsayen"
Yesu yayi amfani da wata tambayan domin ya gabatar da abin da yake soya koyar. AT: "zan gaya maku wata abu wanda zan kwatanta da mulkin Allah."
Yesu ya kwatan ta mulkin sama kamar yisti data ke cikin kullun burodi. AT: "Mulikn Allah kamar yisti ne"
Karami yisti ne ake bukata ya ta da kullun . Wannan za'a iya fadan ta da saukin ganawa kamar tadda take a UDB.
Wannan garin na da yawa, tunda kowane mudu yana kamar lita 13.zaka iya amfani da ajilida al'adan ku suke amfani da ita su auna gari. AT: "wannan garin na da yawa"
Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa Alla .AT: "Allah zai cece mutane kadan ne?
"Yi kokari domin ka shiga ta matsatsiyar kofa." Yesu yana maganar hanyan shiga mulkin Allah kamar karamin kafa ne a gidan.tumda Yesu ya na magana da kungiyan, "ku" a wannan umurni jam'i ne.
Da cewa tabbatacceyar kafan matsatsiya ce yana da wuya ka shiga ciki. juya shi a inda za ka ajiye ma'a nar tukuru.
ya nuna cewa ba za su iya shiga ba domin wahalar shigan. iya na gaba ya bayyana wahalar.
"bayan da mai shi"
Wannan na nufin mai gidan dake da matsatsiyar kofa a ayan wanda su regaya. wannan misali Allah ne a masayin mahukuncin mulkin.
Yesu ya yi wa taron magana. siffar "kai" jam'i ne. yana yi masu magana kamar baza su shiga mulkin ta matsatsiyar kofan ba.
"buga kofan." wannan ƙoƙene na samun hankalin mai shi.
"tafi daga wurina"
Wannan aikin yana sananniyar aikatawa, nuna babban ɓakin ciki da baƙin ciki. AT: "kuka da cizon hakora domin babban baƙin ciki"
Yesu ya cigaba da magana da taron kamar ba za su shiga mulkin sama ba.
"amma kai da kanka ka jefa waje." Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "amma Allah zai sa ka da karfi a waje"
Wannan na nufin "daga kowane wuri."
zai za na ko ina a yi magana akan murnan mulkin Allah kamar buki. AT: "zasu yi buki a mulkin Allah"
zama farko na nufin muhimmanci ko grimama. AT: "zama mai muhimmanci ... zama mai muhimmanci na karshe" ko "Allah zai grimama ... Allah zai kunyatar"
"anjima bayan Yesu ya gama magana"
juya wannan kamar gargaɗi ne wa Yesu. suna bashi shawara ya tafi wani waje ya zama mara haɗari.
Heridus zai sa mutane su kashe Yesu. AT: "Heridus zai aika mutanen sa su kashe ka"
Yesu yana kiran Heridus yanyawa. yanyawa wata karamin karan daji ne. Ma'ana mai yuwa 1) Heridus ba kurari bane gaba daya 2) Heridusmai sa ruɗewa ne.
"ba kome" ko "duk yadda" ko "duk abinda ya faru"
Shugaban Yahudawa ya nemiya bautawa Allah. amma duk da haka kakan kakanninsu sun kashe annabawan Allah da yawa a Urshelima, kuma Yesu ya san za'a kashe a wurin shima. AT: "
Yesu yayi magana kamar mutanen Urshelima suna jinsa. Yesu ya faɗa haka say biyu domin ya nuna masu yadda yake baƙin ciki da su.
Idan zai zama da mamaki ka yi magana da ƙasar, zaka iya faɗan she dasaukin ganewa cewa Yesu yana magana ne da mutanen ƙasar: "ku mutanen da kuka kashe annabawan kuma kun jefi wanda aka aika maku"
Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "wadanda Allah ya aika maku"
"Na so in." Wannan magana ne ba tanbaya bane.
anyi kwatancin mutane kamar 'ya'yan Urshelima." AT: "in tattara mutanen ki" ko "in tattara mutanen Urshelima"
Wannan ya nuna kwatanci yadda kaza ta ke tattara 'ya'yan ta daga lahani ta wurin rufe su da fukafukanta
Wannan annabine yake yin anbci akan wata abun da ya kusan faru. ya nuna cewa Allah ya daina lura da mutanen Urshelima, da haka miyagu zasu iya faɗawa su kore so. Ma'ana mai yuwa1) Allah zai yashe su. AT: "Allah zai yashe ka" ko 2) ƙasan su zai zama ba komai. AT: "za'a yashe gidan ku"
"baza ku gan ni ba sai lokacin yazo da za ku ce" ko "lokacin daza kugan ni za ku ce"
A nan "suna" yana nufin karfi da ikon Ubangiji.
1Wata ranar Asabaci, ya shiga gidan wani daya daga cikin shugabanin Farisawa domin cin abinci, mutane kuwa suna sa masa idanu. 2Sai ga wani a gabansa mai ciwon fara. 3Yesu ya tambaye masanan attaura da Farisawa, "Ya halata a wakar a ranan Asabaci, ko a'a?"4Amma suka yi shiru. Yesu kuwa ya kama shi, ya warkar da shi, ya kuma sallame shi. 5Sai yace masu, "Wanene a cikinku in yana da jaki ko takarkari ya fadi a rijiya ran Asabaci, ba zai fitar da shi nan da nan ba?" 6Sai suka kasa ba da amsar wadannan abubuwa.7Sa'adda Yesu ya lura da yadda wadanda aka gayyato sun zabi mazaunan alfarma, sai ya ba su misali yana ce masu, 8"Sa'adda wani ya gayyace ka zuwa bikin aure, kada ka zauna a wuri mai daraja, domin yana yiwuwa an gayyaci wani wanda ya fi ka daraja. 9Sa'adda wanda ya gayyace ku duka biyu ya zo, zai ce maka, 'Ka ba mutumin nan wurinka,' sa'annan a kunyace za ka koma mazauni mafi kaskanci.10Amma idan an gayyace ka biki, sai ka je ka zauna a wuri mafi kaskanci, domin idan wanda ya gayyace ka ya zo, yana iya ce maka, 'Aboki, hawo nan mana'. Sannan za ka sami girma kenan a gaban dukan wadanda kuke zaune tare a kan teburi. 11Duk wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, wanda ya kaskantar da kansa, kuma daukaka shi za a yi".12Yesu ya ce wa mutumin da ya gayyace shi, "Idan za ka gayyaci mutum cin abinci ko biki, kada ka gayyaci abokanka, ko 'yan'uwanka, ko danginka, ko makwabtanka masu arziki, kamar yadda suna iya gayyatar ka, sai ya zama an maida maka.13Amma idan za ka kira biki sai ka gayyace matalauta, da nakasassu, da guragu, da makafi, 14za ka kuwa sami albarka da yake ba su da hanyar saka maka. Gama za a saka maka a ranar tashin masu adalci."15Da daya daga cikin wadanda ke zama akan teburi da Yesu ya ji wadannan abubuwa, sai ya ce masa, "Albarka ta tabbata ga wanda zai ci abinci a mulkin Allah!" 16Amma Yesu ya ce masa, "Wani mutum ne ya shirya babban biki ya gayyaci mutane da yawa. 17Da lokacin biki ya yi, sai ya aiki bawansa ya ce wa wadanda aka gayyata, "Ku zo, duk an shirya kome."18Sai dukansu, suka fara kawo dalilai. Na farko ya ce masa, 'Na sayi gona, lalle ne in je in gan ta. Ina rokonka ka dauke mani.' 19Sai wani ya ce, 'Na sayi shanu garma biyar, ina so in gwada su. Ina ronkan ka, ka dauke mani.' 20Wani mutum kuma ya ce, 'Na yi aure, don haka ba zan iya zuwa ba.'21Da bawan ya zo ya fadi wa maigidansa wadannan abubuwa, sai maigidan yayi fushi, ya ce wa bawansa, jeka da sauri ka bi cikin titunan birni da kwararo-kwararo, ka kawo gajiyayyu, da nakasassu, da makafi, da guragu.' 22Sai bawan ya ce, 'Maigida, abin da ka umarta an gama, amma har yanzu da sauran wuri."23Sai maigidan ya ce wa bawan, 'Jeka, ka bi kwararo-kwararo da hanyoyin karkara, ka rinjayi mutane su shigo, don a cika gidana. 24Gama ina gaya maku, babu ko daya daga cikin mutanen da na gayyata da farko da zai dandana bikina."25Ana nan, taron suna tafiya tare da shi, sai ya juya ya ce masu, 26"Duk mai zuwa wurina amma bai ki mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa, da 'ya'yansa, da 'yan'uwansa maza da mata ba - I, har da ransa ma, ba zai iya zama almajirina ba. 27Duk wanda bai dauki gijiyensa ya biyo ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.28Wanene a cikinku wanda yake niyyar gina bene, da ba zai zauna ya yi lissafin abin da zai kashe ba tun da farko, ko yana da ishashen kudi da zai iya kare aikin? 29Kada ya zama bayan da ya sa harsashin ginin, ya kasa gamawa, har duk wadanda suka gani su fara yi masa ba'a, 30su rika cewa, ga mutumin nan ya fara gini amma ya kasa gamawa.'31Ko kuwa wanne sarki ne, in za shi je yaki da wani sarki, da ba zai zauna da farko ya yi shawara ya ga ko shi mai jarumawa dubu goma zai iya karawa da dayan sarkin mai jarumawa dubu ashirin ba? 32In kuwa ba zai iya ba, to tun wancan yana nesa, sai ya aiki wakili ya kuma tambayo sharudan salama. 33Haka ma, ba wani a cikinku wanda bai rabu da duk abin da ya mallaka ba, da zai iya zama almajirina."34"Gishiri abu ne mai kyau, amma idan gishiri ya sane, da me za a dadada shi? 35Ba shi da wani anfani a kasa, ko ya zama taki. Sai dai a zubar kawai. Duk mai kunnen ji, ya ji."
Ranan Asabaci, Yesu yana gidan Farisawa. Aya 1 ya ba da labarin abin da ya auko.
Wannan ya nuna sabuwar abin da ya auko.
"ka ci" ko "Don cin abinci" burodi abu ne mai muhimmanci a sashin abinci kuma an yi amfani da shi alabarin a masayin abinci.
Suna so gan ko za su iya yima sa shari cewa ya yi waniabin da ba kyau.
Wannan kalmar "ga" yana nuna mana wani sabuwar mutum a labarin. yaren ko zasu iya samun wata hanya ta yin haka.Turanci sun yi amfani da "akwai wani mutum a gaban sa"
ciwon fara kuburin jiki ne wanda ruwa yake kawo wa daga wasu sashin a jiki. wasu yaren zasu samu suna wannan yana yi. AT: "yana shan wahala domin shashin jikin sa kubura da ruwa"
"shin dokan ya yarda mana mu yi warkasuwa a ranan Asabaci, ko ya hana"
Shugabanan ikkilsiyan sun ki su amsa tanbayan Yesu.
"Yuse ya kama shi mutumin wanda yake da ciwon fara"
Yesu ya yi amfani domin yana so su ga ne cewa za su taimake yaron su ko jikin su koda rana Asabaci ne. saboda haka yana da kyau ya warkar da mutane ko da ranan Asabaci ne. AT: "Idan wanin ku yana da yaro ko jaki ... za ku cire shi nan da nan."
sun sani da cewa abin da Yesu yake fadi daidai ne amma ba su so su yarda cewa ya fada daidai. AT: "Ba su da abin da zasu ce"
Yesu ya ci gaba da yiwa bakin magana a gidan farisawan wanda suka gayyace shi ya ci abin ci.
Zai za ma da taimako a gane wadannan mutane, kuma a bayyana wannan a wata siffa. AT: "wadan da shugabanan Farisawan suka gayata su ci abin ci"
"kujera na mutane masu daraja" ko "kujeran mutane masu muhimmanci"
Wannan za'a iya bayyana shi a wata siffa. AT: "Idan wani ya gayyace ka" *Dubi:
Wadannan aukuwa na "kai" mufuradi ne. Yesu yana magana da kungiyan kamar ya na magana da kowane dayan su.
Wannan za'a iya bayyana shi a wata siffa. AT: "domin mai bikin za gayaci wani wanda ya fika muhimmmanci"
Wannan aukuwa na "kai" yana nufin mutane biyu wanda suke son kujeran daraja.
"zaka je kunya da"
"wurn da bai da amfani sosai" ko "wurin mutane da ba su da muhimmanci"
Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. " idan wani ya gayace ka"
"ka zauna a nan wurin mutane mafi muhimmanci"
Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: sa'a nan wanda ya gayyaci zai daraja ka"
"wanda yake so ya sami muhimmanci" ko "wanda ya dauki mutum mai muhimmanci"
zai zama mara muhimmanci" ko "za'a bashi wurin mara muhimmanci." Wanna za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "Allah zai za mar da shi mai kaskanci"
"wanda ya zaba ya zama mara muhimmanci" ko "wanda ya dauki wuri mara muhimmanci"
"zai zama mai muhimmanci" ko2 za'a bashi wuri mafi muhimmanci." Wanna za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "Allah zai daukaka shi"
"Farisawan da ya gayyace shi zuwa cin abincin"
"kai" mafuradi ne domin Yesu yana magana kai tsaye da Farisi daya gayyace shi.
wannan mai yuwa ba ya nufin cewa kada su gayyaci wadan nan mutane. kamar su gayyaci wadan su ma. AT: "kada ku yi gayyata kawai" ko "kada ku yi gayyata ko da yaushe"
"domin zasu iya"
"gayyace ku bikin cin abincin dare"
Wanna za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "a wannan hanya zasu biya kui"
zai zama da taimako a kara "har ila yau" tunda wannan bayyanin mai yuwa ba na kowa bane. AT:har ila yau gayyace talaka"
Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT Alllah za yi maka albarka"
"baza su iya gayyatan ka zuwa biki ba"
Wannan na nufin shari'a na karshe. AT: "idan Allah ya dawo da masu adalci rayuwa"
wannan ya shigar da wani mutum.
Mutumin baya maganar wani takamaimain mutum. AT: "Albarka ya tabbata ga duk wanda" ko "yadda yake da kyau ga kowanne"
Wannan kalman " burodi" yana nufin dukan abinci. AT: "shi wanda zai ci abinci"
Yesu ya fara faɗan wani misali.
Mai karaun ya iya gane cewa mai yuwamutumni yana da yaron gida wanda ya shirya abincin ya kuma gayyaci bakin.
Wannan sashin hanya ne na maganan wani mutum wanda ba a bada yakamaiman abu a kan sa ba.
"gayyaci mutane da yawa" ko "gayyaci baki da yawa"
"A lokacin abincin daren" ko "Idan za'a fara cin abin cin daren"
"a ce may ya sa ba su zo cin abincin daren ba"
Mai karatu ya iya gane da cewa wadan nan mutane sun yi magana kai tsaye da yaron gidan wanda mai gidan ya aika
"don Allah ka ya fe ni" ko "don Allah karbi uzuri na"
an yi amfani da shanu biyar domin aja kayan aikin noma. AT: "shanu 10 suyi aiki a filin"
ka yi amfani da furci na halitta a yaren ku. wasu yaren zasu ce "yin aure" ko "taukan mata."
"yaji haushi da mutanen da ya gayyata"
"ku kawo su anan su ci abin cin dare"
Zai zama dole ka fada ba shakka ka bayyana cewa yaron gidan ya yi yadda maigidan ya fada mishi yayi. AT: "da yaron gidan ya je yayi abin da aka ce yayi, ya dawo ya ce"
Wannan za'a iya bayyana shi a wata siffa. AT: "Na yi abin da ka ce inyi"
Wannan ya na nufin hanyoyi da suke wajen gari. AT: "asalin hayoyi garin"
"bukace su su shigo"
Wannan kalman "su" na nufin kowane wanda yaro gidan ya samu. "rinjaye duk wanda ka samu"
saboda mutane su caka gida na"
Wannan kalman "kai" jam'i ne, saboda haka ba 'a sarari yake ba da wanda ake magana.
Wannan kalmar anan "mutane" na nufin na miji da ya baligi" ba mutane gaba daya ba.
Wannan za'a iya bayyana ta a wata siffa. AT: "wadan da na gaya ta"
"zasu ji dadain abincin da na shirya"
A nan "ki" wannan magana ne yadda mutane zasu ƙarancin son da mutane zasu nuna wa mutane wani daban ban da Yesu. AT: Idan wani ya zo wuri na kuma bai nuna mina kauar da fiye da wanda yake nuna wa uban sa ... bazai iya zama almajire na ba " ko "sai dai kawai mutum ya nuna mini kauna fiye da wanda ya ke dashi wa uban sa ... ba zai iya zama almajire na ba"
Wannan za'a iya fadan ta da fi'ili. AT: "Idan wani yana so ya zama almajiri na, sai ya dauki giciyen sa ya bini"
Yesu baya nufin cewa kowan ne kirsta za'a giciye shi. Romawa su kan sa mutane su dauki giciyan su kafi a giciye su kamar alaman cewa mutum ya mika wuya ga Roma. Wannan misalin ya nuna cewa sun mika wuya ga Allah kuma sun yarda su sha wahala a kowa ce hanya domin su zama almajiren Yesu.
Yesu yayi amfani da tambaya domin ya hakikanta wa mutane cewa su kirga farashin aiki kafin su fara shi. AT: "Idan mutum yana so ya gina hasumiya, ba shakka zai zauna ya ƙudura ko yana da kudin da zai kare aikin."
Wannan zai zama hasumiyan kallo. "dogon gini" ko "dogon dandamali na kallon waje"
Zai zama da amfani a kara bayayni. AT: "Idan bai kirga farashin ba"
"bayan da ya gina tushin" ko "bayan da ya gama wata sashin ginin"
An gani da cewa bai iya ya gama ba domin ba shi da isasshen kudi. Wannan za'a iya bayyana. AT: "ba shi da isasshen kudi da zai gama"
Yesu yayi amfani da wannan kalman domin ya gabatar da wani yana yi yadda mutane za su kirga farashi kamin su yanke shawara.
Yesu yayi amfani da wata tambaya domin ya koya wa taro akan yadda zasu kirga farashi. AT: "kun sani cewa sarki ... za zauna tukun na ya nemi shawara ... mutane."
Ma'a na mai yuwa 1) "yi tunani a hankali" ko 2)"ji shawara ma shawarcinka."
"10,000 ... 20,000"
zai zama da taimako ka kara bayyanai.AT: "Idan ya ga da cewa ba zai iya yaki dayan sarkin ba"
"kalmomin da za su tsayar da yakin" ko "abin da dayan sarkin yake so yayi domin a tsayar da yakin"
Wannan za'a iya fadan ta da fi'ili mai yakani. AT: "sai dai wadan sun ku zasu iya ba da abin da suke da shi za su iya zama almajirai na"
"bar dukan abin da yake da shi"
"gishiri yana da amfani." Yesu yana magana akan wadan da zasu zama almajiren sa.
Yesu yayi amfani da tanbaya domin ya koya wa taron. AT: "bazai zama mai gishiri kuma ba." ko "ba wanda zai sa ya zama mai gishiri kuma."
mutane suna amfani da taki wa lambu ko a fili. gishiri n da bashi da ɗanɗano banzane bai isa ma a hadashi da taki ba. AT: @takin da yake warwase" ko taki"
Wannan za'a iya bayyana shi a wata siffa. AT: "wani zaya wurga shi"
zai za na halitta ga wasu yaren su yi amfani da mutum na biyu "kai" wanda yake da kunne, yaji
Ma'ana mai yuwa1)"kowane" tun da mutane na daidai suna da kunne, ko 2)"duk wanda zai iya gane," wanda yake nufin wanda suke so su ji Allah
"ya ji da kyau" ko "ya kasa kunne da abin da Na fada"
1To sai duk masu karbar haraji da masu zunubi suna ta zuwa wurin Yesu suna sauraronsa. 2Dukan Farisawa da Marubuta suna ta gunaguni da junansu, cewa, "Wannan mutum yana karbar masu zunubi, har ma tare suke cin abinci."3Yesu ya fadi wannan misali, ya ce, 4"Idan waninku yana da tumaki dari, sai dayarsu ta bace, wato ba zai bar tasa'in da taran nan a makiyaya, ya bi sawun wadda ta bata gudan nan har sai ya same shi ba? 5Idan kuwa ya same ta, sai ya dauke ta a kafadarsa yana farin ciki.6In ya dawo gida, sai ya kira abokansa da makwabta, yace masu, 'Ku taya ni murna don na samo tunkiyata da ta bata.' 7Ina gaya maku, haka kuma za a yi farin ciki a sama, a kan mai zunubi guda da ya tuba, fiye da kan masu adalci tassa'in da tara wadanda ba su bukatar tuba.8Ko kuwa wacce mace ce, in tana da kudi azurfa guda goma, in ta batar da daya, ba za ta kunna fitila ta share gidan, ta yi ta neman shi har sai ta same shi ba? 9In kuwa ta same shi sai ta tara kawayenta da makwabtanta, ta ce, 'Ku taya ni farin ciki don na sami kudin nan nawa da ya bace.' 10Haka nake gaya maku, abin farin ciki ne ga mala'ikun Allah idan mai zunubi guda ya tuba."11Sai Yesu ya ce, "Akwai wani mutum mai 'ya'ya biyu maza, 12sai karamin ya ce wa mahaifinsa, 'Baba, bani rabona daga cikin dukiyarka.' Sai mahaifinsa ya raba masu dukiyarsa tsakaninsu.13Bayan 'yan kwanaki kadan, sai karamin dan ya tattara duk mallakarsa, ya kama hanya zuwa wata kasa mai nisa. A can ya batas da kudinsa, yana sayan abubuwan da ba ya bukata, ya kuma batas da kudinsa a wajen masha'a. 14Bayan da ya batas da duk abin da ya ke da shi, sai aka yi babbar yunwa a kasar, sai ya shiga fatara.15Ya je ya mika kansa domin aiki ga wani dan kasar, sai ya aike shi cikin gonakinsa domin ya rika ba aladu abinci. 16Har yayi marmarin ya ci daga cikin barbashin da aladu suke ci, domin babu wanda yake ba shi wani abu ya ci.17Amma da hankalinsa ya dawo, ya ce, 'Barorin mahaifina su nawa ne da suke da abinci isasshe, amma ina nan a nan, ina mutuwa sabili da yunwa! 18Zan tashi, in tafi gun mahaifina, in ce masa, "Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka. 19Ban cancanci a kara kira na danka ba; ka mai da ni kamar daya daga cikin barorinka.'"20Sai ya tashi, ya taho wurin mahaifinsa. Amma tun yana daga nesa, sai mahaifinsa ya hango shi tausayi ya kama shi, ya ruga a guje, ya rungume shi, ya yi ta sumbatar sa. 21Dan kuma ya ce masa, 'Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka. Ban isa a kara kira na danka ba.'22Amma mahaifinsa ya ce wa bayinsa, 'Ku yi hamzari ku kawo riga mafi kyau, ku yafa masa. Ku sa masa zobe a hanunsa da takalma a kafafunsa. 23Sa'annan a kawo kiwataccen marakin nan, a yanka. Mu yi buki! 24Gama da na ya mutu a da, amma yanzu yana a raye. Ya bata a da, amma a yanzu an same shi.' Sai suka fara liyafa.25A wannan lokacin, babban dansa yana gona. Da ya kai kusa da gida, ya ji ana kade-kade da raye-raye. 26Sai ya kira wani bawan gidan, ya tambayi manufar wadannan abubuwa. 27Bawan ya ce masa, 'Dan'uwanka ne ya dawo gida, mahaifinka kuma ya yanka kiwataccen marakin nan, saboda ya dawo gida lafiya.'28Amma dan'uwan ya yi fushi, ya ki ya shiga ciki, mahaifinsa kuwa ya fito, ya roke shi. 29Amma babban dan ya amsa wa ubansa ya ce, 'Duba, duk yawan shekarun nan da nake bauta maka, ban taba karya umarnin ka ba, duk da haka ba ka taba bani ko dan taure da zan yi shagali tare da abokaina ba, 30amma da dan nan naka ya zo wanda ya fallasar da dukiyarka a kan karuwai, ka yanka masa kiwataccen marakin nan.31Sai mahaifin ya ce masa, 'Dana, ai kullum kana tare da ni, duk abin da yake nawa naka ne. 32Amma, daidai ne a yi murna da farinciki, don dan'uwan nan naka da ya mutu, amma yanzu yana da rai, da ya bata, amma yanzu an same shi.'"
Bamu san a inda wannan ya faru ba; ya faru randa Yesu yana koyaswa.
Wannan ya ba da almar sabuwar abin da ya auko.
Wannan magana ne domin ya nuna cewa suna da yawa. AT: "masu karban haraji da yawa"
"Wannan mutumin ya bar masu zunubi a gaban sa" ko "Wannan mutumni ya na dangantaka da masu zanubi"
Suna magana akan Yesu.
Wannan kalman" harma" ya nuna cewa harma suna tunanin cewa bai da kyau Yesu ya bar masu zunubi su zo kusa da shi,amma ya fi muni ya ci abinci da su.
A nan "su" anna nufin shugabanen adinin.
Yesu yayi amfani da tabayan domin ya tuna she mutanen cewa idan wani a cikin su ya rasa tunkiya sa, ba shakka za su je su nume shi. AT: "kowane da yan ku ... ba shakka za ku tafi ... sai kun same shi"
tun da misalin ya fara da "waye a cikin ku," wasu yaren zasu fara misalin da mutum na biyu. "Waye a cikin ku, Idan yana da tunkiya dari
"100 ... 99"
Haka ne makiyayi yake daukan tumakin sa. Wannan za'a iya bayyana . AT: " dauke ta a kafadarsa ya kai su gida"
"Idan mai tumakin ya dawo gida" ko "Idan ka dawo gida." ana nufin mai tumakin kamar yadda da ka yi a ayan da ya wuce.
"a wannan hanya" ko "kamar yadda makiyayin da abokan sa da makwabcin sa zasu yi murna"
"kowan ne daya zai yi murna a sama "
Yesu ya yi amfani da gatse yace Farisawan sun yi kuskura su yi tunani cewa ba su bukatan tuba. yaren ka zasu iya samun wata hanya dabam wanda za su iya furta wannan ra'ayi. AT: "mutane tasa'in da tara kamar ka, wanda suke tunani cewa ba su bukatan tuba"
"99"
Yesu ya ci gaba da bada wani misali. akan wata mata mai azurfa 10.
Yesu yayi amfani da tanbaya domin ya tunshe mutanen cewa idan suka rasa kuɗin azurfa su ba shakka zasu neme shi da ƙwazo. AT: "ko wace mata...bashakka zata kunna fitila ... ta nema da ƙwazo sai ta sa me shi."
Wannan yana yin da ba'a gani bane da labari gaskiye akan matan bane. wasu yaren zasu iya samum yadda za su nuna wannan, (Dubi:
"Idan mai zunubi guda ya tuba"
Wannan ya gabatar da wani sabuwar hali a misalin. wasu yaren zasu ce "Akwai wani mutum wanda"
Yaron yana so uban sa ya bashi nan da nan. Yarurukan da suke da siffar ummurni kamar ina som sa nan da nan zasu iya amfani da siffar.
""sashin gadon wanda ka shirya mini in kaba idan ka mutu"
"sakanin yaran sa biyu"
"ya kwashe abubuwan sa" ko "ya sa abubuwan sa a jaka"
"zama baya tunanin abin da zai biyo baya a abin da ya yi" ko "zaman mai wuya"
"rashin ruwa ya fita a gun kuma dukkar ƙasar ba abinci"
"ka rasa abin da kake so" ko "ba sa muwa sosai"
Wannan kalman "shi" yana nufin karamin ɗan.
"karɓa aiki da" ko "ya fara aiki wa"
"mutumin wancan ƙasar"
"ya bawa aladun mutumin abinci"
"yaso so sai ma ya ci." mun gane sosai domin ya na jin yunwa. Wannan za'a iya bayana. AT: "yana jin yunwa sosai har yana murnan ci"
Wannan bawon wake wanda yake yin grima a bayan itacan. AT: " " ko" "
Wannan ƙari na nufin ya gane menene gaskiyan, cewa yayi babban kuskure. AT: "ba shakka ya gane yana yin sa"
Wannan sashin furcin, ba tanbaya bane. AT: "Dukkan barorin mahaifina su nawa ne da suke da abinci isasshe"
Wannan mai yuwa ba maganan ba ne. Wannan karamin ɗan mai yuwa ya na jie yunwa sosai.
Mutanen Yahudawa wani lokaci suna kin fadan wannan kalman " Allah" sai su yi amfani da Wannan kalman "sama" a maimako. AT: " Na yi zunubi ga Allah"
"Ban isa a ci dani ɗanka ba. "Wannan za'a iya bayana shi a wata siffa. AT: "Ban isa a ci dani ɗanka ba
kayi haya na kamar barorinka" ko "kayi haya na sai in zama kamar barorinka." Wannan roƙo na ba ummurni bane. zai iya zama da taimako ka kara don Allah kamar yadda UDB yayi.
sai ya bar ƙasar ya fara tahowa gun ubansa."Wannan kalman "sai" ya ba da alamar abin da ya auko sabo da abin ya faru da farko. aA wannan hali, karamin yaron ya cikin bukata sai ya shirya ya koma gida.
"Amma tun yana daga nesa daga gida" ko " Tun yana daga nesa daga gidan ubansa "
"ya ji tausayin sa" ko "ya so shi daga cikin zuciyar sa"
Wannan uban yayi haka domin ya nuna wa ɗansa cewa ya na kaunar sa kuma ya ji dadi yadda ɗan ya dawo gida. Idan mutane suna tunanin cewa sabo ne ko bai yi kyau wa uban ya rungume shi har ma yayi wa ɗansa sumba, zaka iya sa yadda mutane a yaren ku suke nuna kauna wa yaran su. AT: "ya karbe sa da kauna"
Mutanen Yahudawa wani lokaci suna kin fadan wannan kalman " Allah" sai su yi amfani da Wannan kalman "sama" a maimako. dubi yadda ka juya wanna a [Luka 15:18]
riga mafi kyau a gidan." AT: " ko "tufa mafi kyau"
zobe alama me na iko wanda mutane suke sa wa a hanunsa.
mutane masu kudi a wancan lokacin suna sa takalma. amma daidai na zamani yanzu shi ne "takalma"
marakin karamin saniya ne.mutane suna bawa marakin su abinci domin su yi grima da kyau, idan suna so suyi buki sai su ci marakin. AT: "maraki mafi kyau" ko "karamin dabban da muke ta sa shi yayi ƙiba"
ya bayana cewa suna so a dafa naman za'a iya bayyana. AT: "a yanka a dafa"
Wannan misalin yayi maganar yaron kamar ya mutu. AT: "kamar da na ya mutu a da, amma yanzu yana a raye" ko "na ji kamar da na ya mutu, amma yanzu yana a raye"
Wannan misalin yayi maganar dan yata fi kamar ya bata. AT: "kamar da na ya bata amma yanzu na same shi" ko "da na ya bata amma yanzu ya dawo gida"
ya nuna cewa ya na gona domin ya na aiki a gurin.
Wannan kalman da a ka juya anan kamar "yaron gida" kullum an juya ta kamar "yaro." yana nuna cewa yaron gidan karami ne.
"me yake faruwa"
marakin karamin saniya ne.mutane suna bawa marakin su abinci domin su yi grima da kyau, idan suna so suyi buki sai su ci marakin dubi yadda zaka juya wannan sashin a cikin Luka 15:23. AT: " marakin mafi kyau" ko "karamin dabban da muke ta sa shi yayi ƙiba"
" a yawan shekarun nan"
"Na yi maka matsananciyar aiki mai tauri" ko "Na yi maka aiki mai turi kamar yaron gidan ka"
ban taɓa yimaka rashin biyayya ba ko in karya ummurninka" ko " ko yaushe i na yin biyayya da abin da ka gaya mini in yi"
Karamin akuya kankani ne kuma bai da sada kamar kiwataccen marakin. AT: "koda karamin akuya ne"
"wancan ɗan ka." babban yaron yana nufin ɗan uwan sa domin ya nuna yadda ya ji haushi.
Abinci misali ne na kuɗi. Bayan da wani ya ci abin ci, abin cin kuma bayanan ya zama ba abin da za'a ci. kuɗin da ɗan'uwan sa ya karba babu shi kuma ya zama ba abin da zai kashe. AT: "batar da dukiyan ka" ko "jefar da duk dukiyan ka"
Ma;ana mai yuwa 1) ya yi tunanin cewa yadda ɗan'uwan ya batar da kuɗin sa kinan ko 2) ya yi maganan karuwai kamar sun zuguiguita zunubin ɗan'uwan sa ya aikata a wancan ƙasa mai nisa"
Wannan kalman "shi" na nufin babban ɗan.
Uban yana tunashe babban aɗn cewa wannan ɗan daya dawo ɗan'uwan ka ne
Wannan misalin yayi maganar ɗan'uwan kamar ya mutu. dubi yadda aka juya wannan a [Luka 15:24]
Wannan misali yayi maganar ɗan ya tafi kamar ya bata. dubi yadda za'a juya wannan sashin a [Luka 15:24]
1Yesu ya kuma ce wa almajiransa, "Akwai wani mai arziki da yake da wakili, sai aka yi karan sa da cewa wannan wakili yana fallasar masa da dukiya. 2Sai mai arziki ya kira shi ya ce masa, 'Labarin me nake ji game da kai? Kawo lissafin wakilcin ka, don ba za ka sake zama wakili na ba.'3Sai wakilin ya ce a ransa, 'Kaka zan yi, da yake maigida na zai karbe wakilci daga hannuna? Gashi, ba ni da karfin noma ina kuwa jin kunya in yi roko. 4Na san abin da zan yi domin idan an fitar da ni daga wakilcin, mutane su karbe ni a gidajensu.5Sai wakilin ya kira kowanne daya da maigidansa ke bi bashi, yace wa na farkon, 'Nawa maigida na yake bin ka?' 6Ya ce, 'Garwan mai dari.' Sai ya ce masa, 'Ga takardarka, maza ka zauna, ka rubuta hamsin.' 7Ya kuma ce wa wani, 'Nawa ake binka?' Ya ce, 'Buhu dari na alkama.' Ya ce masa, 'Ga tarkardarka, ka rubuta tamanin.'8Sai maigida ya yaba wa wakilin nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama 'ya'yan zamanin nan a ma'ammalar su da mutanen zamaninsu sun fi 'ya'yan haske wayo. 9Ina gaya maku ku yi abuta ta dukiya ta rashin gaskiya, saboda idan ya kare, su karbe ku a gidaje masu dauwama.10Wanda yake da aminci a karamin abu, mai aminci ne a babban abu, wanda yake marar gaskiya a karamin abu, marar gaskiya ne a babban abu. 11Idan fa ba ku yi aminci da dukiya mara adalci ba, wa zai amince maku da dukiya ta gaskiya? 12Idan kuma ba ku yi aminci da kudin wani ba, wa zai ba ku kudin da ke naku?13Ba bawan da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya ko kuwa ya amince wa dayan, ya raina dayan. Ba za ku iya bauta wa Allah ku kuma bauta wa dukiya ba."14Da Farisawa da ke da kaunar kudi suka ji dukan wadannan abubuwa, suka yi masa ba'a. 15Sai ya ce masu, "Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abin da mutane suke girmamawa kwarai abin kyama ne a gun Allah.16Attaura da litattafan annabawa suna nan har zuwan Yahaya. Tun daga lokacin nan ake yin bisharar mulkin Allah, kowa kuma yana kokarin kutsawa zuwa cikinta. 17Duk da haka, zai fi sauki sama da kasa su shude, da ko digo daya na attaura ya shude.18Duk wanda ya saki matansa ya auri wata ya aikata zina, kuma wanda ma ya auri sakakkiya ya aikata zina.19Akwai wani mai arziki, mai sa tufafi na alfarma masu tsada yana shagalin sa kowace rana. 20Aka ajiye wani gajiyayye a kofarsa, mai suna liazaru wanda duk jikinsa miki ne, 21Shi kuwa yana marmarin ya koshi da barbashin da ke fadowa daga teburin mai arzikin nan har ma karnuka sukan zo suna lasar mikinsa.22Ana nan sai gajiyayyen nan ya mutu, malaiku kuma suka dauke shi suka kai shi wurin Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi, 23yana cikin hades yana shan azaba, sai ya daga kai ya hangi Ibrahim daga nesa, da Li'azaru a kirjinsa.24Sai ya yi kira ya ce, 'Baba Ibrahim, ka ji tausayi na, ka aiko Li'azaru ya tsoma dan yatsansa a ruwa ya sanyaya harshena, don azaba nake sha a cikin wannan wuta.'25Amma Ibrahim ya ce, 'Yaro, ka tuna fa a zamanka na duniya ka sha duniyarka, ka kuma karba abubuwa masu kyau, amma Li'azaru kuma sai wahala. Amma yanzu dadi ake bashi a nan, kai kuwa kana shan azaba. 26Banda haka ma, akwai rami mai zurfi, domin wadanda suke son ketarewa zuwa wurinku kada su iya, kada kuma kowa ya ketaro zuwa wurinmu daga can.'27Sai mai arziki ya ce, 'To ina rokonka, Baba Ibrahim, ka aike shi zuwa gidan mahaifina - 28domin ina da 'yan'uwa maza biyar, ya je ya yi masu gargadi kada su ma su zo wurin azaban nan.'29Amma Ibrahim ya ce, 'Suna da Musa da annabawa; bari su saurare su.' 30Sai mai arziki ya amsa, 'A'a, Baba Ibrahim, idan wani daga cikin matattu ya je wurinsu, zasu tuba.' 31Amma Ibrahim ya ce masa, 'In dai har basu saurari Musa da na annabawa ba, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su rinjayu ba.'"
Yesu ya fara gaya masu wani misali. akan maigida ne da manaja wanda ya ke bin sa kuɗi. wannan dukkan labari daya ne a rana daya kuma ya fara a [Luka 15:13]
Kashi na karshe kai tsaya akan Farisawa ne da marubucin, tagun almajiren Yesu mai yuwa suna cikin taron suna ji.
wannan ya gabatar da wani sabuwar hali a misalin.
Wannan za'a iya bayana a wata siffa. AT: "mutane sun shaida wa mutum mai kuɗin"
"shashancin sarafa arzikin mai kuɗin"
wannan mai kuɖɖin yayi amfani da tsawa wa manajan. AT: "na ji abn dakake yi"
"ka shirya rubutacceyan labari domin ka bawawani kuma" ko "ka shirya rubutaccen labari akan kuɗi na"
manaja yayi wannan tambayan wa kansa, kamar hanya ne na tunawa da abin da zai yi. AT: "ya kamata inyi tunanin abin da zan yi ... aiki"
Wannan na nufin mai kuɗi. manajan ba yaron gida ba ne. AT: "wanda ya bani aiki"
"Bani da karfi sosai da zan yi tonon ƙasa" ko Ba zan iya yin tono ba"
Wannan za'a iya bayana a wata siffa. AT: "idan na rasa aikin wakilci na" ko "idan mai gidana ya kabe aikin wakilci na"
Wannan ya nuna cewa mutane zasu bashi aiki, ko ko wasu abubuwan da zai nema don zama.
"mutane wanda suke da bassshin maigidan sa" ko "mutane wanda suke da abubuwan maigidan sa." a wannan labarin wanda yake bin su bashi sun rike masa mai zaitun da alkama.
"Wanda ake bin sa bashi ya ce ... manajan ya cewa wanda ake bin sa bashi"
wannan kiman 3,000 lita na mai zaitun.
"100 ... 50 ...80"
"Bill" karamin takarda ne wanda yake fadan nawa ake bin ka.
"manajan ya ce wa wani wanda ake bin sa ... wanda ake bin sa ta ce ...manajan ya gaya ma wani ya ce"
zaka iya juya wannan a mudun zamani. AT: "lita ashirin na alkama" ko kwando dubu na alkama"
"rubuta buhu takwas na alkama."zaka iya juya zuwa ga mudun zamani. AT: "rubuta lita dubu gama sha shida" ko "kwando dari takwas"
ayan bai gaya mana yadda maigidan ya koyi aikin manajan.
"yaba" ko "yi magana da kyau akan" ko " yarda da"
ya aikata wayo" ko "yayi abu mai hankali"
wannan ya na nufin manaja marasa aldalci wanda basu damu da Allah ba . AT: "mutanen wannan duniya" ko yan duniya"
A nan " haske" misali ne na abubuwan da ba na Allah ba ne. AT: "mutanen Allah" ko "mutanen allah"
"Ni" na nufin Yesu. Wannan sashin "Na gaya maku" ya nuna alaman labarin da yadda Yesu ya gaya wa mutanen suyi amfani da shi a rayuwan su.
Abin kula anan sine yin aiki da kuɗi domin taimaka wa mutane. AT: "yi abokantaka da mutane tawurin taimaka masu da arzikin duniya"
Ma'ana mai yuwa 1)yesu yayi amfani da da ya kira kuɗi "rashin gaskiya" domin bashe da amfani madawomi. AT: "da yin amfani da kuɗin duniya" ko "Yesu yayi amfani da misali da ya kira kuɗi rashin gaskiya domin mutane wani lokaci suna juya su yi amfani da shi ta hanyan rashin gaskiya. AT: "da yin aiki da kuɗin da ka samu a hanyan rashin gaskiya"
Wannan mai yuwa na nufin 1) Allah a sama,wanda yake jin dadi cewa kana aiki da kuɗi ka taimaki mutane, ko 2)abokan da ka taimaka wa da kuɗi.
Wannan na nufin sama, inda Allah yake zaune.
Mutanen da suke da aminci ...masu aminci ne kuma ...mutanen marar gaskiya marar gaskiya ne kuma." Wannan ya hada da mata.
"mai aminci ko a abubuwa kaɗan" ka tabbata cewa bai yi ka ba ka da aminci sosai ba.
" rashin gaskiya ko ma a abubuwa ɗan kaɗan. "ka tabbata cewa wannan bai yi kamar sau da yawa baka da gaskiya.
Dubi yadda zaka juya wannan a [Luka 16:09]
Yesu yayi amfani da tanbaya domin ya koya wa mutane. AT: "ba wanda zai yarda da kai da arzikin gaskiye." ko ba wanda zai baka arzikin gaskiye kayi wakilin ta."
Wannan yana nufin arzikin na gaskiye, ainihi kodadewa fite da kuɗi.
Yesu ysyi amfani da tanbaya domin ya koya wa mutane. AT: "ba wanda zai baka kuɗi domin kanka."
"yaron gida ba zai"
Ya nuna da cewa ba zai iya bauta wa mai gida dabam dabam a lokaci daya ba"
Wadannan sharaɗi biyu lallai iri daya ne. bambancin kawai shi ne na maigida farko an kishi a sharaɗi na farko, amma maigada na biyu a ki shi a sharaɗi na biyu.
"yaron gidan zai ki"
"ya so daya sosai"
"ko ya raina " ko "yaki dayan"
Wannan yana nufi kamar "ki" a sashin da ya wuce.
Yesu yana ma wasu kungiyan mutane magana, yaren da suke ka jam'i na "kai" zasu iya amfani da shi.
Wannan briki ne a koya suwan Yesu, kamar yadda aya 14 ya gaya mana labarin daga kasa yadda Farisawan suka yi wa yesu ba'a. aya 15,Yesu ya ciga ba da koyasuwa da amsa wa Farisawan.
Wannan kalman ya sa alama matsi a labarin daga kasa.
"wanda suke son samun kuɗi" ko "wanɗan da handaman kuɗi sosai"
"Farisawan sun yi wa Yesu ba'a"
"sai Yesu ya ce wa Farisawan"
"Kun ya kokari kuyi kyau a gaban mutanen"
A nan "zuciya" na nufin begen mutane. AT: Allah ya gane begen ka na gaskiye" ko "Allah ya san muradinka"
wannan za'a iya bayana a wata siffa. AT: "Abubuwan da mutane suke dauka cewa suna da amfani sosai Allah ya ki su"
Wanna yana nufin dukkan maganar Allah Wanda aka rubuta har zuwa wancan lokaci.
wannan yana nufin Yahaya mai baptisma. AT: "Yahaya mai baptisma ya zo"
Wannan za'a iya bayana a wata siffa. AT: "I na koya wa mutane bishara akan mulkin Allah
Wannan yana nufin mutane wadan da suke so so karbe koyasuwan Yesu. AT: Mutane da yawa suna yin duk abubuwan da zasu iya yi domin su shiga cikin ta"
Za'a iya fadan wannan bambancin a umurtan baya. AT: "ko kankanin digo daya na attaura zai dade sosai fiye da yadda sama da ƙasa zai bayana"
"digo" kankanin sashi ne na attaura.ya na nufin wani abune a attaura wanda kamar bashi da amfani, AT: "da ko kankanin bayanin attaura"
"bata2 ko dana bayanuwa"
"duk wanda ya saki matansa" ko "duk mutum da ya saki matansa"
"mai laifin zina ne"
"duk wani mutum da ya mata"
Wannan sashin ya gabatar da wani mutum a labarin Yesu. bai nuna da kyau ko mutum ne na gaskiye komutum ne kawai a labarin da Yesu yake fada domin ya umuta tsini.
"wanda ya sa tufafi mai kyau na lilin da rinan shunayya " ko "wanda ya sa tufafi mai tsada."ranin shunayya da tufafin lilin mai tsada sosai.
"yana jin dadin cin abinci mai tsada kowace rana" ko "yana kashe kuɗi da yawa ya tsaya abin da yake so"
Wannan za'a iya bayana a wata siffa. AT: "mutane sun ajiye wani mai roko mai suna liazaru a kofar sa"
Wannan sashin ya gabatar da wani mutum a labarin Yesu. bai nuna da kyau ko wannan mutum gaskiya ne ko mutum ne kawaia labarin da Yesu yake fada domin ya umurta tsini.
"a kofar gidan mai kuɗin" ko "a hanyan shiga gidan mai dukiyan"
"da miki a duk jikin sa"
"yana marmari da zai ci barbashi abin da ya fadi"
Wannan kalman "sumul" anan an nuna cewa abin da ya bi ya mafi muni fite da abin da aka rigaya an fada akan Liazaru. AT: "karin bayani akan wannan karnuka ma sun zo" ko "mafi muni, karnuka ma sun zo"
Yahudawa suna daukan karnuka kamar dabbobi ne mara tsarki. Liazaru yana ciwo sosai kuma mara ƙarfi ne ya hana karnuka lasan jikin ciwon sa
Wannna sashin anyi amfani da ita domin a sa alam a abin da ya auko a labarin. idan yaren ku suna da hanyan yin haka,zaku iya amfani da ita.
Wannan za'a iya bayana a wata siffa. AT: "malaiku kuma suka dauke shi daga nan"
Wannan ya nuna cewa Ibrahim da Liazaru suna zaune kusa da juna abikin Grika, a rubutun greek na biki. farincikin sama an bayana shi a litafi mai tsarki da ra'ayin biki.
Wannan za'a iya bayana a wata siffa. AT: mutane suka binne shi"
"ya tafi hades, inda yake shan wahala mai ban tsoro"
Wannan kari na nufin " ya kali sama"
"mai kuɗin ya yi kira ya ce" ko "ya yi iho wa Ibrahim"
Ibrahin kakan kakanin Yahudawane har da mai kuɗin.
dan Allah ka ji tausayi na" ko "dan Allah ka ji tausayi na"
"ka aiki liazaru" ko ka gaya wa Liazaru ya zo guna"
wannan don ya nuna kankani abin da ya ke roko. AT: "yana son dan yatsansa"
Ina wahala mai ban tsoro a cinkin wannan wuta" ko "ina shan wahala mai ban tsoro cikin wannan wuta"
mai arzikin daya daga cikin zuriyan Ibrahim ne.
"abubuwa masa kyau" ko "abubuwa masu dadi"
a wata irin hanya karban abubuwan mugunta" ko "a wata hanya karban abubuwan da suka sa shi shan wahala"
wannan ya ba da tabbacen cewa dukkan su sun karbe abu sa'an da suke masu rai a duniya. bawai an ce abin da suka karba daidai bane. AT:" sa'an da ya ke da rai ya karba"
"daidai yake anan" ko murna yake anan"
"wahala"
"kari akan wannan dalili"
Wannan za'a iya bayana a wata siffa. AT: "Allah ya sa katon kwazazzabo tsakanin mu da kai"
mai gangare da zurfi kwarai dakwari mai faɗi" ko "babbab rabuwa" ko " katon kwazazzabo"
"mutanen dasu ke so su ketare bayan kwazazzabo ... kada su iya" ko "idan wani yana so ya ketare ... kada ya iya"
"ka cewa Liazaru ya je gidan mahaifina" ko "don Allah ka aike shi gidan mahaifina"
Wannan na nufin mutanen gidan. AT: "iyali na"
"domin Liazaru ya yi masu gargadi"
"wannan wurin da muke shan azaba" ko "wannan wurin da make shan azaba mai ban tsoro"
Ya nuna cewa Ibrahim yaki ya aiki Liazaru zuwa ga yan'uwan mai kuɗin. Wanna za'a iya bayana . AT: "A'a bazan yi haka ba, domin yan'uwan ka suna da abin da Musa da annabawa suka rubuta da dadewa"
Wannan na nufin rubutun su. AT: "abin da Musa da annbawa suka rubuta"
"yan'uwam ka su saurara ga Musa da annabawa"
Wannan ya bayana yanayin da bai faru ba, amma mai kuɗin yana so ya faru. AT: "idan mutum da ya mutu ya ji wurin su" ko "idan wani wanda ya mutu ya ji ya gargaɗe su"
daga cikin duk wadan da su mutu. wannan furcin ya yi kwatancin duk wanda suka mutu cikin karkashin ƙasa.
A nan "Musa da annabawa" suna nufin abin da suka rubuta. AT: "Idan basu saurari abin da Musa da annabawa suka rubuta ba"
Ibrahim ya bayana abin da zai faru idan yana yin da ba 'a gani ba ya faru. za'a iya bayana a wata siffa. AT: "haka kuma ba wanda ya mutu da zai iya dawo ya basutabbaci" ko "ba za su yarda ba ko da matttace ya gaya masu"
Wannan kalman "daga matattu" yayi maganar duk wanda suka mutu daga karkashin ƙasa. su tashi daga cikin su wato su zama a raye kuma.
1Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su! 2Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.3Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa. 4Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!"5Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.' 6Ubangiji kuwa ya ce, "In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.7Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'? 8Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?9Ba zai yi wa bawan nan godiya ba domin ya yi biyayya da abubuwan da aka umarce shi ya yi, ko zai yi haka? 10Haka kuma, idan kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, 'Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibi ne kurum.'"11Wata rana yana tafiya zuwa Urushalima, sai ya bi iyakar kasar Samariya da Galili. 12Yayin da yana shiga wani kauye kenan, sai wadansu kutare maza guda goma suka tarye shi suna tsaye daga nesa da shi 13sai suka daga murya suka ce, "Yesu, Ubangiji, ka yi mana jinkai."14Da ya gan su, ya ce masu, "Ku je ku nuna kanku a wurin firistoci." Ya zama sa'adda suke tafiya, sai suka tsarkaka. 15Daya daga cikinsu da ya ga an warkar da shi, ya koma, yana ta daukaka Allah da murya mai karfi. 16Ya fadi a gaban Yesu, yana masa godiya. Shi kuwa Basamariye ne.17Yesu ya amsa ya ce, "Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina sauran taran? 18Babu wani da ya dawo ya girmama Allah sai wannan bakon kadai?" 19Sai ya ce masa, "Tashi, kayi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai."20Da Farisawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai bayyana, Yesu ya amsa masu ya ce, "Mulkin Allah ba lura ake yi da shi ba. 21Ba kuwa za a ce, 'Gashi nan!' Ko kuwa, 'Ga shi can ba!' domin mulkin Allah yana tsaknaninku."22Yesu ya ce wa almajiran, "Kwanaki na zuwa da za ku yi begen ganin rana daya cikin ranakun Dan Mutum, amma ba zaku gani ba. 23Za su ce maku, 'Duba can! 'Duba nan!' Amma kada ku je kuna dubawa, ko kuwa ku bi su. 24Kamar yadda walkiya take haskakawa daga wannan bangaren sararin sama zuwa wancan bangaren, haka ma dan mutum zai zama a ranar bayyanuwarsa.25Amma lalle sai ya sha wahaloli dabam dabam tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ki shi. 26Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Dan Mutum. 27Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har zuwa ga ranar da Nuhu ya shiga jirgi - ruwan tufana kuma ya zo, ya hallaka su duka.28Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine. 29Amma a ranar da Lutu, ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da kibiritu daga sama, aka hallaka su duka.30Haka kuma zai zama a ranar bayyanuwar Dan Mutum. 31A ranar nan fa, wanda yake kan soro kada ya sauka domin daukan kayansa daga cikin gida. Haka kuma wanda yake gona kada ya dawo.32Ku tuna fa da matar Lutu. 33Duk mai son ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai same shi.34Ina gaya maku, a wannan dare za a sami mutum biyu a gado daya. Za a dauka daya, a kuma bar dayan. 35Za a sami mata biyu suna nika tare. Za a dauka daya a bar daya." 36137Sai suka tambaye shi, "Ina, Ubangiji?" Sai ya ce masu, "Duk in da gangar jiki yake, a nan ungulai sukan taru."
Yesu ya cigaba da koyasuwa, amma ya sa hankalin sa a kan almajiren sa. wannan labarin daya ne kuma ya fara rana daya a cikin Luka 15:3.
"Abubuwan dasu ke riya wa mutane suyi zunubi ba shakka ya na faruwa"
ga duk wanda zai sa gwaji ya zo" ko "ga duk mutumin da zai sa mutane cikin gwaji"
wannan ya gabatar da yana yin da ba'a gani ba. yana nufin cewa horon mutum da ya wasu tun tube zai zama da tsanani da su mutu a cikin teku.
Wannan za'a iya bayan aa wata siffa. AT: "gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi" ko "ko wani zai rataye masa dutse mai nauyi a wuyan sa a jefa shi"
Wannan ajili na nufin maza tare da mata.
Wannan babba ne sosai. dutsen madauwari mai nauyi wanda ake amfani dashi domin nikan alkama gairn zuwa garin alkama. AT: "dutse mai nauyi"
Wannan anan ana nfin mutune wanda bangaskiyan su har yanzu mara ƙarfi ne. AT: "wannan mutunen wanda bangaskiyan su kanana ne"
Wannan na nufin zunubin da ba na gangan ci ba ne. AT: "yi zunubi"
Wannan bayanin na da sharaɗi kuma na magana akan abin da mai yuwa zai iya faruwa a nan gaba.
"dan'uwa" anan an yi amfani da hankalin wani wanda ku ke da yarda da. AT: "maibi
"gaya masa sosai cewa abin da ya yi bai da kyau" ko "gyara shi"
Wannan yana yin da ba a gani ba ne. ba zai taba faru ba, amma ko da ya faru, Yesu ya gaya wa mutane su yafe.
Wannan lamba bakwai a litafi mai tsarki sananniyar alama ce na cikawa. AT: "sau dayawa a rana, da kowanne lokaci"
Wannan da gajeran fashi ne a koyasuwan Yesu sa'anda almajeran sa suke yi masa magana. sai Yesu ya cigaba da koyasuwa.
"Ɗan Allah kara ma bangaskiya" ko "Ɗan Allah kara mana bangaskiya akan bangaskiyan mu"
kwayar mastad dan kankanin iri ne. Yesu ya nuna cewa basu da ko ɗan bangaskiya. AT: "Idon kuna da bangaskiya ko da karami ne kamar kwayar mastad,, ku" ko "Bangaskiyar ku bai yi babba kamar kwayar mustad ba - amma aidan ku, ne
Idon ba' a gane irin wannan itacen ba, zai zama da taimako a fada wani iri dabam. AT: "itacen ɓaure" ko "itace"
AT: "ka tuge kanka ka kuma dasa kanka a cikin teku" ko "ka cire gigiyan ka a ƙasa ka sa shi a cikin babban teku"
"itacen zai yi maka biyayya." wannan sakamakon na da sharaɗi. zai iya faru idan su na da bangaskiya ne kawai.
Yesu ya tambaye almajeransa domin ya taimake su su yi tunani akan ayukan yaron gida. Wannan zai iya juyata kamar bayyani AT: "amma ba ko ɗaya a cikin ku ...barci zai ce ... zauna ka ci abinci"
"bawa mai yi maka noma a gona ko lura da tumakin ka"
Yesu ya yi amfani da tambaya na buyu domin ya bayana wa al'majeren sa yadda ya kama ta su yi wa bawa. AT: "ba shakka zai ce masa ... ce ka sha"
"yi damara, ka yi mini hidima" ko "ka yi shiri da kyau ka lura da ni." mutane suna yin damara da kyau domin idan suna yin aiki kada rigunar su ya hana su yin aiki.
"Bayan haka sai ka yi mini hidima"
Yesu ya yi amfani da tambayan domin ya nuna wa mutane yadda suke yi wa bayi. AT: "Ba zai yi wa bawan nan godiya ba ... umarce."
AT: "abubuwan da aka umarce shi ya yi"
"daidai" ko "wannan ba gaskiya bane?"
Yesu yana magana da al'majeren sa, yaren da suke da jam'i na "kai" su yi amfani da shi. i:
AT: "da cewa Allah ya umurce ka"
Wannan kwatance ne ya bayana da cewa basu yi abin kirki da za'a yabe su ba. AT: "Mu bayi ne na gama gari" ko Mu bayin ba mu cencenci yabon ka ba"
Wannan sashin an yi amfani da ita domin a sa alamar a sabuwar abin da ya auko. Idan yaren ku na da wata hanya na yin wannan, sai su yi amfani da ita anan.
"da Yesu da al'majeren sa su na tafiya zuwa Urushalima"
Wannan shashin ba'a gane ainihin kauye ba.
AT: "maza goma kutare sun hadu da shi" ko "maza goma wanda suke da kuturta sun hadu da shi"
Wannan motsin jiki da ke nuna abin da ke zuciya mai ladabi domin ba'a barin kutare su zo kusa da mutane.
Wannan kari "a tada murya wani" na nufin a yi magana da ƙarfi. AT: "sun yi kira da murya mai ƙarfi" ko "sun kira da ƙarfi"
Takamenmen tambayan su su warke ne. AT: "Dom Allah ka yi mana jinkai ka warkar da mu"
Kutare suna so su nuna wa firistoci cewa sun warke da ga ciwon kukurta. AT: "ku nuna kanku wa firistoci domin su gwada ku"
Idon mutane sun warke, ba su da tsabta kamar wadan da su ka je biki. Wannan za'a iya bayyana. AT: "sun warke da ga ciwon kuturtan su sai sun zama da tsabta" ko "an warkar da su ga da ciwon kuturta"
"ya gane da cewa ya warke" ko "ya gane cewa Yesu ya warkar da shi"
"ya koma gun Yesu"
"ya daukaka Allah da ƙarfi"
ya durkusa ya sa fuskar sa kusa da kafafun Yesu"ya yi haka domin ya ɗaukaka Yesu
Yesu ya amsa game da abin da mutumin ya yi, amma ya na magana da taron jama'a da suke gun sa. AT: "Yesu ya cewa taron"
Yesu ya amfani da tambayan da bai damu da amsa ba na farko cikin uku domin ya nuna wa mutanen da ke kewaye da shi yadda ya ji mamaki da abin sa cizon yatsa da cewa mutun ɗaya ne cikin goma ya dawo ya ɗaukaka Allah. AT: "maza goma aka warkar" ko "Allah ya warkar da maza goma."
"Mai ya sa sauran taran ba su dawo ba?" AT: "sauran taran ma ya kama ta su dawo, suma."
AT: "Babu wani amma wannan bakon ya dawo ya ɗaukaka Allah!" ko "Allah ya warkar da maza goma, amma wannan bakon ne kawai ya dawo ya ɗaukaka Allah!"
Basamariyan bai da- kakan Yahudawa kuma basu bautawa Allah kamar yadda Yahudawa ke yi.
"Domin bangaskiyarka ka warke." Wannan ra'ayi "bangaskiya" za'a iya furta ta da jam'i "yarda." AT: "Domin ka yarda, ka warke kuma"
Wannan farkon. sabuwar abin da ya auko ne wasu juyin sun fara ta da "Wata rana" ko "sau ɗaya" AT: "Wata rana Farisawa suka tambaye Yesu, "Wane lokaci ne mulkin Allah zai bayyana?"
Mutane na tunanin cewa za su iya ganin wata alama zuwan mulkin. ra'ayin alama za'a iya faɗan ta ba shakka. AT: "Mulkin Allah ba ya zuwa da alama da mutane za su lura da shi"
Ra'ayin isimi nan "masarauta" za'a iya furta da fi'ili " mulki." AT: "Allah ya yi mulki a tsakanin ku"
Ra'yin kwanaki kwanaki masu zuwa na nufin zama jim kaɗan. AT: "Lokaci na zuwa da za ku" ko "Jim ka ɗan"
"za ku so ku gani sosai" ko "za ku so ku ji"
Wannan na nfin mulkin Allah. AT: " ɗaya cikin ranakun da Dan Mutum zai yi malki kamar sarki"
Yesu ya na magana a kansa.
"ba za ka ji shi ba"
Wannan na nufin neman mai ceto. AT: "Dubi nan ga Mai ceton! Ga shi a nan!"
Dalilin zuwa waje za'a iya faɗan ta ba shakka. AT: "ka da ka bi su ka na dubawa"
Zuwan Dan Mutun zai zama mai saukin ganewa da ba zato, kamar yadda da walkiya take bayanuwa. AT: "kamar yadda kowa ya ke ganin walkiya idan ya bayana da" ko "kamar yadda walkiya take bayana ba zato"
Wanna na nufin malkin Allah na nan găba. AT: "zai zama kamar wancan ranar ran da Dan Mutum zai zo ya yi mulki"
"Amma da farko dole ne Dan Mutum ya sha wahala. "Yesu ya na magana a kan sa a masa yin mutum na uku.
AT: "dole mutanen zamanin nan kuma su ki shi"
"Kamar yadda mutane suke yin abubuwa ... haka kuma mutane za su cigaba da yin irin abubuwan"
"zamanin Nuhu" na nufin lokacin da Nuhu ya na a raye kamin Allah ya hukunta mutanen duniya. AT: "lokacin da Nuhu yake a raye"
"zamanin Dan Mutum" na nufin ƙayadadden lokacin kamin Dan Mutum ya zo. AT: "lokacin kamin Dan Mutum ya yi kusan zuwa"
Mutane su na yin abubuwa na gama gari. ba su sani ko su damu cewa Allah ya kusan sharanta su ba.
AT: "iyaye sun bar 'ya'yan su suna auren maza"
"jirgin ruwa" ko "babban kwalekwale"
Wannan kari bai hada da Nuhu da iyalin sa da suke cikin jirgin ba. AT: "hallakar da duka wadan da suke cikin kwalekwalen"
"a zamanin Lutu" na nufin lokaci kamin Allah ya hukun ta birnin sadoma da Gomora. AT: "wani misali shine kamar yadda ya faru a zamanin Lutu" ko "kamar yadda mutane suke yi bayan da Lutu ya mutu"
"mutanen sadoma suna ci suna sha"
"wuta da ƙonannen kibiritu ya na fadowa daga sama kamar ruwa"
"zai zama kamar haka. "AT: "A haka kuma mutane ba za su shirya ba"
AT: " idan Dan Mutum ya bayyana" ko "Idan Dan Mutum ya zo"
Yesu ya na magana a kan sa. AT: "Ni Dan Mutum, na bayyana"
"duk wanda ya ke saman gida kada ya sauko ƙasa" ko "Idan wani ya na saman gidan sa ka da ya sauko ƙasa"
saman gidajen su lebur ne kuma mutane za su iya tafiya ko su zauna akan su.
"dukiyar sa " ko " abubuwan sa"
Kada su dawo gida dauki wani abu. sai su guda da sauri.
"Ku tuna da abin da ya faru da matar Lutu" Wannan gargaɗine. ta dubi baya ta sadoma Allah ya hukunta ta ita kadai da mutanen sadoma. AT: " kada ku yi abin da matar Lutu ta yi"
"Mutanen da suke so su ceci rayuwar su za su rasa shi" ko "duk wanda ya yi kokari ya ceci sohuwar hanyar rayuwan sa zai rasa ransa"
duk"amma mutanen da su ka rasa ransu za su cece shi" ko wanda ya bar hanyar sohuwar rayuwar sa zai ceci ransa
kamar yadda Yesu ya cigaba da yi wa al'majeren sa magana, ya yi nauyi akan muhimmamcin abin da ya ke fada masu.
Wannan na nufin abin da zai faru idan, Dan Mutum ya zo da cikin lokacin dare.
nauyin ba akan mutanen nan biyu ba, amma akan tabbacin cewa za'a ɗauki wasu a bar wasu
"gado" ko "gadon jariri"
Za'a ɗauki mutum ɗaya a bar mutum ɗaya a baya. " Wannan za'a iya bayana ta a wata siffa. AT: "Allah zai aɗuki mutum ɗaya ya bar ɗaya" ko "Mala'iku za su ɗauki ɗaya su bar ɗayan a baya"
Wannan nauyin ba a kan mata biyun nan ba ko ayukan su, amma akan tabbacin cewa za'a ɗauki wasu mutane a bar wasu.
"nikan hatsi tare"
"Ubangiji, a ina wannan zai faru?"
Abayyane, wannan karin magana ne wanda ke nufin "zai zama a fili" ko "za ka sani idan ya faru. "AT: " Idan ungulai sukan taru ya nuna cewa akwai gangar jiki anan haka wadannan abubuwa ya nuna cewa dan Mutum ya na zuwa"
ungulai babban tsuntsaye ne wanda su ke tashi sama tare su kuma ci gagar jikin dabba da suka samu. zaka iya bayyana wannan dabbar kamar haka ko yi amfani da kalmar wata tsuntsu na al'adar wani wuri ka yi wannan.
1Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya, 2yace, "A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.3Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.' 4An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane, 5duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'"6Sai Ubangiji ya ce, "Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada. 7A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne? 8Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?"9Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane, 10"Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.11Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin. 12Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'13Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.' 14Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi."15Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su. 16Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, "Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne. 17Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba."18Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce "Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?" 19Yesu ya ce masa, "Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai. 20Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka." 21Sai shugaban ya ce, "Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta."22Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, "Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni." 23Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.24Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, "Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah! 25Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah."26Wadanda suka ji wannan magana suka ce, "Idan hakane wa zai sami ceto kenan?" 27Yesu ya amsa, "Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah."28Sai Bitrus ya ce, "To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka." 29Yesu ya ce masu, "Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah, 30sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa."31Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, "Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata. 32Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau. 33Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi."34Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.35Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara, 36da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene. 37Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.38Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, "Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai." 39Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, "Dan Dauda, ka yi mani jinkai."40Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi, 41"Me kake so in yi maka?" Ya ce, "Ubangiji, ina so in samu gani."42Yesu ya ce masa, "Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai." 43Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.
Yesuya fara ba da wani misali da ya cigaba da koya wa al'majeren sa. wannan labari ɗaya ne da ya fara a [Luka 17:20]
"Sai Yesu"
za'a fara sabuwar bayyani anan: "karaya. ya ce"
A nan "wani gari" wata hanya ne na gaya wa masu sauraro cewa labarin da ake bada ya faru a wani gari, amma sunar garin da kan ta bai da amfani.
"bai damu da wasu mutane ba"
Yesu ya yi amfani da wannan sashin ya gabatar da wani sabuwar hali a labarin.
gwauruwa mace na wanda maigidan ta ya mutu kuma ba ta sake yin wani aure ba. ma su sauraron Yesu za su iya yin tunani ta kamar wanda bai da wani da zai kula da ita daga wadan da suke so su ma ta illa.
Wannan kalmar "shi" na nufin mai shari'an.
"Kabani mulki mai gaskiya akan"
"abokin gaba na" ko "mutumin da ya ke so ya yi mini illa." Wannan abokan gaba ne a cotun shari'a. ba'a gani ba ko gwauruwa ne ta kai karar mutumin ko mutumin ne ya kai karar gwauruwa.
Wannananan na nufin "mutane" gaba ɗaya.
"addabe ni"
"gajiyar da ni"
"da zuwa guna kullum"
Yesu ya gama ba da misalin yanzu ya na magana akan al'majeren sa,
"yi tunani akan abin da mai shari'an mara gaskiya ya ce." juya wannan a hanyan da mutane za su iya gane cewa Yesu ya riga ya fada abin da mai shari'an ya ce.
Wannan kalmar ya nuna da cewa Yesu ya ga ba da misalin sai ya fara ba da ma'anar sa.
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya koya wa al'majeren sa. AT: "Ba shakka Allah zai kuma ... dare?"
"mutanen da ya zaba"
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya koya wa al'majeren sa. AT: Ba shakka ba zai yi jinkiri a wajen su!"
Yesu ya yi amfani da tambaya domin masu sauraron su dai na tunanin cewaAllah baya yin sauri amsa wa wadan da suka kira bisa sunan sa ga nemam adalci su gane cewa asalin damuwar she ne ba su da bangaskiya na gaskiye cikin Allah. AT: "idan Ɗan Mutun ya zo, ya ka mata ka tabbat cewa zai same ka da gaskiyar bagaskiya a cikin sa." ko "idan Ɗan Mutun ya zo, zai same kadan a duniya wanda sun ba da gaskiya."
Yesu ya na nufin kansa. AT: "Ni, Ɗan Mutum ya zo, zai same ka da gaskiye"
"ga wadansu mutane"
"wanda suka tabbata da kansu cewa su masu adalci ne" ko "wanda suke tunanin cewa su na da adalci"
ki sosai ko ki
"a cikin haikalin
Ma'a nar wanan matani a greka bai fita da saukain ganewa ba. Ma'ana mai yuwa 1) Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa a wannan hanya" ko "Bafarisen ya mike da kansa ya yi addu'a."
ɓarayi mutane ne wanda suke yi wa wasu mutane sata su kwata abubuwan wasu mutane da karfi, ko ta wurin yi masu karari cewa zasu lahani idan sun ki su ba su abin da suka tambaya.
Farisawa sun yarda cewa ma su karban haraji su na da zunubi kamar barayi, mutane marasa adalci, da ma su zina. Wannan za ' iya bayyana. AT: "hakiki ba kamar wannan mai zunubi da karban haraji ba wanda suke cutan mutane"
" komai danake samu"
"tsaye nesa da Farisawan." Wannan alama ne na tawali'u. ko na kirki bai ji cewa ya na kusa da ba Farise ba.
ka " daga idanuwan ka" nanufin cewa ka dubi wana abu. AT: "dubi ta sama" ko "dubi sama"
Wannan furci ne na jiki da babban bakin ciki da nuna tuba da tawali'u. AT: "ya bugun kirjin sa ya nuna bakin ciki"
"Allah, Dao Allah ka yi mini jinkai.ni mai zunubi ne " ko "Allah, dan Allah ka yi mini jinkai ko da shike na yi zunubi da yawa"
Ya zama baratacce Allah ya yafe masa zunubin sa. AT: "Allah ya yafe wa mai karban harajin"
"ba kamar dayan mutumin ba" ko "ba dayan mutumin ba." AT: "ammam Allah bai yafe wa ba Farasen ba"
Da wannan sashin, Yesu ya matsa da ga labarin ya faɗa ƙa'ida da labarin ya ke kwantanta.
AT:"Allah zai kaskantar"
AT: "Allah zai daukaka sosai"
Wannan za'a iya bayyana kamar wata bayani dabam: "taɓa su, amma"
"al'majeran sa suka yi kokari su tsayar da iyayen daga kawo 'ya'ya su gun Yesu"
"Yesu ya gaya wa mutanen su kawo jariransu wurin sa"
Wadan nan bayani guda biyu yana da ma'ana kusan ɗaya an hada su domin a yi nauyi. wa su yaren sukan yi nauyin a hanyoyi dabam dabam. AT: "Hakika ku bar yara kanana su zo wurina"
AT:"na irin mutane ne wadan da suka zamar da kansu kamar yara kanana"
"lallai ina gaya maku." Yesu ys yi amfani da wannan furcin domin ya yi nauyi akan muhimmancin abin da yake so ya faɗa.
Allah ya bukaci mutane su karbi mulkin sa akan su da yarda datawali'u. AT: "Duk wanda ya na so ya shiga mulkin Allah dole ne ya karɓe shi da yarda da tawali'u kamar karamin yaro"
Wannan ya gabatar da wani sabuwar hali a labarin. ya gane shi da masayin sa.
"me ya kamata in yi" ko "me ake bukata a guna"
"karɓe rai da bata karawa." Wannan kalmar "gaji" kullum na nufin dukiya da mutum ya bar wa 'ya'yan sa bayan ya mutu.saboda haka wannan misalin zai iya zama ya gane kansaya zama ɗan Allah kuma yana sa bege ga Allah ya ba shi rai madawami.
Yesu ya yi tambaya domin ya sani cewa shugaban ba zai so amsan Yesu ga shugabanen ba tambaya na aya 18. Yesu bai yi tsammanin shugaban ya amsa tambayan Yesu ba. Yesu ya na so shugaban ya gane cewa amsan Yesu ga shugabanen tambayane daga Allah, waye kadai Allah,sai dai Allah kadai sabada haka ka kira ni managarci shi ne ka hada ni da Allah"
"kada ku yi kisan kai"
"duk wadan nan dokoki"
"Da Yesu ya ji cewa mutumin ya fadi haka"
"ya amsa masa"
"zaka sake yin abu ɗaya" ko "akwai abu ɗaya da har yanzu baka yi ba"
"sayar da duk dukiyan ka" ko "sayar da duk abin da kake da shi"
"ka bada kuɗin wa gajiyayyun mutane"
"wadata a sama" anan na nufin albarkan Allah. AT: "zaka sami albarkan Allah a sama"
"zo ka zama almajiri na"
Wannan maganar motsin rai ne ba tambaya bane. AT:"ya na da wuya sosai ... mulkin Allah.!"
ba zai yu wa rakumi ya shiga ta idon allura ba. mai yuwa Yesu ya yi amfani da alama da nufin cewa zai zama da wuya sosai wa mai kuɗi ya shiga mulkin Allah.
idon allura rami ne a allurar dinki ta inda zare ke wucewa.
"mutanen da su ka ji Yesu ya ce"
ya zamana mai yuwa suna nemam amsa. amma yaza ma kamar sun yi amfani da tanbayan su nuna mamakin su ga abin da Yesu ya ce. AT: "Idan hakane ba wanda zai sami ceto daga zunubi!" ko "wata siffa mai ƙoƙări: "Idan haka Allah ba zai ceci kowa ba!"
"mutane ba za su iya yi ba mai yuwa ne ga Allah ya yi" ko "mutane ba za su iya yi ba Allah zai iya yi"
Wannan sashin na nufin al'majeren ne kawai, kuma ya hada su da shugaba mai kuɗin.
"mun cire zato" ko "mun bari a baya"
duk arzikin mu" ko "duk dukiyan mu"
Yesu ya yi amfani fa furcin domin ya nu na muhimmincin abin da ya ke so ya fada.
Wannan furcin ya so ya hada ba al'majeren kawai ba, duk wani kuma wanda ya so ya yi irin hadayan.
AT: "duk wanda ya bari ... zai samu"
" rai madawami a duniyan mai zuwa"
Yesu ya dauki al'majeren nan goma sha biyu daga gun mutane inda za su zauna su kadai.
Wannan ya nuna sake mai ma'ana a aikin bisharan Yesu da ya tafi Urushalima na karshe.
AT: " da annabawa suka rubuta"
Wannan na nufin annabawa tsohon alkawari.
Yesy ya na magana akan sa kamar " Dan Mutum." AT: "ni Ɗan Mutum,... Ni ...ni ...ni ...Ni"
AT: "zai faru" ko "zai bayana"
AT: "Domin shugaban Yahudawan zai ba da shi ga al'ummai"
AT: "a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau"
Wannan na nufin rana ta uku bayan ya mutu. duk da haka, al'majeren har yanzu ba su gane wannan ba, zai zama da kyau kada ka bayana wannan idan kana juyawannan aya.
"Ba su ko gane waɗannan abubuwan ba"
Wannan na nufin kwatancen Yesu yadda zai sha wahalaya kuma mutu a Urusalima, sa'anan kuma ya tashi da ga mattatu.
Wannan za'a iya bayyana shi a wata siffa amma ba a gane ba ko Allah ne ko kuma Yesu ne ya boye masu wannan kalman. AT: "Yesu ya boye masu wannan sakon" ko "Allah ya hana su gane abin da Yesu yake gaya ma su"
AT: "abubuwan da Yesu ya faɗa"
Wannan sashin an yi amfani da a nan domin a sa alama akan sabuwar sashin labarin.
"akwai wani makaho a zaune. "A nan" "wani" na nufin cewa mutumin na da amfani kuma sabon kasancewa ne a labarin amma Luka bai ambace sunan sa ba. sabon kasancewa ne a labarin.
zai za ma da taimako ka fadi sabuwar bayyani a nan. AT: "bara da ya ji"
"Mutane a cikin taron sun gaya wa makahon"
Yesu ya zo da ga wani gari a nazarat,wanda ake samu a galili
"yake wucewa ya wuce shi"
Wannan kalmar ya sa alama akan abin da ya faru domin wani abun da ya faru a farko.a wannan yana yi, taron sun gaya wa makahon cewa Yesu ya na kan tafiya.
"ya yi kira" ko "ihu"
Yesu daga zuriyan Dauda ne,sarkin Isra'ila mafi duka.
"ji tausayi na" ko "ka ji tausayi na"
"Mutanen da suke tafiya a gaban taron"
"ka yi shiru" ko "kada ka yi ihu"
Wannan zai iya nufin cewa mutumin ya kara daga murya sosai koya kara daga murya da nacewa.
AT: "mutanen su kawu makahon gun Yesu"
"ka iya gani"
Wannan umurni ne, amma Yesu bai umurci mutumin ya yi wani abu ba. Yesu yana warkar da mutumin da umurni. AT: "ba za ka sami ganin gari ba"
Wannan kalmar misali ne. Domin bangaskiyar mutumin ne Yesu ya warkar da shi. AT: "Na warkar da kai domin ka yarda da ni ne"
"ka yi wa Allah daukaka" ko "yabon Allah"
1Yesu ya shiga Yariko ya na wucewa cikinta. 2Sai ga wani mutum a wurin mai suna Zakka. Shugaba ne na masu karban haraji, kuma mai arziki ne.3Yana kokarin ya ga ko wanene Yesu, amma bai iya gani ba sabo da yawan jama'a, domin shi gajere ne. 4Sai ya ruga gaba ya hau itacen baure domin ya gan shi, saboda Yesu zai wuce ta wannan hanya.5Sa'adda Yesu ya zo wurin, ya kalli sama sai ya ce masa, "Zakka, ka sauko da sauri, domin yau dole in sauka a gidanka." 6Sai ya sauko da sauri, ya karbe shi da farin ciki. 7Sa'adda dukansu suka ga wannan, sai suka yi gunaguni, cewa, "Ya ziyarci mutum mai zunubi."8Zakka ya tsaya ya ce wa Ubangiji, "Duba, Ubangiji, zan ba matalauta rabin arzikina, idan kuma na cuci wani a kome, zan mai da adadinsa sau hudu." 9Yesu ya ce masa, "Yau ceto ya shigo wannan gida, domin shi ma dan Ibrahim ne. 10Gama Dan Mutum ya zo ne domin ya nemi, ya kuma ceci batattun mutane."11Da suka ji wadannan abubuwan, ya cigaba da magana, sannan ya fada masu wani misali, domin yana kusa da Urushalima, sai suka yi tsamani mulkin Allah za ya bayyana nan da nan. 12Sai ya ce, "Akwai wani mutum mai sarauta wanda ya tafi wata kasa mai nisa domin ya karba wa kansa mulki sa'annan ya dawo.13Sai ya kira bayinsa guda goma, ya ba su fam goma, sai ya ce masu, 'Ku yi kasuwanci da wannan har sai na dawo.' 14Amma mutanensa suka ki shi sai suka aiki jakadu bayansa, cewa, 'Ba za mu yarda wannan mutum ya yi mulki a kanmu ba.' 15Anan nan sa'adda ya koma kuma, bayan da ya sami mulkin, sai ya ba da umarni a kira masa bayin da ya basu kudi, domin ya san ribar da suka samu wajen kasuwancin da suka yi.16Na farkon ya zo wurinsa, cewa, 'Ubangiji, fam nan na ka ya yi riban fam goma.' 17Masaraucin ya ce masa, 'Madalla, bawan kirki. Domin ka yi aminci a karamin abu, za a baka iko kan birane goma.'18Na biyun ya zo, yana cewa, 'Fam na ka, Ubangiji, ya yi ribar fam biyar.' 19Sai masarauncin yace masa, 'Ka dauki mulkin birane biyar.'20Wani kuma ya zo, yana cewa, 'Ubangiji, ga fam naka da na ajjiye shi da kyau cikin kaya, 21gama na ji tsoronka, domin kai mutum mai tsanani ne. Kana daukar abu da baka ajiye ba, kana kuma girbin abin da ba ka shuka ba.'22Masarauncin ya ce masa, 'Da kalmominka zan shari'antaka, kai mugun bawa. Ka sani cewa ni mutum mai tsanani ne, ina daukan abinda ban ajiye ba, ina kuma girbin abinda ban shuka ba. 23To don me ba ka kai kudi na wurin masu banki ba, saboda bayan da na dawo zan karbe shi da riba?'24Masaraucin ya ce wa wadanda suke a tsaye a wurin, 'Ku karba fam da ke a wurinsa, ku ba mai fam goman nan.' 25Suka ce masa, 'Ubangiji, yana da fam goma.'26'Ina ce maku, duk wanda yake da abu za a kara masa, amma wadda bai da shi, za a karba sauran da ke wurinsa. 27Amma wadannan abokan gabana, wadanda ba sa so in yi mulki bisansu, a kawo su nan a kashe su a gaba na.'28Da ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi gaba, yana tafiya zuwa Urushalima.29Ananan sa'adda ya zo kusa da Baitfaji da Baitanya, a kan tudu da a ke kira Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, cewa, 30cewa, "Ku tafi cikin kauye da ke gabanku. Sa'adda ku ka shiga, za ku same dan aholaki da ba a taba hawansa ba. Ku kwance sai ku kawo mani shi. 31Idan wani ya tambaye ku, 'Don me ku ke kwance shi?' Ku ce, 'Ubangiji ne ke bukatarsa."32Wadanda aka aike su suka je sun sami aholakin kamar yadda Yesu ya gaya masu. 33Sa'adda suna kwance aholakin, sai masu shi suka ce masu, "Don me ku ke kwance aholakin?" 34Suka ce, "Ubangiji yana bukatar sa." 35Suka kawo wa Yesu, suka shimfida tufafinsu akan aholakin sai suka dora Yesu akansa. 36Da yana cikin tafiya, suka shimfida tufafinsu akan hanya.37Da ya yi kusa da gangaren tudun Zaitun, sai dukan taron almajiransa suka fara yin murna suna kuma yabon Allah da murya mai karfi domin dukan ayukan al'ajibi da suka gani, 38cewa, "Albarka ta tabbata ga sarki da ke zuwa cikin sunan Uba! Salama a sama da daraja mafi daukaka kuma!"39Wadansu Farisawa daga cikin taron jama'a suka ce masa, "Malam, ka tsauta wa almajiranka." 40Yesu ya amsa ya ce, "Ina gaya maku gaskiya, in wadannan sun yi shiru, duwatsu za su yi shewa."41Sa'adda Yesu yana kusatowa, sai ya yi kuka akan birnin, 42cewa, "Da kun san wannan rana, ko ku ma, abubuwan da ke kawo maku salama! Amma yanzu an boye su daga idanunku.43Gama rana zata ta zo a gareki, da makiyan ki zasu gina ganuwa a kewaye da ke, su kuma fada maki daga kowace gefe. 44Za su sare ki kasa tare da 'ya'yanki. Ba za su bar wani dutse akan dan'uwansa ba, domin ba ki lura da lokacin da Allah ya na kokarin ceton ki ba."45Yesu ya shiga Haikalin sai ya fara korar masu sayarwa, 46ya na ce masu, "A rubuce yake, 'Gida na zai zama wurin addu'a,' amma kun mayar da shi kogon mafasa."47Yesu yana nan yana koyarwa kowace rana a cikin haikali. Amma manyan firistoci da marubuta da shugabanin jama'a suna so su kashe shi, 48amma ba su sami hanyar yin wannan ba, domin mutane suna sauraron sa sosai.
Aya 1-2 zai ba da labarin da ga kasa na abin da ya auko.
Wannan kalmar "duba" ya nuna mana wani sabuwar mutum a labarin. me yuwa yaren ku suna da wa ta hanya na yin haka. AT: "kwai wani mutum wanda ya"
Wannan labari ne da ga kasa akan Zakka.
"Zakka yana ƙoƙari"
"domin shi gajere ne"
Mai walafawar ya ga ma ba da labari daga kasa na abin da ya auko yanzu ya fara kwatanta abin da ya faru da kanta.
"itacen 'ya'yan baure." yana haifan kewayyayen ''ya'ya mai kimanin 2.5 santi mita. AT: " 'ya'yan baure" ko itace"
"itacen" ko "ida Zakka ya ke"
"Zakka ya yi sauri"
Yahudawan sun ki jinin mai karban harajin kuma su yi tunanin cewa kada wani mutum mai kyau ya yi haɗu da su.
"Yesu ya ji gidan mutum mai zunubi ya ziyarci shi"
"mai zunubi a fili" ko "mai zunubi da gaskiye"
Wannan na nufin Yesu.
" zan mai da adadinsa sau hudu fiye da yadda na karba a gun su"
An gane da cewa cat ya na zuwa ne da ga Allah. AT: "Allah ya ceci wannan iyali"
Wannan kalmar "gida" a nan na nufin muttanen da suke zama a wannan gida ka kuma iyali.
"wannan mutumin ma" ko "Zakka kuma"
Ma'ana masu yuwa 1) "zuriyar Ibrahim" 2) "mutum wanda ya na da bangaskiya kamar yadda Ibrshim ya yi."
Yesu ya na magana akan sa. AT: "Ni ne ɗan Mutum, zo"
" mutanen da suka yi gilo daga Allah" ko "wadan da suka yi gilo ta hanyar zunubi da ga Allah"
Yahudawa sun yarda da cewa Mai ceto zai kafa mulkin sa nan da nan idan ya zo Urusalima. AT: "da cewa nan da nan Yesu zai fara yin mulkin bisa mulkin Allah"
Wani mutum wanda shi daya ne da cikin kungiyan masu mulikn" ko "Wani mutum da ga iyali mai muhimmanci"
Wannan hoton karanin sarki ne zuwa ga babban sarki. babban sarkin zai bawa karamin sarkin dama da ika ya yi mulki bisa ga mutanen ƙasar sa.
Yesu ya cigaba da bada misalin ya fara a cikin Luka 19:11(./11.md).
"Mai sarautan ya yi kira." zai zama da amfani ka fada cewa mutumin ya yi kira kamin ya ji ya karɓe mulkin. AT: "kamin ya tafi, ya yi kira"
"bama kowa fam ɗaya"
fam kuwa 600 nauyin sa, mia yuwa na azurfa. kowane fam dai dai ne da kwana 100' hakin da za 'a biya mutane na kusan aikin watani hudu, fam goma zai zama na hakin shekara uku. AT: "ƙerarren kuɗi goma mai amfani" ko "kuɗi mai yawa"
"Yi kasuwanci da wannan kuɗi" ko "Yi amfani da wannan kuɗi domin ka sami wani"
"mutanen ƙasar sa"
"kungiyan mutane domin su ji a madadin su" ko "sakonni ɗaya wa"
Wannan sashin an yi amfani da ita anan domin a sa alama akan abu mai amfani da ya faru a labarin. Idan yaren uk na da wata hanyan in haka sai ku yi amfani da ita anan.
"bayan da ya zama sarki"
AT: "ya zo gun sa"
"kuɗi nawa suka samu"
"Bawa na farko"
"ya zo gaban mai sarautan"
Ya nuna da cewa bawan nan ne ya jawo riban. AT: "Na yi amfani da famna ka na yi riban fam goma kuma"
fam kuwa 600 nauyin sa, mia yuwa na azurfa. kowane fam dai dai ne da kwana 100' hakin da za 'a biya mutane na kusan aikin watani hudu. Dubi yadda zaka juya wannan a [Luka 19:13]
"Ka yi mai kyau. "mai yuwa yaren ku na da sashin da wanda ya ba wani aiki zai yi amfani da shi ya nuna ya karɓe shi, kamar "aiki mai kyau."
Wannan na nufin fam ɗaya wanda mai sarautan ya kalla kamar ba kuɗi mai yawa bane.
"Bawa na biyu"
Ya nuna da cewa bawan nan ne ya jawo riban. AT: "Ubangiji, Na yi amfani da famna ka na yi riban fam biyar kuma"
"Zaka sami iko bisa birane biyar
"wani bawan ya zo"
"ya naɗe a kaya sai ya boye"
"mutum mai sashin baya na jirki" ko "mutum wanda ya na tsammanin da yawa da ga gun bayin sa"
Wannan mai yuwa karin magana ne. mutumin da ya ke dauka wa da ga cikin abin da aka ajiye ko kuma da ga cikin abin da ba komai da bai sa a cikin misali ba ga wani ya ci riba da ga ikin wahala na wa su. AT: "Kana daukar abu da baka ajiye ba" ko "Kana kamar mutun wanda ya ke daukar abin da wa su mutane su ka ajiye"
Wannan mai yuwa karin magana ne. mutum da ya griɓe abincin da wani dabam ya shuka misal ne na wani wanda ya ke cin muriyan aikin wahala da wasu su ka yi. AT: "ka na kamar mutum wanda ya griɓe 'ya'yan itace da wa su mutane suka shuka"
"kalmominka" na nufin duk abin da ya faɗa. AT: "bisa ga abin da ka faɗa"
wannan mai sarautan ya na maimaita abin da bawan ya faɗa akan sa. bai faɗa cewa haka gaskiya bane. AT: "Kace cewa ni mutum ne mai neman hakki"
mai sarautn ya yi amfani da tambaya domin ya kwaɓe mugun bawan. AT: "da ka sa kuɗi na ... riba."
"ara wa banki kuɗi na." Al'adan da ba su da banki za su iya juya shi kamar wani ya karbi aron kuɗi na."
Banki kasuwanci ne da suke ajiye kuɗi da kyau wa mutane. banki sun ara kuɗi wa wasu domin riba. sabo da haka ya biya wata kuɗi, ko riba, wa wadan da suka ajiye kuɗin su a banki.
"da na karba kuɗin da riba" ko " da na sami riba akai"
riba kuɗi ne da banki su ke biyan mutane wanda suka ajiye kuɗin su a banki.
Mai sarautan ya zama sarki. Dubi yadda za ka juya wannan a Luka 19:12.
"mutanen da suka tsaya kusa da su"
"yana da fan goma dama!"
Wannan srakin ne yake magana. wasu masu juyawan za su so su fara da wannan ayan da "sai sarkin ya amsa, Na gaya maka " ko "amma sarkin ya ce Na gaya maka wannan"
Ya nuna cewa abin da ya ke da shi kuɗi ne da ya samu ta wurin amfani da fam na sa da aminci. AT: "duk wanda ya yi amfani da abin da aka ba sa da kyau, zan ba sa kuma" ko "ga duk wanda ya yi amfani da abin da na ba shi da kyau zan ba shi kuma"
Ya nuna da cewa mutumin bai da kuɗi domin bai ya amfani da fam nasa da aminci. AT: "daga mutumin da bai yi aiki da abin da na ba shi da kyau ba"
AT: "zan karba da ga gun sa"
tunda abokan gaba na ba su nan, wa su yaren za so ce "wadancan abokan gaba na."
"Da Yesu ya faɗi wadannan abubuwa"
Urushalima ya na sama da Yariko, daidai ne wa Isra'ilawa su yi maganr tafiya sama zu wa Urushalima
Wannan sashin an yi amfani da ita domin a sa alama akan sabuwar abin da ya auko. Idan yaren ku na da wata hanya na yin haka, za ku iya yin amfani da ita anan.
Wannan kalmar "shi" na nufin Yesu. al'majeren sa su na tafiya tare da shi.
Baitfaji gari ne ɗa
"tudun da ake kira hauwan Zaitun" ko "tudun ana kira dutsen itacen Zaitun"
"karamin jaki" ko "karamin dabban hauwa"
AT: "da ba wanda ya taba hauwansa"
Yesu ya gaya wa al'majeren sa yadda za su amsa tambayan da ba'a riga an tambaye su ba. koda shi ke mutanen da suke a kauyen su yi kusa su yi tambayan.
Faɗan na ciki za a iya juya ta kaman ba faɗan ba na hanya kusu-kusa ba. AT: "Idan wani ya tambaye ku, Don me ku ke kwance shi, Ku ce
AT: "Al'majerai biyu da Yesu ya aika"
"mai aholakin"
"sa rigan sarautan su akan dan aholakin."alkyabba rigunar sarauta ne na waje.
"taimaki Yesu ya hau kan aholakin"
"mutane suka shimfida tufafinsu." Wannan alama ne na ba wani daraja.
" da Yesu ya yi kusa." al'majeren sa su na tafi ya da shi.
" daga ida hanya ya ƙasa daga tudun Zaitun"
"mayan abubuwa da suka gan Yesu ya yi"
su na fadan wannan akan Yesu.
A nan "suna" na nufin iko da ƙarfi.kuma Uangiji na nufin Allah.
"bari a sami salama a sama" ko "Muna so mu gan salama a sama"
"Bari a sami daukaka a sama" ko Wmuna so mu ga daukaka a sama." Wannan kalmar "a sama" na nufin sama, wada shine misalin Allah, wanda yake zaune a sama. AT: "bari kowa ya ba wa Allah daukaka wanda ya ke saman sama"
"a cikin taro mai yawa"
"gaya wa al'majeren kasu daina yin wadannan abubuwan"
Yesu ya fada wannan domin ya yi nauyin akan abin da zai fada nan gaba.
Wannan yana yin da ba 'a gani bane.wasu masu juyawa za su so su bayyana abn da Yesu yake nufi daya ce: "a'a, ba zan kwaɓe su ba,idan wadannan mutane za su yi shiru ... za su yi ihu"
"duwasun za su kira yabo"
Wannan na nufin Urushalima.
Wannan kalmar "ita"na nufin brinin Urushalima, amma ya na wakilcen mutanen da ke zaune cikin brinin.
Yesu ya nuna bakin cikin sa da cewa mutanen Urushalima sun rasa daman zama na salama da Allah.
Wannan kalmar "kai" mafuradi ne domin Yesu ya na magana da brinin. Amma idan wannan zai zama mai saɓa wa dabi'a a yaren ku za ku iya amfani da jam'i na "kai" ku nufa ga mutanen brinin.
"idanuwan ka" na nufin gani. AT: "ba za ka iya ganin su ba"
Me ya biyo bakin cikin Yesu.
Wannan ya nuna da cewa za su faskan ce lokacin wahala. wasu yaren ba su yin maga na akan lokaci "zuwa." AT: "a nan gaba wadannan abubuwan za su faru da ku: abokan gaban ku" ko "ba da ji ma wa ba za ku faskanci lokacin damuwoyi. abokan gaban ku"
Wannan kalmar "ke" mafuradi ne domin Yesu yana magana da brinin kamar yadda zai yi da mace. Amma idan wannan zai saɓa wa dabi'a a yaren ku za ku iya amfani da jam'i na "ke" ku nufa ga mutanen brinin.
Wannan na nufin bamgo da zai tsare mutane daga fitan wajen brinin.
Yesu ya na magana da mutanen brinin kamar ya na magana da brinin da kanta kamar yadda yake magana da mace. ya yi maganar mutanen da suke zama a brinin kamar su matane yarane, haka yaran brinin. a sare brinin shi ne a rushe bangon ta da gigegigenta, a kuma sare 'ya'yan ta wato a kashe wanda suke zaune a cikin ta. AT: "za su rushe ki gaba ɗaya su kuma kashe dukkan wanda suke zaune a cikin ta" ko "za su rushe brinin ki gaba ɗaya su kuma kashe dukkan ku"
"ke ba ki yarda"
za ka iya bayyana cewa ya shiga Urushalima, ida haikalin yake. AT: "Yesu ya shiga Urishalima sai ya je cikin harabar haikalin"
Firistoci ne kawai ake bari su shiga cikin ginin haikalin. AT: "shiga cikin harabar haikalin
"wurga waje" ko "fitar waje da ƙarfi"
Wannan tambayane daga Ishaya. AT: "alittafin yace" ko "Annabi ya rubuta wadannan kalmomin a cikin littafin"
Wannan kalmar "-na" na nufin Allah "gida" kuma na nufin haikali.
"wurin da mutane suke yi mini addu'a"
Yesu ya na maganar haikali kamar wurin da barayi suke haduwa. AT: "wurin da barayi suke boyewa"
"a cikin harabar haikalin" ko "a haikalin"
"sun kasa kunne sosai ga abin da Yesu yake fadi"
1Ana nan wata rana, Yesu yana kan koyarwa a haikali da wa'azin bishara, sai shugaban firistoci da marubuta suka zo wurinsa da dattawa. 2Suka yi magana, su na ce masa, "Gaya mana da wanne iko ne ka ke yin wadannan abubuwan? Ko wanene ya baka wannan ikon?"3Ya amsa sai ya ce masu, "Ni ma zan yi maku tambaya. Gaya mani game 4da baptisman Yahaya. Daga sama take ko kuwa daga mutane ne?"5Sai suka yi mahawara da junansu, suna cewa, "In mun ce, 'Daga sama,' zai ce, 'To don me ba ku ba da gaskiya gareshi ba?' 6Amma in mun ce, 'Daga mutane ne,' dukan mutane za su jejjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata a ransu Yahaya annabi ne."7Sai suka amsa cewa ba su san ko daga ina ne take ba. 8Yesu yace masu, "To haka ni ma ba zan gaya maku ko da wanne iko nake yin wadannan abubuwan ba."9Ya gaya wa mutane wannan misali, "Wani mutum ya dasa gonar inabi, ya ba wadansu manoma jinginarta, sai ya tafi wata kasa har ya dade. 10Da lokacin girbi ya yi sai ya aiki wani bawansa zuwa wurin manoman, saboda su bashi daga cikin anfanin gonar. Amma manoman suka doke shi, sai suka kore shi hannu wofi.11Ya aike wani bawa kuma sai suka daddoke shi, suka kunyatar da shi, suka kore shi hannu wofi. 12Ya kuma sake aike na uku suka yi masa rauni, suka jefar da shi a waje.13Sai mai gonar inabin ya ce, 'Me zan yi? Zan aiki kaunattacen dana. Watakila zasu ba shi daraja.' 14Amma sa'adda manoman suka gan shi, suka yi shawara a tsakaninsu, cewa, 'Wannan ne magajin. Bari mu kashe shi, saboda gadon ya zama namu.'15Suka jefar da shi waje daga gonar, suka kashe shi. Menene ubangijin gonar inabin zai yi da su? 16Zai zo ya halakar da wadannan manoma, sai ya ba wadansu gonar." Da suka ji wannan, suka ce, "Allah ya sawake!"17Amma Yesu ya kalle su, sai yace, "Menene ma'anar wannan nassi? 'Dutsen da magina suka ki, an mayar da shi kan kusurwa'? 18Duk wanda ya fadi kan dutsen zai farfashe. Amma duk wanda dutsen ya fadi a kansa, zai rugurguza shi."19Sai marubutan da manyan firistocin suka so su kama shi a wannan sa'a, domin sun sani ya yi wannan misali a kansu ne. Amma sun ji tsoron mutane. 20Suna fakonsa, suka aiki magewaya, wadanda suke kamar masu adalci, saboda su sami kuskure cikin maganarsa, don su mika shi ga hukumci da kuma ikon gwamna.21Suka tambaye shi, cewa, "Malam, mun sani da cewa kana fada da koyar da abin ke daidai, kuma ba wanda yake cusa maka ra'ayi, amma kana koyar da gaskiya game da hanyar Allah. 22Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?"23Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu, 24"Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?" Suka ce, "Na Kaisar ne."25Sai ya ce masu, "To sai ku ba Kaisar abin da ke na Kaisar, ku kuma ba Allah, abin da ke na Allah." 26Marubutan da manyan firistocin ba su sami abin zargi cikin maganarsa, a gaban mutane ba. Suka yi mamakin amsar sa, ba su kuma ce komai ba.27Sa'adda wadansu Sadukiyawa suka zo wurinsa, wadan da suka ce babu tashin mattatu, 28suka tambaye shi, cewa, "Malam, Musa ya rubuta mana cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, mai mace kuma ba shi da yaro, sai dan'uwansa ya auri matar, ya samar wa dan'uwansa yaro.29Akwai 'yan'uwa guda bakwai kuma na farin ya yi aure, sai ya mutu babu da, 30haka ma na biyun. 31Na ukun ya aure ta, haka nan na bakwai ma bai bar yaya ba, har suka mutu. 32Daga baya sai matar ma ta mutu. 33To a ranar tashin mattatu, matar wa za ta zama? Domin duka bakwai din sun aure ta."34Yesu ya ce masu, "'Ya'yan duniyan nan suna aure, ana kuma ba da su ga aure. 35Amma wadanda aka ga cancantarsu a waccan tsara, sun isa su sami tashin mattatu, ba za suyi aure ko a aurar da su ba. 36Gama ba za su mutu kuma ba, domin suna daidai da mala'iku kuma su 'ya'yan Allah ne, da shike su 'ya'yan tashin matattu ne.37Amma batun tashi matattu, ko Musa ma ya nuna wannan, a cikin jeji, inda ya kira Ubangiji, Allah na Ibrahim da kuma Allah na Ishaku da Allah na Yakubu. 38Yanzu shi ba Allahn matattu ba ne, amma na masu rai, saboda duka suna raye a wurinsa."39Wadansu marubuta suka amsa, "Malam, ka amsa da kyau." 40Gama ba su sake yi masa wadansu tambayoyi ba.41Yesu ya ce masu, "Yaya suke cewa Almasihu dan Dauda ne? 42Gama Dauda da kansa ya ce a cikin littafin Zabura, Ubangiji ya ce wa Ubangiji na, 'Zauna a hannun dama na, 43sai na maida makiyanka a karkashin tafin sawunka.' 44Dauda ya kira Kristi 'Ubangiji', to ta yaya ya zama dan Dauda?"45Dukan mutane suna ji ya ce wa almajiransa, 46"Ku yi hankali da marubuta, wadanda suna son tafiya da manyan riguna, suna kuma son a gaishe su a cikin kasuwanni, da mayan wuraren zama a cikin majami'u, da kuma manyan wurare a wurin bukukkuwa. 47Suna kuma kwace wa gwamraye gidaje, suna kuma badda kama ta wurin yin doguwar addu'a. Wadannan za su sha hukumci mai girma."
sai shugaban firistoci da marubuta da dattawa suka yiwa Yesu tambaya a haikali.
Wannan sashin an yi amfani da ita anan domin a sa alama a wata sabuwar sashin labarin.
"a cikin harabar haikalin" ko "a haikalin"
Yesu ya amsa wa shugaban firistoci, marubuta da dattawa.
"Yesu ya amsa"
Wannan kalmar "Ni ma ... zan yi maku tambaya" bayyani ne. Wannan kalmar "ku gaya mini" ummurni ne.
Yesu ya sani cewa iko yahaya ya zo daga sama ne, baya tambaya saboda bayayni. ya yi tambayan saboda shugabanen Yahudawa su gaya wa masu sauraron abin da suke tunani.wannan tambayan ba ya bukatan amnsa amma mai yuwa za ka iya juya shi kamar tambaya. AT: "ku na tunanin cewa ikon Yahaya ya yi wa mutane baftisma ya zo daga sama ne ko daga mutane" ko "Allah ne ya cewa Yahaya ya yi wa mutane baftisma, mutane ne suka ci masa ya yi"
"daga Allah." Mutanen Yahudawa ba su Allah da sunan sa " "kowa ne lokaci su na amfani da "sama" a mai mako shi.
" Sun yi batun" ko "Sun duba amsan su"
"asakanin su" ko "da kowanne ɗayan su"
Wa su yaren za su so su yi amfani da faɖi. AT: "Idan na ce ikon Yahaya daga sama ne, shi"
"Yesu zai ce"
Wa su yaren za su so su yi amfani da faɖi. AT: "Idan na ce ikon Yahaya daga mutane ne,"
"kashe mu da jefan mu da duwatsu." shari'an Allah ya yi umurtan cewa mutanen sa su na jefin wadan can mutanen sa wanda suke yi ma sa ba'a ko annabawan sa.
"sai shugaban firistoci, marubutan, da dattawan." Wannan kalmar "sai" ya sa alama akan wani abu da ya faru domin wani abun da ya faru da farko. a wannan hali, sun yi mahawara da kansu a cikin Luka 20:5-6, kuma ba su samu amsan da suke so su fada ba.
AT: "sun ce, ' ba mu san inda ya fito ba."'
"daga ina baftisman Yahaya ya fito." AT: "daga ina ikon Yahaya ya yi wa mutane baftisma ya fito" ko "wa ya bawa Yahaya iko ya yi wa mutane baftisma"
"Ni ma ba zan gaya maku ba." Yesu ya sani cewa ba su so su gaya masa amsan, sai ya amsa masu a irin yana yin, AT: "kamar yadda ba za ku gaya mini ba ni ma ba zan gaya maku ba"
"Ya bar wasu masu manoman itacen inabi su yi aiki da shi domin furfura da kuɗi" ko "Ya bar wasu masu manoman itacen inabi su yi aiki da shi su biya shi anjima." biyan zai zama ko da kuɗi ko kuma da amfanin gona.
Wadannnan mutane ne wadan da suke yin kiwon itacen inabi su grimar da inabin. AT: "manoman inabi"
"lokacin dasuka yarda zasu biya shi." Wannan zai zama lokacin gribi.
"waɗan su inabin" ko "waɗan su abin da suka haifar a gonar inabin." zai iya zama abin da suka samu daga inabin ko kuɗin da suka samu da suka siyar da inabin.
Hanun wofi misali ne na "ba komai." AT: "suka kore shi ba biyan shi" ko "suka kore shi ba inabin"
"daddoke wancan bawan "
"wulakanta shi"
"harma bawa na uku" ko "wanu bawa kuma." Wannan kalmar "tukunna" ya ɗan ambata wani tabbatcan abu da cewa mai gonar bai kamata ba ya aike bawa na biyu ba, amma ya je har ya aiki bawa na uku.
"jima wancan bawan ciwo"
" jefar da shi a wajen gonar inabin"
Wannan tambayan ya yi nauyin cewa mai gonar inabin ya yi tunani a hankali akan abin da zai yi. AT: "ga abin da zai yi:"
"sa'adda manoman suka ga ɗan shi"
Bawai suna tambayan izni bane.Sun fada haka domin su karfafa juna ne su kashi magajin.
"Manoman itacen inabin suka kori ɗan daga gonar"
Yesu ya amfani da tambaya ya sa ma su sauraron su kasa kunne ga abin da mai gonar inabin zai yi. AT: "To yanzu, ku saurari abin da ubangijin gonar inabin zai yi ma su."
"Allah ya sa kar ya faru"
"Amma Yesu ya duɓe su" ko "Amma Yesu ya kalle su." ya yi haka domin ya reke su su gane abin da ya ke fada.
Yesu ya yi amfani da tambay adimon ya koya wa taron. AT: "Ya kamata ku gane nassin: 'Dutsen ... kusurwa'"
"wannan littafin"
Wannan shi ne farko na misalai uku a cikin anabci daga littafin Zabura. Wannan na nufin Mai ceto kamar shi ne dutsen da magina suka zaba kar su yi aiki da shi, amma Allah ya mai da shi dutse ma fi amfani.
"Dutsen da magina suka ki cewa ba shi da kyau sosai domin aikin gini." a wancan kwanaki mutane su na amfani da duwatsu su gini bangon gidaje da wa su ganaginai.
Wannan na nufin shugabanen addini wadan da suka ki Yesu a masa yin Mai ceto.
"babban dutse na gini" ko "dutsen gini mafi amfani"
Wannan misalin na biyu ya yi maganar mutane wanda suka ki Mai ceto kamar sun faɗi akan dutse sun ji ciwo.
Wannan shi ne saka mokon fadowa akan dutsen. AT: "zai farfashe"
"Amma akan duk wanda dutsen ya faɗi." Wannan misali na uku na magana akan wanda suka ki shi kamar shi babban dutse ne wanda rugurguje su.
A wannan ayan, a "sa hanu akan shi" wani lokaci na nufin a kama shi mutumin. AT: "nemi hanya ku kama shi"
"nan da nan"
Wannan shi ne dalilin da ya sa ba su kama Yesu nan take ba. Mutanen sun ba wa Yesu grima, kuma shugabanen addinin suna tsoronabin da mutane za su yi idan sun kama shi. AT: "ba su kama shi ba domin su na tsoron mutanen"
"marubutan da shugaban firistoci suka aiki magewaya su duba Yesu"
"domin suns so su zaigi Yesu da cewa ya faɗa abin da ba kyau"
hukumci" da " ikon" hanya ne guda biyu wanda na cewa suna so gwamna ya yi wa Yesu shari'a. za'a iya bayya na shi da furci ɗaya ko biyu. AT: "domin gwamna ya hukunta Yesu"
"Magewayan suka tambaye Yesu"
Magewayan suna kokari su ruɗe Yesu. ba su yarda da wadannan abubuwa akan Yesu ba.
"mu" na nufin magawayan.
Ma'ana mai yuwa 1)"ka faɗi gaskiya koda mutane masu muhimmanci ba su son shi" ko 2) "kada ka so wani bisa ɗayan"
Wannan shi ne sashin da magawayan suke fada cewa sun san Yesu.
Su na sammanin Yesu ys ce "i" ko "a'a." Idan ya ce "i" mutanen Yahudawan zasu yi haushi da shi domin ya ce masu su biya harajin ga gomnatin wata ƙasa dabam. Idan ya ce "a'a," shugabanen addinin za su gaya wa Romawa cewa Yesu ya na koya wa mutane su karya dokan Romawa.
Suna tambayan dokan Allah, ba dokan Kaisar ba. AT: "ko dokan mu ya yarda mana"
Domin Kaisar shi ne yake mulkin gomnatin Romawa, za su iya nufin gomnatin Romawa da sunan Kaisar.
"A Yesu ya gane yadda uske da sha'ani mai wuyan gane wa" ko "Amma Yesu ya ga suna so su yi masa tarko." Wannan kalmar "nasu" nanufin magawayan.
Wannan ƙirarren kuɗin azurfa ne na Romawa wanda ya isa ladan aiki na rana ɗaya.
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya amsa wa wadan da suke so su yi masa wayo.
"hoto da suna"
" Sai Yesu ya ce masu"
Wannan kalmar "bayar" an gane a sashin da ya wuce. za'a iya maimaita ta anan. AT: " ku kuma ba Allah"
"Magewayan ba su iya samun abin da ba daidai ba, a abun da ya fada
"amma sun yi mamaki da amsar sa kuma ba su iya ce komai ba"
Wannan sashin ya nuna Sadukiyawa sun zama kungiyan Yahudawa da suka ce ba wanda zai tashi daga mattatu. bai nuna da cewa wasu Sadukiyawa sun yarda da cewa akwai tashin mattatu wa su kuma ba su yarda ba.
"idan dan'uwan mutum ya mutu sa'anda yake da mata amma ba shi da yara"
"mutumin ya aure matan dan'uwar sa gomruwa daya mutu"
Yahudawa sun duba yaro na farko da matan tahaifa wanda ta aure dan'uwan mijin ta da ya mutu kamar shi yaron mijin matan ne na farko. Wannan yaron zai gaji dukiyan jijin mahaifiyar sa na farko da sunar sa.
Wannan mai yuwa ya faru, amma mai yuwa labari ne sun yi su gwada Yesu.
"dan'uwa na ɗaya ... dan'uwa na biyu ... dan'uwa na uku"
"ya mutu ba shi da yara" ko "mutu, amma ba shi da yara"
ba su maimaita takaicecen abubuwa da yawa ba domin a bar labarin guntu. AT: "na biyun ya aure ta abu iri ɗaya kuma ya faru" ko "dan'uwan na biyu ya aure ta ya kuwa mutu ba shi da yara"
"Na ukun ya aure ta"
Ba su maimaita takaicecen abubuwa da yawa ba domin a bar labarin guntu. AT: "a hanya ɗaya sauran yan'uwa bakwai sun aure ta har sun mutu ba su da yara"
"dukka yan'uwa bakwain nan" ko "kowane yan'uwa bakwain"
"Sa'anda mutane suka tashi daga mattatu" ko "Sa'anda mutanen da suka mutu sun dawo a raye kuma." wa su yaren suna da hanyar nuna da cewa Sadukiyawan ba su yarda da cewa za su tashi da ga mattatu ba, kamar "A sammanin tashin mattatun" ko Sammanin mutanen da suka mutu sun tashi daga mattatu."
"Mutanen duniyan nan" ko "Mutanen wannan lokacin." Wannan na nuna bambanci da nutanen da suke sama ko mutanen da su ke raye bayan tashin mattatu.
A al'adu an yi maganar maza suna auren mata da mata kuma ana bada su a aure ga mazan su. AT: "yi aure"
AT: "mutanen waccan tsara da Allah ya duba suna da kirki"
"a tashi su daga mutuwa" ko "su tashi daga mutuwa"
Daga cikin duk wadanda su ka mutu. Wannan furcin ya kwatanta duk mattattun mutane tare a cikin ƙarƙashin ƙasa. su karba tashin mattatu a sakanin su yin maganar sake rayuwa kuma.
A al'adu can an yi maganar maza suna auren mata da mata kuma ana bada su a aure ga mazan su. AT: "ba za suyi aure ba" ko "ba za su sami aure ba." Wannan bayan tashin mattatu.
Wannan bayan tashin mattatu. AT: "Ba za su iya mutuwa kuma ba"
"su 'ya'yan Allah ne domin ya dwao da su daga mattatu"
Wannan kalmar " ko" ya na nan domin Sadukiyawan basu yi mamaki ba da litafin ya ce mattatu sun sahi, amma ba su yi sammanin Musa ya rubuta wani abu kamar haka ba. AT: "Amma ko Musa ya nuna cewa mattatun mutane sun tashi"
AT: "Allah aya sa mattatu sun tashi kuma"
"a wata sashin littafin ida ya rubuta game da konewar jeji" ko "a cikin littafin game da konewar jeji"
"inda Musa ya kira Ubangiji"
"Allah na Ibrahim, Ishaku da Yakubu." Duk suna bauta wa allah ɗaya.
Wannan kalmaran yi amfani d ita a nan domin a sa fashi a asalin koyasuwan. A nan Yesu ys bayyana yadda labarin ya hakikanta da cewa mutane sun tashi da mattatu.
Wadannan magnar tana da ma'ana iri ɗaya an fade ta sau biyu domin nauyi. wasu yaren suna da daban daban na yn nauyin. AT: "Ubangiji shi ne Allah mutanen da suke raye kawai"
"ammam allah mutane maus rai." tunda wadannan mutane sun mutu na fuska, za su zama a raye a ruhaniyance. AT: "amma Allah mutane da ruhun su ya na a raye, ko da shike jikin sy ya mutu"
"domin a gun Allah duk suna a raye" ko "domin ruhun su ya na zaune a gaban Allah"
"wadansu marubutan suka ci wa Yesu." akwai marubutan da suke nan sa'anda Sadukiyawan suke tambayan Yesu.
Ba'a bayyane yake ba ko wannan ya na nufin marubutan ko Sadukiyawan, ko dukan su. yana da kyau ka ajiye bayyanin na gaba ɗaya.
"suna jin tsoro su tambaye shi ... tambayoyi" ko "ba su yi kasadan tambayan ... tambayoyi ba." sun gane da cewa basu san dayawa kamar yadda Yesu ya sani ba, amma ba su so su faɗa haka.Wannan za'a iya bayyana shi. AT: "ba su sake yi masa wani tambaya da wayo ba domin sun ji tsoro kada amsan sa ai hikkma ya sa su su zama wawayi koma"
Donme suka ce ... ɗa?" Yesyu ya yi amfani da tambaya domin ya sa marubutan su yi tunani akan wanene Mai ceto. AT: "Mu yi tunani akan su cewa ... ɗa." ko "Ni zan yi magana akan su cewa ... ɗa"
Annabwa, shugabanen addini, da mutanen Yahudawa gaba ɗaya sun sani da cewa Mai ceto ɗan Dauda ne. AT: "kowanne ya ce" ko "mutane sun ce"
"Zuriyan sarki Dauda." Wannan kalmar "ɗa" an yi amfani da shi a nan doimn nufin zuriya. a wanan yanayi ya na nufin wanda zia yi sarauta bisa mulkin Allah.
Wannan tambaya ne daga littafin Zabura wanda ya ce "Yahweh ya cewa Ubangiji na." Amma Yahudawa sun daina cewa " Yahweh"sun cigaba da ce Ubangiji" amimakon. AT: "Ubangiji ya ce wa Ubangiji na" ko "Allah ya cewa Ubangiji na"
Dauda na kiran Almasihu "Ubangiji na"
Ka zauna a "hanun dama na Allah" sananniyar aiki ne na karban babban daraja da iko daga Allah. AT: "Zauna a wuri mai daraja a gefe na"
An yi maganar makiyin Mai ceto kamar wani kayan ɗaki wanda zai iya sa ƙafafun sa akai ya huta. Wannan hoton biyayya ne. AT: "sai na maida makiyanka kamar karkashin tafin sawunka" ko "sai na yi maka nasara akan makiyanka"
A al'adun waccan lokaci, an fi bawa baba daraja fiye da yaro. Dauda mu na sunar 'Ubangiji' domin Almasihu ya nuna ya fi Dauda grima.
"to ta yaya Almasihu ya za ma ɗan Dauda?" AT: "Wannan ya nuna da cewa Almasihu ba zuriya Dauda bane kawai"
"ku zama a fadake game da"
Mayan riguna zai nuna cewa suna da muhimmanci. AT: "wanda suke so suna tafiya suna sa riguna su masu muhimmanci"
"Suna kuma cin gudajen gwamraye. "An yi maganar marubutan kamar suna dabba ne masu jin yunwa wanda suka cinye gidajen gwamraye. Wannan kalmar "gidaje" kalmane na duk inda gwamruwa take zama kuma dukkan kayanta da tasa a gidanta. AT: "sun kuma dauka wa gwamruwan dukkan kayanta"
"suna yin bokon adalci su kuma yi doguwar addu'a" ko "suna yin doguwar addu'a saboda mutane su gan su"
"Za su karɓi shari'a mafi tsanani." AT: "Ba shakka Allah zai hukumta su da tsanani"
1Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji. 2Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki. 3Sai ya ce, "Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu. 4Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi."5Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce, 6"Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba."7Sai suka yi masa tambaya, cewa, "Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?" 8Yesu ya amsa, "Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su. 9Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba."10Sa'annan ya ce masu, "Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki. 11Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.12Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana. 13Zai zamar maku zarafin shaida.14Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa, 15gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.16Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku. 17Kowa zai ki ku saboda sunana. 18Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka. 19A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.20Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa. 21Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki. 22Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.23Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan. 24Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.25Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa. 26Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.27Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma. 28Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato."29Yesu ya bada misali, "Duba itacen baure, da duka itatuwa. 30Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma. 31Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.32Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru. 33Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.34Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri 35kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.36Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum."37Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun. 38Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
Wannan shi ne abin da ya auko mai zuwa a labarin. ko a rana ɗaya da sadukiyawa suka tambaye Yesu [Luka 20:27]
za ka iya bayyana menene kyautan. AT: " kyautan kuɗi"
wani akwati ne a cikin haikali wanda mutane suke sa kuɗin su domin yi wa Allah kyauta
Wannan wata hanya ne na gabatar da wani sabuwar hali a labarin.
"kananan ƙerarren kuɗi gu da biyu" ko "kankanana ƙerarrun kuiɗ na tagulla." Wadannan su ne kuɩ mafi ƙanƙanta mafi daraja da mutane suke amfani da su a wancan lokaci. AT: "kwobobi biyu" ko ƙananan kuɗi mai daraja kaɗan"
Wannan na nufin cewa abin da Yesu ya ke so ya faɗa na da amfani sosai.
Yesu ys na magana da al'majeren sa. wannan kalmar " kia" jam'i ne.
Allah ya duba kyautar ta,karamin kuɗi ne,mafi muhimmanci feye da babban kuɗin da mutanen suka bayar. AT: "kyautar gwauruwa ya fi daraja da fiye da babban kyautar da masu kuɗin suka bayar"
"su na da kuɗi dayawa amma sun bayar da karami daga cimim ta"
"wanda take da ƙaramin kuɗi sosai"
abubuwan da mutane suka bawa Allah
Wannan na nufin haikali mai kyau da adonta.
"lokaci na zuwa" ko "wata rana"
Za'a iya fada sabuwar bayyani anan. AT: "bari aka daya. za a rushe su a kasa" ko "bari akak dayan.abokan gaba zasu yaga kowane dutse a ƙasa"
AT: "kowanne dutse za'a cire daga wurin sa kuma za a rushe su ƙasa"
"al'majeren suka yi wa Yesu tambaya" ko al'majeren Yesu suka yi masa tambaya"
Wannan na nufin abin da Yesu ya gama fada game da abokan gaba zasu rushe haikali.
Yesu ya na magana wa almajeren sa. Wannan kalmar "kai" jam'i ne. AT: "kada ku yarda da ƙarya" ko "kada wani ya ruɗe ku"
Mutane na zuwa a cikin sunar sa cewa suna wakilcin sa. AT: "cewa sune ni" ko "naman su sami iko na"
" Ni ne Almasihu" ko "Ni ne Mai ceto"
"Kada ku yarda da su" ko "Kada ku zama al'majeren su"
A nan "yakoki" mai yuwa na nufin faɗa sakanin ƙasashe, "hargitsi" kuma na nufin mutane na faɗa da shugabanen su ko sakanin wasu a cikin ƙasan su. AT: "yakoki da tawaye" ko yakoki da kewayewa"
"kada ku bar wadan nan abubuwa su firgitar da ku" ko "kada ku ji tsoro"
Wannan na nufin shari'an karshe. AT: "karshen duniyan ba zai faru nan da nan ba bayan yakoki da hargitsi" ko "duniyan ba zai kare nan da nan ba bayan wadannan abubuwa sun faru"
"karshen komai" ko "karshenlokaci"
"Sa'annan Yesu ya cewaal'majeren sa." tunda wannan cigaba ne a maganar Yesu daga ayan da ya wuce, wasu yaren za su so su ce "Sa'annan Yesu ya ce ma su."
A nan "Al'umma" misali ne na mutane alumma, "tasar wa" kuma misali ne na hari. Wannan kalmar "alumma" na wakilcin alummai gaba ɗaya, ba wata alumma ɗaya ba. AT: "Mutanen alumma ɗaya za su faaɗ wa mutanen wata alummai" ko "mutanen wasu alummai za su faɗa wa mutanen wa su alummai"
Wannan na nufin kananar yaruruka na mutane dai da ƙasashe biyu.
Wannan kalmar "za ya tasar" an gane daga ayan da ta wuce kuma ta na nufin faɗa wa. AT: "mulki kuma za ya tasar wa mulki" ko "mutanen wata mulki za su tasar wa mutanen wa su mulki"
Wannan kalmar "za'a yi" an gane a sashin da ta wuce. AT: "za a yi yunwa da annoba a wurare dabam dabam" ko "za'a yi lokacin yunwa da cututtuka a wurare dabam dabam"
"al'amura da za su bawa mutane tsoro" ko "al'amura da za su mutane su ji tsoro"
"za su kama ku." Wannan furcin na nufin mutane za su nuna iko a kan al'majeren. AT: "za su kama ku"
mutane zasu" ko abokan gaba zasu"
Yesu yana yi wa al'majeren sa magana. Wannan kalmar " ku" jam'i ne.
"bada ku ga shugabanen majami'u"
"da ba da ku a cikin kurkuku" ko "sa ku a cikin kurkuku"
Wannan kalmar "suna" an yi amfani da shi anan amasa yin Yesu da kansa, AT: "domin na" KO "domin ku na bi na"
"domin ku yi shaida a kai na"
"Domin wannan," nufa ga komai Yesu ya ce, farawa a [Luka 21:10]
Anan "zukata" misali ne na hankalin mutane. AT: "ku kudura hankalin ka" ko "shirya da ƙarfi" :
"kada ki siffa akan lokaci abin da zaku fada ku ƙare kanku game da zargin"
"hikiman da ba wani makiyanku da za su yi tsayayya ko su karyata ku ba"
"Ni zan gaya maku abu mai hikima da za ku fada"
Wannan za'a iya hada su a sashi ɗaya. AT: "kalmomi da hikma" ko "kalma mai hikma"
AT: "har ma da iyaye, abokanaye, da dangi za su bada ku ga hukumomi"
"za su kashe wadan sun ku." Ma'a na mai yuwa 1) "hukumomin za su kashe wadan sun ku" ko 2)wadan da su ka ba da ku za su kashe wa sun ku." Ma'ana na farkon ya fi yuwa.
AT: "Wannan kalmar "kowa" na nuna nauyin yadda mutane da ya wa za su ki al'majeren, ko ta fadawa1) "zai za ma kamar kowa ya ki ka" ko "zai zama kamar kowa ya ki ku" ko 2) gaba ɗaya. AT: "mutane mafi duka za su ki ku" ko "Mutane dayawa za su ki ku"
Yesu ya yi magana akn karamin sashin mutum. ya na yin nauyin cewa mutumin gaba ɗaya ba zai hallaka ba. Yesu ya riga ya fada cewa wasun su za a kashe su, wasu sun gane wannan cewa ba za su ji illa ba a ruhaniyance. AT: "Amma wadannan abuuwa ba za su yi ma ku illa ba " ko "kowane gashi a kan ku zai mara haɗari"
"Da rekewa da ƙarfi." AT :" Idan baku bari ba"
"rai" an gane ya na nufin madowamiyar sashin mutum. AT: "za ku karbi rai" ko "za ku ceci kan ku"
AT: " sojoji sun kewaye Urushalima"
"da cewa ta kusan hallaka" ko "da cewa sun kusa su hallakar da ita"
guje wa haɗari
Wannan na nufin kauyen da ke wajen Urushalima, ba wa alumma ba . AT: "a wajen garin"
"shigo cikin Urushalima"
"wadannan ranakun harasuwa ne" ko "wannan zai zama lokacin da Allah zai haras da garin"
AT: "duk abuin da annabawa suka rubuta a cikin littafi tunda daɗewa"
AT: " zai faru"
"ga iyaye da suke ba wa 'ya'yan su mama"
Ma'ana mai yuwa1) mutanen ƙasar za su sha kunci ko 2) za'a fuskance masifa a ƙasar.
"za'a yi fushi ga mutanen nana wancan lokaci." Allah zai kawo wannan fushin. AT: "wadannan mutane za su ga fushin Allah" ko "Allah zai yi haushi sosai kuma zai hukunta wadanan mutane"
"za'a kashe su ta kaifin takobi." A nan "faɗi ta kaifin takobi" na nufin cewa abokan gaba soja za su kashe su. AT: "abokan gaba soja za su kashe su"
AT: "abokan gaba za su kama su su kai su wa su ƙasashe"
Wannan kalmar "dukka"furci ne a nuna nauyin cewa za'a kai su ƙassashe dayawa. AT: "zuwa wasu ƙasashe dayawa"
Ma'ana mai yuwa1) al'ummai za su ci nasara a Urushalima zauna a cikin ta ko 2) al'ummai za su hallakar da garin Urushalima ko 3) al'ummai za su hallakar da mutanen Urushalima.
Wannan misalin ya yi maganar Urushalima kamar mutanen wasu ƙasashe suna aiki akan ta su kuma rugurguju shida tafin su.
AT: "lokacin al'ummai ya zo ga karshe"
A nan " al'ummai" na nufin mutanen da ke cikin ta. AT: "mutanen al'ummai za su sha kunci"
"kunci saboda za su rude da rurin teku da rakuman ruwa" ko "kunci sabada karan surutun ruwan teku motsin ta mai kaushi zai sauratar da su." Wannan ya yi kamar babban haɗari da kunci da ba'a saba gane ba a saba gane ba a teku.
"abubuwan da za su faru a duniya" ko "abubuwan da za su faru wa duniya"
AT: Ma'ana mai yiwu1)Allag zai grigiza wata rana da tauraru domin kada su yi motsi yadda suka saba ko 2) Allah zai sokani ikokin ruhohi da ke a sama. na farkon aka yaba.
Yesu yana nufin kansa. AT: "ni,Dan Mutum, i na zuwa"
"zuwa ƙasa a cikin gajimarai"
A nan "ƙarfi" mai yuwa na nufin ikon sharanta duniya. Anan "daukaka"zai iya zama hasken wuta. Allahwani lokaci yana nuna daukakar sa da hasken wuta. AT: "ƙarfi sosai da daukaka mai girma" ko "zai zama mai ƙarfi da daukaka sosai"
wani lokaci idan mutane su na tsoro, su kan sunkuya ƙasa saboda kada aji musu ciwo. idan sun dain tsoro za su tashi tsaye. AT: "tashi tsaye da rashin tsoro"
daga kai misali ne na kallon sama. idan suka daga kansu sama,za su iya ganin mai ceton su yana zuwa gun su. AT: "kalli sama"
Allah wanda ya ceci an yi maganar sa kamar shi ceton ne ya s. Wannan kalmar "ceton" wannan tsamo aikatau ne wanda za' aiya juya ta kamar fi'ili. AT: "domin Allah ya kusa ya cece ka"
"Sa'adda sabuwar ganye ya fara girma"
"bazara ya yi kusa ya fara. "Bazara a Isra'ila tana bin inda itacen baure take fitowa kuma lokacin ne bauren take nuna. AT: "lokacin gribi yayi kusa a fara"
Alamar bayanuwa da Yesu ya kwatanta na mulkin Allah kamar almar bayanuwa na ganyen itacen baure ya ke nu na zuwan bazara.
"Allah ya yi kusa ya ƙafa mulkin sa." AT: "Allahya yi kusa ya yi mulki kamar sarki"
Ma'ana mai yiwa1) zamanin da za su gan alama na farko da Yesu ya yi maganar ta ko 2) zamanin da Yesu yake yi masu magana. na farkon ya fi yuwa.
AT: "zai zama da rai sa'anda"
"Sama da ƙasa za ta dena bayanuwa." Wannan kalmar "sama" anan na nufin sararin sama da dukan komai gaban shi.
"maganata ba za ta dena bayanuwa ba" ko "magana ta ba za ta fadi ba." Yesu ya yi amfani da "kalmomin" anan ya nufa duk abin da ya fada.
AT: "zai cigaba har abada"
"zuciya" a nan na nufin hankali da tunanin mutum. AT: "domin kada ku cika"
Yesu anan ya yi maganar zunubin da take biyowa kamar nawaya ne na fuskawadda mutum zai dauka.
"abin da shayeshaye sosai zai yi maka" ko "bugagge"
"damuwa sosai akan wannan rayuwa"
kamar yadda tarko take kulle dabba sa'anda dabban bata sammance ta ba. ranar zata faru sa'anda mutane basu sammance ta ba. AT: "wacan rana za ta faru sa'anda ba ku sammace ta ba, kamar tadda tarko kulle dabba ba zato"
zuwan wacan rana za ta za ma ba zato ba sammani ga wadan da ba su shriya su na kallon ta ba. AT: "rayuwa. gama idan ba ka yi hankali ba ,, wacan rana za ta kulle ka ba zato"
Wannan na nufin ranar da Mai ceto zai dawo. AT: "ranar da Ɗan Mutum zai dawo"
"zai shafi kowa" ko "abin da zai auko a wacan rana da ta shafi kowa"
an yi magaar faskar duniya kamar faskar mutum ne. wato sashin waje. AT: "a faskar dukkan duniya" ko "a dukan duniya"
"ku shriya ma zuwa na"
Ma'ana mai yuwa1) "ƙarfi sosai ku jumre wadannan abubuwa" ko 2) "ku iya guje ma wadannan abubuwa."
"wadannan abubuwan da zai faru." da Yesu ya gama gaya masu akan abbuwan ban tsoro da zai faru, kamar zalumci, yaki, da kamakamai.
"tsaya ba tsoro a gaban Ɗan Mutum." Wannan mai yuwa na nufin sa'anda Ɗan Mutum ya sharanta kowa. mutumin da bai shirya ba zai ji tsoron Ɗan Mutum kuma ba zai iya tsaya wa ba tsoro ba.
"da rana zai koyar" ko "zai koyar kowanne rana." aya na beye ya faɗa game da abubuwan da Yesu da mutane suke yi a kowanne mako kamin ya mutu.
fristoci ne kawai aka bari a cikin haikali" ko "acikin haraban haikalin"
"da dare ya kan je wajen brinin" ko "yana fita kowanna dare"
Wannan kalmar "dukka" mai yuwa an kwatanta domin a yi nauyin cewa taron na da yawa. AT: "mutane dayawa ne a garin" ko "kusan dukka kowa a garin"
"za su zo kowace rana da sassafe"
"su ji shi yana koyarwa"
1Anan nan idin gurasa mara yisti ya yi kusa, wanda a ke kira Idin ketarewa. 2Manyan firistoci da marubuta suka yi shawara yadda za su kashe Yesu, gama suna jin tsoron mutane.3Shaidan ya shiga Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin goma sha biyun. 4Yahuza ya je ya yi shawara da manyan firistoci da Jarumawa yadda zai ba da Yesu a garesu.5Suka yi farin ciki, suka yarda su ba shi kudi. 6Sai ya yarda, sai ya nimi dama yadda zai ba da shi garesu a lokacin da babu taro.7Ranar idin gurasa mara yisti ya yi, da dole za a yi hadayan rago na Idin ketarewa. 8Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya, ya ce masu, "Ku je ku shirya mana abincin Idin ketarewa, domin mu ci." 9Suka tambaye shi, "A ina ka ke so mu shirya?"10Ya amsa masu, "Ku ji, sa'adda ku ka shiga birnin, wani mutum mai dauke da tulun ruwa zai same ku. Ku bishi zuwa cikin gidan da za ya shiga. 11Sai ku gaya wa mai gidan, 'Malam ya ce, "Ina dakin baki, inda zan ci abincin Idin ketarewa da almajirai na?'"12Zai nuna maku babban bene wanda yake a shirye. Ku shirya a can." 13Sai suka tafi, suka sami komai kamar yadda ya gaya masu. Sai suka shirya abincin Idin ketarewan.14Sa'adda lokacin ya yi, ya zauna da almajiran. 15Sai ya ce masu, "Ina da marmari matuka in ci wannan abincin Idin ketarewa da ku kamin in sha wahala. 16Gama na ce maku, ba zan ci shi kuma ba, sai dai an cika shi a mulkin Allah."17Sai Yesu ya dauki koko, sa'adda ya yi godiya, sai yace, "Karba wannan, ku rarraba a tsakaninku. 18Gama ina ce maku, ba zan sha wannan ruwan inabi kuma ba, sai dai mulkin Allah ya zo."19Sai ya dauki gurasa, sa'adda ya yi godiya, ya kakkarya shi, sai ya ba su, cewa, "Wannan jikina ne wanda aka bayar dominku. Ku yi wannan domin tunawa da ni." 20Sai ya dauki kokon kuma bayan jibi, cewa, "Wannan koko sabon alkawari ne cikin jinina, wanda aka zubar dominku.21Amma ku yi lura. Wanda zai bashe ni yana tare da ni a teburi. 22Gama Dan Mutum zai tafi lallai kamar yadda aka kaddara. Amma kaiton wannan mutum da shine za ya bashe shi!" 23Sai suka fara tambaya a tsakaninsu, wanene a cikinmu da zai yi wannan abu.24Sai gardama ta tashi a tsakaninsu game da wanene mafi girma. 25Ya ce masu, "Sarakunan al'ummai suna nuna iko akansu, kuma wadanda suke da iko a kansu ana ce da su masu mulki da daraja.26Amma kada ya zama haka da ku. A maimakon haka, bari wanda ya ke mafi girma a cikinku ya zama mafi kankanta. Bari wanda yafi muhimmanci kuma ya zama kamar mai hidima. 27Gama wanene yafi girma, wanda ya zauna a teburi, ko kuwa wanda yake yin hidima? Ba wanda ya zauna a teburi ba? Duk da haka ina kamar mai hidima a tsakaninku.28Amma ku ne wadanda ku ke tare da ni a cikin jarabobina. 29Na baku mulki, kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, 30domin ku ci ku kuma sha a teburi na mulkina. Za ku zauna a kan kursiyai kuna shari'anta kabilun nan goma sha biyu na Israila.31Siman, Siman, ka yi hankali, shaidan ya nemi izini a bada kai domin ya tankade ka kamar alkama. 32Amma na yi maka addu'a, saboda kada bangaskiyarka ta fadi. Bayan da ka juyo kuma, ka karfafa 'yan'uwanka."33Bitrus ya ce masa, "Ubangiji, ina shirye in tafi tare da kai zuwa cikin kurkuku da zuwa mutuwa." 34Yesu ya amsa masa, "Ina gaya maka, Bitrus, kamin caran zakara a yau, za ka yi musu na sau uku cewa ba ka sanni ba."35Sa'annan Yesu ya ce masu, "Lokacin da na aike ku babu jaka, ko burgami ko takalma, ko kun rasa wani abu? Sai suka amsa, "Babu." 36Ya kuma ce masu, "Amma yanzu, wanda ya ke da jaka, bari ya dauka, da kuma burgami. Wanda ba shi da takobi sai ya sayar da taguwarsa ya sayi guda.37Gama ina ce maku, abin da aka rubuta game da ni dole sai ya cika, 'An lisafta shi kamar daya daga cikin masu karya doka.' Gama abinda aka fada akaina ya cika." 38Sai suka ce, "Ubangiji, duba! Ga takuba biyu." Sai ya ce masu, "Ya isa."39Bayan cin abincin yamma, Yesu ya tafi, kamar yadda ya saba yi, zuwa dutsen Zaitun, sai almajiran suka bi shi. 40Sa'adda suka iso, ya ce masu, "Ku yi addu'a domin kada ku shiga cikin jaraba."41Ya rabu da su misalin nisan jifa, sai ya durkusa kasa ya yi addu'a, 42yana cewa "Uba, in ka yarda, ka dauke wannan kokon daga gareni. Ko da yake ba nufina ba, amma bari naka nufin ya kasance."43Sai mala'ika daga sama ya bayyana a wurinsa, yana karfafa shi. 44Yana cikin wahala sosai, sai ya dukufa cikin addu'a, har zufarsa kuma tana diga a kasa kamar gudajen jini.45Sa'adda ya tashi daga addu'arsa, sai ya zo wurin almajiran, ya same su suna barci domin bakin cikinsu, 46sai ya tambaye su, "Don me kuke barci? Tashi ku yi addu'a, saboda kada ku shiga cikin jaraba."47Sa'adda yana cikin magana, sai, ga taron jama'a suka bayana, tare da Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya na jagabansu. Sai ya zo kusa da Yesu domin ya yi masa sumba, 48amma Yesu ya ce masa, "Yahuza, za ka ba da Dan Mutum da sumba?"49Sa'adda wadanda suke kewaye da Yesu suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, "Ubangiji, mu yi sara da takobi ne?" 50Sai daya daga cikinsu ya kai wa bawan babban firist sara a kunne, sai ya yanke masa kunnensa na dama. 51Yesu ya ce, "Ya isa haka." Sai ya taba kunnensa, sai ya warkar da shi.52Yesu yace wa manyan firistoci, da masu tsaron haikali, da dattawa wadanda suke gaba da shi, "Kun fito kamar za ku kama dan fashi, da takuba da sanduna? 53Sa'adda nake tare da ku kowace rana a haikali, ba ku kama ni ba. Amma wannan shine lokacinku, da kuma ikon duhu."54Suka kama shi, sai suka tafi da shi, suka kawo shi cikin gidan babban firist. Amma Bitrus yana binsa daga nesa. 55Bayan da suka hura wuta a tsakiyar gidan da suka zazzauna tare, Bitrus ya zaune a tsakaninsu.56Sai wata baranya ta ganshi ya zauna a hasken wuta, sai ta zura masa ido ta ce, "Wannan mutum ma yana tare da shi." 57Amma Bitrus ya yi musu, yana cewa, "Mace, ban san shi ba." 58Bayan dan karamin lokaci sai wani mutum ya gan shi, sai ya ce, "Kaima kana daya daga cikinsu." Amma Bitrus ya ce, "Mutumin, ba ni ba ne."59Bayan sa'a daya sai wani mutum ya nace da cewa, "Gaskiya wannan mutum yana tare da shi, gama shi dan Galili ne." 60Amma Bitrus ya ce, "Mutumin, ban san abin da kake fada ba." Sai nan da nan, da yana cikin magana, sai zakara ta yi cara.61Yana juyawa, sai Ubangiji ya dubi Bitrus. Sai Bitrus ya tuna kalmar Ubangiji, sa'adda ya ce masa, "Kafin zakara ya yi cara yau za ka musunce ni sau uku." 62Da fitowarsa waje, Bitrus ya yi kuka mai zafi.63Sai mutanen da ke tsare da Yesu suka yi masa ba'a da bulala kuma. 64Bayan da suka rufe masa idanu, suka tambaye shi, cewa, "Ka yi annabci! Wa ya buge ka?" 65Suka yi wadansu miyagun maganganu na sabo game da Yesu.66Da gari ya waye, sai dattawa suka hadu tare, da manyan firistoci da marubuta. Sai suka kai shi cikin majalisa 67suka ce, "Gaya mana, in kai ne Almasihu." Amma yace masu, "Idan na gaya maku, ba za ku gaskanta ba, 68idan na yi maku tambaya, ba za ku amsa ba.69Amma nan gaba, Dan Mutum zai zauna a hannun dama na ikon Allah." 70Suka ce masa, "Ashe kai Dan Allah ne?" Sai Yesu ya ce masu, "Haka kuka ce, nine." 71Suka ce, "Don me muke neman shaida? Gama mu da kanmu munji daga bakinsa."
Yahuza ya yarda ya ba da Yesu.Wannan ayan ya bada labari na ƙasa akan abin da ya auko.
Wannan kalmar an yi amfani da ita anan domin a gabatar da sabuwar abin da ya auko.
Ana kiran ranar idin da wannan suna domin ranar idin , Yahudawa ba su cin gurasa da aka yi da yisti. AT: "rabar idin sa'anda su ke cin gurasa mara yisti"
"an yi kusa a fara"
Firistoci da marubutan ba su da iko su kashe Yesu da kansu, amma su na sa sammani cewa za su sami wasu su kashe shi. AT: "Yadda za su sa a kashe Yesu" ko "yadda za su sa wani ya kashe Yesu"
Ma'an mai yuwa 1) "suna jin tsoron abin da mutane za su yi" ko 2) "suns tsoro cewa mutane za su zama da Yesu sarki."
Wannan mai yuwa ya na kama da kayan iblis.
"shugaban firistoci"
hafsa na masu tsaron haikalin
"yadda zai taimakesu su kama Yesu"
"Manyan firistocin da kaftin su ka yi farin ciki"
"su bawa Yahuza kuɗi"
"Ya yarda"
Wannan aiki ne da ake kan yi da ya cigaba bayan da labarin ya kare.
"dauke shi"
"asirance" ko "lokacin da babu taron"
" rana ta gurasa mara yisti." Wannan rana ce wanda dukkan Yahudawa za su ci gurasan da aka yi yisti a gidajen su. sa'anna za su bayyana murna na idin gurasa mara yisti na kwanaki bakwai.
kowanna iyali ko kungiya za su kashi tunkiya su ci tare, ana kashi tunkiyoyi da yawa. AT: "dole mutane su kashi tunkiya domin abincin idin ketarewa"
Wannan kalman ne na gaba ɗaya "ku shirya." ba wai Yesu yana gaya wa Yahaya da Bitrus su yi dahuwan dukka ba.
Yesu ya hada da Bitrus da yahaya sa'anda ya ce "mu"Bitrus da yahaya su na cikin kungiyan al'majeren da za su ci abincin.
Wannan kalmar "mu" bai hada da Yesu ba. Yesu ba ya cikin kungiyan da za su shirya abincin.
"yi shirin domin abincin" ko "shirya abincin"
"Yesu ya amsa wa Bitrus da Yahaya"
Yesu ya yi amfani da wannan kalmar domin ya gaya masu kasa kunne su yi daidai abin da ya gaya masu.
"za ku gan mutum ya na dauke da tulun ruwa"
dauke da tuluda ruwa a cikinta." Mai yuwa zai dauka tulun a ƙafadar sa.
"Ku bishi, ku shiga cikin gidan"
Faɗin ya fara da "Ina dakin baki" faɗi na daidai na abin da Yesu ya faɗa, malamin ya na so ya cewa maigidan. zaka iya juya shi kamar faɗin abin da wani ya ce ba ta hanya kusa- kuas ba. AT: "Malamin mu ya tamabaya ina dakin baki wanda zai ci abinin idan ketarewa da al'majeren sa." ko "Malamin mu ya cw ku nuna mana da kin baki inda za mu ci abincin idin ketarewa da mu da sauran al'majeren."
Wannan na nufin Yesu.
"ci abincin idin ketarewa"
Yesu ya cigaba da bawa Bitrus da Yahaya ummurni.
"Maigidan zai nuna maku"
"daki na sama." Idan jama'an ku ba su da gidaje da yake da daki bisa wani dakuna, zaka su ka kwatanta yadda gidaje a birni suke.
"Sai Bitrus da Yahaya suka je"
"Sa'anda lokacin cin abincin ya yi"
"Yesu ya zauna"
"Ni ina so sosai"
Yesu ya na nufin mutuwar sa nan gaba. Wannan kalmar "wahala" anan ta na nufin ka shiga cikin wani yanayin mai wuya da ba ka saba ba ko ka ji zafi sosai.
Yesu ya yi amfani da wannan sashin domin ya yi nauyi akan abin da zai faɗa mai zuwa.
AT: "Ma'ana mai yuwa 1)sa dai dalilin idin ketarewa ya cika. AT: "sai Allah ya cika shi" ko "sai Allah ya cika dalilin idin ketarewan" ko 2) "sai mun bayyana murnan idin ketarewa na ƙarshe"
"ya dauki kokon ruwan inabi sama"
"sa'adda ya yi godiya ga Allah"
"ya cewa annabawan sa"
Su raba abin da ke cikin koko din, ba kuwa kokon da kantaba. AT: "ku raba ruwan inabin da ke cikin kokon a tsakaninku" ko "kowane ɗayan ku ya sha ruwan inabin daga cikin kokon"
Wannan na nufin ruwan da aka matse da ƙarfi daga inabin da ya yi grima a gonar inabin. aruwan inabi ana samun ta daga ruwan inabin da ya tashi.
"sai Allah ya ƙafa mulkin sa" ko "sai Allah ya yi mulki a mulkin sa"
Wannan gura san bai da yisti a ciki, saboda haka a kita take.
"ɓarka shi" ko "ya yaga shi." mai yuwa ya gutsutsura shi ko kuwa ya gutsura shi kashi biyu sai ya bawa annabawan su raba a tsakaninsu. Idan zai yu yi amfani fa da furci da za a iya sa ma kowanne yana yi.
Ma'ana mai yuwa 1) "Wannan gurasan jiki na ne" da 2) "Wannan gurasan na nufin jikina."
AT: "jikina ne wanda aka bayar dominku" ko "jikina ne wanda sadokad dominku"
"ci wannan gurasan"
"domin tunawa da ni"
Wannan kalmar "koko" yana nufin ruwan inabi da yake cikin kokon. AT: "ruwan inabi da yake cikin kokon" ko "Wannan kokon ruwan inabi"
Wannan alkawarin zai faru nan da nan bayan da jininsa ya zuba. AT: "sabuwar alkawarin da za'a yarda ta wurin jinina"
Yesu ya yi maganar mutuwar sa da nufin jininsa ya zubar waje. AT: "wanda aka zubar waje da mutuwa diminku" ko "wanda zai fito waje daga ciwo na dominku sa'anda na mutu"
"Wanda zai ba da ni"
"Gama, lallai, Dan Mutum zai tafi" ko "Gama Dan Mutum zai mutu"
Yesu ya na magana game da kansa a mutum na uku.AT: "Ni, Ɗan Mutum, lallai zan tafi"
AT: "kamar yadda allah ya kadara" ko "kamar yadda Allah ya shirya"
AT: "Amma kaiton wannan mutum wanda shi ne za ya bashe Dan Mutum" ko "Amma yadda zai zama mai ban tsoro ga wannan mutum wanda zai bashe Dan Mutum"
"Sai annabawan suka fara yin muhawara a tsakaninsu"
AT: "mafi muhimmanci" ko "mutanen su yi tunani shi ne mafi muhimminci"
Yesu ya ce ma annabawan"
"yi mulki da ƙarfi bisa Al'ummai"
Mutanen mai yuwa ba su yi tunani waccan mutane masu mulkin wadan suka yi wa mutanen su kirki. AT: "suna so a kira su" ko "suna kiran kansu"
"kada ka aikata haka"
Ana ba wa tsofafin mutane girma a waccan al'adan. shugabanen yawanci tsofofin mutane ne kuma an kiran su "dattibai." Mutum mafi kankanta zai zama mafi kankanta ya darma, da muhimmanci mafi kankantan. AT: "muhimmanci mafi ƙanƙantan"
"bawa"
Wannan ya hada umurnin Yesu a aya 26 da dukkan aya 27. yana nufin mutum mafi muhimmanci ya yi bauta domin Yesu bawa ne.
Gama wanene mafi muhimmanci ... hidima?" Yesu ya yi amfani da wannan tambayan domin ya bayyana wa manzanne wanene mafi girma da gaskiye. AT: "ina sonku ku yi tunani akan wanene mafi girma ... hidima."
"wanda yake cin abinci"
Yesu ya yi amfani da wani tambayan ya koya wa al'majeren sa. AT: "haka ne kam wanda ya zauna a teburi ya fi bawan muhimmanci!"
"Amma ina tare da ku in zama bawa" ko "Amma ina tare da ku in nuna maku yadda bawa ya ke aikatawa." Wannan kalmar "amma"yana nan domin akwai bambanci sakanin abin da mutane suke sammani Yesu ya zama kamar da abin da yake kamar.
"sun tsaya da ni a lokacin da nake fama"
Wasu yaren za su so su saka umarnin. AT: "Jamar yadda Ubana ya bani mulki, Na baku mulki"
Na mai da ku masu mulki a mulkin Allah" ko "Na baku iko ku yi mulki a mulkin" ko "Zan mai da ku sarki"
" kamar yadda Ubana ya bani iko in yi mulki kamar sarki a mulkin"
Sarakai suna zama a kursiyi. Zama a kursiyi sanenniyar alama ce na mulki. AT: "zaku yi aiki kamar sarkai" ko "zaku yi aikin sarakai"
Yesu ya faɗi sunar sa sau biyuya nuna da cewa abin da yake so ya faɗa masa yana da muhimmanci sosai.
Wannan kalmar "kai" na nufin dukakan annabawan.Yaren ku tana da siffofi daba dabam na "kai"ka yi aiki da jam'i.
Wannan na nufin shiaɗan yana so ya gwada al'majeren ya nemi wani abun da ba daidai ba. AT: "gwada ka kamar wani yana wucewa da hatsi ta rariya"
Wannan kalmar "kai" anan yana nufi takamaimai ga Siman. Yaren da ta ke da siffofi na kai dabam daban ta yi amfani da siffar mafuradi.
AT: "saboda ka cigaba da samun bangaskiya" ko "ka cigaba da yarda da ni"
A nan "juye baya kuma" misali ne na sake yarda dani kuma . AT: "Bayan da ka sake yarda da ni kuma" ko "Bayan da ka sake bauta mini"
"ka karfafa yan'uwan ka su sake yin karfi cikin bangaskiyar su" ko "taimake yau'uwanka su yarda da ni"
Wannan na nufin sauran al'majeren. AT: "masubi" ko "sauran al'majeren"
Umurnin wannan sashin ayan za'a iya juya ta. AT: "zaka yi musu sau uku cewa ka sanni kamn zakara tayi cara wannan rana"
AT: "zakara za ta yi cara wannan rana kawai bayan ka yi musu na" ko "kamin zakara ta yi cara wannan rana za ka yi musu"
A nan, caran zakaran ta na nufin wani lokaci ne a rana. zakara ta na cara ne kamin rana ta bayyana da safe.saboda haka, wannan na nufin asalatu.
tsuntsun da take kira da ƙarfi kusa da lokacin da rana ta fito
Ranar Yahudawa ta na farawa bayan da rana ta faɗi.Yesu ya na magana bayan da rana ta faɗi. zakara za ta yi cara kamin safe. safiyan sashi ne na "wannan rana." AT: "yau da dare" ko "da safe"
Yesu ya yi tambaya ya taimake annabawan tunawa yadda mutanen suka basusa;anda su ke tafiya. koda shike wanan tambayan ba ya bukatan amsaKuma Yesu baya bukatan bayyani,ka juya shi kamar tambaya sai dai idan bayyani ne kawai zai sa al'majeren su amsa da cewa sun rasa komai.
Yesu ya na magana da al'majeren sa. Yaren da ta ke da sifofin dabam daban na "kai" su yi amfani da siffar jam'i.
Alabe jaka ne na rike kuɗi. Anan ana amfani da ita a masa yin "kuɗi."
"jakan masu tafiya" ko "jakan abinci"
Zai zama da taimako ga masu sauraron a kara da yawa game da maganar. AT: "Ba mu rasa komai ba" ko "Muna da komai da muke bukata"
Yesu baya nufim takamaimain mutum wanda ba shi da takobi. AT: "Idan wani ba shi da takobi sai ya sayar da taguwarsa"
kwat" ko "tufa na waje"
AT: "abin da annabawa suka rubuta game da acikin littattafai"
Annbawan yaka mata su gane da cewa Allah zai sa komai da yake rubuce a littatafai zai faru. AT: "Allah zai cika" ko "Allah zai sa ya faru"
Anan Yesu yana faɗi littafi.AT: "Mutane sun kirga shi ɗaya daga cikin kungiyan mutane masu karya doka"
"wadanda suke karya doka" ko "mai lefi"
Ma'ana mai yuwa 1) "Gama abin da annabawa suka fada a kaina ya kusan faru" 2) "Gama rayuwana ya kusa ga karshe"
Wannan na nufin mai ƙanƙantaal'majeren Yesu biyu.
Ma'ana mai yuwa 1) suna da takobi isasshe. "yanzu muna da isasshe takobi." ko 2) Yesu ya so su daina magana game da samun takobi." yana gaya masu ne kawai game da hadarin da dukkansu za su fuskata. mai yuwa bawai yana so su siya takobi su yi fada ba.
"domin kada a gwada ku" ko "domin kada wani abu ya gwada ya saku zunubi"
"misalin nisar da wani zai iya jefa dutse." AT: "guntun nesa" ko kimantan gwadawa kamar "mita talatin"
Yesu zai dauki alhakin zunubin kowani mutum akan giciye. Ya yi addu'a ga Uban sa, tambaya ko akwai wanu hanya.
Wannan suna ne mai muhimmanci wa Aallah.
Yesu ya na nufin abin da zai ji kamar kwafin mai ɗaci ruwa ruwa da zai sha. AT: "kada ka bar ni in sha dga wannan kwafin" ko "kada ka bar ni in ji abin da ya yi kusan faru"
"Yesu ya bayyana"
"ya karfafa shi"
"yana shan babban wahala, sai ku,a ya yi addu'a"
"ya yi addu'a mai yawa da gaskiye"
"zufarsa tana diga a ƙasa kamar babban gudajen jini"
"Sa'anda Yesu ya ta shi daga addu'a, ya" ko "bayyaan addu'a,Yesy ya ta shi sai ya"
"ya gani da cewa su na barcidomin su gaji dadaga bakim cikinsu"
Ma'ana mai yuwa 1) "ina mamaki da cewa kuna barci yanzu" ko 2) " bai kama ta kuna barci yanzu ba!"
"domin kada a gwada ku" ko "domin kada wani abu ya gwada ku ya sa ku zunubi"
Wannan kalmae "duba" ya shiya mu ga sabuwar kungiya a labarin Yaren ku sana da hanyan yin haka. AT: "akwai taron da ta bayyana"
Yahuza ya na nuna wa mutanen inda Yesu ya ke.baya gaya wa taron abin da za su yi. AT: " jagaban su zuwa gun Yesu"
"ya gaisheshi da sumba" ko "ya gaishe shi ta wurin yi masa sumba." sa'anda maza su ka gaishe wasu mazan wanda suke iyali ko abokanai, za su yi masu sumba a ƙunci ɗaya ko ƙunci biyu. idan masu karatun ka za su ji kunya su ce na miji zai yi ma wani na miji sumba,sai ka juya shi mafi yawa a hanya na kowa: "ya yi masa gaisuwa na abokantaka."
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya kwaɓe Yahuza da ba da shi da sumba. akulayomi sumba alama ce na ƙauna. AT: "da sumba za ka ba da Ɗan Mutum!"
Yesu yana amfani ta wannan ajali ya yi nufin kansa. AT: "Ni Ɗan Mutum, da"
Wannan na nufin al'majeren Yesu.
Wannan na nufin firistoci da sojoji na zuwa su kama Yesu.
Tambayan game da wani irin fada za su yi
"ɗaya daga cikin al'majeren"
"ya kai wa bawan babban firist sara da takobin"
"Kada ku yi fiye da haka"
"ya taba bawan a inda aka yanka masa kunne"
"Kun fito takuba da sanduna domin kuna tunani cewa ni dan fashi ne?" Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya yi washugabanen Yahudawa. AT: "kunsa ni da cewa ni ba dan fashi bane, duk da haka kun zu wuri na da takuba da sanduna."
"i na tsakanin ku kowanni rana"
firistoci ne kawai suke shiga haikalin. AT: "a cikin haraban haikalin" ko a haikalin"
A wannan ayan, a sa hanu a kai wani na nufin a kama mutumin. AT: "kama ni"
"lokacin ka" ko "lokacin kane ka aikata"
Zai zama da taimako a sake shaidan lokaci. AT: "lokacin ikon duhu"
"tafi da Yesu daga lambun ida suka kama shi"
"cikin haraban gidan babban firist"
"wasu mutane suka yi wuta." wutan domin ya sa mutane suji dumi a lokacin sanyi da dare. AT: "wasu mutane sun kunna wuta domin su ji dumi"
Wannan haraban gidan firist ne. ya na da bango kiwaye da shi, amma babu jinka.
"tare da su"
Ya zauna kusa da wutan ga layin hasken a kak shi.
"sai ta zara wa Bitrus ido ta ce wa sauran mutanen a cikin haraban gidan"
Wannan matan tana gaya wa mutane game da Bitrus cewa ya na tare da Yesu. Mai yuwa ba ta san sunar Bitrus ba.
"Amma Bitrus ya ce ba gaskiya bane"
Bitrus bai san sunar matan ba. Ba zagin ta yake yi ba da ya ki ra ta "mace." Idan mutane za su yi tunanin cewa ya na zagin ta, sai ka yi aiki da hanya na karban mutum a al'adan yadda na miji zai kira matan da bai san sunar ta ba, ko ka bar kalmar.
"Kai ma kana ɗaya daga cikin wanda suna tare da Yseu"
Bitrus bai san sunar matumin ba. Ba zagin sayake yi ba da ya ki ra shi "mutumin." Idan mutane za su yi tunanin cewa ya na zagin shi, sai ka yi aiki da hanya na karban mutum a al'adan yadda na miji zai kira na miji da bai san sunar sa ba, ko ka bar kalmar.
"ya nace da cewa" ko "ya fada da ƙarfi"
Anan "wannan mutumin" na nufin Bitrus. mai maganar mai yuwa bai san sunar Bitrus ba.
Wannan mutumin mai yuwa ya fada cewa Bitrus daga Galili ne daga yadda yake magana.
Bitrus bai san sunar matumin ba. Ba zagin sayake yi ba da ya ki ra shi "mutumin." Idan mutane za su yi tunanin cewa ya na zagin shi, sai ka yi aiki da hanya na karban mutum a al'adan yadda na miji zai kira na miji da bai san sunar sa ba, ko ka bar kalmar. Dubi yadda zaka juya wannan a Luka 22:58,
"Ni ban san abin da kake magana akai ba." Wannan furcin yana nufin cewa Bitrus bai yarda gaba ɗaya da abin da wannan mutumin ya ke fada ba. AT: "abin da ka fada gaba ɗaya ba gaskiya bane" ko "abinda ka fada gaba ɗaya ƙaryane"
"da Bitrus yana cikin magana"
Zakara tana cara ne kamin rana ta fito da safe. Dubi yadda za ka juya sashin kusan ɗayaa Luka 22:34.
"Ubangiji ya juya ya dubi Bitrus"
"abin da Yesu ya fada" da Yesu ya fada cewa Bitrus zai bashe shi
Zakara tana cara ne kamin rana ta fito da safe. Dubi yadda za ka juya sashin kusan ɗayaa Luka 22:34.
Ranar Yahudawa ta na farawa bayan da rana ta faɗo sai ta cegaba zuwa yanma mai zuwa. Yesu ya yi maganar yanman da ta wuce game da abin da zai farukadan kamin asalatu ko da asalatu. AT: "yau da dare"
"musu sau uku cewa baka sanni ba"
"Bitrus ya tafi wajen gidan
"suka rufe masa idanu domin kada ya gani"
Ma su tsaron basu yarda cewa Yesu annabi bane. ko dai,sun yarda da cewa annabin gaskiya zai san wanda ya buga shi ka da idanun sa suna a rufe. Sun kira Yesu annabi,amma suna gwada shi suna nuna masa abin da ya sa ba su yi tunni cewa shi annabai bane. AT: "hakikanta cewa kai annabi ne. gaya ma na wa ya buge ka!" kai annabi wa ya buge ka"
"yi maganar kalma daga Alah!" Wannan bayyanin ya nuna cewa Allah ya kama ta ya nuna wa Yesu wanda ya buge shi tun da an kulle masa ido kuma baya gani.
"Da asalatu safe mai zuwa"
Ma;ana mai yuwa 1) "dattawan suka kai Yesu gun majalisa" 2) "masu tsaron suka kai Yesu gun majalisan dattawan." wasu yare za su ki fadan wanda ya kai shi da amfani da wakilin isimi "su" ko aiki da fi'ilin karban abin da mutane suka yi ba sakewa:" An kai Yesu gun majalisa"
Za'a iya fara sabuwar lbayyani anan. AT: "majalisan. dattawan sun ce wa Yesu"
"Gaya mana Idan kai Almasihu ne"
Yesu yana cewa aidan yayi magana ko ya ce su yi magana, ba za su amsa daidai ba, Wannan sashin tare ya nuna cewa Yesu bai yarada da cewa majalisan suna neman gaskiya ba.
Wannan shi ne farko na biyu bayyanin da Yesu ya yi na yana yin da ba'a gani ba. hanya ne wa Yesu ya amsa ba tare da ba su dalili su ce da cewa yana mai lefin maganar saɓo ne. Mai yuwa yaren ku suna da hanyan nuna cewa aikin nan bai faru ba.
Wannan shi ne bayyanin da Yesu ya yi na biyu na yana yin da ba'a gani ba. Hanya ne wa Yesy ya kwaɓe su ba tare da ba su dalili su fursuna shi ba. Mai yuwa yaren ku suna da hanyan nuna cewa aikin nan bai faru ba.
"daga wannan rana" ko "farawa daga yau"
Yesu ya yi amfani da wannan sashin ya yi nufin kansa. AT: "Ni, Ɗan Mutum zan"
"ka zauna a "hanun dana na Allah" sananniyar alama ce na aikin ƙarban babban daraja da iok daga Allah. AT: "zaune a wurin daraja kusa da ikon Allah"
"Allah mai dukakn ƙarfi." Anan "ƙarfi" na nufin maɗaukakin ikonsa.
Majalisan su yi wannan tambayan domin suna so Yesu ya bayyana masu ganewar suda cewa ya ce shi Ɗan Allah ne. AT: "Sa'anda ka fada haka, kana nufin kai Ɗan Allah ne?"
Wannan suna nu mai muhimmanci ga Yesu.
"I, kamar yadda ku ka fada"
Su yi amfani da tambaya domin nauyin. AT: "ba mu neman wani shaida!"
Wannan sashin "daga bakin sa" na nufin maganar sa. AT: "munji shi ya ce ya bada gaskiya cewa shi Dan Allah ne"
1Sai duk taron suka tashi, suka kawo Yesu gaban Bilatus. 2Suka fara saransa, cewa "Mun same wannan mutum yana ruda kasarmu, ya haramta a ba Kaisar haraji, yana kuma cewa shi da kansa ne Almasihu, sarki."3Bilatus ya tambaye shi, cewa "Shin kaine Sarkin Yahudawa?" Sai Yesu ya amsa masa ya ce, "Haka ka ce." 4Sai Bilatus ya ce wa manyan firistocin da taro mai yawa, "Ban samu ko laifi daya game da wannan mutumin ba." 5Amma suka yi ta cewa, "Yana ta da hankalin mutane da koyarwa a dukan Yahudiya, ya fara daga Galili har zuwa ga wannan wuri."6Sa'adda Bilatus ya ji wannan, sai ya tambaya ko mutumin daga Galiline. 7Sa'adda ya gane cewa yana karkashin mulkin Hirudus, sai ya tura Yesu wurin Hirudus, wanda shi da kansa yana Urushalima a wadannan kwanakin.8Sa'adda Hirudus ya ga Yesu, sai ya cika da farin ciki sosai, saboda ya so ganinsa tunda dadewa. Tun can ya ji game da shi sai ya yi begen ganin wadansu al'ajibai da zai yi. 9Hirudus ya tambaye Yesu cikin kalmomi masu yawa, amma Yesu bai amsa masa da komai ba. 10Sai manyan firistoci da marubuta suka tsaya, suna ta yi masa zargi mai zafi.11Hirudus da sojojinsa suka zarge shi, suka kuma yi masa ba'a, suka sa masa tufafi masu kyau, sa'annan ya sake aika Yesu zuwa wurin Bilatus. 12Sai Hirudus da Bilatus suka zama abokai a wannan rana (da ma su abokai gaba ne).13Bilatus ya kira manyan firistoci tare da masu mulki da kuma taron jama'ar, 14sai ya ce masu, "Kun kawo mani wannan mutum kamar wanda yake jagorar mutane ga munanan ayyuka, ku kuma gani, Ni, na tuhume shi a gabanku, ban sami ko kuskure daya daga mutumin nan game da abinda ku ke zarginsa da shi ba.15Babu, ko Hirudus ma, ya sake komar mana da shi, kun gani, babu wani abu wanda ya yi da ya cancanci mutuwa, 16saboda haka zan yi masa horo sa'annan in sake shi." 17118Amma dukansu suka yi ihu tare, cewa, "A tafi da wannan mutumin, sai a sako mana Barabbas!" 19Barabbas mutum ne wanda aka sa a cikin kurkuku saboda wani tada hankali a cikin birni da kuma kisankai.20Bilatus ya sake yi masu magana, yana so ya saki Yesu. 21Amma suka yi ihu, cewa, "A giciye shi, a giciye shi." 22Sai ya sake ce masu sau na uku, "Don me, wace magunta wannan mutum ya yi? Ban sami wani abu da ya isa sanadin mutuwa game da shi ba. Saboda haka bayan na hore shi, zan sake shi."23Amma suka nace da murya mai karfi, suna so a giciye shi, sai muryarsu ta rinjayi Bilatus. 24Sai Bilatus ya yarda ya yi masu bisa ga abin da suke so. 25Ya sako masu wanda suka tambaya ya ba su wanda aka sa a kurkuku domin tada hankali da kuma kisankai. Amma ya ba da Yesu bisa nufinsu.26Da suka tafi da shi, sai suka kama wani mai suna siman Bakurane, yana zuwa daga karkara, sai suka daura masa giciyen ya dauka, yana biye da Yesu.27Babban taron jama'a, da na mata da suke makoki da kuka dominsa, suna binsa. 28Amma da ya juya wurinsu, Yesu yace, "Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka domina, amma ku yi kuka domin kanku da 'ya'yanku.29Gama ku gani, kwanaki suna zuwa da za su ce, 'Albarka ta tabbata ga bakararru da wadanda basu taba haihuwa ba da kuma wadanda ba a taba shan mamansu ba.' 30Sa'annan za su fara ce wa duwatsu, 'Ku fado bisanmu,' da tuddai ma, 'Ku rufe mu.' 31Gama idan sun yi wadannan abubuwan lokacin da itace yana danye, me zai faru sa'adda ya bushe?"32Aka kai wadansu mutum biyu masu laifi, domin a kashe shi tare da su.33Sa'adda suka zo wurin da a ke kira kwalluwa, nan suka giciye shi da barayin, daya daga hannun damansa dayan kuma daga hannun hagu. 34Yesu yace, "Uba, ka yafe masu, gama basu san abin da suke yi ba." Sai suka jefa kuri'a, suka rarraba tufafinsa.35Mutane sun tsaya suna kallo sa'annan masu mulki suna ta yin masa ba'a, cewa, "Ya ceci wadansu. Bari ya ceci kansa, idan shine Almasihu na Allah, zababben nan."36Sojojin ma suka yi masa dariya, suna zuwa wurinsa, suna mika masa ruwan tsami, 37suna cewa, "Idan kai Sarkin Yahudawa ne, ceci kanka." 38Akwai wata alama bisansa, "Wannan shine Sarkin Yahudawa."39Daya daga cikin barayi wanda aka giciye, ya zage shi, cewa, "Ba kai ne Almasihu ba? Ka ceci kanka da mu." 40Amma dayan ya amsa, ya tsauta masa cewa, "Ba ka tsoron Allah, da yake shari'arka daya ne da nasa? 41Mu kam an yi ma na daidai, gama mun samu bisa ga abin da muka yi. Amma wannan mutum bai yi wani abu mara kyau ba."42Sai ya kara, "Yesu, ka tuna da ni sa'adda ka shiga mulkinka." 43Yesu ya ce masa, "Gaskiya ina ce maka, yau za ka kasance tare da ni a firdausi."44Anan nan a wajen sa'a na shida, sai duhu ya mamaye kasar duka har zuwa sa'a na tara 45sa'adda rana ya fadi. Sai labulen haikalin ya rabu a tsakiya zuwa kasa.46Da kuka da murya mai karfi, Yesu yace, "Uba, na mika Ruhu na a hannunka." Bayan da ya fadi wannan, sai ya mutu. 47Sa'adda jarumin ya ga abin da ya faru, ya daukaka Allah, cewa, "Lallai wannan mutumin mai adalci ne."48Sa'adda dukan taro mai yawa wadanda suka zo tare domin su shaida da idanunsu suka ga abubuwan da suka faru, suka koma suna bugan kirjinsu. 49Amma duk idon sani, da kuma matan da suka bi shi tun daga Galili, suka tsaya daga nesa, suna duban wadannan abubuwa.50Ga shi kuwa, wani mutum mai suna Yusufu, shi dan majalisa ne, nagari ne kuma mutum mai adalci ne 51(bai yarda da shawarar da kuma abin da suka aikata ba), daga Arimatiya a kasar Yahudiya, wanda yake jiran mulkin Allah.52Wannan mutum, ya sami Bilatus, ya tambaya a bashi jikin Yesu. 53Ya saukar da shi kasa, sai ya nade shi cikin likafani na linin mai kyau, ya kwantar da shi cikin kabari da aka sassaka shi daga dutse, inda ba a taba binne wani ba.54Ranar kuwa, ranar shiri ce, Asabaci kuma ta kusato. 55Matan da suka taho da shi tun daga Galili, suka biyo baya, su ga kabarin da inda aka ajiye shi. 56Suka koma, sai suka shirya kayan kamshi da mai. Suka kuma huta a ranar Asabaci bisa ga doka.
An kawo Yesu gaban Bilatus.
"Dukkan shugabanen Yahudawan" ko " Dukkan kungiyan majalisan"
"sun mike" ko "sun mike a ƙfafun su"
ka bayyana a gabam wani na nufin ka shiga ikon sa. AT: "domin Bilatus ya yi ma sa shari'a"
"Mu" na nufin mutanen majalisan, ba wa Bilatus na wasu mutanen da su ke kusa ba.
"ya sa mutanen mu su yi abubuwan da ba daidai ba" ko "sa jaraba da gaya wa mutanen mu su yi ƙarya"
"ya gaya masu kada su biya haraji"
Kaisar na wakilin daula na Romawa. AT: "zuwa ga daula"
"Bilatus ya tambaye Yesu"
Ma'ana mai yuwa 1) da fadan wannan, Yesu ya nuna cewa shi sarkin Yahudawa ne. AT: "I, kamar yadda ka fada nine" ko "I, kamar yadda ka fada ne" ko 2) da fadan wannan, Yesu yana cewa Bilatus, ba Yesu ba, shi ne wanda yake kiran Yesu sarkin Yahudawa. AT: "Kai da kanka ka fada haka"
kungiyan mutane da yawa
"ban sa mi wannan mutumin da halakin komai ba"
"sa damuwa a sakani "
Wannan za'a iya juya ta kamar bayyani. AT: "dukan Yahudiya. yafara sa damuwa a galili yanzu kuma ya na sa damuwa a nan"
"ya ji cewa Yesu ya fara koyasuwa a Galili"
Bilatus yana so ya sani daga wani filiYesu ya zo domin yana so ya sami karaminmai'kacin hukumar gwamnati su yi wa Yesu shari'a. Idan Yesu dan Galili ne, Bilatus zai sa Hiridus ya yi wa Yesu shari'a domin Hiridus yana da iko a Galili.
Wannan na nufin Yesu.
"Bilatus ya gane"
Labarin bai nuna tabbatacciyan cewa Hiridus shi ne yake mulkin Galili. AT: "Yesu yana ƙarƙashin ikon Hiridus domin Hiridus shi ne yake mulkin bisa Galili"
"Bilatus ya aiki"
Wannan na nufin Hiridus.
"a waccan lokaci"
"Hiridus ya cika da farin ciki sosai"
"Hiridus ya so ganin Yesu"
"Hiridus ya ji game da Yesu"
"Hiridus yi begen"
AT: "ya gan shi ya na yin wasu irin al'ajibi"
"Hirudus ya tambaye Yesu da yawa"
"bai amsa ba" ko "bai ba wa Hiridus amsa ba"
"marubutan suna tsaye anan"
sau da yawa su ka zargi Yesu" ko "suka yi masa zargin kowane irin laiifufuka"
"Hirudus da sojojinsa"
"sa masa tufafi masu kyau." mai juyawan kada ya nuna cewa anyi wannan domin a daraja Yesu ko an damu da shi. Sun yi haka su ma Ysu ba'a su kuma yi wasa da shi.
Wannan labarin ya nuna da cewa sun zama abokai domin Hiridus ya ji daɗin Bilatus domin ya bar shi ya yi wa Yesy shari'a. AT: "Hirudus da Bilatus suka zama abokai a wannan rana domin Bilatus ya aiki Yesu zuwa Hiridus domin ya yi masa shari'a"
Wannan labarin dama a kulle yake an karane domin ya nuna cewa labarin ƙasa ne. ka yi aiki da wata irin shiri da masu sauraron ka za su gane.
"kira manyan firistoci tare da masu mulki da kuma taron jama'ar su hadu tare"
Bai zama mai yuwiwa da Bilatus ya cewa taron su zo. Mai yuwa taron har yanzu suna jera su gan abin da za'a yi wa Yesu. AT: "taron haryanzu suna nan"
Wannan na nufin Yesu.
"cewa shi"
"Na yi wa Yesu tambya a gaban ka, kuma." Ya nuna da cewa sun yi shaidanci gaban. AT: "Na yi wa Yesu tambya da ku a masa yin shaiduna, da"
"ban yi tunani cewa yana da laifi ba"
Bilatus ya cigaba da yin magana wa shugabanen Yahudawa da taron.
Zai zama da taimako ka ƙara labarin da ba'a ƙara ba a guntun bayyanin. AT: "ko Hiridus ma bai yi tunanin cewa shi mai liafi bane" ko Ko Hiridus Ya yi tunanin cewa shi mara laifi ne"
"haka ma Hiridus, domin" ko "haka ma Hiridus .Mu san wannan domin"
"Hiridus ya sake komar mana da Yesu," wannan kalmar "mu" yana nufin Bilatus da sojojinsa, da firistoci da marubutan, amma ba wadanda suke jin Bilatus ba.
AT: "bai yi wani abu wanda ya canceci mutuwa ba"
Domin Bilatus bai sami Yesu da wani laifi ba ya ka mata ya sake shi ba tare da horo ba. Ba dole bane ka sa wannan bayyanin ya shiga makama a juyin ba. Bilatus ya horas da Yesu wanda ya san cewa shi ba mai laifi bane, kawai domin ya na tsoron taron.
"Dukkan mutanen taron suka yi ihu"
"A tafi da wannan mutumin! sake." Suna tambayan sa cewa sojojin sa su kashe Yesu. AT: "tafi da wannan mutumin fille kan shi! sake"
"mu" yana nufin taron kawai, ba kuwa ga Bilatus da sojojinsa ba.
Wannan bayyani ne daga ƙasa wanda Luka ya bayar akan wanene Barabbas.
AT: "Wanda Romawa suka sa a cikin kurkuku"
"yana ƙoƙarin ya rinjaye mutanen birnin su yi tawaye wa gwomnatin Romawa"
"yi masu magana kuma" ko "yiwa mutanen magana kuma a cikin taron da ma su mulkin addini"
"domin ya na so ya saki Yesu"
"Bilatus ya ce wa tarom kuma , na uku"
Bilatus ya yi amfani da tambaya domin ya sa taron su gane da cewa Yesu bai yi laifin komai ba. AT: "wannan mutumin bai yi wani abun da ba daidai ba!"
"Bai yi wani abu da ya cancenci mutuwa ba"
Kamar a Luka 23:16, Bilatus ya ka ma ta ya saki Yesu ba tara da horas da shi ba. Duk da haka ya bd Yesu a yi masa horo saboda ya rarrashe taron.
"Ni zan sake shi ya tafi"
"taron suka nace"
"da ihu"
AT: "gama Bilatus ya sa sojojin sa su giciye Yesu"
"Taron suka cigaba da ihu har sai da suka rinjayi Bilatus"
"ya yi abin da taron suka tambaya"
Bilatus ya saki Barabbas daga kurkuku. AT: "Bilatus ka saki Barabbas, wanda taron suka tambaya a sake"
"Bilatus ya umurci sojojin su kawo Yesu ma taron su yi duk abin da suke so"
"Da sojojin suka tafi da Yesu da ga gun da Bilatus ya ke"
Sojojin Romawan su na da iko tilasta mutane su dauki kayan su. Kada ka juya wannan a hanyan da zai nina da cewa an kama siman ko ya yi wani abun da ba daidai ba.
" mutum mai suna siman Bakurane, daga birnin karkara"
"wanda yake zuwa cikin Urushalima daga gefen ƙasar"
"sa masa giciyen a kafadar sa"
"sai yana bi a bayan Yesu"
"Taro da yawa"
Matan suna cikin babban taron, ba'a ware su daban ba.
"suna makoki wa Yesu"
Wannan bai nuna da cewa su al'majeren Yesu bane. Saidai yana nuna cewa suna bin sa a baya ne.
Wannan ya nuna da cewa Yesu ya juya ya kalli matan sai ya yi masu magana kai tsaye.
"Yan matan" birnin na nufin matan birnin. Wannan ba mai ladabi bane. hanya ne daidai na nagama da kungiyan matan daga wuri ɗaya. AT: "Ku mata wanda kuke daga Urushalima"
Mutumin misali ne na abin da ya faru da mutum. AT: "kada ku yi kuka da abubuwan da basu da kyau da ya faru dani. amaimako, ku yi kuka domin abubuwa mafi muni da zai faru da ku da 'ya'yanku" ko " kuna kuka domin abubuwan da ba kyau suna faruwa dani, amma za ku yi kuka sosai sa'anda abubuwan mafi muni za su faru da ku da 'ya'yanku"
Wannan ya nuna dalilin da ya sa matan Urushalima za su yi kuka wa kansu.
"kwanaki suna zuwa"
"da mutane za su ce"
"matan da ba su taba haihu ba"
Wannan kashi an yi amfani da su domin a yi kwantanci sosai akan "bakararru." waccan matan da ba su haihu ba kuma ba su shayar da 'ya'ya ba. zai zama da taimako ka hada wannan da "bakararru." AT: "matan da ba su taba haifan yara ba ko ba su taba shayar da 'ya'ya ba
a waccan lokacin
anbar kalmomin domin a sa sashin ya yi guntu. AT: "za su cewa tudun"
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya sa taron su gane cewa mutane suna yin abubuwa da ba kyau yanzu a lokatai masu kyau, to ba shakka za su yi abubuwa mafi muni a lokacin da ba kyau nana gaba .AT: "akuna gane cewa suna yin wadannana abubuwan da ba kyau tun itacen ya na danye, sai ku tabbata cewa za su yi abubuwa mafi muni sa'anda itacen ya bushe."
Ɗanye itace misali ne na abubuwa masu kyau. Idan yaren ku na da misali kama da wannan za su iya amfani da shi a nan.
Itacen da ya bushe misali ne na abin da ke da amfani kawai a kona.
Wannan mai yuwa ya na nufin Romawa ko shugaba nen Yahudawa ko ba ko dayan su.
AT: "Sojojin suna tafiye da Yesu da masu laifi biyu wanda za a kashe su suma"
Mutane biyu masu laifi" ko "Masu laifi biyu." Luka ya kauce wa " sauran masu laifn domin Yesu bai da laifi, koda shike an yi masa kamar mai laifi. Luka ya kira suaran mutanene masu laifi, amma ba Yesu ba.
Wannan kalmar " su" na hade da sojojin, masu laifin da Yesu.
"sojojin Romawa suka giciye shi"
"sun giciye masu laifin a gefen hanun damar Yesu dayan kuma a gefen hanun damar Yesu"
Wannan kalmar "su" na nufin wadanda suke giciye Yesu. Yesu ya magana da Ubansa da tausayi game da mutanen da suke giciye shi.
Wannan babban suna ne wa allah.
"domin ba su gane abin da suke yi ba." Sojojin Romawa ba su gane cewa suna giciya Dan Allan bane. AT: "Idan ba su san asalin wanda suke giciye ba"
Sojojin suka halarci a wani irin cãca. AT: "su yi cãca"
"jefa sosai su yanke shawara wani soja ne a sakanin su zai tafi da gutsure tufafin Yesu"
"Mutanen suna tsaye agun"
Wannan na nufin Yesu.
Luka ya rikodin kalmomin habaici na shugabanen. Hanyan da kawai Yesu zai ceci wadansu shi ne ta mutuwa amaimakon ya cece kansa.
"Yesu zai iya ceci kansa." sun fadi haka domin su yi wa Yesu ba'a. ba su yarda cewa zai iya ceci kansa, AT: "za mu so mu ga shi ya tabbatar man wanene shi da cetan kansa daga giciye"
"wanda Allah ya zaba"
"zuwa gun Yesu"
"suna ba wa Yesu ruwan tsami ya sha" ruwan tsami abin sha ne mai arhr da mutane suke sha. Sojojin suna yi wa Yesu ba'a da ba shi abin shamai arha ya sha wani da ya ke cewa sshi sarki ne.
Sojojin suna yiwa Yesu ba'a. AT: "bamu yarda dacewa kai sarkin Yahudawa bane, amma idan kai sarki ne sai ka hakikanta mana da cecen kanka"
"takardar sanarwa wanda ake liƙaga allo a samam giciyen Yesu da yake cewa"
Mutanen da suka sa alamar a samam Yesy suna yi masa ba'a. ba su yi tunanin cewa asali she sarki bane.
"zage shi Yesu"
Mai laifin ya yi amfani da tambaya ya yi wa yesu ba'a, AT: "ka ce wai kai Almasihu ne. ceci kanka" ko "Idan asali kai Almasihu ne, zaka ceci kanka"
Mai laifin bai ti tunani da cewa Yesu zai cece su daga giciyen.
"dayan mai laifin ya tsauta masa"
Mai laifin ya yi amfani da tambaya ya yiwa dayan mai laifin tsawa. AT: "ka ji tsoron Allah, domin suna yi ma ka hukunci daidai da yadda suke yi masa" ko "baka da tsoron Allah, tunda ka na yi masa ba'a bayan an yataye ka kan giciye daidai da yadda aka yi masa"
Wannan nan amfani da " mu" na nufin ,asu laifin biyu, ba wa Yesu da sauran mutanen ba.
"Da gaskiye mun cancanci wannan hukunci"
"Mai laifin ya kuma ce"
"ka yi tunani na ka yi mini da kyau"
"shiga ciki" mulkin na nufin a fara mulki. AT: "fara mulki kamar sarki"
"Gaskiya" kara nauyin ga abin da Yesu yana faɗa. AT: "Ina so ka sani da cewa yau"
Wannan wuri ne da masu adalci suke zuwa sa'anda sun mutu. Yesu ya tabbatar da mutumin cewa zai zauna da Allah kuma Allah zai karbe shi. AT: "wurin da masu adalci suke zama" ko "wurin da mutane suke zama da kyau"
"wajen tsakar rana." Wannan ya nuna a'ladun a lokacin kirga sa'a farawa da safiya 6 a. m.
"duka ƙasar ya yi duhu"
"har zuwa 3 p. m." Wannan ya nuna a'ladun a lokacin kirga sa'a farawa da safiya 6 a. m.
Wannan ba ya nufin fadiwar rana. amma, hasken rana ta yi duhu a tsakiyar rana. yi amfani ta ajili ka kwatanta rana ya yi duhu amaimakon rana ta fadi.
"labulencikin haikalin." Wannan she ne labulen da ta raba wuri mafi tsarki da sauran wurin a cikin haikalin.
"labulen haikalin ya yage zuwa kashi biyu." AT: "Allah ya yaga labulen haikalin zuwa kashi biyu daga sama zuwa ƙasa"
"Ihu da ƙarfi." Zai zama da taimako ka nuna yadda wannan yana da dangantaka da abi da ya auko a ayoyin da ya wuce. AT: "Sa'anda waccan ya faru Yesu ya yi ahu da ƙarfi"
"Sahin" a hannunka" Nanu fin a kulan Allah. AT: "Na ba da ruhu ne ga kullan ka" ko "Na baka ruhu na, da sanin cewa zaka kula da shi"
"Bayan da Yesu ya fadi wannan"
"Yesu ya mutu"
Wannan suna ne wa hafsan Romawa wanda yake lura da sauran sojojin Romawa. yana duban gicciye.
AT: "duk abin da ya faru"
"wannan mutumin bai ye abin da ba daidai ba" ko "wannan mutum bai yi wani abun da ba daidai ba"
"wanda suka taru tare"
"gani wannan abin da ya auko" ko "dubi abin da ke faruwa"
AT: "abin da ya faru"
"suka koma gida suna bugan"
Wannan sananniyar shaida ne na nuna bakin ciki da nadama. AT: "buga karjinsu su nuna cewa su na da bakin ciki"
"yi tafiya da Yesu"
"daga nesa da Yesu"
"abin da ya faru"
Wannan kalmar "ga shi kuwa" yana gaya mana wani mutum a labarin. yarenku mai yuwa suna da hanyar yin haka. AT: "akwai wani mutum wanda"
"majalisan Yahudawan"
Menene shawaran za'a iya faɗa ba shakka. AT: "ko da shawaran majalisan a kashe Yesu ko da aikin su a kashe shi"
A nan "ƙasar Yahudiya" yana nufin cewa ana gano wurin a Yahudiya. AT: "garin da yake Arimatiya, wanda yake Yahudiya"
"Wannan mutumin ya je gun Bilatus ya neme jikin Yesu domin ya bizine shi."
"Yusufu ya dauki jikin Yesu akan giciye"
"ya nade jikin Yesu a likafani na linin." Wannan shi ne jana'iza na a'ladaun waccan lokacin.
AT: "wanda wasu suka sassaka a cikin dutse a bakin tuku mai gangare ƙwarai"
wannan za'a iya fadan ta a sabuwar bayyani. AT: "ba wanda ya taba sa jiki a wannan ƙabarin"
"ranar da mutane suke shiri domin hutun Yahudawa kira Asabaci"
Gama ga Yahudawan, ranar ta na fara wa ne bayan rana ta fadi. AT: "rana ta kusato ta fadi, farawan Asabacin"
"wanda suka yi tafiya da Yesu daga jihae Galili"
AT: "yi tafiya da Yusufu da mutanen da suke tare da shi; matan ta ga kabarin da inda a ka binne jikin Yesu a cikin kabarin"
"Matan ta ji gidajen da matan suke zama"
Domin ba su da lokaci da za su daraja Yesu da sa mishi kayan kamshi da mai a jikin saranar da ya mutu, suna so su yi shi da safe na farkon makon. AT: "suka shirya kayan kamshi da mai su sa a jikin Yesu"
"matan ba su yi aiki ba"
"bisa ga dokan Yahudawa" ko "yadda dokan Yahudawan ya bukata." ba'a barsu su shirya jikin ba a ranar Asabaci bisa ga dokan.
1Da sassafe a ranar farko ta mako, suka zo kabarin, suka kawo kayan kamshi wadda suka shirya. 2Sai suka samu dutsen a mirgine shi daga kabarin. 3Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji Yesu ba.4Ya faru kuwa, yayin da suke a rikice game da wannan, ba zato, mutane guda biyu suka tsaya a gabansu da tufafi masu walkiya. 5Sa'adda matan suka sunkuyar da kansu kasa domin tsoro, suka ce wa matan, "Don me kuke neman mai rai ciki matattatu?6Baya nan, amma ya tashi! Ku tuna fa yadda ya yi maku magana tun sa'adda ya ke Galili, 7cewa za a ba da Dan Mutum ga mutane masu zunubi su kuma giciye shi, a rana ta uku, zai tashi kuma"8Sai matan suka tuna da kalmominsa, 9suka koma daga kabarin sai suka gaya wa sha dayan wadannan abubuwan da dukan sauran. 10Su Maryamu Magadaliya, Yuwana, Maryamu uwar Yakubu, da sauran matan da ke tare da su suka ba manzanni rohoton wadannan abubuwan.11Amma manzannin suka dauki maganar kamar ba ta da amfani, kuma ba su bada gaskiya ga matan ba. 12Duk da haka Bitrus ya tashi, sai ya gudu zuwa kabarin, ya sunkuya yana kallon ciki, sai ya gan likaftani linin kadai. Sa'annan Bitrus ya tafi gidansa, yana ta mamakin abinda ya faru.13A ranan nan, sai ga biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani kauye suna Imawus, wanda nisansa kimanin mil ne daga Urushalima. 14Suna tattaunawa da junansu game da dukan abubuwan da suka faru.15Sai ya zama da cewa, sa'adda su ke tattaunawa tare da tambayoyi, sai Yesu da kansa ya matsa kusa yana tafiya tare da su. 16Amma idanunsu basu iya ganewa da shi ba.17Yesu ya ce masu, "Menene ku ke magana akai sa'adda ku ke tafiya?" Suka tsaya a wurin suna bakin ciki. 18Daya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya amsa masa, "Kai ne kadai mutumin da ke Urushalima wanda bai san abubuwan da suka faru a can a wannan kwanakin ba?"19Yesu ya ce masu, "Wadanne abubuwa?" Suka amsa masa, "Abubuwa game da Yesu ba Nazarat, wanda ya ke annabi ne, mai manyan ayuka da kalmomi daga Allah da kuma mutane. 20Da yadda manyan firistoci da masu mulkinmu suka bada shi domin a hukunta shi ga mutuwa a kuma giciye shi.21Amma mun yi begen cewa shine wanda za ya yantar da Isra'ila. I, bayan wannan kuma, yanzu kwana uku kenan tunda wadannan abubuwan suka faru.22Amma har'ila yau, wadansu mata da ke tare da mu sun yi mana abin al'ajabi, da suka kasance a kabarin tunda sassafe. 23Sa'adda ba su sami jikinsa ba, suka zo, da cewa su ma sun ga wahayin mala'iku wadanda suka ce masu ya na da rai. 24Wasu maza wadanda ke tare da mu suka tafi kabarin, suka tarar da shi kamar yadda matan suka fada. Amma ba su ganshi ba."25Yesu ya ce masu, "Ku mutane masu wauta da marasa ba da gaskiya ga abin da annabawa suka fada! 26Bai zama dole ne Almasihu ya sha wahalan wadannan abubuwan ba, ya kuma shiga cikin daukakarsa?" 27Sa'annan da farko daga Musa da har zuwa dukan annabawa, Yesu ya fasara masu duka abubuwa da ke game da kansa a dukan littattafai.28Da suka yi kusa da kauyen, inda suke tafiya, ko da yake Yesu ya yi kamar zai wuce su. 29Amma suka tilasta shi, cewa, "Ka zauna da mu, gama yamma ta yi kusa rana kuma ta kusa karewa." Sai Yesu ya tafi ya zauna da su.30Ya faru cewa, sa'adda ya zauna tare da su domin ya ci abinci, sai ya dauki gurasan, ya albarkace shi, ya kakkarya, sai ya ba su. 31Sa'annan idanunsu suka bude, da suka gane shi, sai ya bace daga garesu, 32Suka ce wa junansu, ashe zuciyarmu ba ta yi kuna a cikinmu ba, sa'adda yake magana da mu a hanya, sa'adda ya bude mana littattafai?"33Suka tashi a wancan sa'a, sai suka koma Urushalima. Suka sami sha dayan nan tare, da wadanda suke tare da su, 34cewa, "Lalle ne Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman." 35Sai suka fadi abubuwan da suka faru a hanya, da yadda aka bayyana masu Yesu sa'adda ya kakkarya gurasa.36Sa'adda suke fadin wadannan abubuwan, sai Yesu ya tsaya a sakaninsu, sai ya ce masu, "Salama a gareku." 37Amma suka firgita suna cike da tsoro, suna tsammani sun ga fatalwa.38Yesu ya ce masu, don me ku ke damuwa? Don me tambayoyi ke tasowa a zuciyarku? 39Duba hannayena da kafafuna, cewa nine da kaina. Taba ni ku gani. Gama ruhu ba shi da jiki da kashi, kamar yadda ku ka ga nake da su." 40Bayan da ya fadi wannan, sai ya nuna masu hannayensa da kafafunsa.41Sa'adda suke cike da farin ciki, da mamaki, Yesu ya ce masu, "Kuna da wani abinci?" 42Sai suka bashi gasasshen kifi. 43Yesu ya karba, ya ci a gabansu.44Sai ya ce masu, "Sa'adda nake tare da ku na gaya maku cewa duka abin da aka rubuta a cikin dokokin Musa da na annabawa da Zabura dole su cika."45Sai ya bude hankalinsu, saboda su gane littattafai. 46Ya ce masu, "A rubuce yake, cewa Almasihu za ya sha wuya, zai tashi kuma daga matattu a rana ta uku. 47Ku yi wa'azin tuba da gafarar zunubai a cikin sunansa ga dukan al'ummai, ku fara daga Urushalima.48Ku shaidu ne ga wadannan abubuwan. 49Duba, ina aiko da alkawarin Ubana a kanku. Amma ku jira a birni, sai an suturta ku da iko daga sama."50Sa'annan Yesu ya tafi tare da su har sai da suka kai kusa da Betanya. Sai ya daga hannunsa ya albarkace su. 51Ya zama sa'adda yake sa masu albarka, ya bar su sai aka dauke shi zuwa cikin sama.52Sai suka yi masa sujada, suka komo Urushalima da murna mai yawa. 53Kullayaumin suna cikin haikali, suna albarkatar Allah.
Matan ta koma kabarin da yajt da makamancinsa ta sa a jikin Yesu.
"kamin asalatu ranar Lahadi"
"matayen suka iso kabarin"
Wannan kabarin an yanke daga duwatsu a bakin teku mai gangare kwarai.
Wannan kayan kamshi iri ɗaya ne da suka shirya a Luka23:56.
"Su ka gani cewa dutsen"
AT: "da cewa wani ya mirgine dutsen"
Wannan babban yanka kewayyaye babba ya isa ya yi tare ƙofar shiga kabarin.yana neman mutane dayawa su mirgine shi.
za ka iya bayyana da cewa ba su sami shi ba domin ba ya wurin. AT: " jikin Ubangiji Yesu ba ya wurin"
Wannan sashin an yi amfani da shi a nan domin a sa alama akan wani abu mai muhimmancida ya auko a labarin. Idan yaren ku na da wani hanya na yin haka za su iya amfani da ita anan.
"sun fara tsoro"
"sunkuyar zuwa ƙasa." Yin wannan ya nuna kaskancin su da biyyaya zu wa ga mutanen.
Wadannan mutanen sun yi amfani da tanbaya mara tsanani su soka matan domin neman rayayye mutum a kabari. AT: "kuke neman mai rai ciki matattatu!" ko "kada ku dinga nemen mutumin da yake da rai a wurin da ake binne matattatun mutane!"
A nan "kai" jam'i ne. ana nufin matan da su ka zo.
Mala'ikun sun gama magana da matan.
"amma ya za ma rayayye kuma." " tashi" anan kari nena "sa ya yi rayuwa kuma." AT: "domin Allah ya ta da shi kuma"
"ku tuna da abin"
Wannan kalmar "ku" jam'i ne. ya na nufin matan mai yuwa kuma da al'majeren.
Wannan shi ne farkon faɗi ba na kusa-kusa ba. za'a iya juya da faɗi na nuna kamar yadda yake a UDB.
Wannan sashin "za'a" na nufin cewa ba shakka wani abu zai faru domin Allah ya riga ya yanke cewa zai faru. AT: "ya zama dole cewa za a ba da Dan Mutum ga mutane masu zunubi wanda kuwa za su giciye shi"
A nan "hannaye" na nufin ƙarfi ko iko.
Yahudawa na kirga kowanne rabin rana kamar rana. saba da haka, ranan da Yesu ya tashi "rana ta uku" domin ya biyo ranar da aka bizine shi da rana ta Asabaci.
A nan "kalmar" na nufin bayaynin da Yesu ya yi. AT: "tuna da abin da Yesu ya fada"
"annabawan goma sha ɗayan da dukan sauran al'majeren da suke tare da su"
Wannan shi ne farkon shida zuwa ga goma sah ɗayan, domin Yahuda ya bar goma sah ɗayan ya ba she Yesu.
Wannan kalmar an yi amfani da shi anan a sa alaman fashe a aslin labarin. Anan Luka ya ba da sunayen wa su mata wanda suka zo daga kabarin san gaya wa annabawan abin da ya faru a gun
"Amma annabawan sun yi tananin cewa abin da matan suka gaya ma su maganar banza ne"
Wannan sashin ya hada Bitrus da sauran annabawan. bai tuɓe abin da matan suka fada ba, amma ya ruga a guje zu wa kabarin ya ga wa kansa.
Wannan kari na da ke nufin "ya fa ra aikatawa." ko da Bitrus yana tsaye ko ya na zaune da ya yanke shawara ya fara aikatawa bai da amfani. AT: "fara awaje"
Bitrus ya sunkuya domin ya ga cikin kabarin domin kabarin da aka yanka a cikin dutse gajere na. AT: "ya sunkuya zu wa gunɗuɗu"
"likaftani linin kadai." wannan na nufin kaya da aka ƙunshe kewaye a jikin Yesu da aka bine shi a ciki [Luka 23:53]
"ya tafi abin sa zu wa gida"
Mai wallafawan ya yi amfani da kalmar domin ya sa alama aka sabuwar abin da ya auko.
"al'majeren biyu"
"a rana ɗayn can." Wannan na nufin ranar da matan suka sami kabarin ba komai.
Wannan sunan gari ne.
"kilomita goma sha ɗaya." babban fili da aka keɓe don wasnni" mita 185 ne
Wannan sashin an yi amfani da shi anan a sa alama a inda aikin ya fara. Ya fara da Yesu ya na zu wa gun su. Idan yaren ku na da wata hanya na yin haka za su iya amfani da ita anan.
Wannan kalmar "da kanda" ya nuna nauyin cewa Yesun da suke magana akai ke nan ya bayayna ga su. tun da ma matan su gan mala'iku, amma ba wanda ya gan Yesu.
"an ajiye idanuwan su domin kada su gane Yesu."iyawar mutane su gane Yesu an yi magana kamar iyawan idanuwa su gane shi.AT: "zai iya zama da cewa Allah ne yahana su daga gane Yesu. AT: "wani abu ya faru da su domn ka da su gane shi" ko "Allah ya hana su da ga gane shi"
"Yesu ya cewa mutane biyun"
Wannan sunan mutum ne.
Kiliyobas ya yi amfani da tambaya ya nuna mamakin sa da cewa wannan mutumin nuna cewa bai san abubuwan da ya ke faruwa a Urushalima ba. AT: "Kai ne kadai mutumin ... kwanakin"
A nan "kai" mafuradi ne.
"Wadanne abubuwa suka faru?" ko "Wadanne abubuwa suka faru a nan wurin?"
Wannan na nufin cewa Allah ya sa Yesu ya zama mai ƙarfi da iko kuma mutane sun ga shi da ikon. AT: "annabi wanda Allah ya ba shi iko ya yi kuma ya koyar da mayan abubuwa da suke da ban mamaki ga mutane"
"ba da shi ga"
AT: "domin gomna ya kashe Yesu ta wurin giciye shi"
Romawa sun yi mulki akan Yahudawa. AT: "wa zai ceci Isra'ilawa da ga magabtan mu Romawa"
Wannan ya gabatar da wani dalili da sun yarda cewa Yesu ba zai ceci Isra'ila ba. AT: "Yanzun da ba zai yuba domin"
Yahudawa su na kirgan kowane rabin rana kamar rana. sabo da haka, ranar da Yesu ya tashi "rana ta uku" domin ya biyo ranar da aka bine shi da ranar Asabanci. Dubi yadda za ka juya Wannan a [Luka24:7]
"tunda ayuka da ya wa sun sa mutuwa Yesu ya bayayna"
Wannan ya gabatar da wani dalilin da ya sa mutanen ba su gane abin da ke faruwa game da Yesu.
"a cikin kugiyan mu"
Matayen su ne wadda suke a kabarin.
"mala'iku a wahayin"
"ba su gan Yesu ba"
A nan "zuciya" misali ne na hankalin mutum. AT: "hankali ku mara sauri ya ƙarba" ko "ku mara sa ƙarba da sauri"
Yesu ya yi amfani da tambaya ya tuna she al'majeran aka abin da annabi ya fada. AT: "Bai zama dole ... daukakarsa."
Wannan na nufin Yesu ya fara mulki ya karba daraja da daukaka.
Musa ya rubata kakarda na farko a litafi mai tsarki. AT: "farawa daga rubutun Musa"
"Yesu ya bayyana masu"
Mutanen biyu sun gane daga aikatawar sa cewa ya na tafiya zuwa ga ɗayan wurin ne. watakila ya cigaba da tafiya akan hanya da suka juye su shiga ƙofar garin.ba alama cewa Yesu ya ruɗe su da kalmomi.
za ka iya yin bayyani akan abin da ya sa suka tilasta ma sa ya yi. Mai yuwa wannan furcin ya nuna ya da suke so su yi magana da shi na dan lokaci kamin su canja hankalin sa. Wannan kalmar "tilas" na nufin a yi aiki da ƙarfi na jiki, amma ya yi kaman sun tabbatar shi da kalmomi. AT: "sun tabbatar da shi sun ce"
Ranan Yahudawa ta na karawa idan yana ta fadi.
"Yesu ya shi ga cikin gidan"
"zauna da al'majeren biyu"
Wannan na nufin gyrasa mara yisti. ba ya nufin abinci gaba ɗaya.
"ya yi godiya ga shi" ko "ya godewa Allah ga shi"
"idanuwan su" na nufin ganewar su. AT: "Sa'annan suka gane" ko "sa'anan sun ankara"
"sun gane shi." Wadannan al'majeran sun san shi kamin ya mutu.
Wannan na nufin atake baya nan a gun. bawai ya na nufin ba'a ganin shi ba.
Sun yi amfani da tanbaya su nuna nauyin su akan wannan haduwa da Yesu. ciwo mai zafin da suke ji da gaskiye sa'anda suke magana da Yesu an yi maganar sa kamar akwai wutan da ya ke konewa a cikin su. AT: "zuciyan mu yana konewa... littattafai."
Mutane biyun su na magana da kan su. Wannan kalmar "mu" shi ne na mutum biyu ga yaren da suka sa wannan bambanci.
Yesu bai buɗe litafi ba ko abin rubutu. "buɗe" na nufin ganewar su. AT: "sa'anda yake bayyana mana littattafai" ko "sa'anda ya samu gane littattafai"
"Su" na nufin mutane ne biyun.
"goma sha ɗayan ... a sauran da suke tare da su, da sauran da suka gaya wa mutane biyun"
"mutane biyun sun gaya ma su"
Wannan na nufin Yesu ya bayyana ma su sa'anda suke tafiya a hanya zuwa garin Imawus.
AT: "yadda suka gane Yesu"
"sa'anda Yesu ya karya gurasan" ko "sa'anda Yesu ya yage gurasan"
"a cikin su"
"Bari ku kasance da salama" ko "Allah ya ba ku salama!" Wannan kalmar "ku" jam'i ne.
"Amma" ya nuna bambanci mai ƙarfi. Yesu ya ga ya masu su zama da salama, amma sun ji tsoro amaimako.
"firgitad da tsoro." Wadannan saahi biyun na nufin abu ɗaya, kuma an yi amfani da su a yi nauyin akan tsoron su.
"tunanin cewa suna ganin irin fatalwa." Har yauzu ba su gane da gaskiye cewa Yesu ya na a raye.
A nan na nufin ruhun mutum da ya mutu.
Yesu yaa yi amfani da tambaya ya karfaf su. AT: "kada ku ji tsoro."
Yesu ya yi amfani da tambaya domin ya kwabe su mara tsanani. Yesu ya na gaya masu kada su yi shakka cewa yana a raye. kalmar "zuciya" misali ne na hankalin mutum. AT: "kada ku yi shakka a zuciyar ku!" ko "ku daina shakka!"
Yesu ya tambaye su su tabbata da taba shi da cewa shi ab fatalwa bane. zai zama da taimako rubuta ko ka hada wannan jumlan. AT: "Taba ni ku gani inada naman jiki da ƙashi da fatalwa bai da shi"
Wannan hanya ne na nufin jiki na fuska.
An gane da cewa hannayensa da ƙafafunsa suna da alamar ƙusa na giciyar sa da zai haƙikanta cewa lallai Yesu ne. Wannan za'a iya bayana shi. AT: "ciwon da yake hanunsa da ƙafarsa"
"Sun cika da murna sosai har ma ba su yarda cewa da gaskiye ne"
Yesu ya yi haka domin ya nuna ma su cewa yana da jiki na fuska. Ruhu ba za su iya cin abinci ba.
"a gabansu" ko "sa'anda suke kallo"
"Sa'adda nake tare da ku kamin"
AT: "Allah zaya cika duk abin da ke rubuce ... Zabura" ko "Allah zai sa duk abin da ke a rubuce ... Zabura ya faru"
Wannan kalmar "dokokin Musa," " annabawa," da " Zabura" sunaye ne daidai na saahin littafi mai tsrki na Ibraniyawa. AT: "duk abin da Musa ya rubuta a cikin dokoki, duk abin da annabawa suka rubuta, da duk abin da marubucin Zabura ya rubuta akai na"
A "buɗe zuciya" kari ne da yake nufin ka sa wani ya gane. AT: " sai ya sa su sun gane littattafai "
AT: "Wannan abin da ya faru ne da daɗewa rubuta"
A wannan aya, "a tashi" shine ka dawo rayuwa kuma. Wannan kalmar "daga mattatu" ya yi maganar duk mutanen da su ka mutu daga ƙarƙashin ƙasa.
AT: "mabiyan Almasihu su yi wa'azi ga mutanen dukan al'ummai da suke so su tuba kuma suna so Allah ya yafe masu zunubin su ta wurin Yesu"
"sunar " sa anan na nufin ikon sa. AT: "da ikon Almasihu"
"dukan kananaa garuruwa" ko dukan kungiyoyin mutane"
"farawa daga Urushalima"
"ku gaya wa wasu da cewa abin da kuka gani akain na gaskiyane." al'majeren sun dubi rayuwan Yesu, mutuwa da tash iwar,kuma za su iya kwatanta wamutane abin da ya yi.
"Zan ba ku abin da Ubana ya yi alkawari zai ba ku." Allah ya yi alkawari zai ba ku Ruhu mai Tsarki. UDB ya bayyana wannan.
Wannan suna ne mai muhimmanci ga Allah.
Ikon Allah zai rufe su a hanya ɗaya kamar yadda riga ya ke rufe mutum. AT: "za ku karbe iko"
"daga sama" ko daga Allah"
"Yesu ya tafi tare da al'majeren wajen garin"
Wannan aiki ne da firist su ke aikatawa idan suka sa wa mutane albarka.
"sa'anda Yesu ya ke tambayan Allah ya yi ma su abu mai kyau"
Tunda Luka bai faɗa wanda ya dauke Yesu sa ba,ba mu san ku Allah ne da kansa ko wani ko mala'iku. Idan yaren ku su na so su fada wanda ya dauke shi,zai zama da kyau su yi amfani da "tafi" a maimakon, kamar yadda UDB ya yi.
"al'majeren suka yi wa Yesu sujada"
"sai suka koma"
Wannan kwatanci ne ya furta cewa su na zuwa cikin haikali kowace rana.
firist ne kawai ake bari su shiga cikin ginin haikalin. AT: "a cikin haikalin"
"yabon Allah"
1A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne. 2Shi kuwa tare da Allah yake tun farko. 3Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.4A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane. 5Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.6Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya. 7Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa. 8Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.9Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.10Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba. 11Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.12Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah. 13Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.14Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya. 15Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, "Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'"16Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri. 17Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu. 18Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.19Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, "Wanene kai?" 20Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, "ba nine Almasihu ba." 21Sai suka tambaye shi, "To kai wanene? Kai Iliya ne?" Yace, "Ba ni ba ne." Suka ce, "Kai ne anabin?" Ya amsa, "A'a".22Sai suka ce masa, "Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?" 23Yace, "Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada."24Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa, 25"To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?".26Yahaya ya amsa masu, cewa, "Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba, 27shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba." 28Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.29Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, "Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya! 30Wannan shine wanda na fada maku cewa, "Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.' 31Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa."32Yahaya ya shaida, cewa, "Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa. 33Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.' 34Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah."35Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa, 36suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, "Duba, ga Dan rago na Allah!"37Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu. 38Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, "Me kuke so?" Suka amsa, "Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?" 39Yace masu, "Zo ku gani." Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.40Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus. 41Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, "Mun sami Almasihu" (wanda ake kira 'Kristi'). 42Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, "Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas," (ma'ana, 'Bitrus').43Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, "ka biyo ni." 44Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus. 45Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, "Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat."46Natana'ilu ya ce masa, "za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?" Filibus yace masa, "Zo ka gani." 47Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, "Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa." 48Natana'ilu yace masa, "Ta yaya ka san ni?" Sai Yesu ya amsa masa yace, "Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka."49Natana'ilu ya amsa, "Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!" 50Yesu ya amsa masa yace, "Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma." 51Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum."
Wannan na nufin farkon farin loƙaci kamin Allah ya halicci samai da duniya.
Wannan na nufin Yesu.
"Allah ya halicci dukan komai ta wurin sa" (Dubi:|)
Idan harshen ku be yarda da kalmar da ba daidai ba yakamata wannan kalman ya bayyana shi da kyau a "An halicci dukkan komai ta wurin sa." AT: "Allah ya halicci komai tare da shi" ko kuma "tare da shi akowai komai da an halitta wadda an riga an halitta " Allah ya halicci tare da shi komai da ya halitta"
"A cikinsa rai ya ke" magana ne game da sa komai ya rayu. kuma, "haske" magana na game da "gaskiya." AT: "shi ne ya sa komai ya rayu. Kuma ya bayyana wa mutane game da gaskiya akan Allah"
A nan "sa" ya na nufin wadda ake kiransa kalma.
Ku yi amfani da kalma ta musamman na "Rai." Idan kuna son ku daidaita, ku fasara ta kamar "rai ta ruhaniya."
A nan "haske" magana ne game da abin da ke da gaskiya da kuma kyau. Anan "duhu" magana ne game da abin da ba daidai ba ko mugu.
A nan "haske" magana ne game da wahayin Allah a cikin Yesu. AT: "nuna yaɗa Yesu ya ke kamar hasken gaskiya na Allah"
A nan haske magana ne da ke wakilcin Yesu wadda ya bayyana gaskiyan game da Allah kuma shi ne wannan gaskiyan.
"ko da shike yana cikin wannan duniya, kuma Allah ya halicci komai ta wurinsa, mutane basu gane shi ba"
Kalmar "duniya" magana ne da ke kamar mutane da suka yi rayuwa a duniya. "Mutanen basu san ko shi waye ne ba"
"Ya zo wurin mutanen kasar sa, amma mutanen kasar sa basu karbe shi ba"
"karɓe shi." Karban wani ya na nufin marabshen sa da kuma martaba shi da daraja da begen gina mutunshi tare da shi.
Kalmar "suna" magana ne da ke kamar halin Yesu do komai game da shi. AT: "gaskanta da shi"
"ya basu yanchin" ko " ya sa komai yiwuwa masu"
Kalmar "'ya'ya" magana ne da ke nufin dangantakan mu da Allah, wadda yake kamar 'ya'ya da Uba.
A nan "jiki" na wakilcin "mutum." AT: "zama mutum"
Jumlan nan "makadaici" na nufin cewa shi dabam ne, babu wani kamarsa. Jumlan "wanda ya zo daga Uban" na nufin cewa shi ne ɗan Uba. AT: "ɗa na Uba wanda ya na nan dabam" ko kuma "Ɗa wanda shi ne kadai na Uba"
Wannan laƙani ne na mahimmi ga Allah
"cike da kyaukyawan aiyuka zuwa gare mu wadda bamu chanchanta ba"
Yohanna na magana game da Yesu. Jumlan "zuwa a bayana" na nufin cewa aikin Yohanna ya riga ya fara kuma aikin Yesu ze fara jim kadan.
"ya fi muhimmanci fiye da ni" ko kuma" ya na da ikon fiye da ni"
Ku yi hankali ka da ku fasara a hanyar da ze nuna cewa Yesu ya fi muhimmi domin ya girmi Yohanna bisa ga shekarun mutuntaka. Yesu ya fi Yahaya domin shi Ɗan Allah ne, wanda ya na da rai kullum.
Wannan kalma na nufin alherin Allah da babu iyaka.
"albarka akan albarka"
kalmar "Yahudawa" na nufin " shugabannin yahudawa". AT: "Shugabannin yahudawa suka aika... zuwa gareshi daga Urushalima"
Jumla na biyu ya bayyana abubuwan da jumla na farko ya bayyana a hanyar da ba daidai ba domin ya nanata cewa Yahaya yana faɗan gaskiya ne, yana kuma cewa ba shi ne Almasihu ba. Mai yiwuwa harshen ku ya na da hanya dabam na yin wannan.
"Me ne zancen, idan ba kai ne mai ceto ba?" ko kuma "Me ya ke faruwa?" ko kuma "Me ku ke yi?"
Yahaya ya shigaba da magana da fristoci da kuma levites.
"fristocin da levites sun ce wa Yahaya"
fristocin da levites, ba Yahaya ba
"Yahaya ya ce"
Yahaya ya na cewa anabcin Ishaya na game da shi. Kalmar "murya" a nan na nufin mutumin da ke kira a cikin jeji. AT: "ni ne ina kira a cikin jeji"
A nan an yi amfani da kalmar "hanya". AT: "shirya kanku wa zuwan Ubangiji kamar yadda mutane su ke shirya hanya wa mutum mai daraja"
Wannan bayanin labari ne game da mutane da sun tambaye Yahaya.
Aya 28 ya faɗa mana asalin bayani game da shirin labarin.
Ya kamata ku bayyana abin da zai yi idan ya zo. AT: "wanda zai yi maku wa'azi bayan na tafi"
Dama kwancen takalma aikin bawa ne.Wannan magana ne na aiki mara daɗi na bawa. AT: "ni, wanda ban cancanta in yi bauta a hanya da ba daɗi" ko "ni. ban cancanci in kwance igiyar takalminsa ba"
Wannan magana ne wadda yake wakilcin cikakken hadayan Allah. Ana kirin Yesu "Ragon Allah" domin an yi hadayarsa domin zunuban mutane.
Kalmar "duniya" magana ne wadda ya ke nufin dukkan mutane a cikin duniya.
Dubi yadda an fasara wannan a cikin 1:15.
saukowa daga sama
Wannan jumlan tamka ne. "Ruhun" ya sauka kamar yadda kurciya yake sauka a kan mutum.
Kalmar "sama" na nufin "sarari."
Wadansu matanin sun ce "Ɗan Allah"; wadansu kuma suka ce "zaɓi na Allah."
Wannan muhimmin laƙani ne wa Yesu, Ɗan Allah.
Wannan wata rana ne. Rana na biyu ne wadda Yahaya ya gan Yesu.
"sa'a ta goma." Wannan Jumlan ya na bayyana loƙacci da rana, kafin duhu, wadda ba za a iya yin tafiya zuwa wata gari ba, mai yiwuwa sa'a hudu na yamma.
Wannan ba Yahaya mai baftisma ba ne. "Yahaya" sanannen suna ne.
Wannan ne labari game da Filibus.
"Natana'ilu ya ce wa Filibus"
Wannan furucin ya bayyana kamar tambaya ne domin a kara nanaci. AT: "Ba bu abu mai kyau da zai fito daga Nazarat!"
AT: "cikakken mutumin gaskiya"
Wannan furucin ya bayyana kamar tambaya domin a ba da nanaci. AT: "ka gaskanta domin na ce, na gan ka a karkashin bishiyan baure'!
Ku fasara wannan a yadda harshen ku zai nanata cewa an fahinci muhimmin abin da ke da gaskiya.
1Bayan kwana uku, akwai aure a Kana ta Galili, mahaifiyar Yesu kuma tana wurin. 2An gayyaci Yesu da almajiransa zuwa auren.3Da ruwan inabin ya kare, maihafiyar Yasu tace masa, "basu da ruwan inabi." 4Yesu yace mata, "Mace, me yasa kika zo wurina? Lokaci na bai yi ba tukuna". 5Maihafiyarsa tace wa ma'aikatan, "Ku yi duk abin da yace maku."6To akwai randunan ruwa na dutse guda shidda a wurin wadanda Yahudawa ke amfani da su domin al'adansu na tsarkakewa, kowace zata iya daukar durom guda. 7Yesu yace masu, "Cika randunan da ruwa". Sai suka cika randunan makil. 8Sai yace wa ma'aikatan, "Ku diba daga ciki ku kai wa shugaban biki." Sai suka yi hakannan.9Shugaban bikin ya dandana ruwan da ya zama ruwan inabin, amma bai san inda ya fito ba (amma ma'aikatan wadanda suka jawo ruwan sun sani). Sai ya kira ango 10yace masa, "Kowane mutum yakan raba ruwan inabi mai kyau da farko, kafin mai arhar bayan an shanye mai kyaun. Amma kai ka ajiye mai kyaun sai yanzu."11Wannan alama ta farko ce da Yesu yayi a Kana ta Galili, ya kuma bayyana daukakarsa, almajiransa kuma suka gaskata da shi.12Bayan wannan, Yesu, da mahaifiyarsa, da 'yan'uwansa da almajiransa suka tafi Kafarnahum, kuma suka zauna can wasu 'yan kwanaki.13To idin ketarewa na Yahudawa ya kusato, Yesu kuwa ya wuce zuwa Urushalima. 14Ya iske wadanda suke sayar da shanu da tumaki da tantabaru, masu canjin kudi kuma na zaune a wurin.15Sai yayi tsumingiya da igiyoyi ya kore su duka daga cikin haikalin, duk da tumakin da shanun. Sai ya watsar da sulallan masu canjin kudin ya birkitar da teburansu. 16Yace wa masu sayar da tantabaru, "Ku fitar da wadannan abubuwa daga nan. Ku daina maida gidan Ubana wurin kasuwanci."17Almajiransa suka tuna a rubuce yake, "Himma domin gidanka za ta cinye ni." 18Sai shugabannin Yahudawa suka amsa suka ce masa, "Wace alama za ka nuna mana, da shike kana yin wadannan abubuwan?" 19Yesu ya amsa, "Ku rushe wannan haikali, kuma a cikin kwana uku zan gina shi."20Sai shugabanin Yahudawa suka ce, "An dauki shekaru arba'in da shidda kamin a gama gina wannan haikalin, za ka dau kwanaki uku kadai wajen gina shi?" 21Amma yana nufin haikali na jikinsa ne. 22Bayan da aka tashe shi daga matattu, sai almajiransa suka tuna ya fadi haka, suka kuma ba da gaskiya ga nassi da wannan kalami da Yesu ya fada.23Kuma, da yana Urushalima a idin ketarewa, a lokacin idin, mutane da yawa suka gaskata ga sunansa, sa'adda suka ga alamun da ya yi. 24Amma Yesu bai yadda da su ba domin ya san su duka, 25saboda baya bukatar wani ya shaida masa game da mutum, domin ya san abinda ke cikin sa.
An gayyaci Yesu da almajiransa zuwa aure. Wannan ayan ya ba da asalin bayani game da shirin labarin.
Yawancin masu fasara su na karanta wannan da cewa bayan kwana na uku ne Yesu ya kira Filibus da Nataniel don su bi shi. Ranar farko ya faru a cikin 1:35 da kuma na biyun a cikin 1:43.
AT: "Wani ya gayyaci Yesu da almajiransa zuwa aure"
Wannan ya na nufin Maryamu. Idan ba shi da kyau ɗa ya kira Uwarsa "Mace" a harshenku, sai ku yi amfani da da wata kalma mai kyau ko kuma ku bari.
An yi wannan tambaya domin a ba da nanaci. AT: "wannan bai shafe ni ba." ko kuma "kadda ku faɗa mani abin da zan yi."
Kalmar "loƙaci" magana ne da ke wakilcin loƙacin da ya cancanta wa Yesu don ya nuna cewa shi ne mai ceto ta wurin aikin al'ajibi. AT: "Loƙacin bai kai ba da zan yi baban abu"
Za ku iya juya wannan zuwa awu na zamani. AT: "75 zuwa lita 115"
Wannan ya na nufin "zuwa sama" ko kuma "cikakke."
Wannan ya na nufin mutumin da ke dauki da shugabancin abinci da ruwan sha.
Wannan ita ce bayanin zancen.
rashin iya bambanta sakanin ruwa mai arha da ruwa mai tsada domin shan giya dayawa
Wannan ayan bata cikin asalin labarin, amma ta na ba da ra'ayi game da labarin.
Wannan sunan wuri ne.
A nan "daukakarsa" ya na nufin baban ikon Yesu. AT: "nuna ikonsa"
Wannan ya na nuna cewa sun wuce daga wuri mai sauki zuwa wuri mai tsawo. Kafarnahum ya na ta arewankudu na Kana da tsawo mai sauki.
Kalmar "'yan'uwansa" na a hade ne da 'yan'uwa da kuma 'yar'uwa. Yesu ya girme dukkan 'yan'uwaninsa.
Wannan ya na nuna cewa ya wuce daga wuri mai sauki zuwa wuri mai tsawo. An gina Urushalima a kan tudu.
Aya na biye ya nuna cewa wadannan mutanin na cikin fegan haikali. An yi wannan wurin domin sujada ne ba domin kasuwanci ba.
Mutane su na sayan dabbobi a cikin fegan haikali domin su yi hadaya wa Allah.
Hukumomin Yahudawa sun so mutanin da za su saya dabbobi don hadaya da cewa su canza kuɗin su zuwa ga wata kuɗi daga "masu canjin kuɗi."
Wannan kalmomin ya na da alamun abubuwan da ya faru domin wani abin da ya faru a farko. Don hakka, Yesu ya gan masu canza kuɗi a zaune a cikin haikali.
"Daina saya da sayad da abubuwa a cikin gidan Ubana"
Wannan jumla ne wadda Yesu ya yi amfani a matsayin haikali.
Wannan lakami ne ta muhimmi da Yesu ya yi amfani wa Allah.
AT: "wani ya rubuto"
Wannan ya na nufin haikali, gidan Allah.
Kalmar "cinye" ya na nuna maganar "wuta." Kaunar Yesu ga haikalin ya na nan ne kamar wuta da ke konewa a cikinsa.
Wannan ya na nufin abu ne wadda ya ke nuna cewa abin gaskiya ne.
Wannan ya na nufin yadda Yesu ya yi wa masu canza kuɗi a cikin haikali.
Yesu ya na bayyana yanayin abin da zai faru idan abin da ba gaskiya ba ne ya zama gaskiya. Don haka, zai gina haikalin idan hukumomin Yahudawa sun rushe ta. Ba wai yana yabon hukumomin Yahudawan don su rushe haikalin ba. Za ku iya fasara kalmomin "rushe" da kuma "gina" ta wurin amfani da kalmomin. AT: "Idan kun rushe wannan haikalin, Haƙiƙa zan gina shi" ko kuma " Za ku iya tabatar da cewa idan kun rushe wannan hakalin, Zan gina shi"
"sa shi ya tsaya"
shekaru arba'in da shidda ... kwanaki uku"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya nuna cewa hukuman Yahudawa sun gane cewa Yesu ya na so ya rushe haikalin sai ya kuma gina ta a kwanaki uku. "gina" karin magana ne na "kafa." AT: "za ku kafa ta a kwanaki uku?" ko kuma "ba za ku iya gina ta a cikin kwanaki uku ba!"
A nan "gaskanta" ya na nufin amsa wani abu ko kuma yarda cewa gaskiya ne.
Wannan ya na nufin kalamin Yesu a cikin 2:19.
Kalmar "yanzu" yana gabatar da mu zuwa ga sabon abu a cikin labarin.
A nan "suna" magana ne da ke wakilcin Yesu. AT: "gaskanta da shi"
Ana iya kiran abin ban mamaki "alamu" domin an yin amfani da su don su nuna cewa Allah mai iko ne wadda yake da iko akan duniya.
A nan kalmar "mutum" ya na wakilcin mutane. AT: "game da mutane, domin ya san abin dake a cikin mutane"
1akwai wani Bafarise da ake kira Nikodimu, shugaba a cikin Yahudawa. 2Wannan mutum ya zo wurin Yesu da dare ya ce masa, "Rabbi, mun sani cewa kai malami ne da kazo daga wurin Allah, gama ba wanda zai iya yin wadannan alamu da kake yi sai idan Allah na tare da shi."3Yesu ya amsa masa, "Hakika, hakika, idan ba a sake haifuwar mutum ba, ba zai iya ganin mulkin Allah ba." 4Nikodimu ya ce masa, "Yaya za a sake haifuwar mutum bayan ya tsufa? Ba zai iya sake shiga cikin cikin uwarsa kuma a haife shi ba, zai iya?"5Yesu ya amsa, "Hakika, hakika, idan ba a haifi mutum da ruwa da kuma Ruhu ba, ba zai iya shiga cikin mulkin Allah ba. 6Abin da aka haifa ta wurin jiki, jiki ne, kuma abin da aka haifa ta wurin Ruhu, Ruhu ne.7Kada ka yi mamaki don na ce maka, 'dole a maya haifuwar ka.' 8Iska takan hura duk inda ta ga dama. Ka kan ji motsin ta, amma ba ka san inda ta fito ko inda za ta tafi ba. Haka duk wanda aka haifa daga Ruhu."9Nikodimu ya amsa yace masa, "Yaya wannan zai yiwu?" 10Yesu ya amsa yace masa, "Kai malami ne a Israila amma ba ka san wadannan al'amura ba? 11Hakika, hakika, ina gaya maka, muna fadin abubuwan da muka sani, kuma muna shaida abubuwan da muka gani. Duk da haka ba ku karbi shaidar mu ba.12Idan na gaya maka abubuwan da ke na duniya amma baka gaskata ba, to yaya zaka gaskata idan na gaya maka abubuwa na sama? 13Babu wanda ya taba hawa zuwa sama sai dai shi wanda ya sauko daga sama: wato Dan Mutum.14Kamar yadda Musa ya ta da maciji a jeji, haka ma dole a ta da Dan Mutum 15domin dukan wadanda suka bada gaskiya gareshi su sami rai na har abada.16Gama Allah ya kaunaci duniya sosai, har ya ba da makadaicin Dansa, domin duk wanda ya bada gaskiya gareshi, kada ya mutu, amma ya samu rai madawwami. 17Gama Allah bai aiko da Dansa cikin duniya domin ya kayar da duniya ba, amma domin a ceci duniya ta wurin sa. 18Duk wanda ya bada gaskiya gare shi ba a kayar da shi ba, amma duk wanda bai bada gaskiya gare shi ba an riga an kayar da shi, domin bai bada gaskiya ga sunan wannan da shi kadai ne Dan Allah ba.19Wannan shi ne dalilin shari'ar, domin haske ya zo duniya, amma mutane suka kaunaci duhu fiye da hasken, sabili da ayyukan su na mugunta ne. 20Domin duk wanda ke mugayen ayyuka ya ki haske, kuma baya zuwa wurin hasken domin kada ayyukansa su bayyanu. 21Sai dai duk wanda yake aikata gaskiya kan zo wurin hasken domin ayyukansa, da ake aiwatarwa ga Allah, su bayyanu.22Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi kasar Yahudiya. A can ya dan zauna tare da su ya kuma yi Baftisma. 23Yahaya ma yana Baftisma a Ainon kusa da Salim domin akwai ruwa da yawa a can. Mutane na zuwa wurin sa yana masu Baftisma, 24domin a lokacin ba a jefa Yahaya a kurkuku ba tukuna.25Sai gardama ta taso tsakanin almajiran Yahaya da wani Bayahude akan al'adun tsarkakewa. 26Suka je wurin Yahaya suka ce, "Rabbi, wanda yake tare da kai a dayan ketaren kogin Urdun, kuma ka shaida shi, duba, yana baftisma, kuma mutane duka suna zuwa wurin sa."27Yahaya ya amsa, "Mutum ba zai iya samun wani abu ba sai an ba shi daga sama. 28Ku da kanku zaku shaida na ce, 'Ba ni ne Almasihu ba' amma amaimakon haka, 'an aiko ni kafin shi.'29Amaryar ta angon ce. Yanzu abokin angon, wanda ke tsaye yana saurarensa, yana murna sosai saboda muryan angon. Murnata ta cika domin wannan. 30Dole shi ya karu, ni kuma in ragu.31Shi wanda ya fito daga sama ya fi kowa. Shi Wanda ya zo daga duniya, na duniya ne, kuma game da duniya yake magana. Shi wanda ya fito daga sama yana saman kowa. 32Ya shaida abubuwan da ya ji ya kuma gani, amma babu wanda ya karbi shaidarsa. 33Duk wanda ya karbi shaidarsa ya tabbatar Allah gaskiya ne.34Domin duk wanda Allah ya aika kan yi magana da kalmomin Allah. Domin bai bada Ruhun da ma'auni ba. 35Uban ya kaunaci Dan, ya kuma ba da dukan komai a hanunsa. 36Shi wanda ya bada gaskiya ga Dan ya na da rai madawwami, amma wanda ya ki yiwa Dan biyayya ba zai ga rai ba, amma fushin Allah na kansa.
Nikodimu ya zo ya gan Yesu.
An yi amfani da wannan kalma a nan domin a nuna sabon sashin labarin da kuma gabatar da Nikodimu.
"A nan "ku" ya na nufin Nikodimu da kuma sauran mutanin majalisan Yahudawa.
Yesu da Nikodimu sun cigaba da magana.
Dubi yadda an fasara wannan a cikin 1:51.
"haifafe daga sama" ko kuma "haifafe na Allah"
Kalmar "mulki" magana ne game da shugabancin Allah. AT: "wurin da Allah yake shugabanci"
Nikodimus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya nanata cewa ba zai iya faruwa ba. AT: "hakika, ba za a iya haifan mutum kuma bayan ya tsufa ba!"
Nikodimus ya kuma yi amfani da wannan tambayan domin ya bayyana ra'ayin shi da cewa haifuwa na biyu ba shi yiwuwa. "hakika, ba zai iya shigan cikin cikin Uwarsa na biyu ba!
"kuma"
wata sashin jikin mace wadda yaro yake girma a ciki
AT: 1) "yi baftisma a cikin ruwa da kuma ruhu" ko kuma 2) "haifafe ta jiki da kuma ta ruhaniya"
Kalmar "mulki" magana ne game da shugabancin Allah a rayuwan mutum. AT: "ya ji shugabancin Allah a rayuwansa"
"Dole ne a haife ku daga sama"
A ainihin harshen, iska da Ruhu kalma daya ne. Mai magana a nan ya na maganan iska kamar mutum ne. AT: "Ruhu mai Tsarki ya na nan kamar iska wadda yake huruwa a duk inda yake so"
Wannan tambayan ya kara bayani ne a jumlan. AT: "Wannan ba ya yiwuwa!" ko kuma "Wannan ba zai iya faruwa ba!"
Wannan tambayan ya kara bayani ne a jumlan. AT: "Kai mallami ne na Israila, Ina mamaki cewa ba ka gane wadannan abubuwa ba!"
Yesu bai haɗa da Nikodimu ba a loƙacin da ya ce "mu". (Dubi:
Wannan tambaya ya nanata rashin gaskantawar Nikodimu. AT: "hakika, ba za ku gaskanta ba idan na gaya maku game da abubuwan sama!"
A dukkan wuraren "ka" ɗaya ne.
abubuwan ruhaniya
Wannan ya na nufin wurin da Allah yake.
Wannan karin magana ne. Wadansu mutane za su "ta da" Yesu kamar yadda Musa ya "ta da" macijin a cikin jeji.
Jejin ya bushe, tsararin wuri, amma a nan ya na nufin wurin da Musa da Isra'ilawa su ka yi tafiya na shekaru arba'in.
A nan "duniya" magana ne da ke nufin kowa a duniya.
Wannan ne irin kauna da ke zuwa daga Allah kuma ya na nan a kan wadansu, ko a loƙacin da bai ribanya ba. Allah da kansa ne kauna kuma shi ne hanyar kauna ta gaskiya.
An bayyana wadannan kalmomin da ke nufin abu ɗaya, na farko daidai sai kuma wadda ba daidai ba. Wadansu harshen su na iya nanata a hanya dabam. AT: "Ainahin dalilin da Allah ya aiko ɗansa a duniya shi ne domin ya cece ta"
"ya hukunta." "Hukunta" ya na nuna cewa Allah ya na karban mutum bayan an hukunta shi. A loƙacin da an kayar da mutum, ana hukunta shi kuma Allah ba ya karban shi.
Wannan muhimmin lakabi ne wa Yesu.
Kalmar "haske" magana ne game da gaskiyar Allah da ke a bayyane a cikin Yesu. Yesu ya yi magana game da kansa a cikin mutum na uku. Idan harshen ku ba ya yarda mutane su yi maganan kansu a cikin mutum na uku, za ku iya bayyana wadda ya kasance hasken. "Duniya" magana ne game da dukkan mutane da suke a cikin duniya. AT: "Wadda yake kamar haske ya bayyana gaskiyar Allah wa dukkan mutane" ko kuma "Ni, wadda nake kamar haske, na zo cikin duniyan"
A nan "duhu" magana ne game da mugu.
AT: "domin kadda hasken ya nuna abin da yake yi" ko kuma "domin kadda hasken ya bayyana ayukansa"
AT: "mutane za su iya ganin ayukansa da kyau" ko kuma "kowa zai iya ganin abubuwan da yake yi da kyau"
Wannan ya na nufin bayan Yesu ya yi magana da Nikodimu. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 2:12.
Wannan kalmomin na nufin "rafi," kamar na ruwa.
wata kauye dake kusa da rafin Joda
"domin akwai rafi dayawa a wurin"
AT: "Yahaya ya na yi masu baftisma" ko kuma "ya na yi masu baftisma"
AT: "Sai almajiran Yahaya da wani Bayahude suka fara jayayya"
faɗa da amfani da kalmomi
A cikin wannan jumlan, "duba" umurni ne dake nufin "sa hankali!" AT: "ka shaida, 'duba! Ya na yin baftisma," ko kuma "ka shaida. ;dubi wancan! Ya na yin baftisma," (Dubi: rc://*/ta/man/translate/figs-explicit)
"Ba bu wanda yake da iko saidai"
A nan maganan "sama" na nufin Allah. AT: "Allah ya ba shi shi"
Wannan "ku" ya na nufin dukkan mutane da Yahaya yake magana da su. AT: "Dukkan ku"
AT: "Allah ya aike ni don in isa kafin shi"
A nan "amarya" da "anga" karin magana ce. Yesu ya na nan kamar "angon" kuma Yahaya ya na nan kamar abokin "angon."
AT: "Don haka na yi farinciki sosai"
Kalmar "na" ya na nufin Yahaya mai baftisma, wadda yake magana.
"Shi" ya na nufin ango, Yesu, wanda zai cigaba da girma a cikin daraja.
"Shi wanda ya fito daga sama ya fi kowa muhimmi"
Yahaya ya na nufin cewa Yesu ya fi shi da shike Yesu ya na daga sama, kuma an haife Yahaya a duniya. AT: "shi wadda yake haifaffe a duniyan nan ya na nan kamar kowane mutum da yake rayuwa a duniya kuma yana magana game da abin da yake faruwa a cikin wannan duniya"
Wannan ya na nufin abu ɗaya ne a jumla na farko. Yahaya ya nanata wannan don bayani.
Yahaya ya na magana game da Yesu. AT: "wadda yake sama ya na magana game da abin da ya ji ya kuma gani a sama"
Yahaya ya nanata bayanin a nan cewa mutane kadan ne suka gaskanta da Yesu. AT: "mutane kadan ne sun gaskanta da shi"
"Duk wanda ya gaskanta da abin da Yesu ya ce"
"nuna" ko "yarda"
"Wannan Yesu, wadda Allah ya aike shi don ya zama wakilinsa"
"Domin shi ne wadda Allah ya ba da dukkan ikon Ruhunsa"
Wadannan muhimmin lakaɓi ne wadda suke kwatanta dangantaka sakanin Allah da Yesu.
Wannan ya na nufin sa a ikonsa.
"mutum da ya gaskanta"
Ana iya bayyana kalmar "fushi". AT: "Allah zai cigaba da hukunta shi" (Dubi: rc://*/ta/man/translate/figs-abstractnouns)
1Da Yesu ya sani cewa Farisawa sun ji cewa yana samun almajirai yana kuma yi masu baftisma fiye da Yahaya 2(ko da shike ba Yesu da kansa ke yin baftismar ba, amma almajiransa ne), 3ya bar Yahudiya ya koma Galili.4Amma ya zamar masa dole ya ratsa ta Samariya. 5Ya zo wani birnin Samariya, mai suna Sika, kusa da filin da Yakubu ya ba dansa Yusufu.6Rijiyar Yakubu na wurin. Da Yesu ya gaji da tafiyarsa sai ya zauna gefen rijiyar. Kusan karfe goma sha biyu na rana ne. 7Wata mace, Ba-Samariya ta zo domin ta dibi ruwa, sai Yesu ya ce mata, "Ba ni ruwa in sha." 8Gama almajiransa sun tafi cikin gari don sayen abinci.9Sai ba-Samariyar tace masa, "Yaya kai da kake Bayahude kake tambaya ta ruwan sha, ni da nike 'yar Samariya?" Domin Yahudawa ba su harka da Samariyawa. 10Sai Yesu ya amsa yace mata, "In da kin san kyautar Allah, da shi wanda yake ce da ke, 'Ba ni ruwan sha,' da kin roke shi, sai kuma ya ba ki ruwan rai."11Matar tace masa, "Mallam, ga shi ba ka da guga, kuma rijiyar tana da zurfi. Ina za ka samu ruwan rai? 12Ai ba ka fi Ubanmu Yakubu ba, ko ka fi shi, shi wanda ya ba mu rijiyar, shi kansa kuma ya sha daga cikin ta, haka kuma 'ya'yansa da shanunsa?"13Yesu ya amsa yace mata, "duk wanda ya sha daga wannan ruwan zai sake jin kishi, 14amma duk wanda ya sha daga ruwa da zan ba shi ba zai sake jin kishi ba. Maimakon haka, ruwan da zan bashi zai zama mabulbular ruwa a cikinsa wanda ke bulbula zuwa rai madawwami."15Matar tace masa, "Mallam, ka ba ni wannan ruwa yadda ba zan kara jin kishi ba ba kuma sai na zo nan don in dibi ruwa ba." 16Yesu ya ce mata, "Je, ki kira maigidanki ku zo nan tare."17Matar ta amsa tace masa, "Ba ni da miji." Yesu yace, "Kin fadi daidai da kika ce, 'ba ni da miji,' 18domin kin auri mazaje har biyar, kuma wanda kike da shi yanzu ba mijin ki bane. Abinda kika fada gaskiya ne."19Matar tace masa, "Mallam, Na ga kai annabi ne. 20Ubaninmu sun yi sujada a wannan dutse, amma kun ce Urushalima ce wurin da ya kamata mutane su yi sujada."21Yesu ya ce mata, "Mace, ki gaskata ni, cewa lokaci na zuwa wanda ba za ku yi wa Uban sujada ba ko akan wannan dutse ko a Urushalima. 22Ku kuna bauta wa abinda ba ku sani ba. Mu muna bauta wa abinda muka sani, gama ceto daga Yahudawa yake.23Sai dai, sa'a tana zuwa, har ma ta yi, wadda masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a cikin ruhu da gaskiya, domin irin wadannan ne Uban ke nema su zama masu yi masa sujada. 24Allah Ruhu ne, kuma mutanen da ke yi masa sujada, dole su yi sujada cikin ruhu da gaskiya."25Matar ta ce masa, "Na san Almasihu na zuwa (wanda ake kira Kristi). Sa'adda ya zo, zai bayyana mana kowane abu. 26Yesu ya ce mata, "Ni ne shi, wanda ke yi maki magana."27A daidai wannan lokaci, almajiransa suka dawo. Suna ta mamakin dalilin da yasa yake magana da mace, amma babu wanda yace, "Me kake so?" Ko kuma, "Don me ka ke magana da ita?"28Sai matar ta bar tulunta, ta koma cikin gari, tace wa mutanen, 29"Ku zo ku ga wani mutum wanda ya gaya mani duk wani abu da na taba yi. Wannan dai ba Almasihun bane, ko kuwa?" 30Suka bar garin suka zo wurinsa.31A wannan lokacin, almajiransa suna rokansa, cewa, "Mallam, ka ci." 32Amma ya ce masu, "ina da abinci da ba ku san komai akai ba." 33Sai almajiran suka ce da junansu, "Babu wanda ya kawo masa wani abu ya ci, ko akwai ne?"34Yesu ya ce masu, "Abincina shine in yi nufin wanda ya aiko ni, in kuma cika aikinsa. 35Ba ku kan ce, 'akwai wata hudu tukuna kafin girbi ya zo ba?' Ina gaya maku, daga idanunku ku ga gonakin, sun rigaya sun isa girbi. 36Shi wanda ke girbi yakan karbi sakamako ya kuma tattara amfanin gona zuwa rai na har abada, ta haka shi mai shuka da shi mai girbi za su yi farinciki tare.37Gama cikin wannan maganar take, 'Wani na shuka, wani kuma na girbi.' 38Na aike ku ku yi girbin abinda ba ku yi aiki a kai ba. Wandansu sun yi aiki, ku kuma kun shiga cikin wahalarsu.39Yawancin Samariyawan da ke wannan birni suka gaskata da shi sabili da labarin matar data bada shaida, "Ya gaya mani duk abinda na taba yi." 40To sa'adda Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roke shi ya zauna tare da su, ya kuwa zauna wurin kwana biyu.41Wasu da dama kuma suka gaskata domin maganarsa. 42Suka cewa matar, "Mun bada gaskiya, ba saboda maganar ki kadai ba, amma mu kanmu munji, yanzu kuma mun sani cewa wannan lallai shine mai ceton duniya."43Bayan wadannan kwana biyu, ya bar wurin zuwa Galili. 44Domin Yesu da kansa yace, ba a girmama annabi a kasarsa. 45Da ya zo Galili, Galiliyawan suka marabce shi. Sun ga dukan abubuwan da ya yi a Urushalima wurin idin, domin su ma sun je idin.46Kuma ya koma Kana ta Galili inda ya mayar da ruwa zuwa ruwan inabi. Akwai wani ma'aikacin fada wanda dansa na rashin lafiya a Kafarnahum. 47Da ya ji cewa Yesu ya bar Yahudiya ya koma Galili, sai ya tafi wurin Yesu ya roke shi ya sauko ya warka da dansa wanda ke bakin mutuwa.48Yesu yace masa, "Idan ba ku ga alamu da mu'ujizai ba, ba za ku gaskata ba." 49Ma'aikacin ya ce masa, "Mallam, ka sauko kafin da na ya mutu." 50Yesu yace masa, "Je ka. Dan ka ya rayu." Mutumin ya gaskata maganar da Yesu ya gaya masa, Sai yayi tafiyarsa.51Yayin da yake sauka kasa, bayinsa suka same shi, suna cewa, danka yana raye. 52Sai ya tambaye su sa'ar da ya fara samun sauki. Suka amsa masa, "Jiya a sa'a ta bakwai zazabin ya bar shi."53Sai Uban ya gane cewa wannan sa'a ce Yesu ya ce masa, "Jeka, danka na raye." Sabili da haka, shi da dukan gidansa suka bada gaskiya. 54Wannan ce alama ta biyu da Yesu ya yi bayan da ya bar Yahudiya zuwa Galili.
Yahaya 4:1-6 ya ba da bayanin abin da zai faru, maganan Yesu da ba-Samarya.
"Yanzu yesu ya na yin ... Yahaya (ko da shike ... ke), kuma Farisawa su ka ji game da ci gaban da yake yi. Ya sani cewa Farisawan sun ji, sai ya bar ... Galili"
An yi amfani da kalmar "yanzu" domin ya nuna ainahin abin da ze faru. A nan Yahaya ya fara faɗan sabon sashin bayyanin.
Maganar "kansa" ya kara bayyana cewa ba Yesu ne ya ke yin baftisma ba, amma almajiransa ne.
"Wannan ruko ne da ladabi, ba umurni ba.
Bai ce wa almajiransa su diba ma shi ruwa ba domin sun tafi.
Kalmar "masa" ya na nufin Yesu.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya domin ya nuna mamakin ba-Samariya, cewa Yesu ya tambaye ta abin sha. AT: "Ban yarda cewa, yadda ke Bayahude, ka na tambayan abin sha ba!"
"ba ya tare da "
Yesu ya yi amfani da maganan "ruwan rai" don ya nuna Ruhu mai Tsarki wadda yake aiki a cikin mutum domin canza da kuma sabonta rayuwa.
Wannan maganan ya zo kamar tambaya domin karin bayani. AT: "Ba ku fi Uban mu Yakubu ba ... shanu!"
"kakaninmu Yakubu"
"sha ruwan da ya fito daga ita"
"ba zai sake shan ruwa kuma ba"
A nan kalmar "mabulbular" magana ne na rai da ke ba da ruwa. AT: "ruwan da zan ba shi zai zama kamar bulbular ruwa a cikinsa"
A nan "rai" ya na nufin "rai na ruhaniya" wadda Allah ne kadai zai iya ba da.
A cikin wannan lamarin, ba-Samariyar ta na kiran Yesu "Mallalm," wadda yake a matsayin biyayya ko ladabi.
"samu ruwa" ko kuma "ja ruwa daga rijiya" ta amfani da guga
Yesu ya sake nanata wannan jumala domin ya bayyana cewa ya san matan ta na faɗan gaskiya ne.
"Na iya gane cewa kai annabi ne"
"Ubaninmu" ko kuma "Kakaninmu"
gaskanta da mutum ya na nufin yarda da cewa abin da mutumin ya ce gaskiya.
Yesu ya na nufin cewa Allah ya bayyana kansa da dokokinsa wa mutanin Yahudawa, ba wa yan samariya ba. Ta wurin littafi ne mutanin Yahudawan sun san Allah da kyau fiye da yan Samariya.
Ceta na har abada daga zunubi ya na zuwa ne daga Allah Uba, wadda shi ne Yahwe, Allah Yahudawa.
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
Wannan ba ya nufin cewa mutanin Yahudawa ne za su cece sauran daga zunubinsu. Ya na nufin cewa Allah ya zabi Yahudawa a matsayin mutane wadda za su gaya wa mutane game da cetonsa. AT: "gama dukkan mutane za su san game da ceton Allah saboda Yahudawan"
Yesu ya ci gaba da magana da ba-Samariyar.
"Koda shike, yanzu ne loƙacin da ya kamata masu sujada na gaskiya su"
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
"yi masa sujada a hanya mai kyau"
Duk kalmomin nan suna nufin "sarkin da Allah ya alkawarta."
Kalmar "bayyana kowane abu" ya na nufin dukkan abin da yakamata mutane su sani. AT: "zai gaya mana kowane abu da ya kamata mu sani"
"Yayin da Yesu ya na faɗan wannan, almajiransa suka dawo daga gari"
Ba sananne abu ne ba-Yahude ya yi magana da mace da bai sani ba, har idan matan ba-Samariyar.
AT: 1) Almajiran suke yi wa Yesu tambayoyin ko kuma 2) "ba bu wadda ya tambayi matan, 'Me ... so?' ko kuma tabayi Yesu, 'Me ... ita?"
ba-Samariyar ta zuguiguita domin ta nu na cewa ta yi farinciki da yadda Yesu ya san komai game ta ita. AT: "Zo ku ga wani mutum wadda ya san ni sosai, koda shike ban san shi ba"
Matan ba ta tabatar cewa Yesu ne Almasihu, sai ta yi tambaya da ta ke tsammanin amsan "babu," amma ta sake yin tambaya a maimakon yin magana domin ta na son mutanin su zaba wa kansu.
"Loƙacin da matan ta na shigan cikin gari"
"almajiran su na gaya wa Yesu" ko kuma "almajiran su na karfafa Yesu"
A nan Yesu ba ya maganan asalin "abinci," amma ya na shirya almajiransa domin koyi ta ruhaniya a cikin 4:34.
Almajiran su na tunani ko ya na magana game da asalin abinci ne. Sun fara tambayan junansu wannan tambaya, su na sa rai da amsan "babu." AT: "hakika ba bu wadda ya kawo masa abinci a loƙacin da muke cikin gari!"
A nan "abinci" magana ce da ke wakilcin "yin biyayya da nufin Allah." AT: "Kamar yadda abinci ya ke kosad da mutum mai yunwa, biyayya da nufin Allah ne abin da ke ƙosad da ni"
"ba wannan ne wata sanannan magana ba"
Kalmomin "gonaki" da "isa girbi" zance ce. Gonakin na wakilcin mutane. Kalmar "isa girbi" ya na nufin cewa mutanin su na shirye domin su karba sakon Yesu, kamar gonaki da sun isa girbi. AT: "Dubi sama ku ga mutane! Su na a shirye don su gaskanta da sako na, kamar 'ya'ya a gonaki na da sun isa mutane su girba su"
A nan "amfanin gona zuwa rai na har abada" magana ce dake wakilcin mutane da sun gaskanta da sakon Almasihu sun kuma karbi rai na har abada. AT: "kuma mutanin da sun gaskanta da sakon sun kuma karbi rai na har abada su ne su na nan kamar amfanin gona da mai girbi yake tarawa"
Kalmomin "shuka" da kuma "girbi" zance ne. Wadda ya na "shuka" ne yake bayyana sakon Yesu. Wadda yake "girbi" ne yake taimake mutanin don su karɓi sakon Yesu. AT: "mutum ɗaya ya na shuka irin, sai kuma wani mutum yana girbe 'ya'yan"
"yanzu kana saduwa da aikinsu"
"gaskanta da" wani ya na nufin "yarda" da mutumin. A nan, wannan ya na kuma nufin gaskanta cewa shi ne Ɗan Allah.
Wannan zuguiguita ce. Matan ta ji daɗi da yadda yesu ya san game da ita. AT: "ya gaya mani abubuwa dayawa game da rayuwana"
A nan "kalma" magana ne da ke wakilcin sakon da Yesu ya faɗa. AT: "sakonsa"
"duniya" magana ne wa masubi a dukkan duniya. AT: "dukkan masubi a cikin duniya"
daga Juda
An kara kalmar "kansa" domin a bayyana cewa Yesu ya "ce" wannan ... Ku na iya fasara wannan a harshen ku a hanyar da zai bayyana wa mutum.
"mutane ba su nuna daraja ko girma wa annabin kasarsu" ko kuma "mutane ba su daraja annabi a garinsa"
A nan idin ita ce idin ketarewa.
An yi amfani da wannan kalma domin a sa alaman fashi a ainahin labarin, a kuma je wata sashin labarin. Idan ku na da wata hanyar yin wannan a harshen ku, za ku iya amfani da shi.
wanin da yake aiki wa sarki
"Sai dai ... ba za ku gaskanta ba." A wadansu harshuna, yana da kyau a fasara wannan jumla a hanya mai kyau. AT: "da ce kun ga abin al'ajibi ne da kun gaskanta"
A nan "kalma" magana ce dake nufin sakon da Yesu ya yi magana. AT: "gaskanta da sakon"
An yi amfani da wannan kalma a abubuwa biyu da ke faruwa a loƙaci ɗaya. Yayin da ma'aikacin ya na tafiya gida, bayinsa suna zuwan samin shi a hanya.
An yi amfani da kalmar "kansa" domin a bayyana kalmar "shi." Idan ku na da wata hanyar yin wannan a harshen ku, za ku iya amfani da shi.
Ana iya kiran abubuwan al'ajibi "alamu" domin su na nuna cewa Allah mai daraja ne wadda yake da cikakken iko a duniya.
1Bayan haka akwai idi na yahudawa, kuma Yesu ya tafi Urashalima. 2To a cikin Urashilima kusa da kofar tumaki akwai tabki, wanda ake kira Baitasda da harshen Ibraniyanci, yana da shirayi biyar. 3Taron mutane dayawa masu ciwo da, makafi da guragu da shanyayyu suna kwance a wurin. 1425Akwai wani mutum a bakin tabki yana kwance yana da rashin lafiya har shekara talatin da takwas. 6Da Yesu ya gan shi yana kwance a wurin sai ya gane ya dade a wurin, sai ya ce masa, "Ko kana so ka warke?"7Sai mai rashin lafiyar ya amsa ya ce, "Malam, bani da kowa da zai sa ni a cikin tabkin idan ruwan ya motsa. Yayinda na ke kokari sai wani ya riga ni." 8Yesu ya ce masa," Ka tashi ka dauki shimfidarka ka tafi."9Nan dan nan Mutumin ya warke, ya dauki shimfidarsa ya tafi. Ranar kuwa Asabar ce.10Sai Yahudawa suka ce da wanda aka warkar din, "Ai, Asabar ce, bai kuwa halatta ka dauki shimfidarka ba." 11Sai ya amsa ya ce, "Ai wanda ya warkar da ni, shine ya ce mani 'Dauki shimfidarka, ka tafi."12Suka tambaye shi, "wane mutum ne ya ce maka, 'Dauki shimfidar ka yi tafiya'?" 13Sai dai, shi wanda aka warka din, ba san ko wanene ya warkar da shi ba, domin Yesu ya riga ya tafi aboye, saboda akwai taro a wurin.14Bayan haka, Yesu ya same shi a Haikalin, ya ce masa, "ka ga fa, ka warke. To, kada ka kara yin zunubi don kada wani abu da ya fi wannan muni ya same ka." 15Sai mutumin ya tafi ya gaya wa Yahuduwa cewa Yesu ne ya warkar da shi.16To saboda haka Yahudawa suka fara tsanantawa Yesu, don ya yi wadannan abubuwa ran Asabar. 17Yesu kuwa ya amsa masu ya ce, "Ubana yana aiki har yanzu, ni ma ina aiki." 18Saboda haka, Yahudawa suka kara nema su kashe shi ba don ya keta Asabar kadai ba, amma kuma domin ya ce Allah Ubansa ne, wato yana maida kansa dai-dai da Allah.19Yesu ya amsa masu ya ce, hakika hakika, ina gaya maku, Dan ba ya yin kome shi kadai, sai abin da ya ga Uba yana yi. 20Domin Uban na kaunar Dan, yana kuma nuna masa dukan abinda shi da kansa yake yi, kuma zai nuna masa abubuwan da suka fi wadannan, domin ku yi mamaki.21Gama kamar yadda Uba yakan tada matattu ya kuma basu rai, haka Dan ma yake bada rai ga duk wanda ya nufa. 22Gama Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya damka dukan hukunci ga Dan, 23domin kowa ya girmama Dan, kamar yadda suke girmama Uban. Shi wanda ba ya girmama Dan, ba ya girmama Uban da ya aiko shi.24Hakika, hakika, duk mai jin Maganata, yana kuma gaskata wanda ya aiko ni, yana da rai madawwami ba kuma za a kashe shi ba, domin ya ratse daga mutuwa zuwa rai,.25Hakika hakika, ina gaya maku, lokaci na zuwa, har ma ya yi da matattatu za su ji muryar Dan Allah, wadanda suka ji kuwa za su rayu.26Kammar yada Uba ya ke da rai a cikinsa, haka ya ba Dan don ya zama da rai cikin kansa. 27Uban ya kuma ba Dan ikon zartar da hukunci, saboda shi ne Dan Mutum.28Kada ku yi mamakin wannan, domin lokaci na zuwa da duk wadanda suke kaburbura za su ji muryarsa, 29su kuma fito: wadanda suka aikata nagarta zawa tashi na rai, wadanda suka aikata mugunta kuwa zuwa tashi na hukunci.30Ba na iya yin kome ni da kai na. Yadda na ke ji, haka nake yin hukunci, Hukunci na kuwa na adalci ne, domin ba nufin kaina nake bi ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni. 31Idan zan yi shaida game da kaina, shaidata baza ta zama gaskiya ba. 32Akwai wani wanda ya ke bada shaida game da ni, na kuwa sani shaidar da yake bayarwa game da ni gaskiya ce.33Kun aika zuwa wurin Yahaya, shi kuma ya yi shaidar gaskiya. 34Duk da haka shaidar da na karba bata mutum bace. Na fadi wadanan abubuwa domin ku sami ceto. 35Yahaya fitila ne mai ci, mai haske ne kuma, kun yarda ku yi farinciki da haskensa dan lokaci kadan.36Amma shaidar da ni ke da ita ta fi ta Yahaya karfi. Domin ayyukan da Uba ya bani ni in yi, wato ainihin ayyukan da nake yi, su ne suke shaida ta cewa, Uba ne ya aiko ni. 37Uba wanda ya aiko ni, shi da kansa ya shaide ni. Ba ku taba jin muryar sa ba, ko ganin kamanninsa. 38Maganarsa kuwa ba ta zaune a zuciyarku, domin baku gaskata da wanda ya aiko ni ba.39Kuna nazarin littattafai, don a tsammaninku a cikinsu za ku sami rai Madawwami, alhali kuwa su ne suke shaidata. 40kuma baku niyyar zuwa wurina domin ku sami rai.41Ba na karbar yabo daga wurin mutane, 42amma na sani baku da kaunar Allah a zuciyarku.43Na zo a cikin sunan Ubana, amma ba ku karbe ni ba. Idan wani ya zo da sunan kansa, za ku karbe shi. 44Ta yaya za ku ba da gaskiya, ku da kuke karban yabo daga junanku, amma ba ku neman yabon dake zuwa daga wurin Allah?45Kada ku yi tunani zan zarge ku a wurin Uba. Mai zargin ku shine Musa, wanda kuka sa begenku a cikin sa. 46Inda kun gaskata Musa, da kun gaskata da ni domin ya yi rubutu game da ni. 47Idan kuwa ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, ta yaya za ku gaskata maganata?"
Wannan ne abin da ya faru a labari na biye, wadda Yesu ya tafi Urushalima ya kuma warkad da mutum. Wadannan Ayoyin sun ba da ainahin bayani game da shirin labarin.
Wannan ya na nufin bayan Yesu ya warkad da ɗan ma'aikacin. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 3:22
"Yahudawan su na bikin idi"
Urashalima ya na kan tudu. Hanyoyi zuwa Urashalima su na tafiya sama da kasan ƙanƙanin tudu. Idan harshen ku ta na da wata hanya dabam na tafiya a kan tudu fiye da na tafiya a kan hanya, za ku iya yin amfani da shi a nan.
Wannan rami ne wadda mutane su ke cika da ruwa. Wata loƙaci suna bin su tabkin da tiles ko da aikin duse.
sunan wuri
jinkan gini wadda bango daya ya bata kuma ya na haɗe da su gini
"mutane dayawa"
"ya na tabkin Baitasda" (John 5:1)
"shekaru talatin da takwas"
"ya fahinci"
"Yesu ya ce wa mutum da ya cakume"
A nan kalmar "Mallam" hanya ce na magana da ladabi.
AT: "loƙacin da mala'ika ya motsa ruwan"
Wannan rami ne a kasa wadda mutane su ke cika da ruwa. Wata loƙaci suna bin su tabkin da tiles ko da aikin duse. Dubi yadda kun fasara "tabkin" a cikin 5:2.
"kullum wani dabam ya na riga ni shigan cikin ruwan"
"tashi tsaye"
"ɗauki shimfidarkuanar ka, ka yi tafiya!"
"mutumin ya samu lafiya kuma"
Marubucin ya yi amfani da kalmar "yanzu" domin ya nuna cewa kalmomin na bayani ne wadda ke biye.
Yahudawa (musamman shugabanin Yahudawa) sun yi fushi a loƙacin da sun ga mutumin ya dauki shimfidarsa a ranar Asabar.
"Ranar hutun Allah ce"
"mutumin da ya sa ni lafiya"
"Shugabanin Yahudawa su ka tambaye mutumin da an warkar da shi"
"Yesu ya same mutumin da ya warkar"
An yi amfani da kalmar "Dubi" a nan domin a jawo hankali zuwa kalmomin da zai bi.
Marubucin ya yi amfani da kalmar "yanzu" don ya nuna cewa kalmomin da suke biye ne ainahin bayanin.
Wannan ya na nufin yin aiki, tare da ko wane abu da ake yi don a bauta wa mutane.
A nan "Yahudawa" magana ce da ke wakilcin "shugabanin Yahudawa." AT: "shugabanin Yahudawa"
"cewa shi kamar Allah ne" ko kuma "cewa ya na da yawan iko kamar Allah"
Wannan muhimmin lakaɓi ne wa Allah.
Yesu ya cigaba da magana da shugabanin Yahudwa.
Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 1:51
"za ku gigice"
Yesu, Ɗan Allah, ya bi shugabancin Ubansa a duniya, domin Yesu ya san cewa Uban ya na kaunarsa.
Wadannan muhimmin lakabi ne wadda ya ke kwatanta dangantaka sakanin Yesu da Allah.
Irin kauna da ya ke zuwa daga Allah ya na duba kirkin wadansu, ko a loƙacin da bai amfane ku ba. Allah da kansa kauna ne kuma shi ne tushen kauna.
Wadannan muhimmin lakaɓi ne wadda ya ke kwatanta dangantaka sakanin Yesu da Allah.
Wannan ya na nufin "rai na ruhaniya."
Kalmar "gama" ya na nuna kwatanci. Ɗan Allah ya na yin hukunci wa Allah Uba.
Dole a girmama a kuma yabe Allah Ɗa kamar Allah Uba. Idan mun kasa girmama Allah Ɗa, to mun kuma kasa girmama Allah Uba.
A nan "magana" zance ne da ke wakilcin sakon Yesu. AT: "duk wanda ya ji sako na"
AT: "za a sharanta shi ya zama da gaskiya"
Muryar Yesu, Ɗan Allah, zai ta da matattu daga kabari.
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
Kalmar "gama" ya na nuna kwatanci. Ɗan Allah ya na da ikon ba da rai, kamar yadda Uban yake.
Wadannan muhimmin lakaɓi ne wadda ya ke kwatanta dangantaka sakanin Yesu da Allah.
Ɗan Allah ya na da ikon Allah Uba don ya yi hukunci.
"Wannan" ya nufin cewa Yesu, Ɗan Mutum, ya na da ikon ba da rai na har abada da kuma yin hukunci.
"ji murya na"
Kalmar "shi" ya na nufin Allah Uba.
Akwai wani kuma wanda ya na gaya wa mutane game da ni"
Wannan ya na nufin Allah.
"abin da ya ke gaya wa mutane game da ni gaskiya ne"
"ba na son shaidar mutum"
AT: "don Allah ya cece ku"
A nan "fitila" da "haske" zance ne. Yahaya ya koya wa mutanin game da Allah kuma wannan ya na nan kamar fitilar da yake haskaka haskensa a cikin duhu. AT: "Yahaya ya koya maku game da Allah kuma wannan ya na nan kamar fitila da ya ke haskaka haskensa. Abin da Yahaya ya ce a dan loƙaci kadan ne ya sa ku murna"
Allah Uba ya aiko Allah Ɗan, Yesu, a duniya. Yesu ya cika abin da Uban ya ba shi ya yi.
Kalmar "kansa" ya na bayyana cewa Uban ne, ba wani ne da kankancin muhimmi ne wadda ya shaida ba.
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
" baku gaskanta da wanda ya aiko ni ba. Haka ne na san cewa ba ku da maganarsa a cikinku"
Yesu ya yi magana game da yadda mutane suke rayuwa bisa maganar Allah kamar gidaje da kuma maganar Allah kamar mutum da ya ke zama a cikin gidaje. AT: "Ba ku rayuwa bisa maganarsa" ko kuma "ba ku biyayya da maganarsa"
"sakon da ya gaya maku"
"za ku samu rai madawwami idan kun karantasu" ko kuma "littafi zai gaya ma ku yadda za ku samu rai madawwami"
"kun ki ku gaskanta da sako na"
amsa
AT: 1) "ba ku kaunar Allah" ko kuma 2) "ba ku karbi kaunar Allah ba."
A nan kalmar "suna" magana ne da ke nuna ikon Allah. AT: "Na zo da ikon Ubana"
Kalmar "suna" magana ne da ke wakilcin iko. AT: "idan wani ya zo a ikonsa"
Wannan magana ya bayyana a matsayin tambaya domin karin nanaci. AT: "Ba yanda za ku gaskanta domin kun karbi yabo ... Allah!"
Wannan ya na nufin gaskanta da Yesu.
"Musa" a nan magana ne na doka da kansa. AT: "Musa ya yi zargin ku a cikin doka, doka da kun sa begenku"
"amincewar ku" ko kuma "gaskantawar ku"
Wannan magana ya bayyana a matsayin tambaya domin karin nanata. AT: "ba ku gaskanta da rubutun shi ba, don haka ba za ku taba gaskanta da maganganuta ba!"
"abin da na faɗa"
1Bayan waddannan abubuwa, Yesu ya ketare tekun Galili, wanda a ke kira tekun Tibariya. 2Sai taro mai yawa suka bi shi domin suna ganin alamu da yake yi akan marasa lafiya. 3Sai Yesu ya hau dutse ya zauna a can tare da almajiransa.4(Kuma da idin Ketarewa, wato idin Yahudawa, ya kusato.) 5Da Yesu ya daga kai sai ya ga babban taro yana zuwa wurinsa, sai ya ce ma Filibus, "Ina za mu sayi gurasar da Mutanen nan za su ci?" 6(Ya fadi haka ne domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi.)7Filibus ya amsa masa, "gurasar dinari biyu ma ba zata ishi kowannensu ya samu ko kadan ba." 8Daya daga cikin almajiransa, wato Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus, ya ce masa, 9"Ga wani dan yaro nan da dunkule biyar na sha'ir, da kifi biyu. Amma menene wadannan za su yi wa mutane masu yawa?"10Yesu ya ce, "ku sa mutane su zauna."( wurin kuwa akwai ciyawa.) Sai mazajen suka zauna, sun kai wajen dubu biyar. 11Sai Yesu ya dauki gurasar, bayan da ya yi godiya, sai ya rarraba wa wadanda suke zaune. Haka kuma ya rarraba kifin gwargwadon abin da zai ishe su. 12Da Mutanen suka ci suka kuma koshi, sai ya ce wa almajiransa, ku tattara gutsattsarin da suka rage, kada ya zama asara."13Sai suka cika kwanduna goma sha biyu da gutsattsarin gurasar nan biyar da ya rage bayan da kowa ya ci. 14Da jama'a suka ga alamar da ya yi, sai suka ce, "Hakika wannan shi ne annabin nan mai zuwa cikin duniya. 15"Da Yesu ya gane suna shirin zuwa su dauke shi da karfi da yaji su nada shi sarki, sai ya sake komawa kan dutsen da kansa.16Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara teku. 17Suka shiga cikin jirgi, suka haye teku zuwa kafarnahum. (A lokacin duhu ya yi, Yesu kuwa bai riga ya iso wurinsu ba tukuna.) 18Iska mai karfin gaske tana kadawa, kuma tekun yana hargowa.19Bayan da almajiran suka yi tuki na wajen kimanin mil ashirin da biyar ko talatin, sai suka hango Yesu yana tafiya a kan teku ya kuma kusa da jirgin, sai suka firgita. 20Amma ya ce masu, "Ni ne! kada ku firgita." 21Sa'an nan suka yarda suka karbe shi a cikin jirgin, kuma nan da nan jirgin ya kai gacci.22Kashe gari, sauran taron da suke tsaye a dayan hayin tekun suka ga cewa babu wani jirgi a wajen sai dayan, Yesu kuma bai shiga ciki da almajiransa ba, amma almajiransa suka tafi su kadai. 23Sai dai, akwai wadansu jirage da suka zo daga Tibariya kusa da wurin da taron suka ci gurasa bayan da Ubangiji ya yi godiya.24Sa'anda taron suka gane cewa Yesu da almajiransa ba su wurin, su da kansu su ka shiga cikin jiragen suka tafi Kafarnahum neman Yesu. 25Da suka same shi a hayin tekun, suka ce masa, "Mallam, yaushe ka zo nan?"26Yesu ya amsa masu, da cewa, "hakika, kuna nema na ne, ba don kun ga alamu ba, amma domin kun ci gurasar nan kun koshi. 27Ku daina yin wahala a kan neman abinci mai lalacewa, sai dai a kan abinci mai dawwama wanda zai kaiku ga rai madawwami wanda Dan Mutum zai ba ku, domin Ubangiji Allah ya sa hatiminsa a kansa."28Sai suka ce Masa, "Me za mu yi, domin mu aikata ayyukan Allah? 29Yesu ya amsa, "Wannan shi ne aikin Allah: wato ku gaskata da wanda ya aiko."30Sai suka ce masa, "To wace alama za ka yi, don mu gani mu gaskata ka? 31Me za ka yi? Kakanninmu sun ci manna a jeji, kamar yadda aka rubuta, "Ya ba su gurasa daga sama su ci."32Sa'an nan Yesu ya ce masu, "hakika, hakika, ina gaya maku ba Musa ne ya ba ku gurasa nan daga sama ba, amma Ubana ne ya baku gurasa ta gaskiya daga sama. 33Gurasar Allah itace mai saukowa daga sama mai kuma bada rai ga duniya," 34Sai suka ce masa, "Mallam, ka rika ba mu irin wannan gurasa kodayaushe."35Yesu ya ce masu, "Ni ne gurasa mai ba da rai. Wanda ya zo wurina ba zai ji yunwa ba, wanda kuma ya gaskanta da ni ba zai kara jin kishi ba. 36Amma na gaya maku cewa, hakika kun gan ni, duk da haka ba ku ba da gaskiya ba. 37Duk wanda Uba ya bani zai zo gare ni, wanda kuwa ya zo gare ni ba zan kore shi ba ko kadan.38Gama na sauko daga sama, ba domin in bi nufin kaina ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni. 39Wannan shi ne nufin wanda ya aiko ni, kada in rasa ko daya daga cikin wadannan da ya bani, sai dai in tashe su a ranar karshe. 40Gama wannan shi ne nufin Ubana, duk wanda yake ganin Dan ya kuma gaskata da shi zai sami rai madawwami, ni kuma zan tashe shi a ranar karshe.41Sai Yahudawa suka yi gunaguni akansa, domin ya ce, "Nine Gurasar da ta sauko daga sama." 42Suka ce, "Ba wannan ne Yesu Dan Yusufu, wanda Ubansa da Uwarsa mun san su ba? Ta yaya yanzu zai ce, 'Na ya sauko daga sama'?43Yesu ya amsa, ya ce masu, "Kada ku yi gunaguni a junanku. 44Ba mai iya zuwa wurina sai dai in Uba wanda ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta karshe. 45A rubuce yake cikin litattafan anabawa cewa, 'Dukkansu Allah zai koya masu'. Duk wanda ya ji ya kuma koya daga wurin Uba, ya kan zo gare ni.46Ba cewa wani ya taba ganin Uban ba, sai shi wanda yake daga wurin Allah - shine ya ga Uban. 47Hakika, hakika, wanda ya bada gaskiya, yana da rai Madawwami.48Ni ne Gurasa ta rai. 49Ubanninku sun ci manna cikin jeji, suka kuma mutu.50Ga gurasa da ta sauko daga sama, domin mutum ya ci daga cikinta ba kuwa zai mutu ba. 51Ni ne gurasa mai rai da ya sauko daga sama. Duk wanda ya ci daga gurasar, zai rayu har abada. Wannan gurasar da zan bayar jiki na ne don ceton duniya."52Sai Yahudawa suka fusata a tsakanin junansu suka kuma fara gardama, cewa, "Yaya mutumin nan zai iya bamu naman jikinsa mu ci? 53Sai Yesu ya ce masu, "hakika, hakika, in ba ku ci naman jikin Dan mutum ba, ba ku kuma sha jininsa ba, ba za ku sami rai a cikin ku ba.54Dukan wanda ya ci nama na ya kuma sha jinina yana da rai Madawwami, ni kuwa zan tashe shi a ranar karshe. 55Domin namana abinci ne na gaske, jinina kuma abin sha ne na gaskiya. 56Duk wanda ya ci namana, ya kuma sha jinina yana zamne a ciki na, ni kuma a cikinsa.57Kamar yadda rayayyen Uba ya aiko ni, nake kuma rayuwa saboda Uban, haka ma wanda ya ci namana, zai rayu sabo da ni. 58Wannan itace gurasar da ta sauko daga sama, ba irin wadda Ubanninku suka ci suka mutu ba. Dukan wanda ya ci gurasar zai rayu har abada." 59Yesu ya fadi wadan nan abubuwa a cikin majami'a sa'ad da yake koyarwa a Kafarnahum.60Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, "Wannan Magana yana da karfi, wa zai iya jinta?" 61Yesu, kuwa da yake ya sani a ransa da cewa almajiransa suna gunagunin wannan, sai ya ce masu, "Wannan ya zamar maku laifi?62Yaya Ke nan in kun ga Dan Mutum yana hawa inda yake a da? 63Ruhu shine mai bayar da rai; Jiki ba ya amfana komai. Kalmomin da na fada maku ruhu ne, da kuma rai.64Amma fa akwai wadansun ku da ba su ba da gaskiya ba. Domin tun farko Yesu ya san wadanda ba su ba da gaskiya ba, da kuma wanda zai bashe shi. 65Ya fada cewa, "shiyasa na gaya maku, ba mai iya zuwa wurina, sai ta wurin Uban."66Bayan haka, da yawa daga cikin almajiransa suka koma da baya, ba su kara tafiya tare da shi ba. 67Sai Yesu ya ce wa goma sha biyun, "ku ba kwa so ku tafi, ko ba haka ba? 68Bitrus ya amsa masa ya ce, "Ya Ubangiji, gun wa za mu je? kai kake da maganar rai madawwami. 69Mu kwa mun gaskata mun kuma sani kai ne mai tsarkin nan na Allah."70Yesu ya ce masu, "Ba ni na zabe ku, goma sha biyu ba, amma dayanku Iblis ne?" 71Wato yana magana akan Yahuda dan Siman Iskariyoti, shi kuwa daya daga cikin sha-biyun ne, wanda zai ba da Yesu.
Yesu ya yi tafiya daga Urushalima zuwa Galili. Taru suka bi shi zuwa saman dutse. Waɗɗannan Aya suna faɗan shirin wannan sashin labarin.
Jumlan "waɗɗannan abubuwa" ya na nufin abubuwan da ya faru a cikin 5:1-46 ya kuma gabatar da abin da zai faru a gaba.
Ya nuna a cikin littafin cewa Yesu ya yi tafiya a kwalekwale ya kuma dauki al'majiransa tare da shi. AT: "Yesu ya yi tafiya da al'majirinsa a kwalekwale"
"mutane da yawa"
Wannan ya na nufin abubuwan al'ajibi da an yi amfani a matsayin shaida cewa Allah ne mai iko wadda ya ke da cikakken iko a komai.
Yahaya ya daina faɗa wa mutane game da abin da zai faru a labarin domin ya ba da tushin bayani game da loƙacin da abin ya faru.
Yahaya ya daina faɗa wa mutane game da abin da zai faru a labarin domin ya bayyana dalilin da Yesu ya tambaye Filibus wurin da za a saya burodi.
Kalmar "kansa" ya bayyana cewa kalmar "shi" ya na nufin Yesu. Yesu ya san abin da zai yi.
Kalmar "dinari" da ya ne da "su dinari." AT: "kuɗin burodi da ya kai kuɗin aikin kuanaki dari"
"dunƙule biyar na sha'ir." Sha'ir sananne abinci ne.
Ana gasa dunƙulan burodi da ya na da siffa. Mai yiwuwa kananan mulmulallen dunƙule ne.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya nanata cewa ba su da abinci da za su ciyad da kowa. AT: "wadannan dunƙule da kifi ba za su isa a ciyad da mutane dayawa ba!"
"kwanta"
Yahaya ya daina faɗa wa mutane game da abin da zai faru a labarin domin ya ba da tushen bayani game da wurin da abin ya faru.
Bayan mai yiwuwa taron ta shafi mata da 'ya'ya 6:4-5, Yahaya ya na kirga mazaje na kadai anan.
Yesu ya yi addu'a wa Allah Uba, ya kuma gode masa da kifi da kuma su dunƙule.
a nan "ya" yana wakilcin "Yesu da al'majiransa." AT: "Yesu da al'majiransa su ka ba da shi"
"al'majiran sun tara"
abincin da ba wadda ya taba ci
Ciyad da mutane dubu biyar da dunƙule da kuma kifi biyu da Yesu ya yi
annabin na musamman da Musa ya ce zai zo cikin duniya.
Wannan ne abu na biye a cikin labarin. Al'majiran Yesu sun fita zuwa rafi a cikin kwalekwale.
Yi amfani da yadda harshenku ya na nuna cewa wannan ne tushen bayani.
Kwalekwale ya na yawan kasance da mutane biyu, hudu, ko shida da suke tuki da matuki a kowane gefe. Al'adunku na iya samu hanya dabam na sa kwalekwale ya haye ruwa.
"filin wasanni" na da tsawo 185. AT: "wajen mita biyar ko shida"
"daina jin tsoro!"
Wannan ya na nufin cewa Yesu ya shiga cikin kwalekwale. AT: "sun karbe shi zuwa cikin kwalekwale da farinciki"
"Tekun Galili"
Yi amfani da yadda harshen ku ya ke nuna cewa wannan ne tushen bayani.
A nan, Yahaya ya kara ba da tushen bayani. Washegari, bayan Yesu ya ciyad da mutane, wadansu jirage da mutane daga Tibariya sun zo su ga Yesu. Ko da shike, Yesu da al'majiransa sun tafi a cikin daren.
Dubi yadda an fasara wannan a cikin 1:51.
Allah Uba ya ba da izini wa Yesu, Ɗan Mutum, don ya ba da rai madawwami ga wanda sun gaskanta da shi.
Waddannan muhimmin laƙani ne da ya ke kwatanta dangantaka a sakanin Yesu da Allah.
"sa hatimi" a abu ya nufin saka alama don ya nuna mai shi. Wannan ya na nufin cewa Ɗan na Uban ne kuma Uban ya yarda da shi a komai.
"Kakanninmu"
Wannan ya na nufin wurin da Allah ya ke.
" gurasa ta gaskiya" magana ce game da Yesu. AT: "Uban ya na ba ku Ɗan a matsayin gurasa ta gaskiya daga sama"
Wannan muhimmin laƙani ne wa Allah.
"ba da rai na ruhaniya ga duniya"
A nan "duniya" magana ne na dukkan mutane da suke gaskanta da Yesu.
Yesu ya kwatanta kansa da gurasa ta wurin gurasan. Kamar yadda gurasa ya na da amfani a rayuwa, Yesu ya na da amfani don rai na ruhaniyar mu. AT: "Kamar yadda abinci yake sa ku rayu, Zan iya ba ku rai ta ruhaniya"
Wannan ya na nufin gaskanta cewa Yesu ne Ɗan Allah, yarda da cewa shi ne mai ceto, da kuma yi rayuwa a hanyar da zai girmama shi.
Allah Uba da kuma Allah Ɗa zai cece wadda sun gaskanta da shi har abada.
Wannan muhimmin laƙani ne wa Allah.
Wannan Jumla ya bayyana abin da ba shi ne yake nufi ba domin nanaci. AT: "Zan ajiye duk wanda ya zo wuri na"
"Uba na, wadda ya aiko ni"
An yi amfani da karin magana domin a bayyana cewa Yesu zai ajiye duk wadda Allah ya ba shi. AT: "In ajiye dukkansu"
A nan tashi karin magana ne na sa mutumin da ya mutu ya kuma rayu kuma. AT: "zan sa su su rayu kuma"
yi magana da rashin farinciki
Kamar yadda gurasa na da amfani a rain mu, haka ne Yesu ya na da amfanai a rai na ruhaniyarmu. Dubi yadda an fasara wannan a cikin 6:35. AT: "Ni ne wadda yake kamar gurasan gaskiya"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya bayana cewa shugabanin Yahudawa ba su yarda cewa Yesu dabam ba ne ba. AT: "Wannan Yesu ne, dan Yusuf, wadda Ubansa da Uwarsa mun sani!
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya bayana cewa shugabanin Yahudawa ba su yarda cewa Yesu ya zo daga sama ba. AT: "Ya na karya ne a lokacin da ya ce ya zo daga sama!"
Wannan karin magana ne. AT: "sa shi ya rayu kuma"
AT: 1) "ja 2) "jawo hankali."
AT: "annabawan sun rubuta"
Yahudawa su na zato cewa Yesu "ɗan Yusuf ne" (See: John 6:42, amma shi ne Ɗan Allah saboda Uban shi ne Allah, ba Yusuf ba. Waddanda sun koya daga Allah Uba sun gaskanta da Yesu, wadda shi ne Allah Ɗa.
Ko da shike ba bu mutum da ke raye a duniya da ya ga Allah Uba, Yesu, Ɗan Allah, ya gan Uban.
Allah ya na ba da "rai Madawwami" ga wadda sun gaskanta da Yesu, Ɗan Allah.
"Kakanninku"
Wannan ya na nufin asalin mutuwa.
A nan "gurasa" magana ne da ya ke nuna Yesu wadda shi ne mai ba da rai na ruhaniya kamar yadda gurasa ya na rike rai. AT: "Ina nan kamar gurasar gaskiya"
"rayu har abada." A nan kalmar "mutu"ya na nufin mutuwa ta ruhaniya.
Wannan ya na nufin "gurasa da ya ke sa mutane su rayu" (John 6:35).
A nan "duniya" magana ne da ke wakilcin rayuwar dukkan mutane a cikin duniya. AT: "cewa zai ba da rai ga dukkan mutane a cikin duniya"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya bayyana cewa shugabanin Yahudawa ba su yarda da abin da Yesu ya ce game da "namansa" ba. AT: "Ba bu yadda wannan mutum zai ba mu namansa mu ci!"
A nan su jumlolin "ci nama" da " sha jinina" karin magana ne da ya ke nuna yadda gaskanta da Yesu, Ɗan Mutum, yake kamar karban abinci da ruwa na ruhaniya. AT: "karɓa Ɗan Mutum kamar yadda ku na karɓan abinci da ruwa"
"ba za ku karɓi rai na har abada ba"
Su jumlan "ci nama" da " sha jinina" karin magana ne. Kamar yadda wani ya na son abinci da ruwa domin ya samu rai, waddanda sun gaskanta da Yesu za su samu rai na ruhaniya. AT: "Duk wanda ya gaskanta da ni don abincin ruhaniyarsu da kuma ruwa za su samu rai na har abada"
"a ranar da Allah zai hukunta kowa"
Kalmomin "abinci ne na gaske" da kuma "sha ne na gaskiya" maganganu ne da yake nufin cewa Yesu ya tanada abincin ruhaniya da ruwan sha wa waddanda sun gaskanta da shi. Karban Yesu a bangaskiya ya na tanada rai na har abada kamar yadda abinci da ruwan sha ya ke amfana jiki. AT: "Ni ce abincin ruhaniya ta gaskiya da kuma ruwan sha"
"na da dangantaka na kusa da ni"
"wadda ya gaskanta da ni"
AT: 1) "Uban da yake ba da rai" ko kuma 2) "Uban da yake rayayye."
"Gurasan" misali ne wa Yesu, wadda ya zo daga sama. AT: "Ina nan kamar gurasa da ya zo daga sama"
Wannan zance ce. Wadda sun yarda da Yesu domin rai na ruhaniyarsu suna nan kamar wadda suke dogara a kan gurasa ko abinci don rayuwarsu. AT: "Duk wadda ya yarda da ni"
"kakanin"
A nan Yahaya ya ba da tushen bayani game da loƙacin da abin ya faru.
Wannan magana ya bayyana a matsayin tambaya domin ya bayana cewa al'majiran sun sha wuyan fahimtar abin da Yesu ya faɗa. AT: "ba bu wadda zai karbe shi!" ko kuma "ya na da wuyan ganewa!"
"Wannan ya ba ku mamaki?" ko kuma "Wannan ya dame ku?"
Yesu ya ba da wannan magana a matsayin tambaya domin ya bayyana cewa al'majiransa za su ga wadansu abubuwa da suke da wuyan fahimta. AT: "Sai ba za ku san abin da za ku yi tunani ba a loƙacin da kun gan ni, Ɗan Mutum, hawa cikin sama!"
Kalmar "amfana" ya na nufin sa abubuwa masu kyau su faru.
AT: 1)kalmomin Yesu a cikin 6:32-58 ko kuma 2) komai da Yesu ya koyar.
"Abin da na faɗa maku"
AT:1) "na game da Ruhu da kuma rai na har abada" ko kuma 2) "na daga Ruhu kuma su na ba da rai" ko kuma 3) "na game da abubuwan ruhaniya da rai."
A nan Yahaya ya ba da tushen bayani game da abin da Yesu ya san zai faru.
Dole ne duk wadda yake so ya gaskanta ya zo wurin Allah ta Ɗan. Allah Uba ne kadai ya na yarda mutane su zo wurin Yesu.
"bi ni ku kuma karbi rai na har abada"
Muhimmin Bayani:
Yesu ya tafi wurare da kafa, gaskiya ne cewa ba su yi tafiya a wurin da ya tafiya ba, amma mai sauraran ya gane cewa wannan magana ya na nuna cewa bai so a ji abin ya ke so ya faɗa ba.
Siman Bitrus ya ba da wannan magana a matsayin tambaya domin ya bayyana cewa ya na so ya bi Yesu kadai. AT: "Ubangiji, ba za mu iya bin wanna ba sai kai!"
A nan "al'majiransa" ya na nufin muhimmin kungiyar mutane da sun bi Yesu.
Wannan bayani ne na "al'majira sha biyun," takamaiman mutane sha biyu da sun bi Yesu don hidimarsa. "al'majira sha biyun"
Yesu ya ba da wannan magana a matsayin tambaya domin ya jawo hankali ga cewa ɗaya daga cikin al'majiransa zai bashe shi. AT: "Na zabe ku da kaina, da haka wani a cikinku bawan shaidan nen!"
1Bayan wadannan abubuwa Yesu ya zagaya cikin Gallili, saboda baya so ya shiga cikin Yahudiya domin Yahudawa suna shirin su kashe shi. 2To Idin Bukkoki na Yahudawa ya kusa.3Sai 'yan'uwansa suka ce da shi, "ka tashi ka tafi Yahudiya, domin almajiranka su ga ayyukan da kake yi su ma. 4Ba wanda ya ke yin wani abu a boye idan dai yana so kowa da kowa ya san shi. Da yake ka na yin wadannan abubuwa sai ka nuna kan ka a fili ga duniya.5Domin ko 'yan'uwansa ma basu bada gaskiya gare shi ba. 6Yesu ya ce dasu, "lokaci na bai yi ba tukuna, amma ku koyaushe lokacin ku ne. 7Duniya baza ta iya kin ku ba, amma ta ki ni saboda ina fadin cewa ayyukanta ba su da kyau.8Ku ku je wurin idin, ni ba zan je wurin idin ba domin lokacina bai yi ba tukuna. 9Bayan da ya gaya masu wadannan abubuwa, ya tsaya a cikin Gallili.10Amma bayan da 'yan'uwansa su ka tafi wurin idin shi ma ya tafi, amma a asirce ba a fili ba. 11Saboda Yahudawa suna neman sa a wurin idin, su na cewa "Ina yake?"12Akwai maganganu dayawa a kansa cikin taron. Wadansu suna cewa, "shi mutumin kirki ne." Wadansu kuma suna cewa,"A'a yana karkatar da hankalin jama'a." 13Amma duk da haka ba wanda ya yi magana a fili a kansa saboda suna jin tsoron Yahudawa.14Sa'anda aka kai rabin idin, sai Yesu ya shiga cikin haikali ya fara koyarwa. 15Yahudawa suna mamaki suna cewa,"Yaya aka yi wannan mutum ya sami ilimi dayawa haka? Shi kuwa bai je makaranta ba." 16Yesu ya ba su amsa ya ce,"Koyarwata ba tawa ba ce, amma ta wanda ya aiko ni ce."17Idan wani yana so ya yi nufinsa, za ya gane koyarwannan ko daga wurin Allah ta zo, ko ko tawa ce ta kaina. 18Ko wanene yake maganar kansa, yana neman darajar kansa kenan, amma ko wanene ya nemi darajar wanda ya aiko ni, wannan mutum mai gaskiya ne, babu rashin adalci a cikin sa.19Ba Musa ya baku dokoki ba? Amma duk da haka ba mai aikata dokokin. Me yasa ku ke so ku kashe ni? 20Taron suka ba shi amsa, "Ka na da aljani. Wanene yake so ya kashe ka?"21Yesu ya amsa ya ce masu, "Nayi aiki daya, dukan ku kuna mamaki da shi. 22Musa ya baku kaciya, {ba kuwa daga Musa take ba, amma daga kakannin kakanni ta ke}, kuma a ranar Asabar kukan yi wa mutum kaciya.23Idan mutum ya karbi kaciya ranar Asabar, domin kada a karya dokar Musa, don me kuka ji haushi na saboda na mai da mutum lafiyayye sarai ranar Asabar? 24Kada ku yi shari'a ta ganin ido, amma ku yi shari'a mai adalci."25Wadansun su daga Urushalima suka ce, "wannan ba shine wannan da suke nema su kashe ba?" 26Kuma duba, yana magana a fili, sannan ba wanda ya ce da shi komai. Ba zai yiwu ba mahukunta su sani cewa wannan Kristi ne, ko ba haka ba? 27da haka, mun san inda wannan mutum ya fito. Amma sa'anda Kristi za ya zo, ba wanda zai san inda ya fito."28Yesu yayi magana da karfi a haikali, yana koyarwa ya na cewa, "Kun san ni kuma kun san inda na fito. Ban zo domin kaina ba, amma wanda ya aiko ni mai gaskiya ne, ku kuwa baku san shi ba. 29Ni na san shi domin daga wurinsa na fito, kuma shine ya aiko ni."30Suna kokari su kama shi, amma ba wanda ya iya sa masa hannu domin sa'arsa ba ta yi ba tukuna. 31Duk da haka wadansu dayawa a cikin taron suka bada gaskiya gare shi suka ce,"Sa'anda Kristi ya zo, zai yi alamu fiye da wadanda wannan mutum ya yi?" 32Farisawa suka ji tattarmukan suna yin rada a kan wadannan abubuwa game da Yesu, Sai manyan malamai da Farisawa su ka aika jami'ai su kama shi.33Sa'annan Yesu yace ma su," jimawa kadan ina tare ku, sa'annan in tafi wurin wanda ya aiko ni. 34Za ku neme ni ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba."35Yahudawa fa su ka cewa junan su, "Ina wannan mutum zai je inda ba za mu iya samun sa ba? Ko za ya tafi wurin Helinawa na warwatsuwa ya koyawa Helinawa? 36Wace kalma ya ke fadi haka, 'za ku neme ni amma ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba'?"37To a rana ta karshe, babbar rana ta idin, Yesu ya mike ya yi magana da karfi cewa, "Idan kowa yana jin kishi, ya zo wuri na ya sha. 38Shi wanda ya bada gaskiya gare ni kamar yadda nassi ya fadi, daga cikin sa rafukan ruwa na rai za su bulbulo."39Amma ya fadi haka a kan Ruhu, wanda wadanda suka bada gaskiya gare shi za su karba; ba a ba da Ruhun ba tukuna, saboda ba a rigaya an daukaka Yesu ba.40Wadansu a cikin taron, sa'anda suka ji wadannan kalmomi, suka ce, "Wannan lallai annabi ne." 41Wadansu suka ce, "Wannan Almasihu ne." Amma wadansu suka ce, "Almasihu zai fito daga Gallili ne? 42Ba nassi ya ce Almasihu zai fito daga cikin dangin Dauda daga Baitalami ba, daga kauyen da Dauda ya fito?43Sai aka sami rabuwa a cikin taron saboda shi. 44Da wadansun su sun kama shi, amma ba wanda ya sa masa hannu.45Sa'annan jami'an suka dawo wurin manyan Fristoci da Farisawa, wadanda suka ce," me yasa ba ku kawo shi ba?" 46Jami'an su ka amsa, "Ba mutumin da ya taba yin magana kamar haka."47Farisawa suka amsa masu, "kuma an karkatar da ku? 48Ko wani daga cikin mahukunta ya bada gaskiya gare shi, ko kuwa daga cikin Farisawa? 49Amma wannan taro da basu san shari'a ba, la'anannu ne."50Nikodimus ya ce masu, (shi wanda ya zo wurin Yesu da, daya daga cikin Farisawa), 51" Ko shari'armu bata hana hukunta mutum ba, sai ta ji daga gare shi ta kuma san abin da ya aikata ba?" 52Suka amsa masa suka ce,"kai ma daga Galili ka fito? Ka yi bincike ka gani ba annanbin da zai fito daga Galili."53Daga nan sai kowa ya tafi gidansa.
Yesu ya na magana wa 'yan'uwansa a cikin Galili. Waddannan sura su na magana game da loƙacin da abin ya faru.
Waɗɗannan kalmomin ya gaya wa mai sauraran cewa marubucin zai fara magana game da sabon abu. "Bayan ya gama magana da al'majiransa" (See: John 6:66-71) ko kuma "da saran loƙaci"
Ya kamata mai saurara ya gane cewa mai yiwuwa Yesu ya yi tafiya ne ba kuwa ya hawo mota ko dabba ba.
A nan "Yahudawa" magana ne na "shugabanin Yahudawa." AT: "shugabanin Yahudawa su na shirin su kashe shi"
"Yanzu loƙacin idin Yahudawa ya yi kusa"
Wannan ya na nufin ainahin kananan 'yan'uwanin Yesu, 'ya'yan Maryamu da Yusuf.
Kalmar "ayyuka" ya na nufin abin mamaki da Yesu ya yi.
Kalmar " kansa" magana ne da ke bayyana kalmar "shi."
A nan "duniya" magana ne game da dukkan mutane a cikin duniya. AT: "dukkan mutane" ko "kowane mutum"
Wannan maganan fashi ne daga ainahin labarin kamar yadda Yahaya ya gaya mana tushen bayanin game da 'yan'uwan Yesu.
"kananun 'yan'uwansa"
Kalmar "loƙaci" karin magana ne. Yesu ya na nufin cewa loƙaci bai kai da zai gama hidimarsa ba. AT: " loƙaci bai kai da zan daina aiki na ba"
"kowane loƙaci ya na da kyau maku"
A nan "duniya" magana ne game da mutane da suke cikin duniya. AT: "Dukka mutane a duniya ba za su iya ki ka ba"
"ina faɗa masu cewa abin da suke yi ba bu kyau"
Yesu ya cigaba da magana da 'yan'uwansa.
A nan Yesu ya na nufin cewa idan ya tafi Urushalima, zai kawo aikinsa ga karshe. AT: "loƙaci na bai kai tukuna da zan tafi Urushalima ba"
'Yan'uwannan ne kannen Yesu.
Urushalima ya na tudu fiye da Galili, wurin da Yesu da 'yan'uwansa suke adda.
Waɗɗannan jumla su na nufin abu ɗaya. Ana sake nanata maganan domin bayani. AT: "ɓoyeyye sosai"
A nan kalmar "Yahudawa" karin magana ne na "shugabanin Yahudawa." kalmar "sa" ya na nufin Yesu. AT: "Shugabanin Yahudawa suna neman Yesu"
Wannan ya na nufin rashin daɗi da mutum ya ke da shi a loƙacin da akwai kurarin lahani a kansa ko kuma wasu.
Kalmar "Yahudawa" magana ne na shugabanin Yahudawa da suke hamayya da Yesu. AT: "shugabanin Yahudawa"
A nan "karkatar" na nufin a rinjaye mutum ya gaskata da abinda ba gaskiya bane. AT: "ya rinjaye mutanin"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya bayana mamakin da shugabanin Yahudawa sun yi akan cewa Yesu ya na da sani sosai .
"amma ya na zuwa daga Allah, wanda ya aiko ni"
"loƙacin da mutum ya na so ya girmama wadda ya aiko shi kadai, mutumin ya na faɗan gaskiya ne. Ba ya karya"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya kara bayani. AT: "Musa ne ya ba ku dokan"
"bi doka"
Yesu ya daidaita muradin shugabanin Yahudawa da suke so su kashe shi domin ya karye dokan Musa. Ya na nufin cewa shugabanin da kansu ba su bin dokan. AT: "Ku na karye dokan da kanku kuma ku na so ku kashe ni!"
"Wannan ya nuna cewa kai mahaukaci ne, ko kuma aljani ya na mulki da kai!"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya kara bayani. AT: "ba bu wadda ya ke so ya kashe ka!"
"abin al'ajibi daya" ko "alama ɗaya"
"dukkanku kun gigice"
Yahaya ya kara tanada karin bayani anan game da kaciya.
Yesu ya na nufin cewa yin kaciya ya na tare da aiki. AT: "kun yi wa ɗa na miji kaciya a ranar Asabar. Wannan ma aiki ce"
"a ranar hutun Yahudawa"
"Idan kun yi wa ɗa na miji kaciya a ranar Asabar domin kada ku karye dokar Musa"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya kara bayani. AT: "kadda ku yi fushi da ni domin na sa mutum lafiya a ranar Asabar!"
Yesu ya na nufin cewa kada mutane su zaba abin da ba daidai ba, amma su tsaya akan abin da su na iya gani. A kowane ayuka akwai wani muradi da ba a iya gani. AT: "Daina hukunta mutane bisa abin da ku na iya gani! Ku fi hankali da abin da ke daidai bisa ga Allah"
Wannan magana ya bayyana a matsayin tambaya ne domin karin bayani. AT: "Wannan Yesu ne wadda suke nema su kashe shi!"
Wannan yana nufin cewa shugabanin Yahudawa basu yin hamaiya da Yesu. AT: "ba su faɗa komai na hamayya da shi ba"
Wannan magana ya bayyana a matsayin tambaya ne domin karin bayani. AT: "Watakila sun yarda da gaskiye cewa shi ne Mai ceto!"
"yi magana da murya mai karfi"
Yesu da mutanin su na cikin faɗan haikali. AT: "a cikin fadan haikali"
Yahaya ya yi amfani da karin magana a cikin wannan jumla. Mutanin sun gaskanta cewa Yesu daga Nazarat ne. Ba su san cewa Allah ne ya aike shi daga sama ba kuma an haife shi a cikin Baitalami. AT: "Dukkan ku kun san ni kuma ku na tunani cewa kun san wurin da na fito"
"akan iko na." Dubi yadda kun fasara "na kansa" a cikin 5:19.
"Allah ne wadda ya aiko ni kuma shi gaskiya ne"
Kalmar "sa'ar" magana ne da ya ke wakilcin loƙacin da ya kamata a kama Yesu, bisa shirin Allah. AT: "ba loƙacin da ya kamata su kama shi ba ne"
Wannan magana ya bayyana a matsayin tambaya ne domin karin bayani. AT: "A loƙacin da Almasihu zai zo, hakika ba zai iya yin alamu fiye da wadda wannan mutumin ya yi ba!"
Wannan ya na nufin abin al'ajibi da ya nuna cewa Yesu ne Almasihu.
"Zan kasance tare da ku na da dan loƙaci kadan"
A nan Yesu ya na nufin Allah Uba, wadda ya aike shi.
"ba za ku iya zuwa wurin da na ke ba"
"Yahudawa" karin magana ne da ke wakilcin shugabanin Yahudawa da suka yi hamayya da Yesu. AT: "shugabanin Yahudawa sun faɗa a sakaninsu"
Wannan ya na nufin Yahudawa da aka baza su a duniyar Greek, a wujen Falistiyawa.
Wannan "kalma" magana ne da ya ke nufin sakon da Yesu ya bayar, wadda shugabanin Yahudawa sun kasa ganewa. AT: "Me ne ya na magana a kai a loƙacin da ya ce"
"babba" ce domin shi ne karshe, ko kuma muhimmin, ranar idi.
A nan kalmar "shi" magana ne da yake nufin yawan son abubuwan Allah, kamar yadda mutum yake "kishi" ruwa. AT: "Waddanda su ke son abubuwan Allah kamar yadda mutum mai kishi yake son ruwa"
Kalmar "sha" magana ne da yake nufin karɓan rai na ruhaniya da Yesu ya tanada. AT: "Ya zo wuri na don ya kashi ƙishirwa ta ruhaniya"
"kamar yadda littafi ya faɗi game da kowane mutum da ya gaskanta da shi"
"rafukan ruwa na rai za su bulbulo" magana da yake wakilcin rai da Yesu ya tanada wa waddanda suke "ƙishirwa" ta ruhaniya. AT: "rai na ruhaniya zai bulbulo kamar rafukan ruwa"
AT: 1) "ruwa da yake ba da rai" ko kuma 2) "ruwa da ya na sa mutane su rayu."
A nan ciki ya na wakilcin cikin mutum, musamman sashen mutum da ba ya bayyane. AT: "daga cikin shi" ko kuma " daga zuciyarsa"
A nan "ya" ya na nufin Yesu.
Yahaya ya na nufin cewa Ruhu zai zo daga baya don ya yi rayuwa a cikin wanda sun gaskanta da Yesu. AT: "Ruhu bai riga ya zo don ya yi rayuwa a cikin masubi ba"
A nan kalmar " daukaka" ya na nufin loƙacin da Allah zai girmama Ɗan bayan mutuwarsa da tashinsa.
Da faɗan wannan, mutanin su na nuna cewa sun gaskanta cewa Yesu ne annabi kamar Musa da Allah ya yi alkawari zai aiko. AT: "Wannan lallai annabi ne wadda yake kamar Musa da muke ta jira"
Wannan magana ya bayyana a matsayin tambaya ne domin karin bayani. AT: "Almasihun ba zai iya zuwa daga Galili ba!"
Wannan magana ya bayyana a matsayin tambaya ne domin karin bayani. AT: "Littafi ya koya cewa Almasihu zai zo daga layin Dauda kuma daga Baitalami, daga kauyen da Dauda ya fito!"
Ana maganar littafi kamar su na iya magana yadda mutum ya na magana. AT: "Annabawa sun rubuta a cikin littafi"
"inda Dauda ya yi rayuwa"
Taron ba su iya yarda da menene ko wanene Yesu ba.
Sa hanu a akan mutum karin magana ne da ke nufin a kama shi ko kuma jingina akan wani abu. AT: "amma ba bu wadda ya ƙwace shi don a kama shi"
"masu tsaron haikali"
Yan Jami'an sun zuguiguita domin su nuna farin cikinsu ga abin da Yesu ya ce. Za ku iys sa a bayyane cewa Jami'an ba su ce sun san komai da kowane mutum a dukkan loƙaci da wurare sun taɓa faɗa ba. "Ba mu taɓa gin wani ya faɗa irin wannan abin ban mamaki kamar wannan mutum ba!"
"Domin sun faɗa cewa, Farisawa"
"amsa Jami'an"
Wannan magana ya bayyana a matsayin tambaya ne domin karin bayani. Farisawa sun yi mamakin amsan Jami'an. AT: "An karkatar da ku ma!"
Wannan magana ya bayyana a matsayin tambaya ne domin karin bayani. AT: "Ba bu wani daga mahukunta ko Farisawa da sun gaskanta da shi!"
Wannan daga dokan Farisawa ne ba dokar Musa ba.
"Ga wannan taro da basu san doka ba, Allah zai sa su halaka!"
Yahaya ya ba da wannan bayani domin ya tunashar da mu game da Nikodimus. Harshen ku na iya samun wata hanyar nuna tushen bayani.
Wannan magana ya bayyana a matsayin tambaya domin karin bayani. AT: "shari'ar mu na Yahudawa bai yarda mana mu hukunta mutum ba ... abin da ya aikata!"
A nan Nikodimus ya yi maganan shari'a kamar mutum ne. Idan wannan ba ya al'adan harshenku, za ku iya fasara ta da wata kalma. AT: "Mu na hukunta mutum" ko "Ba mu hukunta mutum"
shugabanin Yahudawa sun san cewa Nikodimus ba daga Galili ba ne. Sun yi masa wannan tambaya don su yi masa ba'a. AT: "Kai daya daga cikin mutanin baya ne daga Galili!"
Wannan karin magana ne. Za ku iya sa bayani da ba bu a nan. AT: "Yi bincike da kyau a kuma yi karantun abin da an rubuta a cikin littatafe"
Mai yiwuwa wannan ya na nufin cewa an haife Yesu a cikin Galili.
1Yesu ya je Dutsen Zaitun. 2Da sassafe ya dawo Haikali, dukan mutane kuma suka zo wurin sa; yazauna koya masu. 3Sai marubuta da Farisawa suka kawo mace wadda aka kama ta tana zina. Su ka sa ta a tsakiya.4Sai su ka ce da shi, "Malam, wannan mace an kama ta tana cikin yin zina. 5A cikin shari'a, Musa ya bamu umurni mu jejjefe irin wandannan mutume, kai me ka ce game da ita?" 6Sun fadi haka ne domin su gwada shi su sami abinda za su zarge shi da shi, amma Yesu ya sunkuya yayi rubutu da yatsansa a kasa.7Sa'adda suka cigaba da tambayar sa, ya mike tsaye yace masu, "shi wanda ba shi da zunubi a cikin ku, ya fara jifar ta da dutse." 8Ya sake sunkuyawa, ya yi rubutu da yatsansa a kasa.9Da suka ji haka, sai suka fita dai-dai da dai-dai, kama daga babbansu. A karshe dai aka bar Yesu shi kadai, tare da matar wadda ta ke a tsakiyar su. 10Yesu ya tashi tsaye ya ce da ita, "mace, ina masu zargin ki? Ba wanda ya kashe ki? 11Ta ce, "Ba kowa, Ubangiji" Yesu ya ce, "Ni ma ban kashe ki ba. Ki yi tafiyar ki, daga yanzu kada ki kara yin zunubi."12Yesu ya kara yin magana da mutanen cewa, "Ni ne hasken duniya, shi wanda ya biyo ni, ba zai yi tafiya cikin duhu ba, amma za ya sami hasken rai. 13Farisawa suka ce masa, "Kana bada shaida a kan ka, shaidarka ba gaskiya ba ce."14Yesu ya amsa ya ce masu, "Ko ma na bada shaida a kai na, shaidata gaskiya ce, na san daga inda na fito da inda zan tafi, amma ku baku san daga inda na fito ba, baku kuma san inda zan tafi ba. 15Kuna shari'a ta son kai, ni ko ban yi wa kowa shari'a ba. 16Ko ma da na yi shari'a, shari'ata gaskiya ce domin ba ni kadai ba ne, amma ina tare da Uba wanda ya aiko ni.17I, a cikin dokarku an rubuta cewa shaidar mutum biyu gaskiya ce. 18Ni ne ni ke shaidar kaina, kuma Uba wanda ya aiko ni ya na shaida ta.19Su ka ce da shi, "Ina ubanka?" Yesu ya amsa ma su ya ce, "baku san ni ba balle Ubana, in da kun san ni da kun san Uba na kuma."20Ya fadi wadannan kalmomi a kusa da wurin ajiya sa'adda ya ke koyarwa a cikin haikali, kuma ba wanda ya kama shi saboda sa'arsa bata yi ba tukuna.21Ya kara cewa da su,"Zan tafi, za ku neme ni ba za ku same ni ba, za ku mutu cikin zunubinku. Inda ni ke tafiya, ba za ku iya zuwa ba". 22Yahudawa su ka ce,"Zai kashe kansa ne, da ya ce inda ni ke tafiya ba za ku iya zuwa ba?"23Yesu ya ce masu ku daga kasa kuke, Ni kuwa daga bisa ni ke. Ku na wannan duniya ne, Ni kuwa ba na wannan duniya ba ne. 24Shiyasa na ce maku za ku mutu cikin zunubanku. In ba kun bada gaskiya NI NE ba, za ku mutu cikin zunubanku.25Sai kuma suka ce da shi,"Wanene kai?" Yesu ya ce masu, "Abin da na gaya maku tun daga farko. 26Ina da a bubuwa da yawa da zan gaya maku, in kuma hukunta ku a kai. Duk da haka, wanda ya aiko ni, mai gaskiya ne, abubuwan da naji daga wurin sa, wadannan abubuwan su ni ke gaya wa duniya." 27Ba su gane ba yana yi masu magana a kan Uban.28Yesu ya ce, "Sa'adda kuka tada Dan Mutum sama sa'annan za ku gane NI NE, kuma ban yi komi domin kaina ba. Kamar yadda Uba ya koya mani, haka nike fadin wadannan abubuwa. 29Shi wanda ya aiko ni, yana tare da ni kuma bai bar ni ni kadai ba, domin kullum ina yin abubuwan da suke faranta masa rai." 30Sa'adda Yesu ya ke fadin wadannan abubuwa, dayawa suka bada gaskiya gare shi.31Yesu ya gayawa wadancan Yahudawa da suka bada gaskiya gare shi, "Idan kun tsaya a cikin magana ta ku almajiraina ne na gaskiya, 32Kuma za ku san gaskiya, gaskiya kuwa zata 'yantar da ku." 33Suka amsa masa, "Mu zuriyar Ibrahim ne kuma bamu taba yin bauta wurin kowa ba, yaya za ka ce, 'Za a 'yantar da ku'?"34Yesu ya ce masu, "Hakika, hakika, ina ce maku, dukan wanda ya ke aika zunubi bawan zunubi ne. 35Bawa kuwa, ba ya zama a gida dindindin, da yana zama dindindin. 36Saboda haka, idan Dan ya 'yantar da ku zaku zama 'yantattu sosai.37Na san ku zuriyar Ibrahim ne, kuna so ku kashe ni saboda kalma ta bata da wurin zama a cikin ku. 38Na fadi abubuwan da na gani a wurin Ubana, ku kuma kuna yin abubuwan da kuka ji daga wurin ubanku."39Suka amsa suka ce masa, "Ibrahim ne ubanmu" Yesu ya ce masu, "Da ku 'yayan Ibrahim ne da kun yi ayukan da Ibrahim ya yi. 40Amma, yanzu kuna so ku kashe ni, mutumin da ya gaya maku gaskiyar da ya ji daga wurin Allah. Ibrahim bai yi haka ba. 41Kuna yin ayyukan ubanku. Suka ce masa, "mu ba a haife mu cikin fasikanci ba, muna da Uba daya: Allah."42Yesu ya ce masu, "Inda Allah Ubanku ne, da kun kaunace ni, gama na zo daga wurin Allah kuma ga ni anan, gama ba domin kaina nazo ba, shine ya aiko ni. 43Meyasa baku gane magana ta ba? Ai saboda ba za ku iya jin maganata ba ne. 44Ku na ubanku, shaidan ne, kuma kuna so ku yi nufe-nufe na ubanku. Shi mai kisan kai ne tun daga farko kuma ba ya tsayawa gaskiya saboda da babu gaskiya a cikin sa. Sa'anda yake fadin karya, yana maganar halinsa ne domin shi dama makaryaci ne da uban karya kuma.45Dayake ina fadin gaskiya baku bada gaskiya gare ni ba. 46Wanene a cikin ku ya kama ni da zunubi? Idan na fadi gaskiya don me ba ku gaskanta ni ba? 47Shi wanda yake na Allah ya kan ji maganar Allah, ku ba kwa jin maganar Allah da yake ku ba na Allah bane,"48Yahudawa suka amsa suka ce masa, "Bamu fadi gaskiya ba da muka ce kai Basamariye ne kuma kana da aljan?" 49Yesu ya amsa, "Ni ba ni da aljan, ina girmama Ubana, ku kuma ba kwa girmama ni."50Ba na neman daraja domin kaina, akwai wanda ke nema yana kuma hukuntawa. 51Hakika, hakika, iIna ce maku, dukan wanda ya kiyaye maganata, ba za ya ga mutuwa ba."52Sai Yahudawa su ka ce masa, Yanzu mun sani kana da aljan. Ibrahim da annabawa sun mutu, amma kai ka ce, ' dukan wanda ya yi biyayya da maganata ba zai dandana mutuwa ba'. 53Ai baka fi ubanmu Ibrahim girma ba wanda ya mutu, ko ka fi shi? Annabawa kuma sun mutu. Wa kake daukar kanka ne?."54Yesu ya amsa, "Idan na daukaka kaina, daukaka ta banza ce, Ubana ne ya daukaka ni. Wanda kuka ce shi ne Allahnku. 55Ku kuwa ba ku san shi ba, amma ni na san shi. Idan na ce ban san shi ba, na zama kamar ku kenan, makaryaci. Sai dai, Ni na san shi ina kiyaye maganarsa. 56Ubanku Ibrahim ya yi farinciki da ganin rana ta; ya gan ta kuma ya yi murna."57Yahudawa su ka ce masa, "Baka kai shekara hamsin ba tukuna, ka taba ganin Ibrahim?" 58Yesu ya ce masu, "Hakika, hakika, ina ce maku, kafin a haifi Ibrahim, NI NE." 59Suka dauki duwatsu za su jefe shi, amma Yesu ya boye kansa, ya fita daga haikali.
Sura ɗaya ya faɗa mana inda Yesu ya tafi a karshen Sura da ya rigaya wuce.
Sa'an da waddansu litattafe su ke da 7:53-8:1, litattafe na farko musa kyau ba su sa su ba.
Wannan ne ainahin yadda ana magana. Ya na nufin "mutane dayawa."
A nan jumlan "marubuta da Farisawa" karin magana ne da yake wakilcin waddansu mutanin wannan kungiyoyi biyu. AT: "Waddansu marubuta da Farisawa sun kawo" ko kuma "Waddansu mazaje wadda sun koya wa Yahudawa dokoki da waddansu da suke Farisawa"
Wannan jumla ce. AT: "macen da su ka samu ta ke yin zina"
"mutane irin haka" ko "mutane da suke yin haka"
"Don haka kun gaya mana. Me za mu yi game da ita?
Wannan ya na nufin yin amfani da wata tambaya.
Ana iya sa abin da za a zarge a bayyane. AT : "domin su iya yin zargin sa da faɗan abin da ba daidai ba" ko kuma "domin su iya zargin sa da rashin bin dokan Musa ko na Romawa"
Kalmar "su" ya na nufin marubuta da Farisawa.
Ana iya bayyana kalmar "zunubi." AT: "shi wanda bai taba yin zunubi a cikin ku ba" ko kuma "Idan wani a cikin ku bai taba yin zunubi ba"
"bari mutumin"
"ya durkusa"
"đaya bayan ɗaya"
A loƙacin da Yesu ya kira ta "mace," ba wai ya na sun ya sa ta ta ji kamar mara amfani bba ne. Idan mutane a harshenku za su yi tunani cewa ya na yin haka, ana iya fasara ba tare da kalmar "Mace" ba.
A nan "haske" misali ne na wahayin da ya ke zuwa daga Allah. AT: "Ni ne wadda na ke ba da haske a duniya"
Wannan magana ne na mutanin. AT: "mutanin duniya"
Wannan karin magana ne da ya ke nufin "kowane mutum da yake yin abin da ke daidai" ko "kowane mutum da ya ke biyayya da ni"
Yi "tafiya a cikin duhu" magana ne na yin rayuwan zunubi. AT: "ba zai yi rayuwa kamar ya na cikin duhun zunubi ba"
"Hasken rai" magana ne na gaskiya daga Allah wadda yake ba da rai na ruhaniya. AT: "gaskiya da yake kawo rai madawammi"
"Kana faɗan waddannan abubuwa game da kanka"
Farisawa su na nufin cewa shaidar mutum daya kadai ba gaskiya ba ne domin ba za a iya bincikawa ba. AT: "ba za ka iya zama shaidar kanka ba" ko " abin da ka faɗa game da kanka ba zai iya zama gaskiya ba"
"ko da na faɗa waddannan abubuwa game da ni"
"ma'aunin mutum da kuma dokokin mutane"
AT: 1) "ban yi wa kowa shari'a tukuna ba" ko 2) "ba zan yi wa kowa shari'a yanzu ba."
AT: 1) "idan na yi wa mutane shari'a" ko kuma 2) "duk loƙacin da na yi wa mutane shari'a"
AT: 1) "shari'ata zai zama daidai" ko "shari'ata daidai ne."
Yesu, Ɗan Allah, ya na da iko domin dangantaka na musamman da Ubansa.
Abin da bayanin ya ke nufi shi ne Yesu ba shi kadai ba ne a shari'an. AT: "ba ni kadai ba ne a yadda na ke yin shari'a" ko "ba na yin shari'a ni kadai"
Uba da Ɗa su na shari'ata tare. AT: "Uban ya na yin shari'a tare da ni" ko "Uban ya na yin shari'a kamar yadda na ke yi"
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah. Idan dole ne harshen ku zai faɗa Uban wa ne wannan, za ku iya ce " Uba na"
"kalmar "I" ya na nuna cewa Yesu ya na kara akan abin da dama ya na faɗa.
Wannan jumla ce. AT: "Musa ya rubuto"
hikiman a nan shi ne cewa mutum daya ya na iya duba kalmomin dayan mutumin. AT: "Idan mazaje biyu sun faɗa abu daya, mutane sun san cewa gaskiya ne"
Yesu ya shaida kansa. AT: "Na ba ku alamun kai na"
Uban kuma ya na shaida akan Yesu. Za ku iya sa a bayyane cewa wannan ya na nufin shaidar Yesu gaskiya ce. AT: "Uba na wadda ya aiko ni ya kuma kawo alamu game da ni. Don haka ku yarda cewa abin da mu na faɗa maku gaskiya ne"
Yesu ya nuna cewa saninsa, ya na nan kamar sanin Uban ne kuma. Ɗa da Uba Allah ne. "Uba" muhimmin lakami ne wa Allah.
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
Kalmar "sa'a" magana ne na loƙacin da Yesu zai mutu. AT: "loƙaci bai kai da Yesu zai mutu ba"
A nan kalmar "mutu" ya na nufin mutuwa ta ruhaniya. AT: "mutu a loƙacin da ku na cikin zunubi" ko "za ku mutu a loƙacin da ku na yin zunubi"
"ba ku iya zuwa ba"
A nan "Yahudawa" magana ce na "shugabanin Yahudawa." AT: "shugabanin Yahudawa sun ce"
"An haife ku a cikin wannan duniya"
"na zo daga sama"
"Ku na wannan duniya ne"
"NI ba na wannan duniya ba ne"
"zu ku mutu da ba Allah ya yafe ku zunuben ku ba"
AT: 1) Yesu ya na bayyana kansa a kamar Yahweh, wadda ya ke nufin "Ni ne" ko 2) "Yesu ya so mutanin su gani cewa ya na nufin abin da ya rigaya ce shi ne: "Ina daga sama."
Kalmar "Su" ya na nufin shugabanin Yahudawa. (Dubi: John 8:22)
A nan "duniya" magana ne na mutanin da suke rayuwa a cikin duniya. AT: "waddannan abubuwa da na faɗa wa dukka mutane"
Wannan ya na nufin sa Yesu a kan giciye don a kashe shi.
Yesu ya yi amfani da wannan lakabin "Ɗan Mutum" wa kansa.
Kamar Allah Ɗa, Yesu ya san Allah Uba fiye da kowa. AT: 1) Yesu ya na bayyana kansa a mastayin Yahweh ta wurin cewa, "Ni ne Allah" ko 2) Yesu ya na cewa, "ni ne wadda na ke faɗa."
"Ina faɗan abinda Ubana ya koya mani in faɗa." Kalmar "Uba" muhimmin lakami ne wa Allah.
Kalmar "shi" ya na nufin Allah.
"Sa'adda Yesu ya faɗa waddannan kalmomin"
"mutane dayawa sun yarda da shi"
Wannan karin magana ne da ya ke nufin "yin biyyaya da Yesu." AT: "yi biyyaya da abin da na faɗa"
"masu bi na"
Wannan karin magana ne. Yesu ya yi magana akan "gaskiyan" kamar mutum ne. AT: "Idan kun yi biyyaya da Allah, Allah zai yantar da ku"
Wannan ya na nufin abin da Yesu ya bayana game da Allah. AT: "abin da ke gaskiya game da Alla"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya nuna mamakin shugabanin Yahudawa a abin da Yesu ya faɗa. AT: "Ba mu neman a cece mu!"
Dubi yadda an fasara wannan a cikin 1:51.
A nan kalmar "bawa" karin magana ne. Wannan ya na nufin cewa "zunubi" ya na nan kamar maigida ne ga wadda yake yin zunubi. AT: "ya na nan kamar bawan zunubi"
A nan "gida" magana ne na "iyali." AT: "A matsayin cikkaken dan iyalin"
Wannan karin magana ne. Za ku iya fasara shi ta amfani da kalmomin. AT: "ɗan dan gidan ne har abada"
Ya na nufin cewa Yesu ya na magana game da yanci daga zunubi, wadda magana ne na rashin iya yin zunubi. AT: "Idan Ɗan ya 'yantar da ku, zaku iya yantuwa daga zunubi"
"Ɗan" muhimmin lakabi ne na Yesu, Ɗan Allah. Yesu ya yi magana game da kansa ne. AT: "Idan Ni, Ɗan, ya yantar da ku"
A nan "kalma" magana ne na "koyarswa" ko "sakon" Yesu, wadda shugabanin Yahudawa ba karba ba. AT: "ba ku karbi koyarswa na ba" ko kuma "ba ku yarda sako na ta canza rayuwarku ba"
"Ina gaya maku game da abubuwan da na gani a loƙacin da ina tare da Uba na"
Shugabanin Yahudawa ba su gane cewa ta wurin "Ubanku" Yesu ya na nufin shaidan ne ba. AT: "kun kuma cigaba da yin abin da Ubanku ya gaya maku ku yi"
kakane
"Ibrahim bai taba gwada kashe wani da ya gaya mashi gaskiyan wahayi daga Allah ba"
Yesu ya na nufin cewa shaidan ne ubansu. AT: "a'a! Ku na yin abubuwan da ainahin ubanku ya yi"
A nan shugabanin Yahudawa su na nufin cewa Yesu bai san wa ne ainahin Ubansa ba. AT: "Ba mu san game da kai ba, amma ba mu ne ainahin 'ya'yan ba" ko kuma "An haife mu daga aurya da ya kamata"
A nan shugabanin Yahudawa sun amince cewa Allah ne Ubansu na ruhaniya. Wannan mihimmin lakabi ne wa Allah.
Wannan ne irin kauna da ya ke zuwa daga Allah kuma ya na kan kyauwawan mutane (tare da makiyanmu), ko bai amfane mutum ba.
Yesu ya na amfani da wannan tambaya domin ya tsauta wa shugabanin Yahudawa domin rashin jin su. AT: "Zan gaya maku dalilin da ba ku gane abin da na faɗa!"
A nan "magana" ya na nufin "koyarswan" Yesu. AT: "Ai saboda ba za ku yarda da koyarswa ta ba.
"ku na ubanku, shaidan"
A nan "uba" magana ne na wadda ya soma karya. AT: "shi ne wadda ya halittce dukka karya a farko"
"domin ina faɗa maku abubuwan gaskiya game da Allah"
Yesu ya yi amfani da wannan tambaya domin ya bayana cewa bai taba yin zunubi ba. AT: "Ba bu wani a cikin ku da zai iya nuna cewa na taba yin zunubi!"
"Idan na faɗa abubuwan da suke gaskiya"
Yesu ya yi amfani da wannan tambaya don ya tswata shugabanin Yahudawa domin rashin gaskanta. AT: "ba ku da dalilin rashin gaskanta da ni!"
A nan "maganar" ya na nufin "sakon" Allah. AT: "sakon Allah" ko kuma "gaskiya da ya ke zuwa daga Allah"
"Yahudawa" karin magana ne da ya ke wakilcin "shugabanin Yahudawa" da suke hamayya da Yesu. AT: "shugabanin Yahudawa"
shugabanin Yahudawa sun yi amfani da wannan tambaya domin su kushe Yesu su kuma ci masa mutunci. AT: "Hakika mun yi daidai da mu ka ce kai ba-Samariye ne kuma aljani ya na rayuwa a cikin ka!"
Wannan ya na nufin Allah.
A nan "magana" zance ne na "koyarwan" Yesu. AT: "yi biyayya da koyarwa na" ko "yi abin da na ce"
Wannan karin magana ne da yake nufin taba mutuwa. A nan Yesu ya na nufin mutuwa ta ruhaniya. AT: "mutu a ruhaniya"
A nan "Yahudawa" magana ne na "shugabanin Yahudawa" wadda suke hamayya da Yesu. AT: "shugabanin Yahudawa"
"Idan wani ya yi biyayya da koyarswata"
Wannan karin magana ne da yake nufin taba mutuwa. Shugabanin Yahudawa sun yi kuskure ta tunani cewa Yesu ya na magana akan mutuwa ta jiki ne kadai. AT: "mutu"
Shugabanin Yahudawa sun yi amfani da wannan tambaya domin su bayana cewa Yesu bai fi Ibrahim ba.AT: "Hakika ba ka fi Ubanmu Ibrahim wanda ya mutu ba!"
Yahudawa sun yi amfani da wannan tambaya don su kwaɓe Yesu domin ya na tunani cewa ya fi Ibrahim muhimmi. AT: "Kada ka yi tunani cewa ka na da muhimmi!"
Kalmar "Uba" muhimmin lakami ne wa Allah. Ba bu wadda ya san Allah Uba kamar Yesu, Ɗan Allah. AT: "Uba na ne ya na daukaka na, sai kuma ku na ce shi ne Allahnku"
A nan "kalma" magana ne na abin da Allah ya ce. AT: "Ina biyayya da abin da ya ce a yi"
Wannan magana ne na abin da Yesu zai cika a loƙacin rayuwarsa. AT: "abin da zan yi a loƙacin rayuwata"
"ya gan zuwa na ta wurin wahayin Allah sai ya yi murna"
A nan "Yahudawa" magana ne na "shugabanin Yahudawa" wadda sun yi hamayya da Yesu. AT: "shugabanin Yahudawa sun ce masa"
Shugabanin Yahudawa sun yi amfani da wannan tambaya domin su bayana mamakin sun cewa Yesu ya ce ya gan Ibrahim. AT: "Ka na kasa da shekaru hamsin. Da ba ka iya ganin Ibrahim ba!"
Kamar Allah Ɗa, Yesu ya san Allah Uba fiye da kowa. AT: 1) Yesu ya na bayyana kansa kamar Yahweh ta wurin cewa, "Ni ne Allah" ko kuma 2) Yesu ya na cewa, kafin Ibrahim ya kasance, Na kasance."
Shugabanin Yahudawa sun yi fushi a abin da Yesu ya ce. A nan ya na nufin cewa sun so su kashe shi domin ya sa kanshi daidai da Allah. AT: "Sai sun dauki duwasu su kashe shi domin ya ce shi daidai ne da Allah"
1Da Yesu yana wucewa, sai ya ga wani mutum makaho tun daga haihuwa. 2Sai almajiransa suka tambaye shi, "Mallam, wa yayi zunubi, mutumin ne ko iyayensa, har aka haife shi makaho?"3Yesu ya amsa, Ba mutumin ne ko iyayensa suka yi zunubi ba, amma domin aikin Allah ya bayyana a cikinsa. 4Dole mu yi aikin wanda ya aiko ni tunda rana. Dare na zuwa inda ba mai iya yin aiki. 5Yayinda ina duniya, ni ne hasken duniya."6Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar. 7Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike)." Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.8Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, "Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?" 9Wadansu suka ce, "shi ne." Wadansu suka ce, "A'a, amma yana kama da shi." Amma shi ya ce, "Ni ne wannan mutum."10Suka ce masa, "To yaya aka bude maka idanu?" 11Sai ya amsa, "Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani." 12Suka ce masa, "Ina yake?" Ya amsa, "Ban sani ba."13Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa. 14A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu. 15Har yanzu farisawan suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Ya ce masu, "Ya sa mani kasa a idanuna, na wanke, kuma yanzu ina gani."16Wadansu daga cikin farisawa suka ce, "Wannan mutum ba daga Allah yake ba domin ba ya kiyaye ranar Asabar. "Wadansu suka ce, "Yaya mai zunubi zai yi irin wadannan alamu?" Sai rabuwa ta shiga tsakanin su. 17Sai suka tambayi makahon kuma, "Me kake cewa game da shi dashike ya bude maka idanu?" Makahon ya ce, "shi annabi ne." 18Har yanzu kam Yahudawan basu yarda da makantarsa ba da ganin gari da ya samu, sai da suka kirayo iyayen shi wanda ya sami ganin garin.19Su ka tambayi iyayen, "Wannan shine yaronku da kuka ce an haife shi makaho? Yaya yanzu ya ke iya gani?" 20Sai iyayen suka amsa masu, "Mun san wannan yaronmu ne kuma a makaho aka haife shi. 21Yadda ya ke gani yanzu, bamu sani ba, kuma wanda ya bude masa idanu, bamu sani ba. Ku tambaye shi, ba yaro ba ne. Zai iya magana don kansa."22Iyayensa sun fadi wadannan abubuwan, domin suna ji tsoron Yahudawan. Gama Yahudiyawan sun rigaya sun yarda duk wanda yace Yesu Almasihu ne, za a fitar dashi daga majami'a. 23Domin wannan ne, iyayensa suka ce, "Ai shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi."24Suka sake kiran mutumin dake makaho karo na biyu, suka ce masa, "Ka girmama Allah. Mu kam mun sani wannan mutum mai zunubi ne." 25Sai wannan mutum ya amsa, "Ban sani ba ko shi mai zunubi ne. Abu guda daya na sani: da Ni makaho ne, amma yanzu ina gani."26Sai su ka ce masa, "Me ya yi maka? Ta yaya ya bude idanunka?" 27Ya amsa, "Na rigaya na gaya maku, amma ba ku ji ba! Don me kuke so ku sake ji? Ko kuma kuna so ku zama almajiransa, haka ne?28Sai suka kwabe shi suka ce, "kai ne almajirinsa, amma mu almajiran Musa ne. 29Mun sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum, bamu san ko daga ina ne ya zo ba."30Mutumin ya amsa masu ya ce, "Tirkashi, baku san inda ya fito ba, duk da haka shi ya bude mani idanu. 31Mun san da cewa Allah baya jin masu zunubi, amma idan wani mai ibada ne yana kuma yin nufinsa, to yana jin sa.32Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba. 33In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba." 34Suka amsa suka ce masa, "an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?" Sai suka fitar da shi.35Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, "Kana bada gaskiya ga Dan Allah?" 36Sai ya amsa masa yace, "Wanene shi, Ubangiji, da zan bada gaskiya gare shi?" 37Yesu yace masa, "Ai ka gan shi, shine wanda yake magana da kai." 38Mutumin ya ce, "Ubangiji, Na bada gaskiya." Sai ya yi masa sujada.39Yesu ya ce, "Don hukunci na zo wannan duniya domin wadanda ba su gani su gani, saboda kuma wadanda suke gani su zama makafi." 40Wadansu Farisawa wadanda suke tare da shi suka ji wadannan abubuwan, suka tambaye shi, "Muma makafi ne?" 41Yesu ya ce masu, "Inda ku makafi ne, da ba ku da zunubi, amma yanzu kun ce, 'Muna gani', don haka zunubinku ya tabbata.
Sa'ad da Yesu da almajiransa su na tafiya, sun haɗu da wani makaho.
Wannan kalma ya nuna cewa marubucin ya na so ya kwatanta sabon abu.
A nan "Yesu" magana ne na Yesu da almajiransa. AT: "sa'ad da Yesu da almajiransa suka wuce"
Wannan tambaya ya nuna tsohon amincewa na Yahudawa da cewa zunubi ne ya na sa dukka cituttuka da sauran mugun aibi ga jiki. Mallamai sun zata cewa yaro ya na iya yin zunubi daga cikin ciki. AT: "Mallam, mun san cewa zunubi ya na sa mutum makaho. Zunubin wa ne ya sa an haife wannan mutum makaho? Mutumin nan da kansa ne ya yi zunubi, ko iyayensa ne?"
Wannan "mu" ya na tare da Yesu da almajiran da yake magana da su.
A nan "rana" da "dare" karin magana ne. Yesu ya na kwatanta loƙacin da mutane su na iya yin aikin Allah har rana, loƙacin da mutane su na aiki, da kuma dare loƙacin da ba za su iya yin aikin Allah ba.
A nan "duniya" magana ne na mutanin da suke cikin duniya. AT: "yin rayuwa a sakanin mutanin wannan duniya"
A nan "haske" magana ne na gaskiyan wahayin Allah. AT: "wadda ya ke nuna abin da yake gaskiya kamar yadda haske ya na barin mutane su gani abin da yake cikin duhu"
Yesu ya yi amfani da yatsun shi ya kwaɓa datti da yawu. AT: "ya yi amfani da yasunsa ya kwaba dattin da yawu don ya yi laka"
Za ku iya sa a bayyane cewa Yesu ya so mutumin ya wanke lakan a idonshi a cikin tafkin kuma haka mutumin ya yi.
An sami dan yanka a cikin labarin don haka Yahaya zai iya bayana wa masu karatunsa abin da "Siloam" ya ke nufi. AT: "wadda yake nufin "aike"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya domin ya nuna mamakin mutanin. AT: "Wannan mutumin ne wadda ya saba zaune yana roko!"
maƙwabcin mutumin da ya taba makwace sun cigaba da magana da shi.
"To mai ne ya sa ka iya gani?" ko kuma "Ta yaya ka na iya gani yanzu?"
"yi amfani da yatsunsa don ya rufe mun idanu na da laka." Dubi yadda kun fasara irin wannan jumla a cikin 9:6.
Mutanin sun nace cewa sai mutumin ya tafi da su wurin Farisawa. Bu su tilasa shi da karfi ya je ba.
"Ranar hutun Yahudawa"
"Sai Farisawa sun kuma tambaye shi"
Wannan ya na nufin cewa Yesu ba ya kiyaye doka game da yin aiki a ranar hutun Yahudawa.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya nanata cewa alamun Yesu ya nuna cewa shi ba mai zunubi ba ne. "Mai zunubi ba zai iya yin wannan abu ba!"
Wannan wata kalma ne na abin al'ajibi. "Alamu" ya na ba da shaida cewa Allah shi ne mai dukka iko, kuma wadda yake da iko akan duniya.
"Ina tunani shi annabi ne"
A nan "Yahudawa" magana ne na "shugabanin Yahudawa" wadda suka yi hamayya da Yesu. AT: "Yanzu shugabanin Yahudawa ba su yarda ba.
"Su" ya na nufin shugabanin Yahudawa.
"shi na miji ne" ko "shi ba yaro ba ne kuma"
A nan "Yahudawa" ya na nufin shugabanin Yahudawa" wadda sun yi hamayya da Yesu. AT: "sun ji tsoron abin da shugabanin Yahudawa za su iya yi masu"
Wannan ya na nufin rashin daɗi da mutum ya ke da shi a loƙacin da akwai wata kurarin lahani a kansa ko waddansu.
"zai faɗa cewa Yesu Almasihu ne"
A nan "fitar daga majami'a" magana ne na rashin yarda a sake shiga majami'a kuma ba bu sake kasancewa a kungiyar mutane da suke zuwa sujada a majami'a. AT: "ba za a yarda masa ya shiga cikin majami'a ba" ko "ba zai cigaba da zama ɗan majami'a ba"
A nan "su" ya na nufin Yahudawa. ([Yahaya 9:18]
Wannan karin magana ne da mutane suke amfani da shi a loƙacin daukan rantsuwa. AT: "A gaban Allah, faɗa gaskiya" ko kuma "Faɗa gaskiya a gaban Allah"
Wannan ya na nufin Yesu.
Wannan ya na nufin mutumin da ada shi makaho ne.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya bayana mamakin mutumin da cewa shugabanin Yahudawa sun ce masa ya gaya masu abin da ya faru kuma.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin karin fasara a maganan mutumin. Ya san cewa shugabanin Yahudawa ba su so su bi Yesu. Ya na so ya yi masu ba'a anan. AT: "kamar ku na so ku zama almajiransa!"
"Ku na bin Yesu!"
Kalmar "mu" ya na a bayyane. shugabanin Yahudawa su na maganan kansu ne kadai. AT: "amma muna bin Musa"
"Mun tabata cewa Allah ya yi magana da Musa"
A nan shugabanin Yahudawa su na nufin Yesu. Suna nufin cewa ba shi da ikon kiran almajirai. AT: "ba mu san inda ya fito ba ko kuma inda ya sami ikonsa"
Mutumin ya na mamakin cewa shugabanin Yahudawa su na tuhunta ikon Yesu bayan sun san cewa ya na da ikon warkarwa. AT: "cewa ba ku san inda ya ke samu ikonsa ba"
"baya amsa addu'an masu zunubi ... Allah ya na amsa addu'ar sa"
Wannan jumla ne. AT: "ba bu wadda ya taɓa ji game da wani da ya taɓa warkar da mutum makaho tun daga haifuwa ba"
Wannan jumla ya yi amfani da hanyoyi dabam dabam. "Mutum daga Allah ne kadai zai iya yin abu irin wannan!"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin karin bayani. Ya na kuma nufin cewa an haife mutumin da makance domin zunuban iyayensa. AT: "An haife ka dalilin zunuban iyayenka. Ba ka kai ka koyar da mu ba!"
"suka fitar da shi daga majami'a"
Wannan ya na nufin "gaskanta da Yesu," gaskanta cewa shi ne Ɗan Allah, yarda cewa shi ne mai ceto, ku kuma yi rayuwa a hanyar da zai girmama shi.
Kalmar "duniya" ya na nufin "mutane da suke rayuwa a cikin duniya." AT: "zo ya yi rayuwa a sakanin mutanin wannan duniya"
A nan "gani" da "makanta" karin magana ne. Yesu ya banbanta mutane da su ke makance ta ruhaniya da makance na jiki. AT: "domin waddanda suka makance a ruhaniya, amma waɗɗanda su ke so su gan Allah, su na iya ganin shi, kuma waɗɗanda sun riga sun yi tunani cewa za su iya ganin Allah ne za su cigaba a cikin makantansu"
"Ka na tunani cewa mun makance a ruhaniya ne?"
A nan "makanta" magana ne na rashin sanin gaskiyar Allah. AT: "Inda ce kun so ku san gaskiyar Allah, za ku iya gani.
A nan "gani" magana ne na sanin gaskiyar Allah. AT: "Tunda ku na tunani cewa kun riga kun san gaskiyar Allah, za ku cigaba da makance"
1"Hakika, Hakika, ina ce maku, wanda bai shiga ta kofa zuwa garken tumaki ba, amma ya haura ta wata hanya, wannan mutum barawo ne da dan fashi. 2Wanda ya shiga ta kofa shine makiyayin tumakin.3Mai gadin kofar zai bude masa. Tumakin suna jin muryarsa, ya na kuma kiran tumakinsa da sunayensu, ya kuma kai su waje. 4Bayanda ya kawo su duka a waje, yana tafiya a gabansu, sai tumakin su bi shi, domin sun san muryarsa.5Ba za su bi bako ba amma sai dai su guje shi, domin basu san muryar baki ba." 6Yesu ya yi masu magana da wannan misali, amma basu gane wadannan abubuwa da yake gaya masu ba.7Sai Yesu ya ce masu kuma, "Hakika, Hakika, Ina ce maku, Ni ne kofar tumaki. 8Dukan wadanda suka zo kamin ni barayi ne da yan fashi, amma tumakin ba su ji su ba.9Ni ne kofa, In kowa ya shiga ta wurina, zai sami ceto, zai shiga ya fita ya kuma sami wurin kiwo. 10Barawo ba ya zuwa sai don ya yi sata, ya kashe, ya kuma hallakar. Na zo ne domin su sami rai su kuma same shi a yalwace.11Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yana bada ransa domin tumakinsa. 12Wanda yake dan sako kuma, ba makiyayi ba, wanda ba shine mai tumakin ba, in ya ga kyarkeci na zuwa sai ya saki tumakin ya gudu. Sai kyarkecin ya dauke su ya kuma warwatsa su. 13Ya gudu domin shi mai aikin kudi ne kuma bai damu da tumakin ba.14Nine makiyayi mai kyau, na kuma san nawa, nawa kuma sun san ni. 15Uban ya san ni, ni ma na san Uban, na kuma bada raina domin tumakin. 16Ina da wadansu tumaki wadanda ba na wannan garken ba. Wadannan, kuma, dole in kawo su, su ma za su ji muryata saboda za su zama garke daya da makiyayi daya.17Domin wannan ne Uban yake kauna ta: Na bada raina domin in same shi kuma. 18Babu wanda zai dauke shi daga wurina, amma ina bayar da shi da kaina. Ina da ikon bada shi, ina da iko in dauke shi kuma. Na karbi wannan umarnin daga wurin Ubana."19Tsattsaguwa ta sake tashi tsakanin Yahudawa domin wadannan kalmomin. 20Dayawa a cikinsu suka ce, yana da aljani, kuma mahaukaci ne. Don me ku ke sauraronsa?" 21Wadansu suka ce, wadannan ba kalmomin wanda yake da aljani ba ne. Ko mai aljani zai iya bude idanun makaho?"22Sai lokacin idin Tsarkakewa a Urushalima ya zo. 23A lokacin damuna ne, Yesu kuwa yana tafiya a shirayi cikin haikalin Sulaimanu. 24Sai Yahudawa suka zagaye shi suka ce masa, "Har yaushe ne za ka bar mu cikin shakka? In kai ne Almasihun, ka gaya mana dalla-dalla."25Yesu ya ce masu, "Na gaya maku, amma baku gaskata ba. Ayyukan da nake yi a cikin sunan Ubana, su ke yin shaida a kaina. 26Duk da haka baku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.27Tumakina suna jin murya ta; Na san su, suna kuma bi na. 28Ina ba su rai na har abada; ba za su taba mutuwa ba, babu wanda zai kwace su daga hannu na.29Ubana, wanda ya bani su, ya fi kowa girma, kuma ba mai iya kwace su daga hannun Uban. 30Ni da Uban daya ne." 31Sai Yahudawa suka dauki duwatsu kuma domin su jajjefe shi.32Yesu ya amsa masu, "Na nuna maku kyawawan ayyuka masu yawa daga wurin Uban. Saboda wane daga cikin wadannan ayyukan kuke jefe ni?" 33Sai Yahudawa suka amsa masa, "ba don wani aiki mai kyau muke son mu jefe ka ba, amma don sabo, domin kai, mutum ne, amma kana mayar da kanka Allah."34Yesu ya amsa masu, "Ba a rubuce yake a shari'arku ba, 'Na ce, "ku alloli ne"'?" 35In ya kira su alloli, su wadanda maganar Allah ta zo gare su (kuma ba za a iya karya nassi ba), 36kuna gaya wa wanda Uban ya kebe ya kuma aiko cikin duniya, 'Kana sabo', domin Na ce, 'Ni dan Allah ne'?37In ba na aikin Ubana, kada ku gaskata ni. 38Amma, idan ina yin su, ko ba ku gaskata da ni ba, ku gaskata da ayyukan saboda ku sani, ku kuma gane cewa Uban yana ciki na, ni kuma ina cikin Uban." 39Suka sake kokarin kama shi, amma ya yi tafiyarsa, ya fita daga hannunsu.40Ya yi tafiyarsa kuma har gaba da kogin Urdun zuwa inda Yahaya ke yin baftisma ada, ya kuma zauna a wurin. 41Mutane masu yawa suka zo wurinsa, suka ce,"Hakika Yahaya bai yi wasu alamu ba, amma dukan abubuwan da Yahaya ya ce game da wannan mutum gaskiya ne." 42Mutane dayawa suka bada gaskiya gare shi a wurin.
Yesu ya cigaba da magana da Farisawa. Wannan ne sashin labari wadda ya fara a cikin 9:35.
Yesu ya fara magana a cikin misalai.
Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 1:51.
Wannan wurin danga ne wadda makiyayi yana sa tumakinsa.
Wannan ya na nufin yadda ake amfani da kalmomi biyu makamanci domin karin nanaci.
"Mai gadin kofar ya na buɗe wa tumaki kofa"
Wannan mutum ne wadda an yi hayarsa domin ya duba kafar garken tumaki da dare a loƙacin da makiyayin ba ya nan.
"Tumakin ya gi muryan makiyayi"
"ya na tafiya a gabansu"
"domin sun gane muryarsa"
AT: 1) "almajiran ba su gane ba" ko 2) "taron ba su gane ba."
Wannan kwatanci ne daga aikin makiyayi, ta wurin amfani da karin magana. "Makiyayi" karin magana ne na Yesu. "Tumaki" su na wakilcin waɗɗanda suke bin Yesu, kuma "ɓaki" su ne shugabanin Yahudawa, haɗe da Farisawa, wadda sun gwada rudin mutane.
A nan "kofa" magana ne da yake nufin cewa Yesu ya tanada hanya zuwa garken tumaki, wurin da mutanin Allah suke zama a gabansa. AT: "Ina nan kamar kofa da tumaki suke amfani don su shiga cikin garken tumaki"
Wannan Ya na nufin waɗansu mallamai da su ka koyar da mutanen, tare da Farisawa da kuma waɗansu shugabanin Yahudawa. AT: "Dukan malaman da suka zo ba tare da iko na ba"
A nan "kofa" ƙarin magana ne. Ta wurin kiran kansa "kofa," Yesu ya na nuna cewa shi ne yake ba da hanyar gaskiya na shiga mulkin Allah. AT: "Ni da kai na ina nan kamar kofa"
Kalmar "kiwata"ya na nufin wuri mai ciyawa da tumaki ke ci.
Wannan biyu ne. A wadansu harshuna ya fi kyau a yi amfani da jumla mai kyau. AT: "zuwa don ya yi sata kadai"
Maganar a nan shi ne "tumaki," wadda ya na wakilcin mutanin Allah. AT: "sata, kashe, da kuma hallakar da tumaki"
Kalmar "su" ya na nufin tumaki. "Rai" ya na nufin rai madawami. AT: "domin su rayu, ba tare da rashi ba"
A nan "Makiyayi mai kyau" magana ne da yake wakilcin Yesu. AT: "Ina nan kamar Makiyayi mai kyau"
Ba da wani abu ya na nufin ka mika ranka. Wata hanya ne na mara tsanani da yake nufin mutuwa. AT: "mutu"
"mai aikin kudi" magana ne da ya na wakilcin shugabanin Yahudawa da kuma mallamai. AT: "wadda yake kamar mai aikin kudi"
A nan kalmar "tumaki" magana ne da ya na waklicin mutanin Allah. Kamar mai aikin kudi wadda ya saki tumakin, Yesu ya ce shugabanin yahudawa da mallamai ba su damu da mutanin Allah ba.
Allah Uba da Allah Ɗa sun san juna fiye da yadda wani ya san su. "Uba" muhimmin lakami ne wa Allah.
Wannan karamin hanya ne da Yesu zai ce zai mutu domin ya kare tumakinsa. AT: "Na mutu don tumakin"
A nan "wadansu tumaki" karin magana ne na masu bin Yesu wadanda ba Yahudawa ba.
A nan "garke" da "makiyayi" karin magana ne. Dukka masubin Yesu, Yahudawa da waɗɗanda ba Yahudawa ba, za su zama kamar garkin tumaki. Zai zama kamar makiyayi wadda ya damu da dukkan su.
Madauwamin shirin Allah shi ne Allah Ɗa ya ba da rainsa domin ya biya zunuban 'yan Adam. Mutuwar Yesu a kan giciye ya bayyana kaunar Ɗan wa Uban kuma na Uban zuwa ga Ɗan.
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
Wannan irin kauna ya na zuwa daga Allah ne ya na bisa kyaun mutane, ko bai amfani wani ba. Irin wannan kauna ya na kula da mutane, ko mai abin da sun yi.
Wannan karamin hanya ne da Yesu zai ce zai mutu sai ya kuma rayu kuma. AT: "Na yarda in mutu domin in sake rayu"
An yi amfani da "kaina" a nan domin a nanata cewa Yesu ya ba da rainsa. Ba bu wadda zai karɓa daga wurinsa. AT: "Ni da kai na bayar"
"Wannan ne abin da Uba na ya umurce ni in yi." Wannan kalmar "Uba" muhimmin lakami ne wa Allah.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya nanata maganar cewa kada mutane su saurare Yesu. AT: "Kada ku saurare shi!"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin karin bayani. AT: "Hakika aljani ba zai sa makaho ya iya gani ba!" ko kuma "Hakika aljani ba zai iya sa makafe gani ba!"
Wannan hutun ɗari ne na kwana takwas wadda Yahudawa suke amfani don tunawa da wata abin al'ajibi wadda Allah ya sa mai kadan ya cigaba da ba da haske a fitila har kwana takwas. Sun haska fitilar domin su tsarkake haikalin Yahudawa wa Allah. Tsarkaka abu ya na nufin yin alkawari cewa za ku yi amfani da shi a nufi mai kyau.
Wurin da Yesu ya yi tafiya wuri ne da yake wajen filin haikalin. AT: "Yesu ya na tafiya a cikin filin haikali"
Wannan abu ne da an kafa da ya ke a hade da kofan gini; ya na da jinka kuma ya na iya samu katanga ko ba bu.
A nan "Yahudawa" ya na nufin shugabanin Yahudawa wadda sun yi hamayya da Yesu. AT: "Sai shugabanin Yahudawa suka zagaye shi"
Wannan karin magana ne. AT: "sa mu mamaki" ko kuma "hana mu sanin takamaiman?"
A nan "suna" magana ne na ikon Allah. A nan "Uba" muhimmin lakami ne wa Allah. Yesu ya yi abin al'ajibi ta wurin ikon Ubansa. AT: "ta wurin ikon Ubana" ko "da ikon Ubana"
Al'ajibinsa ya ba da shaida game da shi kamar yadda mutumin da yake yin shaida zai ba da shaida a kotun shari'a. AT: "ba da shaida game da ni"
Kalmar "tumaki" magana ne na masubin Yesu. AT: "ba masubina ba" ko "ba almajirai na ba"
Kalmar "tumaki" misali ce ta masubin Yesu. An bayyana Yesu kamar "makiyayi." AT: "Yadda tumaki su na bin muryan makiyayinsu na gaskiya, masu bi na su na jin murya na"
Kalmar "hanu" a nan magana ne da ya na wakilcin karewa da kula na Yesu. AT: "babu wadda zai sata su daga wuri na" ko kuma "za su kasance lafiya a kulawa na"
Kalmar "Uba" muhimmin lakabi ne wa Allah.
Kalmar "hanu" ya na nufin dukiya da kiyayewar Allah. AT: "Ba bu wadda zai sata su daga Ubana"
Yesu, Allah Da, da Allah Uba ɗaya ne. Kalmar "Uba" muhimmin lakami ne wa Allah.
Kalmar "Yahudawa" ya na nufin shugabanin Yahudawa wadda suka yi hamayya da Yesu. AT: "Sai shugabanin Yahudawa suka fara dauka duwatsu kuma"
Yesu ya yi su abubuwan al'ajibi ta wurin ikon Allah. Kalmar "Uba" muhimmin lakami ne wa Allah.
Yesu ya san cewa shugabanin Yahudawa ba su so su jefe shi ba domin ya yi kyauwawan ayyaka.
Kalmar "Yahudawa" karin magana ne da ya na wakilcin shugabanin Yahudawa wadda suka yi hamayya da Yesu. AT: "gefen Yahudawan suka amsa" ko kuma "shugabanin Yahudawa sun amsa masa"
"cewa shi Allah"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin karin bayani. AT: "Ya kamata kun san cewa a rubuce ya ke a shari'ar ku cewa, 'ku alloli ne."
Yesu a nan ya yi magana daga nassi inda Allah ya kira masubinsa "alloli," watakila domin ya zabe su ne su wakilce shi a duniya.
Yesu ya yi maganar sakon Allah kamar mutum ne wanda ya maso kusa da wadanda sun ji shi. AT: "Allah ya faɗi sakonsa"
AT: 1) "ba bu wani da zai iya canza nassi" ko kuma 2) "a ko yaushe nassi yakan kasance gaskiya."
Yesu ya yi amfani da wannan tambaya don ya tsawata abokan gabansa domin sun ce ya na sabo a loƙacin da ya kira kansa "Ɗan Allah." AT: "kada ku ce wa wanda Allah ya kebe don ya aika cikin duniya, 'kana sabo; a loƙacin da na ce ni ne Ɗan Allah!"
"ka na zagin Allah." Abokan gaban Yesu sun gane cewa a loƙacin da an ce shi ne Ɗan Allah, ya na nufin cewa shi daidai ne da Allah.
Wadannan muhimmin lakabi ne da ya na kwatanta dangantaka a sakanin Allah da Yesu.
A nan kalmar "gaskanta" ya na nufin amincewa ko kuma yarda cewa abin da Yesu ya faɗa gaskiya ne.
A nan "gaskanta da" shi ku yarda cewa ayyukan da Yesu ya yi daga Uban ne.
Wadannan karin magana ne da su na bayyana dangantaka na ƙwarai sakanin Allah da Yesu. AT: "Ni da Ubana ɗaya ne a haɗe"
Kalmar "hannu" magana ne da ya na wakilcin kula ko dukiyar shugabanin Yahudawa. AT: "tafi daga su kuma"
Yesu ya na gefen yamma na rafin Urdun. AT: "zuwa gabas na rafin Urdun"
Yesu ya tsaya ta gabas Urdun na dan loƙaci kadan. AT: "Yesu ya zauna na kuanaki dayawa a wurin"
"gaskiya ne cewa Yahaya bai yi wani alamu ba, haƙiƙa bai faɗa gaskiya game da wannan mutum ba, wadda yake yin alamu."
Wadannan abubuwan al'ajibi ne wadda ya ke nuna cewa wani abin gaskiya ne ko kuma ya na amince mutum.
A nan "gaskanta a" ya na nufin amince ko kuma yarda da abin da Yesu ya faɗa gaskiya ne.
1To wani mutum mai suna Li'azaru, yayi rashin lafiya. Shi mutumin Baitanya ne, wato kauyen su Maryamu da 'yar'uwarta Matta. 2Wato wannan Maryamu da ta shafe Ubangiji da mur ta kuma share masa kafafunsa da gashin kanta, wadda dan'uwanta Li'azaru ke rashin lafiya.3'Yan'uwannan mata suka aika sako wurin yesu, cewa, "Ubangiji, duba, shi wanda kake kauna yana rashin lafiya". 4Da Yesu ya ji, sai ya ce "Wannan ciwo ba zai kai ga mutuwa ba, amma domin daukakar Allah ne, domin Dan Allah ya sami daukaka tawurin ta".5Yesu yana kaunar Matta, da 'yar'uwarta da Li'azaru. 6Da yaji cewa Li'azaru na rashin lafiya, sai ya tsaya kwana biyu a inda ya ke. 7Bayan haka, sai ya ce wa almajiransa, "Bari mu je Yahudiya kuma."8Sai almajiransa suka ce masa, "Mallam, harwayau Yahudaya na neman ka domin su jefe ka da duwatsu, kuma kana son komawa can?" 9Yesu ya amsa, "Ba sa'a goma sha biyu ce ta haske a rana guda ba? Idan mutum ya yi tafiya da rana, ba za ya yi tuntube ba, domin yana gani ta wurin hasken wannan duniya.10Amma idan mutum ya yi tafiya chikin dare, za ya yi tuntube domin haske ba ya tare da shi. 11Ya fadi wadannan al'amura, kuma bayan wadannan abubuwa, sai ya ce masu, "Abokinmu Li'azaru ya yi barci, amma zan je don In tashe shi daga barci".12Sai almajirai suka ce masa, "Ubangiji, idan barci yake yi, ai za ya farka." 13Yesu kuwa ya yi maganar mutuwar Li'azaru ne, amma su suna tsammani yana magana akan barci ne na hutu. 14Sai Yesu ya yi masu bayani cewa, "Li'azaru ya mutu.15Ina farinchiki domin ku, da bani a wurin domin ku gaskata. Bari mu je wurinsa." 16Toma wanda ake kira Dan tagwaye, ya ce wa sauran almajirai, "Bari mu tafi domin mu mutu tare da Yesu."17Da Yesu ya iso, sai ya tarar cewa Li'azaru ya rigaya ya yi kwana hudu a kabari. 18Baitanya kuma tana kusa da Urushalima, 'yar tafiya marar nisa ce a tsakanin su. 19Yahudawa dayawa sun zo wurin Maryamu da Matta domin su yi masu ta'aziyar mutuwar dan'uwansu. 20Da Matta ta ji cewa Yesu na zuwa, sai ta tafi domin ta same shi, amma Maryamu na zamne a cikin gida.21Matta ta ce wa Yesu, "Ubangiji, da kana nan tare da mu, da dan'uwana baya mutu ba". 22Ko yanzu na san cewa duk abinda ka roka a wurin Allah, za ya ba ka. 23Yesu ya ce mata, "Dan'uwanki za ya rayu kuma.24Sai Matta ta ce masa, "Na san zaya rayu kuma a tashin mattatu na ranar karshe." 25Yesu ya ce mata, "Ni ne tashin matattu, ni ne kuma rai; wanda ya bada gaskiya gare ni, ko ya mutu, za ya rayu; 26Kuma duk wanda yake raye, ya kuma bada gaskiya gare ni, ba zai mutu ba dadai. Kin gaskata da wannan?"27Sai ta ce masa, "I, Ubangiji, Na gaskata cewa kaine Almasihu, Dan Allah, wanda ke zuwa duniya. 28Sa'adda ta fadi haka, sai ta koma ta kira yar'uwarta Maryamu gefe guda. Ta ce, "mallam ya iso, kuma yana kiran ki." 29Da ta ji haka, sai ta tashi da sauri ta tafi wurin sa.30Yesu bai rigaya ya shiga kauyen ba, yana nan inda Matta ta zo ta same shi. 31Da Yahudawan nan dake tare da Maryamu, wato wadannan da suka zo mata ta'aziya, suka ga ta fita daga chikin gida da sauri, sai suka bi ta, suna tsammanin cewa ta tafi ta yi kuka ne a kabari. 32Da Maryamu ta kai inda Yesu ya ke, sai ta fadi gaban sawayensa, ta ce, "Ubangiji, inda kana tare da mu, da dan'uwana bai mutu ba".33Da Yesu ya gan ta tana kuka, da wadannan Yahudawa da suka bi ta, sai ya yi juyayi a ruhu ya damu kuma; 34sai ya ce, "A ina kuka kwantar da shi?" Sai suka ce masa, "Ubangiji, zo ka gani." 35Yesu ya yi kuka.36Sai Yahudawa suka ce, "Dubi yadda yake kaunar Li'azaru!" 37Amma wadansun su suka ce, "Shi wannan mutum da ya iya ba makaho ganin gari, da bai iya hana wannan mutum mutuwa ba?38Yesu yana cikin juyayi kuma a cikin kansa, sai ya tafi kabarin. Kabarin a kogo ne an kuma rufe bakinsa da dutse. 39Sai Yesu ya ce, "A kawar da dutsen." Matta yar'uwar Li'azaru wanda ya mutu, ta ce wa Yesu, "Ubangiji, Yanzu jikin ya ruba domin ya kai kwana hudu da mutuwa". 40Yesu ya ce mata, "Ba na ce maki idan kin gaskata za ki ga daukakar Allah ba?"41Sai suka kawar da dutsen. Yesu ya daga idanunsa ya ce, "Uba, na gode maka domin kana ji na."42Na san kana ji na a kowane lokaci, amma domin wannan taro da ke tsaye kewaye da ni nike wannan magana, domin su bada gaskiya cewa kaine ka aiko ni."43Bayan ya yi wannan magana, sai ya daga murya ya ce, "Li'azaru, ka fito!" 44Sai mataccen ya fito; kafafunsa da hannayensa na daure da likkafani, fuskarsa kuma na lullube da tsumma. Yesu ya ce masu, "Ku kwance shi, ya tafi".45To dayawa daga cikin yahudawan da suka zo wurin Maryamu suka kuma ga abinda Yesu ya yi, suka gaskata da shi; 46amma wadansu suka koma wurin farisawa suka fada masu abubuwan da Yesu ya yi.47Sai manyan firistoci da farisawa suka tara majalisa wuri guda, suka ce, "menene za mu yi?" Mutumin nan yana alamu masu yawa. 48Idan mun kyale shi haka, duka za su gaskata da shi; Romawa za su zo su kwace wurinmu da al'ummar mu.49Duk da haka, wani daga cikin su wato, Kayafas wanda shine babban firist a wannan shekara, ya ce da su, "baku san komai ba". 50Ba ku lura cewa ya fi maku kyau mutum daya ya mutu domin mutane, a maimakon dukan al'umma ta hallaka."51Ya fadi wannan ne ba don kansa ba, amma sabo da shine babban firist, ya yi anabci ne cewa ya kamata Yesu ya mutu domin al'ummar; 52kuma ba don alummar kawai ba, amma domin a tattara 'ya'yan Allah da suke warwatse ko'ina wuri daya. 53Tun daga wannan rana suka fara neman hanyar da za su kashe Yesu.54Tun daga nan Yesu ya dena tafiya a sarari chikin Yahudawa, amma sai ya koma wani yanki kusa da jeji a wani gari da ake kira Ifraimu. A can kuma ya zamna da almajiransa. 55Idin ketarewa na Yahudawa ya yi kusa, da yawa sun tafi Urushalima daga yankin kasar kamin ranar idi domin su tsarkake kan su.56Suka shiga neman Yesu, suna magana da junan su yayin da suke tsaitsaye a haikali, cewa "me kuke tunani? Ba za ya zo idin bane?" 57Babban firist da farisawa sun rigaya sun ba da umurni cewa duk inda aka ga Yesu a zo a shaida domin su kama shi.
Wadannan Sura su na gabatar da labarin Lazarus da kuma ba da tushen bayana game da shi da kuma yar'uwarsa Maryamu.
Sa'adda Yahaya ya gabatar da Maryamu, yar'uwar Mata, ya ba da bayani game da abin da zai faru anjuma a cikin labarin.
"roke Yesu ya zo"
A nan "kauna" ya na nufin kaunar 'yan'uwa, ta halitta, kauna na mutum a sakanin abokai da dangi.
Yesu ya na nufin cewa ya san abin da zai faru da Li'azaru da ciwonsa. AT: "Mutuwa ba zai zama .karshen sakamakon wannan ciwo ba"
Wannan ya na nufin mutuwa ta jiki.
Yesu ya na nufin cewa ya san abin da zai faru. AT: "amma wannan nufin shi don mutane su gan girman Allah domin abin da ikonsa zai yarda min in yi"
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
Wannan tushen bayani ne.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya nanata cewa almajiran ba su son Yesu ya tafi Urushalima. AT: "Mallam, haƙiƙa ba ka so ka koma can! Yahudawa sun so su jefe ka a loƙacin da ka na wurin!"
Wannan magana ne na shugabanin Yahudawa wadda su ka yi hamayya da Yesu. AT: " shugabanin Yahudawa"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin karin bayani. AT: "kun san cewa rana ya na da sa'a sha biyu na haske!"
Mutane da suke tafiya a cikin hasken rana su na iya gani da kyau kuma ba su yin tuntuɓe. "haske" magana ne na "gaskiya." Yesu ya na nufin cewa mutane da suke rayuwa bisa gaskiya su iya yin abubuwan da Allah ya na so su yi"
Yesu ya cigaba da magana da almajiransa.
A nan "dare" magana ne da ya na nufin tafiyar mutum da babu hasken Allah.
AT: 1) "ba ya iya gani" ko "ba shi da hasken Allah."
A nan "barci" karin magana ne da ya na nufin Li'azaru ya mutu. Idan ku na da wata hanyar faɗa wannan a harshenku, za ku iya yin amfani da shi a nan.
Kalmomin " tashe shi daga barci" karin magana ne. Yesu ya na bayyana shirinsa na sa Li'azaru ya rayu kuma. Idan ku na da karin magana na wannan a harshen ku, za ku iya amfani da shi ana.
Da shike almajiran ba su fahimci abin da yesu ya na nufi ba, sun ce ko Li'azaru ya na hutawa ne kuma zai warke.
"Sai yesu ya gaya masu a kalmomin da za su iya gane"
"domin amfanin ku"
"da ba na wurin. Domin wannan za ku iya gaskanta da ni sosai."
AT: "wadda su ke kira Ɗan tagwaye"
Wannan sunan na miji ne wadda ya na nufin "yan biyu."
AT: "ya ji cewa mutane sun riga sun sa Li'azaru a cikin kabari har kwana hudu kafin"
"nisar kilomita uku." "filinwasanni" mita ɗari da tamanin da biyar.
Li'azaru kaninsu ne. AT: "game da kaninsu"
Li'azaru ne kanin. AT: "har yanzu kani na zai rayu"
Li'azaru ne kanin. AT: "kanin ki zai rayu kuma"
"zai rayu kuma"
A nan "mutu" ya na nufin mutuwa ta jiki.
A nan "rayu" ya na nufin rayuwa ta ruhaniya.
"waɗɗanda su na raye kuma sun gaskanta da ni ba za a raba su daga Allah har abada ba" ko "wadanda su na raye kuma sun gaskanta da ni za su rayu ta ruhaniya tare da Allah har abada"
A nan "mutu" ya na nufin mutuwa ta ruhaniya.
"Matta ta ce wa Yesu"
Matta ta gaskanta cewa Yesu Ubangiji ne, Almasihu, (Mai ceto), Ɗan Allah.
Maryamu kanuwar Matta ne. AT: "ta je ta kira kanuwarta Maryamu"
Wannan lakabi ne da ya na nufin Yesu.
"ya ce ki zo"
Yahaya ya ba da yanka a labarin domin ya ba da tushen bayani game da inda Yesu yake.
Maryamu ta kwanta ko ta durkusa a sawayen Yesu don ta nuna ladabi.
Yahaya ya hada wadannan jumloli masu ma'ana iri ɗaya domin ya bayyana tsananin wuya da kuma fushi mai yiwuwa da Yesu ya ji. AT: "hankalinsa ya tashi sosai"
Wannan wata hanyar tambaya, "A inane kuka binne shi?"
"Yesu ya fara kuka"
Wannan ya na nufin kaunar yan'uwa ko kaunar mutum wa aboki ko ɗan iyali.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya nuna mamakin Yahudawa da cewa Yesu bai warkad da Li'azaru ba. AT: "Ya iya warkad da makaho, ai da ya iya warkad da wannan mutum don kadda ya mutu!" ko "Tun da bai hana mutumin nan daga mutuwa ba, watakila bai warkad da mutumin da an haife shi makaho ba, kamar yadda sun ce ya yi!"
AT: "warkad da idanun"
Yahaya ya tsayar da labarin domin ya kwatanta kabarin da mutanin suka binne Li'aziru.
Matta da Maryamu yayun Li'azaru ne. AT: "Matta, yayar Li'azaru"
"Yanzu za a sami wari" ko "jikin ya na doyi"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya nanata cewa Allah zai yi abin ban mamaki. AT: "Na gaya maki cewa indan kin yarda da ni, za ki gan abin da Allah zai yi!"
Wannan karin magana ne da ya na nufin duba sama. AT: "Yesu ya duba sama"
Yesu ya yi addu'a wa Allah domin wadanda suke akewaye da shi su ji addu'ar sa. "Uba, Na gode da ka ji ni" ko "Uba, Na gode da ka ji addu'a na"
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
"Ina so du gaskanta da cewa kaine ka aiko ni"
"bayan da Yesu ya yi addu'a"
"ya yi ihu"
Al'adan biso na wannan lokacin shi ne a ana nada gawa a cikin dogon likkafani. AT: "Wani ya naɗe likkafani a hannayensa da kafafunsa. Sun kuma daura likkafani a fuskarsa da tsumma"
Kalmar "masu" ya na nufin mutane da suke wurin kuma sun gan abin al'ajibin.
"Sai shugabanne a cikin firistoci"
Marubucin ya yi amfani da wannan kalma domin ya gaya wa mai karatun cewa abin da ya faru a farkon Aya 47 abin da ya faru ne 11:45-46.
Wannan ya na nufin cewa mutanin majalisa su na maganar Yesu ne. AT: "me nene za mu yi game da Yesu?"
Shugabanin Yahudawa sun ji tsoro cewa mutanin za su gwada sa Yesu ya zama sarkin su. AT: "kowa zai yarda da shi su kuma yi wa Romawa tawaye"
Wannan magana ne na sojojin Romawa. AT: "sojojin Romawa za su zo"
"halaka haikalinmu da al'ummar mu"
Wata hanya ne na gabatar da sabon mutum a cikin labarin. Idan ku na da yadda za ku yi shi a harshen ku, za ku iya amfani da shi anan.
Wannan zuguiguitawa ne da Kayafas ya yi amfani don ya zage masu sauraransa. AT: "ba ku gane abin da ya na faruwa ba" ko kuma "ku na magana kamar ba ku san komai ba"
Kayafas ya na nufin cewa sojojin Romawa za su kashe dukka mutanin al'ummar Yahudawa idan an yarda Yesu ya zauna ya kuma sa tawaye. Kalmar "al'umma" magana ne da ya na wakilcin dukkan mutanin Yahudawa. AT: "a maimakon Romawa su kashe dukkan mutanin al'ummar mu"
Kalmar "al'umma" magana ne da ya na nufin mutanin al'ummar Isra'ila.
Wannan karin magana ne. Kalmar "mutane" ya na a bayyane a mahallin. AT: "za a tara zuwa mutane ɗaya"
Wannan ya na nufin mutane da sun zama na Allah ta wurin bangaskiya a cikin Yesu kuma 'ya'yan Allah ne ta ruhaniya.
A nan "Yahudawa" magana ne na shugabanin Yahudawa kuma "tafiya a sarari" ya na nufin "zama a inda kowa zai iya ganin shi." AT: "zamna a inda dukkan Yahudawa za su iya ganin shi" ko kuma "yi tafiya a sarari a sakanin shugabanin Yahudawa da su ka yi hamayya da shi"
kauyen da su na wujen gari da mutane kadan suke zama.
Yesu da almajiransa sun zamnaIfraimu na dan lokaci. AT: "A caan ya zamna da almajiransa na dan lokaci"
An yi amfani da jumlar "tafi" domin Urushalima ya na tudu fiye da sauran wuraran.
Kalmar "su" ya na nufin mutanin Yahudawa wanda sun tafi Urushalima.
Wadannan tambayoyi sun bayyana shakkan cewa Yesu zai zo idin ketarewa. Tambaya na biyu karin magana ne da ya bayyana "kuke tunani."Masu magana su na tunani ko Yesu zai zo idin tun da akwai alamar kamar shi. "Watakila Yesu ba zai zo idin ba. Ya na iya jin tsoro kar a kama shi!"
Wannan tushen bayani ne da ya na fasara dalilin da Yahudawa masubi sun yi tunani ko Yesu zai zo idin ko babu. Idan harshenku ya na da wata hanyar sa tushen bayani, sai ayi amfani da shi anan.
1Kwana shidda kafin idin ketarewa, Yesu ya zo Baitanya inda Li'azaru yake, wato wannan da Yesu ya tada daga matattu. 2Sai suka shirya masa abinci a wurin kuma Matta ce ke hidima, Li'azaru kuwa ya kasance cikin wadanda ke kan tebiri tare da Yesu.3Sai Maryamu ta dauki wani turare da aka yi da man nard, ta shafe kafafun Yesu da shi, ta kuma share kafafun nasa da gashin kanta. Sai gida ya cika da kamshin turaren.4Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin almajiransa, wanda zai bashe shi, ya ce, "5"Me yasa ba a sayar da wannan turare dinari dari uku a ba gajiyayyu ba?" 6Ya fadi haka ba don ya damu da gajiyayyu ba, amma domin shi barawo ne: shi ne ma'aji, kuma yana sata daga jakkar kudi.7Yesu ya ce, "Ku kyale ta ta ajiye abinda ta tanada domin jana'iza ta. 8Gajiyayyu suna tare da ku a koyaushe, ni kuwa ba zan kasance da ku koyaushe ba.9To babban taron Yahudawa sun ji cewa Yesu yana wurin, sai suka zo, ba don Yesu kawai ba amma domin su ga Li'azaru, wanda Yesu ya tada daga matattu. 10Sai manyan firistoci suka kulla makirci akan yadda za su kashe Li'azaru shima; 11domin saboda shi ne yahudawa dayawa suka je suka bada gaskiya ga Yesu.12Kashegari, babban taro suka zo idin. Da suka ji cewa Yesu na zuwa Urushalima,13Sai suka dauki ganyen dabino suka fita gari suka tare shi da kira mai karfi suna cewa, "Hosanna! Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji, Sarkin Isra'ila.14Yesu ya sami wani Aholakin jaki, ya hau kansa; kamar yadda aka rubuta,15"Kada ki ji tsoro ke 'yar Sihiyona; duba, ga Sarkinki na zuwa, zaune a kan danJaki".16Almajiransa basu fahimci wannan al'amari ba da farko, amma bayan da aka daukaka Yesu, sai suka tuna cewa an rubuta wadannan abubuwa game da shi, kuma sun yi masa wadannan abubuwa.17Sai taron da ke tare da Yesu a ranar da ya kira Li'azaru daga kabari ya kuma tashe shi daga matattu, suka bada shaida. 18Domin wannan ne kuma taron suka zo domin su sadu da shi saboda sun ji cewa ya yi wannan alama. 19Don haka, sai farisawa suka shiga magana a tsakanin su suna cewa "Duba, babu abinda zaku iya yi; kun ga, duniya ta gama bin sa.20Akwai wadansu Helinawa cikin wadanda suka je sujada a idin. 21Wadannan suka tafi wurin filibus, mutumin Betsaida da ke Galili, suka ce masa, "Mallam, muna so mu ga Yesu.22Filibus ya tafi ya fadawa Andrawus; sai Andrawus ya tafi tare da Filibus, suka kuwa gaya wa Yesu.23Yesu ya amsa masu ya ce, "sa'a ta zo da za'a daukaka Dan mutum. 24Hakika, hakika, Ina ce maku, in ba kwayar alkama ta fadi kasa ba ta mutu, za ta kasance ita kadai; amma idan ta mutu, za ta bada 'ya'ya masu yawa.25Duk wanda yake son ransa, zai rasa shi; amma wanda ba ya son ransa a duniyan nan za ya kiyaye shi domin rayuwa ta har abada. 26Idan wani na bauta mani, to bari ya biyo ni; kuma duk inda nike, a can bawana zai kasance kuma. Duk wanda ke bauta mani, Uban zai girmama shi.27Yanzu raina na cikin damuwa, to me zan ce? 'Uba, ka cece ni daga wannan sa'a? Amma Saboda wannan dalili ne na zo wannan sa'a. 28Uba, ka daukaka sunanka". Sai wata murya daga sama ta ce, "Na daukaka shi, zan kuma sake daukaka shi. 29Daganan sai taron dake tsaye kuma suka ji muryar, suka ce an yi tsawa. Wasu suka ce, "Mala'ika ya yi magana da shi".30Yesu ya amsa ya ce, "wannnan murya ta zo ba saboda ni ba, amma domin ku." 31Yanzu za'a shar'anta duniya. Yanzu za'a kori mai mulkin duniyan nan.32Sa, annan ni, idan an daga ni daga duniya, zan jawo dukan mutane zuwa gare ni". 33Ya fadi wannan ne domin ya nuna irin mutuwar da za ya yi.34Taro suka amsa masa cewa, "Mun ji a cikin shari'a cewa Almasihu za ya kasance har abada. Yaya za ka ce, 'za'a daga dan mutum'? Wanene wannan dan mutum?" 35Yesu ya ce masu, "Nan da lokaci kadan za ku kasance da haske, ku yi tafiya tun haske na tare da ku, kada duhu ya mamaye ku. Wanda ke tafiya cikin duhu, bai san inda za shi ba. 36Ku gaskata ga haske tun yana tare da ku domin ku zama yayan haske". Yesu ya fadi wadannan abubuwa sannan ya tafi ya boye masu.37Kodashike Yesu ya yi alamu da dama a gabansu, duk da haka ba su gaskata shi ba. 38Saboda maganar annabi Ishaya ta cika, wadda ya ce, "Ubangiji, wa ya gaskata rahoton mu? Ga wa kuma hannun Ubangiji ya bayyana?39Saboda wannan dalili basu gaskata ba, gama Ishaya ya sake cewa, 40ya makantar da su, ya kuma taurare zuciyarsu, saboda kada su gani da idanunsu, su kuma sami fahimta da zuciyarsu, su juyo wurina in warkar da su.41Ishaya ya fadi wadannan abubuwa ne domin ya hangi daukakar Yesu ya kuma yi magana game da shi. 42Amma duk da haka, dayawa cikin shugabanni suka gaskata Yesu. Amma saboda farisawa, basu shaida shi a sarari ba, domin kada a kore su daga majami'a. 43Suna son yabo daga mutane fiye da yabon dake zuwa daga Allah.44Yesu ya yi magana da babbar murya, ya ce, "Wanda ya gaskata ni, ba ni yake gaskatawa kadai ba, amma kuma yana gaskata wanda ya aiko ni, 45kuma wanda ke gani na, yana ganin shi wanda ya aiko ni.46Na zo ne a matsayin haske a duniya, saboda duk wanda ya gaskata da ni ba za ya yi tafiya cikin duhu ba. 47Duk wanda ya ji maganata baya gaskata ba, ba ni hukunta shi; gama ban zo in yi wa duniya hukunci ba, amma don in ceci duniya.48Wanda ya ki ni, ya kuma ki ya karbi magana ta, akwai wanda za ya yi masa hukunci. Kalmar da na fada, ita ce za ta yi masa hukunci a rana ta karshe. 49Maganar da ni ke yi, ba ra'ayina ba ne. Amma Uba wanda ya aiko ni shi ke bani umarni game da abin da zan ce da abin da zan fadi. 50Na san umarninsa rai ne madawwami, don haka na ce - kamar yadda Uba ya fada, haka ni ma nake fadi."
Yesu ya na cin abinci a Baitani a lokacin da Maryamu ta shafa kafafunsa da turare.
Marubucin ya yi amfani da wannan kalmomin domin ya nuna farawan sabon abu.
AT: "ya sa shi ya rayu kuma"
Za ku iya mai da wannan zuwa awu na zamani. "lita" kusan rabin kilo ne. Ko kuma ku yi amfani da wani abu da zai iya rike yawan turaran. AT: "rabin kilo na turare" ko "kwalbar turare"
Wannan wata ruwa-ruwan abu ne mai kamshi da kuma kyau ne da an yi shi daga man itace da fure mai kamshi.
Wannan turane ne da an yi shi daga wata fure a cikin duwasun Nepal, China da kuma India.
AT: "kamshin turarenta ya cika gidan"
"wadda ya sa an iya kama Yesu"
Wannan tambaya ne da ba ya neman amsa. Za ku iya fasara shi kamar babban jumla. AT: "za a iya sayar da wannan turare dinari dari uku a kuma yi amfani da kudin don a taimake talakawa!"
AT: "dinari ɗari uku"
Dainari kudin azurfa ne da ma'aikaci ya ke samuwa a rana ɗaya.
Yahaya ya bayyana dalilin da ya sa Judas ya yi tambaya game da talakawa. Idan harshen ku ya na da wata hanyar nuna tushen bayani, zaku iya yin amfani da shi a nan.
"ya faɗi haka domin shi barawo ne. Bai damu da talakawa ba"
Yesu Ya na nufin cewa ayukkan matan ya nuna cewa su na saurarar mutuwa da bisonsa. AT: "Bar ta ta nuna yadda take kauna na! A haka ne ta shirya biso na"
Yesu ya na nufin cewa akwai hanyoyi dayawa da za a iya taimakon talakawa. AT: "za a sami talakawa koyaushe a sakaninku, kuma za ku iya taimake su a duk loƙacin da ku na so"
A haka, Yesu ya na nufin zai mutu. AT: "Amma ba zan kasance tare da ku kayaushe ba"
An yi amfani da wannan kalma domin a sa layi a ainihin labarin. A nan Yahaya ya yi magana game da sabon kungiyar mutane da sun zo Betini daga Urushalima.
Rayuwar Li'azarus ne ya sa Yahudawa dayawa suka gaskanta da Yesu.
Wannan ya na nufin cewa mutanin Yahudawa dayawa sun na ba da gaskiya ga Yesu"
Marubucin ya yi amfani da waɗannan kalmomi domin ya fara sabon abu.
"babban taron mutane"
Wannan na nufin "Bari Allah ya cece mu yanzu"
Wannan ya bayyana yadda Allah ya na so ya sa abubuwa masu kyau su faru wa mutum.
A nan kalmar nan " suna" magana ne na karfi da ikon mutum. AT: "zuwa kamar wakilin Ubangiji" ko "zuwa a cikin sunan Ubangiji"
A nan Yahaya ya ba da tushen bayani cewa Yesu ya sami jaki. Ya na nufin cewa Yesu zai hawo jaki zuwa Urushalima. AT: "ya sami aholakin jaki sai ya zanna a kai, tafiya zuwa Urushalima"
AT: "yadda annabawa suka rubuta a cikin nassi"
"'Yar Sihiyona" ya na nufin mutanin Urushalima. AT: "ku mutanin Urushalima"
A nan kalmomin "wannan al'amari" ya na nufin kalmomin da annabi ya rubuta game da Yesu.
AT: "loƙacin da Allah ya ɗaukaki Yesu"
Kalmomin "wadannan abubuwa" ya na nufin abin da mutane sun yi a loƙacin da Yesu ya shiga cikin Urushalima a kan jaki (yabon shi da kuma nuna reshen giginya).
"sun ji wadansu su na ce ya yi wannan alama"
"Alama" abu ne ko abin da ya faru, wadda ya na nuna cewa abin gaskiya ne. A wannan magana, "Alamar" ta da Li'azaru ya nuna cewa Yesu ne mai ceto.
Farisawan su na nufin anan cewa ba za a iya hana Yesu ba. AT: "kamar ba za mu iya yin komai don mu hana shi ba"
Farisawa sun yi amfani da wannan zuguiguitawa domin su bayyana mamakin cewa mutane da yawa sun fito don su gan Yesu. AT: "kamar kowa ya na zama almajiransa"
A nan " duniya" magana ne da ya na wakilcin
Wannan jumla "Yanzu wadansu" ya nuna gabatarwar sabobin mutane a cikin labarin.
Yahaya ya na nufin cewa wadannan "helinawa" su na tafiya zuwa yabon Allah a loƙacin ketarewa. AT: "don a yabe Allah a idin ketarewa"
Wannan gari ne a yankin Galili.
Fillibus da Andrawas sun faɗa wa Yesu game da rokon da Helinawa sun yi don su gan shi. AT: "Sun gaya wa Yesu abin da Helinawan sun ce"
Yesu ya na nufin cewa yanzu ne daidan loƙaci da yakamata Allah ya ɗaukaki Ɗan Mutum ta wurin wahala mai zuwa, mutuwa da tashiwa. AT: "Allah zai ɗaukake ni a loƙacin da in na mutu da kuma tashi"
Fasara shi a yadda harshenku ya na nanata cewa abu na-biye ya na da muhiminci kuma gaskiya ne. Dubi yadda kun fasar "Hakika, hakika" a cikin 1: 51.
A nan "kwayar alkama" ko "iri" magana ne na mutuwa, biso, da kuma tashin Yesu.Yadda ana shuka iri kuma ya na girma zuwa shuka da zai ba da 'ya'ya, haka ne mutane dayawa za so gaskanta da Yesu a bayan an kashe shi, an binne shi, ankuma ta da shi daga mattatu.
A nan "son ransa" ya na nufin yadda ka na duba rai na jikinka da amfani fiye da rayukan wadansu. AT: "duk wadda ya na ɗaukakar ransa fiye da wadansu ba zai karɓi rai na har abada ba"
A nan wanda ya "ki ransa" ya na nufin wanda ya na son ran wadansu fiye da ransa. AT: "duk wanda ya ɗauki rayukan wadansu da muhiminci fiye da ransa zai rayu da Allah har abada"
Yesu ya na nufin cewa wadanda sun bauta masa ne za su kasance tare da shi a cikin sama. AT: "Bawa na zai kasance tare da ni a wurin, loƙacin da ina cikin sama"
A nan "Uba" muhimmin lakabi ne wa Allah.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne. Kodashike Yesu ya so ya ki giciye, ya zaba ya yi biyyaya ga Allah a kuma kashe shi. AT: "Ba zan yi addu'a, 'Uba, ka cece ni gaga wannan sa'a!'"
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
A nan "wannan sa'a" magana ne da ya na wakilcin loƙacin da Yesu zai sha wahala ya kuma mutu a kan giciye.
A nan kalmar "suna" magana ne da ya na nufin Allah. AT: "sa ɗaukakar ka sananne" ko "bayyana ɗaukakar ka"
Wannan ya na wakilcin maganar Allah. Wadansu loƙaci, mutane su na kin kiran Allah domin suna daraja shi. AT: "Allah ya yi magana daga sammai"
A nan "wannan duniya" ya na nufin dukka mutane a cikin duniya. AT: "Yanzu ne loƙaci da Allah zai sharanta dukka mutane"
A nan "mai mulki" ya na nufin shaiɗan. AT: "Yanzu ne loƙacin da zan hukunta ikon shaiɗan da ya na mulkin wannan duniya"
Yesu ya na nufin giciyewarsa. AT: "A loƙacin da mutane sun daga ni sama a kan giciye"
Ta wurin giciyensa, Yesu zai tanada hanyar wa kowa don ya gaskanta da shi.
Yahaya ya fasara kalmomin Yesu cewa mutane za su giciye shi. AT: "Ya faɗi wannan domin ya sa mutanin su san yadda zai mutu"
Jumlar "daga" ya na nufin giciye. Za ku iya fasara shi da karin "a kan giciye." AT: "dole ne a daga dan mutum a kan giciye"
AT: 1) "Menene ainahin wannan Ɗan Mutum? ko kuma 2) "Wa ne irin Ɗan Mutum ne ka na magana a kai?"
A nan "haske" ya na nufin koyarswar yesu da ya bayyana gaskiyar Allah. Yi "tafiya cikin duhu" magana ne da ya na nufin yin rayuwa da ba tare da gaskiyar Allah ba. AT: "Magana ta ya na nan kamar haske ne a gareku, domin ya taimake ku ku fahimci yadda za ku yi rayuwa kamar yadda Allah ya na so ku yi. Ba zan kasance tare da ku sosai ba. Yakamata ku bi dokokina tun ina tare da ku. Idan kun ki magana ta, zai zama kamar tafiya ne a cikin duhu kuma ba za ku iya ganin inda za ku je ba"
"Haske" magana ne na koyarswar Yesu da ya bayyana gaskiyar Allah. "'ya'yan haske" magana ne na wadanda sun karɓa sakon Yesu kuma su na rayuwa a bisa gaskiyar Allah. AT: "Tun ina tare da ku, ku gaskanta da abin da ina koyar maku domin gaskiyar Allah ya kasance da ku"
AT: "domin a cika sakon annabi Ishaya"
Wannan ya bayyana kamar tambaya ne da baya neman amsa domin ya nuna tsoratawar annabin cewa mutanin basu gaskanta da sakon shi ba. AT: "Ubangiji, Da ker ne idan wanni ya gaskanta da sakon mu, kodashike sun gan cewa ka na da ikon cece su!"
Wannan magana ne da ya na nufin ikon ceton Ubangiji.
A nan "zuciya" magana ne na hankalin mutum. Jumlar "taurare zuciyarsu" magana ne na sa wani ya zama da taurin kai. Kuma, "fahimta da zuciyarsu" ya na nufin "fahimta sosai." AT: "ya sa su taurin kai ... fahimta sosai"
A nan "juyo" magana ne na "tuba." AT: "kuma za su tuba"
AT: "domin kada mutane su hana su daga tafiya zuwa majami'a.
"Sun so mutane su yaɓe su fiye da yadda sun so Allah ya yaɓe su"
A nan Yahaya ya na nufin cewa taron mutane sun taru domin su ji Yesu ya yi magana. AT: "Yesu ya yi wa taron da suka taru ihu"
A nan kalmar "shi" ya na nufin Allah. AT: "wanda ya gan ni ya gan Allah, wadda ya aike ni"
Yesu ya cigaba da magana da taron.
A nan "haske" magana ne na gurbin Yesu. AT: "Na zo ne in nuna gaskiyan"
A nan "duhu" magana ne na yin rayuwa a rashin sanin gaskiyar Allah. AT: "ba za ya cigaba da makanta a ruhaniya ba"
A nan "yi wa duniya hukunci" ya na nufin hukunci. Yesu bai zo don ya hukunta mutane ba. AT: "idan wani ya ji koyarswa ta ya kuma ki, ban hukunta shi ba. Ban zo don in hukunta mutane ba. Maimako, Na zo ne don in cece wadanda sun gaskanta da ni"
"a lokacin da Allah ya na hukunta zunuban mutane"
"Na san cewa kalmomin da ya umurce ni in fada kalmomi ne da ya na ba da rai na har abada"
1Kamin bukin idin ketarewa, sa'adda Yesu ya san lokaci ya yi da zai tashi daga wannan duniya zuwa wurin Uba, da yake ya kaunaci nasa wadanda ke duniya- ya kaunace su har karshe. 2Iblis ya rigaya ya sa a zuciyar Yahuza Iskariyoti dan Saminu, ya bashe da Yesu.3Ya san cewa Uba ya bada kome a hannunsa, kuma ya zo daga wurin Allah, kuma zai koma wurin Allah. 4Ya tashi daga cin abincin, ya tube tufafinsa, ya dauki tawul ya lullube kansa da shi. 5Sa'an nan ya zuba ruwa a bangaji, ya fara wanke kafafun almajiran, yana shafe su da tawul din da ya lullube jikinsa da shi.6Ya zo wurin Bitrus Saminu, sai Bitrus ya ce masa,"Ubangiji, za ka wanke mani kafa?" 7Yesu ya amsa ya ce, "Abin da nake yi ba za ka fahimce shi yanzu ba, amma daga baya za ka fahimta." 8Bitrus ya ce masa, "Ba za ka taba wanke mani kafa ba." Yesu ya amsa masa ya ce, "In ban wanke maka ba, ba ka da rabo da ni". 9Bitrus ya ce masa, "Ubangiji, ba kafafuna kadai za ka wanke ba, amma da hannayena da kaina."10Yesu ya ce masa, "Duk wanda ya yi wanka ba ya da bukata, sai dai a wanke kafafunsa, amma shi tsarkakakke ne baidaya; ku tsarkakakku ne, amma ba dukanku ba." 11(Don Yesu ya san wanda zai bashe shi, shiyasa ya ce, "Ba dukanku ne ke da tsarki ba.")12Bayan Yesu ya wanke masu kafafu, ya dauki tufafinsa ya zauna kuma, ya ce masu, "Kun san abin da na yi muku? 13kuna kirana, 'Malam, da Ubangiji,' kun fadi daidai, don haka Nake. 14Idan ni Ubangiji da kuma mallam, na wanke maku kafafu, ya kamata kuma ku wanke wa junan ku kafafu. 15Gama na baku misali, saboda ku yi yadda na yi maku.16Lalle hakika ina gaya muku, bawa ba ya fi mai gidansa girma ba; dan aike kuma ba ya fi wanda ya aiko shi girma ba. 17Idan kun san wadannan abubuwa, ku masu albarka ne idan kun aikata su. 18Ba ina magana akan dukanku ba; Na san wadanda na zaba. Amma domin Nassi ya cika: 'Shi Wanda ya ci gurasata, ya tayar mani'.19Ina fada maku wannan yanzu tun kafin haka ta faru domin sa'adda ta faru, ku gaskata Ni ne. 20Hakika, hakika, Ina gaya maku, wanda ya karbi wanda na aiko, Ni ya karba, wanda kuma ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni.21Bayan Yesu ya fadi haka, ya damu a ruhu, ya yi shaida ya ce, "Lalle hakika, ina gaya muku cewa daya daga cikinku zai bashe ni." 22Almajiran suka kalli juna, suna juyayin ko akan wa yake magana.23Daya daga cikin almajiransa, wanda Yesu yake kauna, yana a teburi, jingine a kirjin Yesu. 24Siman Bitrus ya ce wa almajirin, "ka fada mana ko akan wa ya ke magana." 25Sai ya sake jingina a kirjin Yesu, ya ce masa, "Ubangiji, wanene?"26Sannan Yesu ya amsa, "Shine wanda zan tsoma gutsuren gurasa in ba shi." Sannan bayan ya tsoma gurasar, sai ya ba Yahuza Dan Siman Iskariyoti. 27To bayan gurasar, sai shaidan ya shige shi, sai Yesu ya ce masa, "Abinda kake yi, ka yi shi da sauri."28Babu wani a teburin da ya san dalilin dayasa ya fada masa wannan. 29Wadansu sun yi tsamanin cewa, tun da Yahuza ne ke rike da jakkar kudi, Yesu ya ce masa, "Ka sayi abinda muke bukata don idin", ko kuma ya bada wani abu domin gajiyayyu. 30Bayan Yahuza ya karbi gurasar, sai ya fita nan da nan. Da daddare ne kuwa.31Bayan Yahuza ya tafi, Yesu ya ce, "Yanzu an daukaka Dan mutum, kuma an daukaka Allah a cikinsa. 32Allah zai daukaka shi a cikin kansa, kuma zai daukaka shi nan da nan. 33'Ya'ya kanana, ina tare da ku na wani gajeren lokaci. Zaku neme ni, kuma kamar yadda na fadawa Yahudawa, 'in da zan tafi ba za ku iya zuwa ba.' Yanzu kuma na fada maku wannan.34Ina baku sabuwar doka, ku kaunaci juna; kamar yadda na kaunace ku, haka kuma ku kaunaci juna. 35Ta haka kowa zai san ku almajiraina ne, idan kuna kaunar juna."36Siman Bitrus ya ce masa, "Ubangiji, ina za ka?" Yesu ya amsa ya ce, "Inda za ni, ba zaka iya bi na ba yanzu, amma zaka bini daga baya." 37Bitrus ya ce masa, "Ubangiji, don me ba zan iya binka a yanzu ba? Zan bada raina domin ka." 38Yesu ya amsa ya ce, "Za ka bada ranka domina? Lalle hakika, ina gaya maka, kafin zakara ya yi cara zaka yi musu na sau uku."
Ketarewa bai kai ba kuma Yesu ya na tare da almajiransa a abincin dare. Wadannan ayoyin sun bayyana shirin wannan labari, sun kuma ba da tushen bayani game da Yesu da Yahuza.
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
Wannan irin kauna ya na zuwa daga Allah ne ya na bisa kyaun mutane, ko bai amfani wani ba. Irin wannan kauna ya na kula da mutane, ko mai abin da sun yi
Jumlar "sa a zuciyar" karin magana ne da ya na nufin a sa wani ya yi tunanin wani abu. AT: "Iblis ya riga ya sa Yahuza Iskariyoti, dan Saminu, da yin tunanin cin amanar Yesu"
Aya uku ya cigaba da gaya mana game da tushen bayani game da abin da Yesu ya sani. Abin ya fara a aya hudu.
A nan "hannunsa" magana ne da ya na nufin iko da karfi. AT: "ya ba ni cikakken iko a komai"
Yesu ya saba kasancewa da Uban, kuma zai koma wurin bayan aikinsa a duniya ya kare.
Domin yankin na da kura, al'ada ne wa mai gidan da ya ba da abincin ya ba da bawan da zai wanke kafafun baki.
Tambayar Bitrus ya nuna cewa bai so Yesu ya wanke mashi kafa. AT: "Ubangiji, ba daidai ba ne ka wanke mani kafa na ba, mai zunubir!"
Yesu ya yi magana domin ya sa Bitrus ya yarda ya wanke mashi kafa. Yesu ya na nufin cewa dole Bitrus ya yarda Yesu ya wanke masa kafa idan ya na so ya cigaba da zama almajiransa. AT: "Idan na wanke ka, kullum za ka kasance nawa"
A nan "wanka" magana ne da ya na nufin cewa Allah ya wanke ruhaniyar mutum. AT: "Idan wani ya riga ya karbi yafewar Allah, yanzu ya kamata ya karbi wankewa daga zunubansa na kullum"
Yesu ya na nufin cewa wadda zai bashe shi, Yahuza, bai gaskanta da shi ba. Don haka Allah bai yafe masa zunubansa ba. AT: "Ba dukkan ku ne kun karbi yafewar Allah ba"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne don Yesu ya iya bayana muhimincin abin da ya na koyar wa almajiransa. AT: "Ya kamata ku fahimci abin da na yi maku!"
A nan Yesu ya na nufin cewa almajiransa su na da babban daraja masa. AT: "Kun nuna mani babban daraja a lokacin da kun kira ni "Mallam" da "Ubangiji."
Yesu ya na nufin cewa almajiransa su yarda su bi gurbinsa su kuma bauta wa junansu. AT: "ku kuma bauta wa junanku da ladabi"
Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 1:51.
wanin da yafi muhiminci ko iko, ko wanin da ya kamata ya sami saukin rayuwa ko dadin rayuwa sosai.
A nan "albarka" na nufin sa kyaun abubuwa su faru da mutum. AT: "Allah zai albakarkance ka"
AT: "wannan domin nassi ya cika"
Jumlar "ci gurasata" anan karin magana ne na wani da ya na yi kamar aboki. Jumlar "tayar" magana ne kuma daya na nufin mutum da ya zama abokin gaba. Idan ku na da karin magana a harshen ku da ke da wannan ma'ana, za ku iya yin amfani da shi anan. AT: "wadda ya yi kamar shi abokina ne ya koma ya zama makiya na"
"Inna gaya maku abin da zai faru yanzu kafin ya faru"
"Za ku iya gaskanta cewa ni ne wadda na ce ni ne" ko "Za ku iya gaskanta cewa ni ne mai ceto"
damu
"Almajiran sun kalli juna da mamaki: "Wa nene zai ci amanar Yesu?
Wannan ya na nufin Yahaya.
A zamanin Almasihu, Yahudawa su na yawan cin abinci tare kamar salon Greek, wadda suke zauna a gefe daya a kujeru kanana.
An dauke kukwance da kai a gefen wani mai cin abinci a salon Greek kamar nuna babban kauna ne a sakaninsu.
Wannan ya nuna cewa Yahuza daga kawyen Kerot ne.
An fahimci kalmomin "Yahuza ya dauke" a mahalli.
Wannan karin magana ne da ya na nufin shaiɗan ya dauki cikakken shugabancin Yahuza. AT: "Shaiɗan ya dauke shugabancinsa" ko "Shaiɗan ya fara umurce shi"
A nan Yesu ya na magana da Yahuza.
"Ya sauri da abin da ka ke shirin aikatawa!"
"je ka ba da kudade wa talakawa."
Yahaya ya so ya jawo hankali da cewa Yahuza zai aikata muguntarsa ko ayyukan "duhu" a cikin duhun dare. AT: "ya fita nan da nan cikin duhun dare"
AT: "Yanzu mutane za su ga yadda Ɗan Mutum zai karba daukaka kuma da yadda Allah zai karbi daukaka ta wurin abin da Ɗan Mutum ya ke yi"
Kalmar "shi" ya na nufin Ɗan Mutum. Wannan kalmar "kansa" magana ne da ya na nufin Allah. AT: "Allah zai ba da daukaka wa Ɗan Mutum nan da nan"
Yesu ya yi amfani da wannan magana "'Ya'ya kanana" domin ya nuna cewa ya na kaunar almajiransa kamar su 'ya'yan shi ne.
A nan "Yahudawa" magana ne na shugabanin Yahudawa da su ka yi hamayya da Yesu. AT: "kamar yadda na faɗawa Yahudawa"
Wannan irin kauna ya na zuwa daga Allah ne ya na bisa kyaun mutane, ko bai amfani wani ba. Irin wannan kauna ya na kula da mutane, ko mai abin da sun yi
Za ku iya sa a bayyane cewa wannan zuguiguitawa ya na nufin mutane da suka gan yadda almajiran sun kaunace juna.
"ba da raina" ko "mutu"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin karin bayani game maganar Yesu. AT: "Ka ce za ka mutu domina, amma gaskiyan shi ne ba za ka yi ba!"
"za ka ce baka san ni sau uku kafin zakara ya yi cara"
1"Kada zuciyarku ta bachi. Kun gaskata da Allah, sai kuma ku gaskata da ni. 2A gidan Ubana akwai wurin zama dayawa. Da ba haka ba, da na fada maku, domin zan tafi in shirya maku wuri. 3In kuwa na je na shirya maku wuri, zan dawo in karbe ku zuwa wurina domin inda nake kuma ku kasance.4Kun san hanya inda zan tafi." 5Toma ya ce wa Yesu, "Ubangiji, bamu san inda za ka tafi ba, yaya za mu san hanyar?" 6Yesu ya ce masa, "Ni ne hanya, ni ne gaskiya, ni ne rai; Ba mai zuwa wurin Uba sai ta wurina. 7Da kun san ni, da kun san Ubana kuma. Amma daga yanzu kun san shi, kuma kun gan shi."8Filibus ya ce wa Yesu, "Ubangiji, ka nuna mana Uban, wannan za ya ishe mu." 9Yesu ya ce masa, "Ina tare da ku da dadewa, amma har yanzu baka san ni ba, Filibus? Duk wanda ya gan ni, ya ga Uban. Yaya za ka ce, 'Nuna mana Uban'?10Baka gaskata cewa Ina cikin Uban, Uban kuma yana ciki na ba? Maganganun da nake fada maku, ba da ikona nake fadi ba, amma Uban ne da yake zaune a ciki na yake yin ayyukansa. 11Ku gaskata ni cewa ina cikin Uban, Uban kuma na ciki na, ko kuwa ku bada gaskiya domin ayyukan kansu.12"Lalle hakika, ina gaya maku, duk wanda ya gaskata ni zai yi ayyukan da nake yi, kuma zai yi ayyuka fiye da wadannan, domin zan tafi wurin Uba. 13Duk abinda kuka roka da sunana, zan yi shi domin a daukaka Uban cikin Dan. 14Idan kuka roke ni komai cikin sunana, zan yi shi.15"Idan kuna kaunata, za ku kiyaye dokokina. 16Sa, annan zan yi addu'a ga Uba, zai kuwa baku wani mai ta'aziya domin ya kasance tare daku har abada. 17Ruhun gaskiya. Wanda duniya ba zata iya karba ba, domin bata gan shi ba, ko ta san shi. Amma ku kun san shi, domin yana tare da ku, zai kuma kasance a cikin ku.18Ba zan barku ku kadai ba; zan dawo wurin ku. 19Sauran dan gajeren lokaci, duniya kuma ba zata ka ra gani na ba, amma ku kuna gani na. Saboda ina raye, kuma zaku rayu. 20A wannan rana zaku sani ina cikin Ubana, ku kuma kuna ciki na, ni ma ina cikin ku.21Shi wanda yake da dokokina yake kuma bin su, shine ke kauna ta, kuma shi wanda ke kauna ta Ubana zai kaunace shi, Ni ma kuma zan kaunace shi in kuma bayyana kaina gare shi." 22Yahuza (ba Iskariyoti ba) ya ce ma Yesu, "Ubangiji, meyasa za ka bayyana kanka a gare mu, ba ga duniya ba?"23Yesu ya amsa ya ce masa,"Kowa yake kauna ta, zai kiyaye maganata. Ubana kuwa zai kaunace shi, za mu zo wurinsa mu zauna tare da shi. 24Shi wanda baya kauna ta, ba ya kiyaye maganganuna. Maganar da kuke ji ba daga gareni take ba, amma daga Uba wanda ya aiko ni take.25Na fada maku wadannan abubuwa, sa'adda nake tare da ku. 26Saidai, mai ta'aziyar- Ruhu Mai Tsarki wanda Uba zai aiko cikin sunana, zai koya maku kome, kuma zai tunashe ku dukan abinda na fada maku. 27Na bar ku da salama; ina ba ku salamata. Ba kamar yadda duniya ke bayarwa Nake bayarwa ba. Kada zuciyarku ta baci, kuma kada ku tsorata.28Kun ji dai na fada maku, 'zan tafi, kuma Zan dawo gare ku'. Idan kuna kaunata, za ku yi farinciki domin za ni wurin Uban, gama Uban ya fi ni girma. 29Yanzu na fada maku kafin ya faru, domin idan ya faru, ku gaskata.30Ba zan kara magana mai yawa da ku ba, domin mai mulkin duniyan nan yana zuwa. Bashi da iko a kai na, 31amma domin duniya ta san cewa ina kaunar Uban, Ina yin daidai abinda Uban ya Umarce ni. Mu tashi mu tafi daga nan.
An cigaba da sashin labarin daga Aya da ta wuce. Yesu ya ja baya a teburin da almajiransa sai ya cigaba da magana da su.
A nan "zuciya" magana ne na cikin mutum. AT: "daina damuwa"
"akwai wuraran zama dayawa a gidan Ubana"
Wannan ya na nufin sama, wurin da Allah ya na zama.
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
Kalmar "daki" ya na iya nufin daki ɗaya, ko babban wurin zama.
Yesu zai shirya wuri a sama wa kowane mutum da ya gaskanta da shi. "Ku" ya na nufin dukka almajiransa.
"ta yaya zamu san yadda za mu kai wurin?"
AT: 1) "hanya zuwa Allah" ko 2) "wadda ya ke kai mutane zuwa wurin Allah."
AT: 1) "mutumin gaskiyan" ko 2) "wadda ya ke fada kalmomin gaskiya game da Allah."
Wannan magana ne da ya na nufin cewa Yesu zai iya ba da rai wa mutane. AT: "Wadda zai iya san mutane su rayu"
Mutane za su iya zuwa wurin Allah su kuma yi rayuwa da shi idan sun gaskanta da Yesu. AT: "Babu wadda zai iya zuwa wurin Uba ya yi rayuwa da shi sai dai ta wurinsa"
"Uba" muhimmin lakabi ne wa Allah.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin a kara nanata kalmomin Yesu. AT: "Filibus, Na kasance tare da ku almajirai na tsawon loƙaci. Ya kamata kun san ni yanzu!" zu
Ganin Yesu, wadda shi ne Allah, shi ne ganin Allah Uba. "Uba" muhimmin lakabi ne wa Allah.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin a nanata maganar Yesu wa Filibus. AT: " Kada ku dinga ce, "nuna mana Uban!'"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin a nanata maganar Yesu wa Filibus. AT: "yakamata ka gaskanta ... ciki na."
"Abin da ina faɗa maku ba daga ni bane" ko "kalmomin da na faɗa ma ku ba daga ni ba ne"
Yanzu Yesu ya na magana da dukka almajiransa.
Wannan karin magana ne da ya na nufin Allah Uba kuma Yesu ya na da dangantaka da babu kamarsa. AT: "Ni ɗaya ne da Uba, kuma Uban ya na tare da ni" ko kuma "Ni da Uba na muna nan kamar ɗaya ne"
Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 1:51.
Wannan ya na nufin cewa Yesu ne Ɗan Allah.
A nan "suna" magana ne da ya na wakilcin ikon Yesu. AT: "Duk abin da kun roke ni, da amfani da iko na"
AT: "don in iya nuna wa kowa yadda Uba na yake"
Waɗannan muhimmin lakabi ne da ya na kwatanta dangantaka a sakanin Allah da Yesu.
A nan "suna" magana ne da ya na wakilcin ikon Yesu. AT: "Idan kun tambaye ni komai kamar masubi na, zan yi shi" ko kuma "Duk abin da kun tambaye ni, zan yi shi domin ku nawa ne"
Wannan ya na nufin Ruhu mai Tsarki.
Wannan ya na nufin Ruhu mai tsarki wadda ya na koya wa mutane abin da ya ke gaskiya game da Allah.
A nan "duniya" magana ne da ya na nufin mutane da su na hamayya da Allah. AT: "mutane da ba su gaskanta ba za su marabshe shi ba" ko kuma "Wadda su na hamayya da Allah ba za su karbe shi ba"
Anan yesu ya na nufin cewa ba zai bar almajiran shi kaɗai ba tare da wadda zai kula da su ba. AT: "barku kaɗai ba tare da wadda zai kula da ku"
A nan "duniya" magana ne da ya na wakilcin mutane da ba na Allah ba. AT: "marasa bi"
Allah Uba da Yesu sun zauna kamar mutum ɗaya. AT: "za ku san cewa Ubana da Ni ɗaya ne kamar mutum ɗaya"
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
"Ni da Ku muna nan kamar mutum ɗaya"
Wannan irin kauna ya na zuwa daga Allah ne ya na bisa kyaun mutane, ko bai amfani wani ba. Irin wannan kauna ya na kula da mutane, ko mai abin da sun yi
AT: "Ubana zai kaunace duk wadda ya kaunace ni"
Wannan ya na nufin wani almajiri wadda sunan sa Yahuza, ba ga almajiri wadda ya na daga ƙaukyen Keriot wadda ya ci amanar Yesu ba.
A nan kalmar "nuna" ya na nufin bayyana al'ajibin Yesu. AT: "Don me za ka bayyana kanka wa mu kadai" ko " Don me ba za ka bar mu mu gan al'ajibin ka ba?"
A nan "duniya" magana ne da ya na wakilcin mutane da suna hamayya da Allah. AT: "ba ga wadda ba su gaskanta da Allah ba"
"Wadda ya na kauna na zai yi abin da na gaya masa ya yi"
Uban da Ɗan za su yi rayuwa da waɗanda su na biyayya da abin da Yesu ya umurta. AT: "za mu zo mu zauna da shi, mu kuma samu dangantaka da shi"
"Abubuwan da na gaya maku ba abubuwan da na su in faɗa da kaina ba ne"
"sakon"
Loƙacin da Yesu ya ce "ku" ya na magana da dukkan almajiransa ne.
A nan kalmar "suna" magana ne da ya na wakilcin ƙarfi da ikon Yesu. AT: "saboda ni"
"duniya" magana ne da ya na wakilcin mutane da ba su kaunar Allah.
A nan "zuciya" magana ne da ya na wakilcin cikin mutum. AT: "Don haka ku daina damuwa, kuma kada ku ji tsoro"
Wannan irin kauna ya na zuwa daga Allah ne ya na bisa kyaun mutane, ko bai amfani wani ba. Irin wannan kauna ya na kula da mutane, ko mai ne abin da sun yi
A nan Yesu ya na nufin cewa zai koma wurin Uban shi. AT: "Zan koma wurin Uban"
A nan Yesu ya na nufin cewa Uban ya na da babban iko fiye da Ɗan sai kuma Ɗan ya na kan duniya. AT: "Uban ya na da babban iko fiye da yadda na ke da shi a nan"
A nan "mai mulki" ya na nufin Shaidan. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 12:31. AT: "Shaidan da yake mulkin wannan duniya"
A nan Yesu ya na nufin cewa Shaidan ya na zuwa ya yi mashi hari. AT: "shaidan ya na zuwa ya yi mani hari"
A nan "duniya" magana ne wa mutane da ba na Allah ba ne. AT: "domin waɗanda ba na Allah ba su iya sani"
Wannan muhimmin laƙani ne wa Allah.
1"Nine itacen inabi na hakika, Ubana kuwa shi ne manomin. 2Yakan cire duk wani rashe a cikina da ba ya bada 'ya'ya, mai bada 'ya'ya kuwa ya kan gyara shi domin ya kara bada 'ya'ya.3Kun rigaya kun tsarkaka saboda maganar da na yi muku. 4Ku zauna ciki na, Ni kuma cikin ku. Kamar yadda reshe ba ya iya bada 'ya'ya shi kadai sai ya zauna cikin itacen, haka kuma ba za ku iya ba, sai kun zauna ciki na.5Ni ne itacen inabi, ku ne rassan. Wanda ya zauna ciki na, ni kuma cikin sa, yana bada 'ya'ya dayawa, gama in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba. 6Wanda kuma bai zauna a ciki na ba, akan jefar da shi kamar reshe, ya bushe, kuma sukan tattara rassan su jefa a wuta, su kone. 7In kun zauna a ciki na, maganata kuma ta zauna a cikin ku, sai ku roki duk abinda kuke so, za a kuwa yi maku.8Ta haka ake daukaka Ubana: cewa ku bada 'ya'ya dayawa, kuma cewa ku almajiraina ne. 9Kamar yadda Ubana ya kaunace ni, haka Ni ma na kaunace ku; Ku zauna cikin kaunata.10Idan kun kiyaye dokokina, za ku zauna cikin kaunata kamar yadda Na kiyaye dokokin Ubana, na kuma zauna cikin kaunarsa. 11Ina gaya maku wadannan al'amura domin farincikina ya kasance a cikin ku, kuma domin farincikinku ya zama cikakke.12"Wannan shine umarnina, cewa ku kaunaci juna kamar yadda na kaunace ku. 13Babu wanda ke da kaunar da tafi haka, wato ya bada ransa domin abokansa.14Ku abokaina ne idan kuna yin abubuwan da na umarce ku. 15Nan gaba ba zan kara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abinda Ubangijinsa ke yi ba. Na kira ku abokaina, domin na sanar da ku duk abinda na ji daga wurin Ubana.16Ba ku kuka zabe ni ba, amma Ni ne na zabe ku, na aike ku don ku je ku bada 'ya'ya, 'ya'yanku kuma su tabbata. Wannan ya zama domin duk abinda kuka roki Uba a cikin sunana, zai baku. 17Na baku wannan umarni: domin ku kaunaci juna.18In duniya ta ki ku, ku sani cewa ta kini kafin ta ki ku. 19Da ku na duniya ne, da duniya ta kaunace ku kamar nata. Amma saboda ku ba na duniya bane, na kuma zabe ku daga duniya, don haka duniya take kin ku.20Ku tuna da maganar da na yi muku, 'Bawa ba ya fi Ubangijinsa girma ba.' Idan sun tsananta mani, ku ma za su tsananta maku; Idan sun kiyaye maganata, za su kuma kiyaye maganarku. 21Za su yi maku duk wadannan abubuwa saboda sunana, don basu san wanda ya aiko ni ba. 22Da ban zo na yi masu magana ba, da basu da zunubi, amma yanzu, basu da wata hujja don zunubinsu.23Duk wanda ya ki ni ya ki Ubana. 24Da ban yi ayyukan da babu wanda ya taba yinsu a cikin su ba, da basu da zunubi, amma yanzu sun gani, sun kuma ki ni da Ubana duka. 25An yi wannan kuwa domin a cika maganar da ke rubuce a cikin shari'arsu, ' Sun ki ni ba dalili.'26Sa'adda Mai Ta'aziya- wanda zan aiko maku daga wurin Uban, wato, Ruhun gaskiya, wanda ke fita daga wurin Uban-ya zo, zai bada shaida a kai na. 27Ku ma kuna bada shaida saboda kuna tare da ni tun daga farko.
An cigaba da sashin labarin daga Aya da ta wuce. Yesu ya ja baya a teburin da almajiransa sai ya cigaba da magana da su.
A nan "itacen inabi" karin magana ne. Yesu ya kwatanta kansa da itacen inabi. Shi ne tushen rai da ya na sa mutane su rayu a hany da ya cancanci Allah. AT: "ina nan kamar itacen inabi da yake ba da 'ya'ya mai kyau.
"manomin" karin magana ne. "Manomi" mutum ne wadda ya na kula da itacen inabi don ya gan ya ba da 'ya'ya. AT: "Ubana ya na nan kamar manomi"
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
A nan "duk wani rashe" ya na wakilcin mutane, kuma "'ba da 'ya'ya ya na wakilcin yin rayuwa a hanyar da Allah yake so.
"sare da cire"
"shirya kowane rashe"
Maganar da ana nufi a nan shi ne "tsarkakar reshe" wadda an riga an "gyara." AT: "Kamar an riga an gyara ku kuma ku tsarkakan reshe ne domin kun yi biyayya da abin da na koya maku"
Kalmar "ku" ya na nufin almajiran Yesu.
"Idan kun zauna a hade da ni, zan zauna a hade da ku"
Ta wurin zauna a cikin Almasihu, wadda sun zama na shi su na dogara akan shi don kokai. AT: "sa dai kun kasance a hade da ni ku kuma dogara da ni ma komai"
"itacen inabi" magana ne da ya na wakilcin Yesu. "rassan" magana ne da ya na wakilcin wadda su na gaskanta da Yesu sun kuma zama na shi. AT: "Ina nan kamar itacen inabi, kuma ku na nan kamar rassan da ya ke a haɗe da itacen inabi"
A nan Yesu ya na nufin cewa masubinsa su na a haɗe da shi kamar yadda ya na a haɗe da Allah. AT: "shi wadda ya zauna a haɗe da ni, kamar yadda ina zaune a haɗe da Ubana"
Maganan ana ya na nufi reshe mai ba da 'ya'ya wadda ya na wakilcin maibi da ya na sa Allah jin daɗi. Yadda reshe da ya na a haɗe da itacen inabi ya na ba da 'ya'ya dayawa, waɗanda sun kasance a haɗe da Yesu za su yi abubuwa dayawa da zai sa Allah ya ji dadi. AT: "za ku ba da 'ya'ya dayawa"
Maganan anan shi ne reshe mara ba da 'ya'ya da ya na wakilcin waɗanda ba su a haɗe da Yesu. AT: "mai gyaran itacen inabi ya na jefad da shi kamar reshe kuma ya na bushe"
AT: "wutan ya na kone su"
Yesu ya na nufin cewa dole masubi su roki Allah ya amsa adduwowinsu. AT: "roki Allah komai da ku ke so"
AT: "zai yi maku"
AT: "Ya na sa mutane su girmama Ubana"
A nan "ya'ya" magana ne na yin rayuwa don ku sa Allah ya ji dadi. AT: "loƙacin da kun yi rayuwa a hanya da zai ya na sa shi jin dadi"
"nuna cewa ku almajirai na ne"
Yesu ya ba da kaunar da Allah Uba ya na da shi mashi da kuma wadda su na kaunar sa. Anan "Uba" muhimmin lakabi ne wa Allah.
"cigaba amincewa da kuana ta"
Loƙacin da masubin Yesu sun yi masa biyayya, su na nuna kaunar su masa. AT: "loƙacin da kun yi abubuwan da na gaya maku ku yi, ku na zama a cikin kauna ta, kamar yadda ina yin biyayya ga Ubana da kuma zama a cikin kaunarsa"
"Na riga na gaya ma ku wannan abubuwa domin ku sami irin farinciki da ina da shi"
AT: "domin ku zama cikakke da farinciki" ko "domin farincikinku kada ya rasa komai"
Irin wannan kauna ya na zuwa ne daga Allah kuma ya na son amfanin sauran, ko bai amfane shi ba. Irin wannan kauna ya na lura da sauran, ko da me sun yi. AT: "Ba za ku samu babban kauna kamar wannan ba"
Wannan ya na nufin rai na jiki.
"Na gaya maku dukka abin da Uba na ya gaya ma ni"
Yesu ya na nufin cewa ba masubin sa ne suka zeɓa da kansu cewa za su zama almajiransa ba. AT: "Ba ku zaba cewa ku zama almajirai na ba"
A nan "'ya'ya" magana ne da ya na wakilcin rayuwa da ya na girmama Allah. AT: "yi rayuwar da zai girmama Allah"
"cewa abin da ku ka yi ya dadai har abada"
A nan "suna" magana ne da ya na wakilcin ikon Yesu. AT: "Domin ku nawa ne, duk abin da kun roke Uban, zai ba ku shi"
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
Yesu ya yi amfani da wannan kalmar "duniya" a waɗannan ayoyin kamar magana ne da ya na nufin mutane da ba na Allah ba kuma suna hamayya da shi.
Wannan ya na nufin kauna na mutum, kauna na 'yan'uwa ko kauna wa aboki ko ɗan gida.
A nan "maganar" sako ne na Yesu. AT: "Ku tuna da sakon da na faɗa ma ku"
A nan "saboda sunana" magana ne da ya na wakilcin Yesu. Mutane za su sa masubinsa su sha wahala domin su nashi ne. AT: "domin ku nawa ne"
Yesu ya na nufin anan cewa ya ba da sakon Allah tare da wadda ba su yarda da shi ba. AT: "Domin na zo in gaya masu sakon Allah, ba su da hudja a loƙacin da Allah zai hukunta su domin zunubansu"
Kin Allah Ɗan shi ne kin Allah Uba.
Wannan muhimmin laƙani ne wa Allah.
AT: "Domin na yi a cikinsu ayyukan da ba bu wani da ya yi. da basu da zunubi, kuma"
"ba su da wani zunubi." Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 15:22.
"Maganar" dukka sakon Allah. AT: "domin a cika annabci a cikin shari'arsu "
Wannan ya na nufin Tsohon Alkawari, wadda ya na da dukka dokokin Allah ga mutane.
Wannan ya na nufin Ruhu mai Tsarki. Dubi yadda an fasara wannan a cikin 14:16.
Allah Uba ya aiko Allah Ruhu don ya nuna wa duniya cewa Yesu shi ne Allah Ɗa.
Wannan lakabi ne wa Ruhu mai Tsarki. AT: "Ruhun da ya na faɗan gaskiya game da Allah da kuma ni"
A nan "shaida" ya na nufin gaya wa sauran game da Yesu. AT: "Ku kuma dole ne ku gaya wa kowa abin da kun sani game da ni"
A nan "farko" magana ne da ya na nufin farkon ranakun hidimar Yesu. AT: "Daga farkon ranakun da na fara koya wa mutane da kuma yin abubuwan a'lajibi"
1"Na fada maku wannan ne domin kada kuyi tuntube. 2Zasu fitar da ku daga majami'u. Amma, sa'a tana zuwa, wadda idan wani ya kasheku, zai yi zaton aikin Allah yake yi.3Za suyi haka ne kuwa domin ba su san Uban ko ni ba. 4Na fada maku wadannan abubuwa ne domin in lokacin da zasu faru yayi, ku tuna na fada maku." Ban fada maku wadannan abubuwa ba tun da farko, domin ina tare da ku.5Yanzu kuwa za ni wurin wanda ya aiko ni, duk da haka a cikinku, ba wanda ya tambaye ni, 'Ina za ka?' 6Amma saboda na fada maku wadannan abubuwa, bakin ciki ya cika zuciyarku. 7Amma ina gaya maku gaskiya: zai fi ye maku in na tafi. Domin in ban tafi ba, Mai Ta'aziyya ba zai zo gare ku ba, in kuwa na tafi, zan aiko shi gare ku.8Idan kuwa ya zo, Mai Ta'aziyyar zai fadarkar da duniya a kan zunubi, da adalci, da kuma hukunci. 9Game da zunubi, domin basu gaskata da ni ba, 10Game da adalci, domin za ni wurin Uba, kuma ba za ku sake ganina ba, 11game da hukunci kuma, domin an yanke wa mai mulki duniyan nan hukunci.12"Akwai abubuwa da yawa da zan gaya maku, amma ba za ku iya fahimta a yanzu ba. 13Saboda haka, sa'adda Ruhu na gaskiya ya zo, zai bishe ku a cikin dukan gaskiyar, domin ba zai yi magana don kansa ba, sai dai duk abin da ya ji, shi zai fada, zai kuma sanar da ku al'amuran da zasu faru. 14Zai daukaka ni, domin zai dauko abubuwa dake nawa ya sanar da ku.15Duk abinda Uba yake da shi, nawa ne. Domin wannan ne nace zai dauko abubuwa da yake nawa ya sanar da ku. 16"Bayan dan lokaci kadan, ba zaku kara ganina kuma ba. bayan dan lokaci kadan kuma, zaku gan ni."17Sai wadansu almajiransa sukace wa juna, "Me nene wannan da yake fadi mana, 'Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni?' da kuma, ' zan tafi wurin Uba'?" 18Saboda haka sukace, "Me nene wannan da yake fada, 'Bayan dan lokaci kadan'? Bamu san abinda yake fada mana ba."19Yesu kuwa ya ga suna so su tambaye shi, sai ya ce masu, "Wato kuna tambayar juna ne abinda nake nufi da cewa, "Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni'? 20Hakika, hakika, ina gaya maku, zaku yi kuka da makoki, amma duniya za ta yi farin ciki, zaku cika da bakin ciki, amma bakin cikinku zai koma farin ciki. 21Mace takan ji zafi lokacin da take nakuda don lokacin haihuwa ya zo. Amma da zarar ta haifi jinjirin nan, ba ta kara tunawa da zafin, domin ta na fariciki an haifi mutum a duniya.22To yanzu dai kuna bakin ciki, amma zan sake ganinku, kuma ba wanda zai iya kwace maku wannan farin ciki. 23A rannan, ba zaku tambaye ni komai ba. Hakika hakika, ina gaya maku, komai kuka roki Uba a cikin sunana zai ba ku shi. 24Harwa yau, ba ku roki komai cikin sunana ba. Ku roka, zaku karba, domin farin cikin ku ya zama cikakke."25"Na fada maku wadannan abubuwa cikin karin magana. Amma sa'a tana zuwa da ba zan kara fada maku komai ba cikin karin magana, amaimakon haka zan gaya maku komai a sarari game da Uba.26A ranar nan, zaku yi roko a cikin sunana kuma bance maku zan yi addu'a ga Uba a madadinku ba, 27domin Uba da kansa yana kaunarku, domin kun kaunace ni, kun kuma gaskata daga wurin Uban na fito. 28Daga wurin Uban na fito, kuma na shigo duniya. Har wa yau, kuma zan bar duniya in koma wurin Uba."29Almajiransa sukace, duba, "Yanzu kake magana a sarari, ba cikin karin magana ba! 30Yanzu mun sani ka san komai, ba sai wani ya tambaye ka ba. Ta haka muka gaskata daga wurin Allah ka fito." 31Yesu ya amsa masu yace, "Ashe, yanzu kun gaskata?32Duba, sa'a na zuwa, I, sa'ar ta yi, da za a warwatsa ku, kowa ya koma gidansa, kuma ku bar ni ni kadai. Duk da haka kuwa ba ni kadai nake ba, domin Ubana yana tare da ni. 33Na fada maku wannan ne domin a ciki na ku sami salama. A duniya kuna shan tsanani, amma ku karfafa: na yi nasara da duniya,"
An cigaba da sashin labarin daga Aya da ta wuce. Yesu ya ja baya a teburin da almajiransa sai ya cigaba da magana da su.
A nan jumlar "tuntube" ya na nufin daina gaskantawa a cikin Yesu. AT: "ba za ku daina gaskanta da ni ba domin wahalan da za ku gani"
"zai faru wata rana cewa mutum zai kashe ku, zai kuma yi tunani cewa ya na yin abu mai kyau ne wa Allah."
Za su kashe waɗansu masubi domin ba su san Allah Uba ko Yesu ba.
Wannan muhimmin laƙani ne wa Allah.
A nan "loƙaci" magana ne da ya na nufin loƙacin da mutane za su tsananta masubin Yesu. AT: "a loƙacin da za su sa ku ku sha wahala"
Wannan magana ne da ya na nufin ranakun farko na hidimar Yesu. AT: "a loƙacin da kun fara bi na"
A nan "zuciya" magana ne na cikin mutum. AT: "yanzu ku na bakin ciki"
AT: "sadai in na tafi ne mai Ta'aziyya zai zo wurin ku"
Wannan lakabi wa Ruhu mai Tsarki wadda zai kasance da almajiran bayan ya tafi. Dubi yadda kun fasar wannan a cikin 14: 26.
Loƙacin da Ruhu mai Tsarki ya zo, ya fara nuna wa mutane cewa su masu zunubi ne.
Wannan magana ne da ya na nufin mutane a cikin duniya.
"su na da laifin zunubi domin ba su gaskanta da ni ba"
"Idan na koma wurin Allah, kuma ba su gan ni kuma ba, za su san cewa na yi abubuwa da ya kamata"
"Allah zai rike su da alhaki kuma zai hukunta su domin zunuban su, kamar yadda zai hukunta Shaidan, wadda yake mulki da wannan duniya"
A nan "mai mulki" ya na nufin Shaiɗan. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 12:31. AT: "Shaiɗan da ya na mulki da wannan duniya"
"su sako maku" ko "kalmomi maku"
Wannan suna ne wa Ruhu mai Tsarki wadda zai gaya wa mutane game da Allah.
"Gaskiya" ya na nufin gaskiya ta ruhaniya. AT: "zai koya maku dukkan gaskiyar ruhaniya da za ku so ku sani"
Yesu ya na nufin cewa Allah Uba zai yi magana wa Ruhun. AT: "zai faɗa dukka abin da Allah ya gaya mashi ya faɗa"
A nan "abubuwan hankali" ya na nufin koyarwan Yesu da babban ayyuka. AT: "zai bayyana maku cewa abin da na faɗa, na kuma yi hakika gaskiya ne"
Ruhu mai Tsarki zai gaya wa mutane cewa magana da ayyukan Yesu gaskiya ne. AT: "Ruhu mai Tsarki zai gaya wa kowa cewa magana na da ayyuka na gaskiya ne"
"jim kaɗan" ko "kafin loƙaci dayawa su wuce"
"kuma, kafin loƙaci dayawa su wuce"
Wannan ɗan fashi ne a maganar Yesu a yayin da almajiran su ka tambaye juna game da abin da Yesu ya na nufi.
Almajiran ba su gane cewa wannan ya na nufin mutuwar Yesu a kan giciye ba.
AT: 1) Wannan na iya nufin tashiwar Yesu ko 2) Wannan na iya nufin zuwan Yesu a loƙacin karshe.
Wannan muhimmin laƙabi ne wa Allah.
Yesu ya yi amfani da wannan tambaya domin almajiransa su yi binbini da abin da ya gaya masu, domin ya iya fasara a gaba. AT: "Ku na tambayan junanku abin da ina nufi loƙacin da na ce, ... gan ni."
Fasara wannan a yadda harshenku na nanata cewa abin da yake bi ya na da muhiminci kuma gaskiya ne. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 1:51.
A nan "duniya" magana ne wa mutane da suke hamayya da Yesu. AT: "amma mutane da suke hamayya da Yesu za su yi farin ciki"
AT: "amma bakin cikinku zai zama murna" ko "amma daga baya a maimakon yin bakin ciki za ku yi murna sosai"
A nan "zuciya" magana ne na cikin mutum. AT: "za ku yi murna sosai" ko "za ku yi farin ciki sosai"
A nan kalmar "suna" magana ne da ya na nufin mutuntaka da ikon Yesu. AT: "idan kun roki komai na Uban, zai ba ku domin ku nashi ne"
A nan "suna" magana ne da ya na nufin mutuntaka da ikon Yesu. Uban zai ɗaukaki rokon masubi domin dangantakar su da Yesu. AT: "domin ku masubi na ne" ko " a iko na"
AT: "Allah zai ba ku babban farin ciki"
"a harshen da babu sauƙin ganewa"
"ba da jumawa ba zai faru"
"gaya ma ku game da Uban a hanyar da za ku gane da kyau."
A nan "suna" magana ne na mutumtaka da ikon Yesu. AT: "za ko roka domin ku nawa ne"
idan mutum ya na kaunar Yesu, Ɗan, su na kuma kuanar Uban, domin Uban da Ɗan ɗaya ne.
Bayan mutuwarsa da tashin sa, Yesu zai koma wurin Allah Uba.
A nan "Uba" muhimmin laƙani ne wa Allah.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya nuna cewa Yesu ya yi mamaki cewa almajiran sa yanzu ne sun shirya su gaskanta da shi. AT: "don haka, yanzu ne kun gaskanta da ni!
AT: "sauran za su watsar da ku"
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
A nan salama" ya na nufin salama na ciki. AT: "domin ku samu salama na ciki don dangantakar ku da ni"
A nan "duniya" ya na nufin damuwowi da tsanantawa da masubi za su sha daga waɗanda suke hamayya da Allah. AT: "na yi nasara da damuwowin wannan duniya"
1Da Yesu ya fadi wandannan abubuwa, sai ya tada idanunsa sama ya ce, ya Uba, sa'a ta zo; ka daukaka Danka, domin Dan shi ya daukaka ka, 2kamar yadda ka ba shi iko akan dukkan 'yan adam, ya ba da rai madawwami ga duk wanda ka ba shi.3Wannan ne rai madawwami: wato su san ka, Allah makadaici na gaskiya, da shi kuma wanda ka aiko, Yesu Almasihu. 4Na daukaka ka a duniya, na gama aikin da ka ba ni in yi. 5Yanzu, ya Uba, ka daukaka ni tare da kai da daukaka wadda ni ke da ita tare da kai tun kafin duniya ta kasanci.6Na bayyana sunanka ga mutunen da ka ba ni acikin duniya. Na ka suke, ka ba ni su, sun kuwa kiyaye maganarka. 7Yanzu kuwa sun san duk iyakar abinda ka ba ni daga gare ka yake, 8don kuwa maganganun da ka fada mani. Na fada masu, sun kuma karba, sun sani kuwa hakika na fito daga gareka ne, kuma sun gaskata kai ne ka aiko ni.9Ina yi masu addu'a. Ba domin duniya ni ke yin addu'a ba, amma domin wadanda ka bani gama na ka ne. 10Gama dukan abinda ke nawa na ka ne, naka kuwa nawa ne, an kuma daukaka ni a cikinsu. 11Ba na cikin duniya kuma, amma wadannan mutane suna cikin duniya, ni kuwa ina zuwa wurin ka. Ya Uba mai Tsarki, ka adanasu cikin sunanka da ka ba ni domin su zama daya, kamar dai yadda muke daya.12Lokacin da ina tare da su, na adanasu acikin sunanka da ka ba ni. Na kiyaye su, kuma ko daya kuwa daga cikinsu ba ya bace ba, sai dai dan hallakar nan, domin Nassi ya cika. 13Amma yanzu ina zuwa wurinka, Ina fadar wadannan abubuwa tun ina duniya, domin farin cikina ya zama cikakke a zukatansu. 14Na ba su maganarka, kuma duniya ta tsane su domin su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.15Ba ina roko ka dauke su daga cikin duniya ba, amma domin ka tsare su daga mugun nan. 16Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne. 17Ka kebe su domin kanka cikin gaskiya. maganarka gaskiya ce.18Kamar dai yadda ka aiko ni cikin duniya, haka kuma na aike su cikin duniya. 19Na kebe kaina gareka sabili da su, domin su ma kansu a kebe su gareka cikin gaskiya.20Ina addu'a ba domin wadannan kadai ba, amma har da wadanda zasu gaskata da ni ta wurin maganarsu, 21Domin su zama daya dukansu, kamar yadda kai, ya Uba, ka ke ciki na, ni kuma na ke cikin ka. Ina roko suma su kasance a cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa ka aiko ni22Daukakar da ka bani, ita nake basu, domin su zama daya, kamar yadda mu ke daya; 23ni a cikinsu, kai kuma a ciki na. Domin su kammalu cikin zama daya, domin duniya ta sani cewa ka aiko ni, kuma ka kaunace su, kamar yadda ka kaunace ni.24Ya Uba, ina so wadanda ka ba ni, su ma su kasance tare da ni inda nake, domin su dubi daukakata da ka yi mani. Domin ka kaunace ni tun kafin halittar duniya.25Ya Uba mai adalci, duniya kam, ba ta sanka ba, amma ni na sanka; kuma wadannan sun sani kai ne ka aiko ni. 26Na sanar masu da sunanka, zan kuma sanar da shi domin kaunar da ka yi mani ta kasance a cikinsu, ni kuma in kasance a cikinsu,
An cigaba da sashin labarin daga Aya da ta wuce. Yesu ya na ta magana da almajiransa, amma yanzu ya far addu'a ga Allah.
Wannan karin magana ne da ya na nufin duba sama. AT: "ya dubi sama ga sarari"
Wannan ya na nufin sarari.
Yesu ya roki Allah Uba don ya girmama shi domin ya iya ba da ɗaukaka wa Allah.
Waɗannan muhimmin lakabi ne da su na kwatanta dangantaka sakanin Allah da Yesu.
A nan kalmar "sa'a" magana ne da ya na nufin loƙaci ne wa Yesu da zai sha wahala ya kuma mutu. AT: "loƙaci ya kai da zan sha wahala in kuma mutu"
Wannan ya na nufin dukka mutane.
Rai madawwami shi ne sanin Allah makadaici na gaskiya, Allah Uba da Allah Ɗa.
A nan "aiki" magana ne da ya na nufin hidimar Yesu gaba ɗaya.
Yesu ya na da ɗaukaka da Allah "kafin a yi duniya" domin Yesu ne Allah Ɗan. "Uba, ka ba ni ɗaukaka ta wurin kawo ni zuwa gabanka kamar yadda muke kafin mu yi duniya"
Wannan muhimmin laƙani ne wa Allah.
A nan "suna" magana ne da ya na nufin Allah. AT: "Na koya masu game da kai da kuma abin da kake"
A nan "duniya" magana ne da ya na nufin mutanen duniya da sun yi hamayya da Allah. Wannan ya na nufin cewa Allah ya raba masubi ta ruhaniya daga mutanen da basu gaskanta da shi ba.
Wannan karin magana ne da ya na nufin biyayya. AT: "bi koyarswan ka"
A nan kalmar "duniya" magana ne da ya na nufin mutanen da sun yi hamayya da Allah. AT: "Ba na addu'a wa waɗanda ba na ka na"
Wannan magana ne da ya na nufin kasancewa a duniya da kuma kasancewa a cikin mutane da suka yi hamayya da Allah. AT: "a cikin mutane da ba na ka ba"
Yesu ya roki Uban ya adana waɗanda sun gaskanta da shi domin su iya samin dangantaka da Allah.
A nan kalmar "suna" magana ne na karfi da ikon Allah. AT: "ka adanasu da kyau a cikin karfi da ikonka, wadda ka ba ni"
A nan "suna" magana ne da ya na nufin karfi da kiyayewar Allah. AT: "Na adanasu da kiyayewarka"
"wadda an hallakar a cikin su shi ne ɗan hallaka kadai"
Wannan ya na nufin Yahuza, wadda ya bashe Yesu. AT: "wadda tun da dadewa ka zaba ka hallakar"
AT: "domin a cika annabci game da shi a cikin nassi"
AT: "domin ku iya basu babban farin ciki"
"Na faɗa masu sakon ka"
A nan "su" duniya" magana ne da ya na nufin mutanen da sun yi hamayya da Allah. AT: "Mutanen da sun yi hamayya da ku sun tsane masubi na domin su ba na waɗanda ba su gaskanta ba ne, kamar yadda ni ba na su ba"
A cikin wannan magana, "duniya" magana ne na mutane da suka yi hamayya da Allah.
Wannan ya na nufin Shaidan. AT: "kiyaye su daga Shaidan, mugun nan"
Ana iya sa a bayyane dalilin kebe su. Jumlar "ta gaskiya" anan ya na wakilcin ta wurin koyar da gaskiyan. AT: "Sa su su zama mutanen ka ta wurin koya masu gaskiyan"
"Sakon ka gaskiya ne" ko "Abin da ka faɗa gaskiya ne"
A nan cikin "duniya" magana ne da ya na nufin mutane da suke zama a cikin duniya. AT: "ga mutanin duniya"
AT: "domin su kebe kansu da gaskiye ma ka"
"waɗanda za su gaskanta da ni domin su na koyarswa game da ni"
Waɗanda sun gaskanta da Yesu sun zama daya da Uba da kuma Ɗan loƙacin da sun ba da gaskiya.
"Na ɗaukaka masubi na kamar yadda kun ɗaukaka ni"
AT: "domin ku hada su kamar yadda kun hada mu"
"domin su zama ɗaya cikakke"
A nan "duniya" magana ne da ya na nufin mutanin da ba su san Allah ba. AT: "domin dukka mutane su sani"
Wannan irin kauna ya na zuwa daga Allah ne ya na bisa kyaun mutane, ko bai amfani wani ba. Irin wannan kauna ya na kula da mutane, ko mai abin da sun yi
A nan "inda nake" ya na nufin sama. AT: "da ni a sama"
"domin su gan girma na"
A nan Yesu ya na nufin lokaci kafin halitta AT: "kafin halitta duniya"
A nan "Uba" muhimmin lakabi ne.
"duniya" magana ne na mutanin da ba na Allah ba. AT: "waɗanda ba naka ba ne ba su san yadda ka ke ba"
Kalmar "suna" ya na nufin Allah. AT: "Na bayyana maku yadda ka ke"
Wannan irin kauna ya na zuwa daga Allah ne ya na bisa kyaun mutane, ko bai amfani wani ba. Irin wannan kauna ya na kula da mutane, ko mai abin da sun yi
1Bayan Yesu ya fadi wadannan maganganu, ya fita shi da almajiransa zuwa daya barayin kwarin Kidiron, inda wani lambu ya ke, ya kuma shiga da almajiransa. 2Yahuza ma wanda zai bashe shi ya san wurin, domin Yesu ya saba zuwa wurin da almajiransa. 3Yahuza kuwa, bayan ya dauko kungiyar soja daga manyan firistoci, da Farisawa, da 'yan majalisa, suka zo wurin, rike da fitilu, da cociloli, da makamai.4Sai Yesu, da ya san duk abinda ke faruwa da shi, yayiwo gaba, yace masu, "Wa kuke nema" 5Suka amsa masa su ka ce, "Yesu Banazare" Yesu yace masu, Ni ne" Yahuza kuma, wanda ya bashe shi, yana tsaye tare da sojojin.6Sa'adda ya ce masu, "Ni ne", suka koma da baya, suka fadi a kasa. 7Ya sake tambayarsu kuma, "Wa ku ke nema?" su ka ce, "Yesu Banazare."8Yesu ya amsa, "Ai, na gaya maku cewa, Ni ne. In kuwa ni ku ke nema, ku bar wadannan su tafi abinsu;" 9Wannan kuwa domin maganar daya fada ta cika, "Daga cikin wadanda ka ba ni, ko daya bai bace mani ba."10Saminu Bitrus kuwa, da ya ke yana da takobi, ya zaro ya kai wa bawan babban firist sara, ya dauke masa kunnensa na dama, sunan bawan Malkus ne. 11Yesu ya ce wa Bitrus, "Mai da takobin ka kubenta. Ba zan sha kokon da Uba ya ba ni ba.'?12Sai sojojin da hafsan, da 'yan majalisar Yahudawa, suka kama Yesu, suka daure shi. 13Da fari suka tafi da shi wurin Hanana, don shi surukin Kayafa ne, wanda ya ke shi ne babban firist a shekaran nan. 14Kayafa kuma shi ne ya ba Yahudawa shawara, cewa ya fiye masu mutum daya ya mutu domin mutane.15Saminu bitrus ya bi bayan Yesu, haka kuma wani almajirin yayi. Almajirin nan kuwa sananne ne ga babban firist, sai ya shiga har farfajiyar babban firist din tara da Yesu; 16Amma bitrus kuwa ya tsaya a bakin kofa daga waje. Sai daya almajirin da ya ke sananne ga babban firist ya fita, yayi magana da macen da ta ke tsaron kofar, sa'an nan ya shigo da Bitrus.17Sai yarinyar mai tsaron kofar ta ce wa Bitrus, "kai ma ba kana cikin almajiran mutumin nan ba?" Yace "bani ba." 18To, barorin da dogaran Haikali suna tsaye a wurin, sun kuwa hura wutar gawayi, suna jin dumi, gama ana sanyi. Bitrus ma yana tsaye tare da su yana jin dumin.19babban firist ya tambayi Yesu game da almajiransa da koyarwarsa kuma. 20Yesu ya amsa masa, Ai, na yi wa duniya magana a bayyane. Na kuma sha koyarwa a majami'u da Haikali in da Yahudawa duka sukan taru. Ban fadi komai a boye ba. 21Don me kake tambaya ta? Ka tambayi wadanda suka saurare ni a kan abinda na fada, ai, sun san abinda na fada.22Sa'adda Yesu ya fadi wannan, wani daga cikin 'yan majalisar da ke tsaye a wurin ya nushi Yesu, yace, "Kana amsa wa babban firist haka." 23Yesu ya amsa masa yace, "Idan na fadi mugun abu to, ka bada shaida kan hakan. In kuwa dai dai na fada, to, dan me za ka nushe ni?" 24Sai Hanana ya aika daYesu a daure wurin Kayafa, babban firist.25To Saminu Bitrus yana tsaye yana jin dumin. Mutanen kuwa suka ce masa, "Anya kai ma ba cikin almajiransa ka ke ba?" Sai yayi musu yace, "A'a, ba na ciki." 26Sai wani daga cikin bayin babban firist, wato dan'uwan wanda Bitrus ya fillewa kunne, yace, "Ashe, ban gan ka tare da shi a lambun ba? 27Bitrus ya sake yin musu, nan da nan kuwa zakara yayi cara.28Daga wurin Kayafa kuma suka kai Yesu fadar Gwamna. Da asuba ne kuwa, su kansu ba su shiga fadar Gwamnan ba, wai don kada su kazantu su kasa cin jibin Ketarewa. 29Sai bilatus fa ya fita zuwa wurinsu, yace, "Wane zargi ku ke kawowa akan mutumin nan? 30"Sai suka amsa suka ce, "idan da mutumin nan bai yi mugun abu ba, me zai sa mu yi kararsa a wurin ka"31bilatus yace masu, "Ku tafi da shi da kan ku mana, ku hukunta shi bisa ga shari'arku!" Sai Yahudawa su kace masa, "Ai, ba mu da ikon zartar da hukuncin kisa akan kowa." 32Sun fadi Wannan ne don a cika maganar da Yesu yayi, wadda ta kwatanta irin mutuwar da zai yi.33Sai bilatus ya sake shiga cikin fadar Gwamnan, ya kira Yesu ya ce masa, "kai sarkin Yahudawa ne?" 34Yesu ya amsa, "wannan fadarka ce, ko kuwa wadansu ne suka ce da ni haka a wurinka?" 35Bilatus ya amsa "Ni ba Bayahude bane, ko kuwa?" Ai, jama'arka ne da manyan firistoci suka bashe ka gareni. "Me ka yi?"36Yesu ya amsa, "Mulkina ba na duniya nan ba ne. Da mulkina na duniyan nan ne da barorina za su yi yaki kada a bashe ni ga Yahudawa. To, mulkina ba daga nan ya ke ba." 37Sai Bilatus yace masa, "Wato ashe, sarki ne kai?" Yesu ya amsa, "Yadda ka fada, ni sarki ne. Domin wannan dalili aka haife ni, domin kuma wannan dalili na zo cikin duniya, don in bada shaida game da gaskiya. Kowane mai kaunar gaskiya kuma yakan saurari muryata."38Bilatus yace masa, "Menene gaskiya?" Bayan da ya fadi haka, ya sake fitowa wurin Yahudawa, yace masu, "Ni kam, ban sami mutumin nan da wani laifi ba. 39Amma dai kuna da wata al'ada, in Idin Ketarewa ya yi, na kan sakar maku mutum daya. To, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?" 40Sai suka sake daukar kururuwa suna cewa, "A; a, ba wannan mutum ba, sai dai Barabbas." Barabbas din nan kuwa dan fashi ne.
Aya 1-2 ya ba da tushen bayani na abin da zai faru. Aya 1 ya faɗa inda an yi, kuma Aya 2 ya ba da tushen bayani game da Yahuza.
Marubucin ya yi amfani da wannan kalmomi domin a nuna farkon sabon abu.
Kwarin ne a Urushalima da ya ke raba Dutsen haikali daga Dutsen Olives.
Wannan taron itacunan zaitun ne. AT: "inda akwai taron itacunan zaitun"
"Sai Yesu, wadda ya san komai da ya yi kusa ya faru da shi"
"Yesu, mutumin daga Nazare"
Kalmar "shi" bayani ne a wannan littafi. AT: "Ni ne shi"
"wadda ya ba da shi"
Mazan sun faɗi a kasa saboda ikon Yesu. AT: "faɗi a kasa saboda ikon Yesu"
A nan "duniya" ya na nufin kalmomin da Yesu ya yi addu'a. AT: "Wannan ya faru domin a cika kalmomin da ya faɗa a loƙacin da ya na yin addu'a wa Ubansa"
Malkus bawa ne na babban firist.
murfin wuka mai tsini, don wukan kar ya yanka mai shi
Wannan ya bayyana kamar tambaya ne domin a kara nanata jimlar Yesu. AT: "Dole ne in sha daga kokon da Uban ya ba ni!"
A nan "kokon" magana ne da ya na nufin wahala da dole ne Yesu ya jure.
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
A nan "Yahudawa" magana ne na shugabanin Yahudawa wadda sun yi hamayya da Yesu. AT: "shugabanin Yahudawa"
Sojoji suka daure hanayen Yesu domin a hana shi kuɓucewa. AT: "sun kama Yesu sun kuma daura shi domin a hana shi kuɓucewa"
AT: "Yanzu babban firist din ya san wannan almajiran don haka ya iya ya shiga tare da Yesu"
AT: "Sai ɗayan almajirin, wadda babban firist ya sani"
Wannan ya bayyana kamar tambaya ne domin ya sa baiwan ta iya bayana maganar ta da hankali. AT: "Kai ma ɗaya ne daga almajiran mutumin nan da an kama! Ba kai ba ne?
Waɗannan su bayin babban firist ne da kuma dogaran haikali. AT: "An yi tsanyi, sai bayin babban firist da kuma dogaran haikali su yi shirya wutan gawayi sai sun tsaya su na ɗuma kansu a kewaye da shi"
An yi amfani da wannan kalma anan domin a sa fashi daga ainahin labarin domin Yahaya ya iya kara bayani game da mutane da suke ɗuma kansu a kewaye da wuta.
Wannan kefas ne. Dubi 18:13
A nan "koyarswansa" ya na nufin abin da Yesu ya yi ta koya wa mutane. AT: "game da almajiransa da abin da ya koya wa mutane"
Za ku iya sa wannan a bayyane cewa kalmar "duniya" magana ne na mutane da sun ji koyarswan Yesu. Anan zuguiguitawar "duniya" ya nanata cewa Yesu ya yi magana a bayyane. e.
A nan "dukka Yahudawa" zuguiguitawa na da ya na nanata cewa Yesu ya yi magana a inda duk wadda zai ji zai iya jin shi.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin a kara bayani a abin da Yesu ya na faɗa. AT: "Kadda ku dinga yi mun wannan tambaya!"
Wannan ya bayyana kamar tambaya ne domin karin nanaci. AT: "ba haka ne ya kamata ka amsa babban firist ba!"
"gaya mani abin da na faɗa da ba daidai ba"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin a kara nanata abin da Yesu ya na faɗa. AT: "Inda na faɗa abin da daidai ne kadai, kada ku dinga nushe na!"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin a kara nanatawa. AT: "Kai ma ɗaya daga cikin almajiransa ne!"
Wannan magana ya bayyana ne kamar tambaya domin karin nanaci. A nan "shi" ya na nufin Yesu. AT: "Na gan ku tare da mutumin da an kama a cikin taron itacen zaitun! ko ba haka?"
A nan Ya na nufin cewa Bitrus ya yi musan sanin da kuma zama tare da Yesu. AT: "Bitrus ya kuma musanta cewa ya san Yesu ko ya yi zama tare da shi"
A nan ana zaton cewa mai karatun zai tuna cewa Yesu ya ce Bitrus zai musanta shi kafin zakara yayi cara. AT: "yadda Yesu ya ce zai faru"
A nan ya na nufin cewa su na kai Yesu gidan Kafaya. AT: "Sai suka tafi da Yesu daga gidan Kayafa"
Bilatus ba Bayahude ba ne, don haka indan shugabanin Yahudawa sun shiga cikin faɗar sa, za su kazantu. Da wannan ya hana su yin hidimar ketarewa. AT: "su kansu sun tsaya a wajen faɗar Bilatus domin Bilatus ɗan Al'umma ne. Ba su so su zama da kazanta"
AT: "Wannan mutumin nan ya na aikata mugun abu, shi ya sa mun kawo maka don hukunci"
Wannan jumla ya na nufin ba ma makiya.
A nan "Yahudawa" magana ne na shugabanin Yahudawa da suka yi hamayya da Yesu sun kuma kama shi. AT: "Su shugabanin Yahudawan suka ce masa"
Bisa ga dokan Romawa, Yahudawa ba su iya kashe mutum. AT: "Bisa ga dokan Romawa, ba za mu iya kashe mutum ba"
AT: "domin a cika abin da Yesu ya faɗa a farko"
"bisa ga yadda zai mutu"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin Bilatus ya iya nanata cikakken rashin son abubuwan al'adun mutanen Yahudawa. AT: "To, hakika ni ba Bayahude ba ne, kuma ban damu da waɗannan zancen ba!"
"'yan'uwanka Yahudawa"
A nan "duniya" magana ne na mutane da sun hamayya da Yesu. AT: 1) "Mulki na ba na duniya ba ne" ko kuma 2) "Ba na son umurnin wannan duniya domin in yi mulki kamar sarkinsu" ko kuma "Ba daga wannan duniya ne ina da ikon zaman sarki ba."
AT: "a kuma hana shugabanin Yahudawa daga kama ni"
A nan "duniya" magana ne da na nufin mutanen da suke cikin duniya.
A nan "gaskiya" ya na nufin game da Allah. AT: "gaya wa mutane gaskiya game da Allah"
Wannan karin magana ne da ya na nufin kowane mutum da ya na kaunar gaskiya game da Allah.
A nan "murya" magana ne da ya na nufin kalmomin da Yesu ya yi. AT: "abubuwan da na faɗa" ko "ni"
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne domin ya nuna yadda Bilatus ya yarda da cewa ba bu wadda ya san gaskiya. AT: "Ba bu wadda zai san menene gaskiya!"
Wannan karin magana ne. AT: "Ba bu! Kada ku sake wannan mutum! Ku sake Barabbas a maimako"
A nan Yahaya ya ba da tushen bayani game da Barabbas.
1Sai Bilatus yayi wa Yesu bulala. 2Sojojin kuwa suka saka rawanin kaya. Suka kuwa dora wa Yesu a kai suka sa mashi kaya irin na saurata. 3Suka zo wurin sa sukace, "Ranka ya dade, sarkin Yahudawa! sai suka nushe shi.4Sai Bilatus ya sake fita waje yace masu, "Dubi, zan kawo maku mutumin domin ku sani ban same shi da wani laifi ba", 5Yesu kuwa ya fito, da rawanin kaya da kaya irin na sarauta. Sai Bilatus yace "Ga mutumin nan". 6Da manyan firistocin tare da yan majalisar suka ga Yesu, sai suka yi ta ihu suna cewa "A gicciye shi, A gicciye shi" Sai Bilatus yace masu, "ku dauke shi ku gicciye shi, ni kam ban same shi da wani laifi ba".7Sai Yahudawan sukace mashi, "Ai muna da shari'a, kuma bisa ga shari'ar ya cancanci mutuwa domin ya mai da kansa Dan Allah". 8Da Bilatus ya ji wannan zance sai ya tsorata kwarai. 9Sai ya sake shiga fadar Gwamna, yace wa Yesu, "Daga ina ka fito?" amma Yesu bai amsa mashi ba.10Sai Bilatus yace masa "Ba zaka yi mani magana ba? Baka san ina da iko in sake ka ba, kuma in gicciye ka? 11Yesu ya amsa masa, "Ai ba ka da iko a kaina sai dai in an baka daga sama, Saboda haka, wanda ya mika ni a gare ka shine mafi zunubi".12Da jin haka, sai Bilatus yayi kokari a sake shi, amma sai Yahudawa suka tada murya sukace, "In ka saki mutumin nan, kai ba abokin Kaisar bane, duk wanda ya maida kansa sarki, ya sabawa Kaisar". 13Da Bilatus ya ji irin maganganunsu sai ya fito da Yesu waje ya kuma zauna akan kujeransa a inda ake kira "Dakalin shari'a," a Yahudanci kuma, "Gabbata."14To a ran nan ana shirye shiryen idin ketarewa, da misalin sa'a ta shidda kenan, wato tsakar rana, Bilatus yace wa Yahudawan "Ga sarkin ku!" 15Su kuwa suka yi ihu, a tafi da shi, a tafi da shi, a gicciye shi, Bilatus yace masu "In gicciye sarkin ku? Sai manyan firistocin sukace "Ba mu da wani sarki sai Kaisar". 16Sai Bilatus ya mika Yesu domin su gicciye shi.17Sai suka tafi da Yesu, ya fito yana dauke da gicciyen zuwa wurin da ake kira "Wurin kwalluwa" da Yahudanci kuma "Golgota". 18Suka gicciye Yesu a wurin, tare da wasu mutum biyu, daya a kowane gefe, Yesu kuwa na tsikiya.19Bilatus kuwa ya rubuta wata alama a kan gicciyen, "YESU BANAZARE, SARKIN YAHUDAWA". 20Yahudawa da yawa kuwa suka karanta wannan alama domin wurin da aka gicciye Yesu yana kusa da Birnin. Alamar kuwa an rubuta ta da Yahudanci, da Romanci, da Helenanci.21Sai manyan firistocin yahudawa sukace wa Bilatus, kada ka rubuta sarkin Yahudawa, amma kace, 'wannan yace "Ni ne sarkin Yahudawa"'. 22Bilatus kuwa ya amsa, "Abinda na rubuta na rubuta kenan."23Bayan da sojojin suka gicciye Yesu, sai suka yayyaga rigarsa kashi hudu, kowane soja da nasa, kashin, sai kuma alkyabbar. Alkyabbar kuwa bata da dinki an saka tane daga sama har kasa. 24Sai sukace wa junansu, "Kada mu yaga alkyabbar, amma kuzo mu jefa kuri'a a kan ta mu gani ko wanene zai dauke ta, anyi haka ne domin a cika nassi cewa "Sun raba rigata a tsakaninsu, sun kuwa jefa kuri'a domin alkyabbata.25Sojojin suka yi wadannan abubuwa. Uwar Yesu, da 'yar'uwarta, da Maryamu matar Kilofas, da kuma Maryamu Magadaliya. Wadannan mataye suna tsaye kusa da gicciyen Yesu. 26Da Yesu ya ga mahaifiyarsa da almajirin nan da yake kauna tsaye kusa da juna, yace, "Mace, dubi, dan ki!" 27Sai yace wa almajirin, "Dubi, mahaifiyarka!" Daga wannan sa'a almajirin ya dauke ta zuwa gidansa.28Bayan wannan Yesu, saboda ya san yanzu komai ya kammala, domin a cika nassin, sai yace "Ina jin kishi. 29A gefensu kuma akwai gora cike da ruwan inabi mai tsami, sai suka tsoma soso a cikin ruwan inabin mai tsami suka daura a wata sanda sai suka mika masa a baki. 30Da Yesu ya tsotsi ruwan tsamin, sai yace "An gama" Sai ya sunkuyar da kansa ya kuwa saki ruhunsa.31Sai Yahudawan, domin ranar shirye shirye ne, domin kada a bar jikunansu akan gicciye har ranar asabacin (domin asabacin rana ce mai muhimmanci), suka roki Bilatus ya kakkarye kafafunsu kuma ya saukar da su. 32Sai sojojin suka zo suka karya kafafun mutum na farko da kuma mutum na biyun wadanda aka gicciye tare da Yesu. 33Da suka iso kan Yesu sai suka tarar ya riga ya mutu, sai basu kuwa karya kafafunsa ba.34Duk da haka daya daga cikin sojojin ya soki kuibin shi da mashi, nan da nan sai jini da ruwa suka fito. 35Wanda ya ga wannan, shi ya zama shaida, shaidarsa kuwa gaskiya ce. Ya sani cewa abinda ya fada gaskiya ne saboda ku ma ku gaskata.36Wadannan sun faru ne domin a cika nassi, "Babu ko daya daga cikin kasusuwansa da za'a karya". 37Kuma wani nassin yace, "Zasu dube shi wanda suka soka."38Bayan wadannan abubuwa, Yusufu mutumin Arimatiya, wanda yake almajirin Yesu ne (amma a boye saboda tsoron Yahudawa) ya roki Bilatus izini domin ya dauke jikin Yesu. Bilatus kuwa ya bashi izini, sai Yusufu yazo ya dauki jikin. 39Nikodimu ma ya zo, wanda da farko ya zo wurin Yesu da daddare, ya kawo hadin man kamshi na mur da al'ul wajen nauyin awo dari.40Sai suka dauki jikin Yesu suka sa shi a likkafanin lillin tare da kayan kamshin nan, domin jana'iza bisa ga al'adar Yahudawa. 41To a wurin da aka gicciye shi kuwa akwai wani lambu, a cikin lambun kuma akwai sabon kabari wanda ba'a taba sa kowa ba. 42Da yake ranar shirye shirye ce ta Yahudawa, kabarin kuwa na kusa, sai suka sa Yesu a ciki.
An cigaba da sashin labarin daga Aya da ta wuce. Yesu ya na tsaye a gaban Bilatus a yayin da Yahudawa suke zargin shi.
Bilatus bai duke Yesu da kansa ba. Anan "Bilatus" magana ne na sojojin da Bilatus ya umurta su duki Yesu. AT: "Sai Bilatus ya sa sojoin su duke Yesu"
A nan amfani da gaisuwan "ranka ya daɗe" da hanu a sama a gaishe da Caesar ne kadai. A yayin da sojojin su na amfani da kayoyi da kaya irin na sarauta su na yi wa Yesu ba'a, da mamaki ne cewa ba su gane wai a hakika shi sarki ne ba.
Bilatus ya faɗi wannan so biyu domin ya nu na bai yarda cewa Yesu ba shi da laifi ba. Bai so ya hukunta shi. AT: "ban gan dalilin hukunta shi ba"
Rawanin da kaya irin na sarauta kaya ne da sarakuna ne kadai suke sa. Sojojin su yi wa Yesu sutura haka domin su yi mashi ba'a. Dubi 19: 2.
A nan "Yahudawa" magana ne na shugabanin Yahudawa da suka yi hamayya da Yesu. AT: "Shugabanin Yahudawa suka amsa Bilatus"
An hukunta Yesu har ga mutuwa a kan giciye domin ya ce shi ne "Ɗan Allah."
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
Wannan magan ya bayyana kamar tambaya ne. A nan Bilatus ya bayyana mamakinsa cewa Yesu bai yi amfani da loƙacin don ya kare kansa ba. AT: "Ban iya yarda cewa kana kin magana da ni ba!" ko "Amsa ni!"
Wannan magana ya bayyana domin karin nanaci. AT: "Ya kamata ka san cewa zan iya sake ka ko kuma in umurce sojoji na su giciye ka!"
A nan "iko" magana ne da ya na nufin iya yin wani abu ko kuma sa abu ya faru.
AT: "kun na iya aikata ba da son rai na ba saboda Allah ya sa ku"
Wannan hanya ne na daraja Allah.
Wannan jumla anan na nufin mika wa makiya.
A nan " jin haka" na nufin amsar Yesu. AT: "A loƙacin da Bilatus ya ji amsar Yesu"
"yi kokari" a asali ya nuna cewa Bilatus ya yi kokari " ƙwarai ko kuma "sake" don a saki Yesu. AT: "ya yi kokari ƙwarai don a sake Yesu" ko "ya yi ta kokari don a sake Yesu"
A nan "Yahudawa" magana ne da ya na nufin shugabanin Yahudawa da suka yi hamayya da Yesu. A cikin ainahin, " tada murya" ya na nuna cewa sun yi ta ihu. AT: "amma shugabanin Yahudawa suka cigaba da yin ihu"
"kana hamayya da Kaisar"
"ya ce shi na sarki"
A nan "shi" na nufin Bilatus kuma magana ne na "Bilatus ya umurce sojojin." AT: " ya umurce sojojin su kawo Yesu waje"
Mutane masu daraja kamar Bilatus su ke zaune a loƙacin da su na yin aiki, sai mutane da ba su da daraja sosai su na tsaye.
Wannan kujera ne na musamman da mutum mai daraja kamar Bilatus ya ke zauna akai a lokacin da ya na yin hukunci. Idan harshenku ya na da yadda za a kwatanta wannan abu, za ku iya yin amfani da shi a anan.
Wannan dakalin dutse ne da mutane masu daraja ake yarda su je. AT: "a wurin da mutane sun kira Dakalin shari'a, amma"
Wannan ya na nufin harshen da mutanen Israi'la suke yi.
Wannan magana ya sa fashi a cikin labarin domin Yahaya ya iya ba da bayani game da idin ketarewa mai zuwa da rana.
"kusan tsakar rana"
A nan "Yahudawa" magana ne da ya na nufin shugabanin Yahudawa wadda sun yi hamayya da Yesu. AT: "Bilatus ya ce wa shugabanin Yahudawan"
A nan "in" magana ne da ya na nufin sojojin Bilatus wadda zai yi gicciyewan. AT: "Ku na so in gaya wa sojoji na cewa su gicciye sarkin ku a kan gicciye?"
A nan Bilatus ya ba da umurni da sojojin don su gicciye Yesu. AT: "Bilatus ya sa sojojin su gicciye Yesu"
AT: "zuwa wurin da mutane suke kira "Wurin kwakwalluwa,"
Yahudanci harshen mutanene Isra'ila ne. AT: "wadda ake kira a Yahudanci "Golgota."
Wannan karin magana ne. AT: "sun kuma gicciye shi da waɗansu barayi a kan su gicciyensu"
A nan "Bilatus" magana ne na mutumin da ya yi rubutu a kan alaman. A nan "a kan gicciye" ya na nufin gicciyen Yesu. AT: "Bilatus ya kuma umurce wani ya rubuta a alama ya kuma sa shi a kan gicciyen Yesu"
AT: "Sai mutumin ya rubuto kalmomin: Yesu Banazare, sarkin Yahudawa"
AT: "wurin da sojojin suka gicciye Yesu"
AT: "wadda ya shirya alama ne ya rubuto kalmomin a harshuna uku: Yahudanci, da Romanci, da Helenanci"
Wannan harshe ne na gwamnatin Romawa.
Manyan firistocin sun koma zuwa wurin faɗan Bilatus don su yi zangazanga game da maganganun a alaman. AT: "Manyan firistocin sun koma wurin Bilatus sai ya ce"
Bilatus ya na nufin cewa ba zai canza kalmomin a kan alaman ba. AT: "Na riga na rubuto abin da na ke so in rubuta, kuma ba zan canza ta ba"
A karshen aya 24 an yi fashi daga ainahin labari a yayin da Yahaya faɗa yadda wannan abu ya ciika nassi.
sun kuma dauke alkebbarsa." Sojojin sun ajiye alkebbar dabam, ba su raba shi ba. AT: "sun ajiye alkebbar dabam"
Sojojin za su yi caca da alkebbar kuma wadda ya ci ne zai dauka rigan. AT: "mu yi caca da alkebbar sai wadda ya ci ne zai samu ya ajiye"
AT: "Wannan ya cika nassi da ya ce" ko "Wannan ya faru ne domin ya sa nassi ya zama gaskiya"
Hakane sojojin su ka raba kayan Yesu a sakaninsu. AT: "sun yi caca"
Wannan Yahaya ne, marubucin wannan bishara.
A nan kalmar "ɗan" karin magana ne. Yesu ya na son almajiransa, Yahaya, ya zama kamar ɗa wa uwarsa. AT: "Mace, ga mutumin da zai zama kamar ɗa maki"
A nan kalmar "uwa" karin magana ne. Yesu ya na son uwarshi ta zama kamar uwa wa almajiransa, Yahaya. AT: "Yi tunanin wannan macen kamar uwarka ce"
"daga wannan loƙaci"
AT: "ya san cewa ya yi komai da Allah ya aike shi ya yi"
AT: "Wani ya ajiye awurin gorar ruwan inabi mai tsami"
"ruwa mai ɗaci"
A nan "su" na nufin masu gadin Romawa.
karamin abu wadda na iya jikuwa har ya kuma rike ruwa
"a kan rashe a tushe da ake kira hissop"
Yahaya ya na nufin cewa Yesu ya ba da Ruhunsa wa Allah. AT: " ya sunkuyar da kansa ya kuwa ba wa Allah ruhunsa" ko kuma "ya sunkuyar da kansa ya mutu"
A nan "Yahudawa" magana ne na shugabanin Yahudawa da suka yi hamayya da Yesu. AT: "shugabanin Yahudawa"
Wannan lokaci ne kafin idin ketarewa da mutane su na shirya abinci don idin ketarewa.
AT: "kakkarye kafafun mutanen da an yi masu hukunci an kuma saukar da jikunansa daga su gicciye"
AT: "wadda an gicciye shi kusa da Yesu"
Wannan jimla ya ba da tushen bayani ga labarin. Yahaya ya na faɗa wa masu karatu cewa ya na wurin kuma za mu iya gaskanta abin da ya rubuto.
"Shaida" ya na nufin faɗa abin da wani ya gani. AT: "ya faɗa gaskiya game da abin da ya gani"
A nan "gaskanta" ya na nufin sa yardan mu a Yesu. AT: "domin ku sa yardan ku a Yesu"
AT: "ciki magana ne da wani ya rubuto a cikin nassi"
Wannan magana ne daga Zabura 34. AT: "ba bu wadda zai karya kasusuwansa"
Wannan magana ne da Zechariah 12.
Arimatiya karamin gari ne. AT: "Yusufu daga garin Arimatiya"
A nan "Yahudawa" magana ne na shugabanin Yahudawa da suka yi hamayya da Yesu. AT: " saboda tsoron shugabanin Yahudawa"
Yahaya ya na nufin cewa Yusufu na Arimatiya ya na so ya binne jikin Yesu. AT: "izini don a ɗauke jikin Yesu daga gicciye"
Nikodimu ɗaya ne daga cikin Firistoci wadda sun gaskanta da Yesu. Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 3:1.
Waɗannan abubuwan kamshi ne da mutane na shirya gawa don biso.
Za ku iya sa wannan a awu na zamani. "lita" na nan kamar rabin kilo. AT: "kamar kilo 33 a nauyi"
"100"
A nan Yahaya ya sa fashi a cikin labarin domin a ba da tushen bayani game da inda kabarin da za a binne Yesu yake.
AT: "Yanzu a wurin da an gicciye Yesu akwai lambu"
AT: "wadda mutane ba su binne kowa ba"
Bisa shari'an Yahudawa, ba bu wadda zai yi aiki bayan rana ya fadi ranar Juma'a. Farkon Asabar da kuma ketarewa. AT: "An yi kusa a fara idin ketarewa a yamman"
1To da sassafe ranar farko ta mako, da sauran duhu, Maryamu Magadaliya ta zo kabarin, ta tarar an kawar da dutsen daga kabarin. 2Sai ta ruga da gudu zuwa wurin Saminu Bitrus tare da almajirin nan da Yesu ke kauna, tace masu, "Sun dauke Ubangiji daga kabarin, bamu kuwa san inda aka sa shi ba."3Sai Bitrus tare da almajirin nan suka fita, kuma suka tafi kabarin, 4dukansu suka ruga da gudu tare, amma daya almajirin ya riga Bitrus isowa kabarin, 5Sai ya sunkuya ya leka ciki, ya ga likkafanin lillin a wurin, amma fa bai shiga ciki ba.6Sai Saminu Bitrus ya iso daga bayansa sai ya shiga kabarin, ya tarar da likkafanin lillin a ajiye. 7sai fallen kuma da yake kansa. Ba'a ajiye tare da likkafanin ba amma aka linkeshi aka ajiye shi daban.8Sai almajirin nan da ya riga isa kabarin shi ma ya shiga ya gani, sai ya ba da gaskiya. 9Har ya zuwa wannan lokacin basu san nassin daya ce zai tashi daga matattu ba. 10Sai almajiran suka sake komawa gida kuma.11Amma Maryamu tana tsaye a bakin kabarin tana kuka. Yayin da take kuka, sai ta sunkuya ta leka cikin kabarin. 12Sai ta ga mala'iku guda biyu cikin fararen kaya zaune, daya ta wurin kai daya kuma ta wurin kafafu inda aka kwantar da Yesu. 13Sukace mata, "Uwargida don me kike kuka? Sai tace masu, "Domin sun dauke Ubangijina, ban kuwa san inda suka ajiye shi ba.14Bayan ta fadi haka, ta juya sai ta ga Yesu tsaye a wurin. Amma bata san cewa Yesu bane, 15Yesu yace mata, "Uwargida, me yasa kike kuka? Wa kuma kike nema? Domin tana zaton shine mai kula da lambun, sai tace masa, "Maigida in kaine ka dauke shi, gaya mani inda ka sa shi, ni kuwa in dauke shi."16Yesu yace mata, "Maryamu". Sai ta juya, tace masa da Armaniyanci "Rabboni!" wato mallam. 17Yesu yace mata, kada ki taba ni, domin har yanzu ban hau wurin Uba ba tukuna, amma kije wurin 'yan'uwana kice masu, zan je wurin Ubana da Ubanku, Allahna da kuma Allahnku". 18Maryamu Magadaliya ta je tace wa almajiran, "Na ga Ubangiji" Ta kuma ce ya fada mata wadannan abubuwa.19Da yamma a wannan rana, a rana ta farko ta mako, almajiran suna kulle a daki saboda tsoron Yahudawa, Yesu yazo ya tsaya a tsakaninsu, yace "Salama Agareku". 20Bayan ya fadi haka, sai ya nuna masu hannuwansa da kuibinsa. Da almajiran suka ga Ubangiji, sai suka yi farin ciki.21Yesu ya sake ce masu, "salama agareku. "Kamar yadda Uba ya aiko ni, haka Ni ma na aike ku". 22Da Yesu ya fadi haka, sai ya hura masu lumfashinsa, yace masu, "Ku karbi Ruhu Mai Tsarki. 23Duk wanda kuka gafarta wa zunubai, an gafarta masa; kowa kuka rike zunubansa, an rikesu."24Toma, daya daga cikin sha biyun, wanda ake kira Dan Tagwai, baya tare dasu lokacin da Yesu ya bayyana. 25Sauran almajiran sukace masa "Mun ga Ubangiji". Sai yace masu, "In ban ga gurbin kusoshi a hannuwansa ba, in sa yatsana a gurbin kusoshin ba, in kuma sa hannuna cikin kuibinsa ba, ba zan bada gaskiya ba.26Bayan kwana takwas har wa yau almajiran na cikin gida, Toma ma na tare dasu, kofofin suna kulle, sai ga Yesu a tsakaninsu yace, "Salama agareku". 27Sa'an nan yace wa Toma, "Iso nan da yatsanka, dubi hannuwana. Miko hannunka kuma kasa a kuibina, kada ka zama marar bada gaskiya, sai dai, mai bada gaskiya".28Toma ya amsa yace "Ya Ubangijina da Allahna!" 29Yesu yace masa, "Wato saboda ka gan ni, ka bada gaskiya? Albarka ta tabbata ga wadanda basu gani ba, amma kuwa sun bada gaskiya.30Yesu yayi wadansu alamu da yawa dabam dabam a gaban almajiransa, wadanda ba'a rubuta a littafin nan ba. 31Amma an rubuta wadannan ne, domin ku bada gaskiya Yesu shine Almasihu, Dan Allah, ta wurin gaskatawa kuma ku sami rai cikin sunansa.
Wannan ne ranar ta mako bayan da an binne Yesu.
"Lahadi"
AT: "ta tarar cewa wani ya kawar da dutsen"
Wannan jumla ya bayyana a yadda Yahaya kira kansa a cikin littafinsa. Anan kalmar "kauna" ya na nufin kaunar yan'uwa ko kauna wa abokai ko ɗan iyali.
Maryamu Magadaliya ta yi tunani cewa wani ya sata jikin Ubangiji. AT: "Wani ya riga ya ɗauka jikin Ubangiji daga kabari"
Yahaya ya nuna kaskancin shi ta wurin kiran kansa a nan "ɗayan almajirin," a maimakon saka sunansa.
Yahaya ya na nufin cewa waɗannan almajiran su na tafiya zuwa wurin kabarin. AT: "ruga daga kabarin"
Waɗannan kayakin bison Yesu ne da mutane sun kinsa jikin Yesu.
A nan "kansa" na nufin Yesu." AT: "kayan da wani ya rufe fuskan Yesu da shi"
AT: "amma wani ya riga ya linkeshi ya kuma sa a gefe, dabam daga likkafanin lillin"
Da ya gan cewa ba komai a kabarin, ya ba da gakiya cewa Yesu ya tashi daga matattu. AT: "ya gan waɗannan abubuwa sai ya fara gaskantawa cewa Yesu ya tashi daga matattu"
A nan kalmar "su" ya na nufin almajiran da ba su fahimci nissin da ya ce Yesu zai tashi kuma ba. AT: "Har yanzu almajiran ba su fahimci nassin ba"
zama rayeye kuma
Daga dukka waɗanda sun riga sun mutu. Wannan magana ya kwatanta dukka matattu a cikin duniya.
Almajiran sun cigaba da zama a Urushalima. AT: "sun koma inda suke zama a cikin Urushalima"
Mala'ikun sun sa fararen kaya. AT: "ta ga mala'iku guda biyu cikin fararen kaya"
"Sun tambaye ta"
"Domin sun dauke jikin Ubangijina"
"ban kuwa san inda suka ajiye shi ba"
"Yesu ya tambaye ta"
A nan kalmar "shi" na nufin Yesu. AT: "idan ka dauke jikin Yesu"
"gaya mani inda ka sa shi"
Maryamu Magadaliya ta na so ta samu jikin Yesu don ta binne kuma. AT: "zan samu jikin in kuma binne kuma"
Kalmar "Rabboni" ya na nufin mallam a Aramaik, harshen da Yesu da almajiran sa suke yi.
Yesu ya na nufin almajiransa ne da ya yi amfani kalmar "'yan'uwa."
Yesu ya tashi daga matattu ya kuma faɗi cewa zai je sama, zuwa wurin Ubansa, wadda shi ne Allah. AT: "Na yi kusa in koma sama domin in kasance da Ubana da kuma Ubanku, zuwa wadda shi ne Allahna da kuma Allahnku"
Waɗannan muhimmin lakabi ne da ya kwatanta dangantaka a sakanin Yesu da Allah, da kuma masubi da Allah.
Maryamu Magadaliya ta je inda almajiran suke zama sai ta faɗa masu abin da ta gani ta kuma ji. AT: "Maryamu Magadaliya ta je inda almajiran suke sai ta gaya masu"
Wannan na nufin Lahadi.
AT: "almajiran sun kulle kofofin inda suke"
A nan "Yahudawa" magana ne na shugabanin Yahudawa wadda za su iya kama almajiran. AT: "domin sun ji tsoron cewa shugabanin Yahudawa za su kama su"
Wannan sanannan suna ne da ke nufin "Bari Allah ya ba ku salama".
AT: "ya nuna masu rauni a hannuwansa da kuibinsa"
Allah Uba ya aiko Allah Ɗa wadda yanzu ya ke aikan masubi a cikin ikon Allah Ruhu mai Tsarki.
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
AT: "Allah zai gafarta masu"
"Idan ba ku gafarta zunuban wani ba"
AT: "Allah ba zai gafarta maku ba"
Wannan sunan na miji ne da ke nufin "'yan biyu." Dubi yadda kun fasar wannan a cikin 11:15.
Kalmar "shi" nanufin Toma.
AT: "Zan gaskanta idan na gan ... kuibinsa"
Kalmar "shi" na nufin Yesu.
Kalmar "shi" ya na nufin Yesu.
AT: "loƙacin da sun kulle kofofi"
Yesu ya yi amfani da wadannan maganganu "kada ka zama mara bada gaskiya" domin ya nanata kalmomin na biye, "amma ka bada gaskiya." Idan harshen ku bai yarda da abu biyu da ke a karkaceba, ko mai karatun ba zai gane cewa Yesu ya na nanata kalmomin da ka biye, ba sai kun fasara wannan magana. AT: "Wannan ne ma fi muhimmi a gare ku: dole ne ku gaskanta"
A nan "gaskanta" na nufin ba da gaskiya ga Yesu. AT: "ba da gaskiyan ku ga Yesu"
Toma ya gaskanta cewa Yesu ya na da rai domin ya gan shi. AT: "ka gaskanta cewa ina da rai"
Wannan ya na nufin "Allah ya na ba da babban farin ciki ga waɗanda."
Wannan na nufin waɗanda ba su san Yesu ba. AT: "waɗanda basu gan shi da rai ba"
Kalmar "alamu" ya na nufin abin al'ajibi da ya nuna cewa Allah ne mai dukka karfi wadda ya ke da cikakken iko a duniya.
AT: "alamun da marubucin bai rubuta akai ba a cikin wannan littafi"
AT: "amma marubucin ya rubuta game da waɗannan alamun"
Wannan muhimmin lakabi ne wa Allah.
A nan "rai" magana ne da ya na nufin Yesu ya ba da rai. "za ku iya sami rai saboda Yesu"
Wannan ya na nufin rai na ruhaniya.
1Bayan wadannan abubuwa, Yesu ya sake bayyana kansa ga almajiran a bakin tekun Tibariya. Ga yadda ya bayyana kansa: 2Saminu Bitrus na tare da Toma wanda ake kira Dan Tagwai, da Natana'ilu daga Kana ta kasar Galili, da 'ya'yan nan na Zabadi, da kuma wadansu almajiran Yesu biyu. 3Saminu Bitrus yace masu, "Zani su." sukace masa "Mu ma za mu je tare da kai." Sai suka fita suka shiga jirgi, amma a daren nan basu kama komai ba.4To, gari na wayewa, sai ga Yesu tsaye a bakin gaci, amma almajiran basu gane cewa Yesu bane. 5Sai Yesu yace masu, "Samari, kuna da wani abinda za a ci?" Suka amsa masa sukace "A'a". 6Yace masu, "Ku jefa taru dama da jirgin zaku samu wasu." Suka jefa tarunsu har suka kasa jawo shi don yawan kifin.7Sai almajirin nan da Yesu yake kauna yace wa Bitrus, "Ubangiji ne fa!" Da Saminu Bitrus yaji, Ashe, Ubangiji ne, yayi damara da taguwarsa, (don a tube yake), ya fada a tekun. 8Sauran almajiran kuwa suka zo a cikin karamin jirgi, (domin basu da nisa da kasa, kamar kamu dari biyu zuwa sama), janye da tarun cike da kifi. 9Da isowarsu gaci, sai suka ga garwashin wuta a wurin da kifi akai, da kuma gurasa.10Yesu ya ce masu "Ku kawo wandansu daga cikin kifin da kuka kama yanzu". 11Sai Saminu Bitrus ya hau, ya jawo tarun gaci, cike da manyan kifaye dari da hamsin da uku (153). Amma duk da yawansu, tarun bai tsage ba.12Yesu yace masu, "Ku zo ku karya kumallo". Daga cikin almajiran kuwa babu wanda yayi karfin halin tambayarsa "Ko shi wanene?" Domin sunsani Ubangiji ne. 13Yesu zo ya dauki gurasar ya ba su, haka kuma kifin. 14Wannan shine karo na uku da Yesu ya bayyana ga almajiransa bayan tashinsa daga matattu.15Da suka karya kumallon, Yesu yace wa Saminu Bitrus, "Bitrus dan Yahaya, kana kaunata fiye da wadannan?" Bitrus yace masa "I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka" Yesu yace masa "Ka ciyar da 'ya'yan tumakina". 16Ya sake fada masa karo na biyu, "Saminu Dan Yahaya, kana kaunata?" Bitrus Yace masa "I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka". Yesu yace masa, "Ka lura da Tumakina".17Ya sake fada masa, karo na uku, "Bitrus Dan Yahaya, kana kaunata? Sai Bitrus bai ji dadi ba domin Yesu ya fada masa karo na uku, "Kana kaunata" Yace masa, "Ubangiji ka san komai duka, ka sani ina kaunarka." Yesu yace masa "Ka ciyar da tumaki na. 18Hakika, hakika, Ina gaya maka, lokacin da kake kuruciyarka, kakan yi wa kanka damara, ka tafi inda ka ga dama. amma in ka tsufa, zaka mike hannuwanka wani yayi maka damara, ya kai ka inda baka nufa ba."19To Yesu ya fadi haka ne domin ya nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi ga daukakar Allah. Bayan ya fadi haka, sai yace wa Bitrus, ka biyo ni.20Bitrus ya juya sai ya ga almajirin da Yesu yake kauna yana biye dasu; wanda ya jingina a kirgin Yesu lokacin cin jibin nan da yace "Ya Ubangiji, wanene zai bashe ka?" 21Da Bitrus ya gan shi, yace wa Yesu "Ya Ubangiji, Me mutumin nan zai yi?"22Yesu yace masa, "Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka? Ka biyo ni." 23Wannan zance ya yadu cikin 'yan'uwa cewa, wannan almajirin ba zai mutu ba. Alhali Yesu bai cewa Bitrus, wannan almajirin ba zai mutu ba, Amma "Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka?"24Wannan shine almajirin da yake shaida wadannan abubuwa, wanda ya rubuta su, kuma mun tabbata shaidarsa gaskiya ne. 25Akwai kuma sauran abubuwa da yawa wanda Yesu yayi. Idan da an rubuta kowannensu daya bayan daya, ina gaya maku, ko duniya bazata iya daukar litattafan da za a rubuta ba.
Yesu ya nuna kansa kuma ga almajiran a Tekun Tibariya. Aya 2 da 3 ya faɗa mana abin da zai faru a cikin labarin kafin Yesu ya bayyana.
"Bayan waɗansu loƙaci"
AT: "da Toma wanda ake kira Ɗan Tagwai"
Wannan sunan na miji ne da ya na nufin "yan biyu." Dubi yadda an fasara wannan suna a cikin 11:15.
Wannan magana ne na kalma mai daɗi da ya na nufin "Abokai na na ƙwarai."
A nan "wasu" na nufin kifi. AT: "za ku kama wasu kifi a cikin taru ku"
"jawo taru ciki
Wannan irin kauna ya na zuwa daga Allah ne ya na bisa kyaun mutane, ko bai amfani wani ba. Irin wannan kauna ya na kula da mutane, ko mai abin da sun yi
"ya tsare taguwarsa a kewaye da shi" ko "ya sa kayansa"
Wannan tushen bayani ne. Bitrus ya cire kayakin shi domin ya iya yin aiki, amma yanzu da zai gai da Ubangiji, ya so ya kara sa kaya. AT: "don ya tube waɗansu kayakin shi"
Bitrus ya yi tsalle a cikin ruwa sai ya yi yanƙayi zuwa gaɓa. AT: "tsalle zuwa cikin tekun sai ya yi yanƙari zuwa gaɓa"
Wannan karin magana ne da ya na nufin cewa Bitrus ya yi tsalle a cikin ruwa da sauri.
Wannan tushen bayani ne.
"mita 90." Kamu kaɗan ne da rabin mita.
A nan "hau sama" na nufin Saminu Bitrus ya koma wurin kwalekwalen. AT: "Sai Saminu Bitrus ya kuma wurin kwalekwalen"
"jawo taru zuwa gaci"
AT: "basu karye ba"
"cike da manyan kifaye, dari da hamsin da uku." Akwai kifi 153.
abincin safe
Za ku iya fasara wannan maganan adadin jerantawa "uku" kamar "loƙaci 3."
A nan "kauna" na nufin irin kauna dake zuwa daga Allah, wadda ya ke bisa kyaun mutane, ko bai amfani wani ba.
A loƙacin da Bitrus ya amsa, ya yi amfani da kalmar "kauna" wadda yake nufin kaunar 'yan'uwa ko kaunar aboki ko kuma ɗan iyali.
A nan "tumaki" magana ne na mutanen da suke kaunar Yesu kuma suna bin shi. AT: "ka ciyar da mutanen da ina kula da su"
A nan "tumaki" magana ne na mutanen da suke kaunar Yesu kuma suna bin shi. AT: "lura da mutanen da ina kula da su"
Kalmar "shi" ya na nufin Yesu. A nan "na uku" na nufin "loƙaci na uku." AT: "Yesu ya ce mashi na uku"
Wannan loƙacin da Yesu ya yi wannan tambaya ya yi amfani da kalmar "kauna" wadda ya ke nufin kaunar 'yan'uwa ko kaunar aboki ko kuma ɗan iyali.
A nan "tumaki" magana ne da ya na wakilcin waɗanda sun zama na Yesu kuma suna bin shi. AT: "lura da mutanen da ina kula da su"
Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 15: 51.
Yahaya ya yi amfani da wannan kalma domin ya nuna cewa ya na ba da tushen bayani ne kafin ya cigaba da labarin.
A nan Yahaya ya na nufin cewa Bitrus zai mutu a kan gicciye. AT: "don ya nuna cewa Bitrus zai mutu a kan gicciye domin ya ɗaukaka Allah"
A nan kalmar "biyo" na nufin "zaman Almajiri." AT: "cigaba da zama almajiran"
Yahaya ya kira kansa haka a duk lokaci a littafin, a maimakon kiran sunansa.
Wannan ya na nufin abincin dare na karshe. (Dubi: John Chapter 13)
A nan "shi" na nufin "almajirin da Yesu yake kauna."
Bitrus ya na so ya san abin da zai faru da Yahaya. AT: "Ya Ubangiji, me nene zai faru da wannan mutum?"
"Yesu yace wa Bitrus"
A nan "shi" ya na nufin ""almajirin da Yesu yake kauna" a cikin 21:20.
Wannan ya na nufin zuwan Yesu na biyu, dawowar sa duniya daga sama.
Wannan magana ya bayyana kamar tambaya ne don ya bayana tsawa mara tsanani. AT: "ka da ku damu da wannan."
A nan "'yan'uwa" na nufin dukka masubin Yesu.
" almajirin Yahaya"
A nan "shaida" ya na nufin cewa shi da kansa ya na gannin abubuwa. AT: "wadda ya gan dukka waɗannan abubuwa"
A nan "mu" ya na nufin waɗanda sun gaskanta da Yesu. AT: "mu da mun gaskanta da Yesu mun san"
AT: "Idan wani ya rubuto dukkansu"
Yahaya ya zuguiguita domin ya nanata cewa Yesu ya yi abin al'ajibi dayawa fiye da abin da mutane na iya rubutawa a kai a cikin wannan littatafan.
AT: "litattafan da mutane na iya rubutawa game da abin da yi"
1Littafin da na rubuta da farko, Tiyofilos, ya fadi abubuwan da Yesu ya fara yi ya kuma koyar, 2har zuwa ranar da aka karbe shi zuwa sama. Wannan kuwa bayan da ya ba da umarni ga zababbun manzanninsa ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 3Bayan ya sha wahala, ya bayyana kan sa da rai a garesu, da alamu da dama masu gamsarwa. Kwana arba'in ya baiyana kansa a garesu yana yi masu magana game da mulkin Allah.4Yayin da yana zaune tare da su ya basu umarni cewa kada su bar Urushalima, amma su jira alkawarin Uban, wanda ya ce, "Kun ji daga gare ni, 5cewa Yahaya babu shakka ya yi baftisma da ruwa, amma ku za a yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki nan da kwanaki kadan."6Sa'adda suna tare suka tambaye shi, "Ubangiji, a wannan lokaci ne za ka maido da mulki ga Isra'ila?" 7Ya ce masu, "Ba naku bane ku san lokaci ko sa'a wanda Uba ya shirya ta wurin ikonsa. 8Amma za ku karbi iko, idan Ruhu Mai Tsarki ya zo bisanku, sa'annan za ku zama shaidu na cikin Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, har ya zuwa karshen duniya."9Lokacin da Ubangiji Yesu ya fadi wadannan abubuwa, yayin da suna kallon sama, sai aka dauke shi zuwa sama, kuma girgije ya boye shi daga idanunsu. 10Da suka dinga kallon sama yayin da ya tafi, nan da nan, mazaje biyu suka tsaya a gabansu cikin fararen tufafi. 11Suka ce, "Ku mazajen Galili me yasa ku ke tsaye a nan kuna kallon sama? Wannan Yesu wanda ya hau zuwa sama zai dawo kamar yadda kuka gan shi yana tafiya zuwa sama."12Da suka dawo Urushalima daga dutsen Zaitun, wanda ke kusa da Urushalima, tafiyar Asabaci daya ne. 13Da suka iso, sai suka haye zuwa cikin bene inda suke da zama. Sune su Bitrus, Yahaya, Yakubu, Andarawus, Filibus, Toma, Bartalamawus, Matiyu, Yakubu dan Alfa, Siman mai tsattsauran ra'ayi, kuma da Yahuza dan Yakubu. 14Dukansu kuwa suka hada kai gaba daya, yayin da suka ci gaba da naciya cikin addu'a. Tare da su kuma akwai mata, Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma 'yan'uwansa.15A cikin wadannan kwanaki Bitrus ya tashi tsaye a tsakiyar 'yan'uwa, kimanin mutane dari da ashirin, ya ce, 16" 'Yan'uwa, akwai bukatar Nassi ya cika, wanda Ruhu Mai Tsarki ya fada a baya ta bakin Dauda game da Yahuza, wanda ya jagoranci wadanda suka kama Yesu17Domin yana daya daga cikinmu kuma ya karbi rabonsa na ladan wannan hidima," 18(Wannan mutum fa ya sai wa kansa fili da cinikin da ya yi na muguntarsa, kuma a nan ya fado da ka, cikinsa ya fashe, hanjinsa suka zubo waje. 19Duka mazaunan Urushalima suka ji wannan, saboda haka suka kira wannan fili da harshensu "Akeldama" wato, "Filin Jini.")20"Domin an rubuta a littafin Zabura, 'Bari filinsa ya zama kufai, kada a bar kowa ya zauna wurin,'kuma, 'Bari wani ya dauki matsayinsa na shugabanci.'21Saboda haka ya zama dole, daya daga cikin wadanda suke tare da mu tun lokacin da Ubangiji Yesu yana shiga da fita, a tsakaninmu, 22farawa daga baftismar yahaya har zuwa ranar da aka dauke shi daga wurinmu zuwa sama, ya zama daya daga cikin mu wurin shaidar tashinsa." 23Suka gabatar da mutum biyu, Yusufu wanda ake kira Barsabbas, wanda kuma aka yiwa suna Justus, da kuma Matayas.24Su ka yi addu'a suka ce, "Ubangiji, kai ka san zuciyar dukan mutane, ka bayyana mana wanda ka zaba cikin su biyun nan 25Domin ya dauki gurbin da kuma manzancin daga inda Yahuza ya kauce zuwa nashi waje" 26suka jefa kuri'a a kansu; zabe ya fada kan Matayas kuma suka lissafta shi tare da manzanni sha dayan.
Litafin forkon shi ne Bishara ta hannun Luka.
Luka ya rubuto wannan litafi zuwa ga wani mai suna Tiyofilos. Ma'anan Tiyofilos shi ne "abokin Allah"
Wannan na nufin haurawar Yesu zuwa cikin sama. AT: "har zuwa ranar da aka karɓe shi zuwa sama"
Ruhu Mai Tsarki Ya bishe Yesu ya umurci manzanensa game da wasu abubuwa.
Wannan na nufin wahalar Yesu da mutuwar sa bisa kan giciye.
Yesu ya bayana kansa ga manzanensa da kuma sauran almajirensa da dama.
Waɗannan abubuwan sun faru ne a lokacin kwanaki 40 da Yesu ya bayyana kansa wa almajirensa bayan ya tashi daga matattu.
Anan kalmar "shi" na nufin Yesu.
Yayin da yana zama tare da manzanninsa"
Wannan na nufin Ruhu Mai Tsarki. AT: Ruhu Mai Tsarkin, wadda Uban Ya yi alƙawari cewa zai aika.
Idan kun fasara jimla na baya a haɗe da Kalamun na "Ruhu Mai Tsarki," za ku iya canja kalmar "wanda" zuwa "wadda." AT: "game da wadda Yesu ya ce"
Yesu yana nuna bambancin yadda Yahaya na yi wa mutane baptisma da ruwa da yadda Allah zai yi wa masubi baptisma da Ruhu Mai Tsarki.
"Yahaya hakĩka ya yi wa mutane baftisma da ruwa"
Ana iya faɗin wannan a siffar aiki. AT: Allah zai yi maku baftisma"
"za ka sake mayar da Isra'ila babban masarauta kuma"
Yana iya yiwuwa wannan na nufin 1) kalamun "lakatai" da "sa'o'i" na nufin lokaci iri daban-daban. AT: " duka lokaci ko takamaimain rana ko kuma 2) kalamu biyun a takaice na da ma'ana guda. AT: "takamaimain lokaci"
Manzannin za su karɓi ikon da zai iza su su zama shaidun Yesu. AT: "Allah zai inganta ku ... ku zama shaidu na"
Yana iya yiwuwa wannan na nufin 1) "dukan duniya" ko 2) "zuwa wurare a duniya mafi nisa kwarai"
"da suke duba." Manzannin'' na kallon sama" ga Yesu domin ya tashi zuwa sararin sama" AT: "yayin da suke kallon sama" .
Anan iya faɗin wannan a siffar aiki. AT: ya tashi zuwa cikin sama" ko kuma "Allah ya ɗauke shi zuwa sama"
"girgijen ya tare su har basu iya cigaba da ganin sa kuma ba"
"zuba ido sama" ko kuma "ƙura idon su suma"
Mala'ikun sun kira manzannin a matsayin mutanen da ke daga Galili.
Yesu zai dawo daga sama, kamar yadda girgijen sun rufe shi yayin da ya taso zuwa sama.
"Manzannin sun komo"
Wannan na nufin tsawon tafiya wadda, bisa ga al'adun Malaman Yahudawa, ana iya barin mutum yayi tafiya a ranan asabar. AT: " kilomita ɗaya daga nan"
"Da suka kai masaukinsu." Aya 12 ya ce suna komowa Urushalima.
"ɗakin da ke sama a gidan"
Wannan na nufin Manzannin da masubin duk sun haɗa kai da alkawari da manufa ɗaya, kuma babu jayayya a cikin su.
Wannan na nufin almajiran sun saba yin addu'a tare a kullum kuma akai-akai.
Waɗannan kalamun na ba da alamar wata sabuwan sashin labarin. Suna nufin bayan da Yesu Ya hauro sama yayin da almajiren suna haɗuwa a wata ɗaki da ke sama. AT: "A wancan loƙacin"
"ɗari da ashirin"
Anan kalmar "'yan'uwa" na nufin 'yan'uwa masubi, maza da mata.
Ana iya faɗin wannan a siffar aiki. AT: Lallai ne abubuwan da muka karanta a Nassi sun cika"
Kalmar "baki" anan na nufin kalamun da Dauda ya rubuto. AT: "ta kalamun Dauda"
Kalamun "wannan mutum" na nufin Yahuza Iskariyoti.
"kuɗin ladan muguntar da yayi". Kalamun "muguntarsa" na nufin Yahuza Iskariyoti ya basher da Yesu wa mutanen da suka kashe shi.
Wannan na ba da ra'ayin cewa Yahuza ya faɗo daga wani wurin mai tsayi, ba wai ya bi ya faɗo kawai ba. Faɗin ya isa yasa cikin sa ya fashe. Wasu ayoyin nassi sun ce ya ratiye kansa.
Da mutanen da ke zama a Urushalima sun ji yadda Yahuza ya mutu, sun sake wa filin suna.
Ana iya faɗin wannan a siffar aiki. AT: "Domin Dauda ya rubuta a littafin Zabura"
Wadannan jimla biyun suna nufin abu ɗaya ne atakaice. Na biyun yana nanata ma'anan na forkon ta wurin maimaita ra'ayi ɗaya da kalamu daban-daban.
Yana iya yiwuwa wannan na nufin 1) cewa kalmar "fili" na nufin fillin da Yahuza ya mutu Ko Kuma 2) cewa kalmar "fili" na nufin wurin mazaunin Yahuza kuma magana ce da ke nufin zuriyansa.
"ya zama ba kowa a ciki"
Bisa ga nasosin da ya ambato da kuma bisa ga abinda da Yahuza ya yi, Bitrus ya faɗa wa ƙungiyar abinda za su yi.
Bitrus ya ba da jerin halayen da sun cancanta a samu mutumin da zai maye gurbin Yahuza da shi a matsayin manzo.
tafiya ciki da wajen a tsakanin wata taron mutane magana ce da ke nufin kasancewa ɗaya daga cikin taron. AT: "Ubangiji ya zauna a tsakaninmu"
"A nan iya fasara sunan "baftisma" zuwa kalman aiki. Yana iya yiwuwa ma'anan shine 1) "tun daga lokacin da Yahaya yayi wa Yesu baftisma" ko kuma 2) "tun daga lokacin da Yohanna ya yi wa mutane baftisma"
Ana iya faɗin wannan a siffar aiki. AT: "har ranan da Yesu ya bar mu ya kuma haura sama" ko kuma har ranan da Allah ya ɗauke shi daga wurinmu"
A nan kalmar "su" na nufin dukan masubin da ke wurin. AT: "Suka ba da sunayen mutane biyu da suka cika duk halayen da ake bukata da Bitrus ya jera"
Ana iya sanar da wannan a siffar aiki. AT: "Yusufu, wadda mutane ke kira Barsabbas da Justus"
A nan kalmar "su" na nufin dukan masubin, amma dai yana iya yiwuwa ɗaya daga cikin manzanen ne ya furta wadanan kalamun. AT: "Masubin sun yi addu'a tare sa'anan ɗaya daga cikin manzanen ya ce"
A nan kalmar "zukata" na nufin tunani da kuma manufofi. AT: "Ubangiji, kai ka san tunani da kuma manufofin kowa"
A nan kalmar "manzanci" na ba da ma'anar irin "hidimar" da ke akwai. AT: "ya karbi gurbin Yahuza cikin wannan hidimar manzancin" ko kuma "ya karbi gurbin Yahuza cikin bauta a matsayin manzo"
A nan wannan furcin "ƙauce" na mufin cew Yahuza ya daina yin wannan hidimar. AT: "wadda Yahuza ya daina cikawa"
Jimlar nan na nufin mutuwar Yahuza, kuma ya yiwu shari'ar sa bayan mutuwa. AT: "ya je wurin da yakamãta"
Manzannin suka jefa kuri'a domin su yanke shawara tsakanin Yusufu da matayas.
Zaɓen ya nuna cewa Matayas ne wanda zai maye gurbin Yahuza.
Ana iya faɗin wannan a siffar aiki. AT: "masubin sun ɗauke shi ya zama manzo tare da sauran sha-ɗayan"
1Da ranar Fentikos ta zo, dukansu suna tare wuri daya. 2Nan da nan sai ga wata kara daga sama kamar ta babbar iska, kuma ta sauko ta cika duka gidan inda suke zaune. 3Sai ga wasu harsuna kamar na wuta sun bayyana a garesu aka rarraba su, kuma suka zauna bisa kowannensu. 4Dukansu suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka fara magana da wadansu harsuna, yadda Ruhu ya ba su iko su yi magana.5A lokacin akwai Yahudawa dake zaune a Urushalima, mutanen Allah, daga kowace kasa karkashin sama. 6Da suka ji wannan kara jama'a duk suka taru suka rude saboda kowannensu ya ji suna magana da harshensa. 7Suka yi mamaki matuka; suka ce, "Lallai, wadannan duka ba Galiliyawa ba ne?8Yaya mu ke jinsu duka, kowannensu na magana a cikin harshen da aka haife mu? 9Fisiyawa da Mediyawa da Elimawa, da Yahudawa da Kafadokiya, cikin Fontus da Asiya, 10cikin Firgia da Bamfiliya, cikin Masar da yankunan Libiya ta wajen Sur, da baki daga Roma, 11Yahudawa da tubabbun cikin Yahudanci, Kiretawa da Larabawa, duk munji su suna fadi a harshenmu game da manyan ayyukan Allah."12Dukansu suka yi mamaki suka rikice; suka ce da junansu, "Menene ma'anar wannan?" 13Amma wasu suka yi ba'a suka ce, "Sun bugu ne da sabon ruwan inabi."14Amma Bitrus ya tashi tare da sha dayan, ya daga murya ya ce da su, "Mutanen Yahuda da dukanku dake zaune a Urushalima, bari ku san wannan; ku saurari maganata. 15Domin wadannan mutanen ba buguwa suka yi ba yadda kuke zato, domin yanzu karfe tara ne na safe kawai.16Amma wannan shine abinda aka fada ta wurin annabi Yowel. 17Allah ya ce, 'Haka zai kasance a kwanakin karshe, zan zubo Ruhuna a kan dukan mutane, 'ya'yanku maza da mata za su yi anabci, kuma samarinku za su ga wahayoyi, kuma tsofaffinku za su yi mafarkai.18Haka kuma a bisa bayi na maza da mata, a kwanakin nan zan zubo da Ruhuna, kuma za su yi anabci. 19Zan nuna al'ajibai a sararin sama da kuma alamu a bisa duniya, jini da wuta, da girgije.20Rana zata juya ta koma duhu kuma wata ya koma jini, kafin Babbar ranan nan ta Ubangiji ta zo. 21Zai kuma zama dukan wanda ya kira ga sunan Ubangiji zai sami ceto.22Mutanen Isra'ila, ku saurari wadannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar da shi gareku ta wurin manyan ayyuka da ban mamaki da alamu da Allah ya yi ta wurinsa a tsakiyarku, kamar yadda ku da kanku kuka sani. 23Saboda tabbataccen shiri da riga sani na Allah, aka bayar dashi, ku kuma, ta hannun mutane 'yan tawaye, kuka gicciye shi kuma kuka kashe shi. 24Wanda Allah ya tayar, bayan ya cire zafin mutuwa daga gareshi, saboda ba zai yiwu ba ta rike shi.25Gama, game da shi, 'Ina ganin Ubangiji a gabana ko yaushe, domin yana gefen hannun damana saboda kada in firgita. 26Saboda haka zuciyata na farin ciki harshena yana yin murna. Kuma, jikina zai zauna gabagadi.27Gama ba za ka watsar da raina a lahira ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka ya ga ruba ba. 28Ka bayyana mani hanyar rai; da fuskarka zaka cika ni da farin ciki.29'Yan'uwa, zan yi magana da ku gabagadi game da baba Dauda: ya mutu kuma aka bizne shi, kuma kabarinsa na nan tare da mu har yau. 30Domin haka, don shi annabi ne kuma ya san Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa daga cikin zuriyarsa zai sanya wani bisa kursiyinsa. 31Ya hango wannan al'amari kuma ya yi magana game da tashin Almasihu, 'Ba ayi watsi da shi ba a lahira, kuma jikinsa bai ga rubewa ba.'32Wannan Yesun - Allah ya tashe shi, wanda dukanmu shaidu ne. 33Saboda haka yadda aka tashe shi zuwa hannun dama na Allah kuma ya karbi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, shine ya zubo mana wannan da kuke gani kuma kuke ji.34Dauda bai hau zuwa sama ba, amma ya ce, "Ubangiji ya ce wa Ubangijina, "Zauna hannun dama na, 35har sai na maida makiyanka abin takawar sawunka.'" 36Saboda haka, bari gidan Isra'ila su sani tabbas wannan Yesun wanda kuka gicciye, Allah ya maishe shi Ubangiji da kuma Almasihu.37Da suka ji haka sai suka soku a zukatansu, suka cewa Bitrus da sauran manzanni, '"Yan'uwa me za mu yi?" 38Sai Bitrus ya ce masu, "Ku tuba ayi wa kowannenku baftisma, cikin sunan Yesu Almasihu domin gafarar zunubanku, kuma za ku karbi baiwar Ruhu Mai Tsarki. 39Domin alkawarin a gareku ne da 'ya'yanku da duk wadanda ke nesa, dukan iyakar mutanen da Ubangiji Allahnmu zai kira."40Da maganganu da yawa ya ba da shaida kuma ya karfafa su; ya ce, "Ku ceci kan ku daga wannan muguwar tsara." 41Sai suka karbi maganar sa kuma aka yi ma su baftisma, a wannan rana kuma aka sami karin rayuka wajen dubu uku. 42Su ka cigaba cikin koyarwar manzanni da zumunta, cikin kakkaryawar gurasa da kuma cikin addu'o'i.43Tsoro ya sauko bisa kowane rai, kuma aka yi abubuwan ban mamaki da alamu da yawa ta wurin manzannin. 44Duka wadanda suka ba da gaskiya suna tare kuma komai nasu na kowanensu ne, 45kuma suka saida kadarorinsu da mallakarsu kuma suka rarrabawa kowa, bisa ga irin bukatar da kowannensu yake da ita.46A kowace rana suka cigaba tare da nufi daya a cikin haikali, suna kakkarya gurasa a gidaje, kuma suna raba abinci tsakaninsu cikin farin ciki da tawali'u a zuciya; 47Suna yabon Allah kuma suna da tagomashi a gaban dukan mutane. Ubangiji kuma kullum yana kara masu wadanda suke samun ceto.
Wannan wata sabuwar abu ce; yanzu ranar Fentikos ne, kwanaki 50 bayan Idin ketarewa.
Wannan na nufin abin da ya faru ba zato ba tsammani
Yana iya yiwuwa ma'anan shi ne 1)"sama" na nufin Wurin da Allah yake zama. AT: "wata ƙara ta fito daga sama" ko kuma 2) "sama" na nufin sararin sama. AT: "wata ƙara daga sararin sama"
"wata hayaniya kamar ƙaran wata iska mai ƙarfin gaske na hurawa"
Wannan na iya yiwuwa gidan ko ginin babba ne sosai.
Ba lallai ne waɗanan su zama ainihin harsuna ko wuta ba, amma wani abu ne dai yayi kama da su. Yana yiwuwa ma'anan sune 1) harsuna da sun yi kamar anyi su da wuta ko kuma 2) kananan wuta da sun yi kamar harsuna. Idan wuta na ƙona wa, kamar a fitilla, wutan na daukan kamanin harshe.
Wannan na nufin "harsuna kamar wuta" sun warwatsa yadda akwai daya bisa kowane mutum.
Ana iya faɗin wannan a siffar aiki. AT: Ruhu Mai Tsarki ya cika dukan waɗanda suke wurin sa'anan suka"
Waɗanan harsuna ne da basu taba saninsu ba.
A nan "Mutanen Allah" na nufin mutanen da sun mika kai cikin yi wa Allah sujada kuma suna kokarin biyayya da dukan shari'ar Yahudawa.
"kowace ƙasa a duniya." Kalmar "kowace" ƙari ne da ke nanata cewa mutanen daga ƙasashe da dama ne daban-daban kuma. AT: ƙasashe da dama daban-daban"
Wannan na nufin ƙaran da ya yi kama da na wata iska mai ƙarfi.
"babban taron jama'a"
An yi amfani da kalamai biyu a turance masu ma'ana guda domin a nanata tsananin mamakinsu. AT: "Sun yi mamaƙi ƙwarai"
Mutanen sun yi wannan tambayan ne domin su nuna mamakinsu. Anan iya canza tambayan zuwa furcin ban mamaki. AT: Ai waɗanan Galaliyawan ba za su iya sanin harsunanmu ba!"
Yana iya yiwuwa wannan na nufin 1) wannan tambayan ganganci ne da ke bayyana sananin mamakin su ko muma 2) wannan ainihin tambaya ne da mutanen ke buƙatan amsa.
"a cikin harsunan mu da muka koya tun daga haifuwa"
Wannan ya ba da jerin wasu ƙasashe, yankuna, da jahohi da suka fito.
tubabbun cikin Yahudanci
adanan kalamu biyun suna da ma'ana kusan ɗaya. Dukkansu na nanata cewa mutanen basu iya gane abin da ke faruwa ba. AT: "yi mamaki suka rikice"
Wasu mutanen sun zarge masubin da buguwa da sabon ruwan inabi. AT: "Sun bugu"
Wannan na nufin ruwan inabin da ya fara tsami.
Bitrus ya fara maganarsa wa Yahudawan da suke wurin a ranan Fentikos.
Duk manzannin sun tsaya suna goyon bayan jawabin Bitrus.
Wannan karin magana ne da ke nufin "ya yi magana da ƙarfi" (Dubi: rc://*/ta/man/translate/figs-idiom)
Wannan na nufin cewa Bitrus zai yi bayyanin ma'anan abin da mutanen ke gani. Ana iya sanar da wannan a siffar aiki. AT: "ku san wannan" ko kuma "bari in bayyana muku wannan"
Bulus na nufin abinda yake faɗi. AT: "ku kasa kunne sosai ga magana ta"
Bulus na sa rai cewa yakamata masu sauraron su san cewa mutane basu buguwa da safe.
Ana iya faɗin wannan a siffar aiki. AT: "wannan shine abinda Allah ya gaya wa annabi Yowel ya rubuta" ko kuma "wannan shine abinda annabi Yowel ya faɗa"
"Ga abinda zai faru" ko kuma "Ga abinda Ni zan yi"
A nan kalaman nan "zubo" na nufin a bayar a da matukar yawa a yalwace. AT: Zan ba da Ruhuna sosai ga dukan mutane"
"dukan bayi na maza da mata." Wadannan kalamun na nanata cewa Allah zai zubo da Ruhunsa bisa dukan bayin sa, wato maza da mata.
A nan kalaman nan "zubo" na nufin a bayar da matuƙar yawa a yalwace. Duba yadda kun fasara wannan a [Ayyukan Manzanni 2:17]. AT: "Zan ba da Ruhuna a yalwace ga dukan mutane"
"hayaƙi mai ƙauri" ko kuma "hazon hayaƙi"
Wannan na nufin cewa rana zai fito da duhu maimakon hasƙe. AT: Rana zai zama duhu"
Wannan na nufin wata zai fito ja kamar jini. AT: wata zai fito ya zama ja"
Kalamun nan "babba" da "ƙwarai" na da ma'ana kusan ɗaya kuma suna nanata muhimmin ranar. AT: "wannan babbar ranan"
babba kuma ƙyaƙyawa
Ana iya faɗin wannan a siffar aiki. AT: "Ubangiji zai ceci dukan wanda ya kira gare shi"
"ku ji abinda zan faɗa"
Wannan na nufin cewa ya tabbatar cewa shi ne ya zaɓi Yesu domin aikinsa, ya kuma tabbatar da wannan ta wurin al'ajibai.
Ana iya fasara "shiri" da "riga-sani" zuwa kalmar aiki.
AT: "kun bayar da Yesu zuwa ga abokan gabansa" ko kuma 2) Yahuza ya bashe Yesu zuwa gareku.
Ko da shike 'yan tawaye" ne suka giciye Yesu, Bitrus yana ɗorawa taron laifin kashe Yesu domin sun nema ya mutu.
A nan "hannun" na nufin ayyukan 'yan tawaye. AT: "ta wurin ayyukan 'yan tawaye" ko kuma "ta wurin abubuwan da 'yan tawaye suka yi"
AT 1) Yahudawan da basu gaskanta ba sun ba wa Yesu laifuka ko 2) Sojojin Roma da suka yi kisan Yesu.
A nan a tayar karin maganane da ke sa wanda ya mutu ya dawo da rai kuma. AT: "Amma Allah ya sa shi ya rayu kuma"
Bitrus yana maganan mutuwar kamar wani mutum ne da ke ɗaura mutane da igiyoyi masu zafi ya riƙe su. Yana maganar yadda Allah ya cire zafin mutuwar Almasihu kamar Allah ya yanke igiyoyin da suka riƙe Almasihu ya kuma yantas da shi. AT: "ƙãre zafin mutuwa"
AT: "mutuwa ta riƙe shi"
AT: "a kasancewa ta" ko "tare da ni"
Kasancewa a "hannun daman" mutum kan iya nufin kasancewa a wani matsayin taimako ko rayawa. AT: "dap da ni" ko kuma "tare da ni ya taimake ni"
Anan kalmar "jijjigu" na nufin firgita. AT: "mutane ba za su iya sa in firgita ba" ko "ba abin da zai firgitar da ni"
Mutanen kan ɗauka "zuciya" itace cibiyar shauki sa'anan "harshe" ne muryar wanɗanan shaukin. AT: "na yi farin ciki na kuma yi murna"
"jiki" na nufin 1) mutum dai zai mutu AT: ko da shike ni mutum ne, ina da gaba gaɗi ga Allah. ko 2) yana nufin mutum gabaki ɗaya. AT: "Zan yi rayuwa da gaba gaɗi"
Almasihu, Yesu na nufin shi da kansa ne da "Mai Tsarkinka" AT: ba kuwa za ka bar ni, Mai Tsarkinka, in ga ruɓa ba"
A nan Kalmar "ga" a nan na nufin a ɗanɗana abu. Kalmar "ruɓa" na nufin bazuwar jiki bayan mutuwa. AT: "ta ruɓa"
"hanyoyin da ke kai ga rai"
A nan "Fuska" na nufin kasancewar Allah. AT: "mutuƙar farin ciki da na ganka" ko "matuƙar farin ciki da ina gabanka"
murna, jin daɗi
"'Yan'uwana Yahudawa, Ni"
AT: "ya mutu kuma mutane sun bisne shi"
"Allah zai sanya ɗaya daga cikin zuriyan Dauda bisa Kursiyin Dauda." AT: "Allah za zaɓa ɗaya daga cikin zuriyan Dauda ya zama sarki a wurin Dauda
A nan wani daga jikinsa na nufin wani da zai haifa. AT: "wani dan zuriyansa"
AT: "Allah bai ƙyale shi zuwa lahira ba"
A nan Kalmar "ga" na nufin a ɗandana abu. Kalmar "ruɓa" na nufin bazuwar jiki bayan mutuwa. Dubi yadda aka fasara wannan a [Ayyukan Manzanni 2:27] AT: "ko kuwa jikinsa ya ruɓa" ko kuma "ko kuwa ya bar shi ya daɗe a mace har jikinsa ya ruɓe"
Wannan karin magana ne. AT: "Allah ya sa shi ya rayu kuma"
AT: saboda Allah ya daukaka shi zuwa hannun damarsa"
A nan "zubo" na nufin cewa Yesu, wanda shi ne Allah, ya sa waɗanan abubuwan su faru. Abin fakaici ne cewa ya yi wannan ta wurin ba da Ruhun sa Mai Tsarki ga masubi. AT: "ya sa waɗanan abubuwan da"
A nan kalmar nan "zubo" na nufin a bayar da matukar yawa a yalwace. Duba yadda ku fasara irin wannan jimlar a [Ayyukan Manzani 2:17]. AT: "bayar a yalwace"
Zauna a "hannun damar Allah" alama ce na karɓan girmamawa da iko daga Allah. AT: Zauna a wurin daraja a gefena"
Wannan na nufin cewa Allah zai ya sa makiyan Almasihu gaba daya su sha kashi ya kuma sa su a karkashin sa. AT: "sai Na baka nasara bisa duk makiyanka"
Wannan na nufin Kasan Isra'ila. AT: "kowane ba Isra'ila"
"Da mutanen suka ji abinda Bitrus ya faɗa"
AT: "Maganar Bitrus ya soki zukatansa"
Wannan na nufin sun gane cewa su masu laifi ne sai suka yi bakin ciki kwarai. AT: "damu kwarai"
AT: "ku bar mu mu yi muku baftisma"
"a cikin sunan" anan na nufin "ta wurin ikon" AT: ta wurin ikon Yesu Almasihu"
Wannan na nufin 1) "dukan waɗanda ke zama da nisa" ko 2) "dukan mutanen da ke da nisa da Allah."
Anan kalamumin nan "shaida" da kuma "karfafa" na da ma'ana kusan ɗaya kuma suna nanata cewa Bitrus ya karfafa su sosai ne su amince da abinda yake faɗi. AT: "ya karfafasu sosai"
Abin shi ne Allah zai hukunta "wannan muguwar tsaran" AT: "Ku ceci kanku daga hukuncin da waɗanan mugayen mutanen za su sha"
A nan kalmar nan "karɓi" na nufin cewa sun gaskanta da abinda Bitrus na faɗi. AT: "sun gaskanta abinda bitrus ya ce"
AT: "mutane sun yi musu baftisma"
AT: "rayuka kusan dubu uku suka haɗa kai da masubi a wannan rana"
" A nan kalmar "rayuka" na nufin mutane. AT: kusan mutane 3000"
Gurasa na cikin abincin da suke ci. Wannan na iya nufin 1) kowane abincin da suke ci tare. AT: "cin abinci tare" 2) za su ci abinci tare domin tunawa da mutawa da tashiwar Almasihu. AT: "cin jibi tare"
A nan "tsõro" na nufin sun girmama Allah. Kalmar "rai" na nufin mutum gaba ɗaya. AT: "Kowane mutum ya girmama Allah sosai"
AT: 1) "manzanen sun yi abubuwan ban mamaki da alamu da yawa" 2) Allah ya yi abubuwan ban mamaki da alamu da yawa ta wurin manzannin"
"ayyukan mu'ujjizai da aukuwan allahntaka" (Duba yadda kun juya wannan a [Ayyukan Manzani 2:22].
AT: "Dukan su sun gaskanta da abu ɗaya" ko 2) Dukan su sun gaskanta cewa suna wuri ɗaya"
"sun raba mallakarsu da juna"
"fili da abubuwan da suke da su"
A nan "su" na nufin ribar da sukayi daga siyar da kadarorinsu da mallakarsu. AT: "rarraba riban wa kowa"
Sun rarraba raban da suka samu daga siyar da kadarorinsu da mallakarsu ga duk mai bi da ke da bukata.
AT: 1) "sun ci gaba da saduwa tare ko kuma 2) dukansu sun cigaba da hali ɗaya."
Gurasa na cikin abincin da suke ci. AT: "sun ci abinci tare a cikin gidanjensu"
Anan "zuciya" na nufin "shauki". AT: "da farin ciki da kaskanci"
"suna yabon Allah. Dukan mutane kuma sun amincewa da su"
AT: "waɗanda Ubangiji ke basu ceto"
1Sa'adda Bitrus da Yahaya suna hanya zuwa haikali a lokacin addu'ar karfe uku. 2Wani mutum, gurgu ne tun daga haihuwa, ana daukar sa kulluyomi zuwa kofar haikali da ake kira Kyakkyawa, domin bara gun mutanen da ke shiga haikalin. 3Da ya ga Bitrus da Yahaya suna shiga haikalin, sai ya roke su sadaka.4Bitrus da Yahaya kuwa suka zuba masa ido, Bitrus ya ce, "Ka dube mu." 5Gurgun nan kuwa ya dube su, yana tsammanin zai sami wani abu a wurin su. 6Amma Bitrus ya ce, "Azurfa da Zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, zan baka. A cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, Yi tafiya"7Bitrus ya kama hannun damarsa, ya daga shi; nan da nan kafafunsa da kashin idon sawayensa suka samu karfi. 8Da gurgun ya yunkura, ya mike tsaye sai ya fara takawa; ya shiga haikali tare da Bitrus da Yahaya, yana takawa, yana tsalle, yana kuma girmama Allah.9Dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana kuma yabon Allah. 10Sun lura cewa, shine mutumin da ke zama yana bara a Kyakyawar kofar haikali; sai suka cika da mamaki domin abin da ya faru.11Yayin da yake rike da Bitrus da Yahaya, dukan jama'a suka matso wurinsu, a gefen dakalin Sulaimanu, suna ta mamaki kwarai. 12Da Bitrus ya ga haka ya amsa wa jama'ar, "Ya ku mutanen Isra'ila, don me ku ke mamaki?" Don me ku ka zura mana ido, kamar mu ne muka sa shi ya yi tafiya da ikon kanmu ko adalcin mu?13Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, Allah na iyayenmu ya girmama bawansa Yesu. Shi kuka ki kun kuma bashe shi a gaban Bilatus da ya so ya sake shi. 14Kuka ki Mai Tsarkin nan, Mai Adalcin, maimakon haka kuka ce a sakkar maku mai kisan kai.15Kun kashe mai ba da rai, wanda Allah ya tayar daga matattu, mu kuwa shaidu ne ga wannan al'amari. 16Yanzu, ta bangaskiya ga sunansa - wannan mutum da kuke gani kuma kun san shi - ta wurin wannan sunan ne ya sami karfi. Bangaskiya cikin Yesu ta ba shi cikakkiyar lafiya, a gabanku duka.17Ya ku 'yan'uwa, na san kun yi haka ne cikin rashin sani, yadda shugabaninku suka yi. 18Amma duk abubuwan da Allah ya fada ta bakin dukan anabawansa, cewa Almasihunsa zai sha wahala, yanzu ya cika.19Saboda haka, Ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, domin lokacin sabuntuwa daga wurin Ubangiji ya zo; 20domin a aiko maku da Almasihu wanda aka kaddara wato, Yesu.21Shine wanda dole sama ta karbe shi har zuwa lokacin komo da dukan abubuwa, game da abubuwan da Allah ya fada tun da ta bakin annabawansa tsarkaka. 22Musa hakika ya ce, 'Ubangiji Allah zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin, 'yan'uwanku. Za ku saurari dukan abin da zai fada maku. 23Zai kasance kowanne mutum da bai saurari annabin nan ba za a kau da shi gabadaya daga cikin mutanensa.'24I, dukan annabawa tun daga Sama'ila da wadanda suka zo bayansa, sun yi magana sun ambaci wadannan kwanaki. 25Kune 'ya'yan annabawa da na alkawari wanda Allah ya yi da kakanninku, yadda ya ce wa Ibrahim, 'Daga zuriyarka dukan al'uman duniya za su sami albarka.' 26Bayan da Allah ya ta da bawansa, a gareku ne ya fara aiko shi, domin ya albarkace ku tawurin juyadda kowannenku daga muguntarsa."
Wata rana Bitrus da Yahaya sun tafi Haikali.
Aya 2 ya bada hoton baya game da gurgun.
Basu je cikin ginin haikalin inda firistoci ne kaɗai ake bari su je ba. AT: "zuwa tsakar haikalin" ko kuma "zuwa yankin haikali"
A kowace rana, mutane na ɗauƙan wanan mutum, gurgu tun daga haihuwa, sai su ajiye shi kusa da wata kofar haikali
yana kasa iya tafiya
Bitrus da Yahaya sun kalle shi, amma Bitrus ne kadai yayi magana.
wannan na iya nufin 1) "yana kallon shi kai tsaye" ko kuma 2) "yana kallon shi da duk niyarsa"
A nan kalmar "duba" na nufin sa hankali ga wani abu. AT" Gurgun ya sa hankalin sa a kan su"
Waɗannan na nufin kuɗi.
An iya gane cewa Bitrus yana damar iya warkas da mutumin.
A nan kalmar "suna" na nufin ƙarfi da iko. AT: "Da ikon Almasihu Yesu"
...
"Bitrus ya sa shi ya tsaya"
Bai je cikin ginin haikalin inda firistoci ne kaɗai ake bari su je ba. AT: "ya shigo ... yankin haikalin" ko kuma "ya shigo ... zuwa tsakar haikalin"
"sun ɗago cewa mutumin ne" ko kuma "sun gane cewa mutumin ne"
Wannan ne sunan ɗaya dage cikin kofofin haikalin. Duba yadda kun fasara wannan a irin wannan jimla a [Ayyukan Manzanni 3:2]
A nan kalamun nan "mamaki da al'ajibi na nufin kusan abu ɗaya kuma suna nanata mamakin mutanen ne. AT: "sun yi mamaki ƙwarai"
"gefen dakalin Sulaimanu." Wannan wata gefe ne da ke kunshe da layukan ginshiƙai da ke riƙe jinkan, toh shine mutane ke kira sa sunan sarki Sulaimanu.
"tsananin mamaki"
A nan kalmar nan "haka" na nufin mamakin mutanen.
"'yan'uwa ba Isra'ila" Bitrus yana wa taron magana.
Bitrus yana wannan tambayan ne domin ya nanata cewa bai kamata su yu mamakin abinda ya faru ba. AT: "kada ku yi mamaki"
Bulus yana wannan tambayan ne domin ya nanata cewa bai kamata mutanen su ga kamar shi da Yahaya ne sun warkas da mutumin da iyawan su ba. AT: "kada ku zuba mana idanu. Bamu muka sa shi ya yi tafiya da ikon kanmu ko adalcin mu ba.
Wannan na nufin cewa sun kalle su da duk niya ba iyaka. AT: "zuba mana ido" ko kuma "kalle mu"
AT: "ƙin shi a wurin Bilatus"
"da Bilatus ya so ya sake Yesu"
"cewa Bilatus ya sake muku mai kisan kai"
wato Yesu. Wannan na nufin 1 "mai ba wa mutane rai na har abada" ko 2) "mai mulkin rayuwa" ko 3) "mai ba da rai" ko 4) "wadda ke kai mutane ga samun rai"
AT: "wandan Allah ya sa ya rayu kuma"
Wannan kalmar "yanzu" na jan hankalin masu sauraro zuwa kan gurgun.
A nan "suna" na nufin Yesu. Wannan na iya nufin 1) "domin wannan mutumin ya gaskanta da Yesu" ko 2) "domin Yahaya da Ni mun gaskanta da Yesu"
"ya sa shi ya warke"
Wannan na nufin 1) cewa mutanen basu san cewa Yesu ne Almasihu ba ko 2) cewa basu fahimci muhimmancin abinda suka yi ba.
Idan manzanin sun yi magana, yana kamar Allah ne da kansa ke maganan domin shi ne yake faɗa musu abinda za su ce. AT: "Allah ya annabta ta wurin gaya wa annabawa abin da su faɗa"
"Allah ya faɗa tun da sauran loƙaci" ko kuma "Allah ya faɗa kafin su faru"
A nan kalmar "baki" na nufin maganganun da annabawa sun faɗa ko sun rubuto. AT: "maganganun dukan annabawa"
"ku kuma juyo." Anan "juyo" na nufin fara yi wa Ubangiji biyayya. AT: "sai ku fara biyayya da Ubangiji"
A nan "shafe" na nufin gafartawa. An yi maganar zunubi kamar an rubuta su a wani littafi ne da Allah ke gogewa daga littafin a lokacin da ya gafarta su. AT: saboda Allah ya gafarta maku zunuban da kuka yi mishi
"loƙacin taimako daga wurin Ubangiji." Wannan na nufin 1) "loƙacin da Allah zai karfafa ruhunku" ko 2) loƙacin da Allah zai farfaɗo da ku"
A nan kalamun nan "wurin Ubangiji" na nufin Ubangiji da kansa. AT" "daga Ubangiji"
"domin ya aiko maku da Almasihu kuma." Wannan na nufin zuwan Almsihu kuma"
AT: "wadda aka naɗa domin ku"
"shine wanda dole sama ta marabta." Bitrus yana maganar sama kamar wani mutum ne wanda ke marabtan Yesu zuwa gidansa.
Wannan na nufin cewa lallai ne Yesu ya cigaba da zama a sama domin abinda Allah ya shirya kenan.
Wannan na nufin 1) har zuwa loƙacin da Allah zai komo da dukan abubuwa 2) "har loƙacin da Allah zai cika komai da ya anabta."
Da annabawa suka yi magana, yana kamar Allah ne da kansa ke maganan domin shi ne yake faɗa musu abinda za su ce. AT: "game da abubuwan da Allah ya yi magana da ta wurin cewa annabawansa tsarkaka su yi magana game da su"
A nan kalmar "baki" na nufin maganganun da annabawa sun faɗa ko sun rubuto. AT: "maganganun dukan annabawansa tsarkaka"
"za sa ɗaya daga cikin 'yan'uwanku ya zama annabin gaskiya, kuma kowa zai san da shi"
"kasanku"
AT: "shi annabin, Allah zai hallakar da shi gaba ɗaya"
"A gaskiya, dukan annabawa." A nan kalmar "I" na nanata abinda ya biyo.
"tun daga Sama'ila aka cigaba har zuwa dukan annabawan da suka zo a bayansa"
"waɗannan sau" ko kuma "abubuwan da ke faruwa yanzu"
A nan kalmar "'ya'ya" na nufin magadan da za su karɓi abinda annabawa da kuma alkawari ta alkawarta. AT: Kune magadan annabawa da kuma magadan alkawari"
"saboda zuriyanka"
Al'umma na nufin taron mutane ko kasashe. AT: "Zan albarkaci dukan taron mutanen duniya"
"Bayan da Allah ya sa Yesu ya zama bawansa ya kuma sa shi ya zama sananne"
Wannan na nufin Almasihu, Yesu.
"juyawa ... daga" na nufin sa wani ya daina yin wani abu. AT: "sa kowane ɗayanku ya daina yin mugunta" ko kuma "sa kowane ɗayanku ya tuba daga muguntarsa"
1Yayin da Bitrus da Yahaya suna kan magana da mutanen, sai firistoci da shugaban masu tsaron Haikali da kuma Sadukiyawa suka afko masu. 2Sun damu sosai domin Bitrus da Yahaya suna koyar da mutane game da Yesu kuma suna shelar tashinsa daga matattu. 3Suka kama su suka jefa kurkuku sai washegari, domin yamma ta riga ta yi. 4Amma mutane da yawa da suka ji sakon suka ba da gaskiya; kimanin mazaje dubu biyar ne kuwa suka ba da gaskiya.5Washegari, da shugabaninsu, da dattawansu, da Marubuta suka taru a Urushalima. 6Anas babban firist, yana nan, da Kayafa, da Yahaya da Iskandari, da dukan dangin babban firist 7Da suka kawo Bitrus da Yahaya a tsakiyarsu sai suka tambaye su, "Da wanne iko, ko cikin wanne suna k ka yi haka?"8Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya ce, "Ku shugabanni da dattawan jama'a, 9idan mu yau ana tuhumarmu saboda aikin kirki da aka yi ga wannan mara lafiya - ta yaya wannan mutum ya sami lafiya? 10Bari ku da dukan mutanen Isra'ila, ku san wannan, cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, wanda kuka giciye, wanda Allah ya tayar daga matattu ta dalilinsa ne wannan mutumin yake tsaye a gaban ku lafiyayye.11Yesu Almasihu ne dutsen da ku magina kuka ki, amma an mai da shi kan gini. 12Babu ceto daga kowanne mutum, domin babu wani suna da aka bayar karkashin sama, a cikin mutane wanda ta wurinsa za a iya samu ceto."13Sa'adda, suka ga karfin halin Bitrus da Yahaya, suka gane mutane ne talakawa marasa ilimi, sai suka yi mamaki, suka kuma lura suka gane Bitrus da Yahaya sun kasance tare da Yesu. 14Da yake suna ganin mutumin nan da aka warkar tare da su, sai suka rasa abin yi.15Amma bayan sun fitar da manzannin daga majalisa sai suka tattauna a tsakaninsu. 16Suka ce, "Yaya za mu yi da wadannan mutane? Babu shakka aikin al'ajibi ya faru ta wurinsu, kuma sananne ne ga dukan mazauna Urushalima, kuma ba mu da iko mu musanci haka. 17Amma saboda kada ya cigaba da yaduwa cikin mutane, bari mu yi masu kashedi kada su kara magana da kowa cikin wannan suna." 18Suka kira Bitrus da Yahaya suka dokace su kada su kara magana ko kuma koyarwa ko kadan a cikin sunan Yesu.19Amma Bitrus da Yahaya suka amsa suka ce, "Ko ya yi daidai a gaban Allah mu yi maku biyayya fiye da shi, ku hukunta. 20Baza mu iya daina magana game da abubuwan da muka ji kuma muka gani ba."21Bayan sun sake yi wa Bitrus da yahaya kashedi, sai suka sake su, su tafi. Domin ba su iya samu wata hujja da za su hore su a kai ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru. 22Mutumin da ya sami wannan al'ajibi na warkarwa yana sama da shekara arba'in.23Bayan an sake su, Bitrus da Yahaya suka zo cikin mutanensu suka ba da rahoton duk abin da manyan firistoci da dattawa suka fada masu. 24Da suka ji haka, suka daga muryarsu tare ga Allah suka ce, "Ubangiji, kai da ka yi sama da duniya da teku da duk abin da ke cikinsu, 25kai wanda ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin ubanmu Dauda bawanka, ya ce, 'Me ya sa al'ummai suka tunzura, kuma mutane suke tunanin abubuwan banza?26Sarakunan duniya sun hada kansu tare, kuma shugabanninsu sun taru don su yi gaba da Ubangiji, da kuma Almasihunsa.'27Hakika, Hiridus da Buntus Bilatus, tare da al'ummai da mutanen Isra'ila, sun taru a wannan birni domin su yi jayayya da bawanka mai tsarki Yesu, shafaffe. 28Sun taru domin su aiwatar da dukan abin da hannunka da nufinka ya shirya zai faru.29Yanzu, Ya Ubangiji ka dubi kashedin su, ka ba bayin ka ikon furta maganar ka gabagadi. 30Sa'adda ka mika hannunka domin warkarwa, alamu da al'ajibai su faru ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu." 31Bayan sun gama addu'a, wurin da suka taru ya girgiza, suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka furta maganar Allah gabagadi.32Babban taron da suka ba da gaskiya kansu hade yake; kuma ba wanda ya ce da abinda ya mallaka nasa ne; maimakon haka, komai na su daya ne. 33Da iko mai karfi manzannin suka yi shelar shaidarsu game da tashin Yesu Ubangiji daga matattu, babban alheri kuma na bisansu.34Babu wani a cikinsu wanda ya rasa komai, domin masu filaye da gidaje suka sayar suka kawo kudin abin da suka sayar 35sai suka kawo kudin gaban manzanni. Aka rarraba wa kowanne mutum bisa ga bukatarsa.36Yusufu, Balawi, mutumin tsibirin Kubrus, wanda manzannisu ka yi wa lakani da suna Barnaba. (wato, mai karfafa zuciya). 37Yana da fili sai ya sayar da shi ya kawo kudin gaban manzanni.
Bayan da Bitrus da Yahaya sun warkas da mutumin nan da aka haife shi gurgu, Malaman addini sun kama su.
"kusance su" ko kuma "zo wurinsu"
"Sun yi fushi kwarai." Sadukiyawa, musamman, za su fi yin fushi game da abinda Bitrus da Yohanna ke faɗa domin basu gaskanta da tashin mattatu ba.
Bitrus da Yohanna suna cewa Allah zai tayar da mutane daga matattu kamar yadda ya riga ya tayar da Yesu daga cikin matattu. A fasara wannan yadda "tashin matattun" zai nuna cewa ana nufin tashinwar Yesu daga matattu ne da kuma tashiwar kowa ne gabaɗaya.
Daga dukan waɗanda sun riga su mutu. Wannan furcin na bayyana dukan mutane gaba ɗaya da ke cikin karkashin duniya. A dawo daga cikinsu na maganar zama da rai kuma.
"Firistocin, shugaban masu tsaron haikalin, da kuma Sadukiyawan sun kamo Bitrus da Yahaya"
Basu saba tuhurmar mutane da dare ba
Wannan na nufin mazaje kadai kenan, baya haɗe da kimanin mataye da 'ya'ya ba da suka ba da gaskiya ba.
"ta karu zuwa wajen dubu biyar"
A nan kalmar "nasu" na nufin mutanen Yahudawa gabaki ɗaya.
An yi amfani ne da wannan jimlar ne domin a nuna wurinda aka fara ɗauka matakin. Idan harshenku tana da wata hanyar yin haka, za ku iya duban yadda za ku yi amfani da shi anan.
Wannan na nufin majalisar, kotun Yahudawa, wadda ta kunshi waɗannan kungiyoyin mutane kashi ukun.
Waɗanan mazaje biyun 'yan iyalin babban firist ɗin ne. Wannan ba Yahaya manzo ba ne.
"Wa ya baku iko"
A nan kalmar nan "suna" na nufin iko. AT: da ikon wa"
Duba yadda kun juya wannan a [2:4]. AT: Ruhu Mai Tsarki ya cika Bitrus sa ya"
Bitrus yayi wannan tambayar ne domin ya nuna a fili cewa dalilin da ya sa fitinansu kenan. AT: "Kunan tambayan mu a yau ... ta yaya wannan mutumin ya sami lafiya"
"kuna tuhumarmu a yau"
AT: "ta yaya muka sa wannan mutum ya sami lafiya"
AT: Bari dukan ku da kuke mutanen Isra'ila ku san wannan
"ku da kuke tuhumar mu da kuma dukan sauran mutanen Isra'ila"
A nan kalmar "suna" na nufin iko. AT: ta wurin ikon Yesu Almasihu Banazere"
Wannan karin magana ce da ke sa wanda ya mutu ya zama da rai kuma. AT: "wadda Allah ya sa ya rayu kuma"
Bitrus ya ruwaito wannan daga Zabura ne. Wannan na nufin cewa shugabanen addini, kamar magina, sun ki Yesu, amma Allah zai mai da shi mafi amfani a cikin mulkinsa, kamar yadda dutsen kan gini na da amfani"
A nan kalmar "kan" na nufin "mafi amfani"
"ku da magina suka ki" ko kuma "ku a matsayin magina kuka ki shi ba a bakin kome ba"
Ana iya fasara sunan "ceto" anan zuwa kalmar aiki. Kuna iya faɗin wannan haka AT: "Shine kaɗai mutumin da ya iya ceto"
AT: "babu wani suna a karkashin sama da Allah ya bayar a cikin mutane"
Jimlar "suna ... bayar a cikin mutane" na nufin mutumin nan Yesu. AT: "babu wani mutum a karkashi sama, wanda aka ba shi a cikin mutane, ta wadda"
Wannan wata hanya ne da ke nufin ko ina a cikin duniya. AT: "a cikin duniya"
AT: "da za ta cecemu" ko kuma "wanda zai iya ceton mu"
A nan "karfin hali" na nufin yadda Bitrus da Yahaya suka amsa wa shugabanen Yahudawan. AT: "yadda Bitrus da Yahaya suka yi magana da karfin hali" ko kuma "karfin halin da Bitrus da Yahaya suke da shi"
ba wani tsoro
Shugabanen Yahudawan su "gane" saboda yadda Bitrus da Yahaya suka yi magana"
"kuma sun fahimci"
Kalman nan "talakawa" da kuma "marasa ilimi" na da ma'ana kusan ɗaya. Suna nanata cewa Bitrus da Yahaya basu samu wata ƙwararren horoswa cikin shari'ar Yahuwada ba.
AT: mutumin da Bitrus da Yahaya sun warkas"
"babu abin faɗi game da warkar da wannan mutumin da Bitrus da Yahaya suka yi." Anan kalmar "wannan" na nufin abinda Bitrus da Yahaya suka yi.
Wannan nufin Bitrus da Yahaya
Shugabanen Yahudawan sun yi wannan tambayan saboda basu iya tunanin abinda za su iya yi wa Bitrus da Yahaya. AT: Babu abin da za mu iya yi wa waɗannan mutanen"
AT: "Gama duk mazaunan Urushalima sun san cewa sun yi aikin al'ajibi"
ba lallai haka yake ba. Wannan na iya zamanto cewa an yi shi ne domin a nuna cewa shugabanen suna ganin cewa wannan babban damuwane. AT: "mutane da dame da ke zama a Urusahlima" ko kuma "mutanen da ke zama a ko'ina a Urushalima"
A nan kalmar "ya" na nufin kowani al'ajibi ko kuma koyarwar Bitrus da Yahaya za su iya cigaba da yi. AT: "saboda kada labarin wannan al'ajibin ya cigaba da yaduwa" ko kuma "saboda kada mutane su kara jin game da wannan al'ajibin"
A nan kalmar "suna" na nufin mutuminan Yesu. AT: "kar ko ku kara magana da kowa game da wannan mutumin, Yesu"
A nan jimlar "a gaban Allah" na nufin ra'ayin Allah. AT: Ko Allah na ganin hakan daidaine"
Shugabannin Yahudawan sun sake yin barazanan horas da Bitrus da Yohanna.
Ko dashike Shugabannin Yahudawan sun yi wa Bitrus da Yahaya barazana, ba su iya samun wata dalilin horas da su har ba tare da sa mutane su ta da hargitsi ba.
AT: "saboda abin da Bitrus da Yahaya suka yi"
"Mutum wadda Bitrus da Yahaya suka warkar ta al'ajibi"
Jimlar nan "mutanensu" na nufin sauran masubi. AT: "je wuring sauran masubi"
A daga murya karin maganane da ke nufin yin magana. "suka farin yin magana tare ga Allah" (Dubi: rc://*/ta/man/translate/figs-idiom)
Wannan na nufin ce Ruhu Mai Tsarki ya sa Dauda ya faɗi ko kuwa ya rubuta abin da Allah ya faɗa.
kalmar nan "baki" na nufin maganar da Dauda ya faɗi ko ya rubuto. AT: "ta wurin maganar bawanka, ubanmu Dauda
A nan "uba" na nufin "kakani"
Wannan tambayan ganganci ne da ke nanata azancin gãba da Allah. AT: "Kasashen Al'ummai baza su yi fushi ba, kuma mutanen baza su yi tunanin abubuwan banza ba"
Waɗannan "abubuwan banzan" na kunshe da shirin gãba Allah. AT: "mutanen suna tunanin abubuwan banza na gãba da Allah"
...
Waɗannan jimla biyun na nufin kusan abu ɗaya. Dukan su suna nanata cewa ƙoƙarin duk shugabannin duniya su yi hamaya da Allah.
Waɗannan jimla biyun na nufin sun haɗa rundunar soja domin faɗa da yaƙi
A nan kalmar nan "Ubangiji" na nufin Allah. A cikin Zabura, kalmar "Almasihu" na nufin shafaffe na Allah
"wannan birni" na nufin Urushalima
Yesu wadda ke bauta maka da aminci"
A nan an yi amfani da kalmar nan "hannu" mai nufin ikon Allah. Bugu da ƙari, jimlar nan "hannunka" da nufinka da ka shirya" na nuna ikon Allah da shirinsa. AT "aiwatar da duk abin da ka shirya domin kai mai iko ne kuma kã yi dukan abinda ka shirya"
A nan kalmar "dubi" roko ne ga Allah ya lura da yadda shugabannin Yahudawan na yi wa masubi barazana. AT: "lura da yadda suke barazana su hore mu"
Kalmar "magana" anan na nufin sakon Allah. AT: "furta maganarka da gabagaɗi" ko kuma "zama da gabagaɗi da muke furta sakonka"
A nan kalmar nan "hannu" na nufin ikon Allah. Wannan roƙo ne ga Allah ya nuna ikonsa. AT: A yayin da kake nuna ikon ka ta wurin warkas da mutane"
A nan kalmar nan "suna" na nufin iko. AT: ta wurin ikon bawanka mai tsarki Yesu"
...
Duba yadda kuka fasara wannan a
AT: "suna tunani ta hanya ɗaya kuma suna son abubuwa ɗaya"
"sun rarrraba mallakarsu da juna" Duba yadda kun fasara wannan a [2:44]
Wannan na iya nufin 1) cewa Allah yan sa wa masubin albarka sosai ko kuma 2) cewa mutanen da ke Urushalima su na ganin masubin da girma sosai.
AT: "Mutane da dama da ke da filaye ko gidaje" ko kuma "mutane masu filaye ko gidaje" Dubi:
...
AT: "kuɗaɗen da suka samu da abubuwan da sun sayar"
AT: "suka miko wa manzannin" ko "sun ba wa manzannin"
A nan iya fasara sunan nan "bukata" da kalmar aiki. AT: suka rarraba kudaden go kowane mai bi da ke bukatarsa"
Manzannin sun yi amfani da wannan suna ne domin su nuna cewa Yusufu mutum ne da ya karfafa sauran mutane. "Ɗan " karin magana ne da ke bayyana yanayi ko halin mutum. AT: "mai karfafawa" ko kuma "wanda ke karfafawa"
1Sai wani mai suna Hananiya da matarsa Safiratu, suka sayar da filinsu, 2Hananiya kuwa ya boye wasu daga cikin kudin filin, (kuma da sanin matarsa), sa'annan suka kawo ragowar kudin a gaban manzannin.3Amma Bitrus ya ce, "Hananiya don me shaidan ya cika zuciyarka, har ka yi wa Ruhu Mai Tsarki karya? Har ka boye wasu daga kudin filin? 4Sa'adda ba ka sayar da filin ba, ba mallakarka bane? Bayan da ka sayar ma, ba naka bane? Don me kayi irin wannan tunanin a zuciyarka? To ba mutane ka yi wa karya ba, Allah ka yi wa." 5Nan take da jin haka, Hananiya ya fadi ya ja numfashinsa na karshe. Dukan mutanen da suka ji labarin kuwa tsoro mai girma ya afko masu 6Matasa suka zo suka nannade gawarsa, suka fitar da shi waje suka binne shi.7Bayan wajen sa'a uku, sai matarsa ta iso, ba tare da sanin abin da ya faru ba. 8Sai Bitrus ya ce mata, "ki gaya mini ko nawa kuka sayar da filin?" Sai ta amsa, "ta ce kaza ne."9Sa'annan Bitrus ya ce mata, "Don me kuka shirya wannan makidar tare da mijinki don ku gwada Ruhun Ubangiji? Kiji tafiyar wadanda suka bizne mijinki a bakin kofa, kuma za su dauke ki yanzu." 10Nan take sai ta fadi a gabansa, ta ja numfashinta na karshe, matasan kuwa suka zo suka same ta ta mutu; sai suka dauki gawarta suka kai waje suka kuma bizne ta kusa da mijinta. 11Tsoro mai girma kuwa ya afko wa iklisiyar gaba daya da dakan wadanda suka ji wadan nan al'amura.12Ayyukan alamu da ban mamaki masu yawa kuwa sun faru ga mutane, ta hannun manzannin. Dukansu kuma suna nan tare a dakalin Sulaimanu, 13Sai dai babu mai karfin halin ya hada kai tare dasu; amma suna da kwarjini sosai a gaban jama'a.14Har wa yau aka rika samun karin masu ba da gaskiya, dinbin jama'a, maza da mata, 15har sukan dauki marasa lafiya su kai su bakin titi, suna kwantar da su a bisa gadaje da shinfidu, domin idan Bitrus ya zo wucewa ko da inuwarsa ma ta taba wasunsu. 16Mutane dayawa kuwa sukan zo daga garuruwan da ke kewaye da Urushalima, suna kuma kawo masu rashin lafiya, da wadanda aljannu ke damunsu, aka kuma warkar da su duka.17Amma babban firist ya taso tare da duk wadanda ke tare da shi (wato 'yan darikar Sadukiyawa); suka cika da kishi matuka 18suka kama manzannin suka kuma jefasu a kurkuku.19A cikin dare sai mala'ikan Ubangiji ya bude kofofin kurkukun ya kuma fito da su waje, ya ce, 20"Kuje ku tsaya a gaban haikali ku kuma gaya wa mutane maganar wannan rai." 21Sa'adda suka ji haka, sai suka tafi haikalin da wayewar gari suka yi koyarwa. Amma babban firist da jama'arsa suka zo suka kuma kira taro da kuma dukan yan majalisa, da dattawan jama'ar Isra'ilawa suka fito suka kuma ba da umarni, a fito masu da manzannin.22Amma ma'aikatan da suka je kurkukun basu sami kowa, a kurkukunba, sai suka dawo suka ba da rahoto, 23Su ka ce kurkukun a rufe gam da masu gadi suna nan a tsaye a bakin kofar amma da muka shiga, bamu sami kowa a ciki ba.24Yanzu sa'adda shugaban haikalin da manyan firistoci suka ji wadannan kalamai, sai suka rikice sosai game da su, suka ce yanzu me wannan zai haifar. 25Sai wani ya zo ya ce masu, "Wadannan mutanen da kuka jefa a kurkuku suna can a cikin haikali suna koyar da jama'a."26Sai shugaban haikalin ya je da ma'aikatansa suka kawosu, ba tare da tashin hankali ba, domin gudun kada jama'a su jejjefesu. 27Da suka kawo su, sai suka gabatar da su gaban majalisa, babban firist kuwa ya tuhume su, 28cewa "Ba mun yi maku kashedi da karfi kada ku yi koyarwa cikin wannan sunan ba? Amma ga shi duk kun cika Urushalima da koyarwarku, kuna kuma neman kusa jinin mutumin nan ya sauko kanmu."29Amma Bitrus da manzannin suka amsa suka ce, "Dole mu yi wa Allah biyayya ba mutane ba. 30Allah na ubanenmu ya ta da Yesu, wanda kuka kashe, ta wurin rateye shi a bisa itace, 31Allah kuwa ya daukaka shi a hannun damarsa, domin ya zama sarki da kuma mai ceto, ya ba Isra'ila tuba da gafarar zunubai. 32Mu kuwa shaidu ne ga wadannan al'amura, haka ma Ruhu Mai Tarki, wanda Allah ya bayar ga dukan wadanda suka yi biyayya a gareshi."33Da yan majalisa suka ji haka sai suka fusata kwarai da gaske, har suka nemi su kashe manzannin. 34Amma wani Bafarise mai suna Gamaliel, malami ne kuma na attaura wanda dukan jama'a suna martabawa, sai ya mike ya ba da umarni cewa a fid da manzannin waje na dan lokaci.35Sai ya ce masu "Ya ku mutanen Isra'ila, ku lura sosai da a binda kuke niyyar yi wa mutanen nan, 36A kwanakin baya wani ya zo mai suna Tudas ya dauki kansa wani abu, kimanin mutane dari hudu ne suka bishi, amma da aka kashe shi jama'arsa baki daya sai suka watse, ba wanda ya kara jin labarinsu. 37Bayansa kuma, aka yi wani mai suna Yahuza na Galili wanda a kwanakin kidaya, ya zo ya rinjayi mutane da yawa, shima ya lalace, duk wadanda suka bi shi kuwa suka watse.38Don haka ina gaya maku ku rabu da mutanen nan, domin idan shirinsu ko kuma ayyukansu na mutane ne za su lalace. 39Amnma idan abin nan daga Allah yake baza ku iya lalata su ba; kada ya zama kuna gaba da Allah." Sai suka rinjayu.40Da suka kira manzannin ciki suka yi masu duka, sai suka umarce su da cewa kada su sake koyarwa a cikin sunan Yesu, sai suka barsu suka tafi. 41Suka fita daga cikin majalisar, suna murna domin sun cancanta su sha wulakanci saboda sunan. 42Bayan haka kullayomin suna zuwa haikali, suna bi gida gida, suna wa'azi, suna kuma koyarwa ba fasawa cewa Yesu shine Almasihu.
Luka ya cigaba da labarin yadda sabobin masubi sun raba mallakarsu da sauran masubi. Sa'annan ya faɗi yanda masubi guda biyu, Hananiya da Safiratu.
An yi amfani da wannan kalman anan don a sa alamar yanke ainihin labarin a faɗi wata sabuwan bangaren labarin.
"matarsa ma na da sanin cewa ya ajiye sauran kuɗin"
Wannan na nufin sun ba wa manzannin kuɗin. AT: "ba da shi wa manzannin" ko kuma "ba wa manzannin"
Idan harshen ku ba ta amfani da tambayoyin ganganci, za ku iya canza waɗannan zuwa zance.
Bitrus ya yi amfani da wannan tambayan ne don ya sauta wa Hananiya. AT: "'da baka bar shaiɗan ya cika zuciyarka har ka yi karya ... gona."
A nan kalmar nan "zuciya"na nufin nufi ko shauƙi. Jimlar nan "Shaiɗan ya cika zuciyarka" karin magana ne da ke iya nufin 1) "Shaiɗan ya shawo kanna dabaɗaya" ko kuma 2) "shaiɗan ya rinjaye ka"
Wannan na nufin cewa Hananiya ya faɗa wa manzannin cewa ya bayar da dukan yawan kuɗin da ya karɓo ne daga sayar da gonarsa.
Bitrus na amfani ne da wannan tambayan don ya sautar wa Hananiya. AT: "Sa'adda ba ka sayar da filin ba, ai naka ne ..."
"Sa'adda baka sayar da shi ba"
Bitrus yana amfani da wannan tambayan ne don ya sautawwa Hananiya. AT: "bayan da ka sayarma, kana da mulki a kan kuɗin da ka karɓa"
AT: bayan da ka sayar da shi"
Bitrus yayi amfani ne da wannan tambayan ya sauta wa Hananiya. Anan kalmar nan "zuciya" na nufin nufi da shauƙi. AT: "Da ba ka yi tunanin yin haka ba"
A nan "ja nufashinsa na ƙarshe" wata hanyar ɗa'a ne na faɗin cewa ya mutu. Hananiya ya fãɗi ya mutu, ba wai ya mutu don ya fãɗi bane. AT: "mutu sai ya fãda kasa"
"Matar Hananiya ta shigo" ko kuma "Safiratu ta shigo"
"cewa mijinta ya mutu"
"ko nawa kuɗin." Wannan na nufin yawan kuɗin da Hananiya ya bawa manzannin.
Bitrus ya yi wannan tambayan ne don ya sauta wa Safiratu. AT: "Da ba ki yarda ba da mijinki ku gwada Ruhun Ubangiji tare!"
"kun yarda tare ku biyu"
A nan kalmar nan "gwada" na nufin a kalubale ko a jarrabta. Suna kokarin gani ko za su iya wa Allah ƙarya su tafi ba tare da samun hukuncinsa ba.
A nan kalmar na "tafiyar" na nufin mutanen. AT: "mutanen da suka bizne mijinki"
Wannan na nufin cewa da ta mutu, ta faɗi a kasa a gaban Bitrus. Kada a rikice wannan furci da faɗiwar mutum kasa mai nuna alamar kaskance.
A nan "ja nufashinta na ƙarshe" wata hanyar ɗa'a ne na faɗin cewa ta mutu. Duba yadda kun fasara irin wannan jimlar a [5:5]
ko "Ayyukan alamu da ban mamakisun faru a cikin mutanen ta hannun manzannin." AT: "Manzannin sun yi ayyukan alamu na ban mamaki a tsakanin mutanen"
"aukuwar allahntaka da ayyukan mu'ujizai." Duba yadda kun fasara wannan kalamun a [2:22].
Anan kalmar nan "hannun" na nufin manzannin. AT: ta wurin manzannin"
"gefen dakalin Sulaimanu." Wannan wata gefe ne da ke kunshe da layukan ginshiƙai da ke riƙe jinkan, wadda shine mutane ke kiran sa sunan sarki Sulaimanu. Duba yadda kuka fasara "dakalin da a ke ce da ita na Suleimanu" a [3:11]
AT: "mutanen sun ba wa masubin girma sosai"
Duba yadda kun fasara "aka sami" a [2:41]. AT: Karin masubi cikin Ubangiji"
Ana nufin cewa Allah zai warkar da su idan inuwar Bitrus ya taɓa su.
"waɗanda ruhuhi mara tsarki suka damesu"
AT: Allah ya warkar da su duka" ko kuma "manzannin sun warkar da su duka"
Wannan na fara wata labari ne da ya bambanta. Za a iya fasara wannan a wata hanyar da harshen daku ke gabatar da labarin da ya bambanta.
A nan kalmar nan "taso" na nufin cewa babban firist ya dauki mataki, ba wai ya tsaya daga wurin zamansa ba. AT: babban firist ɗin ya ɗauki mataki"
AT: "suka zama da kishi sosai"
Wannan na nufin cewa sun cafke su da ƙarfi. Da sun umurce masugadi su yi haka. AT: "sa masugadin su kãmã manzannin"
Basu je cikin ginin haikalin inda firistoci ne kaɗai ake bari su je ba. AT: "zuwa tsakar haikalin" ko kuma "zuwa yankin haikalin"
Kalmar nan "magana" na nufin sakon da manzannin sun riga sun shela. Wannan na iya nufin 1) "dukan sakon rai na har abada" ko kuma 2) " gabaɗayar sakon wannan sabuwar hanyar rayuwa"
"da wuri ya fara haske." Kodashike mala'ikan ya fito da su waje da dare, amma rana tana kan haurowa a loƙacin da manzannin suka kai tsakar haikalin.
Wannan na nuna cewa wani ya je kurkukun. AT "aike wannan zuwa kurkukun ya kawo manzanannin.
Kalmar nan "kowa" na nufin manzannin. Wannan na nuna cewa babu kowa a kurkukun in ba manzannin ba. AT: ba mu same su a ciki ba"
"sun yi mamaki sosai" ko kuma "sun ruɗe sosai"
"game da maganar da suka fito ji" ko kuma "game da waɗannan abubuwan"
"menene zai zama sakamakon wannan"
Basu je cikin ginin haikalin inda firistoci ne kaɗai ake bari su je ba. AT: suna koyarwa a zuwa tsakar haikalin"
...''sai suka ji tsoro''
A nan kalmar nan "suna" na nufin Yesu da kansa. Duba yadda kuka fasara wannan a [4:17]. AT: faɗa wa kowa game da mutumin nan, Yesu"
An yi maganar koyar wa mutane masu yawa a birnin kamar suna cika birnin ne da koyarwa. AT: "Kun koyar wa mutane da yawa a Urushalima game da shi" ko kuma "kun yi koyarwa game da shi a Urushalima gaba ɗaya"
A nan kalmar nan "jini" na nufin mutuwa, kuma a sa jinin wani a kan mutane na nufin cewa sune da laifin mutuwar mutumin. AT: "neman sa man alhakin mutuwar wannan mutum"
Bitrus ya yi magana a maɗadin manzannin da ya faɗi waɗannan kalaman"
A nan "ta da" karin magana ne. AT: "Allahn Ubannen mu ne ya sa Yesu ya sake rayuwa kuma"
Zama a "hannun damar Allah" alama ce na samun baban martaba da iko daga wurin Allah. AT: "Allah ya ɗaukaka shi zuwa wurin martaba a gefensa"
A nan "Bitrus" yana amfani ne da kalmar nan "bishaya" ya nuna giciyen da aka yi shi da katako. AT: "ta wurin rateye shi a bisa giciye
Ana iya fasara kalamun nan "tuba" da "gafara" zuwa kalmar aiki. AT: ya ba wa mutanen Isra'ila damar tuba su kuma samu sa Allah ya gafarta zunubansu"
Kalmar nan "Isra'ila" na nufin mutanen Yahudawa.
Waɗandan sun mika kanzu ga ikon Allah"
Luka ya gabatar da Gamaliel, sai ya bayar da tarihinsa.
AT: "wanda dukan mutanen ke martabawa"
AT: Umurce masugadin su fid da manzannin waje"
"yi tunani da kyau da" ko kuma "yi hankali da." Gamaliel yana masu gargaɗi ne kada su yi wani abinda za su yi baƙin cikinsa nan gaba.
Wannan na iya nufin 1) "Tudas yayi tawaye" ko kuma 2) "Tudas ya ɓullo"
"ɗauki kansu wani mai muhimmanci"
AT: "mutane suka kashe shi"
AT: "dukan mutanen da suke binsa suka watse" ko kuma "jama'ar da suke binsa suka kama hanyan su daban-daban"
Wannan na nufin cewa basu yi abinda suka shirya su yi ba.
"Bayan Tudas"
"loƙacin ƙiɗaya mutanen ƙasa"
Wannan na nufin ya rinjayi wasu mutane tare da shi kuma suka yi wan gwamnatin Roma tawaye. AT: sa mutane da yawa sun bi shi" ko kuma "sa mutane da yawa sun haɗa kai da shi a tawaye"
Gamaliel yana gaya wa shugananen Yahudawa cewa kada su kara hores da manzannin kuma ko su mayar da su kurkuku kuma .
"idan mutane ne sun kirkiro wannan shirin ko sun yi wannan aikin"
AT: wani zai lalace su"
A nan kalmar nan "abin" na nufin "shirin ko aikin." AT: "idan Allah ne ya kirkiro wannan shirin ko ya umurta waɗannan mutanen su yi wannan aikin"
AT: Sai Gamaliel ya rinjaye su"
Kungiyan majilisan na iya dokaci masu gadin haikalin su aikata waɗannan abubuwan.
A nan "suna" na nufin ikon Yesu. Duba yadda kun fasara inrin wannan jimlar a [4:18]. AT: "su kara koyarwa a cikin ikon Yesu"
Manzannin san yi murna domin Allah ya martaba su ta wurin barin shugabannen Yahudawan su wulakantasu. AT" "Allah ya lisaftasu cikin waɗanda sun cancanta su sha wulakanci saboda Sunan"
A nan "Sunan" na nufin Yesu. AT: "saboda Yesu"
Bayan wannan ranan, kowace rana." Wannan jimlar na nuna alamar abinda manzannin suka yi kowace rana har zuwa kwanakin da sun biyo baya.
Basu je cikin ginin haikalin inda firistoci ne kaɗai ake bari su je ba. AT: "a cikin haikalin da kuma cikin gidajen mutane daban-daban"
1A wadannan kwanaki, yawan almajiran ya ci gaba da ribanbanya, sai Yahudawan da suke zama a kasar Helanawa suka fara gunaguni game da Yahudawan Isra'ila, domin basu damu da gwamrayensu, wajen raba abinci da ake yi kullum.2Manzannin nan sha biyu suka kira taron almajiran suka ce masu, "Bai kamata mu bar maganar Allah mu shiga hidimar rabon abinci ba. 3Don haka ku zabi 'yan'uwa maza daga cikinku, mutane bakwai wadanda a ke ganin su da daraja, cike da Ruhu da kuma hikima, wadanda za mu zaba suyi wannan hidima. 4Mu kuwa mu ci gaba da da addu'a da kuma hidimar kalmar."5Maganar su kuwa ta farantawa dukan jama'a rai sosai. Sai suka zabi Istifanus, shi kuwa mutum ne cike da bangaskiya kuma da Ruhu Mai Tsarki da Filibus, da Birokoros, da Nikanar, da Timan, da Barminas, da kuma Nikolas, mutmin Antakiya wanda ya yi tuban Yahudanci. 6Masu bin kuwa suka gabatar da wadannan mutanen a gaban manzannin, su kuwa suka yi masu addu'a suka kuma dora hannuwansu a kansu.7Sai maganar Allah ta yawaita; yawan almajiran kuwa ya rubanbanya matuka a Urushalima; firistoci da yawa na Yahudawa suka bada gaskiya.8Sai Istifanus, cike da alheri da iko, ya rika yin ayyukan ban mamaki da alamu a cikin jama'a. 9Amma sai ga wadansu mutane daga wata majami'a da ake kira majami'ar Yantattu, wato su Kuramiyawa da Iskandariyawa, da kuma wasu daga kasar Kilikiya da Asiya. Wadannan mutanen kuwa suna muhawara da Istifanus.10Amma suka kasa yin tsayayya da Istifanus, saboda irin hikima da Ruhun da Istifanus ya ke magana da shi. 11Sai a asirce suka zuga wasu mutane su je su ce, "Ai munji Istifanus yana maganganun sabo game da Musa da kuma Allah."12Sai suka zuga mutanen, har da dattawa da marubuta suka tunkari Istifanus, suka kama shi, suka kawo shi gaban majalisa. 13Suka kawo masu shaidar karya suka ce, "Wannan mutumin har yanzu bai dena maganganun gaba akan wannan wuri mai tsarki da kuma shari'a ba. 14Domin kuwa mun ji shi, yana cewa wannan Yesu Banazarat zai rushe wannan wuri zai kuma canza al'adun da muka gada daga wurin Musa." 15Dukan wadanda suke zaune a majalisar suka zuba masa ido, sai suka ga fuskarsa kamar ta mala'ika.
Wannan shine forkon wata bangaren labarin. Luka yana ba da muhummin bayyanin tarihin da zai tamaka a fahimtar labarin.
Duba yadda ake gabatar da sabuwar bangaren labari a harshen ku.
"na karuwa kwarai da gaskiya"
Waɗannan su ne Yahudawa da sun yi rayuwarsu mafi yawa a wata yankin Roma waje da Isra'ila, kuma sun tashi suna yin Grika. Harshen su da al'adan su na da banbanci da wa na waɗanda suka tashi a Isra'ila.
Waɗannan sune Yahudawa da suka taso a Isra'ila suna yin Yahudanci. A wannan loƙacin Ikkilisiyar ta kunshi yahudawa ne da kuma tubabbu da addinin Yahudanci kawai.
matayen da mazajensu sun mutu
AT: "Yahudawa masubin ba su damu da gwamrayen Halenawan ba"
"kyale su" ko "manta da su." An manta da mutane da dama da da suke buƙatan taimako
Kuɗaden da ake ba wa manzannin wanda ake amfani da raguwansa a siya abinci wa gwamrayen ikkilisiya na farko.
Wannan na nufin a haɗe da Matiyas, wadda aka zaba a [1:26]
"dukan almajira" ko "dukan masubi"
An faɗi wannan ne domin a nanata muhimmancin hidimar su na koyar da maganar Allah. AT: "daina wa'azi da koyar da maganar Allah"
Wannan jimlar na nufin a raba wa mutanen abinci"
Wannan na iya nufin 1) mutanen na da halaye uku-- a ke ganin su da daraja, suna cike da Ruhu Mai Tsarki, kuma da hikima ko kuma 2) Mutanen suna da halaye biyu-- cike da Ruhu Mai Tsarki, da kuma cike da hikima.
"Mutanen da aka san su da kirki" ko kuma "mutanen da an yarda da su"
"ɗauki nawayan wannan aiki"
Zai zama da amfani sosai a yi karin bayani a kan wannan. AT: "hidimar koyar wa da wa'azin sakon"
"Dukan jama'ar sun so shawarwarinsu"
Waaɗnnan sunayen Grika ne, kuma suna ba da ra'ayin cewa dukan mutanen da aka zaba daga taron Yahudawa ne masu jin Halenanci ne.
Bahalane da ya tuba zuwa addinin Yahudawa
Wannan na nufin zuba albarku da kuma ɗaura nawaya da ikon aiki ga mutane bakwai din.
AT: "mutanen da sun gaskanta da maganar Allah sun ƙaru" ko kuma "kimamun mutanen da sun gaskata da sakon Allah sun ƙaru"
"ke bin wannan sabuwar koyaswa"
Wannan na iya nufin 1) sakon bisharar amincewa da Yesu ko kuma 2) koyaswar ikkilisiya ko kuma 3) koyaswar bi.
Wannan itace ce forƙon wata sabuwar bangaren labarin.
Wannan na gabatar da Istifanus a matsayin ainihin mai jan hankali a wannan labarin.
Kalamun nan "alheri" da "iko" anan na nufin ikon Allah. Anan iya kãrin bayani game da wannan. AT: Allah na ba wa Istifanus ikon yin"
"Yantattu" na nufin mutanen da ke bayi ne dama daga wurare daban-daban. Ba a san ko mutanen da aka jera suna cikin majami'ar ko kuma sun bi sun shiga muhawara da Istifanus ba ne.
"suna musu da Istifanus"
Wannan na nufin cewa ba za su iya ƙaryata abinda shi ya faɗa ba. AT: "ba za su iya musanta ba"
wannan na nufin Ruhu Mai Tsarki
An basu kuɗi su ba da shaidar ƙarya. AT: "wasu mutane so yi ƙarya su ce"
"abubuwan da ba kyau game"
"sa mutanen, da dattawan, da marubuta su yi fushi kwarai da Istifanus"
"cafke shi suka kuma riƙe shi yadda ba zai iya kubucewa ba"
"cigaba da magana"
Jimlar nan "gãɗa" na nufin "an miƙo" AT: "koyas da kakanninmu"
Wannan karin maganar na nufin sun kalle shi da kyau. Anan "ido" na nufin kallo. AT: "kalle shi da sosai" ko kuma "sun gan shi"
Wannan jimlar na nufin kwatanta fuskar sa da na mala'ika amma ba tare da ya faɗi abinda ya haɗa su ba.
1Sai babban firist ya ce, "Wadannan al'amura gaskiya ne?" 2Sai Istifanus ya amsa ya ce, "Ya 'yan'uwa da ubanni, ku saurare ni, Allah Madaukaki ya bayyana ga ubanmu Ibrahim tun yana can kasar Mesofotamiya, kafin ma ya zauna a kasar Haran; 3ya ce masa, 'Ka bar kasarka da danginka, ka tafi kasar da zan nuna maka.'4Sa'annan ya bar kasar Kaldiyawa ya zo ya zauna a Haran; daga can, bayan rasuwar mahaifinsa, sai Allah ya kira shi zuwa wannan kasa da kuke ciki. 5Amma Allah bai ba shi kasar gado ba tukuna, ko da misalin tafin sawunsa. Amma ya alkawarta - ko da yake bai riga ya haifi da ba tukuna - wanda zai ba shi kasar gado, shi da zuriyarsa, a bayansa.6Allah ya yi magana da shi kamar haka, cewa zuriyarsa za su yi bakonci a wata kasa wadda ba tasu ba, mutanen wannan kasar kuwa za su gwada masu bakar azaba su kuma bautar da su har shekaru dari hudu. 7'Kuma zan hukunta wannan al'umma da ta bautar da su,' Allah ya ce, 'Bayan haka za su fito daga wannan kasa su bauta mini a wannan wuri.' 8Allah ya ba Ibrahim alkawarin kaciya, sai Ibrahim ya haifi Ishaku ya yi masa kaciya a rana ta takwas; Ishaku ya haifi Yakubu, Yakubu kuma ya haifi ubanni Isra'ila su goma sha biyu.9Wadannan 'yan'uwa suka yi kyashin danuwansu Yusifu suka sayar da shi bauta zuwa Masar. Amma Allah na tare da shi. 10Ya kuwa cece shi daga dukan sharin da yan uwansa suka kulla masa, Allah kuwa ya ba shi tagomashi da hikima a gaban Fir'auna, sarkin Masar. Fir'auna kuwa ya mai da shi mai mulki a dukan kasar Masar da kuma dukan mallakarsa.11Sai aka yi babbar yunwa a dukan kasar Masar da ta Kan'ana, iyayenmu suka sha wuya saboda rashin abinci. 12Amma lokacin da Yakubu ya ji akwai hatsi a kasar Masar, sai ya aiki ubannimu a karo na farko. 13Da suka je a karo na biyu, sai Yusifu ya bayyana kansa ga yanuwansa; a wannan lokaci ne Fir'auna ya gane da yanuwan Yusufu.14Yusufu ya aiki yanuwansa su kawo Yakubu ubansu da dukan mallakarsu da iyalansu zuwa Masar, Dukansu mutane saba'in da biyar ne. 15Yakubu ya tafi ya zauna a Masar; shi da zuriyarsa har mutuwar su. 16Aka dauke su zuwa Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya da kudin azurfa daga hannun yayan Hamor a Shekem.17Yayin da alkawarin Allah ya kusato wanda Allah ya fada wa Ibrahim, mutanen suka karu suka hayayyafa kwarai a Masar, 18Sai a ka yi wani sarki a Masar wanda bai san Yusifu ba, 19Wannan sarki ya yaudari kakkaninmu ya yi masu mugunta kwarai da gaske, har ma ya kai ga suna barin jariransu cikin hasari don su ceci rayukansu.20A wannan lokaci ne aka haifi Musa, kuma kyakkyawan yaro ne sai aka yi renon sa tsawon wata uku a gidan mahaifinsa a asirce. 21Yayin da aka jefar da shi, sai diyar Fir'auna ta dauke shi ta rene shi kamar danta.22Aka ilimantar da Musa da dukan ilimi irin na Masar; kuma ya shahara cikin fasahar magana da kuma ayyukansa. 23Amma lokacin da yakai shekara arba'in, sai ya yi niyyar ya ziyarci 'yan'uwansa, Isra'ilawa. 24Sai ya ga wani na cin zalin Ba Isra'ile, Musa kuwa ya taimaki wanda ake kwara ta wurin murkushe Bamasaren: 25zaton Musa 'yan'uwansa za su fahimci taimakon Allah ne ya zo masu amma ina! Basu gane ba.26Washegari ya ga wasu Isra'ilawa na fada da junansu; ya yi kokari ya raba su; sai ya ce masu, 'Malamai, ku 'yan'uwan juna ne; don me kuke fada da junanku?' 27Amma shi wanda ake kwarar makwabcinsa ya ture Musa a gefe guda, ya ce, 'Wa ya nada ka shugaba ko alkali akanmu? 28Kana so ka kashe ni ne, kamar yadda ka kashe Bamasaren nan jiya?'29Da jin haka sai Musa ya gudu, zuwa kasar Midinawa, a matsayin dan gudun hijira. Anan ya haifi "ya'ya biyu maza. 30Bayan da shekaru arba'in suka wuce, sai mala'ika ya bayyana gare shi a jeji, kusa da dutsen Sinai, a cikin harshen wuta a cikin jeji.31Sa'adda Musa ya ga wutar, mamaki ya kama shi; sai ya maso kusa don ya kara dubawa, sai ya ji muryar Ubangiji na cewa, 32'Nine Allah na ubanninka, Ibrahim, da na Ishaku, da na Yakubu.' Musa ya razana har ma bai sake daga kai ya duba ba.33Ubangiji ya ce masa, 'Tube takalminka, domin in da kake tsaye wuri mai tsarki ne. 34Ba shakka na ga wahalar da mutane na ke sha a Masar, kuma na ji nishinsu, don haka na zo in cece su, yanzu fa sai ka zo, in aike ka zuwa Masar.'35Wannan fa shine Musan da suka ki, harma da cewa, 'Wanene ya nada ka alkali ko shugaba a kanmu?' Shine kuma wanda Allah ya aiko masu a matsayin shugaba da kuma mai ceto. Allah ya aiko shi ta hannun mala'ikan da ya gani a daji. 36Bayan alamu da al'ajibai iri-iri a Masar da kuma Baharmaliya, Musa ya fito da su daga Masar da kuma cikin jeji, a lokacin da suka yi tafiya shekara arbain. 37Wannan shine Musan da ya cewa Isra'ilawa, 'Ubangiji zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin Yan'uwan ku.'38Wannan shine mutumin da ke tare da mutane a jeji. Karkashin jagorancin mala'ikan da ya yi magana da shi a dutsen Sinai. Wannan ne mutumin da ke tare da ubannen mu, wannan shi ne mutumin da ya ba mu maganar Allah mai rai. 39Wannan shine mutumin da ubannenmu suka ki su yi masa biyayya; su ka fitar da shi daga cikinsu, suka kudurta a zuciyarsu za su koma masar. 40A lokacin ne suka cewa Haruna, 'ya yi masu allolin da za su jagorance su zuwa masar. Domin kuwa ga zancen Musan nan da ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba.'41Sai suka kera dan maraki suka kawo wa gunkin hadaya, suka yi murna da abin da hannayensu suka kera. 42Allah ya bashe su su bauta wa tauraran sama, kamar yadda yake a rubuce cikin littattafafan annabawa, 'Kun mika mani hadayu na yankakkun dabbobi a jeji ne a shekaru arba'in din nan ya ku Isra'ilawa?'43Kun yarda da haikalin Molek da kuma tauraron allahn nan Rafem, da kuma siffofin nan da kuka kera don ku yi masu sujada; don haka zan kai ku bauta har gaba da Babila.'44Kakkaninmu suna da alfarwa ta sujada domin shaida a cikin jeji, kamar yadda Allah ya umarta yayin da ya yi magana da Musa, cewa ya yi shi bisa ga salon da aka nuna mashi. 45Wannan shine Alfarwar da kakkaninmu suka zo da shi, a lokacin Joshuwa. Wannan ya faru ne yayin da suka mallaki wannan kasa ta al'ummai da Allah ya kora a gaban kakkaninmu. Haka abin yake har ya zuwa zamanin Dauda, 46wanda ya sami tagomashi a wurin Allah; don ya gina masujada domin Allah na Yakubu.47Amma Sulaimanu ne ya gina Gidan Allah. 48Sai dai Madaukaki ba yakan zauna a gidan da hannaye suka gina ba, kamar yadda annabin ya ce, 49'Sama kursiyina ce, duniya kuwa wurin ajjiye sawayena ne. To wane irin gida za ku gina mani? inji Ubangiji: ko kuwa ina ne wurin da zan huta? 50Ko ba hannayena ne suka yi dukan wadannan ba?'51Ku mutane masu taurin kai masu zuciya mara kaciya da kunnuwa marasa ji, kullum kuna gaba da Ruhu Mai Tsarki, kuna aikata abin da kakkaninku suka aikata. 52Wane annabi ne kakkaninku ba su tsanantawa ba? Sun kashe annabawan da suka rigayi zuwan Mai Adalcin nan, kuma kun zama wadanda suka kasance masu bashe shi da masu kashe shi, 53kune mutanen da kuka karbi shari'a wadda mala'iku suka bayar, amma ba ku kiyaye ta ba".54Yayin da majalisar suka ji wannan, sai ransu ya baci kwarai, har suna cizon hakoransu don gaba da Istifanus. 55Amma shi, cike da Ruhu Mai Tsarki, sai ya daga idonsa sama, ya ga daukakar Allah; ya kuma hango Yesu na tsaye a hannun daman Allah. 56Istifanus ya ce, "Duba, ina ganin sama ta bude, ga Dan Mutum na tsaye a hannun dama na Allah."57Amma yan majalisar suka daga murya da karfi, suka yi ihu, suka kuma toshe kunnuwansu, gaba dayansu suka afka masa; 58suka fitar da shi bayan gari, suka jejjefe shi da duwatsu, don shaida sai suka tube manyan rigunansu suka ajiye a gaban wani matashi da ake ce da shi Shawulu.59Lokacin da suke kan jifan Istifanus, ya dinga kira yana cewa, "Ya Ubangiji Yesu, ka karbi ruhu na." 60Ya durkusa ya daga murya da karfi, ya ce, "Ya Ubangiji, kada ka rike wannan zunubi a kansu." Yayin da ya fadi wannan, sai ya yi barci.
Bangaren labarin Istifanus da aka fara a [6:8] ya cigaba. Istifanus ya fara amsa wa babban firist da majalisar sa ta wurin magana game da abubuwan da suka faru a tarihin Isra'ila. Yawancin wannan tarihin ya fito ne daga rubuce-rubucen Musa.
Kalmar nan "na mu" ya haɗa da Istifanus, majalisar Yahudawa wadda yake wa magana, da kuma masu sauraro duka. Kalmar nan "ka" wa mutum ɗaya ne kuma yana nufin Ibarahim ne.
Istifanus matukar ba wa majalisar girma ne ta wurin gaishe su a matsayin 'yan'uwa gaba ɗaya.
"Bai ba da shi ba ko kaɗan"
Wannan na iya nufin 1) wurin da zai ishe shi tsayawa ko kuma 2) wurin da zai ishe shi ya taka. AT: "wata matuƙar kankanin filin"
"domin Ibrahim ya mallaka ya ba wa zuriyarsa"
Zai zama da taimako a ce wannan ya faru kamun wannan maganar a aya da ke baya. AT: "Daga baya Allah ya ce wa Ibrahim"
"shekaru 400"
"al'umma" na nufin mutanen da ke kasar. AT: "Zan hukunta mutanen kasar"
"wannan al'umma da za su wa bauta"
Yahaduwa za su fahimci cewa wannan alkawalin zai bukaci Ibrahim ya yi wa duk mazajen iyalinsa kaciya. AT: "Ya yi alkawali da Ibrahim ya yi wa 'ya'yan iyalinsa maza kaciya"
Labarin ya komo kan zuriyan Ibrahim.
Yakubu ya zama mahaifin." Istifanus ya takaita haka.
"manyan 'ya'yan Yakubu" ko kuma "yayun Yusufu"
Yahudawan sun san cewa kakanin su, sun sayar da Yusufu zuwa bauta a Masar. AT: "suka sayar da shi zuwa Masar a matsayin bawa"
Wannan wata karin magana ne da ke nufin taimakon mutum. AT: ya taimake shi"
Wannan na nufin dukan mutanen kasar Masar. AT: "dukan mutanen kasar Masar"
Wannan na nufin dukiyansa. AT: "komai da yake da shi"
"ƙarancin abinci ta zo." Kasa ta daina ba da abinci.
Wannan na nufin Yakubu da 'ya'yansa, kakkanin mutanen Yahudawa duka.
Hatsi ne abincin kowa a wancan loƙacin.
Duka jimla biyun na nufin 'ya'uwansa Yusufu manya.
"da suka ƙara tafiya kuma"
Yusufu ya bayyana kansa ga 'yan'uwansa a matsayin ɗan'uwansu.
AT: "ya sani da cewa su 'yan iyalin Yusufu ne"
"ya aiki 'yan'uwansa su koma kan'ana" ko kuma "ya aiko su gida"
...
"Yakubu da 'yan'uwansa da suka zama kakkaninmu a yau"
AT: "Zuriyar Yakubu sun ɗauko jikin Yakubu da na 'ya'yansa zuwa ... suka binne sa"
"da kuɗi"
A wasu harsuna, yana iya zama da amfani a ce mutanen sun karu a yauwa kamar ace alkawarin ya zo.
Loƙacin da Allah zai cika alkawalin sa wa Allah ya yi kusa.
"wani saiki ya fara mulki"
"Yufufu" na nufin halin Yusufu. AT: "wanda ba san yadda Yusufu ya taimake Masar ba"
Haka ne labarin Musa ya shigo cikin wannan labarin.
Wannan karin magana ne da ke nuna cewa Musa kyakkyawa ne sasai.
AT: "iyayensa suka yi renon sa" ko kuma "iyayensa sun kula da shi"
An jefar da Musa saboda umarnin da Fir'auna ya bayar. AT: "Yayin da iyayensa suka jefar" ko kuma "Da iyayensa suka yar da shi"
Ta mashi dukan abinda uwa na kwarai ke iya yi wa ɗan cikinta. Yi amfani da ainihin kalmar harshen ku da kuke mora ku bayyana abinda uwa ke yi domin ta tabbatar cewa ɗan ta ya yi girma da ƙyau sosai.
AT: "Masarawan suka ilimintar da Musa"
An kara nanata wannan ne don a nuna cewa musa ya horu a makarantu mafi kyau da ke Masar.
"inganci cikin magana da ayyukansa" ko kuma "ya zama da rinjayaa cikin abinda yake faɗi da aikatawa"
Wannan jimlar "ya yi niyyar" na nufin ya kudura a zuciyar sa. AT: "ya zo tunaninsa"
Wannan na nufin mutanensa, ba ma iyalin kawai ba. AT: "ya ga yadda mutanensa, 'ya'yan Isra'ila suke"
AT: Da ya ga Bamasaran na cin mutuncin Ba Isra'ile, Musa ya taimaki Ba Isra'ile ta wurin murkushe Bamasaran da ke sananta wa"
Musa ya bugi Bamasaran da ƙarfi har ya kashe shi.
"ya yi tunanin"
AT: "na taimakon su ta wurin abinda Musa ya yi" ko kuma "na amfani da abinda musa ke yi ya yantad da su"
Yakamata masu sauraron sun sani daga tarihin da ke Fitowa cewa mutane biyu ne amma Istifanus bai saka shi haka ba.
"sa su daina faɗa"
Musa ya magana ne da Isra'ilawan da ke faɗa.
Musa ya yi wannan tambayan ne don ya ƙarfafa su su daina faɗa. AT: "ku daina faɗa da juna!"
Mutumin ya yi amfani ne da wannan tambayan ya tsauta wa Musa. AT: "ba ka da iko a kan mu!"
Mutumin ya yi amfani ne da wannan tambayan ya yi wa Musa ƙashedin cewa shi maiyuwa da wasu sun san cewa Musa ya ƙashe wani Bamasaren.
Wannan na ba da tabbacin cewa Musa ya fahimci cewa Isra'ilawan sun sa da cewa ya ƙashe wani Bamasaren kwana ɗaya kamun [7:28]
"Bayan da shekaru arbain suka wuce." Wannan shi ne yawan kwanakin da Musa ya yi a Midina. AT: "shekaru arbain bayan da Musa ya gudu daga Masar"
Masu sauraron Istifannus sun san da cewa Allah ya yi magana ta wurin mala'ika.
Musa ya sha mamakin cewa jejin ba ta kone wa da wuta, Dama masu sauraron Istifanus sun san da wannan. AT: "domin jejin ba ta kone wa ba"
Wannan na nufin cewa dama musa ya maso kusa ne ya bincika, amma sai ya komo baya don tsoron da ya ji muryar.
"Nine Allahn da kakkaninku sauka yi wa sujada"
Musa ya firgita don tsoro. AT: "Musa ya razana da tsoro"
Allah ya gaya wa Musa wannan ne don ya girmama Allah"
Wannan na nuna wurin da Allah yake kasancewa, Ana ɗaukan dai dai yankin da Allah yake yã zama ko kuma yã zama da tsarki.
"na ga da tabbaci." Ba shakka na kara nanata ganin.
Kalmar nan "na" na nanata cewa waɗannan mutanen sun zama na Allah. AT: "zuriyar Ibrahim, Ishaku, da Yakubu"
"da kaina zan yantad da su"
"ka shirya." Allah ya ba da umurni ne anan.
Wannan na mayar da mu zuwa ga abubuwan da suka aiku da aka rubuta a [7:27-28]
Sun yi amfani ne da wannan tambayan su tsauta wa Musa. Duba yadda kuka fasara wannan tambayan gangancin a [7:27]. AT: "Ba ka da iko a kan mu!"
...
Hannun na nufin abinda mutum ya yi. A wannan zancen, Mala'ikan ya umuci Musa ya koma kasar Masar. Istififanus na magana kamar mala'ikan na da hannu ne da za a iya gani. Kuna iya buƙaci ko kara bayyana abinda mala'ikan ya yi. AT: "ta wurin abinda mala'ikan ya yi" ko kuma "ta wurin samun mala'ikan ... daji umurce shi ya koma Masar"
Masu sauraron Istifanus sun san game da shekaru arbain da Isra'ilawa suka yi a cikin jeji. AT: loƙacin ... shekara arbain da mutanen Isra'ila suka rayu a cikin jeji"
"sa wani ia zama annabi"
"daga cikin mutanenku"
Musa ne wannan mutumin da ke tare da Isra'ilawa"
Jimlar nan "wannan shine mutumin" a wannan nassin na nufin Musa.
Allah ne ya bayar da maganan. AT: "wannan shi ne mutumin da Allah ya bashi maganar rai ya ba mu"
Wannan na iya nufin 1) "sakon da ke jurewa" ko kuma 2) "maganar da ke ba da rai"
Wannan na nufin kiyayyan da suka yi wa Musa. AT: "suka ki shi a matsayin shugaban su"
Anan "zuciya" na nufin tunanin mutane. Ayi abu a zuciya na nufin a yi marmarin aikata abin.AT: "suka yi marmari su koma"
"Da suka yi marmari su koma Masar"
Masu sauraron Istifanus sun san cewa ɗan marakin da suka ƙera gunki ne. AT: "suka ƙera wata gunki a sifar ɗan maraki"
Waɗannan su jimlar na wannan gunkin ɗan marafin ne.
"Allah ya juya musu baya." Wannan matakin na nuna cewa Allah bai ji daɗin mutanen ba kuma bai cigaba da taimakon su ba. AT: "Allah ya daina gyara su"
"ya yi watsi da su"
Daga ainihin jimlar, wannan na iya nufin 1) tauraran kawai ko kuma 2) rana, wata, da tauraro
Wannan ba shakka na nufin tarin rubuce-rubuce da dama na annabawan Tsohon Alkawali da aka haɗa a gungura ɗaya. Wannan na iya ma haɗe da rubuce-rubucen Amo.
Allah ya yi wannan tambayan ne don ya nuna masu cewa basu yi masa sujada ta wurin haɗayun su ba. AT: "ba ku ko daraja ni ba sa'an da kuke miko yankakkun dabbobi da haɗayu ... Isra'ilawa"
Wannan na nufin kasar Isra'ila gabaki ɗaya. AT: "dukanku Isra'ilawa"
Wannan na nufin cewa sun ɗauki gumakai da suna tafiya a cikin jeji. AT: "kun ɗauke su da ku zuwa wurare"
gidan bukkan da wani allah mai suna molek ke zama
tauraron da an fi gane ta da wani allah mai suna Rafem
Sun ƙera gumakai da sifofi alloli Molek da Rafem don su yi masu sujada.
"zan cire ku zuwa wurare har ma gaba da Babila." Wannan zai zama shari'ar Allah.
Wata bukka da sanduki (akwati) ke zama a ciki tare da dokoki goma (10) da aka ƙera a kan dutse a cikin ta.
jimlar nan "a loƙacin Joshuwa" na nufin cewa kakkaninsu sun yi waɗannan abubuwan bisa ga bishewar Joshuwa. AT: "kakkaninmu, bisa ga umarni daga Joshua sun karbi wannan alfarwa suka zo da shi"
Wannan jimlan na nuna dalilin da ya sa kakanin su iya kwace kasar ya zama na su. AT: "Allah ya tilasta al'umman su bar kasar a gaban kakkaninmu"
Wannan na iya nufin 1) "Yayin da kakkaninmu na kallo, Allah ya kwaci kasar daga al'ummai ya kuma kore su" 2) "Da kakkanin mu suka zo, sai Allah ya kwaci kasar daga al'ummai ya kuma kore su"
Wannan na nufin mutanen da ke zama a kasan kamun Isra'ila. AT" "mutanen da ke zaune dã a wurin"
"ya tilasata su su bar kasar"
"gidan domin sanduki wurin da Allahn Yakubu zai iya zama" Dauda ya buƙaci wurin zama na dindindim domin sandukin ya zauna a Urushalima, ba a buƙa ba.
Hannaye na nufin mutane. AT: "da mutane suka gina"
Shi annabin yana kwatanta girman darajar kasancewar Allah ne da yadda ba shi yiwuwa mutum ya gina wa Allah wurin da zai huta a duniya tun da shike duniyan gaba ɗaya wurin ajiye sawun sa ne kawai.
Allah ya yi wannan tambayan ne domin ya nuna cewa aikin banza ne kokarin mutum ya kula da Allah. AT: "Ba za ku iya gina mani gida daidai yadda zai ishe ni ba!"
Allah ya yi wannan tambayan ne don ya nuna cewa mutum ba zai iya tanada wa Allah wurin hutu ba. AT: "Babu wani wurin hutu da ya mani kyau!"
Allah ya yi wannan tambayan ne don ya nuna cewa mutum bai halice kome ba. AT: "Hannayena ne suka yi dukan kome!"
Istifanus ya daina haɗa kai da malamen Yahudawan ya koma sauta musu.
Wannan baya nufin cewa kawunansu na da tauri ba, amma yana nufin cewa su "basu ji."
Yahudawa na ɗaukan marasa kaciya a matsayin marasa yi wa Allah biyayya. Istifanus yana amfani ne da marasa kaciya da kunnuwa marasa ji" a maɗɗaɗin malaman Yahudawa da suke yi kamar al'ummai suke yi loƙacin da basu biyayya da Allah. AT: "kun ki ku yi biyayya ku kuma ji"
Wannan na nufin Almasihu, shafeffen.
Istifanus yana wannan tambayan ne don ya nuna musu cewa basu koya kome daga kuskuren kakkaninsu ba. AT: "Kakkaninsu sun tsanantawa kowane annabi!"
"ku ma kun bashe shi kun kuma kashe shi"
"masu ƙashe Mai Adalcin" ko kuma "masu ƙashe Almasihu"
"shari'un da Allah ya sa mala'iku su bawa kakkaninku
Labarin ya juya anan; hadisin ya zo ga ƙarshe anan, sai majalisar suka ɗauki mataki.
"ransu ya baci" na nufin suka yi fushi kwarai da gaskiya. AT: "sai suka yi fushi kwarai da gaskiya" ko kuma "sa suka yi fushi sosai"
Wannan matakin na nuna matukar bakin cikinsu da Istifanus ko kuma matukar kiyayyar su da Istifanus. AT: "suka yi fushi ƙwarai da gaskiya har ya kai su ga cizon hakora" ko kuma "suka motsa hakoransu yayin da suke kallon Istifanus"
"ya zuba idon sa sama." Yana yi kamar Istifanus ne kaɗai ya ga wannan wahayin banda suran jama'ar da ke taron.
Mutane sukan ga ɗaukakar Allah a matsayin hasken wuta. AT: "ya ga wata hasken wutar Allah"
A tsaya a "hannun damar Allah" alama ce na samun daukaka da ikon Allah. AT: "sai ya hango Yesu a wurin ɗaukaka da iko a gefen Allah" Dubi:
Istifanus na nufin Yesu kenan.
"suka sa hannayensu bisa kunuwansu." Sun yi haka ne domin su nuna cewa basu so su ji abin da Istifanus yake faɗi.
"suka kãmo shi suka jawo shi da ƙarfi bayan gari"
Waɗannan manyan tufafi ne da ake sako wa domin tare sanyi. Suna kamar su suweita ne ko kwot.
Sun ajiye su a wurin domin Shawulu ya rika duba su.
Shawulu yana irinsu shekaru 30 ne a lokacin.
"ga ruhu na." Zai zama da taimako idan aka nuna cewa wannan roƙo ne. AT: "ina roƙo, ka karbi ruhu na"
Wannan alamar biyayya ne ga Allah
Ana iya sanar da wannan a tabbacecciyar sifa. AT: "ka gafarta masu wannan zunubin"
Yin barci anan na nufin mutuwa. AT: "mutu"
1Bulus ya amince da mutuwarsa. A wannan rana tsanani mai zafi ya fara tasowa akan Iklisiya da take a Urushalima, sai masu bangaskiya duka suka bazu ko ina a cikin garuruwan Yahudiya da Samariya, sai manzannin kadai aka bari. 2Amintattun mutane suka bizne Istifanus suka yi babban makoki game da shi. 3Amma Shawulu ya yi wa Iklisiya mugunta kwarai, ya dinga shiga gida gida yana jawo mutane maza da mata, kuma yana kulle su cikin kurkuku.4Duk da haka masu bangaskiyar nan da suka warwatsu suka tafi suka dinga yada wa'azin maganar. 5Filibus ya tafi can Samariya ya yi shelar Almasihu.6Da taron mutane suka ji kuma suka ga alamun da Filibus yake yi, sai suka mai da hankali dukansu domin su ji abinda yake fadi. 7Domin kazaman ruhohi sun fito daga cikin mutane da yawa da suka saurare shi suna kuka da kururuwa; nakasassun mutane dayawa da guragu suka warke. 8Kuma aka yi farin ciki mai girma a birnin.9Amma akwai wani mutum a cikin birnin da ake kira Siman, wanda tun farko shi masafi ne da kuma dan dabo, yana yi wa mutanen Samariya abubuwan ban mamaki, yayin da yake kiran kansa wani mai muhimmanci. 10Dukan Samariyawa, manya da yara, suna sauraronsa, su kan ce, "Wannan mutum shine ikon Allahn nan wanda ake kira mai girma." 11Suna sauraron sa, domin ya dade yana yi masu abubuwan mamaki da tsafe-tsafensa.12Amma da suka yi bangaskiya da wa'azin bisharar da Filibus yake yi game da mulkin Allah da sunan Yesu Almasihu, sai aka yi masu Baftisma dukansu maza da mata. 13Har shima Siman da kansa ya ba da gaskiya. Bayan an yi masa Baftisma ya cigaba da bin Filibus, da ya ga ana nuna alamu da manyan ayyuka, sai ya yi mamaki.14Da manzannin da ke Urushalima suka ji labarin Samariya ta karbi maganar Allah, sai suka aika masu Bitrus da Yahaya. 15Da suka iso, suka yi masu addu'a, domin su karbi Ruhu Mai Tsarki. 16Domin har wannan lokaci, Ruhu Mai Tsarki bai sauko kan kowannensu ba; an dai yi masu baftisma ne kadai cikin sunan Ubangiji Yesu. 17Sai Bitrus da Yahaya suka dora masu hannuwansu, sai suka karbi Ruhu Mai Tsarki.18Sa'adda Siman yaga ana bayar da Ruhu Mai Tsarki ta wurin dorawar hannuwan manzanni, ya basu kudi. 19Ya ce, "Ku bani wannan iko, ni ma, don duk wanda na dora wa hannu ya karbi Ruhu Mai Tsarki."20Amma Bitrus yace masa, "Azurfarka ta lalace tare da kai, saboda kana tunanin za ka malaki baiwar Ubangiji da kudi. 21Baka da wani rabo a wannan al'amari, domin zuciyarka ba daidai take da Allah ba. 22Saboda haka ka tuba daga wannan muguntarka, ka kuma yi addu'a ga Ubangiji, domin mai yiwuwa ya gafarta maka game da manufar zuciyarka. 23Domin na gane kana cikin bacin rai da kuma cikin daurin zunubi."24Siman ya amsa ya ce, "Kayi addu'a ga Ubangiji domina, kada wani daga cikin abubuwan nan da ka fada ya faru da ni."25Sa'anda Bitrus da Yahaya suka bada shaida kuma suka fadi maganar Ubangiji, sun koma Urushalima; akan hanya, suka yi wa'azin bishara a kauyukan samariyawa da yawa.26Yanzu kuwa Mala'ikan Ubangiji ya yi wa Filibus magana cewa, "Tashi ka tafi ta kudu da hanyar da ta yi kasa daga Urushalima zuwa Gaza" (wannan hanyar yana cikin hamada.) 27Ya kuwa tashi ya tafi. Sai ga wani mutum daga Habasha, baba ne mai babban matsayi a karkashin Kandakatu, sarauniyar Habasha. Shine yake mulkin dukan dukiyarta. Ya zo Urushalima domin ya yi ibada. 28Yana komawa zaune cikin karussarsa, kuma yana karanta Littafin annabi Ishaya.29Ruhun ya ce wa Filibus, "Ka je kusa da karussar nan." 30Sai Filibus ya gudu ya same shi, kuma ya ji shi yana karanta littafin annabi Ishaya, sai ya ce, "Ka fahimci abin da kake karantawa?" 31Bahabashen ya ce. "Yaya zan iya, idan ba wani ya bishe ni ba?" Ya roki Filibus ya shigo cikin karussar ya zauna tare da shi.32Wannan kuwa shine nassin da Bahabashen yake karantawa, "An kai shi kamar tunkiya zuwa mayanka; shiru kuma, kamar dan rago a hannun masu sosayarsa, bai bude baki ba. 33Cikin kaskancinsa aka yi masa shari'a da rashin adalci: Wa zai bada tarihin tsararsa? Domin an dauke ransa daga duniya."34Sai baban ya tambayi Filibus, ya ce, "Na roke ka, gaya mani, game da wa annabin yake magana? Da kansa, ko kuwa wani mutum dabam?" 35Filibus ya fara magana; akan littafin Ishaya, ya kuwa yi masa wa'azi akan Yesu.36Yayin da suke tafiya akan hanya, sai suka iso bakin wani kogi; Baban ya ce, "Duba, ga ruwa anan; me zai hana ayi mani baftisma?" 37Filibus ya ce," Idan ka gaskanta da zuciya daya, ana iya yi maka baftisma." Sai Bahabashen ya ce, "Na gaskata Yesu Almasihu shine Dan Allah." 38Sai Bahabashen ya umarta a tsai da karussar. Sai suka zo wurin ruwa dukan su biyu, Filibus da baban, Filibus kuwa yayi masa baftisma.39Yayin da suka fito daga cikin ruwan, Ruhun Ubangiji ya dauke Filibus; baban bai sake ganin shi ba, sai ya ci gaba da tafiyar sa yana murna. 40Amma Filibus ya bayyana a Azotus. Ya ratsa wannan yankin yana wa'azin bishara a dukan garuruwan, har sa'anda ya iso Kaisariya.
Labarin ya maso daga kan Istifanus zawa Bulus a waɗannan ayoyi.
Yana iya zama da taimako wa masu sauraro a masar da bangaren labarin Istifanus gaba ɗaya kamar yadda UDB ta yi
Wannan bangaren aya 1 na ba da bayyanin tsanantawa da ya taso bayan rasuwan Istifanus. Wannan ya bayyana dalilin da ya sa Bulus yana tsananta wa masu bi a aya 3.
Wannan na nufin ranar da Istifanus ya rasu. (Dubi: [7:59-60]
Kalmar na "duka" na nufin cewa masubi da yawa suka bar Urushalima saboda tsanantawa.
Wannan na nufin cewa manzannin ne suka rege a Urusalima ko da yake su ma sun ɗandana matukar tsanantawa.
"Mutane masu tsoron Allah" ko kuma "Mutanen da ke da tsoron Allah"
suka yi babban makokin mutuwarsa"
Bulus ya ɗauki masubi Yahudawa da ƙarfi daga gidajen su ya jefa su a kurkuku.
"gidaje ɗaya bayan ɗaya"
Wannan na nufin maza da mata da suka gaskata da Yesu.
Dalilin warwatsuwan nan fa tsanantawa ne kamar yadda aka ambata a baya. AT: "wadda suka gudu wa babban tsanantawar, suka kuma tafi"
"maganar" anan na nufin "sakon." AT: suka dinga wa'azin sakon Allah"
...Wannan karin magana ''tafi can'' an yi amfani da shi anan don samariya na kasa da isra'ila.
Wannan na iya nufin 1) Luka ya sammanin cewa masu karatunsa za su san birnin da yake rubutu a kai. AT: "babbar garin birnin Samariya" ko kuma 2) Luka bai zaci masu karatunsa su san wace gari ne yake rubutu a kai ba. AT: "wata birni a Samariya"
Laƙabin nan "Almasihu" na nufin Yesu. AT: "faɗi musu cewa Yesu shi ne Almasihu"
"Da mutane masu yawa a birnin Samariya." An kayyade wurin a baya. (Dubi: [8:5]
Sun mai da hankalinsu ne saboda dukan warkaswan da Filibus yayi.
"waɗanda ke da su" ko kuma "waɗanda kazaman ruhohi ke mulki da su"
Jimlar nan "wannan birnin" na nufin mutanen da ke murna. AT: "Kuma mutanen birnin suna murna"
Haka ake gabatar da sabun mutum zuwa cikin labarin. Harshen ku na iya moran wasu kalamu daban don gabatar da sabuwar mutum zuwa cikin labarin.
"birnin Samariya" (Dubi: [8:5])
Kalmar nan "duka" na nufin masu yawa. AT: "Samariyawa ma su yawa" ko kuma "Samariyawan da ke birnin"
Waɗannan jimla da nufin mutane daga kowane bangare. AT: "komen muhimmancinsu"
Mutane suna cewa Siman ne wannan ikon Allahn da ake ce da shi "Iko Mai girma."
Wannan na iya nufin 1) Wakilin Allah mai iko ko kuma 2) Allah ko kuma 3) mutum mafi iko 4) malaika. Da shike ba bayyana kamar a fili ba, ya fi a fasara ta da "ikon Allah mai girma"
AT: "Filibus ya masu baftisma" ko kuma "Filibus ya yi wa sabobbin tuban baftisma"
An yi amfani ne da wannan kalmar "da kansa" don a nanata cewa Siman ya ba da gaskiya. AT: "Siman ma yana cikin waɗanda suka ba da gaskiya"
AT: "Filibus ya yi wa Siman baftisma"
Ana iya faɗin wannan a wata sabuwan jimla. AT: "Da ya ga"
Wannan na fara wata sabuwan bangaren labarin yadda Samariyawa suka fara zama masubi.
Wannan na nufin mutane masu yawa, da sun zama masubi a yankin Samariya.
"suka ba da gaskiya" ko kuma "suka yarda"
"da Bitrus da Yahaya suka isa"
...
"Bitrus da Yahaya suka yi wa masubi Samariyawa addu'a"
"domin masubi Samariyawa su karɓi Ruhu Mai Tsarki"
AT: Filibus ya dai yi wa Masubi Samariyawa baftisma ne kadai"
A nan "suna" na nufin iko, kuma yin baftisma a cikin sunan nan na a madaddin baftisma domin kasancewa a karkashin ikonsa. AT: "an dai yi masu baftisma ne kadai domin su zama almajiran Yesu"
"su" anan na nufin mutanen Samariya da suka gaskata da sakon bisharan da Istifanus ya yi.
Wannan alama ce da ke nuna cewa Bitrus da Yahaya suna so Allah ya ba wa masubi Ruhu Mai Tsarki.
AT: "manzannin suka ba su Ruhu Mai Tsarkin ta wurin dorawar hannuwan manzanni"
"don in ba da Ruhu Mai Tsarki ga duk wanda na dora wa hannu"
"bari kai da kuɗinka ku hallaka"
Wannan na nufin iya ba da Ruhu Mai Tsarki ta wurin ɗora hannaye a kan mutane.
AT: "ba za ka iya haɗa hannu a wannan aikin ba"
A nan "zuciya" na nufin tunani ko manufofin. AT: "manufofinka ba daidai suke ba"
A nan "zuciya" na nufin tunanin mutum. AT: "domin abinda ka yi niyar yi" ko kuma "domin abinda kake tunanin yi"
"waɗannan mugayen tunani"
"ma yiwuwa yana shirye ya gafarta"
A nan "cikin bacin rai" na nufin matukar kishi. AT: "matukar kishi"
Ana maganar "ɗurin zunubi" kamar zunubi na iya hana Siman ya kuma ɗaure shi. Yana nufin cewa Siman ba zai iya daina yin zunubi da kansa ba. AT: "domin kã cigaba da zunubi kamar wadda ke ɗaure" ko kuma "kana kamar ɗaurere ne ga zunubi"
AT: "abubuwan da ka faɗa ... kada su faru da ni"
Bitrus da Yahaya sun faɗi abinda suka sani da kansu game da Yesu wa Samariyawan.
"magana" anan na nufin "sako." Bitrus da Yahaya sun ba da bayanin Yesu wa Samariyawa.
A nan "kauyuka" na nufin mutanen da ke cikinsu. AT: "zuwa da mutanen da ke cikin kauyukan Samariyawa da yawa" (Dubi:
Wannan ya sa alamar canjin yanayin labarin ne.
Waɗannan kalamun aikin na aiki tare ne domin nanata cewa ya shirya ya fara tafiya mai nesa da zai ɗauki ɗan loƙaci. AT: "Shirya don tafiya"
An yi amfani ne da wannan jimlar "yi ƙasa" domin Urushalima na sama da Gaza.
Masu ilimi sun yarda cewa Luka ya ƙara wannan maganar domin ya bayyana yankin da Filibus zai tafi.
Kalmar nan "sai" na jan hankalinmu zuwa ga wani sabon mutum da ya shigo labarin. Yana iya yiwuwa harshenku tana da wata hanyar yin haka.
Nanacin "bãbã" anan na game da matsayin da mutumin Habasha ke da shi a gwamnati, ba kawai domin yanayin sa na fiɗiya ba.
Wannan wata lakani ne da ake kiran duk sauraniya a Habasha. Yana kamar yadda ake amfani da kalmar Fir'auna wa duk sarki a Masar.
Wannan na nuna cewa shi ba'alummi ne wadda ya gaskata da Allah, ya kuwa zo ya yi wa Allah ibada a haikali. AT: "ya zo ne ya yi wa Allah ibada a haikalin da ke Urushalima"
Mai'yiwuwa "keken doki" za ta fi shiga da wannan yanayin. An fi ambata karusarsa a matsayin abin hawa zuwa yaƙi, ba lallai abin hawa domin tafiya mai nesa ba. Kazalika, mutane na iya tuƙin karusarsa a tsaye.
Wato littafin Ishaya da ke Tsohon Alkawali. AT: "yana karatu daga littafin Ishaya"
Filibus ya gane cewa wannan na mufi ya zai je kusa da mutumin da ke tukin karussarsa. AT: "ka raka mutumin da ke cikin wannan karussarsa"
Wato littafin Ishaya da ke Tsohon Alkawali. AT: "yana karutu daga littafin Ishaya"
Shi Habashan na da basira kuma yana iya karatu, amma ya rasa fahimi na ruhaniya. AT: "Kana fahimtar ma'annan abinda kake karantawa?"
Ana wannan tambayan ne domin a nuna cewa hakika ba zai iya fahimtar abida yake karantawa ba idan ba tare da an taimake shi ba. AT: "ba zan iya fahimtar haka ba sai dai idan wani ya bishe ni"
A nan sammanin cewa Filibus ya yarda ya yi tafiya da shi a hanyan domin ya fassara masa nassosin
Masu soyarsa sune masu aske gashin rago domin a iya amfani da shi.
AT: "Aka wulakãntashi kuma ba masa shari'a da adalci ba" ko kuma "ya bar masu masa zargin sa suka ci mutuncinsa ya kuma sha wahalan rashin adalci"
Ana amfani ne da wannan tambayan domin a nanata cewa babu tsararsa. AT: "Babu wanda zai iya magana akan tsararsa, gama ba za a samu ko ɗaya ba"
Wannan na nufin mutuwarsa. AT: "Mutane ne suka kashe shi" ko kuma "mutane ne suka ɗauki ransa daga duniya"
"Don Allah ka fạɗa mani"
Wannan na nufin rubuce rubucen Ishaya da ke cikin Tsohon Alkawali. AT: "a cikin rubuce rubucen Ishaya"
"ya koya wa baban bisharar Yesu.
"suka cigaba da tafiya a hanya"
Baban ya yi wannan tambaya ne domin Filibus ya bashi damar yin baftisma. AT: "no roke ka bari in yi baftisma"
"ya ce wa ma tukin karussarsa ya tsaya"
"baban bai sake ganin Filibus ba"
Wannan alama ce cewa Filibus na tafiya tsakanin wurin da ya wa Habashan baftisma da Azotus. Filibus ya bi ya ɓace a hanyar Gaza ya sake fitowa a birnin Azotus.
Wannan na nufin yankin da ke kewaye da birnin Azotus.
"a dukan garuruwan da ke wannan yankin"
1Amma Shawulu, ya cigaba da maganganun tsoratarwa har ma da na kisa ga almajiran Ubangiji, ya tafi wurin babban firist 2kuma ya roke shi wasiku zuwaga majami'un da ke Dimashku, domin idan ya sami wani da ke na wannan hanya, maza ko mata, ya kawo su Urushalima a daure.3Yayin da yana tafiya, ya kasance da ya iso kusa da Dimashku, nan da nan sai ga wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi; 4Sai ya fadi a kasa kuma yaji wata murya na ce da shi, "Shawulu, Shawulu, me yasa kake tsananta mani?"5Shawulu ya amsa, "Wanene kai, Ubangiji?" Ubangiji ya ce, "Nine Yesu wanda kake tsanantawa; 6amma ka tashi, ka shiga cikin birnin, kuma za a gaya maka abinda lallai ne kayi. 7Mutanen da ke tafiya tare da Shawulu suka tsaya shiru sun rasa abin fada, suna sauraron muryar, amma ba su ga kowa ba.8Shawulu ya tashi daga kasa, kuma daga ya bude idanunsa, baya ganin komai; sai suka kama hannuwansa suka yi masa jagora suka kawo shi cikin birnin Dimashku. 9Har kwana uku ba ya kallo, kuma ba ya ci balle sha.10Akwai wani almajiri a Dimashku mai suna Hananiya; sai Ubangiji ya yi magana da shi cikin wahayi, ya ce, "Hananiya." Sai ya ce, "Duba, gani nan Ubangiji." 11Ubangiji ya ce masa, "Tashi, ka tafi titin da ake kira Mikakke, kuma a gidan wani mai suna Yahuza ka tambaya mutum daga Tarsus mai suna Shawulu; gama yana addu'a; 12kuma ya gani cikin wahayi mutum mai suna Hananiya na shigowa kuma ya daura masa hannu, domin idanunsa su bude."13Amma Hananiya ya amsa, "Ubangiji, na ji labari daga wurin mutane da yawa game da mutumin nan, da irin muguntar da ya aikata ga tsarkakan mutanenka da ke Urushalima. 14An bashi izini daga babban firist domin ya kama dukan wanda ke kira bisa sunanka." 15Amma Ubangiji ya ce masa, "Jeka, gama shi zababben kayan aiki na ne, wanda zai yada sunana ga al'ummai da sarakuna da 'ya'yan Isra'ila; 16Domin zan nuna masa irin wahalar da zai sha sabo da sunana."17Sai Hananiya ya tafi, ya shiga gidan. Ya dora masa hannu a kai, ya ce, "Dan'uwa Shawulu, Ubangiji Yesu, wanda ya bayyana a gareka a hanya sa'adda kake zuwa, ya aiko ni domin ka sami ganin gari ka kuma cika da Ruhu Mai Tsarki." 18Nan take wani abu kamar bawo ya fado daga idanun Shawulu, kuma ya sami ganin gari; ya tashi aka yi masa baftisma; 19kuma ya ci abinci sai aka karfafa shi. Ya zauna tare da almajirai a Dimashku kwanaki da yawa.20Nan take ya fara shellar Yesu cikin haikali, yana cewa shine dan Allah. 21Dukan wadanda suka saurare shi suka yi mamaki suka ce "Ba wannan mutumin ne yake hallaka mutanen Urushalima da ke kira bisa ga wannan suna ba? Ya kuma zo nan domin ya ba da su a daure ga manyan firistoci." 22Amma Shawulu kuwa ya sami iko sosai, kuma yana haddasa damuwa tare da rinjaya tsakanin Yahudawan dake zama a Dimashku ta wurin tabbatar da Yesu shine Almasihu.23Bayan kwanaki da yawa, sai Yahudawan suka yi shiri domin su kashe shi. 24Amma shirin su ya zama sananne ga Shawulu. Suna fakkon sa ta wurin tsaron kofar birnin dare da rana domin su kashe shi. 25Amma da tsakar dare almajiransa suka daukeshi a kwando, suka zurara shi ta katanga.26Sa'adda ya zo Urushalima, Shawulu ya yi niyyar hada kai da almajirai, amma dukansu suna tsoronsa, domin ba su yarda cewa shima ya zama almajiri ba. 27Amma Barnaba ya dauke shi ya kawo shi wurin manzannin. Ya kuwa gaya musu yadda Shawulu ya sadu da Ubangiji a hanya, har Ubangiji ya yi magana da shi, kuma yadda Shawulu ya yi wa'azi cikin sunan Yesu gabagadi a Dimashku.28Ya sadu da su lokacin shigar su da fitar su a Urushalima. Ya yi wa'azi gabagadi cikin sunan Ubangiji Yesu 29kuma yana muhawara da Yahudawan Helenanci; amma sun ci gaba da kokarin kashe shi. 30Da 'yan'uwa suka gane haka, sai suka kawo shi Kaisariya, suka kuwa tura shi zuwa Tarsus.31Sa'annan iklisiya dake dukan kasar Yahudiya, Galili da kuma Samariya suka sami salama da kuma ginuwa; suka kuwa ci gaba da tafiya cikin tsoron Ubangiji, da kuma ta'aziyar Ruhu Mai Tsarki, iklisiyar kuwa ta karu da yawan mutane. 32Har ta kai, yayin da Bitrus ya zaga dukan yankin kasar, ya dawo wurin masu bi dake zama a garin Lidda.33A can kuwa ya sami wani mutum mai suna Iniyasu, wanda yake shanyayye ne, yana kwance har tsawon shekara takwas a kan gado. 34Bitrus ya ce masa, "Iniyasu, Yesu Almasihu ya warkar da kai. Tashi ka nade shimfidarka." Nan take sai ya mike. 35Sai duk mazauna kasar Lidda da kasar Sarona suka ga mutumin, suka kuma juyo ga Ubangiji.36Yanzu kuwa a Yafa akwai wata almajira, mai suna Tabita, ma'ana "Dokas." Wannan matar kuwa tana chike da ayyukan nagarta da halin tausayi da take yi ga mabukata. 37Ya kai ga cewa a kwanakin can ta yi rashin lafiya har ta mutu; da suka wanke gawar ta suka kwantar da ita a bene.38Da shike Lidda na kusa da Yafa, almajiran kuma sun ji cewa Bitrus yana can, suka aika mutane biyu wurinsa. Suna rokansa, "Ka zo garemu ba tare da jinkiri ba." 39Bitrus ya tashi ya tafi da su, da isowar sa, suka kai shi benen. Sai dukan gwamrayen suka tsaya kusa da shi suna kuka, sai suka dauko riguna da sutura da Dokas ta dinka lokacin da take tare da su.40Bitrus ya fitar da su duka daga cikin dakin, ya durkusa, ya yi addu'a; sai, ya juya wurin gawar, ya ce, "Tabita, tashi." Ta bude idanunta, da ta ga Bitrus ta zauna, 41Bitrus kuwa ya mika hannunsa ya tashe ta; sa'annan ya kira masu bi da gwamrayen, ya mika ta a raye garesu. 42Wannan al'amari ya zama sananne cikin dukan Yafa, kuma mutane da yawa suka bada gaskiya ga Ubangiji. 43Ya kasance, cewa, Bitrus ya zauna kwanaki da dama a Yafa tare da wani mutum mai suna Saminu, majemi.
Labarin ya komo kan Bulus da samun cetonsa.
Waɗannan ayoyin suna ba da tarihin abubuwan da Bulus ya rika yi tun daga mutuwar Istifanus.
AT: cigaba da maganganun tsoratarwa, har ma da kisan almajiran"
Wannan na nufin mutanen da ke majami'un. AT: "zuwaga mutanen da ke majami'un" ko kuma "zuwaga shugabanin da ke majami'un"
...''in ya sami wani'' ko ''har ya sami wani''
"da ke bin koyarwar Yesu Almasihu"
Wannan wata lakani ce da aka san masu bi da shi a wancan loƙaci.
"ya kawo su a matsayin yan gidan kurkuku a Urushalima." Za a iya kara bayanin manufan Bulus idan aka kara cewa "domin ya shugabanin Yahudawa su masu shari'a su kuma yanka masu hụkunci"
Shawulu ya bar Urushalima za shi Dimashku
Wannan furcin na ba da alamar canji a labarin cewa wani abu da na zai faru.
"wani wuta daga sama ya haska kewaye da shi"
Wannan na iya nufin 1) sama, wurin da Allah ke kasancewa ko kuma 2) sararin sama. Ma'anan na forkon ya fi gaskiya. Yi amfani da wannan ma'anan idan harshen ku ta na da wata kalma daban masa.
Wannan na iya nufin cewa 1)"Shawulu ya yi tsalle zuwa ƙasa" ko kuma "Haken ya sa shi ya fada ƙasa" ko kuma "Shawulu ya faɗi ƙasa kamar wanda ya sume." Faduwar Shawulu dai ba hatsari ba ne.
Wannan tambayan ganganci ne na sauta wa Shawulu. A wasu harsuna ana iya faɗin sa ba da tambaya ba
Ba wai Shawulu yana amicewa da cewa Yesu Ubangiji ba ne. Ya yi amfani ne da wannan lakani domin ya fahimci cewa yana magana ne da wata iko na allahntaka.
"ta shi ka je cikin birnin Dimashku"
AT: "wani zai faɗa maka"
"sun ji muryar amma basu ga kowa ba"
A fili yake cewa Bulus ne kadai ya dandana wannan hasken.
Wannan na nuna cewa ya rufe idanunsa saboda yawan hasken.
"bai iya ganin komai ba." Shawulu ya makance.
"na makance" ko kuma "ba ya iya ganin komai"
Ba a bayyana ko shi ne ya zaɓa kada ya ci ko ya sha ba saboda ibada, ko kuma bai ma ji marmarin haka saboda halin da yake ciki. Ya fi kada ma aba da wata takamemmenn dalili.
Wannan na gabatar da wani sabuwar mutum a cikin labarin.
"Hananiya ya ce"
"ka je Mikakkiyar titi"
Ba wannan Yahuza ne ya bashe Yesu ba. Wannan Yahuza shi ne mai gidan da ke Dimashku in da Shawulu yake zama.
"wani mutum daga birnin Tarsus mai suna Shawulu" ko kuma "shawulu da ke Tarsus"
Wannan alama ce na ba wa Shawulu albarku na ruhaniya."
"ya iya gani kuma"
A nan "tsarkaka people" na nufin Masubi. AT: "mutanen da ke Urushalima da sun gaskanta da kai"
A nan daukan cewa iyakar iko da izini da aka ba wa Shawulu ya tsaya ne kan mutanen Yahudawa a wannan loƙaci.
A nan "sunanka" na nufin Yesu.
"zababben kayan aiki" na nufin wani abin da aka kebe domin wata hidima. AT: "na zabe shi ya bauta mini"
Wannan furci ne na gana wa ko kuma sanar da Yesu. AT: "domin ya sanar da ni"
Wannan furcin na nufin "sanar wa mutane game da ni"
Zai zama da taimako idan a sanar cewa Hananiya ya je gidan kamun ya shigo ciki. AT: "Sai Hananiya ya tafi, da ya samo gidan da Shawulu yake, sai ya shigo"
AT: "ya aiko ni domin ka sami ganin gari Ruhu Mai Tsarki ya kuma cika ka"
...
"ya iya ganin gari kuma"
AT: ya tashi sai Hananiya ya masa baftisma"
Wannan wata laƙaɓi ne ma muhimanci na Yesu.
AT: "Waɗanda suka saurare shi" ko kuma "Da daman su da suka saurare shi"
Wannan tambayan ganganci ne da ke nanata cewa lallai Shawulu ya tsananta wa masubi. AT: "Ai wannan ne mutumin da ya hallaka mutanen da ke Urushalima da ke kira bisa ga sunan Yesu!"
"A nan "suna" na nufin Yesu. AT: "sunan Yesu"
Suna damuwa ƙwarai domin ba su iya samun wata hanya na ƙaryata muhawarar Shawulu cewa Yesu Almasihu ne.
Wato shugabanin Yahudawan. AT: "Shugabanin Yahudawan"
AT: "Amma wani ya faɗa wa Shawulu game da shawaransa" ko kuma "Bulus ya san game da shirinsu"
Birnin yana da katanga kewaye da shi. Mutane na iya shiga ko fita daga birnin ta kofofin ne kawai.
mutanen da suka ba da gaskiya ga sakon Shawulu game da Yesu kuma sun bin koyaswansa.
"suka yi amfani da igiyoyi suka sauke shi a wata babban kwando ta wata rami a katangan.
A nan "dukansu" na iya yiwuwa ya hada da kowannensu, AT: "amma suna tsoronsa"
Wannan wata hanya ne na cewa ya yi wa'azi bishara ko koyar da sakon Yesu Almasihu ba tsoro. AT: "ya yi wa'azin bisharan Yesu a fili"
Wato Bulus kenan. Kalmar nan "su" kuma na iya nufin manzannin da kuma sauran almajiran da ke Urushalima.
Wannan na iya nufin 1) wannan na iya zama Ubangiji Yesu wadda Bulus ke magana akai. AT: "game da Ubangiji Yesu" ko kuma 2) "suna" na nufin iko. AT: "karkashin ikon Ubangiji Yesu" ko kuma "da ikon da Ubangiji Yesu ya ba shi"
Shawulu ya yi koƙarin tattaunawa da Yahudawan da ke Halenanci.
"Kalmar nan 'yan'uwan' na nufin masubi da ke Urushalima.
Kaisariya na kasa da Urushalima d tadawa.
Kaisariya kuwa tashan saukan jiragen ruwa ne. Mai yiwuwa 'yan'uwan sun turo shi Tarsus ta jirgin ruwa ne.
Wannan ne forƙon kiran ikkilisiyoyi fiye da ɗaya a matsayin ikkilisiya guda. Anan yana nufin dukan masubi a dukan kungiyoyin da ke Isra'ila gabaɗaya.
"suka zauna lafiya." Wannan na nufin cewa tsanantawar da aka fara daga kisan Istifanus ya kare.
Maginan na kuma Allah ne ko kuma Ruhu Mai Tsarki. AT: "Allah ya taimake su sun yi girma" ko kuma "Ruhu Mai Tsarki ya gina su"
"tafiya" anan magana ce da ke nufin "rayuwa". AT: "suna rayuwar biyayya ga Ubangiji" ko kuma " suka cigaba da girmama ubangiji"
Wannan jimlar na nuna alamar wata sabuwan bangaren labarin.
"tare da samun karfawa da taimakon Ruhu Mai Tsarki"
Wannan na nufin cewa Bitrus ya ziyarce masubi da ke wurare da dama a yankin Yahudiya, Galili, da Samaria.
Lidda na kasa da sauran wuraren ta yake tafiya.
Lidda wata birni ne da ke kilomita 18 gabas maso kudancin Yafa. Anan kiran wannan birni Lod a Tsohon Alkawali da kuma Isra'ila ta yau.
Bitrus ba fito nema wani shanyayyen mutum da gangan ba ne, ya dai faru hake ne dai da shi. AT: "A can kuwa ya sadu da wani mutum"
Wannan na gabatar da Iniyasu ne a matsayin wani sabon mutum a labarin.
Wannan dai tarihin Iniyasu kenan.
ba iya tafiya ba, mai yiwuwa ma ba ya iya motsi daga kwankwasonsa.
"ka kintsa taburmarka"
Wannan na nufin mutane masu yawa da ke wurin. AT: "waɗanda ke kasar Lidda da kuma kasar Sarona" ko kum "mutane da yawa da ke kasar Lidda da kuma kassar Sarona"
Birnin Lidda a sararin Sarona ya ke.
Yana iya zama da taimako a sanar cewa sun ga mutumin a warke. AT: "suka ga mutumin da Bitrus ya warkar"
A nan "juyo ga Ubangiji" na nufin suka fara biyayya ga Ubangiji. AT: "sai suka tuba daga zunubansu suka fara yi wa Allah biyayya"
Tabita shi ne sunan ta a Harshen Yahudanci, sa'annan Dokas shine sunan ta a harshen Hallenanci. Duka sunaye biyun dai na nufin "barewa." AT: "sunanta a Hallenaci ita ce Dokas"
"tana yin abubuwa da yawa masu kyau"
Wannan na mayar da mu zuwa ga loƙacin da Bitrus ke Yafa. AT: "Ya kai ga loƙacin da Bitrus yana kusa"
Wannan wankin domin shirin bizne ta ne.
Wannan dai nuna jikin mamaci ne na ɗan loƙaci yayin jana'izi.
"almajiran suka aiko mutane biyu wurin Bitrus"
"wata dakin sama wurin da jikin Dokas yake a kwanciye"
Yana iya yiwuwa dukan gwamrayen garin suna kasace a waurin tunda ba babbar gar ba ce.
Matayen da mazan su sun mutu kuma suna buƙatan taimako
"loƙacin da take da rai tare da almajiran"
"ya ce masu su bar dakin." Bitrus ya fitar da su duka daga dakin domin ya kasance shi kadai a wurin ya yi wa Tabita addu'a.
Bitrus ya kama hannun ta ya taimake ta tsayawa.
Gwamrayen na iya zama masubi su ma amma ba ambaci hakan ka tsaye ba domin Tabita ta na da muhimanci sosai a garesu.
Wannan na nufin abin al'ajibin da Bitrus yayi na tayar da Tabita daga matattu. AT: Mutane da ke Yafa duka sun ji wannan al'amarin"
"suka ba da gaskiya ga bisharar Ubangiji Yesu"
Wani mai suna Saminu, da ke yi fata daga jikin dabbobi"
1An yi wani Mutum a birnin Kaisariya, mai suna Karniliyas, shugaban sojoji ne na kungiyar da ake kira Italiya. 2Mutum ne mai ibada, wanda ya mika kansa da iyalinsa ga bautar Allah; ya kan bada taimakon kudi mai yawa ga Yahudawa, kuma yana addu'a ko yaushe ga Allah.3Wajen sa'a ta tara ga yini, an bayyana masa cikin wahayi mala'kan Ubangiji na zuwa gare shi sai mala'ikan ya ce masa, "Karniliyas!" 4Karniliyas ya zuba wa mala'ikan ido a tsorace ya ce "Menene, mai gida?" mala'ikan ya ce masa, "Addu'ar ka da taimakon ka ga talakawa ya kai sama matsayin sadaka abin tunawa a gaban Allah, 5"Yanzu ka aika mutane zuwa birnin Yafa su kawo mutum mai suna Saminu wanda ake kira Bitrus. 6Yana zama tare da Saminu majemi, wanda gidansa ke bakin teku.7Da mala'ikan da ya yi magana da shi ya tafi, Karniliyas ya kira biyu daga barorin gidansa, da kuma soja guda mai bautar Allah daga cikin sojojin da suke masa hidima. 8Karniliyas ya fada masu dukan abin ya faru sai ya aike su Yafa.9Washe gari wajen sa'a ta shida (tsakar rana) suna cikin tafiya da suka yi kusa da birni, Bitrus ya hau kan bene don ya yi addu'a. 10Sai ya ji yunwa kuma yana bukatar wani abinda da zai ci, amma a yayin da mutanen na dafa abinci, sai ya ga wahayi. 11Sai ya ga sararin sama ya bude kuma wani tasa na saukowa, wani abu kamar babban mayafi yana saukowa zuwa duniya, ana zuro shi ta kusuryoyinsa hudu. 12A cikinsu kuwa akwai dukan halitun dabbobi masu kafa hudu da kuma masu rarrafe a duniya da tsunstayen sama.13Sai murya ta yi magana da shi; "Tashi, Bitrus, yanka ka ci " 14Amma Bitrus ya ce "Ba haka ba, Ubangiji, gama ban taba cin abu mara tsarki ko mai kazanta ba." 15Amma muryar ta sake zuwa masa karo na biyu kuma; "Abinda Allah ya tsarkake, kada ka kira shi kazantacce." 16Wannan ya faru sau uku; nan da nan sai aka dauki tasar zuwa sama.17A yayin da Bitrus na cikin rudani game da ma'anar wahayin da ya gani, sai ga mutanen da Karniliyas ya aika suna tsaye a bakin kofar gidan, bayan sun tambayi hanyar zuwa gidan, 18Kuma suka yi sallama suna tambaya ko Saminu wanda ake kira Bitrus ya sauka a nan.19A yayin da Bitrus yana kan tunani akan wahayin, Ruhu ya ce masa, "Duba, mutane uku na neman ka." 20Tashi ka sauka ka tafi tare da su. Kada ka yi jinkirin tafiya tare da su, domin Nine na aike su." 21Bitrus kuwa ya sauko wurin mutanen ya ce, "Ni ne wanda kuke nema. Me ya sa kuka zo?"22Suka ce, "Shugaban soja mai suna Karniliyas, adalin mutum kuma mai bautar Allah, yana da kyakkyawar shaida a dukan al'umman Yahudawa, shi ne wanda mala'ika mai tsarki na Allah ya aika domin ka zo gidansa, ya ji sako daga wurinka." 23Sai Bitrus ya gayyace su su zo ciki kuma su zauna tare da shi. Washegari sai ya tafi tare da su, kuma wadansu 'yan'uwa daga Yafa suka raka shi.24Kashegari suka shiga Kaisariya, Karniliyas kuwa yana jiran su; har ma ya gayyaci 'yan'uwansa da kuma abokansa na kusa.25Ya kasance sa'adda Bitrus ya shiga, Karniliyas ya sadu da shi kuma ya durkusa ya yi masa sujada. 26Amma Bitrus ya tashe shi yana cewa, "Tashi tsaye! Ni ma mutum ne."27A lokacin da Bitrus yake magana da shi, ya shiga ciki sai ya tarar da mutane da yawa sun taru a wuri daya. 28Ya ce masu, "Ku da kanku kun sani bai dace Bayahuden mutum ya yi ma'amulla ko ya ziyarci wani ko wata kabila ba. Amma Allah ya ce da ni kada in ce da kowa mara tsarki ko kazantacce. 29Wannan shine yasa na zo ba tare da musu ba, a lokacin da kuka kira ni. Don haka na tambaye ku me ya sa kuka aika in zo."30Karniliyas ya ce "Kwanaki hudu da sun wuce a daidai wannan lokaci, ina addu'a da cikin sa'a na tara (karfe uku) a gidana, sai na ga mutum tsaye a gabana da tufafi mai haske. 31Ya ce, "Karniliyas, Allah ya ji addu'ar ka, kuma taimakon ka ga talakawa ya tuna ma Allah da kai. 32Saboda haka ka aika da wani Yafa, ya kira maka mutum mai suna Saminu wanda ake kira Bitrus. Yana zama a gidan Saminu majemi, da ke bakin teku. 133Don haka nan da nan na aika a kira ku. Kuna da kirki da kuka zo. Yanzu haka, duk muna nan a gaban Allah, don jin duk abin da Ubangiji ya umarce ku da ku faɗi.” 234Sai Bitrus ya bude bakinsa ya ce, "Gaskiya, na fahimci Allah baya nuna bambanci. 35Maimakon haka, cikin kowace al'umma duk mai ibada kuma mai aikata adalci karbabbe ne a gare shi.36Ku kun san sakon da ya aika wa mutanen Isra'ila, a lokacin da ya sanar da labarin mai kyau na salama ta wurin Yesu Kristi, wanda shine Ubangiji na duka. 37Ku da kanku kun san al'amuran da suka kasance, wanda ya faru cikin Yahudiya, farawa daga Galili, bayan sanarwar baftismar da Yahaya ya yi. 38Al'amura game da Yesu Banazare, yadda Allah ya kebe shi da Ruhu Mai Tsarki da iko kuma. Ya kuma ci gaba da aikin alheri da warkarwa ga dukan wadanda shaidan ya daure, domin Allah yana tare da shi.39Mu shaidu ne ga dukan abubuwan da ya yi a kasar Yahudawa da cikn Urushalima, wannan Yesu wanda suka kashe, ta wurin giciye shi a akan itace. 40Wannan mutumin, Allah ya ta da shi rana ta uku ya kuma maishe shi sananne, 41ba ga dukan mutane ba, amma ga shaidun da Allah ya zaba tun da farko - mu kanmu, wadanda muka ci muka sha tare da shi bayan tashin sa daga matattu,42Ya umarce mu mu yi wa mutane wa'azi mu kuma tabbatar cewa shine wanda Allah ya zaba ya yi shariya bisa masu rai da matattu. 43Gareshi ne dukan annabawa suka yi shaida, domin dukan wanda ya bada gaskiya gareshi ya sami gafarar zunubai ta wurin sunansa.`44Sa'adda Bitrus yana kan magana game da wadannan abubuwa, Ruhu Mai Tsarki ya sauko a kan dukan wadanda suke sauraron wa'azin sa. 45Mutanen da ke kungiyar masu bi da suka yarda da kaciya, dukan wadanda suka zo tare da Bitrus suka yi mamaki, domin baiwar Ruhu Mai Tsarki ya sauko a kan al'ummai.46Domin sun ji al'umman nan suna magana da wasu harsuna suna yabon Allah. Sai Bitrus ya amsa, 47"Ko akwai wanda zai hana wa wadannan baftisma ta ruwa, da shike suma sun karbi Ruhu Mai Tsarki kamar mu?" 48Sai ya ba da umarni a yi masu baftisma cikin sunan Yesu Kristi. Sai suka roke shi ya kasance da su na wasu kwanaki.
Wannan ne forƙon bangaren labarin Karniliyas.
Waɗannan ayoyin suna ba da tarihi game da Karniliyas.
Wannan wata hanya ne na gabatar da sabuwar mutum a wannan sashin tarihin.
"sunan sa Karniliya. Shugaban sojoji ne da ke da sojoji 100 a karkashinsa daga sojojin Roma da ke bangaren Italiya.
"Ya gaskata da Allah yana kuma neman ya girmama ya kuma mika kansa ga Allah muddin ransa."
Kalmar nan "mika kai" a nan na nuna matuƙar bangirma datsoron Allah.
Wannan na nufin yawancin loƙaci. AT: yana wa Allah addu'a sosai" ko kuma ""yana wa Allah addu'a kulayomi"
"da karfe uku na rana." Wannan ne daidai loƙacin da Yahudawa sukan yi addu'a.
"an bayyana wa Karniliyas"
A nan iya cewa taimakonsa da addu'oinsa sun sami karba a wurin Allah. AT: "Allah yana jin dadin addu'oi da sadakarka ... abin karma a wurin sa"
mutumin da ke yin fata daga jikin dabbobi
"Da wahayin Karniliyas game da malaikan ya kare."
"ɗaya daga cikin sojojin da ke bauta masa, da ke wa Allah sujada kuma." Wannan sojan mai bi ne. Hakan yana da wuya a samu a cikin sojojin Roma, saboda haka yana iya yiwuwa ma cewa sauran sojojin Karniliyas ba masubi ba ne.
...
Karniliyas ya yi bayyanin wahayinsa ga bayinsa, ɗaya daga cikin sojojinsa.
"ya aiko bayinsa biyu, ɗayan su kuma soja ne kuma an aiko shi Yafa ne
"tsakar rana"
Kan gidajen shimfiɗaɗɗe ne, kuma mutane sun kan ya abubuwa da dama a bisan su.
"kamin mutanen su gama dafa abincin"
"Allah ya nuna masa wahayi"
Wannan ne forƙon wahayin Bitrus. Za a iya fara ta da wata sabuwan jimla.
...
...
Daga amshin Bitrus a aya na gaba, za a iya tunanin cewa shari'ar Musa bai umurce Yahudawan su ce wasu dabbobin ba. AT: "dabbobi da tsuntsayen da shari'ar Musa ya hana Yahudawa ci"
Ba ambaci mai maganan ba. Yana iya yiwuwa "muryar" nan na Allah ne, ko da shike ya na iya ma ya zama muryar Malaikan Allah ne.
"Ni ba zan yi haka ba"
Ana ɗaukan cewa shari'ar Musa bai ba wa masubin da ke rayuwa kamun mutuwar Almasihu daman cin wasu dabbobi da ke mayafin domin su ƙazantacecce na.
Idan Allah ne mai magana, yana magana game da kansa kamar shi ne mutum na uku a wurin. AT: "Abinda Ni, Allah, na tsarkake"
Ba lallai kome ne da Bitrus ya gani ya faru sau uku ba. Wannan jimlar na iya nufin, "Abinda Allah ya tsarkaka, kada ka ce da shi kazantatce" ne aka maimaita sau uku. Ko da shika, ya fi kyau a ce "Wannan ya faru sau uku" da a yi ta koƙarin ba da wasu bayyani.
Wannan na nufin cewa Bitrus ba iya gane abinda wahayin ke nufi ba.
Kalmar nan "sai" na jan hankalin mu zuwa ga bayyani na ban mamaki da ya biyo baya a wannan sha'anin, mutan biyun da ke tsaye a ƙofar.
"suka tsaya a bakin kofar gidan." Ana dauƙan cewa wannan gidan na da bango da kuma kofa wadda ake bi a shigo ta.
Hakan ya faru kamin su iso gidan. Ana iya sanar da wannan a ayan da ke kamin wannan kamar yadda aka yi a UDB.
Mutanen Karniliyas suna kasance a kofa, a waje yayin da suna tambayan game Bitrus.
"yana kan tunanin ma'anar wahayin"
"Ruhu Mai Tsarki"
"ka kasa kunne daomin abinda nake so in gaya maka gaskiya ne kuma mai muhimanci ne: mutane uku"
Wasu nasosi na da suna da kimamun mutane daban-daban.
"sauka daga saman gidan"
Ya na da sauki Bitrus ya ki yin marmarin tafiya tare da su, domin su baƙi ne, kuma Al'ummai ne.
"Ni ne mutumin da kuke nema"
(Dubi: )
kalmar "bautar Allah" anan nu nufin mutuƙar ban girma da tsoron Allah.
Ana moran kalmar nan "dukan" domin a nanata yadda Yahudawa da yawa sun san da shi.
Tafiya Kaisariya na da nesa su bi su kama hanya da rana haka.
...
Wannan na nufin masubi da ke Yafa.
Wato bayan da suka bar Yafa kenan. Tafiyar Kaisariya na ɗaukansu fiya da ini ɗaya.
...
"sa'adda Bitrus ya shigo gidan"
"ya durkusa ya sa fuskarsa kusa da karfa Bitrus." Ya yi haka ne domin ya girmama Bitrus.
Ya yi haka ne musamman don ya nuna cewa yana sujada.
Wannan wata ɗan tsauta wa ne ko kuma gyara ne wa Karniliyas don kada ya yi wa Bitrus sujada. AT: "Ka daina yin haka! Ni ma fa mutum ne kamar ka"
"Al'ummai da yawa sun taru a wuri ɗaya." Ana ɗaukan cewa mutanen nan da Karniliyas ya gayyata Al'ummai ne.
Bitrus yana magana ne da Karniliyas da kuma gayyatattun baƙinsa.
"an hana Bayahuden mutum." Wannan na nufin shari'ar adinin Yahudanci.
Wannan na nufin mutanen da ba Yahudawa ba lallai wurin da suke zama ba.
Karniliyas yana nufin yini ɗaya kamun dare a uku kamun ya fara magana da Bitrus. Bisa ga kirgen Littafi Mai Tsarki ana kirga ranar da ake ne, don haka kamun dare uku da suka wuce shi ne "kwanaki huɗu da suka wuce." Da shike al'adun Yammaci a yau ba su kirge da kwanan da ake ciki, masu juyi da yawa sukan rubuta "kwanaki uku da suka wuce.
Wasu mannyan ma su karatu sun ce "azumi da addu'a" suke yi, a maimakon "addu'a" kawai.
Daidai lokacin da Yahudawa ke yi wa Allah addu'a da rana.
.lokaci ne da rana da Yahudawa suke yin sujada ga Allah.
"ya jawo da hankalin Allah zuwa kanka." Wannan bai nuna cewa Allah ya manta ba ne.
"fada wa Saminu wadda a ke kira Bitrus ya zo gare ka"
"da sauri"
Wanna furcin wata hanya ne na gode wa Bitrus da zuwa. AT: "Hakika na gode sosai da zuwa"
...
AT: da Ubangiji ya ce ka faɗa"
"Bitrus ya fara masu magana"
Wannan na nufin cewa abinda zai fada masu yana da muhimmanci sosai su sani.
...
"yana karaban duk wanda ke masa ibada mai aikata adalci"
Kalmar nan "ibada" anan na nuna matuƙar ban girma da tsoron Allah."
An takaita tsawon wannan jimlar zuwa wasu gajerun jimla a UDB.
A nan "duka" na nufin "dukan mutane"
AT: "Yahudiya gabakiɗaya" ko kuma "a wurare da dama cikin Yahudiya"
"bayan da Yahaya ya yi wa mutanen wa'azi su tuɓa ya masu baftisma"
an yi maganan Ruhu mai tsarki da ikon Allah kamar wanni abu ne wanda za a zuba a kan mutum
AT: "waɗanda shaiɗan ya daure" ko kuma "mutane da dama da shaiɗan ya ɗaure"
Wannan karin maganan "yana tare da shi" na nufin "yana taimakonsa."
Wannan na nufin Yahudiya ne a wannan loƙacin.
AT: "giciye shi a bisa giciyen katako"
A nan a tayar karin magana ne da ke nufin a sa mutum da ya mutu ya tashi kuma. AT: "Allah ya rayar da shi kuma"
"rana ta uku bayan ya mutu"
"ya bar mutane da dama su ganshi bayan ya ta da shi daga matattu"
Daga dukan waɗanda suka mutu. Wannan furcin na bayyana cewa dukan matattu gabaɗaya suna karkashin duniya.
"Allah ya zabe shi Yesu"
Wannan na nufin mutanen da suke da rai da kuma muutanen da sun riga sun mutu. AT: "mutanen da ke da rai da kuma mutanen da sun riga sun mutu"
"Dukan annabawa sun ba da shaida akan Yesu"
AT: "Allah za gafarta zunuban duk wanda ya ba da gaskiya ga Yesu domin abinda Yesu ya yi"
Anan "sunansa" na nufin abinda Yesu ya yi. Ma'anan "sunansa" shi ne Allah mai ceto. AT: "ta wurin abinda Yesu ya yi masu"
A nan kalmar nan "sauko" na nufin "ya faru da sauri." AT: "Ruhu Mai Tsarki ya bi ya zo"
A nan "duka" na nufin dukan Al'ummai da ke a gidan suna sauraron Bitrus.
Wannan wata hanya ce da ke nufin Yahudawa masu bi.
Wannan na nufin Ruhu Mai Tsarki da kansa da aka ba su.
AT: "Allah ya sauko da Ruhu Mai Tsarki"
AT: "bayar a yalwace"
kyautar baiwar
A nan "ma" na nuna cewa an riga an ba da Ruhu Mai Tsarki ga masubi Yahudawa.
Waɗannan sanannun harsuna ne da suka sa Yahudawa suka amince cewa lalle Al'umman suna yabon Allah.
Bitrus ya yi amfani ne da wannan tambayan ya karfafa Yahudawa masu bi da cewa a yi wa Al'ummai masu bi baftisma. AT: "Kada wani ya hana waɗannan mutanen da ruwa! Mu yi masu baftisma domin sun karbi ... mu!"
Ana ɗaukan cewa Yahudawa masubi ne za su yi masu baftisma. AT: "Bitrus ya umarce Al'ummai masubi su bar Yahudawa masubi su yi masu baftisma" ko kuma "Bitrus ya umarce Yahudawa masu bi su yi masu baftisma"
Anan "cikin sunan Yesu Kiristi" na nuna cewa dalilin baftismar su shi ne domin sun gaskanta da Yesu. AT: "a yi masu baftisma a mastayin masu bi a cikin Yesu Kristi"
1Yanzu Manzani da 'yan'uwa wadanda suke cikin Yahudiya suka ji cewa al'ummai ma sun karbi maganar Allah 2Lokacin da Bitrus ya je Urushalima, wadanda suke na kaciya suka zarge shi; 3suka ce, "Ka hada kai tare da mutane marasa kaciya kana ci tare da su!"4Amma Bitrus ya fara bayyana masu dalla-dalla; ya ce, 5Ina addu'a a cikin birnin Yafa, sai na ga wahayi game da taska yana saukowa, kamar babban mayafi da aka saukar daga sama ta kusurwan nan hudu. Ya sauko gabana. 6Na zura masa ido kuma na yi tunani a kansa, na ga dabbobi masu kafa hudu na duniya, miyagun dabbobi, da masu rarrafe, da tsuntsayen sama.7Sai na ji murya tana ce da ni, "Tashi, Bitrus, yanka ka ci." 8Na ce, "Ba haka ba, Ubangiji: gama babu abu mara tsarki ko mai kazanta da ya taba shiga bakina." 9Amma murya ta amsa kuma daga sama cewa, "Abin da Allah ya kira mai tsarki, kada ka kira shi mara tsarki." 10Wannan ya faru sau uku, sai dukan komai ya koma sama.11Nan da nan sai ga mutane uku tsaye a gaban gidan da muke; an aike su daga Kaisariya zuwa gare ni. 12Ruhun ya umurce ni in tafi tare da su, ba tare da nuna banbanci game da su ba. Yan'uwan nan shida sun tafi tare da ni, sai muka shiga gidan mutumin. 13Ya fada mana yadda ya ga mala'ika tsaye a cikin gidansa yana cewa "Aiki mutane zuwa Yafa, su kirawo Saminu wanda ake kira Bitrus. 14Zai gaya maku sakon da za ku sami ceto kai da dukan gidanka."15Da na fara magana da su, Ruhu Mai Tsarki ya sauko akansu kamar yadda ya sauko mana tun da farko. 16Sai na tuna da maganar Ubangiji, yadda ya ce,"Hakika Yahaya ya yi baptisma da ruwa, amma ku za a yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki."17To, idan Allah ya yi masu baiwa kamar yadda ya yi mana yayin da muka bada gaskiya ga Ubangiji Yesu Almasihu, wane ni da zan yi jayayya da Allah? 18Da suka ji wadannan abubuwa, suka rasa ta cewa, amma suka daukaka Allah suka ce "Ga al'ummai ma Allah ya basu tuba zuwa rai."19Sai wadanda suka warwatsu saboda tsananin da ya bi bayan mutuwan Istifanas, suka yadu har zuwa Finikiya, Kuburus da Antakiya, amma suka yi wa'azin Yesu ga Yahudawa kadai. 20Amma wadan sunsu, mutane daga Kuburus da Kurane, suka zo Antakiya suka yi magana da hellenawa, suna yi masu wa'azin Ubangiji Yesu. 21Kuma ikon Ubangiji yana tare da su, har mutane da yawa suka gaskata kuma suka juyo wurin Ubangiji.22Labari game da su ya iso kunnen ikilisiya da ke Urushalima: sai suka aika da Barnaba zuwa can Antakiya. 23Da ya iso kuma ya ga kyautar Allah, sai ya yi farinciki; ya karfafa su dukka su kafu cikin Ubangiji da dukan zuciyar su. 24Domin shi mutumin kirki ne, cike kuma da Ruhu Mai Tsarki da bangaskiya, sai mutane da yawa suka karu ga Ubangiji.25Sai Barnaba ya tafi Tarsus domin ya nemi Shawulu. 26Da ya same shi, ya kawo shi Antakiya. Ya kasance, shekara guda suna taruwa tare da ikilisiya suka koyar da mutane da yawa. A Antakiya ne aka fara kiran almajiran Krista.27A cikin kwanakin nan wadansu annabawa daga Urushalima suka zo Antakiya. 28Daya daga cikinsu, mai suna Agabas ya mike tsaye yayi magana da ikon Ruhu cewa za a yi tsanani fari ko'ina a duniya. Wannan ya faru ne a zamanin Kalaudiya.29Sai, almajiran, suka dau niyya kowa gwargwadon karfinsa, su aika wa 'yan'uwa da ke Yahudiya da taimako. 30Suka yi haka; sun aika wa dattawa da kudi ta hanun Barnaba da Shawulu.
Bitrus ya iso Urushalima ya fara wa Yahudawa da ke wurin magana.
Wannan farƙon wata sabuwar hali ne a labarin.
Wannan na sa alamar wata sabuwar bangaren labarin.
Wato "'yan'uwa" na nufin masubi da ke cikin Yahudiya.
"waɗanda ke cikin yankin Yahudiya"
Wannan furci na nuna gaskiyar cewa Al'ummai ma sun gaskanta da sakon Yesu. AT: "sun gaskanta da sakon Allah game da Yesu"
...
Wannan na nufin wasu Yahudawa da sun gaskanta cewa dole ne a yi wa kowane mai bi kaciya. AT: "wasu Yahudawa masu bi a Urushalima da ke so dukan masubin Almasihu ya yi kaciya"
jimlar nan "mutane marasa kaciya" na nufin Al'ummai.
Al'addun Yahudawa ba su yarda Yahudawa su ci tare da Al'ummai ba.
Biitrus bai zarga abinda Yahudawa suka gaskanta da shi ba amma ya amsa masu ne a hanyar da za su gane.
"daidai abinda ya faru"
... Duba yadda aka juya wannan a [10:11]
"da kursuwansa guda huɗu a dakace" ko kuma "da kursuwansa huɗu a sama da sauransu" Duba yadda aka juya wannan a [10:11]
Daga amshin Bitrus, ya a iya ɗaukan cewa shari'ar Musa ya umarce Yahudawa kada su ci wasun su. Duba yadda aka fasara irin wannan jimlar a [10:12]. AT: "dabbobi da sunsaye da shari'ar Musa ya hana Yahudwa ci"
Wannan na iyan nufin dabbobi da mutane ba su iya kiwonso ko kuma bi da su ba.
Wato hallitu masu rarrafe kenan
Ba a ambaci mai maganan ba. Maiyiwuwa "muryar" kuwa na Allah ne, kodashike yana ma kuma iya zama mala'ikar Allah ne. Duba yadda aka fasara "murya" a [10:13]
"Ba zan yi haka ba" Duba yadda fasara wannan a [10:14]
Wannan a fili yake cewa dabbobin da ya gani dabbobi ne da dokar Yahudawa a Tsohon Alkawali ya hana Yahudawa ci. AT: "Ina cin naman tsarkakku da tsabatattun dabbobi ne kawai"
Bisa ga shari'ar Yahudawa na Tsohon Alkawali, mutum na iya zama "marar tsarki" ta hanyoyi da dama, kamar su cin haramtaccen dabbobi.
wato dabbobin da ke a mayafin kenan.
ka lallai ne cewa kome ya sake faruwa ne sau uku ba. Wannan na iya nufin "Abinda Allah ya tsarkake, kada ka kira shi mara tsarki. Kodashike, ya fi ma a saukake a ce "Hakan ya faru ne sau uku" a maimakon koƙarin bada dukkan labaran. Duba yadda aka fasara wannan a [10:16]
Wannan kalmar na jan hankalin mu ne zuwaga sabobin mutane a labarin. Mayiwuwa harshenku tana da wata hanyar yin haka.
"ba da batan lokaci ba" ko kuma "a dai dai lokacin"
AT: "wani ya aike su"
"cewa kada in damu da da cewa su Al'ummai ne"
"'Yan'uwan nan shida sun tafi tare da ni zuwa Kaisariya"
Waɗannan Yahudawa shida masubi"
Wato gidan Karniliyas.
...
AT: "Allah zai cece ku"
Wato dukkan mutanen da ke gidanka. AT: "kowan da ke gidanka"
Wannan na nufin cewa Bitrus bai gama magana ba, amma yana da da sauran magana.
Bitrus ya bar wasu abubuwa domin ya takaita labarin. AT: "Ruhu Mai Tsarkin ya sauko akan Al'ummai masubin, kamar yadda ya sauko akon Yahudawa masubi a ranar Fentikos"
Bitrus na nufin ranar Fentikos"
AT: "Allah zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki"
Bitrus na amfani ne da wannan tambayan don yă nanata cewa shi dai biyayya da Allah yake yi. AT: "Dashike Allah ya basu ... na zaɓi kada in yi gãba da Allah!"
Bitrus na nufin baiwar Ruhu Mai Tsarki.
"basu yi jayayya da Bitrus ba"
"Allah ya ba da tuɓa da ke kai ga rai wa Al'ummai suma." A nan "rai" nan nufin rai na har'abada. AT: "Allah ya bar Al'ummai su ma su tuɓa su rayu har'abada"
Yahudawa sun fãra sananta wa masubin Yesu domin Istifanus ya faɗi ya kuma aikata abubuwan da Yahudawa basu so ba. Saboda wannan tsanantawa, mabiyan Yesu da yawa sun bar Urushalima suka warwatsu zuwa wurare dabam dabam.
"suka tafi hanyoyi dabam dabam"
AT: "wanda Yahudawa ke tsananta masu saboda haka suka bar Urushalima"
tsanin da ya faru saboda abinda Istifanus ya faɗa ya kuma yi
Masubin sun ɗauka cewa maganar Allah domin Yahudawa ne kawai, ba domin Al'ummai ba.
Waɗannan Hallenawan Al'ummai ne, ba Yahudawa ba. AT: "suka yi magana da Al'ummai da suke Hallenanci ma"
Ikon Allah na nufin ikon taimakonsa. AT: "Allah yana iza waɗannan masubi su yi wa'azi"
A nan "juyo wa Ubangiji" karin magana ne da ke nufin fãra yi wa Ubangiji biyayya. AT: "sai suka tuɓa daga zunubansu suka fãra yi wa Ubangiji biyayya"
A nan "kunne" na nufin labarin abubuwan da suka faru da masubi sun ji. AT: "masubin da ke ikkilisiya"
"ga yadda Allah ya motsa cikin ƙauna domin masubi"
"ya riƙa ƙarfafasu"
"su kafu da aminci ga Ubangiji" ko kuma "su cigaba da dogara ga Allah"
A nan "zuciya" na nufin abinda mutum ke so ko marmarin. AT: "da dukkan son so" or "da mika kai gabaƙiɗaya"
Ruhu Mai Tsarki ne ya bi da Barnaba ya yi da yake biyayya da Ruhu Mai Tsarki.
A nan "karu" na nufin cewa sun gaskanta da Ubangiji kamar yadda sauran mutane. AT: "mutane masu yawan gaskiye su ma sun gaskata da Ubangiji"
"tafi birnin Tarsus"
Waɗannan kalamun na nufin cewa sun ɗauki lokaci sun kuma yi koƙari domin Barnaba ya same Shawulu.
Wannan na bada wata sabuwar abu da ya faru cikin labarin.
Barnaba da Shawulu suka taru tare da ikkilisiyar"
Wannan na nufin cewa sauran mutane suna kiran masubi da wannan suna. AT: "Mutanen Antakiya suka kira almajiran Kirista." Wato masu bin Yesu
"na farƙo a Antakiya"
Urushalima na sama da Antakiya ne a tadawa. Don haka, 'yan Isra'ila ma suna iya maganar haurowa zuwa Urushalima ko kuma saukowa da wurin.
"sunansa Agabus ne"
"Ruhu Mai Tsarki ya bishe shi yă yi anabci"
"za a yi wata babbar karancin abinci"
Wannan na nufin a yankin duniya da suka sani. AT: "a dukkan yankin duniya da mutane ke ciki" ko kuma "a Ɗaular Romawa gabaƙiɗaya"
Masu sauraron Luka za su san cewa Kaladiya shi ne sarkin Ɗaular Roma a wannan lokaci. AT: "a lokacin da Kalaudiya yana mulkin Ɗaular Roma"
Wannan kalma na nuna alamar abinda ya faru ta dalilin wani abinda ya faru tukuna. A wannan hali, sun turo koɗi domin anabcin Agabus ko kuma karancin abincin.
Waɗanda sun fi arziki suka aika da mai yawa, marasa arziki kuma suka aiko da kadan.
"masubin da ke Yahudiya"
Hannu wata karin magana ne da ke nufin abinda mutumin ya yi gabaƙiɗaya. AT: "ta wurin raƙiyar Barnaba da Shawulu"
1A lokacin nan Sarki Hiridus ya sa wa wasu masu bi hannu domin ya musguna masu. 2Ya kashe Yakubu dan'uwan Yahaya da takobi.3Bayan da ya ga hakan ya gamshi Yahudawa, sai ya kama Bitrus ma. 4Bayan ya kama shi, sai ya tsare shi a kurkuku ya kuwa sa sojoji hudu su dinga tsaron sa; yana niyyar kawo shi gaban mutanen a bayan Idin katarewa.5To, Bitrus na tsare a kurkuku, amma 'yan'uwa na iklisiya suna yin addu'a ga Allah sosai domin sa. 6Ana kamar gobe Hiridus zai fitar da shi, a wannan daren, Bitrus yana barci a tsakanin sojoji biyu, daure da sarkoki biyu; sojoji kuma na gadi a bakin kurkukun.7Ba zato, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana a gareshi, haske ya haskaka dakin. Ya taba Bitrus a gefe ya tashe shi kuma ya ce, "Tashi da sauri." Sai ga sarkokin suka zube daga hannunsa. 8Mala'ikan ya ce masa, "Yi damara ka sa takalmanka." Bitrus kuwa yayi haka. Mala'ikan ce ma sa, "Yafa mayafinka, ka biyo ni."9Bitrus kuwa ya bi mala'ikan suka fita waje. Bai gane abin da mala'ikan ke yi zahiri ne ba. Yana zaton ko yana ganin wahayi ne. 10Bayan da suka wuce masu tsaron fari da na biyu, sun kai kofar da aka yi da karfe wadda ta mike zuwa cikin gari; ta bude masu da kanta. Suka fita sun bi titin, kuma nan take kuma sai mala'ikan ya bar shi.11Da Bitrus ya komo hayyacin sa, ya ce, "Hakika yanzu na gane Ubangiji ya aiko da mala'ikansa don ya kubutar da ni daga hannun Hiridus da abin da Yahudawa suke zato." 12Da ya gane haka, ya zo gidan Maryamu mahaifiyar Yahaya wanda sunan mahaifinsa Markus; masu bi da yawa sun taru a can suna addu'a.13Da ya kwankwasa kofar gidan, sai baiwar gidan mai suna Roda ta zo don ta bude kofar. 14Da ta gane muryar Bitrus, don farin ciki ta kasa bude kofar; maimakon haka, ta koma daki a guje, don ta basu labari Bitrus na tsaye a bakin kofa. 15Suka ce mata, "Kin haukace." Amma ta nace da cewa haka ne. Suka ce, "Mala'ikansa ne."16Amma Bitrus ya ci gaba da kwankwasawa, da suka bude kofar, sai suka ga ai shine, suka sha mamaki kwarai. 17Bitrus kuwa ya yi masu hannu yana, masu alama su yi shuru. Sai ya gaya masu labarin yadda Ubangiji ya kubutar da shi daga kurkukun. Ya ce, "Ku gaya wa Yakubu da dukan 'yan'uwa abin da ya faru." Sai ya bar su, ya tafi wani wuri.18Sa'anda gari ya waye ba karamar hargowa ce ta tashi a cikin sojojin ba, game da abin da ya faru da Bitrus. 19Bayan da Hiridus ya neme shi kuma bai same shi ba, sai ya tambayi masu tsaron kuma ya bada umarni a kashe su. Sai ya gangara daga Yahudiya zuwa Kaisariya ya yi zamansa a can.20Yanzu kuwa Hiridus ya yi fushi sosai da mutanen Taya da Sidon. Suka tafi wurinsa tare. Suka roki Bilastasa, mataimakin sarkin, ya taimake su. Sai suka nemi sasantawa don suna samun abinci daga kasarsa ne. 21A ranan da aka kayyade, Hirudus ya sha damara da kayan saurata kuma ya zauna akan kursiyi; ya yi masu jawabi.22Mutanen suka yi ihu, "Wannan muryar allahce, ba ta mutum ba!" 23Nan take mala'ika Ubangiji ya buge shi don bai ba Allah daukaka ba, nan take tsutsotsi suka cinye shi har ya mutu.24Maganar Allah ta yadu tana ta ribabbanya. 25Bayan Barnaba da Shawulu sun gama aikin su a Urushalima. Suna dawowa, suka zo tare da Yahaya wanda sunan mahaifinsa Markus ne.
Wannan na ba da wata tsanantawa da aka fara da kisan Yakubu, sa'annan da ɗaurin Bitrus a kurkuku, da kuma sakin sa.
Wannan tarihi ne na Kisan Yakubu da Hiridus yayi.
Wannan na ba da wata sabuwar sashin labarin.
Wato lokacin babban yunwar.
Wannan na nufin cewa Hiridus ya kamo masubi. Duba yadda aka fasara wannan a [5:18] AT: "aike sojoji su kama"
Yakubu da Bitrus ne kawai aka ambata, wannan na nuna kenan cewa su ne shugabanen ikkilisiyar da ke Urushalima
"domin ya ba wa masubi su wahala"
Wannan na nuna yadda aka ƙashe Yakubu.
Wannan na iya nufin 1) Hiridus da kansa ne ya ƙashe shi ko kuma 2) Hiridus ne ya ba da doka cewa a ƙashe shi. AT: "Hiridus ne ya ba da doka sai suka ƙashe shi"
"Da Hiridus ya dago cewa kisan Yakubu ya gamshi shugabanin Yahudawa"
"ya sa shugabanin Yahudawa farin ciki"
"Hiridus ya yi haka" ko kuma "Hakan ya faru ne"
Wannan na nufin lokacin idin adinin keterewa na adinin Yahudawa. AT: "idin lokacin da mutanen Yahudawa sukan ci abinci marar yisti"
sojoji kashi huɗu." ko wane kashi suna na sojoji huɗu da suka yi tsaron Bitrus, kashi ɗaya bayan ɗaya. Suka raba yini ɗaya sau huɗu. A kowane lokaci, sijoji biyu na iya kasacewa da shi a ciki, sai sauran biyun a kofar shiga.
"Hiridus ya shirya ya yanke wa Bitrus hukunci a gaban jama'a" ko kuma "Hiridus ya shirya yanke wa Bitrus hukunci a ganan mutanen Yahudawa"
Wannan na nuna cewa sojojin sun ci gaba da tsare Bitrus a kurkuku. AT: "sojojin suka cigaba da tsaron Bitrus a kurkuku"
AT: "taron masu bi da ke Urushalima suka yi wa Allah addu'a sosai dominsa"
cigaba kuma tare da miƙa kai
Ana iya kara bayyana cewa Hiridus ya yi niyya yă ƙashe shi. AT: "Hakan ya faru ne kamar gobe Hiridus zai fitar da Bitrus daga kurkuku domin hukunci, sa'annan ya ƙashe shi"
"a kafe da sarƙoki biyu." Yana iya zaman cewa kowane sarka na haɗe a hannun masu tsaro da ke tsaye a hago da manar Bitrus.
"na tsaron kofofin kurkukun"
Wannan kalma na jan hankalin mu ne mu kassa hankalin mu ga abin ban mamaki da ke biye da shi.
"kusa da shi" ko kuma "a gefensa"
"cikin ɗakin kurkukun"
"Mala'ikan ya tashe Bitrus" ko kuma "Mala'ikan ya zungure Bitrus." Ba shakka Bitrus yana wata matuƙar barci ne da ya zama lallai mala'ikan ya tashe shi.
Mala'ika ya sa sarkokin suka zuɓe daga hannayen Bitrus ba tare da ya taɓa su ba.
"Bitus kuwa ya yi abinda mala'ikan ya ce yă yi" ko kuma "Bitrus ya yi biyayya"
"Bai fahimci"
AT: "abinda mala'ikan ya yi ya faru da gaske ne ba"
Wannan na nuna cewa sojojin basu iya ganin Bitrus da mala'ikan yayin da suke wucewa su ba. AT: "Masu tsaron kofa na fari da na biyu basu gansu yayin da suke wuce su ba, sa'annan
...
Ana iya fahimci kalmar nan "masu tsaro" daga jimla da ke baya. AT: "da kuma masu tasro na biyun"
"Bitrus da malaikan suka iso ƙofar ƙarfe"
"wanda ke buɗe zuwa cikin birnin" ko kuma "wanda ya miƙe daga gidan kurkukun zuwa cikin garni"
A nan "da kanta" na nufin tsakanin Bitrus da mala'ikan ba wanda ya buɗe ƙofan. AT: "kofar ta yi lilo ta buɗu da kanta" ko kuma "kofar ta buɗe kanta domin su"
"suka yi tafiya a wata titi"
"ya barshi nan da nan" ko kuma "ya ɓace nan da nan"
Wannan karin magana ne. "Da Bitrus ya komo hankalinsa" ko kuma "Da Bitrus ya tuna cewa abinda ya faru zahiri ne"
A nan "hannun Hiridus" na nufin "riƙon Hiridus" ko kuma "shirin Hiridus." AT: "ya cire ni daga mummunan shirin da Hiridus ke da shi dominna.
"ya cece ni"
A nan "Yahudawa" na iya nufin shugabanin Yahudawa. AT: "dukkan abinda Yahudawa sun aza zai faru da ni"
Ya zo ga sanin cewa Allah ya cece shi.
A nan kiran Yahaya ma Markus. AT: "Yahaya, wadda mutane ke kiransa Markus"
"Bitrus ya ƙwanƙwasa." Taɓa ƙofa wata al'ada ne na yau da kullum a Yahudanci da ke sa mutane su san cewa an zo masu fatan ziyara. Kuna iya canza wannan ya yi daidai da al'adan ku.
"ƙofar shiga gidan" ko kuma "ƙofar shiga daga kan titi zuwa hařabar gidan"
Ta zo ƙofar ta tambaya wa ke ƙwanƙwasawa"
"saboda matuƙar farin ciki" ko kuma "cike da farin ciki"
"bata buɗe kofar ba" ko kuma "ta manta ta buɗe kofar"
Ka iya so ma ce "wurga da gudu zuwa cikin ɗaki da ke gidan"
"ta faɗa masu" ko kuma "ta ce"
"tsaye a wajen ƙofar." Har yanzu Bitrus na nan tsaye a waje.
Mutanen ba kadai sun ƙi yarda da ita ba, amma suka tsauta mata cewa tana hauka. AT: "kina hauka"
"ta nace cewa abinda ta faɗa gaskiya ne"
"suka amsa"
"Abinda kin gani, malaikan Bitrus ne." Wasu Yahudwa sun gaskanta da mala'iku masu tsaro, saboda haka me yiwuwa suna ɗaukan cewa mala'ikan Bitrus ne ya zo wurinsu.
Kalmar nan "ci gaba" na nufin cewa Bitrus ya riƙa ƙwanƙwasawa duk loƙacin da mutanen cikin nan suna ta magana.
"faɗa masu waɗannan abubuwan"
"sauran masubi"
"da safe"
A nan amfani ne da wannan jimlar don a nanata zahirin abinda ya faru. AT: "an samu wata babbar hargowa a cikin sojojin game da abinda ya faru da Bitrus"
"Bayan da Hiridus ya neme Bitrus bai iya samun shi ba"
Wannan na iya cewa 1) "da Hiridus ya ji cewa Bitrus ya bata, ya je da kansa ya neme shi a kurkuku" ko kuma 2) "da Hiridus ya ji cewa Bitrus, ya aike sauran sojojin su duba kurkukun."
A mulkin Roma, hukuncin da ake ba wa masu taron kurkuku idan wani daga kurkuku ya gudu shi ne a ƙashe masu gadin gidan kurkukun.
An yi amfani ne da wannan kalmar "ya gangara" domin Kaisariya yana kasa da Yahudiya.
Ba lallai ne ake nufin dukkan mutanen Taya da Sidon sun tafi wurin Hiridus. AT: "Wakilai na mutanen Taya da Sidon sun tafi tare domin su yi tattauna da Hiridus"
"Waɗannan mutanen sun roƙi Bilastasa"
Wannan mataimaki ne ko kuma wani babban jami'in soji na Sarki Hiridus"
"waɗannan mutanen sun nema zaman lafiya"
Mai yiwuwa suna sayan abincin ne ma. AT: "mutanen Taya da Sidon suna sayan dukkan abincin su daga wurin mutanen da Hiridus ke sarautar su ne"
A nan ɗaukan cewa Hiridus ya hana masu abincin ne domin yana fushi da mutanen Taya da Sidon.
Wannan na iya nufin ranan da Hiridus ya sa domin haɗuwa da wakilan. AT: "A ranar da Hiridus ya sa don ya haɗu da su"
tufafi ne masu yawan sada da za su nuna cewa shi ne sarkin.
wato wurin da Hiridus ya shirya ya yi wa mutanen da suka zo ganin sa Jawabi.
"ba da jimawa ba" ko kuma "Yayin da mutanen suna kan yabon Hiridus, mala'ika"
"ya wa Hiridus hari" ko kuma "sa Hiridus ya zama da rashin lafiya sosai"
Hiridus ya bar mutanen nan su yi yi masa sujada a maimakon ya ce masu su yi wa Allah sujada.
A nan "tsutsotsi" na nufin tsutsotsin da ke cikin jiki, maiyiwuwa tsutsosin hanji. AT: "tsutsotsi suka cinye cikin Hiridus har ga mutuwa"
AT: "Maganar Allah kuwa ta bazu zuwa wurare da dama kuma mutane da yawa sun gaskanta da shi."
"sakon da Allah ya aika game da Yesu"
Wannan na nufin lokacin da suka kawo kuɗi daga masu bi da ke Antakiya a [11:29-30]. AT: "suka danka kuɗaden zuwa ga shugabanin ikkilisiyar da ke Urushalima
Suka komo Antakiya daga Urushalima. AT: "Barnaba da Shawulu suka komo Antakiya"
1A cikin iklisiyar da take Antakiya, akwai annabawa da malamai. Sune su Barnabas, Saminu (wadda ake kira Baki) da Lukiya Bakurame da Manayin (wanda aka yi renon su tare da sarki Hiridus mai mulki) da Shawulu. 2Sa'adda suke bauta wa Allah tare da azumi, sai Ruhu Mai Tsarki ya ce, "Ku kebe mani Barnaba da Shawulu domin aikin da na kiraye su". 3Bayan taron sun yi addu'a da azumi, sai suka sa masu hannu, su suka sallame su.4Sai Shawulu da Barnabas suka yi biyayya da Ruhu Mai Tsarki suka tafi Sulukiya; daga nan suka ketare zuwa tsibirin Kuburus. 5Sa'adda suke garin Salami, suka koyar da maganar Ubangiji a majami'un Yahudawa, suna kuma tare da Yahaya Markus mai taimakonsu.6Bayan sun zaga tsibirin duka har Bafusa, nan suka iske wani Bayahude mai suna Bar-yeshua mai tsafi kuma annabin karya. 7Wannan mai tsafin wanda ke tare da Makaddas, shi Sarjus Bulus mutum mai basira ne. Wannan kuwa ya kira Shawulu da Barnaba domin yana so ya ji maganar Allah. 8Amma Elimas "mai tsafi" (fasarar sunansa kenan) ya yi adawa da su; yana so ya baudar da Makaddashin daga bangaskiya.9Amma Shawulu wanda ake ce da shi Bulus yana cike da Ruhu Mai Tsarki ya kafa masa ido. 10Sai ya ce, "Kai dan iblis, kana cike da kowace irin yaudara da mugunta. Kai abokin gabar kowanne irin adalci ne. Ba za ka daina karkata mikakkakun hanyoyin Ubangiji ba?11Yanzu ga hannun Ubangiji bisa kanka, zaka zama makaho. Ba za ka ga rana ba nan da dan lokaci." Nan take kuwa sai wani hazo da duhu suka rufe shi ya fara yawo yana neman mutane su yi masa jagora. 12Bayan da Makaddashin ya ga abin da ya faru ya ba da gaskiya saboda ya yi mamakin koyarwa game da Ubangiji.13Bulus da abokansa suka shirya suka ketare a jirgin ruwa daga Bafusa zuwa Firjiya a Bamfiliya. Amma Yahaya ya bar su ya koma Urushalima. 14Bulus da abokansa suka tafi daga Firjiya zuwa Antakiya na kasar Bisidiya. Nan suka shiga majami'a ran Asabaci suka zauna. 15Bayan karatun dokoki da annabawa, shugabanin iklisiyar suka tura sako cewa, "'Yan'uwa, idan kuna da wani sakon karfafawa ga jama'a ku fadi."16Bulus kuwa ya tashi ya yi alama da hannunsa ya ce, "Mutanen Isra'ila da ku wadanda kuke girmama Allah, ku ji. 17Allahn Isar'ila ya zabi kakkaninmu ya kuma ribabbanya su sa'adda suke kasar Masar da kuma madaukakin iko ya fito da su daga cikinta. 18Ya yi hakuri da su a jeji har na tsawon shekara arba'in.19Bayan ya hallaka kasashe bakwai a kasar Kan'ana, ya ba kakkaninmu kasar nan gado. 20Duk wadanan abubuwan sun faru shekaru dari hudu da hamsin da suka wuce. Bayan wadannan, Allah ya ba su alkalai har sai da annabi Sama'ila ya zo.21Sai jama'a suka roka a ba su sarki, Allah kuwa ya ba su Saul dan Kish, mutumin kabilar Binyamin ya zama sarki har na tsawon shekara arba'in. 22Allah kuwa ya cire shi daga kan kujerar sarauta, ya daga Dauda ya zama sarkinsu. A kan Dauda ne Allah ya ce, 'Na sami Dauda dan Yessi, mutumin da zuciyata ke so; zai yi duk abin da nake so'.23Daga zuriyar mutumin nan Allah ya fito da mai ceto, Yesu, kamar yadda aka alkawarta zai yi. 24Wannan ya faru kafin Yesu ya zo, Yahaya ya yi shelar baftimar tuba ga jamma'ar Isra'ila. 25Sa'adda Yahaya ya gama aikin sa, sai ya ce, 'Wanene ni a tsamanin ku? Ba nine shi ba. Amma ku saurara, akwai wani mai zuwa bayana wanda maballin takalminsa ban isa in kwance ba.'26Yan'uwa 'ya'ya daga zuriyar Ibrahim, da wadanda ke bautar Allah a cikinku, saboda mune aka turo sakon ceto. 27Saboda wadanda ke zaune cikin Urushalima, da masu mulkinsu, ba su gane shi ba, kuma sun cika fadin annabawa da a ke karantawa kowace ranar Asabaci ta wurin kashe shi.28Duk da cewa ba su sami dalilin mutuwa a kansa ba, suka roki Bilatus ya kashe shi. 29Bayan sun gama duk abin da aka rubuta game da shi, sai suka sauke shi daga giciye suka sa shi a cikin kabari.30Amma Allah ya tashe shi daga matattu. 31Mutanen da suka zo tare da shi daga Galili da Urushalima kuwa suka yi ta ganinsa har kwanaki da yawa. Wadanan mutane kuma sune shaidunsa ga jama'a a yanzu.32Mun kawo maku labari mai dadi game da alkawaran da aka yi wa kakkaninmu. 33Ubangiji ya bar mana alkawaran. Don haka ya ta da Yesu daga matattu. Kamar yadda ya ke a littafin zabura ta biyu: "Kai da na ne yau na zama mahaifinka." 34Kuma dalilin tayar da shi daga matattu shine saboda kada jikinsa ya rube, ya yi magana kamar haka: "Zan baku albarkun Dauda masu tsarki tabatattu."35Wannan shine dalilin da ya yi magana kuma a wata Zabura, 'Ba za ka bar Mai Tsarkinka ya rube ba.' 36Bayan Dawuda ya yi wa Allah bauta a cikin zuciyarsa da kuma abin da Allah yake so, ya mutu, aka binne shi tare da kakkaninsa, ya kuma ruba, 37amma wanda Allah ya tayar bai ga ruba ba.38'Yan'uwa, ku sani cewa ta wurin mutumin nan aka yi maku wa'azin gafarar zunubai. 39Ta wurinsa ne duk wanda ya ba da gaskiya zai kubuta daga dukan abin da dokar Musa bata 'yantar da ku a kai ba.40Saboda haka ku yi hankali da abubuwan da annabawa suka fada kada su faru a kanku: 41'Ku masu reni, za ku rude don mamaki, ku kuma shude; saboda ina aiki a cikin kwananakinku, aikin da ba za ku yarda ba ko da wani ya gaya maku."42Da Bulus da Barnaba suna fita kenan, sai jama'a suka rokesu, su sake yin irin wannan magana ranar Assabaci mai zuwa. 43Bayan da sujadar ta kare, Yahudawa da yawa da kuma wadanda suka shiga addinin Yahudanci suka bi Bulus da Barnaba, sai suka gargade su da su cigaba da aikin alherin Allah.44Da Asabaci ta kewayo, kusan dukan garin suka taru domin su ji maganar Ubangiji. 45Sa'adda Yahudawa suka ga taron jama'a, sai suka cika da kishi suna karyata abubuwan da Bulus ya fada suka kuma aibata shi.46Amma Bulus da Barnaba sun yi magana gabagadi suka ce, "Dole ne a fara fada maku maganar Allah. Amma da yake kun ture ta, kun nuna baku cancanci rai madawwami ba soboda haka zamu juya ga al'ummai. 47Don haka Ubangiji ya umarce mu, cewa, 'Na sa ku haske ga al'ummai, saboda ku kawo ceto ga iyakar duniya.'"48Da al'ummai suka ji haka, sai suka yi murna suka kuma yabi kalmar Ubangiji. Dukan wadanda aka kaddarawa samin rai madawwami suka tuba. 49Kalmar Ubangiji kuwa ta bazu a kowanne bangaren yankin.50Amma Yahudawan suka zuga wadansu mata masu sujada, masu daraja da kuma shugabannin mazan garin. Wannan ya tayar da tsanani ga Bulus da Barnaba har suka fitar da su daga iyakar garinsu. 51Amma Bulus da Barnaba suka kade masu kurar kafarsu. Suka tafi garin Ikoniya. 52Amma almajiran suka cika da farin ciki da kuma Ruhu Mai Tsarki.
Luka ya fara faɗin aikin tafiye tafiye da ikkilisiyar Antakiya sun turo Barnaba da Shawulu su je.
Aya 1 na ba da tarihin mutanen da ke ikkilisiyar Antakiya.
"A wannan lokacin a ikkilisiyar da take Antakiya"
Waaɗannan sunayen maza ne
Maniyan mai yiwuwa abikin wasane na Hiridus ko kuma abokin na kusa da suka yi girma tare.
"Zaɓa domin su yi mani aiki"
Wannan na nufin cewa Allah ya zaɓe su domin su yi wannan aiki.
"suka sa wa mutanen nan da Ubangiji ya keɓe domin hidimarsa hannu." Hakan ya nuna cewa shugabanin su amnice cewa Ruhu Mai Tsarki ne ya kiraye Barnaba da Shawulu su yi wannan aiki.
"suka sallame waɗannan mutanen" ko kuma "suka sallame waɗannan mutanen so je su yi aikin da Ruhu Mai Tsarki ya ce su yi"
Wannan kalmar tana sa alamar wani abinda ya faru ne ta dalilin abinda ya bi baya. A wannan hali, Barnaba ne da Shawulu Ruhu Mai Tsarki ya keɓe.
Sulukiya tana kasa da Antakiya.
wata gari ne kusa da teku
Garin salamis tana kan tsibirin Kuburus.
"Maganar Allah" anan karin magana ne da ke nufin "sakon Allah" AT: "Shelar maganar Allah"
Wannan na iya nufin cewa 1) "akwai majami'u da yawa a birnin Salami wurin da Barnaba da Shawulu suka yi jawabi" ko kuma "2) "Barnaba da Shawulu sun fara daga majami'a da ke Salami ne kamun suka ci gaba da bishara a dukkan majami'un da sun samu yayin da suka yi tafiyi a yankin tsibirin Kuburus"
"Yahaya Markus ya je tare da su yana kuma taimakon su"
...
Sun haye daga ɗayan hayin tsibirin suka yada bishara a kowane gari da suka bi.
wata babar birnin da ke tsibirin Kuburus inda muƙaddas suke
A nan "iske" na nufin sun zo wurin ba tare da shirin neman sa ba. AT: "suka haɗu" ko kuma "suka same"
"wani mutum mai yin maita" ko kuma "wani mutum mai da ya gwaninta a yin sihiri"
Bar-yeshua" na nufin "Ɗan Yesu." Babu wani dangartaka tsakanin wannan mutumin da Yesu Almasihu. Ba wuya a samu masu suna Yesu a wannan lokaci.
...
Wato shugaban da ke mulkin lardin Roma. AT: "shugaba"
Wannan ita ce tarihin Sajus Bulus.
"Maganar Allah" wata karin magana ce mai nufin "sakon Allah" AT: "yana so ya ji sako daga Allah"
Wato Bar-Yeshua kenan da akan ce da shi "mai tsafi"
"haka ake kiransa a Hallenanci"
"ya yi gãba da su, ta wurin ƙokarin bauɗar" ko kuma "ya yi ko kuma "ya yi ƙokarin hana su ta wurin"
A nan "bauɗar ... daga" karin magana ne da ke nufin a rinjaye mutum kada ya yi wani abi. AT: "yi ƙokarin rinjayan shugaban ya ki gaskata da wa'azin bishara"
"Shawulu" ne sunar sa a Yahudanci, kuma "Bulus" itace sunar sa a harshen Roma. Dashike yana magana ne da ma'aikacin gwamnatin Roma, ya yi amafani ne da sunarsa a harshen Roma. AT: "Shawulu da ke kiran kansa Bulus"
"ya zuba masa ido"
Bulus yana cewa mutumin yana yi kamar ibilis. AT: "Kai kamar ibilis ne" ko kuma "Kana yi kamar ibilis"
"kana da niyyar sa mutane su gaskanta da abinda ba gaskiya ba ta wurin ƙarya da riƙa aikata abinda ba daidai ba"
A wannan hali na nufin kyuya da rashin rashin ƙwazon bin maganar Allah"
Bulus yana kasa Elimas da ibilis ne. Yadda ibilis yana gãba da Allah, da kuma adalci, haka ma Elima.
Bulus yana amfani ne da wannan tambayan domin ya tsauta wa Elima saboda yin gãba da Allah. AT: "kana riƙa musunta gaskiya game da Ubangiji Allah cewa ƙarya ne"
A nan "miƙaƙƙun hanyoyi" na nufin hanyoyi masu gaskiya. AT: "hanyoyin gaskiya na Allah"
A nan "hannu" na nufin &&&&&&&&&&
AT: "Allah zai sa ka makance"
Elizama zai zama makaho gabaɗaya da ko rana ba zai iya gani ba. AT: "Ko rana ba za ka iya gani ba"
"ba ɗan lokaci" ko kuma "har lokacin da Allah ya zaɓa"
"idanun Elimas suka zama wani iri har sun yi duhu" ko kuma "Elimas ya fara gani kadan kadan har bai iya ganin kome kuma ba"
"Elimas ya ɓata"
"ya ba da gaskiya ga Yesu"
AT: "koyarwa game da Ubangiji ya bashi mamaki kwarai"
Wannan na nuna wata sabuwar bangaren labarin.
"suka yi tafiya a jirgin ruwa daga Paphos"
"iso Firjiya da ke Bamfiliya"
"Amma Yahaya ya bar Bulus da Barnaba"
"birnin Antakiya yana lardin Bisidiya"
"dokoki da annabawa" na nufin bangaren litattafan Yahudawa da aka karana. AT: "Bayan wani ya yi karatu daga litattafan attaura da kuma rubuce rubucen annabawa"
"suka ce wa wani ya faɗa" ko kuma "suka gaya wa wani ya ce"
Mutanen majami'a suna amfani ne da wannan kalma "'yan'uwa" don su nuna cewa Bulus da Barnaba suma Yahudawa ne.
"idan kuna da wani abun faɗi ku ƙarfafa mu"
"muna roƙo ku faɗi" ko kuma "muna roƙo ku gaya mana"
Wannan na iya nufin cewa ya motsa hannun sa yă nuna cewa ya yi shirin yin magana. AT: "ya motsa hannunsa yă nuna cewa zai yi magana"
Wannan na nufin Al'ummai da suka tuɓa zuwa adinin Yahudanci. AT: "ku da ba Isra'ilawa ba amma kuna wa Allah ibada"
"Allah, ku saurare ni" ko kuma "Allah, ku saurare abinda zan faɗa"
"Allahn da mutanen Isra'ila ke bauta wa"
...
"ya sa sun kara yawa sosai"
Wato ƙarfin ikon Allah.
"ya fito da su daga Kasar Masar"
Wannan na nufin "ya jure da su." Wasu juyi suna da wata kalma daban da ke nufin "ya kula da su." AT: "Allah ya jimre da rashin biyayyan su" ko kuma "Allah ya kula da su"
A nan kalmar nan "kasashe" na nufin kungiyoyin mutane dabandaban ba yanki ko iyakar kasa ba.
"ɗauki sama da shekaru 450 da ƙarewa.
"har zuwa lokacin annabi Samaila"
"zama tsarkinsu har na tsawon shekara arba'in"
Wannan ambacin na nufin Allah ya sa Shawulu ya daina zama sarki. AT: "ya ƙi Bulus daga zama sarki"
"sarkin Isra'ila" ko kuma "sarki a bisa Isra'ilawa"
"Allah ya ce game da Dauda"
"na na gãne da cewa"
Wannan furcin na nufin cewa "mutum ne da ke son abinda Ni ma ina so."
"Daga Zuriyan Dauda." An saka wannan a farkon jimalan ne domin a nanata cewa lallai ne mai ceton ya zama wani daga zuriyan Dauda. (Dubi: [13:22])
Wato jama'ar Isra'ila kenan. AT: "ba wa jama'ar Isra'ila"
"kamar yadda Allah ya alkawarta zai yi"
AT: "baftismar yin tuba" ko kuma "baftismar da mutane ke roƙa a masu idan suna so su tuba daga zunubansu"
Yahaya ya yi wannan ta tambayan ne domin ya sa mutane su yi tunanin ko shi wanene. AT: "Yi tunani ko ni wanene"
Yahaya yana magana ne game da Almasihu, wadda a ke zaton zuwansa. AT: "Ba nine Almasihu ba"
Wannan yana nanata muhimmancin maganar da zai biyo baya.
Wato Almasihu kenan. AT: "Almasihu zai zo ba da jimawa ba"
"Ni ban isa in kwance takalminsa ba." Shi Almasihu ɗin ya fi Yahaya daraja har ma bai ji ya isa ya yi mafi kaskancin abu masa ba.
Bulus yana ba da wannan jawabin ga masu sauraronsa tubabbun Yahudawa da Hallenawa ne domin ya tunashe su game da masayinsu ta musamman a matsayin masu bauta wa Allah na gaskiya.
AT: "Allah ya turo da sakon wannan ceton"
AT: "cewa Allah zai cece mutane"
"ba su gãne cewa wannan mutumin Yesu shi ne wanda Allah ya turo yă cece su"
A nan "faɗin" na nufin sakon annabawan. AT: "rubuce rubucen annabawa" ko kuma "sakon annabawan"
AT: "da mutum ke karantawa"
"sun kuwa yi daidai abinda annabawan sun ce za su yi a cikin litattafan annabawan"
"ba su sami wani dalilin da za sa s kashe Yesu ba"
Kalmar "roƙi" anan kalma ne mai ƙarfi da ke nufin a nuna buƙata, roƙo, neman izini.
"Bayan da sun gama yi wa Yesu dukkan abubuwan da annabawa suka ce za su faru da shi"
Za zama da taimako a ce Yesu ya mutu kamun hakan ya faru. AT: "suka kashe Yesu sa'annan suka sauke shi daga giciyen bayan da ya mutu"
...
"Amma" na nuna wata babbar banbanci tsakanin abinda mutanen suka yi da abinda Allah ya yi.
"ya tashe shi daga cikin waɗanda sun mutu." "Yă kasance da mattu na nufin cewa Yesu ya riga ya mutu.
A nan, a tashe shi karin magana ne na sa wanda ya mutu yă rayu kuma. AT: "ya sa shi ya rayu kuma"
Daga cikin dukkan waɗanda sun riga sun mutu. Wannan furucin na bayyana dukkan matattu gabaɗaya da ke karkashin kasa. A tayar da mutum daga cikin su na maganar cewa mutumin na da rai kuma.
AT: "Almajiran da suka yi tafiya tare da Yesu daga Galili zuwa Urushalima suka ga Yesu har kwanaki da yawa"
Mu dai sani daga wasu rubuce rubuce cewa wannan kwanaki 40 ne. Fasara "kwanaki da yawa" da kalmar da zai yi daidai da wannan tsawon lokacin.
"su ne yanzu suna shaida wa mutane game da Yesu" ko kuma "sune yanzu suna gaya wa mutane game da Yesu"
Allah ya cika mana waɗannan alkawaran da ya yi wa kakkanninmu"
"mu" waɗanda muke 'ya'yan kakkanin mu." Bulus yana magana ne da tubabbun Yahudawa da Al'ummai da ke majami'ar da ke Antakiya na garin Pisidiya. Waɗannan su ne kakkanin Yahudawa na jiki, da kuma kakkanin tubabbun a ruhu.
A nan tayar wa wata karin magana ne na sa mutumin da ya mutu ya tashi kuma. AT: "taurin sa Yesu ya tashi kuma"
"Haka aka rubuta a cikin Zabura ta biru"
"Zabura 2"
Waɗanan wasu laƙabi ne da ke bayyana dangartakan da ke tsakanin Yesu da Allah.
"Allah ya yi magana haka game da rayar da Yesu kuma ne domin kada ma yă sake mutuwa kuma"
"tabbacin albarku"
Masu sauraron Bulus na iya fahimtar cewa wannan Zaburan na magane ne game da Almasihu. AT: "A wata Zaburan Dauda, ya yi magana game da Almasihu"
"Dauda ya kuma ce." Dauda ne marubucin Zabura 16 inda aka ruwaito wannan.
AT: "Ba za ka bar jikin Mai Tsarkinka ya ruɓa ba"
Dauda yana magana da Allah ne anan.
"a lokacin da yake ruyuwa"
"ya yi abinda Allah ya so yayi" ko kuma "ya yi abinda ya gamshi Allah"
...
"aka binne shi tare da kakkaninsa da suka mutu"
Wannan jimlar "ya kuma ruɓa" na nufin "jikinsa ya ruɓa." AT: "jikinsa kuwa ya ruba"
"amma Yesu wanda"
A nan a tayar wata karin magana ne da ke sa wanda ya mutu ya yi rai kuma. AT: "Allah ya sa ya rayu kuma"
Wannan jimlar "bai ga ruɓa ba" wata hanya ce na cewa "bai ruɓa ba"
"ku san wannan" ko kuma "wannan na da muhimmanci ku sani"
AT: "cewa mun fada maku cewa ana iya gafarta maku zunuban ku ta wurin Yesu ne"
AT: "cewa Allah na iya gafarta zunubanku"
"Ta wurinsa ne duk mutumin da ya ba da gaskiya" ko kuma "Duk wanda ya ba da gaskiya gare shi"
AT: "Yesu yana kubutar da duk wanda ya ba da gaskiya"
"dukan zunubai"
A nan daukan cewa abinda za su yi hankali da shi itace sakon Bulus. AT: "ku ba da hankalinku ga abinda na faɗa maku"
"saboda abinda da annabawa sun yi magana akai"
"ku 'yan adawa"
...
"ku kuma mutu"
"ina yin wani abu" ko kuma "ina wata hidima"
"a zamaninku"
"In yin wani abu wanda"
"ko da wani ya faɗa maku game da shi"
"Da Bulus da Barmaba suna fitowa kenan"
...
A nan "magana" na nufin jawabin da Bulus ya yi. AT: "wannan jawabin"
Wannan na iya nufin 1) wannan na ƙarin bayyani akan "Da Bulus da Barnaba suna fita kenan" a aya 42 ko kuma 2) Bulus da Barnaba sun bar taron kamun a tashi, sa annan wannan ya faru ne nan gaba.
Waɗannan ba Yahudawa ba ne amma sun tuba zuwa adinin Yahudanci.
"sai Bulus da Barnaba suka yi magana da su suka gargaɗe su"
Ana ɗaukan cewa sun gaskanta ne da jawabin Bulus cewa Yesu Almasihu ne. AT: "da su cigaba da gaskanta cewa Allah yana gafarta zunuban mutane saboda abinda Yesu ya yi ne"
"garin" anan na madadin jama'ar da ke garin. Wannan jimlar na nuna matukar shigar kalmar Ubangiji a wannan gari. AT: "kusan duka mutanen garin"
Ana ɗaukan cewa Bulus da Barnaba ne suka yi maganar Ubangiji. AT: "domin su saurare Bulus da Barnaba suna magana game da Ubangiji Yesu"
A nan "Yahudawa" na nufin shugaban Yahudawa. AT: "shugaban Yahudawa"
A nan ana maganar kishi kamar wani abu ne da ke iya cika mutum. AT: "suka zama da kishi"
"musunta" ko kuma "yi gãba"
...
Ana ɗaukan cewa Allah ya umarta ayi haka. AT: "Allah ya Umarta"
AT: "maganar Allah" anan na nufin "sako daga Allah" AT: "mu fara faɗa maku wannan sako daga Allah tukuna" ko kuma "mu fara faɗa maka wannan maganar Allah tukuna"
"kun nuna baku cancanci rai na har abada ba" ko kuma "kuna yi kamar baku cancanci rai madawwami ba"
"za mu tafi gun Al'ummai" Bulus da Barnaba suna cewa za su kai wa Al'ummai bishara. AT: "za mu bar ku mu fara wa Al'ummai bishara"
Ana maganar gaskiya game da Yesu ne kamar wani hasken wuta ne da mutane ke iya gani.
Kalmar nan "iyaka" na nufin ko ina. AT: "gaya wa mutane da ke ko ina a cikin duniya cewa ina so in cece su"
Kalmar nan "iyaka" na nufin ko ina. AT: "gaya wa mutane da ke ko ina a cikin duniya cewa ina so in cece su"
A nan "kalmar" na nufin sako game da Yesu da suka gaskata da shi. AT: "suka kuma yabi Allah don sakon da suka ji game da Ubangiji Yesu"
AT: "Dukan waɗanda Allah ya kaddarawa samin rai na har abada sun gaskata" ko kuma "Dukan waɗanda Allah ya zaɓa su sami rai madawammi"
A nan "kalmar" na nufin sako game da Yesu. AT: "Waɗanda sun gaskanta suka yada kalmar Ubangiji zuwa ko ina a yankin" ko kuma "Waɗanda sun gaskanta suka tafi ko ina a yankin suna gaya wa mutane sakon Yesu"
"shawo kan" ko kuma "yaudare"
"mutane mafi daraja"
"Suka shawo kan shugabannin maza da mata su tsananta wa Bulus da Barnaba"
"suka fitar da Bulus da Barnaba daga garinsu"
Wannan alama ce na nuna wa marasabin cewa Allah ya ƙi si kuma zai hukunta su.
Wannan na iya nufin sabobin tuɓa da ke garin Antakiya a garin Fisidiya wurin da Bulus da Sila suka fito bari.
1A lokacin da Bulus da Barnaba sun shiga garin Ikoniya suka shiga majami'an Yahudawa suka yi wa'azi yadda har mutane da yawa daga cikin Yahudawa da Hellinawa suka ba da gaskiya. 2Amma Yahudawa da basu yi biyayya ba, suka zuga al'umman har suka yi fushi da 'yan'uwan.3Suka zauna a wurin na tsawon lokaci, suna yni maganarsu gabagadi da ikon Ubangiji, yana kuma shaidar sakon alherinsa. Ya yi wannan ta wurin alamu da al'ajibai ta hannun Bulus da Barnaba. 4Saboda haka mutanen garin sun rabu: wadansun su suka bi ra'ayin Yahudawa, wasu kuwa sun bi manzannin.5Al'umman garin da Yahudawa sun nemi jan hankali shugabanninsu, don su wulakanta Bulus da Barnaba, su jajjefe su, 6da suka gane haka suka gudu zuwa biranen Likoniya, Listira da Darbe, da garuruwa wadanda ke kewaye da su, 7a can suka yi wa'azin bishara.8A Listira akwai wani wanda ke zaune bai taba tashi da kafafunsa ba, don shi gurgu ne tun daga haihuwa. 9Wannan mutumin ya ji Bulus yana magana. Bulus ya kafa masa ido, ya gane mutumin na da bangaskiya da za a warkar da shi. Sai ya ce masa da murya mai karfi, "Tashi ka tsaya akan kafafunka" 10Sai mutumin ya yi tsalle ya fara tafiya da kafafunsa, yana yawo.11Da jama'an garin sun ga abin da Bulus ya yi, suka tada muryarsu suna cewa da Likoniyanci, "Ai alloli sun ziyarce mu daga sama, da kamanin mutane." 12Suna kiran Barnaba da sunan "Zafsa," Bulus kuwa suka kira shi da sunan "Hamisa" domin shine yafi yin magana. 13Sai firist din zafsa wanda dakin yin masa sujada na kofar birni; ya kawo bijimai biyu da furannin da aka saka su kamar gammo; shi da jama'arsa suna so su yi masa hadaya.14Amma da manzannin, wato Barnaba da Bulus, su ka ji labarin, suka yage rigunansu, suka hanzarta zuwa gun taron mutanen. 15Suna ta cewa, "Kuji! Ku mutane don me kuke wannan abin? Mu fa mutane ne kamarku. Mun kawo maku labari mai dadi ne, da cewa, ku rabu da abubuwa marar amfani, ku koma ga Allah mai rai, wanda ya hallici sama da kasa da teku da dukan abubuwa da ke cikinsu. 16A da dai ya bar mutane su yi abinda suka ga dama.17Duk da haka, bai bar kansa ba tare da shaida ba, don yana bada abubuwa masu kyau, yana ba ku ruwan sama, lokatai masu albarka, ya cika ranku da abinci da farin ciki." 18Duk da wadannan kalmomin da kyar, Bulus da Barnaba suka iya tsayar da su daga yi masu hadaya.19Amma wasu Yahudawa daga Antakiya da wasunsu daga Ikoniya suka rinjayi tarun jama'ar. Suka jajjefi Bulus suka ja shi zuwa wajen garin, suna ganin kamar ya mutu. 20Duk da haka da almajirai suka kewaye shi a tsaitsaye, sai ya tashi ya koma cikin garin. Washegari, ya tafi Darba tare Barnaba.21Bayan sun yi wa'azin bishara a wannan birnin suka kuma sami almajirai da yawa, suka dawo Listira, da Ikoniya da Antikiya. 22Suna karfafa zuciyar almajiran su rike bangaskiyarsu, su ci gaba da ita, suna ce masu, "Ta wurin jimrewa mai yawa zamu shiga mulkin Allah, don haka dole ne mu sha wahala."23Da suka zabar masu dattawa a kowace iklisiya, sai suka yi addu'oi da azumi, suka mika su ga Ubangiji, ga wanda suka gaskanta a gareshi. 24Sa'annan sun bi ta Bisidiya suka kai Bamfiliya. 25Da suka yi maganarsu a Biriya, sun wuce zuwa har Italiya. 26Ta jirgin ruwa zuwa Antakiya, a nan ne aka mika su ga alherin Allah don aikin da suka gama a yanzu.27Da isowarsu Antakiya sun tara 'yan iklisiya a wuri daya, sun ba da labarin dukan abin da Allah ya yi ta wurinsu. Da yadda Ya bude kofa a wurin al'ummai ta bangaskiya. 28Sun zauna tare da almajiran na tsawon lokaci.
An cigaba da ba da labarin Bulus da Barnaba a Ikoniya.
Wannan na iya nufin 1) "Sai ya kasance a garin Ikoniya cewa" 2) A garin Ikoniya kamar yadda aka saba"
"suka yi magana da ƙarfi sosai" Yana da taimako idan a sanar da cewa sun yi magane ne game da Yesu. AT: "suka yi magane game da Yesu sosai"
Wannan na nufin wasu Yahudawa da basu gaskanta da bisharar Yesu ba.
suka sa su fushi da abinda ake faɗi
aka zuga al'umman
A nan "'yan'uwan na nufin Bulus da Barnaba da kuma sabobin tuba.
"Duk da haka sun zauna a wurin" Bulus da Barnaba sun zauna a Ikoniya sun taimaki jama'a da dama da suka ba da gaskiya a [14:1]. Idan "Duk da haka" zai kawo wani rikicewa a harshen ku, ana iya cire shi kawai.
"ya nuna cewa sakon alherinsa gaskiya ne"
"game da sakon alherin Ubangiji"
AT: "ta wurin iza Bulus da Barnaba su yi alamu da al'ajibai"
A nan "hannu" na nufin ta koƙarin mutane biyun nan bisa ga bishewar Ruhu Mai Tsarki. AT: "ta hiddimar Bulus da Barnaba"
AT: "yawancin mutanen garin sumka raɓu" ko kuma "yawancin mutanen garin basu yařda da juna ba"
"suka goyi bayan Yahudawa" ko kuma "suka yarda da Yahudawa." Taron farin da aka ambata basu karɓi sakon alherin ba.
Taron na biyun da aka ambata sun karɓi sakon alherin. AT: "suka goyi bayan manzaninnin"
Wato Bulus da Barnaba kenan. Anan ana iya ce da "manzannin" "waɗanda aka aiko"
"su yi koƙarin rinjayan shugabannin Ikoniya." Anan "nemi" na nufin cewa basu iya jan hankalin su gabaɗaya kamun manzannin suka bar garin ba.
"don su daka Bulus da Barnaba su kuma ƙashe su ta wurin jefin su da wuwatsu"
Wata lařdi a Ƙaramar Asiya
Wata birni a Karamar Asiya kudancin Ikonoya kuma arewacin Darbe
Wata birnin a Karamar Asiya kudancin Ikoniya da listira
Bulus da Barnaba ma sun yi wa'azzin bishara a can"
Bulus da Barnaba suna kasar Listira yanzu.
Wannan na gabatar da wata sabuwar mutum kenan a labarin.
"ba ya iya motsa ƙafofinsa" ko kuma "ba ya iya tafiya da ƙafafunsa ba"
"an haife shi shi gurgu ne"
mutumin da ba ya iya tafiya da ƙafafu
"Bulus ya zuba masa ido"
Ana iya fasara "bangaskiya" anan da "gaskanta." AT: "ya gaskanta cewa Yesu zai iya warkar da shi" ko kuma "ya gaskanta cewa Yesu zi iya ba shi lafiya" (Dubi: and
"ya tashi sama." Wannan na nufin cewa ƙafafunsa sun warke sarai.
Wato warkar da gurgun kenan.
A tada murya na nufin a yi magana da ƙarfi. AT: "suka yi magan da ƙarfi" (Dubi: rc://*/ta/man/translate/figs-idiom)
Jama'an da yawa suka gaskanta cewa Bulus da Barnaba allolin al'ummai ne suka sauka musu daga sama.AT: "Ai alloli sun Sauka mana daga sama"
a nasu harshen Likoniya." Mutanen Listira suka iya yin Likoniyanci da kuma Girka.
Waɗannan mutanen sun gaskanta cewa lallai ne allolin sun canza kamanin su domin su zama kamar sauran mutane.
Zasfa shi ne tsarki bisa dukkan sauran allolin al'ummai.
Hamisa shi ne wani allahn al'ummai da ke kawo saƙonni daga wurin Zasfa da sauran alloli.
Zai zama da taimako a kara takamaimain bayani akan wannan firist. AT: "Akwai wata haikali da mutane ke ɓautar Zasfa a ƙofar shiga garin. Da wannan firist da ke hidima a haikalin ya ji abinda Bulus da Barnaba suka yi, ya kawo"
Bijimain na hadaya ne. Furannin na na yi wa Bulus da Barnaba kamar gammo ne akai ko kuma a sa a bisa bijimain hadayan.
"Ƙofofin birane sukan zama wurin taron mutanen gari ne gaba ɗaya.
"suna so su yi wa Bulus da Barnaba hadaya a madadin alloli Zasfa da Hamisa"
Maiyiwuwa Luka anan yana moran "manzannin" kamar yadda akan moranshi wa "ɗan aika."
Wannan alama ce na nuna matuƙar bakin ciki da rashin gamsuwar su cewa taron suna so su yi masu hadaya.
Barnaba da Bulus suna tsauta wa mutanen ne saboda hadaya da suke so su yi masu. AT: "Ku Mutane, kada ku ya haka!"
"mana sujada"
Da haka, Barnaba da Bulus suna cewa su ba alloli ba kenan. AT: "Ai muma 'yan adam ne kamarku. Mu ba alloli ba ne!"
"kama da ku ta kowane yanayi"
A nan "rabu da ... ga" na karin maganan ne da ke nufin a daina yi wani abu, a kuma fara yin wani abu dabam. AT: "ku daina ɓauta wa allolin ƙarya da ba za su iya taimakonku ba, a maimakon haka, ku fara bauta wa Allah mai rai
"Allag da ke rayayye da gaske"
"a lokatai da suka wuce" ko kuma "har sai yanzu"
Wato su yi rayuwar kansu. AT: "su yi rayuwa yadda ya gamshe su" ko kuma "su yi duk abinda suke so su yi"
AT: "Allah ya bar shi da shaida" ko kuma "Allah ya shaida"
"kamar yadda yakke a fili"
A nan "ranku" na nufin mutanen. AT: "yana baku isheshen abubuwan ci da kuma sa kawo farin ciki"
Bulus da Barnaba suka hana taron daga yi masu hadaya, amma basu same hakan da sauki ba.
"sun sha wuya a tsayar da su"
Zai zama da taimako a faɗi abinda suka rinjayi taron su yi. AT: "suka rinjayi jama'ar don kada su gaskanta da Bulus da Barnaba, amma su yi masu tawaye.
Ba lallai ne wannan su zama wannan taron da aka yi maganar su a iya da ta gabata ba. Domin akwai ɗan banbancin lokaci a tsakani, kuma wannan na iya zama su wani taro ne dabam gabaɗaya.
"domin suna gani kamar ya riga ya mutu"
Wato sabobin tuɓa kenan da ke garin Listira.
"Bulus suka sake shiga garin Listira tare da masubin"
"Bulus da Barnaba suka tafi garin Darba"
"Darba" (Dubi: [Acts 14:20])
A nan "zuciyar" na nufin almajiran. Wannan na nanata yadda suke ji da kuma imaninsu. AT: "Bulus da Barnaba sun ƙarfafa masubin su cigaba da gaskanta da sakon Yesu" ko kuma "Bulus da Barnaba suka ƙarfafa masubin su cigaba da girma ƙwarai a ɗangartakarsu da Yesu"
"da ƙarfafa masubin su cigaba da dogara ga Yesu"
"Da Bulus da Barnaba suka zaɓa shugabanni a kowace sabuwar taron masubi"
Wannan na iya nufin 1) "Bulus da Barnaba suka miƙa dattawa da suka zaɓa" ko kuma 2) "Bulus da Barnaba suka ɗanka shugabannin da sauran masubi"
"su" anan ya ɗangarta ga zaɓin da kun yi na ma'annar "na su" a jimlar da ta gabata na abinda ake nufi (ko dattawa ko shugabanni, da kuma sauran mutane)
"Magana" anan na nufin "Maganar Allah." AT "Da suka yi maganar Allah a Bariyata"
Ataliya yana kasa da Bariyata.
AT: a nan ne masubi da ke garin Antakiya suka miƙa Bulus da Barnaba ga alherin Allah" ko kuma "anan ne mutanen Antakiya suka yi addu'a Allah ya kiyaye ya kuma tsare Bulus da Barnaba"
"suka kirkiro masubi suka taru a haɗu tare"
Ana maganar yadda Allah ya ba wa Al'ummai zarafi su gaskanta kamar ya buɗe wata ƙofa ne da tun can yana hana su shiga cikin bangaskiya. AT: "Allah ya mai da shi abu mai yiwuwa Al'ummai su gaskanta"
1Wadansu mutane suka zo daga Yahudiya suka koyar da 'yan'uwa, cewa, "Idan ba yi maku kaciya bisa ga al'addar Musa ba, ba za ku sami ceto ba." 2Da Bulus da Barnaba suka tunkare su da mahawara, sai 'yan'uwa suka yanke shawara Bulus da Barnaba da wasu su je Urushalima wurin manzanni da dattawa a kan wannan magana.3Da shike iklisiya ce ta aike su, sai suka bi ta Finikiya da ta Samariya suka sanar da tuban al'ummai. Ya kawo murna mai yawa a wurin 'yan'uwa. 4Bayan sun zo Urushalima, sai iklisiya da manzanni da dattawa, suka marabce su, sai suka fada masu abin da Allah ya yi ta wurinsu.5Amma wadansu mutane wadanda suka ba da gaskiya daga cikin Farisawa, suka tashi suka ce, "Dole ne a yi masu kaciya a kuma umarce su su kiyaye dokar Musa." 6Sai manzanin da dattawan suka taru don su duba wannan lamari.7Bayan mahawara mai tsanani, sai Bitrus ya tashi ya ce masu, "'Yan'uwa, kun san lokacin baya da ya wuce, Allah ya yi zabi a cikinku, cewa ta bakina ne al'ummai za su ji bishara, su kuma ba da gaskiya. 8Allah, wanda ya san zuciya, ya yi masu shaida, ya kuma basu Ruhu Mai Tsarki kamar yadda ya yi mana; 9kuma bai bambanta mu da su ba, ya tsabtace zuciyarsu ta wurin bangaskiya.10To, saboda haka don me kuke gwada Allah, kuna sa wa almajirai nauyi a wuya wanda ubanninmu duk da mu ba mu iya dauka ba? 11Amma mun gaskanta za mu samu ceto ta wurin alherin Ubangiji Yesu, kamar yadda suke."12Dukan taron jama'ar suka yi shiru sa'adda suke sauraron sakon shaidar da mamakin abin da Allah ya yi ta wurin Bulus da Barnaba a cikin al'ummai.13Bayan sun gama magana, Yakubu ya amsa, ya ce, "'Yan'uwa, ku ji ni. 14Saminu ya fada yadda Allah ya fara nuna jinkai ga al'ummai domin ya dauke jama'a daga cikinsu domin sunansa.15Maganar annabawa ta yarda da wannan, kamar yadda yake a rubuce, 16'Bayan wadannan abubuwa zan dawo, zan gina gidan Dauda wanda ya fadi kasa; in sake gina bangonsa, in tsayar da shi, 17saboda sauran jama'a su nemi fuskar Ubangiji, har da al'ummai da ake kira da sunana. 18Wannan shine abin da Ubangiji ya fadi, shi wanda ya yi wadannan abubuwa da aka sani tun zamanin da.19Saboda haka, a gani na kada mu matsa wa al'umman da suka juyo gun Allah; 20amma zamu rubuta masu da cewa, su guje wa gumaka da zina da faskanci da maye da cin mushe. 21Tun zamanin da akwai mutane a kowanne birni wadanda suke wa'azi da karatun Musa a majami'u kowanne Asabaci."22Sai ya yi wa manzanin kyau su da dattawa da dukan iklisiyar su zabi Yahuza da Barnaba da Sila da dattawan iklisiya a tura su Antakiya tare da Bulus da Barnaba. 23Sai suka rubuta wasika, "Manzani da dattawa da 'yan'uwa zuwa ga al'ummai 'yan'uwa a Antakiya da Suriya da Kilikiya, gaisuwa mai yawa.24Mun ji cewa wasu mutane daga cikinmu wadanda ba mu umarce su ba, sun fita daga cikinmu sun yi maku koyarwar da ta daga maku hankali. 25Ya yi kyau da dukanmu, muka amince mu zabi wadansu mutane mu tura su wurinku tare da Bulus da Barnaba, 26mutane wadanda suka sadaukar da ransu domin sunan Ubangiji Yesu Almasihu.27Mun aika Yahuza da Sila su gaya maku wadannan abubuwa. 28Saboda haka ya yi kyau Ruhu Mai Tsarki da mu, kada mu sa maku nauyi fiye da wadannan abubuwan: 29ku bar yi wa gumaka hadaya, ku bar cin mushe da shan kayan maye da zina da faskanci, in kun kiyaye wadannan abubuwa za ku zauna lafiya. Ku huta lafiya."30Da aka sallame su, sai suka je Antakiya. Bayan sun tara jama'a sai suka ba su wasikar. 31Bayan da suka karanta ta, sai suka yi murna sosai saboda karfafawa. 32Yahuza da Sila, da shike su annabawa ne, suka karfafa 'yan'uwa da kalmomi masu yawa.33Bayan sun yi kwananki a wurin, sai aka sallame su zuwa wurin 'yan'uwa wadanda suka aiko su. 34Amma ya gamshe Sila ya zauna a wurin. 35Amma Bulus da Barnaba suka tsaya a Antakiya da sauran 'yan'uwa, suna koyar da maganar Ubangiji.36Bayan kwanaki kadan Bulus ya ce ma Barnaba, "Mu koma yanzu mu ziyarci dukan 'yan'uwa da muka yi masu bisharar Ubangiji, mu ga yadda suke. 37Barnaba yana so su dauki Yahaya wanda kuma ake kira Markus. 38Amma Bulus ya yi tunanin bai kamata a tafi da Markus ba, tun da ya bar su a Bamfiliya bai ci gaba da su ba.39Nan jayayya ta tashi tsakaninsu, har suka rabu da juna sai Barnaba ya tafi tare da Markus suka ketare zuwa Kuburus. 40Amma Bulus ya zabi Sila suka tafi, bayan 'yan'uwa sun yi masu addu'ar alherin Allah ya kiyaye su. 41Bulus ya tafi ya zazzaga Suriya da Kilikiya yana ta karfafa iklisiyoyin.
Bulus da Barnaba suna nan a garin Antakiya yayin da aka samu wata jayayya game da Al'ummai da kaciya.
"waɗansu mutane." Ana iya kara bayyana wannan a fili cewa waɗanan mutanen Yahudawa ne da suka gaskanta da Yesu.
Yahudiya yana ɗan sama da Antakiya.
A nan 'yan'uwa na matsayin masubin Almasihu. Ana ɗaukan cewa suna Antakiya ne. AT: "suka koyar wa masubi da ke Antakiya" ko kuma "suna koyar da masubi a Antakiya"
AT: "saida an yi maku kaciya bisa ga al'adar Musa, Allah ba zai cece ku ba" ko kuma "Allah ba zai cece ku daga zunubanku ba sai kun yi kaciya bisa ga shari'ar Musa"
Ana iya kara bayannin kalamun nan "ƙaramar gardama" da "muhawara" a fili. AT: "suka tunkare su da muhawara tare da Mutanen Yahudiya"
Urushalima yana sama da kusan ko wane wuri a Isra'ila, saboda haka, daidai ne Isra'ilawan su yi maganar haurowa zuwa Urushalima.
"wannan zancen"
A nan kalaman nan "Su", "su", sa kuma "na su" na nufin Bulus, Barnaba, da dai irin sauransu. (Dubi: [Acts 15:2])
AT: "Da shike taron masubi ne suka aike su daga Antakiya zuwa Urushalima"
A nan "ikkilisiya" tana nufin jama'ar ikkililsiya.
Kalamun nan "suka bi" da "suka nanar" na nuna cewa sun ɗan zauna na wasu lokatai a a wurare daban daban suna ba da bayyani filla-filla na abinda Allah ke yi.
Kalmar nan "tuɓa" na nuna cewa Al'ummain sun fara ƙin allolin su na ƙarya suna gaskanta da Allah. AT: suka sanar wa taron masubi a waɗannan wurare cewa Al'ummai ma suna gaskanta da Allah"
Ana maganar yadda sakonsu ya sa 'yan'uwan murna ne kamar ita "murna" ɗin wata abu ne da ake iya ɗauko suka kawo wa 'yan'uwan. AT: "Abinda suka faɗa ya sa masubin su yi farin ciki"
wato masubi.
AT: "manzannin, dattawa, sa sauran taron masubi suka marabace su"
"ta wurinsu"
A nan, Luka yana bambanta waɗanda sun gaskanta cewa ana iya samun ceto ta wurin Yesu ne kadai da kuma waɗanda suka gaskanta cewa ceto ta wurin Yesu ne da kuma kaciya kamun a sami ceto.
"su yi biyayya da dokar Musa"
Shugabannin Ikkilisiyar suka tattauna ko Al'ummai ɗin suna buƙatar a yi masu kaciya da kuma su kiyaye dokar Musa kamun Allah ya ceci su daga zunubansu.
Bulus yana magana ne da dukkan masubi da ke kasancewa a wurin.
A nan "baki" na nufin Bitrus. AT: "daga gareni" ko kuma "ta wurina"
"yakamata al'ummai su ji"
AT: "bisharar Yesu"
A nan "zuciya" na nufin "ainihin tunanin 'yan'adam." AT: "wanda ya san tunanin 'yan'adam" ko kuma "wanda ya san abinda mutane ke tunani"
"ya yi wa Al'ummai shaida"
"ya sa Ruhu Mai Tsarki ya sauko a kan su."
Allah bai bi da Yahudawa masubi da dabam da Al'ummai masu bi ba.
Ana maganar gafarar zunuban da Allah ya yi wa Al'ummai ne kamar yadda ake tsabtace wani abu. A nan "zuciya" na nufin ainihin tunanin mutum. AT: "ya gafarta masu domin sun gaskanta da Yesu"
Wannan bata nufin "a daidai wannan lokaci," amma ana amfani ne da ita domin a jawo hankalinmu zuwa ga wat abu mai muhimmanci da ya biyo baya.
Bitrus yana amfani ne da wannan tambayan domin ya gaya wa Yahudawa masubi cewa kada su buƙaci waɗanda ba Yahudawa ba su yi kaciya kamun su samu ceto. AT: "Kada ku gwada Allah ta wurin nauyaya wa masubi da ba Yahudawa ba da nauyi da mu Yahudawa ba iya ɗuka ba!"
Wato kakkaninsu Yahudawa.
AT: "Amma mun gaskanta cewa Ubangiji Yesu zai cece mu ta wurin alherinsa, kamar yadda ya cece waɗanda ba Yahudawa ba."
"Kowa" ko kuma "Kungiyar gaba ɗaya" (See: [Acts 15:6])
"Allah ya sa"
"'yan'uwa masubi, ku ji." Mai yiwuwa Yakubu yana magana da Maza ne kadai.
"saboda yă zaɓi jama'a daga cikinsu"
"domin sunan Allah." Anan "suna" na nufin Allah. AT: "domin kansa"
A nan "magana" na nufin sakon. AT: "Abinda annabawa sun faɗa ta yarda" ko kuma "Annabawa sun yarda"
"tabbata da wannan gaskiyar"
AT: "kamar yadda suka rubuta" ko kuma "kamar yadda Annabi Amoz ya rubuta tun da daɗe wa"
Wannan na maganar zabe da Allah zai sãke yi daga zuriyar Dauda domin ya yi mulki a bisa mutanensa kamar yana sãke shirya wata gida ne da ya riga ya rushe.
A nan "gida" na nufin Iyalin Dauda.
Wannan na magana ne game da yadda mutane ke son yi wa Allah biyayya da kuma kara koya game da shi kamar suna neman sa ne.
A nan "jama'a" sun haɗa da maza da mata. AT: "sauran mutane"
Allah yana magana game da kansa ne, amma ya yi kamar akwai mutum na uku da yake magana akai. AT: "su nemi fuska ta, Ubangiji"
AT: "a haɗe da dukkan Al'ummai da suke nawa"
A nan "sunana" na nufin Allah.
AT: "da jama'a sun sani"
Ana iya kara bayyanan a fili dalilin da ya sa Yakubu ba ya so a matsa wa Al'umman. AT: "kada mu umarci Al'umman su yi kaciya su kuma kiyaye dokokin Musa"
Ana maganar mutumin da ya fara biyayya da Allah ne kamar anan iya ganin yadda mutumin ya juya ga Allah.
Zina da fasikanci, cin abinda aka maƙure, da kuma cin nama tare da jini suna cikin bukukkuwan bautar gunakai da allolin ƙarya.
Wannan na iya nufin cin namar wata dabba da wani ya miƙa hadaya ga wata gunki ko wani abinda ya shafe bautar gumaka.
Allah bai yarda Yahudawa su ci nama da ke da jini a cinkinta ba. Haka ma, ko Musa daga rubuce rubucen sa a littafin Farawa, Allah ya haramta shan jini. Sabodahaka, ba za su iya cin wata dabba da wani ya maƙure ba domin ba a janye jini daga namar dabban yadda ya kamata ba.
Yakubu na nufin cewa Al'ummai sun san muhimmancin waaɗnnan dokokin domin Yahudawa sun yi jawabin su a kowani birnin da ke da majami'a. Anan ɗaukan cewa Al'ummai ma suna iya zuwa gun malamain majami'u don karin bayyani game da waɗannan dokokin.
A nan "Musa" na nufin littattfen shari'ar Musa. AT: "An yi shelar shari'ar Musa" ko kuma "Yahudawa sun koyar da shari'ar Musa"
kalmar nan "kowanne" anan na nufin wurare da dama. AT: "a birane da dama" )
Musa a nan na nufin shari'ar. AT: "kuma ana karanta shari'ar" ko kuma "kuma sun karanta shair'ar"
A nan "ikkilisiyar" na nufin jama'ar da ke ikkilisiyar Urushalima. AT: "ikkilisiyar Urushalima" ko kuma "al'umman masubi gabaɗaya da ke Urushalima"
Sunan mutumin kenan. "Barsaba" dai wani suna ne kuma da mutane kam kiransa da shi.
Wannan itace gabatarwar wasikar. Harshen ku na iya samun wata hanyar gabatar da marubucin wasika da kuma wadda aka rubuta masu. AT: "Ga wasika daga 'yan'uwan ku, manzanni da dattawa. Muna rubuta maki Al'ummai masubi da ke Antakiya, Suriya, da Kilikiya. Gaisuwa mai yawa a gare ku" ko kuma "Zuwa ga 'yan'uwan mu Al'ummai da ke Antakiya, Suriya, da Kilikiya. Gaisuwa mai yawa daga manzanni da dattawa, 'yan'uwanku"
A nan kalmar nan "'yan'uwa" na nufin sauran masubi. Manzannin da dattawa suna amfani ne da wannan kalmar don su tabbatar wa Al'umma masubi da cewa sun karɓe su a matsayin 'yan'uwa masubi.
Wannan dai sunan wata lardi ne da ke Karamar Asiya arewacin tsibirin Kuburus.
"wasu mutane"
"ƙodashike ba mu umarce su su je ba"
A nan "hankali" na nufin mutane. AT: "sun koya maku abubuwan da suka dame ku"
Mutanen da suka aika su ne Yahuza da ake kira Barsaba da kuma Sila. (Dubi:[15:22])
A nan "suna" na nufin mutum gabaɗaya. AT: "domin sun ba da gaskiya ga Ubangijinmu Yesu Almasihu" ko kuma "domin suna bauta wa Ubangijinmu Yesu Almasihu"
Wannan jimlar na nanata cewa Yahuza da Sila za su faɗi abu ɗaya da manzanni da dattawa sun rubuta. AT: "wanda da kansu za su yi maku magana game da abubuwan da muka rubuta"
Wannan na maganar dokokin da mutane ke buƙatar kiyaye wa ne kamar sun zama wasu kayayyaki e=ne da mutane za su ɗaɗɗauka a bisa kafaɗansu.
Wannan na nufin cewa ba yarda su ci naman wata dabba da wani ya miƙa wa gumaka hadaya ba.
Wannan na nufin shan jini ko cin naman da ba a janye jinin sa ba.
Dabba da aka musƙure ya mutu, amma ba janye jinin sa ba.
Wannan na sanar da ƙarshen wasikar. AT: "Wassalam" ko kuma "Ku zamna lafiya" ko kuma "Allah ya bishe ku"
Kalmar nan "su" na nufin Bulus, Barnaba, Yahuza, da Sila. AT: "Don haka da aka sallame su, sai suka tafi Antakiya"
AT: "Da aka sallame manzannin da dattawa huɗun" ko kuma "Da masubi da ke Urushalima suka aiko su"
Antakiya tana kasa da Urushalima a tadawa.
"masubi da ke Antakiya sun yi murna sosai"
AT: "saboda abinda manzanni da dattawan sun rubuta ya ƙarfafasu"
Annabawa malamai ne da ke da izini daga Allah su yi magana a madadin sa. AT: "da shike su annabawa ne" ko kuma "ga su ma annanbawa ne"
An yi maganar taimaka wa wani ya dogara sosai ga Yesu kamar an ƙara masu ƙarfin jiki
Kalmar nan "sun" na nufin Yahuza da Sila. AT: "Bayan sun zauna a wurin na ɗan lokaci. AT: "Bayan sun zauna a wurin na ɗan lokaci"
AT: "'yan'uwan suka sallame Yahuza da Sila sun koma lafiya"
"'zuwa wurin masubi da ke Urushalima da suka aike Yahuza da Sila" (Dubi: (See: [Acts 15:22]))
Kalmar nan "su" anan na nufin Bulus da Barnaba kenan.
A nan "maganar" na nufin sako. AT: "sakon Ubangiji"
"Ina mai shawaran cewa yanzu mu koma"
"kula da 'yan'uwa" ko kuma "yi koƙarin tallafe wa masubi"
Suna so su ga yanayin 'yan'uwan da kuma yadda suna kan riƙe da gaskiyar maganar Allah.
"su ɗauki Yahaya, wadda ake kira Markus"
Kalmar nan "bai kamata" ba na nufin ba daidai ba ne. AT: "Bulus ya yi tunanin cewa tafiya da Marku ba zai yi kyau ba"
Wannan wata lardi ne a Karamar Asiya. Duba yadda aka fasara wannan a [2:10]
"bai ci gaba da aiki tare da su ba a lokacin" ko kuma "bai cigaba da hidima tare da su ba"
A nan iya sanar "jayayya" anan ta da "rashin amincewa." AT: "Suka ƙi amincewa da juna"
AT: "bayan da masubi da ke Antakiya suka danƙa Bulus ga alherin Ubangiji" ko kuma "da masubi da ke Antakiya suka yi addu'a ga Ubangiji don ya kiyaye Bulus yă kuma ƙaunace shi"
Jamlar da da wannan ke bi na nuna cewa Sila yana tare da Bulus. AT: "sun tafi" ko kuma "Bulus da Sila suna tafe" ko kuma "Bulus ya ɗauki Sila sun tafe
Waɗannan su ne lardodin da ke Karamar Asiya kusa da tsibirin Kuburus.
Kalmar nan "ikkilisiyoyin" na nufin taron masubi da ke Suriya da Kilikiya. AT: "ta ƙarfafa masubin da ke ikkilisiyoyin" ko kuma "suna taimaka wa taron masubi su ƙara dangana ga Yesu"
1Bulus ya kuma isa Darbe da Listira, in da akwai wani almajiri mai suna Timoti a wurin, dan wata Bayahudiya wadda ta ba da gaskiya; ubansa kuwa Baheline ne. 2Ana maganar kirki a kansa ta bakin 'yan'uwa da ke Listira da Ikoniyan. 3Bulus ya yi wa Timoti kaciya, domin yana so su yi tafiya tare, domin kuma saboda Yahudawan da ke wurin, sun san cewa ubansa Baheline ne.4Suna shiga cikin biranen, suna yi wa iklisiyoyi gargadi da su yi biyayya da umurnan da Manzanni da dattawa suka rubuta a Urushalima. 5Bangaskiyar iklisiyoyi kuwa ta karu, ana kuma samun karuwa na wadanda suke ba da gaskiya kowace rana.6Bulus da abokan aikin sa sun shiga cikin lardin Firigiya da Galatiya, tun da Ruhu Mai Tsarki ya hana su wa'azin kalmar a cikin yankin Asiya. 7Sun zo kusa da Misiya, da nufin shiga cikin Bitiniya, Ruhun Yesu ya hana su. 8Da suka ratse ta cikin Misiya, sai suka shiga birnin Taruwasa.9Bulus ya ga wahayi cikin dare, wani mutumin Makidoniya na kiransa, yana cewa. "Ka zo Makidoniya ka taimake mu". 10Bulus, da ganin haka, ya kama hanya zuwa Makidoniya, da tunanin Allah ne ya ke so su kai wa mutanen Makidoniya bishara.11Da barin Taruwasa, Bulus da kungiyarsa sun shiga jirgin ruwa zuwa Samutaraki, da gari ya waye kuma sun tafi Niyafolis; 12Daga nan kuma suka tafi Filibi, birni na Makidoniya, mai muhimmanci ne a yankin Roma, in da mun yi zango kwanaki da dama. 13Ranar Asabaci mun je kofar gari, gefen rafi, da tunanin samun wurin addu'a. Mun zauna mun kuma yi magana da matan da sun taru a wurin.14Wata mace mai suna Lidiya, 'yar kasuwa ce a birnin Tiyatira, mai bautar Allah ce, ta saurare mu. Ubangiji ya bude zuciyarta, ta mai da hankali ga maganar da Bulus ke fadi. 15Sa'anda da aka yi mata Baftisma tare da mutanen gidanta, ta ce da mu, "Idan kun dauke ni mai bautar Allah, ku zo gidana ku zauna." Sai ta rinjaye mu.16A daidai wannan lokaci, muna tafiya wurin addu'a, wata yarinya mai ruhun duba ta hadu da mu. Iyayen gijinta na arziki da ita sosai. 17Tana bin Bulus, tare da mu, tana fadi da murya mai karfi cewa, "Wadannan mutanen, bayin Allah mafi daukaka ne, suna sanar maku hanyar ceto ne". 18Ta dauki kwanaki tana haka. Amma Bulus ya yi fushi da ita ainun, ya juya ya umarci ruhun, ya ce, "Na umarce ka, ka rabu da ita a cikin sunan Yesu Almasihu". Ruhun ya yi biyayya ya rabu da ita nan take.19Da iyayengijinta suka ga cewa hanyar shigar kudinsu ta toshe, sai suka kama Bulus da Sila, suka ja su cikin kasuwa suka kai su gaban mahunkunta. 20Da suka kai su Kotu, suka ce, "Wadannan mutane Yahudawa ne, suna kawo tashin hankali a birninmu. 21Suna koyar da abubuwa da ba su karbuwa a gare mu, balle mu aikata, a matsayinmu na Romawa."22Sai jama'a gaba daya sun tayar wa Bulus da Sila; alkalan kuma sun yage rigunansu, sun ba da umarni a duki Bulus da Sila da bulala. 23Bayan dukan, an jefa su Bulus a kurkuku, an ba mai tsaron kurkukun umurni ya kulle su da kyau, kada su gudu. 24Shi kuma ya yi hakanan, ya sa masu sarkoki a kafafun su, kamar yadda aka umurce shi.25Da tsakar dare, Bulus da Sila suna yin adu'a, su na raira wakoki ga Allah, sauran 'yan sarkar su na jin su. 26Nan da nan sai ga wata girgizar kasa, wadda ta sa ginshikan kurkukun sun kadu, nan da nan kofofin kurkukun sun bude, 'yan sarka kuma, sarkokin su sun karkatse.27Mai tsaron kurkukun ya tashi daga barci ya ga kofofin kurkukun a bude, ya zaro takobi, zai kashe kan sa, a tunanin sa, 'yan sarkar sun gudu. 28Amma Bulus ya ta da murya da karfi, ya ce, "kada kayi wa kanka barna, domin dukan mu muna nan".29Mai tsaron kurkukun ya aika a kawo fitila, ya shiga ciki a gurguje da rawan jiki, ya fadi a gaban Bulus da Sila, 30ya fitar da su waje ya ce, "Shugabanni, me ya kamata in yi domin in tsira?" 31Sun ce masa, "ka ba da gaskiya ga Yesu Ubangiji, da kai da gidan ka, za ku sami tsira".32Bulus da Sila suka fada masa maganar Ubangiji, tare da iyalinsa. 33Shi mai tsaron kurkukun ya dauke su cikin daren, ya wanke raunukansu, an kuma yi masa Baftisma nan da nan tare da iyalinsa. 34Ya kai Bulus da Sila gidansa, ya ba su abinci. Murna ta cika gidan mai tsaron kurkukun, domin iyalin sa duka sun ba da gaskiya ga Allah.35Da gari ya waye, alkalai sun ba da sako a saki Bulus da Sila. 36Mai tsaron kurkukun kuwa ya sanar wa Bulus wannan magana ta alkalan, saboda haka ya ce wa Bulus, "Ku tafi cikin salama".37Amma Bulus ya ce masu, "Sun yi mana duka a fili a gaban mutane mu da muke Romawa, ba a kashe mu ba, sun kuma sa mu a kurkuku; suna koran mu a asirce? Su zo da kansu su fitar da mu. 38Masu tsaron kurkuku sun mayar da maganar Bulus ga alkalan, wanda ya sa sun firgita, da jin cewa Bulus da Sila Romawa ne. 39Alkalai da kansu sun zo sun roki Bulus da Sila; da suka fitar da su daga kurkukun, sun ce wa Bulus da Sila su bar birnin.40Da hakanan ne Bulus da Sila suka fita daga kurkuku, sun je gidan Lidiya. Da Bulus da Sila sun ga 'yan'uwa, sun karfafa su, sa'annan suka bar birnin.
Wannan ya cigaba da tafiye-tafiyen bisharar Bulus tare da Sila.
An gabatar da Timoti a wannan labarin, ya kuma haɗa kai da Bulus da Sila. Aya 1 da 2 na bada takamaimain tarihin Timoti.
Ana iya fasara "isa" da "je"
Wannan sunan wani gari ne a karamar Asiya. Duba yadda aka fasara wannan a [14:16].
Wannan kalmar "sai ga" na jan hankalin mu ne ga wani sabon mutum a labarin. Harshen ku na iya samun wata hanyar yin haka.
Ana fahimtar "ga Almasihu". AT: "wadda ta ba da gaskiya ga Almasihu"
AT: "'yan'uwan suna maganar kirki a kansa" ko kuma "Timoty yana da shaida mai kyau a gaban 'yan'uwan" ko kuma "'yan'uwan suna faɗin abubuwa masu kyau game da shi"
A nan "'yan'uwan" na nufin masubi. AT: " ta wurin masubi
Mai yiwuwa Bulus ne kansa ya yi wa Timoti Kaciya, amma ya fi yi kamar Bulus ya sa wani ne dabam ya yi wa Timoti kaciya.
"domin Yahudawan da suke zama a waɗannan wuraren da Bulus da Timoti za su je"
Dashike Halenawa basu yi wa 'ya'yan su kaciya, Yahudawa za su san cewa Timoti ba shi da kaciya, kuma za su ki Bulus da Timoti kafin ma su saurare bisharar su game da Almasihu.
"da 'yan ikkilisiya su yi biyayya" ko kuma "da masubi su yi biyayya"
AT: "da Manzanni da dattawa da ke Urushalima suka rubuta"
AT: "Masubin sun kara ƙarfi a bangaskiyarsu, kuma ana kuma samun karin mutane da suke tuba zuwa bi kowace rana"
Ana maganar taimakon mutum ya gaskanta da gabadadi kamar karin kuzari ne.
A nan wannan na nufin masubi da ke ikkilisiyoyin.
Wato lardin Asiya. Duba yadda aka fasara wannan sunan a [2:10]
AT: "Ruhu Mai Tsarki ya hana su" ko kuma "Ruhu Mai Tsarki bai yarda masu ba"
A nan "kalma" na nufin "sako." AT: "sakon almasihu"
A nan ana iya fasara "zo" da "je" ko kuma "iso"
Waɗannan wasu lardodi biyu ne kuma da ke Asiya.
"Ruhu Mai Tsarki"
Taruwasa yana kasa da Misiya a tadawa.
A nan ana iya fassara "shiga" da "je"
"Bulus ya ga wahayi daga Allah" ko kuma "Bulus ya samu wata wahayi daga Allah"
"na roƙonsa" ko kuma "yana gayyatansa"
Akwai wata taiku tsakanin Makidoniya da Taruwasa. AT: "Ka ƙetaro zuwa ƙasar Makidoniya"
A nan kalamun nan "mu" da kuma "na mu" na nufin Bulus ne da abokan tafiyarsa a haɗe da Luka, wanda shi ne marubucin Ayyukan Manzanni.
Waɗannan birane ne da ke gaɓar teku a kusa da Filibi a Makidoniya.
A nan ana iya juya wannan kalmar "zo" zuwa "je" ko kuma "iso."
Wannan wata gari ce a wajen Italiya da mutanen suka zo daga Roma ke zama. Jama'ar da ke a wannan wurin ma suna da dama da 'yanci ɗaya da waɗanda ke biranen Italiya. Suna iya mulkin kansu kuma ba lallai ne su biya haraji ba.
A nan "wata mace" na gabatar mana da wata sabuwar mutum kenan a wannan labarin. AT: "Akwai waa mace mai suna Lydia"
A nan "tufafi" ne aka fahimta. AT: "'yar kasuwa ce mai sayar da tufafi masu jan launi"
Wato sunar garin kenan.
Mai yi wa Allah ibada shi ne ba Al'ummi da ke yabon Allah, yana kuma binsa, amma baya biyayya da dukkan dokokin Yahudawa.
Wato Allah ya sa ta gaskanta da sakon kenan. AT: "Ubangiji ya sa ta ta saurara da kyau ta kuma ba da gaskiya"
A nan "zuciya" na nufin hankalin mutum. Kuma marubucin wannan wasika na maganar "zuciya" da "hankali" kamar wata akwati ne da mutum ke iya buɗe wa idan anyi shirin cika ta da abubuwa.
AT: "maganar da Bulus yayi"
AT: Da aka yi wa Lidiya da mutanen gidanta baftisma"
A nan "gida" na nufin mutanen da ke zama a gidanta. AT: "mutanen gidanta" ko kuma " 'iyalin ta da ma'aikatan gidanta"
Wannan jimlar na sa alammar wata sabuwar bangare ne a labarin. Idan harshen ku na da wata hanya ta musamman na yin haka, ana iya yin amfani da shi anan.
Wannan jimla "wata yarinya" na gabatar mana ne da wata sabuwar mutum a labarin. AT: "akwai wata yarinya"
Wani ruhun miyagu yakan yi magana da ita game da abinda zai faru da mutane nan ba da jimawa sosai ba.
Ana maganar yadda mutum na iya samun ceto ne anan kamar wata hanya ne da mutum ke iya wuce wa ko ya bi. AT: "yadda Allah zai cece ku"
AT: "Amma ta sa Bulus ya ji fushi da ita ƙwarai, sai ya juya"
A nan "suna" na nufin yin magana da iko ko a matsayin wakilin Yesu Almasihu.
"ruhun ya rabu da ita nan da nan"
"wato masu yarinyar"
Ana iya sanar da wannan a fili dalilin rashin sammanin samu kuɗinsu ya toshe. AT: "Da iyayengijinta suka ga cewa ba za ta iya tara masu kuɗi kuma da ta wurin yin duba"
"zuwa cikin jama'a" Wato wurin da ake kasuwanci kenan, inda ake siya da sayar da kayaki, shanu, ko hařkoki na tafiya.
ko kuma "domin mahukuntan su yanke masu hukunci"
"Da suka kawo su ga mahukunta"
masu mulki ko mahukunta
A nan "kalmar nan "mu" na nufin jama'ar garin a haɗe da Alƙalan da ke mulkinta.
"gaskanta ko biyayya" ko kuma "karɓa ko ma a yi"
AT: "umarce sojojin su duke su da bulala"
"aka buge su sosai da bulala"
"an faɗi wa mai tsaron kurkukun ya tabbatar cewa basu tsira daga kurkukun ba"
mutumin da ke da hakin kula da dukkan mutanen da ke ɗaure a kurkuku.
"shi kuma yayi na'am da wannan umarni"
"ɗaura kafafunsu da kyau a cikin turu""
wata katako ne ki itace ne mai rami da ke hana kafar mutum iya motsi.
AT: "girgizar ƙasar ta sa ginshikin kurkun suna kaduwa"
Da ginshikin ta kadu, kurkukun gabaɗaya ya kadu.
AT: "duk kofofin suka buɗu"
AT: "sarkokin kowa suka ɓalle"
AT: "Mai tsaron kurkukun ya farfado"
"ya yi shirin kashe kansa." Mai tsaron kurkukun ya gumaci ya ɗauki ransa a maimakon gamuwa da sakamakon barin ya kurkukun su gudu.
Ana iya bayyana a fili dalilin da ya sa mai tsaron kurkukun ya bukaci wuta. AT: "ya aika a kawo mas wuta domin yă iya ganin wanda ke cikin kurkun har yanzu"
Kalmar nan "wuta" na nufin abu mai iya ba da haske. AT: "tocila" ko kuma "fitulu"
"ya shiga kurkukun da sauri"
Mai tsaron Kurkukun ya kaskantar da kansa ta wurin durkusawa a gaban Bulus da Sila.
"ya fitar da su wajen kurkuku"
AT: "me nake buƙata in yi domin Allah ya cece ni daga zunubaina"
AT: "Allah zai cece ka" ko kuma "Allah zai cece ka daga zunubanka"
A nan "gida" na nufin mutanen da ke gidan. AT: "dukkan 'yan gidanka" ko kuma "iyalinka"
A nan "magana" na nufin sako. AT: "Sai suka faɗa masa sakon Ubangiji Yesu"
AT: "Bulus da Sila suka yi wa mai tsaron kurkukun baftisma tare da dukkan iyalinsa"
Ana amfani ne da wannan kalmar a sa alamar dakatawa daga ainihin labarin. Anan Luka yana faɗin abu na ƙarshe a labarin da aka fara a [16:16]
A nan "sako" na nufin "kalma" ko kuma "umarni." AT: "suka aika da sako ga masu tsaron" ko kuma ""suka ba da umarni ga masu tsaron"
A nan "aika" na nufin cewa hukumomin su aike wani yă kai wa masu tsaron sakonsu.
"Ku sake mutanen nan" ko kuma "Ku bar mutanen nan su tafi"
"ku fita daga kurkuku"
Mai yiwuwa Bulus yana magana da mai tsaron kurkukun, amma yana nufin cewa mai tsaron kurkukuun ya gaya wa hukumomin abinda ya faɗa. AT" ya ce wa mai tsaron kurkuku"
A nan "Su" na nufin hukumomin da sun umarci sojoji su yi masu duka. AT: "Hukumomin sun umarci sojojinsu su yi mana duka a fili a gaban jama'a"
mu da muke Romawa ne, sun kuma sa sojojin su suka sa mu a kurkuku ba tare da wata shaida a kotu cewa muna da laifi ba"
Bulus yana amfani ne da wannan tambayan don ya nanata cewa ba zai bar hukumomin su fitar su daga garin a asirce ba bayan da sun yi wa Bulus da Sila ba dadi. AT: "Ba zan taɓa bar su su fitar mu daga garin nan a asirce ba!"
A nan an yi amfani ne da "da kansu" domin nanatawa.
Zaman 'ɗan Roma na nufin zaman tabbaceccen dangari Lardin. Yangarinci na ba da yanci daga tsanantawa da kuma yanci a sauare mutum kamun hukunci. Shugabanen garin na tsoron cewa, shugabani mafi muhimmanci na gaba da su na iya sanin yadda yan garin suka yi wa Bulus da Sila ba dadi.
A nan ana iya juya "zo" zuwa "je"
...
A nan "'yan'uwa" na nufin masubi, ko maza ko mata. AT: "sun ga masubin"
1Bayan sun wuce biranen Amfibolis da Aboloniya, sun iso birnin Tasalunika, in da akwai wata majami'ar Yahudawa a wurin. 2Bulus, kamar yadda ya saba, ya nufi wurinsu, yana tattaunawa da su har Asabaci uku, daga cikin littattafai.3Bulus ya bude littattafai yana bayyana masu cewa, dole ne Almasihu ya sha wahala, ya kuma tashi daga matattu. Ya ce, "Wannan Yesu kuwa da nake sanar maku, shine Almasihu". 4Wasu Yahudawa sun yarda, sun bi Bulus da Sila, da wadansu Helenawa, da Shugabannin Mata da jama'a da yawa.5Yahudawan da basu ba da gaskiya ba suka cika da kishi, suka dauki wadansu 'yan ta'adda daga cikin kasuwa, suka tada tarzoma cikin birnin, mutane da yawa na bin su. Sun kai hari a gidan Yason, da niyyar fitar da Bulus da Sila a gaban jama'a. 6Amma da ba su ga Bulus da Sila ba, suka ja Yason da wasu 'yan'uwa masu bi zuwa gaban mahukuntar birnin, suna cewa, "Wadannan ne fa masu ta da zaune tsaye, gashi sun zo mana. 7Wadannan mutane da Yason ya marabta, sun saba wa dokokin Kaisar; Suna cewa akwai wani sarki mai suna - Yesu."8Da taron jama'a, da mahukuntan birnin suka ji haka, sun damu. 9Bayan da sun amshi kudi daga wurin Yason da sauran 'yan'uwan, sai suka sake su.10A wannan daren, 'yan'uwa masu bi suka fitar da Bulus da Sila, suka aike su garin Biriya. Da isar su can, su ka nufa majami'ar Yahudawa. 11Mutanen Biriya daban suke da na Tasalunika, sun yarda da sakon Bulus da zuciya daya, suna kuma binciken littattafai kowace rana domin su tabbatar da sakon Bulus, ko gaskiya ne. 12Saboda haka mutane da yawa cikin su sun ba da gaskiya, tare da wadansu sannanun mata Helenawa da maza da yawa.13Amma da Yahudawan Tasalunika suka ji cewa Bulus yana wa'azin kalmar Allah a Biriya, sun haura can, sun tada hankulan jama'a. 14Nan da nan, masu bi na Biriya sun dauki Bulus sun aika shi zuwa teku, an bar Sila da Timoti a Biriya tukuna. 15Wadanda sun fitar da Bulus, sun kai shi har zuwa birnin Atina. Bulus ya ba su sako, su fada wa Sila da Timoti suyi hanzari su same shi.16Sa'anda Bulus yana jiran zuwan Sila da Timoti a Atina, ya yi fushi a ransa, da ya ga birnin cike da gumakai. 17Ya tattauna da Yahudawa a cikin majami'a tare da masu yin sujada ga Allah, da kuma wadanda yake samu a kowace rana, a kasuwa.18Amma wadan su Abikuriyawa da masana sun yi karo da shi. Wadansun su na cewa, "Menene wannan sakaren ke cewa?" Wadansu kuma sun ce, "Da alama mai wa'azi ne na wasu alloli dabam," domin yana wa'azin Yesu da tashin sa daga matattu.19Suka dauki Bulus zuwa Tudun Arasa, suna cewa, "Ko za ka sanar mana da wannan sabuwar koyaswar taka? 20Abubbuwan da kake fadi, baki ne a gare mu. Muna so mu san ma'anar su." 21(Atiniyawa da bakin da ke cikinsu, suna ba da lokacin su ga fadin sabobbin abubuwa da sauraron su).22Bulus ya tsaya a tsakiyar Tudun Arasa ya ce, "Ku mutanen Atiniya na lura masu kwazon addini ne ku. 23Na lura da abubuwan sujadar ku yayin da nake zagawa, amma na ga wani bagadi da rubutu a kansa mai cewa, "Ga Allah wanda ba a sani ba." Abin da kuke bauta wa cikin rashin sani, shi nake sanar maku.24Allahn da ya yi duniya da kome da ke cikinta, tun da ya ke shine Ubangijin sama da kasa, ba ya zama a haikalin da mutane suka gina da hannu. 25Ba ya neman taimakon kowa, babu kuma wanda ya isa ya ba shi. Shine ke ba da rai, da numfashi da kowanne abu.26Daga mutum daya ya hallici dukan al'umman duniya, ya rarraba, ya kuma sanya kowa a inda ya shirya masa. 27Domin su nemi Allah ko za su iya kaiwa zuwa gareshi su same shi, ga shi kuwa ba ya nesa da kowannenmu.28A cikinsa muke rayuwa, muna walwala, kamar yadda wani daga cikin masananku yace, 'Mu 'ya'yansa ne'. 29Idan mu 'ya'yan Allah ne, bai kamata mu danganta Allah da zinariya ko azurfa, ko kuma duwatsu da itatuwa da an sassaka ba.30Saboda haka ne, Allah ya kawar da kwanakin jahilci, amma ya ba da umarni kowa a ko'ina ya tuba. 31Akwai ranar da ya shirya zai yi wa duniya shari'a cikin adalci, ta wurin mutumin da ya zaba. Allah ya nuna wannan mutumin, ta wurin ta da shi daga matattu".32Da mutanen Atina sun ji batun tashi daga matattu, wadansu suka yi wa Bulus ba'a; amma wadansu kuma sun ce, "Za mu saurare ka kuma, a kan wannan maganar." 33Bayan haka, Bulus ya bar su. 34Amma wasu maza a cikinsu sun yarda da bisharar, sun ba da gaskiya, hade da Diyonisiyus dan Majalisar Tudun Arasa da wata mace mai suna Damaris, da wadansu tare da su.
Wannan na cigaba da labarin tafiyar bishara ne na Bulus, Sila, da Timoti. Sun isa garin Tasalonica, da saukin ganewa ba tare da Luka ba, tun da ya ce "su" ba "mu" ba.
A nan kalmar nan "su" na nufin Bulus da Sila.Ƙwatanta [16:40] Kalmar nan "su" na kuma nufin Yahudawa da ke majami'a a Tasalonica. check: them and they
A nan amfani ne da wannan kalmar a nuna kauchewa daga ainihin labarin. Anan Luka, marubucin, ya fara faɗin wata sabuwar bangaren labarin.
"sun yi tafiya ta"
Waɗannan su ne biranen da ke gaɓar teku a Makidoniya.
A nan ana iya juya kalmar nan "zo" zuwa "je" ko kuma "iso." AT: "suka iso birnin" ko kuma "suka iso garin"
"kamar yadda halinsa yake" ko kuma "kamar yadda ya saba yi." Bulus ya saba zuwa majami'a a ranar Asabar lokacin da Yahudawa za su kasance.
"a kowace rasar Asabar ha makonni uku"
Bulus yana masu bayanin abinda Littattafain ke nufi domin ya hakikanta wa Yahudawa da cewa Yesu shafaffe na Allah ne
"yana basu dalilai" ko kuma "yana muhawara da su" ko kuma "yana bincikawa da su"
Wannan na iya nufin 1) Ana maganar faɗin ma'anar littattafai a yadda mutane za su iya fahimtar ne kamar Bulus yana buɗe wani abu ne da mutane na iya ganin abinda ke cikinsa ko kuma 2) Bulus yana ainihim buɗe wata littafi ne sa'annan yana karatu daga cikinta.
"yana cikin shirin Allah"
"yă dawo da rai"
Daga cikin waɗanda sun mutu. Wannan bayyanin na bayyana dukkan matattun mutane gabaɗaya da ke ƙarƙashin duniya. Dawuwa daga cikinsu na maganar zama rayayye kuma.
AT: "Yahudawa sun gaskanta" ko kuma "Yahudawa sun fahimta"
"sun haɗa hannu tare da Bulus"
Wato Halenawa da ke yi wa Allah ibada amma ba su juya zuwa ga addinin Yahudanci ta wurin kaciya ba.
Wannan ma bai ka ma a nanata ba cewa shugabanin mata da yawa sun bi su. AT: "Shugabannin mata da yawa"
Ana maganar yin kishi kamar wani abu ne da ake iya cika da shi. AT: "cika da kishi sosai" ko kuma "yi matuar fushi"
Ana iya bayana a fili cewa waɗannan Yahudawan sunsa kishi cewa wasu yahudawa da Girkawa sun gaskanta da jawabin Bulus.
A nan "ɗauki" bai nuna cewa Yahudawan sun ɗauke su da ƙarfi ba ne. Amma yana nufin cewa Yahudawan su rinjaye su su taimake su.
"wasu mugayen mutane." Kalmar nan "mutane" na nufin musamman maza ne.
"daga cikin garin." Wato wurin da ake harkokin siya da sayay da abubuwa, shanike, da ayyuka daban daban kenan.
A nan "birni" na nufin mutanen da ke garin. AT: "suka sa mutane garin suka ta da hargitsi" ko kuma "suka sa mutanen garin suka ta da faɗa"
Wannan na iya nufin cewa mutanen suka riƙa jefa duwatsu a gidan domin su balle kofar gidan.
Wannan dai sunan wani mutum ne.
Wannan na iya nufin ko kuma "jama'a" 1) shugabanin ƙasa ko taron masu yanke shari'a ko ɗaukan shari'a ko kuma 2) taron 'yan banza ko 'yan iska.
AT: "wasu masubi"
"gaban ma'aikatan hukuma"
Mutanen Yahudawa kenan suna magana, kuma wannan jimlar "Waɗannan" na nufin "Bulus da Sila."
Wannan jimlar wata hanya ne na cewa Bulus da Sila suna ta da hargitsi duk inda sun je. Shugabannin Yahudawa suna kara gishri ga albarkacin da Bulus da Sila ke da shi da koyarwarsu. AT: "suna ta da rikici a ko ina a duniya" ko kuma "suna ta da rikici duk inda sun je"
Wannan jimlar na ba da alamar cewa Yason ya amince da jawabin manzannin mai ta da hargitisi.
"sun damu"
Yason da sauran mutanen sun biya ma'aikatan hukumar garin kuɗi a matsayin ɗaukan alkawarin zaman lafiya; ana iya mayar masu da wannan kuɗin idan kome ya yi daidai ko kuma ana iya amfani da shi a gyara abubuwan da suka lalace saboda hargitsin da ya faru.
Kalmar nan "sauran" na nufin sauran masubi da Yahudawan suka kawo gaba ma'aikatan hukuma.
,"ma'aikatan hukumar sun bar Yason da sauran masubin sun tafi"
Kalmar nan "'yan'uwa masubi" na nufin maza da mata masubi. AT: "masubin"
Waɗannan mutane ta musamman suna da marmarin bimbini da tunani sosai game da sabobin koyarwa fifye da sauran mutane. AT: "sun fi shirya zukatansu" ko kuma "suna da marmarin kasa kunne"
A nan "sakon" na nufin koyarwar. AT: "su saurare koyarwar"
Waɗannan mutanen Biriyan suna shirye su bincika koyarwar Bulus daga Littafi Mai Tsarki.
"suna karatun littafai suna kuma kintata ta a kowace rana"
"abubuwan da Bulus ke koyarwa gaskiya"
AT: "sun je can sun hanzuga" )
sai sun tada jama'an" ko kuma "suka sa mutanen sun zama da firgaba da tsõro"
Wato maza da mata masu bi. (Dubi:
"zuwa gaɓar teku." Dagan nan mai yiwuwa Bulus zai yi tashi ya yi wata tafiya zuwa wata gari.
"masu wa Bulus rakiya" ko kuma "waɗanda suke tafiya tare da Bulus"
"ya faɗa masu cewa su gargadas da Sila da Timoti."
A nan "ransa" na nufin Bulus da kansa. AT: "hankalinsa ya tashi domin ya ga cewa garin yana cike da gumakai ko ta ina" ko kuma "ganin gumakai a ko ina a garin ya tayar masa da hankali"
ya yi muhawwara" ko kuma "ya yi shawara" Wato akwai hulda da masu sauraro, ba wai Bulus yana ta jawabi shi kaɗai ba. Su ma suna magana da shi.
Wato Al'ummai (wanda ba Yahudawa ba) da ke Yabon Allah suna kuma bin sa, amma ba su kiyaye duka dokokin Yahudawa.
"a cikin taron jama'a." Wurin harkokin siya da sayarwa.
Waɗannan mutanen sun gaskanta cewa dukkan abubuwa sun dai kasance haka ne kawai kuma allolin suna fama da farin ciki, don haka, ba su damu da yin mulki a bisa duniya ba. Sun musunce tashin mattatu, don suna son annashuwa ne kurum.
Waɗannan mutanen sun gaskanta cewa ana samun 'yanci ta wurin yin murabus da ƙaddara. Sun ƙi cewa akwai wani Allah mai ƙaunar kowane mutum, da kuma tashin mattatu.
"sun saɗu da shi"
"Waɗansu masanan sua cewa"
A nan amfani ne da kalmar nan "sakare" wa sunsaye da ke cin hatsi a masayin abincinsu. Yana nufin mutumin da ke da karancin sani game da wani abu. Masanan suna cewa Bulus yana da karancin sani wanda basu isa su sa a saurare shi ba. AT: "Menene wanna mutum marar ilimi"
"Waɗansu masanan kuma sun ce"
"Ga alama kamar shi mai shelar" ko kuma "Kamar yana da nufin tarin mutane ne su gaskanta sa nasa irin sani"
Ba wai wannan tana nufin "bare" ba ne, amma yana nufin "bãƙi", wato, Allolin da Girkawa da Romawa ba su masu sujada ba ko basu san da su ba.
Ba wai sun ɗaura Bulus ba. Masanan sun gayyace Bulus ya yi magana da shugabanninsu bisa ga ka'ida.
A "Tudun Arasa" ne shugabannin sukan haɗu. AT: "zuwa wurin shugabannin da ke haɗuwa a Arasa"
A nan shugabannin Tudun Arasa ne ke magana. Ana iya sanar da wannan a wata sabuwar jimala. AT: "Tudun Arasa. Shugabannin sun ce wa Bulus"
Wannan wata sanannen dutse ne mai tudu a Atiniya da kotun kolin Atiniya suka hadu.
Ana maganar koyarwar Bulus game da Yesu da kuma tashin mattatu kamar wani abu ne da iya kai shi ga wani. AT: "Domin kana koyar da wasu abubuwa ne da bamu taba jin su ba"
Ana amfani ne da waɗannan kalmomin a datsa aya ga ainihin labarin. Anan, Luka yana ba da takaitaccen tarihin mazaunan Atiniya ne da kuma marmarin da suke da shi na koyan sabobin abubuwa"
Wannan kalmar "dukkan" na nufin masu yawa. AT: "yanzu Atiniyawa masu yawa da bãƙin da ke cikinsu" ko kuma "yanzu mafi yawan Atiniyawa da bãƙin da ke cikinsu"
"Atiniyawa" na nufin mutane daga Atiniya, wata gari kusa da gaɓar teku kasa da Makidoniya (ƙasar Helas ayau" )
"'yan wasu ƙasashe da ban"
Ana maganar "lokaci" ne anan kama wani abu ne da mutume ke iya ba wa wani. AT: "suna amfani da lokacinsu ga faɗi ko sauraro" ko kuma "basu yin komai ba illa faɗi ko sauraro"
"tattauna sabobin sani" ko kuma "suna faɗin abubuwa da ke sabobi ne a gare su"
Bulus yana nufin yadda Atiniyawa suke nuna wa allolinsu girma a fili ta wurin adduo'i, gina bagadi, da kuma ba da hadayu"
"Domin da nake wucewa" ko kuma "da nake tafiya"
Wannan na iya nufin 1) ga wani Allah ta musamman da ba a sani ba" ko kuma 2) ga wani allag da ba sani ba" Wannan ita ce wata rubutu ne ta musamman ko kuma alama da aka sa a wannan bagadi.
A hanya mafi dacewa, "duniya" na nufin sama da duniya da kamai a cikinsu.
"domin shi ne Ubangiji" Anan "shi" yana nufin allahn da ba sani ba da aka ambata a [17:23] da Bulus ke yin bayani shi ne Ubangiji Allah.
A nan amfani da kalamun nan "sama" da "duniya" gabadaya a nuna cewa dukkan abubuwa da ke sama da duniya.
A nan "hannaye" na nufin mutane. AT: "gina da hannayen mutane" ko kuma "da mutane suka gina"
A nan "taimako" na nan kamar yadda likita ke taimake mutum marar lafiya har ya samu lafiya kuma. AT: "Hannayen mutane basu taimake shi ba"
A nan "hannaye" na nufin mutum gabaɗaya. AT: "gun 'yan adam"
"domin shi da kansa." An kara kalmar nan "kansa" ne domin nanatawa.
Wato Adamu, mutumi na farko da Allah ya halita. A nan iya sanar da wanna a haɗe da Hauwa'u. Ta wurin Adamu da Hauwa'u ne Allah ya yi dukkan sauran mutane. AT: "iyali ɗaya"
AT: "ya kuma rarraba lokatai da wurare da za su kasance"
A nan "su nemi Allah" na nufin su yi marmarin sanin shi, haka kuma "kaiwa zuwa gareshi su same shi" na nufin yi masa addu'a da samun dangartaka da shi. AT: "domin su yi marmarin sanin Allah su kuma iya yi masa auud'a har ma su kasance a cikin mutanensa"
AT: "Ga shi kuwa yana kurkusa da kowane ɗayanmu"
"Saboda shi ne"
Da shike Allah ne ya hallice kowa, ana maganar dukkan mutane ne kamar su 'ya'ya ne na jiki ga Allah.
A nan "Allah" na nufin assalin Allah ko kuma halayarsa. AT: "cewa Allah"
AT: "wadda mutum ya yi amfani da gwanintarsa zuwa wani abu da ya kera" ko kuma "kamanni da mutane suka sassaka ta wurin dabararsa su"
"Domin abinda na faɗa maku gaskiya be"
"Allah ya bi ya ƙi hukunta mutane a lokacin jahilci"
Wannan na nufin kamun Allah ya bayyana kansa cikakke ta wurin Yesus Almasihu da kuma kamun mutane su san yadda za su yi sahihiyar biyayya da Allah.
Wato jama'a dukka, maza da mata. AT: "jama'a dukka"
da mutumin da ya zaɓa zai yi wa duniya shari'a cikin adalci"
A nan "duniya" na nufin mutane dagaɗaya. AT: "zai yi wa dukkan mutane shari'a"
"cikin gaskiya" ko kuma "daida"
"Allah ya nuna zaɓin sa da ya yi na wannan mutumin"
Waɗannan ne mutanen da ke nan a Tudun Arasa suna sauraron Bulus.
"waɗansu suka yi wa Bulus zuliya" ko kuma "waɗansu suka yi wa Bulus Dariya." Waɗannan din basu yarda cewa abu mai yiwuwa ne mutum da ya mutu yă dawo da rai kuma ba."
Diyonisiyus sunar wani mutum ne. Majalisar Tudun Arasa ɗaya daga cikin alkalai ne da ke majalisar Tudun Arasa.
Wannan sunar wata mata ne.
1Bayan haka sai Bulus ya tafi Antakiya daga nan, ya wuce Korinti. 2A can ya sadu da wani Bayahude mai sunan Akila, dan kasar Buntus ne; bai dade da zuwa garin ba, daga Italiya ya zo da matarsa mai suna Balkisu, saboda Kalaudiyas ya ba da umarni dukan Yahudawa su bar Roma; sai Bulus ya je wurinsu. 3Bulus ya zauna a gidansu don sana'arsu daya ce, wato, masu aikin Tanti ne.4Saboda haka Bulus na zuwa majami'a, yana yin nazari tare da su a kowace Asabaci. Yana kokari ya rinjayi Yahudawa da Helinawa. 5Amma a lokacin da Sila da Timoti suka iso Makidoniya, Ruhu ya matsa Bulus ya shaida wa Yahudawa cewa Yesu Almasihu ne. 6Lokacin da Yahudawa suka tayar masa suna zarginsa. Bulus ya kakkabe rigansa a gabansu yana cewa, "Alhakin jininku yana kanku; daga yanzu zan koma wurin al'ummai."7Da ya bar wurinsu, ya tafi gidan Taitus Yustus mai wa Allah sujada. Gidansa na kusa da majami'a. 8Kiristus shine shugaban majami'a, sai shi da dukan iyalin gidansa sun ba da gaskiya ga Ubangiji. Korantiyawa da yawa suka ji jawabin Bulus suka ba da gaskiya, aka yi masu Baftisma.9Da dare Ubangiji ya ce wa Bulus a cikin wahayi, "Kada ka ji tsoro, amma ka yi magana kada kuma ka yi shuru. 10Gama ina tare da kai, ba wanda zai cutar da kai, gama ina da mutane anan garin." 11Bulus ya zauna a nan tsawon shekara daya da wata shida, yana koyar masu da maganar Allah.12Amma da Galiyo ya samu zaman gwamnan Akaya, sai Yahudawa suka tayar wa Bulus har suka kai shi gaban dakalin shari'a. 13Suna cewa, "Wannan mutumin yana kokarin rinjayar mutane su yi sujadar da ta saba wa dokarmu."14Duk da haka kafin Bulus ya yi magana, Galiyo ya ce wa Yahudawa, "Ku Yahudawa in da karar ku ta wani babban laifi ce wanda ya aikata, da sai in hukunta. 15Amma tun da ya ke akan al'amurar, kalmomi ne, da ta sunaye da dokokin ku, ku je ku sasanta al'amuran ku."16Galiyo ya kore su daga dakalin shari'a. 17Saboda haka sai suka kama Sastanisu, suka yi masa duka sosai a gaban dakalin shari'a. Amma Galiyo bai damu da yadda suka karasa ba.18Bulus kuwa, bayan ya zauna tare da su na wasu kwanaki masu yawa, ya bar 'yan'uwan zuwa Suriya ta jirgin ruwa, tare da Balkisu da Akila. Kafin ya bar tashar jiragen ruwa da ke a Sankuriya, ya tafi saboda ya aske kansa, domin ya dauki alkawarin Banazare. 19Da suka iso Afisa, Bulus ya bar Balkisu da Akila anan. Shi kuwa ya shiga majami'ar Yahudawa yana nazari tare da su.20Da suka roki Bulus ya zauna da su na tsawon lokaci, bai yarda ba. 21Ya kama hanyarsa ya bar su ya ce, "In Allah ya yardar mani zan dawo wurinku wata rana." Sai ya shiga jirgin ruwa daga Afisa.22Daga saukar su a Kaisariya, sai ya haura zuwa Urushalima ya gai da iklisiya daga nan ya tafi Antakiya. 23Bayan ya zauna na dan lokaci a wurin, Bulus ya kama hanyarsa zuwa yakin Galatiya da Firjiya anan ya karfafa almajirai.24A nan dai akwai wani Bayahude mai suna Afolos, dan asalin Iskandariya ne da haihuwa, ya zo Afisa. Shi masani ne a maganar Allah. 25Afolos dai ya sami horo daga maganar Ubangiji. Shi mai kokari ne a ruhu, yana wa'azi da koyarwa daidai game da Yesu. Amma ya san da Baftismar Yahaya ne kadai. 26Afolos ya fara wa'azinsa da gabagadi a cikin majami'a. Da Balkisu da Akila suka ji shi sai suka yi abokantaka da shi, suka kara bayyana masa game da labarin hanyar Allah mafi daidai.27Da ya so ya wuce zuwa cikin Akaya 'yan'uwa suka karfafa shi, sun rubuta wa almajiran da ke a Akaya, don su karbe shi da hannu biyu. Da ya iso wurinsu, ya kuwa karfafa 'yan'uwa da sun ba da gaskiya ta wurin alheri. 28Afolos ya ba Yahudawa mamaki da irin ikon da yake da shi da gwanintarsa, yadda yake nunawa daga nassoshi cewa Yesu shine Almasihu.
Wannan wata bangare ne labarin tafiye tafiyen Bulus yayin da ya tafi Korintus.
Ana gabatar da Akila da Bilkisu ne a labarin a ayoyi 2 da 3 da kuma takaitaccen tarihinsu.
"Bayan da waɗannan abubuwa sun faru a Atina"
Atina itace ce wata birni mafi muhimmanci a Hellas. Duba yadda aka juya wannan a [17:15]
Wannan na iya nufin 1) Bulus ya bi ya same ko kuma 2) Bulus ya yi niyyar samun.
A nan jimlar nan "wani" na gabatar da wani sabon mutum kenan a labarin,
Buntua wata lardi ce da ke kudancin gaɓar tekun baƙin Teku.
Wannan na iya nufin a shekaran da ta gabata.
Wannan sunar wata ƙasa ne. Roma itace cibiyar garin Italiya.
Kalaudiyas ne shugaban Roma a wannan lokacin. Duba Yadda aka juya wannan a [11:28]
"yana irin aikin da suke yi"
"Saboda haka Bulus yayi muhawara" ko kuma "Saboda haka Bulus ya tattauna." Ya ba da dalilai. Wato a maimakon wa'azi kawa, Bulus yayi magana ya kuma hulda da su.
Wannan na iya nufin 1) "Ya sa Yahudawa da Halinawa su gaskanta" ko kuma 2) "Yana ta ƙoƙarin rinjayar Yahudawa da Halinawa."
AT: "Ruhu ya tilasta Bulus"
Wannan wata alama ce da ke nuna cewa Bulus ba zai cigaba da koya wa Yahudawan game da Yesu. Yana barinsu ga hukuncin Allah.
Ana "alhaki" na nufin alhakin laifinsu. "kanku" kuma anan yana nufin mutum gabaɗaya. Bulus yana faɗi wa Yahudawan cewa su ne da hakin hukuncin da za su fuskanta domin rashin jinsu idan su ƙi tuɓa. AT: "Ku ne da ɗaukan hakin hukuncin zunubinku"
Waɗannan sunayen maza ne.
Mai yi wa Allah sujada Bahaline da ke yabon Allah yana kuma binsa amma ba lallai ne yana kiyaye dukkan dokokin Yahudawa ba.
Wani jahili mai da ke tallafa wa tafiyar da majami'a, ba lallai malamin ba.
A nan "gida" na nufin mutanen da ke zama tare. AT: "mutanen da ke zama tare da shi a gidansa"
AT: "sun samu yin baftisma"
Ubangiji yana ba da umarni ɗaya a hanyoyi biyu don ya nanata wa Bulus cewa lallai yă cigaba da wa'azi. AT: "Kada ka kuskura ka ji tsoro, a maimakon haka, ka cigaba da magana kuma kada ka yi shiru"
Ubangiji yana ba da umarni ɗaya a hanyoyi biyu daban daban don yă umarce Bulus da babban murya cewa ya cigaba da magana. AT: "lallai ne ka ci gaba da magana"
Ana iya sanar a fili abinda Ubangiji ke so Bulus yă faɗa. AT: "kada ka daina yin bishara"
"akawai mutane da yawa a wannan garin sa sun sa bangaskiyar su a gareni" ko kuma " mutane da yawa a wannan garin za su sa bangaskiyar su gareni"
Wannan ne maganar ne ke kammala wannan bangaren labarin. "maganar Allah" anan na nufin Littafi Mai Tsarki gabaɗaya. AT: "Bulus ya zauna a wurin ... yana koyar masu da Littafi Mai Tsarki"
Wannan sunan wani mutum ne.
Wannan na nufin shugabannin Yahudawan da basu gaskanta da Yesu ba.
"suka taru" ko kuma "suka haɗu"
Yahudawan sun ɗauki Bulus da ƙarfi ne zuwa gaban kotu. A nan "dakalin shari'a" na nufin wurin da Galiyo ke zama lokacin yanke hukunci a kotu. AT: "suka kai shi domin gwamna yă yanke masa hukunci a dakalin shari'a"
Galiyo shi ne gwamnar Roma na wannan lardin.
A nan "doka" na nufin dokar Musa da kuma al'adun Yahudawa na zamanin Bulus.
"Ni ba zan yanke hukuncin waɗanna zantukan ba"
"Galiya ya sallame su daga dakalin shari'a." Anan "dakalin shari'a" na nufin wurin da Galiyo ke zama lokacin yanke hukunci a kotu. AT: "Galiyo ya sa sun tashi a gabansa a kotu" ko kuma "Gaiyo ya sa sun bar kotun"
Wannan na ƙara nanata yadda mutanen ke ji. AT: "jama'a da yawa suka kama" ko kuma "da yawan su sun raruma"
Wannan na iya nufin 1) Haleniyawan sun dũke Sastanisu a kotun a gaban dakalin shari'ar domin shi shugaban Yahudawa ne ko kuma 2) mai yiwuwa Sastanisu mai bi ne cikin Almasihu, don haka, Yahudawa suka masu dũka a gaban kotu.
"Sastanisu" shi ne shugaban Yahudawa da majami'ar da ke Korintus.
"suka riƙa bubbuge shi" ko kuma "suka riƙa naushinsa"
Kalmar nan "'yan'uwan" na nufin masubi, maza da mata. AT: "ya bar 'yan'uwa masubi"
Bulus ya shigo wata jirgi ruwa da ya tashi zuwa ƙasar Suriya. Balkisu da Akila suka je tare da shi.
Wannan wata alamace da ke nuna cikar wa'adin. AT: "ya sa wani yă aske hashi kansa"
"yana tattaunawa tare" ko kuma "yana muhawara tare"
"da yake yi masu ban kwana"
"isowar su Kaisariya." Anyi amfani ne da wannan kalmar "sauka" domin nuna cewa sun iso a jirgin ruwa ne.
Ya yi tafiya zuwa birnin Urushalima. An yi amfani ne da jimlar nan "ya haura" domin Urushalima yana sama da Kaisariya a tadawa.
A nan "ikilisiya" na nufin masubi da ke Urushalima. AT: "ya gai da jama'ar ikilisiyar Urushalima"
Antakiya yana ƙasa da Urushalima a tadawa.
"Bulus ya yi gaba" ko kuma "Bulus ya tafi"
AT: Bayan da ya ɗan zauna a wurin kaɗan"
Wannan na nuna sun kauce daga ainihin labarin.
Jimlar nan "wani" na nuna cewa Luka yana gabatar da wani sabon mutum a wannan labarin.
"mutumin da aka haifa a garin Iskandariya." Wannan wata gari ne a Masar a arewacin gabarr tekun Afirka.
"ya iya magana"
"ya san maganar Allah sosai." Ya fahimci rubuce rubucen Tsohon Alkawali da kyau.
Wasu masubi sun koya wa Afolos yadda Ubangiji Yesu yake son mutane su yi rayuwa"
A nan "ruhu" na nufin shi Afolos da kansa. AT: "Shi mai aminci ne ƙwarai"
"Baftismar da Yahaya ya yi." Wannan kwatanci ne na baftismar Yahaya da yayi da ruwa da kuma baftismar Yesu wadda yake yi ne da Ruhu Mai Tsarki.
Ana maganar yadda Allah ya ke so mutane su yi rayuwa ne kamar wata hanya ne da mutum ke iya bi yă yi tafiya.
"cikakke"
"yă je yankin Akaya." Anyi amfani ne da kalmar nan "wuce" domin Afolos ya ketere Tekun Aijiya don ya kai Akaya daga Afisus.
Kalmar nan "'yan'uwa" anan na nufin masubi, maza da mata. Anan iya bayana a fili cewa waɗannan masubi ne a Afisus. AT: "'yan'uwa masubi da ke Afisus"
"sun rubuta wasika zuwa ga masubi da ke Akaya"
"da sun gaskanta cewa samun ceto ta wurin alherin ne" ko kuma "da ta wurin alherin Allah suka gaskanta da Yesu"
"A muhawara cikin Jama'a, Afolos da iƙo da gwaninta ya nuna wa Yahudawa kuskurensu"
"yayin da Yesu yake nuna masu ta wurin nassohi cewa Yesu ne Almasihu"
1Sa'adda Afolos yake a Koranti, Bulus ya zagaya kasar tudu ya zo birnin Afisa, a nan kuma ya sami wadansu almajirai. 2Bulus ya ce masu, "Ko kun karbi Ruhu Mai Tsarki sa'anda kuka ba da gaskiya?" Suka amsa, "A'a bamu taba jin labarin Ruhu Mai Tsarki ba.3Bulus ya ce, "Wacce irin baftisma aka yi maku?" Suka ce, "Baftismar Yahaya" 4Bulus ya amsa ya ce, "Yahaya ya yi wa mutane baftismar tuba, ya ce su ba da gaskiya wanda zai zo bayansa, wato, Yesu kenan."5Da mutanen suka ji haka, sai aka yi masu baftisma cikin sunan Ubangiji Yesu. 6Sa'adda Bulus ya dibiya hannu a kansu, Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauka a kansu suka yi magana da harsuna da kuma annabci. 7Su wajen mutum goma sha biyu ne.8Bulus ya shiga majami'a ya yi ta koyarwa gabagadi misalin tsawon wata uku. Yana bi da su cikin nazarin maganar yana fahimtar da mutane su gaskanta game da abubuwa da suka shafi mulkin Allah. 9Amma sa'adda wadansu Yahudawa suka taurare, suka ki yin biyayya, sai suka fara bata hanyar Almasihu a gaban taron. Saboda haka sai Bulus ya janye daga wurinsu tare da wadanda suka ba da gaskiya. Ya fara koyarwa a makarantar Tiranus. 10Haka ya cigaba shekaru biyu har duk mazaunan Asiya suka ji maganar Ubangiji, Yahudawa da Helenawa.11Allah ya yi manyan al'ajibai ta hannun Bulus, 12har marasa lafiya suka warke, mugayen ruhohi suka fito daga cikin mutane, sa'adda suka karbi kyallaye da mayafai daga jikin Bulus.13Amma akwai Yahudawa masu tsubu da suka biyo ta wajen, suka dauka wa kansu su yi amfani da sunan Yesu. Suka ce, "Mun dokace ku cikin sunan Yesu wanda Bulus yake wa'azinsa, ku fita." 14Wadanda suka yi wannan su bakwai ne 'ya'yan wani babban firist Bayahude mai suna Siba.15Mugun ruhun ya amsa ya ce, "Na san Yesu, na san Bulus, amma ku, su wanene?" 16Sai mugun ruhun da ke cikin mutumin ya fada a kan matsubatan ya fi karfinsu ya kuma bubuge su. Suka runtuma da gudu suka fice daga dakin tsirara da raunuka. 17Wannan ya zama sanannen abu ga dukan mutane, Yahudawa da Helenawa mazaunan Afisa. Suka ji tsoro kwarai, sunan Ubangiji Yesu ya sami daukaka.18Masu bi da yawa kuma, suka zo suka furta mugayen ayyukan da suka aikata. 19Masu sihiri suka kawo littattafansu suka kona a gaban mutane. Da aka yi jimilar tamaninsu, aka samu sun kai dubu hamsin na azurfa. 20Sai maganar Ubangiji ta yadu da iko ta hanyoyi da yawa.21Da Bulus ya kammala aikinsa na bishara a Afisa, Ruhu ya bishe shi sai ya bi ta Makidoniya da Akiya a kan hanyarsa zuwa Urushalima. Ya ce, "Bayan na je can, dole in je Roma." 22Bulus ya aiki almajiransa biyu Timoti da Irastus zuwa Makidoniya, wadanda suka taimake shi. Amma shi da kansa ya jira a Asiya na dan lokaci.23A wannan lokacin sai aka yi babban tashin hankali a Afisa game da wannan Hanyar. 24Wani Makeri mai suna Damatrayus wanda ke kera sifoffin gunkin azurfa na Dayana, wanda sana'a ce mai kawo wa makera riba sosai. 25Ya tattara makera ya ce da su, "Kun sa ni da wanan sana'a ne muke samun kudi mai yawa.26Kun gani kun kuma ji cewa, ba a Afisa kadai ba, amma har da fadin kasar Asiya wannan Bulus ya rinjayi mutane da yawa. Yana cewa babu alloli da ake kerawa da hannu. 27Ba sana'ar mu kadai ke cikin hatsari ba, amma har da haikalin allahnmu Dayana babba zai zama mara amfani. Ta haka za ta rasa girmanta, ita da dukan kasar Asiya da duniya ke wa sujada."28Da suka ji haka sai suka fusata kwarai, suka yi kira mai karfi suna cewa "Mai girma ce Dayana ta Afisa." 29Gari gaba daya ya rude, jama'a kuma sun hanzarta zuwa wurin taron. Kafin wannan lokaci, sun riga sun kama abokan tafiyar Bulus, wato Gayus da Aristakas wadanda suka zo daga Makidoniya.30Bulus ya yi niyya ya shiga cikin taron jama'ar, amma almajiran suka hana shi. 31Haka nan ma wadansu abokan Bulus da ke shugabanin yankin al'umma Asiya sun aika masa da roko mai karfi kada ya shiga dandalin. 32Wadansu mutane na kirarin wani abu, wadansu kuma na kirarin wani abu dabam, domin jama'a sun rude. Da yawa daga cikinsu ma ba su san dalilin taruwarsu ba.33Yahudawa suka kawo Iskandari ya tsaya a gaban taruwan jama'a. Iskandari ya mika hannunsa sama domin ya yi bayani ga jama'a. 34Amma da suka gane shi Bayahude ne, sai dukansu suka kwala ihu wajen sa'a biyu, "Mai girma ce Dayana ta Afisa."35Da magatakardar garin ya sha kan jama'a, sai ya ce, "Ya ku mutanen Afisa, wanene bai san cewa birnin Afisa cibiya ce na allahn nan Dayana mai girma da na sifar da ta fado daga sama ba? 36Tun da ba a karyata wadannan abubuwa ba, ya kamata ku yi shuru don kada ku yi wani abu a gaggauce. 37Gama kun kawo wadannan mutane a wannan dakin sharia ba a kan su mafasa ne na haikali ba ko kuma masu sabo ga allahnmu ba.38Saboda haka idan Damatrayas da makeran da ke tare da su na da wata tuhuma a kan wani, kotuna suna nan a bude masu shari'a kuma suna nan. Ba ri su kai karar junansu. 39Amma idan akwai maganganu na dubawa, za a daidaita su a taronmu na lokaci lokaci. 40Domin hakika muna cikin hatsarin zargi game da hargitsin yau. Babu dalilin wanan yamutsi domin ba mu da bayani a kansa." 41Da ya fadi haka, sai ya sallami taron.
Bulus ya tafi Afisus.
"Ƙasar tudu" wata yanki ne a Asiya da ake ce da ita a yau Turkey zuwa arewacin Afisus. Mai yiwuwa Bulus ya tafiya ta kasa ne a bisa tekun Aijiya zuwa Afisus (wato Turkey a yau) wadda ke gabacin Korintus ta teku.
Wannan kalmar na nuna alamar wata sabuwar bangaren labarin. Idan harshenku tana da wata hanya ta musamman na yin haka, kuna iya amfani da ita anan.
"ya yi tafiya ta"
Wato ko Ruhu Mai Tsarki ya sauko masu.
"bamu taɓa jin game da Ruhu Mai Tsarki ba"
AT: "wace irin baftisma aka yi maku?"
A nan iya juya wannan zuwa kammalallen jimla. AT: "An yi mana baftismar da Yahaya ke koyarwa akai"
AT: "baftismar da mutane ke roƙa a masu yayin da suka zo tuba"
A nan "wanda" na nufin Yesu kenan.
Wato wadda zai zo bayan Yahaya mai Baftisma nan gaba, ba wai mai binsa a jiki ba.
A nan "mutane" na nufin almajiran da ke magana da Bulus a Afisus. [19:1]
AT: "suka yi baftisma"
A nan "suna" na nufin iƙon da izinin Yesu. AT: "as matasyin masubin Ubangiji Yesu"
"ya dora hannayensa a bisa kansu." Mai yuwuwa ya dora hannayensa a bisa kafadan su ko a kansu. AT: "ya dora hannayensa a bisa kansu ya masu addu'a"
Ba kamar yadda yake a [2:3-4] ba. babu takamaimian bayani game da waɗanda sun fahimci abubuwan da suke faɗi.
Wannan na nuna kimamun mutanen da aka masu baftisma.
"mutum 12"
"Bulus yakan shiga taron majami'a na kimamun wata uku kuma a can yana magana da gabagadi"
"yana kawar masu da shakka da tabbacecen koyarwa"
A nan "mulki" na nufin shugabacin Allah a matsayin sarki. AT: "game da mulkin Allah a matsayin sarki" ko kuma "game da yadda Allah zai nuna kansa a matsayin sarki"
wato suka ƙi su ba da gaskiya. AT: "wasu Yahudawa sun ƙi su karɓa su kuma yi biyayya da sakon"
Ana maganar abinda Almasihu ke so mutane su gaskkanta da shi ne kamar wani hanya ne da mutum ae iya tafiya a cikinta. Kamar kalmar nan, "hanyar" wani laƙabi ne na Masubi a wannan lokacin. AT: "suka fara faɗin mugayen abubuwa wa taron game da bi" ko kuma "suka fara faɗa wa taron mugayen abubuwa a kan mabiyaen Almasihu da kuma mabiyan koyarwarsa game da Allah" (Dubi: and 9:2)
"suka fara faɗin mugayen abubuwa game da"
"a babbar ɗakin da Tiranus ke koyar da mutane"
Wannan sunan wani ne.
Wannan na iya nufin 1) Bulus ya yi wa'azin bishara ga jama'a da dama a dukkan Asiya ko kuma 2) Bisharar Bulus ya fito zuwa dukkan Asiya daga Afisus ta wurin Afisawan da kuma jama'ar da suka ziyarci Afisus da suka zo daga dukkan Asiya.
A nan "maganar" na nufin sakon. AT: "sakon Ubangiji"
A nan "hannu" na nufin Bulus da kansa. AT: Allah yana sa Bulus yă yi mu'ajizai ko kuma "Allah yana yin mu'ajizai ta wurin Bulus"
AT: "har man yayin da a kai wa marasa lafiya adikansa da kuma rigar aikin da suka taɓa Bulus"
Wannan na iya nufin 1) kayayyakin aiki da Bulus ya taɓa ko kuma 2) kayayyakin da Bulus ya saka ko ya yi amfani da su.
tufafu da ake iya sawa a kai
tufafin sa ake sawa a ayi aiki don su tare ainihin tufafun da mutum ya sa.
"marasa lafiya sun samu lafiya"
Wato mutanen da basu da lafiya. AT: "mutanen da ba lafiya" ko kuma "waɗanda basu da lafiya"
masu korin aljannu daga mutane ko wurare
A nan "suna" na nufin iƙon da izini
"Yesu" suna ne na yau da kullum a wannan lokacin, don haka masu tsubu suna son mutane su san wanda suke magana akai.
Wato iƙo da izininYesu. AT: "da izinin Yesu" ko kuma "da iƙon Yesu"
Wannan sunan wani ne.
"Na san Yesu da kuma Bulus" ko kuma "Na san Yesu, na Kuma san Bulus"
Ruhun ya yi wannan tambayan ne don yan nanata cewa matsubutan ba su da iƙo ko izini a kan mugayen ruhohi. AT: "amma ni ban san ku ba!" ko kuma "amma ku, baku da iƙo akai na!"
Wannan na nufin cewa mugun ruhin yake cikinsa ya dira akan matsubutan.
Matsubutan sun runtuma da gudu da jikunansu a tuɓe.
AT: "sun ɗaukaka sunan Ubangiji Yesu" ko kuma "sun ɗauki sunan Ubangiji Yesu da girma"
Wato iƙo da izinin Yesu.
"suka tattara litattafansu." Kalaman nan "litattafai" na nufin litattafan da ke ɗauke da ka'idodin sihiri.
"a gaban kowa da kowa"
"tumanin litattafan"
"50,000"
Kowane "azurfa" yana kusan kuɗin da ake biyan mai koduga a kowace rana.
"saboda waɗannan mannyan ayyuka, mutane masu yana sun ji bisharar Ubangiji Yesu"
An yi amfani ne da wannan kalmar don a sa alamar kaucewa daga ainihin labarin. Anan, Luka ya fãra faɗin wata sabuwar bangaren labarin.
"Bulus ya kammala aikin da Allah ke da shi dominsa a Afisa"
Wannan na iya nufin 1) Bulus ya zaɓa da taimakon Ruhu Mai Tsarki ko kuma 2) Bulus ya zaɓa a ransa, wato ya kudura a zuciyansa.
Akiya itace lardin Roma wurin da Korintus yake. Itace babbar birnin da ke ƙasar Helas kuma cibiyar lardin. Duba yadda aka juya wannan a [18:12].
"dole in kama hanya zuwa Roma"
Wannan sunan wani ne.
An ƙara bayyana a fili a ayoyin da ke gaba cewa Bulus ya tsaya a Afisus.
An maimaita wannan ne domin nanaci.
Wannan dai itace takaitaccen bayanni na farkon zancen.
"zuciyar mutanen ya ɓace ƙwarai" Duba yadda aka juya wannan a [12:18].
Wato na adinin Kirista kenan. Duba yadda aka juya wannan a [9:1]
Yadda aka yi amfani da kalmar nan "wani" yana gabatar da wani sabon mutum kenan a wannan labarin.
maƙerin tagula ne da ke aiki da su azurfa don yă kera kayan ado kamar su zinariya da sauransu.
Wannan dai sunan wani mutum ne. Damatrayus maƙerin azurfa ne a Afisus kuma yana gãba da Bulus da kuma ikkilisiyar da ke wurin.
"yana kawo kuɗi sosai ga duk masu ƙeran gumakai"
Sana'a itace aiki da mutum ke yi. AT: "sauran masu yin irin wannan aikin"
"kun zo ga sani da kuma fahimtar cewa"
Wato yadda Bulus ke hana mutane bautar gumakai kenan. AT: "ya sa mutanae da yawa suka daina bautar gumakai"
A nan "hannu" na nufin mutum gabaɗaya. AT: "Yana cewa gumakai da mutane ke ƙerawa ba ainihin alloli bane"
AT: "cewa mutane ba za su siya gumakan mu kuma ba"
AT: "mutane ba za su ga amfanin zuwa haikali don bautar allahnmu Artimas babba"
Girmar artimas yana samowa ne daga abinda mutane ke sammani da ita.
Wannan na nufin cewa jama'a masu yawa kenan domin a nuna cewa ita sananne ne a ko ina. A nan kalmomin nan "Asiya" da "duniya" na nufin jama'ar da ke Asiya da dukkan wuraren da aka sani a duniya. AT: "ita da jama'a da masu yawa a Asiya da sauran wurare a duniya ke bauta wa"
Wato maƙeran kena. AT: "suka yi fushi ƙwarai"
"suka daga murya sosai" ko kuma "suka yi ihu sosai"
Ana "gari" na nufin mutanen. AT: "Sai hankalin mutanen garin gabaɗaya ya tashi suka fara ihu"
Wannan dai taron 'yan banza ne ku kuma dai a ce na hargitsi ne.
Dandalin Afisus wuri ne da jama'a sukan taru domin tarurruka da kuma nishaɗi kamar su wasanni da kuma waƙoki da kaɗe-kaɗe. Wuri ne da ke waje da kujeru masu iya ɗaukan mutane dubbai.
Mutanen da ke tare da Bulus.
Waɗannan sunayen mutane ne maza
Dandalin Afisus wuri ne da jama'a sukan taru domin tarurruka da kuma nishaɗi kamar su wasanni da kuma waƙoki da kaɗe-kaɗe. Wuri ne da ke waje da kujeru masu iya ɗaukan mutane dubbai. Duba yadda aka juya "dandali" a [19:29]
Wannan sunan wani mutum ne.
Ana iya bayyani a fili cewa Iskandari yana nu na wa mutane ne da cewa ya son su yi shiru. AT: "ya motsa ga taron don su yi shiru"
"yana so ya yi wata bayyani"
Ana maganar ta da muryar mutane a lokaci ɗaya ne kamar suna ihun da murya ɗaya ne. AT: "cikin ɗaya" ko kuma "tare"
Wato "marubuci" ko kuma "sakatare" kenan.
Magatakardan ya yi wannan tambayan ne domin yă tabbatar wa taron cewa suna da gaskiya yă kuma karfafa su. AT: "kowa ya san cewa garin Afisus cibiya ce da ke kula da haikalin ... sama."
Magatakardan garin yana amfani ne da "bai" don ya nanata cewa dukkan mutane sun san da haka.
Jama'ar Afisa ne suna kula da kuma tsere haikalin Artimas.
Akwai sifar wata allah a cikin haikalin Artimas. An sifanta ta ne daga wata dutse ne da ta faɗo daga sararin sama. Mutane suka sammanain cewa dutsensa ta faɗo ne daga Zafsa, mai mulkin allolin Halenanwa (gumakai).
"Da shike kun san da waɗannan abubuwa"
"kada ku yi wani abu kamun ku zo kuna tunani aka"
ba tare da tunani sosai
Kalmomin nan "waɗannan mutane" na nufin Gayus da Aristakas ne, abokan tafiyar Bulus. (Dubi: [19:29])
"Domin abina nan da na faɗa maku gaskiya ne." Shi magatakardan garin ya faɗa a [19:37] cewa Gayus da Aristakas ba barayi bane ko masu zagin sha'anin addina ba.
Ana iya sanar da kalmar nan "ƙara" na zuwa "zargi" AT: "su na son su zargi wani"
Wakilan hukumar Romawa masu yanke hukuncin kiyaye doka a kotu
Wannan bata nufin cewa Dimitiriyas da waɗanda ke tare da sh zasu zargi juna. Yana nufin cewa wannan wuri ne da mutane gabaɗaya na iya faɗi zarginsu. AT: "Waɗannan mutane na iya zarge junansu"
"Amma idan kuna da wasu maganganu daomin tattaunawa"
AT: "sai mu daidaita a taron mu na lokaci lokaci"
Wannan na nufin taron jama'an gari gabaɗaya wanda shi magatakardar yake shugabancinsa.
AT: "cikin hatsarin zargi daga hukumar Romawa akan hargitsin da ta taso a yau.
1Bayan da rikici ya kare, Bulus ya aika a kira al'majiran, ya karfafa su. Sa'annan ya yi bankwana da su, ya tashi zai tafi Makidoniya. 2Bayan ya ratsa cikin lardunan yana yi wa masu bi gargadi sosai, sai ya zo kasar Helenawa. 3Sa'adda ya yi wata uku a wurin, Yahudawa suka kulla masa makirci, yayin da yake shirin hawa Jirgi zuwa Suriya, sai ya canza ra'ayi ya koma ta Makidoniya.4Masu yi wa Bulus rakiyar zuwa yankin Asiya sun hada da Sobatarus dan Burus daga Biriya; Gayus mutumin Derbe; Timoti da Aristakus da Sakundus, dukansu masu bi ne daga Tasalonika; da Tikikus da Trofimus daga Asiya. 5Amma wadansu har suka rigaye mu, suka jira mu a Taruwasa. 6Da muka shiga Jirgi daga Filibi bayan kwanakin Gurasa mara yisti; bayan kwanaki biyar muka iske su a Taruwasa; kwananmu bakwai a wurin.7A rana ta fari ga mako, da muka taru domin karya gurasa. Bulus ya yi wa masubi jawabi, don ya yi niyyar ya tafi da wayewar gari; jawabinsa ya kai har tsakar dare. 8A benen da suka taru akwai fitilu da yawa.9Wani matashi mai suna Aftikos yana zaune a kan taga, barci mai nauyi ya dauke shi; da shike Bulus ya tsawaita jawabinsa, saurayin da shike barci mai nauyi ya dauke shi sai ya fado daga kan bene na uku aka dauke shi matacce. 10Sai Bulus ya sauka ya mike a bisansa ya rungume shi, sa'annan ya ce, "Kada kowa ya damu; domin yana darai bai mutu ba."11Sa'annan ya hawo kan bene domin cin gurasa tare da su, ya yi magana da su har gari ya waye daga nan ya bar su. 12Suka kawo saurayin da rai, sun sami ta'aziya ba kadan ba.13Amma mu, da muka riga Bulus zuwa gun Jirgin, muka shiga zuwa Asos, mun shirya mu dauki Bulus a jirgi amma shi ya kudurta ya yi tafiya a kasa. 14Da muka sadu a Asos, mun dauke shi a Jirgin ruwa zuwa Mitilitus.15Bayan tashin mu daga can, washegari muka zo tsibirin Kiyos. Washegari kuma muka zo birnin Militus. 16Amma Bulus ya kudurta wucewa Afisa a Jirgi, don kada ya bata lokaci a Asiya, don yana sauri in ya yiwu ranar Fentekos ta same shi a Urushalima.17Daga Militus ya aika a kira masa dattawan iklisiyar Afisa. 18Da suka zo wurinsa sai ya ce masu, "Ku da kanku kun san tun daga ranar da na sa kafata a Asiya, irin zaman da muka yi da kasancewar mu tare. 19Na bauta wa Ubangiji da tawaliu har da hawaye, da wahalun da na sha saboda makircin Yahudawa. 20Kun sani ban ji nauyin sanar da ku kowanne abu mai amfani ba, na bi ku gida gida ina koyar da ku abubuwa a sarari. 21Kunsan yadda na gargadi Yahudawa da Hellenawa game da tuba ga Allah da bangaskiya ga Ubangiji Yesu.22Yanzu fa, gashi, zan tafi Urushalima, Ruhu Mai Tsarki ya nuna mani a fili dole in je, ban san abin da zai faru da ni a can ba. 23Sai dai Ruhu Mai Tsarki ya nuna mani a kowanne gari cewa, sarkoki da wahalu suna jira na. 24Amma ban dauka cewa raina yana da wani amfani gare ni ba, domin in cika tsere da hidimar da na karba daga wurin Ubangiji Yesu, ta shaidar bisharan alherin Allah.25Yanzu fa, duba, na san dukanku, wadanda na yi wa wa'azin mulkin Allah, ba za ku kara gani na ba. 26Don haka na shaida maku a wannan rana, ba ni da alhakin jinin kowanne mutum. 27Don banji nauyin sanar maku da dukan nufin Allah a gare ku ba.28Saboda haka ku kula da kanku, da masubi da Ruhu Mai Tsarki ya sanya ku shugabanni. Ku kula ku yi kiwon iklisiyar Allah, wadda ya saya da jininsa. 29Na sani cewa bayan tafiyata, kyarketai masu zafi za su shiga tsakaninku, kuma baza su rangwanta wa masubi ba. 30Na sani har daga cikinku wadansu mazaje za su zo su fadi gurbattatun zantattuka, domin su janye almajirai zuwa gare su.31Saboda haka ku yi lura. Ku tuna da cewa shekara uku ban fasa yi wa kowannenku gargadi da hawaye dare da rana ba. 32Yanzu ina mika ku ga Allah, da maganar Alherinsa, wadda take da ikon gina ku ta kuma ba ku gado tare da dukan wadanda ke cikin kebabbu na Allah.33Ban yi kyashin azurfa, ko zinariya, ko tufafin wani ba. 34Ku da kanku kun sani na yi aiki da hannuwana, na biya bukatu na da na wadanda ke tare da ni. 35Na zama maku abin koyi a kowace hanya game da yadda za ku taimaka wa nakasassu ta wurin aiki, da yadda za ku tuna da maganar Ubangiji Yesu, maganar da shi da kansa ya ce: "Bayarwa tafi karba albarka."36Bayan da ya yi magana haka, ya durkusa ya yi addu'a tare da su duka. 37Dukansu kuwa suka yi kuka mai tsannani, suka rungume shi kuma suka sunbace shi. 38Suka yi bakin ciki musamman domin abin da ya ce masu, ba za su kara ganinsa ba. Sai dukansu suka yi masa rakiya zuwa wurin jirgin ruwa.
Bulus ya bar Afisa ya cigaba da tafiye tafiyensa.
"Bayan hargitsin"
"ya yi masu sallama"
"ya ƙarfafa masubin sosai" ko kuma "ya faɗi maganganun ƙarfafawa sosai ga masubi"
"Bayan da ya kasance a waurin na wata uku." Ana maganar lokaci anan kamar wani abu ne da mutum ke iya yi
AT: "Yahudawa suka kulla masa makirci a ɓoye"
Wannan na nufin wasu Yahudawa. AT: "Wasu Yahudaw"
"yayin da ya gama shirin hawa jirgi zuwa Suriya"
A nan kalmar nan "shi" yana nufin Bulus ne. (Dubi: [21:1])
"Masu tafiya da shi"
Waɗannan duka sunayen mutane ne, maza.
Duk waɗannan sunayen wurare ne.
Waɗannan sunayen mutane ne, maza. Duba yadda aka juya waɗannan sunayen a [19:29].
"waɗannan mutane duk sun tafi kamun mu"
Wannan na nufin lokacin idin adinin keterewa na adinin Yahudawa. Duba yadda aka juya wannan a [12:3]
Gurasa yana cikin cin abincin su na kullum. Wannan nu iya nufin 1) Wato cin abinci tare kurum. AT: "ci abinci" ko kuma 2) wato abinci da za su ci tare domin tunawa da mutuwa Yesu da tashinsa. AT: "domin cin Jibin Ubangiji"
"ya cigaba da jawabi"
Mai yiwuwa wannan itace hawa ta uku a gidan.
Wannan wata buɗadden wuri ne a bango da ke da wata dakali da zai ishe mutum zama.
Wannan sunan wani mutum ne.
Ana maganar barci ne kamar wani abu ne mai nauyi da ke iya ɗaukan mutum. AT: "ya shiga barci da kyau" ko kuma "ya gaji sosai sosai har a ƙarshe ya shiga barci sosai"
Da suka sauko su duba yanayin da yake ciki, sai samu ya riga ya mutu. AT: "bene na uku; da suka ɗauke shi, sun samu ya riga ya mutu"
Wato bene biyu daga bene da ke ƙasa. Idan al'adan ku ba ta kirga bene na ƙasa, ana iya sanar da wannan a matsayin "bene na biyu"
Gurasa wata abinci ne na yau da kullum a lokacin cin abinci. A nan "gutsuttura gurasa na iya nufin cewa rarraba wasu abincin ci ba gurasa kadai ba.
"ya tafi"
Wato Aftikos kenan [20:9]. Wannan na iya nufin 1) shi saurayi ne wanda ya fi shekara 14 ko kuma 2) shi saurayi ne tsakanin 9 da 14 ko kuma 3) kalmar nan "sauayi" na iya nufin cewa shi bara ne
Kalmar nan "kanmu" na ƙara nanaci ne sa'annan yana bambanta Luka da abokan tafiyarsa da Bulus, wadda bai yi tafiyar sa ta jirgin ruwa ba.
Asus wata gari ne ƙasa da Beram a ƙasar Turkey a baƙin Tekun Aijiya.
An ce da kanshi ne domin a nanata cewa abinda Bulus ya kudurta a zuciyar sa kenan.
"yayi tafiya ta ƙasa"
Mitilini wani gari ne da ke garin Mitilini a ƙasar Turkey a baƙin Tekun Aijiya.
"kusa da tsibirin" daga ƙetaren tsibirin"
Kiyos wata tsibiri ne da ba ta baƙin tekun ƙasar Turkey a yau a Tekun Aijiya.
"muka iso tsibirin Samas"
Samas wata tsibiri ne a kudancin Kiyos a Tekun Aijiya a baƙin tekun Turkey a yau.
Militas wata gari ne da ke da tashan jirgi a yamma da ƙaramar Asiya kusa da baƙin Kogin Miyanda.
Bulus ya kamo hanya a jirgin ruwa suka wuce tashan jirgi da ke Afisa, gaba da kudu domin su sauka a ƙasar Militini.
A nan maganar "lokaci" ne kamar wani abu ne da mutum ke iya amfani da shi ko ƙashewa. AT: "domin kada yă cigaba da tsayawa a wurin na 'yan lokaci" ko kuma "domin kada yă makara"
Militini tashin jirgi ne da ke yammacin ƙaramar Asiya kusa da kogin Miyanda. Duba yadda aka juya wannan a [20:15]
Ana amfani ne da kalmar nan "da kanku" ne domin nanata maganar.
A nan "kafa" na nufin mutumin gabaɗaya. AT: "Na shigo Asiya"
AT: "yadda na riƙa bi da kaina lokacin da nake tare da ku"
AT: "ƙasƙanci" ko kuma "halin ƙasƙanci"
A nan "hawaye" na nufin rashin jin daɗi da kuma kuka. AT: "Da kuka yayin da nake bauta wa Ubangiji"
Wannan ba ta nufin dukkan Yahudawa. Amma yana nuna mana ne waɗanda suka ƙulla haka. AT: "wasu Yahudawa"
"Kun san yadda ban taɓa yin shiru ba, amma na riƙa sanar da ku"
Bulus ya koya wa mutane a cikin gidajen su. An fahimci kalmomin nan "na koyar". AT: "Kuma na koyar da ku a lokacin da nake gidajenku"
AT: "cewa akwai buƙata su tuba a gaban Allah, su kuma gaskanta ga Ubangiji Yesu Almasihun mu"
AT: "domin Ruhu Mai Tsarki ne ya iza ni in tafi can"
"kuma ban san abinda zai faru da ni a wurin ba"
A nan "sarkoki" na nufin kamu da ɗaurin Bulus a kurku. AT: "za a ɗaura ni a kurku a sa ni in sha wuya"
Ana maganar hidima da tsere ne kamar wasu abubuwa ne da Yesu ya bayar sa'annan Bulus ya karɓa. Anan "tsere" da "hidima" abu ɗaya ne. Bulus ya maimaita su ne domin nanaci. AT: "domin in kammala aikin da Ubangiji Yesu ya umarta in yi"
Bulus yana maganar kammala aikin Yesu ya umarce shi ya yi ne kamar gudun tsere ne.
"ta gaya wa mutane bisharan alherin Allah." Wannan itace hidimar da Bulus ya karɓa daga wurin Yesu.
"Yanzu, ku mayar da hankali domin na san"
"na san cewa dukkanku"
A nan "mulki" na nufin shugabancin Allah a matsayin sarki". AT: "ga waɗanda na yi masu jawabin shugabancin Allah a matsayin sarki" ko kuma "ga waɗanda na yi masu jawabin yadda Allah zai bayyana kansa a matsayin sarki"
AT: "ba za ƙu ƙara gani na a wanna duniyan kuma ba"
A nan "jini" na nufin mutuwar mutum, wadda, a wannan yanayin, ba mutuwar jiki ba ne amma mutuwa a ruhu yayin da Allah ya furta cewa mutum yana da alhakin zunibi. Bulus ya gaskiya na Allah. AT: "Ni na na da alhakin kowa da Allah ya shar'anta da hakin zunubi ta dalilin ba da gaskiya ga Yesu"
A nan, wannan na nufin kowane mutum, miji ko mace. AT: "kowane mutum"
"Don ban yi shiru in ƙi faɗa maku ba" AT: "Domin haƙiƙa na faɗa maku"
"Dashike nan da na faɗa maku gaskiya ne," na nufin dukkan abinda Bulus ya faɗa a maganar sa game da barin su.
Shugabannin Ikkilisiya na da hakin kula da al'umman masubi kamar yadda makiyayin tumaki ke tsare garkensa daga ƙyarkeci. AT: "taron masubi da Ruhu Mai Tsarki ya ɗanka maku. Ku tabbatar kun kula da ikilisiyar Allah"
Ana kamanta zuɓar da "jinin" Yesu anan a matsayin biyar Allah ne saboda zunubanmu. AT: "jama'ar da Almasihu ya cetas da zunubansu ta wurin zuɓar da jininsa a bisa giciye"
A nan "jini" na nufin mutuwar Almasihu.
Ana ba da misalin masu ƙoyarwar ƙarya ne da kuma masu kawo illa ga taron masubi kamar su ƙyarketai ne da ke cin tumaki a garke. AT: "abokan gãba da yawa za su shiga cikinku don su yi wa taron masubi illa"
Ana maganar masu koyarwar ƙarya su rinjaye masubi su fara bin koyarwar sa ne kamar yana rinjayar tumaki ne daga garke zuwa wurinsu. AT: "domin su rinjaye mutane wadda suke almajirai su zama almajiransu"
"ku zama a faɗake ku kuma tuna" ko kuma "ku zama a faɗake kuna tuna"
"ku zama a farke da lura kuma" ko kuma "ku yi shirya." Ana maganar shirin shugabannin masubi domin duk wanda yana son ya yi wa taron masubi barna kamar yadda sojoji masu tsaro ne ke tsaro da kyau domin abokan gãba.
"Ku cigaba da tuna cewa" ko kuma "Kada ku manta cewa"
Ba cewa ake wai bulu ya koyar masu kowane rana har shekara uku ba, amma ya ɗauki lokaci cikin tsawon shekara uku.
"Ban daina faɗakad da ku ba"
Ana "magana" na nufin jawabi. AT: "Ina addu'a Allah yă cigaba da kula da ku yă kuma taimake ku ku da gaskanta da jawabin da na yi maku game da alherinsa"
a ba wa wani dabam hakin kula da wani ko wani abu.
Ana maganar bangaskiyar mutum ne kamar wani ganuwa ne da ake ginata sama da karfi kuma. AT: "wadda ke da ikon sa ku ƙara zama da ƙarfi a bangaskiyanku"
Ana maganar "maganar alherinsa" ne kamar Allah ne da kansa zai ba wa masubi gãdo. AT: "Allah zai ba ku gãdo"
Ana magana albarkun da Allah ke ba wa masubi ne kamar kuɗi ne ko kuma wasu dukiya da ɗa na iya gãda daga mahaifinsa.
"Ban yi marmarin kuɗin wani ba" ko kuma "Ban yi marmarin kuɗin wani don kaina ba"
Tufafi ma dukiya ne; yawansu shi ne yawan arzikin mutum.
Kalmar nan "hannu" a nan na nufin mutumin da kansa. AT: "Ina yin aiki ne da kaina in samu kuɗi in biya bukatuna"
"ku yi aiki domin ku samu kuɗi ku taimaka wa mutanen da ba su iya samo wa kansu"
AT: nakasassun mutane" ko kuma "waɗanda ba su da ƙarfi"
"marar lafiya"
A nan "magana" na nufin abinda Yesu ya faɗa.
Wato mutum yana samun tagomashin Allah yana kuma ɗandana farin ciki mai yawa idan ya ba wa sauran mutane fiye da yawan karɓawa daga wurin wasu.
Al'ada ne na yau da kullum a durkusa yayin da ake yin addu'a. Alama ce na kaskanci a gaban Allah.
...
Sumbacin mutum a kumatu alama ce na nuna ɗayantaka ku kuma ƙauna a Gabas ta tsakiya.
AT: "ba za ku ƙara ganina a duniyan nan kuma ba.
1Da muka rabu da su, muka shiga jirgin ruwa muka mike hanya zuwa birnin Kos, washegari sai birnin Rodusa, daga nan sai kuma zuwa birnin Batara. 2Da muka sami jirgi mai hayewa zuwa Fonisiya sai muka shiga.3Da muka hango tsibirin Kubrus muka bar shi a hagun mu muka nufi Suriya, muka sauka a birnin Taya domin a nan ne jirgin ruwan zai sauke kayansa. 4Bayan mun sami almajirai sai muka zauna can kwana bakwai. Al'majiran suka ce ma Bulus, ta wurin Ruhu, kada ma ya je Urushalima.5Bayan 'yan kwanaki muka cigaba da tafiyarmu. Dukansu da matansu da 'ya'yansu suka raka mu har bayan birnin. Sa'annan muka durkusa a bakin gacci muka yi addu'a muka yi sallama da juna. 6Sai muka shiga jirgin ruwa, su kuma suka koma gida.7Da muka gama tafiyarmu a Taya muka iso Talamayas. A nan ne muka gaisa da 'yan'uwa, muka zamna kwana daya da su. 8Washegari muka tashi muka tafi Kaisariya. Muka shiga gidan Filibus mai shaida bishara, daya daga cikin bakwai din, muka zauna da shi. 9Wannan mutum yana da 'ya'ya hudu mata, budurwai masu yin annabci.10Sa'anda muka zauna can 'yan kwanaki, wani annabi ya zo daga Yahudiya mai suna Agabus. 11Ya zo wurinmu ya dauki damarar Bulus ya daure tasa kafar da hannayensa ya ce, "Ruhu Mai Tsarki ya ce, 'Haka Yahudawa za su daure mai wannan damarar, zasu kuma bashe shi ga al'ummai.'"12Da muka ji wannan sakon, sai dukanmu da mazaunan wurin muka roki Bulus kada ya tafi Urushalima. 13Sai Bulus ya amsa ya ce, "Me kuke yi, kuna kuka kuna karya mani zuciya? Bama a shirye don dauri kadai nake ba har ma da mutuwa a Urushalima, sabili da sunan Ubangiji Yesu." 14Tun da Bulus bashi da niyyar a rinjaye shi, muka daina kuka muka ce, "Bari nufin Ubangiji ya tabbata."15Bayan wadannan kwanaki, muka dauki jakkunanmu muka haura Urushalima. 16Wadansu almjirai daga Kaisariya suka bi mu. Sun zo ne tare da wani ana ce da shi Manason, mutumin Kuburus mai bi na farko, wanda za mu zauna da shi.17Da muka isa Urushalima, 'yan'uwa suka marabce mu da farin ciki. 18Washegari Bulus ya tafi tare da mu zuwa wurin Bitrus, dukan dattawa kuma suna nan. 19Bayan ya gaishe su, sai ya shaida masu daya bayan daya abubuwan da Allah ya yi cikin al'ummai ta wurin hidimarsa.20Da suka ji haka, suka yabi Ubangiji suka ce masa, "Ka gani, dan'uwa, dubban Yahudawa sun bada gaskiya suna kuma da niyyar kiyaye shari'a. 21An kuma gaya masu a kanka cewa, kana koya wa Yahudawan da suke zaune cikin al'ummai su yi watsi da Musa. Kana koya masu kada su yi wa 'ya'yansu kaciya, kada kuma su bi tsofaffin al'adu.22Me ya kamata mu yi? Hakika za su ji ka zo. 23Sabo da haka ka yi abin da muka fada maka yanzu. Muna da maza hudu da suka dauki wa'adi. 24Tafi da wadannan ka tsarkake kanka tare da su, ka dauki dukan dawainiyar su dana askin kai. Ta haka kowanne mutum zai sani abubuwan da ake fadi a kanka karya ne. Za su sani cewa kai mai kiyaye shari'a ne.25Game da al'umman da suka bada gaskiya mun yi masu wasika, mun bada umarni su kaurace kansu daga sadakokin da aka mika wa gumaku, da jini, da abin da aka makare da kuma fasikanci. 26Sai Bulus ya dauki mazannan, washegari ya tsarkake kansa tare da su, suka shiga haikali, domin ya sanar da cikar ranakun tsarkakewarsu, wato ranar ba da sadaka domin kowanne dayansu.27Da kwanakin nan bakwai suka yi gab da cika, wadansu Yahudawa daga Asiya suka ga Bulus a haikali, sai suka zuga taro, suka danke shi. 28Suna ta kururuwa, "Mutanen Isra'ila ku taimaka mana. Wannan shine mutumin da ke koya wa dukan mutane ko'ina abubuwa gaba da mutane, da shari'a da kuma wannan wurin. Banda haka ya kawo Helenawa cikin haikalin nan ya kazantar da wannan wuri tsatsarka." 29Domin dama sun ga Tarofimas mutumin Afisa tare da Bulus cikin birni, suka yi zaton ya kawo shi cikin haikali.30Sai duk gari ya rude, mutane suka runtuma suka danke Bulus. Suka ja shi waje daga cikin haikalin, nan da nan aka rufe kofofin. 31Suna kokarin kashe shi kenan, sai labari ya kai wurin hafsan sojoji cewa Urushalima duk ta yamutse da tarzoma.32Nan take ya dauki mayaka da jarumawa, suka sheka da gudu wurin taron. Da mutane suka ga hafsan sojoji da rundunansa sai suka daina dukan Bulus. 33Sai hafsan ya tafi ya danke Bulus ya sa aka daure shi da sarkoki biyu. Ya tambaya ko shi wanene da kuma laifinsa.34Wadansu cikin taron suna ta kururuwa wadansu su ce wannan, wadansu su ce, wancan. Tunda hafsan bai fahimci abin da suke fadi ba, sabo da ihunsu, ya dokaci a shigar da Bulus farfajiyar sojoji. 35Da suka kai matakala, sojoji suka dauki Bulus sabo da tsananin husatar taron jama'a. 36Domin taron suka biyo baya suna ihu suna cewa, "A kashe shi."37An kusa shigar da shi farfajiyan kenan sai Bulus ya ce wa babban hafsan, "Ko ka yarda inyi magana da kai?" Hafsan ya ce, "Ka iya Helenanci? 38Ashe ba kai ne Bamasaren nan da kwanakin baya ka haddasa tawaye, ka dauki 'yan ta'adda dubu hudu ka kai su jeji ba?"39Bulus ya ce, "Ni Ba'ibrane ne daga birnin Tarsus a Kilikiya. Ni dan kasar babban birni ne. Ka amince mani in yi magana da mutanen." 40Da hafsan ya bashi izni, Bulus ya mike a kan matakala ya daga hannayensa sama ya yi nuni su yi shuru. Da wuri ya yi tsit, Bulus ya yi masu magana da Ibraniyanci. Ya ce,
Marubucin Luka, Bulus da abokan tafiyansu sun cigaba da tafiye tafiyensu.
A nan kalmar nan "mu" na nufin Luka, Bulus, da waɗanda ke tafiya tare da su, amma ba masu karatu ba.
"muka tafi birnin Kos" ko kuma "muka wuce zuwa garin Kos"
Kos wata tsibiri ne na Hellas daban da baƙin Turkey a yau da ke kudancin tekun jaha Aijiya.
Rodusa tsibirin Hallas ne da ke daban da tsibirin Turkey a yau a kudancin Tekun Aijiya a jiha kuduncin Kos dakuwa arewa ta gaba na Karita.
Batara wata birni ne a baƙin kogin kudu ta yamma na Turkey a yau kudancin Tekun da ke Tekun Bahar Rum.
A nan "jirgin mai hayewa" na nufin ƙungiyar da ke tafiya a jirgin. AT: "Da muka sami jirgin a da ƙungiyar da ke hayewa zuwa Fonisiya"
A nan dai "hayewa" ba ta nufin cewa jirgin tana kan hayewa ba amma tana nufin cewa jirgin za ta haye Fonisiya ba da jimawa ba. AT: "jirgi da za ta ketere ruwa" ko kuma "jirgin da za ta tashi"
"muka wuce tsibirin a gefen hagu" hagun itace gefen "masukin" jirgin ruwan.
A nan "jirgin" na nufin ƙungiyar da ke tafiya a jirgin ruwan. AT: "ƙungiyar da ke tafiya a jirgin za su sauke kayansa"
"Waɗannan masubi suka gaya wa Bulus abinda Ruhu Mai Tsarki ya bayyana masu. Suka "ta ce masa sau da dama"
AT: "Bayan kwanaki bakwai" ko kuma "Da lokacin tafiya ya kai"
Hali ne na yau da kullum a durkusa yayin da ake yin addu'a. Yin haka alama ce na kaskanci a gaban Allah.
"muka koma gida"
Talamayas wata gari ne a Taya ta kudu, Lebanon. Talamayas itace Akir, Isra'ila a yau.
"'yan'uwa masubi"
"bakwai" ɗin na nufin mutanen da aka zaɓa su raɓa abinci su kuma taimake gwamraye a 6:5.
"Filibus" daga aya 8.
mai bishara
A nan amafani ne da wannan kalmar anan don a sa alamar kauchewa daga ainihin labarin. Anan, Luka yana faɗin tarihin Filibus ne da 'ya'yansa, mata.
"budurwai huɗu mata da sukan karɓan maganar Allah su kuma ba da shi ga mutane.
Wannan na gabatar da wani sabon mutum ne a labarin.
Agabus mutumin Yahudiya ne.
"ya ciro ɗamarar Bulus daga ƙudun Bulus"
Ana sanar da sakon wani da cikin sanar da furcin wani. AT: "Ruhu Mai Tsarki ya ce haka ne Yahudawan Urushalima za su ɗaure ... ga al'ummain.
Wannan na nufin Yahudawan da za su aikata wannan, ba wai dukkan Yahudawa ba. AT: "shugabannin Yahudawa" ko kuma "wasu Yahudawan"
"miƙa shi"
AT: "ga masu yanke shari'a na al'ummai"
Wato masu iƙo a cikin al'ummai. AT: "al'ummai masu iƙo"
Bulus ya yi wannan tambaya ne domin yă nuna wa masubi cewa su daina ƙoƙarin jawo hankalinsa. AT: "Ku daina wannan abinda kuke yi. Kuka da kuke yi yana ƙarya mani zuciya"
Ana maganar sa mutum yin baƙin ciki ne kamar zuciya ne da ke ƙarye wa. A nan "zuciya" na nufin yadda mutum ke ji. AT: "sanyaya mini gwiwa" ko "baƙanta mini rai"
AT: "bama kadai don su ɗaure ni kawai ba"
A nan "suna" na nufin Yesu da kansa. AT: "sabili da Ubangiji Yesu" ko kuma "domin na ba da gaskiya ga Ubangiji Yesu"
AT: "ba ya so mu rinjaye shi ya je Urushalima"
AT: "Bari komai ta kasance yadda Aallah ya shirya ta"
"Akwai wani tare da su"
Manason wani ne daga tsibirin Kuburus"
Wato, Manason yana ɗaya daga cikin waɗanda suka fara gaskanta da Yesu.
A nan "'yan'uwa" na nufin masubi da ke Urushalima, ko miji ko mace. AT: "'yan'uwa masubi suka marabce mu"
"ya ba da ƙwaƙwaran labarin su duka"
A nan "ɗan'uwa" na nufin "ɗan'uwa mai bi"
Yana nan a bayyane cewa akwai wasu Yahudawa da ke ɓata koyarwar da Bulus ke yi. Shi bai hana Yahudawa kiyaye shari'ar Musa ba. Sakon sa dai shi ne basu buƙatan kaciya da wasu al'adu kamun Yesu yă iya cetonsu. Ana iya ƙara bayyana cewa shugabannim Yahudawa masubi da ke Urushalima na da sanin cewa koyarwar Bulus gaskiya ne.
AT: "Mutane sun gaya wa Yahudawa masubin"
A nan "Musa" na nufin shari'ar Musa. AT: "su daina kiyaye shari'un da Musa ya ba mu"
A nan maganar biyayya da tsofofin al'adu ne kamar al'adun ne suke jagora yayin da mutanen ki bi a baya. AT: "kada su yi biyayya da tsofofin al'adu" ko kuma "kada su gwaninta a tsofofin al'adu"
"al'adun da Yahudawa suka saba kiyayewa"
"maza huɗu da suka yi wa Allah alkawari." Wato irin alkawarai wanda mutum ba zai sha ruwan inabi ba ko kuma yă aske gashin kansa har sai bayan wasu lokatai da aka keɓe.
Sai sun tsarkake kansu kamun su iya shiga sujada a haikalli.
"ka biya masu dukkan buƙatunsu." Kashe kanshen za su tafi dukka wajen siyan ɗan tinkiya na mace da na miji, rago, da kuma hatsida baye bayen sha.
Wannan alama ne cewa mutum ya kammala alkawarin da ya yi wa Allah.
AT: "abubuwan da mutane ke faɗi a kanka"
Ana maganar kiyaye shari'a ne kamar shari'ar shugaba ne da mutane ke iya bi a baya. AT: "yi biyayya da shari'a" ko kuma "yi rayuwa da ta dace da shari'ar Musa da kuma sauran al'adun Yahudawa"
Waɗannanduka ka'idodi ne game da abinda za su iya ci. An hana su cin naman dabbobin da aka sadaukad wa gunki, nama da ke da jini a cikinta, da kuma naman dabban da aka maƙure domin akwai jini a cikinta. Duba yadda aka juya irin wannan jimlar a [15:20].
AT: "su guje naman dabba da wani ya sadaukad ga gunki"
Ana iya ƙara bayyani akan dabbobin da aka muƙure. AT: "daga dabbobin da wani ya maɍƙure" ko kuma "daga dabbobin da wani ya maƙure do a ci amma ba tare da an janye jininsa ba.
Wato mutane huɗun nan da suka ɗauki wa'adi.
Kamun ya shiga gefen haikali inda ake buƙatar Yahudawa su tsarkake kansu tukuna. Wannan tsarkakewar ya shafe ma'amalan da Yahudawa ke yi da Halenawa.
Basu shigo cikin wurin da babban firist ne kawai ke iya shiga a haikalin ba. Sun shiga harrabar haikali. AT: "suka shigo harrabar haikali"
Wannan wata hanyar tsarkakewa ne da ake buƙata su cika domin su iya shiga harrabar haikali.
AT: "har sai sun miƙa dabba domin sadaka"
Wato kwanaki bakwai na tsarkakewa kenan.
Ba wai Bulus yana cikin haikalin ne ba. Yana harraban haikalin ne. AT: "a harrabar haikali"
Ana maganar hanzuga mutane su yi matuƙar fushi da Bulus kamar sun zuka hankalin taron ne. AT: "suka sa mutane da yawa a cikin taron sun yi fushi ƙwarai da Bulus"
A nan "suka ɗanke shi" na nufin a "kama" ko kuma "riƙe." Duba yadda aka juya "suka ɗanke" a [5:18] AT: "suka riƙe Bulus"
"mutanen Isra'ila, da shari'ar Musa, da kuma haikali"
Yahudawa ne kawai akan bari shi shigo wasu wurare a cokon harrabar haikalin da ke Urushalima.
wannan karin bayyani ne. Luka yana bayyana dalilin da ya sa Yahudawa daga Asiya suna ɗaukan cewa Bulus ya kawo Bahalene cikin haikali.
Wannan shi ne mutumin da ake zargin Bulus cewa ya shigo da shi haikali wurinda Yahudawa ne kadai su ke shiga. Duba yadda aka juya sunan sa a [20:4]
Kalmar nan "duk" na nufin masu yawa. Kalmar nan "gari" na nufin Urushalima. AT: "Mutane masu yawa a barin suka yi fushi da Bulus"
"suka kama Bulus" ko kuma "suka riƙo Bulus"
An rufe kofofin domin kada a yi hargitsin a harrabar haikali. AT: "Nan da nan sai wasu Yahudawa suka rufe kofofin haikali. ko kuma " Nan da nan sai masu tsaron haikalin suka rufe kofofin"
A nan "labari" na nufin ɗan aika da ya je ya faɗi labarin. AT: "mai ba wa babban hafsan sojoji labari"
Ana amfani da jimlar nan "ya kai wurin" ne domin babbar hafsan yana wata sansani ne da ke haɗe da haikali a sama da harrabar haikali.
Wato shugaban sojojin Roma da ke shugabantar sojoji 600
Kalmar nan "Urushalima" na nufin Urushalima. Kalmar nan "duk" na nufin hankalin mutane masu yawa zai tashi. AT: "mutane da yawa a Urushalima suna yamutase"
Akwai mataka na sauka daga sansanin zuwa harrabar.
AT: "ya umarci sojojinsa su ɗaura shi"
Wannan na nufin cewa sun ɗaure Bulus kusa da sojojin Roma biru, ɗaya a kowane gefensa.
Ana iya sanar da wannan a matsayin ambacin abinda wani ya faɗa. AT: "Ya tambaya, 'Wanene wannan mutumin? Menene laifinsa?"
Babbar hafsan sojojin yana magana da taron ne, ba da Bulus ba.
Ana iya fahimtar kalaman nan "suna kururuwa" a jimla na baya. AT: "sai wasu suna kururuwa wani daban" ko kuma "sai wasu kuma a cikin taron na kururuwar wani abu daban"
Wato shugaban sojojin Roma da ke shugabantar sojoji 600.
AT: "ya dokaci sojojinsa su sgigar da Bulus"
Wannan sansanin yana haɗe sa wajen harrabar haikali.
AT: "Da Bulus ya shigo matakan sansanin, sojojin sun ɗauke shi"
Taron suka amfani ne da wata hanya mai sauki da kuma wata hanya daban na roƙo a ƙashe Bulus. AT: "Ku ɗauki ransa" ko kuma "Ku ƙashe shi"
AT: "Da sojojin suka yi shirin kawo Bulus"
Wannan sansanin yana haɗe sa wajen harrabar haikali.
Babban hafsan sojojin yana tambaya domin ya nuna mamakinsa cewa Bulus ba wanda yake tunanin shi ne ba. AT: "Ashe ka iya Halenanci. Ina tsammanin ko kai ne Bamasaren da ke haddasa tawaye a jeji ba, tare da 'yan ta'adda dubu huɗu"
Ba da jimawa ba kamun zuwa Bulus, wani mutum da masar wanda ba ambaci sunansa ba, ya haddasa tawaye ga Roma a Urushalima. Jim kaɗan sai ya tsere da gudu zuwa jeji, sai kuma shugaban sojojin yana mamamki ko Bulus ne wannan mutumin.
AT: "sa mutane suka tayar wa mulkin Roma"
"'yan ta'adda 4,000"
Wato taron Yahudawa masu tawaye da mulkin Roma da duk wanda ke goyon bayan Romawa.
"Na roƙe ka" ko "I na roƙon ka"
"don Allah ka amince mini" ko kuma "don Allah ka yarda mini"
AT: "hafsan ya amince wa Bulus ya yi magana"
Kalmar nan "matakala" a nan na nufin mataka zuwa sansanin.
Ana iya karin bayyanin dalilin da ya sa Bulus ya daga hannayensa. AT: "ya daga hannayensa domin mutanen su yi shiru"
Da mutanen suka yi tsit gabaƙiɗaya"
1"Yanuwa da Ubanni, ku saurari kariya ta zuwa gare ku yanzu." 2Da taron sun ji Bulus na magana a harshen Ibraniyawa sai sun yi tsit. Ya ce,3Ni Bayahude ne daga garin Tarwasa na Kilikiya, amma a karkashin Gamaliyal aka ilimantar da ni. An horar da ni sosai bisa ga bin hanyar dokokin kakkaninmu. Ina da himma ga bin Allah kamar yadda ku ma kuna da ita. 4Na tsananta wa wannan Hanyan har ga mutuwa; na daure maza da mata sa'annan na jefa su cikin gidan yari. 5Hakannan ma babban firist da dukan dattawa za su ba da shaida cewa na karbi izini daga wurinsu domin 'yan'uwa da ke a Dimashku, saboda in tafi can. Haki na shine in daure mabiyan Hanyan nan, in kawo su Urushalima domin a hukunta su.6Sa'anda ina cikin tafiya, ina kuma kusa da Dimashku, da tsakar rana sai farat daya ga babban haske daga sama ya haskaka kewaye dani. 7Na fadi kasa sa'anan na ji murya na ce da ni, 'Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mani?' 8Na amsa, 'Wanene kai, Ubangiji?' Ya ce mani, 'Nine Yesu Banazarat wanda kake tsananta wa.'9Wadanda ke tare da ni sun ga hasken, amma ba su gane muryar wanda ya yi magana da ni ba. 10Na ce, 'Me zan yi ya Ubangiji?" Ubangiji ya ce mani, 'Tashi ka tafi cikin Dimashku, a can za a fada maka abinda wajibi ne ka yi. 11Ban iya ganin wuri ba domin walkiyar hasken, sai na tafi cikin Dimashku ta wurin jagorancin wadanda ke tare da ni.12A can na sami wani mai suna Ananiya, mai tsoron Allah bisa ga sharia, da kyakyawan suna kuma a gaban Yahudawa da ke zama a can. 13Ya zo gare ni ya ce, 'Dan'uwa Shawulu, karbi ganin gari.' A daidai wannan sa'a na gan shi.14Sa'annan ya ce, 'Allah na kakkaninmu ya zabe ka ka san nufinsa, ka ga Mai Adalcin nan, ka kuma ji muryar da ke fitowa daga bakinsa. 15Gama za ka zama mashaidinsa ga dukan mutane game da abinda ka gani da wanda ka ji. 16A yanzu me ka ke jira? 'Tashi a yi maka baftisma a wanke zunubanka, kana kira bisa sunansa.'17Bayan da na dawo Urushalima, sa'anda ina addu'a a cikin haikali, sai na karbi wahayi. 18Na gan shi ya ce mani, 'Gaggauta ka bar Urushalima yanzu, domin ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.'19Na ce, 'Ubangiji, su da kansu sun san yadda na sa su a kurkuku na kuma doddoke wadanda suka gaskanta da kai a kowacce masujada. 20A sa'anda a ke zubar da jinin mashaidinka Istifanus, ina nan tsaye ina goyon baya, ina kuma lura da rigunan wadanda suka kashe shi.' 21Amma ya ce mani, 'Tafi, domin zan aike ka can wurin Al'ummai.'22Mutanen sun bar shi yayi magana har zuwa ga wannan lokacin. Amma sai suka ta da murya suna cewa, 'A kawar da wannan dan taliki daga duniya: don bai kamata ya rayu ba.' 23Sa'anda suke tadda muryarsu, suna jefar da tufafinsu da kuma baza kura a iska, 24babban hafsan ya umarta a kawo Bulus a farfajiyan. Ya umarta da cewa a bincike shi da bulala, domin ya san dalilin da suka ta da ihu gaba da shi haka.25Bayan da suka daure shi da tsirkiya, Bulus ya ce wa Jarumin da ke kusa da shi, "Ko daidai ne bisa ga doka a yi wa Barome wanda ma sharia ba ta kashe shi ba bulala?" 26Da Jarumin ya ji haka, ya tafi wurin babban hafsan, yana cewa, "Me kake so ka yi? Gama wanan mutumin dan asalin Roma ne."27Babban hafsa ya zo ya ce masa, "Gaya mani, kai dan asalin Roma ne?" Bulus ya ce, "Haka ne." 28Babban hafsan ya amsa masa, "Da kudi masu yawa na sayi yancin zama dan kasa." Amma Bulus ya ce, "An haife ni dan kasar Roma. 29"Sai mutanen da sun zo su tuhume shi sun bar shi nan da nan. Babban hafsa shi ma ya tsorata da ya gane Bulus dan asalin Roma ne, domin ya riga ya daure shi.30Washegari, babban hafsan ya so ya san gaskiyar tuhuma da Yahudawa suke yi a kan Bulus. Sai ya kwance shi daga sarka, ya kuma umarci babban firist da dukan majalisa su sadu. Sai ya kawo Bulus ya sa shi a tsakiyarsu.
Bulus yana magana da taron Yahudawa a Urushalima.
Aya 2 yana ba da karin bayyani.
Wannan wata hanya ne mai sauki na yi wa tsaran Bulus da 'yan gaba da shi a tsakanin mas sauraro.
"yanzu zan yi maku bayyanin" ko kuma "yanzu zan zan gabatar maku"
Harshen Ibraniyawa itace harshen Yahudawa da.
AT: "Amma ni dalibin malam Gamaliyal ne a nan Urushalima"
A nan "kařkashi" na nufin yadda mutum zai zauna yayin da yake koyo daga malami. AT: "ta wurin Gamaliyal"
Gamaliyal wani sanannen malamin dokar Yahudawa ne sosai. Duba yadda aka juya wanna a [5:34]
AT: "Ya horar da shi a hanyar da zai iya kiyaye kowane dokar kakkaninmu" ko kuma "Horaswar da na samu sun bi daki daki yadda dokokin kakkaninmu"
"dokokin kakkaininmu." Wato dokokin da Allah ya ba jama'ar Isra'ila ta wurin Musa.
"Na miƙa kai in yi biyayya da Allah" ko kuma "Ina da marmarin yi wa Allah hidima"
"daidai yadda kuma kuke a yau." Bulus yana ƙwatanta kansa da taron jama'ar.
A nan "wannan hanyan" na nufin mutanen da ke na wannan taron mutanen da ake ce da su "hanyar." AT: "Na tasananta wa mutanen da ke na wannan hanya"
Haka a ke ce da adinin Kirist ko kuma masu bi a da. Duba yadda aka juya "wannan Hanyan" a [9:2].
Ana iya juya kalmar nan "mutuwa" zuwa "kisa" ko kuma "mutu". AT: "kuma na nema hanyoyin kasahe shi su" ko kuma "har ma na sa suka mutu"
"ina ɗaure mutane maza da mata ina sa su a kurkuku"
"za su iya shaida" ko kuma "za su iya faɗa maku"
babbar firist da dattawa sun bani wasiku"
Ana "'yan'uwa" na nufin "'yan'uwa Yahudawa."
Sun bani umarni na ɗaura da sarkoki waɗanda ke 'yan hanya in mayar da su Urushalima"
AT: "domin su karɓi hukuncinsu" ko kuma "domin hukumar Yahudawa su hukunta su"
Ana amfani ne da wannan jimlar don a nuna wurin da zancen ya fara. Idan harshenku tana da wata hanya ta musamman na yin haka, kuna iya moransa anan.
A nan "murya" na nufin mai magana. AT: "Na ji wani ya ce mini"
A nan "murya" na nufin mutumin da yake magana. AT: "basu fahimci abinda mai magana da ni ke cewa ba"
AT: "a can wani zai faɗa maka" ko kuma "a wurin za ka san"
"Na zama makahu saboda tsananin walkiyar hasken"
A nan "jagoranci" na nufin waɗanda ke bi da Bulus. AT: "waɗanda suka bi da ni zuwa Damishku"
Wannan Hananiya daban ne da wanda ya mutu dama [5:3], kuna iya juya wannan yadda kuka yi a [5:1]
Hananiya na da ƙwazo ƙwarai game da kiyaye shari'ar Allah.
AT: "Yahudawa da ke zama a wurin suna ba da kyakyawar shaida a kansa"
A nan "Ɗan'uwa" wata hanya ne may kyau na yaba wa mutum. AT: "Abokina Shawulu"
AT: "fara gani kuma"
Wannan wata hanya ne na nuna cewa abu ya faru nan da nan. AT: "nan take" ko kuma "nan da nan" ko kuma"
"abinda Allah ke shiryawa yana kuma sa yă faru"
Da "murya" da "baƙi" duka suna nufin mai magana. AT: "ka kuma ji shi yana magana da kai kai tsaye"
A nan "mutane" na nufin jama'a maza da mata. AT: "ga dukkan jama'a"
Ana amfani ne da kalmar nan "yanzu" a nan ba wai don yana nufin "a daidai wannan sa'a" ba, amma domin a jawo hankali ne ga wata muhimmin zance da ke bin wannan.
An yi amfani ne da wannan tambaya domin a gargaɗe Bulus ya yi baftisma. AT: "Kada ka jira" ko kuma "Kada ka ɓata lokaci"
AT: "bari in yi maka baftisma" ko kuma "karɓi baftisma"
Kamar yadda wanke jiki ke cire datti, kira ga sunan Yesu domin gafarrar zunubai yana tsabtacce zukatan mutum daga zunubi. AT: "ka roƙa gafarrar zunubanku"
A nan "suna" na nufin Ubangiji. AT: "kana kira bisa Ubangiji ko kuma "kana dogara ga Ubangiji"
AT: "na samu wani wahayi" ko kuma "Allah ya bani wata wahayi"
"Na gan Yesu yana ce mini"
"waɗanda suke Urushalima ba za su yarda da abinda za ka faaɗ masu akai na ba"
Ana amfani ne da kalmar nan "da kansu" domin nanaci.
"Bulus ya je masujadai da dama yana neman Yahudawa da suka gaskanta da Yesu.
A nan "jini" na nufin rai na Istifanus. A zuɓar kuma na nufin a ƙashe. AT: "sun ƙashe Istifanus mai ba da shaida a kanka.
Wannan jimlar "daga duniya" na kara nanata ne da cewa a kawar da irin mutumin. AT: "Ƙasheshi"
"Yayin da suka." Ana amfani ne da jimlar nan "Sa'anda suke" domin a sa alamar abubuwa biyu da ke aukuwa a lokaci ɗaya.
Wannan na nuna cewa Yahudawa da ke wurin sun yi fushi domin Bulus ya saɓa wa Allah ta wurin maganarsa.
hafsan sojojin Roma ko kuma shugabana sojojin kusan 600
AT: "ya umurce sojojinsa su kawo Bulus"
Wannan sansanin yana haɗe sa wajen harrabar haikali. Duba yadda aka juya wannan a [21:34]
Shi shugaban sojojin yana so Bulus ya sha azaba ne ta wurin yi masa duka domin ya tabbatar cewa Bulus ya faɗa masu gaskiya. AT: "Ya umarce sojojinsa su bulali Bulus don su tilasta shi ya faɗa masu gaskiya"
Ana amfani ne da kalmar nan "kansa" domin nanaci.
wato tsirkiyar laida ko kuma na fatan dabba.
Bulus yana amfani ne da wannan tambayan domin yă sa Shugaban yă bincike ko daidai ne da aka sa sojoji su bulali Bulus. AT: "Ba daidai ba ne bisa ga doka a bulali mutumin da ke Baome ba tare da an yi masa bincike ba!"
An yi amfani ne da wannan tambaya domin a sa shugaban ya ƙara tunani shirinsa yă bulali Bulus. AT: "Kada ka yi haka!"
A nan ana iya juya "zo" zuwa "je"
"Bayan da na biya hukumar Roma kuɗi masu yawa ne." Shi hafsan ya yi wannan magana ne domin ya san cewa yana da wuya ƙwarai mutum ya zama Barome, yana kuma ɗaukan cewa ba gaskiya ne Bulus ke faɗi ba.
"Na sami yancin zama ɗan ƙasa." AT: "na zama ɗan ƙasa"
Muddin Uban mutum ɗan ƙasa Roma ne, to lallai ne 'ya'yansa su zamanto 'yan ƙasar Roma daga haihuwa.
"mutanen da suka yi shirin tuhumar" ko kuma "mutanen da suke shirin su tuhume"
Mai yiwuwa "babbar hafsan" na nufin babbar hafsan sojojin. AT: "Don haka, babbar hafsan ya umurce sojojin su kwance sarkokin Bulus"
Daga sansanin, akwai wani matakala saukowa daha harrabar haikalin.
1Bulus ya kura wa yan majalisa ido yace, '"Yan'uwa, na yi rayuwa tare da Allah da lamiri mai kyau har wannan ranan." 2Babban firist Hannaniya ya ba wandanda suke tsaye tare da shi urmarni su buge bakinsa. 3Bulus ya ce, "Allah zai buge ka, kai munafiki. Kana zama domin ka shari'anta ni da shari'a, kuma ka umarce a buge ni, gaba da sharia?"4Wanda suka tsaya a gefe suka ce, "Kada ka zage babban firis na Allah." Bulus yace, "Ban sani ba, 'yan'uwa, cewa shi babban firis ne. 5Domin a rubuce yake, Ba za ku zargi shugaban mutanenku ba."6Da Bulus ya ga cewa, daya bangaren Sadukiyawa ne dayan kuma Farisawa, ya yi magana da karfi a majalisa, '"Yan'uwa, ni Bafarise ne, dan Farisawa. Don tabbacin tashin matattu ne kuna shari'anta ni." 7Daya fadi haka, mahawara ta fara a tsakanin Farisawa da Sadukiyawa, sai taron ya rabu kashi biyu. 8Don Sadukiyawa suka ce babu tashin matattu, babu mala'iku, babu kuma ruhohi, amma Farisawa suka ce dukan abubuwan nan sun kasance.9Sai mahawara ta tashi, wadansu marubutan Farisawa suka tashi da mahawara cewa, "Ba mu same mutumin nan da laifi ba sam. Ko mala'iku da ruhohi ne suka yi masa magana?" 10Da jayayya ta tashi, babban hafsa ya ji tsoro kada su yayaga Bulus, sai ya umarce sojoji suje su kwato shi da karfi daga 'yan majalisa, su tafi da shi farfajiya.11Da dare Ubangiji ya tsaya kusa da shi yace, "Kada ka ji tsoro, kamar yadda ka ba da shaida game da ni a Urushalima, dole zaka sake zama shaida a Roma."12Da gari ya waye, wadansu Yahudawa sun yi yarjejeniya suka dauka wa kansu la'ana: suka ce ba za su ci ba ba za su sha ba sai sun kashe Bulus. 13Mutane fiye da arba'in suka kulla wannan makirci.14Suka je wurin manyan firistoci da dattawa suka ce, "Mun sa wa kanmu la'ana, ba za mu ci ba, ba za mu sha ba sai mun kashe Bulus. 15Yanzu, bari majalisa ta ba wa babban hafsa izini a kawo shi a gaba, kamar zai yanke hukunci. Mu kam, a shirye muke mu kashe shi kafin ya iso nan.16Amma dan yar'uwan Bulus ya ji suna labe, sai ya tafi ya shiga farfajiyar ya fada wa Bulus. 17Bulus ya kira daya daga cikin jarumai yace, "Dauki saurayin nan ka kai shi wurin babban hafsa, don yana da abin da zai fada masa."18Jarumin ya dauke saurayin ya kai shi wurin babban hafsa yace, "Bulus dan sarka ne yace in kawo saurayin nan a gaban ka. Yana da abin da zai fada maka." 19Babban hafsa ya kai shi wani lungu, sai ya tambaye shi, "Menene kake so ka fada mani?"20Saurayin yace, "Yahudawa sun yarda su roke ka ka kawo Bulus gobe a majalisa, kamar zasu kara bincike a kan al'amarin. 21Amma kada ka yarda da su, mutane fiye da arba'in suna jiransa. Sun sa wa kansu la'anna, ba za su ci ba ba za su sha ba sai dai sun kashe shi. Yanzu a shirye suke; suna jira ka ba su izini."22Sai babban hafsa yace wa saurayin ya tafi, da ya gama masa magana, "Kar ka fada wa wani al'amuran." 23Sai ya kira jarumai biyu yace, "Ku shirya sojoji dari biyu, yan dawakai saba'in, masu daukar mashi dari biyu su tafi kaisariya karfe uku na dare." 24Ya umarta a shirya dabbobin da Bulus zai hawo da zasu kai shi lafiya wurin Filikus gwamna.25Sai ya rubuta wasika a misalin haka: 26Gaisuwa zuwa Kuludiyas Lisiyas zuwa ga mai martaba gwamna Filikus. 27Yahudawa sun kama wannan mutumin suna shirin kashe shi, na abko masu da sojoji na kwace shi, bayan da na ji shi Barome ne.28Inna son sani dalilin zarginsa, sai na kai shi majalisa. 29Na gane cewa ana zarginsa ne a kan tambayoyi game da shari'ansu, amma ba wani zargi da ya cancanci dauri ko mutuwa. 30Da aka sanar da ni shirin makircin, sai na tura shi wurinka ba da bata lokaci ba, na umarce masu zarginsa su kawo zarginsu wurinka. Huta lafiya."31Sai sojoji suka yi biyayya da umarni da aka basu: suka dauki Bulus suka kawo shi dadare a wurin Antibatris. 32Da gari ya yawe, yan dawakai suka tafi tare da shi kuma sauran sojoji suka koma farfajiya. 33Bayan da yandawakan suka isa Kaisiririya sun mika wasika ga gwamna, suka kuma danka Bulus a hanunsa.34Da gwamna ya karanta wasikar, sai ya tambaye su daga wani yanki ne Bulus ya fito; da ya ji daga yankin kilikiya ne, 35Yace zan saurare ka sosai lokacin da masu zargin ka sun zo. Sai ya umarta a tsare shi a fadar Hiridus.
Bulus yana gaban babban firist da kuma majalisarsa. (Dubi: [22:30])
Wannan na nufin "'Yan'uwa Yahudawa"
"Na san cewa har wa yau na yi abinda Allah yake so in yi"
Sunan mutumin kenan. Kodashike wannan sunan daban ne da Hananiya da ke a [5:1]), da kuma wanda ke a [9:10]).
Bulus yana nuna wa Hananiya ne cewa kodashike, ya fita kamar mutumin kirki, amma yana nan cike da mugun tunani a zuciyansa. AT" ...
Bulus yana amfani ne da wannan tambayan domin ya nuna munafincin Hananiya. AT: "Ka zauna a nan ka shar'anta ... gãba da shari'a."
AT: "ka umarci mutane su buge ni"
Mutanen suna amfani ne da wanna tambayan domin su yi wa Bulus tsawa domin abinda ya faɗa a [23:3]. AT: "Kada ka zage babban firis na Allah!"
Bulus zai furta abinda Musa ya rubuta kenan a cikin Shari'a. AT: "Gama Musa ya rubuta a cikin shari'a"
A nan "ɗa" na nufin shi ainihin ɗan Bafarisi ne da kuma zuriyar Farisiyawa. AT: "kuma mahaifi na da kakkani na farisiyawa ne"
A nan iya sanar da wannan kalmar "tashi" zuwa "dawuwa da rai." Ana kuma iya sanar da kalmar nan "mutuwa" zuwa "waɗanda suka mutu." AT: "waɗanda suka mutu za su samu rai kuma, ... ni"
AT: "kuna shar'a'anta ni"
"mutanen da ke taron suka ƙi yarda da juna sam"
Wannan yana kara ba da hasken bayyani ne game da Sadukiyawa da Farisiyawa
"Sai suka fara yi wa juna ihu." Kalmar nan "sai" yana nuna abin da ya faru domin wani abu daban da ya faru a baya. A wannan hali, abinda ya faru a baya shine Bulus ya furta gaskantawar shi da tashin matattu.
Farisiyawan suna sauta wa sadukiyawan ta wurin tabbatar masu cewa akwai ruhohi da mala'iku kuma suna iya magana da mutane. AT: "Mai'yiwuwa wani ruhu ko mala'ika ya yi magana da shi!"
A nan iya mayar da waɗannan kalmomi "jayayya mai tsanani" zuwa "gardama mai tsanani." AT: "Da suka fara wata gardama mai tsanani"
wani shugaban sojojin Roma mai mai shugabancin sojoji 600
Jimlar nan "a yi kaca kaca da Bulus" na maganar yadda mutanne za su iya yi wa Bulus illa. AT: "za su iya yayyaga Bulus kaca kaca" ko kuma "za su yi wa Bulus wata babbar rauni a jiki"
"su yi amfani da ƙarfin jiki su tafi da shi"
Wannan sansanin yana haɗe sa wajen harrabar haikali. Duba yadda aka juya wannan a [21:34]
Wato bayan daren da Bulus ya je gaban majalisa. AT: "A Daren nan"
A nan iya fahimtar waănnan kalmomin "game da na". AT: "ba da shaida a kai na a Roma" ko kuma "ka shaide ne a Roma"
"suka shirya kansu da manufa ɗaya" andn, domin su ƙashe Bulus.
A nan iya kara bayyana dalilin da zai sa la'ana ya bi su. AT: "sun roƙi Allah ya la'antasu idan basu yi abinda sun alkawarta su yi ba"
"mutum 40"
"suka haɗa wannan shiri" ko kuma "suka yi shirya su ƙashe Bulus"
A nan kalmar nan "Su" na nufin Yahudawa arba'in da ke [23:13] ne
A nan maganar ɗaukan alkawari ne da kuma roƙon Allah ya la'anta su idan basu cika alkwarinsu ba kamar wani abu ne da za su ida sa wa a bisa kapaɗansu. AT: "Mun ɗauki rantsuwa cewa ba za mu ci kome ba har sai mun kashe Bulus. Mun roƙi Allah ya la'anta mu idan ba mu cika wannan alkwarin ba"
"Da shike abin nan da muka faɗa gaskiya ne, ko kuma "Da shile mun sa wa kanmu a wannan la'ana"
Ba "a dai dai wannan lokaci" ake nufi ba, amma ana amfani ne da wanna domin a jawo hankali mutane a akan wani abu mai muhimmanci da ke bi a baya.
"kawo Bulus daga sansanin domin yă same ku"
"kamar kuna so ku ƙara sani game da abinda Bulus ya yi"
"suna bagon Bulus" ko kuma "suna jira su kashe Bulus"
Sansanin yana haɗe ne da harrabar wajen haikali. Dubia yadda aka juya wannan a [21:34]
"Bulus ɗan sarka ne ya ce in zo in yi magana da shi"
Da shike Babban hafsan ya kai saurayin, ya kuma ce da shi saurayi, wannan na nufin cewa, ɗan ƙanen Bulus yana iya zama mai shekara 12 zuwa 15.
Wannan bai shafe dukkan Yahudawa ba, amma dukkan taron Yahudawa da ke wurin. AT: "Wasu Yahudawan sun yarda"
"ka kawo Bulus daga sansanin"
"suna son su ƙara sani game da laifin da Bulus ya yi"
"sun shirya bagon Bulus" ko kuma "sun shirya su kashe Bulus"
"Sun rantse cewa ba za su ci ko su sha komai ba har sai sun kashe Bulus. Sun ce ma Allah ya la'anta su idan basu cika alkawarin yin abinda sun ce za su yi ba"
"ya kira gareshi"
"jarumai 2"
'yan dawakai 70"
"sojoji dari biyu da aka masu ɗamarar yaƙi da mashi"
wato 9:00 p.m. da dare.
Wannan ce gabatarwa ta musumman a wasikar. Babbar hafsan ya fara da kansa. Ana iya gane wannan da "ina rubutowa". AT: "Ni, Kuludiyas Lisiyas, ina rubutowa zuwa gareka, mai martaba, gwamna Filikus. Gaisuwa mai yawa zuwa gareka"
"zuwa ga gwamna Filikus da ya cancanci dukkan girma"
A nan "Yahudawa" na nufin "wasu Yahudawa." AT: "wasu Yahudawa sun kama wannan mutum"
AT: "sun yi shirin kashe Bulus"
"Ni da sojoji na muka iso wurin d a Bulus da Yahudawan suke"
AT: "cewa suna zarginsa a kan tambayoyi game da"
AT: "amma ba wanda ya zarge shi da wani abu da zai sa hukumomin Romawa su kashe shi ko su ɗaure shi ba"
AT: "Daga baya na gane"
Kalmar nan "sai" na nuna alama ne cewa hakan ya faru ne ta dalilin wani abu da ya faru a baya. A wannan karo, abinda ya faru a baya shi ne umarnin da babbar hafsan ya bayar cewa sojoji su raka Bulus.
A nan ana iya juya "kawo" zuwa "kai." AT: "Suka samo Bulus sai sun kai shi da dare"
A nan iya sanar da wannan a matsayin furci. AT: "Ya tambaye Bulus, 'daga wani yanki ka fito?' Da
AT: "Bulus ya ce, 'Ni daga Kilikiya ne.' Sai gwamna ya ce"
"Zan saurare duk maganan da kake da shi"
AT: "ya umurci sojoji su tsare shi" ko kuma "ya umarci sojoji su masa tsaro"
1Bayan kwanaki biyar, sai Ananiyas babban firist, Wasu dattawa da wani masanin shari'a mai suna Tartilus, sun tafi can. Suka kai karar Bulus gaban gwamna. 2Lokacin da Bulus ya tsaya gaban gwamna, Tartilus ya fara zarginsa yace wa gwamnan, "Saboda kai mun sami zaman lafiya; sa'annan hangen gabanka ya kawo gyara a kasarmu; 3don haka duk abin da ka yi mun karba da godiya, ya mai girma Filikus.4Domin kada in wahalsheka, ina roko a yi mani nasiha don in yi magana kadan. 5An iske mutumin nan yana barna irir iri, yana kuma zuga jama'ar Yahudawa a dukan duniya su yi tayarwa. 6Har ma ya yi kokarin kazantar da haikali; saboda haka muka kama shi. 17Amma Lisiyas jami'i ya zo ya kwace shi da karfi daga hannunmu. 8Idan ka binciki Bulus game da wadannan al'amura, kai ma, zai tabbatar maka abin da muke zarginsa a kai. 9Dukan Yahudawa suna zargin Bulus cewa wadannan abubuwa gaskiya ne.10lokacin da gwamnan ya alamta wa Bulus ya yi magana sai yace, "Yanzu na fahimci cewar da dadewa kana mulkin kasarnan, don haka da farin ciki zan yi maka bayani. 11Zaka iya tabbatarwa cewa bai kai kwana sha biyu ba tun da nake zuwa Urushalima don yin sujada. 12Da suka same ni a haikali, ban yi jayayya ko kawo rudami a tsakanin jama'a ba. 13Don haka ba su da tabbas akan abinda suke zargina a kansa yau.14Amma na sanar da kai, bisa ga abin da suke kira darika, haka ni ma nake bautawa Allah na kakanninmu. Na yi aminci wajen kiyaye dukan abin da ke a rubuce a Attaurat da litattafan annabawa. 15Ina sa bege ga Allah, kamar yadda za a yi tashin matattu, masu adalci da miyagu; 16a kan haka kuma, nake kokarin zama mara abin zargi a gaban Allah da mutane ina yin haka cikin dukan al'amura.17Bayan wadansu shekaru na zo in kawo wasu sadakoki da baikon yardar rai. 18Cikin kudurin yin haka, sai wasu Yahudawa daga kasar Asiya suka iske ni a cikin ka'idodin tsarkakewa a haikali, ba da taro ko ta da hargitsi ba. 19Yakamata wadannan mutanen su zo gabarka a yau, har idan suna da wani zargi a kai na.20In kuwa ba haka ba bari mutanennan su fada in sun taba iske ni da wani aibu a duk lokacin da na gurfana a gaban majalisar Yahudawa; 21sai dai ko a kan abu daya da na fada da babbar murya sa'adda na tsaya a gabansu, 'Wato batun tashin matattu wanda ake tuhumata ake neman yi mani hukunci yau.'"22Filikus yana da cikakken sanin tafarkin Hanyar, shi yasa ya daga shari'ar. Yace da su, "Duk sa'anda Lisiyas mai ba da umarni ya zo daga Urushalima, zan yanke hukunci." 23Sa'annan ya umarci jarumin ya lura da Bulus, amma ya yi sassauci, kada ya hana abokansa su ziyarce shi ko su taimake shi.24Bayan wadansu kwanaki, Filikus da mai dakinsa Druskila, ita Bayahudiya ce, ya kuma aika a kira Bulus ya saurare shi game da bangaskiya cikin Kristi Yesu. 25Amma sa'adda Bulus yake bayyana zancen adalci, kamunkai, da hukunci mai zuwa, Filikus ya firgita ya ce, "Yanzu ka tafi. Amma idan na sami zarafi an jima, zan sake neman ka."26A wannan lokacin, yasa zuciya Bulus zai bashi kudi, yayi ta nemansa akai-akai domin yayi magana da shi. 27Bayan shekaru biyu, Borkiyas Festas ya zama gwamna bayan Filikus, domin neman farin jini a wurin Yahudawa, ya ci gaba da tsaron Bulus a gidan yari.
A nan gwada Bulus a Kaisariya. Tartilus ya miƙa wa Gwamna Filikus ƙarar da ke kan Bulus.
A nan kalmar nan "kai" na nufin Filikus, gwamna.
"bayan kwanaki biyar da sojojin Roma suka kai Bulus Kaisariya"
Wannan sunan wani mutum ne.
Wannan sunan wani mutum ne. Wannan Hananiya daban ne da wanda aka yi maganarsa a [5:1], da kuma Hananiya da ke [9:10]. Duba yadda aka juya wannan a 23:1
"wani lauya." Tartilus wani shaharren Masanin shari'ar Romawa ne, ya kasance a kotu ne musamman domin ya zargi Bulus.
"tafi Kaisariya inda Bulus yake dama"
"gaban gwamna wanda shi ne alkali a kotun"
"Ya fara ƙarar a gaban gwamna cewa Bulus ya ƙarye doka."
Ana "mu" na nufin 'yan gari da ke karkashin mulkin Filikus. AT: "mu, jama'a da kake mulkimu, muna zaman lafiya"
"sa'annan shirin da ka yi ya ƙara ƙyau ƙasarmu"
"Filikus gwamna wanda ya cancanci dukkan girma" Filikus ne gwamnar Roma da ke mulkin dukkan yankin. Duba yadda aka juya irin wannan jimlar a [23:25]
Wannan na iya nufin 1) "domin kada in ci maka lokaci" ko kuma "domin kada in gajiyad da kai"
"yi hakuri ka ɗan saurare maganar da zan yi"
Ana maganar Bulus kamar wani aloba ne da ke yaduwa daga wannan mutim zuwa wancan mutum. AT: "mutumin nan fitinanne ne"
Wannan dai karin magana ne domin a jaddada zargin da ke kan Bulus.
Jimlar nan "ɗariƙar Nazarawa" wata suna ne na masubi. AT: "Yana kuma shugabantan taron jama'a da ake ce da su mabiyan Nazarawa"
Wanna wata ƙaramar ƙungiya a cikin manyan ƙungiyoyi. Tartilus yana ganin masubi a matsayin wata ƙaramar ƙungiya a cikin adinin Yahudanci.
"ka gane ko waɗannan zargin da muka kawo a kansa gaskiya ne" ko kuma "ka gane ko yana da laifin abubuwan da muka zarge shi akai"
Wannan na nufin shugabannin Yahudawa da ke wurin da ake gwada Bulus.
"gwamnan ya motsa"
A nan "ƙasa" na nufin mutanen ƙasar Yahudawa. AT: "mai shari'ar mutanen ƙasar Yahudawa"
"bayana maka yanayina"
"kwana 12 tun"
"ta da hargitisi" anan karin magana ne da ke nufin ta da hankulan mutane. AT: "ban ta da hankalin taron ba"
"ɗaukan laifofin munana ayyukansu" ko kuma "zargin laifofi
"Na shaida maka wannan" ko kuma "Na furta maka wannan"
Jimlar nan "hanyar" wata laƙabi ne da ke nufin masubi a zamanin Bulus.
Wanna wata ƙaramar ƙungiya a cikin manyan ƙungiyoyi. Tartilus yana ganin masubi a matsayin wata ƙaramar ƙungiya a cikin adinin Yahudanci. Duba yadda aka juya "ɗariƙa" a [24:5]
Bulus yana amfani ne da wannan kalmar "haka" don yă nuna cewa shi, a matsayinsa na maibin Yesu, yana bauta wa Allah yadda kakkaininsu na Yahudawa suka yi. Yana shugabantar wata "ɗariƙa" ko kuma yana koyar da wata sabuwan abu da ke gãba da addininsu na zamanin dã.
"kamar yadda waɗannan mutanen suka yi" Anan "waɗannan" na nufin Yahudawa masu zargin Bulus a kotu.
Ana iya sanar da kalmar nan "tashin" zuwa "ta da" AT: "cewa Allah zai ta da dukkan waɗanda suka mutu, da masu adalci da marasa adalci"
Wannan na nufin mutane masu adalci da mugayen mutane. AT: "mutane masu adalci da mutane marasa adalci" ko kuma "waɗanda suka aikata abinda ke daidai da waɗanda suka aikata abinda ba daidai ba"
"nake himma kullum" ko kuma "ina iya ƙoƙari"
A nan "lamiri" nan nufin tunani ko kuma hankalin mutum da ke iya sanin abinda ke daidai da wanda ba daidai ba. AT: "zama marar laifi" ko kuma "in riƙa aikata abinda ke daidai"
"a gaban Allah"
Wannan kalmar na nuna dabara a muhawarar Bulus. Ana ya bayyana yanayin Urushalima a lokacin da wasu Yahudawa suka kama shi.
"bayan wasu shekaru nesa da Urushalima"
A nan ana iya juya kalmar nan "na zo" zuwa "na je." AT: "Na je in tallafawa wa mutane na ta wurin kawo masu gudumawar kuɗi"
"a cikin haikali bayan na gama ka'idodin tsarkake kaina"
Ana iya sanar da wannan a wata sabuwar jimla. AT: "Ban hada taro ba, ba ma ina ƙoƙarin ta da hargitisi ba
"Yahudawa daga Asiya"
"idan suna da wani abin faɗi"
Wato mutanen majalisar da ke nan a Urusahlima a lokacin shari'ar Bulus.
"su faɗi abinda na yi wanda ba daidaiba da za su iya su hakikanta"
A nan iya sanar da kalmar nan "tashin matattu" zuwa "Allah zai tashe su da rai" AT: "Wato saboda na gaskanta cewa Allah zai ta da matattu ne
AT: "kana yi mini shari'a a yau"
Wannan wata laƙabi ne na Masubi. Duba yadda aka juya shi wannan [9:2]
"sa'anda Lisiyas mai ba da umarni ya ko kuma "in Lisiyas ma ba da umarni ya zo"
Wannan ne sunan babban hafsan. Duba yadda aka juya wannan sunan a [23:26]
Urushalima yana tudu fiye da Kaisariya, don haka ana iya ce mutum ya sauko daga Urushalima.
"zan yanke maka hukunci game da zargin da ke a kanka" ko kuma "zan shar'anta ko kana da laifi"
"ba wa Bulus yanci kadak wanda ba a ba sauran 'yan kurkuku"
"Bayan kwanaki da dama"
Wannan sunan wata mace ce.
Wato mace a Yahudawa. AT: "wadda Bayahudiya ce"
Mai yiwuwa Filikus ya ji tabbacin zunubansa"
"a daidai wannan lokaci"
Filikus yana sa zuciya Bulus zai bashi toshiya don a sake shi.
"don haka Filikus yakan aika ya gan Bulus akai akai don yă yi magana da Bulus"
Wannan shi ne sabon Gwamnar Roma wanda ya maye gurbin Filikus.
A nan "Yahudawa" na nufin shigabannin Yahudawa. AT: "domin yana so shugabannin Yahudawa so so shi"
"ya bar Bulus a Kurkuku"
1Da Festas ya shiga lardin, kuma bayan kwana uku, ya tashi daga Kaisariya ya tafi Urushalima. 2Sai babban firist da manyan Yahudawa suka kawo wa Festas sara a kan Bulus. 3Suka roki tagomashi wurin Festas ya kira Bulus zuwa Urushalima domin su kashe shi a hanya.4Amma Festas ya amsa masu cewa, Bulus dan sarka ne a Kaisariya, kuma ba da dadewa ba shi da kansa zai koma can. 5"Saboda haka duk wadanda za su iya, su biyo mu. Idan akwai wani laifi game da mutumin, sai ku zarge shi."6Bayan kwana takwas ko goma, sai ya gangara zuwa Kaisariya. Washegari ya zauna bisa kursiyin shari'a ya bada umarni a kawo Bulus a gabansa. 7Da Bulus ya iso, Yahudawa daga Urushalima suka tsaya kusa, suka yi ta kawo kararraki, amma basu iya tabbatar da su ba. 8Bulus ya kare kansa ya ce, "Ban yi wa kowa laifi ba, ko Yahudawa, ko haikali, ko kuma Kaisar."9Amma Festas yana neman farin jini wajen Yahudawa, sabo da haka ya tambayi Bulus ya ce, "Kana so ka je Urushalima in shari'anta ka a can game da wadannan abubuwa?" 10Bulus ya ce, "Ina tsaye a Ddakalin Shari'ar Kaisar inda dole a shari'anta ni. Ban yi wa Yahudawa laifi ba, kamar yadda ka sani sosai.11Idan lallai na yi laifi kuma na yi abin da ya chanchanci mutuwa, ban ki ba in mutu. Amma idan zarginsu karya ne, kada kowa ya bashe ni gare su. Ina daukaka kara zuwa ga Kaisar." 12Bayan Festas ya tattauna da majalisa ya amsa ya ce, "Kana kira ga Kaisar; za ka tafi wurin Kaisar."13Bayan wadansu kwanaki, sarki Agaribas da Barniki suka iso Kaisariya domin su ziyarci Festas. 14Da ya kasance kwanaki da yawa, Festas ya fada wa sarki labarin Bulus ya ce, "Akwai wani mutum dan sarka da Filikus ya bari a kurkuku. 15Sa'anda nake a Urushalima, babban firist da dattawan Yahudawa suka kawo kararsa gare ni, suka roka a kashe shi. 16Game da wannan na amsa na ce masu, ba al'adar Romawa ba ce a ba da mutum tagomashi; sai wanda ake kararsa an bashi zarafi ya kare kansa a gaban masu kararsa, ya kuma bada hujjojinsa game da kararakin.17Saboda haka, da duk suka taru ban bata lokaci ba, washegari na zauna a kujerar shari'a, na ba da umarni a kawo mutumin. 18Da masu karar suka fadi kararsu, sai na fahimci karar ba wani muhimmin abu a cikinta. 19Sai dai na ga cewa jayayya ce tsakanin su ta addini a kan wani Yesu da ya mutu, wanda Bulus ya ce yana da rai. 20Na rasa yadda zan bincike wannan al'amarin, sai na tambaye shi ko zai je Urushalima a shari'anta shi kan wadannan abubuwa.21Amma da Bulus ya nemi a lura da shi, Kaisar ya shari'anta shi, sai na ba da umarni a ajiye shi har sai na aika shi wurin Kaisar." 22Agaribas yace wa Festas. "Zan so ni ma in saurari mutumin nan." "Gobe za ka ji shi," in ji Fostus.23Washegari Agaribas da Barniki suka zo tare da kasaitaccen taro suka shiga dakin taro tare da hafsoshi da shugabanin gari. Da Festas ya ba da umarni, aka fito da Bulus wurinsu. 24Festas ya ce, "Sarki Agaribas da dukanku da kuke tare da mu a nan, kun ga mutumin nan, dukan Yahudawa sun gana da ni a Urushalima da nan kuma. Suna mani ihu cewa, bai chanchanta a bar shi da rai ba.25Na gane bai yi wani abin da ya chanchanci mutuwa ba; amma saboda ya daukaka kara zuwa Kaisar, na yanke shawara in aika shi. 26Amma ba ni da wani dalili na musamman da zan rubuta wasika ga Kaisar. Saboda wannan dalili na kawo shi gabanku, masamman kai ya sarki Agaribas. Domin in sami karin abin da zan rubuta game da shi. 27Gama a ganina wauta ce in aika dan sarka ba tare da na rubuta laifi a kansa ba."
Bulus ya cigaba da zama a ɗaure a Kaisariya.
Festas ya Zama Gwamnar Kaisariya. Dubi yaka aka juya wannan a [24:27]
Wannan kalmar na nuna alamar wani sabon abin da ya faru a labarin.
Wannan na iya nufin 1)Festas ya fito fara mulki a yankin. ko kuma 2) Festas dai ya iso yankin.
An yi amfani da jimlar nan "ya tashi" domin Urushalima yana sama da Kaisariya a tadawa.
Ana maganar ƙara kamar wani abu ne da mutum ke iya kawo wa wani. AT: "Sai babban firist da shugabanin Yahudawa suka kawo karan Bulus ga Festas"
A nan kalmar nan "sa" na nufin Festas.
Wato Festas zai umarci su su kai Bulus zuwa Urushalima. AT: "cewa yă umarci sojojinsa su kai Bulus zuwa Urushalima"
"za su yi bagon Bulus.
Ana iya sanar da wannan a matsayin furci. AT: "Amma Festas ya ce, 'Bulus ɗan sarka ne a Kaisariya, kuma ni da kai na zan koma can ba da dadewa ba."
Ana iya fara jimlar waɗannan kalmomin "ya ce". AT: "Amma ya ce, "Saboda haka, waɗanda za su iya zuwa Kaisariya su biyo mu"
"Idan Bulus yana da wani laifi"
"sai ku zarge shi da laifin ƙetere doka" ko kuma "sai ku kawo karansa"
Urushalima yana sama da Kaisariya bisa ga labarin ƙasa. Don haka, yana da sauki a ce mutum ya sauko daga Urushalima.
A nan "kursiyin shari'a na nufin zaman Festas a matsayin alkalin da ke binciken maganar Bulus. AT: "ya zauna a kursiyin yanke hukunci" ko kuma "ya zauna a matsayin mai yanke hukunci"
AT: "sojojinsa su kawo Bulus gabansa"
"Da ya zo ya tsaya gaban Festas"
Ana maganar mugun laifi kamar wani abu ne da mutum ke iya kawo kotu. AT: "sun zargi Bulus da laifuffuka masu nauyi da yawa"
Bulus ya ce shi bai ƙetere wani doka game da wanda za su iys shiga haikalin da ke Urushalima ba"
A nan "Yahudawa" na nufin shugabannin Yahudawa. AT: "yana so ya gamshi shugabannin Yahudawa"
Urushalima yana sama da Kaisariya bisa ga labarin ƙasa. Don haka, yana da sauki a ce mutum ya sauko daga Urushalima.
AT: "inda ni zan shar'anta ka a game da waɗannan ƙararraki.
"dakalin shari'a" na nufin ikon da Kaisar ke da shi na shar'anta Bulus. AT: "Na roƙa in saya a gaban Kaisar don ya shar'anta ni ne"
Bulus yana magana ne idan maganar da za a kawo a kansa gaskiya ne. Idan yana da laifi, zai karɓi hukuncin, amma shi ya tabbatar cewa ba shi da laifi.
"idan na aikata laifin da ya cancanci mutuwa ne ya zama hukunci na"
"idan ƙararraki da aka yi a kaina ba gaskiya ba ne"
Wanna na iya nufin 1) Festas bashi da iko bisa ga shari'a ya bashe Bulus ga waɗannan masu zargin ko kuma 2) Bulus yana cewa idan ba shi da laifin komai, kada gwamna ya amince da roƙon Yahudawa.
"Ina roƙo a kai ni gaba Kaisar don ya shar'anta ni"
Ba wannan Majalisar bane ake ta maganar su a matsayin "majalisa" a Ayyukan Manzanni gabaɗaya. Wannan ne majalisar siyasa da ke gwamnatin Roma. AT: "da nasa mashawarta"
don su ziyarci Fe stas game da zancnen aikin hukuma"
AT: "Da Filikus ya bar nan, ya bar wani mutum a nan kurkuku"
Filikus ne gwamnar Roma na wannan yankin kuma yana zama ne a Kaisariya. Duba yadda aka juya wannan a [23:24]
Ana maganar ƙarar mutum a kotu ne kamar wani abu ne da mutum ke iya kai kotu. AT: "ya yi magana da ni game da mutumin nan"
Wannan na nufin cewa suna roƙo a ƙashe Bulus. AT: "sun roƙe ni in ƙashe shi" ko kuma "sun roƙe ni in tabbatar mishi da laifin da zai kai shi ga mutuwa"
A nan "ba da" na nufin a kai wani wurin wasu don su hukunta ko kuma su ƙashe shi. AT: "bari wani yă hukunta ko ma wa" ko kuma "bari ku hukunta wani da mutuwa"
Wannan na nufin su hadu da masu ƙararrakin sa. AT: "a gaban mutumin da aka zarge shi da laifi ya haɗu da masu zarginsa fuska da fuska"
"Da shike abinda na faɗa maku gaskiya ne." Festas ya fito ce gaya masu cewa duk mutumin da aka kai ƙaransa zai bayyana a gaban masu ƙaran don ya yi nasa magana akan ƙaran.
"da shugabannin Yahudawan sun zo sun same ni anan"
A nan "kujerar sheri'a" na nufin shari'ar da Festas yake kan yi akan Bulus. AT: "na zauna a bisa kujerar in yanke shari'a" ko kuma "na zauna a matasyin alkali"
AT: "na umarci sojojin su kawo Bulus gabana"
A nan "addini" na nufin ra'ayin mutane akan rayuwa da kuma abinda ya wuci ikon ɗan Adam.
A "shar'anta" karin magana ne da ke nufin a yanke wa mutum hukunci don a san ko mutumin yana da laifi ko babu. AT: "ya je yi masa shari'a a akan waɗannan laifuffuka" ko kuma "don mai yanke shari'a yă san ko waɗannan ƙararraki a kansa gaskiya ne ko ba gaskiya ba ne"
AT: "Amma Bulus ya nace a bar shi da masu tsaron Romawa har zuwa loƙacin da sarki zai zo yă shar'anta shi"
AT: "Sai na umarci sojoji su ajiye shi a wurinsu" ko kuma "Sai na ce wa sojoji su tsare shi"
"Ana iya fara jimlar da kalmomin nan "Festas ya ce" AT: "Festas ya ce, 'zan ba ka lokaci ka saurare Bulus gobe'"
"tare da kasaitaccen taro su basu girma"
Wannan wata babban ɗaki ne da jama'a kan taru domin bukukkuwa, da shari'u, da kuma wasu abubuwa.
AT: "sojojin sun fito da Bulus ya bayyana a gabansu"
Ana amfani ne da kalmar nan "dukkan" domin a nanata cewa Yahudawa masu yawa sosai suna son Bulus yă mutu. AT: "Yahudawa masu yawa sosai" ko kuma "shugabaninnin Yahudawa da dama"
"suna yi mani magana da ƙarfi"
Ana iya juya wannan a wata hanya daban. AT: "A ƙashe shi nan yanzu yanzu"
"domin ya ce yana so sarki ne ya yanke masa shari'a"
Sarkin shi ne mai mulƙin ƙasashen da ke yankin Roma. Ya mulƙe ƙasashe da lardodi masu yawa.
"Na kawo Bulus a gaban ku dukka, musamman kai, ya Sarki Agaribas."
"domin in sami wani abu kuma da zan rubuta" ko kuma "domin in san abinda zan rubuta"
Ana iya juya kalmar nan "wauta" da kuma "ba tare da" a wata hanya daban. AT: " a yana da kyau idan na aika da aɗn sarka, in rubuta"
Wannan na iya nufin 1) zargin da Shugabannin Yahudawa suka kawa a kansa ba ko kuma "ƙararrakin dokar Romawa da sun shafe Bulus.
1Sai Agaribas ya ce wa Bulus, "Za ka iya kare kan ka." Sai Bulus ya daga hannunsa ya fara kare kansa. 2"Ina farinciki, ya sarki Agaribas, game da saran da Yahudawa ke kawowa a kaina yau; 3musamman ma don kai masani ne game da al'adun Yahudawa da al'amuransu. Don haka, ina rokanka ka yi hakuri ka saurare ni.4Hakika, dukan Yahudawa sun san yadda na yi rayuwa ta daga kurciyata a kasa ta, da kuma Urushalima. 5Sun san ni tun farko, kuma yakamata su yarda cewa na yi rayuwa kamar Bafarase, darikan nan mai tsatsauran ra'ayi ta addininmu.6Yanzu ina tsaye a nan dominn a shari'anta ni, saboda alkawalin da Allah ya yi wa ubanninmu. 7Domin wannan shine alkawalin da kabilunmu goma sha biyu suka sa zuciya su karba, yayin da suke yin sujada da himma ga Allah dare da rana. Saboda wanan bege, Sarki Agaribas, Yahudawa ke tuhuma ta. 8Me ya sa wani zai yi tunani cewa abin mamaki ne Allah ya ta da mattatu?9Da, na yi tunanin yin abubuwa gaba da sunan Yesu Banazarat. 10Na yi wadanan a Urshalima. Na kulle masu bi da yawa a kurkuku, sanadiyar iko da na samu daga wurin manyan firistoci, kuma da ake kashe su ma, ina ba da goyon baya. 11Na wahalshe su sau dayawa a cikin dukan majamiu ina kuma yin kokari in tilasta masu su yi sabo. Na yi gaba mai zafi da su kuma na tsananta masu har zuwa birane na wadansu kasashe.12A sa'anda nake yin wannan, na tafi Dimashku da izinin manyan firistoci; 13a cikin tafiyata kuma, da tsakar rana, ya sarki, na ga haske daga sama da ya fi rana sheki, ya haskaka kewaye da ni da kuma wadanda ke tafiya tare da ni. 14Da dukanmu muka fadi kasa, na ji wata murya na magana da ni a harshen Ibraniyawa tana cewa, 'Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mani? Yana da wuya ka hauri abin da ke mai tsini.'15Sai na ce, 'Wanene kai ya Ubangiji?' Ubangiji ya amsa, 'Ni ne Yesu wanda kake tsanantawa. 16Yanzu ka tashi tsaye domin saboda wannan dalili ne na bayyana gare ka in sanya ka, ka zama bawa da mashaidi na game da abubuwan da ka sani a kaina yanzu da wadanda zan bayyana maka daga bisani; 17Zan kubutar da kai daga wurin mutane da kuma al'ummai da zan aike ka wurinsu, 18domin ka bude idanunsu ka juyo su daga duhu zuwa haske da daga ikon Shaidan zuwa ga Allah, domin su karbi gafarar zunubai da gado da zan ba wadanda na kebe wa kaina ta wurin bangaskiya gare ni.'19Saboda haka, sarki Agaribas, ban yi rashin biyayya da wahayin da na gani daga sama ba; 20amma, da farko ga wadanda ke a Dimashku, sa'annan a Urushalima da kasar Yahudiya gaba daya, da dukan Al'ummai, na yi wa'azi domin su tuba su kuma juyo ga Allah, su yi ayyukan da suka chanchanci tuba. 21Domin wannan dalili ne Yahudawa suka kama ni a cikin haikali kuma suke kokari su kashe ni.22Allah ya taimake ni har wa yau, domin in iya tsayawa gaban mutane kanana da manya, in bada shaida game da iyakar abin da annabawa da Musa suka fada zai faru; 23wato lallai Almasihu zai sha wahala, ya kuma zama na farko da za'a rayar daga matattu ya kuma yi shelar haske zuwa ga mutanen Yahudawa da Al'ummai."24Da Bulus ya gama kare kansa, Festas ya yi magana da babban murya, "Bulus, kana hauka; yawan iliminka yasa ka hauka." 25Amma Bulus ya ce, "Ba na hauka, ya mai girma Festas; amma da karfin zuciya nake fadi kalmomin gaskiya da na natsuwa. 26Saboda sarkin ya san wadannan abubuwa duka; shi ya sa nake magana gabagadi, don na hakikance cewa, ba abin da ke a boye gare shi; gama ba a yi wadannan abubuwa a boye ba.27Ko ka gaskanta da annabawa, Sarki Agaribas? Na sani ka gaskanta." 28Agaribas ya ce wa Bulus, "A cikin karamin lokaci kana so ka rinjaye ni ka mai da ni Krista?" 29Bulus ya ce, "Ina roko ga Allah, domin ko a karamin lokaci ko a dogon lokaci, ba kai kadai ba, amma har da wadanda ke sauraro na yau su zama kamar ni, amma ban da wadannan sarkokin."30Sai sarki ya tashi tsaye tare da gwamna da Barniki da dukan wadanda ke zaune tare da su; 31da suka bar dakin taron, suka ci gaba da magana da juna suna cewa, "Wannan mutum bai yi wani abin da ya chanchanci mutuwa ko kuma dauri ba." 32Agaribas ya ce wa Fastos, "Da mutumin nan bai daukaka kara zuwa ga Kaisar ba da an sake shi."
Festas ya kawo Bulus gaban Agaribas. A aya 2, Bulus ya ƙare kansa game da ƙarar da aka kawo a kansa.
Agaribas ne sarkin da ke kan mulki a Palastini, ko da shike yana mulkin kananan ƙasashe ne. Duba yadda aka juya wannan sunan a [25:13].
"miƙa hannunsa" ko kuma "ya yi motsi da hannunsa"
AT: "ya fara ƙare kansa daga masu zarginsa"
Bulus yana farin ciki domin ya ɗauki bayyanawarsa a gaban Agaribas yă zama wani zarafi ne mai na yin bishara.
Wannan jimlar na nufin mutum yă bayyana halin da yake ciki, don jama'a da ke kotu su tattauna su kuma yanke hukunci. AT: "in ƙari kaina"
A nan iya sanar da kalmar nan "ƙararraki" zuwa ƙara." AT: "ga dukkan ƙararrakin da Yahudawa ke yi a kaina"
Wannan bai haɗa da kowane Bayahuɗe ba. AT: "shugabannin Yahudawa"
Ana iya ƙara bayani akan irin al'amuran da ake magana a kai. AT: "al'amuran addini"
Wato ana nufin masu yawa kenan. Wannan na iya nufin 1) Wannan na nufin Yahudawa dai da sun san game da Bulus. AT: "Yahudawan" ko kuma "2) wato Yahudawan da sun san Bulus. AT: "shugabannin Yahudawa"
Wannan na iya nufin 1) a cikin mutanensa, ba lallai a zancen ƙasar Isra'ila ba ko kuma 2) in ƙasar Isra'ila.
"ɗarikar addinin Yahudawa da ta fi kiyaye kowace ka'ida"
A nan "ku" na nufin jama'ar da ke sauraron Bulus.
Wannan na nuna alamar ƙaucewar Bulus daga maganar da yake yi na abubuwan baya zuwa maganar abubuwan kansa a lokacin da ake ciki.
AT: "ga ni a nan, in da suna mini bahasi"
Ana maganar alkawalin ne anan kamar wani abu ne da mutum ke iya nema har yă gani. AT: "Ina jira, ina kuma sa zuciya ga Allah zuwa ga cikar alkawarin da ya yi wa kakkaninmu"
Jimlar nan "kabilanmu goma sha biyu" na nufin mutanen waɗannan kabilu. AT: "Wannan shi ne 'yanuwanmu Yahudawa na kabilu goma sha biyu ke jira"
Ana maganar alkawali kamar wani abu ne da mutum ke iya karɓa.
Waɗannan matsanancin kalmomin "dare" da "rana" na nufin suna "wa Allah sujada akai akai."
Ba dukkan Yahudawa aka nufi ba. AT: "Shugabannin Yahudawa ke"
Bulus yana amfani ne da wannan tambayan yă kalubalanci Yahudawan da ke wurin. Sun gaskanta cewa Allah na iya ta da matattu amma ba su yarda cewa Allah ya ta da Yesu ba. Ana iya sanar da wannan cikin jimla. AT: "Ba wanin ku da bai gaskanta cewa Allah yana ta da matattu ba"
A nan a tayar wata karin magana ce ta sa wanda ya mutu ya tashi kuma. AT: "yana sa matattu su tashi kuma"
Bulus yana amfani ne da wannan jimlar yă matsowa zuwa wani bangaren ƙare kansa. Yanzu ya fara bayanin yanda shi ma a dã ya tsananta wa Mutanen Yesu.
Kalmar nan "suna" na nufin koyarwa akan mutumin. AT: "in hana mutume koyarwa game da Yesu"
AT: "Na amince da sauran shuganannin Yahudawan cewa su yanke wa masubi hukuncin mutuwa"
Wannan na iya nufin 1) Bulus ya wahalshe wasu masubi da sau da dama ko kuma 2) Bulus ya wahalshe masubi daban daban sau da dama.
Bulus yana amfani ne da wannan jimlar domin yă dasa wata aya a kare kansa da yake yi. Yanzu yana maganar lokancin da ya gan Yesu har ya zama almajirinsa.
Wannan kalmar na ba da alamar abubuwa biyu da ke faruwa a lokaci guda. A wannan sa'a, Bulus ya tafi Damisku lokacin da yake sananta wa masubi.
Bulus yana riƙe da wasiku daga Shugabannin Yahudawa, wanda ke bashi izini ya sananta wa Yahudawa masubi.
A nan "murya" na nufin mai magana. AT: "na ji wani yana magana da ni cewa"
Wato ana maganar yadda Bulus yă ki karɓin Yesu ne amma yă sananta wa masubi kamar shi wani takarkari ne da ke hauri sanda mai tsini da mutum ke amfani da shi yana kiwon dabba. Wannan na nufin cewa Bulus ya yi wa kansa ne rauni. AT: "Kana dai yi wa kanka ne rauni kamar yadda takarkari ke hauri sanda mai tsihi"
Ana maganar taimakon mutum yă fahimci gaskiya ne kamar taimakon mutum ne ya buɗe idanunsa.
Ana maganar taimaka wa mutum yă daina aikata mugunta ne yă kuma fãra dogara ga Allah yana kuma yi masa biyayya kamar mutumin yana jagoran wani daga wuri mai duhu zuwa wuri mai haske.
Ana maganar tamaka wa mutum yă daina yi wa shaidan biyayya ne yă kuma fãra biyayya Ga Allah kamar mutumin yana juyo wa ne daga wurin da shaidan ke mulki ana kuma jagoransa zuwa wurin da Allah ke mulki.
AT: "domin Allah yă gafarce zunubansu"
Ana iya juya wanna kalmar gãdo zuwa gãda. AT: "domin su gãda abinda zan bayar
Ana maganar albarkun da Yesu ke ba wa waɗanda sun gaskanta da shi ne kamar wasu kayan gãdo ne da 'ya'ya ke samu ne na mahaifinsu.
Ana maganar zaɓen da Yesu ya yi wa wasu su zama na shi kamar ya keɓe su ne daga sauran mutane.
"domin sun gaskanta da ni." Anan, Bulus ya gama furcin maganar Allah.
"Da shike abinda na faɗa gaskiya ne." Bulus ya fito yin bayanin abinda Ubangiji ya umarce shi a wahayin.
AT: "na yi biyayya"
Wato abinda mutumin ya faɗa wa Bulus a wahayin. AT: "abinda mutum na sama ya faɗa mani a wahayin"
Ana maganar fara dogara ga Allah ne kamar mutum ya juya ne ya fãra tafiya zuwa wurin Allah." AT: "dogara ga Allah"
AT: "su kuma fãra ayyukan da za su hakikanci cewa sun tuba"
AT: "game da daidai abinda"
Bulus na nufin rubuce rubucen annabawan Tsohon Alkawali gaba ɗaya.
Ana iya karin bayyani anan cewa lallai ne Almasihu ma yă mutu. AT: "wato lallai ne Almasihu yă sha wahala har ma yă mutu"
yă sake rayuwa
Jimlar nan "matattu" na nufin ruhohin waɗanda sun mutu. A rayu daga cikinsu na nufin a sake samun rai kuma.
zai yi shelar sakon hasken." Ana maganar yadda Allah ke ceto ne kamr mutum yana maganar gaskiya ne. AT: "zai yi shelar sakon yadda Allahe ke ceton mutane"
"kana maganan banza ne" ko kuma "kai mahaukaci ne"
"iliminka yayi yawa har a shi yanzu ka haukache"
AT: "ina cikin hankali na ... kuma" ko kuma "ina iya tunani da kyau ... kuma"
"Festas, wanda ya cancanci dukkan daraja"
Har yanzu Bulus yana magana da Sarki Agariba ne, amma yana magana da shi a matsyin mutum na uku. AT: "Saboda kai ... da kai ... gare ka"
Bulus bai ji tsoron faɗa wa sarkin game da Almasihu ba. AT: "nake magana da gabagaɗi"
AT: "na tabbata"
AT: "cewa ya san da haka" ko kuma "cewa kana da sanin wannan"
"ba su faru a ɓoye ba"
Wato, yin abu a asirce kammar mutum ya shigo wani wuri ne da ba a iya ganinshi. AT: "a cikin duhu" ko kuma "a asirce"
Bulus yana wannan tambayan ne domin ya tunashe Agaribas da cewa Agaribas ya riga ya gaskanta da abinda annabawa sun faɗa game da Yesu. AT: "Ai ka riga ka gaskanta da abinda annabawan Yahudawa suka faɗa, Sarki Agaribas."
Agaribas yana amfani ne da wannan tambayan do ya nuna wa Bulus cewa ba zai iya ya rinjaye shi da sauke haka ba tare da kara wasu shaidu ba. AT: "Lallai fa, a ganinka za ka iya rinjaya na in gaskanta da Yesu a saukakke haka!"
A nan "sarkoki" na nufin zama ɗaurarre. AT: "amma, alhali ma, ba na son ka zama ɗaurarre kaman ni"
"Sai Sarki Agaribas ya tashi tsaye, tare da Gwamna Festas"
Wannan wata babban daki ne na bukukkuwa, sauraron kararraki da sauron taro.
Ana iya sanar da kalmar nan "mutuwa" zuwa "mutu". AT: "Wannan mutum bai chanchanci ya mutu ko a rufe shi a ɗaure shi a kurkuku ba"
AT: Da wannan mutum ya samu 'yanci" ko kuma "Da na sake mutuminan"
1Bayan da aka amince zamu tafi Italiya, sun mika Bulus tare da wadansu daurarru a hanun wani jarumi mai suna Yuliyas, daga batalian Agustas. 2Muka shiga Jirgin ruwa daga Adramatiya, wanda ke shirin tashi zuwa kusa da gefen tekun Asiya. Sai muka je teku. Aristakus mutumin Tasalonika a Makidoniya ya tafi tare damu.3Washegari muka sauka birnin Sidon, inda Yuliyas ya nuna wa Bulus karamci ya kuma yarda abokansa su bi shi don ya kula da su. 4Daga wurin, muka bi teku muka tafi ta Tsibirin Kubrus, domin matsananciyar iska da ke gaba damu. 5Sa'adda muka ketare ruwa zuwa sassan Kilikiya da Bamfiliya, muka zo Mira ta birnin Lisiya. 6Anan, jarumin ya sami jirgin ruwa daga Iskandariya wanda za shi Italiya. Ya samu cikinsa.7Kwana da kwanaki muna tafiya a hankali a karshe da kyar muka sauka kusa da Sinidus, iska ta hana mu tafiya, sai muka ratsa ta Karita, kusa da Salmina. 8Da wahala muka bi ta makurda har muka zo wani wuri da ake kira Mafaka Mai Kyau wanda ke kusa da birnin Lasiya.9Yanzu mun dauki dogon lokaci, gashi lokacin azumin Yahudawa ya wuce, tafiyar kuma ta zama da hatsari. Bulus ya gargade su, 10ya ce, "Jama'a, na gane tafiyarmu zata zamar mana da barna da asara mai yawa, ba ga kaya da jirgin kadai ba amma har da rayukan mu." 11Amma jarumin ya fi mai da hankali ga maganar shugabansa da mai jirgin ruwan, fiye da abubuwan da Bulus ya fadi.12Da shike tashar ba za ta yi dadin zama da hunturu ba, mafi yawa sun ba da shawara a bar wurin, in maiyiwuwa ne muga mun kai birnin Finikiya, don mu yi hunturu a can. Finikiya tashar jirgin ruwa ce a Karita, tana fuskantar arewa maso gabas da kudu maso gabas. 13Sa'adda iska daga kudu ta huro a hankali, sun tsammaci bukatarsu ta biya. Sai suka janye linzamin jirgin ruwan sukabi ta Karita kusa da gaba.14Amma bayan wani dan lokaci sai iska mai karfi da ake kira Yurokilidon, ta fara bugun mu daga tsibirin. 15Sa'adda Jirgin ruwan ya kasa fuskantar iskar, sai muka bi inda iskar ta nufa. 16Sai muka bi ta inda muka sami kariya kusa da wani dan tsibiri wanda ake kira Kauda; kuma da wahala muka daure karamin jirgin a jikin babban.17Bayanda suka daga shi, sun yi amfani da igiyoyi don su daure jirgin don gudun fadawa kan yashin Sirtis, suka bar jirgin yana ta korarsu. 18Mun yi ta fama da hadari ba kadan ba, da gari ya waye ma'aikatan jirgin suka fara zubar da kaya daga jirgin.19A rana ta uku, ma'aikatan jirgi suka jefar da kaya daga cikin jirgin da hannuwansu. 20Kwanaki dayawa ba mu ga hasken rana da taurari a bisan mu ba. Babban hadari kadai ke dukanmu, duk mun fidda zuciya zamu tsira.21Sa'adda sun dade basu ci abinci ba, sai Bulus ya tashi a gaban ma'aikatan jirgi yace, "Jama'a, da kun saurare ni, da bamu tashi daga Karita ba, balle mu fuskanci wannan barna da asarar. 22Yanzu fa ina karfafa ku kuyi karfin hali, domin ba wanda zai rasa ransa a cikinku, sai dai jirgin kadai za a rasa.23Domin daren da ya gabata mala'ikan Allah wanda ni nasa ne, wanda kuma nake bautawa -mala'ikansa ya tsaya kusa dani 24ya ce, "Kada ka ji tsoro, Bulus, dole ka tsaya gaban Kaisar, duba kuma, Allah cikin jinkansa ya baka dukan wadannan da ke tafiya tare da kai. 25Domin haka, jama'a, kuyi karfin hali, domin na gaskanta da Allah, kamar yadda aka fada mani haka zai faru. 26Amma lallai dole ne a jefa mu kan wani tsibiri".27Sa'adda dare na goma sha hudu ya yi, ana ta tura mu nan da can a cikin tekun Adriyat, wajen tsakar dare, ma'aikatan jirgin sun tsammaci sun kusanci wata kasa. 28Da suka gwada sai suka iske kamu ashirin; bayan dan lokaci kadan, sun sake aunawa sai suka iske kamu sha biyar ne. 29Tsoro ya kama su ko watakila a jefar da mu kan duwatsu, sai suka jefa linzami hudu daga karshen jirgin suka yi addu'a don gari ya waye da sauri.30Ma'aikatan jirgin ruwan suna neman hanyar da za su rabu da jirgin kuma sun jefa karamin jirgin a cikin teku. Suka yi kamar zasu jefa wasu linzamai daga gaban jirgin. 31Amma Bulus ya ce ma jarumi da sojojin, "Idan mutanen nan ba zasu tsaya cikin jirgin ba, ba zaku tsira ba". 32Sai sojojin suka yanke igiyoyin jirgin suka kuma barshi ya fadi.33Da gari ya fara wayewa, Bulus ya roke su duka su dan ci abinci, ya ce, "Yau kwana goma sha hudu kenan ba ku ci kome ba. 34Saboda haka na roke ku ku ci abinci, domin wannan saboda lafiyarku ne; kuma ko gashin kanku daya baza ku rasa ba". 35Da ya fadi haka sai ya dauki gurasa ya yi godiya ga Allah a idanun kowa. Sai ya gutsutsura gurasa ya fara ci.36Sai dukansu suka karfafu suka kuma ci abinci. 37Mu mutane 276 (dari biyu da saba'in da shida) ne cikin jirgin. 38Da suka ci suka koshi, suka zubar da alkamar cikin teku domin su rage nauyin jirgin.39Da gari ya waye, basu fahimci kasar ba, amma suka hangi wani lungu a gacci, sai suka yi shawara tsakaninsu ko su tuka jirgin zuwa cikin lungun. 40Sai suka yanke linzaman suka bar su cikin tekun. Cikin lokaci guda suka kwance igiyoyin da ke juya jirgin, suka saki filafilan goshin jirgi suka nufi gabar tekun. 41Da suka iso inda ruwa biyu suka hadu, sai jirgin ya tsaya kasa. Gaban jirgin ya kafe a nan, ba damar matsawa, sai kuma kurar jirgin ta fara kakkaryewa saboda haukan rakuman ruwa.42Shirin sojojin ne su kashe 'yan kurkukun domin kada su yi iyo su tsere. 43Amma shi hafsan ya so ya ceci Bulus, sai ya tsai da shirin su, ya ba da umarni, duk masu iya iyo su yi tsalle su fada ruwa su kai gacci. 44Sa'annan sauran mazajen su biyo baya, wadansu a kan karyayyun katakai, wadansu akan abubuwan da ke a jirgin. Ta haka ne dukanmu muka kai gacci lafiya.
Bulus, ɗaurarre, ya kama hanyarsa zuwa ƙasar Roma.
Kalmar nan "mu" ya shafe marubucin Ayyukan Manzanni, Bulus, da sauran mutanen da ke tafiya da Bulus, banda masu karatu.
AT: "Bayan da sarki da gwamna suka amince"
Italiya sunar wata yanki ne da ƙasar Roma take. Duba yadda ake juya "Italiya" a [18:2]
AT: "aka sa wani jarumi mai suna Yiliyas, na batalian Agustas, a matsayin mai lura da Bulus sa wasu ɗaurarru"
Wannan na iya nufin: 1) "su" na nufin gwamna da sarkin ko kuma 2) "su" na nufin "suran ma'aikatan Roma.
"Yuliyas sunan wani mutum ne.
Wannan shi ne sunar batalia ko soja da jarumin ya fito. Wasu.
A nan "jirgi ...wanda ke shirin tashi" na nufin ƙungiyar ma'aikatan jirgin. AT: "Muka shiga jirgin ruwa ... wanda ma'aikatan jirgin na shirin tashiwa"
Wannan na iya nufin 1) Jirgin ruwa da ta fito daga Adramatiya ko kuma 2) Jirgin ruwa da aka yi rajistanta ko mai aiki da takardan izinin aiki daga Adramatiya.
"nan da nan zai tashi" ko kuma "zai tafi nan da nan"
"muka fara tafiyar mu a teku"
Aritakus mutumin Makidoniya ne amma ya riƙa aiki da Bulus a ƙasar Afisus. Duba yadda aka juya wannan a [19:29]
"Yuliyas ya nuna wa Bulus halin abokin ƙwarai." Duba yadda aka fasara "Yuliyas" a [27:1]
AT: je wurin abokansa don su kula da shi" ko kuma "je wurin abokansa don su taimaka masa da duk abubuwan da yake bukata"
"muka fara tashi a jirgin ruwa muka tafi"
"tsibirin Kuburus" wate gefen Tsibirin ne da ke tare iska mai ƙarfi, don haka jiragen ruwa masu tafiya basu iya ƙauce wa daga fagen su.
Wannan wata yanki ne a Ƙaramar Asiya. Duba yadda aka juya wannan a [2:10]
Ana iya karin bayyani cewa sun suka daga jirgin ruwan a Mira. AT: "suka zo Mira, ta birnin Lisiya, inda suka sauka daga jirgin ruwan"
Mira sunar wata birni ce.
Lisiya wata yankin Roma ne, da ke tsibirin kudanci ta yamma na ƙasar Turki a yau.
Ana ɗaukan cewa ƙungiyar ma'aikata jirgin ruwan za su tashi zuwa Italiya. AT: "sami wata jirgin ruwan da ƙungiyar ma'aikatanta suka taso daga Iskandariya kuma za suna kokarin tasowa zuwa Italiya"
Wannan sunan wata birni ce.
Ana iya bayyana a fili dalilin da ya sa suka yi ta tafiya a hankali da kuma wahala da suka sha saboda iska da ke ɓullowa daga ɗayan gefensu ne.
Wannan at tsohon mazauni ne da ke ƙasar Turki a ya.
"muka kasa tafiya ta wancan gefen saboda iska mai ƙarfi"
"sa muka ratsa ta Karita wurin da ba iska sosai"
Wannan wata birni ce mara laushi a Karita.
Ana iya bayyana a fili cewa ko da shike iskan ba ta da ƙarfi kamar na da, amma har yazu ta kai ta sa tafiya ta zama da wahala.
Wannan wata tasha ce kusa da Lasiya, a tsibirin da ke kudancin Karita.
Wannan wata wata birni ce mara laushi da Karita.
Tafiyansu daga Kaisariya zuwa Mafaka Mai Kyau ya ci masu lokaci fiye da yadda suka shirya saboda gefen da iska ke ɓullowa.
Marubicin yan haɗa kansa, da Bulus, da kuma masu tafiya tare da su, amma banda mai karatu.
Ana wannan azumin ne a Ranar yin Kafara, wanda yakan zo a ƙarshen watan tara ko a farkon watan goma bisa ga kalanda na ƙasashen Yammaci. Bayan wannan lokaci, akwai hatsarin lokacin iska mai ƙarfi.
"idan mun yi tafiya yanzu, za mu sha barna da asara masu yawa"
Bulus ya haɗa kansa da masu sauraronsa, don haka wannan ya shafe su dukka.
A nan "asara" na nufin barna a zancen abubuwa sa'annan hallaka a zancen mutane.
Kaya anan na nufin kaya waɗanda jirgin ruwa ke ɗauka. AT: "ba jirgin kadai ba, har na dikiyan da ke jirgin"
AT: "da Bulus ya ce"
Ana iya faa a fili dalilin da ya sa tashar ba za ta yi dadin zama da hunturun ba. AT: "tashan ba ta tsare wurin tsayan jirgin ruwa yadda yakamata a lokacin da hunturu na fita da hadari
wani wuri ne a kusa da kasa da ya fi kyau ga jiragen ruwa
Finikiya wata garin tasha ne da ke kudancin tsibirin Karita.
Ana maganar lokacin hunturu kamar wani abu ne da mutum ke iya yi. AT: "don mu zamna a can saboda lokacin sanyi"
A nan "fuskantar arewa maso gabas da kudu maso kudu" na nufin mabudin tashar suna waɗannan gefen. AT: "ya budu zuwa ta arewa maso gabas da kudu maso gabas"
Waɗannan kwatancen na bisa ga haura.war rana da fitanta. Arewa maso gabas tana ɗan kusa da gefen hago na fitar rana. Kudu maso gabas tana ɗan kusa da gefen dama na fitar rana. Wasu juyin na cewa "arewa maso yamma da kudu maso yamma."
A nan "Janye" na nufin a ja daga cikin ruwa. Linzamin jirgin ruwa wani abu ne ma nauyi da ke a haɗe da wani igiya da ke tsare jirgin ruwar. Ana jefa linzamin jirgin ruwan zuwa cikin ruwan yă lume zuwa kasan tekun don yă tsare jirgin ruwan daga kaucewa.
"bayan ɗan karamin lokaci"
"wani iska mai ƙarfi, mai hatsari kuma"
"ake kira iska mai ƙarfi daga arewa maso gabas." Wannan kalmar "Yurokilidon" ya zo ne daga ainihin harshen da aka rubuta littafi. Kuna iya juya wannan kalmar yadda zai yi dai dai da harshen ku.
"ta huro daga tsibirin karita, ta bugo jirgin mu da ƙarfi"
"Sa'adda iskan ta bugo da ƙarfi ƙwarai a gaban jirgin har ma muka kasa tafiya"
AT: "muka kasa tafiya gaba, sai muka bar iskan ta bi da mu inda ta nufa"
"Sai muka bi gefen tsibirin, inda iskar ba ƙarfi sosai"
Wannan tsibirin yana kudancin tsibirin Karita.
Wannan wata ƙaramin jirgi ne da akan ja shi a bayan jirgin kuma wani lokaci akan shigo jirgin a ɗaura a kasan. Ana amfani ne da wanns jirgin domin dalilai da yawa, har ma a haɗe da tsira daga lumewar jirgi.
"suka daga karamin jirgin" ko kuma "suka jawo karamin jirgin daga babban jirgin"
Sun ɗaure jirgin don kar jirgin ba zai raɓu sa'adda iskan ya huro.
yashin Sirtis wurare ne masu zurfi inda jirage suna iya maƙalewa a yashin. Sirtis yana tsibirin Libiya, a arewacin Africa.
Suka jefa sarkokin jirgin a ruwan don ya rage gudun jirgin zuwa wurin da iskan zai iya ƙorarsu. Ana sake sarkan zuwa cikin ruwan ne don ya tsare jirgin daga kauche na da can. Duba yadda aka juya wannan a [27:13]
AT: "yana tafiya ta kowani gefen da iskan ke huramu"
AT: "Iskan ya hura mu barkatai gaba da baya har muka ji raunuka muka kuma gurje saboda iskan"
"su" wato ma'aikatan jirgin kenan. Sun yi haka ne don su rage nauyin jirginsu hana shi daga lumewa
Kayayyakin da ake tafiya da su a jirgin ruwan kenan. Duba yadda aka juya wannan a [27:10]. AT: "su amfanin da ke jirgin"
A nan "kaya" na nufin kayakin da ma'aikatan jirgin na buƙata don su yi tafiya da jirgin; su magance, hau, tsakiyar katsko, a toshe a magance, igiyoyin, filafilai da dai sauransu. Wannan na nuna alamar yadda yanayin gaggawa da suka shiga yake.
Ba su iya ganin rana da taurari ba saboda iskar haɗari. Ma'aikatan jirgin suna bukatar rana da taurari ne don su san inda suke da inda suka nufa.
"Babban haɗari yana dukanmu gaba da baya"
AT: "kowa ya daina sa zuciya cewa za mu tsira"
A nan "su" na nufin ma'aikatan jirgin. Ana ɗaukan cewa, Luka, Bulus, da waɗanda ke tare da asu ba su ci abinci dama ba. AT: "Sa'ad da muke daɗe na sawon lokaci ba cin abinci"
"a cikin mutanen"
"har kuma hakan ya sa mu fuskanci wannan lahani da asarar"
"Bulus yana magana ne da ma'aikatan jirgin. A nan ɗaukan cewa, Bulus nna nufin shi da waɗanda ke tare da shi ma ba za su mutu ba. AT: "babu wanninmu da zai mutu"
Ana amfani ne da "rasa" anan a matsayin hallaka. AT: "amma iskan zai hallakar da jirgin"
Jimlar nan "tsaya a gaban Kaisar" na nufin Tafiyar Bulus kotu da yardarsa Kaisar ya shar'anta shi. AT: "Lallai ne ka bayyana a gaban Kaisar don yă shar'anta ka"
"ya zaɓa ya bar dukkan waɗanda ke tare da kai su rayu"
AT: "kamar yadda mala'ikan ya faɗa mini"
"Lallai ne mu tuƙa jirginmu don ya jujjugu a bisa wani tsibiri"
Ana iya sanar da wannan jerin lamba "goma sha huɗu" zuwa "sha huɗu." AT: "Bayan ƙwana 14 da iskan ya fara, da daren"
AT: "da tekun ke hura mu gaba da baya"
Wannan ita ce tekun da ke tsakanin Italia da Ƙasar Hellas.
"Suka gwada zurfin ruwan tekun." Sun gwada durfin ruwan ta wurin jefa wata igiya da abu mai nauyi zuwa ƙarshen ruwan"
"Kamu" ɗaya itace ce rabo ɗaya a ma'aunan auna zurfin ruwa. AT: suka iske mita 40"
"Kamu" ɗaya itace ce rabo ɗaya a ma'aunan auna zurfin ruwa. Kamu ɗaya tana kai kusan mita biyu. AT: "suka iske mita 30"
Linzami wani abu ne mai nauyi da ake haɗa shi da wani igiya domi a sare jirgi. Akan jefa linzamin a ruwa har ya sauka kansa tekun, don yă hana tekun masowa nan da can. Duba yadda aka juya wannan a [27:13]
"daga bayan jirgin"
Wannan wata ƙaramin jirgi ne da akan ja shi a bayan jirgin kuma wani lokaci akan shigo jirgin a ɗaura a kasan. Ana amfani ne da wanns jirgin domin dalilai da yawa, har ma a haɗe da tsira daga lumewar jirgi. Duba yadda kun juya wannan a [27:16]
"daga gaban jirgin"
"Ai sai waɗannan mutanen sun tsaya a jirgin kamun mu tsira"
"Da gari ya kussan wayewa"
Jerin lamba "goma sha huɗu" anan na iya zama "sha huɗu." AT: "ƙwana 14"
Wannan wata hanya ce na cewa babu wata illa da zai same su. AT: "dukkan ku za ku rayu daga wannan bala'in lafiya"
"ya tsinka gurasa" ko kuma "ya diba gutsurin gurasa"
AT: "Wannan ya ƙarfafa su dukka"
mu ɗari biyu da saba'in da shida a jirgin." Wannan ne bayyanin tarihin.
Wata babbar yankin ruwa da ke saurauta ke kewaye da kasa
"suka ga ƙasar amma basu fahimce shi kamar wani wurin da suka sani ba"
"yanke igiyoyin suka bar su a baya"
"Wata gungumen Itace da ke bayan jirgin ruwan da ake tuka jirgin da shi.
"kyallen da aka rataya su a gaban jirgin." Kyallen wata babban yaɗi ne da ke tsare hana iska matsar da jirgin.
"suka tuka jirgin zuwa gabar tekun"
Wato ruwa da ke tafiya a gefe ɗaya ba tsayawa. Wani lokaci, ana iya samun ruwa da ke ketere ɗaya. Wannan na iya sa ƙasar da ke ƙarkashin ruwar yă taru har ya sa ruwa ya kara zama na bisa-bisa.
"Gaban jirgin "
"bayan jirgin"
"Sojojin suna shirin"
"sa ya hana su yin abinda suka yi shirin yi"
"su yi tsalle daga jirgin ruwan zuwa ruwa"
"waɗansu a kan katakai"
1Sa'adda muka sauka lafiya, sai muka ji cewa sunan tsibirin Malita. 2Mutanen garin sun nuna mana alheri matuka don sun hura wuta don mu ji dimi, saboda ruwan sama da sanyin da ake yi.3Amma sa'adda Bulus ya tara kiraruwa don hura wuta, sai maciji saboda zafin wuta, ya fito ya nade hannuwansa. 4Da mazaunan garin suka ga maciji ya nade hannuwansa, sai suka cema junansu, "Ba shakka wannan mutumin mai kisan kai ne, koda shike ya tsira daga Teku, sharia baza ta barshi da rai ba".5Amma ya karkade macijin cikin wuta ba tare da ya cutar da shi ba. 6Sun saurara su gani ko zai kumbura ko ya fadi matacce. Amma da suka jira dan lokaci basu ga wata matsala ta same shi ba sai suka canza tunaninsu sukace shi wani allah ne.7A kusa da wannan wurin tsibirin akwai wasu gonakin wani babban mutumin tsibirin, mai suna Babiliyas. Ya karbe mu ya biya bukatun mu har kwana uku. 8Ana nan ashe mahaifin Babiliyas yana fama da zazzabi da atuni. Bulus ya shiga, yayi masa addu'a, ya dibiya masa hannu, ya sami warkarwa. 9Sa'adda wannan ya faru, sauran marasa lafiya da ke tsibirin sun zo sun sami warkarwa. 10Mutanen sun mutunta mu kwarai. Yayin da muke shirin tafiya, sun bamu duk abinda muke bukata.11Bayan watanni uku, mun shiga jirgin Iskandariya wanda tun da hunturu yake a tsibirin mai zane kamannin Tagwaye Maza. 12Bayan saukar mu a birnin Sirakus, mun yi kwana uku a wurin.13Daga nan sai muka tafi, har muka zo birnin Rigiyum. Bayan kwana daya iska mai karfi daga kudu ta taso, a cikin kwana biyu muka iso Butiyoli. 14A can muka iske wasu 'yan'uwa suka roke mu mu zauna tare da su har kwana bakwai. Ta wannan hanyar ce muka zo Roma. 15Daga can da 'yan'uwa suka ji labarin mu, suka fito don su tarbe mu tun daga Kasuwar Abiyas da kuma Rumfuna Uku. Da Bulus ya gan su, ya yi wa Allah godiya ya kuma sami karfafawa.16Sa'adda muka shiga Roma, aka yardar wa Bulus ya zauna shi kadai tare da sojan da ke tsaronsa. 17Ana nan bayan kwana uku, Bulus ya kira shugabannin Yahudawa. Bayan da suka taru, sai ya ce masu, "Yan'uwa, ko da shike ban yi wa kowa laifi ko keta al'adun Ubanninmu ba, duk da haka an bashe ni daurarre tun daga Urushalima zuwa ga hannunwan mutanen Roma. 18Bayan tuhumata, sun yi kudirin saki na, domin ban yi laifin da ya cancanci mutuwa ba.19Amma da Yahudawa suka tsaya a kan ra'ayin su, ya zama dole in daukaka kara zuwa ga Kaisar, ba domin ina da wani dalilin da zan yi karar al'ummata ba ne. 20Saboda wannan ne na bukaci ganinku in yi magana da ku. Saboda begen da Isra'ila suke da shi ya sa nake daure da wannan sarkar".21Sai suka ce masa, "Bamu karbi wasiku daga Yahudiya game da kai ba, babu kuma wani daga cikin 'yan'uwa wanda ya kawo mana wani rahoto ko wata magana game da kai. 22Amma muna so mu ji daga gare ka abin da kayi tunani ka kuma gani game da wannan darikar, gama mun sani ana kushenta a ko'ina."23Sa'adda suka sa masa rana, mutane da dama suka same shi a masaukinsa. Ya gabatarda zantattukan a gare su, yana tabbatar da bayyanuwar mulkin Allah. Har ya nemi ya rinjaye su a kan zancen Yesu, tun daga attaurat ta Musa zuwa litattafan annabawa, ya yi wannan tun daga safiya har yamma. 24Wasu sun kawar da shakkar abin da aka fada, amma wadansu basu gaskanta ba.25Da shike ba su yarda da junansu ba, sai suka tafi bayan da Bulus ya fadi kalma daya, "Ruhu Mai Tsarki ya yi magana ta bakin annabi Ishaya zuwa ga kakanninku. 26Ya ce, 'Jeka wurin al'umman nan ka ce, cikin ji zaku ji amma ba zaku fahimta ba; zaku gani amma ba zaku gane ba.27Amma zuciyar mutanen nan ta yi kanta, kunnuwansu sun ji da kyar, sun rufe idanunsu; don kada su gani su gane, su kuma ji da kunuwansu, kuma su fahimta da zuciyarsu, domin su juyo ni kuma in warkar da su."28Saboda haka, sai ku sani cewa wannan ceto na Allah an aikar da shi zuwa ga Al'ummai, za su kuma saurara." 29130Bulus ya zauna shekaru biyu a cikin gidan hayarsa, yana marabtar duk wadanda suka zo wurinsa. 31Yana wa'azin mulkin Allah, yana koyarwa da al'amuran Ubangiji Yesu Kristi gaba gadi. Ba wanda ya hana shi.
Bayan aukuwar haɗarin jirgin ruwar, Jama'ar da ke tsibirin Malita sun taimaka wa Bulus da kowa da kowa da ke jirgin. Suka yi zama a wurin har na wata 3.
A nan kalmar nan "mu" na nufin Bulus, marubucin, da kuma waɗanda suake tafiya tare da su, ammam ba masu karatu ba.
AT: "Sa'adda muka iso lafiya"
Bulus da Luka suka ji sunan tsibirin. AT: "muka ji daga baƙin mutanen" ko kuma "muka ji daga mazaunan wurin"
Malita wata tsibiri ce da ke kudancin tsibirin Sicily a yau.
"Ainihin 'yan wurin"
Ana maganar alheri kamar wani abu ne musamman da ake iya nunawa. AT: "ba ƙaramin alheri suka nuna mana ba"
"nuna mana baban alheri matuka"
"sun haɗa ƙirare da su reshe suka ƙone su"
Wannan na iya nufin 1) "suka marabci dukkan mutanen da ke jirgin ruwan" ko kuma 2) "suka marabci Bulus da dukkan abokan tafiyansa."
"sai maciji mai dafi sosai ya fito daga tarin itatuwan"
"ya cije Bulus a hannu ya kuma ɗafa hannun"
"Haƙikka, wannan mutumin mai kisan kai ne" ko kuma "Lallai wannan mutumin mai kisan kai ne"
kalmar nan "shari'a" sunan wani allah ne da suke bauta wa. AT: "allah da ake kira "shari'a"
"ya karkaɗe hannun sa don macijin ya faɗi daga hannunsa cikin wuta"
"Bai ji ma Bulus ba ko sam"
Wannan na iya nufin 1) jikinsa ya kumbura saboda defin macijin ko kuma 2) zai yi zafi ƙwarai da zazzabi.
AT: "kome akansa yana yadda yakamata"
Ana maganar yin wata tunani daban aka yanayi ne kamar mutum yana canza tunanisa. AT: "suka sãke tunani kuma"
AT: "cewa, 'lallai wannan wani allah ne"
Mai yiwuwa akwai wata bangaskiya da suke da shi cewa mutumin da har ya rayu bayan cizon maciji mai dafi sosai allah ne ko kuma na allah ne shi.
Ana amfani ne da wannan do a gabatar da wani sabon mutum ko abinda ya faru a labarin.
Wannan na iya nufin 1) ainihin shugaban mutanen ko kuma 2) wani mafi muhimmanci a tsibirin, mai yiwuwa domin dukiyarsa"
Wannan sunan wani mutum ne.
Wannan na ƙarin bayani ne game da mahaifin Babiliyas da zai zama da muhimmanci ƙwarai a fahimtar labarin.
yana fama da "rashin lafiya"
Atini wani ciwa ne da ke kama hankin mutum.
"ya taɓa shi da hannayensa"
AT: "ya warkar da su ma"
Mai yiwuwa sun mutunta Bulus da waɗanda ke tare da shi ta wurin ba su kyautai.
"wanda ƙungiyar ma'aikatan jirgin sun bari a tsibirin don lokacin sanyi"
Wannan na iya nufin 1) wata jirgi da ta zo daga Iskandariya, ko kuma 2) wata jirgi da aka yi mata rajista ko kuma aka ba ta takardin izinin aiki a Iskandariya.
A sashin gaba da jirgin ruwan, akwai siffar gumakai biyu da ake ce da su "tagwaye maza." Sunayen su na Kasto da Pollus.
Siracus wata gari ne a tsibirin kudu maso gabas na tsibirin Sikili a yau, daidai kudu maso yamma na Italiya.
Wannan wata gari ne na tsaha da ke kudu maso yammacin ƙareshen ƙasar Italiya.
"iskan ta fara tasowa ne daga kudu"
Butiyoli yana garin Napalis tsibirin yamma na ƙasar Italiya.
"A can muka sadu"
Wato masubin Yesu kenan, a haɗe da maza da mata. AT: "''yan'uwa masubi"
AT: "suka gayacce mu"
Da zara Bulus ya isao Butiyoli, sauran tafiyarsa zuwa ƙasar Roma a kasa ne dukka. AT: "Sa'annan bayan da mun yi ƙwana bakwai da su, sai mun tafi ƙasar Roma"
"da suka ji cewa muna zuwa"
Ana maganar samun ƙarfafawa ne kamar wani abu ne da mutum ke iya ɗaukawa. AT: "wannan ya ƙarfafa shi, sa'annan ya yi wa Allah godiya"
AT: "Da muka iso ƙasar Roma, sai hukumar Roma suka ba wa Bulus izinin"
Ana amfani ne da wanna jimlar don a dasa aya ga wata sabuwar bangaren labarin. Idan harshenku tana da wata hanya ta musamman na yin haka, kuna iya amfani da shi anan.
Wato shugabannin ma'aikatan gwamnati ko kuma na addini da ke Roma.
"yi wa mutanen mu laifi" ko kuma "yi wa Yahudawa laifi"
AT: "wasu Yahudawa sun kama ni a Urushalima suka da ni a hannuwan hukumar Romawa"
A nan "hannuwan" na nufin iko ko kuma mulki.
"ban yi wani abinda zai sa su su ƙashe ni ba"
Wannan bai shafi Yahudawa dukka ba. AT: "shugabannin Yahudaw"
"suka yi gardama da abinda hukumar Roma suke son si yi"
AT: "ya zama lallai ne in roƙa Kaisar yă yanke mini shari'a"
Ana iya juya kalmar nan "kara" zuwa "zargi." Anan "al'umma" na nufin jamar. AT: "amma ba wai don ina so in zarge al'ummata a gabar Kaisar bane.
Wannan na iya nufin 1) mutanen Isra'ila suna bidan zuwan Almasihu da gabagadi ko kuma 2) jama'ar Isra'ila
A nan "Isra'ila" na nufin mutanen. AT: "mutanen Isra'ila" ko kuma "Yahudawa"
A nan "ɗaure da wannan sarkar" na nufin zaman ɗaurarre. AT: "cewa ni ɗaurarre ne"
A nan "'yan'uwa" na nufin 'yan'uwa Yahudawa. AT: "babu kuma wani daga cikin 'yan'uwan mu Yahudawa"
Wata ƙaramar taro ne a tsakanin wata babban taro. Anan wanna na nufin waɗanda suka gaskanta da Yesu. AT: "kayi tunani game da darikar da kake"
AT: "domin mun sani"
AT: "Yahudawa da yawa a dukkan kasashen da ke cikin ikon Roma na faɗin munanan abubuwa akasa"
"suka zaɓa wani lokaci da zai yi magana da su"
A nan "mulkin Allah" na nufin mulkin Allah a matsayin mai sarauta. AT: "ya faɗa masu game da sarautar Allah a matsayinsa na sarki" ko kuma "ya faɗa masu yadda Allah zai nuna masu kansa a matsayin sarki"
A nan " litattafan annabawa" na nufin abinda suka rubuta. AT: "daga abinda annabawa suka rubuta"
AT: "Bulus ya samu ya ƙarfafa wasun su"
A nan "kalma" na nufin sako ko bayani. AT: "bayan da Bulus ya ƙara faɗi wani abu" ko kuma "Bulus ya yi wannan bayani"
AT: "Ruhu Mai Tsarki ya yi magana mai kyau ta wurin baƙin annabi Ishaya zuwa ga kakanninku sa'ad da Ruhu ya ce wa Ishaya yă gaya masu cewa za su ji amma ba za su fahimta ba; za su kuma gani amma ba za su gane ba"
Ana maimaita kalmomin nan "ji" da "gani" ne domin nanaci. "Za ku ji kam da kyau ... za ku kuma gani sosai"
Duk waɗannan a takaice na nufin abu ɗaya ne. Suna nanata ne cewa Mutanen Yahudawa ba za su fahimci shirin Allah ba.
Ana maganar mutanen da sun ƙi su fahimci abinda Allah ke cewa ne ko yi kamar zuciyar su ne ta yi kanta. Ana "zuciya" na nufin hankalin.
Ana maganar mutanen da sun ƙi su fahimci abinda Allah ke cewa ne ko yi kamar ba su iya ji kuma suna rufe idanunsu don su gani.
A nan "zuciya" na nufin hankali.
Ana maganar fara biyayya da Allah kamar mutum ne da ake iya ganinsa yana juyo wa zuwa ga Allah.
Wannan na nufin ba a jiki kadai Allah zai warkar da su ba. Amma zai warkar da su a ruhaniya ta wurin gafarta masu zunubansu.
Ana maganar yadda Allah yana ceton mutane ne kamar wani abu ne da aka aika. AT: "Allah yana aikan bayinsa zuwa ga Al'ummai su faɗa masu game da yadda zai cece su"
"wasunsu kuma za su saurara." Wannan amsa da Al'ummai za su yi ya banbanta da yadda Yahudawa suka amsa a wancan lokaci.
A nan "mulkin Allah" na nufin sarautar Allah a matsayin Sarki. AT: "Yana wa'azi akan sarautar Allah a matsayin Sarki" ko kuma "Yana wa'azin akan yadda Allah zai nuna kansa a matsayin sarki"
1Bulus, bawan Yesu Almasihu, kirayayye ya zama manzo, kuma kebabbe domin bisharar Allah. 2Wannan itace bisharar da ya alkawarta tuntuni ta wurin annabawansa ta wurin tsarkakakkun littattafan sa. 3Game da Dansa ne, haifaffe daga zuriyar Dauda ga zancen jiki.4Ta wurin tashinsa daga mattatu aka aiyana shi ya zama Dan Allah ta wurin ikon Ruhu na tsarkakewa. Yesu Almasihu Ubangijimu. 5Ta wurinsa muka karbi alheri da manzanci sabo da biyayyar imani a cikin dukkan al'ummai, domin darajar sunansa. 6cikin wadannan al'ummai kwa, ku ma an kiraku ku zama na Yesu Almasihu.7Wannan wasika ga dukkanku ne da kuke cikin Roma, kaunatattu na Allah, kirayayyun mutane tsarkakakku. Bari alheri ya kasance tare daku, da salama daga Allah Ubanmu, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.8Abu na farko dai ina yi wa Allah na godiya ta wurin Yesu Almasihu domin ku duka, domin kuwa ana labarta bangaskiyarku ko ina a cikin dukkan duniya. 9Domin kuwa Allah shi ne shaida ta, wanda nake bautawa a cikin ruhuna a cikin bisharar Dansa, yadda a koyaushe na ke ambaton ku. 10A kullum ina roko cikin addu'o'ina domin ta kowanne hali in yi nasarar zuwa gare ku da izinin Allah.11Gama ina marmarin ganin ku, domin in baku wata baiwa ta ruhaniya, domin in karfafa ku. 12Wato ina dokin in sami cikakkiyar karfafawa a cikin ku, ta wurin bangaskiyar junanmu, wato tawa da taku.13Yanzu fa bana so ku rasa sani, yan'uwa, sau da yawa nake yin niyyar zuwa wurinku, amma har yanzu hakan din bata samu ba. Na so yin hakan din ne don in sami 'ya'ya na ruhu a cikinku kamar dai yadda ya ke a sauran Al'ummai. 14Ina dauke da nawayar Hellinawa da ta sauran jama'a, masu hikima da marasa hikima. 15Don a shirye na ke in sanar da bishara a gare ku, ku da kuke cikin Roma.16Don kuwa ni ba na jin kunyar yin bishara, don ita ce ikon Allah don samun ceto ga duk wanda ya gaskata, da farko dai Yahudawa kana kuma Hellinawa,17Domin a cikin ta adalcin Allah ya bayyana daga bangaskiy zuwa bangaskiya, kamar yadda yake a rubuce, "Mai adalci zai rayu ne tawurin bangaskiya."18Domin fushin Allah ya bayyana ne daga sama gaba da rashin ibada da rashin adalci na yan'adam, wadanda suke danne gaskiya ta wurin rashin adalcin su. 19Dalili kuwa abinda yakamata a sani game da Allah a bayyane ya ke a gare su. Domin kuwa Allah ya bayyana masu shi a zahiri.20Domin al'amuransa da ba'a iya gani a bayyane suke tun halittar duniya. A na iya gane su ta wurin halitatattun abubuwa. Wadannan al'amura kuwa sune madawwamin ikonsa da Allahntakarsa. Sakamakon haka, wadannan mutane ba su da hujja. 21Dalili kuwa, koda suna jin sun san Allah, amma basu darajanta shi a matsayin Allah ba, ko kuma su nuna masa godiya. Maimakon haka, suka zama wawaye a cikin tunaninsu, zukatansu marasa tunani sun duhunta.22Suna daukar kansu akan masu hikima ne su, amma sai ga su sun zama wawaye. 23Sun musanya daukakar Allah madawwami da ta kamannin abubuwan da basa dawwama, kamar mutum, da tsuntsaye, da dabbobi masu kafafu hurhudu, da masu jan ciki.24Saboda haka Allah ya bashe su ga sha'awoyin kazantar zukatansu, su wulakantar da jukunansu a junansu. 25Sune suka musanya gaskiyar Allah da karya, Kuma suke sujada da bauta ga halittaccen abu, maimakon Mahaliccin, Wanda yake abin yabo har abada. Amin.26Saboda haka Allah ya bashe su, ga sha'awowin su na lalata da wulakanci, har matansu suka canza ka'idar jima'i da aka saba zuwa madigo mace da mace. 27Mazajensu ma suka sauya ka'idar jima'i tsakanin mace da miji zuwa namiji da namiji suna yin aikin lalata. Maza su na kwana da maza suna aikata aikin ban kyama, suna kuwa girbe sakamakon aiknsu na ban kyama.28Tunda shike ba su amince da Allah a cikkin al'amuransu ba, Allah ya bashe su ga bataccen hankalinsu, su aikata wadannan munanan abubuwa.29Suna cike da dukkan rashin adalci, mugunta, kyashi, keta, kuma cike da kishi, kisan kai, tarzoma, makirci, da kuma munanan manufafofi. 30Masu gulma da kage, makiyan Allah. Masu tada zaune tsaye, masu taurin kai, da ruba, masu kaga kowadanne miyagun abubuwa, kuma masu kin yin biyayya ga iyayensu. 31Masu duhun zuciya; masu cin amana, marasa soyayya, da kuma rashin tausayi.32Suna sane da tsarin Allah cewa masu yin irin wadannan al'amura sun cancanci hukuncin mutuwa. Ba kuwa yin wadannan abubuwan ka dai suke yi ba, harma goyon bayan masu yinsu suke yi.
Mai yiwuwa harshen ku na da wata hanya da take gabatar da marubucin wasika. Yana iya yiwuwa ku bayyana wadanda Bulus ya rubuto masu wasikar a ayan nan ta fari
AT: "Allah ya kira ni don in zama manzo ya kuma zaɓe ni in shaida wa mutane bishara"
Wannan na nufin cewa Allah ya naɗa ko ya zaɓe mutane su zama 'ya'yan sa, su zama bayin sa da kuma masu shaida sakon ceto ta wurin Yesu.
Allah ya yi wa mutanen sa alkawari cewa zai kafa mulkin sa. Ya ce wa annabawa su rubuta waɗannan alkawaran cikin littattafai.
Wannan na nufin "bisharar Allah", Labari mai kyau da Allah ya alkawarta cewa zai aiko da Ɗan sa cikin duniya.
Wannan laƙabi ce mai muhimmanci na Yesu, Ɗan Allah.
A nan kalman nan "jiki" na nufin jiki nan ta duniya. AT: "shi wanda ke daga zuriyar Dauda bisa ga halitan jiki" ko "wanda ke haifaffe daga iyalin Dauda"
A nan Bulus ya yi maganar takalifin sa don wa'azi.
Kalman nan "shi" na nufin Yesu Almasihu. AT: "Da iƙo Allah ya ce da shi Ɗan Allah"
"tawurin tashe sa da aka yi daga cikin su mutanen da suka mutu." Wannan na maganar dukan mutanen da suka mutu har ma da duniya ta mugayen ruhohi, kuma tashiwa da rai faɗaɗɗe ne kamar tashin mattatu daga cikin su.
Wannan na nufin Ruhu Mai Tsarki.
Allah ya ba wa Bulus kyautar zaman manzo. AT: "Allah ya mai da ni manzo." Wannan gatanci ne ta musamman"
Kalman nan "mu" anan na nufin Bulus ne da kuma manzanin nan dake mabiyan Yesu amma banda masubi dake ikkilisiyar da take a Roma.
Bulus ya yi amfani da wannan kalman "suna" kamar wata kalma ce da ake amfani da ita a maɗadin ainihin abin da ake magana a kai wanda anan tana nufin Yesu. AT: "Domin koyar da dukan al'ummai su yi biyayya saboda bangaskiyar su a gare shi"
AT: "Ina rubuta wannan wasikar ga ku da ke a Roma waɗanda Allah ya ƙaunace su ya kuma zaɓa don su zama mutanensa"
AT: "Bari Allah ya baku alheri da salama" ko "Bari Allah ya albarkace ku ya kuma baku salamar zuciya"
Kalman nan "Uba" lakani ce mai muhimmanci na Allah.
yankin Roma itace duniyan da Bulus da masu karanta wasikar sa sun sani kuma suna iya tafiye-tafiye ciki
Bulus ya nanata cewa yana yi musu addu'a kuma Allah ya gan shi a sa'adda yana yi masu addu'a. Kalman nan "don" yawancin lokatai ba a juya shi.
Ruhun mutum wata bangare ce tasa da ke iya sanin Allah da kuma gaskatawa cikin sa.
Labari mai kyau (bishara) ta Littafi Mai Tsarki ita ce Ɗan Allah ya bada kansa domin ceton duniya.
"Na yi magana da Allah game da ku"
"Ina addu'a a kowace lokaci , Ina roƙon Allah don ... in yi nasara ... cikin zuwa ziyartan ku"
"ta kowace hanyan da Allah ya bari"
"daga baya" ko "daga karshe"
"saboda muradin Allah"
"Domin lailai ina so in gan ku"
Bulus na so ya karfafa runahaniyar kristocin ta Romawa. AT: "waɗansu baiwa da za su taimake ku ku yi girma cikin ruhaniya"
AT: "Ina nufin cewa so nake mu karfafar Juna ta wurin bayyana bangaskiyar mu cikin Almasihu"
Bulus ya nanata cewa yana so su samu sanin wannan labari. Zaka iya juya wannan nau'i biyu cikin tabbatacen tsari. AT: "Ina so ku sani"
A nan wannan na nufin Krista ne, haɗe maza da mata.
AT: "ko wace lokaci wani abu kan hana ni"
Kalman "amfani" kwatanci ne da ke a madaɗin mutane da ke a Roma waɗanda Bulus ke so su gaskata da bishara. AT: "don mutane cikin ku su iya sa begensu cikin Yesu"
Al'ummai cikin waɗansu yanki ta inda ya riga ya je.
Yin amfani da kwatancin nan "bashi," Bulus ya yi magana a kan aiki bautar Allah kamar wata bashi ne ta kuɗi da Allah ke bin sa. AT: "Lailai ne in kai bishara zuwa ga"
Kuna iya juya wannan cikin tabbatacen tsari. AT: "Na sa begen dungum cikin bishara"
A nan "bada gaskiya" na ma'anan cewa mutum ya sa begen sa cikin Almasihu. AT: "gama ta wurin bishara ce Allah cikin ikonsa ya cece duk wanda suka sa begen su cikin Almasihu"
"ga mutanen Yahudawa sa'anan kuma Al'ummai"
A nan "farko" na ma'anan zuwa kafin sauran bisa ga lokaci.
A nan "ta" na nufin bishara. Bulus ya bayyana dalilin sa begen sa dungum cikin bishara.
Bulus ya yi maganar sakon bishara kamar wani abu ta duniya ne da Allah zai iya nuna wa mutane a fili. Ku na iya juya wannan cikin tsari mai aiki. AT: "Allah ya fada mana cewa ta wurin bangaskiya ne mutane su kan zama adalai tun farko har zuwa karshe"
AT: "kamar yadda wani ya rubuta cikin litattafai"
A nan "adalai" na nufin waɗanda su ka sa begen su ga Allah. AT: "ai mutanen da suka sa begen su ga Allah su ne ya dube su a matsayin waɗanda aka daidaita da shi, su kuma za su rayu har abada"
AT: "Gama Allah ya nuna fushin sa"
Bulus ya yi anfani da Kalman nan "gama" don ya nuna wa mutane cewa abin da ya fada cikin Romawa 1:17 gaskiya ne.
kalmomin nan "rashin bin Allah" da "rashin adalci" suna ce mai tsamo da ake iya bayyana ta tawurin amfani da kalma kamar "rashin bin Allah" ta na kamanta mutane, "rashin adalci" kuma kamanin ayyukan su ne. Sunayen nan kalma ce da ke nuna mutanen da Allah ke fushi da su. Ku na iya juya wannan cikin sifar aiki. AT: "Allah ya bayyana fushin sa daga sama ga mutane domin rashin bin Allahn su da kuma ayyukan duhu"
"gaskiya" anan na nufin gaskiyar labarin game da Allah. AT: "boye labari ta gaskiya game da Allah"
AT: "su na iya sanin Allah saboda abubuwan da suna iya gani a fili"
A nan "bayyana masu" na ma'anan cewa Allah ya nuna musu gaskiyar game da kansa. AT: "domin Allah ya bayyana wa kowa yadda yake"
Bulus ya yi maganar fahimtar al'amuran Allah marasa gănuwa ga mutane kamar mutane sun gan al'amuran. AT: "Gama mutane sun fahimci al'amuran Allah marasa gănuwa kamar haka, madawamiyar iƙon sa da allahntakarsa"
"dukan al'amura da kuma halin Allah" ko "abubuwa game da Allah da ya nuna cewa shi Allah ne"
Wannan na nufin sammai da duniya da kuma dukan abin da ke cikin su.
AT: "saboda abubuwan da Allah ya halita" ko "domin mutane sun gan abubuwan da Allah ya halita"
"wannan mutanen ba su da hujjan cewa ba su sani ba"
AT: "suna tunanin munanan abubuwa"
A nan "duhu" kalma ce da ke a misalin rashin fahimtar mutane. Anan "zuciya" wata kalma ce da ke misalin tunanin mutum ko kuwa rayukan. AT: "sun zama marasa fahimtar abin da Allah ke so su sani ba"
"A sa'ada suke da'awa wai su masu hikima, sun zama wawaye"
mutanen bisa ga Romawa 1:18
"sauya gaskiyar cewa Allah maɗaukaki ne kuma ba zai mutu ba" ko "ba su gaskata cewa Allah shine maɗaukaki kuma ba zai taɓa mutuwa ba"
"maimakon haka sun zabi su bauta wa gumaka da ke kamanin"
"waɗansu mutane da za su mutu"
"kamar tsuntsaye, dabbobi ko abubuwa masu rarrafe"
"domin abin nan da na fada gaskiya ce"
"Allah ya bar su ga shiga cikin"
"yan' adam" bisa ga Romawa 1:18
A nan "sha'awace-sha'awacen zukatansu" adaɗin magana ne da ke a madaɗin mugayen abubuwan da suke so su aikata. AT: "halin kazanta ita ce babbar muradin su "
Wannan daddin magana ce da ke nufin aikata lalata. AT: "sun aikata lalata da kuma abubuwa masu banƙyama"
A nan "halita" na nufin abubuwan da Allah ya halita. AT: "Sun yi sujada ga abubuwan da Allah ya halita"
"maimakon"
"saboda bautar gumaka da kuma zunubin lalata"
"sha'anin sha'awace-sha'awace ta kunya"
"domin matansu"
AT: "yin jima'i ta hanyar da ba shirin Allah ba"
A nan "ma'amalarsu ta halal" adaɗin magana ce da ke nuna ɗangantakan mace da miji cikin juma'i. AT: "maza dayawa sun bar ma'amalarsu ta halal da mata"
"kasance da sha'awar waɗansu maza"
"sun yi abubuwan da ya kamata su ji kunya, amma basu ji kunya ba"
"maza, kuma Allah ya hukunta su da ãdalci bisa ga kuskuren da suka yi"
halin da ba daidai ba, ba kuskure game da gaskiya
"Ba su yi tunanin cewa yana da muhimmanci su san Allah ba"
Waɗannan kalmomi na nufin "yan' adam" cikin [Romawa 1:18]
A nan "battacen hankalinsu" na ma'anan zuciya mai tunanin abubuwa ta haram. AT: "Allah ya bar zuciyar su da ke cike da halin banza da kuma haramtaccen tunani ta mulke su"
"abin kunya" ko "zunubi"
AT: "Su na da muradi mai karfi na" ko "Su na cike da muradin mai karfi na yin ayyuka na" (Dubi:
AT: "Kullayomi yanwanci suna kishin suaran mutane... yawanci muradin kullayomi ita ce kisan kai ... suna sa gardama da kuma hargitsi tsakanin mutane ...don rudin waɗansu ... suna magana ta rashin jituwar su game da waɗansu"
mai ɓatanci ya kan faɗa abin da ba daidai ba game da wani don ya ɓata masa suna.
"tunanin sabuwar hanyar yin mugunta ga wadansu"
"Suna sane da yadda Allah yake so su yi rayuwa"
A nan "aikata" na nufin cigaba da yi ko halin yin mugayen abubuwa. AT: "kuma dukan wanɗanda suka cigaba da aikata mugayen abubuwa"
"cancanci mutuwa"
"irin waɗannan mugayen abubuwa"
A nan kalman nan "aikata" na nufin cigaba da aikata mugayen abubuwa. AT: "waɗanda suka cigaba da aikata mugayen abubuwa"
1Saboda da haka baka da hujja, kai mutum, kai mai shara'antawa, domin kuwa abinda kake shara'antawa akan wasu kana kada kanka da kanka. Domin kuwa kai mai shar'antaawa kana aikata wadannan abubuwa. 2Amma mun san cewa shari'ar Allah ta gaskiya ce sa'adda zata fado wa masu aikata wadannan irin abubuwa.3Amma ka lura da wannan, ya kai mutum, mai shara'anta masu aikata wadannan ababuwa. Duk da shike kaima kana aikatawa. Kana jin zaka kubucewa hukuncin Allah? 4Ko kana raina falalar alheransa da yake yi ta wajen jinkirin hukuncinsa, da hakurinsa? Baka san cewa alheransa musanman domin su kai ka ga tuba bane?5Amma saboda taurin kanka da zuciyarka marar tuba, kana tanadarwa kanka fushi, a ranar fushi, wato ranar bayyanuwar shari'ar adalci ta Allah. 6Zai baiwa kowanne mutum daidai sakamakon ayyukansa: 7Ga wadanda kuma suka nace da yin ayyukan alheri ba fasawa, sun samarwa kansu, yabo da daraja, da rai na har'abada.8Amma ga masu son kai, wadanda suka ki yin biyayya ga gaskiya, suka yiwa rashin adalci biyayya, fushi da hasala mai zafi zai afko masu. 9Allah kuma zai sauko da bala'i da bakin ciki ga dukkan rayukan da suka aikata mugunta, ga Yahudawa da fari, sannan kuma Hellinawa.10Amma yabo daraja da salama zasu kasance ga dukkan wadanda suka aikata ayukan alheri, ga Yahudawa da fari sannan Hellanawa. 11Domin kuwa Allah ba mai tara bane. 12Ga wadanda suka yi zunubi batare da shari'aba, zasu hallaka ba tare da shari'a ba, ga wadanda suka yi zunubi cikin shari'a kuma za'a hukunta su bisa ga shari'a.13Domin kuwa ba masu jin shari'ar ne masu adalci agaban Allah ba, amma masu aikatawa ne zasu samu barata. 14Gama al'umai da basu san shari'a ba, bisa ga dabi'a sun yi abinda ke na shari'a, sun kuma zame wa kansu shari'a, koda shike basu da shari'ar.15Dalilin haka kuwa sun nuna cewa ayukan da shari'a take bukata na nan a rubuce a zuciyarsu. lamirinsu kuma na yi masu shaida, tunanainsu kuma, ko dai yana kashe su, ko kuma yana karesu. 16hakanan kuma ga Allah. Wannan zai faru ranar da Allah zai shara'anta asiran boye na dukkan mutane, bisa ga bishara ta cikin Yesu Almasihu.17Da shike kana kiran kanka Bayahude, kana zaune akan shari'a, kana alfahari cikin Allah, 18ka san nufinsa, ka kuma san abubuwan da suka bambanta da hakan, ka kuma sami koyarwa cikin shari'ar. 19Da shike kana da gabagadi akan cewa kai jagora ne ga makafi, haske ga wadanda suke cikin duhu, 20mai horo ga marasa hikima, mai koyar da jarirai, kuma a cikin shari'ar kana da abin da ya shafi sani da kuma gaskiya.21ku da kuke koyar da wadansu, ba ku koyar da kanku? ku da kuke wa'azi kada ayi sata, ba ku yin sata? 22Ku da ke wa'azi kada ayi zina, ba ku yin zina? ku da ke hana bautar gumaka, ba ku yin sata a haikali?23ku masu murna da tinkaho cikin shari'ar, ba kwa wulakanta Allah cikin kurakuranku na rashin bin shari'a? 24"Domin kuwa an wulakanta sunan Allah cikin Al'umai sabili da ku," kamar yadda aka riga aka rubuta.25Lallai kuwa kaciya tana da riba a gare ku, idan kuka kiyaye doka, amma idan ku marasa bin doka ne kaciyarku ta zama rashin kaciya. 26domin kuwa idan mutum marar kaciya zai kiyaye dukkan bukatun doka, baza'a iya daukan rashin kaciyarsa a matsayin mai kaciya ba? 27Sannan idan mutum marar kaciya ta jini zai kiyaye dukkan dokoki, ba zai iya shara'anta ku masu kaciya ta shari'a ba? Haka kuma ya kasance ne domin kuna da shari'a a rubuce da kuma kaciya amma ba kwa bin doka!28Domin shi kuwa ba Bayahude bane a waje; ba kuwa mai kaciyar da aka tsaga fata ba. 29Amma Bayahude ne ta ciki, sanna kuma mai kaciyar zuciya da kuma ruhu ba wasika ba, irin wanna mutumin yabonsa ba daga wurin mutane yake zuwa ba, amma daga Allah.
Bulus ya tabbatar cewa dukan mutane masu zunubi ne, ya kuma tunashe su cewa dukan mutane mugaye ne.
Kalman nan "saboda haka" na nuna sabon bangaren wasikar. Ta kuma kawo ga karshen maganar bisa ga abin da Bulus ya faɗa cikin [Romawa 1:1-32]. AT: Dashike Allah zai hukunta waɗanda sun cigaba da yin zunubi, hakika ba zai bar zunubin ka ba"
Bulus yana rubutu anan kamar yana magana da bayahuden da ke muhawara da shi. Bulus yana yin wannan domin ya koyawa masu sauraronsa cewa Allah zai hukunta duk wanda ya cigaba da yin zunubi, ko Bayahude ko kuwa Ba'al'ummi.
A nan wakilan sunan nan "kai" mufuradi ne. (Dubi:
Bulus ya yi amfani da kalman nan "mutum" anan don ya sautawa wanda zai iya tunanin shara'anta sauran mutane kamar Allah. AT: "Kai ma ɗan adam ne amma kana shara'anta sauran mutane sa'annan kana cewa sun cancanci hukuncin Allah" Dubi:
"Amma kana shara'anta kanka domin kaima ka yi mugayen abubuwa kamar yadda suka yi"
A nan wakilin sunan nan "mu" na iya yiwuwa ya shafe krista da kuma Yahudawa waɗanda ba masubi ba.
Bulus yai maganar "shari'ar Allah" anan kamar rayayye ce kuma zata iya "faɗo" kan mutane. AT: "Allah zai shara'anta waɗannan mutanen da gaskiya da kuma adalci"
"mutane masu aikata mugayen abubuwan nan"
"don haka, ku lura da wannan" ko "Saboda haka, ku lura da wannan"
"yi tunani game da abin nan da zan faɗa maka"
Yi amfani da kalman nan ta ɗan adam "ko kai waye ne"
"Kai mai cewa wani ya cancanci hukuncin Allah amma kana yin mugayen abubuwa daidai da su"
Wannan furuci ta bayyana cikin sifar tambaya don a kara nanatawa. Ka na iya juya wannan tambaya a matsayin magana da ba tabbaci. AT: "Haƙika baza ka tsira da ga shari'ar Allah ba!"
Wannan furuci ta bayyana cikin sifar tambaya don a kara nanatawa. Ka na iya juya wannan tambaya a matsayin tabbataccen magana. AT: Kada ka yi kamar bata da muhimmanci cewa Allah nagari ne kuma yana hakurin jira na sawon loƙaci kafin ya hukunta mutane don adalcinsa zai sa su su tuba"
"duba falalar ... hakurin mara muhimmanci" ko "duba ... mara kyau"
Wannan furuci ta bayyana cikin sifar tambaya don a kara nanatawa. Ka na iya juya wannan tambaya a matsayin tabbataccen magana. AT: Lalle ne ka sani cewa Allah ya nuna maka cewa shi nagari ne don ka iya tuba!"
Bulus ya yi amfani da maganar don ya kwatanta mutum da ya ki yin biyayya ga Allah da wani abu mai karfi kamar dutse. Ya kuma yi amfani da kalman nan "zuciya" a maɗaɗin zuciyar mutum ko kuwa rai. AT: "Domin kun ƙi ku kasa kunne kun kuma ki tuba"
Wannan hanya biyu ce da za ka iya haɗa kamar "zuciya mara tuba" AT: "taurin zuciya"
Maganar nan "ajiya" na nufin misali da yakan nufin mutum na tara dukiyoyinsa ya na kuma sa su a wuri mai kyau. Bulus ya ce a maimakon dukiya, mutumin yana tara hukuncin Allah. kamar yadda suka daɗe cikin rashin tuba haka ma tsanancin hukuncin. AT: ka na sa hukuncin ka ta zama mafi muni"
Dukan wannan maganar nan na nufin ranan nan ɗaya. AT: "Sa'ada Allah ya nuna fushinsa ga kowa kuma yana sharanta dukan mutane da adalci"
"bada sakamako daidai ko hukunci"
"kowane mutum bisa ga abinda da mutumin ya yi"
wannan na nufin cewa sun yi aiki cikin hanyar da zai kai ga daidaitawa mai kyau daga Allah a ranar shari'a.
Suna so Allah ya yabe su ya kuma girmama su, kuma ba su so su mutu.
Wannan na nufin ruɓewa na jiki, ba hali ba.
"son kai" ko "damuwa da abin da ke sa su kadai farin ciki"
Waɗannan maganganun na nufin abu ɗaya. Na biyun ya ƙara zurfin farkon.
Kalmomin nan "fushi" da "hasala mai zafi" na nufin abu daya ne ya kuma nanata fushin Allah ne. AT: "Allah zai nuna mummunan fushinsa"
A nan kalman nan "fushi" karin magana ne da ke nufin hukuncin Allah mai tsanani ga mugayen mutane. (Dubi:
Kalmomin nan "tsanani" da "wahala" a takaice na nufin abu ɗaya ne anan kuma ta nanata yadda munin hukuncin Allah zai zama. AT: "hukunci mai ban tsoro za ta auku zuwa ga"
A nan Bulus yayi amfani da kalman nan "rai" a matsayin karin magana ne da ke nufin mutum. AT: " bisa kan kowane mutum"
"cigaba da aikata mugayen abubuwa"
"Allah zai sharanta mutanen Yahudawa da farko sa'annan waɗanda ba mutanen Yahudawa ba"
Ma'ana mai iya yiwuwa suna kamar haka 1) "farko bisa ga loƙaci" ko 2) "lailai haƙĩƙa"
"Amma Allah zai bada yabo, girma da salama"
"cigaba da aikata abin da ke nagari"
Ku na iya juya wannan cikin tabbataciyar sifar. AT: "Gama Allah yana yi wa dukan mutane daidai yadda ya kamata"
"Don waɗanda suka yi zunubi"
Bulus ya maimaita "rashin shari'a" don nanata cewa ko mutum bai san dokan Musa ba. In sun yi zunubi, Allah zai sharanta su. AT: "a rashin sanin shari'ar Musa haƙika duk da haka za su mutu a ruhaniya"
"duk waɗanɗa suka yi zunubi"
Allah zai sharanta masu zunubi bisa shar'arsa. AT: "kuma ku da kun san shari'a Musa, Allah zai sharantasu bisa ga ita shari'ar" (Dubi: and activepassive)
Aya 14 da 15 sun tura asalin maganar da Bulus ya ba wa masu karanta wasikarsa don ƙara sanar da su. In kuna da wata hanya da ke nuna tura magana ciki kamar wannan a harshenku, kuna iya amfani da ita anan.
A nan "shari'an" na nufin shari'an Musa. AT: "ba waɗanda suka ji shari'an Musa kawai ba"
"waɗanda Allah ya tube su a matsayin adalai"
"amma waɗanda ke biyayya da shari'ar Musa"
AT: "waɗanda Allah zai ƙarbe"
Maganar nan "shari'an wa kansu" karin magana ne da ke nufin mutanen nan suna biyayya ga shari'an Allah. AT: "suna da shari'an Allah cikin zukatansu"
A nan "shari'ar" na nufin shari'ar Musa. AT: "basu da shari'an da Allah ya ba wa Musa"
"Tawurin yin biyayya ga shari'ar ya nu"
A nan "zukata" karin magana da ke nu tunani ko kuwa cikin mutum. Maganan nan "a rubuce a zuciyarsu" karin magana ne ta sanin abu cikin zuciyar su. AT: "cewa Allah ya rubuta cikin zukatansu abin da shari'ar ke buƙata su yi" ko "cewa sun san abin da Allah yana so su bisa ga shari'ansa"
A nan "yin shaida" na nufin sanin da suka samu tawurin shari'ar da Allah ya rubuta a zukatansu. AT: "ta fada musu ko suna rashin biyayya ko kuwa biyayya ga shari'ar Allah"
Wannan ta karasa maganar Bulus daga [Romawa 2:13]. "Wannan zai faru ne a sa'anda Allah zai sharanta"
"tundashike kana kiran kanka Bayahudi"
Maganar nan "dogara akan shari'an" na misalin gaskatawar cewa baza su iya zama adalai ba tawurin biyayya ga shari'an. AT: "dangan kan shari'an Musa"
"da kuma sane da nufin Allah"
AT: "domin mutane sun koyar da kai abin da ke daidai bisa ga shari'an" ko "domin ka koya daga shari'an"
A nan "makafi" da "waɗanda suke tafiya cikin duhu" wakilcin mutane ne wadda ba su fahimcin shari'ar ba. AT: "cewa domin ka koyar da shari'ar, kai da kan ka kana kamar ja gora ne ga makafi, kai kuma kana kamar haske ne ga mutanen da sun ɓata cikin duhu"
"ka horad da waɗanda suka yi abin da ba daidai ba"
A nan Bulus ya kwatanta waɗanda basu san shari'an ba da kananan 'ya'ya. AT: "kuma ka koyar da waɗanda ba su san shari'an ba"
Sanin gaskiya dake cikin shari'ar na zuwa ne daga wurin Allah. AT: "domin ka tabbata cewa ka fahimci gaskiyar da Allah ya bayar cikin shari'an"
Bulus yana amfani da tambaya domin ya kwaɓe masu sauraronsa. AT: "Kana koyawa waɗansu, amma ba ka koyar da kanka!" ko "kana koyawa waɗansu amma ba ka aikata abin da kake koyarwa!"
Bulus yana amfani da tambaya domin ya kwaɓe masu sauraronsa. AT: "Kana cewa mutane kada su yi sata, amma kai kana sata!"
Bulus yana amfani da tambaya domin ya kwaɓe masu sauraronsa. AT: "Kana cewa mutane kada su yi zina, amma kai kana zina!"
Bulus yana amfani da tambaya domin ya kwaɓe masu sauraronsa. AT: "Kana cewa wai kana ƙyamar gumaka, amma kana sata a ɗakin gunki!"
Ma'ana mai iya yiwuwa suna kamar haka 1) "satan abubuwa daga ɗakin gunkin al'umma su kuma sayar don su sami riba" ko 2) "kada ku aika kuɗi dake na Allah zuwa haikalin da ke a Urushalima."
Bulus yana amfani da tambaya domin ya kwaɓe masu sauraronsa. AT: "ai mugunta ne in kana taƙama da shari'ar, sa'annan a lokaci guɗa kana rashin biyayya da ita, ta haka kuma kana kawo kunyatawa ga Allah!"
AT: "Al'ummai da yawa sun yi saɓon sunan Allah"
Kalman nan "suna" kalma ce da ke nufin Allah, ba sunan shi kawai ba.
Na faɗi wannan duka domin kaciya bata da riba a gareku"
"in baku yi biyayya ga dokokin da ke cikin shari'ar ba"
"kamar ba a yi muku kaciya ba"
"mutum da ba a iy masa kaciya ba"
"biyayya da abinda Allah ya umurta cikin shari'an"
Bulus ya yi tambayoyi biyu anan domin ya nana cewa ba kaciya ne ke daidaita mutum da Allah ba. Ba lailai a juya wannan cikin tambaya ba. AT: "Allah zai dube shi a matsayin wanda ya yi kaciya. Wanda ba ayi masa kaciya ta jiki ba zai sharanta ku ... shari'an."
Wannan na nufin al'adun Yahudawa, karmar kaciya, wanda mutane ke iya gani.
Wannan na nufn canji ta jikin mutum a sa'ada an yi masa kaciya.
Wannan na nufin jiki. AT: "jiki"
Waɗannan kalmomin suna da ma'ana kusan iri daya. ta farkon "shi bayahude ne wadda a ciki," ta bayyana ta biyun, "kaciyar ta zuci ne."
Wannan na nufin daraja da kuma muraɗin wannan mutum da Allah ya sake she yana da shi.
A nan "zuciya" na nufin cikin mutum.
A nan "wasika" na nufin Littafi Mai Tsarki. AT: "Tawurin aikin Ruhu Mai Tsarki, ba domin ku san Littafi Mai Tsarki ba"
Wannan na nufin cikin, ruhun mutum wanda "Ruhun Allah" ya canza shi"
1To ina fifikon da bayahude yake dashi? Kuma ina ribar kaciya? 2Akwai muhimmancinsu ta kowacce hanya. Tun farko dai, yahudawa ne aka dankawa wahayi daga Allah.3Idan wasu yahudawa basu bada gaskiya ba fa? Rashin bangaskiyarsu zai hana amincin Allah aiki? 4Bazai taba zama haka ba. Maimakon haka, bari Allah ya zama mai gaskiya, ko da kowanne mutum makaryaci ne. Kamar yadda aka rubuta, "Domin a nuna kai mai adalci cikin maganganunka, kuma kayi nasara a lokacin da aka kawo ka gaban shari'a."5Amma idan rashin adalcinmu ya nuna adalcin Allah, to me zamu ce? Allah ba marar adalci ba ne, wanda ke aiwatar da fushinsa, ko kuwa? Ina magana bisa ga tunanin mutuntaka. 6Bazai taba zama haka ba. Domin idan haka ne ta yaya Allah zai shar'anta duniya?7Amma idan gaskiyar Allah ta wurin karyata ta habaka yabonsa, To me yasa ake shar'anta ni a matsayin mai zunubi? 8To me zai hana ace kamar yadda ake fadin zancen karya a kanmu, wasu kuma sun dauka cewa mun fadi hakan, "Bari muyi mugunta, domin nagarta tazo?" Hukuncin su halal ne.9To me kenan? Zamu ba kanmu hujja ne? ko kadan. Domin mun riga munyi zargin yahudawa da hellinawa, da cewar dukkansu, suna karkashin zunubi. 10Kamar yadda aka rubuta, babu wani mai adalci, babu ko daya.11Babu wani mai fahimta. Babu wani mai neman Allah. 12Dukansu sun kauce hanya, dukansu gaba daya sun zama marasa amfani. Babu mai aikin nagarta, a'a, babu ko da guda daya.13Makogwaronsu a bude yake kamar kabari. Harsunansu na dauke da cuta. Dafin macizai na karkashin lebunansu. 14Bakunansu cike suke da la'ana da daci.15Sawayensu na saurin zuwa zubar da jini. 16Tafarkinsu wahala ce da lalacewa. 17Wadannan mutane basu san hanyar salama ba. 18Babu tsoron Allah a idanunsu."19To mun san dai duk abin da shari'a tace, shari'a na magana ne da wadanda ke karkashinta, domin a rufe kowanne baki, domin dukan duniya ta bada amsa a gaban Allah. 20Domin a gabansa babu wanda zai barata ta wurin ayukan shari'a. Domin ta wurin shari'a ne sanin zunubi yazo.21Amma yanzu ba tare da shari'a ba an bayyana sanin adalcin Allah, wanda shari'a da annabawa suke shaidawa. 22Wato, adalcin Allah ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu ga dukkan wadanda ke bada gaskiya. Domin babu bambanci:23Domin duk sun yi zunubi sun kuma kasa kaiwa ga darajar Allah, 24Da alherinsa an baratar da mu ta wurin fansar dake cikin Yesu Almasihu.25Amma Allah ya bayar da Yesu Almasihu wanda yake hadayar fansa ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya mika Almasihu a matsayin tabbacin hukuncinsa, sabo da kuma ketarewar zunubanmu na baya 26cikin hakurinsa. Duk wannan ya faru ne domin a bayyana adalcinsa cikin wannan zamani, domin ya tabbatar da kansa mai hukunci, kuma ya nuna shine mai baratar da kowa saboda bangaskiya cikin Yesu.27To ina fahariya? An fitar da ita. A kan wane dalilin? Don ayyuka? A'a, amma ta dalilin bangaskiya. 28Domin wannan muka kammala cewar ana baratar da mutum ta wurin bangaskiya ba tare da ayyukan shari'a ba.29Ko kuwa Allah Allahn yahudawa ne kadai? Shi ba Allahn al'ummai bane? I, na al'ummai ne kuma. 30Idan dai lallai Allah daya ne, zai baratar da mai kaciya ta wurin bangaskiya, da marar kaciya kuma ta wurin bangaskiya.31Mun kawar da shari'a kenan ta wurin bangaskiya? ba zai taba kasancewa haka ba. Maimako ma, muna inganta shari'a kenan.
Bulus ya shaida ribar da Yahudawa su na da shi ta dalilin shari'ar da Allah ya ba su.
Bulus ya mika ra'ayin da mutane za su iya samu bayan sun ji abin da ya rubuto a sura 2. Ya yi wannan ne domin ya faɗa musu a aya ta 2. AT: "Waɗansu na iya cewa, 'To menene ribar Bayahude? kuma menene amfanin kaciya?" ko "waɗansu na iya cewa, 'in gaskiya ce, to bayahude ba shi da wata riba, kuma babu wata amfani cikin yin kaciya."'
Bulus ya amsa batun da aka kawo a aya ta 1. Anan "akwai" na nufin zama ɗaya daga cikin mutanen Yahudawa. AT: "Amma akwai babbar riba a zaman Bayahude"
Ma'ana mai iya yiwuwa suna kamar haka 1) "Da farko dai bisa ga lokaci" ko 2) "Lailai Hakika" ko 3) "Mafi muhimmanci."
A nan "wahayi" na nufin maganar Allah da kuma alkawarensa. AT: "Allah ya bada waɗannan maganganun da ta kunshi alkawarinsa zuwa ga Yahudawa"
Bulus ya yi amfani da wannan tambayoyin domin ya sa mutane su yi tunani. AT: "Waɗansu Yahudawa ba su yi aminci ga Allah ba. To, sai mu ce, bisa ga wannan, cewa Allah ba zai cika alkawarinsa ba?"
Wannan maganar na bayyan cewa wannan ba zai faru ba. Yana iya yiwua kuna da wata hanya a harshen ku da za ku iya yin amfani da ita. "Wannan ba mai yiwuwa bane!" ko "haƙika ba haka ba!"
"maimakon haka sai mu ce, bari"
Allah zai zama mai gaskiya a koyaushe kuma zai cika alkawarensa. AT: "Allah a koyaushe yana aikata abin nan da ya alkawarta"
Kalmomin nan "kowane" da "maƙarya" don a kara nanata cewa Allah ne kadai mai gaskiya ga alkawarensa a koyaushe. AT: "in kowane mutum maƙaryaci ne"
AT: "Litattafai kansu sun yarda da abinda nake faɗi"
Waɗannan maganganun na da ma'ana kusan iri daya. AT: "Dole kowa ya amince cewa abinda da kun faɗa gaskiya ne, kuma za ku yi nasara a koyaushe in wani ya zargi ku"
Bulus ya yi amfani da wannan tambaya don ya nuna abin da waɗansu mutane suna jayayya a kai sa'annan kuma ya sa masu karatunsa su yi tunani game da abin da yake faɗi gaskiya ne ko ba gaskiya. AT: "Waɗansu sun ce tundashike rashin adalcin mu ta nuna adalcin Allah, to Allah ba mai adalci bane in ya hukuntamu"
A nan "fushi" na nufin hukunci. AT: "aiwatar da hukuncinsa a kan mu" ko "hukunta mu"
"abinda waɗansu mutane ke faɗa shine nake faɗi" ko "wannan shine abin da waɗansu mutane ke fada"
Bulus ya yi amfani da wannan tambayar don ya nuna cewa muhawarar da ke gãba da bisharar mara amfani ne, tundashike Yahudawa ma sun gaskanta cewa Allah zai shara'anta dukan mutane. AT: "Mun sani cewa Allah zai shara'anta duniya!"
"duniya" na nufin dukan mutane da ke rayuwa cikin duniya. AT: kowa dake cikin duniya"
A nan Bulus na tunanin cewa wani na iya cigaba da ƙin bisharar. Cewa abokin gãba na muhara saboda zunubinsa ta nuna adalcin Allah, don haka Allah kada ya maishe shi mai zunubi a ranar shari'a in, a misali, ya yi ƙarya.
Anan Bulus ya yi tambaya don ya nuna yadda ba'ar muhawarar abokan gãban da yake tunaninsu take. AT: "Ni ma zan iya cewa ... zo!"
"Waɗansu sun yi ƙarya cewa wannan shine abin da muna faɗa"
Zata zama daidai a sa'ada Allah ya hukunta waɗannan abokan gãban Bulus, don ƙarya game da abin da Bulus ya yi ta koyarwa.
Bulus ya yi waɗannan tambayoyin don nanata ainihin nufinsa. AT: "Mu Yahudawa kada mu yi tunanin zamu guje wa hukuncin Allah, wai don mu Yahudawa ne!"
Waɗannan kalmomin sun fi ƙarfin "a'a" kawai, amma bai kai ƙarfin "cikakken a'a!" ba
AT: "Kamar yadda annabawa suka rubuta cikin Litattafai"
Babu wani wanda ya fahimci abin da ke daidai AT: "Lailai, babu wani wanda ya fahimci abin da ke daidai"
A nan "biɗan Allah" na nufin samun ɗangantaka da Allah. AT: "Babu wani mai ƙoƙarin samun sahilin ɗangantaka mai kyau da Allah"
Wannan karin magana ne da ke nufin mutane basu so su yi tunani game da Allah. Suna so kauce masa. AT: "Dukan su sun juya baya ga Allah"
Tundashike babu wani wanda ke yin abu mai kyau, sun marasa amfani ne ga Allah. AT: "Kowa ya zama mara amfani ga Allah"
Kalman nan "su" na nufin "Yahudawa da kuma Helenawa" ta [Romawa 3:9]
Kalman nan "maƙogwaro" na nufin dukan abin da mutane suke cewa dake mara adalci da kuma ƙyama. Anan "buɗaɗɗen kabari" na nufin ɗoyin kalmomi marasa kyau na mutanen.
Kalman nan "harsuna" na nufin kalmomin karya da mutanen ke faɗa. AT: Mutane na faɗan karya"
A nan "dafin macizai" na a maɗaɗɗin babbar hastarin miyagun kalmomin da mutanen na faɗi. Kalman nan "leɓuna" na nufin kalmomin mutanen. AT: "Miyagun kalmominsu na cutar da mutane daidai kamar dafin maciji" )
A nan "bakuna" na a maɗaɗɗin miyagun kalmomin mutanen. Kalman nan "cike" na nufin sau da yawa mutanen na maganar la'ana da kuma magana mai daci. AT: "Sau da yawa sukan faɗi la'ana da kuma mugayen kalmomi"
Waɗannan kalmomin na nufin Yahudawa ne da kuma Helenawa cikin [Romawa 3:9]
A nan "Sawaye" na nufin mutanen da kansu. Kalman nan "jini" na nufin kashe mutane. AT: "Su na hanzarin yin lahani da kisan mutane"
A nan "lalacewa da wahala" na nufin lahanin da mutanen nan ke sa waɗansu su sha. AT: "ƙoƙarinsu shine su rushe waɗansu su kuma sa su su sha wahala"
"yadda za su yi zaman cikin salama da sauran mutane." "hanyar" ita hanya ce ko kuma tafarki.
A nan "tsoro" na nufin girmama Allah da kuma yarda a daraja shi. AT: "Kowa ya ki ya ba Allah darajar da ya cancanci shi"
Bulus ya yi maganar shari'ar kamar da rai kuma tana da muryarta. AT: "dukan abin da shari'ar ta ce mutane su yi don" ko "duk dokokin da Musa ya rubuta cikin shari'ar ne don"
"waɗanda lailai ne su yi biyayya ga shari'ar"
A nan "baki" na nufin kalmomin da mutane ke faɗi. AT: "domin babu wasu wanda za su iya ce wani abu ƙarɓaɓɓe don kare kanssu"
A nan "duniya" na nufin dukan mutanen da ke cikin duniya. AT: "cewa Allah ya iya ce da kowa dake cikin duniya mai laifi ne."
A nan "jiki" na nufin dukan 'yan adam.
Wannan na iya nufin 1) "Don Haka" ko 2) "Wannan domin"
"a sa'ada wani ya san shari'ar Allah, sai ya gane cewa ya yi zunubi"
kalman nan "yanzu" na nufin tun loƙacin da Yesu ya zo cikin duniya.
AT: "Allah ya bayyana hanyar daidaitawa tare da shi ba tare da yin biyayya ga shari'ar ba"
Kalman nan "shari'an da kuma annabawa" na nufin bangaren litattafan da Musa da kuma annabawa sun rubuta cikin litattafan Yahudawa. Bulus ya bayyana su anan kamar su mutane ne da ke shaida a kotu. AT: Abinda Musa da Annabawa sun rubuta ta tabbatar da wannan"
A nan "adalci" na nufin daidaitawa ga Allah. AT: "daidaitawa ga Allah na kai ga dogara ga Yesu Almasihu"
Bulus na nufin cewa Allah ya karɓi kowa ta hanya ɗaya. AT: "Babu wata bambanci tsakanin Yahudawa da Al'ummai"
A nan "darajar Allah" na nufin siffar Allah da kuma dabi'ar sa. AT: "sun ƙãsa zama kamar Allah"
Anan "baratar" na nufin daidaitawa da Allah. AT: "Allah ya yi musu kyautar daidaitasu da kansa, domin Almasihu Yesu ya yantar da su"
Wannan na nufin cewa an daidaita su ba tare da sun tãrã ko kuma sun cancanci a daidaita su ba. A kyauta Allah ya daidaita su. AT: "an daidaita su ga Allah ba tare da sun samu ita ba"
Wannan na nufin mutuwar Yesu hadaya ce domin zunubai. AT: "cikin mutuwarsa hadaya ce domin zunubai"
Ma'ana mai iya yiwuwa na kamar haka 1) ƙyale ko 2) yafewa.
"Ya yi wannan ne don ya nuna yadda Allah yana daidaita mutane da kansa"
"Ta haka ya nuna cewa shi mai hukunci ne da kuma mai ce da kowane mai bada gaskiya ga Yesu, mai adalci"
Bulus ya yi wannan tambaya don ya nuna cewa babu wata dalilin da mutane za su yi fahariya game da biyayyarsu ga shari'ar. AT: "Saboda haka babu wata hanyar cewa Allah ya yi mana alheri don mun yi biyayya ga shari'ar. An fid the fahariya"
Bulus ya yi tambaya ya kuma bada amsa tambayar don nanata cewa duk abin nan da ya faɗa haƙika gaskiya ne. Kuna iya juya wannan har da kalmomin da Bulus ke nufi. AT: "A kan wace dalili za mu fid da fahariya? shine mu fid da fahariay saboda kyawawan ayyuka? A'a, ko dai, mu fid da ita saboda bangaskiya"
A nan "bangaskiya" na nufin bada gaskiyar mutumin ga Allah. "mutum" anan na nufin kowane mutum. AT: "Allah na daidata kowane mutum mai gaskantawa ga Allah" ko "Sa'ada Allah ya daidaita mutum, ya yi wannan ne domin mutumin ya gaskanta ga Allah"
"ko bai yi ayyukan shari'ar ba"
Bulus ya yi wannan tambaya don ya nanatawa ne. AT: "Haƙika ku da ku ke Yahudawa kada ku yi tunanin cewa ku kadai ne Allah zai karɓe ku!"
Bulus ya yi wannan tambayar don nanata abin da yake ƙoƙorin faɗa. AT: "Zai karbi waɗanda ba Yahudawa ba, wato Al'ummai"
A nan "masu kaciya" na nufin Yahudawa, "marasa kaciya" kuwa na nufin waɗanda ba Yahudawa ba. AT: "Allah zai daidaita Yahudawa duk da waɗanda ba Yahudawa ba ga kansa ta wurin bangaskiyarsu cikin Almasihu"
Bulus ya yi tambayar da yana iya yiwuwa wani mai karatu yana da shi. AT: "wani na iya cewa za mu iya kawar da shari'ar don muna da bangaskiya."
"muna biyayya ga shari'ar"
Wannan na nufin Bulus, sauran masubi, da masu karatu.
1Me kenan zamu ce game da Ibrahim, kakanmu a jiki, me ya samu? 2Domin idan Ibrahim ya sami kubutarwa ta wurin ayuka, ai da ya sami dalilin fahariya, amma ba a gaban Allah ba. 3Kuma fa me nassi ke fadi? "Ibrahim ya bada gaskiya ga Allah, sai aka lisafta ta adalci gare shi."4Yanzu fa shi dake yin ayyuka, ladansa ba a lisafta shi alheri ba ne, amma abun da ke nasa. 5Amma kuma shi da bai da ayyuka kuma maimakon haka ya gaskanta ga wanda ke kubutar da masu zunubai, bangaskiyarsa an lisafta ta a misalin adalci.6Dauda ya yi furcin albarka bisa mutumin da Allah ya lisafta mai adalci da rashin ayyuka. 7Sai ya ce, "Masu albarka ne wadanda aka yafe laifofinsu, kuma wadanda zunubansu a rufe suke. 8Mai albarka ne mutumin da ko kadan Ubangiji ba zaya lisafta zunubin sa ba."9To albarkar da aka fadi ko a bisansu wadanda aka yi wa kaciya ne kadai, ko kuwa a bisan su ma marasa kaciya? Domin mun yi furcin, "Bangaskiyar Ibrahim an lisafta ta adalci ce agare shi." 10Yaya aka lisafta ta? Bayan Ibrahim ya yi kaciya, ko kuwa a rashin kaciya? Ba a cikin kaciya ba, amma a rashin kaciya.11Ibrahim ya amshi alamar kaciya. Wannan shi ne hatimin adalcin bangaskiyar da ya ke da ita tun cikin rashin kaciyarsa. Albarkacin wannan alama ce, ta sa shi ya zama uban dukkan wadanda suka badagaskiya, ko da shike ba su da kaciya. Wato ma'ana, adalci za a lisafta masu. 12Wannan kuma yana da ma'anar cewa Ibrahim ya zama uban kaciya ga wadanda suka fito ba domin masu kaciya kadai ba, amma kuma domin wadanda ke biyo matakin ubanmu Ibrahim. Kuma wannan itace bangaskiyar da ya ke da ita a rashin kaciya.13Domin ba ta wurin shari'a aka bada alkawarin nan da aka yi wa Ibrahim da zuriyarsa ba, wannan alkawarin da ya ce zasu gaji duniya. Maimako, a ta wurin adalcin bangaskiya ne. 14Domin idan su da ke na shari'a magada ne, bangaskiya bata da komai, kuma alkawarin an wofintar da shi kenan. 15Domin shari'a ta kan jawo fushi, amma ta wurin rashin shari'a, babu karya umarni.16Saboda wannan dalili haka ta faru ta wurin bangaskiya, domin ya zama bisa ga alheri. Kamar haka, alkawarin ya tabbata ga dukkan zuriya. Kuma wannan zuriya ba zata kunshi wadanda suke da sanin shari'a ba kadai, har ma da wadanda ke daga bangaskiyar Ibrahim. Saboda shi ne uban dukkan kowa, 17kamar yadda aka rubuta, "Na maishe ka uba ga kasashe masu yawa." Ibrahim na gaban aminin sa, wato, Allah, mai bada rai ga mattatu kuma ya kan kira abubuwan da basu da rai su kuma kasance.18Duk da halin da ke a bayyane, Ibrahim ya gaskata ga Allah kai tsaye game da abubuwan da ke nan gaba. Sai ya zama uba ga kasashe masu yawa, kamar yadda aka ambata, "... Haka zuriyarka zata kasance." 19Ba ya karaya a bangaskiya ba. Ibrahim ya yarda da cewa jikinsa ya rigaya ya tsufa (shekarun sa na misalin dari). Ya kuma yarda da cewa mahaifar Saratu bata iya bada 'ya'ya ba.20Amma domin alkawarin Allah, Ibrahim bai ji nauyin rashin bangaskiya ba. Maimakon haka, ya sami karfafawa a bangaskiyarsa sai ya daukaka Allah. 21Ya na da cikakkiyar gamsuwa cewa idan Allah ya yi alkawari, shi mai iya kammalawa ne. 22Haka nan ne kuma aka lisafta masa wannan a matsayin adalci.23To ba'a rubuta kawai damin amfaninsa kadai ba, da aka lisafta dominsa. 24A rubuce yake domin mu, domin wadanda za'a lisafta su, mu da muka bada gaskiya gare shi wanda ya tada Yesu Ubangijinmu daga matattu. 25Wannan shi ne wanda aka bashe shi domin zunubanmu kuma an tada shi saboda fasar mu.
Bulus ya tabbatar da cewa ko a zamanin dã an daidaita masubi da Allah ta wurin bangaskiya ba ta wurin shari'ar ba.
Bulus ya yi amfani da tambayan don ya kama hankalin masu karatunsa ya kuma fara magana game da wani abu sabo. AT: "Wannan shine abin da Ibrahim kakan kakaninmu na jiki ya samu"
Bulus ya yi amfani da wannan tambayar domin ya kara nanatawa. Ya yi maganar littafin kamar tana da rai kuma ta iya magana. AT: "Gama za mu iya karantawa cikin littafin"
AT: Allah ya dubi Ibrahim a matsayin mutum mai adalci"
AT: "babu wanda ke lisafta abin da mai daukan aiki ya biya shi a matsayin kyauta daga mai ɗaukan aiki"
AT: "amma abin yake bin mai ɗaukan sa aiki"
"ga Allah, wanda ke daidaita"
AT: "Allah ya dubi bangakiyar mutumin a misalin adalci" ko "Allah ya dubi adalcin mutumin saboda bangaskiyar sa"
Dauda kuwa ya rubuta game da albarkan Allah ga mutumin da Allah ya mai da shi adali ba tare da ayyuka ba"
An bayyan abu ɗaya ta hanyoyi uku dabam dabam. AT: "Ubangijin ya yafe waɗanda sun karye shari'ar ... waɗanda zunubansu Ubangiji ya rufe ... waɗanda zunubansu Ubangiji ba zai lisafta ba"
Wannan furucin ta bayyana cikin sifar tambaya don kara nanaci. AT: Shin, Allah ya albarkaci masu kaciya ne kawai, ko kuwa da waɗanda ma ba su yi kaciya ba?"
Wannan na nufin mutanen Yahudawa. AT: "Yahudawa"
Wannan na nufin mutane wanda ba Yahudawa ba. AT: "Al'ummai"
AT: "Allah ya dubi bangaskiya Ibrahim a matsayin adalci"
Bulus ya yi wannan tambayoyi don ya kara nanata maganarsa. AT: "Yaushe Allah ya dubi Ibrahim a matsayin mai adalci? Shin, kafin kaciyar sa ne, ko kuwa bayan kaciyar?"
Ta faru ne kafin a yi masa kaciya, ba bayan kaciyarsa ba"
A nan "adalcin bangaskiya" na nufin cewa Allah ya dubi shi a matsayi mai adalci. AT: "alama da za a iya ganin cewa Allah ya dubi shi a matsayin mai adalci saboda ya riga ya gaskanta ga Allah tun kafin a yi mada kaciya"
"ko ba a yi musu kaciya ba"
AT: "Wannan na nufin cewa Allah zai dube su a matsayin masu adalci"
A nan "kaciyan" na nufin masu gaskantawa da Allah na gaske, duk da Yahudawa da Al'ummai.
A nan "bin cikin matakin bangaskiyar" na nufin bin gurbin wani. AT: "wanda sun bi gurbin bangaskiyar ubanmu Ibrahim"
an yi magana game da mutanen da Allah ya yi masu alkawari sai ka ce za su gaji kaya da arziki daga wani daga cikin iyali.
Kalmomin nan "alkawaein ta zo" an fahimci su daga maganar fari ne. za ku iya juya wannan ta wurin kara waɗannan kalmomin da ke nufin abu kamar haka. AT: "amma alkawarin ta zo ne tawurin bangaskiya, wadda Allah ya dubi a matsayin adalcin"
A nan "rayuwa ta wurin shari'ar" na nufin biyayya ga shari'ar. AT: "idan waɗanda ke biyayya ga shari'ar ne za su gaji duniya"
"bangaskiya ba ta da daraja, kuma alkawarin bata da ma'ana"
Ana iya bayyana wannan in an cire sunan nan "karya umarnin." AT: "ba bu wanda ya isa ya ketare shari'ar" ko "ba shi yiwuwa a ketare shari'ar"
"don haka"
Kalman nan "shi" na nufin samun abin da Allah ya alkawarta. AT: "ta wurin bangaskiya ne muka sami alkawarin" ko "mun sami alkawarin ta wurin bangaskiya"
A nan "alkawarin zai zama bisa ga alheri" na wakilcin cewa Allah ya da da abin da ya alkawarta saboda alherinsa. AT: "domin abin da ya alkawarta ya zama kyauta" ko "don alkawarinsa ya zama saboda alherinsa"
AT: "dukkan zuriyar Ibrahim haƙika za su ƙarbi abin da Allah ya alkawarta zai bayar"
Wannan na nufin mutanen Yahudawan, wanda takalifin yin biyayya ga dokar Musa.
Wannan na nufin waɗanda suke da bangaskiya kamar Ibrahim kafin ya yi kaciya. AT: "waɗanda suka bada gaskiya kamar yadda Ibrahim ya yi"
A nan kalman nan "mu" na nufin Bulus da kuma dukkan Yahudawa da waɗanda ba Yahudawa ba da suka gaskanta da Almasihu. Ga jiki Ibrahim kakan mutanen Yahudawa ne, amma shi kuma uban waɗanda ke da bangaskiya ne cikin ruhaniya.
Ana iya bayyana inda aka rubuta. AT: "kamar yadda aka rubuta cikin nasin"
A nan kalman nan "ka" mufuradi ne kuma na nufin Ibrahim.
Anan "ga shi wanda ya dogara" na nufin Allah. AT: "Ibrahim na gaban Allah wanda ya dogara a gare shi, wato shi wanda ya ba da rai ga waɗanda suka mutu"
"daga ba komai ya halici kowane abu"
Wannan karin maganan na nufin cewa Ibrahim ya dogara ga Allah kodashike bai nuna masa cewa zai iya samu ɗa ba. AT: Kodashike ba zama mai yiwuwa a gare shi ya samu zuriya ba, amma ya gaskanta da Allah"
AT: "kamar yadda Allah ya ce wa Ibrahim"
Ana iya bayyana cikakken alkawarin da Allah ya ba wa Ibrahim. AT: "za ka kasance da zuriya da ba za ka iya kidaya ba"
AT: "Ya kasance da ƙarfi cikin bangaskiyar sa, kodashiƙe"
Ku na iya juya wannan cikin tabbatacciya sifa. AT: "cigaba da aiki cikin bangaskiya"
AT: "ya kasance da ƙarfi cikin bangaskiyarsa"
"Ibrahim ya tabbata"
"Allah zai iya yin"
AT: "Saboda haka Allah ya lisafta bangasikiya Ibrahim a matsayin adalci" ko "Saboda haka Allah ya dubi adalcin Ibrahim don Ibrahim ya bada gaskiya gare shi"
"yanzu" an yi amfani da ita anan don a haɗa daidaita Ibrahim da aka yi ta wurin bangasikiya da kuma daidaita masubi na yanzu ta wurin bangaskiya cikin mutuwa da tashin Almasihu.
"ga Ibrahim kaɗai"
AT: "da Allah ya lisafta masa adalci" ko "Allah ya dube shi a matsayin mai adalci"
Kalman nan "mu" na nufin Bulus tare da duk masubi cikin Almasihu.
AT: "don amfanin mu ne kuwa, domin Allah zai dube mu a matsayin masu adalci kuma inda mun bada gaskiya"
"Tashe ... daga mattattu" anan na nufin "sa wani ya rayu kuma." AT: "shi wanda ya sa Yesu Ubangijimu ya rayu kuma"
AT: wanda Allah ya bashe shi ga masu gãbã don zunubanmu da kuma wanda Allah ya rayar don ya daidaita mu da shi"
1Tun da shike mun sami barata, sabili da bangaskiya, mun sami salama tare da Allah ta wurin Yesu Almasihu. 2. Ta wurin sa kuma mun sami iso zuwa ga alheri inda muke tsayawa albarkacin bangaskiyarmu. Muna murna da gabagadin da Allah ya ba mu game da abin da zai faru, gabagadin da zamu dandana nan gaba cikin daukakar Allah.3Ba kuwa haka kadai ba, amma muna murna da shan wahalolinmu. Mun san cewa shan wuya na haifar da 4Jimiri, Jimiri kuma na kawo amincewa, amincewa na kawo gabagadi game da abin da zai zo nan gaba. 5Wannan gabagadi wato begen da muke da shi baya kunyatarwa, domin kuwa an kwarara mana kaunar Allah a cikin zuciyarmu ta wurin Ruhu Mai Tsarki, da aka ba mu.6Domin kuwa ko yayin da muke raunana, Almasihu ya mutu a lokacin da ke dai dai domin marasa ibada.7To ai kuwa yana da wuya kwarai wani mutum ya yarda ya mutu don mutumin kirki ma. Watakila, wani na iyayin kasada ya yarda ya mutu don nagarin mutum.8Amma Allah ya tabbatar mana da kaunarsa a gare mu, don kuwa tun muna masu zunubi, Almasihu ya mutu domin mu. 9Balle ma yanzu, da muka barata ta wurin jininsa, za mu sami tsira daga fushin Allah.10Domin kuwa, in tun muna makiya, aka sulhunta mu da Allah ta wurin mutuwar Dansa, balle ma, yanzu da muka sami sulhu, zamu sami tsira ta wurin ransa.11Bama haka kadai ba, amma muna murna a cikin Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu, wanda ta wurinsa ne muka sami wannan sulhu.12Saboda haka, kamar yadda ta wurin mutum daya zunubi ya shigo cikin duniya, ta haka mutuwa ta shigo ta dalilin zunubi. 13Domin kuwa tun kafin a bada shari'a, zunubi na nan a duniya, amma ba' a lissafin zunubi in da ba shari'a.14Duk da haka, mutuwa ta mallake tun daga Adamu har Musa, har ma wadanda basu yi zunubin keta umarni irin na Adamu ba, wanda yake misalin mai zuwan nan a gaba. 15Amma kyautar ba kamar keta umarnin take ba. Domin in sabo da laifin mutum dayan nan ne, da yawa suke mutuwa, haka ma alherin sa da baiwarsa ta wurin mutum dayan nan, Yesu Almasihu, sai baiwar ta wadata zuwa ga masu yawa.16Domin kyautar ba kamar sakamakon wannan da yayi zunubin bace. Ta haka din nan ne, hukuncin nan mai tsanani ya zo sabo da zunubin mutum dayan. Har yanzu dai, wannan baiwa ta yanci ta zo ne bayan laifuffuka masu yawa. 17Domin, idan sabo da laifin mutum dayan nan ne, mutuwa ta mallake, saboda dayan, haka ma wadanda suka karbi alheri mai yawa da kuma baiwar adalci ta wurin ran, Yesu Almasihu.18Don haka, kamar yadda zunubin dayan ya sa hukunci ya zo kan dukka, haka ma aikin adalci na dayan zai kawo barata da rai ga mutane masu yawa.19Kuma kamar yadda rashin biyayyar dayan ta sa mutane masu yawan gaske su zama masu zunubi, haka ma ta biyayyar dayan mutane da yawan gaske za su sami adalci.20Amma shari'a ta zo, inda ta sa zunubi ya habaka. Amma inda zunubi ya habaka, alheri ma ya habaka ribin ribi. 21Wannan ya faru ne, don kamar yadda zunubi yai mallaka zuwa mutuwa, haka kuma alheri ya mallaka zuwa adalci da rai na har abada ta wurin Yesu Almasihu Ubangijin mu.
Bulus ya fara faɗin abubuwa dabam dabam da zai faru sa'adda Allah ya daidai masubi da kansa.
"domin an daidaita mu"
Duk aukuwar "mu" da "na mu" na nufin dukkan masubi kuma ya kamata a sanya su.
"saboda Ubangijinmu Yesu Almasihu"
A nan "Ubangiji" na nufin cewa Yesu Allah ne.
A nan "albarkacin bangaskiyar" na nufin dogarar mu ga Yesu, wanda ta yaddar mana mu tsaya a gaban Allah. AT: "Domin mun dogara ga Yesu, Allah ya ba mu yancin zuwa gabansa"
Kalman nan "wannan" na nufin ra'ayin da aka bayyana [Roman 5:1-2]
duk aukuwar "mu" na nufin dukkan masubi kuma ya kamata a haɗa su.
Wannan tabbatacin cewa Allah zai cika dukkan alkawaransa ga waɗanda suka dogara ga Almasihu.
Bulus ya yi magana game da "gabagadi" sai ka ce ta na da rai. AT: "muna da gabagadin cewa za mu ƙarbi abubuwan da muna jira"
A nan "zukatan" na a maɗaɗɗin tunanin mutum, ji, ko cikin mutum. Maganan na "an kwarara mana ƙaunar Allah a cikin zukatan mu" nufin ƙaunar Allah ga mutanen sa. AT: "domin ya ƙaunace mu sasai" ko "domin Allah ya nuna mana yadda yake ƙaunar mu"
Kalman nan "mu" anan na nufin dukkan masubi kuma ya kamata a haɗa su.
"yana da wuya a samu wani da zai yarda ya mutu ko saboda mutum mai adalci.
"Amma za a iya samun wani wanda zai yarda ya mutu saboda mutum nagari"
Za ku iya juya wannan aikataun jimlar da ta shige ta wurin yin amfani da "nuna."
Duk aukuwar "mu" na nufin dukkan masubi haɗe.
A nan "daidaitawa" na nufin cewa Allah ya sa mu cikin ɗanganta mai kyauda kansa. AT: "me kenan Allah zai yi mana yanzu da ya daidaita mu da kansa saboda mutuwar Yesu a kan giciye"
Wannan na nufin mutuwar haɗaya da Yesu ya yi a kan giciya.
Wannan na nufin cewa ta wurin mutuwar haɗayar da Yesu ya yi a kan giciye, Allah ya yafe mana mana ya kuma cece mu daga hukuncin nan ta jahannama domin zunubanmu.
A nan "fushi" na nufin hukunci Allah a kan waɗanda suka yi masa zunubi. AT: "hukuncin Allah"
Duk aukuwar "mu" na nufin dukkan masubi haɗe.
"Ɗan Allah ... ran Ɗan Allah"
Mutuwar Ɗan Allah ta ba mu rai madawwamiyar yafe ta kuma sa mu mun zama abokai da Allah, wato ga waɗanda suka bada gaskiya ga Yesu. AT: "Allah ya bar mu mu sami ɗangantaka ma salama da shi saboda ɗansa ya mutu domin mu"
Wannan lakani ne mai muhimmanci ta Yesu Ɗan Allah.
AT: "yanzu kam Allah ya maishe mu abokan sa kuma"
Bulus ya bayyana zunubi kamar wani abu ne mai hatsari da ta shigo cikin duniya ta wurin aikin "mutum ɗayan nan" wato Adamu. Wannan zunubi kuwa ta zama kofa wadda mutuwa, wadda ke nuna hoton wani abu kuma mai hatsari, ta shigo duniya.
Wannan na nufin cewa mutane su na zunubi tun kafin Allah ya bada shari'ar. AT: "Mutanen suna zunubi tun kafin Allah ya ba wa Musa shari'ar"
Wannan na nufin cewa Allah bai lisafta wa mutane zunubansu ba kafin a ba da shari'ar. AT: Amma Allah bai rubuta zunubi gaba da shari'ar ba kafin ya bada shari'ar"
"Ko da shiƙe abin nan da na faɗa gaskiya ne, mutu" ko kuma "Babu rubutacciyar shari'a tun daga loƙacin Adamu zuwa loƙacin Musa, amma mutuwa." (Dubi: [Romans 5:13])
Bulus yana magana game da mutuwa sai ka ce sarki ne da ke mulki. AT: "mutane sun cigaba da mutuwa tun loƙacin Adamu har zuwa loƙacin Musa a matsayi sakamakon zunubansu"
"har ma mutanen da zububansu dabam ne da na Adamu sun cigaba da mutuwa"
Adamu misalin Alamsihu ne wanda ya bayyana a gaba. Shi kusan iri ɗaya ne da shi.
Anan "ɗaya" na nufin Adamu. AT: "Domin in ta wurin zunubin mutun ɗayan nan da yawa su mutu"
A nan "alheri" na nufin kyatar Allah da ke samamme ga kowa ta wurin Yesu Almasihu. AT: "har ma ta wurin mutumin nan Yesu Almasihu, wanda ya mutu domin dukkan mu, Allah ya ba mu kyauta rai madawwani, ƙodashiƙe ba mu cancance ta ba"
A nan "kyautar" na nufin cewa Allah a yalwace ya shafe zunubanmu. AT: "Kyautar ba kamar sakamakon zunubin Adamu ba ne"
A nan Bulus ya bada dalilai biyu da "kyautar ba kamar sakamakon zunubi Adamu bane." "hukuncin halaka" na nufin cewa mun cancanci hukuncin Allah saboda zunubanmu. AT: "Domin a wannan bangare, Allah ya ce dukkan mutane sun cancanci hukunci saboda zunubin mutum ɗayan nan, amma a wata bangare dabam kuwa"
Wannan na nufin yadda Allah ya daidaita mu da kansa ko da shike ba mu cancanci a daidata mu ba. AT: "irin kyautar Allah don ya daidaita mu tare da kansa"
"bayan zunuban mutane dayawa"
Wannan na nufin zunubin Adamu.
A nan Bulus ya yi magana game da "mutuwa" kamar sarki ne wanda ke mulki. "Mulkin" mutuwa ta kan sa kowa ya mutu. AT: "kowa ya mutu"
"ta wurin zunubin nan ɗaya da Adamu ya aikata" ko kuwa "saboda zunubin Adamu"
A nan "hukunci" na nufin hukuncin Allah. AT: "dukan mutane sun cancanci hukuncin Allah saboda zunubi"
hadayan Yesu Almasihu
A nan "kuɓuta" na nufin cewa Allah zai iya daidaita mutane zuwa gare shi. AT: "Allah ya daidaita dukan mutane wa kansa"
rashin biyayyar Adamu
AT: "mutane da yawa sun yi zunubi"
biyayyar Yesu
AT: Allah zai daidaita mutane dayawa wa kansa"
Anan Bulus ya yi magana game da shari'ar sai ka ce mutum. AT: "Allah ya ba wa Musa shari'ar"
"zunubi ta karu"
A nan "alheri" na nufin albarkun Allah da ba a cancanci ta ba. AT: "Allah ya cigaba a yin kirki gare su, a ta hanyar da bai cancance su ba"
A nan Bulus ya yi magana game da mutuwa sai ka ce sarki ne da ke mulki. AT: "kamar yadda zunubi ta jawo mutuwa"
Bulus ya yi magana game da "alheri" anan sai ka ce wani sarkin ne da ke mulki. AT: "alheri ta ba wa mutane rai madawwami ta wurin adalcin Yesu Alamasihu Ubangijin mu"
Bulus ya yi magana game da "alheri" anan sai ka ce sarkin ne da ke mulki. Kalman nan "adalci" na nufin ikon Allah don daidaita mutane wa kansa. AT: "ha kama Allah zai ba da kyatar sa a yalwace ga mutane don ya daidaita su wa kansa"
Bulus ya haɗa da kansa, masu karatunsa, da dukkan masubi.
1Me kuwa zamu ce yanzu? Sai mu ci gaba da yin zunubi domin Alheri ya yawaita? 2Ba zai taba faruwa ba. 'Yaya za'ace mu da muka mutu cikin zunubi mu ci gaba da rayuwa cikin sa? 3Ba ku san cewa duk wadanda aka yi masu baftisma cikin Almasihu Yesu an yi masu baftisma har ya zuwa mutuwarsa ne ba?4An kuwa binne mu tare da shi, ta wurin baftisma cikin mutuwarsa. Haka kuma ya kasance ne domin kamar yadda Almasihu ya tashi daga matattu cikin daukakar Uba. Sakamakon haka muma zamu yi tafiya cikin sabuwar rayuwa. 5Domin kuwa idan muna tare dashi cikin kamannin mutuwarsa zamu kuwa zauna tare dashi har ga kamannin tashinsa.6Mun kuma san cewa, an giciye wannan tsohon mutunmin nan namu tare dashi, domin a hallaka jikin zunubi. wanna kuwa ya kasance ne domin kada mu ci gaba da bautar zunubi. 7Duk kuma wanda ya mutu an ambace shi a matayin adali akan zunubi.8Amma idan muka mutu tare da Almasihu, mun bada gaskiya zamu yi rayuwa tare dashi. 9Muna da sanen cewa an tada Almasihu daga matattu, don haka kuwa ba matacce yake ba. Mutuwa kuma bata da iko a kansa.10Game da mutuwar da yayi ga zunubi yayi sau daya kuma domin dukka. Rayuwar da yake yi kuma yana yi wa Allah ne. 11Don haka ku ma sai ku dauki kanku a matsayin matattu ga zunubi amma rayayyu ga Allah cikin Almasihu Yesu.12Sabili da haka kada ku bar zunubi yayi mulki a cikin jikinku, har ku yi biyayya ga sha'awarsa. 13Kada ku mika gabobin jikinku ga zunubi a matsayin kayan aikin rashin adalci. Amma ku mika kanku ga Allah rayayyu daga mutuwa. Ku kuma mika gabobin jikinku ga Allah a matsayin kayan aiki na adalci. 14kada ku ba zunubi dama yayi mulki a kanku, domin ba karkashin doka kuke ba, amma karkashin alheri kuke.15To sai me? Sai mu yi zunubi wai don ba a karkashin doka muke ba amma alheri. ba zai taba faruwa ba. 16Ba ku san cewa duk ga wanda kuka mika kanku a matsayin bayi, a gareshi ku bayi ne ba? Wannan fa gaskiya ne, ko dai ku bayi ne ga zunubi wanda kaiwa ga mutuwa ko kuma bayi ga biyayya wanda ke kaiwa ga adalci.17Amma godiya ta tabbata ga Allah! domin da ku bayin zunubi ne, amma kun yi biyayya daga zuciyarku irin salon koyarwar da aka baku. 18An 'yantar daku daga bautar zunubi, an kuma maishe ku bayin adalci.19Ina magana da ku kamar mutum, domin kasawarku ta nama da jini. Kamar yadda kuka mika gabobin jikinku ga kazamta da miyagun ayyuka, haka ma yanzu ku mika gabobin jikinku a matsayin bayi na adalci. 20Domin a lokacin da kuke bayin zunubi, ku yantattu ne ga adalci. 21A wannan lokacin wanne amfani kuka samu na ayyukan da yanzu kuke jin kunyarsu? Domin kuwa sakamakon wadannan ayyuka shine mutuwa.22Amma yanzu da da aka yantar daku daga zunubi aka mai da ku bayin Allah, amfaninsa ku kuwa shine tsarkakewarku. Sakamakon kuwa shine rai na har abada. 23Don kuwa sakamakon zunubi mutuwa ne. Amma kyautar Allah itace rai madauwami cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu.
A karkashin alheri, Bulus ya faɗa wa waɗanda suka gaskanta da Yesu cewa su yi sabon rayuwa kamar su mattattu ne ga zunubi da kuma rayayyu ne ga Allah.
Bulus ya yi waɗannan tambayoyi nan don ya jawo hankalin masu karatunsa ne. AT: "To, me za mu ce game da duk wannan? Haƙika ba za mu cigaba da yin zunubi ba wai don Allherin Allah ya yawaita ba!
kalman nan "mu" na nufin Bulus, masu karatun sa da sauran mutane.
A nan "mutu cikn zunubi" na nufin cewa masubi Yesu su na kamar mattattun mutane ne wanda zunubi ba za ta iya shafe su ba. Bulus ya yi amfani da wannan tambayar don nanaci ne. AT: "Muna kamar mutanen da zunubi ba ta shafe su ba! Don haka ba za mu cigaba da zunubi ba!"
Bulus ya yi amfani da wannan tambaya don ya kara nanaci. AT: "Tuna fa, a sa'adda an yi mana baftisma don a nuna cewa muna da ɗangantaka da Almasihu, wannan kuma na nuna cewa mun mutu tare da Almasihu a kan giciye!"
Anan Bulus ya yi magana game da baftimar masubi sai ka ce mutuwa ne da kuma biso. AT: "A sa'adda aka yi mana baftisma, ya na nan kamar an binne mu ne cikin kabari tare da Almasihu"
A ta da wani daga matattu na nufin a sa wani ya sake rayuwa kuma. Wannan na kwatanta sabuwar rayuwar ruhaniya na masubi da dawowar Yesu da rai kuma cikin jiki. Sabuwar rayuwa ta ruhaniya na masubi na ba mutumin ikon yin biyayya ga Allah. AT: "kamar yadda Uban ya tashe shi da matattu bayan mutuwarsa, mu ma mun sami sabuwan rayuwa ta ruhaniya mu kuma yi biyayya ga Allah"
Daga cikin dukan waɗanda suka mutu. Wannan maganar ta bayyana dukan mutanen da suka mutu tare da karkashi duniya. A tashe mutum daga cikin su na magana ne game da sake rayuwa kuma.
Bulus ya kwatanta haɗa mu da aka yi da Almasihu da mutuwa. Waɗanda suna tare da Almasihu cikin mutuwar sa za su kuwa tashi tare da shi. AT: "mutu tare da shi...dawo da rai tare da shi"
"tsohon mutumin" na nufin mutumin kafin ya ba da gaskiya ga Yesu. Bulus ya bayyana tsohon mutumin nan na mu mai zunubi kamar mutuwa kan giciye tare da Yesu a sa'adda muka bada gaskiya ga Yesu. AT: "mutumin nan namu mai zunubi ya mutu kan giciye tare da Yesu"
Wannan na nufin mutumin nan na da, amma yanzu kam ba ya a raye.
Wannan na nufin gabadayan mai zunubi. AT: "halin mu na zunubi"
AT: "zai mutu"
AT: "kada zunubi ta mashe mu bawan ta" ko "kada mu zama bayi ga zunubi"
A nan "adali" na nufin ikon Allah ya daidaita mutane wa kansa. AT: "A sa'adda Allah ya daidaita mutum wa kansa. wannan mutumin zunubi ba ta shugabantan sa"
A nan "mutu" na nufin cewa zunubi ba ta shugabantan masubi.
A nan a tashe, na nufin a sa wani wanda ya mutu ya rayu kuma. AT: "mun sani da cewa tun da shiƙe Allah ya dawo da Almasihu da rai kuma bayan ya mutu"
A nan "mutuwa" an bayyanata kamar sarki ko mai mulki da ke da iko bisa mutane. AT: "ba Zai sake mututwa ba" Dubi:
Maganar "sau ɗaya domin dukka" na nufin a gama wani abu gabaɗaya.Ku na yi bayyan ma'anar wannan a juyin ku. AT: "Gama a sa'adda ya mutu, ya ƙarye ikon zunubi gabaɗaya"
"Saboda wannan dalili ku dauke"
"yi tunanin kanku kamar" ko kuwa "dubi kanku kamar"
Kamar yadda ba za a yi sa gawa dole ya yi wani abu ba, zunubi ba ta da ikon sa masubi su yi rashin biyayya ga Allah. AT: "sai ka ce kun mutu ga ikon zunubi"
mutu ga iƙon zunubi, amma rayayyu don girmama Allah"
"rayu don girmama Allah ta wurin iƙon da Almasihu Yesu ya ba ku"
Bulus ya yi magana game da zunubin da mutane ke yi sai ka ce zunubi maigida ko sarki ne da ke mulkin su. AT: "Kada ku bar sha'awace sha'awace ta zunubi ta yi mulkin ku"
Wannan magana na nufin gabobin jikunan mutum, wanda zai mutu. AT: "ku"
Bulus ya yi magana game da muguwar sha'awace sha'awacen mutum sai ka ce zunubi maigida ne da ke da muguwar sha'awace sha'awace
Hoton mai zunubi ne da ke miƙa "gabobin jikinsa" ga maigidansa ko sarki. "gabobin jiki" na nufin gabadiyar mutum. AT: "Kada ku miƙa kanku ga zunubi don yi abin da ba daidai ba"
A nan "rayayyu" na nufin sabon rai ta ruhaniyan masubi. AT: "Amma ku miƙa kanku ga Allah, domin ya ba ku sabon rayuwa ta ruhaniya" ko kuwa "Amma ku miƙa kanku ga Allah kamar waɗanda suka mutu amma yanzu su na raye"
A nan "gabobin jiki" na nufin gabaɗayan mutum. AT: "bari Allah ya yi amfani da ku don jin daɗin ran sa"
Bulus ya yi magana game da "zunubi" anan sai ka ce sarkin ne da ke mulki bisa mutane. AT: "Kada ku bar sha'awace sha'awace ta zunubi ta bi da ku ci abin da kuke yi" ko kuwa "Kada ku bar kanku ku yi mugayen abubuwan da kuke so ku yi"
Zama "ƙarƙashin shari'ar" na nufin miƙa kai ga matuƙa da rashin ƙarfin ta. Kuna iya bayyana ma'ana wannan a juyinku. AT: "Gama ba a ɗaure ku ga shari'ar Musa ba wanda ba ta iya ba ku iƙon barin zunubi ba"
Zama "ƙarkashin alheri" na nufin kyautar Allah ta ba ku iƙon barin yin zunubi. Kuna iya bayyana ma'anar wannan a juyin ku. AT: "amma kuna ɗaure bisa alherin Allah wanda ke ba ku iƙon barin zunubi"
Bulus yana amfani da tambaya don ya nanata cewa rayuwa ƙarƙashin alheri dalilin zunubi ba ne. AT: "Duk da haka, ba domin muna ɗaure ga alherin maimakon shari'ar Musa sai ya zama cewa an ce mu yi zunubi ba"
"Ba za mu taba so hakan ya faru ba" ko "Ina roƙon Allah ya taimake ni kada in aikata wannan! "Wannan magana na nuna muradi ta musamman cewa wannan bai faru ba. Yana iya yiwuwa ku na da magana makamancin haka a harshen ku da za ku iya amfani da ita anan. Dubi yadda ku ka juya wannan cikin [Romawa 3:31].
Bulus ya yi amfani da wannan tambayar da on ya kwaɓe du wanda zai iya tunanin cewa Allah ya ba da alherinsa ta zama dalilin yi zunibi. AT: "Ku sani cewa ku bayi ne ga maigidan da kun zaɓa ku yi wa biyayya!"
A nan, Bulus ya yi magana game da "zunubi" da kuma "biyayya" sai ka ce su iyayengiji ne da bayi za su yi masu biyayya. AT: "ko dai ku kamar bayi ne ga zunubi ... ko kuwa kamar bayi ne ga biyayya" ko kuwa "ko dai ku bayi ne ga zunubi ... ko ku bayi ne ga biyayya"
"wanda sakamakon ta mutuwa ... wanda sakamakon ta adalci ne"
"Amma na gode wa Allah!"
Bayin zunubi na nufin samu sha'awar mai ƙarfi ta yi zunubi da ka kasa hana kanka yin zunubi. Yana nan ne kamar zunubi ne ke mulkin mutumin. AT: "kuna kamar bayin zunubi ne" ko kuwa "zunubi ne ke mulkin ku"
A nan kalman nan "zuciya" na nufin muradi yin abu daga sahili ko kuwa muradi na gaskiya. AT: "Amma kun yi biyayya da gaske"
A nan "salo" na nufin wata hanyar rayuwa da ke kai ga adalci. Masubin sun canza tsohon hanyar rayuwa don ya yi daidai da wannan sabon hanyar rayuwar da shugabanen masubi sun ƙoya masu. AT: "ƙoyarwar da shugabanen masubi sun ba su"
AT: "Almasihu ya 'yantar da ku daga zunubi"
Bayin adalci na nufin samun sha'awa mai ƙarfi don yi abin da ke daidai. Wato sai kace adalci na mulkin mutumin. AT: "an maishe ku kamar bayin adalci" ko "adalci ne ke mulkin ku yanzu"
Bulus mai yiwuwa na tsamanin cewa masu karatunsa su na mãmãki, me ya sa Bulus na magana game da 'yanci da kuma zama bawa. Anan yana cewa ya na amfani da waɗannan ra'ayin daga rayuwar su ta kowace rana don ya taimake su su fahimci cewa zunubi ko adalci na mulkin mutane. AT: "Ina magana game da wannan cikin kalmomin mutane" ko "Ina amfani da misalin rayuwar kowace rana"
Sau da yawa Bulus ya yi amfani da kalma nan "jiki" kamar kishiyar "ruhu". AT: "domin ba ku fahimci gabaɗayan abubuwan ruhaniya ba"
A nan "gabobin jiki" na nufin gabaɗayan mutum. AT: "miƙa kan ku a matsayin bayi ga kowace abu da ke miyagu kuma ba ta faranta wa Allah rai"
A nan "gabobin jiki" na nufin gabadayan mutum. AT: "miƙa kanku a matsayin bayi ga abin da ke daidai a gaban Allah don ya keɓe ku ya kuma ba ku iƙon bauta masa"
A nan "yantattu ne ga adalci" na nufin ba abin da ya haɗa ku da adalci. Mutanen su rayuwa kamar ba abin da ya haɗa su da abin da ke daidai. AT: "Wato kamar dã ku 'yantattu ne ga adalci" ko "ku na yi kamar ba lallai ne ku yi abinda da ke daidai ba" ko
"amfani" na nufin "sakamako" ko "abin da ya fito." Bulus ya yi wannan tambayar don ya nanata cewa sakamakon zunubi ba abu mai kyau ba ne. AT: "Babu abu mai kyau da ta zo daga waɗannan abubuwan da ke sa ku kunya yanzu" ko "Ba ku sami kome ba ta wurin aikata waɗannan abubuwan nan da ke sa ku kunya yanzu"
AT: "Amma yanzu da ku 'yantattu ne daga zunubi kun kuma zama bayin Allah" ko "Amman yanzu da Allah ya 'yantar da ku daga zunubi ya kuma maishe ku bayinsa"
Zaman "'yantattu daga zunubi" na nufin ikon ta rashin yin zunubi. AT: "Amma yanzu da Allah ya ba ku iƙon rashin yin zunubi"
Zaman "mai da ku bayin" ga Allah na nufin iƙon bauta da kuma biyayya ga Allah. AT: "Allah ya ba ku iƙon bauta masa"
A nan "amfani" na nufin "sakamako" ko kuwa "amfani." AT: "amfaninsa kuwa ita ce tsarkakewarku" ko "amfaninsa kuwa shine ku yi rayuwar tsarki"
"Sakamakon duk wannan ita ce za ku yi rayuwa har abada tare da Allah"
Kalman nan "haki" na nufin ladan aikin da aka ba wa wabi don aikin su. "Gama in kun bautawa zunubi, za ku karɓi mutuwar ruhaniya a matsayin lada" ko "Gama in kun cigaba da yin zunubi, Allah zai hukunta ku da mutuwar ruhaniya"
"amma Allah ya bada rai madawwamin ga waɗanda ke na Almasihu Yesu Ubangijinmu"
1'Yan'uwa, ko baku sani ba (domin ina magana da wadanda suka san shari'a), cewar shari'a na mulkin mutum muddin ransa?2Domin ta wurin shari'a matar aure a daure take muddin mijinta nada rai, amma idan mijinta ya mutu, ta kubuta daga shari'ar aure. 3To don haka idan, mijinta na da rai, sai ta tafi ta zauna da wani mutumin, za'a kirata mazinaciya. Amma idan mijin ya mutu, "yantarciya ce daga shari'a, domin kada ta kasance mazinaciya idan ta auri wani mutum.4Domin wannan, 'yan'uwana, ku ma an sa kun mutu ga shari'a ta wurin jikin Almasihu, saboda a hada ku aure da wani, wato, ga wanda aka tashe shi daga matattu, domin mu haifawa Allah 'ya'ya. 5Domin sa'adda muke cikin jiki, ana motsa dabi'armu ta zunubi dake cikin jikunan mu ta wurin shari'a domin mu haifi 'ya'ya zuwa mutuwa.6Amma yanzu an kubutar damu daga shari'a, mun mutu daga abin da ya daure mu, domin mu yi bauta cikin sabuntuwar Ruhu, ba cikin tsohon rubutun shari'a ba.7To me zamu ce kenan? ita shari'ar kanta zunubi ce? ba zai taba faruwa ba. Duk da haka. Idan ba ta wurin shari'a ba, ba zan taba sanin zunubi ba, in ba ta wurin shari'a ba. Ba zan taba kyashin abin wani ba, har sai da shari'a tace, "Kada kayi kyashi." 8Amma zunubi, sai ya dauki zarafi ta wurin dokar, ya jawo dukkan sha'awa dake cikina. Domin in da babu shari'a, zunubi matacce ne.9Ada na rayu sau daya ba tare da shari'a ba, amma da dokar ta zo, sai zunubi ya farfado, ni kuma na mutu. 10Dokar wadda ta kamata ta kawo rai, sai na same ta matacciya.11Domin zunubin, ya dauki zarafi ta wurin dokar, ya rude ni, kuma ta wurin dokar ya kashe ni. 12Domin haka, shari'ar na da tsarki, dokar na da tsarki, adalci da kuma kyau.13To abu mai kyau ya zamar mani mutuwa kenan? ba zai taba zama haka ba. Amma zunubi, domin ya nuna shi zunubi ne ta wurin abin da ke mai kyau, sai ya kawo mutuwa a cikina. Wannan ya kasance haka ne domin ta wurin dokar, zunubi ya zama cikakken zunubi. 14Domin mun san shari'a mai Ruhaniya ce, amma ni ina cikin jiki. An sai da ni karkashin bautar zunubi.15Domin ni ma ban fahimci abin da nake aikatawa ba. Domin abin da nake so in aikata, ba shi nake aikatawa ba, kuma abin da bana so, shi nake aikatawa. 16Amma idan na aikata abin da bana so, na amince da shari'a kenan, cewar shari'a nada kyau.17Amma yanzu ba ni ke aikata abin ba, amma zunubi da ke zaune a cikina. 18Domin na san a cikina, wato cikin jikina, babu wani abu mai kyau. Domin marmarin aikata abu mai kyau na tare da ni, amma ba ni iya aikatawa.19Domin abu mai kyau da na ke so in aikata bana iyawa, amma muguntar da ba na so ita na ke aikatawa. 20To idan na yi abin da ba ni so in aikata, wato kenan ba ni bane ke aikatawa, amma zunubin da ke zaune a cikina. 21Don haka, sai na iske, akwai ka'ida a cikina dake son aikata abu mai kyau, amma kuma ainihin mugunta na tare dani.22Domin a cikina ina murna da shari'ar Allah. 23Amma ina ganin wasu ka'idoji daban a gabobin jikina, su na yaki da wannan sabuwar ka'idar da ke cikin tunanina, suna kuma sanya ni bauta ta wurin ka'idar zunubi wadda ke cikin gabobin jikina.24Ni wahalallen mutum ne! wa zai kubutar dani daga wannan jiki na mutuwa? 25Amma godiya ga Allah ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu! Domin haka ni kaina a wannan hannu bisa ga tunani na ina bautawa shari'ar Allah. Duk da haka, ta wani gefen ina bautawa ka'idar zunubi da ke tare da jikina.
Bulus ya bayyana yadda shari'ar ke mulkin waɗanda ke rayuwa ƙarƙashi shari'ar.
Bulus ya yi wannan tambayar do ya ƙara nanaci. AT: "haƙika kun sani cewa dole ne mutane su yi biyayya ga shari'ar in dai suna raye"
A nan wannan na nufin masubi, duk tare da maza da mata.
Bulus ya bada misalin wannan a [Romawa 7:2-3]
A nan "ɗaura take ga mijinta bisa ga shari'ar" na nufin an gama mace da mijinta bisa ga dokar aure. AT: "bisa ga shari'a, macen da ta yi aure an gama ta da mijinta"
Wannan na nufin macen da ta yi aure.
AT: "Allah zai dube ta a matsayin mazinaciya" ko "mutane za kira ta mazinaciya"
A nan yanciya daga shari'ar na nufin ba lallai a yi biyayya ga shari'ar ba. Cikin wannan yanayi macen ba ta bukatan yin biyayya ga shari'ar da ta ce mata ma'aurata ba za su iya auran wani mutum ba. AT: "ba ta bukata ta yi biyayya ga shari'ar"
Ɗangantakan wannnan ta kai mu baya zuwa [Romawa 7:1]
AT: "ku kuma kun mutu ga shari'ar a don ta wurin Almasihu kun mutu a kan giciye"
"Tashe" a nan na nufin "a sa wani ya sake rayuwa kuma." AT: "ga shi wanda aka sa shi ya sake rayuwa kuma" ko "ga shi wanda Allah ya tashe shi daga matattu" ko "ga shi wanda Allah ya sa shi ya sake rayu kuma"
A nan "'ya'ya" na nufin ayyukan da ke faranta wa Allah rai. AT: "mu iya yin abubuwan da zasu faranta wa Allah"
A nan "'ya'ya" na nufin "sakamakon ayyukan wani" ko "abin da ta fito ta dalilin ayyukan." AT: "wanda ke kai ga mutuwa cikin ruhu" ko "sakamoko wanda ita ce mutuwar mu ta ruhaniya"
AT: "Allah ya kubutar da mu daga shari'ar"
Wannan na nufin Bulus da kuma masubi.
Wannan na nufin shari'ar. AT: "ga shari'ar da ta ɗaure mu"
Wannan na nufin shari'ar Musa. AT: "shari'ar Musa:
Bulus na gabatar da sabon kan magana ne.
"I mana, wannan ba gaskiya bane!" Wannan magana na bada amsar tambayar da ke baya. Mai yiwuwa kuna da magana makamancin haka a harshen ku da za ku iya amfani da ita anan. Dubi yadda ku ka juya wannan cikin [Romawa 9: 14]
Bulus ya kwatanta zunubi da mutumin da ya iya ƙwaiƙoyo
"sha'awa ta ta yin zunubi"
Wannan kalman na tare da sha'awar samun abin da ke na wasu mutane da kuma sha'awa ta sha'anin jiki da ba daidai ba.
"inda babu shari'ar, babu karya dokan saboda haka babu zunubi"
Wannan na nufin 1) "na gane cewa ina zunubi" ko 2) "ina da sha'awa mai karfi ta yi zunubi"
Bulus ya yi magana game da umurnin Allah sai ka ce ta na kai ga mutuwa cikin jiki. AT: "Allah ya ba ni dokar don in rayu, amma a maimakon haka ta kashe ni"
Kamar yadda take cikin [Romawa 7:7-8], Bulus na bayyana zunub kama mutum wanda zai iya yin abubuwa uku: ɗauki zarafi, ruɗe, da kuma kisa. AT: "Domin ina so in yi zunubi, na ruɗe kai na ta wurin yin tunanin cewa zan iya yin zunubi in kuma yi biyayya ga doƙar a loƙaci ɗaya, amma Allah ya hukunta ni saboda rashin biyayya ta ga doƙar ta wurin raba sakani na da shi"
Bulus ya kwatanta zunubi da mutumin da ke ƙwaiƙoyo. Dubi yadda kun juya wannan cikin [Romawa 7:8]
Bulus ya yi magana game da kayes da mai zunubi sai ka ce ta na kai ga mutuwa ta jiki. AT: "ta raba ni da Allah"
cikakke, babu zunubi
Bulus na gabatar da sabon kan magana ne.
Bulus ya yi amfani da tambaya don kara nanaci ne.
Wannan na nufin shari'ar Allah.
"sa ni in mutu"
Bulus na duban zunub kamar ita mutum ne da zai iya yin wani abu.
"raba ni da Allah"
"domin na yi rashin biyayya ga doƙar"
"ban da tabbacin dalilin da ya sa ina yi wasu abubuwan da nake yi"
"domin abin da na yi"
Kalmomin nan "ba shi nake aikatawa ba" na nanata cewa Bulus ba ya yi abin da yake so yayi a kai a kai kamar yadda ya ke so ko kuwa cewa yana aikata abin da ba ya so ya aikata sau da yawa"
kalmomin nan "na aikata" da ke nufin cewa ya cika yin abin ba ya so ya yi, nanaci ne cewa Bulus na aikata abinda ba ya so ya aikata sua da yawa. AT: "abubuwan da na san cewa ba su da kyau su ne abubuwan da na ke aikatawa wani loƙaci"
"amma dai, in na aikata"
"na san cewa shari'ar Allah na da kyau"
Bulus ya bayyana zunubi kamar abu mai rai ne da ke da iƙon shi zuciyar sa.
A nan "jiki" na nufin hali mutuntaka na zunubi. AT: "halin zunubi na"
"abubuwa masu kyau" ko kuwa "ayyuka masu kyau"
"muguwar abubuwa" ko kuwa "muguwar ayyuka"
Bulus ya yi magana game da "zunubi" sai ka ce ta na da rai kuma ta rayuwa cikin sa.
Bulus ya yi magana game da "mutunta" anan sai ka ce ta na da rai ta na kuma rayuwa cikin sa.
Wannan ruhu mutumin da ya dogara ga Almasihu ne da aka farkar.
"Ina yi aikata abin da tsohon hali ya faɗa mini in yi ne kadai, ba ga sabon rayuwa ta hanyar da Ruhun ya nuna mini ba"
Wannan sabon halin ruhaniya ne da ke raye.
Wannan tsohon hali ne. yadda mutane suke a sa'adda aka haife su.
"hali na ta zunubi"
Bulus ya yi amfani da tambaya don ya bayyana babbar shauƙinsa. In harshen ku na da wata hanyan nuna babbar shauƙin ta wurin amfani da maganar da ke nuna motsin rai ko kuwa tambaya, to yi amfani da ita anan. AT: "Ina so wani ya kubutar da ni daga ikon abin da jiki na ke sha'awar ta!"
"cece ni"
Wannan na nufin jikin nan mai mutuwa ta duniya.
Wannan ita ce amsar tambayar da ke cikin 7:24.
Tunani da kuma jiki an yi amfani da su anan do a nuna yadda aka kwatanta bautar shari'ar Allah ko kuwa ƙa'idar zunubi. Da tunanin ko iyawa, wani zai iya zaɓan faranta da yi wa Allah biyayya da kuma jikin ko halin mutuntaka a bauta wa zunubi. AT: "Tunani na ta zaɓa ta faranta wa Allah rai, amma jiki na ta zaɓa ta yi biyayya ga zunubi"
1Saboda haka babu kayarwa yanzu ga wadanda ke cikin Almasihu Yesu. 2Domin ka'idar ruhun rai a cikin Almasihu Yesu ta maishe mu 'yanttatu daga ka'idar zunubi da mutuwa.3Saboda abin da shari'a bata iya aikatawa ba domin kasawa ta wurin jiki, Allah ya yi. Ya aiko da dansa a kamanin jiki mai zunubi domin ya zama hadaya domin zunubi, sai ya yi Allah wadai da zunubi a cikin jiki. 4Ya yi haka domin bukatar shari'a ta sami cika a cikinmu, mu da muke tafe ba ta gwargwadon jiki ba, amma ta gwargwadon ruhaniya. 5Wadanda ke rayuwa gwargwadon jiki sukan lura da al'amuran jiki, amma su da ke rayuwa a gwargwadon Ruhu sukan mai da hankali ga al'amuran Ruhu.6To kwallafa rai ga jiki mutuwa ce, amma kwallafa rai ga Ruhu rai ne da salama. 7Haka yake domin kwallafa rai ga jiki gaba yake da Allah, gama baya biyyaya ga shari'ar Allah, balle ma ya iya. 8Wadanda ke a jiki ba su iya faranta wa Allah zuciya.9Duk da haka, ba ku cikin jiki amma a cikin Ruhu, idan gaskiya ne, Ruhun Allah na rayuwa cikinku. Amma idan wani ba shi da Ruhun Almasihu, shi ba na sa bane. 10In Almasihu na cikinka, jikin ka fa matacce ne ga zunubi, amma ruhu na rayuwa bisa ga adalci.11Idan Ruhun wanda ya tada Yesu daga matattu na raye a cikinku, to shi wanda ya tada Almasihu da ga matattu za ya bada rai ga jikinku masu matuwa ta wurin Ruhunsa, da ke rayuwa a cikin ku.12To, 'yan' uwa, muna da hakki amma ba bisa jiki ba, da za mu yi rayuwa bisa ga dabi'ar jiki. 13Gama idan kun yi rayuwa gwargwadon jiki, za ku mutu kenan, amma idan ta wurin Ruhu ku ka kashe ayyukan jiki, za ku rayu.14Gama duk wadanda Ruhun Allah ke bishe su, su 'ya 'yan Allah ne. 15Gama ba ku karbi ruhun bauta da ke sa tsoro ba. Maimakon haka, kun karbi ruhun diyanci, ta wurinsa muke tadda murya muna kira, "Abba, Uba!"16kansa na bada shaida tare da namu ruhun cewa mu 'ya'yan Allah ne. 17Idan mu 'ya'ya ne, ai mu magada ne kenan, magadan Allah. Kuma mu magada ne tare da Almasihu, hakika idan mun sha wahala tare da shi za a kuma daukaka mu tare da shi.18Gama na yi la'akari cewa wahalonin zamanin nan ba su isa a kwatanta su da daukakar da za'a bayyana mana ba. 19Saboda yadda halitta ke marmarin bayyanuwar 'ya'yan Allah.20Gama an kaskantar da halitta ga banza, ba da nufin ta ba, amma na shi wanda ya kaskantar da ita. Ta na cikin tabbacin alkawarin. 21Cewa halitta kanta za ta kubuta daga bautar rubewa, kuma za a kawo ta zuwa ga 'yantarwa na yabon daukakar 'ya'yan Allah. 22Gama mun sani dukan halitta na nishi da zafin nakuda tare har ya zuwa yanzu.23Ba haka kadai ba, amma ko mu kanmu, da ke nunar farko na Ruhu--mu kanmu muna nishi acikin mu, muna jiran diyancinmu, wato ceton jikinmu kenan. 24Gama ta wanan hakikancewa aka cece mu. Amma dai abin da muke da tabbacin zai faru ba mu gan shi ba tukuna, domin wanene wa ke begen tabbatacce abin da yake gani? 25Amma idan muna da tabbacin abin da ba mu gani ba tukuna, to sai mu jjira shi da hakuri.26Hakanan, Ruhu kuma ke taimako a kasawarmu. Gama ba mu da san yadda zamu yi addu'a ba, amma Ruhu kansa na roko a madadinmu da nishe-nishen da ba'a iya ambatawa. 27Shi da ke bidar zuciya yana sane da tunanin Ruhu, domin yana roko a madadin masu badagaskiya ta wurin nufin Allah.28Mun san cewa ga wadanda ke kaunar Allah, yakan aikata dukan al'amura domin su zuwa ga alheri, ga duk wadanda aka kira bisa ga nufinsa. Dukan abubuwa sukan zama alheri. 29Saboda wadanda ya sani tuntuni su ne ya kardara su zama da kamanin dansa, domin ya zama dan fari a cikin 'yan'uwa masu yawa. 30Su da ya kaddara, ya kiraye su. Wadanda ya kira, su ya kubutar. Su da ya kubutar, sune kuma ya daukaka.31Me zamu ce game da wadannan al'amura? Idan Allah na tare da mu, wake gaba da mu? 32Shi da baya hana dansa ba, amma ya bada shi a madadinmu dukka, me zai hana shi bamu dukkan abubuwa a yalwace tare da shi?33Wa zaya kawo wata tuhuma ga zababbu na Allah? Allah ne ke "yantarwa. 34Wanene ke hukumtawa? Almasihu ne da ya mutu sabili da mu har ma fiye da haka, shi wanda kuma aka tasar. Yana mulki tare da Allah a wuri mai daukaka, shi ne kuma ya ke roko sabili da mu.35Wa za ya raba mu da kaunar Allah? Kunci, ko bacin rai, ko tsanani, ko yunwa, ko tsiraci, ko hadari, ko takobi? 36Kamar yadda aka rubuta, "Saboda kai ake kisanmu dukkan yini. An mai da mu kamar tumaki yanka."37A dukan al'amuran nan mun fi karfi a ce da mu masu nasara ta wurin shi da ke kaunar mu. 38Gama na tabata cewa ko mutuwa, ko rai, ko mala'iku, ko mulkoki, ko al'amuran yanzu, ko al'amura masu zuwa, ko iko, 39ko tsawo, ko zurfi, kai ko wace irin halitta, ba su isa su raba mu da kaunar Allah, da ke a cikin Almasihu Yesu Ubangijin mu ba.
Bulus ya bada amsa ga gwagwarmayar sa da zunubi da nagarta.
A nan "kayarwa" na nufin a hukunta mutane. AT: "Allah ba zai kayar ko hukunta waɗanda suke tare da Almasihu Yesu ba"
"saboda wannan dalili" ko kuwa "saboda abin nan da na faɗa maku yanzun nan gaskiya ne"
Wannan na nufin Ruhun Allah. AT: "Ruhun Allah cikin Almasihu Yesu"
'Yantuwa daga ka'idar zunubi da mutuwa na nufin cewa ka'idar zunubi da mutuwa ba da mulki. AT: "ya sa ka'idar zunubi da mutuwa ba su mulkin ku a yanzu kuma"
Ma'ana mai yiwuwa su ne cewa wannan na nufin 1) ka'idar da ke sa mutane su yi zunubi, zunubin su kuwa na sa su su mutu. AT: "ka'idar da take da zunubi da mutuwa" ko kuwa 2) ka'idar cewa mutane sun yi zunubi sun kuma mutu.
Shari'ar anan an bayyana ta kama mutum wanda bai iya karya ikon zunubi ba. AT: "Gama shari'ar bata da ikon hana mu yi zunubi saboda ikon zunubi tsakanin mu na da karfi sosai. Amma Allah ya hana mu yin zunubi"
"saboda halin zunubi na mutane"
Ɗan Allah har'abada ya biya bukatar fushin Allah mai tsarki gãbã da zunubi ta wurin bada jikinsa da rayuwarsa ta mutuntaka a matsayin madawwamiyar hadaya don zunubi.
Wannan lakani ne mai muhimmanci na Yesu, Ɗan Allah.
"wanda ke kama da kowane mutum mai zunubi"
"saboda ya iya mutuwa a matsayin hadaya don zunuban mu"
"Allah ya karye ikon zunubi ta wurin jikin Ɗansa"
AT: "mu iya cika abin da shari'ar ke buƙata"
Tafiya a tafarkin na nufin yadda mutane ke rayuwa. Jiki karin magana ne ta halin zunubin 'yan adam. AT: "mu da ba mu yin biyayya ga sha'awace sha'awacen zunubi ba"
"amma wanda ke biyayya ga Ruhu Mai Tsarki"
A nan Bulus ya yi magana game da "jiki" da kuma "ruhu" sai ka ce mutane ne da ke raye. AT: "yadda mutane masu zunubi suke tunani ... yadda mutane da ke kasa kunne ga tunanin Ruhu Mai Tsarki"
A nan wannan na nufin raba mutum da Allah.
Wannan na nufin mutanen da ke yin abin da halin zunubi ya gaya musu su yi.
aiki bisa ga haili ku na zunubi" Dubi yadda kun juya "jiki" cikin [Romawa 8:5]
"aiki bisa ga Ruhu Mai Tsarki"
Waɗanan duk na nufin Ruhu Mai Tsarki.
Wannan magana ba ta nufin cewa Bulus ya na shakka cewa wasun su suna da Ruhun Allah. Bulus ya na so su gane cewa Dukkan su suna da Ruhun Allah. AT: "tundashiƙe" ko kuwa "saboda"
Za a iya bayyana yadda Almasihu ke rayuwa cikin mutum. AT: "In Almasihu na rayuwa cikinku ta wurin Ruhu Mai Tsarki"
Ma'ana ma yiwuwa suna kamar haka 1) mutum ya mutu ga iƙon zunubi a ruhaniya ko kuwa 2) jikinsa wanda muke iya gani za ta mutu saboda zunubi.
Ma'an mai yiwuwa suna kamar haka 1) mutum na da rai cikin ruhun saboda Allah ya ba shi ikon aikata abin da ke daidai ko kuwa 2) Allah zai dawo da mutumin zuwa rai bayan ya mutu saboda Allah mai adalci ne, ya kuma ba wa masubi rai madawwami.
Bulus na tsammanin cewa Ruhun Mai Tsarki na raye cikin masu karantun sa. AT: "Tundashiƙe Ruhu ... na raye a cikin ku"
"Allah, wanda ya tada"
A nan "tada" na nufin sa wani wanda ya mutu ya rayu kuma. AT: "sa Yesu ya rayu kuma"
"jikun ta duniya" ko kuwa "jikin, wanda zai mutu wata rana"
"saboda abin nan da na faɗa maku gaskiya ne"
A nan wannan na nufin masubi maza da mata dukka.
Bulus yana magana game da biyayya sai ka ce biyan wata hakki ne. AT: "ya kamata mu yi biyayya"
Haka kuma Bulus ya yi magana game da biyayya sai ka ce biyan wata hakki ne. Za ku iya sa abin da kalman "hakki" ta nufi. AT: "amma mu ba masu biyan hakki ga jiki bane, kuma ba lallai ne mu yi biyayya ga sha'awace sha'awacen mu ta zunubi ba"
"domin in kun yi rayuwa don ku faranta wa sha'awace sha'awacen ku ta zunubi kawai"
"haƙikia za a raba ku da Allah"
Bulus ya yi magana game da "tsohon mutum" cewa an giciye ta da Almasihu kamar mutumin da ke da nawayan sha'awace sha'awacen sa ta zunubi. AT: "amma in ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki kun bar yin biyayya ga sha'awace sha'awacen ku ta zunubi"
AT: Gama duk mutanen da Ruhun Allah ke bishe su"
A nan na nufin dukkan masu bada gaskiya ga Yesu, sau da yawa ana juya shi "'ya'yan Allah."
"wanda ya samu mu ta da murya mu kira"
"Abba" "Uban" ne a harshen Aramiyanci
Bulus ya yi magana game da masubi sai ka ce za su gaji wata kaya da dukiya daga ɗaya daga cikin iyali. AT: "mu kuma wata rana za mu karbi abin da Allah ya alkawarta mana"
Bulus ya yi magana game da masubi sai ka ce za su gaji kaya da dukiya daga ɗaya daga cikin iyali. Allah zai ba mu abin nan da ya ba wa Almasihu. AT: "za mu kuma karɓi abin da Allah ya alkawarta mana kuma tare da Almasihu"
Allah zai ɗaukaka masubi a sa'adda ya ɗaukaka Almasihu. AT: "cewa Allah zai ɗaukaka mu tare da shi"
Wannan na nanata "na yi la'akari." ba ta nufin "saboda"
AT: "ba zan iya kwatanta wahalolin mu ta yanzu da"
AT: "Allah zai bayyana" ko kuwa "Allah zai sa a sani"
Bulus ya bayyana dukkan abin da Allah ya halita kamar mutum ne wanda ke marmarin jiran wani abu.
AT: "loƙacin da Allah zai bayyana 'ya'yan sa"
AT: "Gama Allah ya sa abin da ya halita ta zama da rashin iƙon cimma burinsa" (Dubi:
A nan Bulus ya bayyana "halita" kamar mutum wanda ke da muradi. AT: "ba wai domin abin da halitattun abubuwa ke so ba ne, amma domin abin da Allah ke so ne"
AT: "Domin Allah ya san da cewa zai cece halita"
A nan bautar ruɓewa na nufin haƙika zai ruɓe. AT: daga zama kamar bayi zuwa ga ruɓewa"
"'Yantarwa" anan na da bambanci da zama bawa zuwa ga ruɓewa. wannan na nufin cewa halita ba za ta ruɓe ba. AT: "cewa za ta samu ɗaukakar 'yanci daga ruɓewa kamar 'ya'yan Allah"
Halitan an kwatanta ta da macen da ke nakuda a sa'adda ta ke haihuwa. AT: Gama mun san cewa dukkan abubuwan da Allah ya halita na so ta sami yanci kuma suna nishin ta kamar macen da ke haihuwa"
Bulus ya kwatanta karbar Ruhu Mai Tsarki na masubi da nunan fari da kuma kayan lambu ta loƙacin da ke girma. Wannan na nanata cewa Ruhu Mai Tsarki farkon abin da Allah zai ba wa masubi ne. AT: "wanda suka sami farkon kyautar da Allah ya ba mu, wato, Ruhu Mai Tsarki"
A nan "dayancinmu" na nufin sa'adda muka zama cikakken 'yan iyalin Allah kamar 'ya'yan da aka karbe su. Kalman nan "ceto" ba nufin sa'ada Allah ya cece mu. AT: "jiran sa'adda za mu zama cikakkun 'yan iyalin Allah kuma ya cece jikunan mu daga ruɓewa da kuma mututwa"
AT: "Gama Allah ya cece mu saboda begen mu na cikin sa"
Bulus ya yi wannan tambaya don ya taimake masu sauraron sa su fahimci mecece "bege". AT: "Amma in muna jira da gabagadi, ai wannan na nufin cewa ba mu riga mun sami abin da muke so ba kenan. Babu wanda ke da gabagadi in har ya riga ya sami abin da yake so"
"nishe-nishe da ba za mu iya bayyana ta ba cikin kalmomin"
A nan "Shi" na nufin Allah. Anan "zuciya" na nufin tunanin mutum da kuma shauƙi. Maganar "bidar zuciya" na nufin jaraba tunanin da shauƙi. AT: "Allah, wanda ya san dukkan tunani da kuma yadda suke ji"
AT: "ga waɗanda Allah ya zaɓe su"
"waɗanda ya sani tun kafin ya halici duniya"
"ya kuma sa ta ta zama hanyar da ya kadara" ko kuwa "ya kuma shirya tun da wurin"
Allah ya shirya tun daga farko halita ya sa waɗanda suka bada gaskiya ga Yesu, Ɗan Allah su yi girma cikin mutanen wanda suna kamar Yesu. AT: "zai canza su su zama kamar Ɗansa"
domin Ɗansa ya zama ɗan fari"
A nan "'yan'uwa" na nufin masubi mata da maza dukka. AT: "a cikin 'yan'uwa maza da mata masu yawa wanda ke na iyalin Allah"
"Waɗanda Allah ya yi musu shiri tundawuri"
A nan "kubutar" na nanata cewa wannan lallai zai faru. AT: "waɗannan da ya daidaita su ga kansa" Dubi:
Kalman "ɗaukaka" na nanata cewa wannan lallai zai faru. AT: " waɗannan ne ya kuma ɗaukaka"
Bulus ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata ainihin nufin abin da ya faɗa a baya. AT: "Wannan ita ce abin da ya kamata mu sani daga duk wannan: tundashiƙe Allah na taimakon mu, babu wanda zai ci nasara a kanmu" Dubi:
Allah Uban ya aiko da Allah Ɗan, Yesu Almasihu zuwa giciyen a matsayin hadaya mai tsarki, mara matuka wanda ake bukata don biya bukatar Allah mara iyaka, halin sa na tsarki gaba da zunubin 'yan adam. Anan "Ɗa" lakani ne ma muhimanci na Yesu, Ɗan Allah.
"amma ya sa shi karkashin iƙon abokan gabansa"
Bulus ya yi amfani da tambaya fon ya nanaci. AT: "haƙika shi zai ba mua kome kyauta!"
"bamu dukkan abubuwa"
Bulus ya yi amfani da tambaya don nanaci. AT: "Babu wanda zai zarge mu a gaban Allah saboda shine wanda ke daidaita mu wa kansa"
Bulus ya yi amfani da tambayar don nanaci. Ba ya bukatar amsa. AT: "Babu wanda zai hukunta mu!"
A nan a ta da na nufin a sa wani wanda ya mutu ya rayu kuma. AT: "wanda kodashiƙe mafi muhimanci, Allah ya tashe shi faga matattu" ko kuwa "wanda kodashiƙe mafi muhimanci ya tashi da rai"
Zama a "hannun daman Allah" alama ce ta karbar daraja da iko daga wurin Allah. AT: "wanda ke wurin mai daraja tare da Allah"
Bulus ya yi wannan tambayar don ya koya cewa babu abin da ta isa ta raba mu da ƙaunar da Almasihu ke yi mana. AT: "babu wanda zai raba mu da ƙaunar ƙaunar da Almasihu ke yi mana!" ko kuwa "Babu abin da zai raba mu daga ƙaunar da Almasihu ke yi mana!"
Kalman nan "zai raba mu daga ƙaunar da Almasihu ke yi mana" an fahimci ta faga tambayar da ke a baya. AT: "shin Kunci, ko bacin rai, ko tsananin, ko yunwa, ko tsiraici, ko hatsari, ko takobi ne za ta raba mu da ƙaunar da Almasihu ke yi mana?"
Waɗannan kalmomin su na nufin abu ɗaya ne.
A nan "kai" na nufin Allah ne. AT: "domin ka"
A nan "mu" na nufin shi wanda ya rubuto wannan sashin Nassin ba mai sauraro wato Allah. Maganar nan "yini zubur" na nanata hatsarin da suke cikin ne. Bulus ya yi amfani da wannan sashin Nassin don ya nuna cewa dukkan wanda ke na Allah, to sai ya sammaci loƙacin wahala. AT: "abokan gaban mu su koƙarin kashe mu"
A nan Bulus ya kwatanta dabbobi da waɗanda mutane ke kashe su saboda biyayyar su ga Allah. AT: "ran mu ba ta daraja kuma a gare su da tumakin da suke kashe"
"mu na da cikakken nasara"
Ku na iya bayyana irin ƙaunar da Yesu ya nuna mana. AT: "saboda Yesu, wanda ya ƙaunace mu sosai har ma yana shirye ya mutu domin mu"
"ba ni da shakka" ko kuwa "ina da gabagadi"
Wannan na iya nufin 1) aljanu ko 2) sarakuna da masu mulki.
Wannan na iya nufin1) ruhohi da ke da iƙo ko 2) mutane da ke da iƙo.
1Gaskiya ne nake gaskiya nake fada cikin Almasihu. Ba karya nake yi ba. Lamirina, na shaida a cikin Ruhu Mai Tsarki. 2cewa ina da matukar bakin-ciki da takaici marar karewa a zuciyata.3Dama ace, a la'anta ni, in rabu da Almasihu saboda 'yan'uwana, wato dangina da suke zuriyata bisa ga jiki. 4Sune Isra'ilawa, sun sami karbuwa, da daukaka, da baiwar shari'a, da yi wa Allah sujada, da alkawarai. 5Dukkan ubanni nasu ne daga cikinsu Almasihu ya fito bisa ga jiki- wanda shi ke Allah bisa kowa. Yabo ya tabbata a gare shi har abada. Amin.6Amma ba wai alkawarin Allah ya kasa ba ne, ba dukkan Isra'ilawa ne suke Isra'ilawa na gaskiya ba. 7Haka nan, ba dukkan zuriyar Ibrahim ne 'ya'yansa ba. Amma "ta wurin Ishiyaku ne za'a kira zuriyarka."8Yana nuna mana cewa ba 'ya'yan jiki su ne 'ya'yan Allah ba. Amma 'ya'yan alkawari ne ake kirga su, kuma aka kebe su. 9Wanna ce kalmar alkawari, "badi warhaka zan dawo, Saratu kuwa zata sami da."10Amma ba wannan kadai ba, bayan Rifkatu ta dauki ciki daga gun mijinta, ubammu Ishiyaku. 11Yaran nan kafin ma a haife su, balle ma a ce sun yi wani abu mai kyau ko laifi, saboda zaben da Allah yayi, bai danganta da abin da suka yi ba, ko don aiki ba, amma don shine mai kira-- 12kamar yadda Ya ce, mata, "babban zaya yiwa karamin bauta," haka nassi yace, 13"Kamar yadda aka rubuta: "Yakubu na ke kauna, amma Isuwa na ki shi."14To me zamu ce kenan? Allah ya yi rashin adalci kenan? Ko kadan. 15Gama ya ce wa Musa, "Ina nuna jinkai ga wanda zan yi wa jinkai, zan ji tausayi ga wanda zan tausaya masa." 16Saboda haka, ba don wanda ke da aniya ba ne, ko kuwa wanda yake kokari ba, amma saboda Allah mai nuna jinkai.17Gama nassi ya ce da Fir'auna, "Saboda wannan dalilin ne, na tada kai, don in nuna ikona mai karfi a kanka, don sunana ya yadu ga dukkan duniya." 18Ta haka Allah ya nuna jinkansa ga wanda ya so, ya taurarar da zuciyar wanda ya ga dama.19Za kuce mani, to don me, "Yake kama mu da llaifi? Wa ya taba yin jayayya da nufinsa?" 20In ma mun duba, kai mutum wanene kai da zaka ja da Allah? Ko abin da aka gina zai ce wa magininsa, "Don me yasa ka ginani haka?" 21Ko maginin ba shi da iko akan yimbu daya da zai gina tukunya mai daraja, wata kuma tukunyar don kowanne irin aiki?22In ace Allah, dake niyyar nuna fushinsa da ikonsa, ya sanu, sai ya jure da matukar hakuri mai yawa da tukwanen fushi da ya shirya don hallakarwar fa? 23To ko ma ya yi haka don ya nuna yalwar daukakarsa da take dauke da alheri, wanda ya shirya don daukakarsa tun farko? 24Zai yiwu ma ya yi haka ne domin mu, mu da ya kira, ba ma daga cikin Yahudawa kadai ba, amma har ma daga cikin al'ummai?25Kamar yadda ya ce a cikin littafin Yusha'u: "zan kira wadanda ba mutanena ba mutanena, da kuma kaunatattunta wadanda ba kaunatattu ba. 26Zai zama kuma a inda aka ce da su, "ku ba mutanena bane, za a kisa su 'ya'yan Allah mai rai."'27Ishaya ya yi kira game da Isra'ila, "in a ce yawan 'ya'yan Isra'ila zasu zama kamar yashi a bakin teku, ragowarsu ne kawai za su sami ceto. 28Ubangiji zai tabbatar da cikar kalmarsa a duniya, ba kuwa da dadewa ba. 29Yadda Ishaya ya rubuta ada, "In da ba Ubangiji mai runduna bai bar mana zuriya ba, da zamu zama kamar Saduma, da kuma an maida mu kamar Gomarata.30To me za mu ce kenan? Ko al'ummai, da ba sa neman adalci, sun samu adalci ta wurin bangaskiya. 31Amma Isra'ila, wadanda suka nemi adalcinsu ta wurin shari'a, ba su kai ga gaci ba.32To don me? don ba su neme shi da bangaskiya ba, amma ta ayyuka. Sun yi tuntube a kan dutse da zai sa laifi. 33Kamar yadda aka rubuta, "Ga, shi na ajiye dutse a kan Sihiyona dutsen tuntube mai sa laifi. Ga wanda ya bada gaskiya gare shi ba zai ji kunya ba."
Bulus ya bayyana muradin sa cewa al'uman Israila su sami ceto. Sa'annan ya nanata bambamcin hanyar da Allah ya shiryar musu don su gaskanta.
Waɗannan maganganu biyun na nufin abu ɗaya ne. Bulus ya yi amfani da su don ya nanata cewa ya na faɗin gaskiya ne.
"Ruhu Mai Tsarki na mulkin lamirina kuma ya tabbata cewa abin nan da na faɗa"
A nan "takaici mara karewa a zuciyata" karin magana ne da Bulus ya yi amfani da ita don matsanancin baƙin cikin sa. AT: "ina gaya mu cewa ina matukar juyayi sosai da kuma zurfin"
Waɗannan maganganu biyun na nufin abu ɗaya ne. Bulus ya yi amfani da su tare don ya nanata matukar shauƙinsa take.
AT: "Ni kaina san so Allah ya la'anta ni ya kuma raba ni da Almasihu har'abada in wannan zau taimake 'yan'uwana Isra'ilawa, mutane na, su gaskanta da Almasihu"
A nan wannan na nufin masubi maza da mata dukka.
"Su, Isra'ilawa ne kamar ni. Allah ya zaɓe su su zama zuriyar Yakub"
A nan Bulus ya yi amfani da "karɓuwa" don ya nuna cewa Isra'ilawa suna kamar 'ya'yan Allah ne. AT: "Su na da Allah a matsayin Ubansu"
A nan "Almasihu ya fito bisa ga jiki" na nufin cewa Almasihu ga jiki daga zuriyar ubannin Isra'ila ne. AT: "Almasihu ya zo cikin jiki a matsayin zuriya ne daga ubannin su"
"Amma Allah bai kãsã cika alkawarensa bane" ko "Allah ya cika alkawarensa"
Allah bai yi alkawarensa ga dukan zuriyar Isra'ila (ko Yakub) ga jiki ba, amma ga zuriyarsa ta ruhaniya, wato, waɗanda suka dogara ga Yesu.
"Haka kuma ba dukkansu bane 'ya'yan Allah kawai wai don du zuriyar Ibrahim ne ba"
A nan "'ya'yan ta jiki" na nufin zuriyar Ibrahim ta jiki. AT: "ba dukkan zuriyar Ibrahim"
Wannan na nufin mutane da ke zuriyar ne cikin ruhaniya, wato waɗanda ke da bangaskiya cikin Yesu.
Wannan na nufin mutane wanda za su gaji alkawaren da Allah ya ba wa Ibrahim.
"waɗannan ne kalmomin da Allah ya yi amfani da ita a sa'adda ya yi alkawarin"
Kuna iya juya wannan cikin sifar aiki don bayyana cewa Allah zai ba wa Saratu ɗa. AT: "Zan ba wa Saratu ɗa"
Yana iya yiwuwa a al'adan ku kuna bukatan sa 9:11 bayan 9:12 don saukin fahimta. AT: "ubanmu Ishaku, an ce mata, 'babban zai bauta wa karamin.' Yanzu kam ba a haifi 'ya'yan ba tukuna ... domin shi wanda ya kira. Kamar yadda aka"
Bulus ya dubi Ishaku a matasyin "ubanmu" domin Ishaku kakan kakan Bulus ne da kuma Yahudawa masubi da ke a Roma.
"ta sami ciki"
"kafin ma a haifi 'ya'yan kuma kafin ma su yi wani abu, ko mai kyau ko mummuna"
saboda abin da Allah ke so ta faru bisa ga nufinsa za ta faru"
"kafin ma a haifi 'ya'yan"
"ba wai domin wani abin da suka yi ba"
domin Allah
"Allah ya cewa Rifkatu, 'babban ɗan zai bauta wa karamin ɗan"
Kalman nan "ƙi" zuguiguici ne. Allah yana ƙaunar Yakub fiye da yadda yake ƙaunar Isuwa. Ba wai a zahiri ya ƙi Isuwa ba ne.
Bulus ya yi amfani da wannan tambayar don ya jawo hankalin masu karatunsa.
"Wannan ba mai yiwuwa bane!" ko "haƙika ba haka ba!" Wannan maganar ta yi matukar musu cewa wannan zai iya faru. yana iya yiwuwa kuna da wata magana makamanci haka a harshen ku da za ku iya amfani da ita anan.
Bulus yi yi magana game da maganar Allah tare da Musa sai ka ce yana faru ne a wannan zamanin. AT: "Gama Allah ya ce wa Musa"
"ba don abin mutane ke so ko kuwa saboda suna ƙoƙarin sosai"
Bulus ya yi magana game da mutum wanda ke yi abubuwa masu kyau don ya sami tagomashi daga wurin Allah sai ka ce mutum da ke tsere.
A nan yadda nasin yake sai ka ce Allah na magana ne da Fir'auna AT: "an rubuta a nasin cewa Allah ya ce"
Allah na nufin shi kansa ne.
mufuradi
"Tada" anan karin magana na "a sa abu ta zama abin da ita ce." AT: "Na mai da kai mutum mai iko"
AT: "don mutane su iya yin shelar sunana"
Wannan na nufin ko 1) Allah cikin dukkan Allahntakansa. AT: "wanene ni" ko 2) ga sunan sa. AT: "yadda na ke da girma"
"ko'ina da akwai mutane"
Allah ya sa wanda ya ga da ma, taurin kai.
Bulus na magana da masu zurfin tunani game da koyarwar sa kamar yana magana ne da mutum ɗaya. Mai yiwuwa kun bukaci yi amfani da jam'i anan.
Waɗannan tambayoyi da Bulus ya yi amfani da su na kara nanaci ne. Za ku iya juya wannan cikin magana ma nauyi.
kalmomin nan "shi" da "na shi" anan na nufin Allah.
Bulus ya yi amfani da iƙon da magini tukwane ke da shi don yin kowane abu da ya ke so daga yumbu don nuna makamacin abu game da iƙon mahalici ya yi kowane abu da ya ke so da halitarsa. Bulus ya yi waɗannan tamɓayoyin don ya nanata abin da ya ke ƙoƙarin faɗa.
Kalman nan "ka" anan na nufin Allah ne. Bulus ya yi amfani da wannan tamɓayar don ya kara nanatawa ne. Kuna iya juya wannan kamar magana na na kwarai. AT: "Ya Allah, bai kamata ka ginani haka ba!"
Bulus ya yi magana game da mutane sai ka ce su tukwane ne. AT: "mutanen da suka cancanci hukunci ... mutanen da suka cancanci jinƙan"
Bulus ya kwatanta ayyukan Allah na ban mamaki da babbar "dukiya." AT: "ɗaukakarsa, wanda ke da daraja na kwarai, kan"
A nan "ɗaukaka" na nufin rayuwa cikin sama tare da Allah. AT: wanda ya shirya tun da wurin don su yi rayuwa da shi"
Kalman nan "mu" anan na nufin Bulus da 'yan'uwa masubi.
A nan "kira" na nufin cewa Allah ya naɗa ko ya zaɓe mutane su zama 'ya'yansa, su zama bayinsa da kuma masu shelar saƙon cetonsa tawurin Yesu.
A nan "ya" na nufin Allah. "kamar yadda Allah ya faɗa kuma cikin litaffin cewa Yusha'u ya rubuto"
Yusha'u annabi ne a dã.
"Zan zaɓa wa mutane na waɗanda ba mutane ba"
A nan "ta" na nufin ma Yusha'u, Gomer, wanda ke a maɗaɗɗin al'umar Isra'ila. AT: "Zan zaɓe ta ita wanda ban ƙaunace ta ba ta zama wanda ina ƙauna"
Kalman nan "rayayye" mai yiwuwa na nufin gaskiyar cewa Allah shine Allah na gaskiya, kuma shi ba kamar allolin karya bane. AT: "'ya'yan Allah na gaskiye"
"kira"
A nan Bulus ya kwatanta yawan mutanen Isra'ila da yashin teku. AT: "yawan da ba za a iya kirgawa ba"
Bulus ya yi amfani da kalman nan "ceto" a fannin ruhaniya. Idan Allah ya cece mutum, wannan na nufin cewa ta wurin gaskantawa ne da mutuwar Yesu a kan giciye, Allah ya yafe masa ya kuma kubutar da shi daga hukuncin zunubansa. AT: "Allah zai cece"
Anan kalman nan "mu" da "mu" na nufin Ishaya da waɗanda ya yi magana game da su. (Dubi:
A nan "cikar kalmarsa" na nufin yadda ya shirya cewa zai hukunta mutane. AT: "Ubangiji zai hukunta mutane a duniya bisa ga yadda ya faɗa"
Allah ya hallaka mutanen Saduma da Gomarata saboda zunubansu. AT: "da an hallaka mu kamar mutanen Saduma da Gomarata" ko "da Allah ya hallaka mu dukka kamar yadda ya hallaka birnin Saduma da Gomarata"
Bulus ya yi amfani da wannan tambayar do ya kama hankalin masu karatunsa. AT: "Wannan ita ce abin da lallai ne mu faɗa"
"za mu ce cewa Al'ummai"
waɗanda ƙoƙarin faranta wa Allah rai"
A nan "ta wurin bangaskiya" na nufin dogarar wani ga Almasihu. Za ku iy bayyana wannan cikin juyin ku. AT: "domin Allah ya daidaita su da kansa a sa'adda sun dogara ga Almasihu"
Wannan na nufin cewa Isra'ilawa ba su iya faranta wa Allah rai ba ta wurin yi ƙoƙarin bin shari'ar. Kuna iya bayyana wannan cikin juyin ku. AT: "ba su iya faranta wa Allah rai ba ta wurin bin shari'ar don ba su iya bin ta ba"
Wannan magana ce da bai cika ba. Kuna iya bayyana kalmar a juyin ku. Bulus ya yi wannan tambayar don ya sami hankalin masu karatunsa. AT: "Me ya za ba su iya kai ga adalci ba?"
Wannan na nufin abubuwan da mutane ke ƙoƙarin yi don su farantawa Allah. AT: "ta wurin aikata abubuwan da zai farantawa Allah rai" ko kuwa "ta wurin bin shari'an"
Za ku iya nuna cewa Ishaya ya rubuto wannan. AT: kamar yadda annabi Ishaya ya rubuto"
A nan Sihiyona na misalin Isra'ila. AT: "a Isra'ila"
Duka maganganu biyun na nufin abu ɗaya ne, kuma na nufin Yesu da mutuwarsa a kan giciye. wato sai kace mutane sun yi tuntuɓe a kan dutse domin sun yi ƙyamar ta sa'adda sun dubi mutuwar Yesu a kan giciye.
Domin dutse na a maɗaɗɗin mutum, mai yiwuwa ku bukaci juya "gaskanta da shi."
1'Yan'uwana, muradin zuciyata da dukkan addu'oi na ga Allah dominsu shine don su sami ceton. 2Domin na shaida game da su cewa suna da kwazo game da Allah, amma ba a kan sani ba. 3Don, ba su da sani akan adalcin Allah, suna kokarin tabbatar da adalcin kansu. Ba su bada kan su ga adalcin Allah ba.4Gama Almasihu shi ne cikar doka zuwa ga adalci ga dukkan wadanda suka gaskata. 5Musa kam ya rubuta game da adalci da zai samu ta shari'a: "mutumin da ya aikata adalcin shari'a, zai rayu ta wurin wannan adalcin."6Amma adalcin da ya zo ta wurin bangaskiya yace, "Kada ku ce a zuciyarku, wa zai hau zuwa sama?"(don ya sauko da Almasihu kasa). 7Kada ku ce, "Wa zai gangara zuwa kasa?" (Wato wa zai fito da Almasihu daga cikin matattu).8Amma me yake cewa? "kalmar tana kusa da kai a cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka." Wato kalmar bangaskiya, wadda muke shaidawa. 9Don idan da bakinka, ka shaida Yesu Ubangiji ne, kuma ka gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tashe shi daga matattu, za ka sami ceto. 10Don da zuciya ne mutum yake gaskatawa zuwa ga adalci, da kuma baki ne yake shaida zuwa ga ceto.11Don nassi na cewa, "Duk wanda ya gaskata da shi ba zai ji kunya ba," 12Gama ba bambanci tsakanin Bayahude da Ba'al'ume. Gama dukkansu Ubangijinsu daya ne, Shi mayalwaci ne ga dukkan wanda ya kira shi. 13Duk wanda ya kira sunan Ubangiji zai sami ceto.14To ta yaya zasu kira ga wanda basu gaskata ba? Kuma ta yaya zasu gaskata ga wanda ba su taba jin labarinsa ba? 15Kuma ta yaya zasu ji in ba ayi masu wa'azi ba? Kuma ta yaya zasu yi wa'azin in ba an aike su ba? - Kamar yadda yake a rubuce, "Ina misalin kyau na kafafun wadanda ke shaida labarin farin ciki na abubuwa masu kyau!"16Amma ba dukkansu ne suka ji bishara ba. Gama Ishaya ya ce, "Ubangiji, wa ya gaskata da sakon? 17Saboda haka bangaskiya na zuwa ta wurin ji, jin kuwa daga maganar Almasihu.18Amma na ce, "ko basu ji ba ne? I, tabbas" muryarsu ta kai dukkan duniya, kuma kalmominsu sun kai har karshen duniya."19yau, na ce, "Ko Isra'ila basu sani ba ne?" Da farko Musa ya ce, "Zan sa kuyi fushi da kishi da abin da ba al'umma ba. Abin da nake nufi nan shine al'ummar da basu da fahinta, zan more su, in tayar maku da hankali."20Amma Ishaya da karfin hali ya ce, "Ga wadanda basu neme ni ba suka same ni. Na bayyana ga wadanda basu nemi ni ba. 21"Amma ga Isra'ila kam ya ce, "na mika hannu na ga masu rashin biyayya dukkan tsawon rana, domin su mutane ne masu taurin kai."
Bulus ya cigaba da bayyana muraɗinsa saboda Isra'ila su gaskanta amma ya nanata cewa duk waɗanda ke Yahudawa har ma da kowane mutum zai iya samun ceto ta wurin bada gaskiya ga Yesu ne.
Anan wannan na nufin Masubi, maza da mata dukka.
Anan "zuciya" na nufin shauƙin mutumin ko kuwa cikinsa. AT: "babbar muraɗi na"
"ita ce Allah zai cece Yahudawa"
"Na yi shela cikin gaskiya game da su"
A nan "adalcin" na nufin hanyar da Allah ke daidaita mutane wa kansa. Ku na iya bayyana wannan cikin juyin ku. AT: "Gama ba su san yadda Allah ke daidaita mutane da kansa ba"
"Ba su yarda da hanyar da Allah ke daidaita mutane wa kansa ba"
"Gama Almasihu ya cika bukatar shari'ar gabaɗaya"
A nan "bada gaskiya" na nufin "dogara." AT: "don ya daidaita dukkan wanda ya dogara a gare shi a gaban Allah"
Bulus ya yi magana game da "adalci" sai ka ce ta na raye kuma na iya tafiya. AT: "yadda shari'ar ke daidaita mutum a gaban Allah"
Don a daidaita ga Allah ta wurin shari'ar, lallai ne mutumin ya kiyaye shari'ar daidai, hakan kuwa ba mai yiwuwa bane. AT: "Mutumin da ya kiyaye shari'ar babu kuskure zai rayu saboda shari'ar zata daidaita shi a gaban Allah"
Kalmomin nan "zai rayu" na iya nufin 1) rai madawwami ko kuwa 2) rayuwar mutum da ke zumunta da Allah.
A nan "adalci" an bayyana ta kamar mutumin da ke iya magana. AT: "Amma Musa ya rubuta wannan game da yadda bangaskiya ke daidaita mutum da Allah"
Musa na magana da mutane sai ka ce yana magana da mutum ɗaya ne. Anan "zuciya" na nufin zuciyar mutum ko mutum na ciki. AT: "Kada ku ce wa kanku"
Musa ya yi amfani da wannan tambayar don ya koyawa masu sauraronsa. Umurninsa na baya cewa "Kada ku ce" na bukatan amsar da ke nuna cewa "babu". kuna iya juya wannan tambayar zuwa maganar da ba tambaya ba. AT: "Babu wanda zai iya hau zuwa sama"
"don su sa Almasihu ya sauko zuwa duniya"
Musa ya yi amfani tambaya don ya koyawa masu sauraron sa. Umurnin sa na baya "Kada ku ce" na bukatan amsar da ke nuna cewa "babu." Kuna iya juya wannan tambayar zuwa maganar da ba tambaya ba. AT: "Bubu wani mutum da zai iya gangarowa ya shiga wurin da ruhohin mutanen da suka mutu suke" (Dubi:
Daga cikin duk waɗanda suka mutu. Wannan furcin na bayyan dukkan mutanen da suka mutu cikin karkashin ƙasa. A fid da wani da cikin su na nufin sake rayuwa kuma.
Wannan kalman na magana game da mutuwa ta jiki.
Kalman nan "yake" na nufin "adalcin" ta [Romawa 10:6]. Anan Bulus ya bayyana "adalci" kamar mutum da zai iya magana. Bulus ya yi amfani da tambaya don ya nanata amsar da yake ƙoƙarin bayarwa. AT: " Amma wannan ita ce abin da Musa ya faɗa"
Bulus ya yi magana game da saƙon Allah sai ka ce mutum ne da ke iya tafiya. AT: "Ka riga ka ji saƙon"
Kalman "baki" na nufin abin da mutu ya faɗa. AT: "Ka san yadda za ka yi magana ... saƙon Allah"
Wannan kalmomin "cikin zuciyarka" na nufin abinda mutum ya yi tunaninsa ya kuma bada gaskiya. AT: "ka san abin ... saƙon Allah na nufi"
"Saƙon Allah na faɗa mana cewa lallai ne mu bada gaskiya a gare shi"
"In ka shaida cewa Yesu Ubangiji"
A nan "zuciya" na nufin hankali ko kuwa cikin mutum. AT: "gaskanta cikin tunani ka" ko kuwa "gaskanta da gaske"
"Tashe" anan na nufin "a sa wani ya sake rayuwa kuma." AT: "sa shi ya sake rayuwa kuma"
AT: "Allah zai cece ka"
A nan "zuciya" na walkilcin tunan ko son rai. AT: "Gama da Zuciya mutum ke dogara kuma a daidaita shi a gaban Allah, da baki kuma mutum ke shaidawa, Allah kuwa ya cece shi"
A nan "baki" na wakilcin iya magana ta mutum.
Bulus ya yi magana game da Nassin sai ka ce ya na a raye kuma yana da murya. Ku na iya bayyana a fili wanda ya rubuta Nassin da Bulus ya yi amfani da ita ana. AT: "Gama Ishaya ya rubuta a cikin Nassin"
Wannan daidai ne da : "Dukkan wanda ba gaskanta ba zai kunyata." An yi amfani da wannan don a nanaci ne. AT: "Allah zai daraja dukkan wanda ya gaskanta da shi"
Bulus na nufin cewa Allah zai yi da dukkan mutanen daidai. Ku na iya bayyana wannan a fili cikin juyin ku. AT: "daidai haka Allah ke yi da Yahudawa da waɗanda ba Yahudawa"
A nan "shi mayalwaci" na nufin cewa Allah zai zuɓo da yalwar albarkarsa. Ku na iya bayyana wannan a juyin ku. AT: "a yalwace ya albarkaci duk wanda ya dogara a gare shi"
Anan kalman "suna" na nufin Yesu. AT: "Ubangiji zai cece duk wanda ya dogara a gare shi"
Bulus ya yi wannan magana don ya nanata muhimancin kai bisharar Almasihu ga waɗanda ba su ji ba. Kalman nan "su" na nufin waɗanda ba na Allah ba tukuna. AT: "Waɗanda ba su gaskanta da Allah ba, ba za su iya kira bisan sa ba!"
Bulus ya yi amfani da wata tambayar kuma ta dalili iri ɗaya. AT: "Kuma ba za su iya gaskanta da shi ba in har ba su ji saƙonsa ba!" ko kuwa "Kuma ba za su iya gaskanta da shi ba in ba su ji saƙo game da shi ba!"
A nan wannan na nufin yardar cewa abin da wannan mutum ya faɗa gaskiya ne.
Bulus ya yi amfani da wata tambaya kuma don dalili iri ɗaya ne. AT: "Kuma ba za su iya jin saƙon ba in wani ba gaya musu ba!"
Bulus ya yi amfani da wata tambay kuma don dalili ɗaya. Kalman nan "su" na nufin waɗanda ke na Allah. AT: "Haka kuma ba za su iya faɗa wa wasu mutane saƙon ba sai dai in wani ya aike su!"
Bulus ya yi amfani da "ƙafafu" na wakilcin waɗanda ke matafiye kuma suna kawo saƙon ga waɗanda ba su ji ba. AT: "Ta na da kyau inda masu kai saƙo suka zo don su gaya mana saƙon Bishara"
A nan "su" na nufin Yahudawa. "Amma ba dukkan Yahudawa suka kasakunne ba"
Bulus ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa Ishaya ya yi annabci cikin Nassi cewa Yahudawa dayawa ba za su gaskanta da Yesu ba. Ku na iya juya wannan kamar wata magana. AT: "Ubangiji, yawancinsu ba su gaskanta da saƙon mu ba"
A nan "mu" na nufin Allah da Ishaya.
A nan "bangaskiya" na nufin "bada gaskiya ga Almasihu"
"ji tawurin kasakunne ga saƙo game da Almasihu"
Bulus ya yi amfani da tambaya don nanaci. kuna iya juya wannan kamar magana. AT: "Amma, na ce hakika Yahudawa sun ji saƙon game da Almasihu" (Dubi: and
Waɗannan maganganu biyun na nufin abu ɗaya ne, kuma Bulus ya yi amfani da su don nanaci. Kalman nan "tasu" na nufin rana, wata da tauraru. Anan an bayyana su kamar masu saƙo zuwa ga 'yan adam da ke gaya wa mutane game da ALlah. Wannan na nufin cewa kassancewar su na nuna iko da ɗaukakan Allah. Kuna iya bayyana cewa Bulus ya faɗi daga Nassi Anna. AT: "Kamar yadda take a Nassi, 'rana, wata da tauraru abib shaida ce iko da ɗaukakan Allah, kowa kuwa a duniya na ganinsu ya kuma san gaskiya game da Allah.'"
Bulus ya yi amfani da tambaya don nanaci. Kalman nan "Isra'ila" na nufin mutanen da ke kasar Isra'ila. AT: "Kuma ina gaya muku, mutanen Isra'ila ba su san saƙon"
Wannan na nufin cewa Musa ya rubuta abin da Allah ya ce. "Ni" na nufin Allah, "Ku" na nufin "Isra'ila. AT: "Da farko Musa ya ce cewa Allah zai sa ku fushi ... Allah zai motsa su"
ta wurin waɗanda kuke duban su a matsayin al'umma ta gaske" ko kuwa "tawurin mutane wanda ba zu ciki wata al'umma ba"
A nan "rashin fahimta" na nufin cewa mutane ba su dan Allah ba. AT: "Ta wurin mutanen da ba sun san ni ba ko umurni na"
"Zan sa ku fushi" ko kuwa "zan sa ku ku yi fushi"
Wannan na nufin banin Isra'ila.
A nan kalman nan "Ni," "-na" na nufin Allah.
Wannan na nufin Annabi Ishaya ya rubuta abin da Allah ya ce.
Annabawa sun cika magana game da abubuwan da ke gaba sai ka ce sun riga sun faru. Wannan na nanata cewa anabcin haƙika zai cika. AT: "Kodashiƙe al'ummai ba za su neme ni ba, za su same ni"
"Na maishe kaina sananne"
"Ya" na nufin Allah, wanda ke magana da Ishaya.
Wannan jimla an yi amfani da ita don a nanata cewa Allah ya cigaba da ƙoƙarin . "cigaba"
"Na yi ƙoƙarin marabtan ku, in kuma taimake ku, amma kun ƙi taimakon da na ba ku, kun cigaba da rashin biyayya"
1Sai na ce, Allah ya ki mutanensa ne? Ba zai taba yiwuwa ba. Domin ni ma ba-Isra'ile ne, na zuriyar Ibrahim, a kabilar Bilyaminu. 2Allah bai ki mutanen sa da ya ke da rigyasaninsu ba. Ko kun san abin da nassi ya ce game da Iliya, yadda ya kai karar Isra'ila a gaban Allah? 3Ya ce, "Ubangiji, sun kashe annabawanka, sun rushe alfarwanka kuma, Ni kadai ne na rage, ga shi suna neman su kashe ni."4Amma wacce amsa ce Allah ya ba shi? Ya ce, "Ina da mutane dubu bakwai da na kebe don kaina, da ba su taba rusuna wa Ba'al ba." 5Ban da haka ma, ban da haka ma a wannan lokacin akwai sauran zabe na alheri.6Amma tun da ta wurin alheri ne, ba ga ayyuka ba. In ba haka ba, alheri ba zai zama alheri ba kenan. 7Sai kuma me? Abin da Isra'ila ke nema, ba su samu ba, amma zababbun sun same shi, saura kuma sun taurare. 8Kamar yadda yake a rubuce, "Allah ya ba su ruhun rashin fahimta, ga idanu amma ba za su gani ba, ga kunnuwa amma ba za su ji ba, har zuwa wannan rana."9Dauda kuma ya ce, "bari teburinsu ya zama taru, da tarko, ya zama dutsen tuntube da abin ramako a gare su. 10Bari idanunsu ya duhunta domin kada su gani; bayansu kuma a duke kullum."11Na ce, "sun yi tuntube domin su fadi ne?" Kada abu kamar haka ya faru. A maimakon haka, juyawa baya da suka yi ya sa, ceto ya zo ga Al'ummai, domin ya sa su kishi. 12Idan yanzu juyawa baya da sun yi ya zama arziki ga duniya, rashin su kuma arziki ga Al'ummai, yaya kwatancin girmansa zai kasance in sun zo ga kammala?13Yanzu ina magana da ku ku da ke Al'ummai. Tunda yake ni ne manzo ga Al'ummai, ina kuma fahariya cikin hidimata. 14Yana yiwuwa in sa "yan'uwa na kishi, domin mu ceci wadansu su.15Idan kinsu ya kawo sulhuntawa ga duniya, Karbarsu kuma zata zama yaya? Zata zama rai ne daga mutuwa. 16'ya'yan farko sunan haka ma kakkabensu yake, Idan saiwar itace na nan, haka ma rassan za su zama.17Amma idan an karye wasu daga cikin rassan, idan ku rassan zaitun na ainihi ne, da aka samu daga cinkinsu, kuma idan kuna da gado tare da su, acikin saiwar itacen zaitun din. 18Kada ku yi fahariya a kan rassan. Amma idan kuka yi fahariya to ba ku bane masu karfafa saiwar amma saiwar ce ke karfafa ku.19Kana iya cewa, "An karye rassan domin a same ni a ciki." 20Wannan gaskiya ne! Saboda rashin bangaskiyarsu ne ya sa aka karye su daga rassan, amma ku tsaya da karfi acikin bangaskiyarku. Kada ku dauki kanku fiye da yadda ya kamata, amma ku ji tsoro. 21Domin idan Allah bai bar ainihin rassan ba, to ba zai bar ku ba.22Ku duba yadda irin ayyuka masu tsananni na Allah. Ta daya hannun kuma, tsanannin kan zoa kan Yahudawa wadanda suka fadi. Har 'ila yau jinkai Allah ya zo maku, idan kun cigaba cikin alherinsa baza a sare ku ba. Amma in kun ki za a sare ku.23Hakanan, idan ba su ci gaba cikin rashin bangaskiyarsu ba, za a maida su cikin itacen. Domin Allah zai iya sake maida su. 24Idan an yanke ka daga itacen zaitun da ke na jeji, har ya yiwu an hada ka cikin itacen zaitun na ainihi, yaya kuma wadannan Yahudawa wadanda sune ainihin rassan, da za'a maido cikin zaitun da ke na ainihi?25Yan'uwa, ba na so ku kasance cikin duhu a game da wannan asirin, domin kada ku zama da hikima cikin tunaninku. Wannan asirin shine cewa wannan taurarewa ta faru a Isra'ila, har sai da Al'ummai suka shigo ciki.26Ta haka dukan Isra'ila za su tsira, kamar yadda yake a rubuce: "Daga cikin Sihiyona mai Kubutarwa zai fito; Zai kawar da kazanta daga cikin Yakubu. 27Wannan zai zama alkawarina da su, sa'adda na kawar da zunubansu."28A wani bangaren kuma game da bishara, su makiya ne amamadinku, ta wani fannin kuma bisa ga zabin Allah su kaunattatu ne saboda ubanni. 29Domin baye-baye da kiran Allah basa canzawa.30Domin ku ma da ba ku yin biyayya ga Allah, amma yanzu kun sami jinkai saboda rashin biyayyarsu. 31Ta wannan hanyar dai, wadannan Yahudawan sun zama marasa biyayya. Sakamakon haka shine ta wurin jinkan da aka nuna maku, suma su samu jikai yanzu. 32Domin Allah ya rufe kowa ga rashin biyayya, domin ya nuna jinkai ga kowa.33Ina misalin zurfin wadata da kuma hikima da sani na Allah! Hukunce-hukuncensa sun fi gaban a bincika, hanyoyinsa kuma sun fi gaban ganewa! 34Don wanene ya san tunanin Ubangiji? Wanene kuma ya zama mai bashi shawara?35Ko kuma, wanene ya fara ba Allah wani abu, domin a biya shi?" 36Daga wurinsa ne, ta wurinsa ne kuma, a gare shi ne kuma dukan abu suka fito. A gare shi daukaka ta tabbata har abada. Amin.
Ƙodashiƙe Isra'ila a matsayin al'umma sun ƙi Allah, Allah yana so su fahimci ceto da ke samuwa tawurin alheri ba tare da ayyuka ba.
"Ni Bulus, na ce"
Bulus ya yi wannan tambaya don ya iya amsa tambayar wasu Yahudawa wanda sun yi fushi cewa Allah ya haɗa al'ummai cikin mutanensa, tundashiƙe mutanen Yahudawa sun taurara zuciyarsu.
"Wannan ba mai yiwuwa ba!" ko kuwa "Haƙika ba haka!" Wannan maganan ta ba da tabbacin cewa wannan ba zai faru ba. Mai yiwuwa kuna da magana makamancin haka a harshen ku da za ku iya amfani da ita ana. Dubi yadda kuka juya wannan cikin [Romawa 9: 14].
Wannan na nufin kabilar da ke daga Biliyaminu, ɗaya daga cikin kabilu 12 cikin wanda Allah ya raba mutanen Isra'ila.
"wanda ya sani tun kafin loƙaci"
AT: "Haƙika kun san Abin da Nassin ta faɗa game da sa'adda Iliya ya yi roƙo game da Isra'ila"
Bulus ya yi magana game da Nassin sai ka ce suna iya yin magana.
"su" na nufin mutanen Isra'ila.
"Ni" anan na nufin Iliya.
"son su kashe ni"
Bulus na amfani da wannan tambayar don ya kai masu karatunsa zuwa ga abin da zai faɗa a gaba. AT: "Ta yaya Allah ya amsa shi?"
"shi" na nufin Iliya.
"Mutane 7,000"
A nan wannan na nufin ƙaramin bangare mutane wanda Allah ya zaɓa su sami alherinsa.
Bulus ya cigaba da bayana yadda jinkan Allah ke aiki. AT: Amma dashike jinkan Allah na aiki tawurin alheri"
"Me za mu ce kenan?" Bulus ya yi wannan tambayar don ya kai masu karatunsa nufinsa na gaba. Ku na iya juya wannan cikin furuci. AT: "Wannan ita ce abin da ya kamata mu tuni"
Wannan na nufin cewa mutanen ba su fahimta a ruhaniyar su. Ba su iya ji ko su karɓi gaskiyar ruhaniya ba.
A nan wannan na nufin "samun halayen," kamar "ruhun hikima."
Ra'ayin cewa, a gani da idanu, ana duban ta daidai ne da samun fahimta.
Ra'ayin cewa, a ji da kunnuwa, a duban ta daidai ne da yin biyayya.
"Tebur" anan na wakilcin shagalgalin, kuma "raga" da "tarko" na wakilcin hukunci. AT: "Ya Allah ka maishe da shagalgalinsu kamar tarko da zata kama su"
"sanadin tuntuɓe" wani abu ne da ke sa mutum ya faɗi. Anan ta na wakilcin abu da ke gwada mutum do ya yi zunubi. AT: "wani abu da ke gwadasu su yi zunubi"
"wani abu ne da ke bada zarafin yin ramako a kansu"
A nan "tanƙwara bayansu" wata karin magana ne na sa bayi a dole su ɗauka kaya mai nauyi a bayansu. Wannan na nufin a sa mutum ya sha wahala. AT: "sa su shan wahala kamar mutane da ke ɗauke da kaya mai nauyi"
Bulus ya yi amfani da wannan tambaya do ya kara nanaci. AT: "Shin, Allah ya ƙi su har abada domin sun yi zunubi ne?
Dubi yadda kuka juya wannan jimla cikin [Romawa 10:19]
Waɗannan jimla biyun na nufin abu ɗaya ne a takaice. In lallai ne, to za ku iya haɗa su cikin juyin ku. AT: "Sa'adda Yahudawa suka faɗi a ruhaniya, sakamakon ita ce Allah ya albarkaci wanda ba Yahudawa ba a yalwace"
Domin Yahudawa sun ƙi Almasihu, Allah ya sa wa Al'ummai albarka a yalwace ta wurin ba su zarafi su karɓi Almasihu.
A nan "duniya" na nufin mutane wanda ke rayuwa cikin duniya musamman Al'ummai.
Dubi yadda kuka juya wannan jimla cikin [Romawa 10:19]
Wannan na nufin "'yan'uwana Yahudawa"
Allah zai cece waɗanda sun gaskanta. AT: "Maiyiwuwa wasu za su gaskanta, Allah kuma zai cece su"
"Domin in saboda Allah ya ƙi su, shi zai sulhunta duniya wa kansa"
"su" na nufin Yahudawa waɗanda ba su gaskanta ba.
Bulus ya yi wannan tambayar don ya nanata cewa sa'adda Allah ya karɓi Yahudawa, zai zama abin al'ajibi ne. AT: "yaya za ta zama a sa'adda Allah ya karɓe su? Zai zama kamar sun tashi ne daga cikin matattu!" ko kuwa "Sa'adda Allah ya karɓe su, zai zama kamar sun mutum sai suka dawo da rai kuma!"
Wannan kalman na magana ne game da dukkan mutane da suka mutu cikin ƙarƙashin kasa.
Bulus ya yi magana game da Ibrahim, Ishaku da Yakub, kakkanin Isra'ila, sai ka ce su ne tsaba na farƙo ko kuwa "'ya'yan fari" da za a girɓe. Yana kuma magana game da Isra'ila wanda ke zuriyar waɗanna mutane sai ka ce "kakkaben yake" da ke samuwa daga tsaba. AT: "Idan Ibrahim shine na farko da aka lisafta cikin abin da aka mika wa Allah, dukkan kakkaninmu wanda suke bi, su ma sai a lisafta a matsayin dukiyan Allah"
Bulus na magana a kan Ibrahim, Ishaku da Yakub, kakanin Isra'ila sai ka ce su saiwar itace ne, Isra'ila wanda su ne zuriyar waɗannan mutane, sai ka ce su "rassan" itacen ne."
Mutane a kullum su kan miƙa wa Allah amfanin gona na farko da suka girbe. Anan "'ya'yan fari" na a maɗaɗɗin mutane da suka fara gaskantawa da Almasihu.
"ku" da kuma jimla "rassan zaitun na jeji ne," na nufin Al'ummai wanda sun karɓi ceto tawurin Yesu.
A nan Bulus ya dubi Yahudawa wanda suka ƙi Yesu kamar "rassan da aka karye." AT: "Amma in wani ya karye wasu rassan"
A nan Bulus ya yi magana game da Al'umma masubi sai ka ce su "rassan da aka ɗaura aure mata aure ne." AT: "Allah ya haɗa ku da itacen da ke cikin sauran rassan"
A nan "saiwar itacen" na nufin alkawaren Allah
A nan "rassan" na nufin mutane Yahudawa. AT: "Kada ku ce kun fi Yahudawa mutanen da Allah ya ƙi"
Haka kuma Bulus na nufin Al'umma masubi sune rassan. Allah ya cece su kawai domin alkawaren da ya yi wa Yahudawa.
Anan "rassan" na nufin Yahudawa wanda sun ƙi Yesu kuma wanda Allah ya ƙi yanzu. AT: "Allah ya sare rassan nan"
Bulus na nufin Al'umma masubi wanda Allah ya karɓe su a wannan jimlar da ya yi amfani da ita. AT: "don ya ɗaura ni a kai"
"tasu" da "su" na nufin mutane Yahudawa wanda ba su gaskanta ba.
Bulus ya yi magana game da adalcin Al'umma masubi sai ka ce suna kafe ne kuma babu wanda zai iya tura su. AT: "Amma ku, ku na nan saboda bangaskiyarku"
A nan "asalin rassan" na nufin mutanen Yahudawa wanda sun ƙi Yesu. AT: "Dashiƙe Allah bai bar waɗannan Yahudawa wanda ba su bada gaskiya ba, wanda ke girma kamar asalin rassan itace da ke daga gigiyan, to ka sani, in ba ka bada gaskiya ba, ba zai bar ka ba"
Bulus yana tuna wa Al'umma masubi cewa ƙodashiƙe Allah ya yi masu alheri, ba zai yi jinkirin yi musu shari'a da kuma hukunci ba.
Za a iya bayana wanna in an cire "tsanani" da kuma "alheri." AT: "Allah ya tsananta wa Yahudawa da suka faɗi ... amma Allah ya yi muku alheri"
An yi magana game da yin abin da ba daidai ba sai ka ce faɗiwa ne. AT: "Yahudawan da suka yi abin da ba daidai ba" ko kuwa "Yahudawan da sun ƙi su dogara ga Almasihu"
Ana iya sake faɗin wannan in an cire sunan nan "alheri." AT: "in kun cigaba da yi abin da ke daidai don ya cigaba da yin muku alheri"
Bulus ya sake amfani da misalin reshe wanda Allah zai iya "sarewa" in ya na bukata ya sare. Anan "sarewa" na nufin ƙi ƙarbar wani. AT: "In ba haka ba Allah zai sare ku" ko kuwa "In ba haka ba Allah zai ƙi karɓa ku"
Fi'ilin maganar nan "ba su cigaba cikin rashin badagaskiya ba" korau biyu. AT: "Idan Yahudawan su fara gaskanta da Almasihu"
Bulus ya yi magana game da Yahudawa sai ka ce su rassa ne da za ɗaura musu aure da itace in sun fara gaskantawa da Yesu. AT: "Allah zai komar da su zuwa"
Wannan abin da ya cika faruwa ne wato reshe da bai bushe ba na itace an haɗa wani itacen don sabuwar rassan ta cigaba da girma a cikin wannan itace.
Bulus ya cigaba da magana game da Al'umma masubi da Yahudawa sai ka ce rassa itace ne. AT: "Gama idan Allah ya sare ku wanda ainihin itace zaitun na jeji ne, har ya yiwu ya haɗa ku cikin itacen zaitun mai kyau, yaya kuma Yahudawa wanda su ne ainihi rassan, za haɗa su cikin itace zaitun da ke na ainihi?"
Bulus ya yi magana game da Yahuda da kuma Al'ummai kamar su rassa ne. "ainihin rassan" na wakilcin Yahudawa, "rassa da aka ɗaura musu aure da itace" na wakilcin Al'umma masubi.
Dukkan bayyanuwa "ku" ko "su" na nufin Yahudawa ne.
Bulus anan ya yi amfani da korau biyu. AT: "Ina so ku sani"
A nan "'yan'uwa" na nufin Masubi mazaje da mataye dukka.
"Ni" na nufin Bulus.
"ku" da "naku" na nufin Al'umma masubi.
Bulus baya so Al'umma masubi su yi tunanin cewa suna da hikima fiye da Yahudawa masubi. AT: "don kada ku yi tunani kuna da hikima fiye da yadda kuke"
Bulus ya yi magana game da "taurarewa" ko kuwa taurin kai kamar taurin wani abu na jiki. wasu Yahudawa sun ƙi su karɓi ceto ta wurin Yesu. AT: "mutane daya na Isra'ila sun cigaba da taurarewa"
Kalman nan "har sai" anan na nufin cewa wasu Yahudawa za su gaskanta bayan Allah ya gama kawo al'umma zuwa cikin Ikkilisiya.
AT: "Ta haka Allah zai cece Isra'ila
AT: "Kamar yadda yake rubuce a nassin"
An yi amfani da "Sihiyona" anan ma dawamammen wurin ne na Allah. AT: "Daga wurin da Allah yake a tsakanin Yahudawa:
"shi wanda ya kowa mutanensa ga ceto"
Bulus ya yi magana game da rashin bin Allah sai ka ce wani abu ne da wani ke iya cirewa, mai yiwuwa kamar wani ya fid da tufa.
An yi amfani da "Yakub" a matsayin Isra'ila. AT: "daga mutanen Isra'ila"
Bulus ya yi magana game da zunubi sai ka ce wani abu ne da a iya kawar da shi. AT: "Zan kawar da nawayar zunubansu"
Ku na iya bayyana dalilin da ya sa Bulus ya ambata bisharan. AT: "Domin Yahudawa sun ƙi bisharan"
Ku na iya bayyana ko su maƙiyan wa ne su a fili, da yadda ta zama saboda Al'ummai ne. AT: "su maƙiyan Allah ne saboda da ku" ko kuwa "Allah mashe su maƙiya don ku ma ku ji bisharan"
Ku na iya bayyana dalilin da ya sa Bulus ya ambata zaɓe. AT: "domin Allah ya zaɓe Yahudawa" ko kuwa "saboda Allah ya zaɓe Yahudawa"
Ku na iya bayyana wanda ya ƙaunaci Yahudawa a fili da kuma dalilin da ya sa Bulus ya ambata kakkaninsu. AT: "Har wa yau, Allah yana ƙaunarsu saboda abin da ya yi alkawari zai yi wa kakkaninsu"
Bulus ya yi magana game da albarkar ruhaniya da ta jiki da Allah ya alkawarta zai ba wa mutane sai ka ce wata kyauta ne. Kiran Allah na nufin cewa Allah ya kira Yahudawa su zama mutanensa. AT: "Gama Allah bai canza zuciyarsa ba game da abin nan da ya yi alkawari zai ba su, game da yadda ya kira su su zama mutanen sa kuma"
"a dã ba ku yi biyayya ba"
A nan jinkai na nufin albarkar Allah da ba ta cancanci wani ba. AT: "Domin Yahudawa sun ƙi Yesu, ku kun sami albarkar da ba ta cancance ku ba"
Wannan na nufin Al'umma masubi, kuma jam'i ne
Allah ya yi da mutanen da suka yi masa rashin biyayya kamar 'yan kurkuku wanda ba su iya gudwa daga kurkuku ba. AT: "Allah ya mashe su 'yan kurkuku wato su waɗanda suka yi masa rashin biyayya. Yanzu kam ba za su iya bar yi wa Allah rashin biyayya ba"
A nan "hikima" da "sani" a takaice na nufin abu ɗaya ne. AT: "Dubi yadda amfanin hikimar Allah da saninsa take da ban mamaki!"
"Mu kam gabaɗaya mun kasa fahimta abubuwa da ya shirya, mun kuma kasa gane hanyoyinsa a gare mu"
Bulus ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata cewa babu wani wanda yake da hikima kamar Ubangiji. AT: "Babu wanda ya taɓa sani zuciyar Ubangiji, babu kuma wanda ya taɓa zama mashawarcinsa."
A nan "zuciya" na nufin sanin abubuwa ko kuwa yin tunani game da abubuwa. AT: "dukkan abin da Ubangiji ya sani" ko kuwa "abin da Ubangiji na tunani game da su"
Bulus ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata ainihin abin da yake so ya faɗa. AT: "babu wanda ya taɓa ba wa Allah wani abu da bai fara samuwa da wurin Allah ba" * **Daga wurinsa ... tawurinsa ...masa **- Anan, duk aukuwar "sa" na nufin Allah.
Bulus ya yi amfani da wannan don muradinsa ne dukkan mutane su ɗaukaka Allah. Ku na iya bayyana wannan a fili cikin juyin ku. AT: "Bari dukkan mutane su girmama shi har abada"
1Ina rokon ku 'yan'uwa, saboda yawan jinkan nan na Allah, da ku mika jikunanku hadaya mai rai, mai tsarki kuma abar karba ga Allah. wannan itace hidimarku ta zahiri. 2Kada ku kamantu da wannan duniya, amma ku sami canzawa ta wurin sabunta tunaninku, kuyi haka don ku san abin da ke nagari, karbabbe, kuma cikakken nufin Allah.3Don ina cewa, saboda alherin da aka bani, ka da waninku ya daukaka kansa fiye da inda Allah ya ajiye shi; a maimakon haka ku kasance da hikima, gwargwadon yadda Allah yaba kowa bangaskiya.4Domin muna da gababuwa da yawa a jiki daya, amma ba dukansu ne ke yin aiki iri daya ba. 5haka yake a garemu, kamar yadda muke da yawa haka cikin jikin Almasihu, dukkanmu gabobin juna ne.6Muna da baye-baye dabam-dabam bisa ga alherin da aka bayar a gare mu. Idan baiwar wani anabci ne, yayi shi bisa ga iyakar bangaskiyarsa. 7In wani yana da baiwar hidima, sai yayi hidimarsa. Idan baiwar wani koyarwa ce, yayi koyarwa. 8Idan baiwar wani karfafawa ce, yayi ta karfafawa; Idan baiwar wani bayarwa ce, yayi ta da hannu sake; Idan baiwar wani shugabanci ne, yayi shi da kula; Idan baiwar wani nuna jinkai ne, yayi shi da sakakkiyar zuciya.9Ku nuna kauna ba tare da riya ba. Ku Ki duk abin da ke mugu ku aikata abin da ke nagari. 10Akan kaunar 'yan'uwa kuma, ku kaunaci juna yadda ya kamata; akan ban girma kuma, ku ba juna girma.11Akan himma kuma, kada ku yi sanyi; akan ruhu kuma, ku sa kwazo; Game da Ubangiji kuma, ku yi masa hidima. 12Akan gabagadi kuma, ku yi shi da farin ciki; akan tashin hankali kuma, ku cika da hakuri; akan adu'a kuma, ku nace. 13Ku zama masu biyan bukatar tsarkaka, ku zama masu karbar baki a gidajenku.14Ku albarkaci masu tsananta maku, kada ku la'anta kowa. 15Ku yi farinciki tare da masu farinciki; Ku yi hawaye tare da masu hawaye. 16Tunanin ku ya zama daya. Kada tunaninku ya zama na fahariya, amma ku yi abokantaka da matalauta. Kada wani a cikin ku ya kasance da tunanin yafi kowa.17Kada ku rama mugunta da mugunta. Ku yi ayukan nagarta a gaban kowa. 18Ku yi duk abin da za ku iya yi domin ku yi zaman salama tare da kowa.19'Yan'uwa, kada ku yi ramako, ku bar Allah ya rama maku. A rubuce yake, "'Ramako nawa ne; zan saka wa kowa,' in ji Ubangiji." 20"Amma idan makiyin ka na jin yunwa, ba shi abinci ya ci. Idan yana jin kishin ruwa, ba shi ruwan sha. Idan kun yi haka, garwashin wuta ne za ku saka akan duk makiyi." 21Kada mugunta ta rinjaye ku, amma ku rinjayi mugunta ta wurin yin aikin nagarta.
Bulus ya faɗi yadda ya kamata rayuwar maibi ta kasance da yadda ya kamata masubi su yi bauta.
A nan "'yan'uwa" na nufin 'yan'uwa masubi maza da mata. AT: "'yan'uwa masubi, saboda da matuƙar jinkain da Allah ya ba ku, Ina so ku"
A nan Bulus ya yi amfani da kalman nan "jikuna" don ya na nufin mutum gabaɗayasa. Bulus na kwatanta maibi cikin Alamsihu wanda ke matuƙar biyayya ga Allah da dabbobin da Yahudawa kan yanka su kuma miƙa wa Allah. AT: "miƙa kanku gabaɗaya ga Allah tun kuna raye kamar hadayar da ta mutu a kan bagadin haikali"
Wannan na iya nufin 1) haɗaya wanda ka ba wa Allah kai kaɗai kuma wanda ya faranta masa rai" ko kuwa 2) abar karɓa ga Allah domin mai tsarki ne"
"Wannan hanya ce da ke daidai na yi wa Allah sujada"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) "Kada ku yi hali kamar yadda duniya ke yi" ko kuwa 2) "Kada ku yi tunani yadda duniya ke yi"
Wannan na iya nufin 1) "Kada ku bar duniya ta gaya muku abin da za ku yi da kuma tunani" ko kuwa 2) "Kada ku bar kanku ku aikata abin da duniya ke yi."
Wannan na nufin marasa bi da ke rayuwa a wannan duniya.
AT: "amma bar Allah ya canza yadda kuke tunani da kuma halinku"
A nan "alheri" na nufin zaɓen da Allah ya yi wa Bulus ya zama manzo da kuma shugaban ikkilisiya. Ku na iya bayyana wannan a fili cikin juyin ku. AT: "domin Allah ya zaɓe ni in zama manzo"
"cewa kada wani a tsakanin ku ya yi tunani cewa ya fi sauran mutane"
"Amma ku zama da hikima a yadda kuke tunani game da kanku"
Bulus na nufin cewa masubi na ba iyawa daban dabam daidai bisa ga bangaskiyarsu ga Allah. AT: "dashiƙe Allah ya ba wa kowanen ku iyawa daban dabam domin dogararku a gare shi"
Bulus ya yi amfani da wannan kalman don ya nuna cewa yanzu ka zai bayyana dalilin da ya sa kada masubi su yi tunani sun fi sauran mutane.
Bulus ya dubi dukkan masubi cikin Almasihu kamar su gabobi ne na jikin ɗan'adam. Ya yi wannan ne domin ya yi misali cewa ƙodashiƙe masubi na iya yi bautar Almasihu ta hanya daban dabam, kowan mutum na Almasihu ne kuma yana bauta a hanya mai muhimmanci.
Waɗannan abubuwa ne kamar idanu, ciki, da hannaye.
Bulus ya yi magana game da masubi kamar Allah ya haɗa su a gu ɗaya kamar gabobin jikin ɗan'adam. AT: "Allah ya haɗa kowane maibi tare da dukkan masubi"
Bulus ya yi magana game da iyawar daban dabam na masubi kamar kyauta ce daga Allah a yalwace. AT: "Allah ya ba kowanenmu iya na yi abubuwa daban dabam domin sa"
Wannan na iya nufin 1) "sai ya yi annabce annabce ba fiye da bangaskiyar da Allah ya ba shi ba" ko kuwa 2) "sai ya yi annabce annabce da ta yarda da koyarwa ta bangaskiyarmu."
A nan "bayaswa" na nufin ba da kuɗi da wasu abubuwa ga mutane. Ku na iya bayyana ma'anar wanna a fili cikin juyin ku. AT: "In wani na da baiwar bayaswa ta kuɗi ko kuwa wasu abubuwa ga mutanen da cikin bukata"
AT: "Lallai ne ku yi sahilin ƙaunaci mutane da kuma gaskiya"
Kalman da Bulus ya yi amfani da ita anan na nufin irin ƙaunar da ke zuwa daga wurin Allah da ke mayar da hankali ga amfani wasu ko mutum bai sami riba ba.
A nan Bulus ya fara bada tsarin sunayen abubuwa tara, kowanne da sifar "Game da ... zama" don ya gaya wa masubi irin mutane da ya kamata zu zama. Yana iya yiwuwa kuna bukantan juya wasu daga cikin abubuwan kamar "Game da ... yi." Sunayen sun cigaba har zuwa [Romawa 12: 13]
"game da yadda kuke ƙaunar 'yan'uwa masubi"
AT: "nuna ƙauna ga juna"
"Ku daraja da kuma girmama juna" ko kuwa "Ku daraja 'yan'uwan ku masubi ta wurin girmamasu"
"Kada ku zama ragwaye ciki aikin ku, amma ku himmantu ga bin Ruhu da kuma bautar Ubangiji"
"Jira cikin hakuri a duk sa'ad da kuna da damuwa"
Wannan ita ce abu na karshe cikin sunayen abubuwan da ya fara cikin [Romawa 12:9]. "A sa'ad da 'yan'uwa masubi na cikin matsala, ku taimake su da abin da suke bukata"
"Ku marabce su a cikin gidanku a kullayaumi sa'ad da suke bukatan wurin zama"
Wannan wata karin magana ne da nufin rayuwar ɗayantaka. AT: "Ku yarda da juna" ko kuwa "Ku yi rayuwar ɗayantaka da juna"
"Kada ku nuna cewa kun fi wasu muhimmanci"
"ku marabci mutanen da kamar basu da muhimmanci"
"kada ku yi tunani kamar kuna da hikima fiye da kowa kuma"
"Kada ku yi mugayen abubuwa ga wanda ya yi muku mugayen abubuwa"
"Ku yi abubuwan da kowa da duba a matsayin abu nagari"
"ku yi kowane abin da za ku iya yi don ku zauna lafiya da kowa"
A nan "fushi" na nufin hukuncin Allah. AT: "ku bar Allah ya hukunta cu"
AT: "Domin wani ya rubuta"
Waɗannan jimla biyun na nufin abu ɗaya ne a takaice, na kuma nanata cewa Allah zai rama wa mutanensa. AT: "Hakika zan rama maku"
Duk "ka" da "-ka" ga mutum ɗaya ne.
Cikin 12:20 Bulus ya faɗi daga wata bangare ne a Nassin. AT: "Amma Nassin ma ya ce, 'In maƙiyanka na jin yunwa ... kansa'"
"ba shi abinci"
Bulus ya yi magana game da albarkun da miyagu za su samu kamar an zuba garwashin wuta ne a kansu. Wannan na iya nufin 1) "sa mutum da ya yi muku mugunta ya ji ba daɗi game da yadda ya muzguna muku" ko kuwa 2) "ba wa Allah dalilin masananciyar shari'a ga maƙiyinku."
Bulus ya bayana "mugunta" kamar sai ka ce mutun. AT: "Kada ku bar waɗanda ke mugaye su yi nasara da ku, amma ku yi nasara da waɗanda ke mugaye ta wurin aikata nagargarun ayyuka"
1Bari kowa yayi biyayya da hukuma, saboda babu wata hukuma sai dai in tazo daga Allah; mahukunta da suke nan kuwa daga Allah ne. 2Saboda da haka duk wanda ya ja hukuma ya ja da dokar Allah; kuma dukan wadanda suka ki hukuma za su sha hukunci.3Don kuwa mahukunta ba abin tsoro ne ga masu nagarta ba, amma ga masu aikata laifi. Kuna so ku zama marasa tsoron hukuma? Kuyi abu nagari, zaku sami yabo daga yin hakan. 4Saboda shi bawan Allah ne a gare ku don nagarta. Amma in kun yi abu mara kyau, kuyi tsoro, saboda ba ya dauke da takobi ba tare da dalili ba. Don shi bawan Allah ne mai saka wa mugu da fushi. 5Saboda haka dole kuyi biyayya, ba don fushi ba, amma saboda lamiri.6Saboda wannan ne kuke biyan haraji. Don masu mulki bayin Allah ne, wadanda suke yin haka kullum. 7Ku bawa kowa hakkinsa; haraji ga mai haraji; kudin fito ga mai fito; tsoro ga wanda ya cancanci tsoro; girma ga wanda cancanci girmamawa.8Kada ku rike bashin kowa, sai dai ku kaunaci juna. Domin duk wanda ya kaunaci dan'uwansa ya cika doka. 9To, "Kada kuyi zina, kada kuyi kisa, kada kuyi sata, kada kuyi kyashi, idan har akwai wata doka kuma, an takaita ta a wannan jimlar: "Ka kaunaci dan'uwanka kamar kanka." 10Kauna bata cutar da makwabci. Domin haka, kauna tace cikar shari'a.11Saboda wannan, kun san lokaci yayi, ku farka daga barci. Domin cetonmu yana kusa fiye da yadda muke tsammani. 12Dare yayi nisa, gari ya kusan wayewa. Don haka, sai mu rabu da ayyukan duhu, mu yafa makaman haske.13Sai muyi tafiya yadda ya kamata, kamar da rana, ba a cikin shashanci ko buguwa ba. Kada kuma muyi tafiya cikin fasikanci da muguwar sha'awa, ba kuma cikin husuma ko kishi ba. 14Amma ku yafa Ubangiji Yesu Almasihu, kada kuwa ku tanadi halin mutumtaka, don biye wa muguwar sha'awarsa.
Bulus ya ga ya wa masubi yadda za su yi rayuwa a karkashin masu mulkinsu.
A nan "rai" na nufin gabaɗayan mutum. "Dukkan maibi ya yi biyayya" ko kuwa "Kowa ya yi biyayya"
"ma'aikatan gwamnati"
domin
"Dukkan iƙo na zuwa daga wurin Allah"
AT: "Mutane masu mulki sun kassancea wurin domin Allah ya sa su a wurin"
"mahukuntan gwamnati" ko kuwa "muhukuntan da Allah ya sa a wurin iƙo"
AT: "Allah zai hukunta waɗanda ke rashin biyayya ga mahukuntan gwamnati"
Masu mulki ba sa sa mutane nagari su ji tsoro.
Ana iya gane mutane ta wurin "nagargarun ayyuka" ko kuwa "mugayen ayyuka"
Bulus ya yi amfani da wannan tambayar don ya ja hankalin mutane su yi tunani game da abin da suna bukata su yi don kada su ji tsoron mahukunta. AT: "Bari in gaya muku yadda za ku zama marasa tsoron mahunta."
Gwamnati sa su faɗa nagargarun abubuwa game da mutanen da ke aikata abu nagari.
AT: "ya na ɗauke da takobi ta dalili nagari" ko kuwa "ya na da iƙon hukunta mutane, kuma shi zai hukunta mutane"
Gwamnatin Romawa na ɗauke da guntun takoni a matsayin alamar ikonsu.
A nan "fushi" na wakilcin hukuncin da mutane za su samu in sun yi mugayen ayyuka. AT: "mutum da ya hukunta mutana na kamar fushin gwamnatin gaba da mugu"
"ba domin kada gwamnati su hukunta ku ba, amma kuwa domin ku samu lamiri mai kyau a gaban Allah"
"Saboda gwamnati na hukunta masu aikata mugunta"
Bulus na magana da masubi ne anan.
"Wannan ita ce dalilin da ya sa ya kamata ku biya haraji: mahukunta"
"tafiyad da" ko kuwa "aiki a kan"
kalman na "biya" an fahimci ta daga jimla na baya. AT: "Biya haraji ga mai haraji, da fito ga mai fito. Wanda suka cancanci ladabi, ladabi da girma ga wanda ya cancanci girmamawa"
A nan biyan tsoro da girma na nufin ladabi da girmamawa ga waɗanda sun cancanci tsoro da girma. AT: "Yi tsoro ga waɗanda sun cancanci tsoro, da girma ga waɗanda sun cancanci girmamawa" ko kuwa "Ladabi ga waɗanda sun cancanci ladabi, da girma ga waɗanda sun cancanci girmamawa"
Wannan wani irin haraji ne.
Wannan korau biyu ne. AT: "Ku biya dukkan bashin da kowa ke bin ku, ku kuma ƙaunaci juna"
Wannan aikatau jam'i ce kuma na nufin dukkan masubi ta Roma.
Wannan ita ce bashi ɗayan da ke nan kamar yadda aka rubuta a baya.
Wannan na nufin irin ƙaunar da ke zuwa daga Allah da ke mayar da hankali ga amfani wasu ko mutum kansa bai sami riba ba.
yi sha'awa samun ko kuwa karban abin da ke na wani
Wannan jimla na ba da hoton ƙauna kamar mutum da ke nuna kirki ga sauran mutane. AT: "Mutanen da ke ƙaunar maƙwabcinsu ba sa cutuar su"
Bulus ya yi magana game da bukatan masubi da ke Roma su canza halinsu, kamar suna bukantan su tashi daga barci ne.
Bulus ya yi magana game da lokaci da mutane ke aikata miyagun ayyuka kamar dare. AT: "Lokacin zunubi ta kusan kai ga karshe" ko kuwa "Ta na nan kamar dare ta kusan kai ga karshe"
Bulus ya yi magana game da lokaci da mutane ke aikata abin da ke daidai kama rana. AT: "lokacin adalci zata fara jim kaɗan" ko kuwa "wato kamar rana za ta yi jim kaɗan"
Bulus ya yi magana game da "ayyukan duhu" kamar sutura ne da mutum ya ajiye a gefe. Anan "rabu da" na nufin cewa a bar yin wani abu. Anan "duhu" na nufin mugu. AT: "Don haka, sai mu bar aikata miyagun abubuwa da mutane ke yi a cikin duhu"
A nan "haske" na nufin abi nagari da kuma daidai. Bulus ya yi magana game da aikata abin da ke daidai kamar yafa makami ne don tsaron mutum da kansa. AT: "Sai mu fara yi abin da ke daidai. Yin haka kuwa zai tsare mu daga abin da ke mugu kamar yadda makami ke tsaron soja"
Bulus ya haɗa da masu karatunsa da sauran masubi tare da kansa kuma.
Bulus ya yi magana game yin rayuwa kamar masubi na gaskiya kamar wani na tafiya ne da rana. AT: "Sai mu yi tafiya cikin haske da sanin cewa kowa na iya ganin mu"
Waɗannan ra'ayin a takaice na nufin abu ɗaya ne. Za ku iya haɗa su a juyin ku. AT: "ayyuka na shashanci"
Wannan na nufin shirya mugunta da kuma musu tare da mutane.
Wannan na nufin jin bacin rai game da wanim nasarar wani ko riba fiye da wasu.
Bulus ya yi magana game da bin halin Almasihu kamar mayafi ne da mutane ke iya gani.
Idan harshen ku na da jam'i na umurni, to sai a yi amfani da ita anan.
A nan "jiki" na nufin halin ta jiki na mutum wanda ke gaba da Allah. Wannan halin zunubi ne na 'yan adam. AT: "ko kaɗan kada ku bar tsohon muguwar zuciyar ku ta samu zarafin aikata muyagun abubuwa"
1Ku karbi duk wanda yake da rarraunar bangaskiya, ba tare da sukar ra'ayinsa ba. 2Wani yana da bangaskiyar yaci komai, wani wanda yake da rauni yakanci ganye ne kawai.3Kada wanda yake cin komai ya raina wanda baya cin kowanne abu. Kada kuma wanda baya cin kowanne abu ya shara'anta sauran da suke cin komai. Saboda Allah ya karbe shi. 4Kai wanene, kai wanene da kake ganin laifin bawan wani? Tsayawarsa ko faduwarsa ai hakin maigidansa ne, amma Ubangiji yana da ikon tsai da shi.5Wani yakan daukaka wata rana fiye da sauran. Wani kuma yana daukan ranakun daidai. Kowa ya zauna a cikin hakakkewa akan ra'ayinsa. 6Shi wanda ya kula da wata rana, ya kula da ita don Ubangiji. Kuma wanda yaci, yaci ne domin Ubangiji, domin yana yi wa Allah godiya. Shi wanda bai ci ba, yaki ci ne domin Ubangiji. Shima yana yi wa Allah godiya.7Domin babu wanda yake rayuwa don kansa a cikinmu, kuma babu mai mutuwa don kansa. 8Domin in muna raye, muna raye don Ubangiji. Kuma in mun mutu, mun mutu ne don Ubangiji. Ashe, ko muna raye, ko a mace mu na Ubangiji ne. 9Domin wannan dalilin Almasihu ya mutu ya kuma tashi, saboda ya zama Ubangiji ga matattu da rayayyu.10Amma ku don me kuke shara'anta yan'uwanku? kai kuma don me kake raina dan'uwanka? Dukan mu zamu tsaya gaban kursiyin shari'ar Allah. 11Domin a rubuce yake, "Na rantse, "inji Ubangiji", kowacce gwiwa zata rusuna mani, kowanne harshe kuwa zai yabi Allah."12Domin kowannenmu zai fadi abin da shi yayi da bakinsa a gaban Allah. 13Saboda da haka kada muyi wa juna shari'a, amma maimakon haka ku dauki wannan kudduri, don kada kowa ya zama sanadin tuntunbe ko faduwa ga dan'uwansa.14Na sani na kuma tabbata tsakani na da Ubangiji Yesu, ba abin da yake mara tsarki ga asalinsa. Sai dai ga wanda ya dauke shi marar tsarki ne yake zama marar tsarki. 15Idan har abincinka na cutar da dan'uwanka, ba ka tafiya cikin kauna. Kada ka lalata wanda Yesu ya mutu domin sa da abincinka.16Saboda haka, kada abubuwan da aka dauka kyawawa su zama abin zargi ga wadansu. 17Saboda mulkin Allah ba maganar ci da sha ba ne, amma game da adalci ne, salama, da farin ciki a cikin Ruhu Mai Tsarki.18Domin wanda yake bautar Almasihu a wannan hanya, karbabbe ne ga Allah, kuma jama'a sun yarda da shi. 19Don haka, mu nemi abubuwa na salama da abubuwan da zasu gina juna.20Kada ku lalata aikin Allah don abinci. Komai yana da tsarki, amma kaiton mutumin da yake cin abin da zai sa shi ya fadi. 21Bashi da kyau a ci nama ko a sha ruwan inabi, ko duk abin da zai jawo faduwar dan'uwanka.22Wannan bangaskiyar da kuke da ita, ku adana ta tsakaninku da Allah. Mai albarka ne wanda zuciyarsa bata da laifi akan abin da hankalinsa ya ga daidai ne. 23Duk wanda yayi shakka amma kuma yaci, ya sani yayi laifi kenan, domin ba tare da bangaskiya bane. Duk abin da ba na bangaskya bane zunubi ne.
Bulus ya karfafa masubi su tuna cewa amsa wa Allah.
Wannan na nufin waɗanda ji kamar suna da laifi game da ci da kuma shan wasu abubuwa.
"kuma kada ku shara'anta su saboda ra'ayinsu"
A nan "bangaskiya" na nufin yin abin da mutum ya gaskanta cewa Allah ya faɗa masa ya yi.
Wannan na bayana mutumin da ya gaskanta cewa Allah ba ya so ya ci nama.
Bulus ya yi amfani da tambaya don ya sauta wa waɗanda ke shara'anta wasu. Kuna iya juya wannan cikin magana. AT: "Kai ba Allah ba ne, saboda haka ba ba ka izinin shara'anta wani bawansan ba!"
"kai" anan ba mutum fiye da daya ba ne.
Bulus ya yi magana game da Allah sai ka ce shi maigida ne da ke da bayi. AT: "Ai maigidan ne kaɗai ke da iƙo yanke shawara ko zai karbi bawan ko kuwa"
Bulus ya yi magana game da bawan da ke karɓaɓɓe ga Allah kamar kamar an "tsai da shi ne" a maimakon ya faɗi. AT. "Amma Ubangiji zai karɓe shi domin ya na da iƙon mayar da bawan ya zama karɓaɓɓe"
"Wani na tunani rana guda ya fi muhimanci fiye da sauran, amma wani kuma na tunanin dukkan ranaku ɗaya ne"
Ku na iya bayana ma'anar wanna a fili. AT: "Bari kowane mutum ya tabbata cewa abin da yake yi don girmama Ubangiji ne"
A nan "kula" na nufin yin sujada. AT: "Mutumin da ke sujada a rana ta musamman yana yi haka don girmam Ubangiji ne"
kalman nan "kowane abu" an fahimci ta ne daga [Romawa 14: 03]. Ana iya sake nanata ta anan. AT: "mutumin da ke cin kowane irin abinci"
ya ci don girmama Ubangiji" ko "ya ci ta wannan hanyar don ya girmama Ubangiji ne"
Kalman nan "kowane abu" an fahimci ta ne daga [Romawa 14:03]. Anan iya sake nanata ta anan. AT: "Shi wanda ba ya ci kowane abu" ko "Mutumin da ba ya cin wasu iri abinci"
"ya ƙi cin waɗannan abincin don ya girmama Ubangiji ne" ko "ya ci ta haka don ya girmama Ubangiji ne"
A nan "rayuwa don kansa" na nufin rayuwa don faranta wa kansa rai. AT: "Kada mu yi rayuwa don kawai mu farantawa kanmu rai"
Wannan na nufin mutuwar wani ya shafe sauran mutane. AT: "kada mu yi tunanin cewa in mun mutu, mutuwar mu za ta shafe mu kawai ne"
Bulus ya haɗa da masu karatunsa ne.
Ta wurin amfani da waɗannan tambayoyin, Bulus na nuna yadda yana bukata ya sauta wa wasu daga cikin masu karatunsa. AT: "ba daidai ne ka shara'anta ɗan'uwanka ba, kuma ba daidai ne ka raina ɗan'uwanka ba!" ko "ka shara'anta da kuma raina ɗan'uwanka!"
A nan wannan na nufin 'yan'uwa masubi, maza ko kuwa mata.
"Kursiyin shari'a" na nufin iƙon Allah don shari'a. AT: "Gama Allah zai shara'anta mu dukka"
AT: "Gama wani ya rubuta cikin Nassin: 'kamar"
An yi amfani da maganannan don a fara ransuwa ko kuwa alkawari. AT: "Ku tabbata cewa wannan gaskiya ne"
Bulus ya yi amfani da kalmomin nan "gwiwa" da "harshe" do yana nufin mutum gabaɗayansa. Haka kuma, Ubangiji ya yi amfani da kalman nan "Allah" don ya na nufin kansa. AT: "kowane mutun zai rusuna ya kuma miƙa yabo zuwa a gare ni"
"lallai ne ya yi bayanin halayensa ga Allah"
A nan "sanadin tuntuɓe" da "faduwa" a takaice na nufin abu ɗaya ne. AT: "maimakon haka bari ya zama maƙasudinku kada ku yi ko ku faɗa wani abin da zai iya sa ɗan'uwa maibi ya yi zunubi"
A nan kalmomin nan "sani" da "na tabbata" a takaice na nufin abu ɗaya ne; Bulus ya yi amfani da su don ya nanata tabbacinsa ne. AT: "Na hakikance saboda ɗangantakana da Ubangiji Yesu"
Za a iya juya wannan cikin tabbataciyar magana. AT: "kowane abu kanta mai tsarki ne"
"ga asalin ta" ko kuwa "saboda abin da ta ke"
A nan Bulus na nufin cewa mutum ya yi nesa da kowane abin da yake tunani marar tsarki ne. Kuna iya bayana wannan a fili cikin juyin ku. AT: "Amma in mutum na tunanin cewa wani abu marar tsarki, to ga wannan mutum abin marar tsarki ne saboda haka sai ya yi nesa da shi"
"Idan ka cutar da bangaskiyar ɗan'uwanka mai bi a kan zancen abinci." Anan kalman nan "ka" na nufin waɗanda ke da ƙarfi cikin bangaska "'ɗan'uwa" na nufin waɗanda ke raunana cikin bangaskiya.
Bulus ya yi magana game da halin masubi kamar tana tafiya. AT: "saboda haka ba ka nuna ƙauna"
"Idan wani na tunani cewa wani abu na zargi ne, to kada ka aikata shi, ko ka ɗauka kyakkyawa ne"
Bulus na cewa Allah ya kafa mulkinsa don ya ba mu ɗangantaka mai kyau da kansa, ya kuma yi tanaɗin salama da farin ciki. AT: "Gama Allah ba kafa mulkinsa saboda ya yi mulki kan abin da muke ci ko sha ba. Ya kafa mulkinsa ne saboda mu samu ɗangantaka ma kyau da shi, ta haka kuma zai ba mu salama da farin ciki"
AT; "mutane za su amince da shi" ko kuwa "mutane za su ba shi girma"
A nan "gina juna" na nufin taimakon juna don girma cikin bangaskiya. AT: "Sai mu nemi rayuwan zaman salama tare da kuma taimakon juna don girma da ƙarfi cikin bangaskiya"
Ku na iya bayana ma'anar wannan jimlar a fili. AT: "Kada ka warware abin da Allah ya yi wa ɗan'uwa maibi wai domin ka na so ka ci wani irin abinci"
A nan abin da ke "sa shi tuntuɓe" na nufin ta na sa ɗan'uwa raunana ya yi abin da lamirinsa bai amince da shi ba. AT: "amma zai zama zunubi in wani ya ci abincin da wani ɗan'uwa ke tunanin cewa ba daidai ne a ci ba, idan ta wurin ci wannan ya sa ɗan'uwa raunana ya yi abinda lamirinsa ba amince ba"
"Zai fi kyau kada ka ci nama ko ka sha ruwan inabi ko kuwa ka yi wani abu da zai iya sa ɗan'uwanka zunubi"
Wannan na nufin mai ƙarfin cikin bangaskiya, "ɗan'uwa" na nufin raunana cikin bangaskiya.
Wannan na nufin imani game da ci da sha.
mufuradi. Domin Bulus na magana da masubi, mai yiwuwa ya zama lallai ku juya wannan ta wurin amfani da jam'i.
"Albarka ta tabbata ga waɗanda ba sa zargin kansu don abin da sun amince za su aikata"
AT: "Allah zai ce da wannan mutum ya yi abin da ba daidai ba in har bai tabbata ko daidai ne ya ci wani irin abinci ba, amma ya ci" ko kuwa "Mutumin da bai tabbata ko daidai ne a ci wani irin abinci ba, amma ya ci ko ta wace hanya zai sami damuwa cikin lamirinsa"
Kowane abin da "ba daga bangaskiya ba" wannan abu ne wanda Allah ba ya so ka yi. Ku na iya bayana ma'anar wannan a fili anan. AT: "Allah zai ce da cewa ba yi daidai ba domin yana ci abin da ya bada gaaskiya Allah ba ya son sa da ci"
kowane abin da "ba na bangaskiya ba" abu ne wanda Allah ba ya so ka yi. Ku na iya bayana ma'anar wannan a fili anan. AT: "ka na zunubi idan ka yi wani abin da ba ka gaskanta cewa Allah na so ka yi ba"
1Yanzu mu da muke da karfi ya kamata mu dau nauyi raunana, kuma bai dace mu nuna son kai ba. 2Bari kowannenmu ya faranta wa makwabcinsa rai, domin wannan yana da kyau, don a gina shi.3Domin Almasihu bai faranta wa kansa rai ba. Kamar yadda aka rubuta, "zagin da wadansu suka yi masa ya sauka a kaina." 4Don abin da aka rubuta a baya an rubuta ne domin a gargade mu, domin ta hakuri da karfafawar litattafai mu sami karfi.5Yanzu Allah mai hakuri da karfafawa ya baku zuciya daya ta zaman tare da juna bisa ga halin Yesu Almasihu. 6Domin ya yi haka ne da zuciya daya domin ku yi yabo da bakinku daya. 7Domin ku karbi juna, kamar yadda Yesu ma ya karbe ku domin a daukaka Allah.8Saboda na ce an mai da Almasihu bawan kaciya a madadin gaskiyar Allah. Ya yi wannan ne don a tabbatar da alkawarai da aka ba kakanin kakaninmu. 9Domin Al'umai su daukaka Allah saboda jinkansa, kamar yadda ya ke a arubuce, "Domin ta haka zan yabe ka cikin Al'umai in yi wakar yabon sunanka."10Kuma an ce. "Ku yi faranciki, ku Al'ummai tare da mutanensa." 11Kuma." Ku yabi Ubangiji, ku dukan Al'ummai; bari dukan mutane su yabe shi."12Kuma, Ishaya ya ce "Za a sami tsatson Yessi, wanda zai tashi ya yi mulki a kan Al'umai, Al'umai za su sami karfin hali a cikinsa."13Yanzu Allah mai karfafawa ya cika ku da dukkan farin ciki salama, saboda da bangaskiyarku, domin ku sami cikkakiyar karafafawa, ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki.14Ni kaina na amince da ku, yan'uwa. Kuma na amince cewa ku da kanku kuna cike da alheri, cike da dukkan sani. Na amince cewa za ku sami zarafi ku gargadi juna.15Amma ina rubuta maku da gabagadi kan wadansu abubuwa, domin in tunasheku, saboda baiwar da aka bani daga wurin Allah. 16Cewa baiwar ta sa na zama bawan Almasihu Yesu da aka aika ga Al'ummai, limami na bisharar Allah. Zan yi wannan saboda baikon Al'ummai ya zama karbabbe, kuma kebbabe ga Allah ta wurin Ruhu Mai Tsarki.17Don haka ina jin dadi cikin Yesu Almasihu da abubuwa na Allah. 18Domin ba ni da abin da zan ce, sai abin da Yesu ya aikata ta wurina, domin Al'ummai su yi biyayya ta magana da aiki. 19Ta wurin alamu, da al'jibai, da ikon Ruhu Mai Tsarki. Daga Urushalima, da kewaye har zuwa Ilirikum, an kai bisharar Almasihu ko'ina dukka.20A cikin hanyar nan, burina in sanar da bishara, amma a inda ba a san Yesu ta wurin sunansa ba, don kada in sa gini akan harshashi wani. 21Kamar yadda yake a rubuce."Wadanda ba a taba fada wa labarinsa ba, su gane. Wadanda ba su taba jin labarinsa ba su fahimta."22Saboda an hana ni zuwa wurin ku a lokatai da dama. 23Amma yanzu bani da sauran wani wuri a lardin nan, kuma cikin shekaru masu yawa ina da marmarin in zo wurin ku.24Duk lokacin da zan tafi Asbaniya ina begen ganin ku yayin wucewa, don ku raka ni bayan na ji dadin zama da ku na dan lokaci. 25Amma yanzu ina tafiya Urushalima don in yi wa tsarkaka hidima.26Domin abin farinciki ne ga mutanen Makidoniya da Akaya su yi bayarwa domin gajiyayyu masu bada gaskiya wadanda suke a Urushalima. 27Suna jin dadi domin hakika kamar bashi ne a kansu. Domin Al'ummai sun yi tarayya da su cikin ayyukan ruhaniya, ya zama hakki a kansu su ma su taimake su da abubuwa.28Domin lokacin da na gama basu kudin, zan zo gareku a hanyata ta zuwa Asbaniya. 29Na san cewa lokacin da na zo gareku, zan zo da cikakkun albarku na Almasihu.30Yanzu ina rokonku, yan'uwa, ta wurin Ubangiji Yesu Almasihu, da kaunar Ruhu Mai Tsarki, ku yi ta fama tare da ni a cikin yin addu'o, inku ga Allah saboda ni. 31Kuyi haka saboda in tsira daga wadanda suke masu biyayya ga Yahudiya, domin kuma hidimata saboda Urushalima ta zama karbabbiya. 32Ku yi addu'a cewa in zo wurinku da farinciki ta wurin nufin Allah, cewa tare da ni da ku, mu sami hutu.33Allah na salama ya kasance tare da ku duka. Amin.
Bulus ya gama wannan sashin game da rayuwar masubi don wasu ta wurin tunashe su yadda Almasihu ya yi rayuwa.
Ku juya wannan ta wurin yin amfani da kalmomin da ake amfani da shi a harshen don gabatar sabuwar zance.
Anan "karfi" na nufin mutanen da ke da karfi cikin bangaskiyarsu. Sun gaskanta cewa Allah ya ba su iznin cin kowane irin abinci. AT: "mu da muke da karfin cikin bangaskiya"
Wannan na nufin Bulus, masu karatunsa da kuma sauran masubi.
A nan "raunanan" na nufin mutanen da ke raunana cikin bangaskiyar. Sun gaskanta cewa Allah bai yarda musu su ci wasu irin abinci. AT: "waɗanda ke raunana cikin bangaskiya"
Ta wurin wannan, Bulus na nufin karfafa bangaskiyar wani. AT: "a karfafa bangaskiyarsa"
A nan Bulus na nufin nassin da Almasihu
Zagin da waɗansu suka yi wa Allah ya sauka a kan Almasihu.
AT: "Don a dã, annabawa sun rubuta kome cikin Nassosin don su koya mana"
Bulus ya haɗa masu karatunsa da suaran masubi.
A nan "sami gabagadi" na nufin cewa masubi za su san cewa Allah zai cikata alkawarensu. Za ku iya bayana ma'anar a fili cikin juyin ku. AT: "ta haka nassosin za su karfafa mu mu sa sammanin cewa Allah zai yi mana kowane abin da ya alkawarta"
"addu'a ta ita ce ... Allah ... zai yi"
A nan zama da "zuciya ɗaya" na nufin a yarda da juna. AT: "yarda da juna" ko "zama ɗaya"
Wannan na nufin a zama ɗaya cikin yabon Allah. AT: "yabe Allah tare cikin ɗayantaka kamar baki ɗaya ke magana"
"karɓi juna"
Kalman "na" na nufin Bulus.
A nan "mai kaciya" na nufin Yahudawa. AT: "Yesu Almasihu ya zama bawan Yahudawa"
Waɗannan ne makasuɗi biyu da ya sa Almasihu ya zama bawa ga masu kaciya. AT: "domin a tabbatar da alkawaren ... da kuma domin Al'umai su ɗaukaka Allah saboda jinkansa"
A nan "ubannin" na nufin kakkanin mutanen Yahudawa. AT: "alkawaren da Allah ya ba wa kakkanin Yahudawa"
AT: "kamar yadda wani ya rubuta cikin nassosin"
A nan "sunanka" na nufin Allah. AT: "yi maka wakar yabo"
"Kuma nassin ya ce"
Wannan na nyfin mutanen Allah. Ku na iya bayana wannan a fili cikin juyinku. AT: "tare da mutenen Allah"
"yabe Ubangiji"
Yessi uban Sarki Dauda ne a jiki. AT: "zuriyar Yessi"
A nan "sa" na nufin zuriyar Yessi, Mai Ceton. Waɗanda ba Yahudawa za su yarda cewa shi zai cika alkawarensa. AT: "Mutanen da ba Yahudawa ba ba za su iya yarda da shi cewa zai yi abin da ya alkawarta"
Bulus ya zuguiguta anan don ya nanana nufinsa. AT: "cika ku da matuƙar farin ciki da salama"
Bulus ya tabbata cewa masubi a Roma na girmama juna cikin halayensu. AT: "Ni kaina na tabbata babu shakka cewa ku kanku kun yi wa juna abu mai kyau ta hanya mai kyau"
A nan wannan na nufin 'yan'uwa masubi, duk mazaje da mataye.
Bulus anan ya nanata ainihin nufinsa. AT: "cika da cikakkiyar sani don bin Allah"
A nan "gargaɗi" na nufin a koyar. AT: "kuma iya koyar da juna"
Bulus ya yi magana game da alheri kamar kyauta a jiki da Allah ya ba shi. Allah ya zaɓi Bulus ya zama manzo ko dashiƙe ya tsanantawa masubi kafin ya zama mai bin Yesu. AT: "alherin da Allah ya ba ni"
Bulus ya yi magana game da wa'azin bisharasa kamar shi, a matsayin firist, yana mika baiko ga Allah. AT: "Al'ummai sun farantawa Allah rai a sa'ad da sun yi masa biyayya"
A nan "Waɗanan abubuwan" na nufin abin da Almasihu ya yi ta wurin Bulus. AT: "Saboda biyayyar Al'ummai, zan yi magana game da abin da Almasihu ya yi ta wurin na cikin furuci da aikatawa da kuma ta wurin iƙon alamu da al'ajibai ta wurin iƙon Ruhu Mai Tsarki"
Waɗannan kalmomin biyu a takaice na nufin abu ɗaya na kuma nufin iri iri al'ajibai.
Wannan daga birnin Urushalima har zuwa nesa da lardin Ilirikum, wani wuri kusa da Italiya.
Bulus na so ya yi wa'azi ga mutanen da ba su taba ji game da Almasihu ba. AT: "Saboda wannan, ina so in yi wa'azin bishara a wuraren da mutane ba su taba ji game da Almasihu ba"
Bulus ya yi magana game da aikinsa kamar yana gini ne kan harshashi. AT: "don kada in cigaba da aikin da wani ya riga ya fara. Ba na so in zama kamar mutum wanda ya yi ginin gida kan harshashin wani"
A nan Bulus na nufin abin da Ishaya ya rubuta cikin nassosin. Ana iya bayyana ma'anar wannan a fili. AT: "Abin da ke faru daidai ne kamar abin da Ishaya ya rubuta cikin nassosin"
A nan Bulus ya yi magana game da "bushăra" ko sako game da Almasihu kamar rayayye ne kuma na iya tafiya da kanta. AT: "Waɗanda ba wanda ya taɓa faɗa wa labari game da shi"
AT: "sun kuma hana ni" ku kuwa "mutane kuwa sun hana ni"
Bulus na nufin cewa babu wani wurin a waɗannan yankunan da mutane ke rayuwa da ba su ji game da Almasihu ba. AT: "babu waɗansu wuraren cikin waɗannan yankunan da mutane ba su ji game da Almasihu ba"
Wannan lardin roma ne ta yammancin Roma inda muraɗin Bulus ne ya yi ziyara.
"a sa'ad da Ina wucewa cikin Roma" ko kuwa "a sa'ad da ina hanya ta"
A nan Bulus na nufin cewa yana so masubi da ke Roma su yi masa tanaɗin wasu kuɗi don tafiyarsa"
"na ji daɗin zama da ku na dan lokaci" ko kuwa "na ji daɗin ziyartanku"
A nan kalmomin nan "Makidoniya" da "Akaya" na nufin mutanen da ke rayuwa a waɗannan wurare. AT: "masubi a lardin Makidoniya da Akaya sun yi murna"
"Masubi da ke a Makidoniya da Akaya sun ji daɗin aikata ta"
"haƙika mutanen Makidoniya da Akaya su kamar bashi ne ga masubi da ke Urushelima"
"dashiƙe Al'ummai sun yi tarayya da su cikin ayyukan ruhaniyan masubi da ke Urushalima, Al'ummai na da bashin bauta ga masubi da ke Urushalima.
Bulus ya yi magana game da kuɗin da zai kai Urushalima kamar 'ya'yan itace ne da ya karɓa daga wurin su. AT: "cikin koshin lafiya ya kai wannan baikon zuwa gare su"
Wannan magana na nufin cewa Almasihu zai albarkaci Bulus da Masubi da ke Roma. AT: "Na kuma sani cewa sa'ad da na ziyarce ku, Almasihu zai albarkace mu a yalwace"
"Ina karfafa ku"
"ku nace" ko "ku yi gwagwarmaya"
AT: "Allah zai kubutar da ni daga waɗanda suke rashin biyayya" ko "Allah zai sa waɗanda suke rashin biyayya su yi nesa don kada su yi mini lahani"
Anan Bulus ya bayana muraɗin sa cewa masubi da ke Urushalima za su karɓe kuɗin da ya kawo daga masubi da ke Makidoniya da Akaya da farin ciki. AT: "addu'a ta ita ce masubi da ke Urushalima za su karɓi kuɗin da na kawo musu da farin ciki"
"Allahn na salama" na nufin Allahn da ke sa masubi su sami salamar zuci. AT: "Ina addu'a cewa Allah wanda ya sa dukkanmu mu sami salamar zuci"
1Ina gabatar muku da fibi 'yar'uwarmu, wanda take hidima a Ikilisiya dake cikin Kankiriya. 2Domin ku karbe ta cikin Ubangij. A hanyar da ta dace ga masu bada gaskiya, ku tsaya tare da ita cikin kowacce bukata. Domin ita da kanta ta zama da taimako ga masu yawa, har da ni ma.3Ku gai da Bilkisu da Akila abokan aiki cikin Yesu Almasihu. 4Wadanda sabo da ni suka sadaukar da ransu. Ina godiya garesu, ba ni kadai ba, amma kuma da dukan Ikilisiyoyin Al 'mmai. 5Gaida Ikilisiya da ke gidansu. Ku gai da Abainitas kaunataccena. Wanda shi ya fara bada gaskiya ga Almasihu a Asiya.6Ku gai da Maryamu, wadda ta yi maku aiki tukuru. 7Ku gai da Andaranikas da Yuniyas, yan'uwana da abokan kurkukuna. Su sanannu ne cikin manzani, wadanda suke cikin Almasihu kafin ni. 8Ku gai da Amfiliyas kaunatace na cikin Ubangiji.9Ku gai da Urbanas abokin aikinmu cikin Almasihu, da Istakis kaunataccena. 10Ku gai da Abalis amintacce cikin Almasihu. Ku gai da wadanda su ke gidan Aristobulus. 11Ku gai da Hirudiya, dan'uwa na, da wadanda ke gidan Narkissa, wadanda ke cikin Ubangiji.12Ku gai da Tarafina daTarafusa, masu aikin Ubangiji. 13Ku gai da Barsisa kaunatacciya, wadda ta yi aikin Ubangiji da yawa. Ku gai da Rufas zababbe cikin Ubangiji da mamarsa da ni. 14Ku gai da Asinkiritas da Filiguna da Hamis da Baturobas da Hamisu da kuma yan'uwa da ke tare da su.15Ku gai da Filolugus daYuliya da Niriyas da yan'uwansa, da Ulumfas da kuma dukan tsarkaka da ke tare su. 16Ku gaggai da juna da tsatsarkar sumba. Dukan Ikilisiyoyin Almasihu na gaishe ku.17Yanzu ina rokon ku, yan'wa, ku yi tunani fa game da masu kawo rabuwa da tuntube. Sabanin koyarwar da ku ka koya. Ku yi nesa da su. 18Domin irin mutanen nan ba sa bauta wa Ubangiji Yesu, sai dai tumbinsu. Ta dadin bakinsu suke rudin zuciyar marasa laifi.19Domin rayuwar biyayyarku takai ga kunnen kowa, na yi farin ciki da ku, amma ina so ku zama da hikima game da abin ya ke mai kyau, ku zama marasa laifi ga abin da ke na mugunta. 20Allah na salama zai sa ku tattake Shaidan da sauri kalkashin sawayen ku. Alherin Ubangijin mu Yesu Almasihu ya kasance tare da ku.21Timoti abokin aikina, yana gaishe ku, haka Lukiyas da Yason da Susibataras da kuma yan'uwana. 22Ni Tartiyas wanda ya rubuta wasikan nan, na gaisheku cikin Ubangiji.23Gayus mai masaukina da kuma dukan Ikilisiya, suna gaishe ku. Arastas ma'ajin birni na gaishe ku, da Kwartus dan'uwanmu. 24Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu ya kasance tare da ku dukka. Amin.25Yanzu ga wanda ke da Ikon karfafa ku bisa ga bisharata da wa'azin Yesu Almasihu, wanda ta gare shi ne aka bayyana asiran nan da suke boye tun da dadewa, 26amma yanzu sanannu ne ta wurin litattafan Annabawa bisa umarnin Allah madauwami, domin biyayyar bangaskiya cikin Al'ummai dukka.27Ga Allah mai hikima kadai, ta wurin Yesu Almasihu daukaka ta tabbata har abada. Amin.
Bulus ya gaishe da masubi da yawa dake Roma ta wurin ambata suna.
"Ina so ku ba wa Fibi girma"
Wannan suna ce na ta mace.
Kalman "mu" na nufin Bulus da dukkan masubi. AT: "'yar'uwarmu cikin Almasihu"
Wannan a dă wurin jirgin ruwa ne a birnin Hellas.
Bulus ya karfafa masubi da ke Roma da su marabci Fibi kamar 'yar'uwa maibi. AT: "marbce ta domin dukkan mu na Ubangiji ne"
"Ta hanyar da masubi ya kamat su marabci sauran masubi"
Bulus ya karfafa masubi da ke a Roma cewa su ba wa Fibi kowane abu da take bukata. AT: "taimake ta tawurin ba ta kowane abin da take bukata"
"taimake mutane da yawa, ta kuma taimake ni"
Biriska matan Akila.
"abokan aikin" Bulus mutane ne wanda suna gaya wa mutane game da Yesu. AT: "wanda muke aikin gaya wa mutane game da Almasihu Yesu tare"
"Gaida masubi da ke taruwa su yi sujada a gidansu"
Wannan sunan na miji ne.
Bulus ya yi magana game da Abainitas kamar shi 'ya'yan itace ne da aka girba. AT: "mutum na farko a ƙasar Asiya da ya bada gaskiya da Yesu"
Wannan sunan mace ce.
Waɗannan sunayen maza ne.
Wannan na iya zama 1) Yuniyas sunan mace ce, ko, ba kamar haka ba, 2) Yuniyas, sunan na miji ne.
AT: "Manzannan sun san su kwarai da gaske"
"abokai na ƙaunatattu da 'yan'uwa masubi"
Waɗannan sunayen maza ne.
Kalman nan "amintacce" na nufin wani wanda aka gwada shi an kuma tabbatar cewa shi na ƙwarai ne. AT: "wanda Almasihu ya amince"
Wannan na nufin waɗanda sun dogara ga Yesu. AT: "wanda ke masubi" ko "wanda ke na Ubangiji"
Waɗannan sunayen mata ne.
Waɗannan sunayen maza.
AT: "wanda Ubangiji ya zaɓa"
Bulus ya yi magana game da uwar Rufas karma uwarsa ce. AT: "uwa tasa, wanda ni ma ina tunanin ta kamar uwa ta" (Dubi:
A nan wannan na nufin 'yan'uwa masubi, mazaje da mataye dukka.
Waɗannan sunayen maza ne.
Sunan mace ce. Yuliya mai yiwuwa matar Filolugus.
nuna so ga 'yan'uwa masubi
A nan Bulus ya yi magana ta gabaɗaya game da Ikkilisiyoyin Almasihu. AT: "Masubi cikin dukkan ikkilisiyoyin fa ke wannan yanki na mika sakon gaisuwarsu zuwa gare ku"
"yi hankali da"
Wannan na nufin waɗanda ke musu suna kuma hana wasu dogara ga Yesu. AT: "masu sa masubi musu da juna da kuma rashin bada gaskiya ga Allah"
"Su na koyar da abubuwan da bai yi daidai da gaskiyar da kuka koya ba"
"Yi Nesa" anan na nufi "ƙin kassa kunne." AT: "Kada ku kassa kunne a gare su"
Kalmomin nan "suna bautawa", an fahimci ta daga magana da ke a baya. Wannan ana iya bayana ta cikin wata jimla dabam. AT: "Maimakon haka, su na bauta wa cikinsu"
Kalmomin nan "romon" da "flattering" a takaice na nufin abu ɗaya ne. Bulus na nanata yadda waɗannan mutane de ruɗin masubi. AT: "Ta wurin faɗin abubuwan da ke kamar mai kyau da kuma gaskiya"
A nan "zuciya" na nufin tunanin mutum ko kuwa cikin sa. AT: "sun ruɗe masubi marasa laifi"
Wannan na nufin waɗanda ke da sauƙin kai, marasa azanci da butulci. AT: "marasa azancin da suka dogara a gare su" ko "waɗanda ba su sani cewa waɗannan malaman na ruɗin su ba"
A nan Bulus ya yi magana game da biyayyar masubi da ke a Roma kamar mutum ne da zai iya zuwa wurin mutane. AT: "Don kowa ya ji yadda ku ke biyayya ga Yesu"
Maganar nan "tattake ... a karkashin sawayen ku" na nufin matuƙar nasara kan maƙiyi. Anan Bulus ya yi magana game da nasara kan Shaidan kamar masubi da ke Roma na tattake maƙiyi da karkashin sawayensu. AT: "Allah zai ba ku salama da matuƙar nasara kan Shaidan ba da jimawa ba"
"ba haɗa kai da miyagun abubuwa"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Tartiyas shine wanda ya rubuta abin da Bulus ya faɗa.
"gaisheku kamar ɗan'uwan maibi"
Waɗannan sunayen mazaje ne.
Wannan na nufin Gayus, mutumin da Bulus da 'yan'uwa masubi na taruwa don sujada a gidansa.
Wannan mutum ne wanda ke kula da kuɗaɗen kungiya.
A nan kalman nan "yanzu" alamace ta ƙarshen bangaren wasiƙa. Idan ku na da wata hanya na yin wannan a harshen ku, kuna iya amfani da ita ana.
Bulus ya yi magana game da samun bangaskiya mai karfi kamar mutum ne da ke tsaye a maimakon faɗiwa. AT: "a sa bangaskiyarku ta yi karfi"
"ta wurin bisharar da na yi wa'azinta game da Yesu Almasihu"
Bulus ya ce cewa Allah ya bayyana gaskiyar da aka ɓoye a dă ga masubi. Ya yi magana game da waɗannan gaskiyar kamar wata asiri ne. AT: "somin Allah ya bayyana asirin da ya ajiye tun dă ga masubi"
Aikatau nan "sananne" da "bayyana" a takaice na nufin abu ɗaya. Bulus ya yi amfani da su dukka don ya nanata ainihin maganarsa. Ku na iya haɗa waɗannan kalmomin. AT: "amma yanzu Allah madawwami ya sa ta ta zama sananne ga dukkan Al'ummai ta wurin rubuce rubucen annabawa"
A nan "biyayya" da "bangaskiya" sunaye ne. Ku na iya amfani da aikatau na "biyayya" da "dogara" cikin juyin ku. Ya kamata ku bayyana shi wanda zai yi biyayya ya kuma dogara. AT: "domin dukkan Al'ummai za su yi biyayya ga Allah domin sun dogara a gare shi"
A nan "ta wurin Yesu Almasihu" na nufin abin da Yesu ya yi. A bada "ɗaukaka" na nufin yabo ga Allah. AT: "Saboda abin da Yesu Almasihu ya yi mana, za mu yabe shi kaɗai wanda shi ne Allah, shi kaɗai kuma mai hikima. Amin"
1Bulus, kirayayye daga Almsihu Yesu don zama manzo ta wurin nufin Allah, da dan'uwanmu Sastanisu, 2zuwa ga Ikilisiyar Allah da ke korinti, zuwa ga wadanda aka kebe su cikin Almasihu Yesu, wadanda aka kira domin su zama al'umma maitsarki. Muna kuma rubuta wa dukan masu kira bisa sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu a ko'ina, wato Ubangijinsu da Ubangijinmu kuma. 3Bari alheri da salama su zo gare ku daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Almasihu.4Kodayaushe ina gode wa Allahna domin ku, saboda alherin Allah da Almasihu Yesu ya yi maku. 5Ya ba ku arziki ta kowace hanya, cikin dukkan magana da dukkan ilimi. 6Kamar yadda shaida game da Almasihu ta tabbata gaskiya a tsakaninku.7Saboda haka baku rasa wata baiwa ta ruhaniya ba yayinda kuke marmarin jiran bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Almasihu. 8Zai kuma karfafa ku zuwa karshe, saboda ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Almasihu. 9Allah mai aminci ne shi wanda ya kira ku zuwa zumunta ta Dansa, Yesu Almasihu Ubangijimu.10Ina rokon ku, yan'uwa, cikin sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu, ku yarda da juna, kada tsattsaguwa ta kasance tsakanin ku. Ina rokon ku ku zama da zuciya daya da kuma nufi daya. 11Gama mutanen gidan Kulowi sun kawo kara cewa akwai tsattsaguwa a cikin ku.12Ina nufin: kowannen ku na cewa, "Ina bayan Bulus," ko " Ina bayan Afollos," ko "Ina bayan Kefas," ko "Ina bayan Almasihu." 13Almasihu a rarrabe yake? An gicciye Bulus domin ku? Ko an yi maku baftisma a cikin sunan Bulus?14Na godewa Allah domin ban yi wa wanin ku baftisma ba, sai dai Kirisfus da Gayus. 15Na yi wannan saboda kada wani ya ce an yi maku baftisma a cikin sunana. 16(Na kuma yi wa iyalin gidan Sitifanas baftisma. Banda haka, ban sani ko na yi wa wani baftisma ba.)17Gama Almasihu bai aiko ni domin yin baftisma ba, amma domin yin wa'azin bishara. Bai aiko ni domin in yi wa'azi da kalmomin hikimar mutum ba, saboda kada giciyen Almasihu ya rasa ikonsa.18Gama wa'azin gicciye wauta ne ga wadanda su ke mutuwa. Amma cikin wadanda Allah ke ceto, ikon Allah ne. 19Gama a rubuce yake, "Zan watsar da hikimar masu hikima. Zan dode fahimtar masu basira."20Ina mai hikima? Ina masani? Ina mai muhawara na duniyan nan? Allah bai juya hikimar duniya zuwa wauta ba? 21Tunda duniya cikin hikimarta bata san Allah ba, ya gamshi Allah ta wurin wautar wa'azi ya ceci masu bada gaskiya.22Gama Yahudawa suna bidar al'ajibai, Helinawa kuma suna neman hikima. 23Amma muna wa'azin Almasihu gicciyayye, dutsen tuntube ga yahudawa da kuma wauta ga Helinawa.24Amma ga wadanda Allah ya kira, Yahudawa da Helinawa, muna wa'azin Almasihu a matsayin iko da kuma hikimar Allah. 25Gama wautar Allah tafi mutane hikima, kuma rashin karfin Allah yafi mutane karfi.26Dubi kiranku, yan'uwa. Ba dukkan ku ke da hikima a ma'aunin mutane ba. Ba dukkan ku ke da iko ba. Ba dukkan ku ke da haifuwa ta sarauta ba. 27Amma Allah ya zabi abubuwan da suke wofi na duniya domin ya kunyatar da masu hikima. Allah ya zabi abin da ke marar karfi a duniya domin ya kunyatar da abinda ke mai karfi.28Allah ya zabi abinda ke marar daraja da kuma renanne a duniya. Ya ma zabi abubuwan da ake dauka ba komai ba, domin ya wofinta abubuwan da ake dauka masu daraja. 29Ya yi wannan ne domin kada wani ya sami dalilin fahariya a gabansa.30Domin abinda Allah ya yi, yanzu kuna cikin Almasihu Yesu, wanda ya zamar mana hikima daga Allah. Ya zama adalcinmu, da tsarkinmu da fansarmu. 31A sakamakon haka, kamar yadda nassi ya ce, "Bari mai yin fahariya, ya yi fahariya cikin Ubangiji."
Bulus da Sastanisu sun rubuto wannan wasikar ne zuwa ga masubi da ke ikilisiya a Koronti.
Harshen ku na da wata hanya ta musamman na gabatar da marubucin wasika da kuma masu sauraro. AT: "Ni, Bulus, na rubuta maku wannan wasika ku a Koronti da kuke ba da gaskiya ga Allah"
Wannan ya na nuna cewa Bulus da korontiyawan sun san Sastanisu. AT: "Sastanisu ɗan'uwa da ni da ku mun sani"
Anan "keɓe" na nufin mutane wanda Allah ya shirya domin su ɗaukakka shi. AT: "ga waɗanda Yesu Almasihu ya keɓe su wa Allah" ko "ga waɗanda Allah ya keɓe ma kansa saboda su na cewa Almasihu Yesu ne"
AT: "waɗanda Allah ya kira su zama sarkaken mutane"
"sunan" na nufin Yesu Almasihu da kansa. AT: "masu kira bisa Ubangiji Yesu Almasihu"
Kalman "namu" na haɗe da masu sauraran Bulus. Yesu ne Ubangijin Bulus da Korontiyawan da kuma Ubangijin dukkan ikilisiyoyi.
Bulus ya kwatanta matsayin maibi da kuma zumunta cikin Almasihu yayin da suke jiran zuwan sa.
Bulus na magana game da bangaskiya kaman wani abu ne a bayyane wanda Yesu ya ba wa masubi kyauta. AT: "saboda Almasihu Yesu ya sa shi yiwuwa ma Allah ya yi ma ku kirki"
AT:1) "Almasihu ya ba ku arziki" ko kuma 2) "Allah Ya ba ku arziki"
Bulus ya na magana a muhimmin kalmomi. AT: "ya ba ku arziki da dukkan irin albarku na ruhaniya"
Allah ya sa ku ku gaya wa sauran game da sakon Allah a hanyoyi dayyawa.
Allah ya sa ku, ku gane sakon Allah a hanyoyi dayyawa
AT: 1) "kun gani wa kanku cewa abin da muke cewa game da Almasihu gaskiya ne" ko kuma 2) "sauran mutane sun gani daga ganin yadda yanzu ku ke rayuwa saboda abun da mu da ku muka faɗa game da Almasihu gaskiya ne."
"domin abin da na riga na faɗa gaskiya ne"
Ana iya bayana wannan da kyau. AT: "ku na da kowane baiwa ta ruhaniya"
AT 1) "lokacin da Allah zai bayyana Ubangiji Yesu Almasihu" kokuwa 2) "lokacin da Ubangijinmu Yesu Almasihu zai bayyana kan sa."
Babu wata dalilin da Allah zai hukunta ku.
"Allah zai yi komai da ya ce zai yi"
Wannan muhimmin laƙabi ne ma Yesu, Ɗan Allah.
Anan wannan na nufin su masubi, tare da maza da mata.
"sunan" na nufin Yesu Almasihu da kansa kenan. AT: "ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu"
"cewa ku yi rayuwa a cikin jituwa da juna"
"cewa kadda a samu rabe rabe a tsakaninku"
"rayuwa cikin zaman ɗaya"
Wannan na nufin 'yan gida, bayi, da sauran da ke sashin iyalin na Kulowi, mace, ne shugaba.
"ku na cikin ƙungiya da ke faɗa da junan ku"
Bulus yana bayyana yawancin halin raɓuwa yake
Bulus ya so ne ya nanata gaskiyan cewa Alamsihu ɗaya ne ba a rarrabe yake ba. "ba mai yiwuwa bane a raɓa Almasihu a yadda kuke yi ba!"
Bulus ya so ne ya nanata cewa Almasihu ne an gicciye ba Bulus ko Apollos ba. AT: "haƙiƙa ba Bulus bane wanda suka sa a mutuwa akan gicciye domin ceton ku ba!"
Bulus ya so ya nanata cewa dukkan mu mun yi baftisma a cikin sunan Almasihu. AT: "Ba a cikin sunan Bulus ne aka yi maku baftisma ba!"
"kaɗai"
Dama shi shugaban ikilisiya da ya zama mai bi.
Ya yi tafiya tare da Manzo Bulus.
"Suna" na wakilcin "iƙo." Wannan na nufin cewa Bulus bai yi ma wasu baftisma ba domin za su iya ce sun zama almajiran Bulus. AT: "waɗansunku suna gani cewa na yi maku baftisma domin ku zama almajirai na"
Wannan na nufin iyalin gidan da kuma bayi a cikin gidan da Sitifanas, na miji, ne shugaba.
Wannan na nufin cewa baftisma ba ainahin maƙasudin bisharar Bulus ba ne.
Bulus na maganan "kalmomin hikimar mutum" kaman mutane ne, gicciyen kaman kunshi, da kuma ƙarfi kaman abun da na bayyane da Yesu zai iya sa a cikin kunshi. AT: "kalmomin hikimar mutum ... kadda waɗancan kalmomin hikimar mutum su wofintar da karfin gicciyen Almasihu " ko kuma "kalmomin hikimar mutum ... kadda mutane su daina gaskanta da sako game da Yesu su kuma fara tunani cewa ina da muhimmanci fiye da Yesu"
"wa'azi a kan giciyewar" ko "sako akan mutuwan Almasihu a kan giciye"
"mara hankali" ko "wawa"
A nan "mutuwa" na nufin yanayin mutuwa ta ruhaniya.
"Allah ne na aiki da iko a cikin mu"
"Zan rikita mutane masu basira" ko kuma " Zan sa shirin da mutane masu basira suke yi ya kasa"
Bulus na nanata cewa gaskiya babu mutane masu hikima. AT: "A kwatance da hikimar bishara, babu mutane masu hikima, babu masani, babu muhawara!"
Mutumin da an ɗauke shi kaman wanda ya yi karatu sosai
Mutum da ke yin muhawara a kan abin da ya sani ko wanda de ke gwani a cikin muhawaran
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya nanata abin da Allah ya yi ma hikimar duniyan nan. AT: "Allah ya nuna cewa dukkan abin da sun kira hikma, wauta ne ta ainahi"
AT: 1) "dukkan waɗanda sun bada gaskiya a sakon" ko 2) "dukkan waɗanda sun bada gaskiya ga Almasihu."
"game da Almasihu, wanda ya mutu a bisa gicciye"
Sakon ceto ta wurin gicciyen Almasihu ya hana Yahudawa daga gaskanta da Yesu, kaman yadda mutum ke iya tuntuɓe a kan dutse a hanya. AT: "ba ƙarbabe ba" ko "laifi sosai"
"ga mutanen da Allah ya kira"
"muna koyarwa game da Almasihu" ko kuma "mu na gayawa dukkan mutane game da Almasihu"
AT: 1) "Allah ya yi hikima da iko ta wurin aika Almasihu ya mutu domin mu" ko "Ta wurin Almasihu, Allah ya nuna iko dakarfinsa"
AT: "Almasihu na da iko kuma ta wurin Almasihu ne Allah ya cece mu"
AT: "Allah ya nuna abin da ke cikin hikimar sa ta wurin Almasihu."
AT: 1) Bulus na maganar zance game da wautar Allah. Bulus ya san cewa Allah ba wawa ba ne ko na da rashin ƙarfi. AT: "Abin da ke da alaman wautar Allah tafi mutune hikima, kuma abin da ke da alaman rashin ƙarfin Allah yafi karfin mutanen" ko 2) Bulus na magana daga fanin mutanen Girka wadda su na iya tunani cewa Allah wawa ne ko mara ƙarfi. AT: "Abin da mutane ke kira wautar Allah ta fi abin da mutane ke kira hikima, kuma abin da mutane ke kira rashin ƙarfin Allah ta fi ƙarfin na mutane"
Ana iya bayana wannan da kyau. AT: "ku ƙadan"
"Abin da yawancin mutane za su kira hikima"
"musamman domin gidan ku na da muhimmi"
Bulus ya mamaita kalmomin iri ɗaya a jimla biyu da ke nufin abu ɗaya sau da dama don ya nanata bambanci sakanin yanda Allah na yin abubuwa da kuma yanda mutane ke tunani ya yi.
"Allah ya zaɓi ya yi amfani da waɗanda duniya ke gani suke da wofi don ya kunyatar da masu gani su na da hikima"
"Allah ya zaɓi ya yi amfani da waɗanda duniya ke gani mara ƙarfi domin ya kunyatar da masu gani su na da ƙarfi"
Mutanen da Allah ya ƙi su. AT: "mutane masu tawali'u da an ki su"
AT: "wanda mutane ke ɗauka da rashin daraja"
"ba komai ba. Ya yi haka domin ya nuna cewa abubuwan da a ke ɗauka da daraja wofi ne"
AT: "abubuwan da mutane sun ɗauka na da kuɗi" ko kuma "abubuwan da mutane sun ɗauka ne da girma"
"Allah ya yi wannan"
Wannan na nufin aikin almasihu a kan gicciye.
Wannan kalmomin na nufin Bulus, wanda na tare da shi, da kuma Korontiyawa.
AT: 1) "Almasihu Yesu, wanda ya bayana mana hikimar Allah" ko kuma 2) "Almasihu Yesu, wanda ya ba mu hikiman Allah."
"Idan mutum na fahariya, ya yi fahariya don girman Almasihu"
1Lokacin da na zo wurin ku, yan'uwa, ban zo da gwanintar magana ko hikima ba yayinda na yi shelar boyayyun bayanai game da Allah. 1 2Domin na kudura a zuciyata kada in san komai lokacin da nake tare da ku, sai dai Yesu Almasihu, gicciyayye.3Ina tare da ku cikin kasawa, da tsoro, da fargaba mai yawa. 4Kuma sakona da shelata basu tare da kalmomin hikima masu daukar hankali. Maimakon haka, sun zo da bayyanuwar Ruhu da iko, 5saboda kada bangaskiyarku ta zama cikin hikimar mutane, amma cikin ikon Allah.6Yanzu muna maganar hikima ga wadanda suka ginu, amma ba hikima ta duniyan nan ba, ko ta masu mulkin wannan zamani, wadanda suke shudewa. 7Maimakon haka, muna maganar hikimar Allah ta boyayyar gaskiya, boyayyar hikima da Allah ya kaddara kafin zamanin daukakarmu.8Babu wani mai mulki na zamanin nan da ya san wannan hikimar, domin inda sun gane ta a wancan lokacin, da basu gicciye Ubangijin daukaka ba. 9Amma kamar yadda yake a rubuce, "Abubuwan da babu idon da ya gani, babu kunnen da ya ji, babu zuciyar da ta yi tsammanin sa, abubuwan da Allah ya shirya wa wadanda suke kaunarsa.10Wadannan ne abubuwan da Allah ya bayyana mana ta wurin Ruhu. Gama Ruhu yana bincika komai, har ma abubuwa masu zurfi na Allah. 11Gama wanene ya san tunanin mutum, sai dai ko ruhun mutumin da ke cikinsa? Haka ma, babu wanda ya san abubuwa masu zurfi na Allah sai dai Ruhun Allah.12Ba mu karbi ruhu na duniya ba, amma Ruhun da ya zo daga wurin Allah, domin mu san abubuwan da aka bamu a sake daga wurin Allah. 13Muna maganar wadannan abubuwa da kalmomin da hikimar da mutum baza ta iya koyarwa ba, amma wadanda Ruhu ke koyar da mu. Ruhu yana fassara kalmomi na ruhaniya da hikima ta ruhaniya.14Mutum marar ruhaniya ba ya karbar abubuwan da suke daga Ruhun Allah, gama wauta suke a gareshi. Ba zai iya sanin su ba domin Ruhu ne yake bayyana su. 15Shi wanda yake mai ruhaniya yana shari'anta dukan abubuwa, amma shi baya karkashin shari'ar sauran mutane. 16"Wa zai iya sanin zuciyar Ubangiji, da zai iya ba shi umarni?" Amma mu muna da lamiri irin na Almasihu.
Bulus ya bambanta hikimar mutum da hikimar Allah. Ya nanata cewa hikima ta ruhaniya na zuwa daga Allah.
Wannan anan na nufin yan'uwa masubi, tare da maza da mata.
A lokacin da Bulus ya ce "na kudura kada in san komai " ya zuguiguita don ya nanata cewa ya kudura ya natsu da kuma koyar game da Yesu Almasihu. AT: "na kudura in koyar da komai ... sai dai Yesu Almasihu" ko "na kudura kada in koyar da komai ... sai dai Yesu Almasihu"
"Ina ziyara tare da ku"
AT: 1) "kasawan jiki" ko kuma 2) "ji kaman bazan iya yin abin da na so in yi ba."
kalmomi da na da hikima wanda mai magana na bege yasa mutane su yi ko kuma su ba da gaskiya a wani abu
Bulus ya katse ainahin muhawarar sa don ya bayana abin da ya ke nufi da "hikima" ga wanda ya so ya yi magana.
An yi amfani da kalman "Yanzu" domin a sa alama a ainahin koyarwan. Bulus ya fara bayana cewa hikiman Allah, hikiman gaskiya ne.
"Hikima" magana mai zuzzurfar ma'ana ne da ana iya bayana a siffa "dabara." AT: "yi maganan kalmomin dabara" or "yi maganan sakon dabara"
"masubi da sun ginu"
"Kafin Allah ya halice komai"
"domin a tabatar da ɗaukarmu nan gaba"
"Yesu, Ubangijin da ya isa alfarma"
Wannan ba cikakken jumla ba ne ama wadansu fasaran na sa ta cika. "abubuwan da babu idon da ya gani ... yi tsammanin; wannan ne abubuwan ... wadanda suke kaunarsa." Waɗansu ba su karasawa ama su na nuna cewa ba cikakke ba ne ta wurin amfani da su aya da waƙafi da kuma fara da aya mai zuwa kamar cigabawan wannan aya: "Abubuwan da babu idon da ya gani ... yi tsammanin ... abubuwan ... waɗanda suke kaunarsa'-"
Wanda aka riɓanya sau uku na nufin dukan sashin mutum domin a nanata cewda babu mutum da ya taba sanin abin da Allah ya shirya.
Ubangiji ya halicci abin ban mamaki a cikin sama ma wanda suke ƙaunrsa.
Bulus ya yi magana game da gaskiya akan Yesu da giccye. Idan an yi amfani da 2:9 kaman jumla da bai cika, "waɗannan ne abubuwan."
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya nanata cewa ba wanda ya san abin da mutum ke tunani sai mutumin da kansa. AT: "Ba bu wanda ya san abin da mutum yake tunani sai Ruhun mutumin"
Wannan na nufin cikin mutumin, halittar ruhaniyan sa.
AT: "Ruhu mai Tsarki ne kadai ya san zurfin abubuwan Allah"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "wanda Allah ya bamu a sake" ko "wanda Allah ya bamu ta alheri"
Ruhu mai Tsarki na bayana gaskiyar Allah ga masubi a cikin kalmomin Ruhu na kuma basu hikimar sa.
mutum da ba mai bi ba, wanda bai karɓa Ruhu mai Tsarki ba
"domin gane wannan abubuwa na neman taimakon Ruhu"
"Mai bi da ya riga ya karɓi Ruhun"
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya nanata cewa ba wanda ya san zuciyar Ubangiji. Ba wanda ke da hikima kaman Allah. AT: "Ba wanda zai iya sanin zuciyar Ubangiji, don haka ba bu wanda zai iya koya ma shi abin da bai riga ya sani ba"
1Amma ni, yan'uwa, ba zan iya magana da ku kamar mutane masu ruhaniya ba, amma kamar mutane masu jiki, kamar jarirai cikin Almasihu. 2Na shayar da ku da Madara ba da nama ba, don baku isa cin nama ba, kuma ko yanzu ma baku isa ba.3Gama har yanzu ku masu jiki ne. Muddin akwai kishi da jayayya a tsakaninku, ashe, ku ba masu jiki ba ne, kuma kuna tafiya bisa magwajin mutane? 4Domin in wani ya ce, "Ina bayan Bulus," wani kuma ya ce, "Ina bayan Afollos," ashe, ba zaman mutuntaka kuke yi ba? 5To wanene Afollos? Wanene kuma Bulus? Bayi ne wadanda kuka bada gaskiya ta wurin su, kowannen su kuwa Allah ya bashi ayyuka.6Ni nayi shuka, Afolos yayi banruwa, amma Allah ne ya sa girma. 7Don haka, da mai shukar da mai banruwan, ba komi bane. Amma Allah ne mai sa girman.8Da mai shukar, da mai banruwan, duk daya suke, kuma kowannen su zai sami nasa lada, gwargwadon aikinsa. 9Gama mu abokan aiki ne na Allah. Ku gonar Allah ne, ginin Allah kuma.10Bisa ga alherin Allah da aka bani a matsayin gwanin magini, na kafa harsashi, wani kuma yana dora gini a kai. Sai dai kowane mutum, ya lura da yadda yake dora ginin. 11Gama ba wanda ke iya kafa wani harsashin daban da wanda aka rigaya aka kafa, wato, Yesu Almasihu.12Yanzu fa in wani ya dora gini a kan harashin da zinariya, ko azurfa, ko duwatsu masu daraja, ko itace, ko ciyawa, ko tattaka, 13aikinsa zai bayyanu, domin ranar nan zata tona shi. Gama za a bayyana shi cikin wuta. Wutar kuwa zata gwada ingancin aikin da kowa ya yi.14Duk wanda aikinsa ya tsaya, zai karbi lada; 15amma duk wanda aikinsa ya kone, zai sha Asara, amma shi kansa zai tsira, sai dai kamar ta tsakiyar wuta.16Ashe, baku san ku haikalin Allah ne ba, Ruhun Allah kuma yana zaune a cikin ku? 17Idan wani ya lalata haikalin Allah, Allah zai lalata shi. Gama haikalin Allah mai tsarki ne, kuma haka ku ke.18Kada kowa ya rudi kansa. Idan wani a cikin ku na ganin shi mai hikima ne a wannan zamani, bari ya zama" wawa" domin ya zama mai hikima. 19Gama hikimar duniyar nan wauta ce a gun Allah. Gama a rubuce yake, "Yakan kama masu hikima a cin makircin su." 20Har wa yau, "Ubangiji ya san tunanin masu hikima banza ne."21haka ba sauran fariya akan mutane! Domin kuwa kome naku ne, 22Ko Bulus, ko Afollos, ko kefas, ko duniya, ko rai, ko mutuwa, ko abubuwa na yanzu, ko abubuwa masu zuwa. Duka naku ne, 23Ku kuwa na Almasihu ne, Almasihu kuma na Allah ne.
Bulus ya tunashar da masubi na Korontiyawa game da yanda suke rayuwa maimakon nuna halin zaman su a gaban Allah. Ya kuma tuna masu cewa mutumin da ya koyar da su, ba shi da muhimmi kaman Allah da ya ba da girman su.
A nan na nufin yan'uwa masubi tare da maza da mata.
mutane masu bin ruhaniya
mutane masu bin sha'awan su
An kwatanta Korantiyawa da jarirai da suna kanana da kuma fahimta. AT: "kamar ƙaramin mai bi a cikin Almasihu"
Korantiyawan na iya fahimtan gaskiya mai sauki kaman jarirai da na iya shan madara kadai. Ba su shirya sosai don su gane baban gaskiyan ba kaman jarirai masu shekaru wanda su iya cin abinci mai kauri yanzu.
Na nufin cewa ba su shirya su fahimci koyarswa mai wuya ba. AT: "haryanzu ba ku shirya ku fahimci koyarswa mai wahala game da bin Almasihu ba"
nuna hali har yanzu bisa zunubi ko sha'awa na duniya
Bulus ya na kwaɓe Korontiyawa domin halin zunubin su. Ana "tafiya" magana ne game da "hukuncin halin ku," zaban abin da ke da kyau ko mar kyau. AT: "Ya kamata ku ji kunya domin ku na yin hali bisa sha'awan zunubi kuma ku na amfani da ma'aunin mutum don ku shirya ko halin ku na da kyau ko ba bu kyau!"
Bulus ya na kwaɓen Korontiyawan. AT: "Ya kamata ku ji kunya domin ku na rayuwa irin yanda mutane marasa Ruhu su ke yi"
Bulus na nanata cewa kada Korotiyawa su bi su domin shi da Afollos ba ainahin tushen bisharan ba. AT: "ba daidai ba ne ku kafa kungiyoyi don ku bi Afollos da Bulus!" ko
Bulus na maganan kansa kaman yana magana game da wani ne. AT: "ba ni da amfani!" ko kuma "Wa ne ne ni?"
Bulus ya amsa tambayansa da cewa shi da Afollos bayin Allah ne. AT: "Bulus da Afollos bayin Allah ne, kuma kun gaskanta da Almasihu domin muna bauta ma shi"
Ana iya bayana wannan da labarin da an fahimta. AT: "Mu bayi ne ta wurin wanda ku gaskanta. Mu mutane ne kadai da Allah ya ba da aiki"
An kwatanta sanin Allah da iri da yakamata dole a shuka domin ya yi girma. AT: "Ina nan kaman wani da na shuka iri a lambu, a lokacin da na yi maku wa'azin kalmar Allah.
Kaman yadda iri na son ruwa, bangaskiya na buƙatar karin koyarswa domin ya yi girma. AT: "ya na nan kaman wanda yana banruwa a lambu, a lokacin da Afollos ya cigaba da koya maku maganar Allah"
Yadda shuke-shuke na ci gaba, haka ne bangaskiya da sani a cikin Allah na girma, na kuma zama da zurfi da kuma karfi. AT: "Amma Allah ya sa ku ku yi girma" ko "amma yanda Allah ya na sa shuke-shuke su yi girma, ya na sa ku ku yi girma ta ruhaniya"
Bulus ya ce lallei ba shi ko Afollos ne ke da alhakin girman ruhuniyan masubi ba, Ama yin Allah ne.
Anan bayar da girma na nufin sa girma. Ana iya bayana "girma" mai zuzzurfar ma'ana da fi'ilin magana. AT: "Allah ne na sa ku ku mutu"
Bulus ya yi magana game da gayawa mutane labari mai kyau da kuma koya ma wanda sun amince kamar su na shuka da yin banruwa.
AT: 1) "hadadden manufa" ko 2) "daidan muhimmanci."
adadin kuɗi da ma'aikaci na karɓa domin aikinsa.
Wannan na nufin Bulus da Afollos ba ikilisiyoyin Koronti ba.
Bulus ya ɗauki kansa da Afollos a matsayin masu yin aiki tare.
Wannan na iya nufin 1) kasancewa lambun Allah na nufin na Allah. AT: "ku na nan kaman lambu na Allah" ko kuma 2) kasancewa lambun Allah na nufin yadda Allah na sa mu mu yi girma. AT: "ku na nan kamar lambun da Allah ya na sa shi girma"
Wannan na iya nufin 1) kasancewa ginin Allah na wakilcin na Allah. "ku na nan kaman gini na Allah" ko kuma 2) kasancewa ginin Allah na wakilcin yadda Allah na sa mu mu yi zama abin da yake so. AT: "ku na nan kamar gini da Allah ya na ginawa"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "Bisa ga aikin da Allah ya bani in yi"
Bulus ya daidaita koyarwan bangaskiyansa da ceto cikin Yesu Almasihu zuwa ga kafa harsashi don gini.
Bulus na nufin mutum ko mutane da su ke koyar da Korontiyawa a lokacin kaman sun zama kafinta wanda suke gina gini a bisa harsashi
Wannan na nufin muhimmin ma'aikatan Allah. AT: "bari kowane mutum da ke bautan Allah"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "ba wanda ke iya kafa wani harsashin daban da wanda, ni Bulus, na kafa" ko kuma "na riga na kafa harsashin da kowa zai iya fafa"
Ma su gini su amfani da zinariya, ko azurfa, ko duwatsu masu daraja kamar ado a su gini. Bulus ya yi maganan abin da masu gin sukan yi a lokacin gini domin ya kwatanta abin da malamai a Korontiyawa su ke yi.
An kwatanta kanyan aiki da ana amfani a gina sabon gini da darajan ruhania da ake amfani domin gina halin mutum da kuma ayuka a zaman sa a duniya. AT: "ko mutum ya yi gini da kaya masu daraja da za su daɗe ko kuma da kaya masu arha da za su ƙone da sauri"
"duwatsu masu tsada"
AT: "Allah zai nuna wa kowa abin da mai ginin ya yi"
"Ranar" magana ne na lokacin da Allah zai yi shari'a. Zai zama kaman rana ta zo domin ta bayana abin da ya faru da dare, a lokacin da Allah ya nuna ma kowa abin da mallaman nan su yi.
Wutan Allah zai hukuta ayukan mutum da kokarin sa, kaman yanda wuta ya ke bayana ƙarfin gini ko kuma bata rashin ƙarfin sa. AT: "Allah zai yi amfani da wuta don ya nuna ingancin aikinsa"
"aiki ya daɗe" ko "aiki ya haye"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "idan wuta ya lalatar da aikin wani" ko kuma " idan wuta ya ɓata aikin wani"
Ana iya bayana isimin nan "asara" da fi'ilin "rasa." AT: "zai rasa ladan sa"
AT: "Amma Allah zai cece shi"
Bulus na kwaɓan Korontiywa. AT: "ku na yi kaman ba ku san cewa ku haikalin Allah ba ne, kuma Ruhun Allah na zaune a cikin ku!"
kada kowa ya yarda da karya cewa shi kansa na da hikima a cikin duniyan nan.
bisa ga yanda mutanen da ba su gaskanta ke yanke abin hikima
"domin mutumin ya yarda ya samu mutanen da ba su gaskanta ba su kira shi wawa"
Allah na kama mutanen da su na tunani cewa su na da fasaha na kuma amfani da dabarun su domin ya kama su.
"Ubangiji ya san cewa abinda mutanen sa masu tunani cewa suna da wayo suna shirin yi banza ne"
mara amfani
"kun zama na Almasihu, Almasihu kuma ya zama na Allah"
1Ga yadda za ku dauke mu, kamar bayin Almasihu da kuma masu rikon asiran Allah. 2Hade da wannan, ana bukatar wakilai su zama amintattu.3Amma a gare ni, karamin abu ne ku yi mani shari'a, ko a wata kotu irin ta mutane. Gama bani yi wa kaina shari'a. 4Ban sani ko akwai wani zargi a kaina ba, amma wannan bai nuna cewa bani da laifi ba. Ubangiji ne mai yi mani shari'a.5Sabili da haka, kada ku yanke shari'a kafin lokaci, kafin Ubangiji ya dawo. Zai bayyana dukkan boyayyun ayyuka na duhu, ya kuma tona nufe-nufen zuciya. San nan kowa zai samu yabonsa daga wurin Allah.6Yan'uwa, ina dora wadannan ka'idoji a kaina da Afollos domin ku, yadda ta wurin mu za ku koyi ma'anar maganar nan cewa, "kada ku zarce abin da aka rubuta." Ya zama haka domin kada waninku ya kumbura yana nuna fifiko ga wani akan wani. 7Gama wa yaga bambanci tsakanin ku da wasu? Me kuke da shi da ba kyauta kuka karba ba? Idan kyauta kuka karba, don me kuke fahariya kamar ba haka ba ne?8Kun rigaya kun sami dukkan abubuwan da kuke bukata! Kun rigaya kun zama mawadata! Kun rigaya kun fara mulki- kuma ba tare da mu ba! Hakika, marmarina shine ku yi mulki, domin mu yi mulki tare da ku. 9A tunanina, mu manzanni, Allah ya sa mu a jerin karshe kamar mutanen da aka zartar wa hukuncin mutuwa. Mun zama abin kallo ga duniya, ga mala'iku, ga mutane kuma.10Mun zama marasa wayo sabili da Almasihu, amma ku masu hikima ne a cikin Almasihu. Mu raunana ne, amma ku masu karfi ne. Ana ganin mu marasa daraja, ku kuwa masu daraja. 11Har zuwa wannan sa'a, muna masu yunwa da kishi, marasa tufafi masu kyau, mun sha kazamin duka, kuma mun zama marasa gidaje.12Mun yi fama sosai, muna aiki da hanuwanmu. Sa'adda an aibata mu, muna sa albarka. Sa'adda an tsananta mana, muna jurewa. 13Sa'adda an zage mu, muna magana da nasiha. Mun zama, kuma har yanzu an dauke mu a matsayin kayan shara na duniya da abubuwa mafi kazamta duka.14Ban rubuta wadannan abubuwa domin in kunyata ku ba, amma domin in yi maku gyara kamar kaunatattun yayana. 15Ko da kuna da masu riko dubu goma a cikin Almasihu, ba ku da ubanni da yawa. Gama ni na zama ubanku cikin Almasihu Yesu ta wurin bishara. 16Don haka, ina kira gare ku da ku zama masu koyi da ni.17Shiyasa na aiko Timoti wurin ku, kaunatacce da amintaccen dana cikin Ubangiji. Zai tunashe ku hanyoyina cikin Almasihu, kamar yadda nake koyar da su ko'ina da kowace Ikilisiya.18Amma yanzu, wadansun ku sun zama masu fahariya, suna yin kamar ba zan zo wurinku ba.19Amma zan zo gare ku ba da dadewa ba, idan Ubangiji ya nufa. Sannan zan san fiye da maganar masu fahariya, amma kuma zan ga ikonsu. 20Gama Mulkin Allah ba magana kadai ya kunsa ba, amma ya kunshi iko. 21Me kuke so? In zo wurin ku da sanda ne ko kuwa da kauna da ruhun nasiha?
Bayan da ya tuna wa mutunen cewa kada su yi takama da wadda ya koya masu game da Almasihu da kuma wadda ya yi masu baftisma, Bulus ya tunashar da masubi na Koronti cewa yakamata dukan masubi su zama bayi masu tawali'u.
Bulus ya na magana game kansa kaman ya na magana akan waɗansu mutane. AT: "Ana bukata mu zama"
Bulus ya na kwatanta bambanci sakanin hukuncin mutum da hukuncin Allah. Hukuncin mutum ba shi da muhimanci idan aka kwatanta shi da gaskiyar hukuncin Allah akan mutum.
"Ban ji wannan ya kushe ni cewa ina yin abu da ba daidai ba"
"rashin zargi bai nuna cewa bani da laifi ba. Allah ya san ko bani da laifi ko ina da laifi"
"Domin abin da na fada gaskiya ne"
Anan "bayyana dukkan boyayyun ayyuka na duhu" magana ne da na sa abubuwan da an aikata a boye sananne ga kowa. Anan "zuciya" zance ne akan tunani da nufin mutum. AT: "Kamar haske da ya na haskaka a kan abubuwa a cikin duhu, Allah zai bayyana abin da mutane sun aikata a duhu da kuma abin da sun shirya a asirce"
Wannan na nufin masubi, tare da maza da mata.
"domin amfanin ku"
Bulus ya na magana da Korontiyawa kamar sun zama mutum daya.
Bulus ya na tsawata wa Korontiyawa da suke tunani cewa sun fi wadanda sun ji bishara daga wani dabam. AT: "Gama babu bambamci a sakanin ku da wadansu." ko kuma "Gama ba ku gaba da waɗansu mutanen."
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya nanata cewa basu samu abin da suke da shi don ladan aikinsu ba. AT: "Dukan abin da kuke da shi, kyuata ne da kun karɓa." ko kuma "Allah ya ba ku komai da kuke da shi kyauta!"
Bulus ya na tsawata masu domin yin fahariya da abin da suke da shi. AT: "kadda ku yi fahariya kaman ba ku yi haka ba." ko kuma "ba ku da iƙon yin fahariya!"
Jumlan "yi haka" na nufin karɓan abin da suke da shi a kyauta. AT: "kamar yadda ba ku karɓa a kyauta ba" ko kuma "kamar kun samu don ladan aikin ku"
Bulus ya yi magana anan domin ya kunyatar da Korontiyawan, ya kuma sa su su gane cewa zunubi ne su na yi a loƙacin da suna takama da junansu da kuma mallamansu.
Bulus ya bayana hanyoyi biyu da Allah ya sa manzannin sa a gwaji domin duniya su gani.
Allah ya gwada manzanninsa kamar yadda fursuna a karshen farati na sojojin Romawa, wadda a na ci masu mutunci da su kafin a yi masu kisa.
Allah ya sa manzannin a gwaji kamar wadda za a ci masu mutunci.
AT: 1) "duniya" na da abin da ya wuce iƙon ɗan-adam
Bulus ya yi amfani da maganan domin ya kunyatar da Korontiyawan don su yi tunanin abin da yake faɗa.
"Mutuane suna na yi maku Korontiyawa kaman ku mutane masu muhimmanci"
"Mutane na kunyatar da mu manzanni"
"Har yanzu"
Wannan na nufin bugawa da hanu, ba da bulala ko kulki ba. AT: "mutane sun duke ne"
Bulus na nufin cewa su na da wuraran zama, amma sun kewaye wurare dabam dabam. Ba su da kafaffiyar gida.
AT:"Loƙacin da mutane na aibata mu, mun sa masu albarka" ko kuma " "Loƙacin da mutane na raina mu, mun sa masu albarka"
AT: "Loƙacin da mutane ke tsananta mu"
AT: "Loƙacin da mutane ke kushe mu"
"Mutane sun fara ɗaukan mu--kuma har yanzu su na ɗaukan mu--zama datti na duniya"
"Ban yi niya in kunyata ku ba, amma domin in kara gyara ku" ko kuma "ba wai ina kokarin kunyatar da ku bane, amma ina so in gyara ku ne"
faɗa ma wani cewa abin da suke aikatawa ba daidai bane kuma zai sa mugun abu ya faru
Wannan magana ne akan lamban mutanen da ke lura da su, domin a nanata muhimmin Uba daya na ruhaniya.AT: "yawan wakilai" ko kuma "babban tarun wakilai"
Domin Bulus ya bi da su zuwa ga Almasihu, ya na nan kamar Uba ne a wurin Korontiyawan
A farko, Bulus na natata cewa ɗangantakansa da Korontiyawa na da muhimmi a "cikin Almasihu", na biyu domin ya zo saboda ya faɗa masu game da bisharan, na uku na cewa shine a wadda yake kamar Uba a gare su. "saboda Allah ya hada ku ga Almasihu a loƙacin da na faɗa maku game da labari mai kyau cewa ni ne na zama Uban ku"
"Wadda ina ƙauna, wadda na koyar game da Almasihu kaman dana ne"
Wannan kalma na nuna cewa Bulus ya na canja batunsa domin ya tsautawa halin girman kai na masubi a Koronti.
"zan ziyarce ku"
Bulus ya na yin roko na karshe ga Korontiyawa, yadda ya saba tsautawa masu game da kuskuren da sun yi. AT: "fada mani abin da ku na so ya faru yanzu"
Bulus ya na ba wa Korontiyawa halaya biyu da suke gaba da juna wanda zai iya yin amfani da shi a gabatar da su. AT: "Idan ku na so, zan iya zuwa in hukunta ku, ko kuma zan iya zuwa don in nuna maku yadda ina kaunar ku ta kasancewa da hankali da ku"
"na alheri" ko kuma "na taushi"
1Mun ji cewa akwai lalata mai kazanta a cikin ku, irin lalatar ba ba a yarda da ita ba ko a cikin al'ummai. Labarin da na samu shine, wani daga cikin ku yana kwana da matar mahaifinsa. 2Kuma kuna fahariya sosai! Ba bakinciki ya kamata ku yi ba? Shi wanda ya yi haka, dole a fitar da shi daga cikin ku.3Gama Kodashike ba ni tare da ku cikin jiki, amma ina tare daku a ruhu, na rigaya na hukunta wanda yayi wannan, tamkar ina wurin. 4Lokacin da ku ka taru a cikin sunan Ubangijinmu Yesu, ruhuna yana nan tare da ku cikin ikon Ubangiji Yesu, na rigaya na hukunta wannan mutum. 5Na yi haka ne domin in mika wannan mutum ga Shaidan domin a hallaka jikin, don ruhunsa ya tsira a ranar Ubangiji.6Fahariyarku bata yi kyau ba. Ko baku sani ba yisti dan kadan ya kan bata dukan dunkule? 7Ku tsarkake kan ku daga tsohon yisti domin ku zama sabon dunkule, wato gurasar da ba ta da yisti. Gama an yi hadayar Almsihu, dan ragonmu na idi. 8Don haka, bari mu yi idinmu ba da tsohon yisti ba, wato yisti irin na rashin tabi'a da mugunta. Maimakon haka, bari muyi bukin idi da gurasa marar yisti ta aminci da gaskiya.9Na rubuta maku a cikin wasikata cewa kada ku yi hudda da fasikan mutane. 10Ba ina nufin fasikan mutane na wannan duniya ba, ko masu zari, ko 'yan'damfara, ko masu bautar gumaka, tunda kafin ku rabu da su sai kun bar wannan duniya.11Amma yanzu ina rubuta maku cewa kada ku yi hudda da duk wanda ake kira dan'uwa amma yana zama cikin fasikanci, ko zari, ko bautar gumaka, ko in shi mai ashar ne, ko mashayi, ko dan'damfara. Kada ko abinci ku ci da irin wannan mutum. 12Domin ta yaya zan iya shar'anta wadanda ba 'yan Ikklisiya ba? Maimakon haka, ba ku ne zaku shar'anta wadanda ke cikin ikilisiya ba? 13Amma Allah ke shar'anta wadanda ke waje. "Ku fitar da mugun mutumin daga cikin ku."
Bulus ya bayana game da irin zunubansu da ya ji, da kuma yadda masubi na Korontiyawan su na fahariya da amincewan su game da mutumin nan da zunubinsa.
AT: "cewa, ko Al'ummai ba su yarda ba"
"kwana da" magana ne na "yin zina da" AT: wani daga cikin ku na yin zina da"
matar Ubansa, amma mai yuwuwa ba Uwarsa ba
Ana amfani da wannan tambayan domin a tsawta Korontiyawan. AT: "maimako ku yi bakinci akan wannan!"
AT: "Dole ne ku fitar da wanda ya yi wannan a sakaninku"
"ina nan da ku a ruhu." Zama tare da su a ruhu na wakilcin kula da su ko kuma son zama tare da su. AT: "Ina kula da ku" ko kuma "Ina so in zauna da ku"
AT: 1) "na riga na yanke abin da za ku yi ma wadda ya yi wannan" ko kuma 2) "na samu mutumin da ya yi wannan laifin"
"loƙacin da ku na tare" ko kuma "loƙacin da kun hadu tare"
suna iya nufin 1) sunan Ubangiji Yesu magana ne da ke walkincin ikon sa. AT: "da iƙon Ubangiji Yesunmu" ko kuma 2) taruwa a cikin sunan Ubangiji na nufin saduwa domin yin masa sujada. AT: "domin yin sujada wa Ubangijinmu Yesu"
miƙa mutumin ga Shaidan na wakilcin rashin yarda wa mutumin ya kasance a kungiyan su domin shaidan ya iya yin masa lahani. AT: "sa wannan mutumin ya bar kungiyan ku domin Shaidan ya iya yi masa lahani"
Suna iya nufin 1) na nufin "jikin" sa. AT: "domin Shaidan ya lahata jikinsa" ko kuma 2) "jiki" magana ne na halin mutuntaka. AT: "domin a halaƙar da halin mutuntakansa" ko kuma "domin kada ya ci gaba da rayuwa a bisa halin mutuntakarsa"
AT: "domin mai yiwuwa, Allah ya cece ruhunsa a ranar Ubangiji"
"Fahariyarku babu kyau"
yadda ana shafa yisti dan kadan a dukan dukulen burodi, haka ne zunubi kadan na shafi duka zumuntar masubi.
Kamar yadda ragon idi na rufe zunuban Isra'ila ta wurin bangaskiya a kowane shekara, haka ne mutuwar Almasihu ya rufe zunuban dukan wadanda sun gaskanta da shi ta wurin bangaskiya na madauwami. AT: "Ubangiji ya yi hadayar Almasihu, ragon idinmu"
Wannan na nufin mutanen da sun gaskanta da Almasihu amma su na wannan ayukan.
mutanen da sun zaba su yi rayuwan fasikanci, wadda ba masubi ba
"waɗanda su ke da haɗama" ko kuma "waɗanda su ke so su zama marasa adalci domin su samu abin da wadansu ke da shi"
Wannan na nufin mutanen da suke yaudara don su samu kayan wadansu.
"yakamata ku guje duka mutane"
"duk wanda ya kira kansa"
Wannan na nufin maibi, namiji ko na mace.
Bulus ya na nanata cewa ba shi ne zai shar'anta mutanen wadanda ba 'yan Ikklisiya ba. AT: "Ba ni ba ne yakamata in shar'anta mutane waɗanda ba na Ikklisiya ba"
Bulus ya na yi ma Korontiyawan tsawa. "ku san cewa ku ne yakamata ku shar'anta wadanda ke cikin ikilisiya"
1Idan wani a cikin ku yana jayayya da wani, to sai ya tafi kotu gaban alkali marar bada gaskiya, a maimakon gaban masu bi? 2Ko ba ku sani ba, masubi ne za su yiwa duniya shari'a? Kuma idan ku za ku yi wa duniya shari'a, sai ku kasa sasanta al'amura marasa mahimmanci? 3Baku sani ba mu za mu yiwa mala'iku shari'a? Balle shari'ar al'amuran wannan rai?4Idan kuna shar'anta al'amuran yau da kullum, don me ku ke kai irin wadannan matsaloli gaban wadanda ba 'yan ikilisiya ba? 5Na fadi wannan domin ku kunyata. Babu wani mai hikima a cikin ku ko daya da zai iya sasanta gardama a tsakanin 'yan'uwa? 6Amma kamar yadda yake, mai bi ya na kai karar mai bi a kotu, kuma a gaban mai shari'a wanda ba mai bi ba!7Kasancewar rashin jituwa a tsakanin Kirista na nuna cewa kun rigaya kun gaza. Don me ba za ka shanye laifi ba? Don me ba za ka yarda a kware ka ba? 8Amma kun yi wa wadansu laifi kun kuma cutar su, su kuwa 'yan'uwanku ne!9Ba ku sani ba marasa adalci ba za su gaji Mulkin Allah ba? Kada ku gaskata karya. Da fasikai, da masu bautar gumaka, da mazinata, da karuwai maza, da masu ludu, 10da barayi, da masu zari, da mashaya, da masu zage-zage, da 'yan damfara - ba waninsu da zai gaji Mulkin Allah. 11Kuma da haka wadansu a cikinku suke, amma an tsarkake ku, an mika ku ga Allah, an maida tsayuwar ku dai-dai a gaban Allah a cikin sunan Ubangji Yesu Almasihu, kuma ta wurin Ruhun Allahnmu.12Dukkan abu halal ne a gare ni", amma ba kowanne abu ne mai amfani ba. "Dukan abu halal ne a gare ni," amma ba zan yarda wani abu ya mallake ni ba. 13"Abinci don ciki ne, kuma ciki don abinci ne", amma Allah za ya kawar da su duka. Ba a yi jiki saboda fasikanci ba. Maimakon haka, jiki don Ubangiji ne, kuma Ubangiji zai yi wa jiki tanaji.14Allah ya tada Ubangiji, kuma za ya tashe mu ta wurin ikonsa. 15Ba ku sani ba jikunanku gabobi ne na Almasihu? Na dauki gabobin Almasihu in hada su da karuwa? Allah ya sawwake!16Ko baku sani ba dukan wanda yake hade da karuwa, ya zama jiki daya da ita kenan? 17Kamar yadda Littafi ya fadi, "Su biyun za su zama nama daya." Amma wanda yake hade da Ubangiji ya zama ruhu daya da shi kenan.18Ku gujewa fasikanci! Kowane zunubi mutum yake aikatawa a waje da jikinsa yake, amma mutum mai fasikanci yana zunubi gaba da jikinsa.19Ba ku sani ba jikinku haikali ne na Ruhu Mai-tsarki, wanda yake zaune a cikinku, wanda ku ka samu daga wurin Allah? Ba ku sani ba cewa ku ba na kanku ba ne? 20An saye ku da tsada. Don haka, ku daukaka Allah da jikin ku.
Bulus ya kuma bayana yadda masubi za su shirya saɓani da suaran masubi.
saɓani ko kuma muhawara
Bulus ya na nanata cewa dole ne masubi su tsai da saɓani a sakanin su. AT: "kar ya yi karfin halin tafiya ... masubi!" ko kuma "ya ji tsoron Allah, kadda ya tafi ... masubi!"
wurin da alkalin karamar hukuman gwamnati na duba magana da kuma tsai da mai daidai.
Bulus ya na kunyatar da Korontiyawan domin yadda su na aikatawa kamar basu sani ba .
Domin za a basu baban aiki nan gaba, yakamata su dauki nauyin abubuwa kadan yanzu. AT: "za ku yi wa duniya shari'a a loƙaci gaba, yakamata ku sasanta wannan al'amura yanzu."
"daina muhawara game da abubuwan wannan rai"
Bulus ya na mamaki cewa ba su da alaman sani. AT: "kun san cewa za mu yiwa mala'iku shari'a."
Bulus ya sa kansa da Korontiyawan.
Domin za a basu baban aiki nan gaba, yakamata su dauki nauyin abubuwa kadan yanzu. AT: "Domin za mu yi wa mala'iku shari'a, ya kamata mu san cewa Allah zai sa mu mu yi shari'ar a'lamarin wannan rai."
AT: 1) " wannan tambayane ko kuma 2) wannan bayani ne, "a loƙacin baya da kun sasanta al'amura da ke da muhimminci a wannan rayuwan, ba ku watsar da gardama a sakanin masubi da ya kamata marasabi ne sun sasanta ba" ko kuma 3) wannan umurni ne, "loƙacin da kun sasanta al'amura da suke da muhiminci a wannan rayuwan, na waɗanda ba su da ...a cikin ikilisiya cewa wai ku sasanta al'amuran!"
"Idan an kira ku domin ku daidata game da rayuwa na kulum" ko kuma "Idan dole ne ya kamata ku sasanta al'amuran da ke da muhiminci a wannan rayuwan"
Bulus ya na sawta ma Korontiyawa game da yadda suke sasanta maganganun nan. AT: 1) "ku daina ba da maganganun nan ga mutanen da yan ikilisiya ba." ko kuma 2) "za ku iya ba da maganganun nan wa membobin ikilisiya wadda sauran masubi ba su dauke su komai ba."
"domin rashin mutuncin ku" ko kuma "domin ya nuna yadda kun kasa a wannan al'amarin"
Bulus ya na kunyatar da Korontiyawan. AT: "yakamata ku ji kunyar domin ba ku iya samu mai bi da hikiman da zai sasanta jayayya a sakanin masubi"
Anan na nufin 'yan'uwa masubi tare da maza da mata.
"Ama yadda yake yanzu" ko kuma "Ama maimako"
"masubi wadda suna da gardama da junansu su na tambayan mai shari'a wanda ba mai bi ba ya yi masu hukunci"
AT: "mai bi ya yarda da maganan"
"ya na da rashin cin nasara"
Bulus ya cigaba da kunyatar da Korontiyawan. AT: "zai zama mafi kyau idan kun bar waɗansu su yi maku laifi da kuma cuce ku, da ku kai su kotu."
Dukan masubi a cikin Almasihu 'yan'uwan juna ne. "'yan'uwanku masubi"
Bulus ya nanata cewa yakamata su san wannan gaskiyar. AT: "kun riga ku san cewa"
Karɓan abin da Allah ya yi ma masubi alkawari na nan ne kamar gaje kaya da dukiya daka ɗan iyali.
Allah ba zai hukunta su kamar masu adalci a shari'an ba, kuma ba za su shiga rai mai dawami ba.
AT: 1) "magana ne game da ayukan ludu ko kuma 2) "Bulus ya na sa sunayen ayuka dabam dabam ne.
AT: 1) mazaje da suke yarda wadansu mazaje su kwana da su ko kuma 2) mazaje da suke yarda wadansu mazajen su biya su domin su kwana da su ko kuma 3) mazaje da suke yarda waɗansu mazaje su kwana da su a masayin ayukan addini.
mazaje da suke kwuna da waɗansu mazajen
mutanen da suke sata daga waɗansu
mutanen da suke da niyan yin amfani da mugun hanya domin su ɗauki kayan waɗansu
mutanen da suke sata daga waɗanda sun yarda da su
AT: "Allah ya wanke ku"
AT: "Allah ya keɓe ku wa kansa"
AT: "Allaha ya daidaita ku da shi"
Anan "suna" magana ne game da ƙarfi da ikon Yesu Almasihu. AT: "ta wurin ƙarfi da ikon Ubangji Yesu Almasihun mu"
AT: 1) Bulus ya na amsa abin da waɗansu Korontiyawan za su iya yin tunani, "waɗansu sun ce, 'zan iya in yi komai" ko kuma 2) Bulus ya na faɗan abin da ya ke tunani cewa daidai ne, "Allah ya yarda ma ni in yi komai."
Bulus ya na amsa wadda a ce, "kowanne abu halal ne a gare ni." AT: "amma ba kowanne abu ne ya ke da kyau a gare ni ba"
AT: "ba zan yarda wadanan abubuwa su yi mulki a kai na kamar maigida ba"
AT: 1) "Bulus ya na gyara abin da waɗansu Korontiyawan za su iya yin tunani, "abinci don ciki, kuma ciki don abinci ne," ta wurin amsa cewa Allah zai kawar da cikin da kuma abincin duka ko kuma 2) Bulus ya yarda cewa "abinci don ciki, kuma ciki don abinci ne," amma ya kara cewa Allah zai kawar da su duka.
Wannan na iya nufin cewa mai maganan na magana game da jiki da kuma jima'i, amma ku fasara wannan kamar "ciki" da "abinci."
"hallaƙa"
"sa Ubangiji ya rayu kuma"
Kalman da an fasara kamar "gabobi" na nufin sashi na jiki. An yi maganan kasancewan mu da Almasihu kaman muna cikin jikinsa. Mun zama na shi sosai, har jikinmu ya zama na shi. Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya tuna wa mutanin game da abin da yakamata sun sani. AT: "Ku san cewa jikin ku na Almasihu ne"
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya nanata yadda ba kyau wanin da ya zama na Almasihu ya je wurin karuwa. AT: "Ina cikin Almasihu. Ba zan ɗauka jiki na in hadda da karuwa ba!" ko kuma "Mu na cikin jikin Almasihu. Ba lalai ba ne mu ɗauki jikinmu mu hadda da karuwa ba!"
"Kadda wancan ya faru!" ko kuma "kadda mu yi haka!"
Bulus ya fara koyar da Korontiyawan ta wurin nanata gaskiyan da sun riga sun sani. "Ina so in tuna maku cewa ... ita."
AT: "a loƙacin da na miji a haɗa jikinsa da jikin karuwa, yana nan kamar jikinsu ya zama jiki ɗaya"
AT: "a loƙacin da Ubangiji ya hada ruhunsa da ruhun mutum, yana nan kamar ruhohin sun zama ruhu ɗaya"
Bulus na magana game da mutum da ke kin zunubin fasikanci kamar mutumin ya na gudun hatsari. AT: "tashi daga"
Su na iya nufin 1) Bulus ya na nuna cewa zunubin fasikanci ba bu kyau domin yana gaba da jikin mai zunubi da kuma waɗansu. ko kuma 2) Bulus ya na faɗan abin da waɗansu Korontiyawan suke tunani. AT: "fasikanci! Waɗansunku na ce, 'kowane zunubin da mutum ya yi na wajen jiki; amma na ce"
"mugun ayuka da mutum yake yi"
Bulus ya cigaba da koyar da Korontiyawan ta wurin nanata abin da sun riga sun sani. AT: "Ina so in tuna maku ... Allah, cewa ku ba na kanku ba ne."
jikin kowane mai bi haikali ne na Ruhu mai Tsarki
Wani haikali aka sadaukar domin Allahntaka, kuma wurin ne suke zama. A haka, jikin kowane mai bi na Koronti ya na nan kamar haikali ne domin Ruhu mai Tsarki na nan a sakaninsu.
Allah ya biya wa yancin Korontiyawa daga bautar zunubi. AT: "Allah ya biya wa yancinku"
"domin abin da na faɗa daidai ne"
1Game da abubuwan da kuka rubuto: "Yayi kyau ga mutum kada ya taba mace." 2Amma Saboda jarabobi na ayyukan fasikanci masu yawa, ya kamata kowane mutum ya kasance da matarsa, kowace mace kuma ta kasance da mijinta.3Kowanne maigidanci ya ba matarsa hakin ta, kuma kowace mace ta ba maigidan ta hakinsa na saduwa da juna. 4Matan ba ta da iko akan jikin ta amma maigidan ne. Haka ma, maigidan bashi da iko akan jikinsa amma matar ce.5Kada ku hana wa junanku saduwa, sai dai da yardar junanku domin wani dan lokaci. Kuyi haka domin ku bada kanku ga addu'a. Daganan sai ku sake saduwa, domin kada Shaidan ya jarabce ku saboda rashin kamun kanku. 6Amma ina fada maku wadannan abubuwa ne a matsayin nuni, ba a matsayin umurni ba. 7Na so da kowa da kowa kamar ni yake. Amma kowa na da baiwarsa daga wurin Allah. Wani na da irin wannan baiwar, wani kuma waccan.8Ga marasa aure da gwamraye, Ina cewa, yana da kyau a garesu su zauna ba aure, kamar yadda nike. 9Amma idan baza su iya kame kansu ba, ya kamata su yi aure. Gama yafi masu kyau su yi aure da su kuna da sha'awa.10Ga masu aure kwa, ina bada wannan umarni- ba ni ba, amma Ubangiji: "Kada mace ta rabu da mijinta." 11Amma idan har ta rabu da mijinta, sai ta zauna ba aure ko kuma ta shirya da shi. Haka kuma " Kada miji ya saki matarsa."12Amma ga sauran ina cewa-Ni, ba Ubangiji ba-idan wani dan'uwa yana da mata wadda ba mai bi ba, kuma idan ta yarda ta zauna da shi, to kada ya sake ta. 13Idan kuwa mace tana da miji marar bi, idan ya yarda ya zauna tare da ita, to kada ta kashe aure da shi. 14Gama miji marar bada gaskiya ya zama kebabbe saboda matarsa, sannan mata marar bada gaskiya ta zama kebbiya saboda mijinta mai bi. In ba haka ba 'ya'yanku za su zama marasa tsarki, amma a zahiri su kebabbu ne.15Amma idan abokin aure marar bi ya fita, a bar shi ya tafi. A irin wannan hali, dan'uwa ko 'yar'uwa ba a daure suke ga alkawarinsu ba. Allah ya kira mu da mu zauna cikin salama. 16Yaya kika sani, ke mace, ko za ki ceci mijinki? ko yaya ka sani, kai miji, ko za ka ceci matarka?17Bari dai kowa ya yi rayuwar da Ubangiji ya aiyana masa, kamar yadda Allah ya kirawo shi. Wannan ce ka'idata a dukkan ikilisiyu. 18Mutum na da kaciya sa'adda aka kira shi ga bada gaskiya? Kada yayi kokarin bayyana kamar marar kaciya. Mutum ba shi da kaciya sa'adda aka kira ga bangaskiya? To kada ya bidi kaciya. 19Gama kaciya ko rashin kaciya ba shine mahimmin abu ba. Mahimmin abu shine biyayya da dokokin Allah.20Kowa ya tsaya cikin kiran da yake lokacin da Allah ya kira shi ga bada gaskiya.21Kai bawa ne lokacin da Allah ya kirawo ka? Kada ka damu da haka. Amma idan kana da zarafin samun 'yanci, ka yi haka. 22Domin wanda Ubangiji ya kira shi lokacin da yake bawa, shi 'yantacce ne na Ubangiji. Hakanan kuma, wanda shike 'yantacce lokacin da aka kira shi ga bada gaskiya, Bawan Almasihu ne.23An saye ku da tsada, donhaka kada ku zama bayin mutane. 24Yan'uwa, a kowace irin rayuwa kowannenmu ke ciki lokacin da aka kira mu ga bada gaskiya, bari mu tsaya a haka.25Game da wadanda basu taba aure ba, ba ni da wani umarni daga wurin Ubangiji. Amma ina bada ra'ayina kamar mutum wanda, ta wurin jinkan Allah, yake yardajje.26Don haka, Ina ganin saboda yamutsin dake tafe ba da jimawa ba, ya yi kyau mutum ya zauna yadda yake.27Kana daure da mace? Kada ka nemi 'yanci daga gare ta. Baka daure da mace? Kada ka nemi auren mace. 28Amma idan ka yi aure, ba ka yi zunubi ba. Kuma idan mace marar aure ta yi aure, bata yi zunubi ba. Saidai su wadanda suka yi aure za sha wahalhalu iri-iri a yayinda suke raye, kuma ina so in raba ku da su.29Amma wannan nike fadi ya'nuwa: lokaci ya kure. Daga yanzu, bari wadanda suke da mata suyi rayuwa kamar basu da su. 30Masu kuka su zama kamar marasa kuka, masu farinciki kamar marasa farinciki, masu sayen abubuwa kamar marasa komai. 31Wadanda suke harka da duniya kamar ba su harka da ita, domin ka'idar duniyan nan tana kawowa ga karshe.32Ina so ku kubuta daga damuwa mai yawa. Mutum marar aure yana tunani akan al'amuran Ubangiji, yadda zai gamshe shi. 33Amma mai aure yana tunani akan al'amuran duniya, yadda za ya gamshi matarsa, 34hankalinsa ya rabu. Mace marar aure ko budurwa tana tunanin al'amuran Ubangiji, yadda za ta kebe kanta a jiki da ruhu. Amma mace mai aure tana tunanin al'amuran duniya, yadda za ta gamshi mijinta.35Ina fadar wannan domin amfaninku ne, ba domin in takura ku ba. Na fadi wannan domin abinda ke daidai, yadda zaku bi Ubangiji ba tare da hankalinku ya rabu ba.36Amma idan wani yana tunani da cewa baya yin abinda ya dace ga budurwarsa- idan ta wuce shekarun aure, kuma hakan ya zama dole- sai yayi abinda yake so. Ba zunubi yake yi ba. Sai suyi aure. 37Amma idan ya tsaya da karfi a zuciyarsa, idan baya shan wani matsi kuma yana iya kame kansa, har ya kudurta a zuciyarsa yayi haka, wato ya kiyaye budurwarsa da yake tashi, to hakan ya yi daidai. 38Don haka, shi wanda ya auri budurwarsa yayi daidai, sannan shi wanda ya zabi yaki yin aure yafi yin daidai.39Mace tana a daure ga mijinta a duk tsawon rayuwarsa. Amma idan mijin ya mutu, tana da 'yanci ta auri duk wanda take so ta aura, amma a cikin Ubangiji. 40Amma a ganina, za ta fi farinciki idan za ta zauna yadda take. Kuma ina tunanin ni ma ina da Ruhun Allah.
Bulus ya ba masubi takamaiman dokoki game da aure.
Bulus ya na gabatar da sabon batu a cikin koyaswarsa.
Korontiyawa sun rubuto wasika wa Bulus don su tambaye shi game da amsoshi akan waɗansu tambayoyin.
AT: 1) Bulus ya na faɗan abin da Korontiyawa sun rubuto, "game da: kun rubuto, ' 'Yayi kyau wa na miji kada ya taɓa mace.' gaskiya ne, amma saboda" ko kuma 2) Bulus ya faɗa abin da ya na tunani, "game da: amsa na shi ne i, ya na da kyau kaɗa na miji ya taɓa mace. Amma Saboda"
"ya na da taimako sosai"
AT: 1) "na miji" na nufin na miji mai aure. AT: "mai gida" ko kuma 2) "na miji na nufin kowane mutum.
Su na iya nufin 1) "taɓa mace" magana ne game da yin jima'i. AT: "kada ya yi jima'i da matar sa a dan loƙaci" ko kuma 2) "taba mace" magana ne game da aure. AT: "kada ya yi aure"
"Amma saboda Shaidan yana jarabtan mutane don su yi fasikanci, kowane" ko kuma "Amma mu na so mu yi fasikanci saboda zunubi, don kowane"
An umurta cewa ya kamata mazaje da mataye su ringa kwuana da abokan aurensu.
An riga an gane kalmomin "ya ba" da "hakin saduwa da juna" a jumla da ya wuce. AT: "haka kuma, kowace mace ta ba maigidan ta hakinsa na saduwa da juna"
Kalman "ƙi" na nufin hana wani abin ya ke da yancin karbawa. "Kada ku ki saduwa da abokan aurenku"
domin ku iya samu loƙacin addu'a mai zurfi
"danƙa kanku"
"kwana tare kuma"
"domin bayan wadansu kwanaki, sha'awar ku zai fi karfin ku"
AT: Bulus ya na faɗa wa Korotiyawan cewa ya na barin su ne, ba wai ya na umurtasu ba ne, 1) don yin aure da kuma kwana tare ko kuma 2) don daina kwana tare na dan loƙaci.
Ko Bulus bai taɓa aure ba ko kuma matanshi ta mutu. Da shakka ne idan ya taba yin saki.
"Allah ya na sa mutane su yi abubuwa dabam dabam. Ya na sa mutum daya ya yi abu ɗaya, ya na kuma sa wani ya yi wani abu dabam"
"wannan waɗanda ba su yi aure ba ne"
"ga matayen da mazajensu sun mutu"
"domin rayuwa a cikin son marmarin kwana da wani kullum"
Ma su sauraran Bulus ba su san bambancin rabu wadda saki ba. Daina zama da wani na nufin kashe aure. AT: "kaɗa ku saka"
AT: "ta sasanta da mijinta, ta kuma koma mashi"
Ma su sauraran Bulus ba su san bambancin rabu wada saki ba. Aikata wannan shi kashe aure. AT: "kada ku rabu daga"
"isa"
AT: 1) "Gama Allah ya kebe miji marar bada gaskiya wa kansa saboda matarsa da ta bada gaskiya" ko kuma 2) "Allah ya na yi ma miji mara bada gaskiya kamar yadda zai yi wa ɗa saboda matarsa wadda ta bada gaskiya"
waɗannan ne kalmomin Greek na "miji" da "mace."
Su na iya nufin 1) "Allah ya keɓe mata marar bada gaskiya wa kansa saboda mijinta da ya bada gaskiya" ko kuma 2) "Allah ya na yi ma mata mara bada gaskiya kamar yadda zai yi wa 'ya saboda mijinta wadda ya bada gaskiya"
na miji ko mai gida da ya ba da gaskiya
AT: 1) Allah ya kebesu wa kansa" ko kuma 2) "Allah ya yi masu kamar yadda zai yi wa 'ya'yansa"
Anan "ɗan'uwa" da "'yar'uwa" na nufin mata da miji masubi. Anan "ɗaure suke ga alkawarinsu" magana ne da ke nufi cewa ba a tilas'a mutumin ya yi abin da sun yi alkawari cewa za su yi ba. AT: "A irin wannan halin, Allah ba ya bukutan mai aure da ya gaskanta ya cigaba da bin alkawarin aure"
Bulus ya na magana da Korontiyawan kamar su mutane daya ne, duka misalai na "ku" daya ne.
Bulus ya yi amfani da tambayan domin ya sa mata su yi tunani da zurfi game da abin da yake faɗa. AT: "baza ki san ko za ki cece mijin ki da bai gaskanta ba."
Bulus ya yi amfani da tambayan domin ya sa maza su yi tunani da zurfi game da abin da yake faɗa. AT: "baza ka san ko za ka cece matar ka da bata gaskanta ba."
"ko wane mai bi"
Bulus ya na koyar da masubi a dukkan ikilisiyu don su aikata a wannan hanya.
Bulus yana magana da masu kaciya
Yanzu Bulus yana magana da marasa kaciya. AT: "Ga marasa kaciya, A loƙacin da Allah ya kira ku ku gaskanta, ba ku yi kaciya ba"
Anan, kalmomin "mu" na nufin dukan masubi tare da masu sauraran Bulus.
Anan " kira" na nufin aiki ko masayi da ku ke ciki. AT: "yi rayuwa da aiki yadda ku ke yi"
Bulus ya na magana da Korontiyawa kaman su ɗaya ne, duka misalai na "ku" da umurnin "zama" daya ne.
AT: "ga waɗanda su bayi ne a loƙacin da Allah ya kira ku ku gaskanta, na faɗa wannan: kada ka damu"
Allah ya yafe wannan 'yantaccen mutum, don haka yana da salama daga Haidan da zunubi.
AT: "Almasihu ya saye ku ta wurin mutuwa domin ku"
Anan, wannan na nufin yanuwa masubi tare da maza da mata.
AT: "A loƙacin da Allah ya kira mu mu gaskanta da shi"
Bulus bai san koyarwa game da Yesu da ya yi magana akan yanayin nan ba. AT: "Allah bai umurce ni in faɗa wani abu game da mutanin da basu taba yin aure ba"
"Na faɗa maku abin da nake tunani"
"domin, ta wurin jinkan Ubangiji, Ina yardajje"
Bulus ya na magana da Korontiyawan kaman ya na magana ne da kowane mutum, waɗannan misalai "ku" da " da kuma umurnin "kadda ku nema" daya ne. Ka na auren mata ne? Kada ... Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya bayana yanayi mai yiwuwa. Ana iya fasara tambayan kamar jumla tare da "idan."Idan kun yi aure, kada"
"kada ka kuskura ka sake ta" ko kuma "ka gwada rabuwa da ita"
"kada ka kuskura yin aure"
Kalman"wannan" na nufin irin damuwa ta duniya da masu aure ke iya samu. AT: "Ina so in taimake ku don kada ku samu damuwa ta duniya"
"Akwai ƙanƙanin loƙaci" ko kuma "Loƙaci ya yi kusan tafi"
yi kuka ko bakin ciki da hawaye
"waɗanda suke harka kullum da marasa bi"
"su nuna ta wurin ayukan su cewa sun sa begensu ga Allah"
"kubuta" karin magana ne da ke nufin yin rayuwa ba tare da tunani kulum ba."
"sa hankali a"
"ya na so ya sa Allah ya ji dadin sa, ya na kuma so ya sa matansa ta ji dandin sa a loƙaci daya"
ƙuntata
"iya duƙufa a"
"ba kirki" ko kuma "ba darajawa"
AT: "macen da ya yi alkawari ya aura" ko kuma 2) "budurwan 'yar shi."
AT: 1) "ya aure budurwansa" ko kuma 2) "ya bar 'yar shi ta yi aure."
Anan "tsaya da karfi" magana ne na shirya abu ba shaka. Anan "zuciya" magana ne game da hankalin ko tunanin mutum. AT: "Amma idan ya shirya da karfi a zuciyarsa"
Anan "ɗaure" magana ne game da ɗangantaka a sakanin mutane da suke taimakon juna ta ruhaniya, ayuka da kauna. Anan na nufin saduwan aure. AT: "mace ta na aure da mijinta" ko kuma "mace ta na a haɗe da mijinta"
"sai ya mutu"
"duk wanda take bukata"
"idan sabon mijin mai bi ne"
"fahintana na maganan Allah"
mafi yawan wadata, mafi yawan murna
"kasance ba aure"
1Game da abinci da ake yiwa gumakai hadaya: Mun sani cewa, "Dukanmu muna da ilimi." Ilimi ya kan kawo takama, amma kauna tana ginawa. 2Idan wani yana tunanin ya san wani abu, wannan mutumin bai rigaya ya san abinda ya kamata ya sani ba. 3Amma idan wani yana kaunar Allah, to ya san da wannan mutum.4Game da abincin da aka yiwa gumakai hadaya: Mun san cewa, "Gunki a duniyan nan ba wani abu bane," kuma cewa" Babu wani Allah sai guda daya." 5To wata kila ma a ce wadanda ake kira alloli sun kasance, ko a cikin sama ko duniya, kamar yadda akwai wadanda ake ce dasu "alloli dabam dabam a duniya ko a sama," kamar yadda akwai "alloli da iyayengiji" da yawa. 6"Amma a wurin mu, Allah daya ne, Uban dukan duniya, daga wurinsa aka halita dukan abu, domin sa muke rayuwa, Ubangiji Yesu Almasihu daya, wanda ta wurin sa kome ya kasance, mu kuma daga wurinsa muke."7Amma ba kowa ke da wannan ilimi ba. Shi ya sa tun da, wadan su na bauta wa gunki, kuma suna cin wannan abincin kamar abin da aka mika wa gunki. Lamirin su ya kazantu sabo da yana da rauni.8Amma ba abinci ke bamu tagomashi a wurin Allah ba. Ko mun ci, bamu kara karbuwan mu ba, ko ba mu ci ba, ba mu rage karbuwan mu ba. 9Amma, ka yi hatara kada 'yancin ka ya zama sanadiyar tuntuben wani mai rarraunar bangaskiya. 10Anar misali, idan wani mai rarraunar lamiri ya hango ka mai ilimi, kana cin abincin da aka mika wa gunki, ai ba ka bashi kwarin gwiwa kenan yaci abincin da aka mika wa gunki ba?11Sabili da ganewar ka akan yanayin gumaka, dan'uwa rarrauna wanda Yesu ya mutu domin sa ya hallaka. 12Saboda haka, idan ka saba wa 'yan'uwa masu raunin a lamiri, ka yi zunubi a gaban Almasihu. 13Idan abinci zai sa dan'uwa na yayi tuntube, zan huta cin nama, domin kada in jawo wa 'yan'uwana faduwa.
Bulus ya tuna wa masubi cewa ƙodashike gumakai ba su da iƙo, yakamata masubi su yi hankali kadda su taɓa wadanda ba su yi karfi a bi ba, wadda su na iya tunani cewa sun damu da gumakai. Ya faɗa wa masubi cewa su yi hankali da yancin da suke da shi a cikin Almasihu.
"Mu" na nufin Bulus, ƙodashike ya na rubutu musamman wa masubi na Korontiyawa, da dukkan masubi.
Bulus ya yi amfani da wannan jumla domin ya yi gaba game da tambayan da Korontiyawan sun tambaye shi.
Al'ummai masu sujada zasu mika hatsi, kifi, kaza, ko nama wa allolinsu. Firis zai kona wani kashin a kan tebur a cikin Majami'a. Bulus ya na magana game da kashin da firis zai ba wa masu sujada domin su ci ko kuma su sayad a kasuwa.
"Ilimi ya kan kawo takama wa mutane." Anan "takama" magana ne game da sa wani girman kai. Ana iya bayana "Ilimi" da "sani." AT: "Ilimi na sa mutane girman kai" ko kuma "Mutanin da suke tunani cewa sun sani sosai suna zama da girman kai"
Ana iya bayan kalmar "kauna". AT: "amma a loƙacin da mun kaunace mutane, muna ginasu"
Gina mutane na wakilcin taimaka masu su yi girma da karfi a cikin bangaskiyansu. AT: "ƙauna na karfafa mutane" ko kuma "a loƙacin da mun kaunace mutane, mu na karfafasu"
"ya gaskanta cewa ya san komai game da wani abu"
AT: "Allah ya san wancan mutumin"
Mia yiwuwa Bulus ya na fadan jumlan da wadansu Korontiyawan su yi amfani. Zaman "komai" na wakilcin rashin iƙo. AT: "Mun sani, kamar yadda ku na son faɗa, cewa gunki a wannan duniya ba shi da iƙo kuma babu wani Allah sai guda ɗaya"
"abubuwan da mutane ke kira alloli"
Bulus bai yarda cewa akwai alloli dayawa da kuma iyayengiji da yawa ba, amma ya yarda cewa kafirai sun gaskanta akwai.
"Amma mun san cewa Allah ɗaya ne"
"dukkan mutane ... waɗansu mutanen da sun zama masubi yanzu"
lahani ko illa
Bulus ya yi magana game da abinci kamar mutum ne da zai iya sa Allah ya marabce mu. AT: "abinci ba ya ba mu tagomashi da Allah" ko kuma "abincin da muke ci ba ya sa Allah ya ji dadinmu"
AT: "Waɗansu mutane na iya tunani cewa idan bamu ci wadansu abubuwan ba, Allah zai ƙaunace mu kadan. Basu yi daidai ba. Wadanda suke tunani cewa Allah zai ƙaunace mu sosai idan mun ci waɗancan abubuwa, basu yi daidai ba"
masubi da ba su da karfi a bangaskiyansu
Bulus ya na magana da Korontiyawan kaman su mutum daya ne, kalmomin nan ɗaya ne.
abin da ya gane cewa daidai ko ba daidai ba ne
"ƙarfafa ya ci"
Bulus ya na magana da Korontiyawa kamar su mutum daya ne, kalmar "ku" anan daya ne.
ɗan'uwa ko 'yar'uwa da ba shi da karfi a bangaskiyansa zai yi zunubi ko ya rasa bangaskiyansa.
"Domin abin da na faɗa daidai ne"
Anan "abinci" magana ne game da mutum da yake cin abinci. AT: "idan na sa ta wurin cin" ko kuma "idan na, domin abin da na ci, sa"
1Ni ba yantacce bane? Ni ba Manzo ba ne? Ban ga Ubangijinmu Yesu ba? ba ku ne aikin hannuna cikin Ubangiji ba? 2Idan ni ba Manzo ba ne ga wadansu, hakika ni Manzo ne a gare ku. Ai kune shedar manzanci na cikin Ubangiji.3Ga kariya ta zuwa masu zargi na, 4Ba mu da 'yanci mu ci mu sha? 5Ba mu da 'yanci mu dauki mace mai bada gaskiya kamar sauran manzanni da Kefas da 'yan'uwan Ubangiji? 6ko ni da Barnabas ne kawai muka cancanci aiki?7Wake aikin soja daga aljihunsa? Wake shuka gonar inabi baya ci daga 'ya'yan ta ba? Ko kuwa wake kiwon tumaki ba ya shan madarasu? 8Ina wannan zance da ikon mutum ne? Doka bata fadi haka ba?9Gama a rubuce yake a attaura ta Musa cewa, Takarkari mai tattake hatsi kada a sa masa takunkumi. Amma shanu ne Ubangiji ke zance a kai? 10Ba don mu yake magana ba? An rubuta domin mu ne. Domin wanda yake noma, yayi cikin bege. mai tattake hatsi kuma yayi da begen samu. 11Idan mun yi shuka ta ruhaniya a rayuwarku, mai wuya ne mu girbi kayan ku na jiki?12Idan wadansu sun mori wannan 'yanci a gurin ku, ba mu fi su cancanta ba? duk da haka bamu yi amfani da wannan 'yancin ba, maimakon haka, mun yi jimriya da duk abin da zaya hana bisharar Yesu Almasihu. 13Baku sani ba masu bauta a haikali suna samun abincinsu ne daga haikalin? Baku sani ba masu bauta a bagadi, suna da rabo daga abin da ake kawowa kan bagadin? 14Haka kuma Ubangiji ya umarta masu aikin bishara zasu ci abincinsu ta hanyar bishara.15Amma ban yi amfani da wannan 'yanci ba, ba kuma ina rubuta maku domin ayi mani wani abu bane, na gwanmace in mutu maimakon wani ya hana ni wannan fahariya. 16Ko nayi shelar bishara, ba ni da dalilin fahariya domin ya zama dole in yi. Kaito na idan ban yi shelar bishara ba17Idan na yi hidimar nan da yardar zuciyata, ina da sakamako, idan kuma ba da yaddar zuciyata ba, harwa yau akwai nauwaya akai na. 18To menene sakamako na? shi ne in yi shelar bishara kyauta, da haka ba zan yi amfani the 'yanci na cikin bishara ba19Ko da shike ni 'yantacce ne ga duka, amma na mai da kaina bawan kowa domin in ribato masu yawa, 20Ga yahudawa, na zama bayahude, domin in ribato yahudawa, ga wadanda ke karkashin shari'a, na maishe kaina kamarsu, domin in ribato wadanda ke karkashinta. Na aikata wannan ko da shike bana karkashin shari'a21Ga wadanda basu karkashin shari'a, na maishe kaina kamar su. Ko da shike ban rabu da shari'ar Allah ba. Amma ina karkashin dokar Almasihu. Na yi haka ne domin in ribato wadanda ba sa karkashin shari'a. 22Ga marasa karfi, na maishe kaina kamar marar karfi, domin in ribato raunana. Na mai da kaina dukan abu ga dukan mutane domin in sami zarafin da zan ribato wadansu zuwa ceto. 23Ina dukan abu sabili da bishara, domin kuma in sami albarkar da ke cikinta24Baku sani ba mutane da dama suna shiga tsere amma daya neke karbar sakamakon, saboda haka ku yi tsere domin ku karbi sakamako. 25Dan wasa yana motsa jiki da kame kansa. Yana yi saboda ya karbi wannan sakamako mai lalacewa, amma muna tsere domin mu karbi sakamako marar lalacewa. 26Saboda haka ba na tsere ko fada haka nan kamar mai bugun iska. 27Amma ina matse jiki na in maishe shi bawa, kada bayan na yi wa wadansu wa'azi ni kuma a karshe a fitar da ni.
Bulus ya bayana yadda yake amfani da yancin da yana da shi a cikin Almasihu.
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya tuna wa Korontiyawan game da iƙon da yake da shi. AT: "Ni yantaccen mutum ne."
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya tuna wa Korontiyawan game da kansa da kuma iƙon da yake da shi. AT: "ni Manzo ne."
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya tuna wa Korontiyawan game da kansa. AT: "na ga Ubangijinmu Yesu."
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya tuna wa Korontiyawan game da dangantakansu da shi. AT: "kun ganskanta da Almasihu domin na yi aiki yadda Ubangiji yake so in yi.
"shedar" a nan na nufin magana game da alamu da ake so domin a hakikanta wani abu. AT: "ku shedu ne da zan iya yin amfani domin in hakikanta cewa Ubangiji ya zaɓe ni don in zama manzo"
AT: 1) kariyan Bulus ne kalmomin da suke bi ko kuma 2) kalmomin cikin 9:1-2 kariyan Bulus ne, "Ga kariya ta ...ni. Ba."
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya nanata cewa ya san Korontiyawan sun amince da abin da yake faɗa. AT: "mu na da tabacecen iƙon mu karɓa ci da sha daga ikilisiyoyi."
Anan "mu" na nufin Bulus da Barnabas.
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya nanata cewa ya san Korontiyawan sun amince da abin da yake faɗa. AT: "idan mu na da mataye da sun ganskanta, mu na da iko mu ɗauke su kamar yadda sauran mazannin sun yi, da yan'uwanin Ubangiji, da Kafas."
Bulus ya na kunyatar da Korontiyawan. AT: "ku na tunani da alama cewa mutuanen da yakamata su yi aiki domin su samu kuɗi shine ni da Barnabas."
Bulus ya yi amfani da tambaya domin ya nanata cewa ya san Korontiyawan sun amince da abin da yake faɗa. AT: "Mun san cewa babu sojan da zai saya guzurinsa." ko kuma "Mun san cewa kowane soja ya na karɓan guzurinsa daga gwamnati ne."
Bulus ya yi amfani da tambaya domin ya nanata cewa ya san Korontiyawan sun amince da abin da yake faɗa. AT: "Mun san cewa wadda ya shuka gona ne zai ci 'ya'yansa." ko kuma "Mun san cewa ba wadda ya ke tsammani cewa wadda da ya shuka gona ba zai ci 'ya'yansa ba."
Bulus ya yi amfani da tambaya domin ya nanata cewa ya san Korontiyawan sun amince da abin da yake faɗa. AT: "Mun san cewa waɗanda suke kiwon tumaki na samu sha daga tumakin."
Bulus yana kunyatar da Korontiyawan. "ku na tsammani cewa ina ina faɗan abubuwa bisa iƙon mutum."
Bulus yana kunyatar da Korontiyawan. AT: "ku na yi kamar ba ku san cewa wannan ne abin da an rubuta a doka ba."
Musa yana magana da Isra'ilawa kaman su mutum ɗaya ne, wannan dokan daya ne.
Bulus ya yi tambaya domin Korontiyawan su yi tunani game da abin ya ke faɗa ba sai ya faɗa ba. AT: "Ya kamata ku sani ba sai na faɗa maku cewa ba shanu ne Allah ya fi damu da shi ba."i
Bulus ya yi tambaya domin ya nanata jumlan da yake yi. AT: "maimako, haƙiƙa Allah ya na magana game da mu."
Anan "mu" na nufin Bulus da Barnabas.
Bulus ya yi tambaya domin Korontiyawan su yi tunani game da abin da yake faɗa ba sai ya faɗa ba. AT: "Ya kamata ku sani ba sai na faɗa maku cewa taimakun ba zai yi mana yawa in mun karɓa ba."
Bulus ya yi tambaya domin Korontiyawan su yi tunani game da abin da yake faɗa ba sai ya faɗa ba. Anan "mu" na nufin Bulus da Barnabas. AT: "Waɗansu sun mori ... ku, Kun sani ba sai na faɗa maku cewa mu na da wannan iƙo fiye."
Bulus da Korontiyawan su sani cewa waɗansu sun mori iƙon. "tunda wadansu sun mori wannan iƙo"
wadansu ma'aikata na bishara
iƙon da zai sa masubi na Koronti su tanada abubuwa wa waɗanda sun faɗa masu game da bishara
"zama nauyi" ko kuma " daina baza"
Bulus ya na tuna wa Korontiyawan game da abin da sun sani domin ya kara waɗansu bayanen. AT: "Ina so in tuna ma ku cewa wadanda su na bauta a haikali suna samun abincinsu ne daga haikalin."
Bulus ya na tuna wa Korontiyawan game da abin da sun sani domin ya kara waɗansu bayanen. AT: "Ina so in tuna ma ku cewa waɗanda su na bauta a bagadi suna samun abincinsu ne daga bagadi."
Kalmar "bishara" anan magana ne game da 1) mutanen da aka gaya masu game da bisharan, sun karɓa abinci da waɗansu kayakinsu da suna so daga waɗanda suka koya masu game da bisharan," ko kuma 2) shaidan aikin bishara, "sun karba abinci da waɗansu kayakinsu da suke so domin sun yi aikin shelar bisharan."
"wannan abubuwan da na chanchanci"
AT: "domin ku yi mani wani abu"
"ɗauka wannan zarafin, zan yi fahariya"
"dole ne in yi wa'azin bishara"
"in sha wahalan rashin sa'a idan"
"idan na yi wa'azi ba da yarda ba" ko kuma "idan na yi wa'azi domin ina so"
An fahimci kalmomin "na yi wannan" a jumla da ya wuce. AT: "Amma idan na yi wannan ba da yarda ba" ko kuma " Amma idan na yi wannan ƙodashiƙe ba na so" ko kuma "Amma idan na yi wannan domin an sa ni dole in yi"
AT: "Dole ne in yi wannan aikin da Allah ya amince ma ni in karasa"
Bulus ya na shirya su domin sabon bayani da zai ba su. AT: "wannan ne lada na"
"ladan wa'azi na shi ne zan iya yin wa'azi ba da karɓan kuɗi ba"
"yi wa'azin bishara"
"ba zan roke mutane su taimake ni sa'ad da ina tafiya da wa'azi ba"
"ni 'yantacce ne ga duka" karin magana ne da ke nufin yin rayuwa ba tare da yin tunanin abin da zaku yi wa waɗansu ba. AT: "zan iya yin rayuwa ba ba tare da bauta wa waɗansu ba"
"rinjaye waɗansu su gaskanta" ko kuma "taimake waɗansu su san Almasihu"
"ina yi kamar Bayahude" ko kuma "ina yin al'adan Yahudawa"
"Na zama kamar wadda ya miƙa kansa ga bin bukatun shugabancin Yahudawan, yarda da fahimtar su game da litatafan Yahudawan"
"waɗanda ba su biyayya da dokokin Musa"
Bulus ya na tuna wa Korontiyawan game da abin da sun sani domin ya iya kara sabon bayani. AT: "Bari in tuna muka cewa ƙodashiƙe masu tseren su na tserewa, mai tsere daya ne ya ke karɓan lada."
Bulus yana kwatanta zaman rayuwan mai bi da yin aiki ma Allah da tserewa da zama ɗan wasan guje-guje. Kaman tserewa, rayuwa da aikin mai bi na bukatan horo mai tsanani a gefen mai tseren, kuma mai bi na da maƙasudi.d
Bulusya na magana game da ladan da Allah zai ba wa amintaccen mutanensa kamar kyauta ne da a ke ba wa masu wasannin guje-guje.
Sakamako taren ganye ne da an murɗa tare. An ba da sakamako a amtsayin kyauta wa masu yin wasanni da guje-guje. Bulus ya na magana game da rai madawami kamar sakamako ne da ba zai taɓa bushe ba.
Anan "tserewa" da "bugu" zance ne game da yin rayuwa da bauta wa Allah. AT: "Na san dalilin da na ke gudu sosai, kuma na san abin da nake yi a loƙacin da nake bugu"
Hukuncin tsere ko kuma gasa magana ne game da Allah. AT: "mai shari'an ba zai hana ni ba" ko kuma "Allah ba zai ce na kasa bin dokokin ba"
1Ina son ku sani, 'yan'uwa, cewa ubaninmu duka suna karkashin gajimarai kuma sun bi ta cikin teku. 2Dukansu an yi masu baftisma cikin gajimarai da kuma teku, 3kuma dukansu sun ci abincin ruhaniya iri daya. 4Dukansu sun sha abin sha na ruhaniya iri daya. Gama sun sha daga wani dutsen ruhaniya da ya bisu, kuma wannan dutsen Almasihu ne.5Amma Ubangiji bai ji dadin yawancinsu ba, saboda haka gawawakin su suka bazu a jeji. 6Wadan nan al'amura, an rubuta mana su domin muyi koyi da su, kada mu yi sha'awar miyagun ayyuka kamar yadda suka yi.7Kada ku zama masu bautar gumaka kamar yadda wadansun su suka yi. Wannan kamar yadda aka rubuta ne, "Mutanen sukan zauna su ci su sha kuma su tashi suyi wasa." 8Kada mu shiga zina da faskanci kamar yadda yawancin su suka yi, a rana guda mutane dubu ashirin da uku suka mutu.9Kada mu gwada Almasihu kamar yadda yawancinsu suka yi, macizai suka yi ta kashe su. 10kada kuma ku zama masu gunaguni kamar yadda suka yi, suka yi ta mutuwa a hannun malaikan mutuwa.11Wadannan abubuwa sun faru dasu ne a matsayin misalai a garemu. An rubuta su domin gargadinmu - mu wadanda karshen zamanai yazo kanmu. 12Saboda haka, bari duk wanda yake tunanin shi tsayyaye ne, to yayi hattara kada ya fadi. 13Babu gwajin da ya same ku wanda ba a saba da shi ba cikin dukan mutane. A maimako, Allah mai aminci ne. Da ba zaya bari ku jarabtu ba fiye da iyawarku. Tare da gwajin zai tanadar da hanyar fita, domin ku iya jurewa.14Saboda haka ya kaunatattu na, ku guji bautar gumaka. 15Ina magana da ku kamar masu zurfin tunani, domin ku auna abin da ni ke fadi. 16Kokon albarka da muke sa wa albarka, ba tarayya bane cikin jinin Almasihu? Gurasa da muke karyawa ba tarayya bane cikin jikin Almasihu? 17Domin akwai gurasa guda, mu da muke dayawa jiki daya ne. Dukanmu munci daga gurasa daya ne.18Dubi mutanen Isra'ila: ba wadanda ke cin hadayu ke da rabo a bagadi ba? 19Me nake cewa? gunki wani abu ne? Ko kuma abincin da aka mika wa gunki hadaya wani abu ne?20Amma ina magana game da abubuwan da al'ummai suke hadaya, suna wa aljannu ne hadaya ba Allah ba. Ba na son kuyi tarayya da al'janu! 21Ba zaku sha daga kokon Ubangiji ku kuma sha na Al'janu ba, ba za kuyi zumunta a teburin Ubangiji ku yi a na Al'janu ba. 22Ko muna so mu sa Ubangiji kishi ne? Mun fi shi karfi ne?23"Komai dai dai ne," amma ba komai ke da amfani ba, "Komai dai dai ne," amma ba komai ke gina mutane ba. 24Kada wani ya nemi abinda zaya amfane shi. A maimako, kowa ya nemi abinda zaya amfani makwabcinsa.25Kana iya cin duk abin da ake sayarwa a kasuwa, ba tare da tamboyoyin lamiri ba. 26Gama "duniya da duk abin da ke cikin ta na Ubangiji ne."27Idan marar bangaskiya ya gayyace ka cin abinci, kana kuma da niyyar zuwa, ka je ka ci duk abinda aka kawo maka, ba tare da tamboyoyin lamiri ba.28Amma idan wani ya ce maka, "Wannan abinci an yi wa gumaka hadaya da shi ne" To kada ka ci. Wannan za ka yi ne saboda wanda ya shaida maka, da kuma lamiri (gama duniya da dukan abinda ke cikin ta na Ubangiji ne). 29Ba ina nufin lamirin ka ba, amma lamirin wanda ya fada maka. Don me za a hukunta 'yanci na domin lamirin wani? 30Idan na ci abincin tare da bada godiya, don mi za a zage ni don abin da na bada godiya a kansa?31Saboda haka, ko kana ci ko kana shi, ka yi komai domin daukakar Allah. 32Kada ka zama sanadiyyar tuntube, ga Yahudawa, ko Helenawa, ko ikilisiyar Allah. 33Na yi kokari in farantawa dukan mutane rai cikin dukan abubuwa. Ba riba nake nema wa kaina ba, amma domin kowa. Na yi wannan ne domin su sami ceto.
Bulus ya tuna ma su game da misalin tsohon Ubannin Yahudawa da yadda sun ji da fasikanci da kuma bautan gumakai.
Bulus ya na nufin zamanin Musa a cikin littafin Fitowa a loƙacin da Isra'ilawa sun bi ta Jan Teku a yayin da sojojin Masarawa sun bi su. Kalman "mu" na nufin kansa tare da Korontiyawan.
An san wannan tekun da sunaye biyu, Jan Teku da kuma Tekun Iwa.
"tafiya ta cikin"
"Duka sun bi sun kuma mika kansu ga Musa"
ta gajimarai da su ka wakilci hallarar Allah, sun kuma bi da Isra'ilawa da rana
"sha ruwan ruhaniya iri ɗaya wadda Allah ya kawo ta ruhaniya daga dutse ... dutsen ruhaniya"
"dutse", na nufin dutse wadda ana iya gani. Idan harshen ku ba za ta iya ce dutse "ne" sunan mutum ba, ku ɗauki kalman "dutse" a matsayin magana game da iƙon Almasihu da ke aikia a cikin dutsen. AT: "Almasihu ne ya yi aiki a cikin wancan dutsen"
"rashin jin dadi" ko kuma "fushi"
ubannin Isra'ilawa
"Allah ya baza gawawakin su a kewayen" ko kuma "Allah ya kashe su ya kuma baza gawawakinsu"
filin daji a sakanin Masar da Isra'ila wadda Isra'ilawa sun ragaita na shekaru 40
mutanen da suke bauta wa gumakai
"zauna su ci abinci"
Bulus ya na magana daga al'adun Yahudawa. Yakamata masu sauraran sa sun gane daga wannan kalma cewa mutanen su na bautan gumaka ta wakoki da rawa da kuma yin ayukan faskanci, ba bu jin dadi.
"Allah ya kashe mutane 23,000 a rana daya"
"domin sun aikata waɗancan ayyuka mara daidai na faskanci"
AT: "yi. Sakamakon ita ce, macizai suka kashe su duka"
yi kara
AT: "yi. Sakamakon ita ce, malaika na mutuwa ya kashe su"
"Allah ya hukunta kakaninmu"
Anan " mu" na nufin masubi.
AT: "Allah ya sa Musa ya rubuta domin mu koyi yin abin da yakamata"
"karshen zamani"
kada ya yi zunubi ko kuma ki Allah
AT: "gwajin da yake taɓa ku, gwaji ne da mutane sun ji"
"zai bari a gwada ku a hanyar da za ku iya tsare"
AT: "ba zai bar wani ya gwada ku ba"
Bulus ya na magana game da ayukan bautar gumakai kaman abin da ya ke a bayyane kamar mugun dabba. AT: "ku yi abin da za ku iya domin ku kare kunku daga bautar gumakai"
Bulus ya na magana game da albarkan Allah kamar kokon da ake amfani a hidiman abincin Almasihu.
"wadda muke gode wa Allah"
Bulus ya na tuna wa Korontiyawa game da abin da sun sani, cewa kokon da muke rabawa na wakilcin tarayyanmu a jinin Almasihu. AT: "mu na tarayya a cikin jinin Almasihu."
Bulus ya na tuna wa Korontiyawa game da abin da sun sani. AT: "mu na tarayya a cikin jikin Almasihu a loƙacin da muke raɓa gurasan."
"aikatawa"
gasheshen gurasa guda daya da aka yanka ko kuma gutsure kamin a ci.
Bulus ya na tuna wa Korontiyawan game da abin da sun sani domin ya iya ba su sabon bayani. AT: "waɗanda su ke cin hadayu, su na tarayya a ayuka da albarku na bagadi"
Bulus ya na tuna wa Korontiyawan game da abin da sun sani domin ya iya ba su sabon bayani. AT: "bari in sake duba abin da ina faɗa." ko kuma "ga abin da ina nufi."
Bulus ya na so Korontiyawan su amsa tambayan a zuciyar su domin kadda ya sake faɗa masu. AT: "kun san cewa ba wai ina ce gumki abin gaskiya ba ne."
Bulus ya na so Korontiyawan su amsa tambayan a zuciyar su domin kadda ya sake faɗa masu. AT: "kun san cewa ba wai ina ce wai abincin da ake hadaya wa gumakai na da muhimmi ba."
Bulus ya na magana game da mutum da ya ke sha daga koko daya da al'janu kamar shaida ne cewa mutumin abokin al'janu ne. AT: "ba mai yiwuwa ba ne ku zama abokan gaskiya da Almasihu da kuma al'janu ba"
"ba zai yiwu ku zama daya da mutanen Almasihu da kuma na al'janu ba"
Bulus ya na so Korontiyawan su amsa wannan tambayan a zuciyar su. AT: "Yakamata ku sani ba sai na faɗa ma ku cewa ba kyau ku sa Ubangiji kishi ba."
ga fush ko kiyama
Bulus ya na so Korontiyawan su amsa wannan tambayan a zuciyar su. AT: "Yakamata ku sani ba sai na faɗa ma ku cewa ba mu fi Allah karfi ba."
AT: 1) Bulus ya na amsa abin da waɗansu Korontiyawan za su iya tunani, "wadansu su na ce, 'zan iya yin komai" ko kuma 2) Bulus yana faɗan abin da yake tunani daidai ne, "Allah ya bar ni in yi komai." A fasara wannan a cikin 6:12
"waɗansu abubuwan ba su da amfani"
Gina mutane na wakilcin taimaka masu don su yi girma da karfi a cikin bangaskiyansu. Dubi yadda ake fasara "gina" a cikin 8:1. AT: "ba komai ne yake karfafa mutane ba" ko kuma "waɗansu abubuwan ba su karfafa mutane"
"ku. Allah ya na so ku ci abinci ba tare da shaka ba"
An sa waɗansu fasaran a bayyane 1) siffar "ku" da "ci" daya ne annan, amma Bulus ya yi amfani da su, 2) kalmomin "don me za a hukunta yanci na da lamirin wani?" ya kafa a kan "ci kowane abin da an baku, ba tare da yin tambayoyin lamiri ba" 10:27 ba tare da "lamirin dayan mutumin ba."
Bulus ya na magana da Korontiyawa kamar su mutane daya ne, kalmomin "ku" da umurnin "kada ka ci " daya a nan.
AT: "kalmar "don" na nufin koma zuwa 10: 27, "bai kamata in yi tambayoyin lamiri, don haka me ... lamiri? Idan na ci ... bada godiya?" ko kuma 2) Bulus yana fadan abin da waɗansu Korontiyawan su na tunani, "kamar yadda waɗansunku za su ta yin tunani, "Don me ... lamiri? Idan na ... gade?"
Mai magana ya na son mai sauraransa ya amsa tambayan a cikin zuciyarshi. AT: "yakamata ku sani ba sai na faɗa maku cewa kadda wani ya ce ban yi daidai ba domin ya na da sanin daidai da ba daidai ba da sun bambanta daga nawa.
Mai magana ya na son mai sauraransa ya amsa tambayan a cikin zuciyarshi. AT: "Na ci abincin da godiya, don haka kada wani ya zage ni."
Idan Bulus ba ya fadan abin da Korontiyawan su ke iya tunani, "na" ya na wakilcin waɗanda suke cin nama da godiya. "Idan na ci" ko kuma "Idan mutum ya ci"
"ku kuma gode wa Allah don shi" ko kuma "ku kuma gode wa mutumin da ya ba ni"
"kada ku bata da Yahudawa ko Girkawa" ko kuma "kada ku sa Yahudawa ko Girkawa fushi"
"sa duka mutane murna"
"ba na yin abin da na ke so wa kai na"
yawan mutane
1Ku yi koyi da ni, kamar yadda nake koyi da Almasihu. 2Yanzu ina yaba maku ne, don kuna tunawa da ni cikin abu duka. Ina kuma yaba maku wajen bin al'adun da na ba ku daidai yadda na ba ku. 3Amma fa ina son ku fahimta da cewa, shugaban kowane mutum Almasihu ne, shugaban kowace mace mutumin ne, shugaban Almasihu Allah ne. 4Kuma duk mutumin da ya yi addu'a ko annabci kansa a rufe, ya wulakanta shugabansa.5Amma duk macen da ta yi addu'a ko annabci kanta a bude, ta wulakanta shugabanta. Gama yayi dai dai da idan tayi aski. 6Gama idan mace ba zata rufe kanta ba, to ta yanke gashinta ya zama gajere. Idan abin kunya ne mace ta yanke gashinta ko ta aske kanta, bari ta rufe kanta.7Bai kamata na miji ya rufe kansa ba, tun da yake shi siffa ne da daukakar Allah. Amma mace daukakar namiji ce. 8Don kuwa namiji ba daga jikin mace yake ba. A maimako, matar daga jikin namiji take.9Ba a kuma halicci namiji don mace ba. A maimako, an halicci mace don namiji. 10Shi ya sa mace za ta kasance da alamar iko a kanta, saboda mala'iku.11Duk da haka, a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, haka kuma namiji ba a rabe yake da mace ba. 12Kamar yadda mace take daga namiji, haka ma namiji kuma haihuwar mace ne. Amma dukkan abubuwa daga Allah suke.13Ku hukunta da kanku: Daidai ne mace ta yi addu'a ga Allah kanta a bude? 14Ashe, ko dabi'a bata nuna maku cewa abin kunya ne namiji, ya kasance da dogon gashi ba? 15Ba dabi'a ta koya maku cewa idan mace tana da dogon gashi, daukakar ta ne ba? Gama domin rufewa aka yi mata baiwar gashin. 16To idan wani yana da niyyaryin gardama game da wannan, mu dai bamu da wata al'adar, ikilisiyoyin Allah kuma haka.17Amma game da umarnin dake biye, ban yaba maku ba, taruwarku ba ta kirki ba ce, ta rashin gaskiya ce. 18Farko dai sa'adda kuke, taron ikklisiya, na ji har akwai rarrabuwa tsakaninku, har na fara amincewa da maganar. 19Dole ne a sami tsattsaguwa a tsakaninku, don a iya gane wadanda suke amintattu a cikinku.20Domin, in kun taru a wuri daya, ba jibin Ubangiji kuke ci ba! 21Ya yin da kuke ci, kowa na cin abincinsa ne kamin sauran Wani yana jin yunwa, wani kuma ya zarin ci, har ya bugu. 22Baku da gidajen da zaku ci ku sha, kuna raina ikkilisiyar Allah, kuna kuma wulakanta wa wadanda basu da komai? To, me zan ce maku? Yaba maku zan yi? Ba zan yaba maku ba akan wannan.23Amma abin da na karba a gun Ubangiji shi nake baku cewa Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi ya dauki gurasa. 24Bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, "wanna shi ne jikina wanda yake saboda ku, ku yi domin tunawa da ni."25Ta wannan hanya kuma, sai ya dauki kokon, ya ce, "kokon nan na sabon alkawari ne, da aka tabbatar da shi da cikin jinina. Ku yi haka kuna sha don tunawa da ni." 26Duk sa'adda kuke cin gurasar nan, kuna kuma sha cikin kokon nan, kuna bayyana mutuwar Ubangiji ke nan, har sai ya dawo.27Saboda haka duk wanda ya ci gurasar nan, ko ya sha a cikin kokon nan, na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulakanta jikin Ubangiji da jininsa. 28Sai kowa ya fara auna kansa, kafin ya ci gurasar, ya kuma sha a cikin kokon nan. 29In kowa ya ci, ya sha ba tare da rarrabewa da jikin Ubangiji ba, lalle ya jawowa kansa hukunci, ta wurin ci da sha da ya yi. 30Shi ya sa da yawa a cikin ku suke raunana, kuma suna fama da rashin lafiya, har ma wasun ku da dama suka yi barci.31Amma, in mun auna kanmu, ba a za a hukunta mu ba. 32In kuwa Ubangiji ne ya ke hukunta mu, To, muna horuwa ke nan, don kada a kayar damu tare da duniya.33Saboda haka, ya ku 'yan'uwana, idan kuka tattaru don cin abinci, sai ku jira juna. 34Idan kuwa wani yana jin yunwa, ya ci a gida, kada ya zama taronku ya jawo maku hukunci. Batun sauran abubuwan da kuka rubuta kuwa, zan ba da umarni a kai sa'ad da na zo.
Bayan da ya tuna masu cewa su bi shi yadda yake bin Almasihu, Bulus ya ba da umurni game da yadda maza da mata za su yi rayuwa a matsayin masubi.
"kuna tunawa da ni a kowane loƙaci" ko kuma "kullum ku na kokarin aikata kamar yadda ina so ku aikata" Korontiyawan ba su mata da ko waye ne Bulus ko kuma abin ya koya masu ba.
AT 1) "Domin wannan, Ina so ko kuma 2) "ƙodashiƙe, Ina so."
na da iƙo akan
AT 1) "yakamata mazaje su samu iƙo akan mataye" ko kuma 2) "yakamata maigidan ya kasance da iƙo akan matan"
"yi haka bayan ya saka mayafi a kanshi"
AT: 1) "na kawo kunya wa kansa" ko kuma 2) "na kawo kunya a Almasihu, wadda shi ne shugaba."
AT: 1) "macen da ta yi addu'a ... ta na kawo rashin kunya wa kanta" ko kuma 2) "matan da ta yi addu'a ... kawo rashin kunya wa mijin ta."
Cewa da rashin kayan da aka sa a saman kai, kuma ya na rufe suma da kuma kafaɗa.
kaman ta cire duka suma a kanta da raiza
Alamar kunya ne ko wulakanci wa mace ta yanka suman ta.
Sa a kanta rigan da an sa a saman kai wadda yake rufe suma da kafaɗa.
AT: 1) "ba dole ne ya rufe kansa ba" ko kuma 2) "ba lallai ne ya rufe kansa ba"
Yadda mutum yake nuna iƙon Allah, haka ne macen ta na nuna halin mijin.
Allah ya yi mace ta wurin cire ƙashi daga na miji. AT: "Allah bai yi na miji daga mace ba. A maimako, ya yi mace daga na miji"
Ana iya bayyana waɗannan kalmomin a 11:8 domin mai karatun ya iya ganin kalman "wannan" cikin "wannan ne dalilin ... mala'iku" na nufin kalmomincan "mace ne ɗuakakar namiji" a cikin 11:7.
AT: 1) "don nuna alamar cewa ta na da miji a matsayin shugabanta" ko kuma 2) " don nuna alamar cewa ta na da iƙon yin addu'a ko kuma annabci."
"Dashiƙe abin da na faɗa duka gaskiya ne, abu ma fi muhimmi shi ne wannan: cikin Ubangiji"
AT: 1) "a sakanin masubi, wadda sun kasance na Ubangiji" ko kuma 2) "a cikin duniya, da Allah ya halita."
AT: "mace ta na dogara akan namiji, kuma namiji ya na dogara akan mace"
"Allah ya halicci komai da komai"
"ku hukunta wannan zance bisa ga al'adu da ayukan ikilisiyan da kun sani"
Bulus ya so Korontiyawa su yarda da shi. AT: "mace ta rufe kanta a addu'a ga Allah, domin ta ɗaukaka Allah."
Bulus ya so Korontiyawa su yarda da shi. AT: "dabi'a da kansa ya koya maku ... domin shi."
AT: "Domin Allah ya hallicci mace da gashi"
AT: "Ya yin da na ba ku wannan umarni, a kowai abin da ba zan iya yabon ku ba : A loƙacin"
"umarnin da ina so in yi magana game da"
"tara tare" ko kuma "haɗu"
"ba ku taimake junanku ba; maimako, ku na yi wa junanku illa"
"a matsayin masubi." Bulus ya magana game da kasancewa a cikin gini.
"ku na raɓa kanku zuwa kungiyoyin hamayya"
Suna iya nufin 1) Kalmar "dole" na nuna cewa wannan yanayi na iya faruwa. AT: "Mai yiwuwa za a iya samun tsattsaguwa a tsakaninku" ko kuma 2) Bulus ya yi amfani da maganan nan don ya kunyatar da su domin su na da tsattsaguwa. AT: "kamar ku na tunani cewa dole ne a sami tsattsaguwa a tsakaninku" ko kuma "kamar ku na tunani cewa dole ne ku raɓa kanku"
kungiyoyin hamayya na mutane
AT: 1) "don mutane su san masubi da suke da martaba sosai a sakaninku" ko kuma 2) "don mutane su iya nuna wannan yabo ga sauran mutane a sakaninsu." Mai yiwuwa Bulus ya yi ta amfani da wannan magana, a faɗan abin da ya ke so Korontiyawan su gane, don ya kunyatar da su.
AT: 1) "wadda Allaha ya amince" ko kuma 2) "wadda ku, ikilisiya, ku ka amince."
"za ku iya gaskanta cewa ku na cin abincin Ubangiji, amma ba ku yin shi da daraja"
"wadda za a tara ma abinci"
tsana ko kuma da rashin mutunci da kuma rashin ladabi
ruɗa ko kuma sa jin kunya
Bulus ya na kwaɓan su Korontiyawan. AT: "Ba zan iya ce abu mai kyau game da wannan ba. Ba zan iya yabon ku ba."
"Amma daga Ubangiji ne na ji abin da na faɗa maku, cewa wannan ne: Ubangiji"
AT: "a daren da Yahuda Iskarioti ya bashe shi"
"ya cire gutsure daga shi"
"Gurasan da nake riƙe da shi, jikina ne"
Ya na da kyau a bayana wannan. Korontiyawan sun san kokon da ya ɗauka, don haka ba "kwaf" bane ko "waɗansu kwaf" ko kuma "kowane kwaf ba." AT: 1) kokon ruwa da mutum ze so ya yi amfani da shi ko kuma 2) kokon na uku ko na huɗu na ruwa da Yahudawa sun sha a abincin Idin ketarewa.
"sha daga wannan kokon, kuma a yadda ku na sha daga shi"
koyar game da giciyewa da kuma tashiwa
Anan iya bayyana wurinda Yesu zai zo. AT: "sai Yesu ya dawo duniyannan"
"ci gurasar Ubangiji ko kuma sha kokon Ubangiji"
Bulus ya na magana game da mutum da yana duba tafiyarsa da Allah da kuma yadda ya ke rayuwarsa kamar mutumin ya na neman abin da zai saya. Dubi yadda an fasara "gwada kyau" a cikin 3:13.
AT: 1) "kuma bai yarda cewa ikilisiya ne jikin Ubangiji ba" ko kuma 2) "kuma bai duba cewa yana rike da jikin Ubangiji ba."
Waɗannan kalmomin su na nufin abu iri daya kuma ana iya hada su, kamar a cikin UDB.
"barci" magana ne game da mutuwa. AT: "kuma waɗansunku sun mutu" .
Idan wannan zai nuna kamar Bulus yana magana da wadda sun mutu ne, za ku iya sa shi a bayyane cewa ba haka ba ne. AT: "waɗansu mutanen kungiyanku"
AT: "Allah ba zai hukunta mu ba"
AT: "Ubangiji ya na hukunta mu, ya na horas da mu, domin kadda ya kayar da mu"
an taru domin a ci abinci tare kafin a yi yabon abincin Ubangiji
"ku jira sauran su zo kafin ku fara abincin"
"ya ci kafin zuwa wannan taru"
"ba zai zama rana ne da Allah zai yi maku horo ba"
1Game da baye bayen Ruhu Mai Tsarki 'yan'uwa, bana so ku zama da jahilci.2Kun san cewa lokacin da ku ke al'ummai, an rude ku da alloli marasa magana ta hanyoyi dabam dabam marasa kan gado. 3Saboda haka ina so ku sani babu wanda ya ke magana da Ruhun Allah da zai ce, "Yesu la'ananne ne." Babu kuma wanda zaya ce, "Yesu Ubangili ne," sai dai ta Ruhu Mai Tsarki.4Akwai bay bye iri iri, amma Ruhu daya ne. 5Akwai hidimomi iri iri, amma Ubangiji daya ne. 6Akwai aikace aikace iri iri, amma Allah daya ke bayyanawa kowane mutum yadda zai aiwatar da su.7To ga kowanne an bayar da ikon nuna ayyukan Ruhu a fili domin amfanin kowa. 8Ga wani ta wurin Ruhu an bayar da baiwar hikima, kuma ga wani kalmar sani ta wurin Ruhu daya.9Ga wani an ba shi baiwar bangaskiya ta wurin Ruhun nan, ga wani kuwa an ba shi baiwar warkarwa ta wurin wannan Ruhun. 10Ga wani yin ayyukan iko, ga wani kuwa annabci. Ga wani kuwa an ba shi baiwar bambance ruhohi, ga wani harsuna daban daban, kuma ga wani fassarar harsuna. 11Dukan wadannan Ruhu daya ne ya ke iza su, ya kuma rarraba baye bayen ga kowannen su yadda ya nufa.12Kamar yadda jiki daya ne amma da gabobi da yawa kuma duk gabobin na jiki daya ne, haka nan Almasihu yake. 13Gama ta Ruhu daya aka yi wa kowa baftisma cikin jiki daya, ko Yahudawa ko al'ummai, ko bayi ko 'ya'ya, dukan mu kuwa an shayar da mu Ruhu daya.14Gama jiki ba daya ba ne sungun, amma gabobi ne da yawa. 15Idan kafa ta ce, "tun da dai ni ba hannu ba ne to ni ba fannin jikin bane," wannan baya rage masa matsayin sa a jikin ba. 16Kuma da kunne zaya ce, '"Da yake ni ba ido ba ne, ai, ni ba gabar jiki ba ne," fadar haka ba za ta raba shi da zama gabar jikin ba. 17Idan dukan jikin ya kasance ido ne da me za a ji? Da dukan jikin kunne ne, da me za a sunsuna?18Amma Allah ya shirya gabobin jiki bisa ga tsarin sa. 19Amma da duk jiki gaba daya ce, da ina jikin zai kasance? 20Ga shi akwai gabobi da yawa, kuma jiki daya ne.21Ba da ma ido ya fadawa hannu, "Bana bukatar ka," ko kuma kai ya fadawa kafafu, "Ba na bukatar ku." 22Amma, sai ma gabobin da ake gani kamar raunannu su ne masu humimmanci, gabobin jiki kuwa da ake gani kamar sun kasa sauran daraja, mu kan fi ba su martaba. 23Ta haka gabobinmu marasa kyan gani, akan kara kyautata ganinsu. Gabobin mu masu kyan kuma ba sai an yi masu ado ba. 24Amma Allah ne da kansa ya hada jiki, yana bada mafificiyar martaba ga kaskantacciyar gaba.25Yayi haka ne domin kada a sami tsattsaguwa a cikn jikin, amma domin gabobin su kula da juna da matsananciyar lura. 26Kuma idan gaba daya na wahala, dukan gabobin suna wahala tare. ko kuma idan an girmama gaba daya, dukan gabobin na farin ciki tare. 27Yanzu ku jikin Almasihu ne, saboda haka kuma kowannen ku gabarsa ne.28A cikin ikilisiya, Allah ya sa wasu su zama, na farko manzanni, na biyu annabawa, na uku masu koyarwa, sa'an nan sai masu yin ayyukan iko, sai masu aikin warkarwa, da masu bayar da taimako, da masu aikin tafiyar da al'amura, da masu harsuna daban daban. 29To kowa manzo ne? ko kuwa duka annabawa ne? ko kuma duka masu koyarwa ne? Kowa ne ke yin manyan ayyukan iko?30Ko kuwa dukan su ne suke da baiwar warkarwa? Dukan su ne ke magana da harsuna? ko kuma dukan su ne ke fassara harsuna? 31Amma bari ku himmantu ga neman baiwa mafi girma. Kuma zan nuna maku wata hanya mafificiya.
Bulus ya nuna masu cewa Allah ya ba wa masubi kyauta na musamman. Waɗannan kyautane za su taimaka wa taron masubi.
AT: "Ina so ku sani"
Anan "ruɗi" magana ne game da kawas da shakan yin abin da ba daidai ba. Rudawa ga gumakai na wakilcin rashin kawas da shaka ga bautar gumakai. Ana iya bayana wannan zance a cikin siffa "an ruɗe" da "sun ruɗe ku". AT: "kun riga kun kawas da shaka a wadansu hanyoyin bautar gumakai da ba su iya magana ba" ko kuma "kun yarda da karya shi ya sa kun bauta wa gumakai da ba su iya magana ba"
AT: 1) "ba bu mai bi wadda yana da Ruhun Allah a cikinsa zai iya ce" ko kuma 2) "ba bu wadda yake yin annabci da iƙon Ruhun Allah da zai iya ce."
"Allah zai hukunta Yesu" ko kuma "Allah zai sa Yesu ya sha wahala"
"sa kowa ya kasance da su"
Ana iya bayyana wannan a cikin sifar aiki. Allah ne mai yin bayarswa 12:6. AT: "Allah yana ba wa kowane daya"
AT: Ta wurin Ruhu, Allah ya na ba mutum daya kalmar"
"sakon"
Allah ya na ba da kyautani ta wurin aikin Ruhu.
Bambancin kalmominnan a nan ba su da amfani domin Allah ne ya ba da su ta Ruhu daya.
Bulus yana bayyana wata ra'ayi ta wurin kalmomi biyu. AT: "kalmomin hikima"
Bulus yana bayyana wata ra'ayi ta wurin kalmomi biyu. AT: "kalmomin da suke nuna sani"
Ana iya bayyana wannan a cikin sifar aiki. Dubi yadda an fasara wannan a cikin 12:8. AT: "Allah ya bayar"
An fahimci kalmomin "an bayar" a jumla da ya wuce. AT: "ga wani kuwa an ba shi baiwar warkarwa ta wurin wannan Ruhun"
An fahimci jumlan "an bayar ta Ruhu daya" a jumla da ya wuce. AT: "ga wani kuwa an ba shi annabci ta wurin wannan Ruhun"
An fahimci jumlan "an bayar ta Ruhu daya" a jumla da ya wuce. AT: "ga wani harsuna daban daban ta wurin wannan Ruhun"
Anan "harsuna" na wakilcin yararruka. AT: "baiwar fassarar harsuna dabam dabam"
An fahimci jumlan "an bayar ta Ruhu daya" a jumla da ya wuce. AT: "ga wani fassarar harsuna ta wurin wannan Ruhun"
Wannan baiwan jin abin da wani ya faɗa a wata harshe domin a iya fasara wa mutane a wata harshe abin da wannan mutumin yake faɗa. AT: "baiwar fasara abin da ana faɗa a waɗansu harshen"
Allah ya na ba da kyautan nan ta wurin aikin Ruhu mai Tsarki kadai. Dubi yadda an fasara wannan a cikin 12:8.
AT: 1) Ruhu mai Tsarki ne yake yi mana baftisma, "Don Ruhu daya ne ke yi mana baftisma " ko kuma 2) Ruhun, kamar ruwar baftisma, shi ne abin da ake yi mana baftisma zuwa cikin jiki, "Gama ta Ruhu daya aka yi wa mana baftisma"
"dauri" magana ne game da "bayi." AT: "ko bayin mutane ko 'ya'yan mutane"
AT: "Allah ya bamu Ruhu iri daya, muna raɓa Ruhun kamar yadda mutane na iya raɓa abin sha"
Ana iya sa wannan a jumla. AT: "ba ku iya jin komai ba ... ba ku iya sunsuna komai ba"
Kalmar "gabibi" kalma ne game da sashin jiki, kaman kai, hamata ko gwiwa. AT: "irin sashin jiki ɗaya"
Ana iya sa wannan a jumla. AT: "ba za a sumu jiki ba"
"ba na bukatanku"
"mara amfani"
Wannan na iya nufin sashin siri na jikin mu wadda mutane ke rufewa.
"ana iya hadda jikin , kuma"
AT: "wani ya na daraja gabobi daya"
Ana amfani da kalmar "yanzu" anan domin a jawo hankali zuwa ga muhimmin magana.
AT: 1) "Kyauta na farko cda zan faɗa shi ne manzanni" ko kuma 2) "Kyauta muhimmi shi manzanni."
"masu tanada taimako wa sauran masubi"
"waɗanda suke bi da ikilisiya"
mutumin da na iya magana a harshe daya ko biyu na wata kasa da bai taba koya ba.
Bulus yana tuna wa masu sauraransa game da abin da sun riga sun sani. AT: "Waɗansunsu ne kadai manzanni. Waɗansunsu ne kadai annabawa. Waɗansunsu ne kadai masu koyarwa. Waɗansunsu ne kadai ke yin manyan ayyukan iƙo."
Wannan na iya zama jumla. AT: "Ba dukan su ba ne ke da baiwar warkarwa ba."
Wannan na iya zama jumla. AT: "Ba dukan su ba ne ke magana da harsuna ba."
Wannan na iya zama jumla. AT: "Ba dukan su ba ne ke fassara harsuna ba."
Wannan na nufin gayawa wadansu abin da wani ya faɗa a harshen da basu gane. Dubi yadda an fasara wannan a cikin 2:13
AT: 1) "Dole ne ku bida da marmari kyauta daga Allah da ke taimakon ikilisiya." ko kuma 2) "Ku na nema da marmari kyautanni da ku ke tunani sun fi domin ku na tunani sun fi kyau."
1Koda ya zamanto ina magana da harsunan mutane, har ma da na mala'iku, amma kuma ba ni da kauna, na zama kamar kararrawa mai yawan kara, ko kuge mai amo. 2Ko da ya zamanto ina da baiwar annabci kuma na fahimci dukkan boyayyar gaskiya, da dukkan ilimi, ko ina da matukar bangaskiya, har ma zan iya kawar da duwatsu. muddin ba ni da kauna, ni ba komai ba ne. 3Ko da ya zamanto na bayar da dukan mallakata domin a ciyar da matalauta, in kuma mika jikina domin a kona. Amma in ba ni da kauna, ban sami ribar komai ba. (Na bayar da jikina ne domin inyi fahariya).4Kauna na da hakuri da kirki. kauna bata kishi ko fahariya. kauna ba ta girman kai 5ko fitsara. Bata bautar kanta. Bata saurin fushi, kuma bata ajiyar lissafin laifuffuka. 6Bata farin ciki da rashin adalci. A maimako, tana farin ciki da gaskiya. 7Kauna tana jurewa cikin dukan abubuwa, tana gaskata dukan abubuwa, tana da yarda game da dukan abubuwa, tana daurewa dukan abubuwa.8Kauna ba ta karewa. Idan akwai anabce anabce, zasu wuce. Idan akwai harsuna, zasu bace. Idan akwai ilimi, zaya wuce. 9Domin muna da sani bisa - bisa kuma muna anabci bisa - bisa. 10Sa'adda cikakke ya zo, sai marar kammalar ya wuce.11Da nake yaro, nakan yi magana irinta kuruciya, nakan yi tunani irin na kuruciya, nakan ba da hujjojina irin na kuruciya. Da na isa mutum na bar halayen kuruciya. 12Gama yanzu muna gani sama - sama kamar ta madubi, amma a ranar fuska da fuska, yanzu na sani bisa - bisa, amma a lokacin zan sami cikakken sani kamar yadda aka yi mani cikakken sani. 13To, a yanzu abubuwan nan uku sun tabbata: bangaskiya, da gabagadi mai zuwa, da kuma kauna, amma duk mafi girma a cikinsu ita ce kauna.
Bayan da Bulus ya gama magana game da kyautanni da Allah ya ba wa masubi, Bulus ya nanata abin da ke da muhimmi.
AT: 1) Bulus yana zuguiguitawa don fahimta ne kuma be yarda cewa mutane na yin harshen da mala'iku ke amfani ba, ko kuma 2) "Bulus yana tunani cewa waɗansun da suke magana a harsuna ne masu magana a harshen mala'iku.
na zama kama kayan kiɗe-kiɗe dake yin yawan kara, kara mai bata rai
Baban, tsiriri, mulmulallen kuwanon ƙarfe da ake bugawa da sanda domin ya yi kara mai yawa
gongoni biyu, mulmulallen kuwanon ƙarfe da ake buga wa tare domin ya yi kara
Ana iya bayyana wannan jumla " domin a kona". AT: "Na bar wadda sun hukunta ni su ƙone ni har ga mutuwa"
Anan, Bulus yana magana game da kauna kamar mutum ne.
AT: "Ba bu wadda zai iya sa shi fushi da sauri"
AT: "Ya na farinciki a adalci ne kadai da kuma gaskiya"
Madubi a zamanin Bulus an a yin su da karfe mai kyau maimakon glass kuma ya na nuna abu ba da haske sosai ba.
AT: 1) "yanzu mun ga Almasihu" ko kuma 2) "yanzu mun ga Allah."
"amma za mu gan gan Almasihu fuska da fuska". Wannan na nufin cewa za mu kasance a gaban Almasihu.
An fahimci kalmar "Almasihu". AT: "Zan san Almasihu cikakke"
AT: "Kamar yadda Almasihu ya san ni cikakke"
Ana iya bayana wannan magana. AT: "Dole ne mu gaskanta da Ubangiji, ku sani da gabagadi cewa zai yi abin da ya yi alkawari, ƙaunacee shi da waɗansun"
1Ku dafkaci kauna kuma ku himmatu domin baye bayen ruhaniya, musamman domin kuyi anabci. 2Domin wanda yake magana da harshe bada mutane yake magana ba amma da Allah. domin babu mai fahimtarsa saboda yana zancen boyayyun abubuwa ciki Ruhu.3Amma wanda yake anabci da mutane yake magana domin ya gina su, ya karfafa su, kuma ya ta'azantar dasu. 4Wanda yake magana da wani harshe, kansa yake ginawa, amma mai yin annabci kuwa, ikilisiya yake ginawa.5To, fatana ace dukan ku kuna magana da harsuna. Amma fiye da hakama, fatana ace kuyi anabci. Wanda yake anabci yafi wanda yake magana da harsuna (sai dai idan wani ya fassara domin ikilisiya ta ginu). 6Amma yanzu, 'yan'uwa, in na zo wurin ku ina magana da harsuna, ta yaya zaku karu dani? ba zaya yiwu ba, sai idan nayi maku magana da wahayi, ko sani, ko anabci, ko koyarwa.7Idan kayan kida marasa rai suna fitar da sauti - kamar su sarewa da algaita - kuma basu fitar da amo daban daban, ta yaya wani zaya san irin amon da sarewar da algaitar suke kadawa? 8Domin idan aka busa kaho da sauti marar ma'ana, ta yaya wani zaya san lokacin da ya dace ya shirya zuwa yaki? 9Haka yake game da ku. Idan kuka furta zance marar ma'ana, ta yaya wani zaya fahimci abinda kukace? zaku yita magana, kuma babu wanda zaya fahimce ku.10Babu shakka akwai harsuna daban daban a duniya, kuma babu wanda baya da ma'ana. 11Amma idan ban san ma'anar wani harshe ba, zan zama bare ga mai maganar, kuma mai maganar zaya zama bare a gareni.12haka yake gare ku. Tun da kuna da dokin bayyanuwar Ruhu, ku himmatu da habaka cikin gina ikilisiya. 13To wanda yake magana da harshe yayi addu'a domin ya iya fassarawa. 14Domin idan nayi addu'a da harshe, ruhuna yayi addu'a, amma fahimtata bata karu ba.15To, me zan yi? Zan yi addu'a da ruhuna, in kuma yi addu'a da fahimtata. Zan yi raira waka da ruhuna, kuma in raira waka da fahimtata. 16In ba haka ba, idan ka yi yabon Allah da ruhu kawai, ta yaya wanda yake waje zai ce, "Amin" a kan godiyar da kake yi in bai san abin da kake fada ba?17Babu shakka kayi godiya sosai, amma wanin baya ginu ba. 18Nagodewa Allah ina magana da harsuna fiye da ku duka. 19Duk da haka dai a taron ikilisiya na gwammace in yi magana da kalmomi biyar cikin fahimta saboda inganta wadansu fiye da dubu goma da harshe.20'Yan'uwa, kada ku zama yara cikin tunani, sai dai a wajen aikin mugunta, ku yi halin jarirai, amma a tunaninku ku girma. 21A rubuce yake a shari'a cewa, "zan yi magana da mutanen nan ta wurin mutane masu bakin harsuna, da kuma lebunan baki. Duk da haka kuwa ba za su saurare ni ba", in ji Ubangiji.22Amma harsuna alamu ne, ba ga masu bada gaskiya ba, sai dai ga marasa ba da gaskiya. Annabci kuwa alama ce ga masu ba da gaskiya, amma ba don marasa bangaskiya ba. 23Saboda haka, in dukan ikilisiya ta taru, kowa kuwa yana magana da wasu harsuna, wadansu na waje da kuma marasa ba da gaskiya suka shigo, ashe, ba sai su ce kun haukace ba ba?24In kuwa kowa yana yin annabci, wani kuma marar ba da gaskiya ko wani daga waje ya shigo, maganar kuwa zata ratsa shi. Za a ma hukanta shi a kan maganar, 25asiran zuciyarsa kuma za su tonu. Sakamokon haka, sai ya fadi ya yi wa Allah sujada, zaya furta cewa lallai Allah yana tare da ku.26Sai me kuma 'yan'uwa? idan kuka tattaru, wani yana da zabura, koyarwa, wahayi, harshe, ko fassara. Kuyi komai domin gina ikilisiya. 27Idan wani yayi magana da harshe, bari a sami mutum biyu ko uku a yawansu, kuma kowa yayi daya bayan daya. Sai wani ya fassara abinda aka fada. 28Amma idan babu wanda zaya fassara, bari dukansu suyi shiru a ikilisiya. Bari kowa yayi wa kansa maganar a gida shi kadai da kuma Allah.29Bari annabawa biyu ko uku suyi magana, bari sauran su saurara tare da bambance abinda ake fada. 30Idan kuma anba wani fahimta wanda yana zaune a cikin sujadar, bari wanda yake ta magana kafin yanzu yayi shiru.31Dukanku kuna iya yin annabci daya bayan daya, domin kowannen ku yayi koyi, a kuma samu karfafawa. 32Gama ruhohin annabawa suna karkashin annabawa, 33domin Allah ba Allahn rudu ba ne, na salama ne. Haka yake kuwa a duk ikllisiyoyin masu bangaskiya.34Mataye suyi shiru a ikilisiyoyi. Domin ba a basu dama ba suyi magana. A maimako, su zama masu sadaukar da kansu, kamar yadda doka ta ce. 35Idan akwai abinda suke so su koya, bari su tambayi mazajen su a gida. Domin abin kunya ne mace tayi magana a ikilisiya. 36Daga wurinku maganar Allah ta zo ne? ko kuwa a gare ku kadai ta iso?37In wani yana zaton shi ma annabi ne, ko kuwa mai ruhaniya, to, sai ya fahimta, abin nan da nake rubuta maku umarni ne daga wurin Ubangiji. 38In kuwa wani ya ki kula da wannan, shi ma kada a kula da shi.39Saboda haka, 'yan'uwa, ku yi marmarin yin annabci sosai, sa'an nan kada ku hana kow yin magana da harsuna. 40Sai dai a yi komai ta hanyar da ta dace bisa ga tsari.
Bulus yana so su sani cewa ƙodashiƙe koyarwa ya na muhimminci sosai don yana umurta mutane, yakamata a yi shi a cikin kauna.
Bulus ya na magana game da kauna kamar mutum ne. "ku bi bayan kauna" ko kuma "yi aiki sosai domin ku ƙaunace mutane"
"yi aiki sosai domin ku iya yin anabci"
Gina mutane na wakilcin taimaka ma su domin su yi girma da karfi a cikin bangaskiya. Dubi yadda kun fasara "ginawa" a cikin 8:1. AT: "domin a karfafa su"
Gina mutane na wakilcin taimaka ma su domin su yi girma da karfi a cikin bangaskiya. Dubi yadda kun fasara "ginawa" a cikin 8:1. AT: "karfafa mutane"
Bulus ya na nanata cewa kyautar anabci ya fi kyautar magana da harsuna. AT: "Wanda yake anabci, ya ke da babban kyauta"
Wannan na nufin faɗa wa wadansu abin da wani ya ce a a harshen da basu gane ba. Dubi yadda an fasara wannan a cikin 2:13.
Wannan na iya zama jumla. AT: "Ba zan amfane ku ba." ko kuma "Da ban yi abin da zai taimake ku ba."
Wannan na nufin karan jifa dabam dabam da suke yin launin waƙa, ba ba bambaci a sakanin karan galgaita da sarewa ba.
Bulus yana son Korontiyawan su amsa wannan tambayan da kansu. AT: "ba wadda zai san irin amon da sarewar da algaitar suke kadawa."
launin ko waƙa
Bulus yana son Korontiyawan su amsa wannan tambayan da kansu. AT: "ba wadda zai san lokacin da ya dace a shirya wa yaƙi."
AT: "su na da ma'ana"
"yin abin da ke nuna cewa Ruhu ne na bi da ku"
Bulus ya yi magana game da ikilisiya kamar gida ce da wani zai iya gina, da kuma aikin gina ikilisiya kamar abu ne da mutum zai iya girba. AT: "domin cin nasara sosai a sa mutanen Allah su bauta masa"
Wannan na nufin gaya wa wadansu abin da wani ya ce a a harshen da basu gane ba. Dubi yadda an fasara wannan a cikin 2:13.
An yi maganar rashin fahimtar zuciya game da abin da ake yin addu'a, don haka, maganar rashin karban riba daga addu'a na kamar "hankalin da bata karu ba." AT: "A cikin hankalina da ban gane ba" ko kuma "hankalina ba shi da riba a addu'an, domin ban gane kalmomin da na ke faɗa ba"
Bulus ya na gabatar da kalmasawarsa. AT: "Ga abin da zan yi."
Dole ne addu'a da waƙoki su kasance a harshen da mutanin da sun hallaru su iya ganewa.
"da kalmar da zan gane"
Ƙodashiƙe "ku" anan daya ne, Bulus ya na magana da kowane mutum da ke addu'a a cikin ruhu kadai, amma ba tare da zuciya ba.
Wannan na iya zama jumla. AT: "wanda yake waje ba zai iya ce, 'Amin' ba ... faɗa ba."
AT: 1) "wani mutum" ko kuma "mutane da su sabobi ne a kungiyan ku."
"iya yarda"
Bulus ya na magana da Korontiyawan kamar su mutum daya ne, kalmar "ku" daya ne anan.
Gina mutane na wakilcin taimaka masu su yi girma da karfi a cikin bangaskiya. Dubi yadda za ku fasara "ginu" a cikin 8:1. AT: "dayan mutumin bai karfafu ba" ko kuma" abin da ku ka faɗa ba ya karfafa bare da zai iya ji ba"
Ba kirgen kalmomi ne Bulus yake yi ba, amma ya yi amfani da maganan domin ya nanata cewa kalmomi kadan da ana iya fahimta ya fi daraja fiye da lamban kalmomi a cikin harshen da mutane ba za su iya fahimta ba. AT: "kalmomi 10,000" ko kuma "yawan kalmomi"
Bulus ya faɗa masu cewa manzo Ishaya ya yi magana game da magana a cikin harsuna dabam dabam a shekaru dadama ta ta wuce kafin magana a waɗansu harsuna ya faru a farkon ikilisiyan Almasihu.
Anan "yara" magana ne game da rashin girma a ruhaniya. AT: "kada ku yi tunani kamar yara"
AT: "Manzo ne ya rubuta waɗannan kalmomi a cikin shari'a:"
Waɗannan jumlan na nufin abu iri daya kuma domin nanatawa, an yi amfani da su.
Ana iya bayyana a kuma hada wannan jumla da kyau. AT: "ga masubi ne kadai"
AT: "za su ce ku na hauka."
A takaice, Bulus ya faɗa abu biyu domin nanata. AT: "zai gane cewa yana da laifin zunubi domin ya na ji abin da kuke faɗa"
Anan "zuciya" magana ne game da tunanin mutum. AT: "Allah zai bayyana ma sa asiran da yake cikin zuciyar shi" ko kuma "zai gane asirin zurfin tunanin sa"
"fadi" karin magana ne da ke nufin durkusawa. AT: "zai durkusa ya yi wa Allah yabo"
Bulus ya yi amfani da tambaya domin ya gabatar da sakon sa. AT: "Domin komai da na faɗa maku gaskiya ne, ga abin da ya kamata ku yi, yan'uwana masubi."
"kuma su yi magana daya bayan daya"
AT: "fasara abin da sun faɗa"
Wannan na nufin gaya wa waɗansu abin da wani ya ce a a harshen da basu gane ba. Dubi yadda an bayana "fassara" a cikin 2:13.
AT: 1) annabawa biyu ko uku suke yin magana a taro. ko kuma 2) annabawa biyu ko uku ne suke magana a loƙacin da ya kamata.
AT: "ga abin da sun ce"
AT: "Idan Allah ya ba wani fahimta"
mutum daya ne kadai zai yi annabci ɗai bayan ɗai.
AT: "za ku iya karfafa duka"
Allah ba ya halitan yanayin rudu ta wurin sa mutane su yi magana a loƙaci ɗaya ba.
AT: 1) daina magana, 2) daina magana a loƙacin da wani yake yin anabci, ko kuma 3) ku yi shiru a loƙacin sujada.
Bulus ya nanata cewa ba Korontiyawa kadai ba ne suka fahimci abin da Allah ya ke so masubi su yi ba. AT: "maganar Allah bai zo daga wurin ku a Koronti ba; ba ku ne kadai mutanen da sun fahimci nufin Allah ba."
"maganar Allah" zance ne game da sako daga Allah. AT: "sakon Allah"
Manzon gaskiya ko mutum mai ruhun gaskiya ne zai karba rubutun Bulus yadda ya zo daga Allah.
AT: "kada ku kula da shi"
Bulus ya bayyana cewa an amincecce ne da kuma karbabbe ne magana a cikin harsuna a taron ikilisiya.
Bulus ya na nanata cewa a dinga yin taron ikilisiya a hanyar da ta ɗace. AT: "Amma ku yi komai ta hanyar da ta dace bisa ga tsari" ko kuma "Amma ku yi komai ta hanya da ta ɗace, hanya mai kyau"
1Yanzu ina tunashshe ku 'yan'uwa, game da bisharar nan da nake shelarwa, wadda kuka karba kuke kuma dogara da ita. 2Da wannan bishara aka yi maku ceto, idan kuka rike wa'azi da na yi maku da karfi, sai in dama kun gaskanta a banza.3Domin na baku muhimmin sako kamar na farko da na karba: cewa Almasihu ya mutu domin zunubanmu, bisa ga nassosi, 4cewa kuma an bizne shi, ya kuwa tashi daga matattu a rana ta uku bisa ga nassosi.5Cewa kuma ya bayyana ga Kefas, sa'an nan ga sha biyun. 6Daga nan ya bayyana ga 'yan'uwa sama da dari biyar a lokaci guda. Wadanda mafi yawan su na da rai har yau, amma wasun su sun yi barci. 7Daga nan ya bayyana ga Yakubu, da kuma ga manzannin duka.8A karshe, sai ya bayyana a gare ni, kamar dan da aka haifa bakwaini. 9Gama ni ne mafi kankanta a cikin manzanni. Ban cancanci a kira ni manzo ba, domin na tsanantawa ikklisiyar Allah.10Amma saboda alherin Ubangiji ina matsayin da nake a yau, kuma alherin sa da ke ciki na ba a banza yake ba. A maimako, nayi aiki tukuru fiye da su duka. Amma duk da haka ba ni bane, amma alherin Allah da ke tare da ni. 11Saboda haka ko nine ko Su, haka mukayi wa'azin, haka kuma kuka gaskata.12To idan anyi shela a matsayin cewa Yesu ya tashi daga matattu, tayaya wadansunku su ke cewa babu tashin matattu? 13Amma idan babu tashin matattu, Almasihu ma ai ba a tashe shi ba kenan. 14idan kuwa ba a tashi Almasihu ba, wa'azin mu ya zama banza kenan, haka kuma bangaskiyar ku ta zama banza.15Mun kuma zama shaidun karya game Allah kenan, muna shaida akan Allah cewa ya tashi Almasihu daga matattu alhali ko bai tashe shi ba. 16Domin idan babu tashin matattu, kai, ko Almasihu ma ba a tashe shi ba kenan. 17Idan har ba a tashi Almasihu ba, bangaskiyar ku a banza take, har yanzu kuma, kuna cikin zunuban ku.18To wadanda suka mutu cikin Almasihu kuma sun hallaka kenan, 19idan a wannan rayuwa ce kadai muke da bege cikin Almasihu, to cikin dukkan mutane munfi kowa zama abin tausayi.20Amma yanzu, Almasihu ya tashi daga matattu, wanda ya sa shi ya zama nunar fari cikin tashi daga matattu. 21Domin yadda mutuwa ta shigo duniya ta hanyar mutum guda, hakkan nan ma tashi daga matattu.22Gama kamar yadda a cikin Adamu duka suka mutu, haka kuma a cikin Almasihu za a rayar da duka. 23Amma kowanne da tsarinsa: Almasihu, nunan fari, sannan su wadanda ke na Almasihu za a rayar da su lokacin zuwansa.24Sa'an nan karshen zai gabato, lokacin da Almasihu zai mika mulkin ga Allah Uba. sa'an nan ne zaya kawar da dukkan mulki, martaba da iko. 25Gama mulkinsa zai habaka har sai ya sa dukkan makiyansa a karkashin sawayen sa. 26Mutuwa kuwa, ita ce makiyi na karshe da za'a hallaka.27Domin " yasa dukkan komai a karkashin ikonsa," Amma da aka ce" yasa dukkan komai a karkashin ikonsa," a sarari yake cewa wannan baya hada da wanda yasa dukan komai a karkashin ikonsa ba. 28Idan dukan abu na karkashin mulkinsa, to Dan da kansa zaya kasance a karkashin ikon shi wanda yasa komai a karkashin ikonsa. Wannan zaya kasance ne saboda Allah Uba ya zama dukkan komai cikin dukkan komai.29ko kuma me zai faru da wadanda ake yi wa baftisma domin matattu? Idan kuwa babu tashin matattu sam sam, ina amfanin yi masu baftisma domin su? 30Kuma me yasa muke cikin hadari kowace sa'a?31Ina mutuwa kullum. Wannan nake furtawa ta wurin fahariya, 'yan'uwa, wadda nake da ita cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu. 32Menene ribata, a idanun mutane, idan nayi kokowa da bisashe a Afisa, idan babu tashin matattu? "bari mu ci mu sha, domin gobe zamu mutu."33Kada fa a yaudare ku, domin " tarayya da mugaye takan bata halayen kirki." 34"Ku natsu! kuyi zaman adalci! kada ku cigaba da zunubi. Domin wasunku basu da sanin Allah. Ina fadar wannan domin in baku kunya.35Amma wani zaya ce, "Yaya za'a yi tashin matattu? Wane irin jiki kuma zasu tashi da shi? 36Ku jahilai ne sosai! Abinda ka shuka ba zaya fara girma ba sai ya mutu.37Abinda ka shuka ba jikin da zaya kasance bane, amma kwayar irin ne kawai. Wanda zaya zama alkama ko wani abu daban. 38Amma Allah zaya bashi jiki yadda ya zaba, ga kowane kwayar iri da nashi jikin. 39Ba duka jiki ne yake iri daya ba. A maimako, akwai jiki irin na mutane, akwai kuma wani irin na dabbobi, kuma wani jikin irin na tsuntsaye, kuma da irin na kifi.40Akwai kuma jikina na samaniya da jikina na duniya. Amma daukakar jikin samaniya wata daban ce kuma daukakar jikin duniya daban ce. 41Akwai daukaka irin ta rana, da kuma wata daukakar irin ta wata, da kuma wata daukakar irin ta taurari. Domin wani tauraron ya bambanta da wani wajen daukaka.42Haka yake a tashin matattu. Abinda aka shuka mai lalacewa ne, wanda aka tayar marar lalacewa ne. 43An shuka shi cikin rashin daraja; an tayar da shi cikin daukaka. An shuka shi cikin rauni; an tayar da shi cikin iko. 44An shuka shi jiki na zahiri; an tayar da shi jiki na ruhaniya. Idan akwai jiki na zahiri, to akwai jiki na ruhaniya.45Haka kuma aka rubuta, "Adamu na farko ya zama rayayyen taliki." Adamu na karshe ya zama Ruhu mai bayar da rai. 46Amma na ruhaniyar ba shine ya fara zuwa ba amma na zahirin, daga nan na ruhaniyar.47Mutumin farkon ai daga turbaya ya fito, wato na duniya. Amma shi na biyun daga sama yake. 48kamar yadda mutumin ya fito daga turbaya haka ma wadanda aka halitta da turbaya. kamar yadda mutumin yake daga sama haka ma wadanda ke na sama. 49Kamar yadda muke dauke da jiki mai kamannin turbaya, haka ma zamu kasance da kamannin mutumin sama.50To wannan na fada, 'yan'uwa, cewa nama da jini ba za su gaji mulkin Allah ba. Haka kuma mai lalacewa ba za ya gaji marar lalacewa ba. 51Duba! ina gaya maku asirtacciyar gaskiya: Ba dukanmu zamu mutu ba, amma dukanmu za a canza mu.52Za a canza mu nan da nan, cikin keftawar ido, a kaho na karshe. Domin za a busa kaho, kuma za a tada matattu marasa lalacewa, kuma za a canza mu. 53Domin wannan jiki mai lalacewa dole ya sanya jiki marar lalacewa, kuma wannan jiki mai mutuwa dole ya sanya marar mutuwa.54Amma idan wannan jiki mai lalacewa ya sanya marar lalacewa, kuma wannan jiki mai mutuwa ya sanya marar mutuwa, sai abinda aka rubuta ya cika, "An hadiye mutuwa cikin nasara." 55"Mutuwa, ina nasararki? Mutuwa, ina dafinki?"56Gama dafin mutuwa zunubi ne, kuma ikon zunubi shari'a ce. 57Amma godiya ga Allah, wanda ya bamu nasara ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu!58Saboda haka, ya ku 'yan'uwana kaunatattu, ku dage kuma kada ku jijjigu. Ko yaushe ku habaka da aikin Ubangiji, domin kun san cewa aikinku cikin Ubangiji ba a banza yake ba.
Bulus ya tuna masu cewa bishara ne ta cece su ya kuma faɗa masu abin da bisharan ke nufi. Ya ba su dan darasin tarihi, wadda ya kamala da abin da zai faru.
"taimake ku tunawa"
Bulus ya na magana game da Korontiyawa kamar su gini ne da kuma bishara kamar ita ce tushen da gidan ya ke dogara a kai.
AT: "Allah zai cece ku"
"sakon da nake iya maku wa'azin"
AT: 1) kamar mafi muhimincin abubuwa dayawa ko kuma 2) kamar na farko a cikin lokaci.
"biya domin zunubanmu" ko kuma "domin Allah ya iya yafe zunubanmu"
Bulus ya na nufin rubutun Tsohon Alkawari.
AT: "sun bizne shi"
AT: "Allah ya tashe shi"
"an sa shi ya rayu kuma"
"nuna kansa wa"
500
"barci" anan magana ne game da mutuwa. AT: "waɗansu sun mutum"
"A karshe, bayan ya bayyana ga wadansun"
Wannan magana ne da Bulus na iya nufin cewa ya zama mai bi a bayan sauran manzanin. ko kila ya na nufin cewa, ba kamar sauran manzanin ba, bai gan hidimar Yesu na shekara uku ba. AT: "wani da ya rasa ayukan waɗansu"
Alherin Allah ko kauna ne ya sa Bulus a yadda yake yanzu.
Bulus ya na nanatawa ta wurin magana cewa Allah ya yi aiki ta wurin Bulus. AT: "domin ya yi mun kirki, na iya yin aiki mai kyau"
Bulus ya yi magana game da aiki da ya iya yi domin Allah ya yi masa kirki, kamar Alherin ne ya ke yin aikin. AT: 1) Wannan gaskiya ne, kuma Allah ya yi aikin ya kuma yi amfani da Bulus da kyau a matsayin kayan aiki ko kuma 2) Bulus ya na amfani da magana, da cewa Allah ya so Bulus ya yi aikin ya kuma sa aikin Bulus ya sami sakamako mai kyau.
Bulus ya na amfani da wannan tambayan domin ya fara sabon batu. AT: "ku daina faɗa cewa babu tashin matattu!"
Bulus yana amfani da wannan magana domin ya tabbatar da cewa akuwai tashin matattu. Ya san cewa Almasihu ya tashi, shi ya sa ya bayyana cewa akuwai tashin matattu. Faɗa cewa babu tashin matattu na nan kamar cewa Almasihu bai tashi ba, amma wannan karya ne domin Bulus ya gan Almasihun da ya tashi 15:8.
AT: "Allah bai tashe Almasihu ba"
sa rayayye kuma
Bulus ya na bayyana cewa idan Almasihu bai tashi daga matattu ba, ya zama su na shaida karya ko kuma suna karya game da zuwan Almasihu kuma.
AT: "kowa za su gane cewa mu"
bangaskiyar su na kan Almasihu da ya tashi daga mattatu, da haka bai faru ba, da bangaskiyar su ya zama ba bu amfani.
"na kowa, tare da masubi da kuma marasa bi"
"mutane su ji tuasayin mu fiye da yadda suke ji ma waɗansu"
"kamar yadda yake, Almasihu" ko kuma "wannan ne gaskiyan: Almasihu"
Anan "nunar fari" magana ne da ke kwatanta Almasihu da girbin farko, da ke biye da sauran girbin. Almasihu ne na farko da ya tashi daga matattu. AT: "wadda yake kamar na farkon a girbi"
"tashi" karin magana ne game da "sa ya rayu kuma." AT: "Allah ya tashe Almasihu, wanda shi ne nunar fari na wadda sun mutu"
Ana iya bayyana kalmar "mutuwa." AT: mutane na mutuwa domin mutum daya"
Ana iya bayyana kalmar "tashi." AT: "mutane na tashi daga matattu saboda wani mutum"
Anan kalmomin "shi" da "na shi" na nufin Almasihu.
"zai hana mutanen da suke mulki, wadda suke da iƙon aikata abin da su ke aikatawa"
Sarakuna da sun ci yaƙi za su sa ƙafafunsu a wuyan wadanda sun yake su. AT: "sai Allah ya hallaƙa dukka maƙiyan Almasihu gabadaya"
Bulus ya yi magana game da mutuwa kamar mutum ne wadda Allah zai kashe. AT: "mutuwa ce maƙiya na karshe wadda Allah zai hallaƙa"
Sarakuna da sun ci yaƙi za su sa ƙafafunsu a wuyan waɗanda sun yake su. Dubi yadda an fasara "sa ... a karkashin iƙonsa" a cikin 15:25. AT: "Allah ya hallaƙa dukka maƙiyan Almasihu gabadaya"
AT: "Allah ya sa komai a karkashin iƙon Almasihu"
AT: "Ɗan da kansa zai yi zama a karkashi"
A cikin ayoyin da suka wuce, an kira shi "Almasihu." AT: "Almasihu, Ɗan da kansa"
Wannan lakami ne na muhimmi da ke kwatanta ɗangantaka a sakanin Yesu da Allah.
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya koya wa Korontiyawa. AT: "in ba haka ba zai zama da rashin amfani wa masubi su karbi baftisma wa matattu."
Bulus ya yi amfani da wata yanayi domin ya bayana cewa ana tashin matattu. Faɗa cewa ba bu tashin matattu na nan kamar faɗan cewa kada mutane su yi baftisma domin matattu. Amma waɗansu mutane, watakila waɗansu mutanin ikilisiyan Koronti, sun yi baftisma domin matattu, don haka ya na zata cewa waɗanan mutanin sun yi baftisma domin matattu don sun gaskanta cewa akowai tashin matattu.
AT: "Allah baya tashin matattu"
"ba a sa ya rayu kuma"
Bulus ya yi amfani da wannan tambaya domin ya koyar da Korontiyawan. AT: "basu da dalilin da mutane za su yi ma su baftisma a madadin matattu ba."
Bulus ya yi amfani da wannan tambaya domin ya koyar da Korontiyawan. Dalilin da shi da sauran sun shiga hadari shine waɗansu mutane sun yi fushi cewa suna zato Yesu zai tashe mutane daga matattu. AT: "Idan mutane baza su tashi daga matattu ba, bamu da riban komai a kasancewan mu a cikin hadarin kowace sa'a na koya cewa mutane za su tashi."
Anan "fuskanta mutuwa" na wakilcin sanin cewa zai mutu jim kaɗan. Ya san cewa waɗansu mutane sun so su kashe shi domin ba su so abin da yake koyarwa ba. AT: "Kullum ina yin kasada da rai na!"
Bulus ya yi amfani da wannan jumlan domin ya nuna cewa ya na fuskanta mutuwa kullum. AT: "Zan ku iya sani cewa wannan gaskiya ne, domin kun san game da fahariya ta a cikin ku" ko kuma "Zan ku iya sani cewa wannan gaskiya ne, domin kun san yadda na ke fahariya a cikin ku"
Bulus ya yi fahariya a cikin su domin abin da Almasihu Yesu ya yi masu. AT: "fahariya ta a cikin ku, wadda nake yi domin abin da Almasihu Yesu Ubangijinmu ya yi maku"
"yadda nake faɗa wa waɗansu mutane game da kirkin ku"
Bulus ya na so Korontiyawa su gane ba sai ya gaya masu ba. Wannan na iya zama jumla. AT: "Ban samu riban komai ba ... ta wurin kokowa da bisashe a Afisa ... tashi ba."
Bulus ya na nufin abin da ya yi. 1) Bulus ya na magana game da jayayyan sa da kafirai masani da kuma mutane da sun so su kashe shi ko kuma 2) an sa shi a filin da zai yaki mugayen dabbobi.
Bulus ya kalmasa da cewa idan akowai rai bayan mutuwa, zai yi mana kyau idan mun more wannan rai, domin gobe rain mu zai kare da rashin wata fata.
Idan kun yi rayuwa da mugayen mutane, za ku aikata kamar su. Bulus ya na faɗan karin magana ne.
"Dole ne ku yi tunani game da wannan"
Suna iya nufin 1) mutumin na tambaya da gaskiya ko kuma 2) mutumin ya na amfani da tambayan domin ya yi ba'a game da maganan tashin matattu. AT: "Amma waɗansu za su ce ba su san yadda Allah zai tayar da matattu ba, da kuma irin jiki da Allah zai ba su a tashin matattu."
"wani zai yi tambaya"
Zai zama jiki na ruhaniya ne ko jiki wadda ana iya gani? Wace irin halitta ne jikin za ta kasance da shi? Yi amfani a fasara tambaya na muhimmi wadda wani da zai so ya san amsoshi game da wannan tambayoyin zai iya tambaya.
Bulus ya na magana da Korontiyawa kamar su mutum daya ne, don haka misalin "ku" a nan daya ne.
"Ba ku san game da wannan ba"
Iri ba zai yi girma ba sai an binne a karkashin kasa. Haka kuma, sai mutum ya mutu kafin Allah ya tashe shi.
Bulus ya yi amfani da maganan iri kuma domin ya faɗa cewa Allah ya tayar da mutatcen jikin masubi, amma jikin ba zai bayyana kamar yadda yake ba.
Bulus ya na magana da Korontiyawa kaman su mutum daya ne, don haka kalmar "ku" anan daya ne.
"Allah zai zaɓi irin jiki da zai kasance da shi"
Game da dabbobi, an na iya fasara "jiki" kamar "fata" ko kuma "nama."
AT: 1) rana, wata, tauraru, da sauran haske a cikin sarari ko kuma 2) mutane na samaniya, kamar mala'iku da sauran mutane da sun wuce ikon ɗan Adam.
Wannan na nufin mutane.
"ɗaukaka da jikin samaniya ke da shi dabam ne da ɗaukaka na jikin mutane"
Anan "ɗaukaka" na nufin gwargwadon haske ga idon mutum a sarari.
Marubucin ya yi magana game da jikin mutum da an binne kamar ya zama iri da aka shuka a kasa. Ya kuma yi magana game da tashin jikin mutum daga matattu kamar shuka da yake girma daga irin. AT: "Abin da ya nufi kasa ... Abin da ke fata daga kasa ... ya na nufa cikin kasa ... ya fito daga kasa" ko kuma "Abin da mutane suka binne ... Abin da Allah ya tayar ... Mutane sun binne ... Allah ya tayar"
"an sa shi ya rayu kuma"
"zai iya ruɓa ... ba zai iya ruɓa ba"
"mutum na zahiri ne ya zo da farko. Mutum na ruhaniya daga Allah ne kuma ya zo daga baya ne."
halittace daga hanyoyi ta duniya, da baya a haɗe da Allah
Allah ya yi mutum na farko, Adamu, daga ƙura duniya.
ƙazanta
Yesu Almasihu
"waɗanda sun zama na Allah"
"ya kasance kamar ... zai kuma kasance kamar"
Suna iya nufin 1) jimla biyu nan na nufin abu ɗaya ne. AT: "mutane da za su mutu ba za su gaji mulkin Allah mai dauwama ba" ko kuma 2) jimla na biyu ya karasa tunani da na farkon ya fara. AT: "mutanin da ba su da ƙarfi ba za su gaji mulkin Allah ba. Ko kuma waɗanda za su mutu ne ma su gaji mulkin har'abada"
Waɗanda sun zauna a jikin da an ƙaddara ya mutu.
An yi maganar karɓan abin da Allah ya yi wa masubi alkawari kamar ya na gaji kaya da dukiya daga ɗan iyali.
AT: "Allah zai canza mu dukka"
AT: "Allah zai canza mu"
Zai faru da sauri kamar yadda mutum ya na kefta idonshi ko idonta.
"loƙacin da kaho na karshe ya yi kara"
AT: "Allah zai tada matattu"
"a hanyar da ba zai ruɓa ba ... jikin nan da ba zai iya ruɓa ... ba zai iya ruba ba." Dubi yadda an fasara jumla irin wannan a cikin 15:42
Bulus ya na magana game da yadda Allah ya na sa jikinmu kada su mutu kamar Allah ya na sa ma na sabon kaya.
Anan an yi maganar jiki kamar mutum ne. AT: "loƙacin da wannan jiki mai lalacewa ya zama marar lalacewa" ko kuma "loƙacin da wannan jikin da na iya rubawa ba zai iya ruba kuma ba"
Anan an yi maganar jiki kamar mutum ne. AT: "a loƙacin da wannan jiki mai mutuwa ya zama mara mutuwa" ko kuma "loƙacin da wannan jikin da na iya mutuwa ba zai iya mutuwa ba"
Bulus ya yi magana kamar mutuwa mutum ne, ya kuma yi amfani da wannan tambaya domin ya yi wa iƙon mutuwa gori. AT: "Mutuwa ba shi da nasara. Mutuwa ba shi da dafinki."
Wannan daya ne.
Ta wurin zunubi ne an ƙaddara ma na mutuwa.
Shari'a Allah da Musa ya kawo ne ya bayyana zunubi, ya kuma nuna mana yadda muke zunubi a gaban Allah.
"ya yaƙi mutuwa domin mu"
Bulus ya yi magana game da wani da be bar komai ya hana shi yin abin da ya yi niya ba. AT: "ku ƙudura"
Bulus ya yi magana game da ƙoƙarin da ake yi a aikin Ubangiji kamar sun zama kayan da mutum na iya samu. AT: "Ko yaushe ku yi wa Ubangiji aiki da aminci"
1Yanzu game da zancen tattara gudunmuwa ga masu bi, kamar yadda na umurci ikilisiyun Galatiya, haka za ku yi. 2A ranar farko ga mako, kowannen ku ya ajiye wani abu, yana tarawa bisa ga iyawarku. Ku yi haka don in na zo ba sai an tattara ba.3Sa'adda na zo, zan aiki duk wadanda kuka yarda da su da wasiku don su kai sakonku Urushalima. 4Sannan idan ya dace nima in tafi, sai su tafi tare da ni.5Zan zo wurinku sa'adda na ratsa Makidoniya. Domin zan ratsa ta makidoniya. 6Meyuwa in jima a wurinku, har ma in yi damuna, domin ku taimaka mani game da tafiyata, duk inda za ni.7Gama ba na so in yi maku gani na gajeren lokaci. Don ina so in dau lokaci tare da ku, idan Ubangiji ya yarda. 8Amma zan tsaya Afisus har ranar Fentikos. 9Gama an bude mani kofa mai fadi, kuma akwai magabta da yawa.10Sa'adda Timoti ya zo, ku tabbata ya sami sakewa acikinku, tun da aikin Ubangiji yake yi kamar yadda nake yi. 11Kada fa kowa ya rena shi. Ku tabbata kun sallame shi lafiya, domin ya komo gare ni, don ina duban hanyarsa tare da yan'uwa. 12Game da zancen dan'uwanmu Afollos kuwa, na karfafa shi ya ziyarce ku tare da 'yan'uwa. Sai dai baya sha'awar zuwa yanzu. Amma zai zo sa'adda lokaci ya yi.13Ku zauna a fadake, ku tsaya daram cikin bangaskiya, kuna nuna halin maza, ku yi karfin hali. 14Bari dukan abinda kuke yi ayi shi cikin kauna.15Kun dai sani iyalin gidan Sitefanas su suka fara tuba a Akaya, kuma sun bada kansu ga yi wa masu bi hidima. Yanzu ina rokonku, 'yan'uwa, 16kuyi biyayya da irin wadannan mutane da duk wanda ke taimakawa a cikin aikin, yana kuma fama tare da mu.17Na yi farinciki da zuwan Sitefanas, da Fartunatas, da Akaikas. Sun debe mini kewarku. 18Gama sun wartsakar da ruhuna da naku kuma. Don haka, Sai ku kula da irin wadannan mutane.19Ikilisiyoyin kasar Asiya suna gaishe ku. Akila da Bilkisu, tare da ikilisiyar da take taruwa a gidansu, suna gaishe ku cikin Ubangiji. 20Dukan 'yan'uwa masu bi na gaishe ku. Ku gaida juna da sumba maitsarki.21Ni Bulus, nake rubuta wannnan da hannuna. 22Duk wanda ba ya kaunar Ubangiji bari ya zama la'ananne. Ubangijinmu, Ka zo! 23Alherin Ubangiji Yesu ya kasance tare da ku. 24Bari kaunata ta kasance tare da ku duka a cikin Almasihu Yesu. 1
A rubutunsa na rufewa, Bulus ya tuna wa masubi na Korontiyawa da cewa su karɓa kuɗi wa musubi da suke da bukatu a Urushalima. Ya tuna masu da cewa Timoti zai zo masu kafin ya je wurin Bulus.
Bulus ya na karɓan kuɗi daga ikilisiyoyi domin talakawan Yahudawa masubi a cikin Urushalima da kuma Yahudiya.
"kamar yadda ina ba da su takamaiman umurni"
AT: 1) ajiye shi a gida ko kuma 2) "bar shi tare da ikilisiyan"
"domin ba sai kun sake karban kuɗi kuma ba a loƙacin da ina tare da ku"
Bulus ya na faɗa wa ikilisiyan da cewa su zabi daga cikin mutaninsu wadda za su kai baikonsu a Urushalima. "waɗanda ku ka zaba" ko kuma "mutanin da ku ka naɗa"
AT: 1) "Zan aika da wasikun da zan rubuta" ko kuma 2) "Zan aika da wasikun da za ku rubuta."
Wannan na nufin cewa za su iya ba wa Bulus kuɗi ko kuma wadansu abubuwa da ya na bukata domin shi da 'yan'uwansa na bishara su iya cigaba da tafiya.
Bulus ya na bayyana cewa ya na so ya yi ziyara na tsawon loƙaci, ba na ƙaramin loƙaci ba.
Bulus zai tsaya a Afisus sai wannan ranar idi, wadda ya zo a May ko kuma June, a kwana hamsin a bayan Idin ketarewa. Zai kuma yi tafiya ta Makidoniya, sai ya kuma sauka a cikin Koronti kafin rani ya fara a watan goma sha ɗaya.
Bulus ya yi magana game da loƙacin da Allah ya bashi domin ya rinjaye mutane zuwa ga bishara. Kamar kofa ce da Allah ya buɗe domin ya iya tafiya a cikinsa.
"ku tabbata cewa ba shi da tsoron kasancewa da ku"
Domin Timoti ya fi Bulus ƙarami, wani loƙaci ba a girmama shi yadda ya kamata a matsayin mai koyarwan bishara.
Anan kalmar "mu" na nufin Bulus da ma su sauraransa.
Bulus ya na kwatanta abin da yake son Korontiyawan su yi kamar ya na ba wa soja umurni hudu a yaki. Wannan umurni hudun na nufin abu ɗaya kuma ana amfani da su domin nananci.
Bulus ya yi magana game da mutanin da sun san abin da ke faru kamar sun zama masu tsaro da ke tsaron gari ko kuma lambu. AT: "Yi hankali da wadda kun amince da shi" ko kuma "ku yi hankali da haɗari"
Bulus ya yi magana game da yadda mutane sun cigaba da bin Almasihu bisa koyarwansa kamar sun zama sojojin da sun ƙi su ja da baya a harin makiya. AT: 1) "ku gaskanta da karfi a abin da mun koya maku" ko kuma 2) "ku amince da Almasihu da karfi"
A garin da Bulus da masu sauraransa suke, mazaje su na tanada wa iyalin su ta wurin yin aiki mai karfi da faɗa da masu shigan gari da hari. AT: "ku zama da takalifi"
"Dukkan abin da ku ke yi ya nuna wa mutane cewa ku na kaunan su"
Sitefanas daya ne daga cikin farkon masubi ikilisiyan Koronti.
Wannan sunan lardi a cikin Girka.
Waɗannan mazajen, masubi ne na farko a Korontiya ko kuma dat'tawan ikilisiya da suke aiki tare da Bulus.
"sun shirya da shike ba ku nan."
Bulus ya na cewa ya karfafu da ziyarar su.
Bulus ya fadi a bayyane da cewa umurnin da ke a wasikannan daga gare shi ne, ko da shike ɗaya daga cikin ma'aikatan sa ya rubuta abin da Bulus ke faɗi a sauran wasikun. Bulus ya rubuta na karshen da hannun sa.
"Bari Allah ya la'anta shi." Dubi yanda "la'ananne" an bayana a cikin 12:1.
1Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma Timoti dan'uwan mu, zuwa ga Ikilisiyar Allah da ke a Korantus, da kuma dukan 'yan'uwa da ke yankin kasar Akaya. 2Bari alheri ya kasance tare da ku da kuma salama ta Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.3Bari yabo ya tabbata ga Allah da kuma Uba na Ubangijinmu Yesu Almasihu. Shine Uba na dukan jiyejiyenkai, da kuma Allah na dukan ta'aziya. 4Allah yana ta'azantar da mu a cikin dukan wahalarmu, domin mu iya ta'azantar da wadanda ke cikin kowace wahala. Muna ta'azantar da wasu da irin ta'aziyar da Allah ke ta'azantar da mu.5Gama kamar yadda wahalhalun Almasihu suka karu domin mu, haka kuma ta'aziyarmu ta yawaita cikin Almasihu. 6Amma fa idan muna shan wuya, domin ta'aziyarku ne da cetonku. Haka kuma in mun ta'azantu, domin ta'aziyarku ne. Ta'aziyarku tana aiki ne sosai yayinda kuka jure da irin shan wuyar da mu ma muke sha. 7Kuma gabagadinmu game da ku tabbatacce ne. Mun kuwa sani kamar yadda kuke tarayya cikin shan wahalhalun, haka kuma za ku yi tarayya cikin ta'aziyyar.8Gama ba mu so ku rasa sani, 'yan'uwa, game da tsananin da ya same mu a Asiya. An murkushe mu gaba daya har fiye da karfin mu, har ma mun fidda zuciya za mu rayu. 9Hakika, mun ji hukuncin mutuwa akan mu. Amma wannan ya faru ne domin kada mu dogara ga kanmu, sai dai ga Allah, wanda ke tada matattu. 10Ya kubutar da mu daga wannan mummunan hatsari na mutuwa, kuma zai sake kubutar da mu. Mun kafa begenmu gare shi cewa zai sake kubutar da mu.11Zai aikata wannan yayinda kuka taimake mu da addu'ar ku. Sa'an nan da dama za su bada godiya a madadin mu don tagomashin alheri da aka yi mana ta wurin addu'o'in mutane masu yawa.12Muna kuwa alfahari da haka: wato shaidar lamirinmu. Gama da kyakkyawan nufi da aminci da ke zuwa daga Allah muka tafiyar da rayuwarmu a Duniya. Mun yi wannan ne musamman tare da ku-ba kuwa cikin hikimar Duniya ba, amma ta wurin alherin Allah. 13Bamu rubuta maku abinda ba za ku iya karantawa ko fahimta ba. Ina fata za ku fahimce mu baki daya, 14kamar yadda kuka fahimce mu kadan yanzu. Daganan a ranar Ubangijinmu Yesu za mu zama dalilinku na alfahari, kamar yadda za ku zama namu.15Saboda gabagadin da nake da shi game da haka, naso in zo gare ku da farko, domin ku amfana da ziyara sau biyu. 16Ina da shirin ziyaratar ku a kan hanyata ta zuwa Makidoniya. Daga nan kuma ina da yi niyyar in sake ziyartar ku, a tafiya ta daga Makidoniya, domin ku aike ni a hanyata ta zuwa Yahudiya.17Yayinda nake irin wannan tunani, ina shakka ne? Ina shirya abubuwa ne bisa ga magwajin mutum, ta yadda har zan ce "I, i" da "A, a, a, a" a lokaci guda? 18Amma kamar yadda Allah yake amintacce, ba ma fadin "I" da "A'a" a lokaci guda.19Gama Dan Allah, Yesu Almasihu, wanda Silbanus da Sila, da Ni muka shaida maku, ba "I" da "A, a" ba ne. Maimakon haka, Shi "I" ne a kodayaushe. 20Gama dukan alkawaran Allah 'I' ne a cikin sa. Haka kuma ta wurin sa muna cewa "Amin" zuwa ga daukakar Allah.21Yanzu dai Allah ne ya tabbatar da mu da ku a cikin Almasihu, ya kuma kebe mu. 22Ya sa hatiminsa a kan mu ya kuma ba mu Ruhu a zuciyar mu a matsayin tabbacin abinda zai bamu daga baya.23Maimakon haka, na yi kira ga Allah ya zama shaida domina, cewa dalilin dayasa banzo Korintis ba domin in kare ku ne. 24Ba muna kokarin mu sarrafa yadda bangaskiyar ku za ta zama ba ne. Maimakon haka, muna aiki tare da ku ne domin farincikinku, yayinda kuke tsaye cikin bangaskiyarku.
Bayan gaisuwan Bulus zuwa ga Ikilisiyar da ke Korantus, ya rubuta kuma game da azaba da kuma ta'aziya da ke samu ta wurin Yesu Almasihu
Harshen ku, ya iya yuwa kuna da yadda kuna gabatar da marubucin wasika da kuma masu sauraro. AT: " Ni, Bulus... na rubuto muku wannan wasika, Ikilisiyar Allah dake a Korantus"
wannan na nuna cewa Bulus da Mutanen Korantus sun san Timoti, suna kuma ɗaukansa dan'uwansu cikin ruhaniya.
Wannan sunace yankin gabacin Roma wanda a yau itace Girka.
wannan gaisuwace da Bulus ya saba amfani da ita a wasikarsa
Wannan ana iya bayyana ta kamar haka. AT: Bari mu ɗaukaka Allah da kuma Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu"
"Allah, Wanda shine Uban"
Waɗannan Maganganu biyu suna bayyana abu ɗaya ne a hanyoyi biyu. Dukan maganan suna nufin Allah.
Anan "mu" da "namu" na nuna tare da Korantus.
Bulus ya yi maganan wahalhalun Almasihu kamar wani abu ne wanda za ta iya karu kuma a kidaya. AT: "Gama kamar yadda Almasihu ya sha wahala sosai domin mu"
Ma'anar da ke iya yuwa suna kamar haka 1) wato wahalan Bulus da Timoti sun sha domin sun yi wa'azin sako game da Almasihu ko kuwa 2) wahalan da Almasihu ya sha a madadin su.
Bulus ya yi magana game da ta'aziya kamar wani abu ne wanda zai iya girma.
A nan kalmanan "mu" na nufin Bulus da Timoti, amma ba yan Korantiyawa ba. Ana iya bayyana wannan haka. AT: "Amma in mutane sun wahalal da mu"
Ana iya bayyana wannan haka. AT: "in Allah ya ta'azantar da mu"
"Kuna samun ta'aziya yadda ya kamata"
Wannan za a iya bayanna shi a kalmomi kamar haka. AT: "muna so ku sani"
Bulus da Timoti suna nufin kujewa karma abu mai nauyi da sun dauka.
Bulus da Timoti suna misalin yadda suke ji da wanda an yi masa hukuncin mutuwa. AT: "mun ji kamar wanda aka yanke wa hukuncin kisa"
Kalmomin nan "sa begen mu" an cire su daga maganan. AT: "amma dai, mu sa begen mu ga Allah"
A nan, a ta da, wanin karin magana ne wanda ke nuna cewa wanda ya mutu ya dawo da rai. AT: "wanda ya sa matattu su rayu kuma"
Bulus ya kwatanta yadda ya fid da zuciyarsa saboda damuwar da yake fuskanta da mummunan hatsari na mutuwa ko kuwa hadari mai ban soro. AT: "fid da zuciya"
"shi zai cigaba da ceton da mu"
"Allah zai kubutar da mu daga hadari a sa'alin da, ku mutanen ikilisiyar da ke a Korantus kun kuma taimake mu"
Wannan ana iya bayayana shi karma haka. AT: "tagomashin alheri wanda Allay ya riga da ya ba mu"
Kalman nan ta "takama" da kuma "alfahari" anan an yi amfani ne da su don nufin yadda aka ji lailai an biya bukata da kuma murna domin wani abu.
Bulus yayi maganar alhalin laifi kamar Lamirin shi mutum ne wanda zai iya magana. AT: "mun sani tawurin lamirin mu"
A nan "jiki" na yin misalin dan Adam. AT: "ba mu jigina ga hikimar da adam ba, amma ga alherin Allah
Ana iya bayana wannan cikin kalmomi kamar haka. AT: "kun iya karanta da kuma fahimtar dukan abubuwan da muka rubuta muku"
Bulus ya bayyana sahilin tsammanin sa da muradin mai kyau domin ya zo ya ga masubi da ke a Korantus bayan wasikar sa ta fari.
Kalman nan "wannan" ta na nufin maganar da Bulus ya yi game the Korantiyawa
"kun iya amfana daga ziyarata sau biyu"
"taimaka mini a hanya ta zuwa Yahudiya"
Bulus yayi wannan tambaya domin ya nuna nauyin lafazi cewa yana tabbacin game da shirin ziyarsa zuwa Korantus. sammacin amsar tambayar itace a'a. AT: "dama ba na shakka" ko kuwa "ina da gabagadi cikin shiri na."
Bulus ya yi amfani da wannan tambaya ne domin ya nuna nauyin lafazin sa da cewa shirin sa domin ziyartan Korantiyawa sahili ce. AT: "Ban shirya abubuwa bisa ga ma'aunin ɗan adam ba...a lokaci guda"
Wannan na nufin Bulus bai ce wai zai ziyarci ko kuwa ba zai yi ziyara ba a lokaci guda. Kalmomin nan "i" da "a'a" an maimaita shi domin nuna nauyin lafazi. AT: "ban shirya abubuwa... domin in ce 'I, zan yi ziyara' da 'a'a, hakika ba zan yi ziyara ba' a lokaci guda!"
Yesu ya ce "I" game da alkawarin Allah, ma'ana kuwa itace tabbaci cewa duka gaskiya ce. AT: "Gama Dan Allah... bai ce "I" da "a'a" game da alkawarin Allah ba. Maimakon haka, shi ya kan ce "I" a ƙodayaushe.
Wannan suna ce mai mahimmanci na Yesu da ke bayana ɗangantakarsa da Allah.
Wannan na nufin Yesu shi ne tabbacin dukan alkawarai na Allah. AT: "dukan alkawarai na all ta na tabbaci cikin Yesu Almasihu"
Kalman nan "sa" na nufin Yesu Almasihu.
mana masu yiwuwa suna kamar haka 1) " Allah wanda ya tabbatar da ɗangantakar mu da juna domin muna cikin Almasihu" ko 2) "Allah wanda ya tabbatar da mu kuma da dangantakar ku da Almasihu."
mana masu yiwuwa suna kamar haka 1) "ya aike mu mu yi wa'azin bishara" ko 2) "ya zabe mu mu zama mutanen sa."
Bulus ya yi magana game da Allah ya nuna mu nasa ne kamar Allah ya sa alama a kan mu domin ya nuna alaman cewa mu nasa ne. AT: "she ya sa alamar shaidar ce nasa ne a kan mu" ko "ya nuna cewa mu nasa ne"
A nan Kalman nan "zukata" na nufin
An yi maganar Ruhun Kamar shi wani ne wanda bai isa cikakkiyar biyar rai madawwami ba.
Maganar nan "zama shaida" na nufin mutum na fadin abin da ya gani ko ji domin ya sasanta mahawara. AT: "Na roki Allah ya nuna cewa abin da nake fadi gaskiya ne"
"domin kada in kara sa wahalar da ku"
"muna aiki da ku domin may yiwuwa ku sami farinciki"
Kalman nan "tsaya" na iya nufin abun da ba ya canzawa. AT: "tsaya da karfi cikin bangaskiyar ku"
1Don haka na yanke shawara daga bangarena, ba zan sake zuwa wurin ku cikin yanayi mai tsanani ba. 2Idan na bata maku rai, wa zai karfafa ni, in ba shi wanda na bata wa rai ba?3Na rubuto maku kamar yadda na yi domin idan na zo gareku kada in sami bacin rai a wurin wadanda ya kamata su faranta mani rai. Ina da gabagadi game da dukan ku, cewa farincikin da nake da shi, shine kuke da shi duka. 4Domin kuwa na rubuto maku cikin kunci da bacin rai da kuma hawaye mai yawa. Ba zan so in sake bata maku rai ba. Maimakon haka, na so ku san zurfin kaunar da nake da ita domin ku.5Idan wani ya kawo sanadin bacin rai, ba ni kadai ya kawo wa wannan abin ba, amma ta wani fannin- domin kada a tsananta- har a gare ku duka. 6Hukuncin nan da galibinku kuka yi wa mutumin nan ya isa. 7Don haka, yanzu a maimakon hukunci, ku gafarta masa, ku kuma ta'azantar da shi. Ku yi haka domin kada bakinciki mai yawa ya danne shi.8Don haka ina karfafa ku da ku nuna irin kaunar da kuke yi masa a fili. 9Wannan shine dalilin da ya sa na rubuto maku, domin in gwada ku, ko kuna biyayya cikin komai.10Duk mutumin da kuka gafarta wa, ni ma na gafarta masa. Abin da na gafarta-idan na gafarta wani abu-an gafarta ne domin ku a gaban Almasihu. 11Wannan ya zama haka ne domin kada shaidan ya yaudare mu. Don ba mu jahilci irin makircinsa ba.12Na samu budaddiyar kofa daga wurin Ubangiji yayin da nazo birnin Tarwasa, in yi wa'azin bisharar Almasihu a can. 13Duk da haka, raina bai kwanta ba, domin ban ga dan'uwana Titus a can ba. Sai na bar su a can, na dawo Makidoniya.14Amma godiya ta tabbata ga Allah, wanda cikin Almasihu yake kai mu ga nasara a koyaushe. Ta wurin mu ya baza kamshi mai dadi na saninsa ko'ina. 15Gama mu, kamshi ne mai dadi na Almasihu ga Allah, a tsakanin wadanda ake ceton su, da kuma tsakanin wadanda suke hallaka.16Ga mutanen da suke hallaka, kamshi ne daga mutuwa zuwa mutuwa. Ga wadanda suke samun ceto kuma kamshi ne daga rai zuwa rai. Wanene ya cancanci wadannan abubuwan? 17Gama mu ba kamar sauran mutane muke ba, masu sayar da maganar Allah domin samun riba. Maimakon haka, da tsarkakkiyar manufa, muke magana cikin Almasihu, kamar yadda Allah ya aiko mu, a gaban Allah.
Saboda matukar ƙaunarsa gare su, Bulus ya bayyana cewa tsawtawar sa a wasikarsa ta farko zuwa gare su (tsawtarwa domin yaddarsu da zunubin fasikanci) ta sa shi bai ji dadi ba kamar yadda ta sa mutanen ikilisiyar da take a Korantus da kuma mutum mai rashin adalci
" Na yi shirin"
cikin yanayi da za ta sa ku cikin saka mai wuya"
Bulus ya yin amfani da tambaya da bata bukatan amsa domin ya dada nu muhimincin maganarsa cewa ko shi ko su, ba wanda zai karu in zuwan sa wurinsu zai kawo musu bacin rai. AT: "Idan na bata maku rai, ku waɗanda ke karfafani wa zai karfafa ni, in ba shi wanda ya samu bacin rai daga ni ba"
wanan ana iya bayyana ta cikin kalmomi masu kuzari. AT: "she wanda ya samu bacin rai daga ni"
wannan na nufin wata wasika da Bulus ya rubuto zuwa ga krista da suke a Korantus wanda ba ta nan a yau. AT: " Na rubuto kamar yadda na yi a wasikar wanda na rigaya na rubuto"
Bulu na magana ne game da wata irin halin masubi da suke a Korantus wanda za ta sa shi jin zafi cikin zuciyarsa. Wannan ana iya sa shi cikin magana mai kuzari. AT: " waɗanda ya kamata su faranta mini rai watakila kada su sani bacin rai"
"abin da ke faranta mini rai shi ne abida ke faranta muku rai kuma"
A nan Kalman na "kunci" na nufin jin zafi cikin zuci.
A nan Kalman nan "zuciya" na nufin inda zafin rai take. AT: "da matsanancin bakin ciki"
"da kuka sosai"
"zuwa ga wani iyaka"
Wannan na iya nufin 1) Bana so in fadi shi cikin Tsananci sosai" ko 2) "Bana son in zuguiguita."
Wannan ana iya bayyana ta kalmomi masu kuzari. Kalman nan "hukunci" na iya juya shi ta wurin amfani da aikatau. AT: " Yadda yawanci su suka hukunta mutumin ya isa."
"ya isa"
Wannan na nufin jin zafin zuci mai yawa bai sa shi bakin ciki sosai ba. Wannan ana iya bayyana ta kalmomi masu kuzari. AT: "bakin ciki mai yawa bai danne shi ba."
Wannan na nufin cewa su tabbatar the ƙaunar su ga wannan mutum a gaban dukan masubi.
Wannan na iya nufin 1) "kuna biyayya ga Ubangiji cikin dukan kome" ko 2) kuna biyayya cikin dukan kome da na koyas da ku"
wannan ana iya bayyana ta cikin kalma mai kuzari. AT: "Na gafarce shi domin ku"
Wannan na iya nufin 1) "gafartawa saboda ɗaunar da nake yi muku" ko 2) "gafartawa
Bulus yayi amfani da waɗanan kalmomi domin ya dada bayyan maganar. AT: "Don mun san makircinsa sarai"
Bulus ya yi maganar zarafin da ya samu domin yin wa'azin bishara kamar wat kofa ce da aka barshi ya shiga. wannan ana iya bayyana shi cikin kalmomi masu kuzari. AT: Ubangiji ya bude mini kofa ... in yi wa'azin bishara" ko "Ubangiji ya bani zarafi ... in yi wa'azin bishara"
"Zuciyata ta birkice" ko " Na damu"
Bulus ya yi magana game Titus da nufin shi dan'uwans ne cikin ruhaniya.
"Sai na bar mutanen Tarwasa"
Bulus ya yi magana game da Allah kamar shi wani shugaba mai nasara wanda ke shugabantar farati da shi da kuma abokan aikinsa kamar wanda suke farati. Wannan na iya nufin 1) Allah, wanda cikin Almasihu kan sa muyi tarayya cikin nasararsa a ƙoyaushe" ko 2)"Allah, wanda cikin Almasihu a ƙoyaushe ya na shugabantarmu cikin nasara kamar waɗanda tawurinsu ya sami nasara"
Bulus ya yi maganar sanin Almasihu kamar wata kamshi mai dadi. AT: "Ya sa sanin Almasihu ta bazu ga kowan da ya ji su, sai ka ce wata kamshin turare da ke bazuwa ga duk wanda ke kusa"
"ya baza... ko'ina muka je"
Bulus ya yi maganar aikinsa kamar wata hadayar ƙonawa wanda wani ya miƙa ga Allah.
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) "kamshi mai dadi wanda ita ce sanin Almasihu" ko 2) "kamshi mai dadi wanda Almasihu ya mika."
Ana iya bayyana wannan cikin kalmomi da ke nuna kuzari. AT: "waɗanda Allah ya ceta"
"sanin Almasihu kamshi ce." Wannan ya komar damu zuwa [2 Korantiyawa 2:14]
Ma'an mai yiwuwa suna kamar haka 1) wato kalman nan "mutuwa" an sake maimaita ta domin nauyi lafazi, kuma maganar tana nufin "kamshi mai sa mutuwa" ko 2) "kamshin mutuwa da ke sa mutane su mutu"
Wannan ana iya bayyana ta cikin kalmomi da ke nuna kuzari. AT: "Wanɗanda Allah ke ceta"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) wato kalman nan "rai" an sake maimaita ta domin nauyi lafazi, kuma maganar tana nufin "kamshi mai bada rai" ko 2) "kamshin rai mai ba da rai ga mutane"
Bulus ya yi amfani da wannan tambaya domin ya dada nayin maganarsa cewa babu wanda cancanci yin aikin da Allah ya kira su. AT: "Babu wanda ya cancanci waɗannan abubuwa"
"Kalma" anan kalma ce mai nuna "sako". AT: "masu sayar da sakon Allah"
"manufa mai tsarki"
"muke magana kamar mutanen da ke tare da Almasihu" ko "muke magana da ikon Almasihu"
Wannan ana iya bayyana ta cikin kalmomi da ke nu kuzari. AT: "kamar mutanen da Allah ya aiko"
Bulus da abokanayen aikinsa sun yi wa'azin bishara da sanin cewa Allah na kallon sun. AT: "mun yi magana a gaban Allah"
1Muna fara sake yabon kanmu ne? Ba mu bukatar wasikun shaida daga gare ku ko zuwa gare ku, kamar wadansu mutane, ko ba haka ba? 2Ku da kanku kune wasikar shaidarmu, wadda aka rubuta a zukatanmu, wadda Kuma dukan mutane suka sani suke kuma karantawa. 3Kuma kun nuna ku wasika ne daga Almasihu, wadda muka isar. Ba da tawada aka rubuta ta ba amma da Ruhun Allah mai rai. Ba bisa allunan duwatsu aka rubuta ta ba, amma bisa allunan zukatan mutane.4Gama wannan ne gabagadin da muke da shi cikin Allah ta wurin Almasihu. 5Ba mu da wata gwanintar kanmu da za mu yi takamar wani abu ya zo daga gare mu. Maimakon haka, gwanintar mu daga Allah take. 6Allah ne ya maishe mu kwararrun bayi na sabon alkawari. Wannan alkawari ne ba na rubutu ba amma na Ruhu. Gama rubutu kisa yake yi, amma Ruhu rai yake bayarwa.7To hidimar da ta haifar da mutuwa- wadda aka rubuta bisa duwatsu- ta zo cikin irin wannan daukaka da har Israila ba su iya kallon fuskar Musa kai tsaye ba. Wannan kuwa saboda daukakar da ke fuskarsa ne, daukaka mai shudewa. 8Ina misalin girman daukakar hidimar da Ruhu ke yi?9Gama idan hidimar kayarwa tana da daukaka, ina misalin yalwatar daukaka da hidimar adalchi za ta yi! 10Babu shakka, abin da aka maishe shi mai daukaka a da, ba ya da sauran daukaka a wannan fanni, saboda irin daukakar da ta zarce shi. 11To idan har mai shudewar nan ya na da daukaka, ina misalin daukakar da abu na dindindin zai samu!12Dashike muna da wannan tabbaci, muna da gabagadi sosai. 13Ba kamar Musa muke ba wanda ya sa mayafi ya rufe fuskarsa, ta yadda mutanen Isra'ila basu iya kallon karshen daukaka mai shudewa ba kai tsaye.14Amma tunaninsu ya zama a rufe. Har yau kuwa mayafin na nan sa'adda ake karanta tsohon alkawari. Ba a bude shi ba, saboda a cikin Almasihu ne kadai ake kawar da shi. 15Amma har yau, duk lokacin da ake karanta littafin Musa, akwai mayafi shimfide a zukatansu. 16Amma sa'adda mutum ya juyo wurin Ubangiji, an kawar da mayafin.17To Ubangiji shine Ruhun. Inda Ruhun Ubangiji yake, akwai 'yanci. 18Dukan mu yanzu, da fuskoki marasa mayafi, muna ganin daukakar Ubangiji. Muna samun sakewa zuwa cikin irin wannan daukaka, daga wannan mataki na daukaka zuwa wani matakin, kamar dai daga wurin Ubangiji, wanda shine Ruhun.
Bulus ya tunashe da cewa baya fahariya a sa'ada ya yi musu magana game da abin da ya yi tawurin Almasihu.
Bulus ya yi amfani da wannan tambayar domin ya nuna nauyin maganarsa cewa ba su fahariya da kan su. AT: "Mu ba fara yabon kan mu muke yi kuma ba"
Bulus ya fadi wannan maganar cewa Korantiyawa sun riga sun san game da halin kirki na Bulus da Timoti. Tambayar ta nema amsa. AT: "Haƙika ba mu bukatar wasikun shaida daga gare ku ko zuwa gare ku, kamar waɗansu mutane"
Wannan wasika ce da mutum ke rubutawa domin ya gabart da kuma bada izinin su ga wani dabam.
Bulus ya yi magana game da Korantiyawa kamar su wasikar shaida. da shike sun zama masubi wannan ta zama abin da ta inganta aikin bisharan Bulus ga wanɗansu. AT: "Ku da kanku kuna kamar wasikar shaidarmu"
A nan Kalman nan "zukata" na nufin tunanin su da kuma yadda suke ji. Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1)Bulus da abokan aikinsa sun tabbata cewa Korantiyawa wasikar su ne ta shaida ko 2) Bulus da abokan aikinsa suna lura da Korantiyawa sosai.
Wannan ana iya bayyana shi cikin kalmomi masu kuzari. AT: "cewa kowa na iya sani da karantawa"
Bulus ya bayyana cewa Almasihu ne wanda ya rubuta wannan wasika. AT: "ku wasika ce wanda Almasihu ya rubuta"
"muka kawo"
Bulus ya bayyana cewa Korantiyawa suna kamar wasikun ruhaniya ba kamar wasika bace da mutane ke rubutawa da abubuwan rubutu na jiki.
Wannan ana iya bayyana ta cikin kalmomi masu kuzari. AT: "Ba wasika bace da mutane suka rubuta da tawada amma wasika wanda Ruhun Allah mai rai ya rubuto"
Wannan ana iya bayyana ta cikin kalmomi masu kuzari. AT: "Ba wasika bace da mutane suka zana a allun duwasuba amma wasika da Ruhun Allah mai rai ya rubuto a allunan zukatan mutane"
Bulus ya yi maganar zukatan su kamar wata dutse ko kuwa yumbu da mutane ke iya rubuta wasiku.
Wannan na nufin abida Bulus ya fada yanzun nan. Samin gabagadin sa ta zo ne daga sanin cewa Korantiyawa sune karfin aikinsa gaban Allah.
"cancanta a kanmu" ko "mu kanmu mun isa"
Anan kalman nan "wani abu" na nufin wani abu game da aikin manzoncin Bulus. AT: "takamar cewa wani abu da mu ka yi domin aikin ta zone daga kokarin mu"
"Allah ne ya bamu iyawa"
A nan kalman nan "wasika" na da ma'anan haruffa ta kuma nufin kalmomi da mutane ke rubutawa. Wannan magana ta na nufin dokokin Tsohon Alkawari. AT: "alkawari wanda ba bisa dokokin da mutane suka rubuta ba"
Ruhu Mai Tsarki she ne wanda ya kafa alkawarin Allah da mutane. AT: "amma alkawarin bisa ga abin da Ruhun ya yi ne"
Bulus ya yi maganar dokokin Tsohon Alkawari kamar wani mutum wanda ke kisa. Bin dokokin na kai ga mutuwa cikin ruhu. AT: "rubutaciyar dokokin tana kai ga mutuwa"
ƙodashiƙe doka na kai ga mutuwa, Bulus ya nanata cewa har yanzu ta na fifiko.
"the ministry of death." Wannan na nufin dokokin Tsohon Alkawarin wanda Allah ya bayar tawurin Musa. AT: "aikin da ke sa mutuwa domin tana nan bisa ga dokoki"
"goge dutse zuwa ga haraffai." Wannan ana iya bayyana ta cikin kalmomi masu nuna kuzari. AT: "cewa Allah ya goge dutse zuwa ga haraffi"
"cikin ɗaukaka mai yawa"
"Ba su iya gani ba saboda"
Bulus yayi wannan tambayar domin ya nuna nauyi maganarsa cewa "hidimar da Ruhu ya yi" dole ne ta fi ɗaukaka fiye da "hidimar da an haifa" domin ta kan kai ga rai. AT: "Saboda haka hidimar da Ruhun ke yi dole ne ta fi daukaka"
"aikin Ruhun." Wannan na nufin sabon alkawari wanda Bulus ma'aikaci ne. AT: "aikin da ke bada rai domin ta na bisa Ruhun ne"
"aikin kayarwa." Wannan na nufin doka da ke Tsohon Alkawari. AT: "aikin da ke kayar da mutane domin ta bisa dokan"
A nan Kalman nan "ta yaya" tana nuna alamar maganar kamar maganar motsin rai ba tambaya ba. AT: "sa'an nan hidimar adalci dole ta yelwata fiye da ɗaukaka!"
Bulus ya yi maganar "hidimar adalci" kamar wani abu ne da za ta iya haifuwa ko ta yaɗu. Ya na nufin "hidimar adalci" ya fi ɗaukaka sosai fiye da doka wanda tana da ɗaukaka ita ma.
"aikin adalci." Wannan na nufin sabon Alkawari ce wanda Bulus ma'aikaci ne. AT: "aikin da ke sa mutane su zama da adalci domin bisa ga Ruhun ta ke.
Dokokin Tsohon Alkawarin bata kuma da ɗaukaka in an kwatanta ta da Sabon Alkawari wanda tana da ɗaukaka fiye.
wannan ana iya bayyana ta cikin kalmomi masu nuna kuzari. AT "alkawarin wanda Allah ya maishe ta mai ɗaukaka a da"
"cikin wannan hanya"
Wannan na nufin "hidimar kayeswa," wanda Bulus ya yi maganar ta kamar wani abu mai iya ɓacewa. AT: "abin da ke zuwa ga rashin amfani"
Wannan na nufin abin da Bulus ya gama fada. Begen sa ta zo daga sanin cewa sabon alkawari ta zo ne da madawamiyar daukaka.
"wannan gabagadi"
Wannan na nufin ɗaukakar da ta hakaka fuskar Musa. AT: "ɗaukakar da ke fuskar Musa a sa'alin da take shuɗewa gaba ɗayan ta.
"Amma sun taurara zukatan su." Bulus ya yi magana game da zukatan Israila kamar wani abu ne da zai iya rufuwa ko kuwa tauri. Wannan na nufin ba su iya fahimtar abin da suka gani ba. AT: "Amma Isa'ila ba su iya fahimtar abin da suka gani ba"
Waɗannan na maganganu na nufin lokacin da Bulus ke rubutun sa zuwa ga Korantiyawa.
kamar yadda Israila basu iya ganin fuskar Musa ba domin ya rufe fuskar sa da mayafi, akwai wani mayafi na ruhu da ke hana mutane fahimtar tsohon alkawarin a sa'ada suka karanta.
"a sa'ada sun ji wani na karanta tsohon alkawari"
A nan bayyanuwan kalman nan "ita" na nufin "mayafin." Wannan ana iya bayyana ta cikin kalmomi ma su nuna kuzari. AT: "Babu wanda ke cire mayafin domin tawurin Almasihu ne kadai Allah ke cire ta"
A nan kalman nan "Musa" na nufin dokokin Tsohon Alkawari. Wannan ana iya bayyana ta cikin Kalmomi masu nuna kuzari. AT: duk sa'ada wani ya karanta dokokin Musa"
A nan Kalman nan "Zukata" na misalin tunanin mutane, da kuma an yi maganar rashin fahimtar tsohon Alkawarin ga mutanen kamar wata mayafine da ta rufe zukatan su kamar yadda mayafi zai rufe idan su. AT: "ba su iya fahimtar abin da suka ji ba"
A nan "juyo wurin" na da ma'anan biyayya ga wani. AT: " sa'ada mutun ya fara sujada ga Ubangiji" ko "sa'ada mutum ya fara amince da Ubangiji"
Allah ya ba su iyawa don su fahimta. Wannan maganan ana iya bayyana ta cikin kalmomi masu nuna kuzari. AT: "Allah ya cire mayafin" ko "Allah ya basu iyawa don su fahimta"
A nan kalman nan "mu" na nufin dukan masubi har da Bulus da kuma Korantiyawa.
Ba kamar Israila ba wanɗanda ba su iya ganin ɗaukakař Allah kamar yadda ta bayyana a fuskar Musa ba domin ya rufe ta da mayafi, babu wani abu da zai hana masubi ganin ɗaukakar Allah da kuma fahimtar ta.
Ruhun na sake masubi su zama da ɗaukaka kamar shi. Wannan ana iya bayyana ta cikin kalmomi masu nuna kuari. AT: "Ubangiji na sake mu cikin ɗaukaka kamar sa"
"daga wata yawan ɗaukaka zuwa ga wata yawan ɗaukaka." Wannan na nufin Ruhun na cingaba da kara ɗaukakan masubi.
"kamar dai wannan ta zo daga wurin Ubangiji"
1Don haka, domin muna da wannan hidima, da kuma yadda muka karbi jinkai, ba mu karaya ba. 2Maimakon haka, sai muka rabu da dukan hanyoyin da ke na kunya, kuma na boye. Ba mu rayuwar makirci, kuma bamu yiwa maganar Allah rikon sakaci. Ta wurin gabatar da gaskiya, muna mika kanmu ga lamirin kowa a gaban Allah.3Amma, idan bishararmu a rufe take, tana rufe ne ga wadanda ke hallaka. 4A al'amarinsu, allahn wannan duniya ya makantar da zukatansu marasa bada gaskiya. A sakamakon haka, ba su iya ganin hasken bisharar daukakar Almasihu ba, wanda shine surar Allah.5Gama ba mu yin shelar kanmu, amma Almasihu Yesu a matsayin Ubangiji, mu kuma bayinku saboda Yesu. 6Gama Allah shine wanda ya ce, "Haske zai haskaka daga cikin duhu." Ya haskaka cikin zukatanmu don ya bada hasken sanin daukakar Allah a gaban Yesu Almasihu.7Amma muna da wannan dukiya a randunan yunbu, yadda zai zama a bayyane cewa mafi girman iko na Allah ne ba namu ba. 8Muna shan tsanani ta kowace hanya, ba a ci mu dungum ba. Mun rikice amma ba mu karaya ba, an tsananta mana amma ba a watsar da mu ba. 9Ana tsananta mana amma ba a yashe mu ba. Aka doddoke mu amma ba mu lalace ba. 10Mu dai a kullayaumin muna dauke da mutuwar Yesu a jikkunanmu, saboda a bayyana rayuwar Yesu a jikkunanmu kuma.11Mu da muke a raye kuwa a kulluyaumin ana mika mu ga mutuwa saboda Yesu, domin rayuwar Yesu ta zama a bayyane a jikunanmu na mutuntaka. 12Saboda haka, mutuwa tana aiki a cikinmu, amma rai na aiki a cikinku.13Amma dai muna da wannan Ruhu na bangaskiya kammar yadda aka rubuta: "Na gaskata, saboda haka na furta." Mu ma mun gaskata, haka kuwa muke fada. 14Mun sani cewa wanda ya tada Ubangiji Yesu daga matattu za ya sake tada mu tare da Yesu. Mun san cewa zai gabatar da mu tare da ku a gabansa. 15Dukan abubuwa sabili da ku suke domin, yayin da aka baza alheri ga mutane dayawa, bada godiya ta karu ga daukakar Allah.16Don haka ba mu karaya ba. Kodashike daga waje muna lalacewa, daga ciki ana sabunta mu kulluyaumin. 17Domin wannan 'yar wahala ta dan lokaci tana shirya mu zuwa ga nauyin madauwamiyar daukaka wadda ta wuce gaban aunawa. 18Domin ba muna kallon abubuwan da ake gani bane, amma abubuwan da ba a gani. Abubuwan da muke iya gani ba masu dawwama ba ne, amma abubuwan da ba a gani madawwama ne.
Bulus ya rubuta gaskiyar hidimar sa ta wurin wa'azin Almasihu ba ya kuma yabon kansa. Ya bayyana mutuwa da rayuwar Yesu ta yadda ya yi rayuwa saboda rai ta yi aiki cikin masubi da ke Korantus
Kalman nan "mu" na nufin Bulus da abokan aikin sa, amma banda Korantiyawa.
Wannan maganan ta bayyana yadda Bulus da abokan aikinsa sun "sami wannan hidimar." Kyauta ce wanda Allah ya basu tawurin jinkansa. AT: "domin Allah ya nuna jinkansa gare mu" (Dubi:")
Wannan na nufin Bulus da abokan aikinsa sun ki su yi abin "kunya da kuma abin da ke boye). Bai nuna cewa sun yi waɗannan abubuwa a da ba.
Kalman nan "boye" ta bayyana abubuwan da mutane ke yi a boye. Abin kunya ya kamata ta sa su su ji kunya. AT: "abubuwan da mutane ke yi a boye domin ta na sa kunya"
"zaman yaudara"
"Kalman Allah" a nan ta nufin wata kalma da za a yi amfani da sakon daga Allah a maɗadin ta. Wannan maganan na amfani da abu biyu
Ma'anan wannan shi ne sun tanada shaida ga kowane mutum mai jin su domin ya zaba ko sun yi daidai ko kuwa ba daidai ba.
Wannan na nufin a gaban Allah. Fahimtar Allah da kuma amincewar sa game da gaskiyar Bulus na nufin Allah na iya ganin su. AT: "gaban Allah" ko "da Allah wanda shi ne shaida"
Wannan na mai da mu baya zuwa [2 Korantiyawa 3:14-16]
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "idan mayafi ta rufe bisharar mu, wannan mayafin ta rufe ta"
"bishara da muke wa'azin"
Bulus ya maganar zukantans kamar suna da idanu da kuma rashin iya fahimtarsu kamar zukantansu bata iya gani ba. AT: "allahn wannan duniya ya hana marasa bada gaskiya fahimta"
"allahn da ke mulkin wannan duniyan." Wannan na nufin Shaidan.
Israila ba su iya ganin ɗaukakar Allah da ta haskaka fuskan Musa ba saboda ya rufe she da mayafi. (Dubi: 2 Korantiyawa 3:13), haka nan marasa bada gaskiya ba su iya ganin ɗaukakan Almasihu da ke haskaka wa cikin bishara ba. Wannan na nufin ba us iya fahimtar "bisharar ɗaukakan Almasihu ba"
"hasken da ke zuwa daga bisharan"
"bishara game da ɗaukakan Almasihu"
za ku iya sa kalma ta aikatau a waɗannan maganganun. AT: "amma mu kam shelar Almasihu Yesu a matsayin Ubangiji muke yi da kuma shelar kan mu a matsayin bayin ku"
"saboda Yesu"
Da wannan jumlar, Bulus na nufin Allah mahalincin haske kamar yadda aka bayyana cikin littafin Farawa.
A nan kalman nan "haske" na nufin iya fahimta. Kamar yadda Allah ya halici haske, haka nan ya halici masubi da fahimta. AT: " Ya riga ya nuna ... don mu iya fahimtar ɗaukakar Allah"
A nan kalman nan "zukata" na nufin zuciya da tunani. AT: "cikin zuciyar mu"
"hasken itace sanin ɗaukakar Allah"
"ɗaukakar Allah a fuskan Yesu Almasihu." Kamar yadda daukakar Allah ta ke a fuskar Musa (Dubi: 2 Korantiyawa 3:7), haka nan take haskakawa a fuskar Yesu. Ma'anar wannan kuwa ita ce a sa'ada Bulus na wa'azin bishara, mutane kuwa sun iya gani da kuma fahimtar sakon game da ɗaukakar Allah.
A nan kalmar nan "mu" na nufin Bulus da abokan aikinsa badan Korantiyawa.
Bulus ya yi magana game da bishara kamar wata dukiya, jikin mu kuma kamar randuna da aka yi da yumbu da zata iya fashewa. Nauyi wannan itace suna da daraja kadan ne in an kwatanta da darajar bishara da ka yi wa'azin ta.
"yadda zai zama a bayyane ga mutane" ko "don mutane su sani ba shakka"
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "Mutane sun wahala da mu ta kowace hanya"
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "Mutane na tsananta man amma Allah bai yashe mu ba"
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "Mutane sun doddoke mu amma ba su hallaƙa mu ba"
"Aka ji mana mumunar ciwo"
Bulus ya yi maganar wahalar sa kamar ya taba jin yadda mutuwan Yesu ta ke. AT: "Kullum muna cikin haɗarin mutuwa yadda Yesu ya mutu" ko "kullayaumi muna shan wahala a wani yanayi da mu kan ji kamar mutuwar Yesu"
Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) "jikunan mu zata sake rayuwa domin Yesu na raye" ko 2) "rayuwar ruhu da Yesu ya bayar ta kuma nuna cikin jikinmu."
Ɗaukar mutuwan Yesu tana misalin zama cikin haɗarin mutuwa saboda biyayya ga Yesu. AT: "Ga mu da muke raye, Allah ya kan bishe mu mu fuskanci mutuwa domin muna tare da Yesu" ko "Mutane a kullayaumi kan sa mu cikin haɗarin mutuwa mu da muke raye saboda muna tare da Yesu"
Allah na son rayuwar Yesu ta bayyana cikin mu. Ma'ana mai yiwuwa suna kamar haka 1) "jikunan mu zata rayu kuma domin Yesu yana raye" ko 2) "rayuwar ruhu da Yesu ya bayar ta bayyana cikin jikunan mu." (Dubi yadda kun juya wannan magana cikin 2 Korantiyawa 4:10.
Bulus ya yi maganar mutuwa da rai kamar wani mutum ne da zai iya aiki. Wannan na nufin suna cikin haɗarin mutuwar jiki saboda Korantiyawa su iya samun rai ta ruhaniya.
"hali ɗaya ta bangaskiya." Anan Kalman nan "ruhu" na nufin halin mutum da kuma hali.
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "shi wanda ya rubuta waɗannan kalmomi"
Wannan nasi ce daga Zabura.
A nan tada karin magana ce na sa wani wanda ya mutu ya tashi da rai kuma. AT: "cewa shi wanda ya sa Ubangiji Yesu ya rayu kuma zai" ko " Allah wanda ya tada Ubangiji Yesu zai"
A nan kalman nan "dukan abubuwa" na nufin dukan wahalar da Bulus ya yi misalin su a ayoyi kafin wadannan.
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "sa'ada Allah ya yaɗa alherinsa ga mutane masu yawa"
Bulus ya yi maganar bada godiya kamar kamar wani abu ne da zata iya karuwa da kanta. AT: "mutane dayawa su mika godiya"
Ana iya bayyana wannan kamar tabbaci. AT: "Don muna da gabagadi"
Wannan na nufin jikunan su mai ruɓe wa da kuma mutuwa. AT: "jikunan mu tana kara zama mara karfi tana kuma mutuwa"
Wannan na nufin daga ciki rayuwarsu ta ruhaniya na samun karfi. AT: "ruhaniyan mu tana samun karfin kulluyaumi"
Bulus ya yi maganar wahalarsa da kuma ɗaukaka da Allah zai ba shi kamar waɗansu abubuwa da za a iya gwada nauyin ta. Daukakan ta fi wahalan sosai.
Nauyin ɗaukakar da Bulus zai ji ba za a iya aunawa ba. AT: "wanda ba mai iya aunawa"
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "abubuwan da muna iya gani...abubuwan da ba mu iya gani"
Za ku iya sa aikatau a wannan maganar. AT "amma muna duban abubuwan da ba a gani"
1Mun san cewa idan wannan gidan da muke zaune a ciki ya rushe, muna da wani ginin daga wurin Allah. Gida ne wanda ba hannuwan mutane suka gina ba, amma madawwamin gida ne a cikin sama. 2Domin a cikin wannan jiki muna gurnani, muna jira a suturta mu da wurin zaman mu na samaniya. 3Muna jiran wannan ne domin ta wurin suturtar da mu ba za a same mu tsirara ba.4Gama babu shakka yayinda muke cikin wannan alfarwa, muna gurnani, muna nawaita. Ba mu so muyi zaman hutanci. Maimakon haka, muna so a suturtar da mu, domin rai ya hadiye abu mai mutuwa. 5Wanda kuwa yake shirya mu domin ainihin wannan abu Allah ne, wanda ya ba mu Ruhu a matsayin alkawarin abinda ke zuwa.6Domin wannan mu zama da gabagadi koyaushe. Mu lura da cewa yayinda muka shagala cikin jiki, muna nesa da Ubangiji. 7Gama bisa ga bangaskiya muke tafiya, ba bisa ga ganin ido ba. 8Don haka muna da gabagadi. Mun gwammace mu rabu da jiki domin mu zauna tare da Ubangiji.9Sai muka maishe shi burinmu, ko muna cikin jiki ko nesa, mu gamshe shi. 10Domin tilas dukanmu mu hallara a gaban kursiyin shari'a na Almasihu, saboda kowa ya karbi sakamakon abubuwan da yayi cikin jiki, ko masu kyau ne ko marasa kyau.11Don haka, domin mun san tsoron Ubangiji, muna rinjayar mutane. Allah na ganin yadda muke a fili. Ina fatan hakan a fili take ga lamirinku. 12Ba muna kokarin mu rinjaye ku domin ku kalle mu a matsayin amintattun mutane ba. Maimakon haka, muna ba ku dalilin yin takama da mu, domin ku sami amsar da za ku bada ga wadanda ke fahariya da kasancewarsu amma ba game da abinda ke zuciya ba.13Gama idan mun fita daga hankulanmu, saboda Allah ne. Kuma idan muna cikin hankalinmu, domin ku ne. 14Domin kaunar Almasihu ta tilas ta mu, domin mun tabbatar da wannan: cewa mutum daya ya mutu domin kowa, kuma domin wannan duka sun mutu. 15Kuma Almasihu ya mutu domin kowa, domin wadanda ke raye kada su sake rayuwa domin kansu. A maimakon haka, su yi rayuwa domin shi wanda ya mutu kuma aka tashe shi.16Domin wannan dalili, daga yanzu ba za mu kara shar'anta kowa bisa ga ma'aunin 'yan'adam ba, ko da yake a baya mun taba duban Almasihu a haka. Amma yanzu mun daina shar'anta kowa ta haka. 17Saboda haka, duk wanda ke cikin Almasihu, sabon halitta ne. Tsofaffin al'amura sun shude. Duba, sun zama sababbi.18Dukan wadannan abubuwa daga Allah ne. Ya sulhunta mu da kansa ta wurin Almasihu, ya kuma ba mu hidimar sulhu. 19Wato, cikin Almasihu, Allah na sulhunta duniya zuwa gare shi, ba tare da lissafin zunubansu a kansu ba. Yana damka mana sakon sulhu.20Don haka an zabe mu a matsayin wakilan Almasihu, kamar dai Allah na kira ga mutane ta wurin mu. Muna rokon ku, saboda Almasihu: "ku sulhuntu ga Allah!" 21Shi ya maida Almasihu ya zama hadaya domin zunubinmu. Shine wanda bai taba zunubi ba. Ya yi haka ne don mu zama adalchin Allah a cikin sa.
Bulus a ciga da nuna bambanci tsakanin jikunan masubi ta wannan duniya da kuma na sama wanda Allah zai bayar.
A nan "gida ta duniya" zuwa wani lokaci ƙayadadde kwatanci ce ta jikin mutum. Anan dauwamammen "gini daga wurin Allah" kwatanci ce ta sabon jiki da Allah zai ba wa masu gaskantawa da shi bayan sun mutu.
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "in mutane sun rushe gidan mu ta duniya wanda muke ciki" ko "in mutane sun kashe jikunan mu"
Ma'ana "gidan" anan abu daya da "gini daga Allah." "Hannu" anan misali ce dake nufin gabadayan mutum. Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "Gida ce wanda ba mutane ne suka yi ba"
"wannan Bukka" na nufin abu daya ne da "gidan da muke ciki a wannan duniya." Kalman nan nishi wata ƙara ce wanda wani kan yi a sa'ada su na sa begen samun wani abu mai kyau.
Kalmomin nan "gidan mu na samaniya" na nufin abu daya ne da "gida ne daga Allah." Bulus yayi maganar sabon jiki da masubi za su samu bayan mutuwar su kamar wata gini da kuma sutura da mutum zai iya sa wa.
"ta wurin sa gidanmu na samaniya"
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. "baza mu zauna tsirara ba" ko " Allah ba zai same mu tsirara ba"
Bulus ya yi maganar jikin kamar wata "bukka."
Kalman nan "alfarwa" na nufin "gidan nan ta duniya da muke zama ciki." Kalman nan nishi wata ƙara ce wanda wani kan yi a sa'ada su na sa begen samun wani abu mai kyau. Dubi yadda kun juya wannan cikin 2 Korantiyawa 5:2.
Bulus na nufin shan wahala da jiki ke ji kamar wata abu ne mai nauyi da ke da wuyar ɗaukawa.
Bulus ya yi maganar jikin kamar wata sutura. "Rashin sutura" anan na nufin nutuwar jiki; "sa sutura" na nufin samun jiki na tashin mattatu da Allah zai bayar.
"zama da rashin sutura" ko "zama tsirara"
Bulus ya yi maganar rai kamar wata dabba ce da ke cin "abu mai mututwa." Dawamammen Jiki na tashin mattatu za ta cika gurbin jiki da zai mutu
An yi maganan Ruhun kamar shi ba cikakken fansa ne zuwa ga samun rai madawami. Dubi yadda ka juya magana mai kama cikin 2 Korantiyawa 1:22.
Bulus ya yi maganar jikin kamar wata wuri ne da mutum ke zama. AT: " a yayinda muna zama cikin jiki ta duniya"
"ba mu gida tare da Ubangiji" ko "ba mu cikin sama tare da Ubangiji"
Anan "tafiya"kwatanci ne na "zama" ko "nuna hali." AT: "Muna zama bisa ga bangaskiya ba bisa abinda muke gani ba"
Kalman nan "jiki" anan na nufin jikin ta duniya.
"a gida tare da Ubangiji cikin sama"
Ana iya sa kalman nan "Ubangijin" daga ayoyi dake baya. AT: "ko muna gida tare da Ubangiji ko nesa da Ubangiji"
" faranta wa Ubangiji"
"gaban Almasihu domin shari'a"
"kowane mutun zai karbi abin da ya cancanci shi"
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "abubuwan da ya yi ciki jikin nan ta duniya"
"ko abubuwa nan masu kyau ko mara kyau
"mun san abin da ake nufi da tsoron Ubangiji"
Ma'ana mai iya yiwuwa suna kamar haka 1) "mun rinjaye mutane game da gaskiyar bishara" ko 2) "mun rinjaye mutane da cewa mu ainihin manzanai ne."
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "Ba shakka Allah na ganin wani irin mutane ne muke"
"cewa kun tabbatar da ita"
"don ku iya samun abin fada ga"
Kalman nan "bayyanuwa" anan na nufin abubuwa kamar iyawa da matsayi. "zuciya" kalma ce dake nufin hali na cikin mutum. AT: "waɗanda suke yabon ayukansu amma basu damu da abin da suke a rayukansu na ciki ba"
Bulus ya yi magana game da yadda waɗansu suke tunani game da su da abokan aikin sa. AT: "in mutane na tunani mu mahaukata ne... in mutane na tunani mu masu hankali ne"
Ma'ana mai iya yiwuwa na kamar haka 1) "ƙaunar mu ga Almasihu" ko 2) "Almasihu na ƙaunar mu"
"mutu domin dukan mutane"
"shi wanda ya mutu saboda su wanda Allah ya rayar da shi kuma" ko "Almasihu wanda ya mutu saboda su wanda Allah ya tashe shi"
Ma'ana mai iya yiwuwa suna kamar haka 1) waɗannan kalmomin na nufin "mutu" kawai ko 2) waɗannan kalmomin na nufin duka biyun da "mutu" da kuma "an tashe."
Wannan na nufin abin da Bulus ya gama fada game da rayuwa don Almasihu maimakon rayuwa don jiki.
Bulus ya yi magana a kan mutum da gaskanta da Almasihu kamar sabon mutum wanda Allah ya halici. AT: "sabon mutun ne"
A nan "tsofaffin al'amura" na nufin abubuwa da ke nuna halin mutum kafin sun amince da Almasihu.
Kalman nan "Duba" tana shiryamu mu mai da hankali ga sanarwa mai ban mamaki da ke zuwa.
"Allah ya yi duk waɗannan abubuwa." Wannan na nufin abin da Bulus ya gama fada a ayoyin da ke baya game da sabon abubuwa sun cika gurbin tsohon abubuwa.
Ana iya juya wannan da sashen magana da ke da aikatau. AT: "aikin sulhunta mutane gare shi"
"Wannan na ma'ana"
Kalman nan "duniya" anan na nufin mutane dake cikin duniya. AT: "cikin Almasihu Allah na sulhunta yan Adam wa kansa"
Allah ya ba wa Bulus alhakin baza sako cewa Allah na sulhunta mutane wa kansa.
"sakon game da sulhu"
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "Allah ya naɗa mu wakilan Almasihu"
"waɗanda suna magana a maɗadin Almasihu"
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "Bari Allah ya sulhunta ku zuwa gare shi"
"Allah ya mai da Almasihu hadayan don zunubi"
Kalman nan "namu" da "mu" anan suna haɗe na kuma nufin dukan masubi.
"Almasihu ne wannan da bai taɓa yin zunubi ba"
"Allah ya yi wannan ... adalcin Allah cikin Almasihu"
Maganar nan "adalcin Allah" na nufin adalcin da Allah na bukata kuma wanda ta zo ne daga Allah. AT: " domin mu iya samun adalcin Allah cikin mu ta wurin Almasihu"
1haka, tundashike muna aiki tare, na roke ku kar ku yi watsi da alherin Allah. 2Domin ya ce, "A lokacin alheri na saurare ku, kuma a ranar ceto na agaje ku." Yanzu ne fa, lokacin alheri. Duba, yanzu ne ranar ceto.3Ba mu sa sanadin faduwa a gaban kowannen ku, domin ba mu so hidimarmu ta zama marar amfani.4Maimakon haka, mun tabbatar da kan mu ta wurin dukan ayyukanmu, cewa mu bayin Allah ne. Mu bayinsa ne ta wurin yawan jimiri, azaba, kunci, wahala, 5duka, kurkuku, tarzoma, cikin aiki tukuru, cikin rashin barci yawancin dare, cikin yunwa, 6cikin tsarki, ilimi, hakuri, kirki, cikin Ruhu Mai tsarki, da sahihiyar kauna. 7Mu bayinsa ne cikin kalmar gaskiya, cikin ikon Allah. Muna kuma da makamai na adalci, a hanun dama da hagu.8Muna aiki cikin daraja da rashin daraja, kushe da yabo. Ana zargin mu a kan mu mayaudara ne, duk da haka mu masu gaskiya ne. 9Muna aiki kamar ba a san mu ba, gashi kuwa mu sanannu ne. Muna aiki kamar masu mutuwa-duba! -har yanzu muna raye. Muna aiki kamar wadanda aka hukunta, amma ba hukuncin kisa ba. 10Muna aiki kamar muna bakinciki, amma a koyaushe muna farinciki. Muna aiki kamar matalauta, amma muna azurta mutane dayawa. Muna aiki kamar ba mu da komai, amma mun mallaki komai.11Mun fada maku dukan gaskiyar, Korantiyawa, kuma zuciyar mu a bude ta ke. 12Ba mu kange zukatan ku ba, ku ne kuka kange zukatanku a gare mu. 13Yanzu a sabanin haka-Ina magana da ku kamar yara-ku bude mana zukatanku.14Kada ku yi cudanya da marasa bangaskiya. Wace tarayya ke tsakanin adalci da take shari'a? Ko kuma wace zumunta ce ke tsakanin haske da duhu? 15Wace yarjejeniya ke tsakanin Almasihu da Ibilis? ko kuma me ya hada masu bangaskiya da marasa bangaskiya? 16ko wace yarjejeniya ce a tsakanin haikalin Allah da gumaka? Domin kuwa mu haikali ne na Allah mai rai, kamar yadda Allah ya ce: "Zan zauna a cikin su, in kuma yi tafiya a tsakanin su. Zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena."17Sabili da haka, "Ku fito daga cikin su, kuma ku zama kebabbu," in ji Ubangiji. "Kada ku taba kazamin abu, zan kuma karbe ku. 18Zan zama Uba a gare ku, ku kuma za ku zama 'ya'ya maza da mata a gare ni," in ji Ubangiji Mai iko duka.
Bulus ya takaita yadda tafiya tare ya kamata ya zama don Allah.
cikin aya 2 Bulus ya rubuta da sashin annabi Ishaya.
Bulus na nufin shi da Timoti suna tafiya tare da Allah. AT: Tafiya tare da Allah"
Bulus ya roƙe su sun bar alherin Allah ta yi aiki rayuwar su. Ana iya bayana wannan kalmomi masu nuna tabbaci. AT: "muna rokon ku, ku yi amfani da alherin da kuka karɓa daga wurin Allah"
"Don Allah ya ce." Wannan ya gabatar da nassi daga annabi Ishaya ya faɗa. AT: "Allah ya ce cikin littafi"
Kalmar na "Duba" anan na shirya su da su kassa kunne ga labari mai ban mamaki dake biyowa.
Bulus ya yi maganar abin da zai hana mutum sa begen sa ga Almasihu kamar wani abu da mutumin zai iya yin tuntuɓe ya fadi. AT: "Ba mu so mu yi wani abu da zai hana mutane gaskantawa da sakon mu"
"Kalmar nan "aibata" na nufin mutane ba faɗin abu mara kyau game da aikin Bulus da kuma găba da sakon da ya shaida. Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "ba mu son mutane su iya yin magana mara kyau game da aikin mu"
"Mun haƙikanta cewa mu bayin Allah ne tawurin dukan abin da muke yi"
Bulus ya ambaci iririn yanayi masu wuya wanda a cikin ta sun haƙikanta cewa sun bayin Allah ne.
Bulus ya ambaci waɗansu halin kirki da dama don ya nuna cewa cikin yanayi ma wuya haƙika su bayin Allah ne.
Mika kansu wurin wa'azin bishara cikin iƙon Allah ya nuna cewa haƙika su bayin Allah ne.
"ta wurin maganar sakon Allah game da gaskiya" ko "ta wurin maganar gaskiyar sakon Allah"
"ta wurin nuna ikon Allah ga mutane"
Bulus ya yi maganar adalcin su kamar wata makami da ake amfani da ita a yi yakin ruhaniya.
"adalci kamar sulkin mu" ko "adalci kamar makamin mu"
Ma'ana mai iya yiwuwa suna kamar haka 1) akwai makami a hannu daya da kuma garkuwa a dayan hannun ko 2) suna shirye domin yaki don su iya tsare kowace hari daga kowace hanya.
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "Mutane sun zargi mu wai mu masu yaudara"
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "kamar mutane ba su san mu ba da kuma haƙika mutane sun san mu kwarai"
Kalman nan "Duba" anan na shirya mu mu saurari labari ta ban mamaki zai biyo baya.
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "Muna aiki kamar mutane sun tsananta mana ta dalilin aikin mu amma ba kamar an yi mana hukunci kisa ba"
"sahilin maganar gare ku"
Bulus ya yi maganar ƙaunarsa ga korantiyawa kamar samun zuciya da ke a buɗe. Anan "zuciya" wata magana ce da ake amfani da ita a maɗadin abin da mutum ke ji. AT: "muna kanar ku sosai"
Bulus ya yi maganar rashin ƙaunar Korantiyawa zuwa gare shi kamar zukantan da aka matse ta don shiga matsesen wuri. Anan "zuciya" wata magana ce da ake amfani da ita a maɗadin abin da mutum ke ji.
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "Ba mu kange ku ba" ko " Ba mu ba ku wata dalilin da zai sa ku ki ƙaunar mu ba"
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "zukatan ku tana kange ku" ko "kun bar ƙaunar mu ta dalilin kanku"
"kamar amsar da ta dace"
Bulus ya yi magana da Korantiyawa kamar 'ya'yan sa na ruhaniya. AT: "Na yi magana kamar ni uban ku ne"
Bulus ya karfafa Korantiyawa su ƙaunace shi kamar yadda ya ƙaunace su. AT: "ku ma ku ƙaunace mu" ko "ku ƙaunace mu sosai kamar yadda mun ƙaunace ku"
Ana iya bayyana wannan cikin kalmomi masu nuna i. AT: "sai dai ku yi cudanya da masubi"
Bulus ya yi maganar aiki tare domin manufa ɗaya kamar dabbobi biyu da aka ɗaure don jan keken shanu ko noma. AT: "
Wannan tambaya ce da ke jiran amsa ta a'a. AT: "Don adalci ba ta iya taraya da take shari'a"
Bulus ya yi wannan tambayar domin ya nanata cewa haske da duhu ba za su iya zama tun da shiƙe haske kan kori duhu. Kalmomin nan "haske" da "duhu" na nufin hali da kuma nau'i ta ruhaniya na masubi da marasabi. AT: "Haske ba za ta iya samu ɗangantaka da duhu ba"
Wannan tambaya ce da ke jiran amsa ta a'a. AT: "Babu wata yarjejeniya tsakanin Almasihu da Ibilis?
Wannan wata suna ce ta ibilis.
Wannan tambaya ce da ke jiran amsa ta a'a. AT: " Ba abinda da ya hada mai bada gaskiya da mara bada gaskiy"
Wannan tambaya ce da ke jiran amsa ta a'a. AT: "Babu wata yarjejeniya tsakanin haikalin Allah da gumaka"
Bulus na nifin dukan Krista siffa ce ta haikalin da Allah ke zama ciki. AT: mu na kama da haikali wanda ke mazaunin Allah mai rai"
Wannan nasi ce daga Tsohon Alkawari dake magana akan Allah na tare da mutane a hanyoyi biyu dabam dabam. Kalmomin nan "zaune tsakanin" na magana rayuwa in da wadansu ke rayuwa, kalmomin nan "tafiya tsakanin" kuma na nufin zama tare da su a sa'ada suke rayuwar su. AT: "Zan zama tare da su in kuma taimake su"
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "ku kebe kanku" ko "ku bari in keɓe ku"
Ana iya bayyana wannan cikin kalmomi dake nuna. AT: "Taba abu mai tsabta"
1Kaunatattu, da shike muna da wadannan alkawura, bari mu tsaftace kanmu, daga dukan abubuwan da ke kazantar da jikinmu da ruhunmu. Bari mu bidi tsarki cikin tsoron Allah.2Ku ba mu dama! Bamu bata wa kowa rai ba. Ba mu cutar da kowa ko mu zambaci kowa ba. 3Ba domin in kayar da ku na fadi haka ba. Domin kuwa na riga na fada muku, cewa kuna zuciyar mu, domin mu mutu tare mu kuma rayu tare. 4Ina da muhimmin gabagadi a cikin ku, Ina fahariya da ku. Ina cike da ta'aziya. Farincikina ya cika makil duk da wahalhalunmu.5Yayin da muka zo Makidoniya, jikinmu bai samu hutu ba. A maimakon haka, mun shiga matsaloli ta ko wace hanya ta wurin tashin hankali a waje tsoro kuma a ciki. 6Amma Allah, mai ta'azantar da raunana, ya ta'azantar da mu ta wurin zuwan Titus. 7Ba ta wurin isowar sa kadai Allah ya yi mana ta'aziyya ba. Amma kuma ta wurin ta'aziyyar da Titus ya samu daga wurin ku. Ya gaya mana irin matsananciyar kaunarku, bakincikinku, da zurfin kulawarku a kaina. Na kuwa yi farinciki sosai.8Kodashike wasikata, ta bata maku rai, ban yi da na sanin haka ba. Amma sa'adda na ga wasika ta ta bata maku rai, na yi da na sani. Sai dai bacin ranku, na dan lokaci ne. 9Yanzu kuwa, ina farinciki, ba domin bacin ranku ba, amma domin bacin ranku ya kawo ku ga tuba, kun fuskanci bakinciki na ibada, donhaka ba ku yi rashi ba sabili da mu. 10Domin bakinciki daga Allah ya kan kai ga tuba da ke kammala ceto ba tare da-da na sani ba. Bakinciki na duniya kuwa ya kan kai ga mutuwa.11Ku dubi irin kyakkyawar niyya da bakincikin nan daga Allah ya haifar a cikin ku. Ina misalin girman niyyar nan taku ta nuna cewa baku da laifi. Ina misalin girman fushinku, tsoronku, da sa zuciyarku, himmar ku, da marmarin ku na ganin cewa an yi adalci! A cikin komai, kun nuna kanku marasa laifi a cikin wannan al'amari. 12Kodayake na rubuto maku, ban rubuto saboda mai laifin ba, ko kuma saboda wanda aka yi wa laifin. Na rubuto ne domin himmarku gare mu ta sanu gare ku a gaban Allah.13Dalilin haka ne muka samu karfafawa. Baya ga ta'aziyyar mu, mun kuma yi murna sosai saboda farin cikin Titus, domin ruhunsa ya wartsake ta wurin ku duka. 14Domin kuwa idan na yi fahariya da ku a gaban sa, ban ji kunya ba. A sabanin haka, kamar yadda kowane abu da muka fada maku gaskiya ne, fahariyarmu a kan ku ga Titus ta zama gaskiya.15Kaunarsa a gare ku tana da girma, kamar yadda ya rika tunawa da biyayyarku duka, yadda kuka karbe shi da tsoro da rawar jiki. 16Ina farinciki matuka domin ina da cikakken gabagadi a cikin ku.
Bulus ya cigaba da tunashe su da su rabu da zunubi su kuma biɗi zaman tsarki da nufi daya.
"Ku wanda nake ƙauna" ko "Abokai na na kwarai"
Bulus na cewa ana da su yi nesa daga kowace irin zunubi da zai bata dangantakansu da Allah.
"mu yi ƙoƙarin zaman tsarki"
"Tawurin girmama Allah kwarai"
Wannan na nufin abin da Bulus ya ce [2 Korantiyawa 6:11-13]
"Ban faɗi wannan domin zambar ku cewa kun yi wata laifi ba." Kalman nan "wannan" na nufin abin da Bulus ya faɗa yanzu cewa bai yi wa kowa laifi ba.
Bulus ya yi maganar ƙaunar da shi da abokan aikin sa suke yi wa Korantiyawa kamar sun rike su cikin zukatan su. AT: "ku ƙaunatattun mu ne"
Wannan na nufin Bulus da abokan aikin za su ciga da ƙaunar Korantiyawa a ko wace yanayi. AT: "ko muna raye ko mun mutu"
"mu" na nufin duk da masubi na Korantiyawa
Ana iya bayyana wannan a cikin nau'i mai aiki. AT: "Kun cika ni da ta'aziya"
Bulus ya yi maganar farincikinsa kamar wata ruwa da ya cika shi har lokacin da ta fara zuɓe wa. AT: "Ina da matukar farinciki "
"duk da dukan wahalar mu"
Kalman nan "mu" anan na nuf Bulus da Timoti amma bada Korantiyawa ko Titus.
"Jiki" anan na nufin gabadayan mutumin. AT: "ba mu sami hutu ba" ko "mun gaji kwarai"
Ana iya bayyana wannan cikin nau'i mai aiki. AT: "muna shan wahala ta kowace hanya"
Ma'ana mai iya yiwuwa ta "waje" suna kamar haka 1) "wajen jikunan mu" ko 2) "wajen ikilisiya." kalman nan "ciki" na nufin yadda suke ji a cikin su. AT: "ta wurin tashin hankali tare da mutane da kuma tsoro a cikin mu"
Bulus ya sami ta'aziya tawurin sanin cewa Korantiyawa sun ta'azantar da Titus. AT: "Ta wurin sanin cewa Titus ya sami ta'aziay daga gare ku"
Wannan na nufin wasikar Bulus ta da zuwa ga masubi na Korantiyawa wanda a cikin ta ya tsauta musu don sun karbi cewa maibi na iya yin fasikanci da matan uban sa.
"sa'ada na sani cewa wasika ta"
Ana iya bayyan wannan cikin nau'i mai aiki. AT: "ba domin abin da na faɗa cikin wasika ta ya bata muku rai ba"
"Baku rasa kome ba domin mu tsauta maku." Wannan na nufin ƙodashiƙe wasikar ta sa su baƙin ciki, sun karu ta wurin wasikar domin ta kai su ga tuba. AT: "don haka ba mu yi muku lahani a ko wata hanya ba"
Kalman nan "tuba" ana iya nanata ta don bayyana dangantakan abin da ta bi baya da kuma wanda ke biye da shi. AT: "Gama baƙin ciki wanda Allah ke sa wa na kai ga tuba, tuba kuwa na kai ga ceto"
Ma'ana mai iya yiwuwa suna kamar haka 1) Bulus bai yi 'da na sani' ba saboda baƙin ciki domin baƙin ciki ta kai ga tuban da kuma ceton su ko 2) Korantiyawa ba za su yi 'da na sani' ba don baƙin cikin su ba don ta kai ga tuban da kuma ceton su.
Irin wannan baƙin ciki tana kai ga mutuwa ba ceto ba domin ba ta kai ga tuba. AT: "Baƙin ciki ta duniya tana kai ga mutuwa cikin ruhaniya"
"Duba ka gani don kan ka kyakkyawar ƙuduri"
Anan Kalman nan "Ina misalin" ta sa wannan maganar ta zama kamar maganar motsin rai. AT: "ƙudurin ku don nuna cewa ba ku da laifi kyakyawa ce!"
"fushin ku"
Ana iya bayyana wannan cikin nau'i mai aiki. AT: "cewa wanin ya yi adalci"
"shi wanda ya yi laifi"
Ana iya bayyana wannan cikin nau'i mai aiki. AT: "don ku sani cewa himmarku zuwa gare mu sahili ce"
Wannan na nufin a gaban Allah. Sannin Allah da kuma yardan gaskiyar Bulus na kamar cewa Allah ya iya ganin su. Dubi yadda kun juya wannan cikin [2 Korantiyawa 4:2]
Kalman nan "wannan" anan na nufin yadda Korantiyawa sun karbi wasikar Bulus, kamar yadda ya bayyana a ayan da ke baya. Ana iya bayyana wannan cikin nau'i mai aiki. AT: Wannan ne ta karfafa mu"
Anan kalman nan "ruhu" na nufin yanayin mutum da kuma halinsa. Ana iya bayyana wannan cikin nau'i mai aiki. AT: "kun wartsake ruhun sa dukan ku" ko "dukan ku kun sa shi ya daina damuwa "
"Don ƙodashiƙe na yi fahariya daku a gaban sa"
"ba ku ba ni kunya ba"
"kun hakikanta cewa fahariyarmu game da ku zuwa ga Titus gaskiya ce"
Wannan "biyayya" ana iya bayyana ta da aikatau, "biyayya." AT: "yadda dukan ku ku yi biyayya"
A nan "tsoro" da "rawar jiki" suna da ma'ana mai kama kuma suna nanata karfin tsoro. AT: "kun marabce shi da girmamawa kwarai"
Ma'ana mai iy yiwuwa suna kamar haka 1) "da babban girmamawa wa Allah" ko 2) "da babba girmamawa wa Titus."
1Muna so ku sani, 'yan'uwa, game da alherin Allah da aka bayar ga Ikkilisiyoyin Makidoniya. 2A lokacin babban gwajin wahala, yalwar farincikinsu da tsananin talaucinsu ya haifar da yalwar bayarwa hannu sake.3Domin ina shaida, sun yi bayarwa iya kokarinsu, fiye da abinda ma suke iyawa. Cikin yaddar ransu 4da roko mai yawa suka nace da a ba su zarafi su yi tarayya a wannan hidima ga masu bi. 5Haka ya auku ba kamar yadda muka yi zato ba. A Maimakon haka, sai da suka fara bada kansu ga Ubangiji. Kuma suka bada kansu gare mu bisa ga nufin Allah.6Sai muka karfafa Titus, wanda ya rigaya ya fara wannan aiki, domin ya kammala wannan aiki na bayarwa ta fannin ku. 7Amma kun habaka cikin komai-cikin bangaskiya, cikin magana, cikin sani, cikin aiki tukuru, cikin kaunarku dominmu. Don haka, ku tabbata kun habaka a wannan aiki na bayarwa.8Na fadi haka ne ba kamar ina umurtar ku ba. A maimakon haka, na fadi haka ne in gwada sahihancin kaunarku ta wurin kwatanta ta da himmar sauran mutane. 9Domin kun san alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu. Kodashike shi mai arziki ne, amma ya zama matalauci, domin ta wurin talaucinsa ku yi arziki.10A wannan al'amari zan ba ku shawarar da za ta taimake ku. Shekarar da ta wuce, ba fara wani abu kawai kuka yi ba, amma kun yi marmarin ku yi shi. 11Yanzu ku kammala shi. Kamar yadda kuke da niyya da marmarin yin haka a lokacin, bari ku yi kokari ku kawo shi ga kammalawa iyakar iyawar ku. 12Idan kuna niyya ku yi wannan aiki, abu mai kyau ne karbabbe kuma. Tabbas ya zama dai-dai da abinda mutum ke da shi, ba abinda ba ya da shi ba.13Domin wannan aiki ba domin a nawaita maku sannan wadansu su samu sauki ba ne. A maimakon haka, ya kamata a sami daidaituwa. 14Yalwar ku a wannan lokaci za ta zama abin biyan bukatarsu. Haka nan kuma domin yalwar su ta iya biyan bukatarku, domin a sami daidaituwa. 15Yana nan kamar yadda aka rubuta: "Wanda ke da shi dayawa bai samu raguwar komai ba, kuma wanda yake da kadan bai rasa komai ba."16Amma godiya ga Allah, da yasa a zuciyar Titus marmarin kulawa da ku kamar wadda nake da ita domin ku. 17Gama ba rokon mu kadai ya karba ba, amma ya yi da gaske akan haka. Ya zo gare ku ne da yardar kan sa.18Mun aiko tare da shi dan'uwa da ake yaba masa a tsakanin dukan Ikkilisiyoyi domin ayyukansa a cikin shelar bishara. 19Ba domin wannan kadai ba, amma Ikkilisiyoyi ne suka zabe shi ya tafi tare da mu a cikin yin wannan hidima ta alheri. Wannan domin girmama Ubangiji ne kansa da kuma domin aniyarmu ta taimakawa.20Muna gudun kada kowa ya sa mana laifi game da wannan alheri da muke dauke da shi. 21Niyyar mu ce mu yi kyakkyawan abu, ba a gaban Ubangiji kadai ba, amma a gaban mutane ma.22Mun kuma aiki wani dan'uwan tare da su. Mun sha gwada shi, kuma mun same shi da himma wajen ayyuka da dama. Yanzu kuma ya kara himma, saboda amincewa mai girma da yake da ita gare ku. 23Game da Titus, shi abokin tafiyata ne, kuma abokin aikina domin ku. Game da yan'uwanmu, an aiko su ne daga Ikkilisiyoyi. Su kuwa daraja ne ga Almasihu. 24Don haka, ku nuna masu kaunarku, ku kuma nuna wa Ikilisiyoyi dalilin fahariyarmu game da ku.
Bayan da ya yi bayanin canjin shirin sa da kuma na salon hidimansa, Bulus yayi magana a kan bayaswa.
AT: "alherin Allah da ya ba ikkilisiyoyin Makidoniya"
Bulus ya yi maga game da "farinciki" da "talauci" kaman abu mai rai ne da zai iya bayar da hannu sake. AT: "saboda yawar farincikin mutanen da kuma tsananin talauci, sun zama da bayarwa"
Bulus ya yi maga game da farinciki kaman abun da ana iya gani wadda yana iya yaduwa.
ko da shike ikkilisiyar Makidoniya sun sha gwaji mai tsanani da talauci, ta wurin alherin Allah, sun iya tara kuɗi domin masubi a Urushalima.
"yawan yalwar hannu sake." Kalmar nan "yalwar" na bayyana yalwar bayarwarsu hannu sake.
Wannan na nufin ikkilisiya a Makidoniya.
"da son rai"
Bulus na nufin tanadin kuɗi wa masubi a Urushalima. AT: "Wannan hidima na tanadi wa masubi da ke Urushlima"
Bulus na maganar karban kuɗi daga wurin Korantiyawa domin masubi da ke Urushalima. AT: "wanda ya karfafa bayaswanku tun daga farko"
Ya kamata Titus ya taimakawa Korantiyawa domin su kammala tarin kuɗin. AT: "domin a karfafa ku ku kammala karba da kuma yalwar bayarwa ku"
Bulus ya yi magana game da masubi na Korantiyawa kaman su kaya ne da ke a bayyane. AT: "kun yi koƙari ta hanyoyi da yawa"
AT: "ku tabbata cewa kun yi koƙari a bayaswan ku ga masubi da ke Urushalima"
Bulus na karfafa Korantiyawa cewa su yi yalwar bayarwa ta wurin kwatanta yalwar bayarwar su da na ikklisiyar Makidoniya.
A wannan halin, kalmar nan "alheri" na nanata yalwar bayarwa wanda Yesu ya albarƙaci Korantiyawa da su.
Bulus ya yi magana game da Yesu kamin zuwansa a jiki ne a matsayin mai arziki, da kuma ɗaukan jikin mutum da yayi a mastayin zaman talaka.
Bulus ya yi magana cewa Korantiyawa sun zama da arziki ta ruhania ta dalilin bayyanuwar Yesu a jikin mutum.
Wannan na nufin karban kuɗi domin a ba wa masubi da ke Urushalima. AT: "game da tarin"
AT: "kun yi marmari kun kuma yi niyya ku yi shi"
"kammala shi" ko "kare shi"
A nan kalamun nan "kyau" da kuma "karɓabbe" na da ma'ana iri guda kuma suna nanata kyaun abu . AT: "Abu mai kyau sosai"
"Dole ne bayarwa ya zama dai-dai da abinda mutum ke da shi"
Wannan na nufin karban kuɗi wa masubi da ke Urushalima. AT: "Domin wannan aikin karban kuɗi"
AT: "domin ku saukaka wa wasu ku kuma nawaita wa kanku".
"ya kamata a kasance daidai"
Da shike Korantiyawan suna aiki a wannan zamani yana nuna cewa masubi da ke Urushalima za su kuma taimaka masu a wata loƙaci nan gaba. AT: "Domin nan gaba yalwar su ta iya biyan buƙattarku"
Anan Bulus ya ɗauko wannan daga Fitowa. Ana iya bayana wannan cikin sifar aiki. AT: "yadda Musa ya rubuto"
AT: "na da komai da yake buƙata"
Anan, kalmar "zuciya" na nufin motsin ta ƙauna. Wannan na nufin cewa Allah ya sa Titus ya ƙaunace su. AT: "da ya sa Titus ya kula da ku kamar yadda nake yi"
"irin babar sha'awa" ko "kwakwaran damuwa"
Bulus na nufin yanda ya ce wa Titus ya koma korantus don ya kammala karban bayaswan. AT: "Gamma ba amince wa roƙon mu kadai ya yi don ya taimaka da karɓan bayaswanba"
" tare da Titus"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT:"ɗan'uwa da masubi ke yaba a sakanin dukan iklisiya"
"Ba kadai ne masubi a cikin dukkan iklisiyoyi ke yabon sa ba"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "iklisiyoyi sun kuma zaɓe shi"
" don gudanar da wannan aiki yalwar bayaswa." Wannan na nufin kai baikon Urshalima
" domin nuna kwazonmu don taimakawa"
Wannan na nufin kai baiko ga Urushalima. Ana iya bayana wannan maganan "yalwar bayarwa" da siffa. AT: "Game da yadda muke ɗauke da yelwar kyauta"
" Muna hankali da yadda muke rike wannan kyauta ta hanya mai daraja"
"a ra'ayin Ubangiji... a ra'ayin mutane"
Kalmar "su" na nufin Titus da kuma dan'uwan da aka ambata daga farko
"shi amini na ne wanda ke aiki tare da ni domin taima ma ku"
Wannan na nufin mutane biyu da za su raka Titus.
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "Ikkilisiyoyi sun aiko su"
Ana iya bayana wannan magan. AT: "Za su sa mutane su daraja Almasihu"
1Game da hidima domin tsarkaka, ya dace in rubuta maku. 2Na san marmarinku, wanda na yi fahariya da shi a gaban mutanen Makidoniya. Na gaya masu Akaya sun riga sun shirya tun bara. Kwazon ku ya sa yawancin su sun shiga aiki.3To na aiko maku da 'yan'uwa saboda kada fahariyarmu akanku ta zama a banza, domin kuma ku zauna a shirye, kamar yadda na ce za ku yi. 4Idan kuwa ba haka ba, idan wani cikin makidoniyawa ya biyoni kuma ya tarar da baku shirya ba, za mu ji kunya-ba ni cewa komai game da ku-domin ina da gabagadi a kan ku. 5Sai na ga ya dace in turo 'yan'uwa su zo wurin ku kafin lokaci yayi suyi shirye shirye game da gudummuwar da kuka yi alkawari. Wannan ya zama haka ne domin a shirya shi a matsayin bayarwar albarka, ba wani abin kwace ba.6Batun shine: wanda ya shuka kadan zai girbi kadan, wanda kuma ya shuka da manufar albarka zai girbi albarka 7Bari kowa ya bayar bisa ga yadda ya yi niyya a zuciyarsa. Kada ya bayar da bacin rai ko kamar dole. Gama Allah yana kaunar mai bayarwa da dadin rai.8Allah na da ikon ya sa kowace albarka ta ribanbanya domin ku, domin, a koyaushe, a cikin dukan abubuwa, ku sami duk abinda kuke bukata. Hakan zai kasance domin ku ribabbanya kowanne kyakkyawan aiki. 9Kamar yadda aka rubuta, "Ya rarraba arzikinsa, ya bada shi ga matalauta. Adalcinsa ya dawwama har abada."10Shi wanda ke bayar da iri ga mai shuka da gurasa domin abinci, zai bayar ya kuma ribabbanya maku iri domin shuka. Zai sa girbin adalcinku ya karu. 11Za ku wadata ta kowace hanya domin ku zama masu bayarwa, wannan kuwa zai sa a yi wa Allah godiya ta wurin mu.12Aiwatar da wannan hidima ba biyan bukatun tsarkaka kawai take yi ba. Tana kuma ribanbanya zuwa ayyuka masu yawa na bada godiya ga Allah. 13Domin an gwada ku an tabbatar da ku akan wannan hidima, za ku kuma daukaka Allah ta wurin biyayyar ku ga shaidar bisharar Almasihu. Za ku kuma daukaka Allah ta wurin yalwar bayarwarku gare su da kowa duka. 14Suna marmarin ganin ku, suna kuma yi maku addu'a. Suna yin haka saboda alherin Allah mai girma da ke bisan ku. 15Godiya ga Allah domin kyautarsa wadda ta fi gaban bayyanawa.
Bulus ya cigaba da zancen bayaswa . Yana so ya tabbatar da an yi bayaswa domin masubi dake bukata a Urushalima kafin ya zo saboda da kada ya zama kamar ya ci zarafin su. Ya yi magana game da yanda bayarwa ke albarcance mai bayarwa da kuma daukaki Allah.
Yayin da Bulus ke ambata Akaya, ya na nufin lardin Romawa da ke a kudancin Greece inda Korontus yake.
Wannan na nufin karban kuɗi domin a ba wa masubi a Urushalima. Ma'anan wannan zance na a bayyane. AT: "hidiman bishara ga masubi a Urshalima"
Anan kalmar "Akaya" na nufin mutane da suke zama a wannan lardin, masamman mutane na iklisiyar Koronti. AT: "mutanen Akaya su na ta shiri"
Wannan na nufin Titus da mutane biu da suka raka shi.
Bulus ba ya so waɗansu su yi tunani cewa karya ne abubuwan da ya yi fahariya game da korontiyawa.
"tarar da baku shirya kubayar ba"
Bulus ya yi anfani da korau zance don ya nanata cewa abu iri guda ne ke gaskiya game da korontiyawa. AT: "za ku kuma fin shan kunya"
Daga fahimtar Bulus, 'yan'uwan na tafiya. AT: " 'yan'uwa su tafi wurin ku"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "ba kaman abun da mun tilasta maku ku bayar ba"
Bulus ya yi kwatanci da manomi mai shuki don ya yi bayanin sakamokon bayaswa. kamar da girbin manoma na nan bisa yan da ya shuka, haka ne albarkun Allah ze kasance da yawa ko da kadan bisa Yalwar bayaswar korontiyawa.
A nan kalmar "zuciya" na nufin tunani da motsin zuciya. AT: "bayar kamar yadda ya yi nia"
Ana iya bayana wannan maganan. AT: "ba domin ya zargu ko domin wani yanna tilas'a shi ba"
Allah yana son mutane su bayar da zuciya daya domin su taimake 'yan'uwa masubi.
An bayana alheri kaman abu ne na jiki da mutum na iya samu fiye da yanda zai yi amfani. Yadda mutum ya ke ba da kudi wa masubi, Allah na kuma ba mai bayarwan dukan abin da ya ke so. AT: "Allah na iya baku fiye da ku ke bukata"
Wannan na nufin abin da ke na jiki wanda maibi ke bukata, ba don bukatan Allah ya cece shi daga zunubinsa ba.
"domin ku iya yin kyakyawan ayuka mai yawa"
"Haka yake kaman yadda aka rubuta." Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "Haka yake kamar yadda marubucin ya rubuta"
"Allah mai bayar"
A nan kalmar "gurasa" na nufin abinci muhinmi. AT: "abinci don ci"
Bulus yayi magana game da malakar Korontiyawa kamar iri ne da na bayaswa ga waɗansu kaman su na shuki. AT: "Allah zai albarkance ku don "
Bulus ya kwatanta riɓar da korontiyawa za su samu daga Yalwar bayarwansu da na girbi. AT: "Allah zai albarkance ku domin adalcin ku"
"girbin da ke zuwa daga ayukan adalcin ku." A nan kalmar "adalci" na nufin adalcin ayukan Korontiyawa a bayaswan malakar su ga masubi a Urushalima.
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "Allah zai wadatar da ku"
"Wannan" na nufin yalwar bayaswar korontiyawa. AT: "Wanda sun karbi kyautanen da mun kawo za su gode wa Allah, domin yalwar bayaswar ku" ko "idan mun ba da kyautar ku ga wanda suke so, za su yi wa Allah godiya"
A nan kalmar "hidima" na nufin Bulus da abokan tafiyarsa da sun kawo taimakon ga masubi a cikin Urushalima. AT: "Domin yin wannan hidima ma masubi a Urushalima"
Bulus ya yi magana game da hidimar masubi na Korontiya kaman abu ruwa ruwa ne wanda abu ba zai iya ɗauka ba. AT: "na sa ayuka mafiyawa da mutane za su gode wa Allah"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "Domin wannan hidiman ya tabbatar da ku"
Bulus ya ce Korontiyawa za su daukaka Allah ta wurin aminci da Yesu da kuma yalwar bayarswa ga saura masubi da suke da bukata.
"domin kyautarsa , wadda kalma bazata iya kwatanta ba." ma'anan su na kamar haka1) wannan kyauta na nufin "kyakyawar alheri" da Allah ya ba wa Korantiyawa, wanda ya sa su yalwanta ko 2) wannan kyauta na nufin Yesu Almasihu, da Allah ya ba ma masubi.
1Ni, Bulus, da kaina nake rokon ku, ta wurin tawali'u da nasihar Almasihu. Ina da saukin kai yayinda nake gaban ku, amma ina da gabagadi a gare ku yayinda ba na tare da ku. 2Ina rokon ku, yayinda nake gabanku, ba ni so in zama mai tsaurin hali. Amma ina ganin zan bukaci zama mai gabagadi sa'adda nake tsayayya da su wadanda ke zaton muna zama bisa ga jiki.3Kodashike dai muna tafiya bisa jiki, ba ma yin yaki bisa jiki. 4Domin makaman da muke yaki da su ba na jiki ba ne. Maimakon haka, makamai ne na Allah da ke da ikon rushe ikokin shaidan. Suna kawar da dukan gardandamin da ke kawo kaucewa.5Muna kuma rushe duk wani abinda ke gaba da sanin Allah. Muna kuma kama kowanne tunani zuwa biyayya ga Almasihu. 6Muna kuma shirye mu hukunta kowanne irin aiki na rashin biyayya, da zarar biyayyarku ta tabbata.7Dubi abin da aka sa a bayyane a gaban ku. In har wani ya tabbata shi na Almasihu ne, bari fa ya tunatar da kansa cewa kamar yadda shi na Almasihu ne, hakanan muma muke. 8Ko da zan yi fahariya da ikon da muke dashi, wanda Ubangiji ya ba mu domin mu inganta ku, ba domin mu rushe ku ba, ba zan ji kunya ba.9Ba na so ya zama kamar ina firgita ku ne da wasikuna. 10Domin wadansu mutane na cewa, "Wasikunsa na da iko da firgitarwa, amma in ka gan shi kumama ne. Kalmominsa ba abin saurare ba ne."11Bari wadannan mutane su sani cewa abinda muke fadi a kalmomin wasikunmu lokacin da ba mu nan, haka za mu yi in muna nan. 12Mu dai ba mu hada kanmu da kowa, ko kuma mu kwatanta kanmu da wadanda ke yabon kansu. Amma yayin da suke gwada kansu da junansu, suke kuma kwatanta kansu da junansu, ba su da ganewa.13Saidai, ba za mu yi fahariya fiye da yadda ya kamata ba. Maimakon haka, za mu yi haka ne gwalgwadon iyakar abinda Allah ya sa muyi, iyakar da takai gareku. 14Gama bamu yi zarbabi ba sa'adda muka kai gareku. Mune na farko da muka kai gare ku da bisharar Almasihu.15Ba mu yi fahariya fiye da kima game da aikin wasu ba. Maimakon haka, muna fatan bangaskiyar ku ta karu domin bangaren aikin mu ya kara fadada kwarai, kuma a daidai iyakarsa. 16Muna fatan haka, domin mu kai bishara zuwa yankunan da ke gaba da naku. Ba za mu yi fahariya akan aikin da aka yi a yankin wani ba.17"Amma bari duk wanda zai yi fahariya, ya yi ta cikin Ubangiji." 18Domin ba wanda ya ke shaidar kansa shine yardajje ba. Maimakon haka, sai dai wanda Ubangiji ke shaidarsa.
Bulus ya chanja zancen daga bayaswa zuwa tabatar da ikon shi na koyarswa kamar yada ya saba.
Ana iya furta kalmar "tawali'u" da "nasiha" ta wani hanya. AT: " Ina tawali'u da nasiha, domin Almasihu ya riga ya yi ni haka"
"wanda ke tunani"
Kalmar "jiki" na nufin sifar zunubi. "muna kwoikwayo daga ni'yar mutum"
A nana"tafiya" magana ne na "mai rai" da kuma "jiki" da na nufin rayuwa ta jiki AT: "muna rayuwa a cikin jiki "
Bulus na kokakarin rinjayan korontiyawa domin su gaskanta da shi ba da masu koyaswar karya kaman su na yaki a cikin jiki. Yakamata a bayana wannan kalmomi.
AT: 1) kalmar "jiki" na nufin rayuwa ta jiki. AT: "yi fada da abokan gabanmu ta yin anfani da makamai na jiki" ko kuwa 2) kalmar "jiki" na nufin sifar mutum na zunubi. AT: " yin yaki a hanyar zunubi"
Bulus ya yi magana game da hikima ta Allah dake bayana hikimar mutum ta zama karya kamar shi ne makami da yake rushe gagararran gidan makiya. AT: " makaman da muke yaki da su ... na nuna wa mutane cewa abun da makiyan mu sun fada ba daidai ba ne."
AT: 1) kalmar "jiki" magana ne ta jiki. AT: "ba na jiki ba ne" kokwa 2) kalmar "jiki"na nufin sifar mutum na zunubi. AT: "ba na zunubi ba ne" kokwa " kada ku yarda manna mu yi abun da ba daidai ba"
Bulus na kan magana game da yaki kaman "sanin Allah" rundunan yaƙi ne kuma " dukan abubuwa da ke sama" katanga ne da mutane su ka yi domin su kare mai sarau. AT: "ko wane jayayyan karya da mutane masu girman kai su na tunani karen kansu"
"duk abin da mutane masu girman kai su na yi"
Bulus ya yi magana game da jayayya kaman katanga ne da ke kare rundunar yaƙi. Kalman "gaba da" na nufin "tash tsaye" ba "abin da ke gaba" na kwanta a kan iska. AT: "mutane na haka domin kada su iya sanin wa ne ne Allah" "
Bulus na magana game da tunanin mutane kaman su ne makiyan soja wadda ya kama a fada.AT: "mun nuna masu yadda dabarun da mutanen ke da shi ba daidai bane mu kuma koya wa mutanen su bi umurnin Almasihu"
Kalmomin "aiki na rashin biyayya" magana ne na mutanen da ke ayukan can. AT: "hukunta kowanen ku da ya yi mana rashin biyayya"
AT: 1) wannan doka ne ko 2) wannan zance ne, "kuna duba abunda kuke iya gani da idanunku." Wadansu na tunani cewa wannan a takaice ne da ake iya rubuta a zancen. AT: "kuna duba abinda ke sarai a gaban ku?" kokwa "Kamar ba ku iya gani abun da ke sarai a gabanku ba."
"ya kamata ya tuna"
"cewa kamar yadda mu na Almasihu ne kaman yadda yake"
Bulus na maganan taimaka wa Korontiyawa domin su san Almasihu da kyau kaman ya na kan aikin gini. AT: "domin a taimake ku ku zama ainahin masubin Almasihu ba don a hana ku binsa ba"
"Ina gwada firgita ku"
"bukaci da ƙarfi"
"Ina so waɗannan mutane su sani"
"zamu sake yin irin abin da mun rubuta a cikin wasikun mu a lokacin da ba mu na tare da ku in muna nan "
Duka kwatancin wannan kalmar na nufin kungiyar bishara na Bulus ba Korontiyawa ba.
"kimar mu ta kai ga"
Bulus ya na kara maimaitawa sau biu
Bulus na maganar kyau kaman abun da mutane ke iya gwado tsawon sa. AT: "suka kali junansu ko za su iya tantace"
"sun nuna wa kowa cewa ba su san komai ba"
Bulus ya yi magana da iƙo da yake dashi kamar kasa da yake da mulki, waɗanan abubbuwa da yake da mulki a kan su suna a sakanin iyaka . ko kuwa "inda ta tsaya" na ƙasar sa, sai abubuwan da basu a karkashin iƙonsa su wuce wanan "iyaka."
AT: "ba zan yi fahariya da abubuwan da ba mu da iƙo a kansu ko kuwa zan yi fahariya da abubuwan da muke da iƙo a kansu.
"A kan abubuwan da na karkashin iƙon da Allah"
Bulus ya yi magana da iƙo da yake da shi kamar kasa ne da yake mulki. AT: " kuma kuna cikin iyakan iƙon mu"
"ba mu fita a iyakar mu ba"
AT: "yi fahariya akan abubuwa wanda bamu da iƙo a kai" ko kuwa "yi fahariya kadai akan abubuwa wanda muke da iƙo a kai." Dubi yada aka fasara kalmar a cikin 10:13.
AT: "Allah zai kara buɗe bangaren aikin mu kwarai"
"yankin da Allah ya ba wa wani"
"fahariya akan abun da Allah ya yi"
Wannan na nufin cewa ya tanada kowane mutum da ya ji shi ya kuma duba ko ya yi daidai ko bai yi daidai ba. Dubi yadda "shaidar kanmu" aka fasara a nan 4:2.
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "wanda Ubangiji ya yarda"
za ku iya bayana wannan zancen. AT: "wanda Ubangiji ya yi shaidar sa shi ne Ubangiji ya yardajje"
1Ina fatan za ku jure da ni cikin wauta kadan. Ko da yake lallai kuna jurewa da ni! 2Domin ina kishi sabili da ku. Kishi na kuwa irin na Allah ne domin ku. Tun da na alkawartar da ku a cikin aure ga miji daya. Na kuma yi alkawarin in gabatar da ku kamar budurwa mai tsarki ga Almasihu.3Gama ina fargaba a kan ku, ko watakila, kamar yadda macijin ya yaudari Hauwa'u ta wurin kissarsa, Ya zamana tunaninku ya kauce daga sahihiyar sadaukarwa ga Almasihu. 4Anar misali idan wani ya zo ya kawo shelar wani Yesu daban da wanda muka yi maku wa'azinsa. Ko kuma kun karbi wani ruhu daban da wanda muka karba. Ko kuma kun karbi wata bishara daban da wadda muka karba. Amincewar da kuka yi wa wadannan abubuwa ta isa!5Don kuwa ina tsammanin ba a baya nake ba ga sauran wadanda ake kira manyan manzanni. 6To ko ma ba a ilimantar da ni ba akan yin jawabi, ban rasa horarwar ilimi ba. Ta kowace hanya kuma cikin abubuwa duka mun sanar da ku wannan.7Na yi zunubi ne da na kaskantar da kai na domin a daukaka ku? Domin na yi maku wa'azin bisharar Allah kyauta. 8Na yi wa sauran Ikilisiyoyi kwace ta wurin karbar gudummuwa daga wurin su domin inyi maku hidima. 9Lokacin da ina tare da ku kuma na sami kai na cikin bukata, ban dora wa kowa nauyi ba. Domin 'yan'uwa da suka zo daga Makidoniya sun biya bukatuna. A cikin komai na kebe kaina daga zama nawaya a gare ku, kuma zan cigaba da yin haka.10Kamar yadda gaskiyar Almasihu ke ciki na, ba zan yi shiru da wannan fahariya tawa ba a cikin dukan kasar Akaya. 11Don me? Saboda ba na kaunar ku? Allah ya sani.12Amma abinda na ke yi, zan cigaba da yi. Zan yi haka ne domin in yanke zarafin wadanda ke son samun zarafi kamar mu akan abubuwan da suke fahariya da shi. 13Don irin wadannan mutane manzannin karya ne masu aikin yaudara. Suna badda kama kamar manzannin Almasihu.14Wannan ba abin mamaki ba ne, domin shaidan ma yakan badda kama ya fito kamar mala'ikan haske. 15Ba wani babban abin mamaki ba ne idan bayin sa sun badda kamanninsu don a dauka bayin adalci ne su. Karshen su zai zama sakamakon abin da suka aikata.16Ina kara fadi: Kada wani ya yi zaton ni wawa ne. Idan kun yi zaton hakan, to ku dauke ni kamar wawan don inyi fahariya kadan. 17Abinda nake fadi game da wannan gabagadi mai fahariya ba bisa ga amincewar Ubangiji ba ne, amma ina magana a matsayin wawa. 18Tun da mutane dayawa suna fahariya bisa ga jiki, ni ma zan yi fahariya.19Gama kuna murnar tarayya da wawaye. Ku masu hikima ne! 20Kuma kuna hakuri da wanda zai bautar da ku, idan ya tauye ku, yana amfani da ku don ribar kansa, idan ya dauki kansa fiye da ku, ko ya mammare ku a fuska. 21Ina mai cewa mun kunyata da muka rasa gabagadin yi maku haka. Duk da haka idan wani zai yi fahariya-Ina magana kamar wawa-Ni ma zan yi fahariya.22Su yahudawa ne? Ni ma haka. Su Isra'ilawa ne? Nima haka. Su zuriyar Ibrahim ne? Nima haka. 23Su bayin Almasihu ne? (Ina magana kamar ba ni cikin hankalina) na fi su ma. Na ma yi aiki tukuru fiye da su duka, shiga kurkuku fiye da kowa, a shan duka babu misali, a fuskantar haduran mutuwa da yawa.24Daga hannun yahudawa sau biyar na sha bulala "Arba'in ba daya". 25Sau uku na sha dibga da sanduna. Sau daya aka jejjefe ni da duwatsu. Sau uku na yi hadari a jirgin ruwa. Na yi tsawon dare da yini guda a tsakiyar teku. 26Ina shan tafiye tafiye, cikin hadarin koguna, cikin hadarin 'yan fashi, cikin hadari daga mutane na, cikin hadari daga al'ummai, cikin hadarin birni, cikin hadarin jeji, cikin hadarin teku, cikin hadarin 'yan'uwan karya.27Na sami kaina ina aiki tukuru cikin mawuyacin hali, cikin yin dare dayawa ba barci, cikin yunwa da kishin ruwa, cikin yawan azumi, cikin sanyi da tsiraici. 28Baya ga wadannan duka, akwai nauyi a kaina kullayaumin saboda damuwata akan Ikkilisiyoyi duka. 29Waye kumama, wanda ban zama kumama akan shi ba? Wanene aka sa yayi tuntube, kuma ban kuna ba?30Idan zan yi fahariya, zan yi fahariya akan abinda ke nuna kasawata. 31Allah kuma Uba na Ubangijinmu Yesu, wanda ya isa yabo har abada, ya san ba karya nake yi ba!32A Damasku, gwamnan da ke mulki karkashin sarki Aritas yasa aka yi tsaron birnin Damasku domin a kama ni. 33Amma ta taga cikin kwando aka ziraro ni bayan ganuwar birni, na kuwa kucce daga hannunsa.
Bulus ya ciba da amince cewa shi monzo ne.
"ku bar ni inyi wauta"
Waɗannan kalmomi na maganan kyaun sha'awa mai karfi ne da Korontiyawa su yi imani da Almasihu, da cewa kadda a tilisa su su barshi.
Bulus na maganar kiyayer masubi na Korontiyawa kamar ya yi wa wani mutum alkawari cewa zai shirya ɗiyar sa domin ta aure shi kuma ya damu cewa mutmin ya iya rike alkawarin. AT: "I na nan kamar uba da ya yi alkawari don ya gabatar da ɗiyar sa ga miji guda. Na kuma yi alkawari in riƙe ku kamar budurwa mai tsarki domin in miƙa ku ga Almasihu"
"Gama ina fargaba kila tunanin ku na iya kauce ga halaka daga gaskiya da kauna mai sarki zuwa ga Almasihu yadda ibilis ya yaudare hauwa'u da wayon sa"
Bulus ya yi maganan tunani kaman dabbobi ne da mutane ke iya kai wa hanyan halaka. AT: "wani na iya sa ku gaskanta karya"
"in wani ya zo da"
"wani ruhu dabam da ba ruhu mai Tsarki ba ko kuwa wani bishara dabam da ku ka karɓa a wurin mu"
"yi da wanan abubuwa." Duba yadda an fasara wannan kalamar 11:1.
Bulus ya yi amfani da maganan nan domin ya nuna cewa mallaman nan ba su da amfani kaman yanda mutanen na fada. AT: "wanɗancan mallamai da suke tunani sun fi kowa goni"
Wannan zancen da ba daidai ba na nanata kyaun gaskiya cewa ya yi horo a cikin ilimi. "ilimi" magana ce da za a iya bayana. AT: "Haƙika ina horo a cikin ilimi"
Bulus ya fara ɗauka da cewa ya lura da korontiyawa da kyau. Ana iya fasara wannan zancen, in da bukata. AT: "Ina tunani mun yadda cewa ban yi zunubi ta wurin kaskanta da kaina na domin a ɗaukaka ku"
"yi maku wa'azin bisharar Allah ba da niyan samun abu ba"
Wannan karuwan zance ne don ya nanata cewa Bulus ya karɓa kuɗi daga ikilisiyoyin da bai kamata su ba shi ba. AT: "Na karɓa kuɗi daga sauran Ikilisiyoyi"
Ana iya bayyana wannan. AT: "Ina iya yin muku hidima ba don komai ba"
"Ban taba zama maku da nawayan kuɗi ba." Bulus na maganan wani wanda wani zai kashe kuɗi kaman wani nauyi abu ne da mutane ke dauka. Ma'anan wannan na a bayyane. AT: "Na yi abin da zan iya domin in tabatar cewa ba ku kashe kuɗi ba domin in iya zama tare da ku"
Watakila waɗannan "'yan'uawa" maza ne duka.
"Ba zan zama ma ku da nawaya ba"
Bulus na nanatawa cewa saboda masu sauraran sa su fahinci cewa yana fadan gaskiya game da Almasihu. Za su sani cewa yana fadan gaskiya ne. "Tun da kun san da cewa na san gaskiyan kuma ina shelar gaskiyan game da Almasihu, za ku iya sani ko abin da zan faɗa gaskiya ne. Wannan"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. "Ba wanda da zai iya hana ni in yi fahariya har in tsaya shuru.
Wannan na nufin abin da Bulus ya yi magana a 11:7-9.
"yankin Akaya." Kalmar "gaba" na magana wurin kasa, ba rabuwan siyasa ba ne.
Bulus ya yi magana a fakaice don ya nanata kauna ga Korontiyawa. Ana iya hada waɗannan tamboyoyin ko a mai da shi zance. AT: "saboda bana kaunan ku ne ya sa ba na bukatan in nawaita maku?" ko kuwa "zan ci gaba da hana ku biyan bukatu na domin wanan ya nuna wa sauran da cewa ina ƙauna ku."
kuna iya fahimtan sadarwan bayani. AT: " Allah ya sani ina ƙaunar ku."
Bulus ya yi magana akan karya da maƙiyansa sun faɗa ne kamar wani abu ne da ya ɗaukawa. AT: "Domin in iya sa shi mara yiwuwa"
Bayan fahariyan Bulus shine "ya yi wa'azin bishara kyauta" (11:7), abokan gabansa sun yi fahariya cewa su iya yin magana da kyau (11:5).
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "Don mutanen su yi tunanin cewa su nan kaman mu"
" Ina yin abinda na ke yi domin mutane na son su"
"masu aikin rashin gaskiya"
"Ba manzanne ba , ama su na kokari su mai da kansu kaman manzannin"
Da farin wanan a kamanin korou Bulus na nanatawa da cewa Korontiyawa da su shirya saduwa da "monzon karya" masu yawa
"shaidan ba mala'ikan haske ba ne, ama yana kokarin ya mai da kansa kamar mala'ikan haske"
Anan "haske" zance ne na adalci. AT: "mala'ikan haske"
"Bayinsa ba bayin adalci ba ne, ama suna kokarin mai da kansu kamar bayin adalci"
"karbe ni kamar yadda za ku karɓe wawa: Bari in yi magana, ku kuma maida fahariya kalaman wawa"
A nan maganan "jiki" na nufin mutum a cikin sifar zunubi da riɓa sa. AT: "Game da riban mutumtakansu"
"ku karɓe ni in na yi kwoikoyo kaman wawa" Dubi yadda an fasara zance irin wannan a 11:1.
Bulus na kunyatas da Korontiyawa ta wurare dayawa. AT: "Kuna samani cewa kuna da wayo, ama babu"
Bulus ya yi amfani da abubuwa dabam dabam game da yanda wadansu mutane ke tilisa waɗansu su yi biyaya da dokoki kaman su na tilasa su su zama bayi. AT"sa ku ku bi dokoki dan ba daidai ba".
Bulus ya yi maganan game da manyan manzani masu ɗaukan abubuwan mutane kamar suna cin mutanen ne da kansu. AT: "ya dauki dukan malakan ku"
Mutum na amfani da zarafin wani ta wurin sanin abinda wancan bai sani ba da kuma yin amfani da sanin don ya taimake kansa ya kuma jawo ma wacan mutum lahani.
"Na yarda da kunya cewa ba mu iya riƙe ku ba." Bulus yana amfani da magana dabam dabam don ya fada wa Korontiyawa cewa ba don rashin karfin sa ne ya sa ya riƙe su da kyau ba. AT: " Ba na kunya in ce muna da iƙon yin ma ku mugunta ba, ama mun riƙe ku da kyau"
"Ni ma zan yi fahariya da Kowane abinda wani ya yi fahariya"
Bulus ya yi tambayan da Korontiyawa na iya tambay da kuma amsawa domin ya nanata cewa shi dan Yahudawa ne fiye da su manyan-manzanen nan. In ya yiwu ku riƙe tambayan da amsan. AT: "Su na so ku yi tunani cewa suna da amfani kuma ku bada gaskiya akan abinda su ke ce domin su Yahudawa ne da Israilawa daga zuriyar Ibrahim. To, haka nake. Sun ce su bayin Almasihu ne -ina magana kaman ba na cikin hankalina-ama ina fiye"
"kaman bana iya tunani da kyau"
Kuna iya fahimtar da bayanin na sasai. AT: "Ni bawan Almasihu ne fiye da su"
"Na yi aiki tukuru"
"na shiga kurkuku so dayawa"
Wannan karin magana ne, an zuguiguita ta domin a nanata cewa an duke shi so dayawa. AT: "An duke ni so dayawa" ko "An duke so dayawada ya wuce kirge"
"kuma na yi kusan mutuwa so dayawa"
Wannan sanannen magana ne na shan duka sau 39. A dokan Yahudawa ainahin yadda ake yarda a duke mutum a lokaci shi ne tsula arba'in. Sun saba bulalan mutum so talatin da tara domin su zama da laifin bulalan wani so dayawa idan an kirga ba daidai ba.
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "mutane sun dibga ni da sanduna a itace"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "mutane sun jejejefe ni da duwatsu san da sun zata na mutu"
Bulus na nufin ya kwanta a cikin ruwa bayan da jirgin ta nutse.
Ana iya bayana cikaken ma'anan wannan zancen. AT: "A cikin hatsari daga mutanen da su ka dauke mu yan'uwa a Almasihu, ama sun ci amanar mu"
Bulus ya wuce ne domin ya nuna bukatan suturan sa. AT: "rashin ishashen sutura da zai sa ni dumi"
Bulus ya sani cewa Allah zai kama shi da alhakin yadda ikilisiyoyi su na biyayya da Allah ya kuma yi magana akan wancan sanin kaman abu mai nauyi ne da na tura shi kasa. AT"na san cewa Allah zai tambaye ni don girman ruhanian ikilisiyoyin, Ina yawan ji kaman abu mai nauyi na tura ni kasa"
Ana iya fasara afakaice wannan zancen. AT: "Duk lokacin da wani na kumama, ina jin wanan kumaman ni ma."
Ana iya fasara afakaice wannan zancen. Bulus ya yi amfani da tambayan nan don ya nanata fushin sa a lokacin da an sa dan'uwa maibi yin zunubi. AT: "Ina fushi a duk lokacin da wani ya sa ɗan'uwa yin zunubi."
Bulus ya yi magana game da zunubi kaman yana tuɓe akan abu na kuma fadiwa. AT: "aka kai shi ga zunubi" kokuwa "ya yi sam'mani cewa Allah zai yarda ma shi ya yi zunubi domin abinda wani dabam ya aikata."
Bulus ya yi magana akan jin fushi da zunubi kaman yana da wuta a cikin jikin sa. AT: "Ban na fushi akan sa"
"abinda ke nuna kasawa na"
Bulus na nanata cewa gaskiyane yake fada. AT: "Ina fadin ainahin gaskiyan"
"gwamna wanda sarkin Aritas ya zabi ya fadi wa mazajen su yi tsaron garin"
"domin su rike da kuma kama ni"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "waɗansu mutane sun sa ni a kwando suka ziraro ni a kasa"
Bulus ya yi anfani da hanuwan gwamnan domin kwatanci na gwamna. AT: "daga gwamna"
1Dole ne in yi fahariya, ko dashike bata da ribar komai. Amma zan ci gaba da wahayoyi da ruyoyi daga Ubangiji. 2Na san wani mutum cikin Almasihu, wanda shekaru goma sha hudu da suka wuce-ko a cikin jiki ne ko ba a jiki ba, ban sani ba, Allah ya sani-an dauke shi zuwa sama ta uku.3Kuma na san wannan mutumin-ko cikin jiki ko kuma ba cikin jiki ba, ban sani ba, Allah ya sani- 4an dauke shi zuwa Firdausi ya kuma ji madaukakan al'amura wadanda ba mai iya fadi. 5A madadin irin wannan mutumin zan yi fahariya. Amma a madadin kaina ba zan yi fahariya ba, sai dai game da kumamancina.6Idan ina so inyi takama, ba zai zama wauta ba, domin gaskiya zan rika fada. Amma zan guje wa fahariya, domin kada wani ya dauke ni fiye da abinda ya gani ko ya ji daga gare ni. 7Zan kuma gujewa fahariya saboda irin wadannan gagaruman ruyoyi. Domin kada in cika da girman kai, an ba ni kaya cikin jikina, manzon shaidan ya wahalshe ni, domin kada in yi girman kai dayawa.8Na roki Ubangiji har sau uku domin ya kawar mini da wannan. 9Amma ya ce mani, "Alherina isasshe yake a gare ka, domin ta wurin kumamanci karfi yake cika." Don haka zan gwammace takama a akan kasawata, domin ikon Almasihu ya zauna a ciki na. 10Sabili da haka a gamshe nake ta dalilin Almasihu, cikin kumamanci, ko raini, ko matsaloli, ko jarabobi, ko kuma nawaya. Don ko dayaushe na raunana, ina da karfi kuma.11Na zama wawa! Amma ku ne kuka tilasta mani haka, ya kamata ku yabe ni, domin ban kasa ga wadan da ake kira manyan manzanni ba, ko da shike ni ba komai ba ne. 12Cikakkun alamun mazanni sun faru a tsakanin ku, da cikakken hakuri, alamu da abubuwan ban mamaki da manyan ayyuka. 13Ta yaya kuka zama da rashin muhimmanci akan sauran Ikkilisiyoyin, sai dai don ban zama matsala a gare ku ba? Ku gafarce ni a kan wannan laifin.14Duba! A shirye nake domin in zo gare ku karo na uku. Ba zan so in zamar maku nawaya ba, domin ba kayanku nake so ba. Amma ku nake so. Domin ba 'ya'ya ne ya kamata su yi wa iyaye tanadi ba. Amma iyaye ne ya kamata su yi wa 'ya'ya tanadi. 15Zan yi murnar biyan bukatunku, ko ya kai ga in bada rai na. Idan ni na kaunace ku, sosai, sai ni za a kaunata kadan?16Amma kamar yadda yake, ban nawaita maku ba. Amma, da shike ni mai dabara ne, Ni ne na kama ku da yaudara. 17Ko na cutar da ku ta wurin wadanda na turo maku? 18Rokar Titus na yi domin ya zo gare ku, sa'an nan na turo shi da wani dan'uwa. Ko da na turo Titus, ya cutar da ku ne, ba cikin hanya daya muka yi tafiya ba? Ba a sawu daya muka yi tafiya ba?19Kuna tsammanin a dukan wannan lokaci muna kare kan mu a gaban ku ne? A gaban Allah, a cikin Almasihu muke fadin komai domin ku sami karfi.20Ina tsoro domin idan na zo ba zan same ku yadda nake zato ba. Ina tsoro kuma ba za ku same ni kamar yadda ku ke zato ba. Ina tsoron cewa za a sami gardandami, kishi, barkewar fushi, buri na son kai, gulma, girman kai da yamutsi. 21Ina tsoron cewa bayan na dawo, Allahna zai iya kaskantar da ni a gaban ku. Ina tsoron cewa zan yi bakinciki domin mutane dayawa da suka yi zunubi kafin yanzu, wadanda kuma ba su tuba daga rashin tsarki da zina da fasikanci da ayyukan sha'awa da suka aikata ba.
Bulus ya cigaba da fadan abubuwa da suka faru da shi tun da ya zam mai bi, a tsaren manzoncin sa daga Allah.
"zan cigaba da magana, ama ba yanzu ba"
AT: 1) Bulus ya yi amfani da kalmomin "ruyoyi" da "wahayoyi" don nufin abu ɗaya a handiyadiyas domin nanatawa. AT: "abubuwan da Ubangiji ya yarda kadai ni in gani" kokuwa 2) Bulus na magana game da abubuwa biyu dabam. AT: "asirtacen abubuwa da Ubangiji ya yadda mani in gani da idanu na da wasu abubauwan asiri da ya yi mani magana akai"
Bulus na magana ne akansa kaman yana yi ne da wani dabam, in ya yiwu a fasara wannan a bisa kalma.
Bulus ya cigaba da yin bayani game da kansa kaman wannan ya faru ne da wani mutum ne. "Ban sani ko wannan mutum yana cikin wannan jiki ne ko kuma jikin ruhaniya ba"
"Allah ne kadai ya sani"
Wannan na nufin mazaunin Allah ba sama ko sarari ba (duniya, tamraru, da duniya).
Bulus ya chigaba da magana game da kan sa kaman yana maganan wani ne dabam.
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: 1) "Allah ya ɗauke wannan mutum ... cikin firdausi" kokuwa 2) malaika ya ɗauke wannan mutum ... chikin firdausi." In ya yu, bai zai kyautu a bada sunan wanda ya ɗauke mutumin ba: "wani ya ɗauki ... firdausi"kokuwa "sun ɗauki ... firdausi."
ba zato ba tsammani da karfi an kamo an ɗauko
AT: 1) sama ko 2) sammai na uku 3) wuri na musamman a sama.
"na wanan mutum"
Ana iya bayana wannan a cikin kyaun aiki. AT: "zan yi fahariya don raunawa na"
"babu wani da zai ba ni amana fiye da abinda ya gani ko ya ji daga gare ni"
"saboda waɖannan ruyoyi suna fiye da kowane abu da wani ya taɓa gani"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "Allah ya ba ni kaya a cikin jikin" ko kuma "Allah ya barni in sami kaya a cikin jikin"
An kwatanta al'amarin Bulus a bayane kaman kaya da ke huda jiki. AT: "azaba" ko kuma "bayanannan al'amari"
"bawan Shaiɗan"
"su bani azaba"
"girman kai sasai"
A farkon jumla, Bulus ya sa kalmomin nan domin ya nanata cewa yayi addu'a so da yawa domin wannan "ƙaya". (12:7).
"Ubangiji domin wannan ƙayan a cikin jiki," ko kuma " Ubangiji domin wannan wahalan"
"zan yi maka tagomashi, gama abin da ku ke buƙata kenan"
"gama iƙo na ya fi aiki yayin da kuke kumamanci"
Bulus ya yi magana game da iƙon Almasihu kaman rumfa ce da aka gina a kansa. AT: 1) "mutane na iya ganin cewa ina da iƙon Almasihu" ko kuma 2) "Ina iya samu ikon Almasihu."
AT: 1) "a gamshe nake a cikin kumamanci, raini, matsaloli, jarabobi, da kuma mawiyancin yanayi idan wadannan abubuwa sun zo domin ni na Almasihu ne." kokuwa 2) " a gamshe nake cikin kumamanci ... idan wannan abubuwan ya sa mutane su san Almasihu."
"lokacin da ina kumanci"
"lokacin da mutane na kokarin sa ni fushi ta wurin cewan ni mutum ne mara azanci"
"lokacin da ina shan wuya"
"lokacin da akwai husuma"
Bulus na cewa, lokacin da ba shi da karfi sosia domin yin abin da ya kamata, Almasihu, wadda yake da cikakken iko fiye da Bulus, zai yi aiki ta Bulus domin yin abin da ya kamata. Ko da shike, zai fi kyau a fasara kalmomin dalla-dalla, idan yaren ku ta amince.
"Ina yi kaman wawa"
"Kun tilasta mani in yi magana a haka"
Ana iya bayana waanan a cikin sifar aiki. AT: "ya kamata da yabo ne kun bani"
AT: 1) "yabo" (3:1) kokuwa 2) "shaida" (4:1).
Ta wurin anfani da wata hanya, Bulus yana fada da karfi cewa Korantiyawa da su ke tunani cewa bai isa ba sun yi kuskure. AT: "gama ina da kyau kaman"
Bulus ya yi amfani da maganan nan domin ya nuna cewa mallaman nan ba su da mahimmanci kaman yadda mutane na fadɖa. Dubi yadda wannan an yi fasarar sa a 11:5.AT: "mallaman nan da waɗansu ke tunani cewa sun fi kowa"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki, a kan "alamun." AT: "alamun gaskiya ne ina yi"
yi amfani da kalman a lokaci daya.
Waɗannan su ne "alamun gaskiya na manzo" da Bulus ya yi "da cikaken hakuri"
Bulus na nanata cewa Korontiyawa sun yi kuskure ta wurin zargin shi cewa ya na so ya yi masu lahani. Ana iya fasara zancen atacaike. AT: "Na yi muku kamar yadda na yi wa sauran iklisiyoyi, sai dai ... ku."
"Ban roƙe ku kuɗi ko sauran abubuwa da na ke buƙ ata ba"
Bulus ya yi zance haka ne domin ya kunyatar da Korontiyawa.Shi da su duk sun sani cewa bai yi masu laifi ba, amma suna yi ta masa kaman wadda ya yi masu laifi su.
rashin tambayan su kuɗi da kuma sauran abin da ya ke buƙata
Cikakken ma'anar wannan na a bayyayane. AT: "Abinda nake so shine ku ƙaunace ni ku kuma karɓe ni"
Ba raganar 'ya'ya ne su tara kudi ko wasu abubuwa domin su ba wa lafiyayun iyayen su ba.
Bulus na maganan aikin sa da kuma rayuwar sa kamar kudin ne da shi ko Allah na iya kashewa. AT: "Zan yi ko wace aiki da murna, da kuma murna in yadda Allah ya amince wa mutane su kashe ni"
Kalmar "rayukanku" na matsayin mutane da kan su. AT: "sabili da ku" ko kuma "domin ku zauna lafiya"
Ana iya fasara wannan maganan kaman zance. AT: "idan ina ƙaunan ku sosai, kadda ku ƙaunace ni kadan." ko kuwa "idan ... sosai, ku ƙaunace ni fiye da ku ke yi."
Ba a bayyane ya ke ba cewa kaunar Bulus yana nan "sosai" fiye. Zai fi kyau idan an yi amfani da "mai yawa" ko kuwa "da yawa" za a iya kamantawa da "kankani" a maganan.
Bulus ya yi amfani da wannan zance domin ya kunyatar da Korontiyawa da suke tunani ya yi masu kariya ko da shike bai roƙe su kuɗi ba. AT: "Amma waɗansu na tunanin na yaudaresu kuma na yi amfani da dabara"
Bulus da Korontiyawa sun san amsan kariya ce. Ana iya fasarar wannan maganan kaman zance.AT: "Babu wani da na aiko wurin ku da ya zalunce ku!" )
Bulus da Korontiyawan su san cewa ansar a'a ne. Ana iya fasara wannan magana kaman zance. AT: "Titus bai zalunce ku ba."
Bulus na maganan rayuwa kaman tafiya a kan hanya.Bulus da Korontiyawa sun san amsan tambayan gaskiya ne. Ana iya fasra wannan magana kaman zance. AT: "Dukan mu muna da irin hali iri daya kuma muna rayuwa iri daya."
Bulus ya yi maganan rayuwa kaman tafiya a kan hanya.Bulus da Korontiyawa sun san amsan tambayan i ne. Ana iya fasara wannan magananar kamar zance. AT: "Mu na yin abu iri ɗaya."
Bulus ya yi amfani da wannan tambayan domin ya nuna wani abu da mutanen ke ta tunani. Ya yi wannan domin ya tabatar masu cewa ba gaskiya bane. AT: "watakila kuna tunani dukkan wannan lokaci da cewa muna kare kanmu daga gare ku n."
Bulus yayi magana game da sanin komai na Allah da Bulus ya ke yi kaman Allah na nan a bayyane kuma ya na duban komai da Bulus ya ke faɗa da kuma aikata. AT: "A gaban Allah" ko koma "Da Allah mai shaida" ko kuma "A gaban Allah"
"Don karfafa ku." Bulus yayi maganan sanin yadda za'a bi Allah da kuma marmarin binsa kaman girma ta jiki ne. AT: "Saboda ku san Allah ku kuma yi bi shi da kyau"
"ba zan so abinda na samu ba" ko kuma "ba zan so abin da na gan ku na yi ba"
"ba za ku so abin da kun gani a kai na ba"
kwatancin gardandami, kishi, barkewar fushi, buri na son kai, gulma, girman kai da yamutsi" ana iya fasara su ta yanyer ayuka. AT: 1) "waɗansun ku za su yi gardama da mu, su ji kishin mu, nan da nan su yi fushi da mu, yin magana game da rayuwan mu na girman kai, da kuma jayayya da mu yayin da muke kokarin jagorantar ku" kokuwa 2) "wadan sun ku za su yi gardama da juna, suna maganar tsirin rayuwar juna, da girman kai, da kuma jayayya da waɗanda Allah ya zabe su yi jagora"
"zan yi bakin ciki domin yawancin su ba su bar tsoƒoƒin zunuban su ba"
AT: 1) Bulus na fadin kusan abu daya son uku domin nanatawa. AT: "Ba su bar aikata zunubin zina da suke yi ba" ko kuwa 2) Bulus na maganan zunubai kashi uku.
Anan iya bayana kalman tsarki kaman "abubuwan da ba su gamshi Allah ba." AT: "na yin tunani a tsirance game da sha'awan abubuwan da ba za su gamshi Allah ba"
Maganan "fasikanci" ana iya fasara ta kaman "ayuka mara kyau." AT: "na yin ayukan zina da fasikanci"
Ana iya fasara Kwatancin "aikata" ta wata kalma. AT: "na ... yin abubuwan da ze sa jin dadin fasikanci"
1Wannan ne karo na uku da nake zuwa gare ku, "Ana tabbatar da kowanne zargi ta bakin shaidu biyu ko uku." 2Na riga na yi magana a baya da wadanda suka yi zunubi da kuma sauran a lokacin da ina tare da ku karo na biyu, kuma ina sake fadi: Idan na sake zuwa, ba zan raga masu ba.3Ina fadi maku wannan ne domin kuna neman shaida ko Almasihu na magana ta bakina. Shi ba kasashshe bane zuwa gare ku. Maimakon haka, Shi mai iko ne a cikin ku. 4Domin an gicciye shi cikin kasawa, amma yana da rai ta ikon Allah. Don mu ma kasassu ne a cikin shi, amma za mu rayu tare da shi cikin ikon Allah dake cikinku.5Ku auna kanku ku gani ko kuna cikin bangaskiya. Ku yi wa kanku gwaji. Ba ku lura da cewa Yesu Almasihu yana cikin ku ba? Yana cikin ku, sai dai in ba a amince da ku ba. 6Gama ina da gabagadin cewa za ku iske an amince da mu.7Ina addu'a ga Allah cewa ba za a same ku da laifi ba. Ba wai ina rokon mu bayyana kamar mun ci gwadawar ba. Maimakon haka, ina addu'a ku yi abinda ke dai dai, ko dayake mun yi kamar mun fadi gwadawar. 8Domin bamu iya yin wani abu na tsayayya da gaskiya ba, sai dai mu yi domin gaskiya.9Muna farin ciki idan mun kasa ku kuma kun yi karfi. Muna addu'a kuma domin ku kammalu. 10Na rubuta wadannan abubuwa yayinda ba ni tare da ku, saboda yayin da zan kasance da ku ba zan zamar maku mai fada ba. Ba na so inyi amfani da ikon da Ubangiji ya bani in tsattsaga ku, sai dai in gina ku.11A karshe, 'yan'uwa, ku yi farinciki, ku yi aiki don sabuntuwa, ku karfafa, ku yarda da juna, ku zauna cikin salama. Kuma Allahn kauna da salama zai kasance tare da ku. 12Ku gai da juna da tsattsarkar sumba.13Masu bi duka suna gaishe ku. 14Bari alherin Ubangiji Yesu Almasihu, da kaunar Allah, da zumuntar Ruhu Mai Tsarki su kasance tare da ku duka.
Bulus ya shinfida da cewa Almasihu na magana ta wurin sa, da kuma cewa Bulus yana son ya tsada su, ya karfafa su da kuma sa su yi zamantakewa.
Ana iya iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "Ku gaskanta cewa wani ya yi abu mummuna bayan mutum biyu ko uku sun fada abu iri ɗaya"
"ya ku dukkan sauran mutane"
Ana iya sa wannan a aiki. AT: "sun gicciye shi"
Allah ya ba mu iƙo da hikimar don mu yi rayuwa a ciki da kuma tare da shi.
Bulus ya yi tambaya domin ya nanata zancen sa AT: " ku san cewa Yesu Almasihu yana cikin ku" ko kuma "Yesu Almasihu yana cikin ku. Ya kamata kun riga kun sani!"
AT: 1) rayuwa a cikin kowane mutum 2) "tsakani ku," sakani da muhimmin mutum na kungiya.
"cewa ba za kuyi zunubi ko kadan" ko kuma" cewa ba za ku ki jin mu a lokacin da muke kwaɓe ku ba." Bulus yana nanata bambam zancen sa. AT "cewa za ku yi dukkan kamai daidai"
"zama kwararan mallamai da yin rayuwan gaskiya"
"bamu iya yin abun da ze hana mutane koyan gaskiya ba"
"gaskiya; dukkan abun da muke yi zai sa mutane su koyi gaskiyar"
"domin ku yi girma a cikin ruhania"
"idan na yi amfani da iƙo na"
Bulus ya yi maganan taimaka wa Korontiyawa don su san Almasihu da kyau kaman yana aikin gini. Dubi yanda an fasara irin wannan magana a 10:8 AT: " domin a taimake ku ku zama ainahin mabiyan Almasihu ba a sa ku fit da rai don ku daina binsa ba."
"yi aikin kaiwa ga girma"
"yi rayuwar jituwa da junna"
"da ƙauna ta Masubi"
" waɗanda Allah ya kabe wa kansa"
1Wannan Bulus manzo ne. Manzancina kuwa, bai zo daga mutane ba ko mutum, amma ta wurin Yesu Almasihu da Allah Uba wanda da ya tashe shi daga matattu. 2Ni da dukan 'yan'uwa da nake tare da su a nan, ina rubuto maku ku iklisiyoyi da ke a Galatiya.3Alheri zuwa gare ku da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangjinmu Yesu Almasihu, 4wanda ya ba da kansa domin zunubanmu saboda ya kubutar da mu daga wannan mugun zamani, bisa ga nufin Allah da Ubanmu. 5Daukaka ta tabbata a gare shi har abada abadin.6Na yi mamaki kwarai yadda kuka juya da sauri zuwa wata bishara daban. Na yi mamakin cewa kuna juyawa daga shi wanda ya kira ku ta wurin alherin Almasihu. 7Ba wata bishara, amma akwai wadansu mutane da suke kawo maku rudani kuma suna so su gurbata bisharar Almasihu.8Amma, ko da mu ne ko mala'ika daga sama ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda muka yi shelar ta, la'ananne ne. 9Kamar yadda muka fadi maku a da, yanzu kuma ina sake fada, "Idan wani ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda kuka karba, la'ananne ne." 10To yanzu ina neman shaidar mutane ne ko Allah? Ina neman in gamshi mutane ne? Idan har yanzu ina kokarin in gamshi mutane ne, ni ba bawan Almasihu ba ne.11Ina son ku sani fa 'yan'uwa, cewa bisharar da nake shelar ta ba daga mutane take ba. 12Ban karbe ta daga mutum ba, ba ma wanda ya koyar mani A maimakon haka, ta wurin wahayin Yesu Almasihu ne zuwa gare ni.13Kun riga kun ji game da rayuwa ta a da cikin Yahudanci, yadda da nake da kwazon tsananta wa iklisiyar Allah fiye da misali kuma ina lalatar da ita. 14Ina gaba-gaba cikin Yahudanci fiye da yawancin tsararrakina. A kwazo kuwa fiye da kima game da al'adun ubannina.15Amma ya gamshi Allah ya zabe ni daga cikin mahaifiyata. Ya kira ni ta wurin alherinsa. 16Ya bayyana dansa a gareni, saboda in yi shelar sa cikin al'ummai. Nan da nan, ban nemi shawarar nama da jini ba 17kuma ban tafi Urushalima ba wurin wadanda suka zama manzanni kafin ni. Maimakon haka sai na tafi Arebiya, daga nan sai na dawo Dimashku.18Bayan shekara uku na je Urushalima don in san Kefas, na zauna da shi na kwana goma sha biyar. 19Amma ban ga ko daya daga cikin manzannin ba sai Yakubu kadai, dan'uwan Ubangiji. 20Duba, a gaban Allah, ba karya nake yi ba cikin abin da na rubuta maku.21Daga nan sai na je lardin Suriya da Kilikiya. 22Har a lokacin babu wanda ya san ni a fuska a iklisiyoyin Yahudiya da suke cikin Almasihu, 23amma sai labari kawai suke ji, "Wanda a da yake tsananta mana yanzu yana shelar bangaskiyar da a da yake rusarwa." 24Suna ta daukaka Allah saboda ni.
Bulus, wani manzo ya rubuta wannan wasika zuwa ga ikkilisiyu da ke yankin Galatiya.
"wanda ya sa shi ya rayu kuma"
Nan, wannan na nufin 'yan'uwanmu Krista maza da mata, tunda shike a cikin Kristi duk masubi 'yan iyali daya ne a ruhaniya, kamar yadda Allah shi ne Ubansu na samaniya. AT: "ɗan'uwa da yar'uwa"
"Zunubai" na iya ba da ra'ayi cewa hukuncin zunubi. AT: "ɗaukar hukunci da ya cancanci zunuban mu"
A nan "wannan ... zamani" na bayana iƙokin da ke aiki a cikin zamanin. AT: "domin ya kawo mu ga kariya daga mugayen iƙoki da ke aiki a cikin duniya ta yau"
Wannan yana nufin "Allah Ubanmu". Shi ne Allahnmu da Ubanmu.
Bulus ya ba da dalilin rubuta wannan wasika: yana tunashe su cewa su ci gaba da fahimtar bishara.
" Na yi mamaki" ko kuma "Na gigice." Bulus ya ji kunyan abin da su ke yi.
A nan "juyawa...daga gareshi" na siffanta fara shakka ko kuma rashin dogara ga Allah. AT: "kuka fara saurin shakkan sa"
"Allah, wanda ya kira ku"
A nan wannan na nufin Allah ya nada ko kuma ya zabi mutane su zama yayansa, su bauta masa, da kuma shela kalmarsa na ceto ta wurin Yesu.
"saboda Alherin Almasihu" ko kuma "saboda hadayan alherin Almasihu"
A nan "juyawa zuwa" na siffanta fara gaskanta ga wani abu. AT: "kun kuma fara gaskanta wata bishara daban"
"wasu mutane"
Wannan na bayana abin da bai faru ba kuma ka da ya faru. AT: "da shela" ko kuma "zai shela"
"daban daga bishara" or "daban daga sakon"
"Allah ya hukuta wannan mutumin har abada. "idan akwai yadda aka saba la'ance wani a harshen Hausa, za a iya mora anan.
Waɗannan tambayoyi a takaice na buƙatar amsan "a'a." AT: "bana neman shaidar mutane, amma ina bidar shaidar Allah. Bana neman in gamshi mutane?."
kalmomin nan "idan" da kuma "to" na nuna abin da ba gaskiya ba. "har yanzu bana kokari in gamshi mutane; Ni bawan Almasihu ne" ko kuma "Idan har yanzu ina kokarin gamshi mutane, to ba zan zama bawan Almasihu ba"
Yin amfani da wannan kalmar bai nuna wai Bulus na kokarin cewa Yesu Almasihu da kansa ba mutum bane. Domin Almasihu mutum ne kuma Allah me, duk da haka shi ba mutum mai zunubi bane. Bulus na rubutu game da inda bishara ta fito; da cewa ba daga wasu mutane masu zunubi bane, amma daga Yesu Almasihu.
Zai yiwu ana nufin 1) "Yesu Almasihu da kanshi ne ya bani wahayin bishara" ko kuma 2) "Allah ya sa mun sannin bishara lokacin da ya nuna mun ko wanene Yesu Almasihu."
"hali a wata lokaci" ko kuma "rayuwa kafin yanzu" ko kuma "farkon rayuwa"
Wannan wuri na bada hutun Bulus ya kasance a gaba da Yahudawa da suka tsaran shi wanda suke da manufan zama cikakkun Yahudawa.
"Yahudawa da suke tsara ɗaya da ni
"kakanina"
Zai yiwu ana nufin 1) "Allah ya kira ni in bauta masa domin alherensa" ko kuma 2) "Ya kira ni ta hayar alherinsa."
Zai yiwu ana nufin 1) "bani damar sannin Ɗan sa ko kuma 2) nuna wa duniya ta wurina cewa Yesu Ɗan Allah ne."
Wannan muhimmin lakabi ne na Yesu, Ɗan Allah.
"shelar cewa shi Ɗan Allah ne" ko kuma "wa'azin bishara game da Ɗan Allah"
Wannan furci ne da ke nufin magana da waɗansu. AT: "tambayar mutane su taya ni fahimtar sakon"
"tafi Urushalima." Urushalima na yakin tudai masu tsawo, ya zama wajibi ne a hau tudai da yawa domin a iya isa, shi yasa an saba bayyana tafiya zuwa Urushalima kamar " hauwa zuwa Urushalima."
Wannan musu da ke da baki biyu na haddada cewa Yakubu ne kadai manzon da Bulus ya gani. AT: "manzon da na iya gani kawai shi ne Yakubu"
Bulus na son Galatiyawa su gane cewa ba karya yake yi ba, kuma ya san cewa Allah na jin abin da ya faɗi kuma zai hukunta shi idan bai faɗi gaskiya ba.
Bulus yayi amfani da irin kalmonin nan domin ya nanata cewa abin da yake faɗi gaskiyace. AT: "ba karya na ke yi maku ba a sakon da na rubuta ma ku" ko kuma "game da abubuwan da na rubuta ma ku gaskiya ne na ke faɗi"
"sashin duniya da ake kira"
"amma sun san iyakan abin da suka ji wasu na faɗa game da ni"
"cikin mutane ikilisiyun Yahudiya da suke cikin Almasihu babu wanda ya taɓa saduwa da ni"
1Daga nan, bayan shekara goma sha hudu na koma Urushalima tare da Barnaba. Na kuma dauki Titus tare da ni. 2Na koma ne domin Allah ya nuna mani in koma. Sai na gabatar masu shelar bisharan da nake yi a cikin al'ummai. (Amma a kebe na yi magana da wadanda aka dauka muhimman shugabanni). Na yi haka ne domin in tabbatar da cewa ba gudun banza nake yi ba, ko kuma na yi gudun banza.3Amma ko Titus wanda yake tare da ni, Baheline, ba wanda ya tilasta masa ya yi kaciya. 4Wannan maganar ta taso ne daga 'yan'uwan karya da suka zo cikinmu a boye su ga 'yancin mu a cikin Yesu Almsihu. Sun yi marmarin su maishe mu bayi ga doka. 5Ba mu mika kanmu biyayya gare su ba ko da na sa'a daya, domin gaskiyar bishara ta kasance babu canzawa domin ku.6Amma su wadanda a ke ganin su da muhimmanci ba su taimaka mani da komai ba. Ko su wanene su bai dame ni ba. Allah ba ya karbar wanda mutane suka fi so. 7Maimakon haka, suka ga an danka mani shelar bishara ga wadanda ba su da kaciya. Kamar yadda aka ba Bitrus shelar bishara ga masu kaciya. 8Gama Allah wanda yake yin aiki a cikin Bitrus domin manzanci zuwa ga masu kaciya, haka kuma yake aiki ciki na zuwa ga al'ummai.9Da Yakubu, Kefas, da Yahaya, wadanda a ke gani masu gina ikilisiya, suka fahimci alherin da aka ba ni, suka bamu hannun dama na zumunci ni da Barnaba, Sun yi haka ne kawai domin mu mu tafi zuwa wurin al'ummai, su kuma su je wurin masu kaciya. 10Suna kuma so mu tuna da matalauta. Ni ma ina da aniyar yin haka.11Da Kefas ya kai Antakiya, na yi tsayayya da shi a gabansa domin shine ke da kuskure. 12Da ma Kefas yana cin abinci tare da al'ummai kafin zuwan wasu mutane daga wurin Yakubu. Amma da wadannan mutane suka iso, sai ya dena kuma ya ware kansa daga al'umman. Yana jin tsoron wadannan mutanen da ke bukatar kaciya.13Hakannan ma sauran Yahudawa da suke tare da shi sun bi munafurcin sa. A sakamakon haka Barnaba ma ya bi munafurcin su. 14Da na ga basu bin gaskiyar da take cikin bisharar, na gaya wa Kefas a gaban su duka, "Idan kai Bayahude ne kana rayuwar ka ta al'ummai a maimakon rayuwar Yahudawa, to ta yaya za ka tilasta wa al'ummai su yi zaman Yahudawa?"15Mu da muke Yahudawa daga haihuwa, ba "Al'ummai masu zunubi ba." 16Ku sani fa, babu wanda za a baratar ta ayyukan shari'a. A maimakon haka an baratar da su ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu. Mun zo ga cikin Almasihu Yesu domin mu samu baratarwa ta bangaskiya cikin Almasihu, kuma ba ta ayyukan shari'a ba. Domin ta ayyukan shari'a babu wanda zai samu baratarwa.17Amma idan mun nemi Allah ya baratar da mu cikin Almasihu, mun samu kanmu masu zunubi kenan, Almasihu ya zama bawan zunubi ne? Ko kadan! 18Idan na sake gina dogara ta a kan shari'a, dogarar da na juya wa baya, na nuna kai na mai karya shari'a kenan. 19Ta wurin shari'a na mutu ga shari'a, domin in yi rayuwa irin ta Allah.20An giciye ni tare da Almasihu, ba nine ke rayuwa ba kuma, amma Almasihu ke rayuwa a cikina. Rayuwar da nake yi a yanzu a cikin jiki, ina yin ta ne, ta wurin bangaskiya ga dan Allah, wanda ya kaunace ni ya ba da kansa domina. 21Ban yi watsi da alherin Allah ba, domin idan adalci ya wanzu ta wurin shari'a, ashe Almasihu ya mutu a banza kenan.
Bulus ya cigaba da bayas da tarihin yada ya koyi bishara daga Allah ba manzane ba.
"tafiya." Urushalima wuri ne mai tudai a kasan. Yahudawa kuma suna ganin Urushalima wuri ne a kasa da yafi kusa da sama, zai yiwu Bulus na bada misali ne, ko kuma bada huton wuyan hauwa tudu, a tafiya don a isa Urushalima.
" mafi muhimmancin shugabanni a cikin masubi"
Bulus yayi amfani da kalmar gudu a manufar aiki, kuma ya yi amfani da kalmar musu mai baki biyu domin ya nanata cewa aikin da ya yi na da riɓa. AT: "Na dinga yi, ko kuma da na yi, aikin riɓa ce"
"da ba amfani" ko kuma "ba na kome ba"
za a iya bayyana wannan a ... AT: "a sami wani ya masa kaciya"
"mutanen da suke yaudaran kansu wai su masubi ne su ka shi go Iklisiya", ko kuma "mutane da suke yaudaran kansu wai su masubi ne sun zo cikin mu"
duban mutane a boye don a ga yadda suke zaman 'yanci
'yanci
"Waɗannan masu duba a boye sun yi marmarin" ko kuma "waɗannan 'yan'uwan karya na son"
" a maishe bayi ga doka." Bulus na magana game da tilasawa ga bin al'adun yahudanci da doka ya umurta. Ya na magana game da wannan kamar bauta. al'adan da ya fi muhimminci shi ne kaciya. "tilastamu mu yi biyyaya da doka"
"biyyaya" ko kuma "saurara"
kalmar "ni" anan na bayyani abin da Bulus ke koyaswa. AT: "bai kara komai ba a abin da na koyas" ko kuma "bai gaya mun in kara wani abu ba a abin da na koyas"
"maimako" ko kuma "gwamma"
za iya ambatan wannan cikin aiki, AT: "Allah ya ɗanka mani"
Su mutane ne wanda suka koyas game da Yesu kuma suka tabbatar da mutane su gaskanta cikin Jesus.
za a iya fasara wannan kalmar "Alheri" a kalmar aikatau "yin kirki." AT: "fahimci cewa Allah ya yi mani kirki"
za a iya ambacin wannan cikin aiki. AT: "Alherin da Allah ya ba ni"
riƙe hannun dama kankan alamar zumunci ne. AT: "marabta ...kamar abokan aiki" ko kuma "marabta ...da daraja"
"hannun damar su"
Zai iya buƙace ka bayyana abin da zai tuna game da matalauta. AT: "tuna a lura da bukatun matalauta"
kalmomin nan "a fuskar sa" na bada ra'ayin "wurin da zai iya gani ya kuma ji shi." AT: "Na fuskance shi da kanshi" ko kuma "Na yi tsayaya da ayyukan sa da kaina"
ɗangane da lokaci
"ya dena ci tare da su"
za a iya bayyana dalilin da ya sa Kefas ya ji tsoro haka. AT: "Yana tsoron cewa waɗannan mutane da suke buƙatan kaciya za su sha'ranta shi da yin abin da ba daidai ba" ko kuma " Yana tsoron waɗannan mutane da suke buƙatar kaciya za su bashi laifi domin abubuwan da ya ke yi ba daidai ba" Dubi:
Yahudawan da suka zama masu bi, amma su na buƙatan waɗanda su ka ba da gaskiya cikin Almasihu su yi zama bisa ga al'adun Yahudawa
"zauna baya daga" ko kuma "ƙauce wa"
Anan aka "ciwo" na bayyana rinjaya a yin abin da ba daidai ba. Ana iya bayyana wannan kalmar "ciwo" cikin aiki. AT: "Har Barnaba ya yi kamar su a yin abin da ba daidai ba"
"ba sa rayuwa kamar mutanen da suka gaskanta da bishara" ko kuma "suna rayuwa kamar ba su gaskanta da bishara ba"
Wannan tambaya ne da baya buƙatar amsa tsautawa ne kuma za a iya fassara kamar sanarwa. kalman "ka" na nufin Bitrus. AT: " ba ka yi daidai ba da tilasta Al'ummai su yi rayuwa kamar Yahudawa."
Ya ka iya nufin 1) tilasta ta wurin amfani da kalmomi ko kuma 2) rinjayi.
"ba waɗanda Yahudawa su ke kiran su Al'ummai masu zunubi ba"
"mun gaskanta cikin Almasihu Yesu"
Wannan na nufin mai yiwuwa Bulus ne da wasu amma ba Galatiyawa ba, wanda su da farko Al'ummai ne Dubi:
Kalman "ɗan adam" na nufin gabadayan mutum. AT: "ba mutum"
kalman "baratawa cikin Almasihu" na nufin baratawa domin muna tare da Almasihu aka barata da mu ta dalilin Almasihu.
Kalmomin "an tarar da" na nanata cewa "mu na" lalle ne da zunubi. AT: "mun ga cewa mu ma lallai musa zunubi ne"
"i mana, wannan ba gaskiya ba!" Wannan magana na ba da karfin musun amsa ga tambaya da aka riga yi "Almasihu ya zama bawar zunubi ne? za ku iya amfani da yadda ake yin irin wannan magana a harsha da ku ke amfani da ita.
Wannan lakabi ne mai muhimmanci na Yesu.
Bulus ya ambata kalmar musu domin ya nanata gaskiyar. AT: "Na tabbatar da darajan"
Bulus na bayyana yanayin da bai taɓa faruwa ba.
"inda mutane za su iya zama adalai ta wurin biyyaya da shari'a"
"ashe da Almasihu bai cika komai ba tawurin mutuwa"
1Ku Galatiyawa marasa wayo! Wanne mugun ido ya cuce ku? Ashe, ba Yesu Almasihu gicciyayye aka nuna a gaban idon ku ba? 2Ina so in gane wannan daga wurin ku ne kawai. Kun karbi Ruhun ta wurin ayyukan doka ne ko ta wurin ba da gaskiya ga abin da kuka ji? 3Rashin wayonku ya yi yawa haka ne? Kun fara da Ruhu, sai kuma yanzu ku karasa a cikin jiki?4Kun fuskanci abubuwa da yawa a banza ne - har idan a banza ne? 5To, shi wanda ya ba ku Ruhun, da ayyuka masu iko a tsakanin ku, ya yi ne ta wurin ayyukan shari'a ko ta wurin ji tare da bangaskiya?6Ibrahim "ya ba da gaskiya ga Allah, kuma an lisafta mashi wannan a matsayin adalci." 7Ta wannan hanya ku fahimta su wadanda suka ba da gaskiya, 'ya'yan Ibrahim ne. 8Nassi ya riga ya hangi gaba cewa, ta wurin bangaskiya Allah zai baratar da Al'ummai. An yi wa Ibrahim shelar bishara tuntuni: "A cikinka ne dukan al'ummai za su yi albarka." 9Saboda haka, wadanda suka ba da gaskiya, masu albarka ne tare da Ibrahim wanda ke da bangaskiya.10La'ana na kan wadanda sun dangana ga ayyukan shari'a. Gama a rubuce yake, "La'ananne ne kowanne mutum da bai tsaya ga duk abin da ke a rubuce cikin littafin shari'a ba, ya kuma aikata shi duka."' 11Yanzu a sarari yake, Allah ba ya baratar da kowa ta wurin shari'a, domin "Mai adalci zai rayu ta bangaskiya." 12Doka ba daga bangaskiya take ba, 'Amma a maimakon haka, "Shi wanda ke yin wadannan abubuwa cikin shari'a, zai yi rayuwa ta wurin shari'a."13Almasihu ya fanshe mu daga la'anar shari'a da ya zama la'ananne saboda mu. Kamar yadda yake a rubuce, "La'ananne ne duk wanda aka sargafe a bisa itace." 14Dalilin shine, albarkan da ke bisan Ibrahim ta zo ga al'ummai cikin Almasihu Yesu, domin mu samu karban alkawarin Ruhu ta wurin bangaskiya.15'Yan'uwa, ina magana bisa ga ka'idojin mutane. Idan mutane sun yi yarjejeniya, babu mai kawar da shi ko a kara shi. 16Yanzu fa, an fada alkawaran nan ne ga Ibrahim da zuriyarsa. Bai ce, "ga zuriya ba" da manufar masu yawa; amma a maimakon haka ga daya kadai, "ga zuriyar ka," wanda shine Almasihu.17Yanzu na fadi wannan. Shari'a, wadda ta zo shekaru 430 daga baya, ba ta kawar da alkawarin da Allah ya tabbatar da shi ba tun a baya. 18Domin idan da gadon ya zo ta dalilin shari'a ne, da ba za ya zo kuma ta dalilin alkawari ba. Amma Allah ya ba da shi ga Ibrahim kyauta ta wurin alkawari.19Me ya sa kenan aka ba da shari'a? An kara ta ne saboda laifuffuka, har sai zuriyar Ibrahim din nan ta zo ga wadanda aka yi masu alkawarinta. An kaddamar da ikon shari'ar ta wurin mala'iku, ta hannun matsakaici. 20Yanzu dai matsakanci yana nufin mutum fiye da daya, duk da haka Allah daya ne.21Shari'a tana tsayayya da alkawaran Allah kenan? Ko kadan! Domin idan da an ba da shari'a da ke iya bayar da rai, babu shakka da adalci ya zo ta wurin wannan shari'a. 22A maimakon haka, nassi ya kulle abubuwa duka a karkashin zunubi. Allah ya yi wannan domin alkawarin sa na ceton mu ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu ya samu a ba da shi ga wadanda suka gaskanta.23Amma kafin bangaskiya cikin Almasihu ta zo, an kulle mu kuma aka tsare mu da shari'a har zuwa ga wahayin bangaskiya. 24Daga nan shari'a ta zama mana jagora har sai da Almasihu ya zo, domin mu samu baratarwa ta wurin bangaskiya. 25Yanzu da bangaskiya ta zo, ba mu kuma a karkashin jagora. 26Domin dukanku 'ya'yan Allah ne ta wurin bangaskiya cikin Almasihu Yesu.27Dukanku da aka yi wa baftisma cikin Almasihu, kun suturce kanku da Almasihu. 28Babu Bayahude ko Baheline, bawa ko 'yantacce, babu na miji ko mace, domin dukanku daya ne cikin Almasihu Yesu. 29Idan ku na Almasihu ne, ku zuriyar Ibrahim ne kenan, magada bisa ga alkawarin.
Bulus ya tunashe masu bi a Galatiya da cewa Allah ya basu Ruhun sa a lokacin da suka gaskanta da bishara ta wurin bangaskiya, ba ta wurin aikata shari'ar Allah ba.
Bulus na tsauta wa Galatiyawa ta wurin tambayoyi da suke kamar sanarwa ba su bukatan amsa.
Bulus na amfani da habaici da tambaya da baya bukatan amshi cewa Galatiyawa suna ayuka kamar wani ya sa ma su sihiri. Ba wai ya gaskata wani ya sa ma su sihiri ba ne. AT: "kuna hali kamar wani ya sa ma ku sihiri!"
"ya yi mu ku tsafi" ko kuma "an yi mu ku maita"
Bulus na magana game da sararin koyaswarsa game da Yesu gicciyeyye kamar ya sa hoton kasancewar Yesu a giciye ga jama'a. ya kuma yi magana game da Galatiyawa da su ka ji koyarwar sa kamar sun ga hoton. AT: "ku da kanku kuka ji koyarwar sarai game da kasancewar Yesu a giciye"
Wannan ya cigaba the magana a habaici da ke aya 1. Bulus ya san amsan tambayoyin da ya ke so ya yi.
Fassara wannan tambaya a matsayin tambaya in za ku iya, domin mai karatun za yi tsammanin tambaya ne anan. Kuma, ka tabbata wai mai karatu ya san amsan tambayan nan cewa 'ta wurin gaskatan abin da ka ji," ba "ta wurin yin abin da shari'a ta ce." AT: "kun sami Ruhu, ba ta wurin aikata abin da shari'a ta ce ba, amma ta wurin gaskata abin da kun ji."
Wannan tambaya na nuna cewa Bulus na mamaki kuma har yayi fushi da rashin wayon Galatiyawa. AT: "kuna da wauta sosai!"
kalman "jiki" na ba da ra'ayin kokari. AT: "ta wurin kokarin ku" ko kuma "ta wurin aikin ku"
Bulus na amfani da tambaya ya tunashe Galatiyawa da cewa lokacin da suke wahala, sun gaskata cewa za su sami wasu amfani. AT: "Haƙika ba ku yi tsammanin cewa kuna shan wahalan abubuwa dayawa a banza ba ne ...! ko kuma "Haƙika kun sanni cewa akwai wasu kyawawan shiri domin wahalar abubuwa da yawa ..."
za a iya bayyana a fili cewa sun fuskace wahalar wannan abubuyan domin mutane da suke adawan bangaskiyar su cikin Almasihu. AT: " a banza ne kuka fuskace wahalar abubuwa dayawa daga ma su yi mu ku adawan bangaskiyar ku cikin Almasihu" ko kuma "Kun gaskata cikin Almasihu, da kuma wahalar abubuwa dayawa da kuka sha daga wanda suke adawan Almasihu. Kasancewar bangaskiya da wahalar ku a banza ne"
"mara amfani" ko kuma "ba tare da begen samun wani abu mai kyau ba"
Zai yiwu a nufin 1) Bulus na amfani da wannan irin tambaya ya gargade su kar su bari kwarewansu ya zama a banza. AT: "Kada ku bari ta zama a banza!" ko kuma "Ka da ku daina gaskata cikin Yesu Almasihu kuma barin wahalar ku ta zama a banza." AT: "haƙika ba a banza ba ne!"
Bulus ya tambaya wani tambaya ya tunashe Galatiwaya yada mutane ke samun Ruhu. AT: "Ya ... yi ba ta wurin aikin shari'a ba; yayi ta wurin ji tare da bangaskiya."
Wannan na wakilci mutane da suke aikata abin da shari'a ke bukata. AT: "domin kuna aikata abin da shari'a ta ce mu yi"
harshe ku na iya bukatar cewa abin da mutane suka ji da wanda suka amince a bayyana sosai. AT: "domin kun ji sakon ku ka gaskata cikin Yesu ko kuma "domin kun saurari sakon ku ka kuma amince cikin Yesu"
Allah ya ga bangaskiyar Ibrahim cikin Allah, sanan Allah ya ga Ibrahim a matsayin adali.
"wanda suke da bangaskiya." Manufar wannan kalma "bangaskiya" akan iya bayyana shi cikin aiki "yin imani da." AT: "wanda suka yi imani da"
Wannan na wakilce mutane wanda Allah na kalon su kamar yadda yana kalon Ibrahim. AT: " adali ta hanya ɗaya kamar Ibrahim"
Domin Allah ya yi alkawari wa Ibrahim, suka kuma rubuta kafin alkawarin ta zo ta wurin Almasihu, nassi na kamar wani wanda ya san gobe kafin ta faru. AT: "annabta " ko kuma "gani kafin ta faru"
"ta dalilin abin da ka yi" ko kuma "domin na riga na albarkace ke." kalmar "ka" na nufin Ibrahim ne.
"dukan mutane a cikin duniya." Allah na nanata cewa bai fi son Yuhadawa kadai ba, zababun sa. Shirin sa domin ceto wa Yayudawa da kuma wanda ba Yayudawa.
kasancewa a karkashin la'ana na nufin kasance la'anane. Anan ana nufin kasancewa a madawwamiyar azaba. "Waɗanda suka dogara ga ... shari'a la'anannu ne" ko kuma "Allah zai hukunta har abada wanda suke dogara ga ...shari'a"
Abin da ya ke a sarari za a iya bayyana haka. AT "a sarari Nassin ta ke" ko kuma "Nassi ya koyar a sarari"
za a iya bayyana wannan cikin aiki. AT: "Allah ba zai baratar da kowa ba ta wurin bin shari'a"
wannan kalman "adalci" na nufin adalan mutane. AT: "adalan mutane za su rayu ta wurin bangaskiya"
"abin da shari'a ta ce dole mu aikata"
Zai yiwu ana nufin 1) dole ayi biyaya da su duka" ko kuma 2) "za a hukunta shi ta wurin iya yin abin da shari'a ke bukatar."
kalmar "la'ananne" ana iya bayyana ta cikin aiki da "la'ana." AT: daga kasancewa cikin la'ana domin shari'a" ko kuma "daga kasancewar la'anane ta wurin rashin bayayya da shari'a"
kalman nan "La'ana" za a iya bayyana shi cikin aiki "la'anane," AT: "ta wurin kasance la'ananne domin mu" ko kuma "lokacin da Allah ya la'ance shi maimakon mu"
Kalman "la'ana" anan na bada ra'ayin hukuncin Allah ga mutumin da ya la'anta. AT: "daga gare mu Allah ya hukunta mu domin mun karya shari'a ... da sa Allah ya hukunta shi a maimakon mu...Allah ya hukunta kowa da kowa"
Bulus na sa ran masu sauraro sa su fahimci cewa yana nufin Yesu aka kafa bisan giciye.
"domin Almasihu ya zama la'ananne domin mu, albarkan Ibrahim za ta zo"
domin Almasihu ya zama la'ananne domin mu, ta wurin bangaskiya za mu samu"
kalman "mu" ya hada da mutanen da za su karanta wasikar.
Dubi yadda ku/ka fassara wannan a Galatiyawa 1:2.
"a yadda mutum" ko kuma " da abubuwa mafi yawan mutane sun fahimta"
Wannan kalman na nufin cewa Bulus ya bayyana manufar, yanzu yana fara gabatar da wani muhimmin zance.
"na nufin zuriya masu yawa"
kalman "ka" na nufin wani mutum musamma, wanda shi musamman zuriyar Ibrahim
"shekaru dari hudu da talatin"
Bulus na magana gama da yanayin da ba ta taba kasancewa ba don ya nanata cewa gadon na zuwa wurin alkarine ne kadai. AT: "gadon ya zo gare mu ta wurin alkawari ne, domin ba mu iya kiyaye buƙatar shari'ar Allah ba"
karɓan abin da Allah ya alkawarta wa masubi ne a ke maganar ta kamar wani gadon dukiya ne daga wani dan iyali, da madawwamiyar albarku da kuma fansa.
Bulus ya yi amfani da tambaya da ba ta buƙatar amsa ya gabatar da zancen da zai tattauna a gaba. za a fassara wannan maganar kamar. AT: "Zan gaya mu ku menene manufar shari'a." ko kuma "Bari in gaya mu ku dalilin da ya sa Allah ya bayar da shari'a."
ana iya bayyana wannan cikin aiki. AT: "Allah ya kara ta" ko kuma "God ya kara shari'a"
Ana iya bayyana wannan cikin aiki. AT: "Allah ya bayar da shari'a ta wurin taimakon mala'iku, sai matsakanci ya tilasta ta"
"mai wakilci"
Allah ya ba da alkarinsa ga Ibrahim ba tare da matsakanci ba, amma ya bayar da shari'a ga Musa tare da matsakanci. Ta dalilin haka, ma su karatun wasikar Bulus za su iya yin tsammani cewa shari'an ta wata hanya dai ta sa alkarin ba ta cika ba. Bulus na bayyana abin da masu karatu za iya yin tsammani anan, da kuma zai amsa mu su a cikin aya da ke bi.
"na găba da alkawaran" ko kuma "cikin saɓani da alkawaran"
Wannan anan iya bayyana cikin aiki, da kuma suna "rai" ana iya fassaran aiki "rayuwa." AT: "in da Allah ya bayar da shari'a da ke ba da dama ga wanda suka kiyaye ta su rayu"
"da mun zama adalai ta wurin yin biyyaya da shari'a"
Ana iya ba da wasu ma'ana 1) domin kowa yayi zunubi, Allah ya sa komai a karkashin mulkin shari'a, kamar kulle su a kurkuku, ta haka ne abin da ya alkawarta ga wanda suka gaskata cikin Almasihu Yesu zai iya bayar ga masu gaskatawa. 2) domin mu yi zunubi, Allah ya sa komai a karkashin mulkin shari'a, kamar kulle su a kurkuku. ya yi haka ne domin abin da alkawarta ga wanda suka gaskata cikin Almasihu Yesu ya bayar ga masu gaskatawa."
Bulus na yi da nassi kamar wani mutun ne da yake magana ga da Allah, wanda ya rubuta nassi. AT: "Allah"
za a iya bayyana wannan cikin aiki. AT: "shari'an ta riƙe mu ƙangi, muna cikin kurkuku" ko kuma "shari'an ta riƙe mu ƙangi cikin kurkuku"
wannan ana iya bayyana cikin aiki, da wanda wannan bangaskiya ke ciki na iya bayyana a sarari. AT: " kafin Allah ya bayyana cewa ya kuɓutar da wanda suke da bangaskiya cikin Almasihu" ko kuma " kafin Allah ya bayyana cewa ya kuɓutar da wanda suke dõgara cikin Almasihu
Fiye da jagora kawai "wani da ya ke ba da dubawa ga yaro," a yawanci wannan bawa ne wanda aikinsa tilasta umurni da halin da iyaye suka bayar, ya kuma kai rahoto ga iyaye game da halin yaron.
"kafin lokacin da Almasihu ya zo"
kafin zuwan Almasihu, Allah ya yi shirin kuɓutar da mu. lokacin da Almasihu ya zo, ya cika shirin sa na kuɓutar da mu. ana iya bayyana wannan ciki aiki. AT: "sabõda haka Allah ya bayyana mu adalai"
" domin dukanku wanda aka yi muku baftisma cikin Almasihu"
Ana iya nufin 1) wannan nafin kamar an hada su da Almasihu. AT: "kun zama a haɗe da Almasihu" ko kuma "na Almasihu" ko kuma 2) wannan na nufin kamar cewa sun zama kamar Almasihu. AT: " a zama kamar Almasihu"
Allah baya ganin bambanci tsakanin Bayahude da Ba'al'umme, bawa da 'yantace, namiji da mace"
mutanen da Allah ya yi ma su alkari su ake magana akai kamar za su gãji dukiya daga wani ɗan iyali.
1Ina cewa muddin magaji yaro ne, babu bambancin sa da bawa, ko da yake shine mai mallakan dukan kadarorin. 2A maimakon haka, yana karkashin masu jagora da amintattu har sai lokacin da mahaifinsa ya ajiye.3Hakannan mu ma, lokaci da muke yara, an rike mu cikin kangi na tushin ka'idojin wannan duniya. 4Amma da lokacin ya yi daidai, Allah ya aiko da dansa, haihuwar mace, haihuwar karkashin shari'a. 5Ya yi haka ne domin ya fanshi wadanda ke a karkashin shari'a, domin mu karbi diyanci a matsayin 'ya'ya.6Domin ku 'ya'ya ne, Allah ya aiko da Ruhun Dansa cikin zuciyarmu, Ruhun wanda ke kirar, "Abba, Uba." 7Saboda wannan dalilin kai ba kuma bawa ba ne amma da. Idan kai da ne, hakannan kuma kai ma magaji ne ta wurin Allah.8Duk da haka a da, da ba ku san Allah ba, bayi ne ku ga alloli wadanda ainihi ba alloli ba ne ko kadan. 9Amma yanzu da kuka san Allah, ko kuma, yanzu da Allah ya san ku, me ya sa kuke sake komawa zuwa ga tushen ka'idodin nan mara karfi da amfani? Kuna so ku sake komawa zaman bayi kuma daga farko?10Kuna kiyaye ranaku na musamman, sabobin watanni, lokatai, da shekaru. 11Ina ji maku tsoro. Ina tsoro cewa kamar na yi aiki cikinku a wofi.12Ina rokon ku 'yan'uwa, ku zama kamar yadda nake, domin ni ma na zama kamar ku. Ba ku yi mani laifin komai ba. 13Amma kun sani cewa saboda rashin lafiya ne na yi maku shelar bishara da farko. 14Ko da yake halin da nake ciki cikin jiki a zahiri ya sa ku cikin gwaji, ba ku raina ni ba ko kuma kuka watsar da ni. A maimakon haka, kun karbe ni kamar mala'ikan Allah, kamar ni Almasihu Yesu ne da kansa.15Saboda haka, yanzu ina murnar taku? Domin ina shaidar ku, idan mai yiwuwa ne, da kun kwakulo idanunku, kun ba ni. 16To kenan, na zama makiyin ku ne saboda na gaya maku gaskiya?17Suna neman ku da himma ba domin wani alheri ba ne. Suna so su raba ni da ku domin ku bi su. 18Yana da kyau ko yaushe a yi himma domin dalilai masu kyau, ba kuma kawai sa'adda ina tare da ku ba.19'Ya'yana kanana, sabili da ku ina cikin zafin nakuda kuma sai Almasihu ya samu kafuwa cikinku. 20Da ma a ce ina tare da ku yanzu in canza muryata, domin ina damuwa a kanku kwarai.21Ku gaya mani, ku da kuke marmarin ku zo karkashin shari'a, ba ku ji abin da shari'ar ta ce ba? 22A rubuce yake cewa, Ibrahim yana da 'ya'ya maza biyu, daya dan baiwa ne, dayan kuma dan 'yantaciyar mace ne. 23Abin lura anan, dan baiwar an haife shi ta hanyar mutuntaka ne, amma dan 'yantaciyar macen, an haife shi ta wurin alkawari ne.24Ana iya bayyana abubuwan nan a hanyar kwatanci kamar haka, wadannan mata na kama da alkawarai ne guda biyu. Dayan alkawarin daga dutsen Sinayi ne. Ta haifi 'ya'ya da ke bayi ne su. Ita ce Hajaratu. 25Yanzu fa, Hajaratu ita ce dutsen Sinayi da ke Arebiya. Misali ce na Urushalima na yanzu, domin tana cikin bauta tare da 'ya'yanta.26Amma Urushalima da ke bisa 'yantacciya ce, ita ce mahaifiyarmu. 27Kamar yadda yake a rubuce, "Ki yi murna, ke bakarariya, ke da ba ki taba haihuwa ba. Ki yi shewa na farinciki, ke da ba ki dandana haihuwan da ba. Domin 'ya'yan bakarariya da yawa suke, fiye da ta mace mai miji."28Yanzu fa, 'yan'uwa, kamar yadda Ishaku yake, haka muke, wato 'ya'yan alkawari. 29A lokacin can, shi wanda aka haife shi ta hanyar mutuntaka ya tsananta wa wanda aka haife shi ta hanyar Ruhu. Haka yake har yanzu.30Amma menene nassi ya ce? "Ka kori baiwar nan tare da danta. Domin dan baiwar nan ba za ya ci gado tare da dan macen nan da ke 'yantacciya ba." 31Saboda haka 'yan'uwa, mu ba 'ya'yan baiwa ba ne, a maimakon haka, mu 'ya'yan macen nan ne da ke 'yantacciya.
Bulus ya ci gaba da tunashe masubi a Galatiya cewa Almasihu ya zo ya fanshi wanda suke karkashi shari'a, ya kuma mayar da su 'ya'ya ba bayi kuma ba.
"ɗaya da"
mutane da suke da iƙon lura da 'ya'ya bisa ga umurnin hukuma
mutanen da wasu ke amince da su waje lura da muhimman abubuwa
kalman "mu" anan na nufin dukan masubi, harda masu karatu wasikar Bulus.
A nan " 'ya'ya" na nufin kamar kasance rashin girma a ruhaniya. AT: "sa'ada mu ke kamar 'ya'ya"
A nan "bauta" na ba da misalin rashin iya hana kaina daga yin wani abu. Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "ƙa'idodin farko na duniya na mulkin mu" ko kuma " mun yi biyayya da ƙa'idodin farko na duniya kamar mun kasance bayi"
Ya yiwu ana nufin 1) wannan na nufin dokoki ko kuma ƙa'idodin halin duniya, ko 2) wannan na nufi da iƙokin ruhu wanda waɗansu ke tunani na mulkin abin da ke faruwa a duniya.
Bulus yayi amfani da misãlin mutun da ke sayan dukiyan da ya ratsa, ko sayan 'yancin wani bawa kamar hoton yadda Yesu ke biya domin zunuban mutanesa ta wurin mutuwa a kan giciye.
Wannan muhimmin lakabi ne na Yesu, Ɗan Allah.
Bulus ya yi amfani da kalmar yaro namiji anan domin zancen game da gado ne. A al'adan shi da masu karatun shi, an saba ba gado ga 'ya'ya maza, ko da yake ba ko yaushe ba. ba wai yana tanatance ko kuma ware 'ya'ya mata ba ne anan.
Ta kiran "Abba, Uba" Ruhun na tabbatar da mu 'ya'ya Allah ne kuma yana kaunar mu.
zuciya anan a nufin bangare a mutum da ke tunani ko ji. AT: "aika Ruhun Ɗan sa ya nuna mana yadda za mu yi tunani da zama"
Wannan muhimmin lakabi ne na Yesu, Ɗan Allah.
Ruhu shi ne wanda ke kira.
Ta wannan hanya ne yaro ke martaba mahaifinsa a harshen gidan Bulus, amma ba a harshen Galatiyawa masu karatu ba. domin ci gaban harshen waje, fassara wannan kalman "Abba" kamar yadda harsha ku ke yi.
Bulus na magana da masu karatun sa kamar mutum daya ne.
ana magana game da mutanen da Allah yayi wa alkawarai kamar za su gaji wani dukiya ne da ga wani ɗan iyali.
"waɗannan abubuwan da suke" ko kuma "waɗannan ruhohin wanda suke"
ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: Allah ya san ku"
A nan "juya baya ga" na kamar fara mayar da hankali ga wani abu kuma. AT: "ka da ku fara mayar da hankalinku ga... ƙa'idodi." ko kuma "ka da ku damu da ... ƙa'idodi."
dubi yadda ku ka fassara wannan magana cikin Galatians 4:3.
Bulus na amfani da wannan tambaya ya tsauta wa mutanen domin suna wani hali kamar bayi. AT: "da alama kuna so ku za bayi kuma." ko kuma "kuna hali kamar kuna so ku sake zama kamar bayi."
Bulus na magana game da aminci da hankalinsu wajen kiyaye lokatan idi, da tunanin cewa kiyaye wannan ne zai daidaita su da Allah. AT: "kun kansanci da hankali a kiyaye idin ranaku da sabobin watanni da na shekaru"
"iya kassance banza" ko kum "ba bu wani sakamako"
A nan wannan na nufin tambaya ko kuma izawa da karfi. Wannan ba kalmar da ake amfani wajen tambayan kuɗi ko abinci ko kuma wasu kaya da ake iya gani ba.
Dubi yadda kuka fassara wannan cikin (Galatiyawa 1:2) (../01/01.md).
ana iya bayyana wannan a tabbataceyar sifa. "kun bi da ni da kyau" ko kuma "kun lura da ni a yadda yakamata"
"ko da yake ya yama mu ku da nauyi ku kalle ni ciki rashin lafiya ta jiki"
ƙiyayya sosai
"a shawo ku ga hada kai da su"
"a raɓa ku da ga gare mu" ko kuma "su sa ku daina kassance da biyyaya da mu"
"himmantu da abin da suka ce da ku ku yi"
Wannan na ba da ra'ayin almajirai ko kuma masu bi. AT: "ku da kuke almajirai domina"
Bulus na amfani da nakuda ya bayyana damuwar sa game da Galatiyawa. AT: " Ina cikin zafi kamar ni wata mace ce da taka haifan ku, kuma zan ci gaba da zama a cikin zafin har sai Almasihu mulkance ku da gaske"
"Ina so in yi wani tambaya" ko kuma "Ina so in gaya mu ku wani abu"
Bulus na gabatar da abin da ce a gaba. AT: "kuna bukatar ku koyi abin da shari'ar ta ce." ko kuma "bari in gaya muku gaskiyar abin da shari'a ta ce."
Wannan labarin 'ya'ya maza biyu na kamar hoton da zan gaya muku yanzu"
"misali" labari ce wanda mutane da abubuwan cikin ta na nufin wasu abubuwa. a misalin Bulus, mata biyu na Galatiyawa 4:22 na nufin alkawarai biyu.
"mata na ba da hoton ... ita hoton"
"Dutsen Sina'i" anan na matsayin shari'an da Musa ya bayar ga 'Israi'lawa a wurin. AT: "Dutsen Sina'i, wajen da Musa ya bayar da shari'a ga Israi'la"
Bulus na magana game da shari'a kamar wani mutum ne. AT: "mutanen da suke karkashin wannan alkawarin na kamar bayi ne wanda ya kammata su yi biyyaya da shari'a"
Hajara baiwa ce, 'ya'yan ta ma bayi ne da ita. AT: "Urushalima, kamar Hagara, baiwa ce, 'ya'yan ta kuma bayi ne da ita"
"ba a ɗaure ba" ko kuma "ba bawa ba"
yi murna
Anan "ke" na nufin bakarãriya mace.
Ana iya nufin cewa Galatiyawa sun zama 'ya'ya Allah 1) ta wurin gaskata alkawarin Allah, ko kuma 2) domin Allah yayi aikin mu'ujizai domin ya cika alkawaren sa ga Ibrahim, farko ya ba Ibrahim ɗa sannan ya mayar da Galatiyawa 'ya'yan Ibrahim wato 'ya'yan Allah.
Wannan na nufin Ibrahim ya zama uban Isma'ilu ta daukan Hajaratu ta zama matarsa. AT: "ta wurin aikin mutuntaka" ko kuma "ta dalilin abin da mutane suka yi"
"domin wani abin da Ruhu ya yi"
kalmomin nan "mu 'ya'ya ne"an fahimce su a maganar baya. Ana iya fassarar wannan kamar wata magana dabam. AT: "amma, mu 'ya'yan 'yantacciyar macen ne"
1Saboda 'yanci ne Almasihu ya yantar da mu. Sai ku dage kada ku sake komawa cikin kangin bauta. 2Duba, ni Bulus, ina gaya maku cewa idan an yi maku kaciya, Almasihu ba zai zama da amfani a gare ku ba a kowace hanya.3Haka kuma, na shaida ga ko wanda mutum wadda aka yi masa kaciya ya zama dole ya yi biyayya da dukan shari'a. 4Kun rabu da Almasihu, dukanku wadanda aka "baratar" ta wurin shari'a. Kun fadi daga alheri.5Domin ta wurin Ruhu, cikin bangaskiya, muna jira gabagadi na adalci. 6A cikin Almasihu kaciya ko rashin kaciya ba shi da ma'ana. Bangaskiya kadai mai aiki ta wurin kauna ita ce mafi muhimmanci. 7Da kuna tsere da kyau, wanene ya tsayar da ku daga yin biyayya da gaskiya? 8Rinjayarwa da ke sa yin wannan, ba daga wanda ya kira ku ba ne9Ai karamin yisti shi yake sa dukan kulli ya kumbura. 10Ina da wannan gabagadin game da ku cikin Ubangiji cewa ba za ku yi tunani a wata hanya daban ba. Shi wanda ya rikita ku zai sha hukunci ko wanene shi.11'Yan'uwa, idan har yanzu wa'azin kaciya nake yi, don me har yanzu ake tsananta mani? Inda haka ne dutsen sanadin tuntube game da gicciye da ya ragargaje. 12Ina fata wadanda suke badda ku su maida kansu babani.13'Yan'uwa, domin Allah ya kira ku zuwa ga yanci, kada dai ku mori yancin nan ya zama zarafi domin jiki. A maimakon haka ta wurin kauna ku yi wa juna hidima. 14Saboda dukan shari'a ta cika ne a cikin doka guda daya; "Ka kaunaci makwabcinka kamar kanka." 15Amma idan kuna cizo da hadiye juna, ku lura kada ku hallakar da junanku.16Na ce, ku yi tafiya cikin Ruhu, ba za ku cika sha'awoyin jiki ba. 17Domin jiki yana gaba mai karfi da Ruhu, Ruhu kuma yana gaba da jiki. Domin wadannan akasin juna suke. Sakamakon shine ba za ku iya yin abin da kuke so ba. 18Amma idan Ruhu ne ke bishe ku, ba ku karkashin shari'a.19Yanzu ayyukan jiki a bayyane suke. Sune al'amuran lalata, rashin tsarki, sha'awoyi, 20bautar gumaka, sihiri, yawan fada, jayayya, kishi, zafin fushi, gasa, tsattsaguwa, hamayya, 21hassada, buguwa, buguwa da tarzoma, da dai sauran irin wadannan abubuwa. Na gargade ku, kamar yadda a da na gargade ku, cewa wadanda suke aikata wadannan abubuwa ba za su gaji mulkin Allah ba.22Amma 'ya'yan Ruhu kauna ne, farinciki, salama, hakuri, kirki, nagarta, bangaskiya, 23tawali'u, da kamun kai. Babu wata shari'a da ke gaba da wadannan abubuwa. 24Wadanda suke na Almasihu Yesu sun giciye halin jiki tare da marmarin sa da miyagun sha'awoyi.25Idan muna zaune cikin Ruhu, mu yi tafiya da Ruhu. 26Kada mu zama masu girman kai, ko muna cakunar juna, ko muna kishin juna.
Bulus yayi amfani da misali ya tunashe masubi ga yin amfani 'yanci su cikin Almasihu domin a cika duka shari'a cikin kaunace maƙwabta kamar kanmu.
"saboda mu iya samun 'yanci ne shi yasa Almasihu ya 'yantar da mu." Ana ba da tabbacin cewa Almasihu ya 'yantar da masubi daga tsohon alkawari. Anan 'yanci daga tsohon alkawari na ma'anar kassance ba wajibi ne a yi biyaya da ita ba. AT: "Almasihu ya 'yantar da mu daga tsohon alkawari domin mu zama da yanci." ko "Almasihu ya 'yantar da mu domin mu iya rayuwa kamar 'yanttatun mutane"
tsayawa da karfi anan na wakilce ɗaukan kuduri ba za ka canja ba. ana iya bayyana yadda ba su canja ba a sarari haka. AT: " kada ku ba da kai ga jayayyan mutane da suke koyas da wani abu dabam" ko "kassance da kudurin zama a 'yanci"
Bulus na amfani da kaciya yana nufin Yahudanci. AT: "in kuka juya ga adinin yahudanci"
A nan kassancewa karkashin kangin bauta na wakilci kassance wajibi ne a biyayya da shari'a. AT: "kada ku yi rayuwa kamar wanda ke karkashin kangin bauta ga shari'a"
"Na furta" ko "Na zama kamar mashaiɗi"
Bulus na amfani da kaciya a nufin kassance Bayahude. AT: "ga duk wanda a zama Bayahude"
"dole ya yi biyayya"
A nan "yanke" na nufin rabuwa daga Almasihu. AT: ka ƙarar da dangantakar da Almasihu" ko "ba ka haɗe da Almasihu"
Bulus na magana cikin habaici anan. Zahiri ya koyas cewa ba wani da za a baratar ta wurin aikata aikin da shari'a ke buƙata. AT: "duk wanda ke tunani za a baratar da shi ta wurin aikata aikin da shari'a ke bukata" ko "wanda ke son baratarwa ta wurin shari'a"
Wanda alheri ya zo daga, ana iya bayyana a sarari. AT: " Allah ba zai yi mu ku alheri ba"
A nan kalman "mu" na nufin Bulus tare da wanda suke ƙoƙarin hana masubi yin kaciya. Ya yiwu ya haɗa har da Galatiyawa.
"Wannan haka ne domin ta wurin Ruhu"
Manufar na mai yiwuwa 1) "ta wurin bangaskiya muna jiran begen adalci" ko 2) muna jira begen adalci da ke zuwa ta wurin bangaskiya."
"muna hakuri da murnan jiran Allah ya daidaita mu da kansa har abada, da kuma tsammanin zai yi"
Wannan na bayyana kassancewa Bayahude ko wanda ba Bayahude ba. AT: "ba kassancewa Bayahude ko ba ka kassance Bayahude ba"
"a maimako, Allah ya damu da bangaskiyar mu a cikin sa, wanda ke ta wurin ƙauna da muke wa wasu"
mara kima
"kuna aikata abin da Yesu ya koyar"
"ba Allah wanda ya kira ku ne ya rinjaye ku wajen yin haka ba"
abinda ya kira su ga, ana iya bayyana a sarari haka. AT: "wanda ya kira ku ku zama mutane sa"
rinjayar wani shi ne sa mutum ya canja abin da ya gaskata zuwa aikata wani abu dadam.
"ba za ku gaskata ga wani abu dabam da abin da na ke gaya muku"
"Allah zai hukunta duk wanda ke matsa muku"
"ke sanadin rashin tabbacinku game da gaskiya" ko "zuga ta da hankili a tsakanin ku"
Mai yiwuwa ana nufin 1) Bulus bai san sunayen mutanen da suke gayawa Galatiyawa da cewa suna bukatar su yi biyayya da shari'ar Musa, ko 2) Bulus baya so Galatiyawa su damu ko ma su rikicer da su na da arziki ko talakawane, ko masu girma ko kanana, ko masu addini ko kuma marasa addini.
Bulus na bayyana wani yanayi ne da bai faruba ta wurin nanata cewa mutane na tsananta mishi domin baya wa'azin mutane na bukatan su zama Yahudawa. Ana iya bayyana wanan cikin sifar aiki. AT: " 'Yan'uwa, kun gani har yanzu bana shelar kiciyar domin Yahudawa suna tsananta mani."
dubi yadda ka fassara wannan cikin Galatiyawa 1:2.
Bulus na bayyana wani yanayi ne da bai faruba domin ya nanata cewa mutane na tsananta mishi domin yana wa'azi cewa Allah na yafe wa mutane domin aikin da Yesu yayi a bisa giciye.
"inda har yanzu ina cewa mutane na bukatan su zama Yahudawa"
Wannan za a iya bayyana cikin sifar aiki. AT: "koyas game da giciye bata da tsanandin tuntubɓe" ko kuma "ba wani abu da ke sa mutane tuntube a koyaswa game da giciye"
Mai yiwuwa ana nufin 1) ciren marainan namiji don su zama baban ya ko kuma 2) janyewa daga al'umman masubi gaba daya.
Bulus na bayar da dalilin rubutun da yayi a Galatiyawa 5:12.
ana iya bayyana wannan a sifar aiki. AT: "Almasihu ya kira ku ga 'yanci"
ana iya bayyana da kyau dangata tsakanin "dama" da "halin mutumta" a haka. AT: "kun samu wata damar nuna halin mutumtakar ku"
Mai yiwuwa ana nufin 1) "za ka in bayyana dukka shari'ar cikin umurni guda, wannan shi ne" ko kuma 2) "ta wurin yin biyayya da umurni guda, kun yi biyayya ga duk umurnai, wannan umurnin shi ne."
tafiya na nufin rayuwa. AT: "bi da rayuwarku cikin iƙon Ruhu Mai tsarki" ko kuma "ku yi rayuwarku cikin dogara ga Ruhu"
managan "biye wa sha'awarce sha'awarcen wani" karin magana ne da ke nufin "biye wa sha'awar wani." AT: "ba zu biye wa abin da halin mutumtakarku ke sha'awar ba"
an yi magana game da halin mutumtaka kamar wani mutum ne da ya ke so yayi zunubi. AT: "abin da ku so ku yi ta dalilin halin mutumtakar ku" ko kuma "abubuwan da ku ke so ku yi domin ku masu zunubi ne"
"ba wajibtar biyayya ga shari'ar Musa ba"
ana iya fassarar kalmar "ayuka" cikin sifar aiki "aikata." AT: "abin da halin mutumtaka ke aikata"
ana magana game da abinda Allah ya Alkawarta ga masubi kamar wani dukiya da ake mallaka a wurin ɗan iyali.
Anan " 'ya'ya' " na nufin "sakamako." AT: "abin da Ruhu ke haifa ita ce kauna ...kamunkai" ko kuma "Ruhun ya kan haifa a cikin mutanen Allah Kauna ... kamunkai"
Bulus na magana game da Masubi da ba su rayuwar mutumtaka kamar halin mutumtaka wani mutum ne da aka kashe a bisa giciye. AT: "rashin rayuwa ta halin mutumtaka da matsananciyar sha'awarta, kamar an kashe ta bisa giciye"
ana magana game da halin mutumtaka kamar wani mutum ne da ke da matsananciyar sha'awa. AT: "halin mutumtakar su, da kuma abubuwan da suke sa karfin bukatar yi game da ita"
"tun da Ruhun Allah ya rayar da mu"
"ya kamata mu"
1'Yan'uwa, idan an kama mutum yana yin wani laifi, ku da kuke da ruhaniya sai ku dawo da mutumin a hanya cikin ruhun tawali'u, ka lura da kanka don kada kai ma ka fada a cikin gwaji. 2Ku dauki damuwar juna, ta yin haka za ku cika shari'ar Almasihu.3Domin idan kowa ya zacci shi wani abu ne alhali shi ba komai ba ne rudin kansa yake yi. 4Sai kowa ya auna aikin sa. Sa'annan zai sami abin da zai yi takama, ba sai ya kwatanta kansa da wani ba. 5Domin kowa zai dauki nauyin kayansa.6Wanda aka koya masa maganar, wajibi ne ya ci amfanin abubuwansa masu kyau duka tare da malaminsa. 7Kada fa a yaudare ku ba a yi wa Allah ba'a. Dukan abin da mutum ya dasa, shine abin da zai girba. 8Domin shi wanda ya shuka wa kansa dabi'ar zunubi zai girbi hallaka, amma shi wanda ya shuka cikin Ruhu, zai girbi rai madawwami daga Ruhu.9Kada mu gaji da aikata nagarta, domin a lokacin da ya dace za mu yi girbi idan ba mu gaji ba. 10Saboda haka, lokacin da muke da zarafi, sai mu yi nagarta ga kowa. Mu yi nagarta mussamman ga wadanda suke na iyalin bangaskiya.11Dubi yawan wasikun da na rubuta maku da hannuna. 12Wadanda suke so su nuna hali mai kyau cikin jiki suke tilasta ku yin kaciya. Suna yin haka ne kadai saboda kada a tsananta masu saboda gicciyen Almasihu. 13Domin ko su wadanda suke masu kaciya ba su kiyaye shari'a. Maimakon haka suna so ne a yi maku kaciya don su yi fahariya game jikinku.14Bari kada ya zama ina fahariya sai dai ta gicciyen Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurinsa ne aka gicciye duniya a gare ni, ni kuma ga duniya. 15Domin kaciya ko rashin kaciya ba komai ba ne. Maimakon haka, sabon halita ne ke da muhimmanci. 16Ga dukan wadanda za su zauna cikin wannan ka'ida, bari salama da jinkai su kasance tare da su da kuma bisa Isra'ila na Allah.17Daga yanzu zuwa nan gaba kada wani ya dame ni, domin ina dauke da tabbai na Yesu a jikina. 18Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu ya kasance da ruhun ku, 'yan'uwa. Amin.
Bulus na koyar da masubi yadda za su lura da 'yan'uwan masubi da kuma yadda Allah ke sakayya.
Dubi yadda kuka fassara wannan cikin Galatiyawa 1:2.
idan kowane a tsakanin ku"
Mai yiwuwa ana iya nufin 1) wani ne dabam ya tarar da wani mutum yana aikatawa. AT: "idan a gano wani na cikin aikata zunubi" ko kuma " 2) wancan mutum ya aikata zunubi ba da nufin yin mugunta ba. AT: "idan wani ya ba da kansa cikin zunubi"
"ku wanda Ruhu ne ke bi da ku" ko kuma "ku wanda kuke rayuwa cikin jagorar Ruhu"
"daidaita mutummin da yayi zunubi" ko kuma "gargadi mutummin da ya yi zunubi ya dawo zuwa ga ɗangantaka mai kyau da Allah"
Mai yiwuwa ana nufin 1) Ruhu ne ke jagoran mutummin da ke yin gargadi ko kuma 2) "da halin tawali'u" ko "cikin halin kirki."
Wannan kalmomin sun zama ga Galatiyawa kamar da mutum da a ke magana domin a nanata cewa da kowani mutum a cikin su ya ke magana da. AT: "ku zama da kula da junanku" ko kuma "ina magana da kowanen ku, kula da kanka"
ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "don kada wani abu ya gwada kai ma ga yin zunubi"
"domin in da." kalmomin da suka biyo suna ba da dalilin da zai sa Galatiyawa su 1) "dauki nauyin juna" (Galatiyawa 6:2] 9./01.md)) ko kuma 2) kuyi lura kada suma da kansu a gwada su (Galatiyawa 6:1) ko 3) "kada a zama da fahariya" ([Galatiyawa 5:26).
"shi muhimmin mutum ne" ko kuma "shi ya fi wasu"
"ba shi da muhimminci" ko kuma " shi bai fi wasu ba"
"dole kowanenku"
"za a yi wa kowa hukunci bisa ga aikin sa. ko kuma "kowanen ku zai ɗauki alhakin aikinsa ne kadai"
"kowani mutum zai"
"mutumin"
"sakon," duk abin da Allah ya ce ko kuma ya umurta
Shuƙi na nufin yin abubuwan da a karshe suna da wasu sakamako, tarawa kuma na wakilce zama da sakamakon abin da mutum ya yi. AT: "domin yadda manomi ke tara duk 'ya'yan irin da ya shuka ya haifa, haka kowa ke zama da sakamakon duk abin da ya yi"
ba maza ne kadai Bulus ke nufi anan ba. AT: "duk abin da mutum ya shuƙa" ko kuma "duk abin da wani ya shuƙa"
shuka iri na bayyana aikata halin da sakamako zai biyo baya. A wannan yanayin, mutum na aikata zunubi domin halin mutumtakarsa ne. AT: "shuƙa irin da yake so domin halin mutumtakarsa" ko kuma "aikata abin da yake so domin halin mutumtakarsa"
an bayyana yadda Allah na hukunta mutumin kamar yadda mutum na girbe amfanin gona. AT: "zai karɓi hukuncin abin da ya aikata"
shuka iri na bayyana aikata halin da sakamako zai biyo baya. A wannan yanayin, mutum na aikata hali mai kyau domin yana sauraron Ruhun Allah. AT: "aikata abubuwan da Ruhun Allah ke so"
"zai karɓi sakayya rai madawwami ta wurin Ruhun Allah"
"mu ci gaba da yin nagarta"
yin nagarta zuwa ga wasu domin zaman lafiyar su
"gama a lokacin da ya ɗace" ko kuma "domin a lokacin da Allah ya zaɓa"
"ta dalilin wannan" ko kuma "domin wannan"
"tun ba....waɗanda" ko kuma "musamman ... waɗanda"
"waɗanda suke gungiyar iyalin Allah ta wurin bangaskiya cikin Almasihu"
Wannan na iya nufin Bulus na so ya nanata 1) maganar da zai bi baya, ko kuma 2) cewa wannan wasikar daga gare shi ne.
Mai yiwuwa ana nufin 1) mai yiwuwa Bulus na da mataimaki wanda ke taye shi rubuta wannan wasika, shi Bulus yana gaya masa abin da zai rubuta, amma shi da kansa ne ya rubuta sashin karshi na wannan wasika, ko kuma 2) Bulus ne ya rubuta dukkan wasikar da kansa.
"sa wasu tunani mai kyau game da su" ko kuma "sa wasu tunanin cewa su mutane ne masu kirki"
"shaidar da ke bayyane a idanuwa" ko kuma " ta wurin himmar su"
"a sa dole" ko kuma " tasiri mai karfi"
" don kada Yuhadawa su tsanata musu domin sun yarda cewa a giciyen Almasihu ne kadai mutane ke samun ceto"
giciye anan na wakilci abin da Almasihu ya yi mana lokacin da ya mutu bisa giciye. AT: "aikin da Yesu ya yi bisa giciye" ko kuma "mutuwar Yesu da tashin sa"
"mutane da suke takarar ku ga yin kaciya"
"domin su iya fahari cewa sun ƙara ku cikin mutanen da suke ƙoƙarin kiyaye shari'a"
"bana taɓa son in yi fahariya da wani sai dai akan giciye" ko kuma "bari in yi fahariya a giciye ne kadai"
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "sha'anin duniya matacen a gare ni" ko kuma "ina kalon duniya kamar wani mai laifi ne da Allah ya riga ya kashe a bisa giciye"
an riga an fahimci wannan kalmomin "kassance giciyaye" a maganar baya. AT: "na kuma kassance giciyaye ga sha'anin duniya"
Mai yiwuwa ana nufin 1) mutane duniya wanda basu damu da Allah ba, ko kuma 2) abubuwan da wanda basu damu da Allah ba suke dauka ke da muhimmaci.
na da muhimmanci wajen Allah
Mai yiwuwa ana nufin 1) sabon tuba cikin Yesu Almasihu, ko kuma 2) sabon rayuwar mai bi.
Mai yiwuwa ana nufin 1) cewa masubi dukka sune Isra'ila na Allah, ko kuma 2) "bari salama da jinkai su kassnce bisa al'ummai masubi da kuma Isra'ila na Allah" ko kuma 3) bari salama ya kassance ga masu kiyaye doka, kuma jinkai ya kassance bisa Isra'ila na Allah."
Wannan na iya nufin "a karshe" ko kuma "a karshen wannan wasikar da na rubuta"
Mai yiwuwa ana nufin 1) Bulus na umurcen Galatiyawa kada su dame shi, "Na umurce ku: kada ku tayar mun da hankali," ko kuma 2)Bulus na gaya ma Galatiyawa cewa yana umurtan kowa da wannan: kada a tayar masa da hankali," ko 3) Bulus na faɗin marmarin zuciyarsa, "bana son wani ya tayar mun da hankali."
Mai yiwuwa ana nufin 1)"yi mun magana game da wannan ai'amari" ko kuma 2) "sa mun nauwaya" ko kuma "ba ni aiki mai nauyi."
waɗannan alamun taɓo ne daga muttanen da suka yi wa Bulus bulala domin basu son sa ya koyar game da Yesu. At: "gama taɓon jiki na sun nuna cewa ina bautan yesu"
"Ina addu'a kyaun zuciyar Ubangiji Yesu ya kassance da ruhun ku"
1Bulus, manzon Yesu Almasihu ta wurin nufin Allah, zuwa ga kebabbu na Allah da ke a Afisa wanda suke aminci cikin Yesu. 2Bari alheri ya kasance da ku, da salama daga wurin Allah Ubanmu da Ubangijinmu Yesu Almasihu.3Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Shine ya albarkace mu da kowanne albarku na ruhaniya da ke cikin sammai cikin Almasihu. 4Kafin halitar duniya, Allah ya zabe mu da muka ba da gaskiya cikin Yesu. Ya zabe mu domin mu yi zaman tsarki da rayuwar da babu aibu a gabansa.5Cikin kauna Allah ya kaddara ya dauke mu mu zama yayansa ta wurin Yesu almasihu. Ya yi wannan domin ya gamshe shi ya yi abin da ya ke so. 6Sakamakon shine Allah ya karbi yabo domin daukakan alherinsa. Wannan shine abinda ya ba mu hannu sake ta wurin kaunataccensa.7Gama cikin kaunataccensa aka fanshe mu ta wurin jininsa, da gafarar zunubai ta wurin wadataccen alherinsa. 8Ya ba da wannan alherin a yalwace cikin dukan hikima da fahimta.9Allah ya bayyana mana gaskiyar al'amarin da aka boye na shirinsa, ta wurin abin da yake so ya nuna cikin Almasihu. 10Idan lokaci ya yi na kammala shirinsa, Allah zai kawo dukan abubuwan da ke sama da kasa cikin Yesu.11An zabe mu cikin Almasihu mu zama abin gado na Allah. Ya yi mana wannan shirin tun da cikin shirin sa, shi mai yin dukan abu ta dalilin nufinsa. 12Allah ya yi haka saboda mu rayu domin yabon daukakarsa. Mune na farko da muka sami bege cikin Almasihu.13A cikin Almasihu ne kuma kuka samu jin maganar gaskiya, bisharan cetonku ta wurin Yesu. A cikinsa ne kuka bada gaskiya aka hatimce ku da Ruhu Mai Tsarki wanda aka alkawarta. 14Ruhun shine tabbacin gadonmu kafin mu kai ga samunsa. Wannan don yabon daukakarsa ne.15Sabo da haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kaunar ku zuwa dukan wadanda aka kebe dominsa. 16Ban fasa tunawa da ku ba ina addu'a saboda ku cikin addu'o'ina.17Ina addu'a da cewa Allah Ubangijinmu Yesu Almasihu, Uban daraja, ya ba ku ruhun basira da wahayin saninsa. 18Ina addu'a idanun zuciyarku su bude domin ku san tabacin kiranku. Ina addu'a dominku san arzikin mulkin gadonsa cikin wadanda aka kebe dominsa.19Ina addu'a ku san ikon nan nasa mai girma mara iyaka da ke cikin mu da muka ba da gaskiya. Wannan girman yana ta wurin aikin karfin ikonsa ne. 20Wannan shine ikon da ya yi aiki cikin Almasihu lokacin da Allah ya tashe shi daga matattu ya sa shi a hannun damansa cikin sammai. 21Ya sanya shi bisa birbishin dukan sarauta, iko, mulki, karfi, da kowanne irin suna. Ya sanya Almasihu ba a wannan zamanin kadai ba, amma da zamani mai zuwa.22Allah ya saka dukan abubuwa a karkashin kafafun Almasihu. Ya sa shi shugaban dukan abubuwa a cikin ikilisiya. 23Ikilisiya jikinsa ne, cikarsa wanda ya cika dukan abubuwa cikin kowacce hanya.
Bulus ya sa sunansa a matsayin marubucin wannan wasikar wa masubi a ikilisiyar Afisus.
sai dai in an rubuta, dukan misalan "ku" da kuma "na ku" na nufin masubi na Afisus da kuma dukan masubi da haka suke suna.
Yaren ku na iya samun wani hanyar gabatar da mawallafi na wasika da kuma masu sauraro. AT: "Ni, Bulus, manzon ... rubuta wannan wasikar maku, Tsarkakun mutanen Allah Afisus"
"cikin Kristi Yesu" da magana kusan iri guda ne da ke baya nufin ainahin abun da ke faru sosai a cikin wasikun Sabon Alkawari. Su na magana akan irin karfin dangantaka mai yu'a tsakanin Kristi da waɗanda sun gaskanta da shi.
Wannan ne gaisuwa da kuma albarka da Bulus na yawan amfani da shi a cikin wasikar shi.
Bulus ya buɗe wasikar sa da magana akan matsayin masubi da lafiyarsu a gaban Allah.
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki: "mu yabe Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu"
"domin Allah ya albarkace mu"
"da kowwane albarku dake zuwa daga Ruhu na Allah"
"cikin bisa halittar duniya." Kalmar "sama" na nufin wurin da Allah yake.
"cikin Kristi" da magana kusan iri guda ne da ke baya nufin ainahin abun da ke faru sosai a cikin wasikun Sabon Alkawari. Su na magana akan irin karfin ɗangantaka mai yu'a tsakanin Kristi da wa'anda sun gaskanta da shi.
Bulus ya yi amfani da kalmomi kusan iri guda domin ya nanata halin kirki mai kyau.
Kalmar "ya," "shi," da kuma "ya" na nufin Allah.
Kalmar "mu" na nufin Bulus, ikilisiyar Afisus, da dukan masubi a cikin Kristi. AT: "Allah ya shiria da daɗewa domin ya karɓe mu"
A nan "karɓa" na nufin a ajiye a gidan Allah.
Allah ya kawo masubi cikin gidan shi ta wurin aikin Yesu Kristi.
"waɗanda yake ƙauna, Yesu Kristi " ko "Ɗansa, wanda yake ƙauna"
Bulus ya yi magana akan alherin Allah kaman kayan dukiya. AT: "girman alherin Allah" ko"yawan alherin Allah"
"ya bamu wannan babban yawan alheri" ko "ya yi mana kirki na ƙwarai"
Wannan na iya nufin 1) "saboda ya na da dukan hikima da fahimta" 2) domin mu iya samun babban hikima da fahimta"
Wannan na iya nufin 1) "saboda ya so ya sa mu mu sani" ko 2) "wanda da ya so."
"kuma ya bayana wannan nufi a cikin Almasihu"
"ta hanyar Almasihui"
Ana iya fadan sabuwar jumla anan. AT: "Ya yi wannan da ni'yar yin shiri" ko "Ya yi wannan, yin tunani akan wani shiri"
"saboda idan lokaci ya kai" ko "saboda lokacin da ya sa"
Ana iya bayana wannan cikin sifar aiki. AT: "Allah ya zaɓe mu mu zama magaji"
"Allah ya zaɓe mu da wuri"
A nan kalmar "mu" na nufin Yahudawa masubi da su ka fara jin bishara, ba masubi a Afisus ba.
"saboda mu yi rayuwar yabonsa domin ɗaukakarsa"
An saka ruwan candle akan wasika an kuma hatimce da abun shaida da ke wakilin mutumin da ya rubuta wasikar. Bulus ya yi amfani da wannan al'ada a matsayin hoto don ya nuna yanda Allah ya yi amfani da Ruhu mai Tsarki domin ya tabbatar mana cewa mu nashi ne. AT: "Allah ya hatimce ku da Ruhu mai Tsarki da alkawarta"
An yi maganar karɖan abun da Allah ya yi alkawari kamar wani ya gaje kaya ko dukiya daga ɗan gida. AT: "an tabbata cewa za mu karɓa abun da Allah ya alkawarta"
Bulus ya yi adu'a ma masubi na Afisus da kuma yabon wa Allah domin ikon da masubi suke dashi ta wurin Almasihu.
Bulus ya yi anfani da "daina ba" saboda ya nanata cewa ya cigaba da gode wa Allah. AT: "na shigaba da gode wa Allah"
"ruhun basira don ganen wahayinsa"
Wannan zance "idanun zuciyarku" na nanata iyawan wani ya samu ganewa. AT: "Saboda ku samu ganewa da haskaka"
Ana iya bayana wannan cikin sifar aiki. AT: saboda Allah ya haskaka zuciyar ku" kokuwa "saboda Allah mai yuwa ya haskaka ganewan ku"
"an yi shi domin gani"
Ana maganar karɓan abin da Allah ya alkawarta wa masubi ne kamar wani ne na gadan kaya da kuma dukiya daga ɗan gidan.
Ana iya bayana wannan cikin sifar aiki. AT: "dukan wanda ya keɓe ma kansa" ko "dukan wanda sun zama cikakken nashi"
Iƙon Allah na fiye da dukan iƙo.
"sabuda anfanin mu" ko "cikin ɗangantaka wa mu"
"baban iƙon sa daku aiki ma mu"
"tashe shi daga matattu " ko "yi shi da rai kuma"
"Almasihu yana zaune a hannun damar Allah" ko "Almasihu yana zauna a wurin mai daraja a gefen Allah"
"duniyan da ya wuce iƙon ɗan Adam." Kalmar "sammai" na nufin wurin da Allah yake. Dubi yanda an fasara a cikin 1:3.
Wannan maganan dabam-dabam ne da na matsayin ya wuce iƙon ɗan Adam, duka biu mala'ika da aljani. AT: "fiye da dukan irin abun da ya wuce iƙon ɗan Adam"
A nan iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: Ma'ana na kamar 1) " kowane suna da mutum ya bayer" ko2) "kowane suna da Allah ya bayer"
Wannan na iya nufin 1) suna kokuwa 2) wurin izni.
"a wannan lokacin"
"a mai zuwa"
" Allah ya sami" ko " Allah ya saka" (UDB)
A nan "kafafun" na misali da Ubangijin Allah, izni, da kuma iko. AT: " dukan abubuwa a karkashin iƙon Almasihu"
Kawai yanda tare da jikin mutum, kai na mulki da dukan abu dake na jikinsa, haka Almasihu ne shugaban jikin ikilisiya.
A nan "shugaban" na nufin shugaba kokuwa wanda ke lura. AT: "sarkin dukan komai a cikin ikilisiya"
Ikilisiya na yawan nufin jikin Kristi.
"Almasihu ya cika ikilisiya da ransa da iƙo kamar da yake bayar da rai wa dukan abubuwa"
1Amma da ku matattu ne cikin zunubanku da laifofinku. 2A cikinsu kuka yi rayuwa bisa ga al'amuran duniyan nan. Kuka biye wa mai sarautar ikokin sararin sama, wannan ruhun ne da ke aiki cikin kangararrun 'ya'ya. 3Da can dukanmu muna cikin wadannan marasa bada gaskiya. Muka biye wa mugun burin jikinmu. Muna aikata halin mutuntaka da na tunaninmu. Bisa ga dabi'a 'ya'ya ne wadanda sun cancanci fushin Allah, kamar wadansu.4Amma Allah mai yalwar jinkai ne, sabili da matukar kauna da ya kaunace mu. 5Sa'anda muke matattu cikin zunubai, ya kawo mu cikin sabon rai tare da Almasihu. Ta wurin alheri aka cece mu. 6Allah ya tashe mu tare ya kuma sa muka zauna tare a matsayi guda cikin Almasihu Yesu. 7Ya yi wannan domin a zamanai masu zuwa ya nuna mana matukar yalwar arzikin alherinsa ta wurin Yesu. Yana nuna mana wannan ta wurin alherinsa.8Domin ta wurin alheri aka cece ku ta wurin bangaskiya, wannan ba daga gare ku ba ne, kyauta ce ta Allah. 9Ba daga ayyuka ba, Saboda wannan dalili kada kowa ya yi fahariya. 10Gama mu aikin hannuwansa ne, halitattu cikin Almasihu Yesu domin mu yi kyawawan ayyuka, wadanda tun da Allah ya tanada, mu yi rayuwa a cikinsu.11Saboda haka ku tuna da ku al'ummai ne a dabi'ar jiki. Ana kiranku "marasa kaciya", abin da ake kira kaciya cikin jiki wadda hannayen mutane ke yi. 12Gama a lokacin nan a rabe kuke da Almasihu. Ku bare ne ga mutanen Isra'ila. Ku baki ne ga wa'adodi na al'kawarai. Ba ku da tabbaci a kan gobe. Ba ku da Allah a cikin duniya.13Amma yanzu a cikin Almasihu Yesu ku da da kuke nesa da Allah, an kawo ku kusa da shi ta wurin jinin Almasihu. 14Gama shine salamar mu. Domin ya mai da biyun daya. Cikin jikinsa ne ya rushe katangar gaba da ta raba mu da juna. 15Wato ya kawar da shari'a mai umarnai da sharudda, domin ya halitta sabon mutum daya a cikinsa. Yin haka ya kawo salama. 16Ya yi haka domin ya sulhunta mutum biyu cikin jiki daya ga Allah ta wurin gicciye. Ta wurin gicciye ya kashe gabar da ke tsakaninsu.17Yesu ya zo ya yi maku shelar salama ku da kuke nesa da ku na kusa. 18Domin ta wurin Yesu dukanmu biyu cikin Ruhu daya muna da hanya zuwa wurin Uba.19Sabo da haka yanzu ku al'ummai, ko daya, ba bare ba ne. Maimakon haka ku abokai ne tare da kebabbun Allah, abokan aiki. 20Wadanda an gina su bisa tushen manzanni da annabawa. Almasihu Yesu da kansa shine mafificin dutsen ginin. 21A cikinsa dukan ginin ya hade tare, suna kuma girma kamar haikali cikin Ubangiji. 22A cikinsa ne kuma ake gina ku gaba daya kun zama mazaunin Allah a cikin Ruhu.
Bulus ya tunashe masubi game da rayuwar su na da kuma yadda suke a gaban Allah yanzu.
Wannan ya nuna yadda mutane masu zunubi sun kasa yin biyaya ga Allah ta haka mutattcen mutum ba ya iya ji ta jiki.
Kalmar "laifofin" da kuma "zunuban" na da ma'ana kusan iri ɗaya. Bulus ya yi amfani da su ne domin ya nanata girman zunuban mutanen.
Manzanni sun kuma yi amfani da "duniya" don nufin halin son kai da daraja mari kirki na mutanen da su ke rayuwa a wannan duniya. AT: "bisa darajan mutane da ke rayuwa a wannan duniya" kokuwa "bin ƙa'idodi na wannan duniya"
Wannan na nufin ibilis ko kuwa shaiɗan.
"ruhun shaɗan, da ke aiki"
Kalmar "jiki" da kuma "zuciya" na misali da dukan mutum.
mutanen da Allah ke fushi da su
"Allah mai yawan jinkai ne" ko "Allah na da kirki domin mu"
"sabili da matuƙar ƙauna domin mu" ko "saboda ya na ƙaunar mu sosai"
Wannan ya nu yanda mutum mai zunubi ya kasa yin biyaya ga Allah sai an bashi sabuwan rai ta ruhaniya kamar mutatcen mutum da ba ya iya ji ta jiki sai dai an tashe shi daga mattatu.
"cikin Almasihu" da magana kusan iri guda ne da ke baya nufin ainahin abun da ke faru sosai a cikin wasikun Sabon Alkawari. Su na magana akan irin karfin ɗangantaka mai yiwuwa tsakanin Almasihu da waɗanda sun gaskanta da shi.
Ana iya bayana wannan cikin sifar aiki. AT: "Allah ya cece mu saboda yawan kirkin sa gare mu"
kaman yada ya tashe Almasihu, zai daga mu sama ma, kuma za mu kasance da Almasihu a sama.
"cikin bisa halittar duniya." Kalmar "sama" na nufin wurin da Allah yake. Dubi yadda an fasara a cikin 1:3.
"cikin Almasihu Yesu" da magana kusan iri guda ne da ke baya nufin ainahin abun da ke faru sosai a cikin wasikun Sabon Alkawari. Su na magana akan irin karfin ɗangantaka da ke tsakanin Almasihu da waɗanda sun gaskanta da shi.
"nan gaba"
Ƙaunar Allah gare mu ne dalilin da ya sa shi ya mun tsira daga hukunci idan mun gaskanta da Yesu. AT: "Allah ya cece ku ta alheri saboda bangaskiyar ku a cikinsa"
Kalmar "wannan" na nufin baya zuwa "wannan ceto bai zo saboda kyaun abubuwan da kun yi ba"ta alheri aka ceceku ta wurin bangaskiya."
"wannan ceto bai zo saboda kyaun abubuwan da kun yi ba"
"cikin Almasihu Yesu" da magana kusan iri guda ne da ke baya nufin ainahin abun da ke faru sosai a cikin wasikun Sabon Alkawari. Su na magana akan irin karfin ɗangantaka mai yu'a tsakanin Almasihu da waɗanda sun gaskanta da shi.
"bi" ko kuwa "yi" (UDB)
Bulus ya tunashar da waɗannan masubi cewa yanzu Allah ya yi Al'ummai da Yahudawa cikin jiki ɗaya ta wurin Almasihu da giciyan sa.
Wannan na nufin mutanen da ba haifafar Yahudawa ba.
Waɗanda ba mutanen Yahudawaba ba su yi kaciya kamar yara kuma don haka Yahudawa sun dauke su mutanen da ba sua bin dokokin Allah AT: "kafiri marasa kaciya"
Wannan wata ka'ida ne na mutanen Yahudawa saboda dukan jinjiraye maza ana yin masu kaciya lokacin da an haife su da kuwana 8. AT: "mutanen da an yi masu kaciya"
"marasabi"
Ma'anan na kamar 1) "Yahudawa, wanda an yi masu kaciya ta mutane" ko 2) "Yahudawa, wanda sun yi ma jikin jiki kaciya."
Ana iya bayana wannan a cikin aiki. AT: "ta abun da mutane ke kira" "ta waɗanda mutane ke kira"
Bulus ya yi wa Al'ummai masubi magana kamar su baki ne, an aje a wajen kasar wa'adodin Allah da kuma al'kawari.
Bulus ya sa alamar nuna bambanci tsakanin Afisawa kamin su yarda da Almasihu kuma bayan sun yarda da Yesu.
Saboda zunuban masubi, an raɓa su daga Allah. Ƙodashiƙe, yanzu Yesu ya kawo su kusa da Allah ta wurin jinin sa.
Jinin Almasihu na nuna mutuwar sa. AT: "ta mutuwar Almasihu" ko kuwa "lokacin da Almasihu ya mutu domin mu"
"Yesu ke bamu salama"
"ya mai da Yahudawa da Al'ummai ɗaya"
"Ta mutuwar jikin sa a kan giciye"
"katangar kiyayya" ko kuwa "katangar mugun nufi"
Kalmar "mu" na nufin Bulus da Afisawan. Su Al'umman an raɓa su daga Yahudawan. AT: "Wancan ya raɓa mu Yahudawa daga Al'ummai daga junan mu"
Jinin Yesu ya biya buƙatar shari'a na Musa saboda duka Yahudawa da Al'ummai su iya zaman salama a cikin Allah.
gudan saban mutane, mutanen ceton 'yan adam duka
Haɗuwa ne da Almasihu ya sa sulhu mai yiwuwa tsakanin Yahudawa da Al'ummai.
"Almasihu ya kawo Yahudawa da Al'ummai tare a cikin salama"
Gicciye anan na nuna mutuwar Almasihu a bisa gicciye. AT: "ta wurin mutuwar Almasihu a bisa gicciye"
An bayyana daina gabar su kamar ya kashe gabar su. Ta mutuwar sa a bisa gicciye Yesu ya cire dalilin da Yahudawa da Al'ummai za su yi gãba da juna. Ko yanzu ya kamata su yi rayuwa ta shari'a na Musa. AT: "hana su daga ƙiyayya da juna"
Bulus na faɗa wa masubi na Afisus cewa masubi na Al'ummai da ke nan sun zama ɗaya tare da manzanen Yahudawa da anabawa; su ne haikali na Allah a cikin Ruhu.
"sanar da bishara na salama" kokuwa "furta bishara na salama"
Wannan na nufin Al'ummai ko kuwa waɗanda ba Yahudawa ba.
Wannan na nufin Yahudawa.
Anan"mu biyu" na nufin Bulus, Yahudawa masubi, da masubi da ba Yahudawa ba.
Dukan masubi, da Yahudawa da Al'ummai, an basu yanci su zo gaban Allah Uba ta Ruhu mai Tsarkin nan ɗaya.
Bulus yana kuma magana game da yanayin ruhaniyar Al'ummain bayan sun zama masubi kaman yadda zai yi magana akan baƙi yadda za su zama 'yan gari na kasa dabam.
Bulus ya yi magana akan mutanen Allah kaman sun zama gini. Almasihu ne shi ne mafificin dutsen ginin, manzane ne tushe, kuma masubin ne abin da an kafa.
Ana iya bayana shi cikin sifar aiki. AT: "Allah ya riga ya gina ku" (Dubi:
Bulus ya cigaba da magana akan iyalin Almasihu kamar gini ce. Yanda mai gini na kafa dutse tare a yin gini, haka ne Almasihu yana kafa mu tare.
"a cikin Almasihu ... a cikin Almasihu Yesu ... a cikin Almasihu "Wannan zancen kwatanacin na nanata irin karfin ɗangantaka da ke tsakanin Almasihu da waɗanda sun gaskanta da shi.
Wannan na kwatanta yanda ana hada masubi tare don su zama wurin da Allah zai yi zaman dawama ta wurin iƙon Ruhu mai Tsarki.
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "Allah na kuma gina ku tare"
1Saboda haka, ni Bulus, dan sarka sabili da Almasihu dominku al'ummai. 2Ina zaton kun ji a kan aiki mai girma na alherin Allah da ya ba ni dominku.3Ina rubuto maku bisa ga wahayin da aka sanashe ni. Wannan ita ce boyayyar gaskiya da na rubuta a takaice a cikin wata wasikar. 4Sa'adda kuka karanta a kan wannan, za ku iya fahimtar basira ta cikin boyayyar gaskiya a kan Almasihu. 5Wanda a zamanun da ba a bayyana wa mutane ba. Amma yanzu an bayyana shi ga manzanni da annabawa kebabbu a cikin Ruhu.6Wannan boyayyar bishara ita ce al'ummai ma abokan gado ne tare da mu, gabobi ne cikin jiki daya. Abokan tarayya ne kuma cikin alkawaran Almasihu Yesu ta wurin bishara. 7Domin wannan na zama bawa ta wurin baiwar alherin Allah da ya bani ta wurin karfin ikonsa.8Allah ne ya ba ni wannan baiwa. Ko da shike nine mafi kankanta cikin kebabbun Allah, in yi shelar bishara ga al'ummai akan wadatar Almasihu marar matuka. 9In kuma fahimtar da dukan mutane a kan shirin Allah, wannan boyayyar gaskiya wadda tun zamanai da suka wuce Allah ya boye, shi da ke mahallicin dukan abubuwa.10Saboda haka, ta wurin ikilisiya, masu iko da masu mulkin sararin sama za su san hikimar Allah ta fuskoki daban daban. 11Wannan ya kasance bisa ga dawwamammen nufi da ya zartar cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu.12Gama a cikin Almasihu muna da gabagadi, da dama, da amincewa sabili da gaskiyar mu a cikinsa. 13Saboda haka ina rokon ku kada ku karaya da wahalar da na sha domin ku wadda ta zama daukakar ku.14Saboda haka nake durkusawa da gwiwa ta a gaban Uba, 15wanda ta wurinsa ake kiran kowanne iyali na sama da na kasa. 16Ina addu'a ya amince maku bisa ga yalwar wadatar daukakarsa, ku karfafa matuka da iko ta wurin Ruhunsa, da yake cikinku.17Ina addu'a Almasihu ya zauna a cikin zuciyar ku ta wurin bangaskiya. Ina kuma addu'a ku kafu ku kuma ginu da zurfi kwarai cikin kaunarsa. 18Ku kasance cikin kaunarsa domin ku gane, tare da dukan masu bi, menene zurfi, da fadi, da tsawon kaunar Almasihu. 19Ina addu'a domin ku san mafificiyar kaunar Almasihu da ta wuce sani. Ku yi wannan domin a cika ku da dukan cikar Allah.20Yanzu ga wanda yake da ikon aikata dukan abu fiye da abin da muke roko ko tunani, bisa ga ikonsa da ke aiki a cikinmu, 21daukaka ta tabbata a gare shi a cikin ikilisiya ta wurin Almasihu Yesu har ya zuwa zamanun zamanai har abada abadin. Amin.
Domin a bayyana wa masubi boyayyen gaskiya game da ikilisiya, Bulus na nufin ɗayantaka na Yahudawa da Al'ummai da kuma haikali wanda yanzu masubi na ciki.
"Saboda alherin Allah gare ku"
"wanda Almasihu Yesu ya sa a sarka"
"alhakin da Allah ya bani na kawo alherin sa gare ku"
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "bisa ga abinn da Allah ya bayyana mani"
Bulus na nufin wani wasikar da ya rubuta wa waɗanan mutane.
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "Allah bai bayyana waɗannan abubuwan wa mutane a zamanin da ya wuce ba"
Ana iya bayyana wannan cikin sifar aiki. AT: "Amma yanzu Ruhu ya bayyana shi" ko "Amma yanzu Ruhu ya sa ya zama sananne"
"manzanni da annabawa wanda Allah ya keɓe su domin su yi wannan aiki"
Wannan ne boyayyen gaskiya da Bulus ya fara bayyanawa a cikin sura na baya. Al'ummai da su ka karɓi Almasihu sun kuma karɓi abu iri guda da Yahudawa masubi.
sau da yawa ikilisiya na nufin jikin Almasihu.
"cikin Almasihu Yesu" da makamanin waɗannan karin magana sun auku sau da dama a wasikun Sabon Alkawari. Sun yi magana ne ƙwarai akan ɗangantaka da ke yiwuwa tsakanin Almasihu da waɗanda suka yarda da shi.
suna iya nufin1) saboda bisharar da Al'ummai suna masu rabo a cikin alkawarin 2) saboda bishara da Al'ummai suna masu gãdo da gabobi na jiki da kuma masu rabo a cikin alkawarin.
"waɗanda Allah ya keɓe wa kansa"
wanda bai iya sani gabadaya ba
Bulus ya yi magana game da gaskiya akan Almasihu da kuma albarkun da yake kawo kamar kayan wadata.
Fahimtar da mutane na wakilin koyar da su. AT: "haskakka haske a kan boyayyen shirin Allah don dukan mutane su sani abun da yake" ko "koyar da dukan mutane abin da boyayyen shirin Allah yake"
Ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. "Allah da ya hallici dukan abubuwa, ya aje wannan boyayyar shirin tun da dadewa a zamanin da suka wuce"
hikimar Allah ta fuskoki daban daban-"Allah zai sa baban hikimar sa ya zama sananne ga dukan masu iƙo da mulkin sararin sama ta wurin ikilisiya"
Kalmomin nan na da ma'ana kusan iri ɗaya. Bulus ya yi amfani da su ne don ya nanata cewa kowane rai na ruhaniya zai san hikimar Allah.
"cikin duniyan da ta wuce na ɗan'adam." Kalmar "sararin" na nufin wurin da Allah yake. Dubi yanda an fasara a 1:3.
hikimar Allah ta fuskoki daban daban- hikimar Allah mai wuyan ganewa
"cikin riƙen dawwamammen nufin" ko kuwa "daidaitawar dawwamammen nufi"
Bulus ya yabe Allah a cikin wahaloli ya kuma yi adu'a domin wannan masubi na Afisus.
"bamu da tsoro" ko kuwa "muna da karfin zuciya"
"dama cikin gaban Allah da amincewa" kokuwa "yancin shiga cikin gaban Allah da amincewa"
yaƙini" kokuwa "tabbaci"
A nan "ɗaukaka" na kwatanta takama wanda za su ji ko za su ji a mulki mai zuwa. Masubi na Ephesus su yi takama akan abun da Bulus ke shan wahala a sarka. AT: "Saboda da anfanin ku" ko "yakamata ku yi takama akan wannan"
"Saboda Allah ya yi dukan wannan wa ni"
Durkusawar gwiwa hoto ne na dukan mutum a cikin halin adu'a. AT: "Ina durkusa a cikin adu'a wa Uba" ko "Ina addu'a da kasƙanta wa Uba"
Yin suna anan halamane kuma wakilin yin halicci. AT: "wanda ya yi halitta da kuma yin sunan kowane iyali a sama da kasa"
"Allah, domin shi mai girma da kuma mai iƙo, zai yarda maku ku zama da karfi da iƙonsa"
"zai baku"
Bulus ya cigaba da addu'ar da ya fara a cikin 3:14.
Wannan ne abu na biyu wanda Bulus ya yi addu'a cewa Allah zai "biya" su Afisawan "bisa ga bisa ga yalwar wadatar na iƙon sa"; na farko shi ne za su "karfafu" (3:14).
A nan "zuciya" na misali da cikin mutum, da kuma "ta wurin" na fada hanyar yadda Almasihu na rayuwa a cikin maibi. Almasihu na rayuwa a cikin zuciyar masubi saboda Allah ta alherinsa ya yarda su sumu bangaskiya.
Ma'anar na kamar 1) "bangaskiya. Ina adu'a ku kafu ku kuma ginu da zurfi ƙwarai cikin ƙaunarsa domin ku gane" kokuwa 2) "bangaskiya don ku ginu da zurfi kwarai cikin ƙaunarsa. Ina addu'a ku gane"
Bulus yana magana game da bangaskyar su kamar itace dake da saiwa mai zuifi ko kuwa gida da a ka gina ta a tushe mai kauri. AT: "saboda ku zama kamar itace da saiwar sa mai zuifi ne da karfi da kuma gini da aka gina a kan dutse"
Wannan ne na biu da Bulus ya durkusar da gwiwar sa a addu'a; na farko shi ne, saboda Almasihu ya biya da kuma su suma karfafawa (3:14) kuma Almasihu ya yi rayuwa a cikin zukatar su ta wurin bangaskiya (3:14). Kuma "gane" shi ne farkon abu da Bulus ya yi addu'a cewa Afisawan dakansu su iya yi.
"dukan masubi a cikin Almasihu" ko kuwa "dukan tsattsarka"
Ma'anar na kamar 1) Wannan kalma na kwatanta girman hikimar Allah, AT: "yadda kowane Allah mai wayo yake" ko 2) wannan kalma na kwatanta ƙauna mai tsanani da Almasihu ke da shi domin mu. AT: "nawa Almasihu yake ƙaunar mu"
Wannan ne abu na biyu da Bulus ya yi addu'a saboda Afisawa su iya yi; na farko shi ne su "gane." AT: " saboda ku san girman hikimar ƙaunar Almasihu domin mu"
Wannan ne abu na uku da Bulus ya durkusa da gwiwan sa ya yi addu'a (3:14); na farko shi ne su "karfafa" (3:14), kuma na biyu shi ne su "iya gane" (3:18).
Bulus ya gama addu'a sa da albarka.
Kalmar "muke" ko "mu" a cikin wannan littafin ya sa ciki dukan Bulus da dukan masubi.
"Yanzu ga Allah, wanda"
Allah na iya yin fiye da muke roƙo, ko tunani.
1Saboda haka a matsayi na na dan sarka saboda Ubangiji; ina rokon ku ku yi zaman rayuwa da ta cancanci kiran da Allah ya kiraye ku. 2Ku zamna da matukar tawali'u da sahihanci da hakuri. Ku karbi juna cikin kauna. 3Ku yi kokarin zaman dayantaka cikin Ruhu kuna hade cikin salama.4Akwai jiki daya da kuma Ruhu daya, kamar yadda aka kira ku a kan begen nan daya. 5Ubangiji daya, bangaskiya daya, da kuma baftisma daya. 6Allah daya ne da Uban duka. Shine bisa duka, ta wurin duka, da kuma cikin duka.7Ko wannenmu an ba shi baiwa bisa ga awon baiwar Almasihu. 8Kamar yadda nassi ya ce, "Da ya haye zuwa cikin sama, ya bi da bayi cikin bauta. Ya kuma yi wa mutane baye baye.9Menene ma'anar, "Ya hau?" Ana cewa kenan ya sauka har cikin zurfin kasa. 10Shi da ya sauka shine kuma wanda ya hau birbishin sammai. Ya yi wannan domin ya cika dukan abubuwa.11Almasihu ya ba da baye baye kamar haka: manzanni, annabawa, masu shelar bishara, makiyaya, da masu koyarwa. 12Ya yi haka domin ya shiryar da masu bi saboda hidima, domin gina jikin Almasihu. 13Ya yi haka har sai mun kai dayantakar bangaskiya da sanin Dan Allah. Ya yi haka har sai mun kai ga manyanta, kamar wadanda suka kai cikakken matsayin nan na falalar Almasihu.14Wannan ya zamanto haka domin kada mu kara zama kamar yara. Kada a yi ta juya mu. Wannan haka yake domin kada mu biye wa iskar kowacce koyarwa ta makirci da wayon mutane masu hikimar yin karya. 15Maimakon haka za mu fadi gaskiya cikin kauna domin mu yi girma cikin dukan tafarkun da ke na sa, shi da yake shugaba, Almasihu. 16Almsihu ya hada dukan jikin masu ba da gaskiya. Jikin yana hade ta wurin kowanne gaba, domin jikin ya yi girma ya gina kansa cikin kauna.17Saboda haka ina yi maku gargadi cikin Ubangiji cewa, kada ku sake yin rayuwa irin ta al'ummai da suke yi cikin azancin wofi marar amfani. 18Sun duhunta cikin tunaninsu. Bare suke da rai irin na Allah, ta wurin jahilcin da ke cikinsu da ta wurin taurare zukatansu. 19Basa jin kunya. Sun mika kansu ga mutumtaka ta yin kazamtattun ayyuka da kowacce zari.20Amma ba haka kuka koyi al'amuran Almasihu ba. 21Ina zaton kun rigaya kun ji a kansa. Ina zaton an koyar da ku cikinsa, kamar yadda gaskiyar Yesu ta ke. 22Dole ku yarda halin ku na da, wato tsohon mutum. Tsohon mutumin ne ya ke lalacewa ta wurin mugun buri.23Ku yarda tsohon mutum domin a sabonta ku cikin ruhun lamirinku. 24Ku yi haka domin ku yafa sabon mutum, mai kamanin Allah. An hallitta shi cikin adalci da tsarki da gaskiya.25Saboda haka ku watsar da karya. "Fadi gaskiya ga makwabcin ka", domin mu gabobin juna ne. 26"Ku yi fushi, amma kada ku yi zunubi." Kada ku bari rana ta fadi kuna kan fushi. 27Kada ku ba shaidan wata kofa.28Duk mai yin sata, kada ya kara yin sata kuma. Maimakon haka, ya yi aiki. Ya yi aiki da hannuwan sa domin ya sami abin da zai taimaka wa gajiyayyu. 29Kada rubabbun maganganu su fito daga cikin bakinku. Maimakon haka, sai ingantattu da za su ba da alheri ga masu ji. 30Kada ku bata wa Ruhu Mai Tsarki na Allah rai domin ta wurin sa ne aka hatimce ku domin ranar fansa.31Sai ku watsar da dukan dacin rai, da hasala, da fushi, da tankiya, da reni tare da dukan mugunta. 32Ku yi wa juna kirki, ku zama da taushin zuciya. Ku yafe wa juna, kamar yadda Allah cikin Almasihu ya gafarta maku.
Saboda abin da Bulus ya yi ta rubuta wa Afisawa, ya fada wa masubi yadda za su yi zaman rayuwan su a matsayin masubi kuma ya nanata cewa masubi su yarda da junansu.
"kamar wani da yake sarka saboda zaɓin sa domin ya bauta wa Ubangiji"
Zama na kaman hayar da aka saba nanata ra'ayin na zaman rayuwa.
"ku zama masu tawali'u, masu hankali, da hakuri"
"ku biɗa zaman tare a cikin salama domin ku kula da ɗayantaka cikin Ruhu"
sau da yawa ikilisiya na nufin jikin Almasihu.
"Ruhu mai Tsarki ɗaya kadai" (UDB)
"Allah ya kira ku domin ku sami amincewa da bege a kiran ku" ko "akwai abu daya da Allah ya zaɓe ku ku amince a ciki kuma ku sa rai ya yi"
Kalmar "duka" anan na nufin "kome da kome."
Bulus na tunashe da masubi akan kyautar da Almasihu ya ba masubi domin su yi amfani da shi a cikin ikilisiya, wanda shi ne dukan jikin masubi.
Maganar anan na daga wakan da sarki Dauda ya rubuta.
Ana iya bayana a cikin aiki. AT: "Allah ya bayar da alheri ga kowanen mu" ko "Allah ya bayar da kyauta ga kowane maibi"
"lokacin da Almasihu ya je cikin sama"
"Almasihu ya je sama"
"Almasihu ya kuma wuce kasa"
su na iya nufin1) zurfin kasa na sashin kasa kokuwa 2) "zurfin sashen" wani hanya ne na nufin kasa." AT: "cikin zurfin sashen, kasan."
"domin ya kasance a ko ina a cikin iƙonsa"
"kammala" kokuwa "biya bukata"
ana iya bayana wanda Almasihu ya bayar da kyautan ba shakka. AT: "Almasihu ya bayar da waɗannan ofisoshin ga ikilisiya" ko "Ya ba mutane wannan alhakin ga ikilisiya
"ya shiryar mutanen da ya keɓe" ko kuwa "ya tanada wa masubi"
"domin su iya yi ma waɗansu hidima"
Bulus na maganar mutanen da suke girma a ruhania kamar suna motsa jiki don su kara karfin motsar jikin su.
"ƙarin kyau"
"jikin Almasihu" na nufin ga dukan mutumin membobi na ikilisiyar Kristi.
Ya kamata masubi su san Yesu a matsayin Ɗan Allah idan sun hadu a bangaskiya da girma a matsayin masubi.
"zama daidai da karfi a bangaskiya" ko "zama tare a cikin bangaskiya."
Wannan mahimmin suna ne wa Yesu.
"kai ga manyantar masubi"
"cikaken girma," "yi girma," ko "cikakke"
Bulus na nufin masubi wanda basu yi girma a cikin ruhaniya kamar su zama yaran da sun samu ji kadan a rayuwa. AT: "zama kaman yara"
Wannan na maganar mai bi da bai manyanta ba kuma na bin koyarwa da ba daidai ba kaman maibin ya zama kwalekwalen da iska ke bugawa a kowane waje a ruwa.
"ta mutane masu wayo da suke da dabara ga masubi da fasahar karya"
Bulus ya yi amfani da jikin mutum ya bayana yanda Almasihu ya sa masubi su yi aiki tare a cikin jituwa kaman yanda kan jiki yake sa gabobin jiki su yi aiki tare don su yi girma da kyau.
"jijiya" ɗauri ne mai karfi dake haɗa kasusuwa ko kuwa gabobin cikin wurin jikin.
"yanda membobin suna ƙaunan juna"
Bulus ya fada masu abun da kar su yi dashiƙe yanzu da su masubi an hatimce su da Ruhu mai Tsarki na Allah.
"Domin abun da na ce, zan fada wani abu mafi karfi don in karfafa ku domin mu duka na Yesu ne"
Tafiya na nuna yanda mutane suna rayuwar su. AT: "daina rayuwa kamar Al'ummai da banzan tunani"
Ba sua tsammani ko tunani da kyau. AT: "sun duhunta tunanin su" kokuwa "Ba su iya ganewa ba"
Ana iya bayana wanan cikin sifar aiki. AT: "Domin ba su san Allah ba, ba za su iya yin rayuwa yanda Allah yake son mutanen sa su yi rayuwa ba." ko "Sun cire kansu daga rai na Allah ta wurin jahilcinsu"
"yanke" ko kuwa "raɓa"
"rashin sani" kokuwa "rashin labari"
Sun ki su saurare Allah su kuma bi koyarwan sa.
Bulus na magana a kan mutanen nan kamar su abu ne da su da kansu aka ba waɗansu mutane, kuma ya yi magana game da yanda suke so su biya bukatar jikin su kaman mutumin ne wanda sun mika kansu. AT: "su na so su biya bukatan jikinsu kadai"
Kalmar "amma" na nufin yanda Al'umai su ke zama, kamar yanda an kwatanta a cikin 4:17. Wannan na nanata cewa abun da masubi suka koya akan Almasihu akasi ne. AT: "Amma abun da kun koya daga Almasihu ba haka bane"
Bulus ya sani cewa Afisawa sun ji kuma sun koya.
sunna iya nufin 1) "mutanin Yesu sun koya maku" ko 2) "wani ya koya maku domin ku mutanin' Yesu."
"yadda komai game Yesu gaskiya ne"
Bulus na magana game da kyauwawan hali kaman sun zama gutsuren tufafi. AT: "domin ku daina rayuwa yadda kuke rayuwa a da"
Bulus na magana game da kyauwawan hali kaman sun zama gutsuren tufafi. AT: "domin ku daina rayuwa ku ta da"
" tsohon mutumin" na nufin "tsohon hali" ko "hali na da."
Bulus ya yi magana akan tsohon halitar mutum kamar mutaccen jiki dake sokawa zawa cikin kabarin sa .
Ana iya bayana a cikin aikin. AT: "domin ku yarda Allah ya sake halin ku da tunanin ku" ko kuwa "domin ku yarda Allah ya baku sabon hali da tunani"
Bulus na magana game da taƙaitaccen darasi kaman su zama gutsuren tufafi. AT: "domin ku yi sabon rayuwa, da aka hallita bisa ga kamannin Allah" ko "domin ku fara rayuwa a cikin sabon hanya da saboda an hallice ku bisa ga kamannin Allah"
"gaskiyar adalci da tsarki"
"ku daina fadin karya"
"mun zama na junan" ko "mu yan gidan Allah ne"
"za ku iya yin fushi, ama kadda ku yi zunubi" ko kuwa "idan kun yi fushi, kadda ku yi zunubi"
"Dole ne ku daina yin fushi kafin dare" ko "Kadda fushin ku ya kai tsawon lokaci"
"Kada ku ba shaidan wata kofa ya kai ku ga zunubi"
Wannan na nufin magana da ke mara tausayi ko mara ladabi.
"domin karfafa juna" ko "domin karfawan juna"
"bukatar su. A haka kuwa za ku taimake waɗanda sun ji ku"
"kada ku tsananta" ko "kadda ku tar da hankalinku"
Ruhu ma Tsarki ya yi wa masubi alkawari cewa Allah zai fanshe su. Bulus na magana game da Ruhu mai Tsarki kamar shi ne alama da Allah ya sa wa masubi domin ya nuna cewa nashi ne. AT: "domin shi ne hatimi da ya tabatar da cewa Allah zai fanshe ku a ranar fansa" ko "domin shi ne ya tabatar cewa Allah ne zai fanshe ku a ranar fansa" ko
Bulus ya gama da umurnin sa game da abinda bai kamata masubi su yi ba ya kuma kare da abun da dole ne su yi.
sunna iya nufin 1) dole ne ku yi shi da kanka ko 2) "dole ne ku yadda Allah ya dauke"
"daina jin fushi akan mugun abubuwa da waɗansu su yi ma ku"
lokacin zafin fushi
taƙaitaccen darasin ajali na fushi
"maimako, dole ne ku yi kirki"
"ladabi" ko "cike da tausayi"
1Saboda haka ku zama masu koyi da Allah, kamar kaunatattun 'ya'yansa. 2Ku yi zama cikin kauna kamar yadda Almasihu ya kaunace mu, ya kuma mika kansa sadaka da hadaya ga Allah dominmu, hadaya mai kanshi abin karba ga Allah.3Fasikanci ko kowacce irin kazamta, ko kazamar lalata kada a ambace su a tsakaninku, don haka ya dace ga masu bi. 4Kada a ambaci batsa, maganar wauta ko alfasha wadanda ba su dace ba. Maimakon haka, mu zama masu godiya.5Domin wannan kun sani cewa ba fasiki, ko mara tsarki, ko mai hadama wato mai bautar gumaka zai sami gado cikin mulkin Almasihu da Allah. 6Kada kowa ya rude ku da maganganun wofi. Saboda wadannan abubuwa ne fushin Allah ke zuwa kan kangararrun 'ya'ya. 7Kada ku yi tarayya tare da su.8Domin da ku duhu ne, amma yanzu ku haske ne cikin Ubangiji. Sai ku yi tafiya kamar 'ya'yan haske. 9Saboda amfanin haske shine dukan alheri, adalci da gaskiya. 10Kuna bidar abin da Ubangiji ke murna da shi. 11Kada ku sa hannu ga ayyuka marasa amfani da ayyukan duhu amma gara a tone su. 12Don abubuwan da suke yi a boye abin kunya ne a bayyana su.13Dukan abu, idan haske ya bayyana su, za a gan su. 14Domin duk abin da aka bayyana ya zama haske. Saboda haka aka ce, "Ka farka, kai mai barci, ka tashi daga cikin matattu; Almasihu kuwa zai haskaka bisanka".15Saboda haka, ku maida hankali yadda kuke rayuwar ku, ba kamar mutane marasa hikima ba amma kamar masu hikima. 16Ku yi lura yadda kuke amfani da lokaci don kwanakin miyagu ne. 17Kada ku zama wawaye. Maimakon haka, ku fahimci ko menene nufin Ubangiji.18Kuma Kada ku bugu da ruwan inabi, don yana iya lalata rayuwa. Maimakon haka, ku cika da Ruhu Mai Tsarki. 19Kuna magana da junanku cikin zabura da wakoki da wakokin ruhaniya, kuna rairawa da yabo da zuciyarku ga Ubangiji. 20Kullum kuna ba da gaskiya domin dukan abubuwa cikin sunan Ubangiji Yesu ga Allah Uba. 21Kuna sarayadda kanku ga juna cikin girmama Almasihu.22Mata, ku yi biyayya ga mazan ku kamar ga Ubangiji. 23Domin miji shine shugaban matarsa kamar yadda Almasihu yake shugaban ikilisiya. Shine kuma mai ceton jiki. 24Amma kamar yadda ikilisiya take biyayya ga Almasihu, haka kuma dole mata suyi ga mazajen su cikin kowanne abu.25Mazaje, ku kaunaci matanku kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya har ya ba da kansa dominta, 26Ya yi wannan domin ya tsarkake ta. Ya wanke mu da ruwan wanki ta wurin kalma. 27Ya yi wannan domin ya mika ma kansa ikilisiya mai daraja, ba tare da tabo ko cikas ko wani abu kamar wadannan, amma ta zama da tsarki da kuma mara aibi.28Hakannan kuma, mazaje su kaunaci matansu kamar jikunnansu. Wanda yake kaunar matarsa yana kaunar kansa. 29Ba wanda ya taba kin jikinsa. Amma, yakan ciyadda shi yana kaunarsa, kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya. 30Domin mu gabobin jikinsa ne.31"Domin wannan mutum zai rabu da ubansa da uwarsa ya manne wa matarsa, su biyu su zama nama daya". 32Wannan asirin gaskiyar, da girma yake, amma ina magana ne game da Almasihu da ikilisiyarsa. 33Duk da haka, kowannenku dole ya kaunaci matarsa kamar kansa, matar kuma dole ta girmama mijinta.
Bulus ya cigaba da faɗa wa masubi yadda ya kamata su yi rayuwa da kuma yadda bai kamata su su yi rayuwa ba a matasyinsu na 'ya'yan Allah.
"Saboda haka ku yi abinda Allah ya yi." Saboda da haka na maida zuwa 4:31 wadda na magana akan dalilin da masubi su yi koyi da Allah, domin Almasihu ya yafe wa masubi.
Allah na so mu yi koyi ko mu bi shi da shiƙe mu 'ya'yansa ne. AT: "kamar 'yadda ƙaunatattu 'ya'ya suna ƙaunar ubanninsu" ko "domin ku 'ya'yan sa ne kuma yana ƙaunar ku sosai"
Wato yadda mutum ke rayuwa. AT: "yi zaman rayuwa na ƙauna"
"Bayaswa da hadaya kamar kamshi mai daɗi zuwa ga Allah"
"kada ku yi wani abu da mutane za su yi tunani kuna da zunubin faskanci ko wani kazanta ko hadama"
"wani halin kirki mara kazanta"
"maimako ku gode wa Allah"
Karɓan abinda Allah ya alkawatar wa masubi ne an yi maganasa kamar wata kayan gãdo da dukiya daga cikin iyali.
kalamai da ba gaskiya a cikin su
Kamar yanda mutum baya iya gani a duhu ba, haka ne mutanen da suke kaunan zunubi sun rasa fahimta na ruhaniya.
Kamar yadda mutum yake gani a haske, haka mutane da Allah ya cece su suke gani yadda za su gamshe Allah.
"yi rayuwa kamar mutane da suka fahimta abinda Allah yake so su yi"
Kamar yadda iche mai lafiya ke ba da 'ya'ya kyawawa, mai bi zai yi abinda ke da kyau, a yi abubuwan adalci da Allah ke so da shi yi yi, da yin kalmomin na gaskiya.
Bulus ya yi maganan rashin amfani, ababan zunubi da marabi ke aikatawa kamar aikin shaidan da mutane ke yi a duhu da ba ba wanda zai gan su. AT: "Kada ku yi ayuka mara amfani, ayukan zunubi da marasa bi"
ayukan da ba su yin abu mai kyau, mai amfani, ko mai riɓa
"a kawo su zuwa ga haske" ko kuwa "a tuɓe su" ko "a nuna a kuma gaya wa mutane yadda waɗanan ayukan mara kyau ne"
Yana a ɓoye idan wanan rubutu yana a haɗe da rubutu daga anabi Ishaya ko rubutu ne daga wakar da masubi sun yi.
"mutane na iya gani sarai dukan abinda ya zo wurin haske."Wannan na kwatanta yadda kalmar Allah na bayana yadda ayukan mutane ke da kyau ko mumuna, ku fasara shi a yanda yake.
Ma'anan su na kamar 1) Bulus na magana ne da marasabi wadda ya kamata su farka daga matattu na ruhaniya yadda dole ne mutum da ya mutu ya rayu kuma domin ya ji, kokuwa 2) Bulus yana magana da masubi na Afisus da ya yi amfani da mutuwa ya kwatanta raunanar ruhaniyarsu.
Wannan yanayin na "kai" na nufin "mai barci" kuma ɗaya ne.
Almasihu zai taimaka wa marabi ya fahimci yanda mugun ayukansa yake da yanda Almasihu zai yafe shi ya kuma bashi sabon rai, kaman yanda haske na bayana yanda abu yake a cikin duhu.
Marasa hikima ba sua yin lura da kansu game da zunubi ba. Ko dashiƙe masu hikima na iya gane zunubi su kuma gudu daga ita. AT: "A hakan dole ne ku yi hankali domin ku yi zama kamar mutum mai hikima ba kaman mara hikima ba"
"ku yi abu mafi muhiminci da lokacin ku," "yi amfani da lokaci da wayo," ko "Sa lokaci domin yin abinda ya fi"
Kalmar "kwanaki" na kwatancin abinda mutane ke yi a wancen kwanaki. AT: "domin mutane da na kewaye da ku na yin dukan mumunan abubuwa"
Bulus ya kare da ka'idodin sa a yadda dukan masubi za su yi rayuwa.
"Da kada ku bugu daga shan ruwan inabi"
"Maimakon Ruhu mai Tsarki ya bi da ku"
Ma'anar su kamar yanda 1) Bulus ya yi amfani da waɗanan kalamai kamar kwatanci ne na "dukan irin waƙoƙin yabon Allah" ko 2) Bulus yana lissafta yanayin waka ta masamman.
Ma'anar su kamar yanda 1) yanda aka rubuta a littafin Zabura ko 2) kowane wakar yabo.
waka da ya ke ɗaukaka Uban ko Ɗansa
Ma'anar su kamar yanda 1) wannan waƙoƙi ne game da Allah kokuwa 2) wannan waƙoƙi ne da Ruhu Mai Tsarki ya bayer kokuwa 3) wannan kalmar daya ne da "waƙoƙi" kuma ba ya neman bambanta kalma.
Bulus ya fara da bayana yadda masubi za su yi biyayya da juna (5:18). Ya fara da umurni wa mataye da mazaje akan yanda za su yi rayua da junan su.
Kalmar "shugaban" yana wakilcin shugaba.
A nan kalmar " kansa" da "Ya" na nufin Almasihui. Kalmar "ta" na nufin ikilisiya.
A nan "ƙauna" na nufin bauta mara son kai ko bayar da ƙauna wa mataye.
"yarda mutane su kashe shi"
sunna iya nufin 1) Bulus na nufin yadda Allah na sa mutanen Almasihu wankaku daga kalman Allah ta baftisma na ruwa a cikin Almasihu ko 2) Bulus ya na cewa Allah ya wanke ruhaniyar mu daga zunubanmu ta wurin kalmar Allah yadda muke wanke jikinmu ta wurin wankewa da ruwa.
Bulus ya na magana akan taron masubi kamar mace ce wadda Yesu zai aura. AT: " domin mu ... yi mu tsarki ... wanke mu"
Bulus ya yi magar ikkilisiya kamar tufafi da an wanke kuma na yanayi mai kyau. Ya yi anfani da wannan ra'ayin a wuri biu domin ya jaddada tsarkin ikkilisiyan.
Maganar "mara kuskure" na nufin asalin abu iri ɗaya kamar "tsarki." Bulus ya yi amfani da biu nan tare domin ya jaddada tsarkin ikklisiya.
Don mutane suna son jikinsu za iya bayana shi a bayyane. AT: "yadda mazaje sunna son jikinsu"
"amma ciyad da"
sunna iya nufin 1) "mu gabagadin jikinsa na masubi" ko 2) masubi sun dace tare su gina jikin Almasihu kamar yadda kashin jikin adam ya ɗace tare su gina mutum.
Ambatawannan na daga rubutun Musa a cikin tsohon alkawari.
Kalmar"ya" da "ya" na nufin namiji maibi wadda ya yi aure.
1'Ya'ya, ku yi biyayya ga iyayenku chikin Ubangiji, domin wannan daidai ne. 2"Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka" (Doka ta fari kenan da alkawari), 3"ta haka za ku yi albarka, domin kwanakinku su yi tsawo a duniya".4Hakanan, ku ubanni kada ku cakuni 'ya'yan ku har su yi fushi, amma ku goye su cikin horon Ubangiji da gargadinsa.5Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya tare da girmamawa da tsoro da zuciya mai gaskiya. Ku yi masu biyayya kamar ga Almasihu. 6Ku yi masu biyayya ba don lallai suna kallonku ba domin ku faranta masu rai. Maimakon haka, ku yi biyayya kamar bayi ga Almasihu. Ku yi nufin Allah daga zuciya. 7Ku yi hidima da dukan zuciya, kamar kuna bautar Ubangiji ba mutane ba. 8Sai ku sani cewa duk abinda mutum ya yi zai karbi sakamako daga wurin Ubangiji, ko shi bawa ne ko 'yantacce.9Ku kuma iyayengiji, ku yi irin wannan ga barorin ku. Kada ku razana su. Kun sani shi wanda ke Ubangijinsu da ku daya ne yana sama. Kun sani tare da shi baya nuna tara.10A karshe, ku karfafa cikin Ubangiji da cikin karfin ikonsa. 11Ku dauki dukan makamai na Allah, domin ku iya dagewa gaba da dabarun shaidan.12Gama yakinmu ba da nama da jini bane. Amma, da ikoki da mulkoki da mahukuntan wannan zamani mai duhu da rundunai masu duhu na mugunta cikin sammai. 13Don haka ku dauki dukan makamai na Allah, domin ku iya tsayawa da karfi cikin muguwar rana. Bayan kun yi komai za ku tsaya da karfi.14Saboda haka ku tsaya da karfi. Ku yi wannan bayan kun yi damara cikin gaskiya kuna yafa sulke na adalci. 15Ku yi wannan bayan kun daure kafafunku da shirin kai bisharar salama. 16Cikin dukan abu ku dauki garkuwar bangaskiya, wadda za ku kashe dukan kibau masu wuta na mugun.17Ku dauki kwalkwalin ceto da takobin Ruhu, wanda shine maganar Allah. 18Tare da kowacce irin addu'a da roko kuna addu'a kullum cikin Ruhu. Da wannan lamiri, kuna tsare wannan da iyakacin kula da dukan juriya da roko saboda dukan masu bi.19Ku yi mani addu'a, domin in karbi sako duk sa'adda na bude bakina. Ku yi addu'a in sami gabagadin bayyana boyayyar gaskiyar bishara. 20Saboda bishara nake jakada cikin sarkoki, yadda a cikinta zan yi magana gabagadi yadda takamata.21Amma domin ku san rayuwa ta, da yadda nake, Tikikus, dan'uwa kaunatacce da amintaccen bawa cikin Ubangiji, zai sanar da ku dukan abu. 22Saboda wannan dalili na aiko shi gare ku, domin ku san al'amuran mu, kuma domin ku sami ta'aziya a zukatan ku.23Bari salama ta kasance tare da 'yan'uwa, kauna da bangaskiya daga wurin Allah Uba da Ubangiji Yesu Almasihu. 24Alheri ya kasance tare da wadannan da suke kaunar Ubangijinmu Yesu Almasihu tare da kauna mara mutuwa.
Bulus ya ci gaba da bayana yanda Almasihu ya kamata su yi biyaya ga juna. Ya bayer da umurni wa 'ya'ya, Ubanni, ma'aikata, da kuma iyayengiji.
Kalmar farko "ku" na nufin abubuwa da yawa. Sai Bulus ya fadi abun da Musa ya ce. Musa na magana da mutanen kamar da mutum ɗaya, "ku" da "ku" na nufin abu ɗaya.
Bulus ya tunasher da 'ya'ya su yi biyaya ga iyayen su.
"kada ku sa 'ya'yan ku fushi" ko " kada ku zama dalilin ''ya'yan ku su yi fushi"
" ku taimakesu su yi girma a tarbiya da koyarwan Ubangiji"
"biyayya." Wannan umurni ne.
Maganar "girmamawa mai zurfi da tsoro " ya jaddada ra'ayin daraja da halin su da kuma ɗauki.
"kamar ka na girgiza da tsoro"
"za da gaskiya gaba ɗaya"
yi biyayya ga iyayengijinku na duniya kamar iyayengijinku na duniya ne Almasihu da kansa.
"yi aiki da farinciki, tun da ku na yin aiki wa Ubangiji ne ba domin mutane ba"
"kukuma ku yi wa bayin kirki" ko " kamar yadda bayi dole ne su yi kirki ga iyayengijinsu, ku kuma dole ne ku yi kirki ga bayin ku (Dubi: 6:5)
"Kun san cewa Almasihu ne shugaban ku barori da iyayengiji, kuma shi yana sama"
"yana shar'anta kowa ta hanya ɗaya"
Bulus ya ba da umurni domin ya sa masubi su dage daga yaƙi da muke ciki wa Allah.
"karfin iƙonsa." Dubi yadda "da cikin baban karfin shi" an fasara kusa da karshen 1:19.
Ya kamata Almasihu su yi amfani da abubuwan da Allah ya basu domin su tsaya da karfi daga ibilis kamar da soldier yake sa makamai domin su kare kansu daga harin makiya.
"dabarun sha'ani mai wuya"
Wannan maganan na nufin mutane ne, ba ruhohi wanda basu da jikunan mutum ba.
Ya kamata Almasihu su yi amfani da abubuwan tsaro da Allah ya basu domin fada da ibilis kamar da soldier yake sa makamai domin su kare kansu daga harin makiya.
Kalmar "tsaya da karfi" na tsaya a maɗaɗin kalmala kari'a ko fada da wani abu. AT: "domin ku iya dage wa ibilis"
Kalmar "tsaya" ya zama wakilin tsayaya ko kuwa fada da wani abu. Dubi yadda aka fasara "tsaya da karfi" a 6:12. "tsaya da ibilis"
Gaskiya na riƙe komai tare wa masubi kamar da damara ke riƙe kaya na soja tare.
Ya kamata mu san gaskiya mu kuma yi ayuka ta hanya da zai gamshi Allah.
sunna iya nufin 1) kyautar adalci na rufe zuciyar maibi kamar da sulke ke tsare ƙirjin soja kokuwa 2) rayuwarmu kamar yadda Allah ke so, ya ba mu warair lamiri domin ya tsare zuciyar mu yadda sulke yake tsare kirjin soja.
Kamar yad'da soja na sa takalma ya bashi karfin ƙafa,ya kamata maibi ya samu sani mai karfi na bishara na salama domin ya yi shelar.
Dole maibi ya yi amfani da bangaskiya da Allah ya bashi domin tsarewa daga harin ibilis, yadda soja yake anfani da sulke domin ya tsare shi daga harin.
Harin na ibilis akan maibi na kaman kibau masu wuta da ya harbi soja daga makiyi
Ceto da Allah ya bayar na kiyaye zuciyar maibi kamar yadda kwalkwali yake tsare kan soldier.
Kalmar Allah, hurarrun daga ruhun mai tsarki, ke kamata ayi anfani domin a yi yaƙi da kuma kare masubi daga ibilis kamar da soldier yake amfani da takobi domin ya yake da kuma kare harin maƙiyi.
"yi addu'a kullum a cikin ruhu yanda ku yi addu'a da yin roƙo musamman"
"domin ku iya yin addu'a haka." Wannan na nufin hali na ɗaukar makami na Allah.
"jurewa a zaman jijjiga, ku yi addu'a wa dukan tsarkaken mutanen Allah" ko "yi adua'a da jijjiga wa dukan masubi"
A karshe, Bulus ya roƙe su da su yi addu'a domin rashin fargaba a yin wa'azi yayin da ya ke cikin kurkuku da kuma cewa zai aiki Tikikus ya karfafa su.
AT: "domin Allah ya bani kalmar" ko kuwa "Allah ya bani sako"
"idan na yi magana. ku yi addu'a in bayana gabagadi"
"magana"
"A yanzu haka, ina cikin kurkuku domin ni mai shalar bashara ne.
Kalmar "addu'a" na iya ganewa daga sura 19.AT: " ku yi addu'a domin dukan lokacin da na yi wa'azin bishara, zan yi shi da gabagadi yan da ya kamata" ko " ku yi addu'a domin in yi wa'azin bishara da gabagadi yadda ya kamata"
Tikikus na ɗaya daga mutanen da sun yi aiki da Bulus.
Bulus ya rufe wasikar sa ga masubi na Afisawa tare da albarka na salama da alheri ga dukan masubi waɗanda suna kaunar Almasihu.
1Bulus da Timoti bayin Almasihu Yesu, zuwa ga dukan wadan da aka kebe cikin Almasihu Yesu da ke a Filibi, tare da masu kula da ikilisiya da dikinoni. 2Bari alheri ya kasance tare da ku da salama daga Allah Ubanmu da Ubagijinmu Yesu Almasihu.3Ina godiya ga Allahna duk lokacin da na tuna da ku. 4Ko yaushe cikin addu'a ta dominku duka, da farin ciki na ke addu'a. 5Ina godiya domin tarayyar ku a cikin bishara tun daga rana ta fari har ya zuwa yanzu. 6Na tabbata game da wannan abu, shi wanda ya fara aiki mai kyau a cikinku zai ci gaba da shi har ya kai ga kammala zuwa ranar Yesu Almasihu.7Daidai ne in ji haka game da dukanku domin kuna zuciya ta. Dukanku abokan tarayya ta ne cikin alherin Allah wajen dauri na da kuma kariyar bishara, da tabbatar da bishara. 8Domin Allah mashaidi na ne, a kan yadda ina da marmarin ku duka cikin zurfin kaunar Almasihu Yesu.9Ina yin wannan addu'a: kaunar ku ta habaka gaba gaba a cikin sani da dukan fahimta. 10Ina addu'a a kan haka domin ku gwada ku zabi mafifitan abubuwa. Ina addu'a domin ku zama sahihai marasa abin zargi a ranar Almasihu. 11Wannan kuma domin a cika ku da 'ya'yan adalci da ake samu ta wurin Yesu Almasihu, zuwa ga daukaka da yabon Allah.12Yanzu ina so ku sani, 'yan'uwa, cewa al'amuran da suka faru da ni sun zama dalilan cin gaban bishara kwarai da gaske. 13Sakamakon haka, sarkokina cikin Almasihu sun zama sanannu ga dukan sojojin fada da kuma sauran jama'a, 14har galibin 'yan'uwa cikin Ubangiji suka karfafa kwarai sabili da sarkokina, suka fito a fili suka yi shelar maganar Allah gabagadi.15Lalle wadansu suna shelar Almasihu cikin kishi da husuma, wadansu kuwa domin kyakyawar manufa. 16Masu shelar Almasihu domin kauna sun sani cewa an ajiye ni nan domin in kare bishara. 17Amma wadansu kuwa suna shelar Almasihu saboda sonkai da rashin gaskiya. A zaton su suna wahalar da ni cikin sarkokina.18Sai kuma me? Ta kowace hanya, ko da gangan ko da gaske, shelar Almasihu ake yi, ina kuma murna da wannan! I, zan yi murna. 19Domin na sani wannan zai kai ga sanadiyar kubuta ta. Wannan zai faru sabili da addu'ar ku, da kuma taimakon Ruhun Yesu Almasihu.20Bisa ga abin da hakikance nake tsammani da tabbaci cewa ba zan kunyata ba. Maimakon haka, da dukan karfin hali kamar kullum, da yanzu kuma, ina da burin kawo daukaka ga Almasihu a cikin jikina. Ina da begen Almasihu ya sami daukaka a cikin jikina ko cikin rayuwa ko cikin mutuwa. 21Domin ni a gare ni rai Almasihu ne, mutuwa kuwa riba ce.22Amma idan ya zamanto rayuwata cikin jiki za ta kawo amfanin hidima to, ban san wanda zan zaba ba. 23Amma dukansu biyu suna jan hankali na. Ina da burin in bar nan in kasance tare da Almasihu, wannan ya fiye mani kwarai! 24Duk da haka rayuwata cikin jiki wajibi ne sabili da ku.25Tunda shike ina da tabbas a kan wannan, na kuma sani zan rayu, in cigaba da kasancewa da ku duka domin cigaban ku, da farincikin ku, cikin bangaskiya. 26Sakamakon haka, takamar ku cikin Almasihu Yesu za ta bunkasa sabili da dawowa ta a gare ku. 27Ku tafiyar da al'amuran ku kamar yadda ya cancanci bisharar Almasihu, ku yi haka domin ko na zo in duba ku, ko bana nan inji yadda kuke tsaye daram cikin ruhu guda. Ina fatan in ji cewa da nufi daya kuke fama tare saboda bangaskiyar nan ta bishara.28Kada ku tsorata da kome da magabtanku za su yi. Alama ce a gare su ta hallakar su. Amma ku kuwa alama ce ta ceton ku, wannan kuwa daga Allah ne. 29Gama an yi maku alheri, sabo da Almasihu, ba gaskantawa da Almasihu kawai ba, amma har ma shan wuya dominsa. 30Kuna da shan wuya irin tawa wanda kuka gani, wanda kun ji nake sha har yanzu.
Bulus da Timoti ne suka rubuta wannan wasiƙa zuwa ga ikkilisiyar Filibi.
Idan Harshen ku na da wata hanya ta musamman na gabatar da marubucin wasiƙa, a yi amfani da shi a nan.
"Timoti. Mu bayin Yesu Almasihu ne"
"zuwa ga dukan masubi da ke cikin Yesu Almasihu"
"shugabanen ikilisiya"
Bulus yana bayyana godiyar sa ga Allah domin 'yan Filibi ma suna wa'azin bishara. AT: "Ina godiya ga Allah domin kuna shelar bishara" .
"na amince"
"Allah, wanda ya fara"
"yadace mani" ko kuma "ya mun kyau"
"ina kaunar ku sosai" .
"kasance maciyan alheri da ni" ko kuma" kasance masu tarayya da ni cikin alheri"
"Allah ya sani" ko kuma "Allah ya fahimta"
Ana iya fassara kalman "tausayi" da wannan kalman aiki "kauna." AT: "kuma ina ƙaunar ku kamar yadda Almasihu yake matukar ƙaunar mu duka"
Bulus ya yi addu'a ga masu bi a Fillibi, kuma yayi magana game da farin ciki da akwai a shan wahala domin Ubangiji.
Bulus na maganar kauna kamar wasu abubuwa ne da bayan samun su mutane za su iya ƙara samu. AT: "na iya kãra"
"fahimta" a nan na nufin game da Allah kuma za a iya ƙãra yin gamsashen bayyanin sa. AT: "sa'an da kun koya kun kuma ƙãra fahimtar abin da zaigamshi Allah"
Wannan na nufin bincika abubuwa sa'an nan a ɗauki masu kyau kawai. AT: "gwaji da zaɓi"
"abin da ya fi gamasar Allah"
kalmomin nan "sahihi" da "marasa abin zargi" na da ma'ana ɗaya. Bulus ya haɗa su ne domin ya nanata halin tsarki. AT: "marar laifi gabaki ɗaya" .
Ma'anoni masu yiwuwa na "'ya'yan adalci" su ne 1) kalma ne da ke nuna halin adalci. AT: "ku kuma za ku yi halin adalci domin Yesu Kiristi ya ba ku dama" ko 2) kalma ne da ke nuna ayuka masu kyau ta dalilin zaman adalci. AT: "ku kuma za ku yi halin ayuka masu kyau domin Yesu Kiristi ya maishe ku adalai
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "Sa'an nan sauran mutane zasu ga yadda kuke girmama Allah" (UDB) or 2) "Sa'an nan mutane za su yaba, su kuma ba wa Allah girma ta dalilin nagarin abubuwan da suka ga kuna yi." Waɗannan ma'anoni masu yiwuwa za su buƙaci sabuwan jumla.
An yi amfani da kalmar na "yanzu" an nan domin a sa alamar wata sabuwar sashin wasiƙar.
A nan wannan yana nufin 'yan'uwa Kirista, maza da mata, domin duk masu bi a cikin Almasihu 'yan iyali ɗaya ne cikin ruhu, da Allah a matsayin Ubansu na sama.
Bulus yana magana ne game da lokacin da ya ke a kurkuku. AT: "wannan abin da na sha wahala, saboda an sa ni kurkuku a kan wa'azin Yesu"
"ya sa mutane da yawa sun ji bishara"
"sarkokina cikin Almasihu" magana ce da ke nufin kasancewa a kurkuku saboda Almasihu. "zuwa ga haske" kalma ce da ke nufin "ya zama sananne." AT: "ya zama sananne cewa ina kurkuku ta dalilin Almasihu"
Ana iya bayana wannan da sifan aiki. AT: "sojojin fada da sauran mutane da yawa a Roma sun san cewa ina cikin sarkoki saboda Yesu."
Bulus ya yi amfani da mahaɗin kalma "cikin" mai ma'ana "saboda." AT: "sarƙoƙina saboda Almasihu" ko kuma "sarkokina saboda ina koyar wa mutane game da Almasihu"
kalmar "sarkoki" a nan na nufin kurkuku. AT: "ɗaurewa ne a kurkuku"
wannan sojoji ne da ke taimaka wa a kare Sarkin Roma.
"wasu mutane suna wa'azin bisharar Almasihu"
"domin basu son mutane su saurare ni, kuma su na so su kawo matsala
"amma sauran mutane suna yi ne saboda suna da kirki kuma suna so su yi taimako.
"Masu shelar Almasihu da kyakyawar manufa"
Ana iya bayana wannan da sifan aiki. AT: 1) "Allah ya zabe ni in kare bishara" ko kuma 2) "Ina kurkuku saboda ina kare bishara."
"in koyar da kowa cewa sakon Yesu gaskiya ne.
"Amma sauran" ko kuma "waɗanda suke shelar Almasihu cikin ƙishi da husuma"
maganan nan "cikin sarkoki" na nufin kurkuku. AT: "tun ina ɗaure a kurkuku" ko kuma"tun ina cikin kurkuku"
Bulus yana amfani ne da wannan tambayan ya faɗi yanda yake ji dangane da yanayin da ya rubuto a 1:15. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) wannan na nufin "ba kome." ko kuma 2) kalmomin nan "zan yi tunani game da wannan" ana iya fahimtarsu a matsayin jikin tambayar. AT: "Sai kuma me zan yi tunani game da wannan?" ko kuma "Ga abin da nake tunani game da haka"
"muddin mutane suna yin wa'azin Almasihu, ba kome ko sun yi shi domin manufofi masu kyau ko da manufofi marasa kyau."
"ina murna domin mutane suna wa'azin Yesu"
"zan bayyana murna" ko kuma "zan yi farin ciki"
"domin mutane suna shelar Almasihu, Allah zai kubutar da ni"
Ainihin ma'anar "kuɓuci," bai fita fili ba ko daga menene Allah zai ceci Bulus. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) Bulus yana nufin taimako daga wani mummunan yanayi, ko kuma 2) Bulus yana nufin samun 'yancin sa daga kurkuku.
"domin kuna yi mani addu'a kuma Ruhun Yesu Almasihu yana taimako na"
"Ruhu Mai Tsarki"
A nan maganan "haki na tunani" da "tabbacin bege" suna da ma'ana ɗaya. Bulus ya yi amfani da su duka ne domin ya nanata karfin sa ran sa. AT: "na tabbata sarai"
Wannan sahshi shi ne sa rai da begen Bulus. AT: "amma ina sa rai da kuma bege cewa da dukan karfi, yanzu kamar kullum, Almasihu zai sammu ɗaukaka"
"yanzu zan kasance da gabagaɗi, kamar yadda na ke ko da yaushe da"
wannan maganan "jikina" na nufin abin da Bulus ya ke yi da jikinsa. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar kaha 1) "zan girmama Almasihu ta wurin abubuwan da nake yi" ko kuma 2) "mutane za su yabi Almasihu saboda abubuwan da nake yi"
"idan na ci gaba da rayuwa ko idan na mutu"
"Domin idan na ci gaba da rayuwa, zan rayu in gamshi Almasihu, kuma idan na mutu, shi zai ma fi alhẽri
Kalman nan "jiki" a nan magana ce da ke nufin kasancewa da rai. AT: "Amma idan zan zama mai rai a cikin jikina: ko kuma "Amma idan na cigaba da rayuwa"
Kalmar nan "ni'ima" a nan yana nufin sakamakon aikin Bulus mai kyau. AT: "wato zan iya in yi aiki kuma aiki na zai ba da kyakyawar sakamako" ko kuma "sa'an nan zan ƙara samun zarafi in ƙarfafa mutane su gaskata da Almasihu"
Bulus yana magana ne game da yadda yana masa wuya ya zaɓa tsakanin rai da mutuwa kamar abubuwa ne masu nauyi, irin su duwatsu ko kuma gungume, suna tura shi daga gefe biyu a lokaci guda. Wataƙila harshen ku zai fi dacewa da yin amfani da abubuwa da ke ja ko dai turi. "Ina cikin tashin hankali. Ban san ko in zaɓi rai ko mutuwa ba"
Bulus ya yi amfani da wannan maganar a nan domin ya nuna cewa ba ya tsoron mutuwa. AT: "Zan so in mutu domin zan je in kasance tare da Almasihu"
"Tun da shike ina da tabbaci cewa ya fi mini amfani in rayu"
"na san cewa zan cikigaba da rayuwa" ko kuma "na san cewa zan daɗa rayuwa"
"saboda ta dalilina" ko kuma "saboda ta wurin abubuwan da nake yi"
Wadannan jumloli biyu suna da ma'ana kusan ɗaya kuma suna nanata muhimmancin ɗayantaka.
"fama tare da zuciya daya." Anyi maganar yarda da juna kamar kasancewa ne da zuciya ɗaya. AT: "yarda da juna da fama tare"
"faman aiki tare"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "a yaɗa bangaskiyar da ke cikin bishara" ko kuma 2) "a gaskata a kuma yi rayuwar yadda bishara ke koya mana"
Wannan umurni ne zuwa ga masubi na Filibi. Idan harshen ku yana da wata hanya da ake ba da umurni ga mutane da yawa, a yi amfani da shi a nan
"ƙarfin halin ku zai nuna musu cewa Allah zai hallakas da su. Zai kuma nuna muku cewa Allah zai cece ku."
"Shi ya sa kuke shan wuya kamar yadda kuka ga na sha, kun kuma ji nake sha har yanzu"
1Idan akwai wani abin karfafawa cikin Almasihu. Idan da wata ta'aziyya daga kaunarsa. Idan akwai zumunta a Ruhu. Idan da tatausan jinkai da tausayi. 2Ku cika farin cikina don ku zama da tunani irin haka, kuna da kauna daya, kuna tarayya cikin Ruhu daya, ku kasance da manufa iri daya.3Kada ku yi komai cikin sonkai ko girman kai. A maimakon haka cikin zuciya mai tawali'u kowa na duban wadansu fiye da kansa. 4Kada kowa ya dubi bukatun sa, amma yana lura da bukatun wadansu.5Ku yi tunani cikin hanya wadda ke cikin Almasihu Yesu. 6Wanda ya yi zama cikin siffar Allah, bai mai da daidaitarsa da Allah wani abin da zai rike ba. 7Maimakon haka, ya wofintar da kansa. Ya dauki siffar bawa. Ya bayyana cikin kamannin mutane. An same shi a bayyane kamar mutum. 8Ya kaskantar da kansa, ya yi biyayya har ga mutuwa, mutuwa ta gicciye.9Saboda haka Allah ya ba shi mafificiyar daukaka. Ya ba shi suna wanda yafi kowanne suna. 10Domin a cikin sunan Yesu kowace gwiwa za ta durkusa, gwiwoyin wadanda ke cikin sama da kuma duniya da kuma karkashin duniya. 11Kuma kowanne harshe zai furta cewa Yesu Almasihu Ubangiji ne, zuwa daukakar Allah Uba.12Domin wannan kaunatattuna, kamar yadda kullum kuke biyayya ba sai ina nan kadai ba. Balle yanzu da bananan, ku yi aikin cetonku da tsoro da far gaba. 13Gama Allah ne yake aiki a cikinku ku yi nufi duka da aikata abin da zai gamshe shi.14Ku yi kowanne abu ba tare da gunaguni da gardama ba. 15Domin ku zama marasa abin zargi kuma masu gaskiya, 'ya'yan Allah marasa aibi. Ku yi haka domin ku haskaka kamar haske a cikin wannan duniya, a tsakiyar karkatacciyar da gurbatacciyar tsara. 16Ku rike kalmar rai da karfi domin in sami dalilin daukaka Almasihu a ranarsa. Sa'annan zan san cewa ban yi tseren banza ba, ban kuma yi wahalar banza ba.17Ko da ana tsiyaye ni kamar sadaka a kan hadaya da kuma hidimar bangaskiyarku, na yi farin ciki, kuma na yi farin ciki tare da ku duka. 18Kamar haka kuma sai ku yi farin ciki, ku yi farin ciki tare da ni.19Amma na yi niyya in aiko da Timoti wurin ku ba da dadewa ba, domin ni ma in sami karfafuwa idan na san al'amuran ku. 20Gama bani da wani wanda halinmu yayi daidai da nasa, wanda yake juyayin ku da gaskiya. 21Domin duka ribar kansu suke nema bata Yesu Almasihu ba.22Amma kun san darajar sa, kamar yadda da ke hidimar mahaifisa, haka ya bauta mani cikin bishara. 23Shi nake sa zuciyar in aiko maku ba da dadewa ba idan naga yadda al'amura nake gudana. 24Amma ina da gabagadi cikin Ubangiji cewa ni da kaina zan zo ba da dadewa ba.25Amma ina tunanin yakamata in sake aiko maku da Abafaroditus, shi dan'uwana ne, abokin aiki, da abokin yaki, manzon ku da kuma bawa domin bukatu na. 26Da shike yana marmarin ku duka, ya damu kwarai da shike kun ji yayi rashin lafiya. 27Da gaske yayi rashin lafiya har ya kusan mutuwa. Amma Allah ya ji tausayin sa, ba shi kadai ba, amma har da ni, domin kada in yi bakin ciki kan bakin ciki.28Domin haka na yi niyyar aiko shi, saboda idan kun sake ganinsa za ku yi farin ciki ni kuma in kubuta daga juyayi. 29Ku karbi Abafaroditus da dukan murna cikin Ubangiji. Ku ga darajar mutane irin sa. 30Domin saboda aikin Almasihu ne ya kusan mutuwa. Ya sadakar da ransa domin ya bauta mani domin ya cika hidimar da ya kamata ku yi mani.
Bulus yana shawartar masubi su kasance da haɗin kai da tawali'u, yana kuma tunashe su da misalin Alnasihu.
"Idan Almasihu ya ƙarfafa ku"
"idan kaunarsa ta baku wata ƙarfafawa"
"idan kuna da zumunci da Ruhu"
"idan kun taba jin jinƙai da tausayi na ayyukan Allah masu yawa"
Bulus yana maganar farin ciki a nan sai ka ce kamar ruwa ne da ke cika randa. AT: "sa ni in yi farin ciki ƙwarai"
"kada ku yi wa kanku hidima ko kuma ku aza kanku fiye da waɗansu"
"kada ku lura da bukatun ku kaɗai, amma har ma da bukatun waɗansu"
"Kasance da irin halin Almasihu Yesu" ko kuma "Yi tunanin abubuwa a hanyar da Almasihu Yesu yayi"
Bulus yana magana ne a nan game da daidaici da Allah Uba kamar wani abu ne da Almasihu zai iya kamawa da hannun sa. Kamar yadda UDB ya bayyana, a lokacin da Almasihu yake duniya, bai daina zama Allah ba; amma ya daina yin ayyuka a matsayin Allah.
"suna" anan kalma ce ke nufin matsayi ko kuma daraja. AT: "matsayi da yafi duk wani mastayi" ko kuma "daraja da yafi duk wani daraja"
Sunan mafi muhimmanci ne, wadda ya kai a yaba masa fiye da duk wani suna
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "a lokacin da kowa da kowa ya ji sunan Yesu" (UDB) ko kuma 2) "a cikin darajar Yesu"
"gwiwa" a nan yana nufin mutum gabaɗaya, kuma durƙusa gwiwa zuwa ƙasa na nufin yin sujada. AT: kowane mutum zai yi wa Allah sujada"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "wurin da mutane ke zuwa a lokacin da sun mutu" ko kuma 2) wurin da aljanu suke zama.
"harshe" a nan yana nufin mutum gabaɗaya. AT: "kowane mutum" ko kuma "kowane mai rai"
kalmar nan "zuwa" yana nuna sakamakon: "sakamakon shi ne za su ɗaukaka Allah Uba"
Bulus ya ƙarfafa masu bi na Filibi ya kuma nuna musu yanda za su yi rayuwa irin a Kirista a gaban mutane; ya kuma tuna musu gurbi da ya bar musu.
"masoya 'yan'uwanna masu bi"
"lokacin da ina can tare da ku"
"lokacin da bana can tare da ku"
"cikagaba da yi wa Allah biyayya"
Waɗannan kalmomin "tsõro" da "fargaba" suna da ma'ana ɗaya ne. Bulus ya yi amfani da su ne ya nanata girmama Allah. AT: "tsõro tare da fargaba" ko kuma "tare da matuƙa girma"
"Allah yana ayyukan sa domin ku yi marmarin yi masa biyayya ku kuma yi masa biyayya"
kalmomin nan "marasa abin zargi" da "masu gaskiya" suna kama sosai a ma'ana kuma an yi amfani da su don a ƙara ƙarfin zancen AT:"marasa abin zargi gaba ɗaya"
Haske misali ne na nagarta da gaskiya. "Haskaka kamar hasken duniya" na misalin zaman nagarta da adalci a hanyar da ta dace har mutanen da suke duniya su gane cewa Allah mai nagarta da gaskiya ne. AT: "saboda ku zama kamar hasken duniya"
A nan kalmar nan "duniya" na nufin mutanen duniya. Wannan kalmar "karkatacciyar" da " gurɓatacciyar" an yi amfani da su tare domin a yi nuni cewa mutanen sun yi zunubi sosai. AT: "a cikin duniya, a saƙanin mutane masu zunubi sosai"
"Ku riƙe da ƙarfi" na nufin gaskata wa da ƙarfi. AT: "cigaba da yarda da kalmar rai da ƙarfi"
"kalmar da ya ke bada rai" ko "kalmar yana nuna yadda zaka yi rayuwa yanda Allah yake so ka yi"
"zuwa ga farin ciki" ko kuma "zuwa ga murna"
wannan yana nufin zuwa lokacin da Yesu zai dawo ya kafa mulkin sa ya kuma yi mulkin duniya. AT: " A lokacin dawowar Almasihu.
Wannan maganan "tseren banza" da kuma "wahalar banza" suna da ma'anna ɗaya. Bulus ya yi amfani da su tare don ya nanata ƙoƙarin aiki da yayi domin ya taimaki mutane su gaskata da Almasihu." AT: "Ban yi ƙoƙarin aiki a banza ba"
Littafin ya na yawan amfani da hoton tafiya domin bayyana halin mutu. Gudu zaman rayuwa ne na mai da hankali.
Bulus yana manganar mutuwarsa kamar shi wani hadayar dabba ne wadda aka zuba masa ruwan inabi ko kuma man zaitun. Abinda Bulus yake nufin shi ne zai mutu da farin ciki saboda mutanen Filibi idan hakan zai sa su su ƙara gamsar da Allah. Kuma, ana iya bayana wannan a cikin sifar aiki. AT: "Amma, ko da 'yan Roma sun yanke shawara domin su kashe ni, zan yi murna ƙwarai idan mutuwa ta zai sa bangaskiyar ku da biyayyar ku ta ƙara gamsar Allah"
Wannan maganan tare suna nuna matuƙar farin ciki. "Ina so kuma ku yi matuƙar farin cikin tare da ni"
"Amma, idan Ubangiji Almasihu ya yarda, ina bege"
"Babu wani a nan da ke ƙaunarku kamar yadda shi yake"
kalmar "su" a nan yana nufin mutane da Bulus bai ji zai iya amince wa ya aika su zuwa Filibi ba. Bulus yana kuma nuna fushin sa da waɗannan mutane, waɗanda yakamata su iya zuwa, amma Bulus bai amince da su cewa za su iya cika manufansu ba.
Bulus yana magana game da Timoti, wanda ya bauta wa Almasihu tare da Bulus, kamar shi ɗa ne da ke bauta wa mahaifinsa. Bulus yana nanata dangantakar mahaifi da ɗa na kusa da yake da shi da Timoti a cikin bautar Almasihu.
"bisharan" a nan yana nufin aikin gaya wa mutane game da Yesu. AT: "a cikin faɗawa mutane game da bisharar"
"ina da tabbaci, idan Allah ya nufa, ni ma zan zo ba da daɗewa ba."
Wannan sunan wani mutum ne da ikilisiyar Filibi suka aika ya yi wa Bulus hidima a kurkuku
Bulus yana maganar Abafaroditus kamar shi soja ne. Yana nufin cewa Abafaroditus ya horu kuma yana da ƙwazo ga bautar Allah, duk da tsananin wahala da dole ne ya sha. AT: "dan'uwa mai bida yayi aiki da gwagwarmaya tare da mu"
"da kuma wanda ya kawo saƙonninku wurina ya kuma taimake ni a lokacin da nake da bukata."
"ya damu kwarai kuma yana so ya kasance tare da ku duka"
Za a iya ƙara bayyana dalilin baƙin cikin. AT: baƙin cikin rabuwa da shi ya ƙara mani baƙin cikin da nake da shi na zama a kurkuku"
"zan rage juyayi" ko kuma "ba zan damu da yawa kamar yadda da nake yi ba"
"ku karɓe shi da farin ciki"
a matsayin da'uwa mai bi a cikin Ubangiji da dukan farin ciki." ko kuma "da matuƙar farin ciki da muke da shi domin Almasihu Yesu yana ƙaunar mu. (UDB)
Bulus yana maganar mutuwa a nan kamar wani wuri ne da wani zai iya zuwa.
Bulus yana maganar bukatunsa sa kamar wasu gora ne da Abafaroditus ya cika su da abubuwa masu kyau wa Bulus."
1A karshe, 'yan'uwana, ku yi farin ciki cikin Ubangiji. In sake rubuta maku wadannan abubuwa ba wani abu mai nauyi ba ne a gare ni. Wadannan abubuwa zasu tsare ku. 2Ku yi hankali da karnuka. Ku yi hankali da miyagun ma'aikata. Ku yi hankali da masu yanke-yanke. 3Gama mune kaciyar. Don mune muke sujada ta wurin Ruhun Allah. Mune masu fahariya chikin Almasihu Yesu, kuma ba mu da gabagadi cikin jiki.4Ko da shike, ni kaina ina gabagadi ga jiki. Idan wani zai iya tunanin gabagadi ga jiki, ni na fi shi. 5An yi mani kaciya a rana ta takwas, daga mutanen Israila, na kabilar Biliyaminu, Bayahuden Yahudawa; ga zancen shari'a Bafarisiye nake.6Wajen himma na tsanantawa ikilisiya. Ga zancen adalci cikin sharia, na zama mara abin zargi. 7Amma duk wadannan abubuwan da suka zama riba a gare ni, na dauke su asara ne saboda Almasihu.8I, lallai ina lisafta dukan wadannan abubuwa asara saboda mafificin sanin Almasihu Yesu Ubangijina. Saboda shine na yi asarar dukan abubuwa. Na maishe su marasa amfani domin in ribato Almasihu, 9a iske ni cikinsa. Ba ni da wani adalcin kaina ta wurin shari'a. Maimakon haka, ina da adalci ta wurin bangaskiya cikin Almasihu, adalcin dake daga wurin Allah ta wurin Bangaskiya. 10Yanzu ina so in san shi da ikon tashinsa, da tarayya cikin shan wuyarsa. In kuma zama kamarsa wajen mutuwarsa, 11domin ta ko kaka in kai ga tashi daga cikin matattu.12Ba wai na rigaya na sami wadannan abubuwa bane, ko kuma na riga na zama cikakke. Amma ina nace bi domin in cafki wannan da Almasihu Yesu ya cafko ni dominsa. 13'Yan'uwa, ban dauka cewa na riga na cafka ba tukuna. Amma akwai abu daya da nake yi: ina mantawa da abin da ke baya, ina kutsawa zuwa ga abin da ke gaba. 14Ina nacewa zuwa ga manufar nan in kai ga samun ladar nasara na madaukakin kiran Allah cikin Almasihu Yesu.15Dukan mu wadanda muke kammalallu, sai mu yi tunani ta wannan hanyar, idan kuwa kun yi tunanin wani abu daban, to Allah zai bayyana maku wannan kuma. 16Sai dai, in da muka rigaya muka kai, bari mu rike shi haka.17Ku zama masu koyi da ni, 'yan'uwa. Ku duba da kyau wadannan da suke tafiya yadda muka zama abin koyi a gare ku. 18Mutane da dama suna tafiya -sune wadanda na ba ku labarin su, yanzu kuma ina fada maku har da hawaye - kamar makiyan gicciyen Almasihu ne. 19Karshen su hallaka ne. Domin allahn su ciki ne, fahariyar su kuma tana cikin kunyar su. Tunanin su na kan al'amuran duniya.20Amma mu 'yangarincin mu a sama yake, daga inda muke sauraron mai ceto, Ubangiji Yesu Almasihu. 21Za ya sake jikinmu na kaskanci ya siffanta shi kamar jikin darajarsa, siffantacce ta karfin ikonsa inda ya sarayar da dukan abubuwa a gare shi.
Bulus yana ba da na sa shaida game da lokacin da yake tsananta wa masu bi domin ya gargaɗi yan'uwan sa masu bi game da Yahudawan da za su yi ƙoƙari sa su su bi dokoki na da.
"Yanzu muna ci gaba, 'yan'uwana" ko kuma "game da sauran al'amura, 'yan'uwana"
Juya wannan kamar yadda yake a 1:12.
"yi farin ciki saboda duk abinda Allah ya yi"
baƙin ciki
"waɗannan abubuwa" a nan na nufin koyaswar Bulus. Za'a iya ƙara wannan a ƙarshen jumla da ya gabata. AT: "domin waɗannan koyaswar za su kare ku daga masu koyaswar ƙarya"
"yi hattara" ko kuma "yi lura"
waɗannan hanyoyi ne daban-daban na bayana ƙungiya guda masu koyaswar ƙarya. Bulus yana amfani ne da magana mai ƙarfi domin ya kai/isad da yadda yake ji game da waɗannan malaman Yahudawa Kirista
Bulus yana magana ne game da yin kaciya don ya zagi masu koyaswar karya. Masu koyaswar karyan sun ce Allah zai ceci mutum mai kaciya ne kaɗai, wanda ya yanke loɓa. An bukaci wannan ne a dokar Musa ga dukan mazan Isra'ila.
Bulus ya yi amfani da "mu" domin ya yi magana game da kansa da dukan masu bi na gaskiya a cikin Almasihu, duk da masu bi na Filibi
Bulus ya yi amfani ne da wannan yana nufin masubi a cikin Almasihu waɗanda ba a yi masu kaciya ta jiki ba amma suna da kaciya ta ruhu, wato sun karɓi Ruhu Mai Tsarki ta wurin bangaskiya. "mutanen Allah na gaske"
"kada ku amince da cewa yanka jiki kawai zai gamshi Allah"
"duk da haka" ko kuma "amma dai"
A nan Bulus yana cewa in da yana yiwuwa ne Allah ya ceci mutane bisa ga abin da suka yi, da lallai Allah zai cece shi. AT: "Babu wani da zai iya yin abubuwan da yawansu za su kai ya gamshi Allah, amma idan akwai wani wanda zai iyan yin abubuwa da yawansu za su kai ya gamshi Allah, to ni zan yi fiye da haka in kuma ganshi allah sosai fiye da kowa"
Bulus ya yi amfani da "kaina" domin jaddadawa. "lallai ni"
Za'a iya sa wannan a sifan aiki. AT: "Wani Firist ya yi mani kaciya"
"bayan kwana bakwai da haifuwa ta" (UDB)
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "ɗan Bayahude mai iyaye Yahudawa" ko kuma 2) "Bayahude tsantsa"
Bayahude yana iya zama Bafarisiye ne idan mahaifinsa Bafarisiye ne. Amma wannan yana sa wa mutumin alhakin rayuwa a matsayin Bafarisiye, da ba da kai na musamman ga dokar Musa. "a matsayi na na Bafarisiye, na miƙa kai gaba ɗaya ga doka."
Bulus a nan yana cewa ya azabta mutane saboda bin Yesu. "na kudura ainun in ji wa masubi Kirista."
"na yi biyayya da doka gaba ɗaya"
Bulus yana komowa ne zuwa ga yabon da ya samu na zama bafarisiye na kwarai. Yana maganar wannan yabo kamar abin da ya wuce ne a matsayin ribar ɗan kasuwa. AT: "cikin duk abin da sauran Yahudawa suka yaba mini"
Bulus yana maganar wancan yabon kamar yana duban sa a matsayin asara ce na kasuwa maimakon riba. Abin da Bulus yake faɗi shi ne, dukan ayukansan na adalci banza ne a gaban Almasihu.
"haƙiƙa" ko kuma "da gaske"
Kalmar "yanzu" yana nanata yadda Bulus ya canja ne tun da ya bar zama bafarisi zuwa zama maibi cikin Almasihu. AT: "yanzu da na gaskata da Almasihu, ina lisafta" Dubi:
Bulus yana cigaba da moron hoton kasuwanci daga 3:6, da cewa banza ne a gaskata da kowane abu daban da Almasihu. "na ɗauki kowane abu banza"
"saboda sannin Almasihu Yesu Ubangijina ya fi daraja sosai"
"Saboda shi na yarda na jefar da dukan abubuwa"
Yi amfani da kalmar da aka saba sa wa abubuwan da ba a so kuma ana jefar da su nesa daga inda mutum yake.
Bulus yana maganr abubuwan da mutum zai iya gaskata da su kamar sharar zubar wa a waje ne. Yana nanata ainihin rashin darajarsu. AT: "Ina daukar su kamar tarkace ne"
"domin in samu Almasihu kadai"
maganar "a iske" salon magana ne da ke nanata "ya zama." AT: "a haƙiƙance tare da Almasihu da gaske"
"ba ina ƙoƙari in gamshi Allah da kaina ta wurin biyayya da doka ba ne.
"ikon sa da yabamu rai"
"shan wuya kamar yadda ya sha, sai ka ce muna shan wuyar abu ɗaya a wuri ɗaya a lokaci ɗaya"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) Bulus yana so Almasihu ya canja shi domin ya mutu kamar yadda Almasihu ya mutu. Ko kuma 2) yana so marmarin sa na zunubi ya zama matacce kamar yanda Yesu yake a mace kafin a tashe shi daga matattu.
Kalmar "ko ta ƙaƙa" yana nufin cewa Bulus bai san menene zai faru da shi a wannan rayuwa ba, amma ko da menen ya faru, zai kai ga rai na har abada. "saboda ko da menen ya rafu, zan sake rayuwa bayan mutuwa."
waɗannan sun haɗa da sanin Almasihu, sanin ikon tashinsa, da tarayya cikin shan wuyar Almasihu, da kasancewa ɗaya da Almasihu a cikin mutuwarsa da tashinsa (3:8).
"don haka ban riga na zama cikakke ba" ko kuma "don haka ban riga na gama girma ba"
"Amma ina ta ƙoƙari"
an yi maganar karbar abubuwan ruhu daga Allah kamar Bulus zai cafke su da hanun sa ne. Kuma Yesu yayi maganar cafke Bulus da hannayen sa AT: "ina iya samun waɗannan abubuwan"
An yi maganar karban abubuwan daga Allah kamar Bulus zai cafke su da hannun sa.AT: "Duk waɗannan abubuwa ba su zama nawa ba tukuna"
kamar yadda mai gudu a wasan tsere baya damuwa da fannin tsere da ya riga ya kammala amma yana mayar da hankali ne ga sauran tsere da ya rage, haka ma Bulus yana magana game da mantawa da ayyukan adinin sa na adalci yana kuma maida hankali a kan tseren rayuwa da Almasihu ya sa a gaban shi domin ya kammala" (Dubi:|Metaphor)
Kamar yadda mai wasan gudu yana nacewa domin nasara, Bulus yana nacewa cikin bauta da kuma rayuwar biyayya ga Almasihu. AT: "ina yin duk abin da na iya don in zama kamar Almasihu, kamar mai gudu da ke tsere zuwa ga karshen layi, domin in zama nashi, kuma Allah ya kira ni zuwa wurinsa bayan na mutu" (Dubi: |Metaphor)
Ma'anoni masu yiwuwa sune, Bulus yayi maganar zama har abada da Allah kamar Allah zai kira Bulus ya haura 1) zuwa sama kamar yadda Yesu yayi ko 2) hawa zuwa dandali inda masu nasara a wasan tsere suke karɓar sakamako a matsayin misalin saduwa da Allah fuska da fuska da kuma karɓar rai na har abada.
Bulus yana so 'yan'uwansa masubi su kasance da marmari ɗaya da ya ambata a 3:8. AT: "Na ƙarfafa dukan mu masubi da ke da ƙarfi a cikin bangaskiya mu yi tunani ɗaya"
"Allah kuma zai sa shi ya zama muku sarai" ko kuma "Allah zai tabbata kun san shi"
"barin dukan mu mu cigaba da biyayya da wannan gaskiya ɗaya da mun riga mun karɓa"
"yi abin da nake yi" ko kuma "yi rayuwa kamar yadda ina rayuwa"
"waɗannan da suna rayuwa kamar yadda nake rayuwa" ko kuma "waɗannan da suna yin abin da nake yi"
An yi maganar halin mutum kamar mutum yana tafiya a kan hanya. AT: "dayawa suna raye" ko "dayawa suna gudanar da rayuwarsu"
Bulus ya katse abinda yake faɗa da waɗannan kalmomi da suke bayyana "da dama." Za'a iya kai su zuwa forkon ko kuma karshen ayan idan akwai bukata.
"na gaya muku sau da dama"
"ina faɗa muku wannan da matukar baƙin ciki"
"giciyen Almasihu" a nan yana nufin "shan wahala da mutuwar Almasihu." Maƙiyan giciyen sune waɗanda suke cewa sun gaskata da Yesu amma basu yarda su sha wahala ko ma su mutu kamar yadda Yesu ya sha ba. AT: a wata hanya da ya nuna a zahiri cewa suna gaba da Yesu, wanda ya yarda ya sha wahala ya kuma mutu bisa giciye"
"wata rana Allah zai hallakar da su"
"ciki" a nan yana nufin marmarin annashuwar mutum ta jiki. Kiran sa allahn su a nan yana nufin cewa suna marmarin waɗannan annashuwan fiye da marmarin su yi wa Allah biyayya. AT: "sun fi marmarin abinci da sauran annashuwar jiki fiye da marmarin biyayya ga Allah.
"kunya" a nan yana madadin yadda ya kamata mutanen su ji kunya amma basu ji. AT: suna fahariya da abubuwan da ya kamata su jawo musu kunya" Dubi:
"duniya" a nan yana nufin dukan abubuwan da ke ba da annashuwar jiki kuma basu girmama Allah. AT: "Dukan tunanin su game da abinda zai gamshe su ne maimakon abin da zai gamshi Allah"
Bulus, ta wurin yin amfani da "na mu" da kuma "mu" a nan, ya shafe shi da masu bi da ke Filibi.
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "mu 'yan same ne" (UDB) ko kuma 2) "garinmu sama ne" ko kuma 3) "gidanmu na gaskiya a sama yake"
za ya canja jikunan mu zuwa masu daraja
"cikin jikuna kamar jikin darajarsa"
za a iya sa wannan a kalmar aiki. AT: "Jiki. Shi za ya canja jikunan mu da wannan ikon da yake amfani da shi ya kula da dukan abubuwa"
1Saboda haka, kaunatattu 'yan'uwana da nake marmari, farin ciki na da rawani na, a wannan hanya ku tsaya daram cikin Ubangiji, kaunatattun abokai. 2Ina rokon Afodiya, ina rokon Sintiki, ku zama da ra'ayi daya cikin Ubangiji. 3Babu shakka, ina sake rokon ku, abokan tarayyar takunkumina na gaske: ku taimaka wa matayen nan. Domin mun yi wahala tare a cikin yada bishara tare da Kilimas da sauran abokan aiki na, wanda sunayensu na rubuce cikin littafin rai.4Yi farin ciki cikin Ubangiji kullayomi. Ina sake cewa, yi farin ciki. 5Bari dukan mutane su ga jimirin ku. Ubangiji ya yi kusa. 6Kada ku damu da kowanne abu, maimakon haka, cikin komai tare da addu'a, da rokeroke, da godiya, bari rokeroken ku su sanu ga Allah. 7Salamar Allah, da ta zarce dukan ganewa za ta tsare zuciyarku da tunaninku cikin Almasihu Yesu.8A karshe, 'yan'uwa, duk abin da ke mai gaskiya, duk abin da ya isa ban girma, duk abin da ke mai adalci, duk abin da ke mai tsabta, duk abin da ke karbabbe, duk abin da ke kawo kauna, duk abin da ke da kyakkyawan ambato, idan akwai yabo, yi tunani a kan wadannan abubuwan. 9Wadannan abubuwan da kuka koya kuka karba kuka ji kuka gani a rayuwa ta, ku aikata wadannan abubuwan. Allah mai salama zai kasance tare da ku.10Na yi farin ciki sosai cikin Ubangiji domin yanzu a karshe kun sabunta kulawar ku game da ni. Kun kula da ni da gaske kwanakin baya, amma ba ku samu zarafin taimako ba. 11Ba don bukata ta bane nake fada wannan. Domin na koyi dangana a kowanne irin yanayi. 12Na san yadda zan zauna cikin bukata, na kuma san yadda zan samu a yalwace. A kowace hanya cikin kowanne abu na koyi asirin yadda zan ci da yawa da yadda zan zauna da yunwa, yadda zan zama a yalwace kuma in zama cikin bukata. 13Zan iya yin komai ta wurinsa shi da yake karfafa ni.14Duk da haka, kun yi zumunta da ni cikin kunci na. 15Kun kuma sani, ku Filibiyawa, cewa da farkon bishara, lokacin da na bar Makidoniya, babu ikilisiya da ta tallafe ni cikin batun bayarwa da karba sai ku kadai. 16Ko lokacin da nake Tassalonika, kun aika da gudumawar biyan bukatu na fiye da sau daya. 17Ba domin ina neman kyauta ba ne. A maimakon haka, ina neman amfani da zai kawo karuwa cikin ajiyar ku.18Na karbi dukan abubuwan, ina da shi a yalwace. An kosar da ni. Na karba ta hanun Abafroditus abubuwa daga wurinku. Shesheki na dadin kamshi mai dandanno, karbabbiyar hadaya mai gamsarwa ga Allah. 19Allah na zai cika dukan bukatunku bisa ga yalwarsa da ke cikin daukaka cikin Almasihu Yesu. 20Yanzu bari daukaka ta tabbata ga Allah da Ubanmu har abada abadin. Amin.21Gai da kowanne mai bi cikin Almasihu Yesu. Dukan 'yan'uwa da ke tare da ni suna gaisuwa. 22Dukan masu bi a nan suna gaisuwa, musamman wadanda suke gidan Kaisar. 23Bari alherin Ubangijin Yesu Almasihu ya zauna tare da ruhunku. Amin
Bulus ya cigaba da waɗansu umurnai ga masu bi na Filibi game da haɗin kai sa'an nan ya ba da umurnai don ya taimake su su yi rayuwa domin Almasihu.
Sa'ad da bulus ya ce, " abokin tarayyar takunkumina na gaske," kalmomin suna nufin mutum ɗaya ne. Bulus bai faɗi sunan mutumin ba. Ya kira shi haka ne domin ya nuna cewa ya yi aikin yaɗa bishara tare da shi.
"'Yan'uwana masubi, ina ƙaunar ku kuma ina matuƙar marmarin ganin ku"
Dubi yadda zaka juya wanna a cikin filibiyawa 1:12.
Bulus ya yi amfani da kalmomin nan "farin ciki" domin ya nun da cewa Ikilisiyar Filibi ne dalilin farincikinsa. Da ganyaye ne a ke yin "rawani," kuma mutum yakan sa shi a kai domin alamar darajantawa bayan ya yi nasara a wata gasa mai muhimmanci. "Rawani a nan yana nufin cewa Ikilisiyar Filibi ta kawo masa daraja a gaban Allah. AT: "Kun bani farin ciki domin kun gaskata da Yesu, kuma ku ne sakamakona da darajar aikin da na yi"
"Sai ku cigaba da rayuwa wa Ubangiji cikin hanyar da na koya muku, kaunatattun abokai"
Waƙannan mata ne masu bi da su ka taimake Bulus a Ikilisiyar Filibi. AT: "na roƙi Afodiya, kuma na roƙi Sintiki"
Maganar "zama da ra'ayi ɗaya" na nufin zama da hali ɗaya ko zaɓi daya. AT: "yarda da juna domin dukan ku kun gaskata da Ubangiji ɗaya ne"
"ka" a nan na nufin "abokin tarayyar takunkumi" ne.
Kilimas wani mutum ne maibi kuma ma'aikaci ne a Ikilisiyar Filibi.
"wanda Allah ya rubuta sunayen su cikin litafin rai"
Fasara wannan kamar yadda aka yi a 3:1.
Ma'anoni masu yiwuwa 1) Almasihu Yesu yana kusa da masubi cikin ruhu ko kuma 2) ranar da Yesu zai dawo duniya ya yi kusa.
"duk abin da ya faru da ku, ku tambayi All dukan abin da kuke bukata tare da addu'a da godiya"
"salamar da Ubangiji ke bayarwa"
"wanda ya fi abinda za mu iya ganewa"
A nan ana magana game da salamar Allah kamar soja ne da ke kare yadda muke ji da kuma tunanin mu daga damuwa. AT: "zai zama kamar soja ne yayi tsaron yadda kuke ji da kuma tunanin ku daga damuwa game da matsalolin rayuwa"
Yayin da Bulus yake kammala wannan wasiƙan, ya faɗin yadda ya kamata masubi su yi rayuwa domin su samu zaman lafiya da Allah.
"duk abuwuwan da ke kyawawa"
"duk abubuwan da mutane ke sha'awa" ko kuma "duk abin da mutane ke darajawa"
"idan suna da hali mai kyau"
kuma idan sune abubuwan da mutane suke yabo"
"da na koyar na kuma nuna muku"
"gamsu" ko kuma "murna"
"komen al'amari da nake ciki"
Bulus ya san yadda zai yi zama da murna ko babu dukiya ko da dukiya.
ƙoshi ko zama a cikin fama da yunwa, da kuma yadda ake samu a yalwace ko kuma zama cikin bukata- Waɗannan jumloli biyu suna nufin abu ɗaya ne. Bulus yana amfani da su ne domin ya nanata cewa ya koyi yadda za'a yi rayuwa da gamsuwa a kowane yanayi.
"zan iya yin kome domin Almasihu yana bani karfi"
Bulus yana maganar wahalu kamar wasu wurare ne da yake. AT: "Sa'ad da abubuwa sun zama da wuya"
Ma'anar bishara, a manufar Bulus a nan, ita ce wa'azin bisharar sa.
Za'a iya sanar da wannan cikin tabbaci. AT: "Ku ne kaɗai ikilisiyar da ta aika mini kuɗi ko kuma kuka tallefe ni"
Bulus yana maganar kyautar Filibi kamar ajiyar banki da ke daɗa ƙaruwa. A wannan yanayi, Allah ya san da kyawawan abubuwan da masubi na Filibi su ka yi. Bulus yana son masubi na Filibi su ba da kyautai domin su karɓi albarku na ruhu. AT: "In son Allah ya daɗ ƙara muku albarku na ruhu"
Wannan na iya nufin 1) Bulus ya karɓi komai da 'yan Filibi suka aika ko kuma 2) Bulus yana amfani da raha ta wurin cigaba da amfani da misalin kasuwanci daga 3:8 don faɗin cewa wannan sashin wasiƙar rasiti ne na kayan da Abafroditus ya isar.
Bulus yana nufin yalwar abubuwan da yake da bukata.
Bulus yayi maganar kyautar ikilisiyar Filibi kamar hadaya ce ga Allah a kan bagadi. Bulus ya nuna da cewa kyautar su karɓaɓɓiya ce ga Allah, kamar hadayar da firist ya ke konawa, wanda yake da kamshi da yake sa Allah ya ji daɗi. AT: "Na tabbatar maku cewa kyautar ku karɓaɓɓiya ce ga Allah, kamar karɓaɓɓiyar hadaya"
Wannan kalma ɗaya ne da wanda aka fassara "an cika" a aya 18. Salon zance ne da ke nufin "zai tanada dukan abuwbuwa da kuke bukata"
"daga ɗaukakar yalwarsa da yake bayarwa ta wurin Almasihu Yesu"
Kalmar nan "yanzu" na nuna addu'ar rufewa da kuma rufe wannan sashin wasiƙar.
Wannan yana nufin mutanen da ke aiki tare da Bulus ko kuma suna yi mishi hidima.
Wasu juyin sun juya wannan ta wurin amfani da "mutum mai tsarki" da "mutane masu tsarki."
Wannan yan nufin bayin da suka yni aiki a fadar Kaisar. "musamman 'yan'uwa masubi da ke aiki a fadar Kaisar"
Bulus yana magana game da masubi ta wurin amfani da wannan kalma "ruhu", wanda shine yake ba wa mutane daman yin dangantaka da Allah. AT: "tare da ku"
1Bulus manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah da Timoti dan'uwanmu, 2zuwa ga masu bada gaskiya da amintattun 'yan'uwa cikin Almasihu da suke a Kolosi. Bari alheri da salama su kasance tare da ku daga wurin Allah Ubanmu. 3Muna godiya ga Uban Ubangijinmu Yesu Kristi, kuma kullum muna addu'a dominku.4Mun ji bangaskiyar ku cikin Almasihu Yesu da kaunar da kuke da ita wa dukan kebabbu ga Allah. 5Kuna da kaunar nan domin bege na hakika ga abin da aka tanadar maku a sama. Kun riga kun ji game da begen nan na hakika maganar gaskiya da bishara, 6wanda ta zo maku. Wannan bishara tana ba da yaya tana kuma hayayyafa da kuma girma a cikin dukan duniya. Tana yin haka a cikinku kuma tun ranar da kuka ji ta kun kuma yi koyi game da alherin Allah cikin gaskiya.7Wannan itace bishara kamar yadda kuka koye ta a wurin Abafaras, kaunataccen abokin bautar mu, wanda ke amintacce mai hidimar Almasihu a madadin mu. 8Abafaras ya bayyana mana kaunarku a Ruhu.9Saboda da wannan kauna, tun daga ranar da muka ji haka, ba mu fasa yi maku addu'a ba. Muna ta roko domin ku cika da sanin nufinsa cikin dukan hikima da fahimta ta ruhaniya. 10Muna ta addu'a domin ku yi tafiya da ta cancanci Ubangiji a kowace hanya da za ta faranta masa rai. Muna ta addu'a cewa za ku ba da 'ya'ya cikin kowanne aikin nagari kuma za ku yi girma cikin sanin Allah.11Muna addu'a ku karfafa a cikin kowanne iyawa bisa ga ikon daukakarsa zuwa ga matukar jimrewa da hakuri. 12Muna addu'a za ku yi godiyar farinciki ga Uban, wanda ya sa kuka samu rabo cikin gado na masu bangaskiya cikin haske.13Ya kwato mu daga mulkin duhu ya kuma maishe mu ga mulkin kaunataccen Dansa. 14Ta wurin Dan ne muka sami fansa, gafarar zunubai.15Dan shine surar Allah mara ganuwa. Shine farkon dukan hallitta. 16Domin ta wurinsa ne aka halicci dukan abubuwa, wadanda ke sama da wadanda ke duniya, masu ganuwa da marasa ganuwa. Ko kursiyai ko mulkoki ko sarautai ko ikoki, dukan abubuwa shi ya hallice su kuma dominsa. 17Ya kasance kafin dukan abubuwa, a cikinsa ne kuma komai yake hade.18Kuma shine kan jikin, ikilisiya. Shine farko da kuma dan fari daga cikin matattu, don haka yana da wuri na fari a cikin dukan abubuwa. 19Domin Allah ya yi farinciki cewa dukan cikarsa ta kasance a cikinsa, 20kuma ya sulhunta kowanne abu zuwa gare shi ta wurin Dan. Allah ya kawo salama ta wurin jinin giciyensa. Allah ya sulhunta duka zuwa gare shi, ko abubuwan da ke duniya ko abubuwan da ke sama.21Domin a da ku baki ne ga Allah, kuma makiyansa ne cikin zuciya da cikin mugun ayyuka. 22Amma yanzu, ya sulhunta ku ta wurin mutuwarsa ta jiki. Ya yi haka domin ya mika ku tsarkakaku, marasa aibu da marasa abin zargi a gabansa, 23idan kuka ci gaba cikin bangaskiya, kafaffu da tsayayyu, marasa kaucewa daga begen ku na hakika na bishara da kuka ji. Wannan itace bishara da aka yi wa kowanne halitaccen taliki a karkashin sama. Wannan itace bishara wadda ni, Bulus, na zama bawa.24Yanzu ina murna da wahala ta domin ku. A jikina cika abin da ya rage cikin wahalar Almasihu domin jikinsa wadda itace ikilisiya. 25Saboda wannan ikilisiya na zama bawa, bisa ga haki da Allah ya ba ni domin ku, domin cika sakon Allah. 26Wannan shine asirin gaskiya da yake a boye shekara da shekaru da zamanai. Amma a yanzu an bayyana shi ga wadanda suka gaskanta da shi. 27A gare su ne Allah ya so ya bayyana yalwar daukakar asirin gaskiyarsa a tsakanin al'ummai. Ya nuna Almasihu ne ke cikin ku, tabbacin daukaka mai zuwa.28Wannan shine wanda muke shella. Muna gargadar da kowanne mutum, muna kuma koyar da kowanne mutum tare da dukan hikima, don mu mika kowanne mutum cikakke cikin Almasihu. 29Domin wannan nake aiki da himma bisa ga karfinsa da yake aiki a cikina da iko.
ko da shike wannan wasiƙa ya fito ne daga Bulus da Timoti zuwa ga masubi na Kolosi, wasiƙar ya tabbatar da cewa Bulus ne marubicin. Yana iya yiwuwa Timoti yana tare da shi kuma shi ne ya rubuta sa'an da Bulus ke magana.
"wadda Allah ya zaɓa ya zama manzon Almasihu Yesu"
Waɗannan kalamun basu haɗa da Kolosiyawa ba.
Bulus yana keɓe masu sauraronsa.
"Imanin ku a cikin Almasihu Yesu"
A nan "bege na haƙiƙa" ya tsaya a madadin abin da maibi zai sa rai da gaske, wa to, abubuwan da Allah ya alkawarta zai yi wa dukkan masubi. Ana maganan waɗannan abubuwan kamar wasu abubuwane da za a iya gani ko taɓawa da Allah ke ajiye wa a sama domin masu bi su mallaka nan gaba. AT: "domin kun haƙiƙance da cewa Allah na Sama zai yi abubuwa masu kyau da ya alkawartar muku.
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "saƙo game da gaskiyar, bisharar" ko kuma 2) "saƙon gaskiya, bisharar"
"'Ya'ya" a nan na nufin "sakamako". AT: "Wannan bisharar tana da sakamako mai kyau da yawa" ko kuma "Wannan bisharan tana samun ƙarin sakamako"
Wannan magnan na nufin yankin duniya da suka sani. AT: "ko ina a duniya"
"alherin Allah ta gaskiya"
Kalamunnan "na mu" da "mu" bai haɗa da Kolosiyawa ba
"bishara. Shi ne daidai da abin da kuka koya daga Abafaras, wanda shi ne ƙaunataccen abokin bautar mu kuma wanda" ko kuma "bishara. Shi ne daidai abin da Abafaras, ƙaunataccen abokin bautar mu, ya koya muku. Shi"
A nan "a madadin mu" yana nufin cewa Abafaras yana yi wa Almasihu aiki wadda Bulus kansa zai yi inda ba don yana kurkuku ba.
mutumin da ya yi wa'azin bishara wa mutanen da ke Kolosi
Bulus yana maganar Ruhu Mai Tsarki kamar wani wuri ne da masubi suke. AT: "yadda Ruhu Mai Tsarki ya sanya ku ku ƙaunaci masubi"
Domin Ruhu ya sanya su su ƙaunace wasu, Bulus ya yi musu addu'a ya kuma faɗa musu yadda yake addu'a domin su.
"Saboda Ruhu Mai Tsarki ya sanya ku ku ƙaunace sauran masubi"
Waɗanan Kalmomi basu haɗa da Kolosiyawa ba.
"daga ranar da Abafaras ya faɗa mana waɗannan abubuwan"
Bulus yana maganar masubi na Kolosi kamar su akwati ne. AT: "domin Allah ya cika ku da abinda kuke bukata ku sani domin ku iya aikata nufinsa"
"saboda Ruhu Mai Tsarki ya sa ku ku zama masu hikima ku kuma fahimci abinda Allah yake so ku yi"
Tafiya a nan na nuna halin rayuwa. AT: domin ku yi rayuwa yadda Allah yake sa rai ku yi
"a hanyoyin da za su gamshi Ubangiji"
Bulus yana maganar masubi na Kolosi kamar su bishiyoyi ne ko kuma shuke-shuke. Kamar yadda shuke-shuke sukan bada 'ya'ya, hakama masubi yakamata su cigaba da samun sanin Almasihu suna kuma yin kyawawan ayuka.
Kalmar nan "mu" yana nufin Bulus da Timoti amma ba Kolosiyawa ba.
Bulus yana maganar masubi na Kolosi kamar Allah zai matsar da su ne cikin wani wurin matuƙar jimrewa da hakuri. Yana addu'a ne domin kadda su daina dogara ga Allah kuma su zama da matuƙar hakuri yayin da suke girmama shi.
"ya bar ku ku samu rabo"
Bulus a nan yana maida da hankalin masu karatunsa a matsayin masu samun albarkun Allah ne. Amma ba wai yana nufin cewa shi kansa ba shi da rabo cikin waɗancan albarkun ba ne.
Karbar abin da Allah ya alkawarta wa masubi kamar cin gadon tarin dũkiya ne daga mallakar wani dangin iyali.
Wannan ra'ayin ya bambanta da ra'ayin mulkin duhu da ke aya na gaba. AT: "cikin darajar kasancewarsa"
"Allah Uba ya kwato"
"Duhu" a nan na nufin iko miyagu. AT: "ikon miyagu da suka bi da mu"
"ƙaunataccen Ɗan Allah Uba, Yesu Almasihu"
Bulus yakan yi magana kamar masubi suna "cikin" Yesu Almasihu ko kuma "cikin" Allah. AT: "ta wajen Ɗan mun sami fansa."
"fansa; Ɗansa ya gafarta zunuban mu" ko kuma "Uban ya gafarta mana ta wurin Ɗansa"
A nan "sura" baya nufin wakilcin wani abu da ake gani. Maimakon haka, "sura" a nan yana nufin cewa ta wurin sanin Ɗan, za mu iya koya yadda Allah Uban yake
Wannan wata suna ce ta Yesu mai muhimmanci, Ɗan Allah.
"Ɗan shine forƙon halitta duka." Furcin nan "Ɗan forƙon halita duka" ba nufin haifuwar Yesu a Baitalami yake ba. Maimakon haka, yanu nufin matsayin dawwawamar Allah Uban. A nan "forƙon halitta duka" na nufin "mafi muhimmanci". Yesu shine mafi muhimmanci da kuma "Ɗan" Allah na musamman. Shi Allah ne. Kalmar "Ɗa" a nan yana nuna dangantaka mafi kusa da Yesu ke da shi da Uban. Ba za'a iya fahimtar wannan dangartakar ba har sai kuma kun yi amfani da kalmomin "ɗa" da "uba" a harshenku.
AT: "Domin Ɗan ya halicci dukkan abubuwa" ko kuma "Allah ya sa Ɗan ya halicci dukkan abubuwa"
Ɗan ya halicci dukan abubuwa wa kansa, wanda sun haɗa da kursiyai, mulkoki ko sarautai, hukumomi, da ikoki
"shi ne ya rayu kafin dukkan abubuwa"
Bulus a nan yana maganar yadda Ɗan ke mulkin dukan abubuwa kamar yana rike da komai a wuri ɗaya. "ya rike komai wuri ɗaya"
"Yesu Almasihu, Ɗan Allah ne kan"
Bulus yana maganar matsayin Yesu a kan ikilisiya kamar kan da ke jikin mutum ne. Kamar yadda kai yana mulkin jiki, haka ma Yesu yana mulkin ikilisiya.
"tushen iko." shine shugaba na forko ko kuma wanda ya ƙirƙiro.
Yesu shi ne forkon mutum da ya mutu ya kuma tashi da rai, ba domin ya sãke mutuwa kuma ba.
"ta wurin jinin da Yesu ya zubar a bisa giciye"
A nan "jini" ya tsaya ne a madadin mutuwar Amasihu a bisa giciye.
"Akwai wani lokaci da ku masubi a Kolosi ma"
"kamar mutane ne da Allah bai san su ba" ko kuma "turo Allah gefe"
Bulus yana bayana Kolosiyawan kamar ana iya gani da ido yadda Yesu ya tsabtace su, ya saka musu tufafi masu tsabta, sa'an nan ya kawo su su tsaya a gabar Allah Uba.
Bulus yana amfani ne da waɗannan kalmomi biyun ya nanata ra'ayin magana ɗaya na zama kammalallu. AT: "kammalallu"
Wannan maganar yana tsaye ne a madaɗin "a fuskar Allah" ko kuma "a zuciyar Allah"
da masubin suka yi shela
"ga kowane mutum a duniya"
A zahiri dai Bulus bawan Allah ne. AT "bishara wadda ni, Bulus, na bauta wa Allah ta wurin yin shela"
Bulus yana magana ne game da shan wahala da ya cigaba da ɗanɗanawa. Yayiwu yana amincewa wa ne anan da cewa akwai wata shan wahala da shi da kuma duk sauran masubi zasu jure kafin Almasihu ya sake zuwa, da kuma cewa Yesu yana haɗakai tare da su cikin ɗanɗana waɗannan wahalu a cikin ruhu. Haƙiƙa ma'anar Bulus anan ba shine cewa wahalar Almasihu kaɗai bai isa tanaɗin ceto ga masubi ba.
Bulus yana magana game da jikinsa kamar wata randa ce da ke iya riƙe wahala.
Bulus yakan yi magana game da ikilisiya, kungiyar dukan masubi, kamar ita ce jikin Yesu.
Wannan na nufin domin cika manufan bisharar Allah, wadda shine a yi wa'azin ta a kuma gaskata. " maganar Allah" anan na nufin saƙo daga Allah. AT: "a yi biyayya da abinda Allah ya umurta"
AT: "Wannan shine asirin gaskiya da Allah ya ɓoye
kalmomin nan "shekara da shekaru" da kuma "zamanai" na nufin tsawon lokaci daga halitar duniya har zuwa lokacin da aka yi wa'azin bisharar.
AT: "a yanzu Allah ya bayyana ta"
Bulus yana maganar darajar wanan asirin gaskiya game da Allah kamar wata taskar dukiya ce mai daraja. "arziki"
Bulus yana maganar masubin kamar su wasu randuna ne da Yesu yake cikin su. Wannan shine wani hanayarsa na bayyana dayantakar masu bi da Almasihu.
"don haka za ku iya sa rai da gabagaɗin samun ɗaukakar Allah"
Waɗanan kalmomi basu haɗa da Kolosiyawa ba.
"muna bada ƙashedi ga kowa"
Zaku iya faɗin a wadda za a miƙa masa kowane mutum. AT: "don mu miƙa kowanne mutum ga Allah"
Zama cikakke na nufin kammalalle a ruhu. AT: "kammalalle a ruhu"
1Ina so ku san yadda na sha faman gaske dominku, domin wadanda ke a Lawudikiya, da kuma wadansu da yawa da a jiki basu taba ganin fuska ta ba. 2Na yi aiki saboda zuciyar su ta sami karfafawa ta wurin hada su cikin kauna zuwa dukan arziki na tabbaci da fahimtar asirin gaskiya na Allah, wato Almasihu. 3A cikinsa dukan taskar hikima da sani ke boye.4Na fadi haka domin kada wani ya yaudare ku da jawabi mai jan hankali. 5Ko da yake ba na tare da ku a jiki, duk da haka ina tare da ku a cikin Ruhu. Ina murnar ganin ku a yanayi mai kyau da kuma karfin bangaskiyar ku cikin Almasihu.6Kamar yadda kuka karbi Almasihu Ubangiji, ku yi tafiya cikinsa. 7Ku kafu da karfi a cikinsa, ku ginu a kansa, ku kafu cikin bangaskiya kamar yadda aka koya maku, ku yawaita cikin yin godiya.8Ku lura kada wani ya rinjaye ku ta hanyar ilimi da yaudarar wofi bisa ga al'adun mutane, bisa ga bin abubuwan duniya, ba na Almasihu ba. 9A cikinsa ne dukan Allahntaka ta bayyana ta jiki.10Ku kuwa kun cika a cikinsa. Shine gaban kowanne iko da sarauta. 11A cikinsa ne aka yi maku kaciya, ba kaciya irin da yan adam suke yi ba, ta cire fatar jiki, amma ta kaciyar Almasihu. 12An binne ku tare da shi ta wurin baftisma. Kuma a cikinsa ne aka ta da ku ta bangaskiya a cikin ikon Allah, wanda ya tashe shi daga mutattu.13A lokacin da kuke matattu cikin laifofinku, a cikin rashin kaciyar ku ta jiki, ya rayar da ku tare da shi kuma ya yafe maku dukan laifofinku. 14Ya share rubutattun basussukanku da ka'idodin da suke gaba da mu. Ya cire su duka ya kafa su a kan giciye. 15Ya cire ikoki da sarautu. A fili ya falasa su ya shugabance su zuwa ga bukin nasara ta wurin giciyensa.16Saboda haka, kada kowa ya shari'anta ku ta wurin ci ko sha, ko kuma sabon wata, ko game da ranakun Assabaci. 17Wadannan sune inuwar abubuwan da ke zuwa nan gaba, amma ainihin shi ne Almasihu.18Kada kowa wanda ke son kaskanci da sujadar mala'iku ya sharantaku ku rasa sakamakonku. Irin wannan mutum yana shiga cikin abubuwan da ya gani ya zama mai girman kai a tunaninsa na jiki. 19Ba ya hade da kai. Daga kan ne dukan jiki da gabobi da jijiyoyi ke amfani suna kuma hade tare; yana girma da girman da Allah yake bayarwa.20In kun mutu tare da Almasihu ga ala'muran duniya, don me kuke rayuwa kamar kuna karkashin duniya: 21"Kada ku rike, ko ku dandana ko ku taba?" 22Dukan wadannan abubuwa karshen su lalacewa ne in ana amfani da su, bisa ga kaidodi da koyarwar mutane. 23Wadannan dokoki suna da hikima ta jiki irin ta addini da aka kago na kaskanci da kuma wahalar da jiki. Amma ba su da amfanin komai a kan abin da jiki ke so.
Bulus ya cigaba da ƙarfafa masubi da ke Kolosi da Lawudikiya don su gane cewa Almasihu Allah ne kuma yana nan cikin masubi, don haka su yi rayuwa kamar yadda sun karɓe shi.
Bulus yayi ƙoƙarin gaske da ganin cewa sun bunƙasa a zaman tsarkinsu da kuma fahimtar bishara.
Wannan wani birni ne da ke kusa da Kolosi wurin da akwai wata ikilisiya da Bulus ke yi masu addu'a.
A nan "ganin fuska" yana nufin mutumin da kansa. AT: "dukan waɗanda basu taɓa ganina da kai na ba" ko kuma "dukan waɗanda ban taba saduwa dasu fuska da fuska ba"
Bulus ya haɗa da Galatiyawa ko da shike ya yi amfani da wata wakilin suna dabam. AT: "saboda zukatansu da naku"
Wannan na nufin zuwan su kusa cikin dangantaka.
Bulus yana maganar mutum da ya gaskata da bisharar gaskiya ne kamar mutumin yana da arziki cikin abubuwan jiki
Allah ne kadai ke iya bayyana wannan sanin.
Yesu Almasihu shine asirin gaskiya da Allah ya bayyana.
Almasihu ne kaɗai ke iya bayyana gaskiyar hikimar Allah da kuma fahimita. AT: "Allah ya ɓoye dukan taskar hikima da kuma sani a cikin Almasihu"
Bulus yana magnar hikima da sanin Allah kamar su dukiyan kaya ne. AT: "matuƙar darajar hikima da sani"
Waɗannan kalmomi suna nufin abu ɗaya ne a nan. Bulus yana amfani da su tare ne domin ya nanata cewa dukan fahimta ta ruhu sun fito ne daga Almasihu.
Wannan yana nufin sa wani ya gaskata cewa wani abu ba gaskiya ba ne, sai yanayin mutumin ya canja har ma ya jawo wahalan sakamakon hakan.
jawabin da ke sa mutum yayi wani tunani dabam
Jikin mutum, na nufin mutumin. AT: "bana tare da ku fuska da fuska"
kasancewa da mutum a ruhu na nufin tunani game da mutumin ko da yaushe. AT: "Ina tunaninku ko da yaushe"
yin abubuwa yadda yakamata
"yadda babu wani ko wani abu da zai sa ku ku daina bada gaskiya"
Tafiya a cikin hanya na nufin yadda mutum ke rayuwarsa. Kalmar nan "a cikinsa" na nufin zama da dangantaka na kusa da Yesu da kuma aikata abubuwan ta ke faranta masa rai. AT: "yi rayuwanku yadda yake so ku yi" ko kuma "yi rayuwar da zai sa mutane su gani cewa ku nasa ne"
Waɗanan kalmomi suna bayyana abin da ake nufi da "tafiya a cikinsa."
Bulus yana maganar mutumin da ke da bangaskiya a cikin Almasihu kamar mutumin ya zama bishiya ne da ke girma da jijiyoyi masu zurfi a ƙasa
Bulus yana maganar mutumin da ke da bangaskiya na gaske a cikin Almasihu kamar wani gini ne da ke da tushe mai ƙarfi.
"ku dogara ga Yesu domin kowane abu"
Ya fi a bayyana wannan ba tare da ambata suna ko kuwa jan hankali zuwa ga mai koyarwar ba, wato Abafaras ((1:7). AT: "kamar yadda kuka koya" ko kuma "kamar yadda sun koya maku" ko kuma "kamar yadda ya koya maku"
Bulus yana maganar yin godiya kamar wani abu ne da mutum na iya daɗa samu. AT: "zama da godiya ga Allah sosai"
"Ku tabbatar cewa"
Bulus yana maganar yadda mutum ke iya gaskata koyaswar ƙarya
koyaswar addini da imanin da basu fito daga Allah ba amma tushen su daga tunanin mutum ne game da Allah da kuma rayuwa.
Bulus yana maganar ra'ayoyin ƙarya da basu kawo komi kuma basu da daraja kamar su randuna ne da babu komi a cikin su.
Duk imanin tsarin al'adun Yahudawa da al'ummai (Halinawa) banza ne. "Abubuwan duniya" na iya nufin ruhohi miyagu da ke cewa sune ke mulkin duniya kuma suna samun girmamawa daga mutane. Amma kima cikin masu fassara sun gano "abubuwan duniya" a matsayin takaitatcen koyaswar mutane game da duniya.
"Halin Allah gabaɗaya ya kasancewa ta siffar jiki a cikin Almasihu"
Bulus yana maganar mutane kamar su wani akwati ne da Allah ya ajiye Almasihu a ciki. AT: "ku kun zama cikakku a cikin Almasihu"
Almasihu ne mai mulki bisa kowane mai mulki
Bulus yana maganar waɗanda ke na Almasihu kamar suna cikin jikin Almasihu ne. AT: "A lokacin da kuka haɗu da ikilisiya ta wurin baftisma, Allah ya maku kaciya"
Da wannan maganan, Bulus yana cewa Allah ya sa masubi sun zama ƙarɓaɓɓu a gareshi ta wata hanya da ke tunashe shi da kaciya, bikin da Yahudawa ke yi domin shigar da 'ya'ya maza cikin al'umman Isra'ila.
Bulus yana maganar baftisma da kuma haɗin kai da taron masubi kamar binnewa ne tare da Almasihu. AT: "Allah ya binne ku da Almasihu a lokacin da kuka haɗa kai da ikilisiya ta wurin baftisma.
Da wannan maganan, Bulus yana maganar sabon rayuwar ruhaniya ta masubi da ke iya yiwuwa domin Allah ya sa Almasihu ya sake rayuwa kuma. AT: "domin kun haɗa kanku da Almasihu, Allah ya ta da ku"
A nan a tayar wata karin magana ne da ke sa mutum da ya mutu ya dawo da rai kuma. AT: "Allah ya tashe ku" ko kuma "Allah ya sa kun rayu kuma"
Bulus ya yi maganar rashin tuba zuwa ga Allah kamar mutuwa ce. AT: "A sa'ad da ku masubi ta Kolosi ba ku iya tuba ga Allah ba"
Da wannan maganan, Bulus yana maganar samun sabon rai na ruhaniya kamar sumun rai na jiki ne.
Dama ku matattu ne domin dalilai biyu: 1) ku matattu ne a ruhaniya, kuna rayuwar aikata zunubi ga Almasihu da kuma 2) ba a yi maku kaciya bisa ga shari'ar Musa ba.
"ya yafe mana, da mu Yahudawa da ku Helinawa, dukan laifofinmu"
Bulus yana maganar yadda Allah ke gafarta zunubanmu kamar yadda mutumin da yake bin mutane da yawa bashin kuɗi ko kayayyaki da yawa ya jante lissafin bashin yadda baza su biya kuma ba.
A lokacin Romawa, ba wuya sojojin Roma su yi fareti na nasara idan sun komo gida, suna nuna duk 'yan firsinan da kuma kayayyakin yaƙi da suka kwaso su sanadiyyar yaƙi. Allah na da nasara bisa ikoki da kuma hukumomin miyagu.
A nan "giciye" yana madadin mutuwar Almasihu a bisa giciye.
Shari'ar Musa ya shafi abinda mutum na iya ci da kuma sha. "gama abinda kuke ci ko abinda kuke sha"
Shari'ar Musa ya keɓe ranakun bukukuwa, sujada, da kuma miƙa hadaya. "don yadda kuke bikin ranakun ci da sha ko sabon wata ko kuma Asabar"
Inuwa bata ba da ainihin yadda abu yake ko kuma sifar abu. Hakannan kuma, al'adun addini kamar su shari'ar Musa na iya nuna zahirin Yesu Almasihu kaɗan ne kawai.
A nan wannan na nufin "gaskiyar," abinda ke bada "inuwar"
A nan Bulus yana maganar masu koyarwar ƙarya kamar su alƙalai ne masu cin hanci da rashawa a takaran wasan guje-guje da tsalle-tsalle da za su iya hana masubi samun kyautar nasaran da ya cancance su, kuma yana maganar Almasihu a matsayin mai ba da wannan kyautar ga mai nasara a irin wannan takara. AT: "kada kowa ... ya hana ku cin nasarar samun wannan kyautar"
Kalmar "ƙasƙanci" a nan na nufin yin abubuwa domin mutane su ga cewa mutum yana da ƙasƙanci. AT: "wanda ke so ku yi abubuwa domin ku nuna cewa kuna da ƙasƙanci"
A nan Bulus yana magana ne game da mutanen da suke ƙirari cewa suna da mafarkai da kuma wahayoyi daga Allah kuma suna magana game da su da nuna girman kai
A nan Bulus yana cewa tunani ta hanyar zunubi na sa mutum ya nuna cewa ya fi kowa sani. AT: "yana girman kai ta wurin tunaninsa na jiki"
A nan ana maganar mutum mai taƙama kamar wani abu ne da za a iya hura shi da iska ya yi girma fiye da yadda yakamata ya kasance
A nan kalman "jiki" yana nufin yanayin mutuntaka na zunubi. "tunanin zunubi da ya fi masa sauƙin yi"
Ana maganar wanda bai gaskanta da Yesu ba a matsayin wanda bai manne wa kan da tabbaci ba. Ana maganar Almasihu ne a matsayin kan jikin. AT: "Bai cafke Almasihu ba, wanda shi ne kamar kan jikin" ko kuma "Bai manne wa Almasihu ba, wadda shine kamar kan jikin"
Bulus yana maganar ikilisiya, da Yesu ne ke mulkin ta yana kuma inganta ta, kamar ita wata jikin mutum ne. AT: "Daga kan ne Allah ke biyan bukatar dukkan jiki ta wurin gaɓoɓi da jijiyoyi yana kuma haɗa su tare"
Da wannan maganan, Bulus yana magana game da maibi ne a matsayin wanda ke tare da Almasihu cikin ruhu: kamar yadda Almasihu ya mutu, hakama maibi ma ya mutu a cikin ruhu; kuma yadda Almasihu ya dawo da rai, hakama masubi zasu dawo da rain, wato maibin ya dawo da rai a ruhu zuwa tuba ga Allah.
Bulus yayi amfani da wannan tambaya ne domin ya tsauta wa Kolosiyawan saboda biye wa ra'ayoyin da ke duniya. AT: "ku daina biyayya da ra'ayoyin duniya! Ku daina gaskata su idan sun ce , 'ku ... taɓa!'"
"yi tunani lallai ne ku yi biyayya da sha'awace-sha'awacen duniya"
"tunanin, sha'awace-sha'awacen, da kuma ra'ayoyi masu yawa na mutanen duniya masu aikata zunubi
"Waɗannan dokokin sun zama kamar hikima ne ga marasabi domin sun sa waɗanda suke bin su su zama kamar masu ƙasƙanci ta wurin raunata jikunan su ne"
"basu hana ku biye wa sha'awace-sha'awacen mutuntakan ku"
1Idan dai Allah ya tashe ku tare da Almasihu, ku nemi abubuwan da ke sama, inda Almasihu ke zaune a hannun dama na Allah. 2Yi tunanin a kan abubuwan da ke sama, ba a kan abubuwan da ke kasa ba. 3Gama ku kun mutu, ranku kuma yana boye tare da Almasihu cikin Allah. 4Sa'anda Almasihu ya bayyana, wanda shine ranku, sa'anan ku kuma zaku bayyana tare da shi cikin daukakarsa.5Ku kashe sha'awacce-sha'awaccen da suke a duniya - zina da fasikanci, rashin tsarki, muguwar sha'awa, mummunar buri, da kuma kwadayi, wadda shine bautar gumaka. 6Saboda wandannan abubuwa ne fushin Allah ke zuwa a kan marasa biyayya. 7A cikin wadannan abubuwa ne kuka yi rayuwa a da da kuke zauna a cikinsu. 8Amma yanzu dole ku kawar da wadannan - zafin rai, fushi, mugayen manufofi, zage-zage, da kazamar magana daga bakinku.9Kada ku yi wa juna karya, domin kun tube tsohon mutumin da ayyukansa, 10kun kuma yafa sabon mutum, wanda ake sabontawa cikin sani bisa ga surar wannan da ya hallice shi. 11A nan ne inda babu Baheline da Bayahude, mai kaciya da marar kaciya, bare, baubawa, ko Basikitiye, bawa ko yantacce, amma Almasihu shine duka, yana kuma cikin duka.12A matsayin ku na zababbun Allah, masu tsarki da kaunatattu sai ku yafa jinkai, ayyukan kirki, saukin kai, kamewa da hakuri. 13Yi hakuri da juna. Ku yi wa juna alheri. Idan wani na da damuwa da wani, ku gafarta kamar yadda Ubangiji ya gafarta maku. 14Fiye da wadanan abubuwa duka, ku kasance da kauna, wanda itace cikakkiyar kammalla.15Bari salamar Almasihu ta mallaki zukatanku. Sabili da wannan salama ce aka kiraye ku cikin jiki daya. Ku yi godiya. 16Ku bar maganar Almasihu ta zauna a cikinku a yalwace. Da dukan hikima, ku koyar, ku kuma gargadi juna da zabura, wakoki, da wakokin yabo na ruhaniya. Kuna rairawa tare da godiya cikin zukatanku ga Allah. 17Kuma duk abin da zaku yi cikin magana ko aiki ku yi duka cikin sunan Ubangiji Yesu. Kuna yin godiya ga Allah Uba ta wurinsa.18Mata, ku yi biyayya ga mazajenku, yadda yakamata a cikin Ubangiji. 19Mazaje, ku kaunaci matayenku, kada ku muzguna masu. 20Yaya, ku yi wa iyayen ku biyayya cikin dukan komai, domin wannan yana faranta wa Ubangiji rai. 21Ku Ubanni, kada ku cakuni 'ya'yanku domin kada su karaya.22Bayi, ku yi wa iyayengijinku na jiki biyayya cikin kowane abu, ba tare da bautan ganin ido ba don faranta wa mutane rai, amma da sahihiyar zuciya. Ji tsoron Ubangiji. 23Duk abin da kuke yi, ku yi aiki daga zuci domin Ubangiji ba domin mutane ba. 24Kun san cewa, zaku karbi sakamako na gado daga wurin Ubangiji. Domin Ubangiji Almasihu kuke bauta wa. 25Domin kowa ya yi rashin adalci zai karbi sakamakon rashin adalcin da ya yi, kuma babu son kai.
Bulus yana yi wa masubi gargaɗi cewa da shi ke su na Almasihu ne, lallai ne su kiyaye aikata wasu abubuwa.
Wannan karin magana ne da ke nufin "saboda"
Kamar yadda Allah ya tashi Almasihu zuwa sama, haka kuma Allah yana ganin masubi da ke Kolosi kamar su ma ya tashe su zuwa sama.
"abubuwan da ke cikin aljanna"
Zama "a hannun dama na Allah" alama ce ta karbar girma da iko daga wurin Allah. AT: "inda Almasihu ke zaune a wurin girma da iko a gefen Allah"
Kamar yadda Yesu ya mutu zahiri, haka ma Allah yana ganin masubi na Kilosi a matsayin waɗanda sun mutu tare da Almasihu.
Bulus yana maganar rayukan mutane kamar wasu abubuwa ne da ake iya ajiye su cikin akwati kuma yana magana kamar Allah shi ne wannan akwati. AT: Wannan na iya nufin 1) "yana kamar Allah ya dauki rayukan ku ya ɓoye tare da Almasihu a gaban Allah" ko 2) "Allah ne kaɗai masani ainihin abinda rayukanku suka ƙumsa, kuma shi zai bayyana shi a lokacin da ya bayyana Almasihu"
Almasihu ne ke ba da rai na ruhu ga maibi.
Bulus yana maganan sha'awacce-sha'awaccen zunubi kamar su gaɓoɓin jikin mutum ne da mutane ke amfani da su su gamsar da kan su.
"halin ƙazamta"
"sha'awar banza"
"da kuma kwaɗayi, wadda ke cikin bautar gumaka" ko "kuma kada ku zama da kwaɗayi domin shi ne bautar gumakai" (UDB)
Fushin Allah a kan waɗanda su ke aikata mugunta kamar yadda ya bayyana ta wurin hukunta su.
"mutane marasa biyayya" ko kuma "mutanen da sun ƙi yi masa biyayya"
Bulus yana maganar yadda mutum ke rayuwa kamar wata hanya ce da mutum ke tafiya a ciki. AT: Waɗanan ne abubuwan da kuke yi a da"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "da kuke yin waɗanan abubuwan" 2) "da kuke rayuwa cikin mutanen da ke rashin biyayya ga Allah"
"marmarin aikata mugunta"
maganar da ke ɓata wa mutane rai
kalmomi da basa nuna ladabi cikin hira
A nan "baki" yana nufin magana. "cikin maganar ku"
Bulus a nan yana maganar yadda mai bi ke kin tsohon halinsa na zunibi kamar wani tsohon tufafi da ake cirowa domin a yafa wani sabon tufafin. Kamar yandda Bulus yake magana, an saba moran tufafi wajen yin magana game da hali a cikin jama'ar Isra'ila.
Wannan na nufin Yesu Almasihu.
Waɗannan kalmomin misalai ne a sashin mutanen da Bulus ya ce ba kome bane ga Allah. Allah yana ganin kowane mutum iri ɗaya ne, babu zancen jinsi, addini, ƙasan da mutum ya fito, matsayin jama'a da mutum ya fito. AT: "jinsi, addini, al'ada, da kuma jama'ar da mutum ya fito ba kome bane"
baƙo wanda bai san al'adun inda yake zama ba
Mutumin da ya fito daga Sikitiya, da ba ya Daular Roma. Helinawa da Romawa kan yi amfani da wannan kalman wa mutumin da ya girma a wurin da ake aikata mugunta a kowane lokaci.
Babu abinda yake a ware ko a cire daga mulkin Almasihu. AT: "Almasihu na da muhimmanci kuma yana rayuwa a cikin duka mutanen sa"
AT: "A matsayin waɗanda Allah ya zaɓa wa kansa, wadda yake marmarin ganin cewa suna rayuwa dominsa kaɗai, kuma wadda yake ƙauna"
Aan maganar waɗannan halaye kamar wasu tufafi ne da ake iya sa wa. AT: "ku zama da jinƙai, halin kirki, sauƙin kai, kamewa, da zuciyar haƙuri" ko kuma "ku zama masu jinƙai, halin kirki, sauƙin kai, kamewa, da hakuri"
"Ku yi haƙuri da juna" ko kuma "Ku riƙe juna ko da kun ba wa juna kunya"
"ku bi da juna fiye da yanda sun cancanci ku bi da su"
AT: "na da wani dalilin da"
AT: "ku yi ƙaunar juna domin hakan zai haɗa ku tare"
Bulus yana maganan salamar da Almasihu ke bayarwa kamar wani mai mulki ne shi. Wannan na iya nufin 1) "Ku yi dukan kome domin ku sami salama a dangantakar ku da juna" ko kuma 2) "Ku bar Allah ya baku salama a cikin zuciyarku"
A nan "zukata" na nufin hankalin mutane. AT: "a cikin hankalin ku"
Bulus yana maganar Kalmar Almasihu kamar wani mutum ne da ke iya kasancewa a cikin sauran mutane. "Maganar Almasihu" na nufin koyaswar Almasihu. AT: "ku yi biyayya da koyaswar Almasihu" ko kuma "A ko da yaushe sai ku gaskata da Alkawarai na Almasihu"
"ku gargaɗas ku kuma ƙarfafa juna"
"da dukan ire-iren waƙoƙin yabo ga Allah"
A nan "zuciya" na nufin hankalin mutum. AT: " rairawa tare da godiya cikin zukatanku" ko "raira tare da godiya"
yin magana ko aikatawa
"domin girmama Almasihu Yesu" ko kuma "tare da ikon Ubangiji Yesu"
Ma'anoni masu yiwuwa sun akamar haka 1) domin girmama Ubangiji Yesu" ko kuma 2) "domin ya sa mutane su san cewa ku na Ubangiji Yesu ne su kuma yi tunani mai kyau game da shi" ko kuma "kamar Ubangiji Yesu ne da kansa yake yi"
Wannan na nufin 1) "domin ya yi manyan ayyuka" ko kuma 2) "domin ya sa mutane su iya magana da Allah suna masa godiya."
"Mata, ku yi biyayya"
"ya kamata" ko kuma "daidaine"
kada ku yi musu kaushi "kada ku yi fushi da"
"kada ku sa 'ya'yanku su yi fushi a banza"
"ku yi wa iyayengijinku na jiki biyayya"
"abubuwa. Kada ku yi biyayya a lokacin da Iyayengijinku ke kallo kaɗai, kamar kuna buƙatar gamsar mutane ne kawai"
"zuciya" anan na nufin tunani ko kuma manufa, AT: "da dukkan manufar gaskiya" ko kuma "da rashin munafinci"
"kamar yadda za ku yi wa Ubangiji aiki"
"gadon sakamakonku"
Anyi maganar karbar abin da Allah ya alkawarta wa masubi kamar gadan mallakar dukiya daga wani ɗan gida ne.
Jumlar nana "karbi sakamako" na nufin a hukunta. AT: za a hukunta dukan wanda ya yi rashin adalci" ko kuma "Allah zai hukunta duk wanda ya yi rashin adalci"
wanda ke kowane irin kuskure na ganganci
A nuna sonkai na nufin a ba wa wasu hukunci daban da na waɗanda suka aikata laifi iri ɗaya. AT: "Allah yana shar'anta kowa daidai" ko kuma "Allah yana shar'anta kowa bisa ga tsari ɗaya"
1Ku iyayengiji, ku ba bayinku abin ke daidai ya kuma dace garesu. Kun sani cewa ku ma, kuna da Ubangiji a sama.2Ku cigaba da himmantuwa ga yin addu'a. Ku zauna a fadake cikin addu'a da godiya. 3Ku yi addu'a tare domin mu kuma, domin Allah ya bude kofa domin kalmar, a fadi asirin gaskiyar Almasihu. Don wannan ne nake cikin sarka. 4Ku yi addu'a domin in iya fadinsa daidai, yadda yakamata in fada.5Ku yi tafiya da hikima game da wadanda suke a waje, ku yi amfani da lokaci. 6Bari maganarku ko yaushe ta zama ta alheri. Bari ta zama da dadin ji domin ku san yadda za ku amsa wa kowanne mutum.7Game da abubuwan da nake ciki, Tikikus zai sanar maku da su. Shi kaunataccen dan'uwa, amintaccen bawa, shi abokin barantaka na ne a cikin Ubangiji. 8Na aike shi wurinku don wannan, domin ku iya sanin halin da muke ciki, don kuma ya karfafa zukatanku. 9Na aike shi tare da Onisimus, amintacce da kuma kaunataccen dan'uwa, wanda daya ne daga cikin ku. Za su gaya maku duk abin da ya faru anan.10Aristarkus, abokin sarka na, yana gaishe ku da Markus, dan'uwan Barnaba (wanda a kansa ne kuka sami umarni; in yazo, ku karbe shi), 11da kuma Yesu wanda ake kira Yustus. Wadannan ne kadai daga cikin masu kaciya abokan aiki na domin mulkin Allah. Sun zama ta'aziya a gare ni.12Abafaras na gaishe ku. Shi daya daga cikinku ne kuma bawan Almasihu Yesu ne. Kullum yana maku addu'a da himma, don ku tsaya cikakku da hakikancewa a cikin nufin Allah. 13Gama ina shaidarsa a kan ya yi aiki da himma domin ku, domin wadanda ke Lawudikiya, da na Hirafolis. 14Luka kaunataccen likita da Dimas suna gaishe ku.15Ku gai da 'yan'uwa dake a Lawudikiya, da Nimfa da ikilisiyar da ke cikin gidanta. 16Lokacin da aka karanta wannan wasika a tsakanin ku, sai a karanta ta kuma a cikin ikilisiyar Lawudikiya, ku kuma tabbata kun karanta wasika daga Lawudikiya. 17Ku gaya wa Arkibas, "Mai da hankali ga hidimar da ka karba cikin Ubangiji, don ka cika shi."18Wannan gaisuwa da hannu na ne - Bulus. Ku tuna da sarka na. Alheri ya tabbata a gare ku.
Bayan magana da iyayengiji, Bulus ya kammala umurnan sa na musamman ga masubi daban-daban a cikin ikilisiyar da ke Kolosi.
Waɗannan kalmomi mun suna da ma'ana kusan ɗaya kuma an yi amfani ne da su domin a nanata abubuwan da ke daidai masu kyau.
Allah yana so dangartakar da ke tsakanin maigida da baransa ya kasance da ƙauna kamar yadda Allah, Ubangijin mu na sama, yake ƙaunar bayinsa na duniya, haɗe da shugabanen barori na duniya.
Kalmar "mu" a nan na nufin Bulus da Timoti ba 'yan Kolosi ba.
"ku dinga yin addu'a da aminci" ko kuma "ku dinga yin addu'a ba fasawa"
Buɗe kofa a nan na nufin ba wa mutum zarafi ya yi wani abu. AT: "Allah zai tanadar da zarafi"
Wannan yana nufin bisharar Yesu Almasihu, wanda ba a gane ba kafin Yesu ya zo.
"sarƙa" a nan na nufin kasancewa a cikin kurkuku. AT: "Saboda shelar sakon Yesu Almasihu ne yanzu ina cikin kurkuku"
"Ku yi addu'a in iya faɗin sakon Yesu Almasihu daidai"
Akan yi amfani tafiya domin bayyana yadda mutum ke gudanar da rayuwarsa. AT: "Ku yi rayuwa a hanyar da zai sa waɗanda ba masubi ba su ga cewa kuna da hikima"
AT: "ku yi iyakar abubuwa masu kyau da zaku iya yi da lokacin ku" ko kuma "ku yi amfani da lokacinku da kyau"
Maganar alheri da kuma main daɗin ji da ke koya wa wasu ko wadda wasu ke jin daɗin ji. AT: "Bari taɗinku a ko yaushe ya zama na alheri da jan hankali"
"domin ku san yadda za ku amsa tambayoyi daga kowa game da Yesu Almasihu" ko kuma "domin ku iya bi da kowane mutum da kyau"
"dukkan abin da ya dinga faruwa da ni" (UDB)
"abokin bauta." Duk da yake Bulus mutum mai 'yanci ne, yana ganin kansa a masayin Bawan Almasihu ne kuma yana ganin Tikikus a masayin abokin bauta ne.
Waɗannan kalmomi basu haɗa da 'yan Kolosi ba
A kan ɗauka da cewa zuciya itace cibiyar shauƙi mai yawa. )
Bulus ya ce da Onisimus dan'uwa Kirista da bawan Almasihu.
"Tikikua da Onisimus za su gaya"
Za su gaya wa masubi a Kolosi duk abinda ke faruwa a wurin da Bulus ke zama a halin yanzu. Al'adu na cewa Bulus yana Roma a tsare a gida ko kuma a cikin kurkuku a wannan lokacin.
yana tare da Bulus a kurkuku a Afisa lokacin da Bulus ya rubuto wanan wasiƙar zuwa Kolosi.
"in Markus ya zo"
"Wannan wani mutum ne da yayi aiki tare da Bulus shi ma"
Bulus ya yi amfani da "kaciya" a nan da nufin Yahudawa domin, bisa ga shiri'ar Tsohon Alkawari, lalle ne a yi wa dukkan Yahudawa maza kaciya. AT: "Waɗannan mutane ukun ne kadai masubi Yahudawa da ke aiki tare da ni domin shelar Allah a matsayin sarki ta wurin Almasihu
"Waɗannan mutanen— Aristarkus, Markus, da Yustus kadai ne daga cikin masu kaciya"
Abafaras ne mutumin da ya yi wa'azin bishara ga mutanen da ke cikin Kolosi. (Dubi: 1:7)
"daga garinku" ko kuma "ɗan garinku"
"wani almajirin Almasihu Yesu mai himma"
"yana yi muku addu'a da naciya"
"ku tsaya kamalallu da gabagaɗi"
"na lura cewa ya yi aiki tukuru domin ku" (UDB)
Wannan wani abokin aiki ne tare da Bulus.
Wannan yanan nufin 'yan uwa masubi, a haɗe da maza da mata.
wata birni ce a kusa da Kolosi sosai da ke da wata ikilisiya
Wata mata mai suna Nimfa da ikilisiya da ke taruwa a gidanta domin sujada. AT: "Nimfa da taron masubi da ke haɗuwa a gidanta" (UDB)
Bulus yana tunashe da Arkibas game da hidimar da Allah ya ba shi kuma wanda wajabi ne ya yi. Kalmomin nan "mai da hankali," "ka karɓa" da kuma "ka cika" duka suna zuwa ga Arkibas ne shi kaɗai
Bulus yakan yi maganar sarƙa idan yana nufin ɗaurinsa a kurkuku. AT: "Ku tuna da ni ku yi mini addu'a yayin da ina kurkuku."
"Alheri" a nan yana a matsayin Allah, mai nuna alheri ko kuma ayyukan kirki ga masubi. AT: "Ina addu'a don Ubangiji Yesu Almasihunmu ya cigaba da nuna alherinsa a gareku duka" (UDB)
1Bulus, Sila, da Timoti zuwa ga Ikilisiyar Tassalonikawa cikin Allah Uba da Ubangiji Yesu Almasihu. Alheri da Salama su kasance a gare ku.2Kullum muna bada godiya ga Allah domin ku dukka, kamar yadda muke ambaton ku a addu'o'in mu. 3Muna tunawa da ku ba fasawa a gaban Allahn mu da Ubanmu kuma ayyukanku na bangaskiya, da kauna. Da hakurin bege na abinda ke gaba cikin Ubangijinmu Yesu Almasihu.4'Yan'uwa kaunatattu na Allah, Mun san kiran ku, 5yadda bishararmu ta zo gare ku ba ta magana kadai ba, amma da iko, ta wurin Ruhu Mai Tsarki, haka kuma tawurin tabbatarwa. Ta haka kuma, kun san irin mutanen da muke acikin ku kuma domin ku.6Kun zama masu koyi da mu da kuma Ubangiji, kamar yadda kuka karbi kalmar cikin tsanani mai yawa da murna tawurin Ruhu Mai Tsaki. 7Sakamakon haka, kuka zama abin misali ga dukkan wadanda ke Makidoniya da na Akaya wadanda suka bada gaskiya.8Gama daga gare kune maganar Allah ta bazu ko ina, ba kuwa Makidoniya da Akaya kadai ba. A maimako, har ma zuwa ko ina bangaskiyarku cikin Allah ta kai. Don haka, bama bukatar muce maku komai. 9Domin su da kansu suna bada labarin irin zuwan mu gare ku. Suna fadin yadda kuka juyo ga Allah daga bautar gumaka don ku bautawa Allah mai rai. 10Suna bayyana cewa kuna jiran bayyanar Dansa daga sama, wanda ya tasar daga matattu. Wannan shine Yesu, wanda ya 'yantad da mu daga fushi mai zuwa.
Bulus ya bayyana kansa a matsayin marubucin wannan wasiƙa, ya kuma gaida Ikilisiya da ke Tasalonika
littafi ta nuna a sarari cewa Bulus ne marubucin wannan wasiƙar.
"Alheri" da "salama" kalmomi ne da ke bayyana halin kirki na zaman lafiya da mutum ke nuna wa zuwa ga mutane. AT: "Allah ya yi muku alheri ya kuma baku salama"
"Ku" na nufin masubi da ke Tasalonika.
"Kullum" a nan na ba da ra'ayin cewa a duk lokacin da Bulus ke addu'a, ba ya fasa miƙa Tasalonikawa ga Allah cikin addu'a.
"muke yi muku addu'a"
ayyuka da aka aikata domin gaskatawa da Allah
Bulus ya cigaba da godiya da yaba wa masubi da ke Tasalonika saboda bangaskiyarsu ga Allah.
A nan wannan na nufin Masubi maza da mata.
Kalman "mu" na nufin Bulus ne, Sila da Timoti, ba masubi na Tasalonika ba
"ba ta abin da mun faɗa kaɗai ba"
AT: 1) Ruhu mai Tsarki ya ba Bulus da abokansa ikon shelar bishara, ko kuma 2) Ruhu mai Tsarki ya sa wa'azin shelar bishara ta zama da iko a cikin masubi da ke Tasalonika, ko 3) Ruhu mai Tsarki ya nuna gaskiyar da ke cikin shelar bishara ta wurin mu'ujizai, al'ajabai da abin ban mamaki.
ana iya sa wannan haka. AT: "Allah ya sa kun tabbata cewa gaskiya ne"
"yadda muka bi da kanmu lokacin"
yin "koyi" na nufin "aikata kamar" ko kuma "kwaikwayon halin wani."
"marabci saƙon" ko kuma "karɓan abin da muka faɗa"
"a mawuyacin lokaci" ko kuma " cikin tsanani"
Wannan wata tsohowar lardi ce a cikin kasar Girka.
...
"magana" anan na nufin "saƙo." AT: "koyarwan Ubangiji"
A nan Bulus yayi magana game da shaidar Masubi da ke Tasalonika kamar wata ƙarar ƙararrawa ko kuma kayan kiɗa da aka buga
Bulus na nufin ikilisiyu da ke kewayen wancan yanki, da suka ji game da masubi na Tasalonika.
A nan "da kansu" na jaddada game da mutanen da suka ji game da masubi da ke Tassalonika.
A nan "zuwa" na nufin irin marabtan da Bulus da abokansa suka samu. AT: "yadda kuka marabce mu da kyau"
A nan "juyo ga...daga" na nufin kassance wa da biyayya ga wani mutum da kuma rashin biyayya ga wani. AT: "Suka faɗa yadda kuka daina bautar gumaka kuka fara bautawa Allah rayaye da gaskiya"
Wannan muhimmin suna ne na Yesu da ke bayyana dangantakarsa da Allah.
"Wanda Allah ya sa shi ya sake rayuwa kuma"
"domin ya zama ba mattace kuma ba." Wannan na nufin tayar da mutum daga cikin matattu, ya kuma kassance rayaye.
A nan Bulus ya haɗa har da masubi na Tasalonika.
1Domin ku da kanku kun sani, 'yan'uwa, cewa zuwan mu gareku, ba a banza yake ba. 2Kun kuma san yadda aka wulakantar damu, aka kuma kunyatar damu a Filibi, kamar yadda kuka sani. Muna nan kuwa da karfin zuciya cikin Allahnmu domin yi maku bisharar Allah cikin fama da yawa.3Domin kuwa gargadinmu zuwa a gare ku ba gurbatacciya bace, ko cikin rashin tsarki, ba kuma ta yaudara bace. 4A maimako, kamar yadda Allah ya amince damu, ya kuma damka mana amanar bishararsa, haka kuma muke yin magana. Muna maganar ba domin mu gamshi mutane ba, amma domin mu gamshi Allah. Domin shi ne yake gwada zuciyarmu.5Domin bamu taba yi maku dadin baki ba, ko sau daya, kamar yadda kuka sani, ko kwadayi a asirce, kamar yadda Allah shine shaidar mu. 6Bamu kuma nemi daukaka daga mutane ko daga gare ku ko kuma wadansu ba. Da mun so da mun mori ikonmu a matsayin manzannin Almasihu.7A maimakon haka, mun kaskantar da kanmu a tsakanin ku kamar yadda uwa take ta'azantar da 'ya'yan ta. 8Don haka muna da kauna domin ku, ba bisharar Allahnmu kadai muke jin dadin yi maku ba, amma harda bada rayukan mu domin ku. Domin kun zama kaunatattu ne a garemu, 9Kufa tuna, 'yan'uwa, game da aikinmu da famarmu. Dare da rana muna aiki sosai domin kada mu nawaita wa kowane dayan ku. A lokacin da muke yi maku bisharar Allah.10Ku shaidu ne, haka ma Allah, yadda muka yi rayuwar tsarki da kuma adalci da rashin abin zargi a wajenku wadanda kuka bada gaskiya. 11Don haka kun kuma sani yadda muka rika yi da kowannenku, kamar uba da 'ya'yansa, yadda muka yi ma ku garadi da kuma karfafa ku, mun kuma shaida. 12Domin ku yi tafiya a hanyar da ta dace ga Allah, wanda ya kira ku zuwa ga mulkinsa da kuma daukakarsa.13Domin wannan dalili ne yasa muke yi wa Allah godiya a koyaushe. Domin a lokacin da kuka karbi maganar Allah daga wurinmu wadda kuka ji, kun karbeta da gaske ba kamar maganar mutum ba. A maimako, kuka karbeta da gaskiyarta, kamar yadda take, maganar Allah. Wannan kalma kuma ita ce ke aiki a cikin ku wadanda kuka yi bangaskiya.14Domin ku 'yan'uwa, kun zama masu koyi da ikilisiyoyin Allah da ke Yahudiya cikin Almasihu Yesu. Domim kuma kun sha wahala irin tamu daga wurin mutanen kasarku kamar yadda suma suka sha a hannun Yahadawa. 15Yahudawane suka kashe Ubangiji Yesu da sauran Annabawa, kuma Yahudawane suka koro mu, Basu gamshi Allah ba. A maimako, suna hamayya da dukkan mutane. 16Sun kuma haramta mana yin magana da Al'ummai domin su sami ceto. Sakamakon haka kuwa kullum suna cika zunubansu. Fushi kuma ya afko kansu daga karshe.17Mu kuma, 'yan'uwa, mun rabu daku na karamin lokaci, a zahiri, ba a zuciya ba, mun kuma yi iyakar kokarinmu da marmarin ganin fuskarku. 18Domin mun yi maramarin zuwa gareku. Ni, Bulus, ba sau daya ba, amma Shaidan ya hanamu. 19To menene begenmu a gaba, ko murnarmu ko rawanin alfahari, a gaban Ubangijinmu Yesu a ranar zuwansa? Ko ba ku bane, da kuma sauran jama'a? 20Don kuwa kune daukakarmu da kuma farin cikinmu.
Bulus na bayyana hidimar masubi da kuma ladar da ke biye.
"ku" da "kanku" na nufin masubi da ke Tasalonika.
A nan ana nufin 'yan'uwa masubi maza da mata.
kalmar "mu" na nufin Bulus, Sila, da Timoti ne, banda masubi na Tasalonika.
Ana iya faɗin wannan ta wata hanya kamar haka. AT: " ya kassance mai daraja"
"aka zalunce mu, aka kuma ci mana mutunci"
"yayin da ake gwagwarmaya cikin gãba"
"cikin gaskiya da tsarki"
Allah ya gwada Bulus ya kuma tabbatar da amincinsa.
Bulus na nufin shelar saƙon bisharar.
kalmar "zuciyar" na nufin tunani da sha'awace sha'awacen mutum. AT: "wanda ya san tunaninmu da sha'awace sha'awacenmu"
Bulus na gaya wa masubi na Tasalonika cewa ɗabi'arsa ba bisa ga lallaɓa, son kai, ko kuma ɗaukaka kai ba ne.
"bamu taɓa yi maku magana cikin yabon ƙarya ba"
A nan "asirce" na bayana cewa an ɓoye abu daga sanin mutane. AT: " ko kuma mun yi amfani da kalmomi domin mu ɓoye ƙwaɗayi" ko kuma "ba mu yi amfani da kalmomi domin ɓoye muguwar sha'awar kuɗin ku ba"
"da mun nace maku ku ba mu kuɗi"
kamar yadda uwa take ta'azantar da 'ya'yan ta cikin tawali'u, haka ma cikin tawali'u ne Bulus, Sila da Timoti suke magana da masubi da ke cikin Tasalonika.
"Wannan ita ce yadda muka nuna ƙaunarmu a gare ku"
"mun ƙaunace ku"
Bulus yayi magana game da saƙon bishara da rayuwarsa da na mutane da suke tare da shi kamar wasu kaya ne da za a iya raba wa da wasu. AT: "bai gamshe mu kaɗai ba mu faɗa maku bisharar Allah, amma mun kassance da ku mun kuma taimaka muku.
"mun kula da ku sosai"
kalamomin "aiki" da "fama" na nufin abu ɗaya ne. Bulus ya yi amfani da su domin ya nanata matuƙan aikin da suka yi. AT: "yadda muka yi aiki tuƙuru"
"Mun yi aiki tukuru don zaman rayuwarmu, domin haka ba zaku bukaci ku tallafa mana ba"
Bulus yayi amfani da kalmomin nan uku domin ya bayana kyaun halin da suka nuna ga masubi da suke Tassalonika.
Bulus ya kwatanta yadda ya ƙarfafa Tasalonikawa kamar yadda uba ke koyar da halin kirki ga 'ya'yansa.
Kalmomin nan "roƙo", "ƙarfafawa", da kuma "izawa" anyi amfani da su tare domin nuna yadda Bulus da tawagar sa suka ƙarfafa Tasalonikawa. AT: " Mun karfafa ku sosai"
kalma "ɗaukaka" na bayana kalma "mulki." At: "zuwa mulkinsa mai daraja"
A nan 'tafiya" na nufin "rayuwa." AT: "yin rayuwa domin mutane su yi tunani mai kyau game da Allah"
Bulus yakan gode wa Allah domin yadda suka ƙarbi saƙon bishara da ya kawo gare su.
"maganar mutum" na nufin duk saƙon da ke zuwa daga kowane mutum. AT: "ba saƙon da ke zuwa daga mutum ba"
"magana" a nan na nufin "saƙo." AT: "kuka ƙarbe ta kamar yadda gaskiyar take, wato saƙon da ta zo daga Allah"
Bulus na magana game da bisharar Allah kamar wani aiki ne da mutum ke yi. "Magana" na nufin "saƙo." AT: "wannan tsari ne na umarnin Allah wanda zai taimakawa waɗanda suka ba da gaskiya su yi aiki da kyau tare"
masubi a Tasalonika sun jimre tsanani kamar Yahudawa masubi. "zama kamar ikilisiyu"
"daga wasu Tasalonikawa"
"Sun yi ƙoƙarin hana mu magana"
Bulus na magana kamar mutum zai iya cika bokiti da zunubi kamar yadda ake cika wa da ruwa.
Wannan na nufin yadda a ƙarshe Allah na yin shari'a da kuma hukunta mutane domin zunubansu.
A nan "zuciya" na nufin tunani da shauƙi. Koda ya ke Bulus da abokan tafiyarsa basu nan a Tasalonika, basu daina tunani da kuma kula da masubi da suke wurin ba. AT: "a zahiri, amma mun cigaba da tunani game da ku"
A nan "fuskarku" na nufin gaba ɗaya mutumin. AT: "ganin ku" ko kuma "kassance da ku"
"Ni, Bulus, na yi ƙoƙarin zuwa gare ku sau da dama"
Bulus ya yi amfani da tambayoyi domin ya nanata dalilin marmarinsa na ganin masubi da ke Tasalonika. AT: "Domin ku da sauran masubi ne begenmu nan gaba, da murnarmu, da rawanin alfahari, a gaban Ubangijinmu Yesu a lokacin zuwansa."
Bulus yayi amfani da "bege" da nufin tabbacin cewa Allah zai saka masa domin aikin sa. Masubi na Tasalonika sune dalilin begensa.
Masubi na Tasalonika sune dalilin murnar sa.
A nan "rawani" na nufin lada ko sakayya da ake ba ƙwararren ɗan wasa da ya yi nasara. maganar "rawanin alfahari" na nufin ladan nasara, ko kuma yin aiki mai kyau.
1Saboda haka, da bamu iya jimrewa ba, sai mukayi tunanin cewa ya dace mu dakata a Atina tukunna. 2Sai muka aikaTimoti, dan'uwanmu dakuma bawan Allah a bisharar Almasihu, domin karfafaku ya kuma ta'azantar daku a fannin bangaskiya. 3Mun yi haka ne saboda kada waninku ya raunana domin wadannan wahaloli. Domin ku da kanku kun sani cewa don haka aka kiraye mu.4Hakika, a lokacin da muke tare daku, mun gaya maku cewa muna daf da shan wahala, haka ya kuma kasance, kamar yadda kuka sani. 5Domin haka, da ban iya jimrewa ba, sai na aiko domin in san yadda bangaskiyar ku take. Watakila ko magafci a wata hanya ya rinjaye ku, sai ya kasance wahalarmu ta zama a banza.6Amma Timoti da ya dawo daga gareku sai ya kawo mamu labari mai dadi akan bangaskiyarku da kuma kaunarku. Yako gaya mana cewa kuna kyakkyawan tunani a kanmu, kuma kuna marmarin ganinmu yadda muke marmarin ganinku. 7Sabili da haka, 'yan'uwana, mun sami ta'aziyya tawurinku domin bangaskiyarku, a cikin dukkan bakin cikinmu da shan wuyamu.8Yanzu a raye muke, idan kun tsaya da karfi a cikin Ubangiji. 9Gama wace irin godiya zamu ba Allah sabili da ku, domin dukan farin cikin da muke dashi a gaban Allah domin ku? 10Dare da rana muke yi maku addu'a sosai domin muga fuskokinku kuma mu cika abin da kuka rasa cikin bangaskiyarku.11Bari Allah da kuma Ubanmu da kansa, da Ubangijinmu Yesu, ya bida sawayen mu zuwa gareku. 12Bari Ubangiji yasa ku karu ku kuma ribambamya a kaunar 'yan'uwanku da dukan mutane, kamar yadda muke maku. 13Bari yayi haka domin ya karfafa zukatanku marassa abin zargi a cikin tsarki a gaban Allah da Ubanmu a lokacin zuwan Ubangijinmu Yesu da dukan tsarkakansa.
Bulus na gaya wa masubi cewa ya aiki Timoti a gare su ya ƙarfafa bangaskiyarsu.
"bamu iya jimre damuwa game da ku ba"
"ya yi kyau ni da Sila mu dakata a Atina"
"ya dace" ko kuma "ya wajibta"
Wannan wata birni ce a yankin ƙasar Akaya wanda take garin Girka ayau.
Wannan maganganu biyun na bayana Timoti ne.
a raunana na nufin kassance wa da tsoro. AT: "kada wani ya razana daga amincewa da Almasihu"
Bulus na tsammanin kowa ya sani cewa Allah ne ya zaɓe su. AT: "Allah ya zaɓe mu"
Wannan na nuna cewa akwai sauran gaskiyan maganar fiye da abin da an gama faɗa.AT: " bugu da ƙari"
"shan wulakanci daga wasu mutane"
Bulus na bayana yadda yake ji ta wannan maganar. AT: " ban iya yin haƙurin jira ba"
Ana nuna cewa Bulus ne ya aiko Timoti. AT: "Na aiki Timoti"
"mun yi aiki tukuru a tsakaninku" ko kuma "koyarwanmu a cikinku"
"mara amfani"
"mu" na nufin Bulus ne da Sila.
A gane cewa wannan bangaskiyar a cikin Almasihu ne. AT: "labari mai kyau game da Bangaskiyarku"
a duk lokacin da suka yi tunanin Bulus, sukan samu tunani mai kyau game da shi.
"kuna so ku gan mu"
A nan " 'Yan'uwa" na nufin 'Yan'uwa masubi.
Wannan na nufin bangaskiya cikin Almasihu. AT: "domin bangaskiyarku a cikin Almasihu"
kalman "wuya" ya bayana dalilin "baƙin cikinmu." AT: "cikin dukkan baƙin cikinmu da ke zuwa daga shan wuyarmu"
Wannan maganar na nufin zaman gamsuwa da rayuwa. AT: "mun samu ƙarfafawa"
"tsaya da ƙarfi" na nufin kassancewa da aminci. AT: "idan kun cigaba da dõgara ga Ubangiji"
AT: "ba zamu iya ba Allah isashen godiya ba domin abubuwan da yayi maku! muna matuƙan farin ciki sabili da ku a duk lokacin da muke yin addu'a ga Allahnmu"
Bulus na magana kamar shi da abokansa na gaban Allah fuska da fuska. Mai yiwuya yana nufin ta wajen addu'a ne.
"duk ƙarfinsa"
kalman "fuska" na nufin ganin su gaba ɗaya. AT: "ziyarce ku"
A wannan ayoyin, kalman "mu" baya nufin ƙungiyar mutane ɗaya a kowane lokaci. A yi lura da fassara domin a gane ainihin ma'ana.
Bulus ya haɗa masubi na Tassalonika da abokan aikinsa.
"Muna addu'a cewa Allahnmu"
Bulus na magana kamar yana so Allah ya nuna masa da tawagarsa hanyar da zasu bi domin ziyarar masubi da ke Tasalonika. Yana nufin cewa, yana so Allah ya ba su zarafin yin haka.
A nan "kansa" na nufin Uban ne, an yi haka domin nanaci ne.
Bulus na magana game da ƙauna kamar wani abu ne da ake samuwa sannan a iya ƙarawa.
A nan "zuciya" na nufin abin da mutum ya yarda dashi, ya kuma amince da shi. AT: "ƙarfafa ku, domin ku zama"
"a lokacin da Yesu ya dawo duniya"
"tare da dukkan waɗanda suke nasa"
1A karshe, 'yan'uwa, muna karfafa ku kuma muna yi maku gargadi cikin Ubangiji Yesu. Yadda kuka karbi umarni a garemu game da yadda dole za kuyi tafiya kuma ku gamshi Allah, kuma a cikin wannan hanya ku tafi, ku kuma wuce haka. 2Domin kun san umarnin da muka baku cikin Ubangiji Yesu.3Gama wannan ne nufin Allah: kebewar ku - cewa ku kauce wa zina da fasikanci, 4Cewa kowannenku ya san yadda zai rike mata tasa cikin tsarki da girmamawa. 5Kada kayi mata cikin zautuwar sha'awa (kamar al'ummai wadanda basu san Allah ba). 6Kada wani ya kuskura yaci amanar dan'uwansa akan wannan al'amari. Gama Ubangiji mai ramuwa ne akan dukkan wadannan al'amura, Kamar yadda a baya muka yi maku kashedi kuma muka shaida.7Gama Allah bai kira mu ga rashin tsarki ba, amma ga rayuwar tsarki. 8Domin haka, duk wanda yaki wannan ba mutane yaki ba, amma Allah, wanda ya bada Ruhunsa Mai Tsarki a gareku.9Game da kaunar 'yan'uwa, baku bukatar wani ya sake rubuta maku, gama ku da kanku Allah ya koyar da ku kaunar 'yan'uwa. 10Ba shakka, kunayin haka ga dukkan 'yan'uwa wadanda ke cikin dukkan Makidoniya. Amma muna gargadin ku 'yan'uwa, kuyi haka bugu da kari. 11Kuma muna gargadin ku 'yan'uwa kuyi kokari ku zauna a natse, ku kula da al'amuranku, kuyi aiki da hannuwanku, Yadda muka umarceku a baya. 12Kuyi haka domin tafiyar ku ta zama dai dai a gaban wadanda basu bada gaskiya ba, kuma ya zama baku cikin bukatar komai.13Bamu so ku zama da rashin fahimta ba, 'yan'uwa, game da wadanda sukayi barci, domin kada kuyi bacin rai kamar sauran wadanda basu da tabbacin abinda ke gaba. 14Domin idan mun bada gaskiya Yesu ya mutu kuma ya tashi, haka kuma tare da Yesu Allah zai maido da duk wadanda suka yi barci a cikinsa. 15Gama muna fada maku wannan daga maganar Ubangiji, cewa mu da muke a raye, da aka bari har zuwan Ubangiji, babu shakka ba za mu riga wadanda suka yi barci ba.16Gama Ubangiji da kan sa zai sauko daga sama. Zai zo da muryar babban mala'ika, da karar kahon Allah, sai matattu cikin Almasihu su fara tashi. 17Sai mu da muke a raye, wadanda aka bari, tare dasu za'a fyauce mu zuwa cikin gizagizai, mu hadu da Ubangiji cikin sararin sama. Haka zamu cigaba da kasancewa da Ubangiji. 18Domin haka ku ta'azantar da juna da wadannan maganganu.
A nan "'yan'uwa" na nufin masubi.
Bulus na amfani da kalmar "ƙarfafa" da kuma "gargaɗi" domin ya nanata ƙarfin yadda suka ƙarfafa 'yan'uwa masubi AT: "mun ƙarfafa ku kwarai"
AT: "muka ƙoyar da ku"
A nan "tafiya" kalma ce da ke nufin yadda ya kamata mutum yayi rayuwa. AT: "ya kamata kuyi rayuwa"
Bulus na maganar umurninsa kamar Yesu ne da kansa ya bayar.
"ku yi nesa daga aikata zina da fasikanci"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "san yadda zai yi rayuwa da matarsa" 2) san yadda zai kula da jikin sa"
"da sha'awar zina da fasikanci mara kyau"
A nan "mutum" na nufin na miji ko ta mace. "ba wani"
Wannan jumlu biyu ne da ke nufin abu ɗaya domin nanata ƙarfin maganan. AT: "aikata abin da ba daidai ba"
AT: "Ubangiji zai hukunta wanda ya ƙetare doka, ya kuma yi kariyan ga wanda aka yi wa laifi"
"faɗa maku kafin lokacin da kuma ba da gargaɗi"
AT: "Allah ya kira mu ga tsabtacewa da rayuwan tsarki"
kalman "mu" na nufin duk masubi.
"duk wanda ya ƙi kula da wannan koyarwan" ko kuma "duk wanda ya yi watsi da wannan koyarwan"
Bulus na bayyana cewa wannan koyarwan daga Allah ne ba mutum ba.
"ƙaunar 'yan'uwa masubi"
"kuna nuna ƙauna zuwa ga dukkan masubi da suke Makidoniya"
"yi ƙoƙari"
Bulus yayi amfani da kalman "natse" da nufin zaman salama cikin al'umma ba tare da jayayya ba. AT: "zama cikin natsuwa da kuma yadda ya kamata"
"ku yi aikinku" ko " ku kula da abubuwan da ke alhakinku ku yi. Wannan na iya nufin da cewa kada mu dinga tsegumi da kuma tsoma baki a al'amuran wasu.
Wannan na nufin yin rayuwa mai ribatowa. AT: "yi na ku aikin domin samun abin da kuke bukata na zaman rayuwa"
A nan "tafiya" na nufin "rayuwa" ne ko kuma "nuna hali." AT: "nuna halin da ya dace"
ta hanyar nuna girmamawa ga wasu da kuma samun girmamawansu.
Bulus na magana game da waɗanda basu bada gaskiya a cikin Almasihu ba kamar suna wajen wani wuri ne da masubi ke ciki. AT: "a idanun waɗanda basu ba da gaskiya cikin Almasihu ba"
Bulus na magana game da masubi waɗanda sun riga sun mutu, da waɗanda suke raye, da kuma waɗanda zasu kassance a raye har lokacin dawowan Almasihu.
AT: "Muna so ku fahimta" ko "Muna so ku sani"
A nan "barci" na nufin mutuwa. AT: "waɗanda suka mutu"
"domin bamu so kuyi baƙin ciki kamar sauran"
makoki, fushi game da wani abu
"kamar mutane waɗanda basu da bege game da alkawari dake zuwa nan gaba." Ana iya bayyana abin da waɗanan mutanen basu da bege a kai. AT: "kamar mutane waɗanda basu da tabbacin cewa zasu tashi daga matattu"
A nan "mu" na nufin Bulus ne da masu sauraronsa.
"tashi domin a sake rayuwa"
A nan "yi barci" na nufin mutuwa ne.
"kalma" a nan na nufin "saƙo" ne. AT: "ta hanyar fahimtar koyarwan Ubangiji"
"a loƙacin da Ubangiji ya dawo"
"Ubangiji zai sauƙo da kasa"
"shugaban mala'ika"
"matattu cikin Almasihu" sune masubi waɗanda suka mutu. AT: "waɗanda suka badagaskiya a cikin Yesu Almasihu, amma sun riga sun mutu zasu zama farkon tashi"
A nan "mu" na nufin duk masubi da basu mutu ba.
kalman "su" na nufin masubi waɗanda suka mutu amma an sake rayar da su.
"hadu da Ubangiji Yesu a cikin sararin sama"
1Yanzu fa game da zancen lokatai da zamanai 'yan'uwa, ba ku da bukatar a rubuta maku wani abu. 2Domin ku da kanku kun sani kwarai cewa ranar zuwan Ubangiji kamar barawo take da dare. 3Da suna zancen "zaman lafiya da kwanciyar rai," sai hallaka ta zo masu ba zato ba tsammani. Zai zama kamar nakudar haihuwa ce da ke kama mace mai ciki. Ba su kwa da wata hanyar kubuta.4Amma ku, 'yan'uwa, ai ba cikin duhu kuke ba har da wannan rana zata mamaye ku kamar barawo. 5Domin dukkan ku 'ya'yan haske ne 'ya'yan rana kuwa. Mu ba 'ya'yan dare ba ne ko na duhu, 6Don haka, kada muyi barci kamar yadda sauran ke yi. Maimakon haka, bari mu kasance muna zaman tsaro kuma muna a fadake. 7Don masu yin barci da dare suke yin barci, haka kuma masu sha su bugu ma da dare suke yi.8Tunda shike mu 'ya'yan rana ne, bari mu zauna a natse. Bari musa sulke na bangaskiya da kauna, mu kuma sa kwalkwali don ceton mu dake gaba. 9Domin Allah bai kaddara mu ga fushinsa ba, sai dai ga samun ceto ta wurin Ubangijin mu Yesu Almasihu. 10Shi ne wanda ya mutu domin mu, don ko da muna raye ko muna mace, mu iya rayuwa tare da shi, 11Domin haka ku ta'azantar da juna ku kuma inganta juna, kamar yadda kuke yi.12Muna rokon ku, 'yan'uwa, ku bada daraja ga wadanda suke aiki a tsakaninku wadanda kuma suke shugabanci a kan ku cikin Ubangiji, wadanda kuma suke horonku. 13Muna kuma rokon ku, da ku kula dasu ku kuma kaunacesu sabili da irin ayyukansu. Ku kuma yi zaman lafiya da junan ku. 14Muna yi maku gargadi 'yan'uwa; ku jawa marassa ji kunne, ku karfafa marassa karfin zuciya, ku taimaki gajiyayyu, kuyi zaman hakuri da kowa.15Ku lura kada wani ya rama mugunta da mugunta, Maimakon haka ma, Ku cigaba da abinda ke mai kyau ga juna da kowa duka. 16Kuyi farin ciki koyaushe. 17Kuyi addu'a ba fasawa. 18A cikin kome kuyi godiya. Domin wannan ne nufin Allah a cikin Yesu Almasihu game daku.19Kada ku hana Ruhun Allah aiki a cikin ku. 20Kada ku raina anabce anabce. 21Ku gwada komai. Ku rike abinda ke mai kyau. 22Ku kaucewa duk wani abinda yayi kama da mugunta.23Bari Allah na salama ya mai da ku cikakun tsarkaka. Bari dukkan ruhun ku, da zuciyar ku, da jikin ku su zama adanannu marassa zargi domin zuwan Ubangijin mu Yesu Almasihu. 24Wanda ya kira ku mai aminci ne, wanda kuma zai aikata.25Yan'uwa, kuyi addu'a domin mu. 26Ku gaida dukkan yan'uwa da tsattsarkar sumba. 27Ina rokon ku saboda Ubangiji ku karanta wasikar nan ga dukkan 'yan'uwa. 28Bari alherin Ubangijin mu Yesu Almasihu shi kasance tareda ku.
Bulus ya cigaba da magana akan ranar da Yesu zai dawo.
A wannan surar, kalman nan "mu" na nufin Bulus, Sila da Timoti, sai dai ko in an ambata cewa ba haka ba ne. Kalman nan "ku" kuma na nufin masubi da ke ikilisiyar da take a Tassalonika.
Wannan na nufin abubuwan da za su auku kafin dawowan Yesu.
A nan "'yan'uwa" na nufin 'yan'uwa masubi.
"da kyau kwarai" ko "babu kuskure"
Kamar yadda ba wanda ya san a wane dare ne ɓarawo zai zo, hakannan kuma ba mu san sa'ad da ranar Ubangiji zai zo ba. AT: "ba tsammani"
"Sa'ad da mutane ke zance"
"sai hallaka ta zo ba zato ko tsammani"
Kamar yadda naƙudan mace take zuwa ba tsammani kuma ba za ta tsaya ba har sai ta haihu, hakannan hallakan za ta zo kuma mutane ba za su iya guje mata ba.
A nan " 'yan'uwa" na nufin 'yan'uwa masubi.
Bulus na magana game da mugunta da rashin sani game da Allah kamar sune duhu. AT: "ku ba jahilai ba ne kamar mutane waɗanda suke rayuwa a cikin duhu"
ranar da Ubandgiji zaya dawo kar ya zama da ban mamaki ba ga masubi.
Bulus na magana game da "gaskiyan" kamar wata haske ne da rana. AT: "Gama kun san gaskiyan, kamar mutane waɗanda suke rayuwa cikin haske, da kuma mutanen rana"
Bulus na magana game da mugunta da rashin sani game da Allah kamar sune duhu. AT: "Mu ba jahilai ba ne kamar mutane waɗanda suke rayuwa a cikin duhu"
Bulus na magana game da jahilcin ruhaniya kamar yin barci. AT: "kada mu zama kamar sauran waɗanda basu san cewa Yesu zai dawo ba"
kalmar "mu" na nufin dukkan masubi.
Bulus ya bayyana game da sani na ruhaniya a matsayin abin da ya sha bam-bam da barci da kuma maye.
kamar yadda mutane ke barci, ba su iya sanin abin da ke faruwa hakanan mutanen wannan duniyan basu san cewa Almasihu zai dawo ba.
Bulus na bayyana cewa da dare ne mutane ke sha su bugu, hakanan mutane da ke da rashin sani game da dawowan Almasihu, ba su rayuwa cikin kamun kai da natsuwa.
Bulus na magana akan sanin gaskiya game da Allah kamar 'ya'yan rana. AT: "mun san gaskiyan" ko "mu samu hasken gaskiyan"
Bulus na bayyana zama a faɗake kamar zama cikin natsuwa da kamun kai. AT: "mu yi rayuwa cikin natsuwa da kamun kai"
kamar yadda mayaƙi ke sa sulke domin tsaron jikin sa, haka maibi da ke rayuwa cikin bangaskiya da ƙauna ke samun tsaro. AT: " mu tsare kanmu da bangaskiya da ƙauna" ko "mu tsare kanmu ta wurin gaskatawa cikin Almasihu da ƙaunarsa"
kamar yadda kwalkwali ke tsare kan mayaki hakane tabaccin ceto ke tsare maibi. AT: " mu tsare kanmu ta wurin tabaccin cewa Almasihu zai cece mu"
A nan "gina" na nufin ƙarfafa. AT: "ƙarfafa juna"
"a girmama da kuma yaba wa waɗanda suke shugabanci"
Wannan na nufin mutanen da Allah ya maishe su shugabane a bisan masubi.
Bulus na gargadin masubi da su girmama kuma su ƙaunaci shugabanensu na ikilisiya.
Bulus yana yi wa masubi gargaɗi da cewa su cigaba da halin farin ciki cikin kowane abu, su yi zaman tsaro cikin addu'a, da kuma godiya cikin kowane abu.
cikin kowane yanayi
Bulus na nufin cewa halayen da ya ambata nufin Allah ne ga masubi.
"Kada ku hana Ruhu Mai Tsarki aiki a tsakanin ku"
"Kada ku raina annabci" ko "Kada ku ƙi kowane abu da Ruhu Mai Tsarki ya faɗa wa wani"
"Ku tabbata cewa kowace saƙon da kuna zaton ya zo daga Allah lallai daga shi ne"
Bulus ya yi magana game da saƙo daga Ruhu Mai Tsarki sai kace wani abu ne da wani ke iya riƙewa a hannayen sa.
Wannan na nufin cewa Allah yana sa mutum ya zama mara zuunubi da kuma mara aibi a gabansa.
A nan "ruhu, zuciya, da jiki" na nufin mutum gaba dayan sa. In har harshen ku ba shi da kalmomin nan guda uku, kuna iya bayyana kamar "dukan rayuwar ku" ko "ku." AT: "Bari Allah ya sa dukan rayuwar ku ta zama mara zunubi" ko "Bari Allah ya mai da ku marasa aibu sarai"
"mai amincin ne wanda ya kira ku"
"zai yi ta taimakon ku"
AT: "Ina zuga ku, kamar a ce Ubangiji ne ke magana da ku, ku karanta wasiƙar nan" ko "da ikon Ubangiji ina umurtar ku, ku karanta wannan wasiƙar"
1Bulus da Silbanus da Timoti, zuwa ga ikilisiyar Tasolonika cikin Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Almasihu. 2Bari alheri ya kasance tare da ku da salama daga Allah Ubanmu da Ubangijinmu Yesu Almasihu.3Lallai ne mu godewa Allah kulluyaumin domin ku, yan'uwa. Domin hakan dai dai ne, saboda bangaskiyarku ta karu sosai, kuma kaunar junanku tana karuwa. 4Mu da kanmu muna fahariya da ku a ikilisiyoyin Allah. Muna maganar hakurinku da bangaskiyarku a cikin dukkan tsananin da kuke fuskanta. Muna maganar kuncin da kuke jimrewa. 5Wannan itace alamar shari'ar Allah ta adalci. Sakamakon haka shine za a dauke ku cancantattu na mulkin Allah wanda kuke wahala dominsa.6Adalci ne ga Allah ya mayar da kunci ga wadanda suke kuntata maku, 7ya kuma baku hutu ku dake shan wuya tare da mu. Zai yi haka ne a bayyanar Ubangiji Yesu daga sama da Mala'ikun ikonsa. 8A cikin wuta mai huruwa zai dau fansa bisa wadanda basu san Allah ba da wadanda basu karbi bisharar Ubangijinmu Yesu almasihu ba.9Za su sha azaba ta hallaka har abada daga fuskar Ubangiji da kuma daukakar ikonsa. 10Zai yi wannan lokacin da yazo a wannan rana don jama'arsa su daukaka shi, kuma ya zama abin mamaki ga dukkan wadanda suka bada gaskiya. Domin kun gaskata shaidarmu a gare ku.11Saboda wannan muke addu'a kullum domin ku. Muna addu'a domin Allahnmu ya sa ku cancanci kiran ku. Muna addu'a ya biya ku muradin ku na yin nagarta da dukkan wani aikin bangaskiya da kuma iko. 12Muna addu'a haka domin sunan Ubangijinmu Yesu ya sami daukaka daga gare ku. Addu'armu itace ya daukaka ku, saboda alherin Allahnmu da Ubangijinmu Yesu Almasihu.
Bulus ne marubucin wannan wasiƙar, amma ya sa Sila da Timoti a matsayin wanɗanda ya aike su da wasiƙar. Ya fara da gaisuwa zuwa Ikilisiyar da take a Tasalonika.
Wannan sunan "Sila" ne a Latanci. Mutum ɗaya ne da wanda aka ambata cikin littafin Ayyukan Manzanai a matsayin wanda ke abokin tafiyar Bulus.
Bulus ya cika amfani da wannan gaisuwar cikin wasiƙunsa.
Bulus ya yi amfani da "kulluyaumi" don ya nuna ma'anar cewa "sau da yawa" ko "a kai a kai". Jumlar nan ta na nanata yawan abubuwan da Allah ke yi a rayuwar Masubi na Tasalonika. AT: "Mu gode wa Allah kulluyaumi"
A nan "'yan'uwa" na nufin 'yan'uwa Masubi, maza da mata duka. AT: "'yan'uwa maza da mata"
"Domin abu mai kyau ne" ko "Don daidai ne"
"kuna ƙaunar juna da gaske"
A nan "juna" na nufin 'yan'uwa Masubi.
A nan "kanmu" an yi amfani da ita ne don nanata taƙamar Bulus.
AT: "Allah zai ɗauke ku cancantattun zama cikin mulkinsa"
Da Bulus ya cigaba, ya yi maganar cewa Allah mai adalci ne.
"Allah ya yi daidai" ko "Allah mai adalci ne"
A nan "a mayar" na nufin a sa wani ya ji daidai kamar yadda ya yi wa wani. AT: "Allah ya sanya wa waɗanda suka sanya muku bala'i, bala'i, ya kuma sassauta muku"
Ku na iya bayyana wa cewa Allah shine wanda ke kawo sauƙi. AT: "don Allah ya ba ku sauƙi"
"mala'ikunsa masu iko"
"shi zai hukunta waɗanda basu san Allah ba da wuta da kuma waɗanda" ko "Sa'an nan da wuta zai hukunta waɗanda ba su san Allah ba da waɗanda"
Anan "Su" na nufin mutane da sun yi rashin biyayya ga bisharar. AT: "Ubangiji zai hukunta su"
A nan "wannan rana" rana ce da Yesu zai dawo duniyan nan.
AT: "A Sa'ad da mutanensa za su ɗaukaka shi, duk waɗanda suka gaskanta za su yi mamakin sa"
Bulus ya nanata yadda ya ke addu'a saboda su. AT: "mu ma muna muku addu'a a koyaushe" ko "muna cigaba da yi muku addu'a"
A nan "kira" na nufin cewa Allah ya zaɓi mutane don su zama 'ya'yansa da bayinsa, don yin shelar saƙon cetonsa ta wurin Yesu.
"sa ku ku iya yin nagarta cikin kowace hanya da kuke so"
AT: Domin ku ɗaukaka sunan Ubangijinmu Yesu"
AT: "Yesu zai ɗaukaka ku"
"saboda alherin Allah"
1Yanzu game da zuwan Ubangijinmu Yesu Almasihu da taruwarmu domin kasancewa tare da shi; muna rokonku yan'uwa, 2kada kuyi saurin damuwa ko ku gigice saboda wani ruhu ko kuma sako ko kuma wasika da ta yi kamar daga wurin mu, da ke cewa ranar zuwan Ubangiji ta rigaya ta zo.3Kada wani ya yaudare ku ta kowace hanya. Domin wannan rana baza ta zo ba sai fandarewar nan ta zo kuma an bayyana mutumin tawayen nan wato dan hallaka. 4Wannan shi ne wanda ya ke gaba, yana kuma daukaka kansa fiye da duk abin da ake kira Allah ko kuma ake bautawa. Sakamakon haka yana zama a kursiyin Allah har ma yana cewa shine Allah.5Baku tuna ba lokacin da nake tare daku na gaya maku wadannan abubuwa? 6Yanzu kun san abinda ke tsaida shi, domin a bayyana shi a lokacin da ya dace. 7Ko yanzu asirin take shari'a ya na aiki, sai dai a kwai wanda ke tsaida shi yanzu har sai an dauke shi.8Sa'anan za'a bayyana dan tawayen, wanda Ubangiji Yesu zai hallaka shi da numfashin bakinsa. Ubangiji zai mayar da shi ba kome ba ta wurin bayyanuwar zuwansa. 9Mai tawayen nan kuwa, zai zo ne bisa ga aikin shaidan da dukan iko, alamu, da al'ajiban karya, 10da kuma dukan yaudara ta rashin adalci. Wadannan abubuwa za su zama ga wadanda suke hallaka, saboda ba su karbi kaunar gaskiya ba domin su sami ceto.11Saboda wannan dalilin Allah ya aiko masu da sabani, saboda su yarda da karya. 12Sakamakon shine dukkan su za'a yi masu shari'a, wato wadanda ba su yarda da gaskiya ba suna kuma jin dadin rashin adalci.13Amma muna masu godiya kulluyaumin ga Allah domin ku, yan'uwa wadanda Ubangiji yake kauna. Ubangiji ya zabe ku a matsayin yayan fari don ceto cikin tsarkakewar Ruhu da gaskatawa da gaskiya. 14Wannan shine abinda ya kira ku gare shi ta wurin bishararmu domin ku sami daukakar Ubangijinmu Yesu Almasihu. 15Saboda haka yan'uwa, ku tsaya da gaske. Ku rike al'adun da aka koya maku, ko ta kalma ko kuma ta wasikarmu.16Yanzu bari Ubangiji Yesu Almasihu da kansa, da Allah Ubanmu wanda ya kaunace mu ya ba mu madawwamiyar ta'aziya da gabagadi mai kyau domin gaba ta wurin alheri, 17ya ta'azantar da ku ya kuma gina zuciyarku cikin kowane aiki mai kyau da kalma.
Bulus ya gargaɗi masubi cewa kada su yarda a yaudare su game da ranar dawowan Yesu.
Kalman nan "yanzu" alama ce ta canjin kan magana cikin umurnin Bulus.
A nan "'yan'uwa" na nufin 'yan'uwa masubi, maza da mata duka. AT: "'ɗan'uwa da 'yar'uwa"
"kada ku yi saurin sa kanku cikin damuwa"
"ta wurin kalmomin baƙin ko ta wurin wasiƙar da ta yi kamar daga gare mu"
"cewa"
Wannan na nufin lokacin da Yesu zai dawo duniya saboda masubi.
"ranar Ubangiji ba zai zo ba"
Wannan na nufin lokacin da ke gaba a sa'ad da mutane dayawa za su juya wa Allah baya.
AT: "Allah ya bayyana mutum mai aikata mugunta"
Bulus ya yi magana a kan hallaka kamar mutum wanda ya haifi ɗa wanda manufar sa ita ce ya hallaka kowani abu gabaki ɗaya. AT: "wanda ya hallaka kowane abu da zai iya"
AT: "kowane abin da mutane ke duba a matsayin Allah ko kuma kowane abu da mutane ke bautawa"
"nuna kansa cewa shi Allah"
Bulus ya yi amfani da tambayar da ba lallai ne a bada amsa ba don ya tunashe su game da koyarwarsa a lokacin da ya ke tare da su a dã. Ana iya bayyana wannan cikin furci. AT: "Na tabbata kun tuna ... waɗannan abubuwan."
Wannan na nufin dawowar Yesu, ranar Ubangiji, da mutum mai aikata mugunta.
AT: "Allah zai bayyana mutum mai aikata mugunta a sa'ad da lokacin ya yi"
Wannan na nufin asirin mai tsarki da Allah ne kaɗai ya sani.
a tsaida wani ita ce a riƙe su ko kuwa a hana su yi abin da suna so su yi.
AT: "Sa'anan Allah zai bar ɗan tawayen nan ya bayyana kansa"
A nan "numfashi" na nufin ikon Allah. AT: "ta wurin ikon kalmomin bakinsa"
A Sa'ad da Yesu ya dawo duniya ya bayyana kansa, zai yi nasara kan wannan mai tawayen.
"da kowace irin iko, alamu, da al'ajiban ƙarya"
Wannan mutumin zai yi amfani da kowace irin mugunta ya yaudari mutane zuwa ga bada gaskiya gare shi a maimakon Allah.
Wannan mutumin da ya sami iko ta wurin Shaiɗan zai yaudari kowane mutum da bai gaskanta da Yesu ba.
A nan "hallaka" na nuna ra'ayin mara matuƙa ko madawamiyar hallaka.
"Domin mutanen basu ƙaunar gaskiyar"
Bulus na magana game da cewa Allah yana barin wani abu ya faru da mutane sai ka ce ya na aiko masu wani abu ne. AT: "Allah yana barin mutumin nan mai aikata mugunta ya yauɗare su"
AT: "Allah zai hukunta dukan su"
"waɗanda ke jin daɗin rashin adalci saboda basu gaskata da gaskiyar ba"
Bulus a yanzu ya canja kan magana.
Bulus ya yi amfani da wannan kalma anan don ya sa alamar cewa akwai canji cikin kan magana.
Kalman nan "kulluyaumi" na nufin kowane lokaci. AT: "mu cigaba da godiya"
A nan "mu" na nufin Bulus, Sila da Timoti.
AT: "Gama Ubangiji na ƙaunar ku, 'yan'uwa"
an yi magana game da zama cikin mutane na farko da aka cece su sai ka ce masubi da ke Tasalonika su "'ya'yan fari" ne. Ana iya bayyana wannan ta wurin fid da kalmomin nan "ceto", "tsarkakewar"
Bulus ya gargaɗi masubi su riƙe bangaskiyarsu cikin Yesu da ƙarfi.
A nan "al'adu' na nufin gaskiyar Alamasihu da Bulus da sauran manzanni suka koya. Bulus ya yi magana game da su sai ka ce masu karatunsa za su iya riƙesu da hannayen su. AT: tuna da "al'adun" ko "gaskata da "gaskiyar"
AT: "mun koya maku"
"ta wurin kalma" anan na nufin "ta wurin umurnin" ko "ta wurin koyarwa." ku na iya bayyana wannan a fili. AT: "ko ta wurin abin da muka koya muku da kanmu ko ta wurin wasiƙar da muka rubuto muku"
Kalman nan "mu" na nufin dukan masubi.
A nan "kansa" na ƙara bada nanaci ga maganan nan "Ubangiji Yesu Almasihu."
A nan "zuciya" na misalin inda shauƙin ta ke. AT: "ta'azantar da ku ya kuma ba ku ƙarfi don"
"kowane abu na gari da kuke yi kuke kuma faɗa"
1Yanzu yan'uwa, ku yi mana addu'a saboda maganar Ubangiji tayi sauri ta sami daukaka, kamar yadda take tare da ku. 2Ku yi addu'a domin mu kubuta daga mutane masu mugunta da keta, gama ba kowa ke da bangaskiya ba. 3Amma Ubangiji mai aminci ne, shi wanda zai kafa ku ya tsare ku daga mugun.4Muna da gabagadi cikin Ubangiji a kan ku, cewa kuna yi, kuma za ku ci gaba da yin abubuwan da muka umurta. 5Ubangiji ya bi da zuciyarku zuwa kaunar Allah da kuma jimrewar almasihu.6Yanzu muna umurtar ku, yan'uwa, a cikin sunan Ubangiji Yesu Almasihu, ku guji duk dan'uwa wanda yake zaman banza ba kuma akan al'adun da kuka karba daga wurin mu ba. 7Saboda ku da kan ku kun sani yana da kyau kuyi koyi da mu. Ba mu yi zama a cikin ku kamar wadanda ba su da tarbiya ba. 8Ba mu kuma ci abincin kowa ba tare da mun biya ba. Maimakon haka, mun yi aiki dare da rana cikin wahala da kunci domin kada mu dora wa kowa nauyi. 9Mun yi haka ba don ba mu da iko ba. Maimakon haka, mun yi wannan ne saboda mu zama abin koyi a wurin ku, domin ku yi koyi da mu.10Lokacin da muke tare da ku, mun umurce ku, "Duk wanda ba ya son yin aiki, kada yaci abinci." 11Saboda mun ji cewa wasun ku sun ki yin aiki. Ba su aiki sai dai shiga shirgin wasu. 12Irin wadannan, muke umurta da kuma karfafa wa cikin Ubangiji Yesu Almasihu, da su yi aiki da natsuwa, suna cin abincin kan su.13Amma ku yan'uwa, kada ku rabu da yin abinda ke daidai. 14In wani yaki biyayya da kalmominmu cikin wannan wasika, ku kula da shi kuma kada kuyi ma'amalar komai dashi, saboda ya ji kunya. 15Kada ku dauke shi a matsayin makiyi, amma ku gargade shi a matsayin dan'uwa.16Bari Ubangijin salama da kansa ya ba ku salama kulluyaumin ta kowace hanya. Ubangiji ya kasance tare da ku duka. 17Wannan ita ce gaisuwa ta, ni Bulus, da hannuna, wanda shine alama a kowace wasika ta. Haka nake rubutu. 18Bari alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu ya kasance tare da ku duka.
Bulus ya roƙi masubi su yi addu'a domin sa da kuma abokansa.
Bulus ya yi amfani da wannan kalma "yanzu" don nuna alamar canji ciki kan maganarsa.
A nan "'yan'uwa" na nufin 'yan'uwa masubi, duk tare da maza da mata. AT: "'ɗan'uwa da 'yar'uwa"
Bulus ya yi magana game da bazuwar maganar Allah sai ka ce ta na guduwa zuwa wurare dabam dabam. AT: "saboda jim kaɗan mutane da yawa za su ji saƙon mu game da Ubangijinmu Yesu su kuma daraja ta, kamar yadda ya faru da ku"
AT: "domin Allah ya cece mu" ko "domin Allah ya kubutar da mu"
"gama yawancin mutane ba su gaskanta da Yesu ba"
"wanda zai ba ku karfi"
"Shaiɗan"
"Mu na da bangaskiya" ko "Mun dogara"
A nan "zuciya" na nufin tunanin ko zuciyar mutum. AT: "sa ku ku fahimci"
Bulus ya yi magana game da ƙaunar Allah da jimrewar Almasihu sai kace masaukin da ke hanya. AT: "yawan yanda Allah ke ƙaunarku da kuma yawan yanda Almasihu ya jimre saboda ku"
"Suna" a nan na nufin Yesu Almasihu. AT: "kamar Ubangijinmu Yesu Almasihu kansa ne ke magana"
A nan "mu" na nufin dukan masubi.
"yi kamar yadda ni da abokan aiki na ke yi"
Bulus ya yi amfani da korau biyu don ya nanata mai yaƙinin na. AT: "mun yi rayuwa cikin ku kamar waɗanda sun sami tarbiya sosai"
"mun yi aiki cikin dare da rana." A nan "dare" da "rana" na nufin "kowane lokaci." AT" mun yi aiki kowane lokaci"
Bulus ya nanata yadda yanayinsa mai wuya yake. Aiki mai wuya na nufin aikin da ke bukatan himma sosai. Ƙunci na nufin sun jimre zafi da wahala. AT: "cikin kowane yanayi mai wuya"
Bulus ya yi amfani da korau biyu don ya nanata mai yaƙinin nan. AT: Haƙika mu na da ikon karban abinci daga gare ku, amma maimakon haka mun yi aiki don abincin mu"
AT: "Idan mutum na son ya ci abinci, to lallai ne ya yi aiki"
A nan "tafiya" na a madadin hali cikin rayuwa. AT: "wasu suna rayuwan zaman banza" ko "wasu suna da ƙiwuya"
Masu shiga shirgin wasu, mutane ne waɗanda ke shigan al'amuran sauran mutane tun ba a nema taimako daga gare su ba.
"cikin natsuwa, cikin kwanciyar rai, da kuma sassauci." Bulus ya gargaɗi masu shiga shirgin wasu su bar shiga cikin al'amuran wasu.
Bulus ya yi amfani da wannan kalman don ya bambata masubi wanda suke da ƙiwuya da kuma masubi da ke da kwazon aiki.
Kalman nan "ku" na nufin duk masubi da ke Tasalonika.
"In wani bai yi biyayya da umurnan mu ba"
Lura ko shi waye ne. AT: "a bayyana wannan mutum a idon jama'a"
Bulus ya umurci masubi da su fita daga sha'anin masubi da ke malalata a matsayin horo.
Za ku iya sa shi a bayyane cewa wannan addu'ar Bulus ne ga Tasalonikawa. AT: "Ina addu'a cewa Ubangijin salama kansa yã ba ku"
A nan "kansa" na nanata cewa Ubangiji zai bada salama ga masubi.
Ni Bulus na rubuta wannan gaisuwan da hannuna, shine na saba yi cikin kowace wasiƙa ta a matsayin alamar cewa wannan wasiƙar haƙiƙa daga ni ne"
Bulus ya bayyana a fili cewa wannan wasiƙar daga shine ba jabu ba ne.
1Bulus, manzon Almasihu Yesu bisa ga umarnin Allah Mai cetonmu, da Almasihu Yesu begenmu, 2zuwa ga Timoti, dana na gaske cikin bangaskiya: Alheri, jinkai da salama daga wurin Allah da Almasihu Yesu Ubangijinmu.3Kamar yadda na nanata maka ka yi, da zan tafi Makidoniya cewa, ka dakata a Afisa domin ka umarci wadansu mutane kada su koyar da wata koyarwa dabam. 4Kada su bata lokacinsu wajen sauraron tatsunniyoyi da kididdiga marar iyaka. Wannan yana haddasa gardandami, maimakon taimakawa shirin Allah, da ke ta wurin bangaskiya.5Manufar shari'a kuwa kauna ce daga tsabtacciyar zuciya, da tsatstsakan lamiri, da kuma sahihiyar bangaskiya. 6Wadansu sun kauce daga tafarkin sun juya zuwa ga maganganun banza. 7Suna so su zama malaman sha'ria, amma basu fahimci abin da suke fada ba ko abin da suka tsaya akai. 8Amma mun sani shari'a tana da kyau idan an yi amfani da ita bisa ga ka'ida.9Gama mun san wannan, shari'a ba domin mai adalci take ba, amma domin marasa bin doka, mutane masu tawaye, da marasa bin Allah, da masu zunubi, da marasa Allah, da masu sabo. An bada shari'a domin masu kisan iyaye maza da iyaye mata, da masu kisan kai, 10Domin fasikai da 'yan ludu, domin masu satar mutane su kai su bauta, domin makaryata, da masu shaidar zur, da kuma dukan abin da ke gaba da amintaccen umarni. 11Wannan umarni bisa ga daukakkiyar bisharar Allah ne mai albarka, wadda aka bani amana.12Ina gode wa Almasihu Yesu Ubangijimu. wanda ya karfafa ni, gama ya karbe ni amintacce, ya sani cikin hidimarsa. 13Dama can ni mai sabo ne, mai tsanantawa kuma dan ta'adda. Amma duk da haka aka yi mani jinkai domin na yi su cikin jahilci da rashin bangaskiya. 14Amma alherin Ubangijinmu ya kwararo mani tare da bangaskiya, da kauna da ke cikin Almasihu Yesu.15Wannan bishara amintacciya ce, ta isa kowa ya karba, cewa Almasihu Yesu ya zo cikin duniya domin ceton masu zunubi, a cikinsu kuwa ni ne mafi lalacewa. 16Saboda haka ne na sami jinkai, domin ta wurina ni na farko, a nuna hakurin Yesu Almasihu. Ya yi wannan domin in zama misali ga wadanda za su bada gaskiya zuwa rai madawwami. 17Yanzu, ga Sarkin zamanai, marar mutuwa, boyayye, Allah makadaici girma, da daukaka su tabbata a gare shi har abada abadin. Amin.18Ina danka wannan umarni gareka, dana, Timoti. Ina haka ne bisa ga anabcin da aka yi a baya game da kai, domin ka shiga yaki mai kyau. 19Ka yi wannan domin ka zama da bangaskiya da kyakkyawan lamiri. Wadansu mutane sun ki sauraron wannan suka yi barin bangaskiyarsu. 20Kamar su Himinayus da Iskandari, wadanda na bada su ga shaidan domin su horu su koyi kin yi sabo.
A wannan littafi sai dai in an faɗa amma, kalma "mu" na nufin Bulus ne da Timoti
"Ni, Bulus manzo marubucin wannan wasiƙa." Ya yiwu akwai yadda ake gabatar da marubucin wasiƙa a harshe ku, toh ayi amfani dashi a nan. In ya zama lalle za a iya faɗa wanene ake rubutawa wasiƙan.
"daga dokan" ko "ta wurin ƙarfin ikon"
"Allah wanda ya cece mu"
A nan "begenmu" na nufin mutumin da muke da bege a kansa. AT: "Almasihu Yesu wanda a cikin shi ne muke da bege" ko "Almasihu Yesu wanda mun gaskata"
Bulus na magana game da dangantakarsa da Timoti kamar na wani Uba da ɗansa. Wannan ya nuna sahihiyar ƙauna da amincewa da Bulus ke dashi game da Timoti. Ya yiwu kuma ta hannun Bulus ne Timoti ya karɓi ceto shiya sa Bulus ya ɗauke shi a matsayin ɗansa. AT: "wanda yake kamar ɗa a wurina"
"Bari alheri, jinkai, da salama su kasance da kai," ko "Bari ka kasance da kyan zuciya, jinkai, da salama"
"Allah, wanda shine Ubanmu." A nan "Uba" muhimmin suna ne na Allah.
"Almasihu Yesu, wanda shine Ubangijimu"
Bulus na gargaɗi wa Timoti kada yayi amfani da koyarwarkarya amma yayi amfani da koyarwa mai kyau daga Allah.
"kamar yadda na roƙe ka" ko "kamar yadda na faɗa maka da karfi"
"jira ni a garin Afisa"
AT: "wani koyarwa dabam da abin da muka koyar"
AT: "kuma ina so ka umurce su kada su mai da hankali"
Wannan ya yiwu labaru game da kakaninsu ne.
Bulus yayi amfani da kalman "mara iyaka" domin ya nuna cewa kididdigan na da tsawo.
rubutacen tarihin asalin mutun daga iyaye har kakaninsa
"wannan yana sa mutane rashin amincewa cikin fushi." Mutanen suna muhawara game da labarin ƙididdiyar asali wanda ma basu san gaskiyarba.
AT: 1 "a maimakon taimaka mana fahimtar shirin Allah game da ceton mu wanda muka koyar wa ta wurin bangaskiya" 2 "maimakon taimaka mana cikin aikin Allah, wanda muke yi ta wurin bangaskiya."
An yi amfani da wannan kalman domin a dakatar da ainihin koyarwa da a ke yi. Anan Bulus ya bayyana manufar umurni da yake ba wa Timoti.
Anan wannan baya nufin Tsohon Alkawari ko dokoki goma amma umurni ne da Bulus ya bayar a 1Timoti 1:3-4.
AT: "ƙauna ce zuwa Allah" ko "a ƙaunaci mutane."
A nan "sahihiya" na nufi cewa mutum ba shi da wata muguwar manufa a ɓoye. "zuciya" kuma anan na nufin tunani da hankalin mutum. AT: "daga tunani mai kyau"
"lamiri da ya zaɓi abu mai kyau ba mumuna ba"
"bangaskiya na gaske" ko "bangaskiya ba tare da munafurci ba"
Bulus na magana game da bangaskiya cikin Almasihu kamar wata buri ne da a ke nufa. Bulus na nufin cewa waɗansu mutane basu cika manufar bangaskiyar su ba, wanda shine ƙauna, kamar yadda ya faɗa a 1:5.
A nan "juya zuwa" na nufin cewa sun daina yin abun da Allah ya umurta.
A nan "shariya" na nufin shari'ar Musa.
"ko da yake basu fahimta ba" ko "basu fahimta ba tukuna"
"abin da suka amince a kan gaskiya"
"mun fahimci cewa shariya tana da amfani"
"idan mutum yayi amfani da ita yadda ya kamata" ko "idan mutum yayi amfani da ita yadda Allah ke so"
"Gama mun fahimci wannan" ko "mun kuma san wannan"
AT: "ba domin adalin mutum bane Allah yayi shari'a"
A nan "mutum" na nufin namiji da mace. AT: "mutum na ƙwarai"
AT: "Allah yayi shari'a"
Wannan na nufin duk wanda ke jima'i da wanda basu yi aure tare ba.
maza da ke jima'i da junansu
"waɗanda suke satar mutane su kuma sayar da su ga bauta" ko "waɗanda suke ɗaukan mutane su sayar da su zuwa bauta"
"da kuma duk waɗanda suke yin wani abu dake gãba da gaskiyar koyarwar masubi"
"bishara mai ɗauke da daraga daga Allah mai albarka" ko kuma "bisharar ɗaukaka da albarkan Allah"
AT: "wadda Allah ya bani ya kuma amince mani"
ya dauke ni abin dogara
Bulus na magana game da hidimar Allah kamar wani wuri ne da ana iya sanya abu. AT: "ya sanya ni cikin hidimarsa" ko "ya naɗa ni bawansa"
"Dama na kassance mutum ne wanda ke maganar banza game da Almasihu." Bulus na magana game da halinsa kafin ya zama maibi.
"mutum wanda ke tsanantawa masubin Almasihu"
"mutum mai halin mugunta." Wannan mutum ne wanda ya saba da halin mugunta ga wasu.
"Amma domin ban gaskata da Yesu ba kuma ban san abin da nake yi ba, na sami jinkai daga wurin Yesu"
"Yesu ya nuna mani jinkai" ko "Yesu yayi mani jinkai"
"da kuma Alheri"
Bulus na magana game da alherin Allah kamar wani ruwa ne da cike a bokati har yana zuba. AT: "Allah ya nuna mani yalwar alheri"
Wannan ne sakamakon yadda Allah ya nuna Alherinsa zuwa Bulus. AT: "wannan shine sanadin bangaskiya da ƙaunar da nake wa Yesu"
Ana magana game da Yesu kamar shi wani bokati ne da ke rike da ruwa. Amma anan "cikin Almasihu" na nufin dangantaka ne da Yesu. AT: "wanda Almasihu Yesu ya sanya mani in ba wa Allah, domin ina tarayya da shi"
"Wannan maganan gaskiya ne"
"mu karɓa ba tare da shakka ba" ko "ya cancanci mu yarda da ita ƙwarai"
AT: "Allah ya nuna mani jinkai" ko "na sami jinkai daga wurin Allah"
'domin ta wurina, mafi zunubi"
An yin amfani da kalman "Yanzu" domin a canza daga asalin koyarwa ne. Anan Bulus na yabon Allah.
"madawwamin sarki" ko "shugaba na har abada"
AT: "Yanzu bari duk mutane su girmama, su kuma ɗaukaka sarkin zamanai har abada, wanda shine Allah makaɗaici, marar mutuwa, ɓoyayye"
Bulus na magana game da umurnin kamar wani abu ne da ya sa a gaban Timoti wanda ana iya gani. AT: "ina danƙa maka wannan umurnin" ko "wannan umurni ne nake ba ka"
Bulus na bayyana dangantakarsa da Timoti kamar na Uba da ɗansa. Ya yiwu ta hanun Bulus ne Timoti ya karɓi bishara shiya sa Bulus na ɗaukarsa a matsayin ɗa. AT: "wanda yake kamar ɗa na gaske"
AT: "bisa ga anabci game da kai daga sauran masubi"
Bulus na magana game da aikin da Timoti ke yi wa Ubangiji kamar yaƙi ne da soja ke yi. AT: "cigaba da matukar aiki wa Ubangiji"
"lamiri da ke zaɓan abu mai ƙyau ba mumuna ba." dubi yadda aka fasara a 1:5.
Bulus na magana game da bangaskiyar waɗanan mutane kamar wani jirgi ne da ya yi haɗari a tẽku.Yana nufi cewa sun illatar da bangaskiyarsu, wato basu gaskata cikin Yesu kuma ba.
Wannan sunayen maza ne.
Bulus na magana kamar ya danka mutanen wa Shaiɗan fuska da fuska. Ya yiwu Bulus ya ƙi amincewa da su a cikin al'umman masubi. Dashike sun bar iyalin masubi Shaiɗan na da iko akan su, kuma zai iya yi masu illa.
AT: "Allah ya koyar da su"
1Don haka da farko dai, Ina roko a yi roke-roke da addu'o'i, da yin roko domin jama, a dukka, da ba da godiya, a yi haka domin dukkan mutane, 2domin sarakuna da dukkan masu mulki, domin mu yi zaman salama da rayuwa a natse cikin Allahntaka da daraja. 3Wannan yana da kyau da karbuwa a gaban Allah mai cetonmu. 4Yana so dukkan mutane su sami ceto, su kai ga sanin gaskiya.5Domin Allah daya ne, Matsakanci kuma daya ne, tsakanin Allah da mutum, wannan mutum Almasihu Yesu ne. 6Ya bada kansa fansa domin kowa, domin shaida a daidaitaccen lokaci. 7Sabo da wannan dalilin, aka sa ni kaina, na zama mai shelar bishara da manzo. Gaskiya nake fada. Ba karya nake yi ba. Ni mai koyarwa ne na al'ummai cikin gaskiya da kuma imani.8Saboda haka, ina so maza da ke a kowanne wuri suyi addu'a, kuma suna daga hannuwa masu tsarki a sama ba tare da fushi da gardama ba. 9Kazalika, ina so mata su sa kayan da ya cancanta, da adon da ya dace da kamun kai. Kada su zama masu kitson gashi da zinariya da azurfa da tufafi masu tsada. 10Ina so su sa tufafin da ya cancanci matan da ke rayuwar Allahntaka ta wurin kyawawan ayyuka.11Mace ta koya cikin natsuwa da saukin kai a cikin komai. 12Ban ba da izini mace ta koyar ko ta nuna iko a kan namiji ba, amma ta zauna da natsuwa.13Adamu ne aka fara halitta, kafin Hauwa'u. 14Ba Adamu ne aka yaudara ba, amma macen ce aka yaudara cikin laifi. 15Duk da haka, zata sami ceto ta wurin haifuwar 'ya'ya, idan suka ci gaba cikin bangaskiya, da kauna da tsarki da sahihiyar zuciya.
Bulus ya ƙarfafa Timoti ya cigaba da yi wa dukkan mutane addu'a.
"mafi muhimmanci" ko "kafin wani abu dai"
AT: "Ina roƙon duk masubi su yi roƙe-roƙe, addu'o'i, cẽton wasu, da kuma godiya ga Allag"
"Na roƙa" ko "Na ce"
A nan "salama" da "natse" na nufin abu ɗaya ne. Bulus na biɗar masubi su iya rayuwa cikin kwanciyar hankali ba matsala da hukuma.
"da ke daraja Allah da kuma bangirma a wurin sauran mutane"
AT: " Allah na so ya ceci dukkan mutane, su kuma kai ga sanin gaskiyan"
Bulus na magana game da koyan gaskiyar Allah kamar wani wuri ne da a ke iya kawo mutane. AT: "cikin sani da karɓan abin da ke gaskiya"
matsakanci, mutum ne da ke taimako wajen shirya yarjejeniya cikin salama tsakanin ɓangarori biyu wanda suke da rashin amincewa tsakanin su. A nan Yesu na taimakawa masu zunubi domin su shiga dangantaka da Allah cikin salama.
"yarda ya mutum"
"a matsayin kuɗin 'yanci" ko "biyan kuɗi domin samun 'yanci"
Ana iya bayana cewa wannan shine shaidar da Allah ke so ya ceci dukkan mutane. AT: "abin shaida ne a daidai lokacin da Allah ke so ya cece dukkan mutane"
Wannan na nufin cewa, wannan ita ce lokacin da Allah ya zaɓa.
"domin wannan" ko "ta dalilin haka"
AT: "Almasihu ya maishe ni Bulus, mai bishara da kuma manzo"
"Ina koyar wa al'ummai saƙon gaskiya da imani." A nan mai yiwuwa Bulus na amfani da "gaskiya" da "imani" domin bayana ra'ayi ɗaya ne. AT: "Ina koyar da al'ummai game da tabatacciyar bangaskiya"
A nan "hannuwa masu tsarki" na nufin mutumin gaba ɗaya na da tsarki. AT: "Ina so maza masu tsarki dake kowanne wuri su ɗaga hannuwansu suna kuma addu'a"
"maza a dukka wurare" ko "maza a ko'ina." A nan kalman "maza" na nufin maza na musamman.
al'ada ne mutane su ɗaga hannuwansu lokacin addu'a
waɗannan kalmomin na nufin abu ɗaya ne. Bulus na jaddada muhimmanci sa kaya yadda ta dace ga mata ba tare da janyo hankalin maza ba.
a zamanin Bulus, matan Roma sukan yi kitso domin yanyo hankali ne. Kitso wata hanya ce da mace ke bada hankalin da bai kamata wa gashinta ta. Idan ba a san kitso ba sai a yi amfani da sanannen kalma. AT: " kada su ƙawata gyaran gashi" ko "kada su dinga shirya gashinsu domin janyo hankalin mutane"
waɗannan suna kama da duwatsu kuma suna da kyau da daraga har ma mutane kan yi amfani da su a matsayin kayan ado. Ana samun su ne a jikin wani irin ƙaramin dabba da ke rayuwa a tẽku.
"wanɗanda suke so su girmama Allah ta wurin ƙyawawan ayyukan da suke yi
"cikin kawaici"
"yi biyayya da abun da aka koyar"
"ban yarda mace"
AT: "Adamu ne na farko da Allah ya halitta" ko "Allah ya halicci Adamu ne da farko"
Ana iya rubuta wannan a fili kamar. AT: "sa'an nan Allah ya halicci Hauwa'u" ko "daga baya Allah ya halicce Hauwa'u"
AT: "kuma ba Adamu bane maciji ya yaudara"
AT: "amma macen ne ta yi rashin biyayya ga Allah a lokacin da macijin ya yaudareta."
A nan "ta" na nufin dukkan mata. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) Allah zai tsare lafiyar mata a lokacin haifan 'ya'ya, ko 2) Allah zai ceci mata daga zunubansu ta wurin matsayinsu na masu haifan 'ya'ya.
AT: "Allah zai cece ta" ko "Allah zai ceci mata"
"idan sun kasance" ko "idan sun cigaba da zama." A nan "su" na nufin mata.
Ana iya fasarar waɗanan cikin fi'ilin magana. AT: "dogara cikin Yesu da ƙaunar mutane da kuma rayuwa cikin tsarki"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) da yanke shawara mai kyau, 2) da hali na ƙwarai 3) da kamunkai."
Idan an riga an fahimci wannan fasarar, to ana iya barin wannan siffar fasarar. AT: "sahihiyar zuciya"
1Wannan magana tabattaciya ce: Idan wani na da marmari ya zama shugaban Ikilisiya, ya na marmarin aiki mai kyau. 2Don haka, wajibi ne shugaban Ikilisiya ya zama mara abin zargi. Ya zama mai mace daya. Wajibi ne ya zama mai kamewa, mai hankali, mai natsuwa mai karbar baki. Wajibi ne ya iya koyarwa. 3Kada ya zama mashayin giya, da mai tankiya. A maimakon haka ya zama da natsuwa, mai salama. Ba mai son kudi ba.4Wajibi ne ya iya lura da gidansa da kyau, 'ya'yansa su zama masu yi masa biyayya da dukkan bangirma. 5Gama idan mutum bai iya sarrafa gidansa ba, ta yaya zai iya lura da Ikkilisiyar Allah?6Bai kamata ya zama sabon tuba ba, domin kada ya kumbura da girman kai, kada ya fadi cikin irin hukunci da aka yi wa Ibilis. 7Wajibi ne kuma ya kasance mai kyakyawar shaida a cikin wadanda ba masubi ba, domin kada ya fadi cikin kunya da kuma tarkon Ibilis.8Hakanan kuma Dikinoni su kasance da halin mutunci, ba masu magana biyu ba. Bai kamata su zama mashayan giya ko masu hadama ba. 9Su zama masu rikon bayyananniyar gaskiyar bangaskiya da lamiri mai tsabta. 10Daidai ne kuma a fara tabbatar da su, daga nan su fara hidima domin basu da abin zargi.11Hakanan ma mata su zama masu mutunci. Bai kamata su zama magulmanta ba, amma masu kamewa da aminci cikin komai. 12Tilas Dikinoni su zama masu mata daya daya. Su iya kulawa da 'ya'yansu da gidajensu. 13Gama wadanda suka yi hidima da kyau sun sami tsayawa mai kyau da gabagadi cikin bangaskiyar da ke cikin Almasihu Yesu.14Ina rubuta maka wadannan abubuwa, da sa zuciya zan zo wurin ka ba da jimawa ba. 15Amma idan na yi jinkiri, ina rubuta maka ne domin ka san yadda za ka gudanar da al'amuranka a cikin gidan Allah, wato Ikklisiyar Allah rayyayiya, ginshiki da kuma mai tallafar gaskiya.16Babu musu an bayyana cewa ibadarmu ta gaskiya da girma take: "Ya bayyana kansa cikin jiki, Ruhu ya baratar da shi, mala'iku suka gan shi, aka yi shelarsa a cikin al'ummai, aka gaskanta shi a duniya, sa'an nan aka dauke shi sama cikin daukaka.
Bulus ya bayar da muhimman umurnai game da yadda rayuwa da halin masu kulla da ikilisiya ya kamata ya kasance.
"aiki mai daraja"
Dole shugaban Ikilisiya ya kasance mai mata ɗaya. Ba a bayana a fili ba ko wannan ya shafi wanda ya taɓa kasancewa gwauro ko wanda aurensa ya mutu, ko wanda bai taɓa aureba.
"kada ya zama mai aikata abubuwa fiye da yadda ake buƙata, mai aikata abu mai ma'ana, mai ɗa'a, ya kuma zamanto abokin baƙi"
"kada ya zama mashayin barasa ko mai son yin faɗa da gardama, maimakon haka ya kasance mai ɗa'a da salama"
"haɗamar kuɗi"
"ya shugabanci" ko "ya lura da abu"
Ma'anonni masu yiwuwa suna kamar haka 1) yaran shugaban su kasance masu biyayya da girmama mahaifinsu, ko 2) yaran shugaban su zama da bangirma ga kowa, ko 3) shugaban ya kasance mai daraja waɗanda suke iyalinsa, a sa'ad da yake shugabantar su.
"cika da girmamawa" ko "daraja mutane a kowane lokaci"
"Gama idan mutum bai iya lura ba"
Bulus ya yi amfani da tambaya ya koyar da Timoti. AT: "ba zai iya lura da Ikilisiyar Allah ba." ko "ba zai iya shugabantar Ikilisiyar Allah ba."
A nan "Ikilisiya" na nufin ƙungiyar jama'ar Allah. AT: "ƙungiyar jama'ar Allah" ko " Masubi da ke ƙarƙashin shugabancin sa"
"kada ya kasance sabon tuba" ko "dole ya kasance mai bi da ya girma"
Bulus na maganar kasancewa cikin hukunci domin laifi kamar wani rami ne da mutum zai iya faɗi a ciki. AT: "Allah ya hukunta shi kamar yadda ya hukunta Ibilis"
"waɗanda ba 'yan Ikilisiya ba." Bulus na magana game da Ikilisiya kamar wani wuri ne da ake shiga, sai kuma marasabi kamar suna wajen Ikilisiyar. AT: "waɗanda ba masubi ba"
Bulus na maganar wulakãnci da yadda Ibilis ke sa mutum ya yi zunubi kamar wani rami ne na tarko da mutun ke faɗi ciki. A nan "faɗi ciki" na nufin yanayin da mutum ya kasance. AT: "domin kada Ibilis ya sa shi zunubi"
"Dikinoni, kamar Shugabanen Ikilisiya"
Bulus na magana game da waɗanan mutanen kamar suna magana biyu ko suna faɗan abubuwa biyu a lokaci guda. Yana nufin cewa mutumin na faɗin abu amma yana nufin wani abu dabam. AT: " kasance da rayuwa mai kyau da kuma tabbatar da maganarsa"
"Dole su cigaba da gaskata gaskiyar saƙon Allah da ke a bayyane gare mu da kuma masubi." wannan na nufin gaskiyar da ke nan a da amma Allah ya nuna masu a wannan lokaci. Bulus na maganar gaskiyar koyarwa game da Allah kamar wani abu ne da mutum ke iya ajiye wa a wurinshi.
AT: "gaskiyar da Allah ya bayyanar"
Bulus na maganar sanin mutum cewa bai aikata wani laifi ba kamar wannan sanin ko lamirin na da tsabta. AT: bangaskiyar sanin cewa sun yi iyakar ƙoƙarinsu su aikata abun da ke daidai"
AT: "Dole ne sauran masubi su amince da su tukuna" ko "su nuna tabbacin kansu tukuna"
Wannan na nufin sauran masubi ma su kimanta waɗanda suke so su zama dikinoni, su kuma yanke shawara ko sun yi daidai su yi hidima a cikin Ikilisiya.
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "mata" na nufin matan dikinoni, ko 2) "mata" na nufin dikinoni da ke mata.
"hali mai kyau" ko "cancanci girmamawa"
"Bai kamata suna muguwar magana game da wasu ba"
"ba tare da aikata fiye da yadda ya kamata ba." dubi yadda aka fasara wannan cikin 1Timoti 3:2
Dole na miji ya kasance da mata ɗaya. Ba a bayana a fili ba ko wannan ya shafi wanda ya taɓa kasancewa gwauro ko wanda aurensa ya mutu, ko wanda bai taɓa aureba. Dubi yadda aka fasara wannan cikin 1 Timoti 3:2
"tafiyad da yaran da kyau da wasu da ke zama a gidajen su"
"ga dikinoni waɗanda" ko "ga waɗannan shugabanen Ikilisiya"
"sama wa kansu" ko "ribato wa kansu"
Ana iya nuna ainihin ma'anar wannan a fili. AT: "suna mai kyau a cikin sauran masubi"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) za su amince da Yesu sosai, ko 2) za su yi magana da gabagaɗi wa wasu mutuna game da bangaskiya a cikin Yesu.
"ammaidan ban iya zuwa wurin da sauri ba" ko "Amma idan wani abu ya riƙe ni ban samu zuwa da sauri ba"
Bulus na maganar kungiyar masubi kamar su iyali ɗaya ne. Ma'anoni masu yiwuwa sana kamar haka 1) Bulus na magana game da halin Timoti ne kadai a cikin Ikilisiya. AT: " domin ka san yadda za ka gudanar da rayuwarka a matsayin ɗan iyalin Allah" ko 2) Bulus na magana da masubi dukka. AT: "domin ku duka ku san yadda zaku gudanar da kanku a matsayinku na 'yan iyalin Allah"
Wannan maganar na ba da bayani game da "gidan Allah" ba wai yana nuna banbanci tsakanin gidan Allah wanda itace Ikilisiya da kuma wanda ba Ikilisiya ba. Ana iya sa wannan cikin sabuwar jumla. AT: "gidan Allah. Waɗanda suke na iyalin Allah suna jama'ar Allah rayayye"
Bulus na maganar yadda masubi sun zama shaidu na gaskiya game da Almasihu kamar sun zama ginshiḷƙi da tushen da ke tallafawa wani gini. Ana iya sa wannan cikin sabuwar jumla. AT: "wato Ikilisiyar Allah rayayye. Kuma tawurin kiyaye gaskiyar koyarwar Allah jama'ar Ikilisiya suna tallafawa gaskiya kamar yadda ginshiƙi da tushe ke tallafawa gini"
Wannan maganar anan na iya ba da ra'ayin cewa Allah ne wanda yake ba da rai ga kowa, kamar yadda yake a cikin UDB.
"ba wanda zai iya ƙaryatawa"
AT: "da cewa gaskiyar da Allah ya bayyana da girma take"
Mai yiwuwa wannan wata waƙa ce da Bulus ya ruwaito. Idan akwai yadda harshenku zai nuna cewa wannan waƙa ne, ku na iya amfani da shi. In kuma babu, to a fasara shi a yadda ya ke.
A nan kalman "ya" ba'a fili ya ke ba. Yana iya nufin "Allah" ne ko "Almasihu." Zai fi kyau a fasara wannan yadda yake "Ya." Idan yazama lallai a ba da takamammen fasara, a sa shi haka "Almasihu wanda shine Allah" ko "Almasihu."
A nan Bulus ya yi amfani da "jiki" da nufin mutum. AT: "a matsayin mutum na gaske"
AT: Ruhun Mai Tsarki ya tabbatar cewa shine wanda ya ce da kansa"
AT: "Mutane ƙasashe dayawa suka faɗa wa wasu game da shi"
AT: "Mutane a wurare dayawa cikin duniya suka gaskata da shi"
AT: "Allah Uban ya ɗauke shi zuwa sama cikin ɗaukaka"
wannan na nufin cewa ya samu iko daga Allah Uba kuma ya cancanci daraja.
1To Ruhu ya fada a fili cewa, a zamanin karshe wadansu mutane za su kauce daga bangaskiya, su mai da hankalin su ga ruhohi masu rudi, da koyarwar aljannu, 2cikin karya da munafunci. Lamirinsu zai yi kanta.3Za su haramta aure da karbar abincin da Allah ya halitta, domin su raba da godiya a cikin wadanda suka bada gaskiya suka kuma san gaskiyar. 4Gama duk abin da Allah ya halitta yana da kyau. Domin duk abin da muka karba da godiya, bai kamata mu ki shi ba. 5Gama an tsarkake shi ta wurin maganar Allah da addu'a.6Idan ka tuna wa 'yan'uwa wadannan abubuwa za ka zama bawan kirki na Almasihu. Domin ana gina ka ne ta wurin maganar bangaskiya da kuma kyakkyawar koyarwa wadda ka bi. 7Amma ka guji labaran almara wadanda tsofaffin mata ke so. Maimakon haka sai ka hori kanka cikin bin Allah. 8Domin horon jiki ya na da amfani kadan. Amma horon kai cikin bin Allah yana da amfani ga dukkan abubuwa. Gama a cikinsa akwai alkawari domin wannan rayuwar da kuma rayuwa mai zuwa.9Maganan nan amintacciyace ta isa a karbe ta dungum. 10Dalilin da ya sa kenan mu ke aiki tukuru. Domin muna sa bege ga Allah mai rai, mai ceton dukkan mutane, musamman masu ba da gaskiya.11Ka yi shela ka kuma koyar da wadannan abubuwa. 12Kada ka yarda kowa ya rena kuruciyarka. Maimakon haka, ka zama abin koyi ga dukkan masubi: a furci, hali, kauna, aminci da kuma tsarki. 13Har sai na zo, ka himmatu da yin karatu, da wa'azi, da kuma koyarwa.14Kada ka yi sakaci da baiwar da ka ke da ita wadda aka baka ta wurin anabci sa'ad da dattawa suka dibiya maka hannayensu. 15Ka kula da wadannan abubuwa. Ka himmatu a cikinsu. Domin ci gabanka ya zama sananne a idanun kowa. 16Ka kula da kanka da kuma koyawarka. Ci gaba a cikinsu. Domin ta yin haka ne za ka ceci kanka da masu sauraronka.
Bulus na gaya wa Timoti abun da Ruhu ya faɗa cewa zai faru, ya kuma ƙarfafa shi cikin abun da zai koyar.
An yi amfani da wannan kalmar a nan domin a canja daga ainahin koyarwan. Bulus ya fara gabatar da sabuwar sashin koyarwan.
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) wannan na nufin zamanin da ke zuwa bayan Bulus ya mutu, ko 2) wannan zamani ne a karshen rayuwar Bulus.
Bulus na maganar yadda mutune ke daina gaskatawa cikin Almasihu kamar yadda mutum ke barin wani wuri ko wani abu. AT: "daina gaskatawa cikin Yesu"
"bayar da hankali" ko "domin suna bayar da hankalinsu"
"ruhohi masu yaudarar mutane da abubuwan da aljanu ke koyarda"
Ana iya faɗin wannan a wata sabuwar jumla. AT: "aljanu. Waɗannan mutane za su kasance munafukai da masu faɗin ƙarya"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) Bulus na maganar mutanen da basu iya ganewa ko sun aikata mumunar abu kamar tunaninsu na da illa da za a iya kwatantashi da fatar da wani ya ƙona da karfe mai zafi, ko 2) Bulus na magana game da waɗanan mutanen kamar Ibilis ya yi musu tabo da karfe mai zafi domin ya nuna cewa su nasa ne.
"waɗanan mutanen za su"
ya nuna cewa za su hana masubi aure. AT: "hana masubi aure"
ya nuna cewa za su hana wasu irin abinci. AT: "za su bukaci masubi su ƙauce wa wasu irin abinci" ko "ba za su yarda mutane su ci wasu irin abinci ba"
AT: "komai da Allah ya halitta yana da kyau"
AT: "kada mu ƙi karɓar duk abun da muka ba Allah godiya" ko "duk abun da muka ci da godiya karɓaɓɓe ne"
A nan "maganar Allah" da "addu'a" na nufin abu daya ne. Addu'ar na amincewa da gaskiyar da Allah ya bayyana. AT: " an keɓe domin aikin Allah ta wurin addu'a da amincewa da kalmarsa"
AT: "mun tsarkake shi" ko "mun keɓe shi"
A nan "kalma" na nufin saƙon Allah ko abun da ya bayyanar.
Bulus na maganar umurninsa kamar wani abu ne da ake iya gani da iddo ana miƙa wa masubi. A nan, a "miƙa wa" na nufin umurni ko a tunatar. AT: "idan kana taimakawa masubi ka tuna da waɗanan abubuwan"
wannan na nufin koyarwar da aka fara a cikin 1 Timoti 3:16.
wannan na nufin masubi maza ko mata.
Bulus na magana game da maganar Allah da koyarwarta kamar wani abu ne da ake gani da ido na ciyad da Timoti domin ya yi karfi. AT: "kalmar gaskiya da kyakyawar koyarwa da ka bi har ya sa ka amincewa da Almasihu da karfi sosai"
"maganar da ke sa mutane su gaskata"
"mummunar labarai da tatsuniyar tsofaffin mata." kalmar "tatsuniya" na nufin abu ɗaya ne da "labari" a cikin 1 Timoti 1:4, don haka a fasara shi haka a nan.
Wannan maganar na iya nufin "wauta" ko "abu mara ma'ana." Ba wai Bulus na da niyyar zagin tsofaffin mata bane. Amma shi Bulus da wanda yake rubuto musu sun fahimci cewa maza na mutuwa kafin mata, don haka an fi samun mata da tunaninsu bashi da zurfi domin shekaru fiye da maza.
horad da kanka ga daraja Allah" ko "horad da kanka ta wurin aikata abun da zai gamshi Allah"
"motsa jiki"
"na da amfani a wannan rayuwar"
"ta isa ka gaskata sosai" ko "ta isa ka amince sosai"
"Wannan ne dalilin"
kalmar "fama" da "aiki tukuru" na nufin abu daya ne. Bulus ya yi amfani da su tare domin ya nuna tsananin hidimar su ga Allah.
Mai yiwuwa a nan "Allah mai rai" na nufin "Allah da ya sa kowane abu ya rayu."
Ana iya ƙara bayyana wannan maganar a fili. AT: "shi mai ceto ne musamman ga wanda suka ba da gaskiya"
"ba da umurni da koyarwar waɗanan abubuwa" ko " ba da umurni da kuma koyar da waɗanan abubuwan kamar yadda na faɗa"
"kada ka yarda kowa ya kalle ka da rashin muhimmanci domin kai saurayi ne"
Ana iya sa kalmomin nan "karatu", "Wa'azi", da "koyarwa" ta wani sifar jumla. Ana iya saka wannan kuwa a cikin fasara. AT: "cigaba da karata wa mutane littafin, ka yi musu wa'azi, da kuma koyar da su"
Bulus na magana game da Timoti kamar shi wani abu ne da za a iya sa baiwar Allah a ciki. AT: "kada ka sake baiwar ka ta Ruhu Mai Tsarki"
AT: "ka tabbata ka yi amfani"
AT: "wadda ka samo sa'ad da shugabanen Ikilisiya suka yi shelar maganar Allah"
Wannan biki ne da dattawar Ikilisiya suka ɗore hannuwarsu bisa Timoti suka kuma yi addu'a Allah ya bashi ikon aikata abun da ya umurce shi ya yi.
Bulus na managa da Timoti game da baiwar Allah kamar wani abu ne da ake iya zama a ciki. AT: "Aikata dukka waɗannan abu ka kuma yi rayuwa bisa ka'idarsu"
Bulus na maganar cigaban Timoti a bautar Allah kamar wani abu ne da mutane ke iya kallo. AT: " domin mutane su gani cewa kana bautar Allah da kyau da kyau"
"ka gudanar da kanka cikin hankali, ka kuma mayar da hankalinka ga koyarwar" ko "lura da halinka, ka kuma sa hankali ga koyarwar"
"ka cigaba da aikata waɗannan abubuwa"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) Timoti zai ceci kansa da kuma waɗanda suke sauraronsa daga hukuncin Allah, ko 2) Timoti zai ceci kansa da kuma masu sauraronsa daga rinjayar mallaman ƙarya.
1Kada ka tsauta wa dattijo. Sai dai ka gargade shi kamar mahaifi. Ka gargadi samari kamar 'yan'uwa. 2Gargadi dattawa mata kamar iyaye mata, 'yan mata kamar 'yan'uwa mata cikin dukkan tsarki.3Ka girmama gwamraye, gwamraye na gaske. 4Amma gwamruwar da take da 'ya'ya ko jikoki, bari su fara nuna bangirma cikin danginsu. Bari su sakawa iya-yensu, domin Allah yana jin dadin haka.5Amma gwamruwa ta gaske da ke ita kadai, ta kafa begenta ga Allah. Kullum tana tsananta yin roke-roke da addu'o'i dare da rana. 6Amma, mace mai son zaman annashuwa ta riga ta mutu, ko da shike tana raye.7Kuma ka yi wa'azin wadannan al'amura donsu zama marasa abin zargi. 8Amma idan mutum bai iya biyan bukatun 'yan'uwansa ba, musamman iyalin gidansa, ya musunci bangaskiya, kuma gara marar bi da shi.9Bari a lisafta mace gwamruwa idan ba ta kasa shekara sittin ba, matar miji daya. 10A san ta da kyawawan ayyuka, ko ta kula da 'ya'yanta, ko tana mai karbar baki, ko mai wanke kafafun masubi, ko mai taimakon wadanda ake tsanantawa, mai naciya ga kowanne kyakkyawan aiki.11Amma game da gwamraye masu kuruciya, kada a sa su cikin lissafi. Domin idan suka fada cikin sha'awoyin jiki da ke gaba da Almasihu, sukan so su yi aure. 12Ta wannan hanya ce sun tara wa kansu tsarguwa saboda sun tada alkawarinsu na fari. 13Sun saba da halin ragwanci, suna yawo gida gida. Ba zama raggwaye kawai su ka yi ba. Amma sun zama magulmata, masu shishshigi, masu karambani. Suna fadin abin da bai dace ba.14Saboda haka ina so gwamraye masu kuruciya su yi aure, su haifi 'ya'ya, su kula da gida, domin kada a ba magabci zarafin zargin mu ga aikata mugunta. 15Domin wadansu sun rigaya sun kauce zuwa ga bin shaidan. 16Idan wata mace mai bada gaskiya tana da gwamraye, bari ta taimakesu, don kada a nawaita wa Ikilisiya, domin Ikilisiya ta iya taimakon gwamraye na gaske.17Dattawa wadanda suke mulki da kyau sun cancanci girmamawa ninki biyu, musamman wadanda suke aiki da kalma da kuma koyarwa. 18Gama nassi ya ce, "Kada a sa takunkumi a bakin takarkari lokacin da yake sussukar hatsi," kuma "Ma'aikaci ya cancanci a biya shi hakinsa."19Kada ka karbi zargi game da dattijo sai shaidu sun kai biyu ko uku. 20Ka tsauta wa masu zunubi gaban kowa domin sauran su ji tsoro.21Na umarce ka a gaban Allah, da Almasihu Yesu, da zababbun mala'iku ka kiyaye ka'idodin nan ban da hassada kuma kada ka yi komai da nuna bambanci. 22Kada ka yi garajen dibiya wa kowa hannuwa. Kada ka yi tarayya cikin zunuban wani. Ka tsare kanka da tsabta.23Kada ka ci gaba da shan ruwa. Amma, maimakon haka ka sha ruwan inabi kadan saboda cikinka da yawan rashin lafiyarka. 24Zunuban wadansu mutane a bayyane suke, sun yi gaba da su cikin hukunci. Amma wadansu zunubansu na bin baya. 25Haka kuma, wadansu kyawawan ayyukansu a bayyane suke, amma wadan sun ma ba su boyuwa.
Bulus ya cigaba da gaya Timoti yadda zai bi da maza, mata, gwauruwaa, da kuma mata masu ƙuruciya a cikin Ikilisiya.
Bulus na ba da waɗannan umurnai ga mutum ɗaya ne, wato Timoti.
"kada ka faɗa wa dattijo baƙin magana"
"A maimako, ka ƙarfafa shi"
Bulus ya yi amfani da waɗannan kwatanci ya gaya wa Timoti cewa ya bi da 'yan'uwa masubi da sahihiyar ƙauna da girmamawa.
Za a iya bayyana wannan a fili, cewa. AT: "gargadi mata masu ƙurciya" ko "karfafa mata masu ƙuruciya"
"tunani da halin tsarki" ko "cikin hanyar tsarki"
"tanadi da girmama gwauraye"
"gwauraye da ba wanda zai yi masu tanadi"
"da farko su koyi" ko "bari su sa fifiko a koyon"
"wa danginsu" ko "ga waɗanda suke zama a gidansu"
"Bari su yi wa iyayensu alherin da suka yi musu"
"Amma wadda ta ke gwauruwar gaske ba ta da iyali"
"ta cigaba da miƙa roƙo da adduo'i"
dukka waɗannan kalmomi suna nufin abu ɗaya ne. Bulus ya yi amfani da su tare domin domin ya jaddad yadda waɗannan gwauraye ke addu'a.
An yi amfani da waɗannan kalmomi "dare" da "rana" da nufin "kowane lokaci." AT: "kowane lokaci"
Bulus na magana game da waɗanda ba sa ƙoƙari su gamshi Allah kamar su mattatu ne. AT: "kamar wadda ya mutu, ba ta jin Allah"
Wannan na nufi ba matacce ba.
"Umurci waɗannan abubuwa"
"domin kada wani ya same su da laifi." Mai yiwuwa "su" na nufi 1) "waɗannan gwaurayen da iyalinsu" 2) "masubi." Zai fi kyau a yi amfani da shi kalmar "su."
"baya taimakon daginsa da bukatu, tun ma ba 'yan iyali da suka kasance a gidansa ba"
"baya aikata bisa ka'idar bangaskiyarmu ba"
"ya fi wanda ba su ba da gaskiya ga Yesu ba muni." Bulus na nufi cewa wannan mutum ya fi marasa bi mugunta domin marasa bi ma suna lura da danginsu. Saboda haka, lalle ne mai bi ya kula da danginsa.
Ya yiwu akwai lisafin gwauraye, ko rubutacce ko ba a rubuce ba. 'Yan Ikilisiya ne ke biya wa waɗannan matan bukatun su na mafaka, tufafi, da abinci. Waɗannan mata kuwa ana sa rai za su duƙufa cikin bautar al'umman masubi.
Kamar yadda Bulus ya bayyana a 5:11-16, gwauraye wanɗanda ba su kai shekaru sittin ba na iya sa ke aure. Saboda haka, al'umman masubi su kula da gwauraye wanda su ka shige shekaru sittin.
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) tana da aminci ga mijin ta, ko 2) ba ta saki mijin ta zuwa auren wani ba.
AT: "Mutane sun shaida da kyawawan ayyukanta"
"ta marabci baƙi cikin iyalin ta"
Wanke kafafun wadda suka yi datti ko da taɓo hanyar biya wa wasu bukata ne, kuma sa su su ji daɗi. Wannan na iya nafin cewa tana da halin tawali'u. AT: "ta saba aikin taimakawa 'yan'uwa masubi"
Wasu juyi sun fasara kalmar cewa "masubi" ko "tsarkaka mutanen Allah." Abu mai muhimminci kawai shine ana nufi 'yan'uwa masubi.
AT: "ta taimaki waɗanda suke wahala"
"ta miƙa kai ga aikata kowane irin kyawawan ayyuka"
"Amma kada ka sa gwauraye masu ƙuruciya a lisafin." Lisafin na gwauraye ne wadda suka kai shekaru sittin zuwa sama da al'umma masubi zasu taimakawa.
"Domin a sa'ad da sun fi so su cika sha'awar su na son aure, to sai su kasa cika alkawarin bautar Almasihu na gwauraye"
"ba su kiyaye wa'adinsu na da ba" ko "ba su yi abun da suka yi alkawarin yi a baya ba"
Wa'adin gwauraye shi ne hidimar da za su yi wa al'aumma masubi muddin ransu, in al'ummar za su tanada musu bukatunsu.
"koyi halin zama ba abun yi"
Duk waɗannan na yiwuwa ana maganar abu ɗaya ne. Waɗannan mutane su daina shishigi, suna shiga harkokin wasu da bai shafe su ba, har ma suna faɗa wa wasu abin da ma ba taimako zai yi ba.
maganar da ba zai taimaki masu sauraro ba
"kula da kowa da kowa da ke cikin gidansu"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) Wannan na nufin Shaiɗan, ko 2) Wannan na nufin marasabi wanda suna gãba da masubi.
A nan "mu" na nufi dukan al'ummar masubi, har da Timoti.
Bulus na maganar amincewa da Almasihu kamar wani hanya ne da ake takawa a bi. Wannan na nufin matar da ta daina biyayya da Yesu, ta kuma fara biyayya da Shaiɗan. AT: "barin hanyar Almasihu zuwa bin Shaiɗan" ko "zaɓi yi wa Shaiɗan biyayya a maimakon yi wa Almasihu"
"kowace mace mai bi" ko "kowace mace wanda ta gaskanta da Almasihu"
"na da gwauruwa a cikin danginta"
Bulus na maganar yadda al'ummar masubi ke taimakon mutane fiye da yadda yakamata su yi kamar suna ɗaukan wani abu ne mai nauyi a bayansu. AT: "domin kada Ikilisiya ta yi ta hidima fiye da iyawanta" ko "domin kada al'ummar masubi su taimaki gwauraye wanda iyalinsu na iya tanada musu"
AT: "duk masubi su dubi dattawan da suke aiki mai kyau da daraja"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "girmamawa da biya" ko 2) "girmama fiye da yadda wasu ke samu"
Bulus na magana game da wa'azin kalmar kamar wani abu ne da mutum yake iya aiki da shi. AT: "waɗanda suke wa'azi da koyar da maganar Allah"
Wannan na nufin abun da wani ya rubuta a cikin nassi. AT: Domin mun karanta a cikin nassi cewa"
Bulus na kawo maganar nan da nufin cewa yakamata al'ummar masubi su biya shugabanen Ikilisiya domin aikinsu.
Wannan wani abu ne da ake sa wa a hanci da bakin dabba don a hana ta cin abinci sa'ad da take aiki
takarkari na "sussukar hatsi" a sa'ad da yake tafiya ko jan wani abu mai nauyi akan hatsin da aka yanke don a raba hatsin da kara. Ana barin takarkarin ya ci daga hatsin a lokacin da yake aiki.
"isa"
Bulus na maganar ƙara kamar wani abu ne da ake iya ɗauka a mika wa mutane su karɓa. AT: "Kada ka yarda da ƙarar da wani ya kawo"
"a kalla biyu" ko "biyu ko fiye"
Wannan na nufin duk wanda yake aikata rashin biyayya ko abu da baya fararta wa Allah rai, ko mutane sun san da abun ko basu sani ba.
"inda kowa da kowa na iya gani"
"domin sauran su ji tsoron aikata zunubi"
Wannan na nufi mala'ikun da Allah da Yesu suka zaɓa domin su yi hidima ta musamman.
Kalmar "son kai" da "gatanci" na nufin abu ɗaya ne. Bulus na jaddada cewa dole Timoti ya yi hukunci cikin adalci da sassauci ga kowa. AT: "kiyaye waɗannan dokoki ba tare da nuna gatanci ko son kai ba"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) dokokin da Bulus ya gaya wa Timoti, ko 2) dokokin da Bulus na shirin faɗa wa Timoti.
ɗora hannu biki ne da shugabanen Ikilisiya ko shugaban ikisiliya ke ɗora wa mutane hanu a kuma yi addu'a ga Allah ya ba su ikon yi wa ikilisiya hidimar da zai gamshi Allah. Yakamata Timoti ya jira sai mutumin ya nuna halin kirki na tsawon lokaci kafin ya keɓe wannan mutumin domin hidima wa jama'ar masubi.
Bulus na maganar zunubin wani kamar wani abu ne da a ke iya rabawa da wasu. AT: "kada ka yi taraya a zunubin wani" ko "kada ka sa hannu a sa'ad da wani na aikata zunubi"
Wannan na nuna cewa ba ruwa kaɗai Bulus ke ce wa Timoti ya sha ba. Yana ce wa Timoti yayi amfani da ruwan inabi a matsayin magani. Ruwar wurin na sa cuta.
AT: "Zunuban wasu mutane a sarari suke"
"zunuban waɗanan mutanen zasu bi su har hukunci." Bulus na maganar zunubai kamar suna motsi. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) Zunuban su a fili suke wa kowa, ba sai wani ya ba da mumunar shaida akan su ba, 2) Zunubansu a fili suke, kuma yanzu Allah zai hukuntasu.
"Amma wasu zunuban daga baya mutane suke gani." Bulus na maganar zunubai kamar suna motsi. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) Timoti da al'ummar masubi ba za su san da wasu zunubai ba sai nan gaba, ko 2) Allah ba za ya hukunta wasu zunubai ba sai a ranar shariya.
"a sarari wasu kyawawan ayyuka suke"
Ana duban ayyukan a matsayin "kyawawa" domin sun dace da halin Allah, da nufinsa.
Bulus na magana game da zunubi kamar wani abu ne da ake iya ɓoye wa. AT: "Amma nan gaba mutane zasu san da kyawawan ayyukan da ba a fili suke ba"
1Bari duk wadanda ke bayi a karkashin karkiya su ga iyayengijinsu sun cancanci dukan daraja. Su yi haka domin kada a sabawa sunan Allah da koyarwarsa. 2Bayin da suke da iyayengiji da ke masu ba da gaskiya kada su rena su saboda su 'yan'uwa ne. A maimakon haka, su yi masu hidima da kwazo. Gama iyayengijin da suke cin ribar aikinsu masu bi ne, kaunattatu kuma. Ka koyar ka kuma bayyana wadannan abubuwa.3Idan ya kasance wani na koyar da wani abu dabam bai kuma yarda da amintaciyar koyarwa ba, wato maganar Ubangijinmu Yesu Almasihu. Alal misali ba su amince da koyarwa da ke kai ga Allahntaka ba. 4Wannan mutum mai girman kai ne, kuma bai san komai ba. A maimakon haka, yana da matukar jayayya da gardama game da kalmomi. Wadannan kalmomi na kawo kishi, da husuma, da zage-zage, da miyagun zace-zace, da 5yawan rashin jituwa tsakanin mutane masu rubabbun hankula. Sun bijire wa gaskiya. Suna tunani cewa ibada hanya ce ta yin arziki." Ka zame daga wadannan abubuwa.6Yanzu bin Allah tare da dangana babbar riba ce. 7Gama ba mu kawo komai a duniya ba, ba zamu iya fita cikinta da komai ba. 8A maimakon haka, mu dangana da abinci da kuma sutura.9To wadanda ke son zama mawadata su kan fada cikin jaraba, cikin tarko. Suna fadawa cikin abubuwan wauta da sha'awoyi masu illa da kowanne abu da ke sa mutane su dulmaya cikin lallacewa da hallaka. 10Gama son kudi shine tushen kowacce irin mugunta. Wadansu mutane garin neman kudi sun kauce daga bangaskiya, sun kuma jawowa kansu bakin ciki mai yawa.11Amma kai, mutumin Allah, ka guji wadannan abubuwa, ka bi adalci, ibada, aminci, kauna, jimiri, da tawali'u. 12Ka yi fama, fama mai kyau na bangaskiya. Ka kama rai madawami da aka kira ka gare shi. A kan wannan ne ka ba da shaida a gaban shaidu masu yawa game da abin da ke da kyau.13Ina ba ka wannan umarni a gaban Allah wanda ke rayar da dukan abubuwa, da gaban Almasihu Yesu, wanda ya fadi abin da ke gaskiya ga Bilatus Babunti. 14Ka bi doka daidai, babu abin zargi har bayanuwar Ubangijinmu Yesu Almasihu.15Allah zai nuna bayyanuwarsa a daidai lokaci- Allah, mai albarka, Makadaicin iko, Sarkin da ke sarauta, Ubangiji mai mulki. 16Shine kadai marar mutuwa, mai zama cikin hasken da ba ya kusantuwa. Ba wanda ke ganinsa, ko ya iya hango shi. Girma ya tabbata a gare shi da kuma madawwamin iko. Amin.17Ka gaya wa masu dukiya a cikin wannan duniya kada su daga kai, kada su sa bege ga arziki mara dawwama. Maimamakon haka, su sa begensu ga Allah wanda ke ba mu wadatar gaske domin jin dadin mu. 18Gaya masu su yi nagarta su arzurta a ayyuka nagari, su zama masu bayarwa hannu sake. 19Ta haka za su ajiye wa kansu harsashi mai kyau kan abin da ke zuwa domin su amshi rayuwa ta kwarai.20Timoti, ka kare abin da aka ba ka. Ka nisanci maganar wauta da gardamomin da ke sabawa juna wanda ake kira ilimi a karyace. 21Wadansu mutane suna shelar wadannan abubuwa, don haka sun kauce wa bangaskiyar. Bari alheri ya kasance tare da kai.
Bulus yana ba da umurnai musamman ga bayi da iyayengida, sannan ya cigaba da ba da umurnai game da zaman rayuwar da zai gamshi Allah.
Bulus na magana game da bayi kamar su takarkari ne da ke ɗauke da kaya. AT: "Bari duk wanda suke aiki a matsayin bayi"
Wannan na nuna cewa Bulus na magana game da masubi. AT: "Bari wanda suke masubi"
AT: "marasabi su girmama sunan Allah da koyarwar nan"
A nan "suna" na nufi yadda Allah yake ko ɗabi'unsa. AT: "ɗabi'un Allah" ko "Allah"
"bangaskiya" ko "bishara"
A nan " 'ya'uwa" na nufi " 'yan'uwa masubi."
AT: "Domin Iyayengidan da bayin ke taimakonsu da aikinsu"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) da kuma bayin da suke ƙaunar su" ko 2) "wanda Allah ke ƙauna"
A nan "Yana" na nufi duk wanda yake koyar da abun da ba daidai ba. Domin bayyana wannan a fili kana iya fasara "yana" kamar "su" a UDB.
"bai san komai game da gaskiyar Allah ba"
Bulus na magana game da mutane da ke jin cewa tilas ne su yi jayayya mara amfani kamar basu da lafiya. waɗannan mutane suna da matukar marmarin jayayya, kuma ba sa son amincewa. AT: "abun da ya ke so kadai shine jayayya" ko "yana neman jayayya"
"gardama da jayayya game da maganganu, da kuma gardama da jayayya masu jawo ƙishi"
"game da ma'anar kalmomi"
jayayya, faɗa
mutane suna faɗin munanan abubuwa game da juna da ba gaskiya
"mutane suna ji kamar wasu suna so su yi musu mugunta"
"muguwar tunani"
A nan kalmar "su" na nufi duk wanda yake koyar da abun da bai daidaita da koyarwa Yesu ba. kalmar "ƙaurace wa gaskiya" na nufin yin watsi ko mance wa da abu. AT: "Sun yi watsi da gaskiyar" ko "Sun mance da gaskiyar"
Wannan na nuna canji daga koyarwar. Bulus ya fara bambamta irin arzikin da mugayen mutane su ke nema ta bin Allah (1Timoti 6:5) da asalin riban da ake samu ta wurin bin Allah. AT: "haƙiƙa"
Kalmar nan "bin Allah" da kuma "wadar zuci" suna bayana yanayin mutum ne. AT: "Abu ne mai riba da yawa idan mutum na bin Allah, kuma yana dangana da abun da yake da shi"
"na da matukar amfani" ko "zai yi ma na abubuwa masu kyau"
"bamu kawo kome duniya ba lokacin da a ka haife mu"
"ba kuwa za mu iya fita da kome ba a sa'ad da mun mutum"
"sai mu"
Bulus na magana game da waɗanda suka yarda jarabar kuɗi ya sa su cikin zunubi, kamar su dabboni ne da suka faɗi a cikin tarkon rami da mafarauci ke yi. AT: "zama masu arziki na da jarabobi sosai da za su fuskanta kuma su yi tsayayya da ita. Za su zama kamar dabbar da ke a tarko
An cigaba da amfani da tarko domin bayani. Wannan na nufin cewa wauta da sha'awoyinsu zasu ka da su. AT: "Kuma kamar yadda dabba ke făɗowa a tarkon mafarauci haka ma zasu făɗa cikin wauta da sha'awoyi masu illatarwa da yawa"
Bulus na magana game da waɗanda suka yarda zunubi ya hallakar da su kamar su wani jirgin ruwa ne da ke nutsewa a ruwa. AT: "zuwa kowane irin muguwar lalata da ke hallakar da mutane kamar su jirgin ruwa ne da ke nutsewa a ruwa"
Bulus na maganar sanadin mugunta kamar wani tushen abun da aka shuka. AT: "Wannan na faruwa haka domin son kuɗi shi ke zama sanadin kowane irin mugunta"
"wanda ke sha'awar kuɗi"
Bulus na maganar muguwar sha'awa kamar su mugayen jagora ne da ke jagorar mutane ta mummunar hanya da gangan. AT: "suka bar sha'awoyinsu suka bauɗar da su daga gaskiya" ko "daina amincewa da gaskiyar"
Bulus na maganar baƙin ciki kamar wani takobi ne da mutum ke amfani da shi ya soki kansa. AT: "suka sa wa kansu baƙin ciki matuƙa"
A nan "kai" na nufi Timoti ne.
"bawan Allah" ko "mutum da ke na Allah"
Bulus na magana game da waɗannan jarabobi da zunubai kamar su abubuwa ne da mutum ke iya yin gudu daga wurin su. AT: "kauce wa waɗannan abubuwan gaba ɗaya"
Mai yiwuwa "waɗannan abubuwa" na nufi 1) "son kuɗi" ko 2) wani koyarwa dabam, girman kai, jayayya, da son kuɗi.
"bi da gudu" ko "bi"
A nan Bulus na maganar yadda mutum na cigaba a cikin bangaskiya kamar ɗan wasan guje-guje ne da ke fama domin nasara, ko mayaƙi ne da yake kan yaƙi. AT: "Yi iyakar ƙoƙarin biyayya da koyarwar Almasihu da yawan kuzari kamar ɗan wasan guje-guje"
An cigaba da bayani. Bulus na maganar yadda mutum yake samun rai madawwami kamar shi wani ɗan wasa ne ko mayaƙi da ke karbar ladar nasara"
AT: "wanda Allah ya ƙira ka sobada shi"
'Ka ba da kyakkyawar shaida" ko "ka shaida gaskiyar"
Bulus na magana a kan wuri domin ya ba da bayani a kan mutanen da Timoti ke magana. AT: "ga shaidu da yawa"
"Wannan ne abun da nake umurtar ka"
"a gaban Allah, wanda yake sa dukan abubuwa su rayu." Wannan na nuna cewa Bulus na biɗar Allah ya zama shaidar shi. AT: "da Allah wanda ya ke sa dukka abubuwa su rayu, ya shaida ni"
"a gaban Almasihu Yesu wanda ke shaida ... Bilatus." Yana nuna cewa Bulus na bidar Yesu ya zama shaidar shi. AT: "da Almasihu Yesu wanda ke shaida ... Bilatus, a matsayin shaida na"
Kalmar "aibi" na a nufin laifi. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) Yesu ba zai sami Timoti da wani aibi ba ko ya zargi da wani laifi ba, ko 2) mutane ba za su sami Timoti da laifi ba ko su zarge shi domin aikata abun da ba daidai ba.
"har sai Ubangiji Yesu Almasihu ya sake zuwa"
Ya na nufin cewa Allah zai nuna bayyanuwar Yesu. AT: "Allah zai nuna bayyanuwar Yesu"
"a lokaci da yakamata"
"wanda ya isa yabo, mai mulkin duniya"
"Shi kaɗai yake da ikon rayuwa har abada"
"zama a babban haske da ba mai iya zuwa kusa"
A nan "dukiya" na bayana sunan abu ne. AT: gaya wa wanda suke da dukiya"
"a cikin abubuwa da suka mallaka da za su iya rasawa." Ana nufin kayayyakin da ake iya gani.
"dukka abubuwan da za su sa mun jin daɗi sosai." Wannan na nufi har ma da kayakin da ake iya gani, amma mai yiwuwa ana nufi kayayyakin duniya da mutane suke mallaka domin neman kasancewa cikin ƙauna, farin ciki, da salama.
Bulus na maganar albarkun ruhaniya kamar dukiyar duniya ne. AT: "yi hidima da taimakawa wasu a hanyoyi da yawa"
A nan Bulus na maganar albarkun Allah da yake bayarwa a sama kamar dukiya ne da mutum ke tara wa domin amfani nan gaba. kuma ana maganar tabbacin yadda ba za a rasa waɗannan albarkun ba kamar harsashin gini. AT: "zai kasance kamar suna tara wa kansu abubuwa masu yawa da Allah zai ba su"
Wannan na tunashewa da bayani wasanni da aka yi a 1 Timoti 6:12, wanda ladar abu ne da mai nasara ke karɓa a hannuwan sa. A nan "ladar" shi ne "rayuwa ta ƙwarai."
AT: "ka yi shelar saƙon gaskiya da aminci, wanda Yesu ya danƙa maka"
kada ka saurari maganganun banza"
AT: "game da abun da wasu mutane ke ƙaryar cewa da shi ilimi"
Bulus na maganar bangaskiya cikin Almasihu kamar wani abu ne da ake ƙoƙarin ci ma buri. AT: "basu fahimci ko gaskata da asalin bangaskiyar ba"
"Bari alherin Allah ya tabbata a gare ku duka." "Ku" na nufi dukan al'ummar masubi.
1Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, bisa ga alkawarin rai da ke cikin Almasihu Yesu, 2zuwa ga Timoti, kaunataccen da: Alheri, jinkai, da salama daga Allah Uba da Almasihu Yesu Ubangijinmu.3Na gode wa Allah, wanda na ke bautawa tun daga kakannina, da lamiri mai tsabta, sa'adda na ke tuna wa da kai cikin addu'o'ina koyaushe (dare da rana). 4Sa'adda na tuna da hawayenka, na yi marmarin ganinka, saboda in cika da farin ciki. 5An tunashshe ni game da sahihiyar bangaskiyarka, wadda ta samo asali daga kakarka Loyis da mahaifiyarka Afiniki. Na kuma tabbata ta na zaune a cikinka.6Wannan shine dalilin da ni ke tunashshe ka cewa ka sake rura baiwar Allah da ke cikinka wadda ka samu sa'adda na dibiya maka hannuwana. 7Domin Allah bai ba mu ruhun tsoro ba, amma na iko da kauna da kamun kai.8Saboda haka kada ka ji kunyar shaida ga me da Ubangijinmu, ko ni, Bulus, daurarrensa. Maimakon haka, ka zama a shirye ka sha wahala domin bishara bisa ga ikon Allah. 9Allah ne ya cecemu kuma ya kira mu da kira mai tsarki. Ya yi wannan, ba ta wurin ayyukanmu ba, amma ta wurin shirinsa da alherinsa. Ya ba mu wadannan abubuwan a cikin Almasihu Yesu kafin farkon zamanai. 10Amma yanzu an bayyana ceton Allah ta wurin bayyanuwar mai cetonmu Almasihu Yesu. Almasihu ne ya kawo karshen mutuwa ya kuma kawo rai marar karshe da ya bayyana ta wurin bishara. 11Domin wannan, an zabe ni mai wa'azi, manzo da mallami zuwa ga al'ummai.12Domin wannan dalili na ke shan wahalar wadannan abubuwa. Amma ban ji kunya ba, domin na san shi, wanda na gaskanta. Na sakankance zai iya adana abinda na mika masa har zuwa ranan nan. 13Ka adana misalin amintattun sakwanni da ka ji daga gare ni, ta wurin bangaskiya da kauna da ke cikin Almasihu Yesu. 14Abu mai kyau da Allah ya danka maka, ka tsare shi ta wurin Ruhu Mai Tsarki, da ke zaune a cikinmu.15Ka dai sani, dukkan wadanda su ke zama a Asiya sun juya mani baya. A cikin kungiyar akwai Fijalas da Harmajanas. 16Bari Ubangiji ya yi wa iyalin Onisifaras jinkai, domin ya na yawan yi mani hidima, kuma ba ya jin kunyar sarkata. 17Maimakon haka, sa'adda ya ke a Roma, ya neme ni da kokarin gaske, ya kuma same ni. 18Bari Ubangiji ya sa, ya sami jinkai daga gare shi a wannan rana. Dukkan hanyoyin da ya taimake ni a kasar Afisa, kun sani sarai.
A wannan littafin, kalmar nan "mu" na nufin Bulus ne da Timoti, sai inda aka ce ba haka ba,
Mai yiwuwa harshen ku na da yadda ake gabatar da marubucin wasiƙa; yi amfani da shi. Haka kuma bayan gabatar da marubucin yana iya yiwuwa a ga bukatar gabatar da wanda ake rubuta wa wasiƙan.
"saboda nufin Allah" ko "domin Allah ya so haka." Bulus ya zama manzo domin haka Allah ya so ba domin zaɓen mutum ba.
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "domin manufar." Wannan na nufin cewa Allah ya zaɓi Bulus domin ya faɗa wa mutane game da alkawarin Allah na samun rai cikin Yesu, ko 2) "bisa dalilin." Wannan na nufin cewa kamar yadda Allah yayi alkawarin rai ta wurin Yesu, haka nan ya mayar da Bulus ya zama manzo.
Bulus na magana game da "rai" kamar wani abu ne da ake samu a cikin Yesu. Wannan na bayyana rai da mutane ke samu ta wurin zama na Almasihu Yesu"
"ɗa da nake so" ko "ɗan da nake ƙauna. Anan "ɗa" kalma ce na ƙauna mai muma girma da amincewa. Mai yiwuwa ta hannun Bulus ne Timoti ya karɓi Almasihu, shiyasa Bulus ya dauke shi a matsayin ɗansa. AT: "wanda ya ke a matsayin ƙaunataccen ɗa na"
"Bari alheri, jinkai, da salama sukasance a gare" ko "Bari ku kasance da alheri, jinkai, da salama a cikin ku daga"
"Allah, wanda shine Ubanmu, da." Wannan muhimmin suna ne na Allah.
"Almasihu Yesu, wanda shine Ubangijimu"
"wanda na bautawa kamar yadda kakannina suka yi"
Bulus na magana game da lamirisa kamar wani abu ne da ake iya wanke wa. Wannan na nufin cewa lamirin mutum da ke so ya aikata abun da ke daidai ba zai kasheshi ba. AT: "sannin cewa na yi iyakan ƙoƙarina in yi abin da ke daidai" ̇
"duk lokacin da nake tune da kai" ko "yayin da a kowane lokaci ina tune da kai"
A nan an yi amfani da "dare da rana" ana nufin " ko da yaushe." AT: "ko da yaushe" ko "kullum"
"Ina son ganin ka sosai"
Bulus na magana game da kanshi kamar shi bokati ne da wani ke iya cika wa. AT: "in cika da murna" ko "in iya samun cikakkiyar farin ciki"
A nan "hawaye" na nufin kuka. AT: "Ina tune da yadda ka yi kuka domina"
AT: "Na tuna da" ko "Na yi tunani game"
"bangaskiyar ka na gaske" ko "bangaskiyarka na gari"
Bulus na magana game da bangaskiyarsu kamar wani abu ne da ke a raye kuma na zaune cikinsu. Bulus na nufin suna da bangaskiya ɗaya. AT: "bangaskiya. Loyis kakarka da Afiniki mahaifiyar ka suna da sahihiyar bangaskiya tun farko, haka kuma na tabata cewa kaima kana da sahihiyar bangaskiya"
Waɗanan sunayen mata ne.
Bulus na karfafa Timoti yayi rayuwa cikin iko, ƙauna, horaswa da kuma ba na kunya ba, domin Bulus na shan wahala a cikin kurkuku sabili da bangaskiyarsa a cikin Almasihu.
"domin wannan dalilin" ko "domin sahihiyar bangaskiyarka a cikin Yesu"
Bulus na magana cewa yakamata Timoti ya fara amfani da baiwarsa kamar yana so ya sake kunna wuta. AT: "ya fara amfani da baiwarsa"
"baiwar Allah da ka samu lokacin da na dibiya maka hannuwana." Wannan na nufin bukin da aka yi inda Bulus ya sanya hannuwa wa Timoti da kuma addu'a ga Allah domin ya bashi ikon aikata abin da ya umurce shi ya yi.
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "ruhu" na nufin "Ruhu mai Tsarki." AT: "Ruhun Allah Mai Tsarki ba ya sa mu kasancewa da tsoro. Ya kan sa mu samu iko da ƙauna da kuma horaswa" 2) "ruhu" na nufin yanayin ɗabi'u. AT: "Allah baya sa mu kasancewa da tsoro amma mu samu iko da ƙauna da kuma horaswa"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) ikon mu iya kama kanmu, 2) ikon gyara wasu mutane wanda suke aikata laifi.
"na shaidawa" ko "na faɗa wa wasu"
"ɗaurarre saboda shi" ko "ɗaurarre domin ina shaida game da Ubangiji"
Bulus na magana game da wahala kamar wani abu ne da ake iya raba wa a tsakanin mutane. AT: "shan wahala tare da ni domin bishara"
"bishara, yanda Allah ya ba ka ƙarfi"
"da kira da ya kebe mu mun zama mutanensa" ko "kasance tsarkakan mutanensa"
"Ya cece mu ya kuma kira mu"
"ba domin mun yi wani abu da ya cancance shi ba"
"amma domin ya shirya ya nuna mana alherinsa"
"ta dalilin dangantakarmu da Almasihu Yesu"
"kafin farkon duniya" ko "kafin zamanai"
Bulus na magana game da ceto kamar wani abu ne wanda za a iya nuna wa mutane. AT: " Allah ya nuna yadda zai cecemu ta wurin aiko da mai cetonmu Almasihu Yesu"
Bulus na magana game da mutuwa kamar wani abu ne da ke zaman kanta ba mutuwa da mutane kan yi ba. AT: "wanda ya halakar da mutuwa" ko " wanda ya sa mutane ba za su zama mattatu na har abada ba"
Bulus na magana game da rai madawami kamar wani abu ne da a ka kawo daga duhu zuwa haske domin mutane su iya gani. AT: "koyar game da rayuwa mara ƙarewa ta wurin shelar bishara"
AT: "Allah ya zaɓe ni in zama mai bishara"
"Domin ni manzo ne"
Bulus na nufin kasancewa a kurkuku.
"Na kawar da shakka"
Bulus na amfani da wannan hoto da ke nuna mutum da aka ba ajiyan wani abu da ya kamata ya kare har lokacin da zai mayar. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) Bulus na dogara da Yesu ya taimakeshi ya kasance da aminci, ko 2)Bulus na sa rai cewa Yesu zai tabbatar mutane sun cigaba da shelar sakon bishara .
Wannan na nufin ranar da Allah zai hukunta dukan mutane.
"cigaba da koyar da kyawawan koyarwa da na koyar da kai" ko "Yi amfani da yadda na saba koyar da kai domin abun da ya kamata ka koyar"
"kamar yadda ka amince da Yesu Almasihu ka kuma ƙaunaceshi"
Wannan na nufin aikin shelar bishara yadda ya kamata.
yakamata Timoti ya yi takatsantsan domin mutane zasu yi hamayya da aikinsa, da kokarin tsayar da shi, da kuma karkatar da maganar sa.
"tare da ikon Ruhu Mai Tsarki"
Wannan na nufin sun daina taimakawa Bulus. Suka ƙyale Bulus domin hukumomin sun jefar da shi cikin kurkuku. AT:"tsayad da taimakamun"
Wannan sunayen mazaje ne.
"ga iyali"
A nan "sarƙa" kalma ce da ke nufin kasancewa a kurkuku. Shi Onisifaras ba ya kunyar cewa Bulus na ɗaure a kurkuku amma ya kan ziyarce shi akai-akai. AT: "ba ya kunyar cewa ina kurkuku"
"Bari Onisifaras ya sami jinkai daga Ubangiji" ko "Bari Ubangiji ya nuna masa jinkai"
Bulus na magana game da jinkai kamar wani abu da ake iya samu.
Wannan na nufin ranar da Allah zai shar'anta dukan mutane.
1Domin wannan kai, dana, ka karfafa cikin alherin da ke cikin Almasihu Yesu. 2Abubuwan da ka ji daga gare ni a bainar jama'a masu yawa, ka danka su ga mutane masu aminci da za su iya koya wa wadansu kuma.3Ka daure shan tsanani tare da ni, kamar amintaccen sojan Almasihu Yesu. 4Ba bu sojan da zai yi bauta yayin da ya nannade kansa da al'amuran wannan rayuwar, domin ya gamshi shugabansa. 5Hakanan, idan wani yana gasa a matsayin dan wasa, ba zai sami rawani ba tukuna har sai in ya karasa tseren bisa ga ka'idodin gasar.6Wajibi ne manomi mai kwazon aiki ya fara karbar amfanin gonarsa. 7Ka yi tunani game da abin da na ke gaya maka, gama Ubangiji zai ba ka ganewa a cikin komai.8Ka tuna da Yesu Almasihu, daga zuriyar Dauda, wanda a ka tayar daga matattu. Bisa ga wa'azin bisharata, 9wanda na ke shan wahala har ya kai ga dauri kamar mai laifi. Amma maganar Allah ba a daure ta ba. 10Saboda haka na jure wa dukkan abubuwa domin wadanda aka zaba, saboda su ma su sami ceton da ke cikin Almasihu Yesu, da daukaka madawwamiya.11Wannan magana tabbatacciya ce: "Idan mun mutu tare da shi, za mu kuma rayu tare da shi. 12Idan mun jure, zamu kuma yi mulki tare da shi. Idan mun yi musun sa, shi ma zai yi musun mu. 13Idan mun zama marasa aminci, shi mai aminci ne koyaushe, domin shi ba zai yiwu ya musunta kansa ba."14Ka yi ta tuna masu da wadannan abubuwan. Ka yi masu kashedi a gaban Allah kada su yi ta dauki ba dadi game da kalmomi. Saboda wannan bai da wani amfani. Domin wannan zai halakar da ma su sauraro. 15Ka yi iyakacin kokarika domin ka mika kanka ma'aikacin Allah wanda aka tabbatar, wanda babu dalilin kunya a gareshi. Wanda ya ke koyar da kalmar gaskiya daidai.16Ka guje wa masu maganar sabo, wanda ya kan kara kaiwa ga rashin bin Allah. 17Maganarsu za ta yadu kamar ciwon daji. Daga cikinsu akwai Himinayus da Filitus. 18Wadannan mutanen sun kauce wa gaskiya. Sun fadi cewa an rigaya an yi tashin matattu. Suka birkitar da bangaskiyar wadansu.19Duk da haka, ginshikin Allah ya tabbata. Ya na da wannan hatimi: "Ubangiji ya san wadanda ke nasa," Kuma "Duk mai kira bisa ga sunan Ubangiji dole ya rabu da rashin adalci." 20A gida mai wadata, ba kayayyaki na zinariya da azurfa ba ne kawai. Haka kuma akwai kayayyaki na itace da yunbu. Wadansu domin aikin mai daraja, wadansu kuma ga aiki mara daraja. 21Idan wani ya tsarkake kansa daga rashin daraja, shi kayan aiki ne mai daraja. An kebe shi, abin aiki domin mai gidan, kuma a shirye domin kowanne aiki mai kyau.22Ka guje wa sha'awoyi na kuruciya, ka nemi adalci, bangaskiya, kauna da salama da wadanda suke kira ga sunan Ubangiji daga zuciya mai tsabta. 23Amma ka ki tambayoyi na wauta da jahilci. Ka sani sukan haifar da gardandami.24Tilas bawan Ubangiji ya guje wa jayayya. A maimakon haka dole ya zama mai tawali'u ga kowa, mai iya koyarwa, kuma mai hakuri. 25Dole ne ya koyarwa mutane da su ke jayayya da shi a cikin tawali'u. Watakila Allah ya ba su ikon tuba domin sanin gaskiyar. 26Suna iya sake dawowa cikin hankalinsu kuma su bar tarkon Ibilis, bayan da ya cafke su domin nufinsa.
Bulus na kallon rayuwan bi na Timoti kamar rayuwar soja, manomi, da kuma ɗan wasan guje-guje da tsalle-tsalle ne.
A nan kalmar "ɗa" na nuna matuƙar ƙauna da amincewa. Ya yiwu kuma ta hannun Bulus ne Timoti ya fara bin Almasihu, shi ya sa Bulus na kallon shi a matsayin ɗansa. AT: "wanda ya ke kamar ɗa na"
Bulus na magana game da ƙarfafawa da dagewa da alherin Allah kan sa masubi su samu. AT: "Bari Allah ya yi amfani da alherin da ya ba ka ta wurin dangantakar ka da Almasihu Yesu ya ba ka ƙarfi"
"da shaidu masu yawa a wurin domin su yarda cewa abin da na faɗa gaskiyane"
Bulus ya yi magana game da umurnin da ya ba Timoti kamar wasu abubuwa ne da Timoti zai iya ba wasu da ya yarda da su akan cewa zasu riƙe yanda ya kamata. AT: "danƙa masu" ko "koyar da su"
Ma'anoni masu yiwuwa 1) "jimre shan wuya kamar yadda nake" ko 2) "tarayya cikin shan wahalata"
Bulus na kamanta wahala saboda Almasihu Yesu da wahalar da amintaccen soja ke jimrewa.
babu sojan da zai yi bauta yayin da ya ke sa hannusa a ayyukan rayuwa ta kowace rana" ko "A lokacin da sojoji ke bauta, basu damuwa da abubuwan da mutane suke yi." kada bayin Almasihu su yarda al'amuran rayuwa na yau da kullum su hana su yin aikin Almasihu.
Bulus na magana game da janye hankali kamar wani raga ne da ke kokorin kada mutane yayin da suke tafiya.
"mai jagoransa" ko "wanda ke ba shi umurni"
Bulus na magana a fakaice game da bayin Almasihu kamar su 'yan wasa ne.
AT: "za a ba shi rawani a matsayin mai nasara amma sai dai in ya yi tseren bisa ka'ida"
"ba zai sami kyautar nasara ba."A zamanin Bulus akan yi wa 'yan wasa da suka yi nasara rawani da wasu irin ganyayyaki"
"yin gasa bisa ka'idodin" ko "biyayya da ka'idodin"
Wannan karin magana na uku kenan da Bulus ke yi wa Timoti. Yakamata mai karatu ya fahimci cewa wajibi ne mabiyan Almasihu su yi aiki da ƙwazo.
Bulus na ba Timoti hoton magana, amma bai bayyana masa manufar maganar ba. Yana sa ran cewa Timoti zai fahimci abin da yake faɗa game da bayin Almasihu.
"game da kowani abu"
Wannan karin magana ce da ke nufin Yesu daga zuriyar Dauda ne. AT: "wanda ke ɗan zuriyar Dauda"
a "tada daga" karin magana ce da ke nufin a sa wanda ya mutu ya kasance da rai kuma. AT: "wanda Allah ya sa ya rayu kuma" ko "wanda Allah ya tada daga matattu"
Bulus na magana game da saƙon bishara kamar na shi ne musamman. Yana nufin cewa wannan shi ne saƙon bishara da yake shela. AT: "bisa ga saƙon bisharar da na ke wa'azi"
A nan "ɗauri da sarƙa" na nufin kasance a kurkuku. AT: "har ya kai ga ɗauri da sarƙa kamar wani mai laifi a kurkuku"
A nan "ɗauri" na magana game da abin da ke faruwa da ɗan kurkuku, kuma wannan ƙarin magana ce da ke nufin cewa ba wanda zai iya tsayar da saƙon Allah. Ana iya fasarar wannan cikin sifar aiki, AT: "ba wanda zai iya sa maganar Allah a kurkuku" ko "ba wanda zai iya hana maganar Allah"
AT: "na mutanen da Allah ya zaɓa"
Bulus na magana game da ceto kamar wani abu ne da ake iya karɓa fuska da fuska. AT: "za a samun ceto daga Almasihu Yesu"
"za su kuma kasance da shi har abada cikin ɗaukakar wurin zaman sa"
"Wannan maganar abin amincewa ce"
Wannan mai yiwuwa kalmar waƙa ce Bulus ya ɗauko. Idan harshenku na da yadda za a sa wannan kamar waƙa to ana iya yin haka. In ba haka ba, za ku iya fasarar yadda ya ke.
Bulus ya yi amfani da wannan maganar da nufin cewa mutane na tarayya da mutuwar Almasihu yayin da sun amince da shi, suna musun kansu, suna kuma yi masa biyayya.
"ko da mun kasa a gaban Allah" ko "ko da ba mu yi abin da mun gaskata Allah na so mu yi ba"
"yana rayuwa bisa ga halinsa ko da yaushe" ko "ba zai aikata abin da ba asalin halinsa ba"
Kalmar "su" na iya nufin "malamai" ko "mutanen ikilisiyar"
Bulus na magana game da yadda Allah ya san shi kamar ya kasance tare da Allah fuska da fuska. Wannan na nuna cewa Allah zai zama mashaidin Timoti. AT: a gaban Allah" ko "da Allah a matsayin mashaidinka"
Ma'anoni masu yiwuwa 1) " ban da gardama akan abubuwan wauta da mutane suke faɗi" ko 2) ban da jayayya game da ma'anar kalmomi"
"Wannan ba ta ba wa kowa riba"
"miƙa kanka ga Allah a matsayin tabbatancen mutum wanda ya cancanta kuma ba dalili ya kunyata"
Bulus na magana da Timoti game da yadda yakamata ya bayyana maganar Allah kamar shi wani gwanin ma'aikaci ne. AT: "kamar ma'aikaci" ko "kamar mai aiki"
Ma'anoni masu yiwuwa 1)"bayyana saƙon daidai game da gaskiya" ko 2) "bayyana gaskiyar saƙon yadda yakamata."
Bulus na magana game irin wannan magana kamar wani abu da za'a iya kaishi zuwa wani sabon wuri, kuma yayi magana game da rashin bin Allah kamar shine wannan sabon wurin. AT: "wanda ya ke sa mutane su ƙara kasance da rashin bin Allah"
ciwon daji na yaɗuwa a jikin mutun da wuri har ya halakar da shi. Wannan ƙarin magana ce da ke nufin cewa maganganun waɗannan mutane zasu cigaba da yaɗuwa daga mutum zuwa mutum har ya kawo lahani ga bangaskiyar waɗanda suka ji. AT: "
Wannan sunayen maza ne.
A nan "ƙauce wa gaskiya" ƙarin magana ne da ke nufin daina gaskatawa ko koyar da abun da ke gaskiya. AT: "wanda suka fara faɗin abubuwan da ba gaskiya ba"
"Allah ya riga ya tashi masubi da suka mutu zuwa ga rai madawwami"
"sabili da su ne waɗansu mutane suka daina ba dagaskiya"
Mai yiwuwa ana nufin 1) "gaskiyar Allah na kamar ƙaƙƙarfan harsashin gini ne" ko 2) "Allah ya kafa mutanen sa kamar ƙaƙƙarfan harsashin gini" ko 3) Amincin Allah na kamar ƙaƙƙarfan harsashin gini." Bulus na bayana wannan kamar wata harsashin gini ne da aka sa a ƙasa.
"wanda ke kira bisa sunan Ubangiji." A nan "sunan Ubangiji" na nufin Ubangiji da kansa. AT: "wanda ke kira ga Ubangiji" ko "wanda ya ce ya gaskata da Almasihu"
Bulus na magana game da rashin adalci kamar wani wuri ne da mutum ke iya bari. AT: "daina kasancewa mai mugunta" ko "daina aikata abun da ba daidai ba"
A nan "kayayyaki" na nufin tasa, faranti, da tukwane, wanda mutane ke sa abinci ko ruwa a ciki. Idan ba kalma daya da ake iya kiran dukan wadanan abubuwan a harshen ku, ku yi amfani da "tasa" ko "tukwane." Bulus na amfani da wannan a matsayin karin magana ne da ke bayyana irin mutane daban-daban.
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "lokaci na musamman ... na kullum" ko 2)irin ayuka da mutuna ke yi a cikin jama'a... irin ayuka da mutane ke yi ba a cikin jama'a ba."
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) " raba kansa da mutanen banza" ko 2) "ya tsarkake kansa." Bulus na magana game da wannan yanayi kamar yadda mutum ke wanke kansa.
Bulus na magana game da wannan mutum kamar shi wani kayan aiki ne mai daraja. AT: "yana kamar kayan aiki mai amfani a lokaci na musamman" ko "yana kamar kayan aiki mai amfani don aikin da mutanen kirki ke yi a gaban jama'a"
AT: "Maigidan ya keɓe shi, kuma yana shirye domin maigidan yayi amfani da shi domin kowani aiki mai kyau"
ba'a keɓe shi ta wurin canja masa wuri ba, amma domin yin wani aiki na musamman. Wasu fasara sun yi amfani da kalmar "tsarkake," amma ayar na bayyana keɓewa.
Bulus na magana game da sha'awoyin kuruciya kamar wani mugun mutum ne ko dabba da Timoti zai guje wa. AT: "kauce wa sha'awoyin kuruciya" ko "ka ƙi aikata abubuwa marasa kyau da matasa ke son aikatawa"
A nan "nemi" na nufin kishiyar "gujewa." Bulus na magana game da adalci kamar wani abu ne da Timoti zai iya gudu zuwa gare shi, domin zai yi masa kyau. AT: " Yi ƙoƙari ka samu adalci" ko "biɗi adalci"
Ma'anoni masi yiwuwa suna kamar haka1) Bulus na so Timoti ya haɗu da sauran masubi cikin neman adalci, bangaskiya, ƙauna da salama, ko 2) Bulus na so Timoti ya kasance cikin salama da sauran masubi, ba tare da jayayya ba.
A nan "kira ga Ubangiji" karin magana ne da ke nufin amincewa da yi wa Ubangiji sujada. AT: "waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada"
A nan "tsabta" na nufin abu mara datti ko abu sahili. "Zuciya" kuma a nan na nufin "tunani" ko "jin tausayi." AT: "sahihiyar hankali" ko " ba tare da munafunci ba"
"ƙi amsa tambayoyin wauta da jahilci." Bulus na nufin cewa wanda suke irin wannan tambayoyin wawaye ne da jahilai. AT: daina amsa tambayoyin da wawayen mutane waɗanda ba su son su san gaskiyar ke tambaya"
Bulus na magana game da tambayoyin jahilci kamar matan da suke haifan yara. AT: "sukan kawo gardandami"
"mai tawali'u" ko "mai hankali"
"koyar da waɗanda" ko "daidaita waɗanda"
Bulus na magana game da tuba kamar wani abu ne da Allah ke ba wa mutane a hannu. AT: " watakila Allah ya ba su damar tuba"
"domin su san gaskiyar"
Bulus na magana game da yadda masu zunubi za su samu tunani mai kyau game da Allah kamar mutane da sun bugu su na dawowa hankalinsa. AT: "Watakila za su yi tunani da kyau kuma"
Bulus na magama game da yadda ibilis ke iya shawo kan masubi zuwa zunubi kamar tarko ne. AT: "daina aikata abin da ibilis ke so"
Ana magana game da shawo kan masubi zuwa aikata zunubi kamar ibilis ya kama su ne kamar bayi. AT: "bayan ya yaudare su zuwa ga yin biyyaya da nufinsa"
1Amma ka san da wannan: a cikin kwanakin karshe za a yi lokuta masu matsananciyar wahala. 2Gama mutane za su zama masu son kansu, masu son kudi, masu Kumburi, da girman kai, masu sabo, marasa biyayya ga iyaye, marasa godiya, da kuma marasa tsarki. 3Za su kasance marasa dabi'a, wadanda basu son jituwa da kowa, masu tsegumi, marasa kamun kai, 'yan tawaye, marasa kaunar nagarta. 4Za su zama masu zagon kasa, taurin kai, masu takama, da masu kaunar anishuwa fiye da kaunar Allah.5Za su kasance da siffar ibada amma za su musunci ikonta. Ka juya daga wadannan mutanen. 6A cikinsu akwai wadanda suke shiga gidaje suna yaudarar mataye marasa hikima. Wadannan ne mataye wadanda suke cike da zunubi, kuma sun kauce hanya sabili da sha'awoyi dabam daban. 7Wadannan matayen suna ta koyo, amma ba za su taba kai wa ga sanin gaskiya ba.8Kamar yadda Yannisu da Yambrisu suka yi jayayya da Musa. Haka nan wadannan malaman karya kuma suke yin tsayayya da gaskiya. Mutane ne lalatattu a zuciya, marasa sahihiyar bangaskiya. 9Amma ba za su yi nisa ba. Domin wautarsu za ta bayyana a fili ga kowa, kamar wadannan mutane.10Amma kai, ka bi koyarwata, da dabi'ata, nufe nufena, da bangaskiyata, da jimriyata, da kaunata, da hakurina, 11da yawan kuncina, da wahalolina, da duk abubuwan da suka faru da ni a Antakiya, da Ikoniya da kuma Listra. Na jure a cikin kuncina. Amma a cikinsu dukka, Ubangiji ya cece ni. 12Duk wadanda su ke so su yi rayuwa ta ibada a cikin Almasihu Yesu za su sha tsanani. 13Miyagun mutane da masu hila za su yi ta kara lalacewa. Za su badda wasu. Su da kansu ma sun bijire.14Amma kai, ka ci gaba da abubuwan da ka koya kuma ka gaskata da zuciya daya. Ka san daga wurin wanda ka koya. 15Ka san da cewa, tun kana dan karamin yaro ka san wadannan littattafai masu tsarki. Wadannan suna iya mai da kai mai hikima domin ceto ta wurin bangaskiya a cikin Almasihu Yesu.16Dukkan Nassi hurarre ne daga Allah. Yana da amfani domin koyarwa, domin tsautawa, domin gyara, kuma domin horarwa cikin adalci. 17Wannan domin mutumin Allah ya zama cikakke ne, shiryayye domin dukkan ayyukan nagarta.
Bulus ya sa Timoti ya sani cewa nan gaba mutane za su daina amincewa da gaskiyar, amma shi Timoti ya cigaba da gaskatawa cikin kalmar Allah ko a lokacin da ake tsananta masa.
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamr haka 1) wannan lokaci ne bayan zamanin Bulus. AT: "nan gaba kafin dawowar Yesu" ko 2)wannan na nufin zamanin masubi, har da zamanin Bulus. AT: "a wannan zamanin kafin ƙarshen"
Ya yiwu wannan zai zama 'yan kwanaki ne, watani, ko ma shekaru ne da masubi zasu jure wahala da haɗari.
A nan "so" na nufin kaunar 'yan uwa ko abokai ko 'yan iyali, kauna ce ta abokai da dangi da mtane ke nuna wa. wannan ba kauna ce da ke zuwa daga Allah ba. AT: "son kai"
"ba su ƙaunar iyalinsu"
"basu son jituwa da kowa" ko "ba su zaman salama da kowa"
AT: "makiyan abu mai kyau
aikata abu da rashin kula ko tunanin me zai biyo baya, ko da sun san mumunar abu da zai iya faruwa
suna takamar cewa sun fi kowa
Bulus na magana game da ibada, da halin girmama Allah kamar wani abu ne mai sifa da iko wanda ake iya gani. AT: "za su kasance da siffar girmama Allah, amma hallayensu na nuna cewa basu gaskata ga iko Allah ba"
"ana ganin su da siffar ibada" ko "kasance kamar ana girmama Allah"
"Juya" a nan karin magana ne da ke nufin kauce wa wani mutum. AT: "kauce wa wannan mutane"
"shiga cikin gidaje su rinjayi"
"raunanan mataye a ruhaniya." Mataye na iya kasance wa raunana a ruhu domin basu kokarin bin Alla ko domin suna zaman banza suna kuma cike da zunubi.
Bulus na magana game da yadda zunubi ke jan hankali kamar an cika zunubin a kan wannan matayen. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "wanɗanda su ke zunubi a kai a kai" ko 2) wanɗanda basu jin daɗin yadda suke cigaba da aikata zunubi." Wannan na ba da ra'ayin cewa wannan mazajen na iya yaudarar matayen nan cikin sauki domin waɗannan matayen basu iya daina aikata zunubi ba.
Bulus na magana game da wannan sha'awoyin kamar suna iya janye mutum ya kauce. AT: "suna sha'awar aikata zunubi ta kowane hali fiye da biyayya ga Almasihu"
wannan sunayen maza ne.
Bulus na magana game da masu jayayya da wani kamar suna gãba ne. AT: "hămayyă"
"hămayyă da bisharar Yesu"
"tunaninsu ya lalace" ko "basu iya tunani mai kyau"
Aka gwada bangaskiyarsu ga biyayyya cikin Almasihu, amma sun gază. AT: "ba tare da sahihiyar bangaskiya ba" ko "sun nuna cewa bangaskiyarsu ba ta gaskiya bace"
Bulus na magana game da malaman ƙarya cewa ba za su yi nasara ba acikin masubi. AT: "ba za su yi nasara ba"
abun da mutane ke iya gani a fili
"na Yannisu da Yambrisu"
Bulus na magana game da maida hankali da waɗannan abubuwan kamar wani ne da ke bin su sa'ad da suna tafiya. AT: "ka lura da koyarwata" ko "ka ba da hankalinka ga koyarwata"
"abun da na koyar da kai ka yi"
"yadda mutum ke tafiyar da rayuwarsa"
yadda mutum na hakuri da waɗansu mutane waɗanda suke yin abubuwa da bai amince ba.
Bulus na magana game da yadda Allah ya cece shi daga wahala da waɗannan hatsarorin kamar Allah ya ɗauke shi daga wani wurin zama ne.
"yin rayuwa ta ibada a matsayin mabiyin Almasihu"
AT: "lailai ne ya jure tsanani"
mai hila mutum ne wanda yake so mutane suyi tunanin cewa shi wani muhimmin mutum ne fiye da yanda ya ke.
"kasance da ƙarin mugunta"
A nan, baɗda wasu, ƙarin magana ne na rinjayar wani zuwa ga amincewa da abun da ba gaskiya ba. AT: "yaudarar kansu da waɗansu" ko "amincewa da ƙarya da kuma koyar da ƙaryan"
Bulus na yi wa Timoti magana game da umarnin Littafi Mai Tsarki kamar wani wuri ne da zai zauna a ciki. AT: kar ka manta da abun da ka koya" ko "ci gaba da aikata abun da ka koya"
Bulus na magana game da Littattafai Masu Tsarki kamar su wani mutum ne wanda zai iya ba wa wani hikima. AT: "Idan ka karanta maganar Allah, za ka iya samun hikima domin cote daga Almasihu Yesu ta wurin bangaskiya"
wasu littattafai sun fasara wannan kamar haka " Dukan Nassi hurarre na Allah ne." Wannan na nufin Allah ne ya sarrafa Nassi ta wurin Ruhunsa ta hayar gaya wa mutane abun da zasu rubuta. AT: "Allah ya yi magana a cikin dukan Nassi ta Ruhunsa"
"Yana da amfani" ko "yana da muhimmanci"
"domin nuna kuskure
"domin magance kuskure"
"domin horar da mutane su kasance da adalci"
wannan na nufin kowane mai bin Allah, na miji ko ta mace. AT: "dukan masubi"
"kasance da shiri"
1Ina bada wannan umarni a gaban Allah da Yesu Almasihu, wanda zai yi wa rayayyu da matattu shari'a, kuma saboda bayyanuwarsa da mulkinsa: 2Ka yi wa'azin Kalma. Ka himmantu a kai ko da zarafi ko ba zarafi. Ka tsautar, ka kwabar, ka gargadar, da dukan hakuri da koyarwa.3Gama lokaci na zuwa wanda mutane ba za su jure wa koyarwar kirki ba. Maimakon haka, zasu tattara wa kansu malamai bisa ga sha'awowin zuciyarsu. Za su rika fada masu abin da kunnuwansu ke so. 4Za su juya kunnuwansu daga koyarwar gaskiya, za su koma wa tatsunniyoyi na banza. 5Amma kai, sai ka natsu a cikin dukan abubuwa. Ka jure wa wahala; ka yi aikin mai bishara, ka cika hidimarka.6Gama ana-tsiyaye ni. Lokacin yin kaurata yayi. 7Na yi tsere na gaskiya; na kuma kammala tseren; na rike bangaskiya. 8An adana mani rawani na adalci, wanda Ubangiji, alkali mai adalci, zai ba ni a ranan nan. Ba ni kadai ba, amma kuma ga dukkan wadanda suke kaunar zuwansa.9Ka yi iyakacin kokarinka ka zo wurina da sauri. 10Domin Dimas ya yashe ni. Ya kaunaci wannan duniyar, ya tafi Tassalonika, Kariskis ya tafi Galatiya, Titus kuma ya tafi Dalmatiya.11Luka ne kadai yake tare da ni. Ka nemo Markus ka zo tare da shi domin yana da amfani a gareni a cikin aikin. 12Na aiki Tikikus zuwa Afisus. 13Ka kawo mani mayafin da na bari a Taruwasa wurin Karbus, idan za ka zo ka taho da shi, duk da littatafan nan, musanman takardun nan.14Iskandari makerin dalma ya kulla mani makirci ba kadan ba. Ubangiji zai biya shi gwargwadon ayyukansa. 15Kai ma ka yi hankali da shi, domin yana tsayyaya da maganganunmu sosai. 16Da farkon kariyar kaina, babu wanda ya goyi bayana. Maimakon haka kowa ya guje ni. Bana so dai a lissafta wannan a kansu.17Amma Ubangiji ya kasance tare da ni, ya kuma karfafa ni, yadda ta wurina, shelar ta sami cika da kyau, domin dukan al'ummai su ji. An kwato ni daga bakin zaki. 18Allah zai kubutar ni daga dukan ayyukan mugunta, ya kuma cece ni domin mulkinsa na sama. Daukaka ta tabatta a gareshi har abada abadin. Amin.19Ka gayar da Briskilla, da Akila, da gidan Onisifurus. 20Arastus ya nan zaune a Korinti, amma na bar Turufimus ya na zazzabi a Militus. 21Ka yi iyakar kokarinka, ka zo kamin hunturu. Yubulus yana gayar da kai, haka ma Budis da Linus da Kalafidiya da dukan 'yan'uwa. 22Bari Ubangiji ya kasance tare da ruhunka. Bari Alheri ya kasance da kai.
Bulus ya cigaba da tunashe da Timoti ya kasance amintacce, da kuma cewa shi Bulus na shirye ya mutu.
ya yiwu cewa Allah da Almasihu Yesu ne shaidun Bulus. AT: "wannan muhimmin Umurni ne da ke a matsayin shaidu na ga Allah da Almasihu Yesu"
"umurni mai muhimmanci"
A nan "rayayyu" da "mattatu" na nufin dukan mutane. AT: "dukan mutane da suka taɓa rayuwa"
A nan "mulki" na a matsayin shugabancin Almasihu Sarki. AT: "matattu, a sa'ad da ya dawo ya yi mulki a matsayin Sarki"
"Kalma" a nan na nufin "saƙo." AT: "saƙo game da Almasihu"
an riga an gane kalmar "zarafi" anan. AT: "ko babu zarafi"
faɗa wa mutum cewa ya aikata abun da ba daidai ba
"gargadar, koyar da mutanen, da kuma haƙuri da su"
"Domin lokaci na zuwa nan gaba"
wannan aya na nuna cewa wannan mutanen za su zama daga al'umman masubi ne.
"ba za su so su saurari koyarwar kirki ba"
Wannan na nufin koyarwar gaskiyar, da ke daidai, bisa ga maganar Allah.
Bulus na magana game da tara malamai kamar an tara wani abu ne. AT: "za su saurari malamai da yawa wanda za su ba su tabbacin cewa babu wani laifi da sha'awowin zunubansu"
Bulus na magana game da yadda mutane ke marmarin jin wani abu kamar kunnuwarsu na ƙaiƙayi kuma sai malamai sun faɗa masu abin da suke so su ji. AT: "wanda suke faɗan iyakan abun da suke son ji sosai"
Bulus na magana game da yadda mutane ba su mayar da hankali kamar yadda ake juya baya domin kar a ji abu. AT: "Ba za su ƙara mayar da hankali da gaskiya ba"
Bulus na magana game da yadda mutane suka fara mayar da hankalinsu ga tatsunniyoyin ƙarya kamar yadda ake juya wa domin a ji magana da kyau. AT: "za su fara mayar da hankali ga koyarwar ƙarya"
Bulus na so masu karatu su samu tunani na kwarai game da kowane abu, yana magana game da wannan abubuwan kamar yana so su zama a natse, ba a buge da giya ba. AT: "yi tunani da kyau"
Wannan na nufin cewa a faɗa wa mutane game da wanene Yesu, abun da ya yi domin su, da kuma yadda za su yi rayuwa domin shi.
Bulus na magana game da shirin mutuwarsa kamar shi kofin ruwan inabi ne wanda ake shirye a zuba kamar hadaya zuwa Allah.
"ƙaura" a nan wata hanyar magana ce da ke nufin mutuwa. AT: "bada jimawa ba zan mutu in bar wannan duniya"
Bulus na maganar jure wahalolisa kamar shi dan wasan tsere ne domin lada. AT: "Na yi iyakan ƙoƙarina"
Bulus na maganar rayuwarsa na hidimar Allah kamar ya dinga wasan guje-guje ne. AT: "Na kammala abunda yakamata in yi"
Bulus na maganar amincewarsa da Almasihu da biyayya ga Allah kamar wani muhimmin dukiya mai daraje ne da yake riƙe da shi. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "Na dinga yin aikina da imani" ko 2)"Na riƙe koyarwar abun da muka gaskata ba kuskure"
AT: "Allah ya keɓe rawanin adalci domina"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) rawanin shi ne ladar da Allah ke bayar wa mutanen da suka yi rayuwa mai kyau, ko 2) rawanin karin magana ne na adalci. Kamar yadda alkalin wasa ke ba da lada ga wanda ya yi nasara, haka ma idan Bulus ya kammala rayuwarsa, Allah zai bayyana shi adali.
wani irin kambi ne da ake yi da ganye domin a bayar ga wanda ya yi nasara a tsere.
"a ranar da Ubangiji ya sake dawowa" ko "a ranar da Allah zai shar'anta mutane"
Bulus na maganar wannan aukuwar kamar ya riga ya faru. Ana iya faɗin wannan kamar abun da zai faru nan gaba. AT: amma kuma zai bayar ga duk waɗanda suke jiran dawowarsa"
"zo ... bada jimawa ba"
Wannan sunayen maza ne.
A nan "duniya" na nufi kayan duniyar da ke kalubalantar abubuwan Allah. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar hake 1) yana ƙauna da gamsuwar wannan duniya da ke na ɗan ƙanƙanin lokaci, ko 2) yana tsoro zai iya mutuwa idan ya kasance tare da Bulus.
waɗannan mutane biyun sun bar Bulus, amma ba wai Bulus na faɗin cewa su ma suna "ƙaunar wannan duniyan" kamar Dimas ba.
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "yana da taimako cikin hidimar Ubangiji" ko 2) "zai iya taimakona ta wurin yi mani hidima."
wani riga mai nauyi da ake sanya wa bayan a sa taguwa
wannan sunan na miji ne.
wannan wani irin lattafi ne da ake yi da fata. Bayan an yi rubuta ko karanta littafin, akan naɗe shi da sanduna da ke ƙarshen littafin
Wannan na iya nufin wani irin littafi na musamman. AT: "musamman wanda aka yi da fatan dabba"
"Iskandari, wanda yake aiki da dalma, ya nuna"
Wannan sunan na miji ne.
Bulus na maganar aikata mugunta kamar sau abubuwa ne da ake nunawa. AT: "ya yi mani mugunta sosai"
Bulus na maganar hukunci kamar biyan kuɗi ne. AT: "Ubangiji zai hukunta shi domin abun da ya aikata mani"
wanɗanan na nufin Iskandari.
A nan "maganganu" na nufin saƙo ko koyarwa. AT: "tsayyaya da saƙon da muke koyarwa"
"A farkon kasancewa na a kotu na bayyana ayyukana"
"babu kowa da ya tsaya da ni ya taimake ni"
AT: "Bana so Allah ya lissafta a kansu" ko "Ina addu'a kada Allah ya hukunta waɗanan masubi domin sun rabu da ni"
Bulus na magana kamar Ubangiji na tare da shi fuska da fuska. AT: "Ubangiji ya taimake ni"
AT: "Domin in iya faɗin dukan saƙon Ubangiji"
Bulus na maganar abu mai hatsari kamar yana hatsarin zaki. Wannan hatsarin na iya zama ta ruhaniya, ko ta jik, ko duka. AT: "An kuɓutar da ni daga baban hatsari"
A nan "gida" na nufin mutanen da suke wurin. AT: "Iyalin Onisifurus"
Wannan sunan namiji ne. dubi yadda aka fasara wannan cikin 2 Timoti 1:16.
Wannan sunayen maza ne.
Wannan sunan wani gari ne kudu daga Afisa.
"ka nemi hanyar zuwa"
"kafin lokacin sanyi"
Ana iya fasara wannan a wani sabuwar jumla. AT: "gai da kai. Budis, Linus, Kalafidiya da dukan 'yan'uwan suma suna gaishe ka"
Wannan sunan mace ce.
A nan " 'yan'uwa" na nufin duk masubi maza da mata. AT: "dukan masubi a nan"
"Ina addu'a cewa Ubangiji ya karfafa ruhunka." A nan "ka" na nufin Timoti ne.
"Ina addu'a Ubangiji ya nuna alherinsa a gareku duka." A nan "ku" na nufin dukan masubi da suke tare da Timoti.
1Bulus, bawan Allah, kuma manzon Yesu Almasihu, ta wurin bangaskiyar zababbun mutanen Allah da sanin gaskiya da ta yadda da allahntaka. 2Wadannan na cikin begen rai marar matuka wanda Allah, wanda babu karya a cikinsa, ya alkawarta kafin dukkan lokatan zamanai. 3A daidai lokaci, ya bayyana maganarsa ta wurin sakonsa da ya damka mani in shelar. Zan yi wannan ta wurin umarnin Allah mai ceton mu.4Zuwa ga Titus, da' na gaske a cikin bangaskiyarmu. Alheri, jinkai da salama daga wurin Allah Uba da Almasihu Yesu mai ceton mu. 5Sabili da wannan ne na bar ka a Karita domin ka daidaita abubuwan da basu cika ba, ka kuma nada dattibai a dukan birane kamar yadda na umarceka.6Dole ne dattijo ya zama marar abin zargi, mijin mace daya, da amintattun 'ya'ya wadanda babu wani zargi na mugunta ko rashin kamun kai a kansu. 7Wajibi ne shugaban Ikklisiya, a matsayin sa na mai kulla da haikalin Allah, ya zama marar aibi. Kada ya zama mai surutu ko rashin hakuri. Kada ya zama mai saurin fushi, ko mashayi, ko mai hayaniya, ko mai handama.8Maimakon haka, ya zama mai karbar baki, abokin abinda ke mai kyau. Dole ne ya zama mai hankali, adali, cike da allahntaka, da kuma kamun kai. 9Ya zama mai rike amintaccen sakon da aka koyar da karfi, yadda zai iya karfafa wasu da koyarwa mai kyau ya kuma yi wa wadanda suke hamayya da shi gyara.10Domin akwai kangararrun mutane dayawa, musamman masu kaciya. Maganganunsu na banza ne. Suna yaudara kuma suna badda mutane. 11Wajibi ne mu hana su. Suna koyar da abinda bai kamata su koyar ba saboda makunyaciyar riba suna kuma rusar da iyalai dungum.12Daya daga cikinsu, kuma mai hikima ne daga cikinsu, yace, "Kirawa manyan makaryata ne, lalatattu kuma miyagun dabbobi, masu kyiuya da zarin cin abinci." 13Wannan magana gaskiya ne, ka yi masu gyara da tsanani yadda zasu kafu a cikin bangaskiya.14Kada ka mai da hankalin ka ga tatsunniyoyi na Yahudawa ko dokokin mutane wadanda sun sauya gaskiya.15Ga wadanda suke da tsarki, komai mai tsarki ne. Amma wadanda suke marasa tsarki da rashin bangaskiya, komai marar tsarki ne. Domin zuciyarsu da lamirinsu sun gurbata. 16Suna cewa sun san Allah, amma sun musanta shi ta wurin ayyukansu. Sun zama abin kyama da marasa biyayya. Ba za a iya tabbaatar dasu ba akan wani aiki maikyau.
a ƙarfafa bangaskiyar
"ta yi daidai don girmama Allah"
"kafin loƙaci ta fara"
"A loƙacin da ya kamata"
Bulus ya yi magana game da maganar Allah kamar wani abu ne da za a iya nuna wa mutane su gani. AT: "Ya sa ni in fahimci saƙonsa"
"ya danƙa mani in kawo" ko "ya ba ni hakin yin wa'azi"
"Allah, wanda ya cece mu"
Kodashike Titus ba ɗan cikin Bulus ba ne, bangakiyarsu ɗaya ne cikin Almasihu. Cikin Almasihu kuwa, Bulus ya dubi Titus a matsayin ɗansa. AT: "kana kamar ɗa a gare ni"
Bulus ya bayyana ɗayantakar bangaskiya cikin Almasihu wanda dukansu ke da shi. AT: "koyarwar da duka mun gaskanta"
Wannan gaisuwa ce wanda Bulus ya saba amfani da ita. Za ka iya bayyana yanda za a fahimta a fili. AT: "Bari ka sami abin lirki da salama a cikin ka"
"Almasihu Yesu wanda shine mai cetonmu"
"Wannan ita ce dalilin"
"Na ce maka ka tsaya a Karita"
"don ka gama shirya abubuwan da ya kamata a yi"
"naɗa dattibai" ko "sanya dattibai"
Cikin Ikkilisiyoyin Masu bi na farko, dattiban masu bi na yin shugabanci ta ruhaniya ga taron masu bi.
Bayan ya gaya wa Titus ya keɓe dattibai a kowace birnin da ke tsibirin Karita, Bulus ya ba da halayen da ake buƙata ga dattibai.
Zama "mara abin zargi" ita ce a san mutum a matsayin wanda ba ya yin munanan abubuwa. AT: "Dole dattijo ya zama wanda ba shi da mummunan suna"
Wannan na nufin cewa yana da mata ɗaya, wato, ba shi da waɗansu mataye balle ƙwaraƙwarai. Zai iya zama cewa baya zina kuma bai saki matar sa ba. AT: "na miji mai mace daya" ko "na miji da ke amminci ga matar sa"
Mai yiwuwa wannan na nufin haka 1) 'ya'ya waɗanda sun gaskata da Yesu ko 2) amintattun 'ya'ya.
ba su da kamun kai, ba su iya kamun kan su ba
Wannan wata suna ce ɗaya da matsayin shugabancin ruhaniya da Bulus ke nufin "dattijo" a 1:6.
Bulus ya yi maganar ikkilisiya kamar iyalin Allah ne, kuma mai kula kamar shi wani bawa ne da ke sarrafa iyalin.
"ba bugagge ba" ko "ba wanda yake shan barasa da yawa ba"
"ba wanda ke sa tashin hankali ba" ko "ba mai son faɗa ba"
Bulus na canzan maganarsa daga abin da bai kamata dattijo ya zama ba zuwa abin da ya kamata dattijo ya zama.
"mutum wanda ke ƙaunar abin da ke da kyau"
Bulus ya yi magana game da duƙufa a cikin bangaskiyar masu bi kamar kãmun bangaskiya da hannu ne. AT: "duƙufa ga" ko "sani da kyau"
Dole ne ya koyar da abin da ke gaskiya game da Allah da kuma wasu al'amuran ruhaniya.
Waɗannan kangararrun mutanen ne da ba su goyi bayan sakon bisharar Bulus ba.
Wannan magana na bayyana kangararrun mutanen da aka ambata a baya. Anan "fanko" na nufin banza, kuma "masu fankon maganganu" su ne mutanen da ke maganganu banza da wofi. AT: "mutane waɗanda ke yin banzan maganganu su kuma yaudari waɗansu"
Wannan na nufin Yahudawan masubi waɗanda ke koyar da cewa dole ne mutane su yi kaciya don su bi Almasihu.
"Dole ne a hana su yaɗa koyarwar su" ko "Dole ne a hana ɓata wasu ta wurin kalmomin su"
Waɗannan abubuwa ne da ba daidai ne a koyar game da Almasihu ba da kuma shari'ar, domin, ba gaskiya ba ne.
Wannan na nufin riba da mutane ke samu ta wurin aikata abubuwan da ba na halal ba.
"suna ɓata iyalai ɗungum." Ainihin zancen ita ce su na rusar da iyalan ta wurin rushe bangaskiyarsu. Mai yiwuwa wannan ya sa 'yan iyalin yin musu da juna.
"Annabi daga Karita" ko "dan Karita wanda su kan su suna ɗauka a matsayin annabi"
"Karitawa suna ƙarya a kowace lokaci." Wannan zuguiguitawa ne da ke nufin cewa yawancin Karitawa suna ƙarya sosai.
Wannan na kwatanta Karitawa da mugun naman daji.
"Lallai ne ka yi amfani da harshen da Karitawa za su fahimta sa'anda ka ke yi musu gyara"
"don su sami bangaskiya mai lafiya" ko "don bangaskiyar su ta zama gaskiya"
Wannan na nufin koyarwar karya na Yahudawa.
Bulus ya yi magana game da gaskiyar kamar wani abu ne da wani ke iya juya mata baya ko kuwa kauce mata. AT: "ƙi gaskiyar"
"In mutane suna da tsarki a cikinsu, kowane abin da suka yi zai zama da tsarki"
"Ga waɗanda ke karɓaɓɓu a wurin Allah"
Bulus ya yi magana game da masu zunubi sai ka ce suna da datti a jikinsu. AT: "In mutane na da ƙazantatciyar hali kuma ba su gaskata ba, ba za su iya yin wani abu mai tsarki ba"
"Yanda suke rayuwa ya nuna cewa ba su san shi ba"
"Su abin ƙyama ne"
1Amma kai, ka fadi abinda yayi daidai da amintaccen umarni. 2Dole tsofaffin mazaje su zama masu kamun kai, masu daraja kansu, masu-hankali, masu aminci cikin bangaskiya, cikin kauna da jurewa.3Haka ma tsofaffin mataye su kame kansu da girma, ba magulmata ba. Kada su zama bayi wajen yawan shan ruwan inabi. Su koyar da abubuwa masu kyau 4domin su koyar da kananan mataye da hikima su kaunaci mazajensu da 'ya'yansu. 5Su horar dasu su zama masu hikima da tsabtar zuci, masu tsaron gidajensu, kuma masu biyayya da mazajensu. Suyi wadannan abubuwa saboda kada maganar Allah ta sami zargi.6Ta haka kuma, ka karfafa samari, su zama masu hankali. 7A kowanne fanni, ka mayar da kan ka abin koyi a cikin kyawawan ayyuka; idan kayi koyarwa, ka nuna mutunci da martaba. 8Ka bada sako lafiyayye marar abin zargi, yadda masu hamayya da maganar Allah zasu ji kunya, domin rashin samun mugun abin fadi akan mu.9Bayi suyi biyayya ga iyayengijin su a cikin komai. Su faranta masu rai, ba suyi gardama dasu ba. 10Kada suyi sata. Maimakon haka, sai su nuna dukan bangaskiya mai kyau, domin suyi wa koyarwarmu game da Allah mai cetonmu kwalliya a cikin dukan komai.11Domin alherin Allah ya bayyana ga dukan mutane. 12Yana koya mana mu musanci miyagun ayyuka, da sha'awoyin duniya. Yana horar damu muyi zama cikin hankali, da adalci a cikin hanyar allahntaka a wannan zamani 13yayin da muke cigaba da jiran karba albarkataccen begenmu, wato bayyanuwar daukakar Ubangiji Allah da kuma mai cetonmu Yesu Almasihu.14Yesu ya bada kansa domin mu, domin ya cece mu daga rashin kiyaye doka ya mai damu masu tsarki, domin sa, mutane na musamman wadanda suke da marmarin aikata kyawawan ayyuka.15Ka yi magana da karfi ka karfafawa wadannan abubuwa. Ka yi gyara da dukan iko. Kada ka bar wani ya raina ka.
Bulus ya ci gaba da ba wa Titus dalilan yin wa'azin maganar Allah, ya kuma bayyana yanda tsofaffin mazaje, da tsofaffin mataye, samari, da bayi ko kuwa barori za su yi rayuwa kamar masu bi.
Bulus na nufin abin da ke da bambanci. AT: "Amma kai, Titus, cikin saɓani da masu koyarwar ƙaryar, ka tabbata ka faɗi abubuwan da ke daidai"
"da sahihiyar koyarwa" ko "da koyarwar da ke daidai"
"zama natsattsu" ko "zama masu kamun kai"
" ... sarrafa sha'awarsu"
A nan kalman nan "sahihiya" na nufin zama da ƙarfi kuma babu shakka. Ana iya bayyana "bangaskiya" "ƙauna," da kuma "jimiri" cikin aikatau. AT: "kuma dole ne su gaskata koyarwar gaskiya game da Allah da ƙarfi, su ƙaunaci wasu da gaske, su kuma ci gaba the bautar Allah ko a lokacin da abubuwa sun yi wuya"
"haka kuma, ka koyar da tsofaffin mataye" ko "ka kuma koyar da tsofaffin mataye"
Wannan kalma na nufin mutane masu faɗin abubuwa marasa kyau game da wasu mutane ko gakiya ne ko ba gakiya ba.
Ana magana game da mutumin da bai iya sarrafa kansa ba, na kuma shan barasa sosai sai kace mutumin bawa ne ga barasa. AT: "kuma kada a sha barasa sosai" ko " ba kuma shagala ga barasa"
"magana" a nan na nufin "saƙo" wanda ya na kuma nufin Allah da kansa. AT: "don kada wani ya zargi maganar Allah" ko "don kada wani ya zargi Allah ta wurin faɗin munanan abubuwa game da saƙonsa"
ya kamata Titus ya karfafa samarin kamar yanda ya kamata ya karfafa tsofaffin mutane.
"nuna kanka ka zama"
"gurbi wanda ke yin abin da ke daidai da kuma abubuwan da sun dace"
Wannan na nuna hoton yanayin da wani ya yi hamayya da Titus sai kuma ya kai ga kunya don ya yi haka. AT: "domin in wani ya yi hamayya da kai, zai iya jin kunya" ko "domin in mutane sun yi hamayya da kai, za su iya jin kunya"
"nasu iyayengijin"
"cikin kowane yanayi" ko "koyaushe"
"sa iyayengijinsu farin ciki" ko "gamsar da iyayengijinsu"
"nuna cewa sun cancanci iyayengijinsu su dogara a gare su"
"cikin kowanne abin da suke yi"
"su iya sa koyarwa game da Allah Mai Cetonmu ta jawo hankali" ko "su sa mutane su fahimci cewa koyarwa game da Allah Mai Cetonmu na da kyau"
"Allahn mu wanda ya cece mu"
Bulus ya yi maganar alherin Allah sai ka ce mutum ne wanda ke zuwa wurin mutane ya kuma koya masu zaman tsarki.
"koya mana kada mu yi rashin biyayya ga Allah"
"sha'awace-sha'awace masu ƙarfi don abubuwan wannan duniya" ko "sha'awace-sha'awace masu ƙarfi don jin daɗin zunubi"
"a yayinda muna rayuwa cikin wannan duniya" ko "a wannan lokacin"
"muna jira don mu marabci"
A nan "ɗaukaka" na nufin Yesu da kansa wanda zai bayyana cikin ɗaukaka. AT: "abu mai kyau da mu ke begen shi, wato, ɗaukakar bayyanuwar Allahnmu da Mai Cetonmu Yesu Almasihu"
Wannan na nufin Yesu ya mutu da son ransa. AT: "ya bada kansa don ya mutu donmin mu"
Bulus ya yi maganar Yesu kamar yana kuɓutar da bayi daga mugun ubangijinsu.
rukunan mutane da ke daraja a wurinsa.
"su na da marmari sosai"
Wannan magana ana iya sa ta a bayyane. AT: "da dukan iko ka yi wa waɗannan mutanen da basu aikata waɗannan abubuwan, gyara"
"Kada ka bar wani"
Wannan maganar ana iya sa ta a bayyane. AT: "ƙin jin maganar ka" ko "ƙin ba ka girma"
1Ka tuna masu su zama masu sadaukar da kai ga masu mulki da masu iko, suyi masu biyayya, su zama a shirye domin kowane kyakkyawan aiki. 2Ka tuna masu kada su zagi kowa, su gujiwa gardama, su bar mutane su bi hanyarsu, su kuma nuna tawali'u ga dukan mutane.3Domin a da, mu da kan mu marasa tunani ne kuma masu rashin biyayya. Mun kauce hanya muka zama bayi ga sha'awoyin duniya da annashuwa. Mun yi zama a cikin mugunta da kishi. Mu lalatattu ne kuma muna kiyyaya da junanmu.4Amma da jinkan Allah mai ceton mu da kaunarsa ga 'yan Adam ta bayyana, 5ba saboda wani aikin adalci da muka yi ba, amma sabili da jinkan sa ne ya cece mu. Ya cece mu ta wurin wankewar sabuwar haihuwa da sabuntuwar Ruhu Mai Tsarki.6Allah ya zubo mana Ruhu Mai Tsarki a wadace ta wurin Yesu Almasihu mai cetonmu. 7Ya yi wannan saboda, bayan mun samu 'yantarwa ta wurin alherinsa, za mu zama magada a cikin begen rai na har abada.8Wannan amintaccen sako ne. Ina son kayi magana gabagadi game da wadannan abubuwa, yadda dukan wadanda suka bada gaskiya ga Allah za suyi kudirin yin kyawawan ayyuka da Allah ya mika masu. Waddannan abubuwa masu kyau ne da kuma riba ga dukan mutane.9Amma ka guji gardandami na wofi, da lissafin asali, da husuma da jayayya game da dokoki. Wadannan abubuwa basu da amfani kuma marasa riba. 10Ka ki duk wani dake kawo tsattsaguwa a tsakaninku, bayan ka tsauta masa sau daya ko biyu, 11ka kuma sani cewa wannan mutumin ya kauce daga hanyar gaskiya, yana zunubi kuma ya kayar da kansa.12Sa'adda na aiki Artimas da Tikikus zuwa wurin ka, kayi hanzari ka same ni a Nikobolis, a can na yi shirin kasancewa a lokacin hunturu. 13Kayi hanzari ka aiko Zinas wanda shi gwani ne a harkar shari'a, da Afolos ta yadda ba zasu rasa komai ba.14Ya kamata Jama'armu su koyi yadda zasu yi ayyuka masu kyau da zasu biya bukatu na gaggawa yadda ba za suyi zaman banza ba.15Dukan wadanda suke tare da ni suna gaishe ka. Ka gai da masu kaunar mu a cikin bangaskiya. Alheri ya kasance tare da dukan ku.
Bulus ya cigaba da ba wa Titus umarni yanda zai koyar da dattibai da mutanen da ke ƙarƙashin kulawarsa a cikin Karita.
"Gayawa mutanenmu kuma abin nan da sun riga sun sani, su miƙa kai" ko "Ka cigaba da tunashe su su mika kai"
"yi kamar yanda masu mulki da masu ikon gwamnati sun faɗa ta wurin yi musu biyayya"
Waɗannan kalmomin biyu suna da ma'ana kusan iri ɗaya kuma an yi amfani da su tare don ya shafi duk waɗanda suna da iko a gwamnati.
"yi shirin yin kyakkyawan aiki a sa'anda kun sami zarafi"
"yi mugun magana game da"
"Domin mu kanmu ma a dã"
"a dã" ko " a wata lokaci" ko "a baya"
"ko mu ma" ko "mu kuma"
"dã wawaye ne" ko "dã marasa hikima"
Bulus ya yi maganar "sha'awoyin da annashuwa" kamar mutane ne wanɗanda za su iya kai wasu ga kaucewa ko kuma zama bayi. A nan "sa wani ya kauce" na nufin sa wani ya gaskata abin da ba gaskiya ba. A nan "bayi ga sha'awoyi iri iri da annashuwa" na nufin rashin iya kamun kai. AT: "mun ruɗi kanmu mun kuma aikata abin da ke daidai a gare mu"
"muguwar sha'awa" ko "sha'awace-sha'awace"
Anan "mugunta" da "ƙishi" kalmomi ne kusan iri ɗaya na zunubi. AT: "Mun cika yin mugayen abubuwa da kuma son abinda wasu na da shi"
"Mun sa wasu sun ƙi mu"
Bulus ya yi maganar alherin Allah da ƙaunar sa kamar su mutane ne da sun zo wurin mu.
"domin ya yi mana jinƙai"
Mai yiwuwa Bulus yana maganar yafewar Allah ga masu zunubi kamar yana wanke su ne a jiki. Ya kuma yi magana game da masu zunubi waɗanda sun yi na'am da Allah kamar an sãke haihuwarsu.
waɗanda suka rubuta Sabon Alkawari sun saba maganar Ruhu Mai Tsarki kamar ruwa-ruwa ne da Allah zai iya zuba wa dayawa. AT: "ba mu Ruhu Mai Tsarki a yalwace"
"sa'adda Yesu ya cece mu"
AT: "dashike Allah ya maishemu marasa zunubi"
An yi maganar mutane waɗanda Allah ya yi musu alkawarensa kamar za su gaji mallaka da dukiya daga wani daga cikin iyali.
Wannan na nufin Allah ya ba da Ruhu Mai Tsarki ga masu bi ta wurin Yesu cikin [Titus 3:7]
"ƙoƙarin yin kyawawan ayyuka"
"don haka ka guje" ko "Saboda haka, guji"
"gardama game da al'amura marasa amfani"
Wannan ita ce nazari a kan dangantakan dangin iyali.
gardama ko faɗa
"shari'ar Musa"
"Guje wa kowane mai"
"Bayan ka tsauta wa mutumin sau ɗaya ko biyu"
"mutum kamar wannan"
Bulus ya yi maganar wani wanda ya yi kuskure kamar ya bar hanyar da dã yake tafiya a kai.
"kawo shari'a a kansa"
"bayan da na aiki"
Waɗannan sunayen maza ne.
"zo da sauri"
"tsaya a loƙacin bazara"
"Kada kayi jinkirin aiko"
"ka kuma aiko Afolos"
Bulus na nufin masu bi a Karita.
"da ya taimake su su iya taimakon mutanen da ke bukatan abubuwa masu amfani nan da nan"
Bulus ya yi maganar kyawawan ayyukan mutane kamar bishiyoyi ne da ke bada 'ya'ya mai kyau. Wannan na nufin su ba da 'ya'ya ko kuwa su zama masu sarrafa 'ya'ya. AT: "bukatu, ta haka za su ba da 'ya'ya" ko "bukatu, ta haka kuma za su yi kyawawan ayuka"
Bulus ya ƙarasa wasiƙar sa zuwa ga Titus.
"Duk mutanen"
Ma'ana mai yiwuwa AT: 1) "masu bi waɗanda suke ƙaunar mu" ko 2) "masubi da ke ƙaunar mu domin bangaskiyar mu ɗaya ne."
Wannan gaisuwa ce da masubi sun saba yi. AT: "Bari Alherin Allah ta kasance a gare ku" ko "Ina roƙo cewa Allah ya yi muku dukkan Alheri"
1Bulus, daurarren Yesu Almasihu, da kuma dan'uwa Timotawus zuwa ga Filimon, kaunataccen abokinmu da kuma abokin aikin mu, 2da Afiya yar'uwanmu da Arkifus abokin aikin mu a filin daga, da kuma Ikilisiyar da take taruwa a gidan ka: 3Alheri da salama su kasance gare ka daga wurin Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Almasihu.4Kowane lokaci ina gode wa Allah. Ina ambaton ku cikin addu'oi na. 5Na ji labarin kauna da bangaskiya da ka ke da ita a cikin Ubangiji Yesu da dukkan yan'uwa masu bi. 6Ina addu'a zumuntar bangaskiyarka ta inganta ga kawo sanin kowane kyakkyawan abu dake cikin mu a cikin Almasihu. 7Na yi farinciki kwarai, na kuma ta'azantu saboda kaunarka, saboda zukatan masu bi sun kwanta ta wurin ka, dan'uwa.8Saboda haka, ko da ya ke ina da gabagadi a cikin Almasihu domin in ba ka umarni ka yi abinda ya kamata ka yi, 9duk da haka sabo da kauna, na fi so in roke ka- Ni, Bulus, dattijo, a yanzu kuma ga ni dan kurkuku domin Almasihu Yesu.10Ina rokon ka saboda da na Onisimus, wanda na zama uba a gare shi sa'adda nake cikin sarkokina. 11Domin a da kam, ba shi da amfani a wurin ka, amma yanzu yana da amfani a gare ka da kuma a gare ni. 12Na kuma aike shi wurinka, shi wanda ya ke a cikin zuciyata kwarai. 13Na so da na rike shi a wuri na, domin ya rika yi mini hidima a madadin ka, a lokacin da ni ke cikin sarkoki saboda bishara.14Amma ba na so in yi wani abu ba tare da sanin ka ba. Ba ni so nagarin aikinka ya zama na dole amma daga kyakkyawar nufi. 15Watakila dalilin da yasa ya rabu da kai na dan lokaci ke nan, domin ka karbe shi kuma har abada. 16Daga yanzu ba za ya zama bawa ba kuma, amma fiye da bawa, wato kaunataccen dan'uwa. Shi kaunatacce ne musamman a gare ni, har fiye da haka ma a gare ka, a cikin jiki da kuma cikin Ubangiji.17Idan ka maishe ni abokin hidima, ka karbe shi kamar yadda za ka karbe ni. 18Idan kuwa ya yi maka abinda ba daidai ba ko kuwa kana bin sa wani abu, ka dauka yana wurina. 19Ni, Bulus, na rubuta wannan da hannuna: zan biya ka. Ba kuwa cewa sai na gaya maka cewa ina bin ka bashin kanka ba. 20I, dan'uwa, ka yi mani alheri cikin Ubangiji; ka ba zuciyata hutu a cikin Almasihu.21Saboda Ina da tabbaci game da biyayyarka, na rubuta maka. Na san za ka yi fiye da abinda na roka. 22Harwayau, ka shirya mani masauki. Domin ina fata ta wurin adu'oinku, nan ba da dadewa ba za a maida ni wurin ku.23Efafaras, abokina cikin Almasihu Yesu a kurkuku yana gaishe ka, 24haka ma Markus da Aristarkus, da Dimas, da Luka abokan aikina. 25Bari Alherin Ubangiji Yesu Almasihu ya kasance da Ruhunka. Amin.
Sau uku Bulus ya nuna kansa a matsayin marubucin wannan wasiƙar. A fili yake cewa Timoti yana tare da Bulus lokacin rubuta wannan wasiƙar, kuma babu mamaki Timotawus ne ya rubuta wasiƙar lokacin da Bulus yake faɗin kalaman. Bulus ya miƙa gaisuwar sa ga wanɗanda ke ikilisiyar da ke taruwa a gidan Filimon.
Mai yiwuwa harshen ka na da wata hanyar ta da take gabatar da marubucin wasiƙa. AT: "Ni, Bulus, ɗan sarka saboda Almasihu Yesu, da kuma Timotawus, ɗan'uwan mu, na rubuta wannan wasiƙa zuwa ga Filimon"
"ɗan sarka saboda Almasihu Yesu." mutanen da suka yi tsayanya da wa'azin Bulus sun horas da shi ta wurin jefa shi a kurkuku.
A nan wannan na nufin abokin aiki mabiyin addinin kirista
wannan kalmar "mu" na nufin Bulus da wanda suke tare.
"wanda yake kamar mu, yake aikin shelar bishara"
A nan "'yar'uwa" na nufin ita daga zumuntar masubi ne. AT: "maibi ce abokiyar aikinmu Afiya" ko "Afiya yar'uwarmu ta ruhaniya ce"
Wannan sunar mutum ne da ke ikilisiya ɗaya da Filimon.
Bulus ya yi magana a nan game da Arkifus kamar su sojoji ne a filin daga. Yana nufin Arkifus mai kwazo ne kwarai, kamar yadda Bulus kansa mai kwazon shelar bishara ne. AT: "abokin aikin mu jarumin mayaƙi na ruhaniya" ko "jarumin mayaƙi wanda yayi faɗa na ruhaniya tare da mu"
"Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Almasihu shi ba ku alheri da salama." Wannan albarka ne.
A nan kalmarnan "mu" na nufin Bulus, da waɗanda suke tare, da masu karanta wasiƙar.
Wannan muhimmin sunan Allah ne.
"domin aikin ka tare da mu"
"ya kai ga sanin abin da ke mai kyau"
"saboda Almasihu"
"Zukata" a nan shine shauƙi ko can cikin mutum. Za a iya ambatarsa a fannoni daban-daban. AT: "ya kan ƙarfafa masu bi" ko "ya taimakawa masu bi"
"ɗan'uwa na ƙwarai," ko "aboki." Bulus ya kira Filimon "ɗan'uwa" domin su masu bi ne kuma domin ya ƙarfafa cewa su abokai ne.
Bulus ya fara da roko da bayyana dalilin wasiƙar sa.
AT: 1) "ƙarfin iko saboda Almasihu" ko 2) "ƙarfin hali saboda Almasihu." "Ƙarfin hali saboda Almasihu ya ba ni ƙarfin iko"
AT: 1) "soboda na san yanda kake ƙaunar mutanen Allah" 2) "saboda kana ƙauna ta" ko 3) "soboda ina ƙaunar ka"
"ɗana Onisimus." Bulus ya yi magana game da abokantakar su da Onisimus kamar yanda uba ya ke ƙaunar ɗansa. Ba wai Onisimus ɗan Bulus ne na asali ba, amma ya karbi koyarwa ta ruhaniya game da Yesu ta wurin Bulus ne, kuma Bulus ya ƙaunace shi. AT: "Onisimus ɗana na ruhaniya"
Wannan suna "Onisimus" na nufin "riba" ko "mai amfani"
A nan "uba" na nufin cewa Bulus ne ya canza Onisimus zuwa mataki na sannin Almasihu. AT: "wanda ya zama ɗa na ruhaniya a gare ni, na koyar da shi game da Almasihu ya kuma karɓi sabon rayuwa yayinda ina sarƙoƙina" ko "wanda ya zama kamar ɗa a gare ni yayinda ina cikin sarƙoƙina"
'Yan kurkuku kunlum na cikin sarƙoƙi. Bulus ya koyar da Onisimus sa'anda yana cikin kurkuku, a cikin kurkuku kuma ya rubuto wannan wasiƙa. AT: "... yayin da ina cikin kurkuku"
Ya yiwu Bulus ya aiki Onisimus tare da wani mai bi dauke da wannan wasiƙa.
A nan "zuciya" na nuna shauƙi na mutum. wannan jimla "wanda ya ke a cikin zuciyata kwarai" na nuna ƙauna da wani ke da shi ga wani. Bulus na faɗin wannan game da Onisimus. AT: "wanda nake ƙauna sosai"
"domin shi zai taimake ni, tun da bazaka kasance a nan ba" ko "domin shi zai iya taimako na a madadin ka"
Bulus ya shigga kurkuku sabo da ya yi shelar bishara a fili. AT: "sabo da na yi shelar bishara a fili"
Bulus ya ambaci abubuwa biyu domin ya sadar da akasin abin da ya ambato. AT: "Amma na so in rike shi a wurina tare da yardarka"
"Ba ni so ka yi nagarin aiki domin na sa ka tilas, saidai domin ka so aikata wa"
"amma domin ka zaɓa ka aikata abu mai kyau"
AT: "Watakila dalilin da ya sa Allah ya dauki Onisimus daga gare ka na ɗan lokaci domin kă"
"a wannan lokacin"
"mai muhimmanci fiye da bawa"
"ɗan'uwa na ƙwarai" ko "ɗan'uwa mai daraja cikin Almashihu"
"ya fi kasance wa da daraja a gareka"
" a matsayin mutum." Bulus na nufin Onisimus wanda ya kasance amintaccen bawa.
"kamar ɗan'uwa a cikin Ubangiji" ko "domin shi na Ubangiji ne"
"idan kayi tunanina a matsayin abokin aiki na Almasihu"
"ka faɗa cewa ni ke rike da basussukan ka"
"Ni, Bulus, na rubuta wannan da kaina." Bulus ne ya rubuto wannan sashi da hannun sa, saboda Filimon ya sa ni kalmomin daga Bulus ne. Da gaske Bulus zai biya shi.
"Ba sai na tunashe ka ba" ko "Ka riga ka sani." Ko da shike Bulus na faɗin cewa bai kamata ya faɗa wa Filimon wannan ba, amma ya cigaba da faɗin hakan. Faɗin hakan ya ƙarfafa gaskiyar abinda Bulus ke faɗa masa.
"ina bin ka bashin rayuwar ka." Bulus na faɗin cewa kada Filimon ya ga kamar yana bin Onisimus ko Bulus bashin wani abu domin Bulu na bin Filimon bashi mai yawa. Dalilin kuma shi ne Bulus na bin Filimon bashin ran sa. AT: "kana riƙe da bashi na mai yawa domin na ceci rayuwar ka" ko "abin da na faɗa maka ya ceci rayuwar ka, soboda haka ina bin ka bashin rayuwar ka"
A nan "hutu" na nufin ta'aziya ko karfafawa. A nan "zuciya" kuma na nufin yanda mutum ke ji, tunani, ko cikin jiki. Bulus ya so Filimon ya ba wa zuciyarsa hutu. AT: "ka karfafa ni a cikin Almasihu" ko "ka ta'azantar da ni a cikin Almasihu" ko "ka ba zuciyata hutu a cikin Almasihu ta wurin karɓar Onisimus"
"Saboda ina da tabbaci za ka iya yin abin da na roƙa"
"Kuma"
"ka shirya mini masauki a gidanka." Bulus ya roƙi Filimon ya masa wannan.
zan sami 'yanci na komowa wurin ku daga waɗanda suka ajiyeni a kurkuku.
Wannan mai bi ne da ke kurkuku tare da Bulus
"wanda yana kurkuku tare da ni saboda bautar Almasihu Yesu"
"Markus da Aristarkus, da Dimas, da Luka abokan aikina, suna gaisheku"
Waɗannan sunayen maza ne
"mazajen da suke aiki tare da ni" ko "dukan waɗanda suna aiki tare da ni."
Kalmar nan "ku" na nufin Filimon da dukan waɗanda suna tattaruwa a gidansa. Kalmar nan "ruhunku" yana nufin mutane da kansu. AT: "Bari Ubangijin mu Yesu Almasihu shi yi maku alheri"
1A zamanin da, Allah ya yi wa kakanin kakanninmu magana ta hanyoyi ma su yawa iri iri, ta bakin annabawa. 2Amma a zamanin nan na karshe, ya yi mana magana ta wurin Dansa, wanda ya sa magajin kome, wanda ta wurinsa ya halicci duniya. 3Shi ne hasken daukakar Allah, ainihin kamanin zatinsa. Ya na rike da dukkan abubuwa ta ikon kalmarsa. Bayan da ya tsarkake zunubanmu, sai ya zauna a hannun dama na madaukaki a can sama.4Ta haka ya ke da fifiko a kan mala'iku, kamar yadda sunansa da ya gada yake da fifiko nesa a kan nasu. 5Domin kuwa wanene a cikin mala'iku Allah ya taba cewa, "Kai Da na ne, yau na zama Uba a gare ka?" kuma, "Zan kasance Uba a gareshi, shi kuma, zai kasance Da a gare ni?"6Kuma, da Allah ya kawo magaji a duniya, sai ya ce, "Dukan mala'ikun Allah su yi masa sujada." 7A game da mala'iku kuma sai ya ce, "yakan mai da mala'ikunsa ruhohi, masu hidimarsa kuma harsunan wuta.8A game da Dan, ya ce "kursiyinka, ya Allah, na har abada abadin ne. Sandar sarautarka sanda ce ta tsantsar gaskiya. 9Ka kaunaci aikin adalci, ka ki aikin sabo. Saboda haka Allah, wato Allahnka, ya shafe ka da man farin ciki fiye da tsararrakinka."10"Tun farko, Ubangiji, kai ne ka hallici duniya. Sammai kuma aikin hannayenka ne. 11Za su hallaka, amma kai madawwami ne. Duk za su tsufa kamar tufafi. 12Za ka nade su kamar mayafi, za su kuma sauya, amma kai kana nan ba sakewa, Har abada shekarunka ba za su kare ba."13Amma wanene a cikin mala'ikun Allah ya taba cewa, "Zauna a hannun dama na, sai na sa makiyanka a karkashin kafafunka?" 14Ashe, ba dukkan mala'iku bane ruhohi, wadanda Allah yakan aika, don su yi wa wadanda za su gaji ceto hidima?
Kodashike wannan wasiƙar bata ambaci masu karɓan ta ba waɗanda aka aika masu, marubucin dai ya rubuto wannan wasiƙar musamman zuwa ga Yahudawa, waɗanda sun fi fahimtar misalai da dama da ya bayar daga Tsohon Alkawari.
"a waɗannan kwanakin ƙarshen." Jmlar na nufin lokacin da Yesu ya fara hidimarsa, har zuwa sa'ada Allah zai ƙaddamad da cikakken mulkin sa a bisa halitarsa.
"Ɗa" a nan wata laƙabi ce mai muhimmanci na Yesu, Ɗan Allah.
Marubucin yana maganar Ɗan kamar zai gaji wata arziki ne ko dukiya daga Ubansa. AT: "yă mallaki dukan komai"
"Ta wurin Ɗan ne Allah ya halici dukkan komai"
"hasken ɗaukakarsa." A nan an haɗa ɗaukakar Allah ne da wuta mai haske kwarai. Marubucin yana cewa Ɗan yana ɗauke da hasken, yana kuma wakilcin ɗaukakar Allah.
"ɗaukaka, sifar Allah." "Ainihin kamaninsa" ya na da ma'ana kusan ɗaya ne da "hasken ɗaukakarsa." Ɗan yana ɗauke da hali da allahntakar Allah, yana kuma wakilcin dukkan koman da Allah yake. AT: "ɗaukaka yana kuma kamar Allah" ko kuma "ɗaukaka, kuma abinda ke gaskiya game da Allah, gaskiya ne game da Ɗan"
"kalmarsa mai iko." A nan "kalma" na nufin wata sako ko umurni. AT: "umurnin sa mai iko"
"tsarkakewa" AT: "bayan da ya gama tsarkakemu daga zunubanmu"
Marubucin yana maganar gafarar zunubai kamar tsarkake mutum ne. AT: "ya sa shi abu mai yiwuwa Allah yă gafarta zunubanmu"
Zama a "hannun damar Allah" alama ce na samun girma da iko daga wurin Allah. AT: "yana zaune a wurin girma da iko a gefen Zatinsa a can sama"
A nan "Zatinsa" na nufin Allah. AT: "Allah maɗaukaki"
"Ɗan ya zama"
A nan "suna" na nufin daraja da iko. AT: "yadda daraja da ikon da ya gãda ke da girma fiye da daraja da ikonsu"
Marubucin yana maganar samun girma da iko a wurin Allah kamar gãdan arziki ne da kuma dukiya mai yawa daga Ubansa. AT: "ya karɓa"
Wannan tambayan na nanata cewa Allah bai taɓa ce da wani mala'ika ɗansa ba. AT: "Domin Allah bai taɓa ce wa wani mala'ikansa 'kai ɗa ne ... ɗa a gare ni ba."
Waɗannan jumloli biyun na nufin abu ɗaya ne.
Wato Yesu kenan. Marubucin yana ce da shi "ɗan fãri" ne domin ya nanata muhimmanci da ikon Ɗan a bisa kowa. Wannan bai nuna cewa Yesu ya taɓa fara kasancewa a wani lokaci a baya ba ko kuma cewa Allah yana da wasu 'ya'ya kuma kamar Yesu ba. AT: "Ɗansa mai girma, tilonsa"
"Allah ya ce"
Wannan na iya nufin 1) "Allah ya sa mala'ikunsa su zama ruhohi, masu bauta masa da iko kamar harsunan wuta" ko kuma 2) Allah ya sa iska da harsunan wuta su zama ''yan aika da kuma masu hidimarsa. A ainihin harshen, kalmar nan "mala'ika" na da ma'ana ɗaya da "ɗan aika" sa'annan kalmar nan "ruhohi" na da ma'ana ɗaya da "iska." Ko ma ta yaya, kwayar maganar itace mala'ikun suna bauta wa Ɗan domin ya fi su girma.
"Amma Allah ya faɗa haka wa Ɗan"
Wannan wani laƙabi ne na Yesu mai muhimmanci, Ɗan Allah.
Kursiyin Ɗan na madadin mulkinsa. AT: "Kai Allah ne, kuma mulkinka zai cigaba har abada abadin"
A nan "sanda" na nufin mulkin Ɗan. AT: "Kuma za ka yi mulki a bisa mutanen ka da gaskiya"
A nan "man farin ciki" na nufin farin cikin da Ɗan yayi yayin da Allah ya girmama shi. AT: "ya girmama ka, ya kuma sa ka zama mai farinciki fiye da kowa"
Marubicin ya cigaba da bayani cewa Yesu ya fi mala'iku.
"kafin komai ma ya kasance"
Marubucin yana maganar yadda Allah ya halicci duniya ne kamar ya yi gini ne a bisa harsashi. AT: "kai ne ka halicci duniya"
A nan "hannaye" na nufin ikon aikin Allah. AT: "Kai ne ka hallici Sammai"
"Sammai da ƙasa duk za su shuɗe" ko kuma "Sammai da ƙasa za su daina kasancewa"
Marubucin na maganar sammai da ƙasa kamar su tufafi ne da za su tsufa har su zama marasa amfani.
Marubucin yana maganar sammai da kasa kamar wasu tufafi ne ko wasu irin riguna ne da ake iya yafa su a kan riguna.
Marubucin yana maganar sammai da kasa kamar su taguwa ne ko wata irin mayafi ne da ake iya sauyasu.
AT: "za ka sauya su"
Ana amfani da tsawon lokaci a madadin kasancewar Allah ta har abada. AT: "ranka ba za ta taɓa ƙarewa ba"
Marubucin yana amfani ne da wannan tambayan don ya nanata cewa Allah bai taɓa faɗin haka wa wani mala'ika ba. AT: "Amma Allah bai faɗa wa wani mala'ika ... ƙafafu"
A zauna a "hannun dama na Allah" wata alama ce ta samun babban girma da iko daga Allah. AT: "Zauna a wurin girma a gefe na"
Ana maganar maƙiyan Almasihu kamar za su zama wani abun taka wa ne da sarki ke taka wa da ƙafafunsa a fãda. Wannan sifar na nuna nasara da rashin daraja ga maƙiyansa.
Marubucin yana amfani ne da wannan tambayan domin ya tunashe da masu karanta wannan wasiƙar cewa mala'iku basu da iko kamar Almasihu, amma suna da nasu hidima dabam. AT: "Dukkan mala'iku ruhohi ne waɗanda ... gaji ceto"
Ana maganar samun abinda Allah ya alkawarta wa masubi kamar gadan dukiya ne ko kuma arziki daga wani ɗan iyali. AT: "ga dukkan waɗanda Allah zai ceta"
1Saboda haka, lalle ne mu kara mai da hankali musamman da abubuwan da mu ka ji, don kada mu yi sakaci, su sullube mana.2Idan kuwa maganar nan da aka fada ta bakin mala'iku ta zama tabbatacciya, har kowanne keta umarni da rashin biyayya, suka gamu da sakamakonsu wanda ya kamace su, 3ta kaka za mu tsira, in mun ki kula da ceto mai girma haka? Domin Ubangiji da kansa, shi ne ya fara sanar da shi, wadanda suka saurare shi kuma suka tabbatar mana da shi. 4San'nan kuma Allah da kansa ya shaida ta wasu alamu, da abubuwan al'ajabai, da mu'ajizai iri iri, da kuma baiwar Ruhu Mai Tsarki dabam dabam da ya rarraba kamar yadda ya nufa.5Ai ba ga mala'iku ba ne Allah ya sa mulkin duniyar nan da za a yi, wanda muke zance. 6Amma wani ya shaida a wani wuri cewa, "Mutum ma menene, har da za ka tuna da shi? Ko dan mutum ma, har da za ka kula da shi?7Ka sa mutum ya gaza mala'iku; Ka nada shi da daukaka da girma. Bisa dukkan hallitta. 8Ka dora shi a kan dukkan halittarka, ka kuma mallakar da kome a karkashin sawayensa. Domin Allah ya mallakar da dukkan abubuwa a karkashinsa. Bai bar kome a kebe ba. Amma kuwa har a yanzu ba mu ga yana sarrafa dukkan abubuwa ba tukuna.9Amma mun ga wani wanda dan lokaci aka sa shi ya gaza mala'iku, shine Yesu, an nada shi da daukaka da girma, saboda shan wuyarsa ta mutuwa, wanan kuwa duk ta wurin alherin Allah ne Yesu ya mutu saboda kowa. 10Saboda haka, ya dace ga Allah, shi da dukkan abubuwa suka kasance domin sa, ta gare shi, domin ya kawo 'ya'ya masu yawa ga samun daukaka. Domin a kammala cetonsu ta wurin shan wuyarsa.11Domin da shi mai tsarkakewar da kuma wadanda aka tsarkaken, duk tushensu daya ne. Saboda wanan dalili ne shi ya sa ba ya jin kunyar kiran su 'ya'uwansa. 12Da yace, "zan sanar da sunanka ga ya'uwana, a tsakiyar taronsu zan yabe ka da waka."13Har wa yau, yace, "Zan dogara a gare shi." Da kuma "Ga ni nan, ni da 'ya'yan da Allah ya ba ni." 14Wato tun da yake 'ya'yan Allah duk suna da nama da jini, Yesu ma ya dauki kamannin haka, ta wurin mutuwa ya hallakar da mai ikon mutuwa, wato Iblis. 15Ya kuma 'yanta duk wadanda tun haihuwarsu suke zaman bauta sabo da tsoron mutuwa.16Don hakika ba mala'iku yake taimako ba, a'a, zuriyar Ibrahim ne yake taimako. 17Saboda haka, lalle ne ya zama kamar yan'uwansa ta kowacce hanya, domin ya zama babban Firist, mai jinkai, mai aminci kuma na al'amarin Allah, ya kuma mika hadayar sulhu ta gafarta zunuban jama'a. 18Tun da yake Yesu ma da kansa ya sha wahala, sa'adda aka gwada shi, don haka, zai taimaki wadanda ake yi wa gwaji.
Wannan shi ne na farko cikin kashedi biyar da marubucin ya bayar.
A nan "mu" na nufin marubucin a haɗe da masu sauraro.
Wannan na iya nufin 1) ana maganar mutanen da sun daina gaskatawa da Allah ne kamar suna sulluɓewa, kamar yadda kwalekwale ke sulluɓewa daga wurin tsayawarsa a ruwa. AT: "domin kada mu daina gaskantawa da shi" ko kuma " 2) ana maganar mutanen da sun daina gaskantawa da maganar Allah kamar suna sulluɓewa ne, kamar yadda kwalekwale ke sulluɓewa daga wurin tsayawarsa a ruwa. AT: "domin kada mu daina biyayya da shi"
Yahudawa sun gaskanta da cewa Allah ya ba da shari'ar sa wa Musa ta wurin mala'iku. AT: "Idan kuwa maganar nan da Allah ya yi ta wurin mala'iku"
Marubucin na da tabbaci cewa waɗannan abubuwa gaskiya ne. AT: "Domin maganar"
A nan "keta" da "rashin biyayya" na tsaye ne a madadin mutanen da ke da laifin waɗannan zunuban. AT: "duk mutumin da ya yi zunubi ya kuma yi rashin biyayya zai gamu da sakamako"
Waɗannan kalmomi biyun a takaice na nufin abu ɗaya.
Marubucin na amfani ne da wannan tambaya domin ya nanata cewa mutanen za su gamu da hukunci idan sun ƙi ceton Allah ta wurin Almasihu. AT: "lallai ne Allah zai hukunta mu idan ba mu kasa kunne ga maganarsa game da yadda zai cece mu ba!"
"ƙi kasa kunne" ko kuma "ɗauke shi da rashin muhimmanci"
AT: "Ubangiji ne da kansa ya fara sanar da wannan sako game da yadda Allah zai cece mu, sa'annan waɗanda suka ji sun tabbatar mana da shi"
"yadda dai yake so ya yi"
Ambacin da ke nan daga littafin Zabura ne a Tsohon Alkawali. Ya cigaba har zuwa sashi na gaba.
"Allah bai sa mala'iku su yi mulki bisa"
A nan "duniya" na nufin mutanen da suke kasancewa a wurin. "za a yi" kuma na nufin duniya da za a yi bayan da Yesu ya dawo. AT: "mutanen da za su kasance a sabuwar duniya da za ayi"
Wannan tambayan ne da ke nanata cewa mutum ba komai ba ne, yana kuma nuna yadda ya zama abun mamaki yadda Allah ke sa hankalinsa a kansu. AT: "mutane ba komai bane, kuma duk da haka kana tunawa da su!"
Wannan karin maganar "ɗan mutum" na nufin 'yan adam. Wannan tambayar na da ma'ana ɗaya ne da na farkon. Yana nuna yadda ya zama abun mamaki yadda Allah ke kula da mutane, wadda ba komai ba ne. AT: "Muhimmancin mutane kaɗan ne, duk da haka kana kula da su!"
AT: "ko wanene ɗan mutum"
Marubucin yana maganar yadda mutane sun gaza a muhimmanci kamar suna tsaye ne a matsayi da ya gaza matsayin mala'iku. AT: "basu da muhimmanci kamar mala'iku"
Waɗannan duka na nufin mutane gabaɗaya, a haɗe da maza da mata. AT: "sa mutane ... ka naɗa su ... sawayensu ... gă su"
Ana maganar kyautar ɗaukaka da girma kamar wata rawani ce a kan ɗan wasan guje-guje da tsalle-tsalle. AT: "kã basu babban girma da ɗaukaka"
Marubucin yana maganar mulkin mutane bisa kowane abu kamar sun taka kowane abu da ƙafafunsu ne. AT: "ka basu mulki bisa kowane abu"
Wannan na nufin cewa dukkan abubuwa za su zama a ƙarƙashin Almasihu. AT: "Allah ya sa su suna mulki bisa dukkan komai"
"Mun san cewa har yanzu mutane basu mulkin dukkan komai"
"mun san akwai wani"
AT: "wadda Allah ya sa"
Duba yadda aka yi fassar wannan a [2:7]
AT: "yă ɗanɗana mutuwa"
AT: "ceci 'ya'ya masu yawa"
A nan wannan na nufin masubin Almasihu, maza da mata. AT: "masubi da yawa"
Wannan na iya nufin 1) wannan wata karin magana ce da marubucin yana zancen ceto kamar wani wuri ne na zuwa , kuma Yesu shi ne wadda ya je wannan wurin kafin jama'ar da ke hanya, yana kuma kai su ga samun ceto. AT: "mai kai jama'a ga samun ceto" ko kuma 2) kalmar da aka fassara a nan "shugaba" na iya nufin "mai kafa" kuma marubucin yana magana ne game da Yesu wanda shi ne ya kafa ceto, ko ya sa shi ya zama abu mai yiwuwa wa Allah ya ceci mutane. AT: "wadda ya sa samun ceto ya zama abu mai yiwuwa"
Ana maganar manyanta da kammalawa kamar mutum ya zama kammalalle ne, mai yiwuwa kammalalle a dukkan gabobin jikinsa.
"mai sa mutane su zama da tsarki" ko kuma "mai tsarkake mutane daga zunubi"
AT: "mutanen da ya tsarkake" ko kuma "mutanen da ya tsarkake daga zunubi"
Za a iya bayyana wannan tushen a fili. AT: "na da tushe ɗaya" ko kuma "na da Uba ɗaya"
"Yesu baya jin kunya"
Wannan na nufin ya ɗauke su a matsayin 'yan'uwansa. AT: "yana farin cikin kiransu 'yan'uwasa"
A nan wannan na nufin dukkan waɗanda suka ba da gaskiya ga Yesu, maza da mata.
A nan "suna" na nufin halin mutum da kuma abinda ya yi. AT: "zan sanar wa 'yan'uwana manyan abubuwan da ka yi"
"yayin da masubi sun taru su yi wa Allah sujada"
"Kuma wani annabi ya rubuto a wata nassi abinda Almasihu ya faɗa game da Allah:"
Wannan na maganar waɗanda suka gaskata da Almasihu kamar su 'ya'ya ne. AT: "waɗanda ke kamar 'ya'ya ... waɗanda ke kamar 'ya'ya a gaban Allah"
Wannan jumlar "nama da jini" na nufin ainihin mutuntakar mutane. AT: "su duk 'yan' adam ne"
"Yesu ya zama ɗan adam kamar su"
AT: "ta rasuwa"
AT: "na da ikon sa mutane su mutu"
Ana maganar tsoron mutuwa kama bauta ne. Ana kuma maganar 'yantar da mutum daga tsoro kamar 'yantar da mutum ne daga bauta. AT: "Wannan saboda ya 'yantar da dukkan mutane ne. Gama mun yi rayuwa kamar bayi domin muna tsoron mutuwa."
...
"ya zama lallai ne wa Yesu"
A nan "'yan'uwa" na nufin mutane gabaɗaya. AT: "kamar 'yan adam"
Mutuwar Almasihu a bisa giciye na nufin cewa Allah na iya gafarta zunubai. AT: "zai sa shi ya yiwu Allah ya gafarta zunuban jama'a"
AT: "Shaiɗan ya gwada shi"
AT: "wadda Shaiɗan ke yi wa gwaji"
1Don haka yanuwana tsarkaka, a bokan kira a samaniya. Yi la'akari da Yesu. wato Manzo da babban firist na shaidar bangaskiyarmu. 2Shi amintacce ne na Allah, wanda ya bashi hidima, kamar yadda Musa ya kasance amintacce a gidan Allah. 3Gama Yesu ya cancanci daukaka mafi girma fiye da ta Musa. Domin wanda ya gina gida, ya fi gidan nan daukaka. 4Gama kowane gida, akwai wanda ya gina shi, amma mai ginin komai shine Allah.5Musa hakika amintaccen bawa ne a gidan Allah, yana ba da shaidar abubuwan da za su faru a nan gaba. 6Amma Almasihu shi Da ne mai mulki a gidan Allah. Mu ne gidansa idan mun rike begenmu da dukkan zuciyarmu.7Saboda haka, kamar yadda Ruhu Mai Tsarki ya fadi: "Yau, Idan kun ji muryarsa, 8kada ku taurare zuciyarku kamar yadda 'ya'yan isra'ila suka yi cikin tawaye a lokacin gwaji a jeji.9A lokacin nan ne kakanninku suka yi mani tawaye, ta wurin gwada ni, bayan shekara arba'in suna ganin ayyukana. 10Saboda haka na yi bakin ciki da wannan tsarar, sai na ce,' Kullum suna yawan bijirewa a zukatansu. Basu san tafarkuna ba.' 11Don haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ba za su shiga cikin hutuna ba."12Ku yi hankali 'yan'uwa kada a tarar da mummunar zuciya marar bangaskiya a tsakaninku, zuciya wadda ke juyawa daga Allah mai rai. 13Maimakon haka, ku karfafa juna a kowacce rana, muddun muna cikin wannan rana kada wani cikinku ya taurare zuciyarsa saboda yaudarar zunubi.14Gama mun zama abokan aiki da Almasihu, idan mun rike begenmu cikinsa da karfi, daga farko zuwa karshe. 15Game da wannan, an fadi "Yau idan kun saurari muryarsa, kada ku taurare zuciyarku, kamar a kwanakin tawaye nan."16Su wanene suka ji muryar Allah suka yi tawaye? Ba wadanda Musa ya yi masu jagora daga Masar ba ne? 17Kuma da su wa Allah ya yi fushi shekara arba'in? Ba da wadanda suka yi zunubi ba ne, wadanda gawawwakinsu suka warwatsu a jeji? 18Da su wa Allah ya rantse ba za su shiga hutunsa ba? In ba wadanda suka yi masa rashin biyayya ba? 19Mun kuma gani cewa basu iya shiga hutunsa ba saboda rashin bangaskiyarsu.
Kashedi na biyun ya fi tsawo, da kuma bayani, ya kuma haɗa da surori 3 da 4. Marubucin ya fara ta wurin nuna cewa Almasihu ya fi bawansa Musa.
A nan 'yan'uwa na nufin masubi kirista, maza da mata.
A nan "samaniya" na nufin Allah. AT: "Allah ya kiraye mu tare"
A nan kalmar nan "manzo" na nufin wanda aka aiko. A wannan nassi, ba ya nufin ko ɗaya daga cikin manzanni goma-sha-biyun. AT: "shi wadda Allah ya aiko kuma shi ne babban firist"
AT: "wadda muka furta" ko kuma "wadda muka ba da gaskiya
Ana maganar mutanen Yahudawa wadda Allah ya bayyana kansa masu kamar su gida ne. AT: "zuwa ga dukkan mutanen Allah"
AT: "Allah ya mai da Yesu mutumin da ya cancanci"
Ana maganar ayyukan hallitar duniya da Allah ya yi ne kamar ya gina gida ne.
kowane gida na da wanda ya gina shi
Ana maganar mutanen Yahudawa da Allah ya bayyana kansa a garesu kamar su zahirin gini ne. Dubi yadda kun fassara wannan a [3:2]
Wannan jumlar na maganar aikin Musa. AT: "Rayuwar Musa da aikinsa sun nuna waɗannan abubuwa"
AT: "Yesu zai faɗa nan gaba"
Wannan wata laƙabi ne mai muhimmanci na Yesu, Ɗan Allah.
AT: "wadda ke mulkin jama'ar Allah"
AT: "Mu ne jama'ar Allah"
AT: "idan mun cigaba da ƙarfin hali da farin cikin jira Allah ya cika alkwarinsa"
Ambacin da ke nan daga littafin Zabura ne a Tsohon Alkawari.
"muryar" Allah na nufin maganar sa. AT: "yayin da kun ji maganar Allah"
A nan "zuciya" na nufin hankalin mutum. Jumlar nan "taurare zuciya" na nufin zama gagararre. AT: "kada ku zama gagararru" ko kuma "kada ku ƙi ji
AT: "kamar yadda kakanninku suka yi wa Allah tawaye, suka gwada shi a jeji"
Wannan na nufin jama'ar Isra'ila.
A nan "ni" yana nufin Allah.
"shekara 40"
"na yi fushi" ko kuma "ban ji daɗi ba ko kaɗan"
A nan "bijerewa a zukatansu" na nufin rashin aminci ga Allah." A nan "zukata" na nufin hankalin mutum ko kuma marmarinsa. AT: "suka riƙa ƙi na" ko kuma "suka riƙa ƙi yi mani biyayya"
Wannan na maganar yanayin bi da rayuwar mutum ne kamar wata tafarki ne ko kuma hanya. AT: "Ba su fahimci yadda na ke so su bi da rayuwarsu ba"
An yi maganar salama da tsaron da Allah ke tanadawa kamar wata hutu ce da yake bayar wa, kuma kamar wata wuri ce da mutane ke iya zuwa. AT: "Ba za su taɓa shiga wurin hutu ba" ko kuma "Ba zan taɓa barin su su ɗanɗana albarkun hutuna ba"
Wannan na nufin masubi, maza da mata. AT: "'yan'uwa masubi"
A nan "zuciya" na nufin hankalin mutum ko kuma ra'ayi. An yi maganar rashin ba da gaskiya da rashin biyayya ga Allah kamar zuciyar da ta juya wa Allah ne a ganin idon mutane. AT: "kada a tarar da kowa a cikinku da ya ƙi gaskiya, ya kuma daina yi wa Allah mai rai biyayya"
"Allah na gaske da ke da rai"
"tun da sauran zarafi"
AT: "yaudarar zunubi ba zai taurare kowa daga cikinku ba"
A nan "mu" na nufin marubucin da masu karatu.
"idan mun cigaba da dogara gareshi da gabagaɗi"
"daga lokacin da muka fara gaskatawa da shi"
Wannan wata hanya ce ta maganar har lokacin mutuwar mutum. AT: "har zuwa mutuwarmu"
AT: "marubucin ya rubuta"
Duba yadda aka fassara wannan a [3:8]. AT: "kamar yadda kakanninku suka yi wa Allah tawaye"
Marubucin yana amfani ne da waɗannan tambayoyin ya koya wa masu karatun wannan wasiƙa. Ana iya haɗin waɗannan tambayoyin a jumla ɗaya, idan akwai bukatar yin haka. AT: "Dukkan waɗanda suka fito daga Masar tare da Musa sun saurari Allah, duk da haka sun yi tawaye."
Marubucin yana amfani ne da waɗannan tambayoyin ya koya wa masu karatun wannan wasiƙa. Ana iya haɗa waɗannan tambayoyin a jumla ɗaya, idan akwai bukatar yin haka. AT: "Har shekaru arba'in, Allah ya yi fushi da waɗanda sun yi zunubi, ya kuma sa suka mutu a jeji."
Marubucin ya yi amfani ne da wannan tambayar domin yă koya wa masu karatun wannan wasika. AT: "Kuma ga waɗanda suka yi rashin biyayya ne ya rantse cewa ba za su taɓa shi hutunsa ba."
An yi maganar salama da tsaron da Allah ke tanadawa kamar wata hutu ce da yake bayar wa, kuma kamar wata wuri ce da mutane ke iya zuwa. AT: "Ba za su taɓa shiga wurin hutu ba" ko kuma "Ba zan taɓa barin su su ɗanɗana albarkun hutuna ba" (Dubi: )
AT: "domin basu gaskata da shi ba"
1Saboda haka, sai muyi lura kwarai don kada wani ya kasa kai ga shiga hutun da aka alkawarta maku na Allah. 2Don mun ji albishir game da hutun Allah kamar yadda aka fada masu. Amma wancan sakon bai anfana ga wadanda suka ji ba tare da sun bada gaskiya ga sakon ba.3Ai mu, wadanda muka gaskata-mune zamu shiga wannan hutun, kamar yadda ya ce, "Yadda na yi rantsuwa cikin fushina, baza su shiga hutu na ba." Ya fadi hakan, ko da yake ya gama aikin hallittarsa tun daga farkon duniya. 4Domin yayi fadi a wani wuri game da rana ta bakwai, "Allah ya huta a rana ta bakwai daga dukkan ayyukansa." 5Ya sake cewa, "Baza su taba shiga hutu na ba."6Saboda haka, tun da hutun Allah na kebe domin masu su shiga, kuma tun da Isra'ilawa da yawa wadanda suka ji sakon nan mai kyau game da hutunsa ba su shiga ba saboda rashin biyayya, 7Allah ya sake shirya wata rana da ake kira, "Yau." Ya sa wannan rana sa'adda yayi magana ta wurin Dauda, wanda ya ce tun da dadewa da aka fara fada, "Yau idan kun ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku."8Don idan Joshua ya ba su hutu, da Allah ba zai sake magana a kan wata rana ba. 9Saboda haka, akwai hutun asabar kebabbe ga mutanen Allah. 10Don shi wanda ya shiga hutun Allah shi kansa ma ya huta daga ayyukansa, kamar yadda Allah yayi da nasa. 11Saboda haka muyi marmarin shiga wancan hutun, don kada kowa ya fadi ga irin rashin biyayyar da suka yi.12Maganar Allah kuwa rayayyiyace, kuma mai ci, fiye da takobi mai kaifi-biyu. Takan ratsa har tsakanin rai da ruhu, kuma tana kaiwa bargo. Takan iya bincika tunanin zuciya da manufarta. 13Babu halittaccen abu da ke boye a idon Allah. Sai dai, kome a sarari yake, kuma a bayyane yake a idonsa wanda lallai ne zamu bada lissafin kanmu a gare shi.14Da yake muna da babban firist wanda ya ratsa sammai, Yesu Dan Allah, sai mu riki bangaskiyarmu da karfi. 15Domin babban firist namu ba marar tausayi ga kasawarmu bane, amma wanda aka jarraba ne ta ko wanne hali irin yadda aka yi mana, sai dai ba'a same shi da zunubi ba. 16Sai mu zo wurin kursiyin alheri gabagadi, domin a yi mana jinkai mu kuwa sami alherin da zai taimake mu a lokacin bukata.
Sura huɗu ya cigaba da yi wa masubu kashedi da aka fara a [3:7]. Allah, ta wurin marubucin, ya ba wa masubi hutu wadda hutun Allah cikin hallitar duniya na ba da misali.
"Domin abinda na fito faɗa maku gaskiya ne" ko kuma "tunda lallai Allah zai hukunta masu rashin biyayya" ([3:19])
An yi maganar Alkawarin Allah kamar wata kyauta ce da Allah ke riƙe da ita yayin da ya ziyarci mutanen. AT: "Allah zai bar ku ku kai ga shiga hutu kamar yadda ya mana alkawari"
An yi maganar salama da tsaron da Allah ke tanadawa kamar wata hutu ne da yake bayar wa, kuma kamar wani wuri ne da mutane ke iya zuwa. AT: "su shiga gun hutu " ko kuma " su ɗanɗana albarkun hutu na Allah"
AT: "Gama mun ji albishirin kamar yadda su ma sun ji"
A nan "su" na nufin kakannin Yahudawa da suke da rai a lokacin Musa.
A nan farkon furcin, "yadda na yi rantsuwa ... hutu," daga Zabura ce. Furci na biyun, "Allah ya huta rana ta ... ayyukansa" daga rubuce-rubucen Musa ne. Furci na ukun, "Ba za su taɓa shiga ... hutu," har yanzu daga Zabura ne.
"mu da muka gaskanta"
An yi maganar salama da tsaron da Allah ke tanadawa kamar wata hutu ne da yake bayar wa, kuma kamar wani wuri ne da mutane ke iya zuwa. AT: "mu da muka gaskanta za mu shiga wannan wurin hutu" mu da muka gaskanta za mu ɗanɗana albarkun hutu na Allah"
"kamar yadda Allah ya ce"
"Yadda na rantse a lokacin matuƙar fushina"
An yi maganar salama da tsaron da Allah ke tanadawa kamar wata hutu ne da yake bayar wa, kuma kamar wani wuri ne da mutane ke iya zuwa. AT: "Ba za su taɓa shiga wurin hutu ba" ko kuma "Ba zan taɓa barin su su ɗanɗana albarkun hutuna ba"
AT: "ya gama hallita" ko kuma "ya gama aikinsa na hallita"
AT: "daga farkon farin duniya"
Wannan jerin lamba ta "bakwai" ce.
An yi maganar salama da tsaron da Allah ke tanadawa kamar wata hutu ne da yake bayar wa, kuma kamar wani wuri ne da mutane ke iya zuwa. AT: "Allah yana barin wasu su shiga wurin hutu ba" ko kuma "Allahn yana barin wasu su ɗanɗana albarkun hutuna ba"
Ana maganar umurnin Allah zuwa ga Isra'ilawa kamar ya basu umurnin da wata babban murya ce. Duba yadda aka fassara wannan a [3:7-8]. AT: "idan kun ji Allah yana magana"
A nan "zuciya" na nufin hankalin mutum. Jumlar nan "taurare zuciya" na nufin zama gagararre. AT: "kada ku zama gagararru" ko kuma "kada ku ƙi ji
An yi maganar salama da tsaron da Allah ke tanadawa kamar wata hutu ne da Joshua ke bayarwa AT: "idan Joshua ya kawo Isra'ilawa zuwa wurin da Allah zai basu hutu"ko kuma "idan Isra'ilawa a lokacin Joshua sun ɗanɗana Albarkun Allah na hutu"
AT: "akwai hutun asabar da Allah ya keɓe wa mutanensa"
An yi maganar salama na har abada da tsaro kamar su ne ranar asabar, ranar sujada na Yahudawa da kuma hutawa daga yin aiki. AT: "hutu na har abada"
An yi maganar salama da tsaron da Allah ke tanadawa kamar wata wuri ce da ake shiga. AT: "mutumin da ya shiga wurin hutun Allah" ko kuma "mutumin da ya ɗanɗana albarkun hutu na Allah"
An yi maganar salama da tsaron da Allah ke tanadawa kamar wata wuri ce da ake shiga. AT: "mu ma mu yi duk abinda muka iya yi don mu huta tare da Allah a wurin da yake"
Ana maganar rashin biyayya kamar wani rami ne da mutum na iya faɗị a ciki. AT: "yi rasahin biyayya kamar yadda suka yi"
A nan "su" na nufin kakannin Ibraniyawa lokacin Musa.
A nan "maganar Allah" na nufin dukkan abinda ya sadu da mutum ko ta wurin magana ko rubuce-rubuce. AT: "Kalmomin Allah kuwa rayayyune"
Ana maganar wannan kamar maganar Allah na da rai. Yana nufin cewa idan Allah ya yi magana, yana da iko da kuma inganci.
Takobi mai kaifi-biyu na iya yanka tsoka. Maganar Allah na ci sosai a nuna abinda ke zuciya da kuma tunanin mutum.
takobi mai kaifi-biyu da ke ci a gefe biyun
Wannan na cibaga da magana a kan maganar Allah kamar wata takobi ce. A nan takobin na ci sosai har ma yana iya yanka zuwa gabobin jikin mutun da ke da wuya ko kuma wadda ma basu yiwuwa a yanke. Wannan na nufin cewa babu abinda ke cikin mu da zamu iya ɓoye wa Allah.
Waɗannan sune bangaren jikin mutum daban daban da ido baya iya gani. "Rai" shi ne abinda ke sa mutum ya zama rayayye. "Ruhu" kuma shi ne bangaren jikin mutum da ke sa mutum ya iya sani ko kuma ya gastanta da Allah.
"bargo" itace tsakiyar kashin jiki.
Wannan na bayyana maganar Allah kamar wani mutum ne da ke iya sanin abu. AT: "Maganar Allah tana fallasa"
"Zuciya" a nan tana nufin tunanin zuciyar mutum AT: "abinda mutum ke tunani ko kuma niyyar yi"
AT: "Ba wani abinda Allah ya hallita da za a iya ɓoye masa"
...
Waɗannan kalmomi na nufin abu ɗaya ne, suna kuma nanata cewa babu abinda za a iya ɓuya wa Allah.
Ana maganar Allah ne kamar yana da idanu. AT: "ga Allah, wanda zai shar'anta yadda muka yi rayuwa"
"wanda ya shigo wurinda Allah yake"
Wannan wata laƙabi ne na Yesu.
Ana maganar bangaskiya da dogara kamar wasu abubuwa ne da mutum na iya cafke su da ƙarfi. AT: "bari mu cigabada da gaskatawa da shi da gabagaɗi"
Wannan na nufin cewa Yesu yana da tausayi ga mutane. AT: " muna da babban firist da ke iya jin tausayi ... haƙiƙa, wanda"
AT: "Wanda ya jimre kowace irin jarraba da muke da su" ko kuma "wadda shaiɗan ya jarrabta a kowace hali da yake jarrabtar mu"
"ba yi zunubi ba"
"wurin kursiyin Allah, wurin da akwai alheri." A nan "kursiyi" na nufin sarautar Allah a matsayin sarki. AT: "inda Allahn mu mai alheri ke zaune a kursiyinsa."
An yi maganar "jinƙai" da "alheri" a nan kamar wasu abubuwa ne da ake iya bayar wa ko samu. AT: "Allah na iya yi mana jinƙai da alheri, zai kuma iya taimakonmu a lokacin bukata"
1Kowanne babban firist, da yake an zabe shi ne daga cikin mutane, a kansa shi ya wakilci mutane ga al'amarin Allah, don ya mika sadakoki da kuma hadayu domin kawar da zunubai. 2Yana kuma iya tafiyar da jahilai da sangartattu a cikin salihanci, tun da shi ke rarrauna ne shi ta ko'ina. 3Saboda haka, wajibi ne ya mika hadayu, ba saboda kawar da zunuban jama'a kadai ba, har ma da na kansa.4Ba wanda zai kai kansa wannan matsayi mai girma, sai dai Allah ya yi kiransa ga haka, kamar yadda aka kirayi Haruna. 5Haka kuma, Almasihu, ba shi ya daukaka kansa ya zama Babban firist ba, sai dai wannan ne ya sa shi, wanda ya ce da shi, "Kai Dana ne; Yau na zama Uba a gare ka."6Kamar dai yadda a wani wuri kuma ya ce, "Kai firist ne na har abada, bisa ga kwatancin Malkisadak."7Almasihu, a lokacin zamansa a duniya, ya yi addu'o'i da roke-roke, tare da kuka mai tsanani, har da hawaye, ga wannan da yake da ikon cetonsa daga mutuwa, aka kuwa saurare shi saboda tsannin mika kansa. 8Ko da yake shi Da ne, ya koyi biyayya ta wurin wuyar da ya sha.9Har ya kai ga kammala, sai ya zama tushe madawwami, ceto ga dukkan wadanda suke masa biyayya. 10Gama Allah yana kiransa Babban firist, bisa ga kwatancin Malkisadak. 11Muna da abu da yawa da za mu fada a game da Yesu, amma zai yi wuyar bayani, da yake basirarku ta dushe.12Ko da yake yanzu kam, ya kamata ku zama masu koyarwa, duk da haka, ashe, ba ku wuce wani ya sake koya muku jigajigan farko na Maganar Allah ba? har ya zamana sai an ba ku madara ba abinci mai tauri ba? 13To, duk wanda yake madara ce abincinsa, bai kware da maganar adalci ba, kamar jariri yake. 14Amma abinci mai tauri, ai, na manya ne, wato wadanda hankalinsu ya horu yau da kullum, don su rarrabe nagarta da mugunta.
Marubucin yana bayyana zunubin firitocin Tsohon Alkawari, sa'an nan yana nuna cewa irin firist a kwatancin Almasihu, wanda shine mai kama da kwatancin Malkisadak, ya fi, ba irin firist a kwatancin Haruna ba.
AT: "wadda Allah ya zaɓa daga cikin mutane"
AT: "Allah yakan sa shi"
...
AT: waɗanda ... sun yaudaru" ko kuma "waɗanda ... sun gaskata da ƙarya"
"waɗanda sun gaskata da rashin gaskiya kuma suna mumunar rayuwa"
Ana maganar rarraunar babban firist kamar wani ne daban ke mulki a bisa shi. AT: "rarraune ne a ruhaniya" ko kuma "rarraune ne ga zunubi"
mamarin aikata zunubi
AT: "Allah ya sa ya zama wajibi ne"
Ambacin da ke nan daga littafin Zabura ne a Tsohon Alkawali.
Ana maganar girma a nan kamar wani wurin ne da ake iya zuwa ko kuma mutum ke iya kai kansa.
AT: "Allah ya yi kiransa ga haka, kamar yadda ya kirayi Haruna"
"Allah ya ce da shi"
Waɗannan jumloli suna nufin abu ɗaya ne. Dubi yadda aka fassara wannan a [1:5].
Waɗannan wasu laƙabi ne da ke bayyanin dangantakar da ke tsakanin Yesu da Allah Uba.
Ana iya fassarawa a fili wanda Allah ke magana a kai. AT: "kuma ya ce wa Almasihu"
"a wani wuri a cikin nassi"
Wannan na nufin cewa Almasihu, a matsayin firist, na da wasu halaye kamar Malkisadak a matsayin firist kenan. AT: "yadda Malkisadak firist da yake "
A nan "lokaci" na nufin tsawon lokacin zamansa a cikin "duniya" kuma na nufin rayuwar da Yesu yayi a duniya. AT: "Da yake rayuwa a duniya"
Waɗannan kalmomi biyun a takaice na da manufa guda.
Wannan na iya nufin 1) Allah na iya ceton Yesu don kada yă mutu. AT: "yă cece shi daga mutuwa" ko kuma 2) Allah na iya ceton Almasihu bayan mutuwa ta wurin rayar da shi kuma. In ya yiwu, a fassara wannan yadda zai ba da ma'ana biyun nan duka.
AT: "Allah kuwa ya ji shi"
Wannan wani laƙabi ne mai muhimmanci na Yesu, Ɗan Allah.
AT: "Har Allah ya kai shi ga kammala"
Wannan na nufin ya yi girma, zai iya girmama Allah a kowane fanin rayuwa.
AT: "yana ceton dukkan waɗanda suke masa biyayya har ma yana sa su rayu har abada"
AT: "Allah ya zaɓe shi"
Ko da shike marubucin ya yi amfani da wannan wakilin suna "mu", babu shakka yana nufin shi da kansa ne. AT: "Ina da abubuwa dayawa da zan faɗa"
Ana nufin basirar iya fahimata da aikatawa ko kuma biyayya. Ana kuma maganar basirar kamar wani gatari ne da ke iya dushe wa. AT: "kuna da matsalar fahimtar wannan"
Anan "jigajigan" na nufin jagora ko kuma ma'auni na ɗaukar ra'ayi. AT: "jigajigan gaskiyar"
Ana maganar koyar da maganar Allah da ke da sauƙin fahimta kamar shi wani madařa ne, abincin da jarirai ke iya ci. AT: "kun zama kamar jarirai, madařa ne kawai za ku iya sha"
Ana maganar koyar da maganar Allah da ke sa wuyar fahimta kamar abinci ne mai tauri, da ya dace ga manyan mutane. AT: madara, a maimakon abinci mai tauri da manya na iya ci
AT: "ke shan madara"
Ana kwatanta girmar ruhaniya da irin abincin da yaro mai girma ke ci. Abinci mai tauri ba na jariri ba ne, kuma wannan karin magana ne da ke bayyana sabon maibi da ke iya koyan wasu koyaswar gaskiya masu sauƙi; amma jim kaɗan, akan bashi abinci mai tauri, kamar yadda idan mutum ya manyanta yana iya koyan abubuwa masu ban wuya.
Ana maganar mutanen da sun horu su fahimci abu kamar sun horu ne su sami basirar fahimta. AT: "Waɗanda sun manyanta kuma suna iya bambamta nagarta da miyagu.
1Saboda haka, sai mu ci gaba a kan ka'idodin farko na al'amarin Almasihu, har ya zuwa kammala, ba wai mu sake koyar da jigajigan nan na tuba da ibada marar tasiri ba, da na gaskatawa da Allah, 2da kuma na koyarwa a kan wanke-wanke, da dora hannu, da tashin matattu, da dawwamammen hukuci. 3Za mu kuwa ci gaba in Allah ya yarda.4Domin wadanda aka haskaka zukatansu sarai, har suka dandana baiwar nan Basamaniya, suka kuma sami rabo na Ruhu Mai Tsarki, 5har su ka dandana dadin Maganar Allah, da ikon zamani mai zuwa, 6sa'an nan kuma suka ridda--ba mai yiwuwa ba ne a sake jawo su ga tuba, tun da yake sake gicciye Dan Allah suke yi su da kansu, suka kuma wulakanta shi a sarari.7Kasa ma da take shanye ruwan da ake yi a kai a kai, take kuma fid da tsire-tsire masu amfani ga wadanda ake nomanta dominsu, Allah yakan sa mata albarka. 8Amma idan tsire-tsirenta kaya ne da kashin yawo, ba ta da amfani ke nan, tana kuma gab da la'antarwa, karshenta dai konewa ne.9Ko da yake mun fadi haka, a game da ku kam, ya kaunatattu mun tabbata kuna abubuwa mafiya kyau na zancen ceto. 10Gama Allah ba marar adalci ba ne, har da zai ki kula da aikinku, da kuma kaunar sunansa da kuke yi, wajen yi wa tsarkaka hidima, har yanzu ma kuna yi.11Muna dai bukata kwarai kowannanku ya nuna irin wannan himma ga yin cikkaken bege, tabbatacce, har ya zuwa karshe. 12Don kada ku yi ragwanci, sai dai ku yi koyi da wadanda suka karbi cikar alkawaran nan, ta wurin bangaskiyarsu da hakurinsu.13Sa'adda Allah ya yi wa Ibrahim alkawari, da yake ba wani wanda ya fi shi girma da zai rantse da shi, sai ya rantse da kansa, 14Ya ce, "Hakika zan yi maka albarka, in kuma ribambamya zuriyarka." 15Ta haka, Ibrahim bayan da ya jure da hakuri, ya karbi cikar alkawarin.16Hakika mutane sukan rantse da abin da ya fi su. Rantsuwa kuma ita ce abar da take tabbatarwa da kowacce magana. 17Don haka, sa'adda Allah yake son kara tabbatar wa magadan alkawarin nan dahir, cewa nufinsa ba mai sakewa ba ne sam, sai ya hada da rantsuwa, 18Domin albarkacin abubuwa guda biyun nan marasa sakewa, masu nuna, cewa ba shi yiwuwa Allah ya yi karya, mu da muka gudu muka sami mafaka, mu karfafa kwarai mu riski abin da muka kafa bege a kai.19Muna da bege, kamar yadda yake ga rai, kafaffe, tabbatacce, shi ne kuma yake shiga har can ciki bayan labulen. 20Inda saboda mu ne Yasu ya riga mu shiga, da yake ya zama Babban Firist na har abada, kwatancin Malkisadak.
Marubucin ya cigaba da abinda sabobin masubi ke bukata zuwa kammala a cikin bi. Ya masu tunin koyarwar farƙo.
AT: "mu daina tattauna abinda mun koya tun farko kurum, yan zu ma ƙara da fahimtar manya-manyan koyaswa"
AT: "Kada mu sake maimaita koyarwar farkon ... na gaskatawa da Allah"
Wato ayyukan zunubi.
...
Ana yin wannan domin a keɓe mutum domin wata hidima ko matsayi ta musamman.
Wato fahimta kenan. AT: "waɗanda sun taɓa fahimtar saƙon bisharar Almasihu"
Ana maganar ɗanɗana ceto ne kamar ɗanɗana daɗin abinci. AT: "waɗanda sun ɗanɗana ikon ceto na Allah"
Ana maganar Ruhu Mai Tsarki da ke saukowa ga masubi kamar wani abu ne da jama'a ke iya rabawa. AT: "wanda suka karɓi Ruhu Mai Tsarki"
Ana maganar koyar maganar Allah kamar ɗanɗana daɗin abinci ne. AT: "Wanda sun koyi daɗin maganar Allah"
Wato ikon Allah da zai zo yayin da mulkinsa zai kasance a duniya gabaƙiɗaya. Dan haka, "ikon" na nufin Allah da kansa, mai riƙe dukkan iko. AT: "sanin yadda Allah zai yi aiki da iko nan gaba"
AT: "wanda sun daina gaskata da Allah"
...
Idan mutane sun yi řidda, yana kamar sun sake giciye Yesu ne kuma. AT: "yana kamar sun sake giciye Ɗan Allah ne don kansu kuma"
Wannan wani laƙabi ne mai muhimmaci na Yesu da ke bayyana dangantakar shi da Allah.
Ana maganar gona da ke cin moriyar ruwan sama kamar mutum ne da ke shan ruwan sama. AT: "ƙasa da ke janye ruwan sama"
Ana maganar gona mai ba da amfani kamar yana haifar su ne. AT: "da ke ba da tsire-tsire"
AT: "ga waɗanda aka shirya masu gonar"
Ruwan sama da amfanin gona da muke gani suna tabbatar mana cewa Allah ya tallafi gonar. Ana maganar gona kamar mutum ne da ke iya karbar albarkun Allah.
A nan "albarka" na nufin tallafi da ga Allah, ba furcin kalmomi ba.
Ana maganar "la'antarwa" kamar wani wuri ne da mutum ke iya matsowa kusa da shi. AT: "yana hatsarin la'anta daga Allah"
Manomin zai ƙone kome da ke gonar"
Kodashike marubucin ya yi amfani da wannan wakilin suna "mu", yana maganar shi da kansa ne kurum. AT: "bani da shakka" ko kuma "ina da tabbaci"
Wannan na nufin cewa suna abubuwa fiye da waɗanda suka ƙi Allah, suka yi masa rashin biyayya, kuma ba za su sake iya tuba ba domin Allah ya gafarce su (Dubi: [6:4-6]) AT: "kuna yin abubuwa masu kyau fiye da abinda na ambata"
AT: "zancen ceton da Allah ke yi maku"
Wannan na iya nufin cewa Allah cikin ădalcinsa zai tuna da dukkan abubuwa masu kyau da jama'ar sa suka yi. AT: "Gama Allah mai ădalci haƙiƙa zai tuna"
"Sunar" Allah na nufin Allah da kansa. AT: "masa"
Kodashike marubucin ya yi amfani da wannan wakilin suna "mu", yana maganar shi da kansa ne kurum. AT: "ina da bukata ƙwarai"
kula, aiki tuƙuru
Za a iya karin bayanin ma'anar wannan a fili. AT: "zuwa ƙarshen rayuwarku"
"zuwa ga samun chikakken tabbaci na karɓan abinda Allah ya alkawarta maku"
Mai "koyi" mutum ne da ke kwaikawayon halayyar mutum.
Ana maganar karɓar alkwarin da Allah ya yi wa masubi kamar gadan dukiya ne ko kuma arziki na wani ɗan iyali. AT : "karɓi abinda Allah ya yi masu alkawari"
"Allah ya ce"
AT: "Zan baka zuriya masu yawa"
"alkwawrin da Allah ya yi masa"
Ana maganar mutanen da Allah ya masu alkwarai kamar za su gada dukiya ne ko kuma arziki ne na wani ɗan iyali. AT: "ga waɗanda za su karɓi abinda Allah ya alkawarta"
"cewa nufinsa ba zai ta taɓa sakewa ba" ko kuma "cewa zai riƙa yin abinda ya ce za yi a koda yaushe"
Wannan na nufin Alkawarin Allah da kuma rantsuwar Allah. Babu wanin su da zai iya sekewa.
Wannan na nufin cewa Allah ya faɗi gaskiya game da wannan yanayin. AT: "game da abinda Allah zai riƙa faɗin gaskiya a ko yaushe"
Ana maganar Masubi da ke dogara ga Allah domin ya ƙare su kamar guduwa ne zuwa wurin tsira. AT: "mu, da muke dogara gareshi"
Wato dogarar mu ga Allah kenan. AT: "za mu cigaba da dogara ga Allalh kamar yadda ya ƙarfafa mu mu yi"
AT: "da Allah ya sa a gabanmu"
Kamar yadda anka yake hana kwale kwale bijirewa a cikin ruwa, Haka Yesu yana kafe mu a gaban Allah. AT: "da ke sa mu rayu a kafe a gaban Allah"
Waɗannan kalmomi biyun a takaice suna da ma'ana guda, kuma suna nanata matuƙar tabbacin da ake da shi a kan anka. AT: "tabbaccen bege"
Ana maganar gabagaɗi ne a nan kamar wani mutum ne da ke iya shigo har cikin wurin mafi tsarki a haikali.
Wannan ne wurin mafi tsarki a cikin haikalin. Ana ɗaukan wannan wurin a matsayin wurin da Allah ya fi kasancewa a cikin jama'arsa. A wannan nassi, wannan na nufin sama, kursiyin Allah.
Wannan na nufin Almasihu a matsayin firist yana da halayya iri ɗaya da Malkisadak a matsyin firist. AT: "haka ma Malkizadak firist ne"
1Wannan ne Malkisadak, sarkin Salem, firist na Allah Madaukaki, wanda ya gamu da Ibrahim na dawowa daga yaki da wasu sarakuna ya kuma albarkace shi. 2Ibrahim ya ba shi ushirin dukkan ganimar da ya samu. Sunansa," Malkisadak," ma'anar itace, "Sarkin adalci," haka ma, "sarkin salem," ma'anar iitace," Sarkin salama," 3Bashi da uwa bashi da uba, ba shi da lissafin asalin zuriya, ba shi da farkon rayuwa ba shi da karshen rai. Shi firist ne na har abada, kamar Dan Allah.4Yanzu fa dubi irin girman wannan mutum. Kakan kakanninmu Ibrahim ya bada ushira ta abubuwan da ya samo na ganimar yaki gare shi. 5Kuma hakika, zuriyar Lawi da suka karbi aikin nan na firistanci suna da umarni daga shari'ar Allah cewa su karbi zakka a gun jama'a, wato, daga yan'uwan su Isra'ilawa, koda shike suma zuriyar Ibrahim ne. 6Amma Malkisadak, shi da ba zuriyar Lawi ba ne, ya karbi zakka daga Ibrahim, ya kuma albarkace shi, shi wanda ya ke da alkawarai.7Ba jayayya, karami shi ke karban albarka daga babba wanda ya girme shi. 8A wannan tsarin mutanen da ke karban zakka wata rana sai ka ga sun mutu, amma a wani kauli mutumin da ya karbi zakka a wurin Ibrahim, ance, wanzaje ne har yau. 9Kuma bisa ka'ida Lawi, wanda ke karban zakka, shi ma ya bada zakka ga Ibrahim, 10Saboda kuwa Lawi na cikin tsatson Ibrahim lokacin da Malkisadak ya gamu da Ibrahim.11Yanzu in da mai yiwuwa ne a sami kammala cikin aikin firistanci na Lawiyawa (domin ta wurin ta ne aka bada shari'a), to ina amfanin wani firist ya zo bisa ga ka'ida irin ta Malkisadak, ba'a kuma ambaci ka'idar Haruna ba? 12Don kuwa lokacin da aka canza firistanci, shari'a kuma dole ne a sauya ta.13Domin mutumin da aka fadi wadannan abubuwa a kansa na wata kabila ne, wadda ba wani mutumin da ya taba yin aiki a kan bagadi. 14Wannan a bayyane yake Ubangijinmu ya zo ne daga zuriyar Yahuza, kabilar da Musa bai taba anbatonsu game da zancen firistanci ba.15Abinda muke fadi a bayyane yake cewa, idan wani firist ya taso da kamanin Malkisadak. 16Wannan sabon firist, ba firist ne da ya taso bisa ga ka'idar zuriya ta yan'adam ba, amma ya zama firist ne ta rayuwa mai iko marar shudewa. 17Domin a rubuce yake cikin littafi ga me da shi; "Kai firist ne na har'abada bisa ga tsari irin na Malkisadak."18Domin doka ta fari an ajiye ta a gefe guda saboda rarrauna ce kuma marar amfani. 19Don kuwa shari'a ba ta iya kamalta kome. Amma fa a kwai bege mai kyau a nan gaba wanda ta gare shi ne zamu sami iso a gun Allah.20Kuma wannan kyakkyawan bege baya faruwa ba tare da rantsuwa ba, don kuwa su wadancan firistocin ba su dauki wata rantsuwa ba. 21Amma Allah yayi rantsuwa game da Yesu cewa, "Ubangiji ya rantse ba kuwa zai fasa tunaninsa ba; 'Kai firist ne har'abada.'"22Ta wurin haka Yesu ya bada tabbatacce da kuma ingataccen alkwari. 23Hakika, mutuwa ta hana firistoci su yi aiki har'abada. Wannan shi ya sa akwai firistoci da yawa daya bayan daya. 24Amma da shi ke Yesu na rayuwa ne har'abada, aikinsa na firist ba a musanya shi sam sam.25Domin haka kuma yana da cikakken ikon ceton wadanda ke gusowa ga Allah ta wurinsa, domin kullum a raye ya ke yana kuma roko dominsu 26. Domin irin wannan babban firist shi ne ya dace da mu. Ba shi da zunubi, marar abin zargi, tsarkakakke, kebabbe daga masu zunubi, ya na sama da sammai dukka.27Ba shi da bukata, kamar manyan firistoci, da ke mika hadayu kullum, da farko don zunubin kansu, sa'annan don zunubin jama'a dukka. Amma Yesu yayi wannan sau daya tak ba kari don kowa da kowa, yayin da ya mika kansa. 28Domin shari'a na nada mutane da ke da gazawa a matsayin firistoci, amma maganar rantsuwa, wadda ta zo a bayan shari'a, ta nada Dan, wanda ya ke cikakke har'abada.
Marubucin ya cigaba da kwatanta Yesu a matsayin firist da kuma Malkisadak a matsayin firist.
Wannan sunan wani gari ne.
Wannan na nufin lokacin da Ibrahim da mutanen sa suka je suka ci sojojin sarakuna huɗu da yaƙi domin su ceci danginsa Lutu, da iyalinsa
"ya ba wa Malkisadak"
"sarki mai adalci ... sarki mai salama"
Ana iya tunani daga wannan nassin cewa ba a taɓa haifan Malkisadak ba, balle ma a ce yă mutu. Amma, yana iya yiwuwa cewa marubucin na nufin cewa Littafi bai ba da wani bayani game da lissafin asalin sa, haifuwarsa, da mutuwarsa ba.
"Malkisadak"
Marubucin ya faɗa haka ne domin ba dukkan 'ya'yan Lawi ba ne sun zama firist. AT: "Zuriyar Lawi da suka zama firist"
"a gun mutanen Isra'ila"
Anan 'yan'uwansu" na nufin cewa dukkan su sun haɗa dangi ta wurin Ibrahim. AT: "daga danginsu"
...
...
Ana maganar abubuwan da Allah ya alkawarta zai yi wa Ibrahim kamar wasu abubuwa ne da ake iya mallaka. AT: "wadda Allah ya furta masa alkawaransa"
...
An yi amfani ne da waɗannan Jumaloli don a kwatanta Lawiyawa firistoci da Malkisadak. Harshen ku na iya samun wata hanyar nanata cewa marubucin yana kwatanci ne.
Ba a taɓa rubutawa a fili cewa Malkizadak ya taɓa mutuwa ba. Marubucin yana maganar rashin bayani game da rasuwar Malkizadak a littattafai kamar sanarwa ne cewa yana da rai har wa yau. AT: "littafi na nuna cewa yana da rai har wa yau"
Da shike ba a haifi Lawi ba tukuna, marubucin yana maganar sa ne kamar har yanzu yana cikin jikin Ibrahim. Ta haka ne marubucin yana bayar da hujja cewa Lawi ya ba da zakka ta wurin Ibrahim
Wannan ba ya nufin "a dai dai wannan lokacin", amma ana amfani ne da wannan a jawo hankali zuwa ga wata jawabinsa mai muhimmanci da ya biyo baya.
Wannan tambayan na nanata cewa ba a sa tsammanin cewa za a samu wani firist mai kama da Malkizadak ba. AT: "ba wanda zai bukaci samun firist da ke kamar Maikizadak, amma ba kamar Haruna ba, yă zo"
"yă bayyana"
Hakan na nufin cewa Almasihu a matsayin firist na da wasu halaye irin ta Malkizadak a matsayin firist. AT: "kamar yadda Malkizadak ma firist ne"
AT: "ba ka'idar Haruna kuma ba" ko kuma "wadda ba firist kamar Haruna ba"
...
Wato Yesu.
AT: "wadda nake magana a kai"
"Ubangijinmu" na nufin Yesu.
"daga kabilar Yahuza"
Amabacin da ke nan daga littafin Zabura ne na sarki Dauda.
"Muna iya fahimta har ma fiye sosai." Anan "mu" na nufin marubucin da masu sauraronsa.
"idan wani firist dabam ya bayyana"
Wannan na nufin cewa Almasihu a matsayin firist na da halaye iri ɗaya da Malkizadak a matsayin firist. AT: "kamar yadda Malkizadak ma dã firist ne"
"Zamar sa firist ba bisa ga ka'idar bane"
AT: "bisa ga ka'idan zuriyar 'yan'adam" ko kuma "ka'idar game da zaman firist daga zuriyar firstoci"
AT: "Domin an shaide shi ta wurin littattafai" ko kuma "Domin haka yake a rubuce game da shi a littattafai"
A nan "ajiye ta a gefe" karin magana ne da ake nufin marar amafani. AT: "Allah ya mayar da dokar ya zama marar amfani"
Ana maganar shari'a ne a nan kamar wani mutum ne da ke iya yin wani abu. AT: "ba wanda zai iya zama kamalalle ta wurin kiyaye doka"
AT: "Allah ya kawo bege mai kyau" ko kuma "Allah ya bamu dalilin kafa bege da gabagadi"
Ana maganar yi wa Allah ibada da kuma samun alherinsa cewa isowa gun sa ne. AT: "kuma saboda wannan bege ne muke zuwa gun Allah" ko kuma "kuma saboda wannan bege ne muke yi wa Allah sujada"
Kalmar nan "wannan" na nufin Yesu a matsayin firist na har abada abadin. Ana iya fassarawa a fillin mai rantsuwar. AT: "Kuma Allah bai zaɓi wannan sabon firist haka kurum ba ba tare da rantsuwa ba! ko kuma "Kuma domin Allah ya a ɗauki rantsuwa ne ya sa Ubangiji ya zama sabon firist ɗin!"
"ya faɗa mana cewa muna iya tabbatar da cewa za a samu wata ingantaccen alkawari"
Ana maganar aikin firist kamar wata kaya ce da Yesu ya mallaka. AT: "shi firist ne da dindindin"
Ana iya ƙarin bayani abinda "Don haka yana" ke nufi. AT: "Da shike Almasihu shi ne babban firist na mu da ke raye har abada, yana"
"waɗanda suka zo gun Allah ta dalilin abinda Yesu ya yi"
"Allah ya ɗaga shi zuwa saman sammai dukka. Marubucin na maganar mallakar girma da iko fiye da kowa ne kamar wani matsayi ne da ke sama da dukkan kome. AT : "Allah ya girmama shi, ya kuma bashi iko fiye da kowa"
A nan "shari'a" karin magana ce da ke nufin masu naɗa manyan firistoci bisa ga shari'ar Musa. Ba akan mutanen ake sa hankali ba, amma da tabbacin cewa sun yi haka bisa ga shari'a. AT: "bisa ga shar'a ne mutane sun naɗa mutane da ke da gazawa a matsayin manyan firistoci" ko kuma "gama bisa ga shari'a, mutane da ke gazawa ne aka naɗa a mastayin manyan firistoci"
"mutane da ke da gazawa a ruhaniya" ko kuma mutane raunana"
"maganar rantsuwa" na wakilcin cewa Allah wadda ya rantse. AT: "Allah ya naɗa Ɗan ta wurin rantsuwarsa, wadda ya yi bayan ya ba da shari'ar" ko kuma "bayan da ya bayar da shari'a, Allah ya ɗauki rantsuwa ya kuma naɗa Ɗansa"
AT: "wanda ya yi wa Allah biyayya gabaƙiɗaya ya kuma zama cikakke"
1Yanzu abin da muke kokarin cewa shine: Muna da babban firist wanda ke zaune a hannun dama na kursiyi mai martaba dake sammai. 2Shi kuwa bawa ne a wannan wuri mai tsarki, haikali na gaskiya wanda Allah ya shirya ba wani bil'adama ba.3Kowanne babban firist kuwa yana mika bayebaye da hadayu. Don haka ya kamata a sami abin hadaya. 4Da a ce Almasihu yana duniya ba zai zama firist ba ko kadan. 5Domin a kwai masu mika hadaya bisa ga shari'a. Suna hidimar misalin abubuwan da suke inuwar sama. Kamar yadda Allah ya yi wa Musa gargadi yayin da ya ke shirin gina Alfarwa: "Duba" Allah ya ce, "kayi komai bisa ga salon da aka koya maka a bisa dutse."6Amma yanzu hidimar da Almasihu ya karba ta dara tasu dukka, domin kuwa shine matsakancin muhimmin alkawari, wanda aka kammala a kan muhimman alkawura. 7Domin kuwa idan alkawarin fari ba shi da laifi babu anfanin neman alkawari na biyu.8Da Allah ya sami laifi akan mutane, sai ya ce "Zan sake sabon alkawari da gidan Isra'ila da kuma gidan Yahuza. 9kuma ba zai zama kamar yadda nayi da kakanninku ba, kamar yadda na rike su a hannu har Na fidda su daga kasar Masar. Basu kuma ci gaba da Alkawarina ba, ni kuwa na yi watsi da su," inji Ubangiji.10Gama wanna shine alkawarin da zan yi da gidan Isra'ila bayan wadannan kwanaki, Inji Ubangiji. Zan sa shari'a ta a bakinsu in kuma rubuta ta a zuciyarsu, Zan kuma zama Allah a garesu, su kuma su zama jama'ata.11Ba za su kuma koyar da makwabta ko yan'uwansu cewa, "ku san Ubangiji" gama dukkanin su za su san ni, daga karami har zuwa babba. 12Zan kuma nuna tausayi ga ayyukan su na rashin adalci, ba kuma zan kara tunawa da zunubansu ba.13A kan fadin "sabo" ya mayar da alkawarin fari tsoho. Wannan kuma da aka ambata tsoho na shirin bacewa.
Bayan da murubucin ya unan cewa firistancin Almasihu ya fi firistancin duniya, ya kuma nuna cewa firistancin duniya yana kamanta salon na sama ne. Almasihu yana da babbar hidima, babbar alkawali.
Wannan bai nuna cewa "a daidain wannan lokacin ba", amma anyi amfani ne da shi domin a jawo hankalinmu zuwa wani bayani da ke biye.
Ko da shike marubucin yana amfani da wakilin suna da ke nuna mutum fiye da ɗaya, "mu," ba shakka yana magana game da shi kansa ne kawai. AT: "Ina cewa" ko kuma "Ina rubutawa"
Zai zauna a "hannun dama na Allah" alama ce na nuna samun wata babbar girma da iko daga Allah. Duba yadda aka fassara wannan a [1:3]. AT: "ke zaune a wurin girma da iko a gefen kurusiyi mai martaba"
Mutane sukan gina haikali daga patan dabbobi, sai su manna shi a jikin wani katako, sai su shirya shi kamar wani bukka. A nan "haikali na gaskiya" na nufin haikali na sama da Allah ya ƙirƙiro"
AT: "Gama Allah yanan sa kowane firist ne"
"yadda Allah ya umarta a cikin shari'a"
Ana amfani ne da waɗannan kalmomi masu ma'anna kusan ɗaya ne domin nanata cewa haikalin misali ne kawai na ainihin haikalin da ke cikin sama. AT: "sifa marar cikakken bayani"
Marubucin yana maganar haikali da ke duniya, wadda yake misalin haikalin da ke sama ne kamar, hakan inuwa ne.
AT: "Yana daidai kamar yadda Allah ya yi wa Musa gargaɗi ne yayin da Musa ya ke"
Ba Musa ne ya yi alfarwar da kansa ba. Ya umarci mutane ne su yi shi. AT: "shirin umartar mutane su yi alfarwar"
"Ku tabbatar cewa"
"gă zane"
AT: "da ni na nuna maka"
Za ku iya ƙarin bayani cewa "dutsen" na nufin dutsen Sina'i . AT: "a bisa dutsen Sina'i "
"Allah ya ba Alamsihu"
Wannan na nufin cewa Almasihu ya sa muhimmin alkawari tsakanin Allah da mutane domin su rayu.
AT: "alkawari. Wannan shi ne muhimmin alkawari da Allah ya yi akan muhimman alkawura" ko kuma "alkawari. Allah ya yi alkawarin muhimman abubuwa da ya yi wannan alkawari"
Waɗannan kalmomi "fari" da kuma "biyu" jerin lambobi ne. AT: "tsohon alkawari ... sabon alkawari"
"yana kammalalle"
A wannan ambacin annabi Irimiya ya yi anabcin sabon alkawari da Allah zai yi.
"akan jama'ar Isra'ila"
"Duba" ko kuma "ku ji" ko kuma "ku kassa kunne ga abinda zan faɗa maku"
Ana maganar abin nan gaba kamar yana nufan mai magana. AT: "za a kai wani lokaci"
Ana maganar jama'ar Isra'ila da na Yahuza kamar gidaje ne. AT: "jama'ar Isra'ila tare da jama'ar Yahuza"
Wannan karin maganar na nufin matuƙar ƙauna da kulawar Allah. AT: "na fidda su daga Masar kamar yadda uba yake bi da ɗan yaron sa"
Ana maganar jama'ar Isra'ila kamar su wani gida ne. AT: "jama'ar Isra'ila"
"bayan wannan lokaci"
Ana maganar umarnan Allah kamar wasu abubuwa ne da ake iya sa wa a wuri. Ana kuma maganar iya tunanin mutane kamar wani wuri ne. AT: Zan sa su iya fahimtar shari'una"
A nan "zuciya" na nufin tunanin mutum. Jumlar nan "rubuta shi a zuciyarsu" karin magana ne da ke nufin ba da ikon sa mutane su yi biyayya da shari'a. AT: "Zan kuma sa a zuciyarsu" ko kuma "Zan ba su ikon iya yin biyayya da shari'a"
"Zan kuma zama Allah da suke bauta wa"
"su kuma zama jama'ar da nake kula da su"
AT: "Ba lallai su koyar wa makwabtansu ko 'yan'uwansu su san ni ba"
Waɗannan duka suna nufin Isra'ilawa
"san" a nan na nufin tunawa.
Wannan na nufin mutane masu aikata miyagun ayyuka"
A nan "tunawa" na nufin "tunani a kai"
'ya kusa gama ɓacewa" ko kuma "zai ɓace nan ba da daɗewa ba"
1To ko da alkawarin farko ma ya na da wurin sujada da kuma ka'idojin sujada a nan duniya. 2Domin a cikin alfarwar akwai daki da aka shirya, daki na waje wanda ake kira wuri mai tsarki. A wannan wuri akwai kebabbun fitilu, akwai teburi da kuma gurasa.3Kuma bayan labule na biyun akwai wani daki, wanda ake kira wuri mafi tsarki. 4Yana da bagadin zinariya domin turare. Yana kuma da akwatin alkawarin, wanda aka lailaye shi gaba daya da zinariya. A cikinsa a kwai kaskon zinariya dake dauke da manna, da sandar Haruna wadda tayi toho, da kuma allunan duwatsu na alkawarin. 5A sama da akwatin alkawarin akwai siffofin kerubobi masu daukaka da suke wa marfin jinkai inuwa, wadanda yanzu ba zamu iya yin bayani akansu ba daki daki.6Bayan an shirya wadannan abubuwa, firistocin alfarwar sukan shiga daki na wajen alfarwar akai akai suna aikin hidimominsu. 7Amma babban firist din ne kadai yake shiga daki na biyun, sau daya tak a shekara, kuma tilas sai tare da jinin hadaya domin kansa, da kuma domin laifuffukan mutane da a kayi ba dagangan ba.8Ruhu Mai Tsarki yana nuna cewar ba'a riga an bayyana hanyar zuwa wuri mafi Tsarki ba muddin alfarwar nan ta farko na a tsaye. 9Wannan ya zama bayani ne game da lokacin yanzu. Da kyaututtuka da hadayu dukka da ake mikawa basu iya sun kammala lamirin mai yin sujadar ba. 10Abinci ne da abin sha kawai wadanda aka hada da bukukuwan wanke wanke dabam dabam. Wadannan duka tsare tsare ne da aka shirya a dinga yi a zahiri har sai an shirya sabuwar ka'ida.11Almasihu yazo a matsayin babban firist na abubuwa masu kyau da suka zo, ta wurin alfarwa babba, kammalalla kuma mafi tsarki wadda ba hannuwan mutane suka gina ba, wadda ba ta wannan duniyar aka halicce ta ba. Amma almasihu ya zo a matsayin babban firist na abubuwa masu kyau da ke zuwa. 12Ba ta jinin awaki da 'yan, maruka bane, amma Almasihu da jininsa ya shiga wuri mafi tsarki sau daya tak domin kowa dukka ya karbo mana fansa ta har abada.13To idan jinin awaki da na bajimai da yayyafa tokar karsana bisa wadanda suka bata tsarkinsu yana tsarkake su ya wanke jikkunansu. 14To balle kuma jinin Almasihu, wanda ta wurin Ruhu madawwami ya mika kansa hadaya marar aibi ga Allah, wanda yake wanke lamirinmu daga matattun ayyuka domin muyi bautar Allah mai rai? 15Domin wannan dalili, Almasihu shine magamin sabon alkawari. Wannan kuwa ya kasance ne domin anyi mutuwar da ta 'yantar da wadanda ke karkashin tsohon alkawari daga sakamakon zunubansu, saboda wadanda Allah ya kira su karbi alkawarin gadonsu madawwami.16Gama duk inda wani ya rubuta wasiyya ya bari, dole ne a tabbatar da mutuwar wanda yayi wasiyyar nan. 17Gama sai inda akayi mutuwa ake amfani da wasiyya, amma ba ta da amfani idan wanda ya rubuta ta yana nan da rai.18Ko alkawari na farko bai tabbata ba sai tare da jini. 19Gama bayan Musa ya bada dukkan dokoki da ke cikin shari'ar ga dukkan mutanen, sai ya dauki jinin 'yan marukan da awakin, tare da ruwa, da jan yadi, da reshen itacen doddoya mai soso, ya yayyafa bisa mutanen da kuma littafin dokokin. 20Daga nan yace, "Wannan ne jinin alkawarin da Allah ya bayar da dokoki gareku."21Ta haka kuma, ya yayyafa jinin bisa alfarwar da dukkan kayayyakin da ke cikinta wanda ake hidimar firistanci da su. 22Kuma bisa ga shari'a, kusan komai da jini ake tsarkake shi. Idan babu zubar da jini to babu gafarar zunubi.23Saboda haka ya zama tilas wadannan kayayyaki na kwaikwayon abubuwan dake cikin sama a tsarkake su da hadayar dabbobi. Duk da haka abubuwa na sama dole a tsarkake su da hadaya mafi kyau. 24Domin Almasihu bai shiga cikin wuri mafi tsarki da aka yi da hannuwa ba, wanda kwaikwayo ne kawai na abin da ke na gaske. Maimakon hakan, ya shiga cikin samaniya da kanta, sa'an nan yaje gaban Allah domin mu.25Bai je wurin don ya mika kansa sau da yawa, kamar yadda firist din alfarwa yake yi ba, wanda yake shiga wuri mafi tsarki kowacce shekara da jinin wata dabba. 26Idan haka ne, to dole ke nan ya sha wahala akai akai tun farkon duniya. Amma yanzu sau daya ne tak aka bayyana shi a karshen zamanai domin ya kauda zunubi ta wurin mika hadayar kansa.27Kamar yadda aka kaddara wa kowa ya mutu sau daya tak, kuma bayan haka sai shari'a. 28Haka kuma Almasihu, wanda aka mika shi sau daya tak domin ya dauke zunuban mutane da yawa, zai kuma bayyana karo na biyu, ba domin yin aikin kawar da zunubi ba, amma domin ceton wadanda suke jiran zuwansa da hakuri.
Marubucin yana ƙarin bayani ne ga Yahudawa masubi cewa shari'ar da alfarwar Tsohon Alkawari misali ne kawai na sabuwar alkawari wanda shi ne mafi kyau.
Wannan na nuna wata sabuwar fanni na koyaswar.
Dubi yadda aka fassara wannan a [8:7]
"yana da cikakken ka'idodi" ko kuma "yana da dokoki"
Marubucin yana cigaba ne da tattaunawar daga [8:7].
An yi alfarwar and kuma shirya shi domin amfani. AT: "Isra'ilawan sun shirya alfarwar"
Dukkan waɗannan kayayyakin hidimar suna nan ne na musamman shi ya sa an morin kalmar nan "da" domin marubicin yana tsammanin cewa masu karatunsa sun riga sun san da waɗannan abubuwa.
AT: "gurasa da aka ajiye gaban Allah" ko kuma "gurasa da firist sukan miƙa wa Allah"
Labule na farkon itace sashi na wajen alfarwar ne, don haka, "labule na biyun" ita ce labulen da ke tsakanin "wuri mai tsarki" da kuma "wuri mafi tsarki"
Wannan shine kalmar kirgen lamba ta biyu.
"a cikin akwatin alkawarin"
Wannan ne sandar da Haruna ke da shi lokacin da Allah ya tabbatar wa jama'ar Isra'ila cewa ya zaɓi Haruna ta wurin sa sandar Haruna ta yi toho.
"wadda ganyayenta da fure suka yi girma"
A nan "duwatsu" wasu shimfiɗaɗɗun duwatsu ne da ke da rubutu a kan su. Wannan na nufin allunan duwatsu ne da aka rubuta dokoki goma a kai.
Da Isra'ilawan suke yin akwatin alkawarin, Allah ya umarce su su ƙera kerubobi biyu da ke fuskantar juna, da fuka-fukansu suna taɓa marfin jinƙan akwatin alkawarin. Ana maganar su ne a nan kamar suna ba wa akwatin alkawarin inuwa. AT: "kerubobi masu ɗaukaka masu rufe marfin jinƙai da fukafukan su"
A nan "kerubobi" suna nufin kerubobi biyu.
Kodashike marubucin ya yi amfani da kalmar nan "mu" da ke nufin fiye da ɗaya, ya fi dacewa a ce yana maganar kansa ne shi ɗaya. AT: "ba zan iya"
AT: "Bayan da firistocin sun shiya waɗannan abubuwa"
AT: "yakan kawo jinin"
Wato jinin bijimi da akuya da babban firist ke miƙa hadaya a rana ta yin kafara.
Wannan na iya nufin 1) ɗaki na ciki da ke cikin alfarwar da ke duniya ko kuma 2) Kasancewar Allah a sama.
Wannan na iya nufin 1) "ɗaki da ke wajen alfarwar na a tsaye" 2) "alfawar da ke dumiya da kuma yanayin hadaya da ke akwai"
"Wannan hoto ne" ko kuma "Wannan alama ce"
"na yanzu"
AT: "da firist ke miƙawa yanzu"
Marubicin yana maganar lamirin mutum kamar wani abu ne da ake iya sa ta tă daɗa kyau har ta zama ba laifi. Lamirin mutum shi ne sanin sa na abinda ke daidai da rashin daidai. Shi ne sanin sa ko ya aikata daidai ko bai aikata daidai ba. Idan ya san cewa ya yi ba daidai ba, muna cewa yana da laifi. AT: "basu iya sa mai ibada ya zama da rashin laifi"
Marubucin ya yi kamar yana maganar mutum ɗaya ne kawai mai yin sujada, amma yana nufin dukkan waɗanda suka taho su yi wa Allah sujada a alfarwa ne.
"har sai Allah ya yi sabuwar ka'idar"
"sabuwar alkawari"
Wannan ba kayan duniya ba ne. Amma yana nufin abubuwa masu kyau da Allah ya alkawarta a sabuwar alkawarinsa.
Wato gida da ke sama ko kuma alfarwa, wadda ya fi muhimmanci, kammalalle kuma fiye ma da alfarwar da ke a duniya.
AT: "wadda ba mutane ne suka gina ta ba"
A nan "hannuwa" na nufin mutum gabaɗaya. AT: "'yan'adam"
Ana maganar kasancewar Allah a sama ne a matsayin wuri mafi tsarki, ɗaki na ciki sosai na cikin alfarwar.
Firist ɗin zai yafa toka kaɗan a bisa jama'ar da suka ɓata tsarkinsu.
...
Marubucin yana amfani ne da wannan tambayan domin ya nanata cewa hadayar Almasihu shi ne mafi iko. AT: "To lallai jinin Almasihu zai tsarkakke lamirin mu har ma fiye daga matattun ayyuka zuwa bautar Allah mai rai! Domin ta wurin ruhu madawwami ne ya miƙa kansa marar aibi ga Allah"
Wannan wani ƙaramin zunubi ne ko kuma kuskure da ake maganarsu a nan kamar ƙaramin ɗigo da ba a saba ganin shi ba ko wani lahani a jikin Almasihu.
A nan lamiri na nufin yadda mutum ke jin alhakin laifi. Bai kamata masubi su ji alhakin zunubin da sun aikata a baya har yanzu ba domin Yesu ya ba da kansa hadaya ya kuma gafarce su.
A nan "tsarkake" na nufin ɗaukan mataki a kan nauyin da lamirin mu ke ji domin zunuban da muka aikata
Ana maganar halayen zunubi ne kamar sun zama na duniyar mattatu.
"Hakan ne ya sa" ko kuma "Saboda haka ne"
Wato Almasihu ne ya sa sabon alkawari tsakanin Allah da 'yan'adam ya kasance.
"don ɗaukan zunuban waɗanda suke ƙarƙashin alkawari na farko." Wannan na iya nufin 1) a nan "zunubansu" karin magana ne da ke nufin alhakin zunubansu" AT: "don ɗaukan alhakin waɗanda ke ƙarƙashin alkawarin farko" ko kuma 2) a nan "zunubansu" karin magana ne da ke nufin hukuncin zunubansu. AT: "ɗaukan hukuncin waɗanda ke ƙarkashin alkawarin farko"
AT: "waɗanda Allah ya zaɓa su zama 'ya'yansa"
Ana maganar karɓan abinda Allah ya alkawarta ne kamar gãdan dukiya ne da kuma arzikin na wani ɗan iyali.
Wannan wata takarda ce bisa tsarin doka da mutum ke sanar da mai mallakar dukiyarsa bayan ya rasu. Ana yin wannan sanarwar a rubuce.
AT: "dole ne wani ya tabbatar cewa wanda ya rubuta wanna wasiyar ha mutu"
AT: "Saboda haka, Allah ya tabbatar da alkawari na farkon ma tare da jini ne"
Firist ɗin yakan tsoma reshen itachen doddoya mai soso a cikin jinin da kuma ruwa sa'an nan ya jijjiga reshen itachen doddoyan domin ya yafa jinin da ruwan su zuzzuba a bisa littattafansu da kuma mutanen. Yayyafawar alama ce na abinda firist ke yi wanda ke nuna cewa dukkan fa'idodin alkawarin ya shafi mutanen da kuma abubuwan su. A nan samun karɓa da littattafan da mutanen ke da shi a wurin Allah sun sabunta kenan.
wani irin ciyawa ne mai ƙarfi da akan same shi da damina , ana amfini ne da shi a bukukkuwan suka shafi yayyafawa
A nan "jini" na nufin dabbobin da aka miƙa su hadaya domin su cika umurnin alkawarin. AT: "jinin da da ya tabbatar da alkawarin
"Musa ya yayyafa"
Yayyafawa alama ce da firistoci ke yi, ta wurin haka suke nuna cewa fa'idodin alkawarin sun shafi mutanen da kuma abubuwansu. Duba yadda aka fassara wannan a [:19]
kayayyakin da ake iya ajiye abubuwa a ciki. A nan tana nufin ko ma wane irin kayan girke-girke ko aiki. AT: "dukkan kayan girke-girke da ake amfani da su a hidimar"
AT: "da firistocin ke amfani da su cikin aikinsu"
Wato ana maganar sa abu ya zama karɓaɓɓe ga Allah a matsayin tsarkakken abu. AT: "firistoci suna amfani ne da jini domin su tsarkake kusan komai"
A nan "zubar da jini" na nufin mutuwar wani abu a matsayin hadaya ga Allah. Wannan na iya nufin cewa dukkan gafarar zunubi na zuwa ne ta wurin zuɓar da jini. AT: "Ana samun gafara ne kaɗai idan wani ya mutu a matsayin hadaya" ko kuma "Allah yana yafe wa kaɗai idan wani ya mutu a matsayin hadaya"
Ana iya bayyana ma'anan wannan a fili. AT: "gafarar zunuban mutane"
AT: "firistocin za su yi amfani da waɗannan hadayun dabbobin su tsarkake abubuwan da ke kwaikwayon abubuwa na sama"
Wato, fiye ma da hadayun da ake amfani da su don a tsarkake kwaikwayon da suke duniya. AT: "amma abubuwan da ke na sama da kansu, Allah ya tsarkake su da hadayu mafi kyau"
A nan "da hannuwa" na nufin "ta wurin 'yan'adam." AT: "wuri mafi tsarki, wadda 'yan'adam suka yi, kuma wanda"
"da ke wuri mafi tsarki"
"Bai shiga sama"
"kowace shekara"
wato da jinin wata dabba wanda aka azabtar, ba da jininsa ba.
"idan da hakane yakan miƙa kansa akai-akai"
kauda zunubi na nufin samun gafarar Allah. AT: "domin yă sa Allah ya gafarta zunubai ta wurin sadaukar da kansa" ko kuma "yă sadaukar da kansa domin Allah ya gafarta zunubi"
AT: "Almasihu ya miƙa kansa sau ɗaya tak"
Ana maganar sa mu mu zama mararsa zunubi a maimakon masu zunubi kamar zunubanmu wasu abubuwa ne da Almasihu ke iya ɗauka wa daga gare mu. AT: "domin Allah ya gafarta zunuban"
Anan "zunubai" na nufin laifin da mutane ke da shi a gaban Allah saboda zunuban da suka aikata.
1Domin shari'a hoto ce na kyawawan abubuwan da ke zuwa, ba ainihin siffar wadannan abubuwa ba. Wadanda ke gusowa kusa da Allah ba za su taba ingantuwa ta wurin hadayu da firistoci ke mikawa shekara da shekaru ba. 2In ba haka ba, ba sai a dena mika hadayun ba? Bisa ga wannan al'amari, inda sun tsarkaka sau daya tak da masu sujada ba su san menene zunubi ba. 3Amma wadannan hadayun sun zama matuni ne na zunubi shekara biye da shekara. 4Domin ba shi yiwuwa jinin bijimai da awakai su kawar da zunubai.5Yayin da Almasihu ya zo duniya, ya ce, "Ba hadayu da sadakoki kake marmari ba. Maimakon haka, ka shirya mini jiki domin hadaya. 6Baka murna domin sadakoki da hadayu na konawa domin zunubi. 7Sai na ce, 'Duba, gani na zo in yi nufinka, kamar yadda aka rubuta akaina.'"8Da fari Yace "ba hadayu, ko sadakoki, ko kuma hadaya ta konawa domin zunubi kake bukata ba. Ba ka kuwa jin dadinsu." Wadannan sune hadayun da ake bayarwa bisa ga shari'a. 9Sa'annan sai ya ce "gani na zo domin in aikata nufinka." Ya kawar da hidimar farko domin ya kafa hidima ta biyu. 10A hidima ta biyu, an kebe mu ga Allah ta wurin nufinsa ta wurin hadayar jikin Yesu Almasihu bugu daya ba kari.11Haka, kowanne firist ya ke tsayawa kulliyomi domin ya yi hidima ga Allah. A kullum yana mika hadayu, iri daya, koda shike ba za su taba kawar da zunubai ba. 12A ta wata hanya kuma, Almasihu ya mika hadaya sau daya tak domin zunubai har abada, ya zauna a hannun dama na Allah. 13Yana jiran har a maida makiyansa matashin sawayensa. 14Domin ta wurin hadaya guda dayan nan ya kammala har abada ga wadanda suka sadaukar da kansu ga Allah.15Kuma Ruhu mai Tsarki ya shaida mana. Abu na farko yace, 16"Wannan shi ne alkawarin da zan yi da su a bayan kwanakin nan,' inji Ubangiji Zan sa dokokina a cikin zukatansu, kuma zan rubuta su a lamirinsu.17Ba zan sake tunawa da zunubansu da kurakuransu ba." 18Yanzu fa duk in da aka sami gafara domin wadannan abubuwa, babu wata hadaya domin zunubi.19Saboda haka, yan'uwa, ba mu da shakkar shigowa wurin nan mafi tsarki ta wurin jinin Yesu. 20Wannan ita ce sabuwar rayayyar hanya da ya bude mana ta wurin labulen, wato ta wurin jikinsa. 21Saboda muna da babban firist a gidan Allah. 22Bari mu matso kusa da sahihiyar zuciya, da kuma cikakken gabagadi cikin bangaskiya, da zuciyarmu wadda aka tsarkake daga mummunan tunani, da kuma jikunanmu wankakku da ruwa mai tsabta.23Bari mu rike da karfi shaidar bangaskiyar begenmu, ba tare da raurawa ba, domin Allahn, da ya yi alkawari, mai aminci ne. 24Bari mu kuma yi lura yadda za mu iza juna ga kauna da ayyuka masu dacewa. 25Kada mu fasa zumunci da juna, kamar yadda wadansu sukan yi. A maimakon haka, bari mu karfafa juna a kulluyomin, kamar yada kuke ganin kusantowar ranan nan.26Saboda idan mun ci gaba da zunubin ganganci bayan mun rigaya mun sami wannan sanin gaskiyar, hadayar irin wannan zunubi bata samuwa. 27Maimakon haka, sai fargabar babban tsoron hukunci, da kuma wuta mai zafi, da zata cinye makiyan Allah.28Dukkan wanda ya ki bin dokar Musa zai mutu ba tausayi ta wurin shaidu biyu ko uku. 29Wanne irin hukunci kuke tsammani ya dace ga wadanda suka raina Dan Allah, duk wadanda suka maida jinin alkawarin nan kamar ba tsarkakakke ba, wanda ta wurin jinin nan ne aka kebe shi ga Allah- wadanda suka wulakantar da Ruhun alheri?30Domin mun san wanda yace, "Ramako nawa ne; Zan yi sakayya." Sa'annan kuma, "Ubangiji zai hukumta jama'arsa." 31Abin tsoro ne a fada cikin hannuwan Allah mai rai!32Amma ku tuna da kwanakin baya, bayan da ku ka sami haske, yadda kuka jure babban fama cikin wahala. 33Aka kunyatar da ku a gaban jama'a, ta wurin ba'a da cin mutunci, kuna kuma dandana irin azabar da wadansu suka shiga ciki. 34Domin kuna da tausayi ga wadanda suke kurkuku, da farin ciki, kun amince da kwace na dukiyarku da aka yi, kun mallaki madauwamiyar mallaka mafi kyau. Dominn kun ji tausayina sa'adda na ke a kurkuku.35Don haka kada ku yarda gabagadinku, wanda ke da babban sakamako. 36Domin kuna bukatar hakuri don ku sami abin da Allah ya alkawarta, bayan kun aikata nufinsa. 37"Domin a dan karamin lokaci, mai zuwan nan zai zo ba zai yi jinkiri ba.38Adalina kuwa zai rayu ta wurin bangaskiya. In kuwa ya ja da baya, ba zan yi farin ciki dashi ba." 39Amma mu bama cikin wadanda suka ja da baya zuwa hallaka. Maimakon haka, muna cikin wadanda suke da bangaskiya domin kula da rayukanmu.
Marubucin yana nuna gazawar shari'a da hadayu, dalilin da ya sa Allah ya ba da shari'a, da kuma kammalawar sabuwar firistanci da kama hadayar Almasihu.
Wannnan na maganar shari'a kamar ita wata hoto ce. Marubucin na nufin cewa ba shari'ar bane abu mai kyau da Allah ya alkawarta. Ya ɗan ambato kaɗan daga abubuwa masu kyaun da Allah zai yi.
"ba ainihin abubuwan da kansu ba"
"kowace shekara"
Marubucin yana amfani ne da wannan tambaya ya sanar cewa ƙarfin hadayun sun gaza. "da sun daina yin hadayun"
"tsayar da kasancewa"
A nan samun tsarkakewa nan nufin ba su kuma da wani hakin zunubi. AT: "da hadayun sun kau da zunuban su" ko kuma "Da Allah ya kawar masu da hakin zunubi"
"ba su san cewa suna da hakin zunubi ba" ko kuma "za su san cewa basu da wata hakin zunubi kuma"
Ana maganar zunubai ne kamar wasu abubuwa ne da jinin dabba ke iya kawar da su yayin da yake zubowa. AT "Gama ba shi yiwuwa jinin bijimai da awaki su sa Allah ya gafarta zunubai"
A nan "jini" na nufin mutuwar waɗannan dabbobi a matsayin hadayu ga Allah.
An faɗi maganar Almasihu alokacin da yake duniya a wata furucin da ke littafin Zabura da Dauda ya rubuta.
A nan "ka" na nufin Allah ne.
"ka shirya mini wata jiki"
Anan "na" na nufin Almasihu ne.
AT: "kamar yadda annabawa suka rubuta game da ni a Littafi"
Wato Littafin Masubi kenan ko kuma rubuce-rubuce masu tsarki.
Duba yadda aka juya waɗannan kalmomi a [10:5-6]
AT: "da firist ke bayarwa"
"Duba" ko "saurara" ko "Sa hankali ga abinda zan faɗa maka"
A nan "hidima" na nufin wata hanyar tuɓa daga zunubai. Ana maganar ƙin aikata shi kamar wani abu ne da ake iya kawar da shi. Ana maganar fara aikata shi na biyu kamar kafa wannan hidimar ne. AT: "Ya hana mutane miƙa hadayar zunubi a hanya ta farko domin ya miƙa hadayan zunuban a hanya ta biyun"
Kalmomin nan "farko" da "biyu" suna jerin kirge ne. AT: "tsohon hidima ... sabuwar hidimar"
AT: "Allah ya kaɓe mu" ko kuma "Allah ya miƙa mu ga kansa"
Ana iya bayyana kalmar nan "miƙa" da kalmomin nan "bayar" ko kuma "hadaya." AT: "domin Yesu Almasihu ya miƙa jikinsa hadaya" ko kuma "domin Yesu Almasihu ya yi hadaya da jikinsa"
"koda yaushe" ko kuma "kowace rana"
Wannan na maganar "zunubai" ne kamar su wasu abubuwa ne da ake iya kawar da su. AT: "ba za su taɓa iya sa Allah ya gafarta zunubai ba"
A zauna "a hannun dama na Allah" misali ne na samun matuƙar daraja da iko daga Allah. Duba yadda aka juya wannan jumlar a [1:3]. AT: "ya zauna a wurin daraja da iko a gefen Allah"
Ana maganar yadda Almasihu zai ƙasƙantar da maƙiyansa ne kamar za a mayar da su wuri ne da zai ajiye kafafunsa a kai. AT: "har sai Allah ya ƙasƙantar da maƙiyansa su zama kamar kujera da zai sa kafafunsa a kai"
AT: "waɗanda Allah yake tsarkekewa" ko kuma "waɗanda Allah ya miƙa su ga kansa"
"da jama'a ta" ko kuma "da mutane na"
"sa'anda lokacin alkawari na da mutane na ya kãre"
A nan "zukatan" na nufin hankalin mutum. Jumlar nan "sa su a cikin zuciyarsa" na nufin iza su su yi biyayya da dokokina. AT: "Zan iza su su yi biyayya da dokokina"
Wannan wata karin magana ne da ke nufin a sa mutane su fahimci doka. AT: "Zan iza su su fahimci dokokina"
"Ba zan tuna da zunubansu da kurakuran su kuma ba. To yanzu" ko kuma "Ba zan yi tunanin zunubansu da kurakuransu kuma ba. To yanzu" Ana iya ƙara bayanin sashin shaidar Ruhu Mai Tsarki na biyun [10:15-16] a fili a juyin ta wurin kammala furucin a karshen aya 16 da kuma fara wani sabuwar furuci a nan. AT: "Sa'annan ya ce, 'Zunubansu da kurakurasu ba zan tuna kuma ba.' To yanzu"
Kalmomin nan "zunubai" da "kurakuran" na da ma'ana ɗaya. Dukansu suna nanata yadda tsananin zunubin yake. AT: "An haramta abubuwan da suka aikata da kuma yadda suka ƙarya doka"
Wannan ba ya nufin "a daidai wannan lokaci", amma yana jan hankali ne zuwa ga wani abu mai muhimmanci da ke biye.
AT: "da Allah ya gafarta waɗannan abubuwan"
Ana iya canja fasalin wannan kalma "hadaya" zuwa "miƙa hadaya" AT: "mutane basu bukatar miƙa hadaya domin zunubi"
Wato dukkan masubin Almasihu kenan, maza da mata. AT: "maza da mata" ko kuma "'yan'uwa masubi"
Wato gaban Allah kenan, ba wai wuri mafi tsarki da ke tsohon alfarwar ba.
A nan "jinin Yesu" na nufin mutuwar Yesu kenan.
Wannan na iya nufin 1) sabuwar hanyar zuwa wurin Allah da Yesu ya zama sanadiyar sa masubi su rayu har abada. ko kuma 2) Yesu yana da rai, kuma ta wurinsa ne masubi ke zuwa gaban Allah.
Labulen da ke a haikalin duniya na wakilllcin maraban da ke tsakanin mutane da aihihin gaban Allah.
A nan "jikinsa" na nufin jikin Yesu kenan, jikinsa kuma yana nufin mutuwarsa. AT: "ta wurin mutuwansa"
Lallai ne a juya wannan a hanyar da zai bayyana a fili cewa Yesu ne wannan "babban firist."
"mai mulki a gidan"
Wannan na maganar jama'ar Allah kamar su ginannen gida ne. AT: "duk jama'ar Allah"
A nan "matso" na nufin yi wa Allah sujada, kamar yadda firist zai haura zuwa haikalin Allah ya miƙa masa hadayar dabbobi.
"da amintattciyar zuciya" ko kuma "da zuciya mai gaskiya." A nan "zuciya" na nufin manufa mai kyau da ƙarfafawar masubi. AT: "da gaskiya" ko kuma "a gaskiya"
"da kuma gabagaɗin bangaskiya" ko kuma "da matuƙar dogara ga Yesu"
AT: "kamar ya tsarkakke zuciyarmu da jininsa"
A nan "zuciya" na nufin lamiri, sanin abinda ke daidai da wanda ba daidai ba. Tsarkakewa na nufin samun gafara da kuma samun matsayin adalci.
...
AT: "kamar ya wake jikunanmu da ruwa mai tsabta"
Idan mau juyi ya fahimci wanna jumlar a matsayin baftismar Maibi, to ana nufin ainihin ruwa kenan, ba alama ba. Amma idan mai juyi na ɗauki ruwa a matsayin ainihin ruwa, to "tsabta" alama ce da ke nufin tsabta a ruhaniya da baftisma ke kawo wa. "Wankin" na nufin samun karɓa a gaban Allah na maibi.
A nan "riƙe da ƙarfi" karin magana ne da ke nufin ƙudiri da mutum ke yi na zuciya da yin abu ba tare da yarda yă bari ba. AT: "Bari mu ƙudura mu cigaba da faɗa wa mutane cewa muna da gabagaɗi domin mun gaskata Allah zai yi abin da ya alkawarta"
Ana maganar rashin tabbacin abu kamar shi wani abu ne dake kaɗawa daga wannan gefen zuwa wancan gefen. AT: "ba tare da rashin tabbaci ba" ko kuma "ba tare da shakka ba"
Ana iya bayyanawa a fili cewa jama'a sukan haɗu domin sujada. AT: "Kada mu daina tattaruwa domin yin sujada"
Anan maganar nan gaba kamar wani abu ne da ke matsowa kusa da mai magana. AT: "kamar yadda kun san cewa Allah zai dawo nan ba da jimawa ba" (Dubi: and
"mun san cewa muna yin zunubi amma duk da haka mun ci gaba da shi akai-kai"
Ana maganar sanin gaskiya kamar wani abu ne da wani ke ba wa wani. AT: "bayan mun san wannan gaskiya"
Gakiya game da Allah.
Babu wanda zai iya miƙa irin wannan sabuwar hadaya domin hadayar Almasihu ne kaɗai ke aiki. AT: "babu wanda zai iya miƙa irin hadaya da zai sa Allah yă gafarta zunubanmu"
A nan "hadayar irin wannan zunubi" na nufin "wata hanya mafi dacewa na miƙa hadayar dabbobi domin kawar da zunubai"
na hukuncin Allah, wato, cewa Allah zai hukunta.
Ana maganar fushin Allah kamar wata wuta ce da ke iya kona maƙiyansa.
Ana ɗaukan cewa wannan na nufin "ta wurin shaidu da basu ƙasa biyu ko uku ba"
Marubucin yanan nanata tsananin hukuncin waɗanda sun ƙi Almasihu ne. AT: "Wannan hukunci ne mai tsanani. Amma hukuncin ma zai fi tsanani ga duk ... alheri!"
AT: "suka ƙi Ɗan Allah"
Wannan wata laƙabi ne mai muhimmanci na Yesu.
Wannan na nuna yadda mutumin ya raina Ɗan Allah. AT: "ta wurin mai da jinin alkawali kamar ba tsarkakke be"
A nan "jini" na nufin mutuwar Almasihu, wadda ta wurinshi ne Allah ya kafa sabuwar alkawari.
AT: "jinin da ta wurin sa ne Allah ya keɓe shi"
"Ruhun Allah, mai tanadin alheri"
Ana maganar ramako kamar wani abu ne da ke na Allah, wanda yana da 'yancin yin yadda ya ga dama da abinda ke nashi. Allah yana da 'yancin ɗaukan ramako a kan maƙiyansa"
Ana maganar ɗaukar ramako kamar biyan wani abu mai hatsari ne da wani ya yi wa wasu.
Ana maganar gamuwa da horon Allah kamar mutum yă faɗa ne a hannun Allah. A nan "hannu"na nufin ikon hukunci na Allah. AT: "a gamu da hukuncin Allah"
"a lokacin da ya wuce"
Ana maganar samun gaskiya kamar Allah ya haska wata wuta ce ga mutum. AT: "bayan da kuka samu sanin gaskiya game da Amasihu"
"yawan wahala da kuka jure"
AT: "mutane suka kunyatar da ku, ta wurin yi maku ba'a da kuma cin mutuncin ku a gaban jama'a"
"kun haɗa kai da waɗansu"
Ana maganar madawamiyar albarkun Allah ne kamar wata "mallaka"
Ana maganar mutum marar gabagaɗi kamar dai mutumin zai yar da bangaskiyar ne, kamar yadda mutum yake yin banza da abin da ba shi da amfani. AT: "kada ku daina zama da gabagaɗi, domin za ku samu babban sakamako na zama da gabagaɗi" ko kuma "kada ku daina dogara ga Allah da gabagaɗi, wanda shi ne zai ba ku babbar lada"
Ana iya ƙara faɗin wannan a fili. AT: "Kamar yadda Allah ya faɗa a Littafi, 'Domin a ɗan karamin lokaci"
"nan da nan"
Wannan na nufin ko ma wanene daga cikin jama'ar Allah gabaɗaya. AT: "Mutane na masu aminci ... In kuwa ɗaya daga cikinsu ya ja da baya ... da mutumin" ko kuma "Mutane na ... in kuwa sun ja da baya ... da su"
A nan "na" da "zan" na nufin Allah kenan.
daina aikata abubuwan nagarta da yake yi
Ana maganar mutumin da ya rasa karfin ziciyar da bangaskiya kamar mutum ne da ke matsawa baya domin tsoron wani abu. Ana kuma maganar "hallaka" kamar wani wuri ne da ake iya zuwa. AT: "waɗanda sun daina dogara ga Allah, wanda zai sa shi ya hallaka mu"
Ana maganar rayuwa har abada da Allah kamar kula da ran mutun ne. A nan "rai" na nufin mutum gabaɗaya"
1Bangaskiya ita ce tabbatawar al'muran da muke begensu. Ita ce tabbatawar al'amuran da idanu basu gani. 2Domin ta wurin ta ne kakanninmu suka sami yardar Allah. 3Ta wurin ta ne aka hallicci duniya da umarnin Allah, har ma abubuwan da ake gani ba'a yi su daga abubuwan da suka kasance ba.4Ta dalilin bangaskiya ne Habila ya mikawa Allah hadaya da ta fi dacewa fiye da ta Kayinu. Don haka ne kuma aka yaba masa akan cewa shi adali ne. Ya sami yardar Allah sabili da sadakarsa da ya bayar. Don haka kuma, harwayau Habila yana magana, ko da shike ya rigaya ya mutu.5Ta dalilin bangaskiya aka dauki Anuhu zuwa sama domin kar ya ga mutuwa. "Ba a same shi ba kuwa, domin Allah ya dauke shi." Kamin a dauke shi an shaida da cewa ya faranta wa Allah zuciya. 6Zai yi wuya matuka a faranta wa Allah zuciya in ba tare da bangaskiya ba. Domin ya kamata dukkan wanda zai zo ga Allah, tilas ne ya bada gaskiya da kasancewar sa, kuma shi mai sakamako ne ga dukkan masu nemansa.7Ta dalilin bangaskiya Nuhu, ya karbi sako daga Allah akan al'amuran da ba'a gani ba, ta wurin girmamawa da rawar jiki. ya gina jirgin ruwa domin ya ceci iyalan sa. Dalilin haka kwa, Allah ya hallakar da duniya, Nuhu kwa ya gaji adalci wadda ke bisa ga bangaskiya.8Ta dalilin bangaskiya ne Ibrahim, sa'an da aka kira shi, ya yi biyayya sai ya tafi wurin da zai karba a matsayin gado. Ya kwa fita bai ma san inda za shi ba. 9Ta dalilin bangaskiya kuma ya zauna bare a kasar alkawari. Ya yi zama cikin Alfarwa tare da Ishaku da Yakubu, magadan alkawari guda tare da shi. 10Domin yana hangar birnin da ke da tushi, Birnin da mai zaiyanar sa da ginin sa shine Allah.11Ta dalilin bangaskiya, Ibrahim ya sami haihuwa ko da shike shi da matarsa Saratu sun yi nisa a cikin shekaru, kuma Saratu bakarariya ce, ta kuma wuce lokacin haihuwa. Tun da shike sun amince da wanda ya yi musu alkawari mai aminci ne. 12Sabo da haka, ta wurin mutumin nan daya, wanda ya ke kamar matacce ne, aka haifi zuriya mai dimbin yawa, su ka yawaita kamar taurari a sama kamar yashi a bakin teku, wanda ba shi kidayuwa.13Dukkan su kuwa suka mutu a cikin bangaskiya ba tare da sun karbi alkawarin ba. Maimakon haka, sun hango, kuma sun marabcesu daga nesa, sai suka amince su baki ne kuma matafiya ne a duniya. 14Gama wadanda suka yi furci haka sun nuna a fili cewa suna bidar kasa ta kansu.15Da kamar suna tunanin kasar da suka fita daga ciki, da sun sa mi damar komawa. 16Amma kamar yadda yake, sun bukaci kasa mafi dacewa, wato, wadda take a sama. Saboda haka ne Allah bai ji kunyar a kira shi Allahnsu ba, da shike ya shirya birni dominsu.17Ta dalilin bangaskiya ne Ibrahim, sa'adda aka yi masa gwaji, akan ya mika Ishaku dansa hadaya. 18Shi ne kuwa makadaicin dansa, wanda aka yi alkawari da cewa, "Ta wurinsa ne za a kira zuriyarka." 19Ibrahim ya yi tunani da cewa Allah na da ikon tada Ishaku ko daga cikin matattu ma, haka kuwa yake a misalce, daga matattun ne ya sake karbarsa.20Ta dalilin bangaskiya ne kuma Ishaku ya albarkaci Yakubu da Isuwa game da abubuwan da ke zuwa a gaba. 21Dalilin bangaskiya ne Yakubu, sa'adda yake bakin mutuwa, ya albarkaci 'ya'yan Yusufu dukkansu biyu. Yakubu ya yi ibada, yana tokare a kan sandarsa. 22Ta dalilin bangaskiya Yusufu, sa'adda karshensa ya kusa, ya yi magana game da fitar 'ya'yan Isra'ila daga Masar har ya umarce su game da kasussuwansa.23Ta dalilin bangaskiya Musa, sa'adda aka haife shi, iyayensa suka 'boye shi kimanin watanni uku domin kyakkyawan yaro ne shi, kuma basu ji tsoron dokar sarki ba. 24Ta dalilin bangaskiya ne kuma Musa, sa'adda ya girma, yaki a kira shi 'dan diyar Fir'auna. 25A maimakon haka, ya amince ya sha azaba tare da jama'ar Allah, a kan shagali da annashuwar zunubi na karamin lokaci. 26Ya fahimci cewa wulakanci domin bin Almasihu babbar wadata ce fiye da dukiyar Masar. Gama ya kafa idanunsa a kan sakamakon da ke gaba.27Ta dalilin bangaskiya Musa ya bar Masar. Bai ji tsoron fushin sarki ba, ya jure kamar yana ganin wannan da ba a iya ganinsa 28Ta dalilin bangaskiya ya yi idin ketarewa da kuma yayyafa jini, domin kada mai hallaka 'ya'yan fari ya taba 'ya'yan fari na Isra'ila.`29Ta dalilin bangaskiya suka haye baharmaliya kamar bushashiyar kasa. Sa'adda Masarawa su ka yi kokarin hayewa, bahar din ta hadiye su. 30Ta dalilin bangaskiya ganuwar Yeriko ta fadi, bayan sun kewaya ta har kwana bakwai. 31Ta dalilin bangaskiya Rahab karuwan nan bata hallaka tare da marasa biyayya ba, don ta saukar da masu leken asirin kasa a gidanta, ta kuma sallame su lafiya.32Me kuma za mu ce? Gama lokaci zai kasa mini idan zan yi magana game da Gidiyon, Barak, Samson, Yefta, Dauda, Sama'ila, da annabawa. 33Ta dalilin bangaskiya suka ci nasara kan kasashe, suka yi aikin adalci, sa'annan suka karbi alkawura. Suka rufe bakin zakuna, 34suka kashe karfin wuta, suka tsira daga bakin takobi, suka sami warkaswa daga cutattuka, suka zama jarumawan yaki, sa'annan suka ci nasara akan rundunar sojojin al'ummai.35Mata kuwa suka karbi matattunsu da aka tayar daga mutuwa. Aka azabtar da wadansu, ba su nemi yancin kansu ba, domin suna begen tashi daga mattatu. 36Wadansu kuwa suka sha ba'a da duka da bulala, har ma da sarka da kurkuku. 37A ka jejjefe su. Aka tsaga su kashi biyu da zarto. A ka karkashe su da takobi. Su na yawo sanye da buzun tumakai da na awaki, suka yi hijira, suka takura, suka wulakantu. 38Duniya ma ba ta dauke su a matsayin komai ba. Suka yi ta yawo a jazza, da duwatsu, da kogwanni, da kuma ramummuka.39Ko da yake mutanen nan amintattun Allah ne domin bangaskiyarsu, basu karbi cikar alkawarin ba tukunna. 40Domin Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau ba kuwa za su kammala ba sai tare da mu.
Marubucin ya faɗi abubuwa uku game da bangaskiya a wanna taƙaitaccen gabatarwa.
Ana amfani ne da wannan kalmar a nan domin a nuna canji daga ainihin koyarwa da ake yi. A nan marubucin ya fara bayyana ma'anan "bangaskiya".
AT: "Idan muna da bangaskiya, muna da tabbacin abubuwan da muke begensu" ko kuma "Bangaskiya ita cene abinda ke barin mutum ya sa zuciya da gabagaɗi a kan wasu abubuwa na musamman"
A nan wannan na nufin tabbacin alkawarai na Allah, musamman ma tabbacin cewa dukkan masubin Yesu za su kasance da Allah a sama har abada.
AT: "da har yanzu ba mu iya gani ba" ko kuma "da har yanzu ba su faru ba"
"Domin suna da tabbaci game da abubuwan da basu faru ba tukuna"
AT: "Allah ya yarda da kakanninmu domin suna da bangaskiya ne"
Marubucin yana magana ne da Ibraniyawa akan kakanninsu.
AT: "Allah ya hallic duniya ta wurin ba ta umarni ta kasance"
AT: "Allah bai halita abubuwan da muke gani daga abubuwa da ake gani ba"
AT: "Allah ya ce da shi mai adalci" ko kuma "Allah ya ce da Habila ma adalci ne"
Ana maganar karatun Littafi da yin koyi da bangaskiyar Habila ne kamar Habila ne da kansa yana kan magana. AT: "Harwayau muna koyi da abinda Habila ya yi"
AT: "Ta wurin bangaskiya ne Anuhu bai mutu ba domin Allah ya ɗauke shi"
Ana maganar mutuwa kamar wani abu ne da ake iya gani da ido. Wato a ɗanɗana mutuwa kenan. AT: "mutu"
AT: "kafin Allah ya ɗauke shi"
Wannan na iya nufin 1) "Allah ya ce Anuhu ya gamshe shi" ko kuma 2) "Mutane sun ce Anuhu ya gamshi Allah."
A nan ana amfani ne da wannan kalmar "to" domin a jawo hankali zuwa ga wata darasi mai muhimmanci da ke biye.
AT: "mutum na iya faranta wa Allah zuciya idan yana da bangaskiya ga Allah"
Ana maganar son yi wa Allah ibada da kuma zama ɗaya daga cikin jama'arsa kamar mutum yana ainihin zuwa gun Allah ne. AT: "cewa dukkan wanda yana son yă zama na Allah ne"
"yana saka wa duk masu"
Ana maganar waɗanda suke da sanin Allah suna kuma ƙoƙarin yi masa biyayya kamar suna neman su same shi ne.
AT: "domin Allah ya faɗa masa"
AT: "akan abubuwan da ba wanda ya taɓa gani" ko kuma "game da abubuwan da basu auku ba tukuna"
An an "duniya" na nufin mutanen duniya. AT: "jama'ar da ke duniya a wannan lokaci"
Ana maganar Nuhu kamar ya gãji dukiya ne da arziki da wani ɗan iyali. AT: "ya samu adalcin Allah"
"wadda Allah ke ba wa waɗanda ke da bangaskiya gare shi"
AT: "sa'an da Allah ya kira shi"
"bar gida zuwa wurin"
Ana maganar ƙasa da Allah ya alkawarta zai ba wa Ibrahim ne kamar wata gãdo ce da zai karɓa. AT: "da Allah zai ba shi"
"Ya kuwa bar gidansa"
Ana iya amfani da wasu kalmomi da za su nuna cewa "alkawari" ɗin na nufin an "alkawarta." AT: "ya zauna bare a ƙasar da Allah ya alkawarta masa"
"magada tare." Wannan na magana game da Ibrahim, Ishaku, da Yakubu ne kamar su magada ne da za su karɓi gãdo daga gun ubansu.
"birini mai tushe." Mai tushe na nufin birni da ke dawamamme. AT: "birnin har abada"
"wadda Allah ne ya zanata ya kuma gina" ko kuma "wadda Allah ne zai zana ta yă kuma gina"
mutum mai zana gine gine da kuma birane
Ana iya juya kalmar nan "bangaskiya" zuwa "gaskata". Wannan na iya nufin 1) Ta dalilin bangaskyar Ibrahim ne" AT: "saboda Ibrahim ya gaskata da Allah ne" ko kuma 2) ta dalilin bangaskiyar Saratu ne. AT: "saboda Saratu ta gaskanta da Allah ne"
"ya iya samun ya zama uba" ko kuma "ya iya samun ɗa"
"domin ya gaskanta da Allah ne, wadda ya ba da wannan alkawari, amintacce ne"
"ya wuce shekarun samu 'ya'ya" ko kuma "tsoho ne ƙwarai"
Wannan na nufin cewa Ibrahim na da zuriya da yawa kenan.
Wannan na nufin cewa kamar yadda akwai yashi sosai a bakin teku, babu mai iya ƙidaya su duka, Ibrahim yana da zuriya da yawa da babu mai iya ƙirga su dukka.
Wannan na maganar alkawaran kamar wasu abubuwa ne da mutum ke karɓa. AT: "ba tare da karɓar abinda Allah ya alkawartar masu ba"
Anan maganar alkawarin da ke nan gaba ne kamar matafiya ne da ke zuwa daga nesa. AT: "bayan sanin abinda Allah zai yi masu nan gaba"
"sai suka amince" ko kuma "sai suka amsa"
A nan "baƙi" da "matafiya" na nufin abu ɗaya ne a takaice. Wannan na nanata cewa wannan duniya ba gidansu ta ainihi ba ce. Suna dai jiran gidansu ta ainihi da Allah zai gina masu.
"ƙasa da za ta zama ta su"
"wadda take ƙasar sama" ko kuma "ƙasa sa sama"
AT: "Allah yana jin daɗi su ce da shi Allahnsu" ko kuma "Allah yana fahariya su ce da shi Allahnsu"
AT: "sa'ad da Allah ya gwada shi"
AT: "wanda Allah ya faɗi"
A nan "kira" na nufin a sanya ko kuma naɗa. AT: "cewa ni zan naɗa zuriyarka"
"Allah na da iko ya sa Ishaku ya rayu kuma"
A wannan aya, "yă tada" na nufin ya sa masa rai. Kalmomin nan "daga matattu" na maganar dukkan matattu gabaɗaya a ƙarƙashin ƙasa.
"a wata yanayin magana." Wannan na nufin cewa a fahimci abinda marubucin zai faɗa kuma ba zahiri ba ne amma karin magana ne. Allah bai tada Ishaku daga matattu a zahiri ba. Amma domin daidai lokacin da Ibrahim zai miƙa hadayar Ishaku sai Allah ya hana shi, to wannan kamar Allah ya tada shi daga mattatu ne.
"daga matattun ne"
"Ibrahim ya sãke karɓar Ishaku"
"Yakubu ya yi wa Allah ibada"
A nan "ƙarshensa" wata hanya ce na maganar mutuwa. AT: "sa'ad da ya yi kusa da mutuwa"
"ya yi maganar lokacin da 'ya'yan Isra'ilawa za su bar ƙasar Masar"
"Isra'ilawa" ko kuma "zuriyar Isra'ila"
Yusufu ya mutu yayin da yake ƙasar Masar. Yana son mutanensa su ɗauki kasusuwansa tare da su a lokacin da za su bar ƙasar Masar domin su bizne ƙassusuwansa a ƙasar da Allah ya yi masu alkawari.
AT: "Musa, iyayensa sun ɓoye shi kimanin watani uku bayan haifuwarsa"
"ya zama babba"
AT: "ya ƙi mutuane su ce da shi"
Ana iya juya wannan kalma "wulakanci" zuwa "rashin bangirma." AT: "rashin samun girma da ga gun mutane domin ya aikata abinda Almasihu ke so"
Ana maganar biyayya da Almasihu kamar binsa ne zuwa wata hanya.
Ana maganar sa hankali gabaɗaya ga cimma burin samun wani abu kamar mutum yana zuba wa abun ido ne har ma ya ƙi yă kalli wani wuri.
Ana maganar Musa ne kamar ya ga Allah, wadda ba a iya gani.
"wanda ba mai iya gani"
Wannan itace Idin Ƙeterewa na farko. Musa ya yi wannan ta dalilin yin biyayya ne da umarnin Allalh game da Ƙeterewar da kuma umartar mutanen su riƙa yin haka a kowace shekara. AT: "ya umarce mutanen su yi biyayya da umarnin Allah game da ƙeterewar da kuma yayyafa jini a kofofinsu" ko kuma "ya kafa Ƙeterewar da kuma yayyafa jini"
Wannan na nufin umurnin Allah ga Isra'ilawa cewa su kashe ɗan tinkiya sai su yafa jininsa a bisa kofofin kowane gida da Isra'ilawan ke zama. Wannan zai hana mai hallakar da 'ya'yan su na fari. Wannan yana ɗaya daga cikin dokokin Ƙeterewar.
A nan "taɓa" yana nufin a yi rauni ko a yi kisan wani. AT: "ba zai jawo rauni ba" ko kuma "ba zai kai ga kisa ba"
A nan kalmar nan "su" na farko na nufin Isra'ilawa, "su" na biyun na nufin "Masarawa", "su" na ukun na nufin ganuwan Yerico.
"Isra'ilawa suka haye Bahar Maliya"
AT: "ruwan ta haɗiye Masarawan"
AT: "Isra'ilawan suka riƙa tafiya suna zagaya ta har kwana bakwai"
"kwana 7"
"da salama ta karɓi masu lekan asirin"
Marubucin yana amfani ne da wannan tambayan don ya nanata cewa akwai misalai da dama da zai iya ambatowa. AT: "Har yanzu akwai misalai da dama".
"ba ni da lokaci isasshe"
Wannan sunan wani mutum ne.
A nan "su" ba ya nufin kowane mutum da aka ambata a 11:32 ya yi dukkan abubuwan da marubucin zai ambato. Marubucin yana dai cewa ga irin abubuwa da waɗanda ke da bangaskiya suka iya yi. AT: "Ai ta dalilin bangaskiya ne mutane kamar haka"
A nan "masarautai" na nufin mutanen da ke zama a wurin. AT: "suka yi nasara da mutanen wasu masarautai"
Waɗanna wasu hanyoyi ne kullum da Allah ke cetas da masubi daga mutuwa. AT: "Zakuna basu cinye su ba, wuta bai ƙone su ba, abokan gabansu basu kashe su ba. Suka"
AT: "samu warkaswa daga gun Allah" (Dubi:
"sa'an nan suka zama jarumawan yaƙi suka kuma ci nasara"
Ana iya sanar da wannan ba tare da an ambaci "tayar" ba. AT: "Mata kuwa suka karɓi matattumsu da rai waɗanda sun mutu"
Ana ɗaukan cewa maƙiyan su na iya sake su daga kurkuku bisa ga wasu ka'idodi. AT: "Wasu sun gwammaci su sha azaba da a sake su daga kurkuku" ko kuma "Wasu sun bar maƙiyansu su sa su su sha azaba da su yi abinda maƙiyan ke so su yi don a sake su"
a sa mutum ya sha wahala da zafi ƙwarai da gaske a hankali da kuma a jiki
Wannan na iya nufin 1) Waɗannan mutane za su ɗanɗana rayuwa mafi kyau a Sama har ma fiye da wanda sun ɗanɗana a nan duniya, ko kuma 2) waɗannan mutanen za su sami tayarwa mafi kyan sosai fiye da waɗanda basu da bangaskiya. Masu bangaskiya za su yi rayuwa tare da Allah har abada. Waɗanda ba su da bangaskiya kuma za su yi rayuwa a raɓe nesa da Allah.
AT: "Mutane kuwa suka yi wa wasu ba'a suka bulalesu ... Mutane suka jefe wasu da duwatsu. Mutane suka tsaga wasu kashi biyu da zarto. Mutane suka karkashe wasu da takobi"
AT: "Allah ya gwada wasu ta wurin barin maƙiyansu su yi masu ba'a, su kuma bulale su, har ma su ɗaure su da sarƙoƙi su kuma jefa su a kurkuku"
"suna tafiya nan da can" ko kuma "rayu kowane lokaci"
"suna sanye da fatan tumaki da na awaki ne kurum"
"ba su da komai" ko kuma "cikin talauce ƙwarai"
A nan "duniya" na nufin mutane. AT: "Mutanen duniyan nan basu cancanci"
Ya zama haka ne domin sun rasa wurin zama ne.
"kogwanni, wasu kuma sun yi zama a ramummuka a cikin ƙasa"
AT: "Allah ya daraja dukkan waɗannan saboda bangaskiyarsu, amma su kansu basu karɓi abinda Allah ya alkawarta ba tukuna"
Wato "alkawarin da Allah ya yi masu"
AT: "domin Allah ya kammala mu tare da su gabakiɗaya"
1Da shike muna kewaye da wannan irin kasaitaccen taro na shaidu, sai mu watsar da dukkan abubuwan dake nawaita mana da kuma zunubin da zai saurin makale ma na. Bari a cikin hakuri mu yi tseren da ke gabanmu. 2Bari mu kafa idonmu ga Yesu, wanda shine mafarin bangaskiyarmu da cikarta. Wanda sabili da murnar da a ka sa a gabansa ya jimre giciye, ya kuma yi watsi da kunyarsa, wanda kuma ya zauna a hannun dama na kursiyin Allah. 3Ku dube shi wanda ya jimre irin wannan adawa daga masu zunubi, domin kada ku gaji ko ku karai.4Ba ku yi tsayayya ko jayayya da zunubi har ta kai ga zub da jininku ba tukunna. Kun kuma manta da gargadin da a ka yi maku a matsayin 'ya'ya: 5"Dana, kada ka dauki horon Ubangiji da wasa, kadda kuma ka yi suwu lokacin da ka sami horonsa," 6Domin kuwa Ubangiji yana horon dukkan wadanda yake kauna, yana kuma hukunta duk wadanda ya karba.7Ku daure wahala a matsayin horo. Allah yana yi da ku kamar 'ya'yansa, domin kuwa wanne da ne wanda ubansa bazai yi masa horo ba? 8Amma idan baku da horo kamar yadda sauran mutane ke da shi, kun zama shegu kenan ba 'ya'ya ba.9Hakannan kuma kamar yadda muke da iyaye a duniya wadanda suke yi mana horo, kuma muna basu daraja. To ba sai mu yiwa Ubanmu na Ruhaniya biyayya don mu rayu ba? 10Ta wani fanni kuwa iyayenmu suna yi mana horo na kwanaki kadan bisa ga yadda suka ga ya dace, Amma Allah kuwa yana yi mana horo domin anfanin kanmu, domin kuma mu sami rabo daga cikin tsarkinsa. 11Ba horon da ke da dadi a lokacin yinsa, amma sai zafi. Sai dai kuma bayan haka yakan haifar da 'ya'ya na ruhaniya da kuma adalci ga dukkan wadanda aka yi rainonsu a ciki.12Don haka sai ku karfafa hannayenku da ke reto, da kuma guwawunku da ke kaduwa. 13Ku bi hanyoyi mikakku domin abin da ya gurgunce kada ya karye amma ya warke.14Ku bidi salama da kowa, da kuma rayuwar tsarki wanda in ba tare da shi, babu wanda zai ga Allah. 15Ku mai da hankali domin kada waninku ya rasa, alherin Allah, kuma kada wani tushe mai daci ya tsiro a cikinku har ya haifar da fitina, domin kada da dama daga cikinku su gurbata ta wurinsa. 16Ku yi hankali kuma kada a sami mazinanci ko marar ibada a cikinku, kamar Isuwa, wanda sabili da abinci ya sayar da 'yancinsa na dan fari. 17Kun kuwa san cewa sa'adda ya yi marmarin ya gaji albarka a gaba, an kishi, domin kuwa bai sami damar tuba ba, ko da shike ya nema har da hawaye.18Domin kuwa baku zo ga dusen da ake tabawa da hannu ba, dutse ne mai ci da wuta, da tukuki da bakin hayaki da hadari. 19Ba Ku zo ga karar kaho mai ban razana da murya mai firgitarwa ba, da masu sauraro suka yi roko kar su sake jinta. 20Don basu iya jimre abin da aka yi doka a kan saba: "koma dabba ce ta taba dutsen, sai a jejjefe ta." 21Abin tsoro ne kuwa kwarai, har Musa yace, "A tsoroce nake kwarai har na firgita."22Maimakon haka kun zone ga Dutsen Sihiyona da kuma birni na Allah mai Rai, kuma na Urushalima ta Samniya, da kuma dubun dubban mala'iku cikin murna da farin ciki. 23Kun zo taro na dukkan 'ya'yan fari, rubuttatu a sama, kuma kun zo ga Allah wanda shine alkalin dukka, hakannan kuma zuwa ga ruhu na adalai wanda a ka rigaya aka tsarkake. 24Kun zo ga Yesu, wanda shine matsakancin sabon alkawari, kuma ga jinin yayyafawa da ke magana fiye da na jinin Habila.25Ku yi lura kada ku ki wannan da ke yi mu ku magana. Gama in har basu kubuta yayin da su ka yi jayayya da wanda ya yi mu su gargadi a duniya ba, balle ma mu ba za mu kubuta ba in mun ki wanda ke mana gargadi daga sama. 26A wani karo, muryar sa ta girgiza duniya. Amma yanzu yayi alkawari da cewa, "Har'ila yau ba duniyar kadai zan girgiza ba, amma har da sammai."27Wannan kalma, "Harl'ila yau," ta bayyana cirewar abubuwan nan da za su girgizu, wato abubuwan da a ka halitta, domin abubuwan da ba zasu girgizu ba su kasance. 28Don haka, samun mulkin da ba za ya girgizu ba, sai mu zama masu godiya, kuma a cikin wannan yanayi mu yi wa Allah sujada cikin daraja da tsaninin gimamawa. 29Domin kuwa Allahnmu wuta ne mai konewa.
Saboda yawan masubi da ke Tsohon Alkawari, marubucin yana maganar rayuwar bangaskiya da masubi za su yi da Yesu a matsayin wanda za su bi gurbinsu.
Kalmar nan "mu" na nufin marbucin da masu karatunsa ne. Kalmar nan "ku" na nufin masu karatu.
Marubucin yana magana game da masubi na Tsohon Alkawari ne kamar su kasaitaccen taron shaidu ne da ke kewaye da masubi na yau. AT: "irin wannan kasaitaccen taron shaidu da ke kewaye da mu" ko kuma "akwai misalai da yawa na mutane masu aminci da muke iya yin koyi da su a Littafi"
A nan "shaidu na nufin masubi na Tsohon Alkawarii da ke sura 11 da suka yi rayuwa kafin tseren bangaskiya da masubi ke yi a yau.
A nan ana maganar "nawaita" da "zunubin da zai saurin maƙale" kamar mutum na iya cire su yă ajiye.
Ana maganar halaye ko kuma ra'ayoyin da ke iya hana masubi gaskata Allah ko yi masa biyayya ne kamar wasu kaya ne masu nauyi da za su sa yă zama da wuya mutum yă ɗauka yayin da yake tsere.
Ana maganar zunubi ne kamar wani taru ne ko wani abu daban da zai iya sa mutane su faɗi. AT: "zunubin da ke sa bin Allah yă zama da wuya"
Ana maganar bin Yesu kamar wasan tsere ne. AT: "Bari mu cigaba da biyayya da abin da Allah ya umarce mu, daidai kamar yadda mai tsere ke cigaba da gudu har sai wasan ya ƙare.
Yesu ne ke bamu bangaskiya, yana kuma cika bangaskiyarmu ta wurin kai mu ga cimma burinmu. AT: "mai ƙirƙiro da kammala bangaskiyarmu" ko kuma "wanda ke sa mu iya samun bangaskiya daga farko zuwa ƙarshe"
Ana maganar murnar da Yesu zai samu kamar Allah Uba ne ya sa a gabansa a matsayin burin cikawa.
Wannan na nufin cewa bai damu da kunyar mutuwa a bisa giciye ba.
Zama a "hannun damar Allah" alama ce ta samun girma da iko daga Allah. Dubi yadda aka fassara irin wannan jumlar a [1:3]. AT: "ya zauna a wurin girma da ikɔ a gefen kurusiyin Allah"
AT: "fid da zuciya"
A nan, ana maganar zunubi kamar wani mutum ne da ke faɗa a yaƙi. AT: "Ba ku riga kun jure hare haren masu zunubi ba tukuna"
Ana maganar ƙin abokan hamayya har mutuwa ne kamar mutum ya kai ga mutuwa.
A nan "jini" na nufin mutuwa. AT: "mutuwa"
Ana maganar littafin Tsohon Alkawari kamar wani mutum ne da ke iya ƙarfafa wasu. AT: "abinda Allah ya gargaɗe ku a Littafi yă ƙarfafaku"
Wato duk wanda ke na Allah ne maza da mata. AT: "a matsayin 'ya'ya ... Ɗana ... kowane ɗa"
A nan, marubucin yana ambacin wannan maganar ne daga littafin Karin Magana a Tsohon Alkawari.
AT: "ka ɗauke horon Ubangiji da muhimmanci, kuma kada ka gaza"
"kada kuma ka fid da zuciya"
AT: "yana horas da kai"
"duk wanda ya karɓa a matsayin ɗansa"
"kă sani cewa a lokacin wahala Allah yana horas da mu ne"
Wannan yana kwatanta yadda Allah ke horas da mutanensa da yadda uba ke horas da nasa 'ya'ya. Ana iya bayyana wannan a fili. AT: "Allah yana yi da ku kamar yadda uba ke yi da 'ya'yansa"
Dukkan inda aka mori waɗannan kalmomi suna nufin maza da mata. AT: "'ya'ya ... ɗa"
Marubucin ya isar da saƙo da wannan tambayar cewa duk uba na kirki yana horas da 'ya'yansa. AT: "kowane uba yana horas da 'ya'yansa!"
AT: "don haka idan Allah bai horas da ku ba kamar yadda yake horas da duk 'ya'yansa"
Ana maganar waɗanda Allah ba ya horas da su kamar su 'ya'ya ne waɗanda aka haife su ga uba da uwa da ba su yi aure ba.
Marubucin yana amfani ne da wannan maganar domin yă nanata cewa yakamata mu yi wa Allah Uba biyayya. AT: "Saboda haka, sosai ma, sai mu yi wa Uban ruhohinmu biyayya mu rayu."
Wannan karin magana yana nuna bambancin "ubanni na jiki." AT: "Uban mu a ruhu" ko kuma "Ubanmu da ke cikin sama"
"domin mu rayu"
Ana maganar "tsarki" kamar wani abu ne da mutane ke iya raɓa, ko kuma ke iya samu. AT: "domin mu zama da tsarki kamar yadda Allah ke da tsarki"
"'ya'ya" a nan na nufin "sakamako" ko kuma "abinda yake kawowa". AT: "yakan haifar da kwanciyar hankali na adalci" ko kuma "yakan haifar da adalci, wadda ke kawo salama"
"waɗanda aka yi rainonmu ta wurin horaswa." Ana maganar horaswa ko kuma gyara da Allah ke yi kamar Allalh ne da kansa. AT: "waɗanda Allah ya yi rainonsu ta wurin horas da su"
Yana iya yiwuwa cewa wannan ya cigaba ne da maganar tseren da ke a [12:1]. Haka nan ne marubucin yake magana game da yin rayuwa a matsayin masubi da kuma taimakon juna.
Ana maganar rayuwa da ke girmama Allah da kuma gamsar Allah kamar wata miƙaƙƙiyar hanya ce da ake bi.
A wannan karin maganar tseren, "gurgu" na nufin mutumin da ke tseren da ya ji rauni kuma yana son yă bari. Wannan dai har yanzu na nufin masubi da kansu. AT: "duk wanda ya gaji kuma yana son yă bar tseren ba zai ƙarye idon kafansa ba"
Ana maganar mutumin da ya daina yi wa Allah biyayya kamar ya ji ciwo ne a kafar sa ko kuma a idon kafarsa a kan hanya. AT: "ba zai ƙarye idon kafarsa ba"
AT: "a maimakon haka, zai zama da ƙarfi" ko kuma "a maimakon haka, Allah zai warkar da shi"
Ana maganar "salama" kamar wani abu ne da sai mutum ya nema. AT: "Ku yi ƙoƙari ku zauna lafiya da kowa"
Ana iya bayyana wannan a matsayin karfafawa. AT: "kuma ku yi ƙoƙari ku yi rayuwar tsarki, domin masu tasrki ne kaƙai za su ga Allah"
Ana iya bayyana wannan a fili. AT: "kuma ku nemi zaman tsarki"
"ba wanda zai karɓi alherin Allah sa'an nan ya bar shi ko kuma "ba wanda ya ke ƙin alherin Allah bayan ya riga ya dogara gareshi"
Ana maganar halin ƙiyayya ko fushi kamar wata tushe ne mai ɗaci. AT: "kada wanin ko yă zama kamar jijiya mai ɗaci, wadda idan ta yi girma takan kawo damuwa tana kuma jawo wa mutane da yawa illa"
AT: "mahaifinsa, Ishaku, ya ƙi ya sa mashi albarka"
AT: "domin kuwa bashi da damar tuba" ko kuma "domin kuwa bashi yiwuwa yă canza ra'ayinshi"
A nan "ya" na nufin Isuwa ne.
AT: "Domin baku zo, kamar yadda mutanen Isra'ila suka zo, ga dutsen da ake iya taɓawa da hannu ba"
Wannan na nufin cewa masubin Almasihu ba su zo ga dutse kamar Dutsen Sina'i da mutum ke iya taɓawa ko gani ba. AT: "da mutum ke iya taɓawa" ko kuma "da mutane ke iya gani da hankalinsu"
"Ba ku riga kun kai gun da ke da ƙaran ƙaho mai ƙarfi ba"
A nan "murya" na nufin wani na magana. AT: "ko wurin da Allah na magana a wata hanya da waɗanda suka ji shi sun roƙe shi kada yă ƙara yin magana da su haka"
AT: "abinda Allah ya yi doka"
AT: "sai ku jejjefe ta"
Marubucin yana maganar Dutsen Sihiyona, dutsen haikalin da ke Urushalima, kamar sama kenan da kanta, wurin zaman Allah
"mala'ikun masu yawa da ba a iya ƙirgawa"
Wannan na maganar masubin Almasihu ne kamar su 'ya'yan fari ne. Wannan na nanata matsayin su na musamman na kasancewa jama'ar Allah.
"waɗanda sunayen su ke a rubuce a sama." AT: "waɗanda Allah ya rubuta sunayensu a sama"
Wannan na nufin cewa Yesu ne ya sa sabon alkawari tsakanin Allah da mutane ya kasance. Duba yadda aka fassara wannnan a [9:15]
AT: "waɗanda Allah ya kammala"
Ana maganar jinin Yesu da jinin Habila kamar mutane ne da ke magana. AT: "jinin yayyafawa na Yesu da ke faɗin abubuwa mafiya kyau fiye da jinin Habilla"
A nan "jini" na nufin mutuwar Yesu, kamar yadda jinin Habila na nufin mutuwarsa.
AT: "ku kasa kunne ga wanda ke yi maku magana"
AT: "idan kuwa mutanen Isra'ila basu kuɓuta da ga shari'a ba"
Wannan na iya nufin 1) "Musa, da ya masu gargaɗi a duniya" ko kuma 2) "Allah, da ya masu gargaɗi a Dutsen Sihiyona"
AT: "in mun yi rashin biyayya da wanda ke mana gargaɗi"
"da Allah ya yi magana, ƙarar muryarsa ta sa duniya ta girgiza"
Yi amfani da kalmoni abinda girgizar ƙasa ke yi yă motsa ƙasa. Wannan na mayar da mu zuwa ga [12:18-21] da abinda ya faru da mutanen suka ga dutse inda da Musa ya karɓi shari'a daga wurin Allah.
AT: na nufin cewa Allah zai cire abubuwan da zai iya girgiza, wato, abubuwan" Dubi: and
Yi amfani da kalmar abinda girgizar ƙasa ke yi yă motsa ƙasa. Wannan na mayar da mu zuwa [12:18-20] da abinda ya faru yayin da mutanen suka gan dutse inda Musa ya karɓi shari'a daga wurin Allah. [12:26]
AT: "da Allah ya halitta"
AT: "abubuwan da basu girgiza" ko kuma "abubuwan da ba za su iya girgiza ba"
Ana iya ƙarin waɗannan kalmomin "domin mu ne" don a ƙara bada bayani mai kyau tsakanin wannan maganar da wanda ke biye. AT: "domin muna samun wata mulki" ko kuma "domin Allah yana naɗa mu mu zama 'yan mulkinsa"
AT: "da ba ta iya girgiza"
"sai mu yi godiya"
Kalmomin nan "dara" da "tsananin girmamawa" na nufin abu ɗaya ne kuma suna nanata matuƙar girmamawa da ya cancanci Allah. AT: da matuƙar ban girma da tsoro"
Ana maganar Allah a nan kamar shi wani wuta ne da ke iya ƙane kowane abu.
1Bari kaunar 'yan'uwa ta cigaba. 2Kada ku manta da karrama baki, domin ta wurin yin haka, wasu suka marabci mala'iku ba tare da saninsu ba.3Ku tuna da wadanda ke cikin kurkuku, kamar dai kuna tare da su cikin wannan hali. Kuma ku tuna da masu shan azaba kamar tare kuke cikin wannan hali 4Bari kowa ya girmama aure, bari kuma a tsarkake gadon aure, gama Allah zai shar'anta fasikai da mazinata.5Bari halinku ya kubuta daga kaunar kudi. Ku dangana da abubuwan da kuke dasu, domin Allah da kansa yace, "Bazan barku ba, ba kuma zan yashe ku ba." 6Bari mu zama da dangana domin mu sami gabagadin cewa, "Ubangiji ne mai taimakona, ba zan ji tsoro ba. To me mutum zai iya yi mani?"7Ku fa lura da wadanda ke shugabanninku, wadanda suka horar da ku cikin maganar Allah, kuma ku lura da sakamakon rayuwarsu, ku yi koyi da bangaskiyarsu. 8Yesu Almasihu daya ne a jiya, da yau, da har abada.9Kada ku kauce zuwa ga bakin koyarwa daban daban, domin yana da kyau zuciya ta ginu ta wurin alheri, amma ba da dokoki game da abinci ba, wadanda basu taimaki wadanda suka kiyayesu ba. 10Muna da bagadin da wadanda ke hidima a cikin alfarwa basu da ikon su ci daga bisansa. 11Babban firist na shiga wuri mai tsarki da jinin dabbobin da aka yanka, hadayar zunubai, amma namansu a kan kai bayan sansani a kone shi.12Domin haka Yesu shima ya sha wahala a bayan kofar birnin, domin ya tsarkake mutane ta wurin jininsa. 13Domin haka bari mu tafi gare shi a bayan sansani dauke da kunyarsa. 14Domin bamu da wani birni dawwamamme a nan. Maimako haka muna bidar birni dake zuwa.15Ta wurin sa kuma, bari kullum mu mika hadayu na yabo ga Allah, yabon kuwa shine kalmomin bakinmu da ke daukaka sunansa. 16Kada kuma mu manta da yin nagarta da kuma taimakon juna, domin Allah na farin ciki sosai da irin wadannan hadayun. 17Ku yi biyayya da sadaukarwa ga shugabanninku, domin suna aikin tsaro a kanku saboda rayukanku, kamar wadanda zasu bada lissafi. Kuyi biyayya gare su saboda su yi aikin lura daku cikin farin ciki, ba da bakin ciki ba, don in su yi da bakin ciki ba zai amfane ku ba.18Kuyi mana addu'a, domin mun tabbata muna da lamiri mai tsabta, kuma muna burin muyi rayuwar dake daidai cikin dukkan al'amura. 19Kuma ina karfafa ku dukka kuyi haka, domin in sami dawowa gareku da sauri.20To bari Allahn salama, wanda ya tada babban makiyayin tumakin nan daga matattu, Ubangijinmu Yesu, ta wurin jinin madawwamin alkawari, 21ya kammala ku da dukan abu mai kyau domin ku aikata nufinsa. Bari yayi aiki a cikinmu wanda zai gamshe shi sosai. Ta wurin Yesu Almasihu, bari daukaka ta tabbata gare shi har abada. Amin.22'Yan'uwa, yanzu dai ina karfafa ku, da ku jurewa takaitacciyar maganar karfafawar da na rubuto maku. 23Ina so ku sani an saki dan'uwan mu Timoti, tare da shi zan zo in gan ku idan ya iso da sauri.24Ku gaida shugabanninku dukka da kuma dukkan masu bada gaskiya. 'Yan'uwa daga can Italiya suna gaishe ku. 25Bari alheri ya kasance tare daku dukka.
A sashi na ƙarshe, marubucin yi wa masubi gargaɗi game da wasu fannoni na rayuwa a kan yadda yakamata su yi rayuwa.
"Ku cigaba da nuna ƙaunar ku ga sauran masubi kamar yadda za ku yi wa 'yan iyalinku"
AT: "Ku tabbatar cewa kun tuna"
"da karɓar baƙi da kuma nuna masu ƙauna"
AT: "kamar dai kuna ɗaure tare da su" ko kuma "kamar dai kuna tare da su a kurkuku"
AT: "waɗanda ake masu ba daɗi" ko kuma "waɗanda suke shan wahala"
Wannan jumlar tana ƙarfafa masubi su dinga yin tunan game da azabar sauran jama'a kamar yadda za su yi tunanin nasu azaba. AT: "kamar ku ne a cikin wahalar"
AT: "Lallai ne maza da mata da suka auri juna su girmama juna"
Wannan na nufin haɗuwa ta jima'i kenan kamar ita ce kaɗai gadon da ma'aurata ke da shi. AT: "Bari maza da mata su daraja dangartakar aurensu da juna, su kuma ƙi kwana da wasu dabam"
A nan "hali" na nufin halin mutum, ko kuma yadda mutumin ke rayuwa; "kubuta daga son kuɗi" na nufin ƙin marmarin ƙara tara kuɗi. Duk mai ƙaunar kuɗi baya dangana da iyakar kuɗin da yake da shi. AT: "kada ƙaunar kuɗi ya ɓata halinku" ko kuma "Kada ku yi marmarin ƙara tara kuɗi"
"Ku ƙoshi"
Wannan wata furci ne daga littafin Zabura a Tsaohon Alkawari.
Marubucin yana amfani ne da wannan tambayan don yă nanata cewa ba ya tsoro domin Allah ne mai taimakonsa. A nan "mutum" na nufin ko ma wanene a ko ina. AT: "ba zan ji tsoron abinda ko ma wanene zai iya yi mani ba"
"abinda Allah ya faɗa"
"ƙarshen yanayinsu"
A nan, ana maganar dogara ga Allah, da kuma yanayin rayuwa da shugabannin nan suka yi ne a matsayin "bangaskiyarsu." AT: "Ku dogara ga Allah, ku yi masa biyayya kuma kamar yadda suka yi"
A nan "jiya" na nufin dukkan lokatai na dã. AT: "ɗaya ne a dã, a yanzu, da kuma a nan gaba har abada"
Wannan sashin yana maganar hadayu na dabbobi da masubin Allah ke yi a lokacin Tsohon Alkawari, wadda ke rufe zunubai ba ƙaramin kafin isowar lokacin mutuwar Almasihu.
Ana maganar rinjaya na koyarwa dabam-dabam kamar mutum na bauɗe wa ne da ƙarfi. AT: "Kada ku bar wasu su rinjaye ku zuwa ga ba da gaskiya ga ire-iren baƙuwar koyarwarsu"
"ire-iren koyarwa da dama da ba bisharar da muka faɗa maku ba"
AT: "Muna ƙara samun ƙarfin yayin da muka yi tunanin yadda Allah ke yi mana alheri, amma ba mu samun ƙarfi ta wurin kiyaye dokoki game da abinci"
A nan "zuciya" wata karin magana ce da ke nufin "hankalin mutum". AT: "mu ginu a ciki"
A nan "su abinci" na nufin dokoki game da abinci. (Dubi:
AT: "waɗanda suke rayuwa ta wurin su" ko kuma waɗanda suka bi da rayuwarsu bisa ga ka'idarsu"
A nan "bagadi" na nufin wurin ibada. Yana kuma nufin dabbobin da firistoci na tsohon alkawari ke miƙa hadaya, wadda daga wurin ne suke samun abincinsu da na iyalensu.
AT: "babban firist ne ke kai, cikin wuri mafi tsarki, jinin dabbobi da firistoci suka yanka domin zunubai"
"yayin da firistoci suna ƙona naman dabobbin"
"nesa da wurin da mutane suke"
"Haka kuma" ko kuma "Domin an ƙona hadaya a bayan zango" [13:11]
Wato a "bayan garin"
Ana maganar biyayya da Yesu kamar mutum ya bar zango ne zuwa wurin da Yesu yake.
Ana maganar babbar kunya kamar wani abu ne da ake iya ɗauka da hannu ko kuma a bayan mutum. AT: "yayin da muka bar mutane su ci mutuncin mu kamar yadda suka ci mutuncinsa"
"muna jira"
Ana maganar yabo kamar wata hadaya ce da dabbobi ko kuma turare na hayaƙi.
AT: "yabo da ke fitowa daga baƙin waɗanda suke ɗaukaka sunansa"
A nan "baƙi" na nufin mutanen da ke magana. AT: "baƙin waɗanda ke ɗaukaka sunansa" ko kuma "waɗanda suke ɗaukaka sunansa"
Sunan mutum na ba da hoton mutumin. AT: "shi"
AT: "Bari mu riƙa tuna wa da aikata nagarta da kuma taimakon sauran mutane a koyaushe"
Ana maganar aikata nagarta da kuma taimakon mutane kamar hadaya ne a bisa bagadi.
Anyi maganar rayukan masu bi, wato ana lafiyar masubi a ruhaniya, kamar wasu abubuwa ne ko dabbobi da masu tsaro ke iya kula da su.
A nan "baƙin ciki" na nufin ɓacin zuciya ko gunaguni (Dubi:
A nan "mu" na nufin marubicin da abokan tafiyarsa, amma ba a haɗe da ma su karatun ba.
A nan "tsabta" na nufin marar laifi ko aibu. AT: "mu tabbata cewa bamu da laifi"
AT: "don Allah ya ɗauke abubuwan da suke hana ni zuwa gareku"
Wannan alama ce ta sabuwar sashe a wasiƙar. A nan, marubucin yana yaba wa Allah yana kuma yin addu'arsa na ƙarshe wa masu karatunsa.
"wanda ya tashi babban makiyayin tumakin, Ubangijinmu Yesu, zuwa ga rai"
Daga dukkan waɗanda sun mutu. Wannan furcin na bayani a kan dukkan mutanen da sun mutu da ke a ƙarƙashin ƙasa. Ta da mutum daga matattu na maganar sa mutumin yă sake zama da rai ne.
Ana maganar Almasihu a matsayinsa na shugaba da kuma mai tsaron dukkan waɗanda sun gaskata da shi ne kamar shi makiyayin tumaki ne.
A nan "jini" na nufin mutuwar Yesu wadna shi ne tushen alkawarin da zai kasance har abada tsakanin Allah da dukkan masubi a cikin Almasihu.
"yă baku kowane abu nagari da kuke bukata domin ku iya aikata nufinsa" ko kuma "ya sa ku iya aikata kowane nagarin abu bisa ga nufinsa"
Kalmar nan "mu" na nufin marubucin da masu karatun.
"wanda dukkan mutane za su yabeshi har abada"
Wannan na nufin dukkan masubi da yake rubuto masu ko maza ko mata. AT: "'yan'uwa masubi"
"da hakuri, ku yi tuanin abinda na rubuto maku domin in ƙarfafa ku"
A nan "magana" na nufin saƙo. AT: "saƙon ƙarfafawa"
AT: "ba ya kurkuku kuma"
Wannan na iya nufin 1) marubucin ba ya Italiya, amma akwai wata ƙungiyar masubi tare da shi da sun fito daga Italiya ko kuma 2) marubucin yana Italiya yayin da yake rubuto wannan wasiƙa.
Wannan shi ne sunan yankin a wannan lokacin. Roma a dã ita ce birnin tarayya na ƙasar Italiya.
1Yakubu, bawan Allah, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu, zuwa ga kabilun nan goma sha biyu da suke warwatse: ina gaishe ku. 2Ku dauke su duka da farin ciki, 'yan'uwana, duk sa'adda kuke fuskantar jarabobi. 3Ku sani cewa gwajin banskiyar ku ta kan haifi jimiri.4Bari jimiri ya cika aikin sa, domin ku kai ga cikakken girma kuma ku kammalu, domin kada ku rasa komai. 5Amma idan waninku yana bukatar hikima, sai ya roki Allah, wanda yake bayarwa a yalwace, ba tare da gori ba ga duk wanda ya roke shi, zai kuwa ba shi.6Amma fa sai ya roka da banskiya ba tare da shakka ba, don mai shakka kamar rakumin ruwan teku yake, wanda iska take korarwa tana tunkudawa. 7Tilas ne wannan mutum kada ya yi tunanin zai karbi wani abu a wurin Ubangiji. 8Irin wannan mutumin mai zuciya biyu ne, mara tsai da hankali a dukan hanyoyin sa.9Bari dan'uwa matalauci ya yi takama da matsayin sa babba, 10amma mutum mai arziki kuma a kaskantaccen matsayin sa, gama zai shude kamar furen ciyawa na jeji. 11Domin rana na bullowa da zafi mai konarwa kuma ya busar da ciyawa. Furen ya fadi, kuma kyaun sa ya lalace. Haka ma, mai arziki zai bushe yana cikin tsakiyar tafiyarsa.12Albarka ta tabbata ga mutum mai jurewa da gwaji. Domin in ya jure gwajin, zai sami rawanin rai, wanda aka yi alkawarin sa ga wadanda ke kaunar Allah. 13Kada wani ya ce idan aka gwada shi, "Wannan gwaji daga wurin Allah ne," domin ba a gwada Allah da mugunta, shi kan sa kuwa ba ya gwada kowa.14Amma kowanne mutum yakan sami gwaji daga muguwar sha'awar sa, wadda take janye shi kuma ta rinjaye shi. 15Bayan da muguwar sha'awar ta dauki ciki, sai ta haifi zunubi. Kuma bayan da zunubi ya yi girma, yakan haifi mutuwa. 16Kada fa ku yaudaru, 'yan'uwana kaunatattu.17Kowace kyakkyawar baiwa, da kowace cikakkiyar baiwa daga sama take. Ta sauko ne daga wurin Uban haskoki. Wanda babu sauyawa ko wata alamar sakewa kamar yadda inuwa ke yi. 18Allah ya zabi ya haife mu ta wurin maganar gaskiya, domin mu zama kamar nunar fari na dukan halittar sa.19Kun san wannan, 'yan'uwana kaunatattu: bari kowanne mutum ya yi hanzarin kasa kunne, da jinkirin yin magana, da kuma jinkirin yin fushi. 20Domin fushin mutum ba ya aikata adalcin Allah. 21Saboda haka, sai ku yar da kowanne irin aikin kazanta da yalwar mugunta. A cikin tawali'u ku karbi dassashiyar maganar, wadda ke iya ceton rayukan ku.22Ku zama masu aikata maganar, kada ku zama masu jin ta kawai, kuna yaudarar kanku. 23Domin duk wanda ya ke mai jin maganar ne kawai, ba mai aikatawa ba, kamar mutum yake mai duba fuskarsa a madubi. 24Yakan dubi kansa sai ya tafi, nan da nan kuwa sai ya manta da kamannin sa. 25Amma duk mai duba shari'ar da bin ka'idar nan ta 'yanci, ya kuma nace biyayya da ita, ba zai zama kamar wanda zai ji ya manta ba, wannan mutum zai zama da albarka a cikin abin da yake yi.26Idan wani yana zaton shi mai addini ne, amma bai kame bakinsa ba, yana yaudarar zuciyarsa ne, addinin mutumin nan na banza ne. 27Addini sahihi kuma marar aibi a gaban Allahnmu da Ubanmu, shine a kula da gwauraye da marayu a cikin kuntatar su, kuma mutum ya kebe kansa ya zama marar aibi daga duniya.
Manzo Yakubu ya rubuta wannan wasika zuwa ga dukan masubi. Yanwancin su Yahudawa ne, kuma mazauna ne a wurare dabam-dabam.
Jimlar nan "wannan wasikar daga" ya tabbatar da. AT: "Wannan wasikar daga Yakubu ne, bawan Allah, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu"
AT: 1) domin Yahudawa masubi, ko 2) domin dukan masubi. "ga mutanen Allah masu aminci"
Kalmar nan "warwatse" na nufin Yahudawan da suke a warwatse a wasu kasashe dake nesa da Isra'ila, kasarsu ta haihuwa. AT: "wanda suka bazu a duniya" ko "wanda suke zama a wasu kasashe"
asalin gaisuwa, kamar "Sannu" ko "Ina kwana"
"Yan'uwana masubi, ku dauke kowani irin jarabobi a masayin abun shagali"
Furcin nan "gwajin," "bangaskiyar ku," da kuma "jimiri." Allah ne ke gwajin, domin, ya sani ko masubi suna da yarda ko suna biyayya da shi. Masubi ("ku") sun yarda da shi kuma suna jimre wahala. AT: "Idan kuna shan wahaloli, Allah yana binciken yanda kuka yarda da shi. Ta dalilin wannan, zaku iya daure kowace irin wahaloli"
An yi maganar jimiri anan kamar mutun da yana aiki. AT: "Ka koyi jure kowani irin wahala"
a cikin kowani yanayi akwai damar yarda da Almashihu da kuma yi masa biyayya
An ambata wannan a bangare mai kyau AT: "samun abinda kake bukata" ko "kasance abinda kake so ka zama"
"roki Allah. shi ne wanda yake bayarwa"
"bayarwa a yalwace ba tare da tsautawa ba"
"Allah zai yi" ko "Allah zai amsa addu'ar ka"
Wannan za iya bayyana shi kamar haka. AT: "da cikakkeyar tabbacin cewa Allah zai amsa"
Duk wanda yayi shakkar Allah zai taimake shi yana kamar ruwan teku ko tafki ne, dake tafiya zuwa a wurare dabam-dabam.
Kalmar nan "zuciya biyu" yana nufin mutum da baya iya yanke shawara don kansa. AT: "ba ya iya yanke shawarar zai bi yesu ko babu"
Anan yana magana ne game da mutum da bai da masaya daya.
"mai bi mara kuɗi iya gwargwaɗo"
Ana magana game da wanda Allah ya ɗaukaka kamar yana tsaye a tudu
Wannan kalmar "muyi takama" an fahimce shi daga maganar baya. AT: "bari mai arziki kuma yă yi takama da kaskancinsa"
"amma mutum mai kuɗi sosai." AT: 1) mai bi dake da kuɗi, ko 2) mai kuɗi mara bi.
Mai bi da ke da kuɗi ya kasance da farin ciki idan Allah ya sa shi shan wahala. AT: "ya kasance da farin ciki domin Allah ya ba shi wuya"
Anyi maganar masu kuɗi kamar furenin jeji, wanda su na nan a raye na ɗan lokaci.
Anyi maganar furen mara kyaun gani kamar kyaun sa ya mutu. AT: "kuma ba sauran ban sha'awa"
Anan karin magana mai kwatanci da fure zai iya ci gaba. Kada ka mutu da sauri kamar furenin da yakan bushe a gajeren lokaci, mai yiwuwa masu arziki ba sukan mutu ba zato ba tsammani amma a maimakon hakan sukan dauki ƙanƙanin lokaci su bace.
Anyi maganar ayyukan mai kuɗi a rayuwar sa na yau da kullum kamar tafiya da yake yi. Wannan misalin ya nuna cewa baya tunanin zuwan mutuwan sa kuma zai dauke shi da mamaki.
Yakubu ya nuna wa masu wanda suka guji cewa Allah baya zama sanadin jaraba; ya gaya masu yadda za su kauce wa jaraba.
"mutumin da ya jurewa gwaji mai sa'a ne " ko "Mutumin da ya jurewa gwaji mai samu ne"
kasancewa da aminci ga Allah a lokacin wahala
Allah ya amince da shi
Anyi maganar rawanin rai kamar furannin ganye ne da aka tubka a kan ƙwararren ɗan wasa mai nasara. AT: "ya samu rawanin rai a masayi lada"
AT: "Allah ya yi alkawarta ga waɗanda suke kaunar sa"
"idan ya bukaci yin abinda ke mugu"
AT: "Allah na ko karin sa ni yin abinda ke na mugunta"
AT: "Ba wanda zai sa Allah yin marmarin mugunta"
"kuma Allah kansa ba ya rinjayar kowa ya aikata mugunta"
Anyi maganar abinda mutun ke sha'awar sa kamar wani mutum ne daban da ke sa shi zunubi
An ci gaba da magana game da muguwar sha'awar kamar wani mutum ne da zai iya jawo wani dabam
janyo hankali, rinjaye wani ya aikata mugunta
An ci gaba da maganar sha'awar kamar mutum, a wannan lokaci yana nan kamar mace mai ciki. An bayyana aihin yaron kamar zunubi. Zunubi wani yă ta mace ce da ta girma, zamanto da ciki, ta kuma haife mutuwa. Wannan karin maganan hoton wani mutum ne da yana mutuwa a ruhaniyance ko kuma a jiki domin muguwar sha'awar da kuma zunubin sa.
"Kada ku bari wani ya yaudare ku" ko "Dakata da yaudaran kanku" bari "
Wannan jimloli biyun na nufin abu iri guda. Yakubu ya yi amfani da wadɗannan domin ya jaddada da cewa ko mai yana da kyau kuma mutum ya fito daga Allah ne.
Allah, mahalici na dukanin hasken dake sararin sama
wannan na bayyana hotunan Allah kamar haske da ba ya canzawa, kamar rãna, wata, duniyoyi da taurari dake sararin sama. wannan ya sha bambam da inuwa da yakan canza kullum a wannan duniya. AT: "Allah baya canzawa. Yana nan daram kamar rãna, wata, da taurari dake sararin sama, yayi dabam da inuwa da yakan bayyana ya kuma bace a doron ƙasa"
wannan kalma "mu" na nufin Yakubu da masu sauraron sa.
Allah, da ya bamu rai madawami, anyi maganar sa kamar shi ya haife mu.
AT: 1) "saƙo game da gaskiya" ko 2) "gaskiyan saƙo."
Yakubu na morar ra'ayin al'adar Yahudanci game da nunar fari amasayin hanya na siffanta darajar masu bi mabiyan addinin kirista na Allah. AT: "domin mu zama kamar bayaswa na nunar fari"
AT: 1) "San wannan" umurni ne, ga mai hankali game da abun da nake kokarin rubutawa ko 2) "Kun san wannan" Zance ne, da ina kokarin tunatar da ku game da abin da kun riga ya kun san ni.
Wannan karin magana da farko na nufin ka yi sauraro da kyau, sa'anan kuma yin tunani akan abun da suka ce mai kyau. Anan "jinkirin yin magana" ba yana nufin yin magana a hankali ba ne.
"banda saurin fushi"
Idan mutum mai fushi ne koda yaushe, ba zai iya aikin Allah ba, wato aikin adalci.
Anyi maganar zunubi da kuma mugunta kamar rigar da zaka saka da iya cirewa. AT: "daina aikata aikin ƙazanta da kuma na mugunta mai yawan gaske"
Anan "ƙazanta," da ke nufin, datti, ya tsaya a matsayin zunubi da kuma mugunta.
"Ba tare da girman kai" ko "Ba tare da alfahari ba"
wannan tinani "dassashe" na nufin saka wani abu a cikin wani. Anan kalmar Allah ya yi magana kamar wanni dassashe itace da ya yi girma a cikin masu bi. AT: "yi biyayya da saƙon Allah da ya yi magana a gare ka"
mutumin da aka ceta da ga gare shi ya zama a bayyane. AT: "an ceto shi daga hukuncin Allah"
Anan kalmar nan "rayukan" na nufin mutane. AT: "kanku"
"Ku zama mutane masu bin umurnin Allah"
"yiwa kanku wauta"
"Domin duk wanda ke saurarar saƙon Allah a cikin nassosin"
Kalmar nan "ne" da kuma "na kalma" za a fahimce shi daga jimla na baya. wannan suna "aikatawa" za iya bayyana cikin aikatau "yi" ko "biyayya." AT: "ba mai aikata kalmar ba" ko "ba mai biyayya da kalmar ba"
mutun mai jin kalmar Allah yana kamar mutun mai duban kamannin sa a madubi.
Kalmar nan "yanayin" Yakubu ya mori wannan domin ya tãtacce ainihin ma'anar kalma "fuska." AT: "fuskarsa"
Ko da yake akwai tabbacin zai iya ganin bukatun yin wani abu, kamar wanke fuska ko gyaran gashin sa, ya kan wuce ya kuma mance da yin hakkan. Wannan yana kama da mutumin da bai yi biyayya da kalmar Allah ba. AT: "sai ya wuce kuma nandanan ya mance da yin abin da yake bukata ya yi"
wannan magana ya ci gaba da ganin siffan shari'ar kamar madubi.
Dangantaka sakanin shari'ar da kuma 'yanci za'a iya bayyana shi a fili. Anan "'yanci" yana iya nufin 'yanci daga zunubi. AT: "shari'ar da bin ka'idar da ke bada 'yanci" ko "shari'ar da bin ka'idar da ke sa mabiyanta su samu 'yanci"
AT: "Allah zai sanya albarka akan mutum da ya yi biyayya ga shari'a"
"zaton yana bautar Allah daidai"
Kamun bakina na matsayin iko akan faɗar magana na. AT: "abin da ya ce"
sa wani ya yarda da abin da ba gaskiya ba
Anan "zuciya" na nufin imanin sa ko tunanin. AT: "kansa"
ya na bautar Allah da wãsa
Yakubu ya yi magana game da addini, a yanda wani ke bautar Allah, kamar ya zama jiki sahihi kuma marar aibi. Wadannan hanyoyi a al'adar Yahudawa da sukan ce wani abu mai karbuwa ne ga Allah. AT: "Yana da karbuwa gabaki ɗaya"
kai tsaye ga Allah
"da marayu"
Marayu da gwauraye na shan wahala domin ubanninsu ko mazajensu sun rasu.
Anyi maganar zunubi kamar wani abu mai datti da zai iya bata mutun, AT: "kada ka bar mugunta na cikin duniya ya saka zunu"
1Ya ku 'yan'uwana, muddin kuna rike da bangaskiyar ku ga Ubangijinmu Yesu Almasihu, Ubangijin daukaka, kada ku nuna bambanci ga wadansu mutane. 2Idan wani mutum ya halarci taron ku da zobban zinariya da tufafi masu kyau, wani matalauci kuma ya shigo da tufafi marasa tsabta. 3Sa'adda kuka kula da mai tufafi masu kyau nan, har kuka ce masa, "Idan ka yarda ka zauna a nan wuri mai kyau," mataulacin nan kuwa kuka ce masa, "Kai ka tsaya daga can," ko kuwa, "Zauna a nan kasa a gaba na," 4Ashe ba kuna zartar da hukunci a tsakanin ku ba ke nan? Ba kun zama alkalai na mungayen tunani kenan ba?5Ku saurara, ya 'yan'uwana kaunatattu, ashe, Allah bai zabi matalautan duniyar nan su zama mawadata cikin bangaskiya ba, su kuma zama magada a cikin mulkin nan da ya yi wa masu kaunar sa alkawari ba? 6Amma, kun wulakanta matalauta! Ashe, ba masu arzikin ne suke matsa maku ba? Ba su ne kuwa suke jan ku zuwa gaban shari'a ba? 7Ba kuma sune ke sabon sunan nan mai girma da ake kiran ku da shi ba?8Duk da haka, idan kuka cika muhimmiyar shari'ar da nassi ya ce, "Ka kaunaci makwabcin ka kamar kanka," to, madalla. 9Amma in kun nuna bambanci, kun yi zunubi kenan, shari'a ta same ku da laifin keta umarni.10Duk wanda yake kiyaye dukan shari'a, amma ya yi tuntube a hanya daya kadai, ya sabi shari'a gaba daya ke nan. 11Domin wanda ya ce, "Kada ka yi zina," shi ne kuma ya ce, "Kada ka yi kisan kai." Idan ba ka yi zina ba amma ka yi kisan kai, ai, ka zama mai taka shari'a kenan.12Saboda haka, ku yi magana ku kuma yi aiki kamar wadanda za a hukunta ta wurin 'yantacciyar shari'a. 13Gama hukunci yana zuwa ba tare da jinkai ba ga wadanda ba su nuna jinkai. Jinkai ya yi nasara a kan hukunci.14Ina amfanin haka, 'yan'uwana, idan wani ya ce yana da bangaskiya, kuma ba shi da ayyuka? Wannan bangaskiyar ba za ta cece shi ba, ko za ta iya? 15Misali, idan wani dan'uwa ko 'yar'uwa ba su da tufa mai kyau ko suna rashin abincin yini. 16Misali, idan waninku kuma ya ce masu, "Ku tafi cikin salama, ku kasance da dumi ku koshi." Idan baku ba su abubuwan da jiki ke bukata ba, ina amfanin wannnan? 17Haka ma, bangaskiya ita kadai, ba tare da aikin da ya nuna ta ba, matacciya ce.18To, wani zai ce, "Ai, kai kana da bangaskiya, ni kuwa ina da ayyuka." Nuna mani bangaskiyar ka ba tare da ayyuka ba, ni kuma in nuna maka bangaskiya ta ta wurin ayyuka na. 19Ka gaskanta cewa Allah daya ne; ka yi daidai. Amma ko aljannu ma sun gaskata, kuma suna rawar jiki. 20Kana so ka sani, kai marar azanci, cewa bangaskiya ba tare da ayyuka ba banza ce?21Ba an baratar da Ibrahim mahaifinmu ta wurin ayyuka ba, sa'adda ya mika Ishaku dansa a bisa bagadi? 22Ka gani, ashe, bangaskiyar sa ta yi aiki da ayyukan sa, kuma da cewa ta wurin ayyuka bangaskiyar sa ta ginu sosai. 23Nassi kuma ya cika da ya ce, "Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lisafta masa ita a matsayin adalci." Aka kuma kira shi abokin Allah. 24Kun ga, ta wurin ayyuka ne mutum yake samu baratarwa ba ta wurin bangaskiya kadai ba.25Ta wannan hanyar kuma, ba Rahab karuwar nan ta samu baratarwa ta wurin ayyuka, da ta marabci masu leken asirin nan ta fitar da su ta wata hanya dabam ba? 26Kamar yadda jiki idan ba tare da ruhu ba matacce ne, haka kuma, bangaskiya ba tare da ayyuka ba matacciya ce.
Yakubu ya cigaba da gaya was Yahudawa masubi da suke a warwase yanda zasu yi zaman kaunan juna kuma ya tunashe su akan kada su so masu arziki fiye da 'yan'uwa matalauta.
Yakubu yayi la'akari da masu sauraronsa wanda su Yahudawa ne masubi AT: "Yan'uwanmu masubi" ko "'Yan'uwanmu maza da mata a cikin Almasihu"
Anyi maganar yarda da Yesu Almasihu kamar wani abu da mutun zai iya rike wa.
Kalmar nan "mu" ya haɗa da Yakubu da sauran 'yan'uwa masubi.
son taimakawa waɗan su mutane fiye da sauran
Yakubu ya fara siffanta yanayin da masubi sun fara daraja masu arziki fiye da matalauta.
"ya yi ado kamar mai arziki"
zauna a wuri mafi girma
tafi wuri mafi kaskanci
tafi wuri mafi muhimmanci
Yakubu na morar tambayoyi da ba su damu da amsa ba domin ya koyar ya kuma yi wa masu karantawa tsawa. AT: "kuna hukunci a sakanin ku kuma kuna zama alkalai na mugayen tunani"
Yakubu ya tsawatawa wa masu sauraron sa kamar iyali. "Maida hankali, zuwa ga 'yan'uwanmu masubi"
Anan Yakubu ya mora tambayoyi da ba su damu da amsa ba domin ya koya wa masu karantawa kada su nuna son kai. Za iya bayyana shi a magana. AT: "Allah ya zaɓe ... kaunar sa"
Wannan na nufin gaba dayan matalautan mutane.AT: "matalautan mutane"
Anyi maganar samun bangaskiya kamar samun wadata ko arziki. Abun na bangaskiya ya kamata ya zama ƙayyadadde. AT: "zama da ciƙankiyar bangaskiya a cikin Alhasihu"
Anyi maganar mutanen da Allah yayi masu alkawarai kamar wadanda za su ci gadon mallaka da kuma dũkiya da daya daga cikin iyali.
Yakubu ya na magana akan dukan masu sauraron sa.
"kun kunyatar da matalautan mutane"
Anan Yakubu ya mora tambayoyi da ba su damu da amsa ba domin ya daidan ta masu sauraron sa. AT: "masu arzikin ne suke matsa maku."
wannan na nufin gaba dayan mutane masu arziki. AT: "mutane masu arziki"
"suke yi muku mugunta"
Anan Yakubu ya mora tambayoyi da ba su damu da amsa ba domin ya daidan ta masu sauraron sa. Za a iya bayyana shi a magana. AT: "Masu arziki suke ... zuwa gaban shari'a."
"a akan tilas ta ku zuwa gaban alkalai su tuhume ku su yi muku shari'a"
Anan Yakubu ya mora tambayoyi da ba su damu da amsa ba domin ya daidan ta ya kuma koya wa masu sauraron sa. Za a iya bayyana shi a magana. AT: "Mutane masu arziki ke saɓon ... ake kiran ku da shi."
Wannan na nufin sunan Almasihu ne. AT: "sunan Almasihu da ya kira ka"
Kalmar nan "ku" na nufin Yahudawa masubi.
"biyayya da shari'ar Allah." Allah ya ba wa Musa asalin dokoki, da an rubuta a cikin Littattafai na Tsohon Alkawari.
Yakubu ya ɗauko daga cikin faɗar Littafin Leviticus
"dukan mutane" ko "kowa da kowa"
"kana yi daidai" ko "kana yin abu mai kyau"
"bada cikanken kulawa ga" ko "bada girma ga"
"yin zunubi" wato, Karya doka.
Anan anyi maganar shari'a kamar mutum da ke hukunci. AT: "laifin rashin ketare dokan Allah"
"Duk wanda ya yi biyayya"
tuntuɓe fadowa ƙasa ne lokacin da mutum ke kokarin tafiya. Anyi maganar rashin biyayya a wani ɓangaren shari'a kamar tuntuɓe a na kan tafiya.
domin rashi biyayya na daya daga cikin abin da ake bukata a shari'a
Wannan na nufin Allah ne, wanda ya bawa Musa dokan.
"Ka yi" shine ka dau mataki.
Anan "kai" na nufin "kowane dayan ku." Kodayake Yakubu na rubutawa zuwa ga yanwacin Yahudawa masubi ne, a wannan magana, ya mora mufuradi kamar yana rubutawa kowane mutum daya.
"Saboda haka dole ku yi magana ku kuma yi biyayya." Yakubu ya umurce dukan mutanen da su yi wannan.
AT: "wa ya sani cewa Allah zai yi muku hukunci ta wurin 'yantacciyar shari'a"
Wannan nassi na nufin Allah zai yi hukunci bisa ga shari'a.
"shari'ar da takan bada ainihin 'yanci"
"Jinkai mafi inganci ne akan" ko "Jinkai ya yaƙi." Anan anyi magana akan jinkai da ãdalci kamar su mutane ne.
Yakubu ya mora tambayoyi da ba su damu da amsa ba domin ya koyar wa masu sauraron sa. AT: "Ba si da kyau ko kaɗan, 'yan'uwanmu masubi, idan wani ya ce yana da bangaskiya, kuma ba shi da ayyuka."
Za a iya sake maganar ta wurin cire ra'ayin sunaye "bangaskiya" da kuma "ayyuka." AT: "idan wani ya ce ya yi ĩmãni da Allah kuma bai yi abin da Allah ya umurce shi kada ya yi ba"
Yakubu ya mora tambayoyi da ba su damu da amsa ba domin ya koya wa masu sauraron sa. Za a iya sake maganar ta wurin cire ra'ayin suna "bangaskiya." AT: "Cewa bangaskiya ba zai iya ceton sa ba" ko "idan mutun bai yi abin da Allah ya umurce shi ba, to ya na cewa bai yi ĩmãni Allah zai iya ceton sa ba"
"an cece shi daga shari'an Allah"
Wannan na nufin "samun isashshen kayan sa wa" ko "samun magwanci"
Abin da ya koshas da su abinci ne. Za a iya bayyana baro-baro. AT: "ku koshi da abinci" ko "samu isasshe ku ci"
ku ci, ku sa, ku kuma rayu a tsanake
Yakubu ya mora tambayoyi da ba su damu da amsa ba domin ya koya wa masu sauraron sa. AT: "game da abin da bai da amfanin."
'Yan'uwanmu masubi cikin Almasihu, koda namiji ko ta mace
Yakubu ya yi magana game da bangaskiya kamar abu mai rai indan mutun ya yi aiki mai kyau, kuma bangaskiya kamar mataccen abu ne idan mutun bai yi ayuka masu kyau ba. Za a iya sake maganar ta wurin cire ra'ayin sunaye "bangaskiya" da kuma "ayyuka". AT: "idan mutum ya ce ya yi ĩmãni da Allah, san nan bai yi abin da Allah ya umurce shi ba, bai yi ĩmãni da Allah ba ke nan"
Yakubu ya bayyana yanayin da wani ke ganin koyarwan sa. Yakubu ya biɗa gyarar ganewar masu sauraron sa game da bangaskiya da kuma ayyuka.
Yakubu ya na bayyanin yanda wani zai iya yin jayayya da gaba da koyarwan sa da kuma yanda zai amsa masa. Za iya sake maganar ta wurin cire ra'ayin sunaye "bangaskiya" da kuma "ayyuka". AT: "'Mun yarda cewa ka yi ĩmãni da Allah kuma kana aikata abin da Allah ya umurta.' Tabbatar mini ĩmãnin ka da Allah da ba za ka iya yin abinda ya umurta ba, ni kuma sai in tabbatar maka da ĩmãni na da Allah ta wurin yin abin da Allah ya umurta"
"ko aljannu ma sun gaskata, amma suna rawar jiki don tsoro." Yakubu ya bambanta tsakanin aljannu da masu neman su nuna sun yi ĩmãni kuma basu da ayyuka masu kyau. Yakubu ya yi magana da cewa alajanun suna da hikima domin suna da tsoron Allah sa'annan wasu basu da shi
Yakubu ya mora tamabaya domin gabatar da koyarwar sa na gaba. AT: "Saurare ni, wawan mutum, zan kuma nuna maka cewa bangaskiya ba tare da ayyuka ba banza ce."
Za a iya sake maganar ta wurin cire ra'ayin sunaye "bangaskiya" da kuma "ayyuka". AT: "idan ba ka aikata abi da Allah ya umurta ba, ya zama banza ce a gare ka a ce ka yi ĩmãni da Allah"
Tun da yake waddannan Yahudawa masu bi ne, sun san labarin Ibrahim, game da abin da Allah ya faɗa musu tuntuni a cikin kalmarsa.
An mora wannan tambaya da ba ta damu da amsa ba domin sukar wawan mutumin mai haddama [2:18]
Yakubu ya yi maganar ayyuka kamar wasu ababai da wani ya manlaka. AT: "barata ta wurin yin aiki mai kyau"
Anan "mahaifi" an mora a bangarin "kakan kaka."
Kalmar nan "ka" ɗan tilo, na nufin mutum mai shiririta. Yakubu na yiwa dukkan masu sauraronsa jawabi kamar mutun guda.
Yakubu ya yi magana kamar "bangaskiya" da kuma "ayyuka" abubuwa ne da sukan yi aiki a wuri guda tawurin taimakon juna. AT: "saboda Ibrahim ya gaskata Allah, tawurin aikata abin da Allah ya umurta. kuma saboda Ibrahim ya aikata abin da Allah ya umurta, ya gaskanta da Allah gabaki ɗaya"
AT: "Wannan nassi kuma ya cika"
"Allah ya na kallon bangaskiyan sa a matsayin adalci." Bangaskiya da kuma adalcin Ibrahim an ɗauke shi tamkar kamar wani abu da za'a iya kirgawa kamar samun daraja.
"ayyuka da kuma bangaskiya baratar da mutum, kuma ba bangaskiya ka dai ba." Yakubu ya yi magana game da ayyuka kamar waddansu abubuwa da za ka iya samu.
Yakubu ya ce abin da ke gaskiya ce game da Ibrahim gaskiya ce kuma game da Rahab. Dukansu sun sami baratarwa ta wurin ayyaku.
Yakubu ya mora tambaya da bai damu da amsa ba domin ya umurce masu sauraron sa. AT: "abin da Rahab karuwar nan ta samu baratarwa ... ta wata hanya dabam."
Yakubu ya tsammanci masu sauraron sa su zama da masananciya game da labarin macen nan Rahab na Tsohon Alkawari.
Mutane masu kawo sakonni daga wani wuri
"sai sun sami taimako suka gudu suka kuma bar birnin"
Yakubu ya na maganan akan bangaskiya ba tare da ayyuka ya na kamar mataccen jikin da bata da ruhu.
1Ba mutane dayawa za su zama masu koyarwa ba, 'yan'uwana. Mun san cewa za mu karbi hukunci mafi tsanani. 2Domin mukan yi tuntube ta hanyoyi dayawa. Duk wanda bai yi tuntube ta hanyar kalmomi ba, shi mutum ne ginanne sosai, wanda ke iya kame dukan jikinsa.3Idan muka sa linzami a bakunan dawakai, domin su yi mana biyayya, za mu iya sarrafa jikunan su gaba daya. 4Ku lura kuma da jiragen ruwa, ko da yake suna da girma sosai kuma iska mai karfi tana kora su, da karamin karfe ne matukin yake juya su inda ya so.5Haka kuma harshe dan karamin gaba ne a jiki, sai fahariyan manyan abubuwa. Ku lura yadda dan karamin wuta yake cinna wa babban jeji wuta. 6Harshe ma wuta ne, a cikin dukan gabobin mu, duniyar zunubai da aka sa cikin fannonin jikunan mu. Yana gurbata dukan jiki, ya kuma sa al'amurar rayuwa su kama da wuta. Shi kuwa gidan wuta ne yake zuga shi.7Domin kowace irin dabbar jeji, tsunsu, da masu jan ciki, da hallittar teku, ana sarrafa su kuma dan Adam har ya sarrafa su ma. 8Amma game da harshe, babu wani a cikin 'yan Adam da ya iya sarrafa shi. Mugunta ne mara hanuwa, cike da dafi mai kisa.9Da wannan harshe muke yabon Ubangiji da kuma Uba, da shi kuma muke la'antar mutane wandanda aka hallitta cikin kamanin Allah. 10Bakin da ake sa albarka, da shi kuma ake la'antarwa. 'Yan'uwana, ai, wannan bai kamata ba.11Mabulbulan ruwa ba zai iya bubbugowa da ruwan dadi da na zartsi tare ba, ko zai iya? 12"Yan'uwana, itacen baure ba zai iya yin zaitun ba, zai iya? Ko kuwa gonar inabi ya yi baure? Haka kuma, ruwan zartsi ba zai iya bayar da ruwan dadi ba.13Ina mai hikima da fahimta a cikin ku? Bari wannan mutumin, ta kyakkyawan zaman sa ya nuna aikin da halin tawali'u da hikima ke sawa. 14Amma in kuna da matsanancin kishi da kazamin buri a cikin zuciyar ku, kada ku yi fahariya da karya game da gaskiya.15Wannan hikima ba irin wadda take saukowa daga sama ba ce, a maimakon haka, ta duniya ce, mara ruhaniya, ta aljanu. 16Domin duk inda kishi da kazamin buri suke, a nan ake samun hargitsi da kowanne irin aikin mugunta. 17Amma hikiman nan ta sama, da farko dai tsattsarka ce, mai lumana ce, kamila ce, mai saukin kai, mai tsananin jinkai, mai yawan alheri, mara gajiya, sahihiya kuma. 18Kuma 'ya'yan adalci wanda ake shukawa a cikin salama a tsakanin wadanda ke kulla zumunci.
Yakubu na yin magana na gabaki daya.
"'yan'uwanmu masubi"
Wannan nassi ya yi magana game da hukunci mafi tsanani da ke zuwa daga wurin Allah bisa kan masu koyarwa game da shi. AT: "Allah zai yi mana mu masu koyarwa shari'a mai tsanani don mun san kalmar sa sosai feye da wasu mutane da muka koyar"
Yakubu ya hada da kansa da kuma sauran masu koyarwa, amma banda masu karantawa, don haka kalmar nan "mu" na nan dabam.
Yakubu yayi magana game da kansa, wasu malamai, da masu karatu, wannan kalmar "mu" a haɗe ne.
Ana magana game da zunubi kamar tuntuɓe ne ayayin da ake tafiya. AT: "faɗi" ko "zunubi"
"baya zunube ta wurin faɗan abubuwa marasa amfani"
"ruhaniyarsa ginanne ne"
Yakubu na nufin zuciyar mutum, shauƙi, da kuma aikinsa. AT: "kame halinsa" ko " kame ayukansa"
Yakubu ya cigaba da wani bayani a kan wannan mahawara cewa kananan abubuwa na iya mulkin manyan abubuwa.
Yakubu yayi magana akan linzamin dawakai. Linzami wata karamar karfece wace ake sakawa a bakin doki domin ya jagorance inda zashi.
"Idan" ko "lokacin"
Doki babban dabbane wanda ake amfani da ita domin daukan abubuwa ko mutane.
jirgin ruwa an kamanta shi da babbar mota wace ke tafiya akan ruwa Matuki karamar karfi ce ko sanda wace ke bayan jirgin ruwa, wace ake amfani dashi don ya jagoranci inda zata. Kalman nan "matuki" za' a iya fassarata a matsayin "kayan aiki."
Za' a iya bayyana ta cikin tsifar aiki. AT: "iska mai ƙarfi na korarsu"
"nada karamin kayan aiki da matukin kan iya amfani dashi wajen juya jirgin duk inda zai je"
Wannan kalmar na harshe na kwatanci ne da linzamin doki da matukin jirgin ruwa yanda aka fada a surorin da suka gabata. AT: "ta haka kuma"
Anan "abubuwa" kalmace wacce ake mora don a nuna yadda waddannan mutane suke fahariya da komai.
"Yi tunani akan"
Domin a fahimtar da mutana hatsarin da harshe kan iya jawowa, Yakubu yayi magana akan barnan da karamin wuta ke iya kawowa. AT: "yadda ɗan karamin macinne yake cinna wa itatuwa wuta"
Harshe kalma ne wacce mutane ke morra. Yakubu ya kirata wuta saboda barnan da takan iya yi. AT: "Harshe na kamanni da wuta"
Ana maganane game da babban illan kalmomin zunubi kamar su duniyace da kansu.
Ana magana ne game da zunubin munanan kalmomi kamar magane ce wadda ke lalata jikin mutum. Yana kuma zama marar ƙarɓiya ga Ubangiji kamar kuma datti ne ga jikin dan adam.
Kalman nan "al'amurar rayuwa" na nufin rayuwar mutum gaba ɗaya. AT: "ta kan lalata rayuwar mutum gaba ɗaya" (Dubi:
Kalman nan "shi kansa" na nufin harshe ne. Anan kuma jahannama na nufin mumunar ikon ibilis. Wannan an iya bayanashe a sifar aiki. AT; "rayuwa saboda ibilis yakan ye aiki da she ta wurin hayyamara amfani.(Dubi:
Wannan sashen "kowace irin"
wannan ɗabbace wanda take rarrafe a kasa.
ɗabbace wanda take zama a cikin teku
Yakubu yayi magana game da harshe kamar wata ɗabban jeji ne. "harshe" wakilin mutum ne kuma yana son sa mutum yayi magana a kan kowace mugunta. Dubi: ko
Yakubu yayi magana akan illan da mutane zasu iya jawowa game da abun da suke faɗawa kamar harshe mugune ko ɗafi hallita wanda zai iya kashe mutum. AT: "Muguntatciyar hallita ne mara hanuwa, cike da dafi mai kisa" ko" halintatciyar mugunta ce mai geje-ama da zashe iya kashe mutum da kuma dafi" Dubi:)
"Muna amfani da harshe mu faɗa kalmomi da"
"Muna rokon Allah ya lahanta mutane
AT: "Wadda Allah ya hallita cikin kamanin sa"
" albarka" ko "la'antarwa" za' a iya juya ta a wata sashen magana. AT: "da baki ɗaya mutun zai sa wa mutane albraka ko ya la' anci mutane" Dubi:
"Waɗanan abubuwa ba daidai ba ne"
Bayyan da Yakubu yayi ta nanata magana cewa kada kalmomin masubi su zama masu sa albarka da la' ana, ya ba da misalai daga halitta domin ya koya wa masu karatu cewa mutane da suka ɗaukaka Allah ta wurin yi masa sujada su kuma zauna a hanyar da ta dace.
Yakubu yayi magana da tambaya da ba ta damu da amsa ba domin ya tunashe masubi da abun da yake faruwa a halitta. AT: "kun san da cewa mabulbulan ruwa ba zai iya bubbugowa da ruwan dadi da na zartsi tare ba."
yakubu yayi amfani da wata tambayan da bata damu da amsa ba kuma domin ya tunashe masubi a kan abubuwan da suke faruwa a halitta. AT: "dan'uwa ka sani da cewa mabulbulan ruwa ba zai iya bubbugowa da ruwan dadi da na zartsi tare ba."
wannan kalma "yi"an gane ta a sashen da ta wucce. Yakubu yayi magana da tambayan da ba ta da amsa domin ya tunashe masubi a kan abubuwan da suke faruwa a halitta. AT: "Ko kuwa gonar inabi ya yi baure? " ko " haka kuwa gonar inabi ba za ta haifi baure ba."
Yakubu yayi amfani da wannan tambayan domin ya koya wa jama' a hallaiya masu kyau. wanan kalman "hikkima" ko"ganewa" suna kama. AT: zan gaya maku yadda mutum mai hikkima da ganewa yi."
wanan za' a iya bayanawa a cire dahii "tawali'u" da "hikkima" AT: amin mutum yayi ayuka da rayuwa mai kyau na hallin kaskanci da hikkima"
Anan "zuciya"
wannan dahin "gaskiya"za a iya fadarta kaman "gaskiya." AT: kada ku yi fahariya da cewa kuna da hikkima, domin haka ba gaskiya bane"
Anan wannan yana nufin "ɗacin kishi da kokari" wadda aka bayyyana a sashen da ta wucce. wannan sashen maganar "daga sama" ana amfani da ita wurin kwatancin "sama" wadda take misalim Allah da kasa. AT:"wanan hikkiman ba irin wadda Allah ya koyar bane daga sama"
wanan kalma "basira" az' a iya fadan ta kamar "hikkima."- AT: duk wananda yayi kamar haka bashi da hikkima yadda Allah na sama ya koya mana. a maimakon haka, ta duniya ce, mara ruhaniya, ta aljanu"
wanan kalma "duniya" tana nufin daraja da ayuka na mutane wadda basu daukaka Allah ba. AT: "basu daraja Allah"
"ba daga ruhu mai sraki ba" ko "mai ruhaniya"
"daga a'ljanu"
wanan kalma "kishi" "kazamin buri" da "hargitsi." AT: "domin idan mutane suna kishi da son kai, wannan yakan sa suyi aikin mugunta a hanyoyin da be dace ba"
"akwai rashin shiri" ko " akwai rashin shiri kankat"
"ko wacce hallayen zunubi" ko "ko wacce aikin zunubi"
anan "daga bisa" ya na misalin "sama" wadda yake misalin Allah da kansa. wannan kalma "hikkima." AT; amma idan mutum yana da hikkima kamar yadda Allah na sama ya koyar, yayi aiki da a tsattsarkarkiyar hanya"
"mai tsarki tun farko"
Anan "kyauwawan ayuka" ta na nufin abubuwa da mutane suke yi masu kyau ta wurin samun hikkima da Allah. AT: "cike da tausayi da ayuka masu kyau"
"da mai gaskiya" ko "dagaskike"
Mutane sunan salama kamar suna sukin iri, adalci kuma ana maganar ta kamar 'ya 'ya ce wadda take grima ta dalilin salama. AT: "sakamakon salama shene adalci" ko "ko kuma wadda suke ayukan salama su temaki mutana a sami salama ya haifi adalci"
wannan kalma "salama"za' a iya fadin ta kamar "kwanciyar rai." AT: "sa mutane su zauna da "kwanciyar rai" ko a taimaki mutane kada su ɓata rai tsakanin juna"
1Me ke kawo gaba da rashin jituwa a tsakanin ku? Ba yana tasowa ne daga muguwar sha'awa da ke yaki a cikin ku ba? 2Kuna sha'awa, kuma ba ku da shi. Kuna kisa da kyashi, kuma ba za ku iya samu ba. Kuna danbe da fada. Har wa yau baku samu ba domin baku tambaya ba. 3Kun roka kuma ba a baku ba saboda kuna roko ta hanya mara kyau, kuna so ku yi amfani da shi domin miyagun sha'awoyin ku.4Ku mazinata! Baku sani ba, abokantaka da duniya, tawaye ne ga Allah? Don haka duk wanda ya shiga abokantaka da duniya ya zama magabcin Allah.5Ko kuna zaton nassi ya fadi haka a banza ne, "Ruhun nan da ke a cikinmu yana da kishi matuka?"6Amma Allah ya bayar da karin alheri, shi ya sa nassi ya ce, "Allah yana gaba da mai girman kai, Amma yana ba da alheri ga mai tawaliu." 7Saboda haka ku mika kan ku ga Allah. Ku yi tsayayya da shaidan, zai kuma guje maku.8Ku matso kusa da Allah, shi kuma za ya matsa kusa da ku. Wanke hannayen ku, ku masu zunubi, ku tsabtace zukatan ku, ku masu zuciya biyu. 9Ku yi bakin ciki, makoki, da kuka! Ku mayar da dariyar ku ta koma bakin ciki, farin cikinku kuma zuwa ga bakin ciki. 10Ku kaskantar da kanku a gaban Ubangiji, shi kuma za ya daukaka ku.11Kada ku rika zargin juna, 'yan'uwa. Wanda ya ke zargin dan'uwa ko shari'anta dan'uwansa, yana zargin shari'a kuma yana hukunta shari'a. Idan ka hukunta shari'a, ya nuna ba ka biyayya da shari'ar, amma mai hukunci. 12Mai ba da shari'a da yin hukunci daya ne. Shine mai iya ceto kuma ya hallakar. Kai wanene, da ke hukunta makwafcin ka?13Saurara, ku da kuke cewa, "Yau ko gobe za mu tafi wancan birnin mu yi shekara guda a wurin, muna kasuwanci, mu kuma yi riba." 14Wa ya san abin da zai faru gobe, kuma yaya rayuwan ka zai kasance? Kai kamar hazo ne mai bayyana bayan dan lokaci kadan ya bace.15Maimakon haka, sai ka ce, "Idan Ubangiji ya nufa, za mu rayu kuma mu yi wannan ko wancan." 16Amma yanzu kana fahariya da shirye shiryen ka na takama. Irin wannan fahariya, mugunta ce. 17Saboda haka ga wanda ya san abin da ya kamata ya aikata amma bai yi ba, ya zama zunubi a gare shi.
Yakubu ya kwubɓi masubi sabo da ayukan duniya da rasin kaskanci. ya kuma izasu su kula da yadda suki maganar da juna.
A wannan sashin kalmar da ake ce "kai da kanka," "naka," da "kai" jam'i ne kuma suna nufin masubi wadda Yakubu ya rubuta masu.
wannan kalma "gãba" da "rashin jituwa" a takaice na nufin abu ɗayane kuma za 'a iya fasarta su cikin aikatau. AT: "Don mai kuke da gãba da rashi jituwa a sakanin ƙu?" ko mai yasa kuke fada a sakanin ku?"
Yakubu yayi amfani da tambayan nan domin ya kwaɓi masu sauraro. za' a iya juya shi kamar bayani. AT; suna zuwa da muguwar sha'awar ku na abubuwa, sha'awar mugunta da yake a sakanin ku"
Ma'ana mai yuwa ne 1) akwai fada a sakanin masubi na wuri ɗaya, 2) faɗa wacce take, anafadin fada ,yana cikin ko wacce mai bi.
wannan kalma "ka ƙashe" wannan na iya faɗin yadda mutane suke yin abu mara kyau don su sami abin da suke so. za'a iya juya ta kamar "ka yi dukan ko wacce irin mugunta ka samu ama baza ka samu ba"
wannan kalma "faɗa" da "jayaya" suna nufin abu ɗaya na. Yakubu yayi amfani da su so nawa mutane suki musu a sakanin sa. AT: "ku fada kullum"
Ma'ana mai yuwa ne 1) "kuna tambaya da muraɗi mara kyau" ko "kuna tambaya da halin mara kyau" ko 2) " kuna tambayan abubuwa marasa kyau "
Yakubu yayi magana akan masubi kamar matayen da suke kwana da mazajen da ba nasu ba. AT: ba ku yin aminci ga Allah!" Dubi:
Yakubu yayi amfani da tambayan domin ya koya wa masu sauraronsa. Wannan za' a iya fasara shi kamar bayani. AT; ka sani ... Allah!"
wannan kalma na nufin ganawa da ko kasan cikin darajan ayukan duniya.
wadda yake aboki da duniya magabci na da Allah. Anan "abokantaka da duniya" ya tsaya ne a masayin abokantaka da duniya, da "gaba da Allah" ya tsaya a masayin gaba ne da Allah. AT; "abokan da duniya abokan gaba na Allah ne"
Yakubu yayi amfanin da tambayan nan domin ya gargaɗe masu sauraro. yin maga na a banza she na yin magana mara amfani. AT: "akwai dalilin da ya sa nassin ya fada"
wasu juyin, duk da ULB da UDB, sun fahimci wannan nassoshin zuwa ga ruhu mai tsarki. wasu juyin sun juya shi kamar "ruhun" kuma na nufin cewa ruhun yan adam wadda aka halita da shi. muna bada shawara cewa kuyi amfanin da ma'anar da aka bayar a wasu juyi da ake amfani da su.
wannan ayan na da dangataka da ayan da ya wuce. "amma ko da shike ruhun mu yakan so abin da baza mu samu ba, ya ba mu alheri da yawa, idan mun kaskantar da kan mu"
"Domin Allah ya bada alheri da yawa, nassin ... Domin Allah ya ba da alheri wa masu tawaliu, ku mika"
wannan na nufin mutane ma su girman kai a duka. AT: "mutane masu girman kai"
wannan na nufin mutane masu tawali'u a duka. AT: "mutane masu tawaliu"
"yi biyayya ga Allah"
yi gãba da shaiɗan" ko "kada ku yi abin da shaiɗan ya ka so"
"zai kuma gudu daga nan"
wannan kalman jam' i ne kuma yana nufin masu sauraro Yakubu.
Anan zuwa kusa na ba da ra'ayin zama mai gaskiya ga Allah.
Waɗan nan maganganu biyun na layi ɗaya da juna.
Wannan magana umurni na ga mutane suyi adalci rayuwa a maimakon rashin adalci. AT:" nuna hali a hanyan da za ta daukaka Allah"
Anan "zuciya" na nufin tunanin mutum da tausayi. AT: ku daidaita niyyar ku da tunanin ku"
Wannan kalman "zuciya biyu" na nufin mutum wadda ba zai iya yanke shawara mai karfi akan abu ba. AT: "mutane masu zuciya biyu" ko mutanen da ba za su iya yanke shawara idan suna so suyi ko karsu yi biyayya ga Allah"
Wannan kalman guda uku nada ma'a na kusan ɗaya. Yakubu yayi amfani da su domin ya jaddada mutane su zama masu rokon gafara da rashin yin biyayya ga Allah.
Wannan na faɗin abu ɗaya na a hanyoyi daban daban domin jaddadawa. wannan kalman "dariya," bakin ciki," "murna" da "bakin ciki" za'a iya juya su kamar fi'ili. AT: "dena dariya kayi bakin ciki. "dena yin murna ama kayi bakin ciki"
ku zama masu kaskanci zuwa ga Allah." An yi magana game da ayukan da aka yi da sanin Allah a zuciya kamar anyi ta ne a gaban Allah.
Yakubu ya nuna cewa Allah zai daraja mutum mai kaskanci ta wurin cewa Allah zai dauke wannan mutum a jiki daga kasan inda wannan mutumin ya mika kansa cikin kaskanci. AT: "zai daraja ka"
"munanan magana akan" or "hamayya"
Yakubu yayi magana akan masubi kaman su 'yan'uwan juna ne. ambatacce maganar sun haɗa da mata da kuma maza. AT: " 'yan'uwamu masubi"
"amma kana yi kamar mutum wadda ya bada dokan"
wannan na nufin Allah ne. "Allah ne kaɖai yake bada doka ya kuma sharanta mutane
wannan tambaya Yakubu yayi amfani da ita domin ya tsauta wa masu sauraron. wannan za'a iya baiyanata kamar sanarwa ne. AT: kai mutum ne kuma baza ka iya sharanta wani mutum ba."
Yakubu yayi magana akan bayar da lokaci kamar wani kuɗi ne. "zauna a chan na shekara"
Yakubu yayi amfani da wannan tambaya domin ya kwabɓi masu sauraron ya kuma koya masubi rayuwa ta jiki bashi da amfani.za a iya bayana sa kamar sanarwa. AT: "ba wadda ya san gabe, kuma rayuwan ka ba zai dawama harabada ba"
Yakubu yayi magana akan mutane kamar hazo ne wadda yaki bayyana bayan dan lokaci kuma ya bace. AT: "kana zama na dan lokaci ne sai kuma ka mutu"
"Maimakon haka, halin ka ya zama"
"zamu jima sosai muyi abin da muka shirya. "kalmanan "mu"baya nufin Yakubu ko masu sauraron amma misaline ga masu sauraron Yakubu su duba yadda ya kamata rayuwa ya zama.
duk wadda ya san ya kamata yayi abu mai kyau amma baiye ba zunubi ne gareshi
1Ku zo yanzu, ku da kuke masu arziki, ku yi ta kuka da kururuwa domin bakin ciki iri-iri da ke zuwa gare ku. 2Arzikin ku ya rube, tufafinku kuma duk cin asu ne. 3Zinariya da azurfarku sun yi tsatsa. Tsatsar su kuwa zai zama shaida a kanku. Zai cinye naman ku kamar wuta. Kun yi ajiyar dukiyarku domin ranakun karshe.4Duba, hakin ma'aikata yana kuka - hakin da kuka hana wa wadanda suka girbe maku gonaki. Kuma kukan masu girbin ya tafi ya kai ga kunnuwan Ubangiji mai Runduna. 5Kun yi zama cikin annashuwa a duniya kuma kun tsunduma kanku. Kun sa zukatan ku sun yi kiba domin ranar yanka. 6Kun hukunta kuma kun kashe adalin mutum. Bai kuwa yi tsayayya da ku ba.7Saboda haka ku yi hakuri, 'yan'uwa, har sai zuwan Ubangiji. Duba, yadda manomi ya kan jira kaka mai amfani daga gona. Da hakuri yake jiran ta har sai ta karbi ruwa na fari da na karshe. 8Ku, ma, ku yi hakuri. Ku karfafa zukatan ku, domin zuwan Ubangiji ya yi kusa.9Kada ku yi gunaguni, 'Yan'uwana, game da juna, don kada a hukunta ku. Duba, mai shari'a na tsaye a bakin kofa. 10Dauki misali, 'yan'uwa, daga shan wuya da hakurin annabawa, wadanda suka yi magana a cikin sunan Ubangiji. 11Duba, mukan kira wadanda suka jimre masu albarka. Kun dai ji irin jimiri da Ayuba ya yi, kun kuma san nufin Ubangiji, yadda yake mai yawan tausayi da jinkai.12Fiye da komai duka, 'yan'uwana, kada ku yi rantsuwa, ko da sama, ko da kasa, ko da kowace irin rantsuwa ma. A maimakon haka bari "I" ya zama "I", in kuwa kun ce "A'a", ya zama "A'a", don kada ku fada a cikin hukunci.13Akwai wanda ke fama a tsakanin ku? Sai ya yi addu'a, akwai wanda yake murna? Sai ya raira wakar yabo. 14Akwai mara lafiya a tsakanin ku? Sai ya kira dattawan ikilisiya, sai su yi masa addu'a. Suna shafa masa mai a cikin sunan Ubangiji. 15Addu'ar bangaskiya zai warkar da mara lafiyan, Ubangiji zai tashe shi. Idan ma ya yi zunubi, Allah zai gafarta masa.16Soboda haka, ku furta zunuban ku ga juna, kuna yi wa juna addu'a, don a warkar da ku. Addu'ar mai adalci tana da karfin aiki kwarai da gaske. 17Iliya dan Adam ne kamar mu. Amma da ya nace da addu'a kada a yi ruwa, ba kuma yi ruwa a kasar ba har shekara uku da wata shida. 18Sai Iliya ya sake yin addu'a. Sammai suka ba da ruwa, kasa kuma ta ba da amfanin ta.19Ya ku 'yan'uwana, idan wanin ku ya baude wa gaskiya, wani kuma ya dawo da shi, 20wannan mutum ya sani cewa, duk wanda ya dawo da mai zunubi a hanya daga baudewar sa, zai cece shi daga mutuwa, kuma zai rufe dunbin zunubai.
Yakubu ya gargaɗe masu kuɗi game da maida hankali ga rayuwan nishaɗi da kuɗi .
AT: 1) Yakubu na bada gargaɗi mai karfi game da masubi da ke da arziki, ko 2) Yakubu na magana ne akan masu arziki marasabi. AT: " ku da kuke da kuɗi kuma kun ce kuna grimama Allah"
Yakubu ya ambata cewa mutanen za su sha wahala mai tsanani nan gaba, kuma ya rubuta game da wahalar kamar wani abu ne da take zuwa garesu. wannan kalman "bakin ciki"za 'a iya juyata kamar aikatau. AT: domin zaku sha tsananin wahala nan gaba "
Arzikin duniya bata jimawa ko kuma wata madowwamiyar daraja. Yakubu yayi magana akan waddannan abubuwa kamar sun rega sun faru. AT: "arzikin ku zai ruba, asu kuma zasu ci tufafinku. zinariyar ku da azurfarku zasu yi tsatsa"
waddannan abubuwan da aka ambata misalin abubuwa ne masu daraja ga mutane masu arziki.
An yi amfani da kalmomin nan domin a siffanta yadda zinariya da azurfa suke hasara. AT: "ke hasara ... yana yin hasara" ko " ke lalacewa ... sun lalace"
Yakubu ya rubuta akan darajan abubuwan yadda suke da hasara kamar mutum ne wadda aka masa zargi a gidan shari'a. AT: "idan Allah yayi maka shari'a hasaran dukiyan ka zai zama kamar wadda aka zargi shi a gidan shari'a. lalacewa su" (Dubi: da )
Anan ana maganar lalacewar kamar wuta ne da zai kona masushi.
Wuta anan na tunashe mutane game da hukuncin Allah mai zuwa akan dukan mugaye.
Wannan na nufin dab da lokacin da Allah zai zo ya shara'anta dukan mutane. mugaye na tunanin cewa suna ajiyan arziki domin lokaci mai zuwa, amma ba su sani da cewa suna ajiye wa kansu shari'a bane. AT: "domin idan Allah zai yi maka shari'a"
Kuɗin da yakamata ayi biya ana maganar sa kamar mutun wadda yake ihu domin rashin gaskiya da aka yi masa. AT: " hakika domin kaki ka biya wadda kayi hayar su suyi maka aiki a ganarka yanuna cewa baka yi daidai ba"
Ana maganar ihun masu girbin kamar za'a jisu a sama. AT: "Ubangiji mai runduna yaji kukan masu gribin"
Ana maganar Ubangiji kaman yana da kunnuwa kamar na mutane.
anan an kalla mutane kamar shanu, dasuke marmari suci abinci suyi kiɓa domin ayanka su abiki. koda shike ba wadda zai yi biki a lokacin shari'a. AT: "haɗamar ku ya shirya ku domin masanancin madowamiyar shari'a"
"zuciyar " an duba ya zama sakiyar begen mutane, yana kuma nufin mutum gaba ɗaya.
Wannan ba halamar "hukunci" cikin azancin shari'a wadda akan sharanta mai laifi zuwa ga mutuwa. maimakon, kokuma na nufin zuwa ga masu karfi kokuma magayen mutane wadda suke wahalar da talakoki har ga mutuwa.
" mutane da suka yi abin da ke da kyau. ba suyi" ana "adalin mutun" na nufin adallen mutane ba a gaya kuwa mutun ɗaya ba . AT: adallen mutane. ba suyi"
"yi hamayyan ku"
akarshe Yakubu ya tunashe masubi game da zuwan Ubangiji ya kuma bada wasu kananan darasi game da yadda za'a zauna wa Ubangiji
"Domin wannan ku jira da hankali"
wannan kalmar na nufin zawan yesu, lokacin da zai fara mulkinsa anan duniya ya kuma sheranta mutane. AT: "har ga zuwan Ubangiji"
Yakubu yayi misali da manomi da masubi domin ya koya masu hakuri.
Yakubu na shirya zuciyar masubi ga sa ziciya. AT: "sa zuciya" ko "sa ajiye bangaskiyar su da karfi"
"Ubangiji yayi kusan dawowa"
Yakubu na rubutawa dukan Yahudawa masubi da ke warwatse.
"akan juna"
AT: Almasihu ba zai yi maku shari'a ba
"ku saurara domin abin da zan faɗa gaskiya na kuma nada amfani: mai shari'a"
Yakubu ya kwatanta Allah, mai shari'a, kamar mutum wadda yake so ya shiga ta kofa yayi nauyin akan zuwan Allah ya yi kusa domin ya sharanta duniya. AT: "mai shari'an yayi kusan zuwa" Dubi:
" yaya annabawan dasu kayi magana acikin sunar Ubangij suka jimre wuya da zalunci"
"Suna" wannan ya tsaya a masayin mutumin Allah. AT: "da ikon Ubangiji" ko "yi maganar Ubangijiwa mutane"
"ku saurara, domin abunda inaso in faɗa gaskiyane kuma nada amfani: mun duba"
"wadda suka cigaba da bin ummurnin Allah ko da shan wuya"
wannan na da amfani 'yan'uwana:" ko "musamman' 'yan'uwana"
wannan na nufin masubi harda mata. AT: 'yan'uwa masubi"
yin "ransuwa" shene kace zaka yi abu, kokuma abu gaskiyane, kokuma manyan ikoki su rike ka ga tambayoyi. AT: kada kayi rantsuwa" ko "kada kayi alkawali"
wannan kalman "sama" da "kasa" na nufin ikoki na jiki ko na ruhu wadda ke sama ko kasa.
"kayi abin da kace zaka yi, ko kace abu gaskiyane, basai kayi rantsuwa ba"
Anan maganar yin hukunci kamar wani ya fadi,rugurguji da nauyin wani abu. AT: "Allah kuma ba zai horas da shiba"
Yakubu yayi amfani da tambayannan domin ya sa mai karatu yayi tunani akan damuwar sa. za'a iya juya ta kamar labari. AT: idan akwai wadda yake jure wa damuwa, sai yayi addu'a"
Yakubu yayi amfani da tambayan nan domin ya sa mai karatu yayi tunani akan albarkan sa. za'a iya juya wannan kamar labari' AT: idan wani yana murna,sai ya raira wakar yabo
Yakubu yayi amfani da tambayan nan domin ya sa mai karatu yayi tunani akan damuwanr sa. za'a iya juya ta kamar labari. AT: "idan Akwai mara lafiya, Sai ya kira"
"Suna" wannan ya tsaya a masayin mutumin Yesu Almasihu. AT: da ikon Ubangiji" ko "da ikon da Ubangiji ya ba su"
Marubucin ya yi magana akan Allah ya na jin addu'a marasa lafiya ya kuma warkar da su kamar addu'a da kansa ya na warkar da mutane. AT: "Ubangiji zai ji addu'ar mai bangaskiya kuma zai warkar da mara lafiya"
"Addu'ar da masu bi suke yi" ko "Addu'ar da mutane ke yi suna bada gaskiya cewa Allah zai yi yadda suka tambaya"
"Ubangiji zai warkar dashi" ko "Ubangiji zai taimakeshi ya koma ayukan sa daidai"
Ku yarda da abin da kuka yi da ba kyau wa sauran masubi domin a yafe maku.
"ga kowan ne dayan ku"
Wannan za'a iya bayyana a wata siffa. AT: "domin Allah ya warkar da kai"
An hallarar da addu'a kamar wani abu mai karfi. AT: "idan mutumin da yake biyyaya ga Allah ya yi addu'a, Allah zai yi abubuwa mai girma"
"3 ... 6"
"addu'a mai ƙosawa" ko "addu'a na ƙwarai"
"Saman" mai yuwa na nufin sararin sama, wanda ya zama shine tushin ruwa. AT: "Ruwa yana fadowa daga sararin sama"
Anan ƙasa ya hallara kamar tushin baroro.
Anan " 'ya'ya" ta tsaya a masayin dukan baroron manomi.
Wannan kalma anan zai iya nufin maza da kuma mata. AT: "'yan'uwanmu masu bi"
Anyi magana game da mai bi da ya bar dogara da kuma yiwa Allah biyayya kamar yanda tumaki kan bace daga cikin garke. Ana kuma yi magana game da mutum da ya lallashe shi kamar makiyayi da ya je neman tumakin da ya bace. AT: "duk lokacin da wani ya bar yiwa Allah biyayya, kuma wani mutum ya taimake shi ya cigaba da yin biyayyan kuma"
Yakubu na nufin Allah zai more kuzarin mutum mai zunubin ya tuba ya kuma tsira. Amma Yakubu yayi magana kamar wani mutun daban da ya ceci ran mai zunubin daga mutuwa.
Anan "mutuwa" na nufin mutuwa na ruhaniya, rabuwa da Allah na har'abada. AT: "zai cece shi daga mutuwan na ruhaniya, kuma Allah zai yafe wa mai zunubin dukan zunuban sa"
AT: 1) mutumin da ya dawo da ɗan'uwa mara biyayya, za'a yafe masa zunubansa ko 2) ɗan'uwa mara biyayya, in ya koma ga Ubangiji, zai yafe zunuban sa. Anyi maganar zunubi kamar wani abu da Allah ya rufe da ba zai gansu ba, domin ya yafe masu.
1Bitrus, manzon Yesu Almasihu, zuwa ga zababbu wadanda suke baki, a warwatse cikin Buntus, Galatiya, kappadokiya, Asiya, da Bitiniya. 2Bisa ga rigasanin Allah Uba, Ta wurin tsarkakewar Ruhu, zuwa biyayya da yayyafar jinin Yesu Almasihu. Alheri da salama su yawaita a gareku.3Albarka ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurin jinkansa mai girma, ya maya haihuwarmu zuwa bege mai rai ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu. 4Zuwa gado marar lalacewa, marar baci, ba kuma zai kode ba. Wanda aka kebe a sama dominku. 5Ku da ikon Allah ya kiyaye ta wurin bangaskiya domin ceto wanda za'a bayyana a karshen zamanai.6Cikin wannan kuna murna da yawa, duk da ya ke ya zama wajibi gare ku yanzu ku yi bakin ciki, a cikin jarabobi iri iri. 7Wannan kuwa da nufin a iske aunawar bangaskiyarku ne, bangaskiyar da tafi zinariya daraja, wadda takan lalace ko da an gwada ta da wuta. Wannan ya faru domin bangaskiyan nan taku ta jawo maku yabo da girma da daukaka a bayyanuwar Yesu Almasihu.8Wanda kuke kauna, ko da yake baku ganshi ba. Ko da yake baku ganinsa yanzu, duk da haka kun bada gaskiya gare shi murnar da ku ke yi kwarai da farin ciki wanda tafi gaban a fadi cike da daukaka. 9Kuna karbar sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku. 10Annabawan da su ka yi annabcin ceton da ya zama naku su ka yi bidassa suka bincike kuma da himma.11Sun nemi su san ko wanene da kuma kowanne lokaci ne Ruhun Almasihu da ke cikinsu yake bayyana ma su. Wannan ya faru ne sa'adda yake gaya ma su tun da wuri game da shan wahalar Almasihu da kuma daukakar da zata biyo baya. 12An kuwa bayyana wa annabawan cewa ba kansu suke hidimtawa ba, amma ku suke yi wa hidima. Wannan shine abin da suke yi game da abin da aka rigaya aka gaya maku, ta wurin wadanda da Ruhu mai Tsarki ya bishe su. Wanda aka aiko daga sama. Wadannan sune abubuwan da mala'iku ma suka yi marmarin a bayyana masu.13Domin wannan fa ku natsu. Ku yi dammara a hankalinku. Ku kafa begenku sarai akan alherin da za'a kawo maku a lokacin bayyanuwar Yesu Almasihu. 14Kamar 'ya'ya masu biyyaya, kada ku biyewa sha'awoyinku na da a zamanin jahilcinku.15Amma yadda shi wanda ya kira ku mai tsarki ne, kuma ku zama da tsarki cikin dukkan al'amuranku. 16Domin a rubuce yake, "Ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne." 17Idan ku na kira bisa gare shi "Uba" shi wanda yake hukuntawa ba da tara ba, amma gwar-gwadon aikin kowane mutum, sai kuyi zaman bakuncinku da tsoro da bangirma.18Kun san cewa ba da azurfa ko zinariya mai lalacewa aka fanshe ku ba, daga halinn wauta da kuka gada daga wurin iyayenku. 19Maimakon haka an fanshe ku da jinin Almasihu mai daraja, marar aibu kamar na dan rago.20An zabi Almasihu tun kafin kafawar duniya, amma a karshen zamanu ya bayyanu a gare ku. 21Ku da kuka bada gaskiya ga Allah ta wurinsa, wanda ya tashe shi daga matattu ya kuma bashi daukaka domin bangaskiyarku da begenku su kasance cikin Allah.22Da shike kun tsarkake rayukanku cikin biyayyar ku ga gaskiya zuwa ga sahihiyar kauna ta 'yan'uwa, sai ku kaunaci junanku da zuciya mai gaskiya. 23da shike an sake hai'huwarku ba daga iri mai lalacewa ba amma daga iri marar rubewa, ta wurin maganar Allah wadda take rayuwa ta kuma dawwama.24Gama "dukkan jiki kamar ciyawa yake, dukkan darajarsa kuwa kamar furen ciyawa take. Ciyawa takan yi yaushi, furenta ya kan yankwane ya fadi, 25amma maganar Ubangiji tabbatacciya ce har abada. "Wannan ita ce maganar bishara wadda akayi maku wa'azinta."
Bitrus ya nuna kansa a matsayin marubucin, ya kuma gaishe da masubi waɗanda yake rubuta musu.
Bitrus ya yi magana game da masu karanta wasiƙarsa kamar mutane da ke zama nesa da gidajensu cikin ƙasashe dabam-dabam.
Da sauran wuraren da Bitrus ya ambata, "Kaffadokiya" da "Bitiniya" yankin Roma ne da ake kira a yau kasar Toki.
"zaɓaɓɓu waɗanda Allah Uban ya zaɓa ... bisa ga rigasaninsa." Allah ya zaɓe su bisa ga rigasaninsa.
"rigasanin" ana iya juya shi cikin magana. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) Allah ya shirya abin da zai yi a kan lokaci. AT: "abin da Allah Uban ya shirya a da" ko 2) Allah ya san abin da zai faru a kan lokaci. AT: "abin da Allah Uban ya sani tun da wuri"
A nan "jinin" na nufin mutuwar Yesu. kamar yadda Musa ya yayyafa jini a kan mutanen Isra'ila don nuna alamar alkawarinsu da Allah, haka masubi suna cikin alkawari da Allah saboda mutuwar Yesu.
Wannan nassin na maganar alheri kamar wani abu ne da masubi za su iya samu, da kuma salama kamar wani abu ne da zata iya ƙãruwa. Alheri wata hanya ce ta kirki da Allah ke yin dangantaka da masubi, salama kuma ita ce yadda masubi suke rayuwa cikin kwanciyar rai da murna tare da Allah.
Kalman nan "mu" na nufin Bitrus ne da kuma waɗanda ya rubuta musu wasiƙar.
"ya sa an săke haihuwarmu"
Kuna iya yin amfani da aikatau ku juya wannan. AT: "da gabagaɗi muna sa rai za mu samu gădo"
An yi maganar samun abin da Allah ya alkawarta wa masubi kamar wata kayar gădo ce da kuma arziki daga wani ɗan iyali.
Bitrus ya yi amfani da waɗannan jimloli don ya bayyana cewa gădon wani abu ne mara aibi kuma madawwami ne.
AT: "Allah yana keɓe shi a sama domin ku"
AT: "Allah yana kiyaye ku"
A nan "iko" wata hanya ce ta cewa Allah yana da ƙarfi kuma shi mai iya tsare masubi ne.
A nan "bangaskiya" na nufin cewa masubi sun dogara ga Almasihu. AT: "saboda bangaskiyar ku"
AT: "cewa Allah yana shirye ya bayyana"
Kalman nan "wannan" na nufin dukan albarkun da Bitrus ya ambata a ayoyin da ke baya.
kamar yadda wuta tana sabunta zinariya, wahala tana gwada yadda dogarar masubi ga Almasihu take.
Allah yana so ya gwada yadda dogarar masubi take a cikin Almasihu.
Bangaskiya ta fi zinariya daraja, domin zinariya bata dawwamma ko an sake sabunta ta da wuta.
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) cewa "Allah zai ɗaukaka ku sosai" saboda bangaskiyar ku ko 2) cewa "bangaskiyar ku zata jawo yabo, girma da ɗaukaka" ga Allah.
"a sa'ad da Yesu Almasihu zai bayyana." Wannan na nufin dawowar Almasihu. AT: "a sa'ad da Yesu Almasihu ya bayyana ga dukan mutane"
"farin ciki mai ban mamaki da kalmomi ba za su iya bayyana ta ba"
Anan kalman nan "rayuka" na nufin mutum. Kalman nan "ceto" ana iya juya ta da aikatau. AT: "ceton ku" ko " Allah ya cece ku"
Kalmomin nan na ba da ra'ayoyi biyu kamar waɗansu al'amurra ne ko kuma abubuwa. "Ceto" na nufin abin da Allah ya yi don ya cece mu, ko kuma abin da ya faru ta dalilin sa. "Alheri" na nufin yadda Allah ke yin dangantaka da masubi cikin kirki.
kalmomin nan "bin diddigi" na nufin abu daya ne da "bincike." waɗannan kalmomin na nanata wuyar da annabawa suka sha don ƙoƙarin fahimtar wannan ceton." AT: "matsanaciyar dubawa da kula"
Bitrus ya cigaba da magana game da binciken annabawan game da ceto.
"Sun yi ƙoƙarin neman gaskiyar"
Wannan na nufin Ruhu Mai Tsarki.
AT: "Allah ya bayyana wa annabawan"
"cewa mala'iku ma suna so su fahimta"
"domin wannan, yi ɗammara." Bitrus ya yi amfani da wadannan kalmomi "don haka" don ya koma baya zuwa ga dukkan abin da ya faɗa game da ceto, bangaskiyar su, da kuma yadda Ruhun Almasihu yake bada wahayin ga annabawan.
Yin ɗammara a hankalinku na nufin shirin aiki ƙwarai da gaskiye. Wannan na samuwa ne daga al'adar shigar da ƙasar riga karkashin ɗamarar dake kewaye da ƙugu domin iya tafiya cikin sauƙi. AT: "ku shirya zukatanku"
A nan kalmar nan "natsu" na nufin hankali mai tsabta da kuma shiri. AT: "Kula da tunaninku" ko "yi kula da abinda ku ke tunani"
AT: "Alherin da Allah zai kawo maku"
Wannan na nufin dawowar Yesu Almasihu. Dubi yadda kuka juya wannan cikin [1 Bitrus 1:7]. AT: "a sa'ad da Yesu Almasihu ya bayyana ga dukan mutane"
"kada ku yi sha'awan abin nan kuma" AT: "kada ku yi rayuwar biye wa sha'awace-sha'awacen"
Wannan na nufin saƙon Allah cikin Littafi Mai Tsarki. AT: "Gama kamar yadda Allah ya faɗa"
Anan kalman nan "Ni" na nufin Allah.
Bitrus ya yi magana game da masu kara wasiƙar kamar su mutane ne da ke zama cikin kasar da ba tasu ba wadda take nesa da gida. AT: "ku yi amfani da lokacin da kuke zama inda ba gidan ku ba"
AT: "Allah ya fanshe ku"
A nan "jini" na madadin mutawar Almasihu bisa giciye.
Yesu ya mutu a madadin hadaya don Allay ya yafe wa mutane zunubansu. AT: "kamar dan rago mara aibu ko tabo da firistocin yahudawa ke yin hadaya" Dubi:
Bitrus ya bayyana ma'ana ɗaya ta hanyoyi dabam-dabam guda biyu don nanata tsarkin Almasihu. AT: "babu lahani"
AT: "Allah ya zaɓi Almasihu"
Ku na iya juya wannan da jumla ta aikatau. AT: "Kafin Allah ya halici duniya"
AT: "Allah ya bayyana shi a gare ku"
A nan "tashe shi," na nufin sa wadda ya mutu ya sake yaruwa kuma. AT: "wadda ya sa shi ya rayu, hakannan kuwa ba ya cikin matattu"
"kuma ɗaukaka shi" ko "kuma nuna cewa shi maɗaukaki ne"
A nan kalmar nan "rayuka" na nufin mutum. AT: "kun tsarkake kan ku"
A nan "tsabta" na nufin samun karbuwa ga Allah.
Kuna iya juya wannan ta wurin yin amfani da jumla ta aikatau. AT: "ta wurin yin biyayya ga gaskiyar"
Wannan na nufin ƙauna tsakanin masubi.
A nan "zuciya" na nufin tunani da kuma shauƙin mutum. A ƙaunaci wani "daga zuciya" na nufin a ƙaunaci wani sasai da dukan miƙa kai. AT: "ƙaunaci junanku da himma da kuma miƙa kai"
Ma'anoni masu yiwuwa su ne cewa Bitrus ya yi magana game da maganar Allah ko dai 1) kamar iri dake girma ya kuma haifi sabon rayuwa cikin masubi ko 2) kamar wata ƙanƙanin ƙwai na jiki miji ko mace dake sa yaro ya yi girma cikin mace.
iri da ba zai ruɓa ba, ko ya bushe, ko kuma ya mutu
Bitrus ya yi magana a kan maganar Allah kamar tana raye har abada. Allah ne ke raye har abada, kuma dokokin sa da alkawuran sa sun dawwama har abada.
Kalmar nan "jiki" na nufin dukan 'yan Adam. annabi Ishaya ya kwatanta 'yan adam duka kamar ciyawa ne da ke girma da kuma mutuwa da sauri. AT: "Dukan mutane za su mutu kamar yadda ciyawa ke mutuwa"
A nan kalmar nan "daraja" na nufin kyakkyawa ko nagarta. Ishaya ya kwatanta abubuwan da mutane ke duba a matsayin abu mai kyau game da 'yan adam da fure dake mutuwa da sauri. AT: "nagartar 'yan adam na tsayawa, kamar yadda fure ke mutuwa nan da nan"
"sakon da ke zuwa daga wurin Ubangiji"
A nan kalmar nan "wannan" na nufin "maganar Ubangiji"
AT: "bisharar da mun sanar da ku"
1Saboda haka sai ku tube dukkan keta, rikici, da riya, kishi, da dukkan mugun zance. 2Kammar jarirai, sababbin haihuwa, ku yi marmarin madara mai ruhaniya wadda take sahihiya, domin ta wurinta kuyi girma zuwa ceto, 3idan kun dandana Ubangiji mai-alheri ne.4Kuzo gareshi rayayyen dutse wanda mutane suka ki, amma zababbe ne mai-daraja wurin Allah. 5Ku kuma kamar rayayyun duwatsu ana gina ku gida mai ruhaniya, domin ku zama tsarka-kan fristoci, domin ku mika hadayu masu ruhaniya abin karba ga Allah ta wurin Yesu Almasihu.6Gama nassi ya ce, "Ga shi na sanya dutse na kan kusurwa, zababe, mai daraja a cikin Sihiyona. Duk wanda ya bada gaskiya gareshi ba zaya kunyata ba."7Daraja a gareku take ku da kun bada gaskiya. Amma, ga wadanda suka ki bada gaskiya, "Dutsen da magina suka ki shine aka mai she shi kan kusurwa". 8kuma, "Dutsen sa tuntube da fa na sa tuntube. "Sun yi tuntube, da shike sun ki biyayya da maganar, an kuwa kaddara su ga wannan.9Amma ku zababben jinsi ne, kungiyar fristoci ba-sarauci, al'umma mai-tsarki, jama'ar mallakar Allah, domin ku sanar da mafifitan al'amuran wanda ya kiraye ku daga chikin duhu zuwa cikin haskensa mai'ban al'ajibi. 10Ku da ba jama'a ba ne a da, amma yanzu jama'ar Allah ne. Da baku sami jinkai ba, amma yanzu kun sami jinkai.11Kaunatattu, ina rokon ku misalin baki da masu-tafiya kuma, ku guje wa sha'awoyin jiki wadanda ke yaki da rai. 12Ku kasance da kyakkyawan hali a cikin al'ummai, domin, sa'adda suke kushen ku kamar masu aikata mugunta, sai su lura da nagargarun ayyukanku su kuma daukaka Allah a ranar zuwansa.13Kuyi biyayya ga kowacce hukuma ta mutane sabili da Ubangiji, ko ga sarki domin shi ne shugaba. 14Ko kuwa ga masu mulki aikakkunsa ne domin su hori masu aikata mugunta da yabawa masu aikata nagarta. 15Gama wannan nufin Allah ne, ta wurin aikin kirki ku, kwabi jahilcin mutane marassa hikima. 16Kamar 'yan'tattu kada ku mori 'yan'cinku kamar mayafin mugunta, amma ku zama kamar bayin Allah. 17Ku girmama dukkan mutane. Ku kaunaci 'yan'uwa, kuji tsoron Allah. Ku girmama sarki.18Ku barori, kuyi biyayya ga iyayen gidanku da dukkan bangirma, ba ga nagargaru da masu saukin kai ba, amma har ga miskilai. 19Gama abin yaba wa ne idan sabili da lamiri zuwa ga Allah in wani ya jimre da shan zalunci. 20Gama wacce riba ke nan idan kun yi zunubi ana horonku kuna jimrewa da hukuncin? amma idan kunyi aikin kirki kuka sha wuya a kansa kuka yi hakuri, wannan abin karba ne wurin Allah.21Gama akan haka aka kiraye ku, gama Almasihu ma yasha azaba saboda ku, ya bar maku gurbi kubi sawunsa. 22Bai taba yin zunubi ba, ba'a taba jin yaudara a bakinsa ba. 23Da'a ka zage shi bai mai da zagi ba. Da ya sha azaba, bai yi kashedi ba, amma ya mika kansa ga wanda yake yin shari'ar adalci.24Shi da kansa ya dauki zunubanmu a cikin jiki nasa ya kai su bisa itace, domin kada a iske mu cikin zunubi, amma muyi rayuwa ga adalci. Ta wurin raunukansa ne kuka warke. 25Dukkanku da kun bata kuna yawo kamar batattun tumaki, amma yanzu kun dawo wurin makiyayi da mai tsaron rayukanku.
Bitrus ya cigaba da koyar da masu karanta wasiƙar sa game da tsarki da kuma biyayya.
An yi maganar waɗannan ayukan zunubi kamar waɗansu abubuwa ne da mutane ke iya wurgawa. Kalman nan "Soboda haka" na nufin komawa zuwa ga abinda Bitrus ya faɗa game da zaman tsarki da biyayya a baya. AT: "don haka, ku tuɓe kowane mugun abu, da riya, da ƙishi, da kowane mugun zance" ko "don haka, ku bar aikata mugunta, ko ruɗu, ko riya, ko ƙishi ko mugayen zance"
Bitrus ya yi magana da masu karanta wasiƙar sa kamar jarirai. Jarirai suna bukatar tsantsan abinci wanda za su iya narkewa da sauki. haka kuma masubi suna bukatar tsantsan koyarwar daga maganar Allah. AT: Kamar yadda jarirai suna marmarin mama daga uwarsu, haka kuma lallai ne ku yi marmarin tsantsan madaran ruhaniya"
"matuƙar marmari" ko "yi begen"
Bitrus ya yi magana game da maganar Allah kamar wata madaran ruhaniya ce da ke da amfani sosai ga 'ya'ya
A nan kalmar nan "ceto" na nufin a sa'ad da Allah ya kammala ceton mutanensa a lokacin da Yesu ya dawo (Dubi 1 Bitrus 1:5).
Bitrus ya yi maganar karuwa cikin sanin Allah da kuma amincin masubi ga Allah kamar su 'ya'ya ne da ke girma.
A nan ɗanɗana na nufin mutum ya jin abu da kansa. AT: "In ka ji alherin Ubangiji zuwa gare ka"
Bitrus ya fara faɗin misalin Yesu da masubi a matsayin rayayyun duwatsu.
Bitrus ya yi magana game da Yesu kamar shi dutse ne cikin gini. AT: "Zo gare shi, wanda shi kamar dutsen gini, amma rayayye, ba mataccen dutse ba"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "wanda shi rayayyen dutse ne" ko 2) "wanda shine dutsen da ke bada rai."
AT: "wanda mutane suka ƙi"
AT: "amma wanda Allah ya zaɓa"
Kamar yadda mutane ke gina haikali a Tsohon Alkawari, masubi kayan da Allah ke amfani da shi ya gina gidan wanda zai yi rayuwa a cikin ta ne.
Bitrus ya kwatanta masu karatunsa da duwatsun da ke raye.
AT: "da Allah ke ginawa zuwa ga gidan ruhaniya"
Anan matsayin firist na nufin frist wanda ke cika aikin sa na wajib
An yi maganar nassin kamar wata akwati. Wannan na nufin kalmomin da mutum ke karantawa cikin nassin. AT: "Wannan ita ce abin da annabin ya rubuta cikin nassosin tun dã.
A nan "ga shi" na jan hankalin mu da mu yi kula da labari mai ban mamaki da ke zuwa.
Allah ne wanda ya zaɓi dutsen. AT: "dutsen kusurwa mai muhimmanci, wanda na zaɓa"
Annabin ya yi magana game da Almasihu cewa shi dutse ne mai muhimmanci na gini.
Wannan na nufin mutane, kamar masu gini,sun ƙi Yesu, amma Allah ya maishe shi dutse mafi muhimanci na gini.
AT: "dutsen da maginan suka ƙi"
Wannan na nufin dutse mafi muhimanci a gini kuma na nufin abu ɗaya da "dutsen kusurwa" cikin [1 Bitrus 2:6].
Waɗannan batutuwa guda biyu na da ma'ana kusan iri ɗaya. Tare, su na nanata cewa mutane za su yi fushi da wannan "dutsen" wanda na nufin Yesu. AT: "dutse wanda mutane za su yi tuntuɓe a kai"
A nan "maganar" na nufin saƙon bishara. Yin rashin biyayya na nufin ba su gaskata ba. "tuntuɓe don ba su gaskanta da saƙo game da Yesu ba"
AT: "abin da Allah ya ƙaddara gare su"
za ku iya bayyana cewa Allah ne ya zaɓe su. AT: "mutane wanda Allah ya zaɓa"
ma'anoni masu yiwuwa 1) "kungiyar sarakuna da kungiyar firistoci" ko 2) "kungiyan firistoci wanda ke yi wa sarki hidima."
"mutanen Allah"
"wanda ya kira ku ku fita"
A nan "duhu" na nufin yanayin mutane masu zunubi wanɗanda ba su san Allah ba; "haske" na nufin yanayin mutane wanɗanda sun san Allah suna kuma aikata adalci. AT: "daga rayuwar zunubi da rashin sanin Allah zuwa ga rayuwa ta sanin sa da kuma faranta masa rai"
wanɗannan kalmomin na nufin abu ɗaya ne. Bitrus ya yi magana game da masu karatunsa a matsayin mutane da ke rayuwa a kasar da ba nasu ba, nesa da gidan. Dubi yadda kuka juya "baƙi" cikin [Bitrus 1:1]
A nan jiki na nufin halin mutuntaka ta 'yan adam cikin wannan duniya mai shuɗewa. AT: "don kada mu bada zarafi ma sha'awace-sha'awacen zunubi"
A nan kalmar nan "zuciya" na nufin rayuwar ruhaniyar mutumin. Bitrus ya yi magana game da sha'awace-sha'awacen zunubi kamar sojoji ne da ke ƙoƙarin rushe ruhaniyar masubi. AT: "biɗan rushe rayuwar ruhaniyar ku"
Ana iya juya "hali" da aikatau. AT: "ku nuna halin kirki" ko "ku nuna halin kirki ta hanya mai kyau"
"in sun zarge ku da"
Ana iya juya "ayyuka" cikin aikatau. AT: "za su lura da nagargarun abubuwan da ku ke yi"
"a ranar da ya zo." Wannan na nufin ranar da Allah zai shar'anta dukkan mutane. AT: "sa'ad da ya zo don ya shar'anta kowa"
Ma'anoni masu yiwuwa 1) cewa tawurin biyayya ga hukumomi, su na biyayya ga Ubangiji wanda ya kafa waɗannan hukumomin ko 2) ta wurin biyayya ga hukumomin, za su girmama Yesu wanda kansa ma ya yi biyayya ga hukumomi.
"sarki wanda shine mafi girma ciki hukumar mutane"
AT: "wanda sarkin ya aika su hori"
"ta wurin aikin nagarta, za ku kwaɓi mutane marasa hikima daga faɗin abubuwan da ba su sani ba"
Bitrus ya yi maganar yanayinsu a matsayin 'yantattun mutane kamar wani abu ne da bai kamata su yi amfani da shi don ɓoye halin zunubi ba. AT: "hujjar yin mugayen abubuwa"
Wannan na nufin dukan masubi.
A nan kalmomin nan "nagari" da "saukin kai" na da ma'ana kusan iri ɗaya na kuma nanata cewa iyayen gidan nan na yi wa bayin su alheri. AT: waɗannan iyayen giji masu alheri"
"marasa tausayi" ko "marasa ladabi ga mutane"
"ta cancanci yabo" ko "ta faranta wa Allah rai"
Ma'anoni masu yiwuwa na asalin wannan nassi suna kamar haka 1) cewa wannan mutum ya karɓi wahala saboda ya san cewa yana biyayya ga Allah ko 2) cewa wannan mutum ya iya jumre hukunci mara adalci saboda ya san cewa Allah ya san yadda yake shan wahala.
Bitrus ya yi wannan tambaya don ya nanata cewa babu wani abin yabo game da shan wahala don yin abin da ba daidai ba. AT: Gama babu wata riba ... in an sha hukunci."
AT: "sa'annan wani ya hukunta ku"
AT: "kun sha wuya sa'ad da wani ya hukunta ku"
A nan kalmar nan "wannan" na nufin jumrewar masubi a sa'ad da suke shan wahala don aikata nagarta, kamar yadda Bitrus ya bayyana. AT: " Allah ya kiraye ku ga wannan"
"don ku bi sawunsa." Bitrus ya yi magana game da bin gurbin Yesu ta hanyar shan wuya kamar wani na tafiya a tafarkin Yesu. AT: "don ku kwaikwayi halin sa"
AT: "babu wani kuwa wanda ya sami yaudara a bakin sa"
A nan "zagi" shi ne a yi maganar ashar ga mutum. AT: " Da mutane suka zage shi, ba mai da zagin ba"
"ya danƙa kansa ga wanda ke shari'ar adalci." Wannan na nufin ya dogara ga Allah ya dauke kunyar da aka sa a kansa daga waɗanda suka tsananta masa.
Tare da nanaci, wannan na nufin Yesu ne.
Anan "ɗauke zunubanmu" na nufin ya sha wahalar hukunci saboda zunubanmu. AT: "sha wahalar hukunci saboda zunubanmu a cikin jikin sa bisa itace"
Wannan na nufin giciye wanda Yesu ya mutu a kai, wanda aka yi ta da itace.
AT: "Allah ya warkar da ku don mutane sun yi masa rauni"
Bitrus ya yi magana game da masu karatunsa kafin su gaskata da Almasihu kamar su na kama da tumakin da ke yawo ba manufa.
Bitrus ya yi magana game da Yesu kamar shi makiyayi ne. Kamar yadda makiyayi ke tsaron tumakin sa, Yesu yana tsaron waɗanda sun dogara a gare shi.
1Haka ku kuma da kuke matan aure, kuyi biyayya da na ku mazajen, domin in har wadansunsu basa biyayya da maganar Allah, halin matansu ya shawo kansu ba tare da magana ba, 2Domin sun ga tsattsakan halinku da ladabinku.3Haka ma adonku kar ya zama na kwalliyar waje kitson kai, kayan zinariya ko tufafi masu kawa. 4Amma bari adon ya zama na mutum na cikin zuciya, kuma adon ya zama kyan nan marar dushewa, na kamun kai da natsatsen ruhu, wanda yake da daraja a gaban Allah.5Haka tsarkakan mata su ka yi ado kamar haka. Suka dogara ga Allah suka yi biyayya ga mazajensu. 6Ta haka Saratu ta yi biyayya ga Ibrahim ta kira shi "ubangiji". Yanzu ku 'ya'yantane in dai kun yi aiki nagari, idan kuma ba ku ji tsoron wahala ba.7Kamar yadda na fada wa matan aure haka ma mazaje, ku zauna da mata da sanin su raunana ne abokan tarayya ne na karbar baiwar rayuwa. Ku dinga yin haka domin a rika jin addu'oinku.8Daga karshe, dukanku ku hada hankulanku, ku zama masu juyayi, masu kauna kamar 'yan'uwa, masu taushin zuciya, masu tawali'u. 9Kada ku rama mugunta da mugunta ko zagi da zagi. A maimakon haka ku cigaba da sa albarka, gama sabili da haka ne musamman aka kiraye ku, domin ku gaji albarka.10"Wanda duk yake so ya more a rayuwarsa ya kuma ga kwanaki masu alheri, to fa, ya kame harshen sa daga mugunta da lebensa daga maganganun yaudara. 11Ya rabu da mugunta ya aikata abin da ke nagari. Bari ya nemi zaman salama ya kuma dimanceta. 12Idanun Ubangiji suna duban adalai, kunnuwansa kuma suna sauraron roke rokensu. Amma fuskar Ubangiji tana gaba da masu aikata mugunta."13Wanene ya isa ya cuce ku idan kun himmatu ga yin abin da ke nagari? 14Amma idan kuna shan wuya saboda adalci, ku masu albarka ne. Kada ku ji tsoron abin da su ke tsoro. Kada ku damu.15Maimakon haka, ku kebe Ubangiji a cikin zukatanku cewa shi mai tsarki ne. Kullum ku zauna da shiri domin ku amsa wa mai tambayar ku dalilin sa begenku ga Allah. Amma fa kuyi haka tare da tawali'u da bangirma. 16Ku zama da tsatsakan lamiri domin mutanen da ke zargin rayuwarku mai kyau cikin Almasihu, su ji kunya domin suna maganar gaba da ku kamar ku mugaye ne. 17Ya fi kyau, a sha wuya akan aiki nagari, idan nufin Allah ne, da a sha wuya sabili da mugun aiki.18Almasihu ya sha wahala sau daya tak sabili da zunubai. Shi da ya ke mai adalci ya sha wahala domin mu marasa adalci, domin ya kawo mu ga Allah. Aka kashe shi cikin jiki, amma aka rayar da shi cikin Ruhu. 19A Ruhu ne, ya je ya yi wa'azi ga ruhohin da ke a yanzu cikin kurkuku. 20Sun yi rashin biyayya ne sa'adda hakurin Allah yake jiransu a lokacin Nuhu a zamanin sassaka jirgin ruwa, sai Allah ya tsirar da mutane kalilan wato rayuka takwas daga cikin ruwa.21Wannan kwatancin baftismar da take cetonmu yanzu ne, ba kamar ta wanke Dauda daga jiki ba, sai dai ta rokon Allah da lamiri mai kyau ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu. 22Ya hau sama. Yana dama ga Allah. Mala'iku, da mulkoki da masu iko dole su yi masa biyayya.
Bitrus ya fara magana da matan aure.
Daidai kamar yadda masubi za su yi "biyayya ga kowane hukuma ta mutane" [1 Bitrus 2:13] da kuma bayi su "yi biyayya" ga iyayen gijinsu [1 Bitrus 2:18], matan aure su yi biyayya ga mazajen su. Kalmomin nan "biyayyay", "bin" da kuma "mika kai" ana iya juya su ta wurin yin amfani da kalma ɗaya.
A nan "maganar" na nufin saƙon bishara. Rashin biyayya na nufin basu gaskata ba. Dubi yadda ku ka juya magana makamancin haka cikin [ 1 Bitrus 2:8]. AT: "Waɗansu mazaje basu gaskata da saƙo game da Yesu ba"
"mai yiwuwa a rinjaye su su gaskata da Almasihu." Wannan na nufin cewa mazajensu da ba su gaskata ba za su zama masubi. AT: "za su iya zama masubi"
"ba tare da matan ta yi wani magana ba." A nan "magana" na nufin wani abin da matan za ta iya faɗa game da Yesu.
Wannan kalmar "halinku" ana iya juya ta cikin aikatau. AT: "za su gani cewa kuna da tsattsarkan hali da ladabi"
Ma'anoni masu yiwuwa 1) "tsattsarkan halinku gare su da kuma yadda kuke girmama su" ko 2) "tsantsan halinku gare su da kuma yadda kuke girmama Allah."
Bitrus ya cigaba da magana da matan aure.
Wannan kalmar "ta" na nufin biyayyar matan auren da kuma halin su ga mazajen su.
A nan kalmomin nan "mutum na cikin zuciya" da "ziciya" na nufin ɗabi'a na ciki da kuma halayya na mutum. AT: "yadda ka ke a ciki" )
"kamun kai da halin zaman lafiya." A nan kalmar nan "natsatse" na nufin "zaman lafiya" ko "natsuwa." Kalmar nan "ruhu" na nufin halin mutum ko hali.
Bitrus ya yi maganar ra'ayin Allah game da mutum kamar mutumin na tsaye a gabansa. AT: "Wanda Allah ya duba cewa yana da daraja"
cewa shi ubangijinta, wato, maigidanta
Bitrus ya ce mata masubi waɗanda sun yi kamar yadda Saratu ta yi ana iya ce da su kamar su ainihin 'ya'yan ta ne.
Wannan na nufin yadda Saratu da waɗansu matan auren ma da suke tsoron Allah suka yi biyayya ga mazajensu cikin [1 Bitrus 3:5-6].
Bitrus ya yi magana game da mataye kamar su akwati ne, kamar yadda maza wani lokaci a kan yi magana a kansu haka. Ana iya juya kalman nan "fahimta" cikin aikatau. AT: "matan aure, tare da fahimtar cewa mace raunanar abokiyar tarayya ce"
ku na iya juya wannan ta wurin yin amfani da fi'ilin magana. AT: "girmama su don ta wurin alheri za su karbi rai madawami wanda Allah ke bayarwa"
An cika maganar "rai madawami" kamar wani abu ne da mutane ke gada.
A nan "wannan" na nufin yadda mazajen aure za su bi da matayen su. AT: "Ku yi rayuwa da matayen ku a wannan hanya"
A "hana" ita ce sa wani abu kada ya faru. AT: "don kada wani abu ya hana addu'o'inku ga karɓuwa" ko "don kada wani abu ya hana ku addu'a kamar yadda ya kama"
"ku zama masu ra'ayi ɗaya ku kuma" ko "zama masu hali iri ɗaya ku kuma"
zama masu hankali da tausayi ga waɗansu
Bitrus ya yi magana a kan daukan mataki game da halin wani mutum kamar biyan bashin waɗannan halayyan. AT: "Kada ku yi mugunta ga wani wanda ya yi muku mugunta ko kuwa zagi ga wanda ya zage ku"
Kuna iya bayyanawa a fili wanda da za a sa masa albarka. AT: "ku cigaba da sa wa waɗanda suka yi muku mugunta ko sun zage ku, albarka"
AT: "sabili da wannan ne Allah ya kiraye ku"
Bitrus ya yi maganar samun albarkan Allah kamar karɓar gado ce. AT: "don ku karɓi albarkar Allah a matsayin dauwamammen mallaka"
Waɗannan maganganu biyun na nufin abu ɗaya ne kuma na nanata sha'awar samun rayuwa mai kyau.
A nan an yi maganar samun abubuwa masu kyau kamar ganin abubuwa masu kyau. Kalmar nan "kwanaki" na nufin dukan rayuwar mutum. AT: "samun abubuwa masu kyau cikin rayuwa"
Kalmomin nan "harshe" da "leɓe" na nufin mutumin da ke magana. Waɗannan na nufin abu ɗaya na kuma nanata dokan cewa kada ka yi karya. AT: "daina faɗin mugayen abubuwa da kuma abubuwa yaudara"
A nan "juyo" na nufin a bar yin wani abu. AT: "ya bar aikata abu mara kyau"
Kalman nan "idanu" na nufin iyawar Ubangiji na sanin abubuwa. An yi maganar cewa Ubangiji ya yarda da adalai kamar yana ganin su. AT: "Ubangiji na ganin adalan" ko "Ubangiji ya yarda da adalai"
Kalman nan "kunnuwa" na nufin cewa Ubangiji ya na sane da abin da mutane ke faɗi. Cewar Allah na jin maganar roƙe-roƙensu na nufin cewa yana kuwa amsa su. AT: "yana jin roƙe-roƙensu" ko "yana amsa roƙe-roƙensu"
Kalmar nan "fuska" na nufin nufin Ubangiji ya yi gaba da maƙiyansa. An yi maganar gaba da wani kamar a ce an sa fuskar wani gaba da mutumin. AT: "Ubangiji na gaba"
Bitrus ya yi wannan tambaya don ya nanata cewa ba mai yiwuwa bane wani ya cuce su in sun yi abubuwan da ke nagari. AT: "Babu wani da zai cuce ku in kun yi abin da ke nagari."
Ku na iya juya wanna da fi'ilin magana. AT: "shan wuya saboda kun yi abin da ke daidai"
AT: "Allah zai albarkace ku"
Waɗannan maganganun na da ma'ana kusan iri ɗaya, na kuma nanata cewa kada masubi su ji tsoron waɗanda ke tsananta masu. AT: "Kada ku ji tsoron abin da mutane za su yi muku:
A nan kalman nan "su" na nufin duk wanda mai yiwuwa ke ƙoƙarin cutan waɗanda Bitrus ke rubuta masu.
"Maimakon zama cikin damuwa, keɓe"
Kalmomin nan "keɓe Ubangiji Almasihu ... mai tsarki ne" na nufin yarda da tsarkin Almasihu. A nan "zuciya" na nufin "cikin mutum." AT: "Yarda a tsakanin ku cewa Ubangiji Almasihu mai tsarki ne" ko "a tsakanin ku, ku girmama Ubangiji Almasihu don shi mai tsarki ne"
Kalmar nan "mu" ya shafi mutanen da Bitrus ke rubuta musu. (Dubi:"
Ya na iya yiwuwa Bitrus na nufin cewa Almasihu ya mutu don ya haɗa dangantaka tsakanin mu da Allah
A nan "jiki" na nufin jikin Almasihu; bisa ga jiki, an kashe Almasihu. AT: "Mutane sun kashe Almasihu cikin jiki"
AT: "ruhun ya rayar da shi"
Ma'anoni masu yiwuwa 1) ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki 2) kasancewa cikin ruhu.
Ma'anoni masu yiwuwa 1) "Ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki, ya tafi" ko 2) "cikin ruhu ya tafi."
Ma'anoni masu yiwuwa na kalmar nan "ruhohi" 1) "mugayen ruhohi" ko 2) "ruhohin mattattun mutane."
Kalman nan "hakkuri" na nufin Allah kansa. Bitrus ya rubuta game da hakkurin Allah sai ka ce mutum ne. AT: "sa'ad da Allah yana jira cikin haƙuri"
AT: "a lokacin Nuhu, sa'ad da yake sassaƙar jirgin ruwa"
A nan kalmar nan "rayuka" na nufin mutane. AT: "mutane takwas"
Bitrus ya ce baftisma ta yi daidai da hanyar da Allah ya ceci Nuhu da iyalinsa cikin jirgin daga ruwan tsufana.
Baftisma hanya ce da Allah ke ceton mutane. AT: "ta wurin baftismar da Allah ya cece ku yanzu"
Ma'anoni masu yiwuwa 1) "roƙon mutum ga Allah ya bashi lamiri mai kyau" ko 2) "alkawarin mutum ga Allah wadda aka yi da lamiri mai kyau, wato, da gaske."
"saboda tashin Yesu Almasihu daga mattattu." Wannan maganar ta kammala bayanin cewa "Wannan alama ce ta baftismar da ta cece ku yanzu."
Zama a "hanun daman Allah" alama ce da ke nufin cewa Allah ya ba wa Yesu babbar daraja da iko bisa kowa. AT: "Almasihu na gefen Allah cikin wurin ɗaukaka da iko"
"yi wa Yesu biyayya"
1Saboda haka, tunda yake Almasihu ya sha wuya a jiki, muma mu sha damara da wannan ra'ayi. Duk wanda ya sha wuya a jiki ya daina aikata zunubi. 2Wannan mutum kuma baya kara zaman biye wa muguwar sha'awar mutumtaka, amma sai dai nufin Allah dukkan sauran kwanakinsa a duniya.3Gama lokaci ya wuce da zamu yi abin da al'ummai suke son yi, wato fajirci, mugayen sha'awace-sha'awace, da buguwa da shashanci da shaye-shaye da bautar gumaku da abubuwan kyama. 4Suna tunanin bakon abu ku ke yi da ba kwa hada kai tare da su yanzu a yin wadannan abubuwa, sai suna zarginku. 5Za su bada lissafi ga wanda yake a shirye ya shari'anta masu rai da matattu. 6Shi yasa aka yi wa matattu wa'azin bishara, cewa ko da shike anyi masu shari'a cikin jikunan mutane, su rayu bisa ga Allah a ruhu.7Karshen dukkan abubuwa yana gabatowa. Saboda haka, ku zama natsatsu, ku natsu cikin tunaninku domin yin addu'oi. 8Gaba da kome, ku himmatu wajen kaunar juna, domin kauna bata neman tona zunuban wadansu. 9Ku yi wa juna bakunta da abubuwa nagari ba tare da gunaguni ba.10Yadda kowanne dayanku ya sami baiwa, kuyi amfani da su domin ku kyautata wa juna, kamar masu rikon amanar bayebaye na Allah, wanda ya ba mu hannu sake. 11Idan wani yana yin wa'azi, ya zamana fadar Allah ya ke fadi, idan wani yana hidima, ya yi da karfin da Allah ya ba shi, domin cikin dukkan abubuwa a daukaka Allah ta wurin Yesu Almasihu. Daukaka da iko nasa ne har abada abadin. Amin.12Ya kaunatattu, kada ku zaci cewa matsananciyar wahalar da ta zo ta gwada ku bakon abu ne, ko kuma wani bakon abu ne yake faruwa a gareku. 13Amma muddin kuna tarayya da Almasihu cikin wahalarsa, ku yi murna, domin kuyi farin ciki da murna sa'adda za a bayyana daukakarsa. 14Idan ana zargin ku sabili da sunan Almasihu, ku masu albarka ne, domin Ruhun daukaka da Ruhun Allah ya tabbata a kanku.15Amma kada kowannen ku ya sha wahala sabo da horon shi mai kisan kai ne, ko barawo, ko mamugunci, ko mai shisshigi. 16Amma in wani yana shan wahala sabili da shi na Almasihu ne, kada ya ji kunya, amma ya daukaka Allah a wannan sunan.17Domin lokaci ya yi da shari'a za ta fara daga gidan iyalin Allah. Idan kuwa za a fara da mu, menene karshen wadanda suka ki biyayya da bisharar Allah? 18Idan mutum, "mai adalci ya tsira da kyar, to, me zai faru da marar bin Allah da mai zunubi kuma?" 19Sabo da haka bari wadanda suke shan wuya bisa ga nufin Allah, su mika rayukansu ga amintaccen Mahalicci suna kuma yin ayyuka nagari.
Bitrus ya cigaba da koyar da masubi game da rayuwar masubi. Ya fara da bayar da karshen maganar sa game da wahalar Almasihu a suran da ke kafin wannan.
"cikin jikinsa"
Maganar nan "ku yi ɗamara" na sa masu karatu su yi tunanin soja wanda ke shirya makamansa don yaƙi. Ya kuma bada hoton "ra'ayi" kamar makamai ko kuma kamar wani makami. A nan wannan na nufin cewa masubi su ɗau kudurin shan wuya cikin zuciyar su kamar yadda Yesu ya yi. AT: "ku shirya kanku da irin tunani da Alamasihu ke da shi"
"ya bar yin zunubi kenan"
abubuwan da mutane masu zunubi ke sha'awan ta
Waɗannan kalmomin na nufin taruwan mutane don a sha barasa fiye da haka kuma sai su yi halin ban kyama.
Wannan misalin masu halin hauka da matuƙar zunubi ne; an yi maganar su sai kace wata ambaliyan ce da ke shafe mutane.
yi kowanne abu da za su iya yi don su biya bukatan sha'awace-sha'awacen jikunan su
Ma'anoni masu yiwuwa 1) "Allah, wanda ke shirye ya shar'anta" ko 2) "Almasihu, wanda ke shirye ya sharanta"
Wannan na nufin dukan mutane, ko suna raye har wa yau ko kuwa sun mutu. AT: "kowane mutum"
Ma'anoni masu yiwuwa 1) "har ma an yi wa mutanen da suka mutu wa'azin bishara" ko 2) "har ma an yi wa waɗanda a dă suna raye amma a yanzu mattattu ne"
Ma'anoni masu yiwuwa 1) Almasihu ya yi wa'azi. AT: "Almasihu ya yi wa'azin bisharar" ko 2) mutane sun yi wa'azi. AT: "mutane sun yi wa'azin bisharar"
Ma'anoni masu yiwuwa 1) Allah ya shar'anta su a wannan rayuwa ta duniya. AT: "Allah ya shar'anta su cikin jikunan su a matsayin 'yan adam" ko 2) mutane sun shar'anta su bisa ga ma'aunin 'yan adam. AT: "mutane sun shar'anta su cikin jikunan su a matsayin 'yan adam"
Wannan batun mutuwa ne a matsayin sifar shari'a na ƙarshe.
Ma'anoni masu yiwuwa 1) "rayuwar ruhaniya kamar yadda Allah ke rayuwa, domin Ruhu Mai Tsarki zai iza su su yi haka" ko 2) rayu bisa ga ma'aunin Allah ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki"
Wannan na nufin ƙarshen duniya loƙacin zuwan Almasihu ta biyu.
An yi magana game da ƙarshen da zai zo ba jimawa sai kace ya na zuwa kurkusa daga nesa. AT: "zai faru ba da jimawa ba"
Waɗannan maganganu biyun na nufin abu ɗaya ne. Bitrus ya yi amfani da su don ya nanata bukatar yin tunani game da rayuwa da shike ƙarsehn duniya ta kusa.
A nan kalman nan "natsu" na nufin ba shakka cikin hankali da kuma zaman shiri. Dubi yadda ku ka jiya wannan cikin [1 Bitrus 1:13]. AT: "ku sarrafa tunanin ku" ko " ku yi hankali da abin da kuke tunaninsu"
"Mafi muhimmanci duka"
Bitrus ya bayyana "ƙauna" sai ka ce wai mutum ne wanda ke sa murfi kan laifofin wasu. Ma'anoni masu yiwuwa 1) "gama mutumin da ke ƙauna kuwa ba zai taɓa yi ƙoƙarin neman sanin ko wani ya yi zunubi ba" ko 2) "gama mutumin da ke ƙauna zai yafe laifofin sauran mutane, ko su na da yawa"
Ku yi wa juna kirki ku kuma marabci baƙi da matafiye
Wannan na nufin iyawa ta ruhu na musamman wanda Allah ya ba wa masubi. AT: "Domin kowane ɗayanku ya karbi iyawa ta ruhu na musamman a matsayin kyauta daga wurin Allah"
AT: "don ta kowace hanya za ku daukaka Allah"
yabo, girmamawa
kamar yadda wuta ke fid da ainihin kyaun zinariya, hakanan gwaje gwage ke fid da ainihin kyaun bangaskiyar mutumin.
Wannan maganganun na nufin abu ɗaya ne kuma na nanata ƙarfin farin cikin. AT: "ku yi murna sosai" ko "ku yi farin ciki ainun"
"sa'ad da Allah ya bayyana daukakar Almasihu"
A nan kalman nan "suna" na nufin Almasihu kansa. AT: "in mutane sun zarge ku don kun gaskata da Almasihu"
Dukan waɗannan na nufin Ruhu Mai Tsarki. AT: "Ruhun ɗaukaka wanda shine Ruhun Allah" ko "Ruhun ɗaukaka na Allah"
na tare da ku
Wannan na nufin mutumin da ke sa kansa cikin ayyukan mutane wanda ba shi da izinin yin haka.
"saboda ya na ɗauke da sunan nan maibi" ko "saboda mutane sun gane cewa shi maibi ne." Kalmomin nan "wannan suna" na nufin kalman nan "maibi."
Wannan na nufin masubi wadda Bitrus ya yi magana game da su cewa su iyalin Allah ne.
Bitrus ya yi amfani da wannan tambaya don ya nanata cewa shari'a Allah zai fi tsanani ga mutane da suka ƙi bishara na masubi. AT: "Idan kuwa an fara da mu, lailai abin da zai zama ga waɗanda sun yi rashin biyayya ga bisharar Allah zai zama da muni."
"me zai faru da waɗanda"
"waɗanda ba su gaskata da bisharar Allah ba." A nan kalman nan "biyayya" na nufin gaskatawa.
Bitrus ya yi amfani da wannan tambaya don ya nanata cewa masu zunubi za su sha wahala fiye da masubi. AT: "mutum mai adalci ... abin da zai haifar wa mara bin Allah da masu zunubi zai fi muni."
me zai faru da marasa bin Allah da masu zunubi"
A nan kalman nan "tsira" na nufin ceto na ƙarshe a sa'ad da Alamasihu ya dawo. AT: "In har mutum mai adalci ya sha wuya kafin Allah ya cece shi"
Kalmomin nan "mara bin Allah" da "mai zunubi na nufin abu ɗaya, su na kuma nanata muguntar waɗannan mutanen. AT: marasa bin Allah, masu zunubi"
A nan kalman nan "rayuka" na nufin mutum gabadayansa. AT: "miƙa kansu" ko "miƙa ransu"
Ana iya juya "yin ayuka nagari" cikin fi'ilin magana. AT: "sa'and da suke nagargarun ayuka" ko "sa'and da suke rayuwa da ta cancanta"
1Ina yiwa dattawan da ke cikinku gargadi, ni da nike dan'uwanku dattijo, mashaidin shan wuyar Almasihu, ni kuma mai samun rabo ne daga cikin daukakar daza a bayyana. 2Saboda haka na gargade ku dattawa, kuyi kiwon garken Allah dake tare da ku. Ku kula da su, ba a kan dole ba, amma domin kuna son yin haka, bisa ga yin Allah. Ku kula da su, ba don cin ribar banza ba amma sabo da yardar rai. 3Kada ku zama kamar masu iko akan mutanen dake hannunku, amma ku zama abin koyi ga garken. 4Sa'adda za a bayyana Sarkin Makiyaya zaku karbi rawanin da darajarsa bata dushewa.5Hakannan, ku kuma samari kuyi biyayya ga dattawa. Dukanku kuyi damara da tawali'u, kuna bauta wa juna, domin Allah ya na tsayayya da mai girman kai, amma yana yiwa masu tawali'u alheri. 6Saboda haka ku kaskantar da kanku karkashin hannuwan Allah mai iko duka domin ya daukaka ku a madaidecin lokaci. 7Ku jibga masa duk taraddadin zuciyarku, domin yana kula da ku.8Ku natsu, ku zauna a fadake. Magabcinku, ibilis, kamar zaki mai ruri yana zazzagawa, yana neman wanda zai cinye. 9Ku yi tsayayyiyar gaba da shi. Ku yi karfi cikin bangaskiyarku. Ku sani fa abokan tarayyarku da suke cikin duniya suna jimrewa da shan wuyan nan irin taku.10Bayan shan wuyarku na dan lokaci kadan, Allah mai alheri mara iyaka, wanda ya kiraye ku zuwa ga madawwamiyar daukakarsa cikin Almasihu, zai kammalaku, ya kafa ku, ya kuma karfafa ku. 11Mulki ya tabbata a gare shi har abada abadin. Amin.12Na amince da Sila amintaccen dan'uwa ne, kuma na rubuto maku a takaice ta hannunsa. Ina yi maku gargadi ina kuma shaida maku cewa abin da na rubuto alherin Allah ne na hakika. Ku kafu a cikinsa. 13Ita matar da ta ke a Babila zababbiya tare da ku, ta na gaisheku, da Markus, dana, yana gaisheku. 14Ku gai da juna da sumbar kauna. Salama ta tabbata a gare ku dukanku da ke cikin Almasihu.
Bitrus ya yi magana game da mazajen da ke dattawa.
Wannan na nuna dawowar Almasihu ta. AT: "ɗaukakar Almasihu da Allah zai bayyana"
Bitrus ya yi magana game da masubi kamar garken tumaki da kuma dattawa kamar makiyaya da suke lura da su.
Ma'anoni masu yiwuwa 1) "mai kula da" wani ma'aikaci ne wadda ke kula da mutanen Allah, ko 2) marubucin na bayyana abin da makiyayi ke yi ("zama makiyayin tumakin Allah"), "kulawa da su."
Dattawa su yi shugabanci ta wurin zama abin koyi ga mutane kada kuma su zama kamar ubangida mara tausayi ga bayinsa.
Kuna iya juya wannan cikin fi'ilin magana. AT: "waɗanda Allah ya sa ƙarƙashin kulawar ku"
Bitrus ya yi magana game da Yesu sai ka ce shi makiyayi ne mai iko kan duk sauran makiyayan. AT: "sa'ad da Yesu, sarkin makiyayin ya bayyana" ko "sa'ad da Allah ya bayyana Yesu, Sarkin makiyayin"
A nan kalmar nan "rawani" na a madadin sakamako da wani ya karɓa a matsayin alamar nasara. Kalmomin nan "bata dusashewa" na nufin cewa madawwamiya ce. AT: "kyauta mai daraja wadda zai dawama"
daraja
Wannan na kai mu baya ga yadda dattawan sun mika kan su ga Shugaban Makiyaya cikin 1 Bitrus 5: 1-4.
Wannan na nufin dukan masubi, ba masu ƙuruciya kawai ba.
Bitrus ya yi maganar samun ingantacciyar halin tawali'u a matsayin sa tufa. AT: "zaman tawali'u ga juna" ko "zama da tawali'u"
A nan kalmar nan "hannu" na nufin ikon Allah don ceton masu tawali'u da kuma hukunta masu girman kai. AT: "ƙarƙashin girman ikon Allah" ko "gaban Allah tare da sanin cewa yana da iko mai girma"
Bitrus ya yi magana game da taraddadi sai ka ce wata kaya mai nauyi ce da mutum ya sa kan Allah a maimakon ɗauka da kansa. AT: "Dogara a gare shi da dukan abubuwan da ke damun ku" ko "ku bar shi ya kula da dukan abubuwan da suke damun ku"
A nan kalmar nan "natsu" na nufin hankali mai tsabta da kuma shiri. AT: "Kula da tunaninku" ko "yi kula da abinda ku ke tunani"
Bitrus ya kamanta ibili da zaki mai ruri. Daidai kamar yadda zaki mai jin yunwa ke cinye abin da ya yi farautar sa, hakanan ibili na neman ya rushe bangaskiyar masubi.
"yawo" ko "yawo na kuma farauta"
tsayayya na nufin yaƙi. AT: "yaƙi da shi"
Bitrus ya yi magana game da 'yan'uwa masubi a matsayin 'yan'uwa ɗaya. AT: "'yan'uwan ku masubi"
"cikin wurare dabam-daban a ko'ina a duniya"
"na guntun lokaci"
a nan kalmar nan "alheri" mai yiwuwa na nufin abubuwan da Allah ya bayar ko kuwa halin Allah. Ma'anoni masu yiwuwa 1) "Allahn da a kulliyomi yana ba mu abin da muke bukata" ko 2) "Allah mai alheri a koyaushe."
"wanda ya zaɓe ku ku sami rabo zuwa ga madawamiyar ɗaukakarsa cikin sama saboda an haɗa ku da Almasihu"
"sa ku zama kammalallu" ko "mayar da ku" ko "sa ku ku zama lafiyayyu"
Waɗannan maganganu biyu suna da ma'an kusan iri ɗaya, wato, Allah zai sa masubi su dogara a gare shi su kuma yi masa biyayya komin wahalar da suke sha.
Sila ne ya rubuto abin da Bitrus ya faɗa masa ya rubuta cikin wasiƙar.
"Na rubuta game da gaskiyar alherin Allah." A nan kalmar nan "alheri" na nufin saƙon bishara wadda ta faɗi irin abubuwan da Allah ya yi wa masubi.
Kalmar nan "ta" na nufin "gaskiyar alherin Allah." An yi maganar miƙa kai ga wannan alherin kamar tsayawa a wuri ɗaya ba matsawa. AT: "Tsaya da ƙarfi da kuma mika kai cikin ta"
A nan "ita matar" mai yiwuwa na nufin kungiyar masubi da ke zama a "Babila." Ma'anoni masu yiwuwa na "Babila" 1) sananniyar alama ce ta birnin Roma, 2) sananniyar alama ce ta duk inda masubi ke shan wahala, ko 3) na nufin birnin Babila. mai yiwuwa ta na nufin birnin Roma.
AT: "wanda Allah ya zaɓa kamar yadda ya zaɓe ku"
Bitrus ya yi magana game da Markus sai ka ce ɗansa ne a ruhaniya. AT: "ɗana cikin ruhaniya" ko "wadda ke kamar ɗa a gare ni"
"sumbar ƙauna" ko "sumbar nuna ƙauna ga juna"
1Siman Bitrus, bawa da manzon Almasihu Yesu, zuwa ga wadanda suka karbi bangaskiya mai daraja kamar yadda muka karba, bangaskiya cikin adalcin Allahnmu da Yesu Almasihu. 2Bari alheri ya kasance tare da ku; bari salama ta karu ta wurin sanin Allah da na Yesu Ubangijinmu.3Dukkan abubuwan ikon Allah na rayuwa da Allahntaka an bamu su ta wurin sanin Allah, wanda ya kira mu ta wurin daukakarsa da nagarta. 4Ta wurin wanan, ya bamu babban alkawari mai daraja. Yayi wanan ne saboda ku zama masu rabo cikin Allahntaka, yayin da ku ka kubuta daga lalacewa da ke cikin duniya saboda mugayen sha'awace sha, awace.5Saboda wanan dalilin kuyi iyakacin kokarinku ku kara nagarta ta wurin bangaskiyarku, kuma ta wurin adalci, sani. 6Ta wurin sani ku kara da kamun kai, kuma ta wurin kamun kanku, ku kara da jimrewa, ta wurin jimrewarku, ku kara da bin Allah. 7Ta wurin bin Allah, ku kara da kauna irin ta 'yan'uwa, ta wurin kauna irin ta 'yan'uwa, ku kara kauna.8Idan wadannan abubuwan suna cikinku, kuma suka yi girma a cikinku, baza a sami bakarare ko rashin 'ya'ya cikin sanin Ubangijinmu Yesu Almasihu ba. 9Amma duk wanda ya rasa wadannan abubuwan yana kallon abin da ke kusa ne kawai; ya makance. Ya manta da cewa an wake shi daga tsofaffin zunubansa.10Saboda haka, 'yan'uwa, kuyi iyakacin kokari ku tabbatar da kiranku da zabenku. Idan kun yi wadannan abubuwan, baza ku yi tuntube ba. 11Ta haka zaku sami shiga cikin mulki na har'abada na Ubangijinmu da Maicetonmu Yesu Almasihu.12Saboda haka a shirye nake kulayomi in tunashe ku game da wadannan abubuwan, ko da yake kun san su, kuma kun yi karfi cikin gaskiya yanzu. 13Ina tunani daidai ne in zuga ku da tuni game da wadannan abubuwan, tun ina cikin wannan jiki. 14Domin na sani jim kadan zan bar wannan jiki, kamar yadda Yesu Almasihu ya nuna mani. 15Zan yi iyakancin kokarina kulayomi domin ku rika tunawa da abubuwan, bayan kaurata.16Domin bamu bi labaru da aka kago na nuna wayo cikinsu ba, da muka fada maku game da iko da bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Almasihu, amma mu shaidu ne na ikonsa. 17Gama ya karbi daukaka da daraja daga wurin Allah Uba lokacin da murya ta zo daga ikon mai daukaka cewa, "Wannan shine dana, kaunataccena, wanda nake jin dadinsa kwarai." 18Mun ji muryar nan da ta zo daga sama, lokacin da mu ke tare da shi a dutse mai tsarki.19Muna da wannan kalmar annabci wanda akwai tabbaci sosai, kun yi daidai idan kun mayar da hankali a kansu. Yana nan kamar fitillar da take walkiya a wuri mai duhu kafin asubahi ya zo, kuma tauraron asubahi ya tashi cikin zukatanku. 20Ku san da wannan tun da farko, cewa babu annabci da ke bisa ga fasarar mutum. 21Domin babu annabcin da ya taba zuwa ta wurin nufin mutum. Maimakon haka, Ruhu Mai Tsarki ne ke iza su, su fadi maganar Allah.
Bitrus ya bayyana kansa a matsayin marubucin, sa'an nan ya gaishe da masubi da ya ke rubuta masu.
Bitrus yana maganan zama bawan Yesu Almasihu. An kuma ba shi matsayi da ikon zama manzon Almasihu.
Cewar mutanen nan sun karɓi bangaskiya na nufin Allah ya ba su irin bangaskiyarmu. AT: "ga waɗanda Allah ya ba su bangaskiya iri ɗaya da tamu mai daraja"
"zuwa ga ku da ku ka karɓi." Bitrus ya na magana da dukkan masubi waɗanda mai yiwuwa za su karanta wannnan wasiƙar.
A nan kalman nan "mu" na nufin Bitrus ne da sauran manzanni, amma banda waɗanda ya ke rubuta masu wasiƙar. AT: "mu manzanni mun karɓa"
Allah ne wanda zai ba wa masubi alheri da salama. AT: "Bari Allah ya ƙara alheri da salamar ku"
Bitrus ya yi maganar salama kamar wani abu ne da zai iya karuwa a girma ko kuwa ƙirge.
Kuna iya juya "sani" ta wurin yin amfani da jumla ta aikatau. AT: "Ta wurin sanin Allah da kuke da shi da kuma Yesu Ubangijinmu"
A nan "bin Allah" na bayanin kalmar nan "rayuwa". AT: "don rayuwar bin Allah"
A nan kalmar nan "mu" na nufin Bitrus da masu sauraron sa.
A nan "waɗannan" na nufin "ɗaukakarsa da kuma kirkin sa."
"ku sami rabo"
yadda Allah yake
Bitrus ya yi magana game da rashin shan wahalar mutane saboda lalacewar da ake samu ta wurin mugayen sha'awace-sha'awacen sai ka ce sun tsere ne daga lalacewa. Kalman nan "lalacewa" ana iya juya ta cikin kalmar aikatau. AT: "kuma don mugayen sha'awace-sha'awace da ke cikin wannan duniya ba zata ƙara lalata ku kuma ba"
Wannan na nufin abinda Bitrus ya faɗa a ayoyin da ke baya. AT: "saboda abin da Allah ya yi"
Wannan na nufin ƙaunar abokai ko kuwa ƙauna tsakanin 'yan iyali, yana kuma iya nufin ƙaunar cikin iyalin ruhu.
Wannan na nufin bangaskiya, kirki, sanin ya kamata, kamunkai, jimiri, bin Allah, son 'yan'uwa, da ƙauna, da Bitrus ya ambato cikin ayoyin da ke a baya.
Bitrus ya yi magana game da mutumin da ba shi da waɗannan ingancin sai ka ce wata gonar da ba ta bada amfani. Ana iya bayanin wannan a cikin kalmomi masu nuna iganci. AT: "za ku bada 'ya'ya" ko "za ku zama da amfani"
Waɗannan kalmomin na nufin abu ɗaya, kuma na nanata cewa wannan mutum ba zai yi amfani ba ko kuwa ya sami wata amfani daga sanin Almasihu. AT: "rashin bada 'ya'ya"
Ana iya juya "sani" ta wurin yin amfani da jumla aikatau. AT: "Ta wurin sanin Allah da kuke da shi da kuma Yesu Ubangijinmu"
duk mutumin da ya rasa waɗannan abubuwa
Bitrus ya yi magana game da mutumin da ba shi da waɗannan ingacin sai ka ce mutum ne da ke ganin abubuwan da ke kusa ne kaɗai ko kuwa mutumin ne da ya makance domin bai fahimci darajar su ba. AT: "shi kamar mutum ne da ba ya iya hangen nesa, wanda ba ya iya ganin muhimmancin su."
Ku na iya amfani da aikatau don juya wannan. AT: "cewa Allah ya tsarkake shi daga zunubansa na dã"
Kalmomin nan "ƙira" da "zaɓe" su na da ma'ana kusan iri ɗaya kuma su na nufin cewa Allah ya zaɓe su don su zama nasa. AT: "ku tabbatar cewa lallai Allahne ya zaɓe ku don ku zama nasa"
A nan kalman nan "tuntuɓe" na nufin 1) aikata zunubi. AT: " ba za ku aikata halin zunubi ba" ko kuwa 2) zama da rashin amininci ga Almasihu ba. AT: "ba za ku zama da rashin aminci ga Almasihu ba"
AT: "Allah zai yi muku cikakkiyar tanadi a mashigar madawwamin mulkinsa"
damar shiga
Bitrus ya yi wa masubi magana game da hakkinsa ta cigaba da tunasashe su da kuma koyas da su.
A nan kalmomin nan "waɗannan abubuwa" na nufin dukkan abubuwan da Bitrus ya faɗa a ayoyin da ke a baya.
"da gaske ku ka gaskata gaskiyar waɗannan abubuwa"
A nan kalmar nan "zuga" na nufin a tashi wani daga barci. Bitrus yana magana game da sa masu karatun sa da su yi tunani game da waɗannan abubuwa sai ka ce ya na tashin su ne daga barci. AT: "a tunashe ku game da waɗannan abubuwa don ku yi tunani game da su"
Bitrus yana magana game da jikinsa sai ka ce wata tanti da yana sa wa kuma zai cire ta. Zama cikin jikinsa na nufin zaman da rai, cire ta kuma na nufin mutuwa.
Bitrus yana magana game da mutuwarsa sai ka ce zai bar wani wuri zuwa wani wuri. AT: "bayan mutuwa ta" ko "bayan na mutu"
A nan kalmar nan "mu" na nufin Bitrus da sauran manzannin, amma banda masu karantun. AT: "don mu manzannin ba mu bi labarin da aka ƙirƙiro ba"
Waɗannan maganganu biyun mai yiwuwa na nufin abu ɗaya ne kuma ana iya juya su kamar magana guda. AT: "ikon zuwan"
Wannan na iya nufin 1) zuwan Ubangijin Yesu na biyu nan gaba ko kuwa 2) farkon zuwan Ubangiji Yesu.
A nan kalman nan "mu" na nufin dukkan masubi.
AT: "sa'ad da ya ji murya na zuwa daga Mabuwãyin Ɗaukaka" ko kuwa "sa'ad da ya ji muryar Mabuwãyin Ɗaukaka ta yi magana da shi" ko kuwa "sa'adda Mabuwãyin Ɗaukaka ya yi magana da shi"
Bitrus yana nufin Allah a cikin ɗaukakarsa. Wannan wata yanayin magana ce da ke ƙoƙarin gujewa amfani da sunan Allah, don girmansa. AT: "Allah, mai madaukakin ɗaukaka, cewa"
Da kalmar nan "Mu," Bitrus yana nufin kansa ne da kuma almajire, wato Yakubu da kuma Yahaya, wanda suka ji muryar Allah. AT: "Mu kanmu mun ji wannan muryar da ta zo daga sama"
"ji muryar shi wanda ya yi magana daga sama"
"mu na tare da Yesu"
Abubuwan da Bitrus da sauran manzannin suka gani, wanda ya bayyana a ayoyin da ke a baya, sun tabbatar da abin da annabawan sun faɗa. AT: "Gama abubuwan da muka gani sun tabbatar da wannan saƙon annabcin"
A nan kalmar nan "mu" na nufin dukkan masubi, duk da Bitrus da masu karatunsa.
Wannan na nufin Tsohon Alkawari. AT: "nassosin da annabawa suka yi magana, ta sa"
Bitrus ya umurci masubi cewa su kasa kunne ga saƙon annabci.
Bitrus yana kwatanta kalmar annabci da fitila da ke bada haske cikin duhu har lokacin da haske za ta zo da safiya. Zuwan safiya na nufin zuwan Almasihu.
Bitrus ya yi magana game Almasihu a matsayin "tauraruwar safiya" wanda ke nuna cewa safiya ta yi kuma ƙarshen duhu ta kusa. Almasihu zai kawo haske ga zukantan masubi, zai kawo ƙarshen shakka da kuma cikakken fahimta game da ko wanene shi. A nan "zukatan" na nufin hankalin mutane. AT: " Almasihu na haskaka hasken sa cikin zukatanku kamar yadda tauraruwar safiya na haskaka duniya"
"Tauraruwar safiya" na nufin tauraro mai kewaye rana, wanda ke fitowa wani lokaci daidai kafin rana na kuma nuna cewa safiya ta kusa.
"Mafi Muhimanci, lallai ne ku fahimci"
Wannan na iya nufin 1) annabawan ba su yi annabcinsu da kansu ba ko kuwa 2) dole mutane su dõgara ga Ruhu Mai Tsarki don su fahimci annabce-annabcen ko kuwa 3) dole mutane su fasara annabce-annabace tare da taimakon jama'a masubi ga baki ɗaya.
Bitrus yana magana game da Ruhu Mai Tsarki na taimakon annabawan da su rubuta abin da Allah ke so su rubuta sai ka ce Ruhu Mai Tsarki yana ɗaukan su daga wani wuri zuwa wani wuri. AT: "mutane sun yi magana daga Allah kamar yadda Ruhu Mai Tsarkin ya shugabace su"
1Annabawan karya sun zo ga mutane, hakannan kuma malaman karya suma sun zo. A asirce za su zo maku da karkatacciyar koyarwa mai hallakarwa, su kuma yi musun sanin Ubangiji da ya fanshe su. Su na jawowa kansu hallaka da sauri. 2Da yawa za su bi gurbinsu, kuma ta wurinsu za a sabawa sahihiyar gaskiya. 3Ta wurin hadama za su ribace ku ta wurin maganganunsu na yaudara. Hallakarsu ba za ta yi jinkiri ba; hukuncinsu na nan tafe.4Allah bai kebe mala'ikkun da suka yi zunubi ba. Maimakon haka ya tura su a cikin bakin duhun jahannama daure da sarkoki, har ya zuwa ranar shari'a. 5Hakan nan kuma bai kebe duniya ta zamanin da ba. Maimakon haka, ya kebe Nuhu, wanda yake wa'azin adalci, tare da mutane bakwai, lokacin da ya kawo ambaliyar ruwan Tsufana a fuskar duniyar marasa bin Allah. 6Sa'annan Allah ya kone biranen Sadoma da Gomrata da wuta ya maishe su toka, wannan ya zama misalin abin da zai faru da marasa ibada.7Amma ga adalinnan Lutu, wanda ya zaku a ransa ta wurin miyagun halayen mutanen, Ubangiji kuwa ya cece shi. 8Ga wannan mutum mai adalci, wanda yayi zama a cikinsu kowace rana ransa na baci, domin abin da yake gani yake kuma ji. 9Saboda haka Allah ya san yadda zai ceci masu adalci daga gwaji, da yadda kuma zai kama masu rashin adalci da hukunci a ranar shari'a.10Wannan kuwa musamman gaskiya ce ga wadanda suka ci gaba da ayyuka na jiki suka kuma raina masu mulki. Suna da taurin kai da kuma yin ganin dama. Ba sa tsoron sabo ga wadanda aka daukaka. 11Ko da shike mala'iku suna da karfi da iko fiye da su, amma basu kawo karar batanci a kansu a gaban Ubangiji ba.12Amma wadannan dabbobi marassa tunani an yi su ne musamman domin a kama a yanka. Suna sabawa abin da ba su sani ba. Zasu halaka. 13Za su sami sakamakon mugun aikinsu. Suna tunanin yin nishadi da rana abin annashuwa ne. Su kan su tababbu ne. Suna jin dadin ayyukansu na yaudara yayin da suke liyafa tare da ku. 14Suna da idanun sha'awace sha'awacen mata mazinata; ba sa koshi da aikata zunubi. Suna rinjayar wandanda ba su da tsayayyan hankali zuwa ga munanan ayyuka, kuma sun kafa zukatansu ga hadama, su 'ya'yan la'ana ne!15Sun bar bin hanyar gaskiya. Sun bijire kuma sun bi hanyar Bal'amu dan Be'or wanda yake kaunar ribar rashin adalci. 16Amma ya karbi tsautawa domin zunubinsa. Jaki ma da baya magana ya tsauta wa haukan annabin da muryar dan adam.17Wadannan mutane suna kamar mabulbullai da babu ruwa. suna nan kamar gizagizai da iska ke korawa. Duhu mai tsanani yana jiransu. 18Su masu babatu ne da girman kai. suna yadaurar mutane ta wurin sha'awowin jiki. Suna yaudarar mutane da suke kokarin su tsere daga wadanda suke rayuwa cikin kuskure. 19Suna masu alkawarin yanci, amma su da kan su bayi ne ga zunubi. Domin mutum bawa ne ga duk abinda ya rinjaye shi.20Duk wanda ya kubuta daga shashanci na duniya ta wurin sanin Ubangiji da mai Ceto Yesu Almasihu, sa'annan ya koma cikin shashaci, yanayinsu na karshe ya zama da muni fiye da na farkon. 21Da ma zai fi masu kada su san hanyar adalci da su san ta amma sa'annan su juya daga ka'ida mai tsarki wanda aka damka masu. 22Wannan karin magana ya zama gaskiya a kan su: "Kare ya dawo yana lashe amansa. Aladen da akayi masa wanka ya koma cikin tabo."
Bitrus ya fara yi wa masubi kashedi game da masu koyarwar ƙarya.
Kamar yadda masu koyarwar ƙarya sun zo suna yauɗaran Isra'ila da kalmomin su, haka kuma masu koyarwar ƙarya za su zo suna koyarwar da karya game da Almasihu.
kalmomin nan "karkatacciyar koyarwa" na nufi ra'ayoyin da ke dabam da koyarwar Almasihu da kuma manzannni. Wannan karkatacciyar koyarwar na rushe bangaskiyar wanɗanda suka gaskanta da ita.
Kalman "ubangidan" a nan na nufin mutumin da ke da bayi. Bitrus yana magana game da Yesu a matsayin mamallakin mutane da ya saya, mutuwarsa ita ce farashin.
haramtaccen hali ta jima'i
Maganan nan "hanyar gaskiya" na nufin bangaskiyar masubi a matsayin hanya ta gaskiya zuwa ga Allah. AT: "marasa bi za su yi saɓo ga hanyar gaskiya"
"shawo kan ku ga bada kuɗi ta wurin yi muku karya"
Bitrus yana magana game da "hallaka" da "hukunci" sai ka ce su mutane ne da za su iya yin abu. Maganganun nan biyu a takaice abu ɗaya ne su na nanata yadda masu koyarwar karya za su hallaka jim kaɗan.
Bitrus yana bada misalan mutanen da ke gãbã da Allah da kuma wanda Allah ya hukunta saboda abinda suka yi.
"bai dena hukunci" ko "ya hukunta"
Kalmomin nan "bakin duhu ta jahannama" kalmomi ne a addinin Helenawa dake nufin wurin da aka hukunta mugayen ruhohi da kuma mugayen mutanen da suka mutu. AT: "ya jefa su cikin jahannama"
AT: "inda zai sa su cikin sarƙar baƙin duhu"
Wannan na iya nufin 1) "a sarƙa cikin wurin da ke da matuƙar duhu" ko kuwa 2) "cikin matuƙar duhun da ta sa su cikin kurkuku kamar sarƙoƙi."
Wannan na nufin ranar shari'a a sa'ad da Allah zai shar'anta kowane mutum.
A nan kalman nan "duniya" na nufin mutanen da ke cikin ta. AT: "bai rangwata wa mutane da sun yi rayuwa cikin duniya ta dã ba"
Allah bai halaka Nuhu da mutane bakwai ba a sa'ad da ya halaka sauran mutane wanda sun yi rayuwa a duniya ta dã.
"kona biranen Saduma da Gwamrata da wuta har suka zama toka"
A nan kalman "su" na nufin Saduma da Gwamrata da kuma mutanen da sun yi rayuwa cikin su.
Saduma da Gwamrata sun zama misalai ne da kuma kashedi na abin da zai faru da waɗanda sun yi wa Allah rashin biyayya.
"haramtacciyar halayen mutanen da ke karya shari'ar Allah"
Wannan na nufi Lutu.
A nan "rai" na nufin tunani da kuma shauƙin Lutu. Haramtacciyar halayen 'yan Saduma da Gwamrata ta dame shi kwarai. AT: "ya damu kwarai da gaske"
Kalmar nan "wannan" na nufin cewa Allah ya sa mutane marasa Adalci cikin kurkuku har ya zuwa ranar shari'a bisa ga 2 Peter 2:9.
A nan "sha'awace sha'awace na jiki" na nufin sha'awace-sha'awace ta halin zunubi na mutuntaka. AT: "waɗanda sun cigaba da dulmuya cikin sha'awace-sha'awace ta zunubi"
"sun ƙi biyayya da mulkin Allah." Anan kalmar nan "mulki" mai yiwuwa na nufin ikon Allah.
A nan "mulki" na a madaddin Allah wanda ke da ikon bada umurni da kuma hukunta rashin biyayya.
"aikata kowane abinda suke so su yi"
Wannan na nufin halitattun ruhohi kamar mala'iku ko kuwa aljannu.
"ƙarfi da iko fiye da masu koyarwar ƙarya"
Kalman nan "su" na nufin mala'iku. Ma'anoni masu yiwuwa na kalmar nan "su" na kamar haka 1) masu ɗaukaka ko kuwa 2) masu koyarwar ƙarya.
Ra'ayin cewa mala'iku na iya zargin waɗannan mugayen mutane na kamar za su iya kai masu hari ta wurin amfani da zargi a matsayin makamai.
Daidai kamar yadda dabbobi ba su da tunani, waɗannan mutane ba za a iya muhawara da su ba. AT: "waɗannan masu koyaswar karya suna kamar dabbobin da ba sa tunani wanda aka kama su domin hallaka"
Suna miyagun maganganu game da abin da ba su sani ko fahimta ba.
AT: "Allah zai halaka su"
Bitrus yana magana game da hukuncin da masu koyaswar ƙarya za su samu kamar wata sakamako ne. AT: "Za su karɓi abinda ya cancance su saboda miyagun ayyukansu"
A nan kalmar nan "nishaɗi" na nufin ɗabi'u marasa kyau duk da handama, shaye- shaye da kuma haramtattun ayyuka. Yin waɗannan abubuwan da rana na nuna cewa waɗannan mutane ba sa kunyan wannan hali.
Kalmomin nan "datti" da "lahani" suna da ma'ana kusan iri ɗaya. Bitrus ya yi magana game da malaman karya sai ka ce su datti ne a tufa, wadda ke sa kunya ga waɗanda suka sa ta. AT: "Su kamar datti ne da kuma lahani a kan tufafi, wadda ke sa kunya"
A nan "idanu" na nufin sha'awace-sha'awace kuma "idanu cike" na nufin cewa sun cika son abu. AT: "Koda yaushe su na son aikata zina"
Kodashike sun yi zunubi don su samu gamsuwa cikin sha'awar su, zunubin da suka yi bai taɓa gamshe su ba.
A nan kalman nan "ran" na nufin mutanen. AT: "Sun rinjayi mutanen da ba sa tsayawa a guri ɗaya"
A nan kalmar nan "zukata" na nufin tunani da shauƙin mutumin. Saboda halayen da suka saba yi, sun hori kansu ga yin tunani da kuma yin ayyuka bisa ga haɗama.
"Waɗannan malaman ƙaryan sun bar bin hanyar gaskiya sun kuma bijire ga bin." Malaman karyan sun ki yin biyayya ga Allah domin su guje wa abin da ke daidai.
An yi magana game da halayen da ke girmama Allah sai ka ce wata hanya ce da za a bi.
Za ku iya yin cikakken bayani cewa Allah ne ya tsauta wa Bala'am. AT: "Allah ya tsauta masa"
Jaki, bisa ga halittar sa ba ya magana, ya yi magana da murya kamar ta ɗan adam.
Allah ya yi amfani da jaki don ya hana munanan ayyukan annabi.
Maɓulɓullai da ke da ruwan sha ga mutane masu jin ƙishi, amma "maɓulɓullai da ba su da ruwa" za su sa masu jin ƙishi cikin kunya. Haka nan kuma, malaman ƙarya, kodashike sun yi alkawaran abubuwa dayawa, ba su iya cika abin da su ka alkawarta ba.
Sa'ad da mutane sun ga hadari, suna stammanin cewa ruwa zai sauko. Sa'ad da guguwa mai karfi ta fura hadarin kamin ruwa ta faɗi mutane za su ji ba daɗi a ran su. Haka nan kuwa malaman ƙarya, kodashike sun yi alkawarin abubuwa da yawa, basu iya cika wa ba.
Kalmar nan "su" na nufin malaman ƙarya. AT: "Allah ya shirya masu duhu mai tsanani"
Suna amfani da kalmomi masu burgewa amma marasa ma'ana.
Tawurin halin zunubi su kan sa mutane su yi haramtaccen ayyuka da kuma ayyuka na zunubi.
Bitrus yana magana game da mutane da ke rayuwa ta zunubi sai ka ce su bayin zunubi ne da ke bukatan 'yanci daga zaman talala.
Wannan magana na nufin mutanen da suka zama sabobbin tuba. Jumlar nan "waɗanda ke rayuwa cikin kuskure" na nufin marasabi wanɗanda ke rayuwa cikin zunubi. AT: "mutanen da ke son su yi rayuwar da ke daidai, maimakon yin rayuwa ta zunubi kamar yadda suka saɓa kuma kamar yadda sauran mutane suke yi"
" 'Yanci" a nan na nufin rayuwa daidai yadda mutum ke so. AT: "Sun yi masu alkawarin cewa za su ba su irin rayuwar da suke so, amma su da kansu bayin zunubi ne"
Bitrus yana magana game da mutum a matsayin bawa ne a sa'ad da wani abu ya mulke shi da kuma wannan abin da ke mulki a matsayin ubangijin mutumin. AT: "Gama in wani abu na mulki a bisa mutum, wannan mutum ya zama kamar bawa ne ga wancan abin"
Kalmar nan "lalacewa" na nufin halin zunubi da ke sa wani ya zama mara tsabta. "Duniya" na nufin al'umma. AT: "Ayyukan da ke kazantar da al'umma"
Ku na iya juya "sani" ta wurin yin amfani da fi'ilin magana. Dubi yadda ku ka juya magana makamancin haka cikin [2 Bitrus 1:2] AT: "ta wurin sanin Ubangiji da Almasihu Yesu Mai ceto"
"yanayinsu ya yi muni fiye da na dã"
Bitrus yana magana game da rayuwa kamar "hanya" ko tafarki. Wannan magana na nufin yin rayuwar da ke daidai bisa ga nufin Allah.
A nan "juyawa daga" na nufin mutum ya bar yin wani abun. AT: "bar yin biyayya ga ka'ida mai tsarki"
AT: "Ka'ida mai tsarki da Allah ya danƙa masu" ko kuwa "ka'idan nan mai tsarki da Allah ya tabbata cewa sun karɓa"
"Wannan karin magana ya shafe su" ko kuwa "Wannan karin magana ta bayyana su"
Bitrus ya yi amfani da karin magana biyu don ya yi misalin yadda malaman ƙarya waɗanda, kodashike sun san "hanyar adalci", suka juya baya zuwa ga abubuwan da ke kazantar da su cikin ruhaniya da kuma ɗabi'u marasa kyau.
1Yanzu, ina rubata maku, kaunatattu, wannan wasika ta biyu domin in tunashe ku, in kuma zuga tunaninku na gaskiya, 2don ku tuna da kalmomin da annabawa tsarkaka suka fada a da, kuma da umurnin Ubangijinmu da mai ceto da aka bayar ta wurin manzaninku.3Ku san wannan da farko, cewa masu ba'a za su zo a kwanakin karshe. Za su yi ba'a kuma su ci gaba bisa ga sha'awowinsu. 4Za su ce, "Ina alkawarin dawowarsa? Tun lokacin da kakaninmu suka mutu, dukkan abubuwa sun kasance yadda suke, tun farkon halitta."5Da gangan suka manta cewa sama da kasa sun kasance daga ruwa, kuma ta wurin ruwa, da dadewa ta wurin umarnin Allah, 6kuma cewa ta wurin wadannan abubuwa duniyar wancan zamani ta halaka, da ambaliyar ruwan tsufana. 7Amma sama da kasa na yanzu, an tanada su domin wuta ta wurin wannan umarnin. An tanada su domin ranar shari'a da halakar marassa ibada.8Kada ku manta da wanan, kaunatattu, cewa rana daya a gun Allah kamar shekaru dubu ne, kuma shekaru dubu kamar rana daya suke. 9Ubangiji baya jinkiri game da alkawaransa kamar yadda wadansu ke ganin jinkiri. Maimakon haka, yana hakuri da ku. Ba ya so ko dayanku ya hallaka, amma kowanenku ya kai ga tuba.10Duk da haka, ranar Ubangiji za ta zo kamar barawo. Sammai za su shude da kara mai karfi. Wuta zata kone komai da komai, kuma duniya da dukkan ayyukan da ke cikinta zasu bayyanu.11Da shike dukkan wadanan abubuwa za a hallaka su haka, wadanne irin mutane yakamata ku zama? Ya kamata kuyi rayuwar tsarki da ta ibada. 12Ku zauna cikin bege da kuma hanzarta zuwan ranar Allah. A ranan nan, za a hallaka sammai da wuta, kuma dukkan komai da komai zai narke cikin zafi mai tsanani. 13Amma bisa ga alkawarinsa, muna jiran sabuwar sama da sabuwar duniya, inda adalci zai kasance.14Saboda haka, kaunatattu, tun da kuna da begen wadannan abubuwa, ku yi iyakacin kokarinku a same ku marassa tabo da marasa aibu a gabansa, cikin salama. 15Kuma, ku dauki hakurin Ubangiji domin ceto ne, kamar yadda kaunataccen danuwanmu Bulus ya rubuta maku bisa ga hikima da aka ba shi. 16Bulus yayi magana akan wadanan abubuwa cikin dukkan wasikunsa, a ciki akwai abubuwa da suke da wuyar ganewa. Jahilai da mutane marassa natsuwa sukan juya ma'anarsu, kamar yadda suke yi wa sauran nassoshi, don hallakar kansu.17Saboda haka, kaunatattu, tun da kun san wadannan abubuwa, ku kula da kanku kada a badda ku ta wurin rudun mutanen da ba su bin doka, har ku rasa amincinku. 18Amma ku yi girma a cikin alheri da sanin Ubangijinmu da mai ceto Yesu Almasihu. Bari daukaka ta tabbata a gare shi yanzu da har abada. Amin.
Bitrus ya fara magana game da ƙarshen zamani.
Bitrus yana magana game da sa masu karantun sa su yi tunani game da waɗannan abubuwa sai ka ce ya tashe su ne daga barci. AT: "in sa ku ku yi tunani masu tsabta"
AT: "Kalmomin da annabawa masu tsarki suka faɗa a dã"
AT: "umurnin Ubangijinmu da Mai Cetonmu, wanda manzannin ku suka ba ku"
"Ku san wannan a matsayin abu mafi muhimmanci." Dubi yadda ku ka juya wannan cikin [2 Bitrus 1:20]
A nan kalman nan "sha'awowi" na nufin sha'awace-sha'awacen zunubi da ke gãbã da nufin Allah. AT: "rayuwa bisa ga sha'awowinsu ta zunubi"
yi, nuna hali
Masu ba'an sun yi wannan tambaya don su nanata cewa su ba su gaskata Yesu zai dawo ba. Kalmar nan "alkawari" na nufin cikan alkawarin cewa Yesu zai dawo. AT: "Alkawarin cewa Yesu zai dawo ba gaskiya ba ne! Ba Zai dawo ba!"
A nan "ubanni" na nufin kakani waɗanda sun yi rayuwa tun da jimawa. Yin barci na nufin mutuwa. AT: "kakaninmu sun mutu"
Masu ba'a sun yi amfani da kalmar nan "dukan" sosai, kuma suna cewa dashike babu wani abu da ya canza a duniya, lallai ba zai zama gaskiya ba ce Yesu zai dawo.
AT: "tun lokacin da Allah ya halici duniya"
AT: "Allah ya kafa sammai da duniya ... tun dã ta wurin kalmarsa"
Wannan na nufin cewa Allah ya sa ƙasa ta kasance daga ruwa, ya tattara ruwa a wuri ɗaya don ƙasa ta kassance.
A nan "waɗannan abubuwa" na nufin kalmar Allah da kuma ruwa.
AT: "Da ambaliyan ruwa, Allah ya hallaka duniya a zamanin dã "
AT: Ta wurin wannan kalma ɗayan, Allah ya keɓe sammai da duniya don wuta"
A nan "umurni" na a madaddin Allah wanda zai bada umurnin: AT "Allah, wanda zai ba da umurni iri ɗaya"
za a iya fara wannan da wata sabuwar jumla. AT: "Yana keɓe su don ranar shari'a"
AT: "domin ranar da zai hukunta da kuma hallakar da mutane marasa bin Allah"
"kada ku kãsa fahimtar wannan" ko "kada ku yi watsi da wannan"
"cewa bisa ga duban Ubangiji, rana ɗaya kamar shekaru dubu ne"
"Ubangiji baya jinkirin cikata alkawarensa"
Wasu mutane na tunanin cewa Ubangiji na jinkirin cikata alkawarensa saboda yadda suke duban lokaci dabam ne da yadda Allah ke duba.
Koda shike Ubangiji na hakuri kuma ya na so mutane su tuba, haiƙƙa zai dawo ya yi shari'a
Bitrus yana magana game da ranar da Allah zai hukunta kowa sai ka ce ɓarawo ne wanda zai zo babu stammani da mamaki kuma zai ɗauki mutane.
"Sammai za su ɓace"
AT: "da wuta Allah zai ƙone komai da komai"
Wannan na iya nufin 1) abubuwan da ke samaniya kamar rana, wata, da taurari ko kuwa 2) abubuwan da ke kunshe a sama da duniya kamar kasa, iska, wuta, da ruwa.
Allah zai ga dukan duniya da kuma ayyukan kowa, zai kuma hukunta kowane abu. AT: "Allah zai bayyana duniya da duk abubuwan da mutane suka aikata a cikin ta"
Bitrus ya fara gaya wa masubi yadda ya kamata su yi rayuwa a yayin da su na jiran ranar Ubangiji.
AT: "Tunda shike Allah zai hallaka duk waɗannan abubuwan ta wannan hanya"
Bitrus ya yi amfani da wannan tambayar don ya nanata abin da zai faɗa nan gaba, cewa su "yi rayuwar tsarki da kuma bin Allah." AT: "kun san irin mutanen da ya kamata ku zama."
AT: Allah zai hallaka sama da wuta, zai kuma narke komai da komai cikin zafi"
Bitrus yana magana game da "adalci" sai ka ce mutum. Wannan na nufin mutane masu adalci. AT: "inda mutane masu adalci za su dawwama" ko kuwa "inda mutanen za su yi rayuwar adalci"
AT: "ku yi iyakacin ƙoƙarin ku ku yi rayuwa a hanyar da ta dace saboda Allah ya same ku marasa tabo da marasa aibu, ku kuma zama da salama tare da shi da kuma juna"
Kalmomin nan "marasa tabo" da "marasa aibu" na nufin abu ɗaya ne na kuma nanata halin tsarki. AT: "tsarki gaba ɗaya"
A nan wannan na nufin "marasa laifi."
Domin Ubangiji mai haƙuri ne, shi ya sa ranar shari'a ba ta zo ba tukuna. Wannan ya ba wa mutane zarafin tuba da kuma ceto, kamar yadda ya bayana cikin [2 Bitrus 3:9] AT: "Kuma, ku yi tunani game da hakkurin Ubangijinmu a matsayin zarafin tuba da kuma ceto aka ba ku"
AT: "bisa ga hikimar da Allah ya ba shi"
"Bulus ya yi magana game da haƙurin Allah da ke kai ga samun ceto a cikin duk wasiƙunsa"
A kwai abubuwan cikin wasiƙun Bulus da ke da wuyar fahimta.
Jahilai da mutane marasa natsuwa sukan yi fasarar da ba daidai ba na abubuwan da ke da wuyar fahimta cikin wasiƙun Bulus.
"wanda ba a koyar da su ba da marasa natsuwa." Ba a koya wa mutanen nan yadda za su fasara nassin da kyau ba kuma ba su kafu cikin gaskiyar bisharar ba.
"kai ga hallakarsu"
"Waɗannan abubuwa" na nufin gaskiya game da haƙurin Allah da kuma koyaswar malaman ƙaryan nan.
"tsare kanku"
A nan "ɓadda" na nufin a rinjayi wani ya yi wani abin da ba daidai ba. AT: "don kada mutanen da ba sa bin doka su yaudare ku su kuma sa ku ku yi abin da ba daidai ba"
An yi magana game da aminci sai ka ce wata mallaka ne da masubi za su iya rasa wa. AT: "ku bar aikata adalci"
A nan girma cikin Alheri da sanin Ubangiji na nufin ƙara samun alherinsa da saninsa. Ana iya bayyana "alheri" da "yi kirki." AT: "ƙara samun alherin Ubangijinmu da Mai cetonmu Yesu Almasihu, da kuma ƙara saninsa" ko kuwa "ku ƙara sanin yadda Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Almasihu ya yi mana kirki, ku san shi yadda ya kamata"
1Abin nan da yake tun daga farko, wanda muka ji, wanda muka gani da idanunmu, wanda muka gani hannuwanmu suka kama, a wajen maganar rai. 2Ran kuwa aka baiyyana shi, muka gani, muka bada shaida, muka gaya maku labarin rai na har abada, wanda da yake a wurin Uba, aka kuma sanar da mu.3Wannan da muka gani muka ji muka baku labari, domin kuyi zumunci da mu, zumuncinmu kuwa tare da Uba yake da Dansa Yesu Almasihu. 4Haka nan, muna rubuta maku wadannan abubuwa domin farin cikinmu ya cika.5Wannan shi ne sakon da muka ji daga wurinsa mu kuwa muka sanar da ku: Allah haske ne a wurinsa kuwa babu duhu ko kadan. 6Idan mun ce muna zumunci da shi kuma muna tafiya cikin duhu, muna yin karya kuma bama aikata gaskiya. 7Amma idan muna tafiya cikin haske kamar yadda yake cikin haske, muna zumunci da juna, jinin Yesu Dansa ya wankemu daga dukka zunubi.8Idan mun ce bamu da zunubi, muna rudin kanmu kenan, ba kuma gaskiya a cikinmu. 9Amma idan mun fadi zunubanmu, shi mai aminci ne, mai adalci da zai gafarta mana zunubanmu, ya kuma wankemu daga dukkan rashin adalci. 10Idan mun ce bamu yi zunubi ba, mun mai da shi makaryaci kenan, maganarsa kuma bata cikinmu.
Yahaya ya cigaba da rubutu game da zumunci sa'anan ya nuna cewa yana iya yiwuwa domin Yesu yana tsakanin masubi da Uban.
Jumlar nan na nufin Yesu, wadda ya kasance kafin a halice kome. AT: "Muna rubuta maku game da shi wanda ya kasance kafin halitar dukan kome"
"forkon dukan kome" ko kuma "halitar duniya"
"wadda muka ji shi ya koyar"
An maimaita wannan ne domin nanaci. AT: "wadda mu da kan mu mun gani"
"Yesu, mai sa mutane su rayu hara abada"
Kalmar nan "rai" a wannan litafin gaba ɗaya na nufin fiye da rai na jiki. A nan yana madadin Yesu, rai na har abada.
AT: "Allah ya sa wannan Rai na har abadan ya zama sananne a gare mu" ko kuma "Allah ya sa mun iya sanin sa, shi Rai na har abadan"
"muka gan shi"
"mun yi alƙawarin gaya wa sauran mutane game da shi"
A nan "Rai na har abada" na nufin shi mai ba da rai, Yesu. AT: "shi wanda ya iza mu mu rayu har abada"
"da ke tare da Allah Uban"
Wato lokacin da yake rayuwa a duniya kenan. AT: "kuma ya zo ya kasance a tsakanin mu"
"muna faɗa muku abin da mu ma muka gani muka ji"
"ku zama abokan mu na kusa. Mu abokai ne da Allah Uban"
Bai fita a fili ko maganar Yahaya ya shafi masu karantun wasiƙar sa ko bai shafe su ba. Za ku iya fasara wannan ko ta wane hanya.
Waɗannan sunaye ne masu muhimmamci da ke bayyana dangartakar da ke tsakanin Allah da Yesu.
"domin ya cika farincikinmu" ko kuma "domin mu sa kanmu mu yi murna sosai"
Daga nan zuwa sura na gaba, Yohaya na rubutu game da zumunci--dangartakarmu da Allah da kuma sauran masubi.
Wannan wata magana ce da ke nufin cewa Allah mai tsarki ne gabaki ɗaya. Al'adun da ke kwatanta abu mai kyau da haske na iya barin wannan haka ba tare da fasara ba. AT: "Allah zallan adalci ne kamar zallan haske"
Wannan na nufin cewa Allah baya taɓa aikata zunubi kuma baya taɓa mugunta. Al'adun da ke kwatanta mugunta da duhu na iya barin duhu ba tare da fasara ba. AT: a cikinsa babu wani mugunta"
A nan "tafiya" na nufin yadda mutum ke rayuwa ko nuna hali. A nan "duhu" na nufin "mugunta" AT: "aikata mugunta"
A nan "tafiya" na nufin yadda mutum ke rayuwa ko nuna hali. A nan "haske" na nufin "mai kyau" ko "daidai." AT: ko "aikata abubuwa masu kyau kamar yadda Allah na da cikakken kyau" ko "ko aikata abin da ke daidai kamar yadda Allah ke daidai cikin komai.
Wannan na nufin mutuwar Yesu
Wannan wata suna ce mai muhimmanci sosai na Yesu, Ɗan Allah.
"ba mu taɓa zunubi ba"
"na yaudaran" ko kuma "na ƙarya"
An yi maganar gaskiya a nan kamar wani abu ne da ake iya samun sa cikin masubi da za a iya gani da ido ko a taɓa da hannu. AT: "bamu gaskata cewa abin da Allah ya faɗa gaskiya bane"
Jumloli biyun nan na nufin abu ɗaya ne. Yahaya ya yi amfani ne da su domin ya nanata cewa ba shakka Allah zai gafarta zunubanmu. AT: "kuma zai gafarta mana dukan inda mun yi kuskure
An ɗauki cewa mutumin da ya ce bashi da zunubi zai ce Allah maƙaryaci ne tunda Allah ya ce kowa mai zunubi ne. AT: "daidai ne da kiransa maƙaryaci, domin ya ce mun yi zunubi"
"Maganarsa" a nan na nufin "saƙo." AT: "bamu fahimci Maganar Allah ba balle ma mu yi biyayya da shi"
1'Ya'yana, na rubuta ma ku wadannan abubuwa domin kada kuyi zunubi. Amma idan wani yayi zunubi muna da matsakanci a wurin Uba, Yesu Almasihu, mai adalci. 2Shine fansar zunubanmu, ba ma namu kadai ba amma na duniya dukka. 3Ta haka muka san cewa mun san shi, idan mun kiyaye dokokinsa.4Duk wanda yace, "Na san Allah" amma bai kiyaye dokokinsa ba, makaryaci ne gaskiya kuwa ba ta cikinsa. 5Amma duk wanda ya kiyaye maganarsa, hakika kaunar Allah ta kammala a cikin wannan mutum. Ta wurin haka muka sani muna cikinsa. 6Duk wanda yace yana cikin Allah dole ne shi da kansa yayi tafiya kamar yadda Yesu Almasihu yayi.7Kaunatattu, ba sabuwar doka nike rubuta maku ba, amma tsohuwar doka ce wadda kuka ji tun farko. Tsohuwar dokar kuwa itace maganar da kuka ji tun farko. 8Amma yanzu ina rubuta maku sabuwar doka wadda gaskiya ce a cikin Almasihu da cikinku, saboda duhu yana wucewa, haske na gaskiya yana haskakawa.9Duk wanda yace yana cikin haske amma yana kin dan'uwansa, yana cikin duhu har yanzu. 10kuma wanda yake kaunar dan'uwansa yana cikin haske babu dalilin tuntube a wurinsa. 11Amma duk wanda yake kin dan'uwansa yana cikin duhu, yana kuma tafiya cikin duhu, bai san ma inda ya nufa ba, domin duhu ya makantar da shi.12Na rubuta maku, ya ku kaunatun 'ya'yana, saboda an gafarta zunubanku domin sunansa. 13Na rubuta maku, ubanni, saboda kun san shi wanda yake tun daga farko. Na rubuta maku matasa saboda kun yi nasara da mugun. Na rubuta maku, yara kanana, saboda kun san Uban. 14Na rubuta maku, Ubanni, saboda kun san shi wanda yake tun daga farko. Na rubuta maku, matasa, saboda kuna da karfi, kuma maganar Allah tana zaune cikinku. Kuma kun yi nasara da mugun.15Kada kuyi kaunar duniya ko abubuwan da suke cikin duniya. Idan wani yayi kaunar duniya, kaunar Uban bata cikinsa. 16Domin dukkan abubuwan da suke a cikin duniya, kwadayi na jiki, abin da idanu suke sha'wa, da rayuwar girman kai ta wofi, ba na Uban bane amma na duniya ne. 17Duniya tana wucewa tare da sha'awarta. Amma dukkan wanda ya aikata nufin Allah zaya kasance har abada.18Yara kanana, sa'a ta karshe ce. Kamar dai yadda kuka ji magafcin Almasihu yana zuwa, ko yanzu ma magaftan Almasihu da yawa sun rigaya sun zo, ta haka muka san sa'a ta karshe ce. 19Sun fita daga cikinmu, dama su bana cikinmu bane. Gama idan da su namu ne da sun ci gaba tare damu. Amma da yake sun fita, ya nuna su ba na cikinmu bane.20Amma ku kun karbi shafewa daga wurin Mai Tsarki, kuma dukkanku kun san gaskiya. 21Bana rubuta maku bane domin baku san gaskiya ba, amma saboda kun santa, kuma ba wata karya da ta fito daga gaskiya.22Wanene makaryaci shine wanda yayi musu cewa Yesu ba Almasihu bane? Wannan mutumin shi ne magafcin Almasihu, tun da yayi musun Uba yayi musun Dan. 23Ba wanda yayi musun Dan kuma yake da Uban. Dukkan wanda ya amince da Dan yana da Uban ma.24A game daku kuma, sai ku bari abinda kuka ji daga farko ya zauna a cikinku. Idan abin da kuka ji daga farko ya zauna a cikinku, kuma zaku kasance a cikin Dan da kuma Uban. 25Alkawarin da ya bamu kenan, rai na har abada. 26Na rubuta maku wadannan abubuwa ne game da wadanda zasu baudar daku.27Game daku, shafewar daku ka samu daga wurinsa tana nan a cikinku, baku bukatar wani ya koyar daku. Amma kamar yadda shafewar da kuka karba a wurinsa ta koya maku dukkan abu, kuma gaskiya ne ba karya bane, tana nan a cikinku kamar yadda a ka koya maku, ku kasance a cikinsa. 28Yanzu fa, 'ya'ya na kaunatattu, ku kasance a cikinsa domin sa'adda zai baiyyana mu zama da gabagadi ba tare da kunya ba a gabansa sa'adda zai zo. 29Idan kun sani shi mai adalci ne, kun sani dukkan wanda ke aikata adalci haifaffe ne daga wurinsa.
Yahaya ya cigaba da rubutu game da zumunci sa'anan ya nuna cewa yana iya yiwuwa domin Yesu yana tsakanin masubI da Uban
Anan kalmar nan "mu" na nufin Yahaya da dukkan masubi kuma "na shi" na nufin na Allah Uban, ko kuma na Yesu.
Yahaya tsohon mutum ne kuma shi ne shugabansu. Yayi amfani ne da wannan furci domin ya nuna yadda yake ƙaunansu. AT: "Ƙaunatattun 'ya'yana a cikin Almasihu" ko kuma "Ku da kuke ƙaunattatu a gare ni kamar 'ya'yan kaina"
"Ina rubuta mu ku wannan wasiƙa"
"Amma sa'and da wani yayi zunubi." Wannan abu ne da ke iya faruwa.
Kalmar nan "matsakanci" a nan na nufin Yesu. AT: "muna da Yesu Almasihu, mai adalci, mai magana da Uban mai kuma roƙa a gafarta mana"
"Allah baya fushi da mu kuma domin Yesu ya sadaukar da ransa saboda zunubanmu" ko kuma "Yesu shi ne wanda ya sadaukar da ransa saboda zunubanmu, don haka, Allah baya fushi da mu kuma a kan zunubanmu.
"mun sani da cewa mun san shi" ko kuma "mun san muna da dangantaka mai kyau da shi"
"idan mun yi biyayya da dokokinsa"
"Duk wanda ya ce" ko "Mutumin da ya ce"
"Ina da dangantaka mai kyau da Allah"
"baya biyayya" ko "rashin biyayya"
"abinda Allah ya ce mishi ya yi"
An yi maganar gaskiya a nan kamar wata abu ce da ake iya samu cikin masubi da za a iya gani da ido ko a taɓa da hannu. AT: "bai gaskata cewa abin da Allah ya faɗa gaskiya bane"
A kiyaye maganar mutum na nufin biyayya. AT: "yana yin abin da Allah ya ce mishi ya yi"
Wannan na iya nufin 1) "ƙaunar Allah" na nufin zuwa ga mutumin da ke ƙaunar Allah, kuma "kammala" na matsayin gabaki ɗaya ko a cike. AT: "mutumin da ke ƙaunar Allah gabaki ɗaya kenan" ko kuma 2) "ƙaunar Allah" na nufin ƙaunar da Allah na yi wa mutane, kuma "kammala" na masatayin cika nufinsa. AT: "ƙaunar Allah na cinma burin sa a cikin rayuwar wannan mutum"
Jumlar nan "muna cikinsa" na nufin maibin da na da dangantaka da Allah. AT: idan mun yi biyayya da abinda Allah ya faɗi, za mu iya tabbatar da cewa muna zumunci da shi" ko kuma "ta haka muka san cewa mun haɗe da Allah"
kasancewa a cikin Allah na nufin a cigaba da zumunta da shi. AT: cigaba da zumunta da Allah" ko kuma "zama a haɗe da Allah"
An yi maganar bi da rayuwa kamar tafiya ne a wata hanya. AT: "lallai ne ya yi rayuwa kamar yadda Yesu Almasihu ya yi" ko kuma "yakamata su yi biyayya da Allah kamar yadda Yesu Almasihu ya yi"
"ku mutane wadda na ke ƙauna, Ina" ko kuma "Ƙaunattun abokai, Ina"
"Na rubuta muku cewa ku ƙaunaci juna, wannan ba wata sabuwar abin yi bane amma tsohuwar dokar da kun taba ji." Yahaya na nufin umurnin Yesu mai cewa a ƙaunaci juna.
A nan "forƙo" na nufin lokacin da sun yanke shawara su bi Yesu. AT: daga forkon lokacin da kun gaskata da Almasihu"
"Tsohuwar dokar itace sakon da kuka ji"
"Amma a wata hanya dokar da na rubuta maku sabuwar doka ce"
"wadda gaskiya ce, kamar yadda ta bayyana a cikin halayen Almasihu da halayen ku"
A nan "duhu" na nufin "mugunta" kuma "haske" na nufin abu "mai kyau." AT: "domin kuna barin yin mugunta kuna kara yin abu mai kyau"
A nan zama "a cikin haske" na nufin yin abinda ke daidai. AT: "yana yin abin da ke daidai"
A nan zama "a cikin duhu" na nufin yin mugunta. AT: "na yin mugunta"
"babu abinda zai sa shi tuntuɓe." Kalmar nan "tuntuɓe" na nufin mutum ya kasa a ruhaniya ko a halin kirki. AT: "babu abinda zai sa shi zunubi" ko kuma "ba zai kasa yin abinda zai gamshi Allah ba"
A nan "tafiya" na nufin yadda mutum na rayuwa ko nuna hali. A nan zama "a cikin duhu" da kuma "tafiya a cikin duhun" na nufin abu ɗaya ne. Wannan na jan hankali ne cewa mugunta ne mutum ya ƙi ɗan'uwansa maibi. AT: ke yin mugunta"
wannan na maganar maibi da baya rayuwa yadda yakamata mai bi ya yi rayuwa. AT: "bai san ma abinda yakamata ya yi ba"
"duhu ya sa shi ba ya iya gani." Duhu na nufin zunubi ko mugunta. AT: "zunubi ya sa ba ya iya fahimtar gaskiya"
Yahaya tsohon mutum ne kuma shi ne shugabansu. Yayi amfani ne da wannan furci domin ya nuna yadda yake ƙaunansu. Duba yadda kun fasara wannan a [1 Yahaya 2:1] AT: "Ƙaunatattun 'ya'yana a cikin Almasihu" ko kuma "Ku da kuke ƙaunattatu a gare ni kamar 'ya'yan kaina"
AT: "Allah ya gafarta zunubanku"
"sunansa" na nufin Almasihu da kuma ko shi wanene. AT: "domin abin da Almasihu ya yi maku"
Kalmar nan "ubanni" a nan na nufin masubi kamilai. AT: "Ina rubuta maku, kamilai masubi"
"wanda yana rayuwa ko da yaushe" ko kuma "wanda yana nan koda yaushe." Yana nufin "Yesu" ko kuma "Allah Uba"
Wannan na iya nufin waɗanda ba sabobbin masubi ba amma suna girma a cikin ruhaniya. AT: "matasa a bi"
A nan "ƙarfi" na maibi ba na jiki bane, amma aminci ga Almasihu.
"maganar Allah" a nan na nufin saƙo daga Allah. Marubucin ya ambaci ƙarin amincin masubi ga Almasihu da kuma sanin sa kamar yana maganar kalmar Allah na nan a cikinsu. AT: "Sakon Allah na cigaba da koyar maku" ko kuma "kun san maganar Allah"
Marubucin na maganar kin yardar da masubi ke yi na bin shaiɗan da kuma lalata shirye-shiryen sa a matsayin wani abun nasara ne.
A 2:15-17 Kalmar nan "duniya" na nufin dukan abubuwan da mutane ke so su yi da ba su girmama Allah. AT: Kada halin ku ya zama kamar na mutanen da suke cikin duniya da basu girmama Allah, kuma basu ƙauna"
"abubuwan da waɗanda basu girmama Allah suke so"
Mutum ba zai iya ƙaunar duniya da kuma dukan abubuwan da basu darajanta Allah ya kuma ƙaunaci Uban a lokaci ɗaya ba.
"baya ƙaunar Uban"
Waɗannan sune jerin wasu abubuwan da ke cikin duniya. Sun bayyana abin da ake nufi da "kome da ke cikin duniya"
"samun ƙaƙƙarfan marmarin aikata zunubi"
"Ƙaƙƙarfan marmarin samun abubuwan da muke iya gani"
Wannan na iya nufin a mallaka da kuma halayya. AT: "yin alfahari da abinda mutum ke yi ko ke da shi" ko kuma "girman kai da mutane ke yi domin abubuwan da suke da shi da abubuwan da suke yi"
"basu zo daga Uban ba ne" ko kuma "ba yadda Uban ya koya mana mu yi rayuwa bane"
"wucewa" ko kuma "watarana ba za a same ta a nan ba"
"masubi da ke girma" Dubi yadda kun fasara wannan a [2:1]
Jumlar "sa'a ta ƙarshe" na nufin kafin Yesu ya dawo. AT: "Yesu zai dawo ba da daɗewa ba"
"akwai mutane da yawa da ke gaba da Almasihu"
"ya zo, kuma saboda haka mun sani" ko kuma "magabtan Almasihu sun zo, yanzu mun sani"
"Sun bar mu"
"amma a gaskiya su ba namu ba ne" ko kuma "a gaskiya su ba namu bane tun farko" Abinda ya sa su ba namu bane da gaske shine domin su ba masubin Yesu bane.
"Mun san wannan domin da basu barmu ba inda su ainihi masubi ne.
"Mun san haka ne domin inda su masubi ne da gaske da basu barmu ba"
Yahaya yana maganar Ruhu Mai Tsarki kamar shi "shafewa ne" da mutane sun karɓa daga wurin Yesu. AT: "Amma Mai Tsarkin ya shafe ku" ko kuma "Amma Yesu, Mai Tsarkin ya ba ku Ruhunsa"
Wannan na nufin Yesu. AT: Yesu, Mai Tsarkin"
AT: Abinda ke gaskiya ... ba wata ƙarya da ta fito daga abinda ke gaskiya"
Wanane maƙaryacin? Duk wanda ya yi musun cewa Yesu ba Almasihu ba ne. Yahaya yayi amfani da wannan tambayan ne don ya nanata su wanene masu ƙarya.
"na ƙin cewa Yesu ne Almasihu" ko kuma "na cewa ba Yesu ne Almasihu ba"
"na ƙin faɗin gaskiya game da Uban da Ɗan" ko kuma "na ƙin Uban da Ɗan."
Waɗannan wasu sunaye ne masu muhimmanci da ke bayyana dangantakar da ke tsakanin Allah da Yesu.
"ke na Uban"
"faɗin gaskiya game da Ɗan"
Wannan yana nuna yadda Yahaya ke gaya musu yadda yakamata su yi rayuwa a mastsayin masu bin Yesu a maimakon yadda masu gãba da Almasihu ke rayuwa.
"ku tuna ku kuma gaskata da abinda kuka ji tun farƙo". Za a iya ƙarin bayyanin yadda suka ji shi, abinda suka ji, da kuma abinda "forƙon" ke nufi: AT: "ku cigaba da gaskata abinda muka koya maku game da Yesu kamar yadda kun gaskata tun da kuka zama masubi"
"abinda mun koya maku game da Yesu lokacin da kuka zama masubi"
Wannan shine alkawarin da ya bamu--rai na har abada" ko kuma "Ya alkawarta mu mu rayu har abada"
A nan "bauɗar da ku" na nufin rinjayar mutum ya gaskata cewa abu ba gaskiya bane. AT: waɗanda suke so su yaudare ku" ko kuma "waɗanda suke so su sa ku ku yarda da ƙarya game da Yesu Almasihu"
Wannan na nufin "Ruhun Allah". Duba rubutun da aka yi game da "shafewa" a [2:20]
AT: "domin shafewarsa yana koya maku dukan abubuwan da kuke buƙata ku sani"
A kasance a cikin mutum na nufin a cigaba da zumunci da shi. Dubi yadda kun fasara "kasance a cikin Allah" a [2:5-6]. AT: "cigaba da zumunci da shi" ko kuma "zama a haɗe da shi"
An yi amfani ne da wannan kalmar don a nuna wata sabuwar bangaren wasiƙar.
Yahaya tsohon mutum ne kuma shi ne shugabansu. Yayi amfani ne da wannan furci domin ya nuna yadda yake ƙaunarsu. AT: "Ƙaunatattu 'ya'yana a cikin Almasihu" ko kuma "Ku da kuke ƙaunatattu a gare ne kamar 'ya'yan kaina"
"mun ganshi"
"rashin tsoro"
...
"yayin da Ya sãke zuwa kuma"
"haifaffe ne na Allah" ko kuma "Ɗan Allah ne"
1Dubi irin kaunar da Allah ya bamu, har da za a kira mu 'ya'yan Allah, haka muke kuwa. Saboda wannan dalili ne duniya bata san muba, saboda bata san shi ba. 2Kaunatattu, yanzu mu 'ya'yan Allahne, kuma ba a bayyana mana yadda zamu zama ba tukuna, mun sani sa'adda Almasihu zai bayyana, zamu zama kamarsa, domin zamu ganshi kamar yadda yake. 3Dukkan wanda yake da wannan bege game da gidan gobe ya kan tsarkake kansa, kamar yadda shima yake da tsarki.4Dukkan wanda yaci gaba da yin zunubi yana ketare shari'a kenan. Gama zunubi ketare shari'a ne. 5Kun sani Almasihu ya bayyana domin ya dauke zunubai ne. Kuma a cikinsa babu zunubi. 6Ba wanda zai kasance a cikinsa da zai cigaba da yin zunubi. Ba wanda zai ci gaba da aikata zunubi da zai ce ya sanshi, ko kuma ya ganshi.7'Ya'yana kaunatattu, kada ku bari kowa ya baudar da ku, wanda yake aikata adalci shi adali ne, kamar yadda Almasihu yake adali. 8Wanda yake aikata zunubi na ibilis ne, gama ibilis yayi zunubi tun daga farko. Dalilin haka ne Dan Allah ya bayyana, domin ya rushe ayyukan ibilis.9Duk wanda aka haife shi daga Allah ba ya yin zunubi, saboda irin Allah na cikinsa. Ba zaya iya ci gaba da yin zunubi ba domin an haife shi daga wurin Allah. 10Ta haka ne ake bambanta 'ya'yan Allah da 'ya'yan ibilis. Dukkan wanda baya aikata adalci ba na Allah bane; haka kuma wanda ba ya kaunar dan'uwansa.11Domin wannan shine sakon da kuka ji tun daga farko: cewa mu kaunaci junanmu, 12ba kamar Kayinu ba wanda yake na shaidan kuma ya kashe dan'uwansa. Me yasa ya kashe shi? Saboda ayyukansa miyagu ne, na dan'uwansa kuma masu adalci ne.13Kada kuyi mamaki 'yan'uwana, idan duniya ta ki ku. 14Mun sani mun ratsa mutuwa zuwa cikin rai, saboda muna kaunar 'yan'uwa. Dukkan wanda ba ya yin kauna, shi matacce ne. 15Dukkan wanda yake kin dan'uwansa, mai kisan kai ne. Kun kuma sani babu rai na har abada a cikin mai kisankai.16Ta wurin haka muka san kauna, da ya ke Almasihu ya bayar da ransa saboda mu. Mu ma ya kamata mu bada ranmu saboda 'yan'uwamu. 17Amma duk wanda yake da kayan duniya, ya ga dan'uwansa cikin bukata, kuma bai ji tausayinsa ba, ta yaya kaunar Allah ke cikinsa? 18'Ya'yana kaunatattu, kada muyi kauna ta fatar baki kawai, amma muyi aikin kauna da gaskiya.19Ta wurin haka mun sani mu masu gaskiya ne kuma mun tabbatar da zuciyarmu a gabansa. 20Gama idan zuciyarmu bata kayar damu ba, Allah ya fi zuciyarmu girma, kuma yana sane da kome. 21Kaunatattu, idan zuciyarmu bata kashe mu ba, muna da gabagadi a gaban Allah. 22Kuma duk abin da muka nema zamu samu a wurinsa, saboda muna kiyaye dokokinsa, muna yin abubuwan da suka gamshe shi.23Kuma ummurninsa kenan: mu bada gaskiya ga sunan Dansa Yesu Almasihu, mu yi kaunar juna kuma kamar yanda ya bamu wannan doka. 24Duk wanda yake kiyaye umarnin Allah, yana cikinsa, Allah kuma yana cikin mutumin. Ta haka muka gane cewa yana cikinmu, Ta wurin Ruhu, wanda ya bamu.
A wannan sashin, Yahaya yana faɗi wa masubi game da sabuwar halittarsu, wadda ba ya iya zunubi.
"Yi tunanin yadda Ubanmu yana matuƙar ƙaunarmu"
"Uban ya kira mu 'ya'yansa"
A nan wannan na nufin mutanen da sun zama na Allah ta wurin bangaskiya cikin Yesu.
Wannan na iya nufin 1) "Saboda mu 'ya'yan Allah ne kuma saboda duniya bata san Allah ba, bata san mu ba." Ko kuma 2) Saboda duniya bata san Allah ba, bata san mu ba."
A nan "duniyan" na nufin mutanen da basu girmama Allah. Ana iya ƙarin bayyanin abinda duniya bata sani ba. AT: "waɗanda basu girmama Allah basu san cewa mu na Allah ba ne, saboda basu san Allah ba"
"Ku mutane da nake ƙauna, mu" ko kuma "Ƙaunattatun abokai, mu, " Dubi yadda aka fasara wannan a [2:7]
AT: "Allah bai riga ya bayyana ba"
Wannan na iya nufin "faɗi" ko "nuna"
Dukan wanda yana sa rai da gabagaɗi a kan ganin Almasihu yadda yake zai tsarkake kansa saboda Almasihu yana da tsarki"
"Almasihu ya bayyana" ko kuma "Uban ya bayyana Almasihu"
"kasance da dangantaka da Allah" Duba yadda kun fasara wannan a [2:2-6]
Yahaya yana amfani da "gani" da "sani" ne domin ya ce mutumin mai yin zunubi bai sadu da Almasihu a ruhu ba. Mutumin da yake rayuwa bisa ga halin zunubi ba zai iya sanin Almasihu ba. AT: "Ba wanda ... bai gaskatawa da shi da gaske ba"
Yahaya tsohon mutum ne kuma shi ne shugabansu. Yayi amfani ne da wannan furci domin ya nuna yadda yake ƙaunarsu. AT: "Ƙaunatattun 'ya'yana a cikin Almasihu" ko kuma "Ku da kuke ƙaunatattu a gare ne kamar 'ya'yan kaina"
A nan "ɓaudar da ku" na nufin a rinjayi mutum har ma ya yarda da abinda ba gaskiya ba ne. AT: "kada ku bar kowa ya mayar da ku wawaye" ko kuma "kada ku bar kowa ya ruɗe ku"
"Shi mai aikata abinda ke daidai yana faranta wa Allah rai kamar yadda Almasihu yana farantawa Allah rai."
"ya zama na ibilis" ko kuma "yana kamar ibilis ne"
Wannan na nufin ainihin forkon haliita kafin mutum ya aikata zunubi na forƙo.AT: "tun ainihin forkon lokacin halita"
AT: "Allah ya bayyana Ɗansa"
Wannan wata suna ce mai muhimmanci sosai na Yesu da ke bayyana dangantakar sa da Allah.
AT: "Duk wanda Allah ya mayar da shi ɗansa"
Wannan na maganar Ruhu Mai Tsarki ne, wanda Allah ke ba wa masubi wanda kuma yake sa su iya gãba da zunubi, su kuma aikata abinda kan gamshi Allah kamar shi wani irin hatsi ne da ake shukawa cikin ƙasa har yayi girma. Wani lokaci, a kan ce da wanna sabuwar halitta. AT: "Ruhu Mai Tsarki"
AT: "Allah ya bashi sabuwar rai na ruhaniya" ko kuma "shi ɗan Allah ne"
AT: "Ta haka ne mu ke sanin 'ya'yan Allah da kuma 'ya'yan ibilis"
Ana iya fahimtar waɗannan kalmomin "na Allah" a fuskoki biyu a jumlar. AT: Dukan wanda bai aikata adalci ba ba daga Allah ba ne; dukan wanda ba ya ƙaunar ɗan'uwansa shi ma ba daga Allah ba ne" ko kuma "waɗanda suke aikata adalci na Allah ne, kuma waɗanda suke ƙaunar 'yan'uwansu na Allah ne su"
A nan "ɗan'uwa" na nufin 'yan'uwa masubi.
Kayinu da Habila ne 'ya'yan Adamu da Hauwa'u, na miji da macen forƙo.
"kada mu yi yadda Kayinu ya yi"
Wannan na nufin Kayinu ɗan'uwan Habila.
Yahaya yana amfani ne da wannan tambayar don ya koya wa masu sauraronsa. AT: "Ya kashe shi ne saboda"
Ana iya fahimtar kalmar nan "ayyuka" ta fuskoki biyu. AT: "Ayyukan Kayinu miyagu ne, ayyukan ɗan'uwansa kuma masu adalci ne" ko kuma "Kayinu ya aikata mugunta, ɗan'uwansa kuma ya yi abinda ke daidai.
"'yan'uwana masubi." Masu karatun wasiƙar Yahaya maza da mata ne.
A nan kalmar nan "duniya" na nufin mutanen da ba su girmama Allah. AT: "idan waɗanda ba su girmama Allah sun ƙi ku masu girmama Allah"
An yi maganar sharaɗin rayuwa da na mutuwa kamar wasu wurare ne da mutum zai iya bari ko zuwa. AT: "Mu ba matattu bane a ruhaniya har yanzu amma muna da rai a ruhu"
Kalmar nan "rai" a wannan wasiƙar gaba ɗaya ya wuci rai na jiki kawai. A nan ya tsaya ne madadin Yesu, rai na har abada. Duba yadda kun fasara wannan a [1:1-2]
"yana mace a ruhaniya har yanza"
Yahaya yana maganar mutumin da ke ƙin ɗan'uwansa maibi a matsayin mai kisankai ne. Tunda mutanen da ke kisan kai su na yin haka ne don sun ƙi sauran mutanen, Allah yana ɗaukan duk wanda ke ƙin wani a matsayin mai laifi kamar wanda ya kashe mutum ne. AT: Dukan wanda ya na ƙin ɗan'uwansa mai laifi ne daidai da wanda ya ƙashe mutum"
"Rai na har abada" wani abu ne da Allah ke ba masubi bayan sun mutu, amma shi ma wani iko ne da Allah ke ba wa masubi a wannan rai don ya taimake su su daina yin zunubi kuma su fara aikata abinda kan gamshe shi. An yi maganar rai na har abada kamar wani mutum ne da na iya zama a cikin mutum. AT: "mai kisan kai ba shi da ikon rayuwa na ruhaniya"
Wannan furcin na nufin "Almasihu ya yarda ya ba da ransa domin mu" ko kuma "Almasihu ya yarda ya mutu domin mu"
mallaka kamar kuɗi, abinci, ko sutura
"ya lura cewa ɗan'uwansa na bukatan taimako"
Anan Bai ji tausayinsa ba na nufin bai nuna masa ƙauna ba. AT: "bai nuna masa ƙauna ba" ko kuma "bai yarda ya taimake shi ba"
Yahaya yana amfani ne da wannan tambayan ya koyar wa masu sauraronsa. AT: "ƙaunar Allah bata cikinsa"
Yahaya tsohon mutum ne kuma shi ne shugabansu. Yayi amfani ne da wannan furci domin ya nuna yadda yake ƙaunarsu. AT: "Ƙaunatattun 'ya'yana a cikin Almasihu" ko kuma "Ku da kuke ƙaunatattu a gare ni kamar 'ya'yan kaina"
Wannan jumlar "ta fatar bãki" na nufin abinda mutum ke faɗi. An bayyana kalmar "ƙaunar" a bangare na biyu na jimlar. AT: "kada ku ce kuna ƙaunar mutane kawai, amma ku nuna cewa kuna matukar ƙaunar mutane ta wurin taimakonsu"
"mun zama masu gaskiya" AT: "muna rayuwa bisa yadda Yesu ya koya mana kenan"
Kalmar nan "zuciya" a nan na nufin yadda mutum ke ji. AT: "ba a zargin mu da laifi"
A nan "zuciya" na nufin tunani ko lamiri. A nan "zuciya na kayar da mu" na nufin zargi" AT" "idan mun san cewa mun yi zunubi kuma hakan ya jawo mana zargi"
A nan "zuciyar" na nufin tunani ko lamiri. "Allah ya fi zuciyarmu" na nufin Allah ya san fiye da mutum. Saboda haka, zai iya shar'anta abubuwa fiye da yadda mutum zai iya. Sakamakon wannan gaskiyar na iya nufin cewa Allah na da yawan jin ƙai fiye da yadda lamirinmu ke ɗauka. AT: "Allah ya sani fiye da mu"
"ku da nake ƙauna, idan" ko kuma "Ƙaunatattun abokai, idan". Duba yadda ku ka fasara wannan a aya [2:7]
Ana maganar ra'ayin Allah kamar ya danganta ne ga abinda yake gani na faruwa a gabansa. AT: "kuma muna yin abinda ya gamshi shi"
"umurni" da "doka" anan na nufin abu ɗaya ne. AT: "Wannan shi ne abinda Allah ya umurce mu mu yi." "Ba da gaskiya ... kamar yadda ya dokacemu muyi"
Wannan wata suna ce mai muhimmanci sosai na Yesu da ke bayyana dangartakansa da Allah.
A nan an bayyana dangantaka ta kusa da ke tsakanin masubi ta wurin amfani da "cikinsa." Dubi yanda aka fasara a [2:-6]
1Kaunatattu, kada ku amince da kowanne ruhu. Amma ku gwada ruhohi ku gani ko na Allah ne, gama annabawan karya masu yawa sun fito zuwa cikin duniya. 2Ta haka zaku gane Ruhun Allah, dukkan ruhun da ya amince Yesu Almasihu ya zo cikin jiki na Allah ne, 3kuma dukkan ruhun da bai amince da Yesu ba, ba na Allah bane. Wannan ruhun magafcin Almasihu ne, wanda kuka ji cewa yana zuwa, ya kuwa rigaya yazo cikin duniya.4'Ya'yana kaunatattu, daga Allah ke, kuma kun rigaya kun yi nasara da su da yake wanda ke cikinku ya fi wanda ke cikin duniya girma. 5Su na duniya ne, saboda haka abin da suke fadi na duniya ne, duniya kuma tana sauraronsu. 6Mu na Allah ne, duk wanda ya san Allah yana saurarenmu. Wanda ba na Allah bane, ba ya sauraronmu. Ta haka muka gane ruhun gaskiya da ruhun karya.7Kaunatattu, mu yi kaunar juna, gama kauna ta Allah ce, wanda yake kauna an haife shi daga wurin Allah, kuma ya san Allah. 8Mutumin da baya kauna ba na Allah ba ne, kuma bai san Allah ba, gama Allah kauna ne.9A cikn haka aka bayyana kaunar Allah a garemu, Allah ya aiko tilon Dansa cikin duniya domin mu rayu ta wurinsa. 10A cikin wannan akwai kauna, ba mune muka kaunaci Allah ba, amma shi ya kaunace mu ya aiko da Dansa ya zama mai gafarta zunubanmu.11Kaunatattu, da yake Allah ya kaunace mu haka, ya kamata mu kaunaci junanmu. 12Ba wanda ya taba ganin Allah. Idan muna kaunar juna, Allah yana zaune cikinmu, kuma kaunarsa tana zaune a cikinmu. 13Ta haka mun sani muna zaune a cikinsa shi kuma a cikinmu, saboda ya bamu Ruhunsa. 14Mun gani mun shaida, cewa Allah ya aiko Dan, domin ya zama mai ceton duniya.15Duk wanda ya amince Yesu Dan Allah ne, Allah na zaune cikinsa, shi kuma a cikin Allah. 16Mun sani kuma mun gaskata da kaunar da Allah yake da ita dominmu, Allah kauna ne wanda yake zama cikin kauna yana zaune cikin Allah, Allah kuma a cikinsa.17Dalilin wannan kauna ta kammala a cikinmu, domin mu kasance da gabagadi a ranar shari'a, domin kamar yanda ya ke haka muma muke a cikin duniyan nan. 18Babu tsoro a cikin kauna. Amma cikkakiyar kauna takan kawar da tsoro, domin kuwa tsoro na tafi tare da hukunci. Amma wanda yake da tsoro ba shi da cikkakiyar kauna.19Muna kauna domin Allah ne ya fara kaunarmu. 20Idan wani ya ce,"Ina kaunar Allah", amma yana kin dan'uwansa, makaryaci ne. Domin wanda baya kaunar dan'uwansa da yake gani, ba zai iya kaunar Allah da bai taba gani ba. 21Wannan ne umarnin da muke da shi daga wurinsa: Duk wanda yake kaunar Allah dole ne ya kaunaci dan'uwansa.
Yahaya yana bada kashedi wa malaman ƙarya wadda suke musun cewa Yesu yana da jikin mutum da malaman da ke magana kamar yadda waɗanda ke ƙaunar duniya ke yi.
"ku mutanen da nake ƙauna, kada ku amince da" ko kuma "Ƙaunatattu abokai, kada ku amince da." Duba yadda kun fasara wannan a [2:7].
A nan, Kalmar nan "ruhu" na nufin ikokin ruhu ko kuma wani halitta da ke ba mutum wata sako ko anabci. AT: "kada ku amince da kowane annabi da ke cewa ya karɓi sako daga wani ruhu"
A nan, kalmar nan "ruhohi" na nufin ikokin ruhaniya ko kuma wani halittada ke ba mutum wani sako ko anabci. AT: "yi tunani a hankali game da abinda annabin ke faɗi"
A nan "jiki" na nufin jikin mutum. AT: "ya zo a matsayin rayayyen mutum" ko kuma "ya zo a wannan jiki da muke iya gani"
Waɗannan ne annabawan da ke gãba da Almasihu, wadda kuka ji cewa suna zuwa, sun kuwa zo cikin duniya"
Yahaya tsohon mutum ne kuma shi ne shugabansu. Yayi amfani ne da wannan furci domin ya nuna yadda yake ƙaunarsu . AT: "ƙaunatattu 'ya'yana a cikin Almasihu" ko kuma "ku da kuke ƙaunatattu a gare ni kamar 'ya'yan kaina"
"baku amince da malaman ƙaryan ba"
"Allah, wanda ke cikinku ya"
Wannan na iya nufin 1) shaiɗan AT: "Shaiɗan, da ke duniya" ko kuma "Shaiɗan, da ke amfani da waɗanda ba su biyayya da Allah" ko kuma 2) masu koyas da abubuwan duniya AT: "masu koyas da abubuwan duniya" (Dubi: )
Wannan na nufin cewa suna samun ikonsu daga duniya ne. "duniya" kuma na nufin "wanda ke cikin duniyan", Shaiɗan. Ko da shike yana kuma iya nufin masu aikata zunubi waɗanda suke jin su suna kuma basu ƙarfi.
"duniya" a nan na nufin "shi wanda ke cikin duniya," Shaiɗan. Ko da shike yana kuma iya nufin masu aikata zunubi waɗanda suke jin su suna kuma basu ƙarfi. AT: "saboda haka suna koyar da abin da suka koya daga mutane masu aikata zunubi"
Kalmar nan "duniya" na nufin mutanen da basu biyayya da Allah. AT: "don haka mutanen da basu biyayya da Allah suna sauraronsu"
"ku mutanen da nake ƙauna, kada ku amince da" ko kuma "Ƙaunatattu abokai, kada ku amince da." Duba yadda kun fasara wannan a [2:7].
"yakamata masubi su ƙaunace sauran masubi"
"kuma domin waɗanda suke ƙaunar 'yan'uwansu masubi sun zama 'ya'yan Allah sun kuma san shi"
"domin Allah ne yakan sa mu mu ƙaunace juna"
Wannan na nufin mutumin da ke da dangantaka da Allah kamar yadda ɗa yake da ubansa.
Jimlar nan "Allah ƙauna ne" na nufin "halin Allah ƙauna ne." AT: "Waɗanda ba su ƙaunar 'yan'uwansu masubi basu san Allah ba domin halin Allah shi ne a ƙaunace mutane.
A cikin haka ... a garemu: Allah ya aiko tilon Ɗansa." Jumlar "A cikin haka" na nufin jumlar nan "Allah ya aiko da tilon Ɗansa."
Ana iya fasara "ƙauna" zuwa kalmar aiki. AT: "Allah ya nuna cewa yana ƙaunar mu"
"domin ya sa mu rayu har abada saboda abinda Yesu yayi"
"Allah ya nuna mana abinda ake nufi da sahihiyar ƙauna"
A nan "gafartawa" na nufin mutuwar Yesu a bisa giciye ya kwantar wa Allah da fushinsa saboda zunubi. AT: "ya aiko Ɗansa ya zama hadayar da ya kwantar wa Allah zuciya saboda zunubanmu"
"ku mutanen da nake ƙauna, kada ku amince da" ko kuma "Ƙaunatattu abokai, kada ku amince da." Duba yadda ku ka fasara wannan a [2:7].
"tunda Allah ya ƙaunace mu haka"
"ya kamata masubi su ƙaunaci sauran masubi"
Zama a cikin mutum na nufin cigaba da zumunta da shi. Dubi yadda ku ka fasara wannan a [2:5-6] AT: "Allah yana cigaba da zumunta da mu ... mu cigaba da zumunta da Allah shi kuma zai cigaba da zumunta da mu" ko kuma "Allah yana haɗe da mu ... mu kuma muna a haɗe da Allah shi kuma yana haɗe da mu"
AT: "shi kuma yana zaune da mu"
"ƙaunar Allah ta cikă a cikinmu"
Fasarar ku na iya fin ba da haske idan kun cire ko "ta haka" ko kuma "saboda" AT: "mun sani ... mu saboda ya bayar" ko kuma "Ta haka mun sani ... mu: ya bayar"
"kuma mu manzannin mun ga Ɗan Allah mun kuma faɗa wa kowa cewa Allah Uban ya aiko Ɗansa ya ceci mutanen da ke wannan duniyan"
Waɗannan wasu sunaye ne da ke bayyana dangantakar da ke tsakanin Allah da Yesu
"Duk wanda ya faɗi gaskiya game da Yesu, cewa shi Ɗan Allah ne"
Wannan wata suna ce mai muhimmanci na Yesu wadda ke bayyana dangantakasa da Allah.
A zauna a cikin mutum yana nufin a cigaba da dangantaka da shi. Dubi yadda ku ka fasara wannan a [2:5-6]. AT: "Allah yana cigaba da zumunta da shi kuma yana cigaba da dangantaka da Allah" ko kuma "Allah yana haɗe da shi shi kuma yana haɗe da Allah"
AT: "shi kuma yana zaune a cikin Allah" (Dubi: Ellipsis)
Wannan na nufin cewa halin Allah ƙauna ne." Dubi yadda kuka fasara wannan a [4:8]
"waɗanda sun cigaba da ƙaunan wasu"
A zauna a cikin mutum na nufin a cigaba da dangantaka da shi. Dubi yadda ku ka fasara wannan a [2:5-6]. AT: "na cigaba da dangantaka da Allah, kuma Allah na cigaba da dangantaka da shi" ko kuma "yana haɗe da Allah, Allah kuma yana haɗe da shi"
Wannan na iya nufin 1) "Dalilin wannan" na maida tunanin mu baya zuwa [4:16]. AT: Domin duk wanda yake rayuwa cikin ƙauna yana cikin Allah, Allah kuma yana cikinsa. Allah ya cika ƙaunar da yake da shi domin mu saboda haka muna da cikakken gabagaɗi" ko kuma 2)"Saboda haka" na nufin "za mu iya samun gabagaɗi". AT: Muna da gabagaɗi cewa Allah zain karɓe mu a ranar da zai shari'anta kowa, don haka mun san irin ƙaunar da yake da shi domin mu"
AT: Allah ya sa ƙaunarsa domin mu yă zama cikakke"
"domin dangantakar da Yesu ke da shi da Allah ɗaya ne da dangantakar da muke da shi da Allah a duniyan nan"
A nan an fasara "ƙauna" kamar wani mutum ne da ke da ikon cire tsoro. Ƙaunar Allah kamalalle ne. AT: "Amma sa'and da ƙaunar mu ta cika, ba za mu ji tsoro kuma ba"
"domin za mu ji tsoro ne kaɗai idan mun san cewa zai hukunta mu"
AT: "Amma idan mutum yana da tsoron cewa Allah zai hukunta shi, ƙaunarsa bai cika ba"
"yana ƙin ɗan'uwansa mai bi"
Idan maganganun biyu a jeri ɗaya na kawo rikecewa, ana iya fasara su dabamdabam. AT: "wanda yake kin ɗan'uwansa, wadda yake gani, ba zai iya ƙaunar Allah ba, wadda bai taɓa gani ba"
1Duk Wanda ya gaskata Yesu shine Almasihu haifaffe na Allah ne. Kuma duk wanda ya kaunaci uba ya kaunaci dan da uban ya haifa. 2Haka muka sani muna kaunar 'ya'yan Allah: yayin da muka kaunaci Allah, kuma muka aikata umarninsa. 3Wannan itace kaunar Allah, cewa mu kiyaye umarninsa. Domin umarninsa ba masu nawaitawa bane.4Duk wanda yake haifaffe na Allah yakan yi nasara da duniya. Wannan itace nasarar da ta rinjayi duniya, wato bangaskiyarmu. 5Wanene wannan mai nasara da duniya? Sai dai wanda ya gaskata Yesu Dan Allah ne.6Wannan shine wanda yazo ta wurin ruwa da jini: Yesu Almasihu. Ya zo ba ta wurin ruwa kadai ba, amma ta wurin ruwa da jini. 7Domin akwai uku wadanda suke bada shaida: 8Ruhu, da ruwa, da kuma jini. Wadannan ukun kuwa manufarsu daya ce.9Idan mun karbi shaidar mutane, shaidar Allah ta fi girma. Wannan ita ce shaidar Allah, wato ya bada shaida akan Dansa. 10Wanda ya gaskata da Dan Allah shaidar tana nan tare da shi. Duk wanda bai bada gaskiya ga Allah ba, ya mai da shi makaryaci kenan, domin bai gaskata da shaidar da Allah ya bayar game da Dansa ba.11Wannan ita ce shaida: Allah ya bamu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Dansa. 12Duk wanda yake da Dan, yana da rai. Duk wanda ba shida Dan Allah kuwa bashi da rai.13Na rubuto maku wannan ne don ku tabbata kuna da rai madawwami--a gare ku wadanda suka gaskata da sunan Dan Allah. 14Wannan shine gabagadin da muke da shi a gabansa, wato, in mun roki kome bisa ga nufinsa, zai ji mu. 15Haka kuma, in mun san yana jinmu--Duk abin da mu ka rokeshi--mun sani muna da duk abin da muka roka daga gare shi.16Idan wani ya ga dan'uwansa ya yi zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yayi masa addu'a, Allah kuwa zai ba shi rai. Ina nufin wadanda suka yi zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yake kai wa ga mutuwa: Ban ce a yi addu'a domin wannan ba. 17Dukkan rashin adalci, zunubi ne, amma akwai zunubin da bai kai ga mutuwa ba.18Mun sani kowanne haiffafe daga wurin Allah ba ya yin zunubi. Amma wanda ke haifaffe daga wurin Allah, ya kan kare shi, mugun nan kuwa ba zai iya yi masa illa ba. 19Mun sani mu na Allah ne, mun kuma sani dukkan duniya tana hannun mugun nan.20Amma mun sani Dan Allah yazo, kuma ya bamu fahimta, domin mu san wanda yake shi ne mai gaskiya. Haka kuma muna cikin wannan wanda shine gaiskiya, kuma cikin Dansa Yesu Almasihu. Shine Allah na gaskiya, da kuma rai na har abada. 21'Ya'ya, ku tsare kanku daga bautar gumaka.
Yahaya yana cigaba da koyaswa masu karatun wasiƙarsa game da ƙaunar Allah da kuma ƙaunar da yakamata masubi su kasance da ita domin sun samu wata sabuwan halitta daga Allah.
"ɗan Allah ne"
"Yayin da mun ƙaunaci Allah mun kuma kiyaye umarninsa, toh mun san cewa muna ƙaunar 'ya'yansa"
"Domin yayin da mun kiyaye umarninsa, shi ne ƙaunar Allah ta gaskiya"
"Umarninsa ba masu wuya bane"
"nauyi" ko "murkushewa" ko "wuya"
"duk 'ya'yan Allah sukan yi nasara"
"na da nasara a kan duniya" ko kuma "suna kin aikata miyagun abubuwan da marasabi ke yi"
A nan "duniya" na nufin dukan mutane masu aikata zunubi da kuma sha'anin miyagu da ke duniya. AT: "dukan abin duniya da ke gãba da Allah"
"Wannan itace abinda ke bamu ikon tsayayya da duk abinda zai kai mu ga yi wa Allah zunubi: bangaskiyar mu" ko kuma "Bangaskiyar mu ne ke bamu ikon tsayayya da duk abinda zai kai mu ga yi wa Allah zunubu"
Yahaya ya yi amfani ne da wannan tambayan ya gabatar da wata sabuwan abu da yake so ya koyar. AT: "Ni zan gaya maku wanda ke mai nasara da duniya"
Wannan na nufin ko ma wa, duk dai wanda ya gaskata da haka. AT: "Duk wanda ya gaskata cewa Yesu Ɗan Allah ne"
Wannan wata suna ce mai muhimmanci na Yesu wadda ke bayyana dangantakarsa da Allah.
Yahaya yana koyarwa a kan Yesu Almasihu da kuma abinda Allah ya faɗi game da shi.
Yesu Almasihu shi ne wanda ya zo ta wurin ruwa da jini. A nan "ruwa" na iya nufin baftismar Yesu, "jini" kuma na iya zama alama ce ta mutuwar Yesu a bisa giciye. AT: "Allah ya nuna cewa Yesu Almasihu Ɗansa ne ta wurin baftismar Yesu da mutuwarsa a bisa giciye"
A nan "ruwa" na nufin baftismar Yesu, "jini" kuma na iya zama alama ce ta mutuwar Yesu a bisa giciye. AT: "Ba ta baftisma ne kawai Allah ya nuna mana cewa Yesu Ɗansa ba ne, amma ta wurin baftismarsa da mutuwarsa a bisa giciye"
Mai fasara na iya ƙarin bayani game da dalilin ya sa yakamata mu gastata da abinda Allah ke faɗi: AT: "idan mun gaskata da abinda mutane ke faɗi, toh sai mu gaskata da abinda Allah ke faɗi domin shi mai faɗin gaskiya ne a ko da yaushe"
Wannan, wato "karɓi shaidar", na nufin a gaskata da abinda wani ke faɗi game da wani abinda ya gani. AT: "gaskata da abinda mutane sun shaida" ko kuma "gaskata abinda mutane ke faɗi game da abinda suka gani"
shaidar Allah ta fi muhimmanci da abin dogaro
Wannan wata suna ce ta Yesu, Ɗan Allah
"Duk mai gaskata da Yesu ya sani da tabbaci cewa Yesu Ɗan Allah ne"
"ya ce da Allah maƙaryaci"
"domin bai gaskata cewa Allah ya faɗi gaskiya game da Ɗansa ba"
"Ga abinda Allah ke faɗi"
A nan "rai" na madaɗin yancin rayuwa har abada ta wurin Alheri da ƙaunar Allah. Dubi yadda ku ka fasara wannan a [1:1-2]
"wannan rai ta wurin Ɗansa ne" ko kuma "Zamu rayu har abada idan muna manne da Ɗansa" ko kuma "Zamu rayu har abada indan mun haɗa kai da Ɗansa"
An yi maganar samun dangantaka na kusa da Ɗan kamar shi ne samun Ɗan. AT: "Shi wanda ke gaskata da Ɗan Allah na da rai. Shi wanda bai gaskata da Ɗan ba ba shi da rai na har abada"
"wannan wasiƙa"
A nan "suna" na nufin Ɗan Allah. AT: "ku da kuka gaskata da Ɗan Allah"
AT: "Muna da gabagaɗi a gaban Allah don mun san cewa"
"idan mun roƙi abubuwan da Allah ke so"
"mun san cewa zamu samu abinda muka roƙa daga Allah"
"ɗan'uwansa maibi"
Wannan na nufin mutuwa na har abada, wato rayuwa na har abada da ba ayi a gaban Allah.
Wannan jumlar "mugun nan" na nufin Shaiɗan, ibilis.
kasancewa a hannun mutum na nufin bishewarsa ko kuma mulkinsa. AT: "mugun ne ke bi da duniya"
A nan "duniya" wata hanya ce da marubutan Littafi ke nufin mazauna cikin duniya da ke tawaye da Allah da kuma tsarin duniya da ke lalace saboda ikon zunibi.
"ya iza mu mu fahimci gaskiyar"
kansancewa a "cikin" mutum na nufin samun dangantaka ta kusa da shi, wato a haɗe da shi ko kuma ku zama nashi. Wannan jumlar "shi ne gaskiya" na nufin Allah mai gaskiya, sa'annan jumlar nan "a cikin Ɗansa Yesu Almasihu" na bayyana yadda muke a cikinsa mai gaskiya. AT: "muna haɗe da shi mai gaskiya ta wurin haɗa kai da Ɗansa Yesu Almasihu"
"mai gaskiya" ko "Allah na asali"
"shi ne" na nufin Yesu Almasihu
Ana ce da shi "rai na har abada" domin shi ne ke ba mu rai na har abada. AT: "da kuma wadda ke ba da rai na har abada"
Yahaya tsohon mutum ne kuma shi ne shugabansu. Yayi amfani ne da wannan furci domin ya nuna yadda yake ƙaunarsu . AT: "ƙaunatattun 'ya'yana a cikin Almasihu" ko kuma "ku da kuke ƙaunatattu a gare ni kamar 'ya'yan kaina"
"ku yi nesa da gumakai" ko "kada ku bauta wa gumaka"
1Daga dattijon zuwa ga uwar gida zababbiya da yayanta, wadanda nake kauna da gaskiya, ba ni kadai ba, amma da dukan wadanda sun san gaskiya - 2domin gaskiya da take cikinmu za ta kuma kasance tare da mu har abada. 3Alheri da jinkai da salama za su kasance tare da mu, daga Allah Uba da kuma daga Yesu Almasihu Dan Uba, a cikin gaskiya da kauna.4Na yi murna sosai sa'anda na sami wadansu yayanki suna tafiya cikin gaskiya, kamar yadda muka karbi wannan umarni daga Uba. 5Yanzu ina rokon ki, uwar gida, ba kamar ina rubuta maki sabon umarni ba, amma wannan da muka samu tun da can, cewa mu kaunaci junanmu. 6Wannan kuma itace kauna, cewa mu yi tafiya bisa ga umarnin sa. Wannan shine umarnin, daidai kamar yadda kuka ji da fari, da cewa ku yi tafiya a cikinsa.7Gama masu yaudara sun fito a duniya, wadanda ba su yarda cewa Yesu ya zo cikin jiki ba. Wannan ne mayaudari da kuma magabcin Almasihu. 8Ku dubi kanku, domin kada ku rasa abubuwan da mu duka muka yi aiki a kansu, amma domin ku karba dukan sakamon ku.9Duk wanda ya ci gaba da tafiya ba cikin koyarwa Almasihu ba, ba shi da Allah. Wanda ya zauna cikin koyarwar kwa yana tare da Uban da kuma Dan. 10Duk wanda ya zo wurinku, ba tare da wannan koyarwar ba, kar ku karbe shi cikin gidanku, kada ma ku gaishe shi. 11Domin duk wanda ya gaishe shi ya yi tarayya da shi kenan cikin miyagun ayyukan sa.12Ina da abubuwa dayawa da nake so in rubuta maki amma al'kalami tawada da takarda baza su iya daukar su duka ba. Amma duk da haka ina begen zuwa gare ki domin mu yi magana fuska da fuska, domin farin cikn mu ya zama cikakke. 13Yayan yar'uwarki zababbiya suna gaishe ki.
Bisa ga al'ada, Yahaya manzo ne marubucin wannan wasiƙar. Kodashike yana iya yiwuwa ya rubuta zuwa ga wata mace ce, amma domin ya rubuta cewa su "ƙaunaci juna", mai yiwuwa wannan zuwa ga wata ikilisiya ce.
Haka ake fara rubuta wasiƙa. Ana iya bayyana sunan marubucin. AT: "Ni, dattijo Yahaya, ina rubuta wannan wasiƙar zuwa ga uwar gida zaɓaɓɓiya da 'ya'yanta"
Wannan na nufin Yahaya ne, manzo da kuma almajirin Yesu. Ya kira kansa "dattijo" domin tsufansa ne ko kuma domin shi shugaba ne na ikilisiya.
Mai yiwuwa wannan na nufin taron jama'a da kuma masubi da suke a wurin.
"ku, mutanen da nake ƙauna da gaske"
waɗanda suka san gaskiya game da Allah da kuma Yesu
Waɗannan muhimman sunaye ne da ke bayyana dangantaka tsakanin Allah da kuma Yesu.
Kalmar nan "gaskiya" ta na bayyana "ƙauna." Mai yiwuwa ana nufin "cikin kauna ta gaskiya."
"kamar yadda Allah Uba ya umurce mu"
"ba kamar ina umurtar ki yin wani sobon abu ba ne"
A nan "farko" na nufin "tun lokacin da muka gaskata." AT: "amma ina rubuta maku abin da Almasihu ya umurce mu tun lokacin farko da muka gaskata."
Ana iya fasarar wannan kamar sabon magana. AT: "afarko. Ya umurce mu cewa mu ƙaunaci junanmu"
Anyi magana game da gudanar da rayuwar mu bisa ga umurnin Allah kamar muna tafiya cikinsu ne. Kalmar nan "shi" na nufin ƙauna. "Kuma ya umurce ku, tun farko da kuka gaskanta, ku yi ƙaunar juna"
Yahaya ya gargaɗe su game da masu yaudara, ya tunashe su domin su cigaba cikin koyaswar Almasihu, kuma ya gargaɗesu da su guje wa waɗanda ba su tsaya cikin koyaswa na Almasihu ba.
"Gama malaman ƙarya dayawa sun bar cikin taron" ko "Gama masu yaudara dayawa suna cikin duniya"
"malamen ƙarya dayawa" ko "masu ruɗi dayawa"
Zuwa cikin jiki kalmomi ne da aka mora domin nuna ainihin mutum. AT: "Yesu Almasihu ya zo ne a matsayin ainihin ɗan Adam"
"Su ne waɗanda suka yaudari wasu suka kuma ki goyon bayan Almasihu kansa"
"Yi la'akari" ko "Maida hankali"
"rasa lada mai zuwa a sama"
"cikakken sakamako a sama"
Wannan na nufin mutumin da yake nuna sani game da Allah da kuma gaskiya fiye da kowa. AT: "Duk wanda ya ce yana da sani mafi yawa game da Allah" ko "Duk wanda yayi rashin biyayya ga gaskiya"
" shi ba na Allah bane"
"Wanda yake bin koyaswar Almasihu yana tare da Uban da kuma Ɗan"
Waɗannan muhimman sunaye ne da ke bayyana dangantaka tsakanin Allah da kuma Yesu.
A nan wannan na nufin marabtarsa da kuma martaba shi domin gina dangantaka da shi.
"ya goyi bayan shi cikin miyagun ayyukan sa" ko "ya taimake shi cikin miyagun ayyukan sa"
Yahaya bai so ya rubuta sauran waɗannan abubuwan ba, amma zai so ya zo ya faɗa masu. Bai faɗa masu cewa zai rubuta masu da wani abu dabam da alƙalami, tawada da kuma takarda ba.
"Fuska da fuska" a nan na nufin yin magana a gabansu. AT: "yi magana a gabanku" ko "yi magana da ku"
A nan, Yahaya na magana game da ikilisiyar da ke tare da shi kamar 'yar'uwar wanda take karanta watsiƙar shi, da kuma masubi da ke tare da ita kamar 'ya'yan ta ne. Wannan na nanata cewa dukan masubi 'ya'yan iyali ɗaya ne cikin ruhu .
1Daga dattijon zuwa ga Gayus, wanda nake kauna da gaske. 2Ya kaunatace na, ina addu'a domin ka samu albarka cikin kowanne al'amari, da kuma koshin lafiya, kamar yadda ruhun ka yake lafiya. 3Na yi farin ciki kwarai sa'adda wadansu 'yan'uwa suka zo suka ba da shaida a kan bangaskiyar ka, kamar yadda ka ke bin gaskiya. 4Ba abin da ya fi faranta mani rai kamar in ji yayana suna tafiya cikin gaskiya.5Ya kaunatace na, kana aiki da aminci zuwa ga 'yan'uwa da baki, 6wadanda suka shaida kaunar ka a gaban ikilisiya. Zai yi kyau ka yi masu taimako da kyakkyawar salama, ta hanyar da ta dace da masu ibada, 7domin sabili da sunan nan ne suka fito, ba su kuma karbar kome a hannun al'ummai. 8Don haka ya kamata mu karbi irin wadannan mutane, domin mu zama abokan aiki tare da su a kan gaskiya.9Na rubuta wasika zuwa ga ikilisiya, amma Diyotariffis, wanda ya fi kowa son girma a cikinsu, bai karbe mu ba. 10Saboda haka, idan na zo, zan tuna masa da irin ayukkan sa, da kuma yadda yake babbata sunayen mu a wurin jama'a da miyagun kalmomi. Wannan ma bai ishe shi ba, har ma yana kin karbar 'yan'uwa. Ya kuma hana wadanda suke son su yin hakan, harma ya kan kore su daga ikilisiya.11Ya kaunatace na, kada ka yi koyi da mugun abu, sai dai abu mai kyau. Dukan wanda yake yin abu mai kyau na Allah ne; mai aikata mugunta kuma bai san Allah ba. 12Dimitiriyas yana da kyakkyawar shaida a gun kowa har a wurin gaskiyar da kanta. Mu ma mun shaida shi, ka kuma san shaidar mu gaskiya ce.13Ina da abubuwa dayawa da zan rubuta maka, amma ban so in rubuta maka su da alkalami da tawada ba. 14Ina sa zuciya mu sadu ba da dadewa ba, sa'annan mu yi magana ido da ido. 15Bari salama ta kasance tare da kai. Abokanmu suna gaishe ka, kuma ka isadda sakon gaisuwar mu ga sauran abokai da sunayen su.
Wannan wasiƙa ce daga Yahaya zuwa ga Gayus. Dukan inda aka mori "ka" ana nufin Gayus ne.
Wannan ya na nufin Yahaya, manzo da kuma almajirin Yesu. Watakila ya kira kansa "dattijo" saboda shekarunsa ko kuma domin shi shugaba ne a ikillisiya. Ana iya sa sunan marubucin a bayyane. "Ni, Yahaya dattijo, ina rubutu."
Wannan ɗan'uwa mai bi ne wadda Yahaya ya rubuto masa wannan wasiƙan.
"wadda na ke ƙauna ta gaskiya"
"ku kasance da nasara cikin kowanne al'amari, ka kuma kasance da ƙoshin lafiya"
"kamar yadda kake lafiya a ruha"
"yan'uwa masubi sun zo." Da alama waɗannan mutanen maza ne duka.
Tafiya a hanya, na nufin yadda mutum yake rayuwarsa. AT: "Ku na rayuwar ku a bisa gaskiyar Allah"
Yahaya yana magana game da wadda ya koyar da su game da bangaskiya cikin Yesu kamar su 'ya'yansa ne. Wannan ya na nanata ƙaunarsa garesu da kulawa da yake da shi dominsu. Yana kuma iya zama cewa shi ne ya kai su ga sanin Ubangiji. AT: " 'ya'yana na ruhu"
Yahaya ya rubuta wannan wasiƙa ne domin ya yaba wa Gayus da yadda ya riƙe mallamai na Littafi masu tafiye tafiye; sai ya yi magana game da mutane biyu , ɗaya mai halin kirki da kuma ɗaya mai hali marar kirki.
A nan ana amfani da kalmar ƙauna domin yan'uwa masubi.
"kana aiki da aminci ga Allah" ko kuma "ka na biyayya da Allah"
"taimaki 'yan'uwa masubi da waɗanda ba ku sansu ba"
"baƙi waɗanda suka faɗa wa masubi a cikin ikilisiya game da yadda ka ƙaunace su"
Yahaya ya na gode wa Gayus domin taimako da ya saba yi wa waɗannan masubi.
A nan "sunan" na nufin Yesu. AT: "saboda sun fita domin su gayawa mutane game da Yesu"
babu karɓar kyauta ko kuma taimako
A nan "Al'umman" ba yana nufin mutane da ba Yahudawa kaɗai ba. Ya na nufin mutane da ba su dogara da Yesu ba.
"domin mu hada kai da su a sanar da gaskiyar Allah ga mutane"
Wannan ya na nufin Gayus da kungiyar masubi waɗanda sukan haɗu domin su bauta wa Allah.
Shi ɗan taron ne.
"wanda ya fi son kasancewa da muhimminci a tsakaninsu" ko kuma "wanda ya na son yi kamar shi ne shugabansu"
"da kuma yadda ya ke faɗin mugayen abubuwa game da mu da ba gaskiya ba"
"bai karɓi 'yan'uwa masubi ba"
"hana waɗanda suke so su karɓi masubi"
"ya tilasa masu su bar taron"
"kada ka yi koyi da mugayen abubuwa da mutane suke yi"
AT: "Amma ka yi koyi da abubuwa masu kyau da mutane su ke yi"
"ya zama na Allah ne"
"ba na Allah ba ne" ko kuma "bai gaskata da Allah ba"
AT: "Dukan waɗanda sun san Dimitiriyas suna shaida shi" ko kuma "Kowane mai bi da ya san Dimitiriyas ya na magana mai kyau game da shi"
Mai yiwuwa wannan mutumin ne Yahaya ya ke so Gayus tare da taron masubi su marabce shi a lokacin da zai ziyarce su.
"gaskiya da kanta tana shaidar shi." A nan an kwatanta "gaskiya" kamar mutum ne da ke magana. AT: "Dukan wadda ya san gaskiyan ya san cewa shi mutumin kirki ne"
Wannan ya na tabbatar da abin da Yahaya yake nufi a nan. AT: "Mun kuma yi magana da kyau game da Dimitiriyas"
Yahaya ba ya so ya rubuta waɗannan abubuwa ko kaɗan. Ba wai ya na ce wa zai rubuta masu wasiƙa da wani abu dabam da alƙalami da kuma tawada ba.
"ido da ido" na nufin "da kansa." AT: "da kansa"
"Bari Allah ya ba ku salama"
"Abokai a nan suna gaishe ka"
"ka isadda sakon gaisuwa na ga masubi a can"
1Yahuza, bawan Yesu Almasihu kuma dan'uwan Yakubu, zuwa ga kirayayyu, kaunatattu a cikin Allah Uba, kebabbu domin Yesu Kristi: 2bari jinkai da salama da kauna su ribabanya a gare ku.3Kaunatattu, ina iyakar kokari in rubuta maku game da ceton mu duka, ya zama dole in gargade ku sosai game da bangaskiya wadda aka mika wa masu bi sau daya tak ba kari. 4Don wasu mutane sun sadado sun shigo da sanda a asirce wadanda an rubuta game da hukuncin su tun da dadewa-mutane marasa imani, wanda suka canza alherin Allah zuwa lalata, kuma sun karyata makadaicin Shugaba da Ubangijinmu, Yesu Almasihu.5Ina so in tunashe ku-ko da shike kun rigaya kun san abin, da cewa Allah ya ceci wasu mutane daga kasar masar, amma daga baya ya hallaka wadanda basu ba da gaskiya ba. 6Kuma mala'iku wadanda ba su rike matsayin ikon su ba, amma suka bar wurin zaman su na ainihi-Allah ya tsare su a sarka na har'abada a cikin bakin duhu domin babban ranar shari'a.7Suna nan kamar Saduma da Gwamrata da kuma biranen da ke kewaye da su, wadanda suka ba da kansu ga fasikanci suna bin sha'awoyi wanda ba na dabi'a ba. Aka mai da su abin misalin wadanda suka sha wuta mara matuka. 8Haka kuma, wadannan masu mafarkan suna lalatar da jikinsu. Suna raina masu mulki, kuma suna fadar miyagun abubuwa a kan masu daukaka.9Amma ko Mika'ilu babban mala'ika, a lokacin da yake jayyaya da muhawara da shaidan a kan gawar Musa, bai kuskura ya fadi wata kalmar hukunci a kansa ba. Maimakon haka ya ce, "Bari Ubangiji ya tsauta maka!" 10Amma waddannan mutane suna kawo batanci game da dukan abin da ba su gane ba. Wadannan mutane masu halin dabbobi ne, suna kwa jawo wa kansu hallaka kenan. 11Kaiton su! Domin sun bi hanyar Kayinu, kuma sun tsunduma cikin kuskuren Bal'amu domin samun riba. Suka hallaka cikin husuma irin ta Kora.12Wadannan hatsari ne a boye cikin bukukuwan ku na kauna. Suna shagali ba kunya ba tsoro, suna ciyar da kansu kadai. Su holokon hadari ne marar ruwa, wanda iska ke korar sa. Su itatuwa ne shirim ba yaya, mattatu ribi biyu, tumbukakku tun daga saiwa. 13Su rakuman teku ne masu hauka, suna fahariya cikin kumfar kunyar su. Su kamar taurari ne masu tartsatsi. Wadanda aka tanada wa duhu baki kirin na har abada.14Ahnuhu, mutum na bakwai daga Adamu, ya yi anabci game da su cewa, "Duba, Ubangiji zai zo da tsarkakan sa dubun dubbai. 15Domin ya zartar da hukunci a kan dukan kowa, ya kuma cakune dukan marasa da'a a cikin dukan ayyukan su na rashin da'a wanda suka aikata a hanyar da bata cancanta ba, da kuma kalmomi masu kaifi da masu zunubi suka fada game da shi." 16Wadannan masu cecekuce ne, masu gunaguni, wadanda ke bin sha'awar su ta mugunta, masu tinkaho da fahariya, masu bambadanci domin ribar kansu.17Amma ku, kaunatattu, ku tuna da kalmomin da manzannin Yesu Almasihunmu suka gaya maku tun da. 18Sun ce maku, "A cikin kwanaki na karshe, za a samu masu ba'a, wadanda ke bin sha'awoyin su na rashin ibada," 19Wadannan mutane masu haddasa tsatsaguwa ne, kuma su yan duniya ne, ba su kuma da Ruhu.20Amma ku, kaunatattu, ku gina kanku a cikin mafificiyar bangaskiyar ku mai daraja, kuma kuna addu'a a cikin Ruhu Mai Tsarki. 21Ku rike kanku a cikin kaunar Allah, kuna kuma jiran jinkan Ubangijinmu Yesu Almasihu wanda ke kawo rai na har abada.22Ku nuna jinkai ga masu shakku. Ceci wadansu ta wurin fizge su daga wuta. 23Ga wadansu kuma ku nuna jinkai da rawar jiki, kuyi kyamar koda tufafin jikinsu ma.24Yanzu, zuwa ga wanda yake da iko ya hana ku tuntube, ya kuma sa ku tsaya a gaban madaukakiyar kasancewarsa, marasa abin zargi da kuma murna mai yawa, 25zuwa ga Allah makadaici mai ceton mu ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu, daukaka, da girma, da mulki, da iko su kasance, kamin dukan lokuta, yanzu, da har abada. Amin.
Yahuza ya gabatar da kansa a matsayin marubucin wannan wasiƙar, ya kuma gaishe da masu karanta ta. Mai yiwuwa shi ɗan'uwan Yesu ne. Akwai kuma masu suna Yahuza guda biyu a Sabon Alkawali.
Yahuza ɗan'uwan Yakubu ne. AT: "Ni ne Yahuza, bawan"
Yakubu da Yahuza 'yan'uwan Yesu ne.
"bari jinkai, salama, da ƙauna su yawaita sosai a gare ku. "Ana maganan waɗannan abubuwan kamar suna ƙaruwa ne ta wurin lamba ko girma. AT: "Bari Allah ya cigaba da yi maku jinkai domin ku yi rayuwar salama, ku kuma kara yin ƙaunar junanku
Yahuza ya gaya wa masubi dalilinsa na rubuta wannan wasiƙar.
"ceton mu da naku"
"Na ji buƙata kwarai in rubuta " ko "Na ji ya kamata in yi rubutu da hanzari"
"domin in karfafa ku, ku tsaya wa koyaswar gaskiya"
"a karshe gaba ɗaya"
"Domin wasu mutane da basu son su jawo hankula a gare su sun shigo cikin masubi a asirce"
AT: "mutane waɗanda Allah ya zaɓa ya hukunta"
Ana magana game da alherin Allah kamar abu ne da za'a iya canza ta zuwa mummunan abu. AT: "wanɗanda sun koyas da cewa alherin Allah ya ba da izini a cigaba da yin rayuwar zunubin lalata"
Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka AT:1) sun koyas da cewa shi ba Allah bane ko 2) waɗannan mutane basu biyayya da Yesu Almasihu.
"Ina son ku tuna"
"ko da shike kun rigaya kun san wannan abin gaba ɗaya"
"Tun da daɗewa Ubangiji ya ceci Isra'ila daga Masar"
Wasu rubutun na nuna "Yesu ne."
"rikon amana da Allah ya basu"
"bar ainihin wurin da aka zaɓa masu"
"Allah ya saka waɗannan mala'ikun a cikin baƙin kurkuku inda baza su iya gudu ba"
A nan "duhu" kalma ce da take nuna wurin da matattu suke ko jahannama. AT: "cikin duhu mai tsanani a jahannama"
rana ta karshe da Allah zai yanke shari'a wa kowa
A nan "biranai" na nufin mutanen da suka yi rayuwa a cikin ta.
Sakamakon zunubin zina da Saduma da Gwamrata su ka yi iri ɗaya ne da mummunan tawaye da mala'ikun nan suka yi.
Hallakar mutanen Saduma da Gwamrata ya zama misali ne ga duk waɗanda suka ƙi Allah.
mutane da suka yi rashin biyyaya ga Allah, mai yiwuwa domin sun ce wahayi ne da suka gani ya basu ikon yin haka
Wannan magana ta bayyana cewa zunubin su ne ya sa jikunansu, wato ayukansu, suka zama mara ƙarɓuwa kamar yadda datti da ke ă cikin ruwa na hana shan ta.
"faɗin zagi"
Wannan na nufin ruhohi, kamar mala'iku.
"bai faɗi wani abu" ko "ba ya so ya faɗi wani abu"
"mummunar kalmar hukunci" ko "mummunar hukunci"
mutane marasa tsoron Allah
"faɗi mummunar abu marar gaskiya game da"
"kowane abu da ba su san ma'anar ba." AT: "duk abubuwa masu kyau da basu gane ba" ko "abubuwa masu ɗaukaka da basu gane ba" (1:8)
"bi hanyar" kalma ce da ke nufi "yi rayuwa iri ɗaya da." AT: "yi rayuwa iri ɗaya da wanda Kayinu ya yi"
Kalman nan "Waɗannan" na nufin "marasa tsoron Allah" na [1:4]
Waɗannan manyan duwatsu ne da ake samu a cikin ruwa na teku. Suna da hatsari sosai domin ma'aikatan jirgin ruwa basu iya gannin su. Jiragen ruwa na iya rushewa nan take idan sun bugi irin waɗanan duwatsun.
AT: 1) waɗannan mutane suna nan kamar itace ne da mutane na begen girbar 'ya'yan ta, amma bata da ko guda, ko 2) itacen da bata taba haifar 'ya'ya ba.
Wannan kalma ce ta rayuwa da ta gamshi Allah, tana kuma taimakon mutane.
Itace da wani ya tumbuke ta, kalma ce da ake amfani wa mutuwa.
Kamar itatuwa da aka tumbuke tushensu daga kasa, haka ne an raba mutanen da basu da tsoron Allah daga Allah wanda shine tushen rayuwa.
Kamar yadda iska mai ƙarfi ke hura rakuman ruwa, hakannanne mutanen da basu da tsoron Allah zasu yi tafiya a hanyoyi dabam-dabam.
Kamar yadda iska ke saka rakuman ruwa hauka domin ya kaɗa kumfa mai datti, haka mutanen nan, ta wurin koyaswan karya da kuma ayukansu, zasu kunyata. AT: "kamar yadda rakuman ruwa ke kawo kumfa da datti, waɗannan mutanen na kazamtar da sauran jama'a da kunyar su.
Waɗanda suka yi karatu game da taurari a zamanin da sun kula da cewa abin da muke kira taurari masu kewaye rana basu tafiya kamar yadda tauraro yake yi. AT: "Suna kama da tauraro da ke tafiya"
A nan "duhu" kalma ce da ke wakilcin inda mattatu suke ko jahannama. A nan "matsanancin duhu" kalma ce da take nufin "duhu baƙi ƙirin." Kalmomin nan " an tanadasu" ana iya bayyana su cikin aiki. AT: "kuma Allah zai saka su cikin baƙin duhu na harabada a jahannama"
Idan aka kidaya Adamu a mastayin mutum na farko, Anuhu ne zai zama na bakwan. Idan ɗan Adamu ne kuma na farkon, Anuhu ne zai zama na shida.
"Ji" ko "Kasa kunne ga abu mai muhinminci da zan fada"
"ya yanke hukunci a kan" ko "ya hukunta"
Mutanen da basu so su yi biyyaya suna kuma kushe mulki na tsoron Allah. "Masu gunaguni" suna magana a asirce, masu "ƙunƙuni" kuma suna magana a fili.
Mutane da suke yabon kansu domin sauran jama'a suji.
"suna yabon karya ga sauran jama'a"
Ana magana game da waɗannan mutane kamar sha'awar su sarakuna ne da suke mulki a kansu. AT: "ba za su taba iya daina rashin biyayya ga Allah ba ta wurin mugayen halayen da suke so su yi"
"Waɗannan ne masu ba'a" ko "Masu ba'an nan ne"
suna tunani kamar yadda marasa tsoron Allah suke yi, suna daraja abubuwan da marasa bi suke daraja wa
Ana magana game da Ruhu mai Tsarki kamar abu ne da mutane ke iya mallaka. AT: "Ruhun baya tare da su"
"kada ku zama kamar su, ƙaunatattuna. A maimakon haka"
Ana magana da su saka bege ga Ubangiji su kuma yi biyayya da shi kamar hanya ce da ake shirin gini.
A nan ana maganar cigaba da iya karɓar ƙaunar Allah kamar wanda yake ajiye kansa ne a wani wuri.
"marmarin saka zuciya domin ganin"
A nan "jinƙai" na tsayawa á madadin Yesu Almasihu ne da kansa, wanda zai nuna jinƙansa wa masubi ta wurin sa su yi rayuwa har abada tare da shi.
"waɗanda har yanzu basu yarda da cewa Yesu Allah bane"
Bayanin nan na nuna yadda ake jawo mutane daga wuta kafin su fara ƙonewa. AT: "ana yi masu duk abin da yakamata domin a tserar da su daga mutuwa da rashin sannin Almasihu. Wannan na kama da ana jawosu ne daga cikin wuta"
"Ku nuna jinƙai ga jama'a, amma ku yi tsoron zunubi kamar yadda suka yi"
Yahuza yana zuguiguita al'amarin don ya gargaɗi masu karatun cewa zasu iya zama kamar waɗannan masu zunubi. AT: "Ku yi da su kamar kuma zaku iya zama masu laifin zunubi tawurin taɓa tufafinsu"
Ɗaukakarsa haske ne sosai da ke nuna girmansa. AT: "ă kuma barku ku ji daɗi ku kuma ɗaukaka ikonsa"
A nan ana magana game da zunubi kamar datti ne ko illa da ke jikin mutum. AT: "inda za a kasance babu zunubi"
"zuwa ga Allah makadaici, wanda ya cece mu tawurin abin da Yesu Almasihu yayi." Wannan na nanata cewa Allah Uba, da Ɗan, mai ceto ne.
Ɗaukaka, da dukan shugabanci, da cikakken mulki akan komai na Allah ne a da, da yanzu da har abada.
1Wannan shine wahayin Yesu Almasihu da Allah ya bashi ya nuna wa bayinsa abinda zai faru ba da dadewa ba. Ya bayyana wannan ta wurin aiko da mala'ikansa ga bawansa Yahaya. 2Yahaya yayi shaida akan abinda ya gani game da maganar Allah da kuma shaidar da aka bayar game da Yesu Almasihu. 3Mai albarka ne wanda ke karanta littafin nan da murya mai karfi, da kuma wadanda ke sauraron kalmomin wannan annabci kuma suke biyayya da abinda aka rubuta a ciki, domin kuwa lokaci ya kusato.4Ni Yahaya, zuwa ga ikilisiyoyi bakwai na kasar Asiya: alheri zuwa gare ku da salama daga wanda ke yanzu, wanda ya kuma kasance a da, shi ne kuma mai zuwa nan gaba, kuma daga ruhohin nan bakwai da ke gaban kursiyinsa, 5kuma daga Yesu Almasihu, wanda ke amintaccen mashaidi, dan fari na tashi daga cikin matattu, kuma mai mulkin sarakunan duniya. Ga wanda ya ke kaunar mu ya kuma kwance mu daga daurin zunubanmu ta wurin jininsa, 6ya maishe mu masu mulki, firistoci na Allahnsa da Ubansa - daukaka da iko su tabbata gare shi har abada abadin, Amin.7Duba yana zuwa tare da gizagizai, kowane ido zai gan shi, har ma da wadanda suka soke shi. Haka kuma dukkan kabilun duniya za su yi makoki saboda da shi. I, Amin. 8"Nine na farko da na karshe", in ji Ubangiji Allah, "Wanda yake shine a yanzu, shine wanda ya kasance a da, kuma shi ne mai zuwa nan gaba, Mai iko duka."9Ni, Yahaya- dan'uwan ku da wanda ke tarayya daku cikin shan wahala, da mulki da tsawon jimrewa wadanda ke cikin Yesu - ina tsibirin da ake kira Batmusa saboda maganar Allah da kuma shaida game da Yesu. 10Ina cikin Ruhu a ranar Ubangiji. Sai naji wata murya mai karfi a baya na kamar ta kaho. 11Ta ce, "Rubuta abinda ka gani a cikin littafi, ka kuma aika wa ikilisiyoyin nan bakwai - ga Afisus, ga Simirna, ga Birgamas, ga Tayatira, ga Sardisu, ga Filadalfiya, da kuma ga Laudikiya."12Na juya don in ga wanda muryarsa ke magana da ni, da na juya sai na ga fitilu bakwai akan madorin su 13A tsakiyar fitilun akwai wani mai kama da dan mutum, yana sanye da doguwar tufa har tafin sawunsa, da damara ta zinariya kewaye a kirjinsa.14Kansa da gashinsa fari fat kamar auduga - kamar dusar kankara, kuma idanun sa kamar harshen wuta. 15Kafaffunsa kamar gogaggiyar tagulla, kamar tagullar da aka tace da wutar makera, muryar sa kuma kamar kugin ambaliyar ruwan teku ne. 16A hannunsa na dama yana rike da taurari bakwai, daga bakinsa kuma kakkaifan takobi mai kaifi biyu ke fitowa. Fuskarsa tana haskakawa kamar sa'adda rana ke haskakawa kwarai.17Lokacin da na gan shi, na fadi kamar mataccen mutum a kafaffunsa. Ya dora hannunsa na dama a kaina ya ce, "Kada ka ji tsoro. Nine na farko da na karshe, 18da kuma wanda ke raye. Na mutu, amma duba ina raye har abada! Kuma ina da mabudin mutuwa da na hades.19Domin haka ka rubuta abinda ka gani, abin da ke yanzu, da abin da zai faru bayan wanan. 20Akan boyayyar ma'ana game da taurari bakwai da ka gani a hannun dama na, da madorin fitilu bakwai na zinariya: Taurarin nan bakwai mala'iku ne na ikilisiyoyi bakwai, kuma madorin fitilun nan bakwai ikilisiyoyi ne bakwai.
Wannan ne gabatarwa na littafin Wahayin Yahaya. Ya bayyana cewa wahayi ne daga Yesu Almasihu yana kuma ba da albarka ga duk waɗanda suka karanta.
Wannan na nufin mutanen da sun gaskata da Almasihu.
"waɗannan ababai zasu faru ba da daɗewa ba"
"Ya sanar da wannan"
Yahaya ne ya rubuto wannan littafi yana kuma nufin kansa ne. AT: "ga ni, Yahaya, bawansa"
"sakon da Allah ya faɗa"
Wannan na iya nufin 1) shaidar da Yahaya ya bayar game da Yesu Almasihu. AT: "ya kuma bayar da shaida game da Yesu Almasihu" ko 2) "shaida da Yesu Almasihu ya faɗa game da kansa"
Yana nufin ga duk wanda ke karanta littafin da murya mai ƙarfi. AT: "duk wanda ke karanta littafin da karfi"
AT: "biyayya da abin da Yahaya ya rubuta a ciki" ko "biyayya da abinda suka karanta a ciki"
"abubuwan da zasu faru, zasu faru ba da daɗewa ba"
Wannan fata ne ko kuma albarka. Yahaya ya yi magana game da waɗannan abubuwa kamar su ne Allah na iya bayarwa, kodashike ya na bege ne Allah ya yi aiki wa mutanen sa ta wurin waɗannan hanyoyin. AT: "1:4-6"
"daga Allah, wanda ke"
Kasancewan nan gaba na nufin zuwa ne.
Lamba ta bakwai ɗin alama ce dake nuna kammalawar aikin gabaɗaya. "ruhohin nan bakawai" na nufin Ruhun Allah ko ruhohi bakwai wanda ke bauta wa Allah.
"mutum na fari da a ka tayar daga mattatu"
Daga cikin dukkan waɗanda suka mutu.
"kuma bamu yanci"
"an shirya mu keɓaɓɓu an kuma fara mulki akan mu kuma ya mayad da mu firistoci"
Wannan na nufin mutum ɗaya ne. AT: "Allah, Ubansa"
Wannan suna ne mai muhinminci na Allah da yake bayanin dangartaka tsakanin Allah da kuma Yesu.
Wannan fata ne ko kuma addu'a. AT: 1) "Bari mutane su daraja ɗaukakarsa da kuma ikon sa" 2) "Bari ya samu ɗaukaka da kuma iko." [ 1:4-6].
Mai yiwuwa wannan na nufin ikonsa a matsayin sarki.
Dashike mutane suna gani da idanuwan su ne, kalman nan "ido" na nufin mutane ne. AT: "kowane mutum" ko "kowa da kowa"
"har da waɗanda suka soke shi zasu gan shi"
An soke hannuwar Yesu da kuma kaffafunsa a lokacin da aka kafa masa ƙusa akan giciye. Wannan na nufin mutanen da suka kashe shi ne. AT: "kashe shi"
yi rami cikin
Wannan shine farko da kuma karshen rubutun baƙaƙe na Girka. AT: 1) "wanda shi ne ya fara komai, ya kuma kai komai ga ƙarshe" ko 2) "wanda tun farko yana raye zai kuma rayu har abada." Idan akwai rashin fahimta ga masu karatu, zaku iya yin tunanin amfani da farko da kuma karshen rubutun baƙaƙen ku. AT: "na farko da kuma karshe"
Wata harshe na iya saka "Ubangiji Allah ya ce" a farko ko kuma karshen dukkan magana.
Waɗannan na nufin masubi na cikin ikilisiyu bakwai.
... AT: [ 1:9]
"saboda na gaya wa wasu maganar Allah"
"shaidar da Allah ya bayar game da Yesu." Fassara kamar [1:2]
Yahaya ya yi magana akan bishewar Ruhun Allah kamar yana cikin Ruhu ne. AT: "Na samu izawa ta wurin Ruhu" ko "Ruhu ya iza ni"
ranar sujadar masubi cikin Almasihu
Muryan na da ƙarfi kamar na ƙaho.
Wannan na nufin kayan kiɗe-kiɗe na waƙa ko domin tara mutane tare a wuri ɗaya domin sanarwai ko taro.
Waɗannan sunaye ne na biranai a yammacin Asiya da a yau ana kira Turkiya.
Yahaya ya fara bayyana abin da ya gani a wahayinsa.
Wannan na nufin wanda ke magana ne. AT: "wanda"
Wanda ke da kamanin mutum.
mayafi da ake sakawa kewaye da ƙirji. Mai yiwuwa ta na da zare mai zinariya cikinta.
Auduga da dusar ƙanƙara misali ne na abubuwan da farare ne sosai. Maimaitawar "fari fat kamar" na nanatawa cewa farare ne sosai.
Wannan gashin rago ne ko akuya. An san da ita fari fat ce sosai.
Ana yi bayanin idanunsa na cike da haske kamar harshen wuta. AT: "idanunsa sun yi haske kamar harshen wuta"
Ana goge tagulla domin ta yi ƙyalli ta kuma nuna haske. AT: "Kafaffunsa sun yi haske sosai kamar gogaggiyar tagulla"
Ana iya fara tace tagullar sa'annan a goge ta. AT: "kamar tagulla da aka tsarkake ta a cikin wutar makera mai zafi aka kuma goge ta"
gongoni mai ƙarfi domin rike wuta mai zafi sosai. Mutane suna saka karfe cikin ta, kuma wuta mai zafin zai kone kowace abu mara kyau da ke a cikin karfen.
Wannan kara ce sosai, kamar karar babban ruwa da ke wucewa na mafaɗar ruwa, ko na rukunin ruwa mai ƙarfi a teku.
Bakin takobi na fitowa daga bakinsa. Takobin da kanta ba ta motsi.
Wannan na nufin takobi mai baki biyu wanda aka wasa duka gefensa domin ya ci a kowane gefe.
Yahaya ya kwanta, ya fuskanci ƙasa. Mai yiwuwa ya firgita sosai kuma ya nuna bangirma wa Yesu.
"Ya taɓa ni da hannunsa na dama"
Wannan na nufin sifar Yesu na har abada. (Dubi: )
Anyi magana game da samun iko akan abubuwa kamar samun mabuɗin sa ne. Nufin bayanin nan shine, yana iya ba da rai ga waɗanda suka mutu ya kuma fitad da su daga Hades. AT: "Ina da iko akan mutuwa da kuma Hades" ko "Ina da iko in ba da rai ga mutanen da suka mutu in kuma fitad da su daga Hades"
Waɗannan taurarin alama ce da ke nufin mala'iku bakwai na ikilisiyoyi bakwain ne.
Maɗorin fitilun alama ce da na nufin ikilisiyoyin nan bakwai. AT: [1:2]
AT:1) mala'iku na sama da suke tsare ikilisiyoyin nan bakwai ko 2) mutum mai ba da saƙo ga ikilisiyoyin nan bakwai.
Wannan na nufin ikilisiyoyi bakwai da su ka kasance a Asia Ƙarama a wancan lokaci. AT: [1:11]
1"Zuwa ga mala'ikan dake ikilisiyar Afisus, ka rubuta: 'Wadannan sune kalmomin wanda ke rike da taurari bakwai a cikin hannun damarsa. wanda yake tafiya a tsakanin zankayen fitilun zinari bakwai, 2"Na san abubuwan da ka yi, da famar ka, da hakurinka da jimirinka. Na sani ba ka jimrewa miyagun mutane, na sani ka gwada wadanda suka ce da kansu, su manzanni ne, amma ba haka ba, ka tarar da su makaryata.3Na san kana da tsawon jimrewa, kuma ka sha wahala sosai sabili da sunana, kuma baka gaji ba. 4Amma ga rashin jin dadi na da kai, ka bar kaunar ka ta fari. 5Domin haka ka tuna daga inda ka fadi. Ka tuba ka yi abubuwan da ka yi da fari. Sai fa ka tuba, zan zo maka in kuma cire fitilar ka daga mazauninta.6Amma kana da wannan: Ka tsani abubuwan da Nikolatawa suka yi, wanda nima na tsana. 7wanda yake da kunnen ji ya saurari abinda Ruhu yake fada wa ikilisiyoyi. Ga wanda yayi nasara zan bashi dama ya ci daga itacen rai, wanda ke cikin firdausin Allah.""8Zuwa ga mala'ikan da ke Ikilisiliyar Samirna rubuta: 'Wadannan su ne kalmomin wanda yake shine farko shine karshe, wanda ya mutu ya sake rayuwa kuma. 9"Na san wahalun ka da talaucin ka amma kana da arziki. Nasan masu bata suna wadanda suke cewa su Yahudawa ne, amma ba haka suke ba. Su majami'ar Shaidan ne.10Kada ka ji tsoron wahalar da zaka fuskanta nan gaba. Duba! Shaidan yana gab da jefa wadansun ku cikin kurkuku, domin a gwada ku, kuma zaku sha wahala ta kwana goma. Kuyi aminci har ga mutuwa zan baku rawanin rai. 11wanda yake da kunne ya saurari abinda Ruhu yake fada wa ikilisiyoyi. Shi wanda yayi nasara ba zai cutu a mutuwa ta biyu ba.""12"Zuwa ga mala'ikan dake ikilisiyar Burgamas rubuta: 'Wadannan ne kalmomin wanda ya ke da takobi mai kaifi biyu; 13"Na san inda kake zama can inda kursiyin shaidan yake. Duk da haka ka rike sunana da karfi, na sani baka yi musun bangaskiyar ka da ni ba, ko a lokacin Antifas mashaidina, amintaccena, wanda aka kashe a tsakaninku, can inda shaidan yake zama.14Amma ga rashin jin dadi na kadan da kai: Kana da wadansu da suke rike da koyarwar Bil'amu kamkam, wanda ya koya wa Balak ya sa abin tuntubi gaban 'ya'yan Isra'ila, domin su ci abincin da aka mika wa gumaka kuma suyi fasikanci. 15Hakannan kuma wasunku sun rike koyarwar Nikolatawa kamkam.16Sabili da haka ka tuba! Idan ka ki zan zo gare ka da sauri, kuma in yi yaki gaba da su da takobi dake cikin bakina. 17Bari wanda yake da kunne ya sauriri abin da Ruhu yake fadawa ikilisiyoyi. Ga wanda yayi nasara zan bada wata boyayyar manna, kuma zan bashi farin dutse da sabon suna a rubuce a kan dutsen, suna wanda ba wanda ya sani, sai shi wanda ya karbe shi.""18Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar Tiyatira rubuta: 'Wadannan sune kalamomin Dan Allah, wanda yake da idanu kamar harshen wuta; sawayen kamar gogaggiyar tagulla: 19"Na san abin da ka yi, kaunar ka, da bangaskiya da hidima da tsawon jimrewar ka. Na san abinda ka yi bada dadewa ba ya fi abinda ka yi da fari.20Amma ga rashin jin dadi na da kai: Kana hakurce wa matar nan Yezebel, wadda take kiran kanta annabiya. Ta wurin koyarwarta, ta rudi bayina suyi fasikanci kuma su ci abincin da aka mika wa gumaka sadaka. 21Na bata lokaci domin ta tuba amma bata so ta tuba da fasikancin ta.22Duba! zan jefa ta a kan gadon jinya, wadanda kuma suka yi zina da ita za su shiga babbar wahala, sai dai in sun tuba daga ayukan ta. 23Zan buga 'ya'yanta da mutuwa, kuma dukan ikilisiyoyi zasu san cewa nine wanda nake bincike tunani da zukata. Zan ba kowanen ku bisa ga ayyukansa.24Amma ga sauran ku dake cikin Tayatira, ga kowanen ku wanda bai rike wannan koyarwar ba, kuma bai san abinda wadansu suke kira zurfafan abubuwan Shaidan ba--ga ku na ce ban sa muku wata nawaya ba.' 25Duk da haka dole ku tsaya da karfi har in zo.26Wanda yayi nasara da wanda ya yi abin da na yi har karshe, a gareshi zan bada iko akan al'ummai 27Zai yi mulkin su da sandar karfe, zai farfasa su kamar randunan yumbu." 28Kamar yadda na karba daga wurin Ubana, ni kuma zan bashi tauraron asubahi. 29Bari wanda yake da kunne ya saurari abinda Ruhu yake fadawa ikilisiyioyi.""
Wannan ne farkon sakon Ɗan Mutum zuwa ga mala'ikan ikilisiyar Afisa.
AT: 1) mala'iku na sama da yake tsare ikilisiyoyin nan bakwai ko 2) mutum mai ba da saƙo ga ikilisiyoyin nan bakwai. [1:20]
AT: Waɗannan taurarin alama ne. Suna a madadin mala'iku na ikilisiyoyi bakwen ne [1:16]
AT: Fitilun alama ne da ke nufin ikilisiyoyi bakwai.[1:12].
"Fama" da kuma "jimiri" irin magana ne da za'a iya bayyana su da aiki "aiki" da kuma "jimriya" AT: "Na san ... cewa kayi ta famar aiki sosai, kuma ka jimre da hakuri"
"amma ba manzanni ba ne"
"ka iya gane wa cewa waɗancan mutane manzanni na ƙarya ne"
"Suna" a nan kalma ce da yana nuna Yesu Almasihu. AT: "domin na" ko "domin kun gaskata da suna na" ko "domin kun gaskanta da ni"
An yi magana game da fid da zuciya kamar gajiya ne. AT: "baka zama mai fid da zuciya ba" ko "baka bari ba"
"Ban yarda maka ba domin" ko "Ina fushi da kai domin"
Anyi magana game da daina yin abu kamar barin shi a baya ne, ƙauna kuma kamar abu ne da ana iya bari a baya. AT: "ka daina ƙauna ta kamar yadda kayi a farko"
Anyi magana game da yanke ƙauna kamar yadda suka saba kamar faɗiwa daga sama ne. AT: "yawan yadda ka canja" ko "yawan ƙauna da ka saba mani"
"Idan baka tuba ba"
AT: Fitilun alama ne da ke nufin ikilisiyoyi bakwai [1:12]
Mutane waɗanda suka bi koyaswar wani mutum wanda ake kira Nikolaus
Anyi magana game da mai son ji kamar samun kunne ne. AT: "Bari wanda yake so ya ji, ya ji" ko "Idan kana so ka ji, ka ji"
Wannan na nufin wanda yayi nasara ne. AT: "duk wadda ya ƙi mugunta" ko "waɗanda suka ƙi yarda da mugunta"
"gonar Allah." Wannan alama na nufin sama ne.
AT: Wannan suna ne na birni a yammacin Asiya da a yau ake ƙira Turkiya [1:11]
AT: Wannan na nufin kasancewar Yesu na har abada [1:17]
"Wahallu" da kuma "talauci" ana iya fasara su kaman aiki ne. AT: "Na san yadda ka sha wahala ka kuma talauce"
"Ɓata suna;" ana iya fasarar wannan kamar aiki. AT: "Na san yadda mutane sun ɓata maka suna-waɗanda suka ce su Yahudawa ne" ko "Na san yadda mutane sun faɗi munanan abubuwa game da kai-waɗanda suka ce su Yahudawa ne"
"amma su ba asalin Yahudawa bane"
Ana magana game da mutanen da suka taru domin su yi biyaya ko ɗaukaka Shaiɗan kamar su majami'a ne, wurin sujada da kuma koyaswan domin Yahudawa.
"A kwanakin nan, Shaiɗan zai saka wasun ku cikin kurkuku"
"Kuyi mani aminci ko za'a kashe ku." AT: "har ga" ba ya nufin cewa ku daina yin aminci a lokacin mutuwa.
"rawanin mai nasara." Wannan ganye ne daga itace zaitun ko ganyayen laurel, shi ake sa wa a kan wanda yayi nassara a wasan guje guje.
AT: 1)"rawani da yake nuna cewa na riga na baku madauwamiyar rai" ko 2) "rayuwa na ƙwarai kamar kyautar mai zasara"
Anyi magana game da mai son ji kamar samun kunne ne. AT: "Bari wanda yake so ya ji, ya ji" ko "Idan kana so ka ji, ka ji [2:7]
"ba zai ga mutuwa ta biyu ba" ko "ba zai mutu so biyu ba"
AT: Wannan sunan wani birni ne a yammacin Asiya da ayau ake ƙira Turkiya. [1:11]
AT: Wannan na nufin takobi mai baki biyu wanda aka wasa duka gefensa domin ya ci ta kowace gefe [1:16]
AT: 1) Ikon Shaiɗan da kuma mugun ra'ayi akan mutane, ko 2) inda Shaiɗan yake mulki.
"Suna" a nan kalma ce da ake amfani wa mutum. Anyi magana game da gaskantawa sosai kamar abu ne da ake riƙewa da ƙarfi. AT: "ka gaskanta da ni sosai"
"Bangaskiya" za'a iya bayyana shi kamar aiki "gaskata." AT: "ka cigaba da gaya wa mutane cewa ka gaskata da ni"
Wannan sunan mutum ne.
"Ban yarda maka ba domin kiman abubuwan da ka yi" ko "Ina fushi da kai domin kiman abubuwa da ka yi." AT: [Revelation 2:4]
AT: "waɗanda suka koyar da abin da Bil'aminu ya koyas; zai" ko "wanda zai yi abin da Bil'aminu ya koyas; zai."
Wannan sunan sarki ne.
Ana magana game da abin da yake jan ra'ayin mutane zuwa yin zunubi kamar ɗutse ne akan hanya da yake saka mutane tuntuɓe. AT: "wanda ya nuna wa Balak yadda zai saka mutanen Isra'ila suyi Zunubi"
"zunubin fasikanci" ko "yin zunubin fasikanci"
"tuba"
AT: "Idan ka ƙi tuba, zan"
"faɗa da su"
Wannan na nufin takobi da ke [Revelation 1:16] AT: "da takobi dake cikin bakina, wanda itace kalmar Allah"
AT: Wannan na nufin duk wanda yayi nassara [2:7] AT: "duk wanda ya ƙi mugunta" ko "waɗanda basu yarda da mugunta ba"
AT: Wannan suna ne na birni yammacin Asiya da a yau ake ƙira Turkiya. [1:11]
Wannan sune mai muhinminci ne naYesu.
AT: "wanda idanun sa na da haske kamar harshen wuta" [Revelation 1:14]
AT: [Wahayin Yahaya 1:15]
Kalmomin nan "ƙauna," "bangaskiya," "hidima," da kuma "jimriya" ana iya bayyana su da kalmar aiki. AT: "Yanda ka ƙaunace ni, ka amince da ni, ka yi mani hidima, ka kuma jimre cikin haƙuri"
AT: "Amman ba yarda da wasu abubuwan da kake yi ba" ko "Amma ina fushi da kai domin wani abun da kake yi" [2:4]
Yesu yayi magana akan wata mata a ikilisiyar su kaman ita ce Sarauniya Yezebel, domin ta yi ayukan zunubi iri ɗaya da wadda Sarauniya Yezebel tayi tun kafin lokacin su. AT: "matar da tayi kamar yadda Yezebel ta yi, da kuma"
"Na bata zarafi domin ta tuba" ko "Na yi zaman jira domin ta tuba"
Kwanciyar ta akan gado zai zama sakamakon ciwo mai tsanani ne da Yesu ya saka mata. AT: [Revelation 2:22]
Yesu, yayi magana game da saka mutane su shiga wahala kamar wurgasu ne cikin wahala. AT: "Zan wurga waɗanda suke yin zina tare da ita su shiga wahala mai tsanani"
"aikata zina"
Wannan na nufin cewa suma sun yi mugayen halayen ta tare da ita. Ta wurin tuba daga ayukan ta, su ma sun tuba daga yin ayukan ta. AT: "idan basu tuba daga aikata mugunta da suna yi ba" ko "idan basu tuba da aikata ayuka tare da ita ba"
"Zan kashe 'ya'yanta"
Yesu yayi magana game da masu bin ta kamar 'ya'yan ta ne. AT: "masu bin ta" ko "Mutane da suke yin abin da ta koyas"
"Zukata" kalma ce da ke nuna yadda ake ji ko sha'awa. AT: "abin da mutane na tunani da kuma so"
Wannan magana ne game da hukunci da kuma sakamako. AT "Zan hukunta ko saka wa kowanen ku"
Ana magana game da yarda da koyaswa kamar riƙe koyaswa ne. AT: "duk wanda bai yarda da koyaswar nan ba"
Kalman na "koyarwa" ana iya bayyana shi kamar aiki. AT: "baka riƙe abin da take koyaswa ba" ko "baka yarda da abin da take koyaswa ba"
AT: "waɗanda suka ƙira su zurfafan abubuwa sun gane cewa daga Shaiɗan ne" ko "waɗansu mutane na ƙiran su zurfafan abubuwa, amma Yesu na cewa waɗancan abubuwan daga Shaiɗan ne.
"abubuwa masu zurfi da Shaiɗan ke koyaswa"
Ana magana game da abubuwan da ake yi a boye kamar suna da zurfi ne. AT: "ɓoyayyun abubuwa"
Wannan annabci ne daga Tsohon Alkawali game da Sarkin Isra'ila, amma Yesu ya yi amfani da shi a nan domin waɗanda ya ba su iko a kan al'umai.
Ana magana game da matsanacin mulki kamar mulki ne da sandar karfe. AT: "Zai yi mulkin su da tsanani kamar yana buga su ne da sandar ƙarfe"
Farfasa su zuwa 'yan gutsure hoton ne da yake nufin 1) hallakar da masu aikata miyagun abubuwa ko 2) yin nasara da abokan gaba. AT: "Zai yi nasara a kan abokan gabansa kamar yana farfasa randunan yumbu ne"
AT: 1) "Kamar yadda na karɓi iko daga wurin Ubana" ko 2) "Kamar yadda na karɓi tauraron asubahi daga wurin Ubana"
Wannan suna mai muhinminci ne na Allah da yake bayyana dangantaka tsakanin Allah da kuma Yesu.
"shi" a nan na nufin wanda yayi nasara.
Wannan tauraro ne mai haske da ke bayyana da asuba kafin gari ya waye. Alama ce tanasara.
1"Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar Sardisu rubuta: 'Wadannan ne kalmomin wanda yake rike da ruhohi bakwai na Allah da taurari bakwai. "Na san abin da ka aikata. Ka yi suna cewa kana raye amma kai mattacce ne. 2Ka farka ka karfafa abin da ya rage amma ya kusan mutuwa, domin ban sami ayyukanka cikakku a gaban Allahna ba.3Domin haka sai ka tuna, da abubuwan da ka karba kuma kaji. Ka yi biyayya da su, ka kuma tuba. Amma idan baka farka ba, zan zo maka kamar barawo, kuma ba zaka farga da sa'ar da zan zo gaba da kai ba. 4Amma akwai sunayen mutane kadan a Sardisu wadanda basu kazantar da tufafinsu ba. Za su yi tafiya tare da ni sanye da fararen tufafi domin sun cancanta.5Wanda ya yi nasara za a sanya mashi fararen tufafi, kuma ba zan taba share sunansa ba daga Littafin Rai, kuma zan fadi sunansa a gaban Ubana, da kuma gaban mala'ikunsa. 6Bari wanda yake da kunne ya saurari abin da Ruhu ke fadawa ikilisiyoyi."'"7Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar cikin Filadelfiya rubuta: kalmomin wanda yake maitsarki ne kuma mai gaskiya - yana rike da mabudin Dauda, yana budewa babu mai rufewa, kuma inda ya rufe ba mai budewa. 8Na san abin da ka aikata. Duba, na sa budaddiyar kofa a gabanka wanda ba mai iya rufewa. Na san kana da karamin karfi, duk da haka ka yi biyayya da maganata kuma baka yi musun sunana ba.9Duba! Wadanda ke na majami'ar Shaidan, wadanda suke cewa su Yahudawa ne; amma maimakon haka karya suke yi. Zan sa su zo su rusuna a kafafunka, kuma za su san cewa ina kaunarka. 10Tun da ka jure cikin hakuri ka kiyaye dokoki na, ni ma zan kiyaye ka daga sa'a ta gwaji da zata sauko kan dukan duniya, domin a gwada mazauna duniya. 11Ina zuwa da sauri. Ka rike abin da kake da shi kamkam domin kada wani ya dauke maka rawani.12Zan sa wanda ya yi nasara ya zama ginshiki a haikalin Allahna, kuma ba zai taba fita daga cikin sa ba. Zan rubuta sunan Allahna a kansa, sunan birnin Allahna (sabuwar Urushalima, mai saukowa daga sama daga wurin Allahna), da kuma sabon sunana. 13Bari wanda yake da kunne ya ji abin da Ruhu ke gayawa ikilisiyoyi."14"Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar da ke Lawudikiya rubuta: 'Wadannan sune kalmomin Amin, madogara da mai shaidar gaskiya, mai mulki bisa hallittar Allah. 15Na san abin da ka aikata, ba ka sanyi ko zafi. Naso ko da kana sanyi ko zafi! 16Amma saboda kai tsaka-tsaka ne - ba zafi ba sanyi - na kusa tofar da kai daga bakina.17Domin ka ce, "Ni mai arziki ne, na mallaki kadarori da yawa, ba na bukatar komai." Amma ba ka sani ba kana cike da takaici ne, abin tausayi, matalauci, makaho kuma tsirara kake. 18Saurari shawara ta: Ka sayi zinariya a wuri na wadda aka goge da wuta domin ka zama mai arziki, domin ka suturta kanka da fararen tufafi masu kyalli domin kada ka nuna kunyar tsiraicin ka, da mai domin ka shafa wa idanunka ka sami gani.19Ina horar da duk wanda nake kauna, ina kuma koya masu yadda za su yi rayuwa. Saboda haka, ka himmatu ka tuba. 20Duba, ina tsaye a bakin kofa ina kwankwasawa. Idan wani ya ji muryata ya bude kofar, zan shigo cikin gidansa, in ci tare da shi, shi kuma tare da ni.21Wanda ya ci nasara, zan bashi dama ya zauna tare da ni bisa kursiyina, kamar yadda nima na ci nasara kuma na zauna da Ubana a kan kursiyinsa. 22Bari wanda yake da kunne ya saurari abin da Ruhu yake fadawa wa ikilisiyoyi."
Wannan ne farkon wasiƙar Ɗan Mutum zuwa ga mala'ikan ikilisiyar dake Sardisu.
AT: [ Wahayi Yahaya 1:11]
AT: [Wahayin Yahaya 1:4]
AT: [Wahayin Yahaya1 16]
Biyayya da kuma girmama Allah na nufin zama a raye ne; rashin biyaya kuma, da rashin girmama shi na nufin mutuwa ne.
Ana magana kuma game da ayuka masu kyau da masubi da ke Sardisu suka yi kamar suna raye ne, amma, suna cikin haɗarin mutuwa. AT: "Ka tashi, ka kuma kammala aikin da ya rage, ko kuma abin da ka yi zai zama a banza" ko "Ka tashi. Idan baka gama abin da ka rigaya ka fara ba, aikin ka na baya zai zama mara amfani"
Zama a shirye ga haɗari na nufin ka farka ne. AT: "Zama shiryaye" ko "Ka yi lura"
Wannan na nufin maganan Allah ne, wanda suka gaskanta. AT: "Maganar Allah da ka ji da kuma gaskiyar da ka gaskanta"
AT: "ka farka" [Wahayin Yahaya 3:2]
Yesu zai zo a lokacin da mutane basu tsamanci zuwan shi ba, kamar yadda barawo ke zuwa alokacin da ba a tsamance shi ba.
"sunaye" kalma ne da mutane na amfani domin kansu. AT: "mutane kaɗan"
Yesu yayi magana akan zunubi a rayuwar mutum kamar ƙazantatccen tufafi ne. AT: "basu ƙazantar da rayuwarsu kaman ƙazantatccen tufafi ba"
Mutane sun cika magana game da rayuwa a masayin "tafiya" AT: "zai yi rayuwa tare da ni"
Fararen tufafi na nuna rayuwa mai tsabta, mara datti. AT: "kuma za'a saka musu fararen tufafi, wanda zai nuna cewa suna da tsabta"
AT: [Wahayin Yahaya 2:7]
AT: "zai sanya fararen tufafi" ko "Zan ba shi fararen tufafi"
Ba zai faɗi sunan mutumin kawai ba, amma zai sanar cewa mutumin nan, nashi ne"
"a gaban Ubana"
Wannan lakaɓi mai muhinminci ne na Allah dake bayyana dangantaka tsakanin Allah da kuma Yesu.
AT: [Wahayin Yahaya 2:7]
AT: [Wahayin Yahaya 1:11]
Yesu yayi magana game da ikon yanke shari'ar wanda zai iya shiga ƙasar sa kamar mabuɗin Sarki Dauda ne.
"yana buɗe kofar shiga ƙasar kuma, ba mai iya rufewa"
"yana kulle kofar kuma, ba mai buɗewa"
"Na riga na buɗe maka kofa"
AT: "ka yi bisa ga koyaswa" ko "ka yi biyayya ga umurnina"
"suna" a nan kalmace da ake amfani wa mutumin da yake da suna. AT: "ni"
AT: [Wahayin Yahaya 2:9]
Wannan alama ce ta miƙa kai, ba sujada ba. AT: "suka rusuna domin miƙa kai"
A nan kalman "ƙafafu" na nuna wanda muntanen nan na rusunawa a gaban shi. AT: "a gaban ka" ko "maka"
"zasu koya" ko "zasu amince"
"zan kuma tsare abin da zai faru da kai daga sa'a ta gwaji" ko "zan tsare ka domin kada ka shiga sa'a ta gwaji"
"lokacin gwaji." Mai yiwuwa wannan na nufin "lokacin da mutane na ƙoƙarin sa ka yi mini rashin biyayya."
Ana magana game da kasancewa nan gaba kamar zuwa ne.
yana zuwa domin yayi sheri'a. AT: "Ina zuwa da sauri domin in yi sheri'a"
Ana magana game da cigaba da gaskantawa sosai cikin Almasihu kamar riƙe abu kamkam ne. AT: "ka cigaba da gaskantawa sosai"
A nan "rawani" na nufin sakamako. AT: [Wahayin Yahaya 2:10]
A nan "Wanda yayi nasara" na nufin duk wanda yayi nasara ne. "ginshikin" na nuna muhinmin madauwamiyar guri ne na mulkin Allah. AT: [Revelation 2:7]
AT: [Wahayin Yahaya 2:7]
AT: [Wahayin Yahaya 1:11]
A nan "Amin" suna ne domin Yesu Almasihu. Ya bamu tabbacin alkawuran Allah ta wurin cewa, amin.
AT: 1) "wanda yake mulkin kowane abu da Allah ya halitta" ko 2) "ta wurin wanda Allah ya hallici komai."
Marubucin yayi magana game da Lawudikiyawan kamar su ruwa ne. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) "sanyi" da "zafi" na nufin ƙurewan abubuwa dake jawo hankalin mutum ga ƙaunan Allah AT: "kana nan kaman ruwan da bai yi sanyi ko zafi ba"
"ka na da ɗumi kanɗan ." Marubucin yayi magana game da mutanen Lawudikiya kamar su ruwa ne da babu sanyi sosai ya rage ƙishi ga waɗanda suke shan ta, kuma babu ɗumi sosai ya dafa abu ko ya warkas da waɗanda suke yin wanka cikin ta. AT: 1) wannan na bayanin mutane da suke da ƙanƙanin tabbaci na ruhaniya ko 2) wannan na bayanin mutanen da Allah bashi da amfani a gare su.
Ana magana game da kin su kamar tofar da su ne daga baki. AT: Zan ƙi ka kamar yadda zan tofar da ruwan da ke tsaka-tsaka ne.
Yesu yayi magana game da ruhaniya mai kyau kamar halli na jiki mai kyau ne. AT: "Kuna nan kamar mutane masu takaici dayawa, abin tausayi, matalauta, makafi kuma tsirara kuke"
A nan "saya" na nufin karɓan abu daga Yesu ne da yake da muhinminci na gaske ga ruhaniyar mutane. AT: "Zo gare ni ka sami arziki na ruhaniya, wanda yana da daraja fiye da zinariyan da aka tace a wuta. Karɓi adalci daga gareni, wadda yake kama da fararen tufafi masu kyalli, domin kar ka sha kunya. Kuma ka karɓi hikima daga wuri na, wanda na nan kamar ceto ne wa idanu, domin ka iya gane abubuwan ruhaniya"
"ka himmatu ka tuba"
Yesu na magana game da yadda yake so mutane suyi dangantaka da shi kamar yana so su gayyace shi cikin gidajen su ne AT: "Ina nan kamar wanda ke tsaye a bakin kofa ina kwankwasawa"
Idan mutane na son wani ya marabce su cikin gidajen su, zasu kwankwasa a bakin kofa. AT: "Ina son ku bar ni in shiga ciki"
Kalman nan "murya ta" na nufin cewa Yesu ne ke magana. AT: "ji ni ina magana" ko "ji ƙira ta"
Wasu harsunan su fi son kalman aikaton nan "shigo" AT: "Zan shigo cikin gidan sa"
Wannan na nufin zaman su tare a matsayin abokane.
Wannan ne ƙarshen sakon Ɗan Mutum ga mala'iku na ikilisiyoyi bakwain
A zauna akan kursiyi na nufin ayi mulki ne. AT: "yi mulki tare da ni" ko "ya zauna a kursiyi na ya kuma yi mulki tare da ni"
1Bayan wadannan abubuwa na duba, sai ga budaddiyar kofa a sama. Muryar fari da na ji kamar kakaki, na cewa hauro in nuna maka abubuwan da dole za su faru bayan wadannan al'amura." 2Nan da nan ina cikin Ruhu, sai na ga wani kursiyin da aka ajiye shi a sama, da wani zaune bisansa. 3Shi da ke zaune a kan tana da kamanin yasfa da yakutu. Akwai Bakangizo kewaye da kursiyin kamanin bakangizon kuwa zumurudu.4A kewaye da kursiyin kuwa akwai kursiyoyi ashirin da hudu, masu zama bisa kursiyoyin nan kuwa dattawa ne ashirin da hudu, sanye da fararen tufafi, da kambunan zinariya bisa kawunansu. 5Daga kursiyin walkiya na ta fitowa, cida, da karar aradu. Fitilu bakwai na ci a gaban kursiyin, fitilun sune ruhohin Allah guda bakwai.6Gaban kursiyin akwai tekun gilashi, mai haske kamar karau. A tsakiyar kursiyin da kewayen kursiyin akwai rayayyun hallitu guda hudu cike da idanu gaba da baya.7Rayayyen hallitta na farko na da kamanin zaki, rayayyen hallitta na biyun kamanin dan maraki ne, rayayyen hailitta na uku fuskar sa kamar dan adam, kuma rayayyen hallitta ta hudu na da kamanin gaggafa mai tashi. 8Dukan rayayyun hallittan nan hudu na da fukafukai shida shida, cike da idanu a bisa da karkashin fukafukan. Dare da rana ba sa daina cewa, Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki ne Ubangiji Allah, mai iko duka, shine da shine yanzu shine mai zuwa."9A dukan lokacin da rayayyun hallittun nan suke ba da girma, daukaka, da godiya ga shi da ke zaune bisa kursiyin, wanda ke raye har abada abadin, 10sai dattawan nan ashirin da hudu suka fadi da fuskokinsu a kasa gaban shi da ke zaune bisa kursiyin. Suka yi sujada ga shi da ke rayuwa har abada abadin, suna jefar da kambinsu a gaban kursiyin, suna cewa, 11"Ka cancanta, ya Ubangijinmu da Allahnmu, ka karbi yabo da daukaka da iko. Domin kai ka hallicci dukan komai, da kuma nufinka ne, suka kasance aka kuma hallicce su.
Yahaya ya fara bayanin wahayin sa akan kursiyin Allah.
"Bayan da na gan wanɗannan abubuwa kenan" ([Wahayin Yahaya 2:1-3:22])
Wannan magana na nufin zarafin da Allah ya ba wa Yahaya ya ga cikin sama, ko da shike, ta wurin wahayi.
Za a iya bayyana yadda muryar nan kamar ƙaho a fili. AT: "na magana da ni da ƙarfi kamar ƙarar ƙaho"
AT: [Wahayin Yahaya 1:10]
Yahaya yayi maganar bishewar Ruhun Allah kamar yana cikin Ruhu ne. AT: [1:10]
Duwatsu masu daraja. Mai yiwuwa yasfa na da haske irin na gilashi ko dutse mai kama da madubi, yukutu kuma jawur ne.
Dutse mai kalar kore kuma mai daraja
"kursiyoyi 24"
Wannan na kama ne da furen da ke fita a itacen zaitun ko ganyen laurel, da aka yi shi da zinariya. Irin waɗannan ganyayen ne ake ba wa masu guje-guje da suka yi nassara su saka a kawunansu.
Yi amfani da harshen ka ta wurin yin bayanin yadda walkiyar take a duk lokacin da ta bayyana.
Haka ne aradu ke yin ƙara da ƙarfi. Yi amfani da harshen ka ta wuring yin bayanin yadda ƙarar tsawa take.
AT: [ 1:4]
AT: 1) Ana magana game da teku kamar ita gilashi ne. "teku da take nan sumul kamar gilashi" ko 2) gilashi kuma kamar teku ce. "gilashi da ta bazu kamar teku"
AT: "mai haske kamar ƙarau"
"Kewaye da kursiyin nan da nan" ko "Kusa da kursiyin da kuma kewaye da shi"
"Mutune rayayyu guda hudu" ko "abubuwa rayayyu guda huɗu"
Yadda kan kowane rayyayen hallita ya bayyana wa Yahaya kwatanci ne da za a fi ganewa da sauri.
"rayayyen mutum" ko "abu mai rai." AT: [4:6]
A bisa da kuma karkashin kowane fukafuki na cike da idanu.
Ana maganar kasancewar shi nan gaba kamar zuwan ne.
Wannan mutum ɗaya ne. Wanda ke zaune a kursiyin na rayuwa har abada abadin.
Kalmomi biyun nan na ma'anar abu guda ne kuma ana sake faɗan sune domin a nanata magana. AT: "na har abada"
Da dalili suka kwanta da kawunansu ƙasa domin su nuna cewa suna sujada ne.
Wannan na kama ne da furen da ke fita a itacen zaitun ko ganyen laurel, wanda aka yi shi da zinariya. Dattatan nan sun ajiye rawanin su a ƙasa da biyayya; wannan ya nuna cewa suna miƙa kai ga ikon Allah ya yi mulkin su." AT: "suka ajiye rawanin su a gaban Allah domin su nuna cewa suna miƙa kai ga shi"
AT: 1) a ajiye abu, ko 2) a yer da abu na dole, kamar mara amfani ne. ("wurgar," [Wahayin Yahaya 2:22])
"Ubangijinmu da Allahnmu." Wannan mutum guda ne, wanda ke zaune a bisa kursiyin.
Waɗannan abubuwan ne Allah yake da su kullum. An yi maganan yabon shi domin yana da su kamar karɓan su ne yake yi. AT: "ka karɓi yabo domin ɗaukakar ka, girma, da kuma iko" ko "saboda kowa ya baka yabo domin kai mai ɗaukaka ne, mai girma ne, kuma mai iko ne"
1Sa'annan na ga a cikin hannun daman wanda ke zaune a kan kursiyin, na ga littafi wanda ke da rubutu ciki da waje, an kuma hatimce shi da hatimai bakwai. 2Na kuma ga wani kakkarfan mala'ika na shela da murya mai karfi, "Wa ya isa ya bude littafin ya kuma bambare hatimin?"3Ba wani a sama ko a kasa ko karkashin kasa da ya iya ya bude littafin ko ya karanta abin da ke cikinsa. 4Na yi kuka mai zafi saboda ba wani da ya cancanta da zai bude littafin ko ya karanta abin da ke cikinsa. 5Amma daya daga cikin dattawan nan ya ce mani, "Kada ka yi kuka. Duba! Zaki na kabilar Yahuza, Tushen Dauda, ya yi nasara. Ya cancanci bude littafin da kuma hatimansa bakwai."6Na ga Dan Rago yana tsaye tsakanin kursiyin da rayayyun halittun nan guda hudu a cikin dattawa. Yana kama da wanda aka kashe. Yana da kafonni bakwai da idanuwa bakwai; wadannan sune ruhohin Allah bakwai da aka aiko zuwa dukan duniya. 7Ya tafi ya karbi littafin daga hannun daman wanda ke zaune bisa kursiyin.8Lokacin da Dan Ragon ya dauki littafin, rayayyun halittun nan hudu da dattawan nan ashirin da hudu suka fadi har kasa a gaban Dan ragon. Kowannen su na dauke da molo da tasar zinariya cike da kayan kamshi, wadanda kuwa sune addu'o'in masu ba da gaskiya.9Suka raira sabuwar waka: "Ka cancanta ka dauki littafinka kuma bude hatimansa. Domin an yanka ka, da jininka ka saya wa Allah mutane daga kowacce kabila, harshe, jama'a da al'umma. 10Ka maishe su mulki da firistoci su bauta wa Allanmu, kuma za su yi mulki a duniya."11Da na duba sai na ji karar mala'iku masu yawa kewaye da kursiyin da rayayyun halitu da kuma dattawa. Jimillarsu ya kai dubbai goma, sau dubbai goma, da dubun dubbai. 12Suka tada murya da karfi suka ce, "Macancanci ne Dan Ragon da aka yanka ya karbi iko, wadata, hikima, karfi, girma, daukaka da yabo."13Na ji kowanne halittaccen abu da ke cikin sama da kasa da karkashin kasa da cikin teku - dukan abubuwan da ke cikinsu - na cewa, "Ga shi wanda ke zaune a kan kursiyin da kuma Dan Ragon, yabo, girma, daraja, da kuma ikon yin mulki, har abada abadin. 14Sai rayayyun halittun nan hudu suka ce, "Amin!" dattawan nan kuma suka fadi da fuskokinsu suka yi sujada.
Yahaya ya cigaba da bayanin abin da ya gani a wahayin sa game da kursiyin Allah.
"Bayan da na ga waɗancan abubuwa, na ga"
Wannan abu iri "ɗaya ne" da na [Revelation 2:3-4]
"littafi wanda ke da rubutu ciki da waje"
"yana kuma da hatimi bakwai da ya kulle"
Mutum zai ɓamɓare hatimin kafin nan ya iya buɗe littafin. AT: "Wa ya cancanci ya ɓamɓare hatimin ya kuma buɗe littafin?"
Wannan na nufin kowane wuri: wurin rayuwar Allah da mala'ikunsa, wurin rayuwar mutane da kuma dabbobi, da kuma inda mattatu suke. AT: "ko'ina a sama ko kasa ko ƙarƙashin ƙasa"
"Ka ji" ko "Kasa kunne ga abin da nake shiri in faɗa maka"
Wannan laƙabi ne da Allah yayi wa mutum daga kabilar Yahuza, zai zama babban sarki. AT: "Wanda ake kira Zaki na kabilar Yahuza" ko "Sarki da ake kira Zaki na kabilar Yahuza"
Ana magana game da wannan sarki kamar shi zaki ne domin zaki na da ƙarfi kwarai.
Wannan laƙabi ne na wanda da Allah ya yi wa zuriyar Dauda alkawali cewa zai zama babban sarki. AT: "wanda ake ce da shi Tushen Dauda"
Ɗan Ragon, ya bayyana a cikin kursiyin.
"ɗan rago" ƙaramar tunkiya ce na miji. A nan kuma na nufin Almasihu ne.
AT: [Wahayin Yahaya 1:4]
AT: "wanda Allah ya aiko cikin dukan duniya"
Ya kusanci kursiyin. Wasu harsunan sun yi amfani da wannan aikatau "zo." AT: "Ya zo"
Wannan ƙaramar tunkiya ce na miji. A nan kuma na nufin Almasihu ne. AT: [Wahayin Yahaya 5:6]
"dattawa ashirin da huɗu
"kwanta a kasa." fuskokinsu na fuskantar ƙasa domin su nuna cewa suna bautan Ɗan Ragon ne. Sun yi haka da dalili; ba cikin kusrkure ko hatsari ne suka yi ba.
AT: 1) "kowane dattijo da rayayyun hallitan" ko 2) "kowane dattijon."
Kayan ƙamshin alamar addu'a ce na masubi ga Allah.
AT: "Domin sun yanka ka" ko "Domin mutane sun kashe ka"
Idan yaren ka ya na da wata kalma na kashe dabba domin yin haɗaya, za ka iya yin amfani da shi a nan.
Da shike jini na nufin rai na mutum ne, rashin jini kuma na nufin mutuwa ne. Mai yiwuwa wannan na nufin "ta wurin mutuwar ka" ko "tawurin mutuwa."
"ka sayi mutane domin su zama na Allah" ko "ka biya farashin domin mutane su zama na Allah"
Wannan na nufin ya shafi kowane mutane na kabilu dabam-dabam.
Yi amfani da kalma na harshen ka domin nuna cewa wannan lambar na da yawa. AT: "zambar dubu ne" ko "ƙirgen dubbai masu yawa ne"
"Ɗan Ragon da aka yanka ya cancanta"
Ɗan Rago na da dukkan waɗannan abubuwa. Ana maganar yabo zama da waɗannan ababai kamar karɓan su ne. AT: [Wahayin Yahaya 4:11] AT: "domin kowa ya girmama shi, ya ɗaukaka shi, ya kuma yabe shi domin shi mai iko ne, mai wadata ne, mai hikima ne, kuma shi mai ƙarfi ne.
Wannan na nufin ko'ina ne. AT: [Wahayin Yahaya 5:3]
"Bari shi wanda ke zaune a kan kursiyin da kuma Ɗan Ragon ya samu"
1Na duba lokacin da Dan Ragon ya bude daya daga cikin hatiman bakwai, sai na ji daya daga cikin rayayyun halittattun hudu ya fada da murya kamar tsawa, "Zo!" 2Sai Na duba sai ga wani farin doki, mahayinsa na rike da baka, kuma an bashi rawani. Ya fito a matsayin mai nasara domin ya yi nasara.3Sa'anda Dan Ragon ya bude hatimi na biyu, sai na ji rayayyen halitta na biyu ya ce, "Zo!" 4Sai wani doki ya fito waje - jawur. Ga mahayin aka bashi dama ya dauke salama daga duniya, domin mutanen ta su karkashe juna. Wannan mahayin an bashi babbar takobi.5Sa'anda Dan Ragon ya bude hatimi na uku, sai na ji rayayyen halita na uku ya ce, "Zo!" Na ga bakin doki, mai hawanta na rike da ma'auni a cikin hannunsa. 6Sai na ji kamar wata murya daga cikin rayayyun halittattun nan hudu ta ce, "Mudun alkama guda a kan albashin yini, kuma mudun sha'ir uku. Amma kar ka bata mai da kuma ruwan inabi."7Da Dan Ragon ya bude hatimi na hudu, na ji muryar rayayyen halitta na hudu ya ce, "Zo!" 8Sai na ga wani doki ruwan toka. Mai hawansa an bashi suna mutuwa, hades kuma tana biye da shi. An basu iko bisa kashi hudu na duniya su kashe da takobi, yunwa, cututtuka, da kuma namomin jeji na duniya.9Da Dan Ragon ya bude hatimi na biyar, a karkashin bagadi sai na ga rayukan wadanda aka kashe saboda maganar Allah, da kuma shaidar da suka rike. 10Suka yi kuka da babban murya, "Sai yaushe ya mai iko duka, Mai Tsarki da gaskiya, zaka shari'anta mazaunan duniya, ka kuma dauki fansar jininmu? 11Sai kowanne dayan su aka bashi farar tufa aka kuma fada masu su kara jira na lokaci kadan har sai adadin abokan bautar su da kuma 'yan'uwansu maza da mata wadanda aka kashe ya cika, kamar yadda aka kashe su.12Da Dan Ragon ya bude hatimi na shidan, ina kallo sai ga babbar girgizar kasa. Rana ta zama baki kirin kamar bakar tufa, wata kuma ya zama kamar jini. 13Taurarin sama suka fado kasa, kamar yadda itacen baure ke karkade 'ya'yansa da basu nuna ba, yayin da babbar iska ta kada. 14Sama kuma ta bace kamar takardar da aka nannade. Kowanne dutse da tsibiri aka kau da shi daga wurinsa.15Sai sarakan duniya da muhimman mutane da sarakunan yaki, attajirai, da masu iko, tare da kowanne mutum, bawa da 'yantacce suka boye cikin duwatsu da tsaunuka. 16Suka ce wa tsaunuka da duwatsu, "Ku fado bisan mu! Ku boye mu daga fuskar wanda yake zaune bisa kursiyin da kuma fushin Dan Ragon. 17Domin babban ranar fushin sa ta zo. Wa zai iya tsayawa?"
Yahaya ya cigaba da bayanin abubuwan suka faru a gaban kursiyin Allah. Ɗan Ragon ya fara buɗe hatimin kan littafin.
Wannan umurni ne ga mutum, mai yiwuwa mahayin farin dokin ne da aka yi maganarsa a aya ta 2.
Wannan na kama ne da furen da ke fita a itacen zaitun ko ganyen laurel, wanda aka yi da zinariya. Irin waɗannan ganyayen ne ake ba wa masu guje-guje da suka yi nassara su saka a kawunansu. AT: "ya karɓi rawani" ko "Allah ya ba shi rawani"
Wannan fure ne da ke fita a itacen zaitun ko ganyen laurel, wanda ake ba wa masu nasara a wasan guje-guje a zamanin Yahaya.
"hatimi na gaba" ko "hatimi lamba ta biyu"
"rayayyen halitta na gaba" ko "rayayyen hallita lamba ta biyu"
AT: "fito waje. Ga ta jawur kamar wuta" ko "fito waje. Ga ta da haske kamar wuta"
AT: "Allah ya ba wa mahayin izini" ko "aka ba wa mahayin mutum"
AT: "aka ba wa wannan mahayi babbar takobi" ko "Allah ya ba wa mahayin nan babbar takobi"
"takobi mai girma sosai" ko "takobi na ƙwarai"
"hatimi na gaba" ko "hattimi lamba ta uku"
"rayayyen halitta na gaba" ko "rayayyen hallita lamba ta uku"
kayan aiki da ake gwada nauyin abu.
Wasu harsuna sun fi so su yi amfani da waɗaṇnan aikatau ă maganar su "kimmanin kuɗi" ko "saya". Akwai alkama kaɗan domin dukan mutane, saboda haka kuɗin yayi tsada sosai. AT: "Yanzu mudun alkama na kimmanin kuɗi dinari guda" ko "Sayan mudun alkama da dinari guda"
"mudu" ma'auni ne na musanman iri ɗaya da na ruwa. AT: "Mudu ɗaya na alkama ... mudu uku na sha'ir" ko "kwano ɗaya na alkama ... kwano uku na sha'ir"
Wannan kuɗi na kai albashin kwana guda. AT: "azurfa ɗaya na kuɗi" ko "albashin aikin kwana guda"
Idan an ɓata mai da ruwan inabi, ba za'a samu dayawa domin mutane su saya ba, kuma farashin zai haura.
Mai yiwuwa waɗannan kalmomi na nufin girbin mai na zaitun da kuma girbin inabi.
"hattimi na gaba" ko "hattimi lamba ta huɗu"
"rayayyen halitta na gaba" ko "rayayyen halitta lamba ta huɗu"
"doki ruwan toka." Wannan kalar mataccen jiki ne, kalar kuma alamar mutuwa ne.
A nan "duniya" na nufin mutanen duniya ne. AT: "kashi huɗu na mutanen duniya"
Takobi makami ne, a nan kuma na nufin yaƙi ne.
Wannan na nufin cewa Mutuwa da Hades zasu zama sanaɗin da namomin jaji zasu yi faɗa wa mutane su kuma kashe mutanen.
"hatimi na gaba" ko "hatimi lamba ta biyar"
Mai yiwuwa wannan a "ƙarƙashin bagadin ne."
AT: "waɗanda wasu suka kashe"
A nan "maganar Allah" magana ce na saƙo daga Allah. Game da "riƙe," ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka: 1) riƙe shaida na nufin ba da gaskiya ga maganar Allah da kuma shaida. AT: "saboda koyaswa na littafin da kuma abun da suka koyas game da Almasihu" ko "Saboda sun ba da gaskiya ga maganar Allah, wanda shi ne shaida" ko 2 riƙe shaida kuma, na nufin ba da shaida game da maganar Allah. AT: "domin sun yi shaida game da maganar Allah"
Kalmar jini anan na nufin mutuwar su ne. AT: "hikunta waɗanda suka kashe mu"
Wannan na nufin cewa Allah ya riga ya shirya mutanen da abokan gaban su za su kashe su.
Wannan kungiyan mutane guda ne, wanda aka yi bayani a hanyoyi biyu: a matsayin masu bauta, da maza da mata. AT: "'yan'uwan su maza da mata waɗanda suke bauta wa Allah tare" ko "abokan su masubi waɗanda suke bauta wa Allah tare"
Akan yi magana game da masubi maza da mata kamar 'yan'uwane ne . AT: " 'yan'uwa masubi"
"hatimi na gaba" ko "hatimi lamba ta shida"
Wasu lokatai, ana yin tufa da bakar gashi ne. Mutane na saka tufa yayin da suke makoki. An yi amfani da wannan ne domin ya saka mutane tunani akan mutuwa da kuma makoki. AT: "baƙa kamar kayan makoki"
An yi amfani da "jini" domin ya jawo hankalin mutane su yi tunani a kan mutuwa. Za a iya bayyana wa mutane a fili, yadda take nan kamar jini. AT: "jawur kamar jini"
AT: "kamar yadda babbar iska take kaɗa itacen ɓaure ta saukar da ɗanyun 'ya'ya"
An cika yin tunanin sama kamar tana da ƙarfi kamar ƙarfe, amma yanzu kamar takarda mara ƙarfi ce aka yi maganarn ta wanda nan da nan akan yaga a kuma naɗe.
Wannan na nufin jarumai ne waɗanda suke ba da umurni a fillin daga.
manyan ramukai na gefen tudai
A nan "fuska" na nufin "gaba ne." AT: "a gaban wanda" ko "wanda"
Ranar fushinsu na nufin lokacin da zasu hukunta mugayen mutane, AT: " wannan lokaci ne na ban tsoro kwarai da za a hukunta mutane"
Ana maganar kasancewan yanzu kamar ya rigaya ya zo ne.
"Su" na nufin Ɗan Ragon da kuma wanda yake kan kursiyin.
An yi maganan yin rai kamar tsayawa ne. An yi wannan tambayan, saboda a bayyana ƙurewar fushinsu da tsoron cewa ba wanda zai iya rayuwa alokacin da Allah zai hukunta shi AT: "Ba wanda zai iya rayuwa"
1Bayan wannan sai na ga mala'iku hudu suna tsaye bisa kusurwoyi hudu na duniya, suka rike iskoki hudu na duniya kamkam domin kada iska ta hura a kan duniya, a kan teku, ko wani itace. 2Sai na ga wani mala'ika na zuwa daga gabas, wanda yake da hatimin Allah mai rai. Ya yi kira da babbar murya da mala'ikun nan hudu da aka basu dama su azabtar da duniya da teku: 3"Kada ku azabtar da duniya, da teku, da itatuwa har sai mun sa hatimi bisa goshin bayin Allahnmu."4Sai naji yawan wadanda aka hatimce: 144, 000, wadanda aka hatimce daga kowacce kabilar mutanen Isra'ila: 5dubu goma sha biyu aka hatimce daga kabilar Yahuza, dubu goma sha biyu daga kabilar Ra'ubainu, dubu goma sha biyu daga kabilar Gad, 6dubu goma sha biyu daga kabilar Ashiru, dubu goma sha biyu daga kabilar Naftali, dubu goma sha biyu daga kabilar Manassa.7Dubu goma sha biyu daga kabilar Saminu, dubu goma sha biyu daga kabilar Lawi, dubu goma sha biyu daga kabilar Issaka, 8dubu goma sha biyu daga kabilar zabaluna, dubu goma sha biyu daga kabilar Yusufu, sai kuma dubu goma sha biyu daga kabilar Bilyaminu aka hatimce.9Bayan wadannan abubuwa na duba, sai ga wani babban taro wanda ba mai iya kirgawa daga kowacce al'umma, kabila, mutane da harsuna tsaye a gaban kursiyin da gaban Dan Ragon. Suna sanye da fararen tufafi da ganyen dabino a hannuwansu, 10kuma suna kira da murya mai karfi: "Ceto ya tabbata ga Allahnmu wanda ke zaune bisa kursiyi, da kuma Dan Ragon!"11Dukan mala'iku suna tsaitsaye kewaye da kursiyin kuma kewaye da dattawan nan da kuma rayayyun halittun nan hudu, suka kwanta rib da ciki da fuskokinsu a gaban kursiyin. Suka yi sujada ga Allah, 12suna cewa, "Amin! yabo, daukaka, hikima, godiya, girma, iko, da karfi su zama na Allahnmu har abada abadin! Amin!"13Sai daya daga cikin dattawan ya tambaye ni, "Su wanene wadannan, da suke sanye da fararen tufafi, kuma daga ina suka fito?" 14Sai nace masa, "Ya shugaba, "Ka sani," sai ya ce mani, "Wadannan sune suka fito daga babban tsanani. Sun wanke tufafin su sun maida su farare cikin jinin Dan Ragon.15Domin wannan dalili, suke gaban kursiyin Allah, kuma suna masa sujada dare da rana cikin haikalinsa. Shi wanda ke zaune bisa kursiyin zai zama runfa a bisan su. 16Ba za su kara jin yunwa ba, ko kishin ruwa ba. Rana ba zata buge su ba, ko kowanne zafi mai kuna. 17Domin Dan Ragon dake tsakiyar kursiyin zai zama makiyayin su, kuma zai bishe su zuwa mabulbulan ruwan rai, kuma Allah zai share dukan hawaye daga idanuwansu."
Yahaya ya fara yin bayani a kan wahayinsa na bayin Allah guda 144,000 waɗanda aka saka musu hatimai. Wannan ya fara bayan da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na shida, wato kafin ya buɗe hatimi na bakwain.
Ana magana game da duniya cewa shimfiɗaɗɗiyar fili ce da ke kamar littafi. Kalman nan "kusurwa huɗu" ya shafi arewa, kudu, gabas, da kuma yamma.
Kalman nan "hatimi" a nan na nufin kayan aiki da ake amfani domin saka alama ta wurin buga shi a kan wani abu mai kama da kakin zuma. A wannan yanayi, za a mori wannan kayan aiki domin saka alama a kan mutanen Allah. AT: "abin saka alama" ko "abin buga hatimi"
Kalman nan "hatimi" ya shafi alama. Wannan alama na nuna cewa mutane na Allah ne, kuma zai tsare su. AT: "saka alama a goshin su"
Goshi na saman fuska ne, bisa idanu.
AT: "Waɗandan mala'ikun Allah suka yi wa alama"
"mutane dubu ɗari da arba'in da huɗu"
"mutane 12,000 daga kabilar"
Wannan sunayen mutanen Isra'ila ne waɗanda aka hatimce.
"babban taro" ko "gaggarumin taron jama'a"
Kalan nan "fari" na nufin tsarki.
"Ceto ya zo daga"
Suna ɗaukaka Allah da kuma Ɗan Ragon. Kalman nan "ceto" za a iya bayyana shi da kalmar aiki "cece." AT: "Allahn mu, wanda ke zaune a bisa kursiyi, kuma da Ɗan Ragon da ya cece mu!"
Waɗanan rayayyun halitattu huɗun ne aka ambato a [Wahayin Yahaya 4:6-8]
A nan "kwanta da fuskoki" karin magana ne da yake nufin a kwanta da ciki a ƙasa. AT: "Shirya kansu" a [Wahayin Yahaya 4:10]. AT: "suka durƙusa a ƙasa"
"Allahnmu ne ya isa ya karɓi yabo, ɗaukaka, hikima, godiya, girma, iko da ƙarfi"
Aikatau ɗin nan "bayar" za a iya yin amfani da kalmomi domin nuna yadda za a ba da yabo, ɗaukaka, da kuma girma "ga" Allah, AT: "Sai mun ba da yabo, ɗaukaka, godiya, da kuma girma ga Allahnmu"
Kalmomi biyun nan na nufin abu ɗaya ne kuma na sake nanata cewa yabo mara ƙarewa ne.
Waɗannan fararen tufafin na nuna cewa su masu adalci ne.
"suka rayu cikin babban tsanani"
"lokacin wahala mai ban tsoro" ko "lokacin da mutane zasu sha mugun wuya"
Ana magana game da zama masu adalci tawurin jinin Ɗan Ragon nan kamar wanke tufafinsu ne a jininsa. AT: " An mayar da su masu adalci tawurin wanke tufafinsu fari cikin jininsa"
Kalman nan "jini" na nufin mutuwar Ɗan Ragon.
Waɗannan duka na nufin mutane waɗanda suka fita daga cikin Babban Tsanani,
Ana amfani da kalmomin biyun nan dare da rana domin nuna yadda suke aiki "kowane lokaci" ko "ba tsayawa"
"zai zama runfa a bisan su." Ana magana game da tsare su kamar yana basu wurin fakewa ne domin su zauna. AT: "basu gun fakewa" ko "zan tsare su"
Ana kwatanta zafin rana da hukunci da ke saka mutane shan wahala. AT: "Rana ba zai kone su ba" ko "Rana ba zai sa su zama marasa ƙarfi ba"
"Ɗan Rago, wanda ke tsaye a tsakiyar kewayen kursiyin"
Dattijon yayi magana akan kula da Ɗan Ragon na nuwa wa mutanen sa kamar kula ne da makiyayi na nuna wa tumakinsa. AT: "Gama Ɗan Ragon ... zai zama kamar makiyayi ne a gare su" ko "Gama Ɗan Ragon ... zai kula da su kamar yadda makiyayi na kula da tumakinsa"
Dattijon yayi magana akan abu da ke ba da rai kamar mabulbula sabon ruwa ne. AT: "zai jagorance su kamar makiyayi ne ke jagorantar tumakinsa zuwa sabon ruwa" ko "zai jagorance su zuwa rai kamar yadda makiyayi na jagorantar tumakinsa zuwa ruwan rai"
Hawaye na nufin ɓacin rai. AT: "Allah zai cire masu ɓacin rai, kamar yadda ake share hawaye" ko "Allah ba zai sa su, su zama masu ɓacin rai kuma ba"
1Lokacin da Dan Ragon nan ya bude hatimi na bakwai, sai aka yi shiru a sama na kimanin rabin sa'a. 2Sa'anan na ga mala'iku bakwai wadanda ke tsaye a gaban Allah, aka kuma basu kahonni bakwai3Wani mala'ika ya zo, rike da tasar turaren konawa na zinariya, a tsaye gaban bagadi. Turaren konawa mai yawa aka bashi saboda ya mika su tare da adu'o'in dukan masu bada gaskiya akan bagadin kona turare na zinariya a gaban kursiyin. 4Hayakin turaren konawa, da adu'o'in masu bada gaskiya, suka tashi sama a gaban Allah daga hanun mala'ikar. 5Mala'ikan ya dauki tasar turaren konawa ya cika ta da wuta daga bagadin. Sa'annan ya wurgo ta kasa zuwa duniya, sai ga tsawar aradu, da cida, da walkiya mai haske, da kuma girgizar kasa.6Mala'ikun nan bakwai wadanda suke da kahonni bakwai suka yi shirin busa su. 7Mala'ika na fari ya hura kahonsa, sai ga kankara da wuta a garwaye da jini. Aka jeho shi kasa zuwa duniya sai kashi daya cikin uku na duniya ya kone, daya cikin uku na itatuwa suka kone, da duk danyar ciyawa suka kone kaf.8Mala'ika na biyu ya busa kahonsa, sai wani abu mai kama da babban dutse mai cin wuta aka jefo shi cikin teku. Kashi daya cikin uku na tekun ya zama jini, 9daya cikin uku na rayayyun halittu da ke cikin ruwa suka mutu, sai daya bisa uku na jiragen ruwa aka hallaka.10Mala'ika na uku ya busa kahonsa, sai gagarumin tauraro ya fado daga sama, yana ci kamar cocila, bisa kashi daya cikin uku na koguna da mabulbulan ruwa. 11Sunan tauraron Daci. Kashi daya cikin uku na ruwaye suka yi daci, sai jama'a da yawa suka mutu domin ruwayen sun yi daci.12Mala'ika na hudu ya busa kahonsa, sai daya cikin kashi uku na rana ya harbu, da daya cikin kashi uku na wata da kuma daya cikin kashi uku na taurari. Sai daya cikin kashi uku nasu duka suka duhunce; daya cikin kashi uku na yini da daya cikin uku na dare suka rasa hasken su.13Da na duba sai na ji gaggafa da take shawagi a tsakiyar sararin sama tana kira da babban murya, "Kaito, kaito, kaito, ga mazaunan duniya sabili da sauran karar kahonni na mala'ikun nan uku da za su busa."
Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na bakwai.
Wannan ne ƙarshen hatimi guda bakwai na kan takardan. AT: "hatimi na gaba" ko "hatimi na ƙarshe" ko "hatimi na bakwai"
Aka ba kowannen su ƙaho guda ɗaya. AT: 1) "Allah ya ba su ƙahonni guda bakwai ko 2) "Ɗan Ragon ya ba su kahonni bakwai"
"zai miƙa turaren wa Allah tawurin konawa"
Wannan na nufin kwanon da ke a hannun mala'ikan. AT: "kwanon da ke a hannun mala'ikan"
Mai yiwuwa kalman nan "wuta" na nufin garwashi ne. AT: "cike da garwashi" ko "cike da wuta na garwashi"
Mala'iku guda bakwan suka busa ƙahonin a lokaci ɗaya.
AT: "Mala'ikan ya wurga ƙanƙara da wuta zuwa ƙasa a duniya garwaye da jini"
AT: "ya ƙona kashi ɗaya cikin duniya, kashi ɗaya cikin uku na itatuwa, da duk danyar ciyawa"
"Mala'ika na gaba" ko "Mala'ika na biyun"
AT: "mala'ikan ya jefa wani abu mai kama da babban dutsen da ke chi da wuta"
Za a iya bayyana kashi "Na ukun" cikin fasarar. AT: "kamar an raba tekun zuwa kashi uku ne, kuma ɗaya daga cikin ya zama jini"
AT: 1) "ya zama jawur kamar jini" ko 2) ya zama ainihin jini.
"rayyayun abubuwa na cikin teku" ko "da kifaye da kuma sauran rayyayun dabbobi na cikin teku"
"gagarumin tauraro da ke chi kamar tocila ya faɗo daga sama." Wutar gagarumin tauraro na nan da kamanin wutan tocila.
wuta da ake sa wa a sanda ya ci ta gefe daya domin ya nuna haske.
Wannan ƙaramar itace ne da yake da ɗaci. Mutane na yin magani da itacen, sun kuma yadda cewa itacen na da dafi. AT: "Sunan tauraron Daci" ko "Sunan tauraron Maganin Ɗaci"
Ana magana game da ruwa mai ɗaci kamar ita ce ɗaci. AT: "ta zama ɗaci"
"suka mutu domin su sha ruwan ɗacin"
Ana magana a kan saka mummunan abu ya faru da rana kamar za a buga shi ne. AT: "ɗaya cikin kashi uku na rana ya canja" ko "Allah ya canja ɗaya cikin kashi uku na rana"
AT: 1) "ɗaya cikin kashi uku na lokacin ya duhunce" ko 2) "ɗaya cikin kashi uku na rana, ɗaya cikin kashi uku na wata, ɗaya cikin kashi uku na tauraron ya zama da duhu"
"babu haske a lokacin ɗaya cikin uku na rana da ɗaya cikin kashi uku na dare" ko "basu yi haske a alokacin ɗaya cikin ukun rana da kuma ɗaya ciki ukun dare"
AT: "domin mala'iku uku da basu riga sun busa ƙahon su ba suna gaf ga busawa"
1Sa'annan mala'ika na biyar ya busa kahonsa. Na ga tauraro daga sama da ya fado zuwa duniya. An ba tauraron nan mabudin hanyar rami marar iyaka. 2Ya bude hanyar rami marar iyaka, sai hayaki ya fito daga kofar kamar hayaki daga babban ramin wuta. Rana da iska suka juya duhu, sabili da hayakin da ke fitowa daga kofar ramin.3Daga cikin hayakin kuwa sai ga fari sun fito zuwa duniya, aka ba su iko kamar na kunamai cikin duniya. 4Aka gaya masu kada su yi wa ciyayi da kowanne koren ganye ko itace illa, sai dai mutanen da basu da hatimin Allah a goshinsu.5Ba a basu izini su kashe wadannan mutane ba, sai dai su azabtar da su na watani biyar. Zafinsu kuwa zai zama kamar na cizon kunama idan ta harbi mutum. 6A kwanakin nan mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su same ta ba. Za su yi marmarin mutuwa, amma mutuwa za ta guje su.7Farin kuwa suna kama da dawakai da aka shirya domin yaki. A bisa kansu akwai wani abu kamar rawanan zinariya, fuskokinsu kuma kamar na 'yan adam. 8Gashinsu kuma kamar na mata yake, hakoransu kamar hakoran zaki. 9Sulkunansu kuma kamar na karfe, karar fikafikansu kuma kamar karar kekunan dawakin yaki masu yawa da dawakai da aka shirya domin zuwa yaki.10Suna da wutsiya da kari kamar kunamai; A wutsiyar su kuma suna da ikon da zai azabtar da mutane na tsawon wata biyar. 11Suna da wani kamar sarki a kansu, mala'ikan rami marar iyaka. Sunansa da Ibraniyanci Abadon, da Helenanci kuma Afoliyon. 12Bala'i na fari ya wuce. Duba! Bayan wannan akwai masifu guda biyu masu zuwa.13Mala'ika na shida ya busa kahonsa, sai na ji murya daga kahonin bagadin zinariya da ke gaban Allah. 14Muryar ta ce wa mala'ika na shida da ke rike da kahon, "Kwance mala'ikun nan hudu da ke daure a babban kogin Yufiretis," 15Mala'iku hudun da aka shirya domin wannan sa'a, da wannan rana, da wannan wata, da kuma wannan shekara, aka sake su su kashe daya bisa uku na 'yan adam.16Yawan sojoji da ke kan dawakai shine 200, 000, 000. Na ji adadin su. 17Haka na ga dawakan a cikin wahayina da mahayansu: Sulkunansu jawur kamar wuta, bakin shudi, da kuma ruwan doruwa. Kawunan dawakan suna kama da na zakuna, daga bakunansu kuma wuta, da hayaki da farar wuta suka fito.18Aka kashe daya bisa uku na mutane ta annoban nan uku: wuta, hayaki da farar wuta da suka fito daka bakunansu. 19Domin iko na dawakan na bakunansu da wutsiyoyinsu - domin wutsiyoyinsu suna kama da macizai, kuma suna da kawuna wadanda dasu suke ji wa mutane rauni.20Sauran 'yan adam, da ba a kashe su ta wannan annoba ba, basu tuba daga ayyukan da suka yi ba. Basu kuma daina bautar aljanu da gumakan zinariya, da azurfa, da tagulla, da dutse, da itace ba - abubuwan da ba su gani, ji, ko tafiya. 21Basu kuma tuba ba daga kisan kai, sihiri, fasikanci, ko kuma ayyukansu na sata ba.
Na biyar cikin mala'ikun ya fara busa ƙahon sa.
Yahaya ya ga tauraron bayan da ya faɗi. Bai ga faɗiwan sa ba.
"mabuɗin da ke buɗe rami mara iyakan"
AT:1) "hanyar rami" wata hanya ce ta bayyana ramin a matsayin doguwa da ƙarama, ko2) "hanyar rami" na nufin buɗewar ramin.
Wannan karamar rami ne mai zurfi sosai. AT:1) ramin ba karshe; ya cigaba da gangara kasa kuma ba iyaka, ko 2) zurfin ramin yayi kaman bashi da karshe ne.
Babban ramin wuta na bada babban hayaƙi, baƙar hayaƙi. AT: "kamar babban hayaƙi dake fitowa daga ramin wuta"
"zama duhu"
taron ƙwari da suke yawo tare a sama. Mutane na tsoron su domin su kan ci duk ganyaye na lambu ko na kan itace.
kunamai suna da gwanin harbi, kuma dafi ne ga sauran dabbobi da kuma mutane. AT: "gwanin harbin mutane kamar kunamai"
ƙananan ƙwari masu dafi suna harbi ne da wutsiyar su. Harbin su na da zafi sosai har ma ya kan kai tsawon lokaci.
Fara da ake gani kullum mugun hatsari ne ga mutane domin idan suka taru, su kan ci duk ciyayi ko ganyaye da aka shuka da kuma na itace. An gaya ma faran kada su yi haka.
An iya gane kalmomin nan "yin ɓarna" ko "yin illa". AT: "sai dai su yi wa mutanen illa"
Kalmar nan "hatimi" a nan na nufin kayan aiki da ake amfani domin saka alama ta wurin buga shi a kan wani abu mai kama da kakin zuma. A wannan yanayi, za a mori wannan kayan aiki domin saka alama a kan mutanen Allah. AT: "hatimi" [Wahayn Yahaya 7:3] "abin saka alamar Allah" ko "abin buga hatimin Allah"
Goshin na bisa fuskan ne, a saman idanu.
"Su" na nufin fara ne. ([Wahayin Yahaya 9:3])
mutanen da faran na harbin su
An iya gane kalmomin nan "bayar da izini" AT: "aka basu izini su azabtar da su kwarai"
Za a ba wa faran nan dama suyi har na watanni biyar.
"saka su cikin tsananin wuya"
Kunama karamar ƙwaro ne dake harbi, mai dafi a karshen doguwar wutsiyar sa. Wannan harbin kan saka zafi mai tsanani har ma ya kai ga mutuwa.
Za a iya sake faɗin wannan domin a cire kalmomi mara amfani. AT: "mutane zasu yi kokarin samun hanyar mutuwa, amma ba za su same ta ba" ko "mutane zasu yi kokarin kashe kansu, amma ba zasu samu hanyar mutuwa ba" (Dubi:
"za su bukaci mutuwa kwarai" ko "za suyi fatan cewa, da sun mutu"
Yahaya ya yi magana game da mutuwa kamar mutum ne, ko dabba da zai iya guduwa. AT: "ba zasu iya mutuwa ba" ko "ba zasu mutu ba"
Waɗannan faran, basu yi kamar faran da muke gani kullum ba. Yahaya ya bayyana su ta wurin faɗin yadda waɗansun su na kama da abubuwa da bam.
Wannan na kama ne da furen da ke fita a itacen zaitun ko ganyen laurel, kuma an yi shi ne da zinariya. Irin waɗannan ganyayen ne ake ba wa masu guje guje da suka yi nassara su saka a kawunansu.
Kalman nan "Su" na nufin fara ne.
AT: [Wahayin Yahaya 9:6] "dake da abin harbi kamar na kunama" ko "da abin harbi irin na kunama da ke saka zafi mai tsanani"
AT:1) suna da ikon yin illa wa mutane har na tsawon watanni biyar, ko 2) zasu harbi mutane har ma su sa su cikin zafi na watanni biyar.
Dukkan sunayen na nufin "Mai lalatar da abu ne"
Ana magana game da kasancewa nan gaba kamar zuwan ne.
Muryan na nufin wanda ke maganan ne. Yahaya bai faɗa wanda yake maganan ba, amma zai iya yiwuwa Allah ne. AT: "na ji wani na magana"
Waɗannan ƙaho ne da aka ƙera su da tsawo a kowace kusurwa guda huɗu na kan bagadin.
Muryan na nufin mai maganan ne. AT: Mai maganan ya ce"
AT: "Mala'ikan ya saƙe mala'iku huɗun da aka shirya su domin ... a wannan shekaran"
AT: "Mala'iku huɗun da Allah ya shirya su"
An yi amfani da kalmomin nan domin nuna cewa akwai wani lokaci na musamman, amma ba kowane lokaci kawai ba. AT: "ainihin wannan lokacin"
Wasu hanyoyin da zaka iya bayyana wannan na kamar haka: "zambar dubu ɗari biyu" ko "dubu ɗari biyu" ko "dubu ashirin sui dubu goma." Idan harshen ka tana da wata kalma na musanman domin yin haka, ka yi amfani da ita. AT: [Wahayi Yahaya 5:11]
"jawur kamar wuta" ko " da haske jawur" AT: [Wahayin Yahaya 6:3]
"rawaya kamar farar wuta" ko "rawaya da haske kamar farar wuta"
"wuta, hayaƙi, da kuma farar hayaƙi ya fito daga bakinsu"
"ɗaya cikin uku na mutanen." AT: "Na uku" [Wahayin Yahaya 8:7]
Kalman nan "iko" za a iya fasarar shi da kalmar siffa. AT: "Domin bakuna, da wutsiyoyin dawakan ne na da iko sosai" ko "gama bakuna, da wutsiyoyin dawakan ne suka yi wa mutane rauni"
AT: "waɗanda annoban nan bai kashe ba"
Waɗannan kalmomin na tunashe mu cewa gunki basu da rai kuma basu cancanta a ɗaukaka su ba. Amma mutane basu daina ɗaukaka su ba. AT: "duk da yake gunki baya gani, ji ko tafiya"
1Sa'anan na ga wani babban mala'ika yana zuwa daga sama. Yana lullube cikin girgije, a bisa kansa akwai bakangizo. Fuskarsa kamar rana, kafafunsa kamar ginshikan wuta. 2Yana rike da karamin littafi a hannunsa, da aka bude, sai ya sa kafarsa ta dama a bisa teku, kafarsa ta hagu kuma a kan kasa.3Sai yayi ihu da babbar murya kamar zaki mai ruri. Lokacin da ya yi ihu, tsawan nan bakwai suka yi magana da karar su. 4Da tsawan nan bakwai suka yi magana, ina dab da rubutu, amma na ji wata murya daga sama cewa, "Ka rike asirin abin da tsawan nan bakwai suka fada. Kada ka rubuta shi."5Sai mala'ikan da na gani tsaye bisa teku da kasa, ya daga hannun damarsa sama. 6Sai ya rantse da wannan da ke raye har abada abadin - wanda ya halicci sama da duk abinda ke cikinsa, da duniya da duk abin da ke a kanta, da teku da dukan abin da ke cikinsa, sai mala'ikan ya ce, "Babu sauran jinkiri. 7Amma a ranar da mala'ika na bakwai yana dab da busa kahonsa, a lokacin ne asirin Allah zai cika, daidai da yadda ya sanar wa bayinsa annabawa."8Muryar da na ji daga sama ta sake magana da ni: "Tafi, ka dauki budadden littafin da ke hannun mala'ikan da ke tsaye bisa teku da kan kasa." 9Sai na tafi wurin mala'ikan na ce da shi ka bani karamin littafin. Yace dani, "Dauki littafin ka ci. Zai sa cikinka ya yi daci, amma a bakinka zai yi zaki kamar zuma."10Na dauki karamin littafin daga hannun mala'ikan na ci. Ya yi zaki sosai a bakina kamar zuma, amma da na ci, sai cikina ya zama da daci. 11Wani yace mani, "Dole ka sake yin annabci kuma game da mutane masu yawa, da al'ummai, da harsuna da sarakuna."
Yahaya ya fara bayanin wahayin babban mala'ika da yake riƙe da littafin. A wahayin Yahaya, yana kallon abin da ke faruwa a duniya. Haka ya faru ne a tsakanin busa ƙaho na shida da na bakwan.
Yahaya ya yi magana game da mala'ikan kaman ya saka gajimare ne a matsayin kayan sa. Ana iya gane wannan bayanin ta wurin magana ne. Ko da shike, domin ba kullum bane ake ganin abubuwan a cikin wahayi, za a iya gane wannan cikin yanayin rubutu.
Yahaya ya kwatanta hasken fuskarsa da hasken rana. AT: "Fuskarsa da haske kamar rana"
AT: "Kafafunsa suna kamar ginshiƙan wuta"
"Ya tsaya da ƙafar shi na dama a bisa teku, ƙafar shi na hagu kuma a kan kasa"
"Sai mala'ikan yayi ihu"
An bayyana tsawan nan kamar mutum ne wanda ya iya magana. AT: " tsawan nan bakwai suka yi magana da babban murya" ko "tsawan yayi ƙara da ƙarfi sau bakwai"
Ana magane akan tsawan da zai auko sau bakwai kamar "tsawa" bakwai ne dabam dabam.
Kalman nan "murya" na nufin kalmar da ke fitowa daga wani wanda ke fiye da mala'ikan. AT: "amma na ji muryar wani na magana daga sama"
Yayi haka domin ya nuna cewa yana rantsuwa da Allah.
"Ya yi roƙo cewa abin da zai faɗa ya zama tabbatatce ta wurin wanda ke raye har abada abadin"
A nan "wanda" na nufin Allah ne.
"Babu sauran jira" ko "Allah ba zai yi jinkiri ba"
AT: "asirin Allah zai cika" ko "Allah zai kammala shirin da yayi a sirance"
Yahaya ya ji murya daga sama, wanda ya ji a 10:3 ya sake mishi magana. [Wahayin Yahaya 10:4]
Kalman nan "murya" na nufin mai maganan ne. AT: "Wanda na ji ke magana daga sama" ko "Wanda ya mini magana daga sama"
Yahaya ya ji
"Mala'ika ya ce mini"
"sa ... tsami" ko "sa ... guba." wannan na nufin mumunan ɗanɗono daga ciki, bayan da aka ci wani abu mara kyau.
Wannan na nufin mutane ne da suke magana da harshen. AT: "harsuna dayawa dabam-dabam" ko "taron mutane dayawa waɗanda suke magana da nasu harshen"
1Aka bani sanda in yi amfani da ita kamar sandar awo. Aka ce mani, "Tashi ka auna haikalin Allah da bagadi, da wadanda ke sujada a cikinsa. 2Amma kada ka auna harabar haikalin, domin an ba da shi ga Al'ummai. Za su tattake birnin mai tsarki har wata arba'in da biyu.3Zan ba shaidu na biyu iko su yi anabci na kwanaki dubu daya da dari biyu da sittin, sanye da tsummoki. 4Wadannan shaidu sune itatuwan zaitun biyu da kuma fitilu biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya. 5Idan wani ya yi niyyar cutar da su, wuta na fitowa daga bakinsu ta lashe makiyansu. Duk mai son cutar da su, dole a kashe shi ta wannan hanya.6Wadannan shaidu suna da iko su kulle sama domin kada a yi ruwa a lokacin da suke anabci. Suna da iko su juya ruwaye su zama jini, su kuma bugi duniya da kowacce irin annoba duk lokacin da suka ga dama. 7Sa'adda suka gama shaidarsu, dabban da ke fitowa daga rami marar iyaka zai yi yaki da su. Zai ci nasara da su ya kashe su.8Gawawwakinsu zasu kwanta kan hanyar babban birnin nan (wanda ma'anar sa ake kira Saduma da Masar) inda aka gicciye Ubangijinsu. 9Wajen kwana uku da rabi wadansu daga dukan mutane, da kabila, da harshe, da al'umma za su yi kallon gawawwakinsu. Za su ki yarda a sa su cikin kabari.10Mazaunan duniya zasu yi murna da biki a kansu. Har za su aika wa juna kyautai saboda annabawan nan biyu da suka azabtar da mazaunan duniya. 11Amma bayan kwana uku da rabi, numfanshin rai daga wurin Allah zai shiga cikinsu sa'annan za su tsaya a kan kafafunsu. Matsanancin tsoro zata fado kan wadanda za su gansu. 12Sa'annan zasu ji murya mai kara daga sama tana ce masu, "Ku hauro nan!" Sa'annan za su tafi sama cikin gajimarai, makiyansu suna kallo.13A waccan sa'a za a yi babbar girgizar kasa, sai kashi daya cikin goma na garin ya fadi. Mutane dubu bakwai za su mutu a girgizar kasar, wadanda suka tsira kuwa za su tsorata su ba da daukaka ga Allah na sama. 14Annoba ta biyu ta wuce. Duba! Annoba ta uku tana zuwa nan da nan.15Sa'annan mala'ika na bakwai ya busa kahonsa, sai muryoyi masu kara suka yi magana cikin sama cewa, "Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Almasihunsa. Zai yi mulki har abada abadin."16Sa'annan dattawan nan ashirin da hudu da ke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fadi fuskokinsu na kasa. Suka yi wa Allah sujada. 17Suka ce, "Mun yi maka godiya, Ubangiji Allah, Madaukaki, wanda yake yanzu da wanda yake a da, saboda ka dauki ikonka mai girma ka fara mulki.18Al'ummai suka fusata, amma hasalar ka ta zo. Lokaci ya zo da za a yi wa mattatu sharia, da zaka ba da sakamako ga bayinka annabawa, da masu ba da gaskiya, da wadanda suka ji tsoron sunanka, karami da babba. Lokaci kuma ya yi da za ka hallaka wadanda ke hallakar da duniya."19Sa'annan aka bude haikalin Allah da ke sama, sai aka ga akwatin alkawarinsa a cikin haikalinsa. Sai ga hasken walkiya, da rugugi, da aradu, da girgizar kasa, da manyan duwatsun kankara.
Yahaya ya fara yin bayani wahayi da ya gani game da karɓan sandar awu da kuma shaidu guda biyu da Allah ya zaɓa. Wannan wahayin ya faru ne bayan da aka busa ƙaho na shida da na bakwan.
AT: "Wani ya bani sanda"
Wannan kalma "mini" ko "ni" na nufin Yahaya ne.
"ƙirga waɗanda suke sujada cikin haikalin"
a yi da abu kamar mara amfani ne, ko a yi tafiya akan sa
"wata 42"
Allah ya cigaba da magana da Yahaya.
"na kwanaki dubu daya da ɗari biyu da sittin" ko "na kwanaki ɗari goma sha biyu da sittin"
Za a iya bayyana dallilin da zasu sanye tsummokin. AT: "kwanankin, suna sa mummunan kaya na makoki" ko "kwanakin: zasu saka kaya mai kaikayi su nuna cewa suna cikin mugun ɓacin rai"
Itatuwan zaitun biyu da fitili biyu alama ne na waɗannan mutanen. AT: "Itatuwa zaitun biyu da fitili biyu da suka tsaya a gaban Ubangijin duniya na madadin waɗannan shaidun ne"
Yahaya na son masu karatun su samu sani game da su domin sheƙaru da suka wuce da dama wani annabi ya yi rubutu akan su. AT: "itatuwan zaitun biyu da kuma fitilu biyu, da aka yi magana a cikin littafin, cewa"
Domin wannan game da abin da zasu faru nan gaba ne, za a iya a faɗan su a kalmomi na gaba. AT: "wuta na fitowa daga bakinsu ta lashe makiyansu"
Ana magana game da ƙonewar wuta kamar dabba ne da zai iya cinye su. AT: "wuta ... ta lashe makiyansu" ko "wuta ... zai ƙone dukkan makiyansu"
Yahaya yayi maganar sama kamar yana da ƙofa ne da ake buɗewa domin a sa ruwa faɗowa ko a kulle domin a hana ruwa. AT: "a hana ruwa faɗowa daga sama"
"su canja"
Yahaya ya yi magana game da annoban nan kamar sanda ce da wani zai iya ya bugi duniya da ita. AT: "ya auko da kowace irin damuwa a duniya"
Wannan siririn rami ne mai zurfi sosai. AT:1) ramin da ba karshe; ya cigaba da gangara ƙasa kuma ba iyaka, ko 2) zurfin ramin yayi kamar bashi da karshe ne. AT: [9:1]
Wannan na nufin jikunan shaidu guda biyun nan.
Birnin na da hanyoni fiye da ɗaya. Wannan fili ne inda jama'a zasu iya ganin su. AT: "a wata hanyar babban birnin" ko "a ainihin hanyar babban birnin"
"kwana 3 da rabin kwana guda" ko "kwana 3.5" "kwana 3,1/2"
Wannan alaman rashin biyayya ne.
"zasu yi murna cewa shaidu guda biyun sun mutu"
Wannan yana nuna yadda mutanen suka yi murna.
Domin wannan dalilin ne mutane zasu yi murna saboda shaidun sun mutu.
Ana maganan samun dama domin yin nufashi kamar wani abu ne da zai iya zuwa cikin mutane. AT: "Allah zai saka shaidu guda biyun nan suyi nunfashi, kuma su zama rayayyu"
Ana maganan tsoro kamar abu ne da zai iya faɗi a kan mutane. AT: "Waɗanda suka gan su zasu ji matsananciyar tsoro"
Mai yiwuwa wannan yana nufin 1) shaidu biyun nan zasu ji, ko 2) mutanen zasu ji abin da ake faɗa wa shaidu biyun nan.
Kalman nan "murya" na nufin wanda yake maganan ne. AT: "wani ya masu magana da ƙarfi daga sama"
"yace wa shaidu biyun nan"
"mutane 7,000"
"wanda basu mutu ba" ko "waɗanda suke kuma yin rayuwa"
"suka faɗa cewa Allah na sama mai dauƙaƙa ne"
"Aka gama abu na biyu mai ban tsoro." AT: Dubi yadda aka juya "Annoba ta fari ta wuce" [Wahayin Yahaya 9:12]
Zuwan na nufin kasancewa nan gaba ne. AT: "Annoba na ukun zai faru ne a kwanakin nan"
Wannan shine mala'ika na bakwai na karshe. "na bakwai" [Wahayin Yahaya 8:1] AT: "mala'ika na karshe"
Kalmomin nan "muryoyi masu ƙara" na nufin wanɗanda suka yi magana da ƙarfi suka ce"
A nan "mulki" na nufin ikon yin mulki a duniya ne. AT: "Ikon yin mulki a duniya ... iko da ya zama na Ubangiji da Almasihunsa
Wannan na nufin kowa ne a duniya. AT: "kowa a cikin duniya"
"Ubangijin mu da Almasihunsa masu mulki ne yanzu a duniya"
"dattawa 24." AT: [Wahayin Yahaya 4:4]
Wannan ƙarin magana ce da take nufin sun faɗi rub da cikinsu a ƙasa. AT: "suka durƙusa" [Wahayin Yahaya 4:10]
AT: kai, Ubangiji Allah, mai mulki bisan kowa. Kai ne wanda yake a yanzu, da wanda yake a da"
"wanda ya kasance" ko "wanda ya rayu"
"wanda ya dinga kasancewa" ko "wanda ya dinga rayuwa"
Za a iya yin bayanin abun da Allah ya yi da ikon sa mai girma. AT: "ka yi nassara da ikon ka kan duk wanda yayi tawaye da kai"
"suka yi fushi sosai"
Ana maganan kasancewan abu a yanzu kamar abun ya riga ya zo ne. AT: "ka yi shirin nuna fushin ka"
Ana maganan kasancewan abu a yanzu kamar abun ya riga ya zo ne. AT: "Lokaci ya kai" ko "Yanzu ne lokacin"
Waɗannan sun yi bayanin abin da "bayin ka" na nufi. Babu bambanci a tsakanin waɗannan kungiyan mutane ukun gaba ɗaya. Anbawan suma masu ba da gaskiya ne kuma suna jin tsoron sunan Allah. "Suna" a nan magana ce da ke nuna Yesu Almasihu ne. AT: "annabawa, da masu ba da gaskiya, da waɗanda suka ji tsoron ka" ko "da annabawa da kuma su waɗanda suka ba da gaskiya suka kuma ji tsoron sunan ka"
AT: "Sai wani ya buɗe haikalin Allah da ke sama"
AT: "Na ga akawatin alkawarinsa a cikin haikalinsa"
Yi amfani da harshen ka ta wurin yin bayanin yadda walkiyar take a duk lokacin da ta bayyana. [4:5]
Haka ne haradu ke yin ƙara da ƙarfi. Yi amfani da harshen ka ta wuring yin bayanin yadda ƙarar aradun take. [4:5]
1Aka ga wata babbar alama a sama: wata mace ta yi lullubi da rana, kuma wata na karkashin kafafunta; rawanin taurari goma sha biyu na bisa kanta. 2Tana da ciki, tana kuma kuka don zafin nakuda - a cikin azabar haihuwa.3Sai aka ga wata alama cikin sama: Duba! Akwai wani katon jan maciji mai kawuna bakwai da kahonni goma, sai kuma ga kambi guda bakwai bisa kawunansa. 4Wutsiyarsa ta share daya bisa uku na taurari a sama ta zubo su kasa. Diragon nan ya tsaya a gaban matar da ta kusan haihuwa, domin lokacin da ta haihu ya lankwame yaronta.5Sai ta haifi da, namiji, wanda zai yi mulkin dukan al'ummai da sandar karfe. Aka fizge yaron ta zuwa ga Allah da kursiyinsa, 6matar kuwa ta gudu zuwa jeji inda Allah ya shirya mata domin a iya lura da ita kwanaki 1, 260.7A lokacin sai yaki ya tashi a sama. Mika'ilu da mala'ikunsa suka yi yaki da diragon, sai diragon da nasa mala'iku suka yake su su ma. 8Amma diragon ba shi da isashen karfin da zai ci nasara. Don haka, shi da mala'ikunsa ba su kara samun wuri a sama ba. 9Sai aka jefa katon diragon nan tare da mala'ikunsa kasa, wato tsohon macijin nan da ake kira Iblis ko Shaidan wanda ke yaudarar dukan duniya.10Sai na ji wata murya mai kara a sama: "Yanzu ceto ya zo, karfi, da mulkin Allahnmu, da iko na Almasihunsa. Gama an jefar da mai sarar 'yan'uwanmu a kasa - shi da yake sarar su a gaban Allah dare da rana.11Suka ci nasara da shi ta wurin jinin Dan Ragon da kuma shaidar maganarsu, gama ba su kaunaci ransu ba, har ga mutuwa. 12Don haka, yi farinciki, ya ku sammai da duk mazauna da ke cikinsu. Amma kaito ga duniya da teku saboda iblis ya sauko gare ku. Yana cike da mummunan fushi, domin ya san lokacin sa ya rage kadan.13Da diragon ya ga an jefar da shi kasa, sai ya fafari matar nan da ta haifi da namiji. 14Amma aka ba matar nan fukafukai biyu na babbar gaggafa domin ta gudu zuwa inda aka shirya mata a jeji. A wannan wuri ne za a lura da ita na dan lokaci, da lokatai, da rabin lokaci - a lokacin da babu macijin.15Macijin ya kwararo ruwa daga bakin sa kamar kogi, don ya kawo ambaliyar da zai kwashe ta. 16Amma kasa ta taimaki matar. Kasa ta bude bakinta ta hadiye kogin da diragon ya kwararo daga bakinsa. 17Sai diragon ya fusata da matar, sai ya tafi ya yi yaki da sauran zuriyarta, wadanda suka yi biyayya da umarnan Allah suna kuma rike da shaida game da Yesu. 18Sai diragon ya tsaya a kan yashi, a gaban teku.
Yahaya ya fara kwatanta macen da ta bayyana a cikin wahayinsa.
AT: "babbar alama ta bayyana a cikin sama" ko "Ni, Yahaya, na gan babban alama a cikin sama"
AT: "macen da ta yi lulluɓi da rana da ta ke da kuma wata a ƙarƙashin ƙafafunta"
Wannan atakaice makamancin rawani ne da aka yi shi daga ganyen laurel ko reshen zaitun, amma tare da taurari goma sha biyu a haɗe a ciki.
"taurari goma sha biyu"
Yahaya ya kwatanta macijin da ya gani a cikin wahayinsa.
Wannan babban, halitta ne mai rarrafe mai kuma ban tsoro, kamar kadangare. Alamar masifa ne da bala'i ga mutanen Yahudawa.
"Da wutsiyarsa ne ya share ɗaya bisa uku na taurari"
"daya bisa uku." Dubi yadda kun fasara wannan a cikin 8:7.
An yi maganar yin mulki da tsanani kamar yin mulki da sandar ƙarfe ne. Dubi yanda kun fasara magana makamanci sa a 2:27.
AT: "Allah ya ɗauki yaron ta da sauri wa kansa"
"na kwanaki dubu ɗaya da dari biyu da sittin" ko "na kwanaki dari goma sha biyu da sittin"
Yahaya ya yi amfani da wannan kalma domin ya sa dabara a labarinsa don ya gabatar da wani abin da ke faruwa a cikin wahayinsa.
"Don haka diragon da mala'ikunsa ba su iya zama a cikin sama ba"
Ana iya ba da labari game da ibilis a cikin jumla dabam bayan maganar cewa an jefa shi zuwa duniya. AT: "an jefa diragon zuwa duniya, kuma an jefa mala'ikunsa tare da shi. Shi ne tsohon Ibilis wadda yake yaudaran duniya kuma ana kiran sa Ibilis ko Shaiɗan"
AT: "Allah ya jefa babban diragon ... da mala'ikunsa daga sama ya kuma turo su zuwa duniya"
Kalmar "Ni" na nufin Yahaya.
Kalmar "murya" ya na nufin wanin da ya ke magana. AT: "Na ji wani ya na magana da ƙarfi daga sama"
An yi maganar ceton mutane da Allah ya na yi ta wurin ikonsa kamar cetonsa da ikonsa abubuwa ne da sun zo. An yi maganar mulkin Allah da ikonsa kamar sun zo ne. AT: "Yanzu Allah ya ceci mutanensa da ikonsa, Allah ya na mulki kamar sarki, kuma Almasihunsa ya na da dukka iko"
"ya soma kasancewa" ko "ya bayyana" ko "ya zama gaskiya." Allah ya na bayyana waɗannan abubuwa domin lokacin da zai faru ya "zo." Ba wai ba su kasance tun farko ba ne.
Wannan ne diragon da an jefa a cikin 12:0.
An yi maganar 'yan'uwa masubi kamar su 'yan'uwa ne. AT: "'yan'uwanmu masubi"
An yi amfani da waɗannan sashen ranaku domin a nuna "dukka lokaci" ko "da rashin dainawa"
"Suka ci nasara da mai kushewa"
Jinin na nufin mutuwarsa. AT: "domin ragon ya zub da jininsa ya kuma mutu domin su"
Ana iya bayyana kalmar "shaida." Ana iya sa a bayyane wanda su ke shaida akai. AT: "ta wurin abin da suka ce a lokacin da sun shaida wa waɗansu game da Yesu"
Masubi sun faɗi gaskiya game da Yesu, ko da shike sun san cewa maƙiyansu za su iya kashe su domin haka. AT: "amma sun cigaba da shaida ko da shike sun san cewa mai yiwuwa za su mutu don haka"
An yi maganar Ibilis kamar abu ne, kuma an yi maganar fushi kamar ruwa ne da ke iya kasance wa a cikinsa. AT: "yana mummunan fushi"
AT: "Diragon ya gane cewa Allah ya jefar da shi da ga sama ya kuma turo shi zuwa duniya"
"ya fafari matan"
"shekaru uku da rabi"
Wannan wata hanya ce na kiran diragon.
Wannan abu ɗaya ne da diragon wanda an ambata da farko a cikin 12:9.
Ruwan ya gudu daga bakinsa kamar gudun kogi. AT: "dayawa"
"ya wanke ta"
An yi maganar duniya kamar abu mai rai ne, kuma an yi maganar rami a cikin duniya kamar baki ne da na iya shanye ruwa. AT: "Rami a kasa ya bude sai kuma ruwa ya tafi cikin ramin"
Ana iya fasara kalmar "shaida." AT: "cigaba da shaida game da Yesu"
1Sai na ga wani dabba yana fitowa daga teku. Yana da kahonni goma da kawuna bakwai. A kan kahonninsa akwai kambi goma, a kan kowanne kansa akwai suna na sabo. 2Wannan dabban da na gani yana kama da damisa, kafafunsa kuma kamar na beyar, bakinsa kuma kamar na zaki. Wannan diragon ya ba shi karfinsa, da kursiyinsa da ikonsa mai girma na sarauta.3Daya daga cikin kawunan dabban ya yi kamar an kashe shi, amma rauninsa mai tsanani ya warke. Sai dukan duniya ta yi mamaki a yayin da suke bin dabban. 4Su ma suka yi wa diragon sujada, domin ya ba dabban ikonsa. Suka yi wa dabban sujada suna ta cewa, "Wanene kamar dabban? Wa kuma zai iya yin fada da shi?"5Aka ba dabban baki da zai iya fadin kalmomin fahariya da sabo. Ya sami izini na zartar da iko har wata arba'in da biyu. 6Sai dabban ya bude bakinsa yana maganganun sabo ga Allah: yana sabon sunansa, da mazauninsa, da kuma wadanda ke zaune a sama.7Aka yarje wa dabbar ya yi yaki da masu bi ya kuma yi nasara da su. An kuma ba shi iko bisa kowacce kabila, da jama'a, da harshe, da al'umma. 8Dukan wadanda ke zaune a duniya za su yi masa sujada, dukan wadanda tun hallitar duniya ba a rubuta sunayensu a littafin rai na Dan Rago ba, wanda aka yanka.9Idan wani yana da kunne, bari ya ji. Duk wanda za a dauke shi zuwa bauta, ga bauta zai tafi. 10Duk wanda za a kashe da takobi, da takobi za a kashe shi. Wannan kira ne na dauriya, hakuri da bangaskiya ga wadanda suke da tsarki.11Sai na ga wani dabban na fitowa daga cikin kasa. Yana da kahonni biyu kamar na dan rago, ya kuma yi magana kamar maciji. 12Ya zartar da dukan ikon dabban na farko a gabansa, ya kuma sa duniya da duk mazaunanta su yi wa dabban nan na farko sujada, wanda aka warkar masa da rauni mai kamar na ajali.13Ya yi manyan al'ajibai. Har ya sa wuta ta sauko kasa daga sama a gaban mutane. 14Ta wurin alamu da aka yarje masa ya yi, ya yaudari mazaunan duniya. Ya ce masu su yi wata siffa don girmama dabban da yake da raunin takobi, amma duk da haka ya rayu.15Aka yarje masa ya ba da numfashi ga siffar dabban domin siffar ta yi magana, ta kuma sa a kashe duk wadanda suka ki yin sujada ga dabban. 16Ya kuma tilasta kowa, kanana da manya, mawadata da matalauta, masu yanci da bayi, su karbi alama a hannun dama ko kuma a goshi. 17Ba shi yiwuwa wani ya saya ko ya sayar sai dai yana da alamar dabban, wato lambar nan da ke wakiltar sunansa.18Wannan na bukatar hikima. Idan wani yana da hikima, sai ya kididdige lambar dabban nan. Gama lambar ta mutum ce. Lambarta itace 666.
Yahaya ya fara kwatanta dabba da ya bayyana a gare shi cikin wahayinsa. Kalmar "Ni" a nan ya na nufin Yahaya.
Wannan babban, halitta ne mai rarrafe mai kuma ban tsoro, kamar kadangare. Alamar masifa da bala'i ne ga mutanen Yahudawa. Ana ƙiran whi wannan diragon Shaiɗan da kuma Ibilis." Dubi yanda an fasara wannan a cikin 12:3.
Diragon ya sa dabban ya yi karfi kamar yadda yake. Bai rasa karfinsa ba, ko da shike ya ba wa dabban.
Waɗannan kalmomi ne da ke nufin ikonsa, kuma an nanata su ne domin a nuna cewa ikon babba ne.
A nan kalmar "kursiyi" ya na nufin ikon mulkin diragon kamar sarki. AT: "girman ikonsa" ko kuma "ikonsa na yin mulki kamar saiki"
AT: "amma rauninsa mai tsanani ya warke"
"mugun rauni." Wannan irin ciwo ne da ya isa ya sa mutum ya mutu.
Kalmar "duniya" ya na nufin mutanen da ke cikin duniya. AT: "Dukkan mutanen da ke cikin duniya"
"yi biyayya da dabban"
"ya sa dabban ya samu yawan iko kamar yanda yake da shi"
Wannan tambaya ya nuna irin mamakin da sun ji game da dabban. AT: "Babu wadda ya ke da iko kamar dabban!"
Wannan tambaya ya nuna irin tsoron ikon dabban da mutanen su ji. AT: "Ba bu wanda zai iya yin faɗa da dabban ya kuma yi nasara!"
AT: "Allah ya ba dabban ... Allah ya ba dabban izini"
Ba da baki, na nufin iya magana. AT: "An bar dabban ya yi magana"
"watanni arba'in da biyu"
"faɗin abubuwan rashin ladabi game da Allah"
Waɗannan su na faɗan yadda dabban ya yi maganan saɓo ga Allah.
AT: "Allah ya ba wa dabban iko"
Wannan ya na nufin cewa mutane daga kowane harshuna su na a haɗe. Dubi yadda kun fasara irin wannan tsarin sunaye a cikin 5:9.
"yi wa dabban sujada"
Wannan jumla ya bayyana waɗanda ke duniya da za su yi wa dabban sujada. AT: "waɗanda Ragon bai rubuta sunayensu ba ... a cikin Littafin rai" ko kuma "waɗanda sunayensu babu ... a cikin Littafin rai"
"a lokacin da an hallice duniya"
"Rago" karamin tunkiya ne. An yi amfani da shi don a kwatanta Almasihu ne. Dubi yanda kun fasara wannan a cikin 5:6.
AT: "wanda mutanen sun yanka"
An yi maganar niya a ji kamar kasancewa da kunne. Dubi yadda kun fasara irin jumlan nan a cikin 2:7. AT: "Bari wanda ya na da niyar ji, ya ji" ko "Idan ku na da niya, ku ji"
Wannan ya na nufin cewa wani ya faɗi wanda za a ɗauka. Idan a na so, masu juyi su na iya faɗin wanda ya yi maganan. AT: "Idan Allah ya faɗa cewa a ɗauki wani" ko "Idan nufin Allah ne cewa a ɗauki wani"
Ana iya bayyana kalmar "bauta" da kalmar "kama." AT: "Idan nufin Allah ne maƙiya su kama wani mutum"
Ana iya bayyana kalmar "bauta" da kalmar "kama." AT: "za a kama shi" ko "makiya za su kama shi"
AT: "Idan nufin Allah ne maƙiya su kashe wani mutum da takobi"
Takobi na wakilcin yaƙi. AT: "a cikin yaƙi"
AT: "makiyan za su kashe shi"
"Dole ne tsarkaka mutanen Allah su yi hanƙuri su kuma zama amintattu"
Yahaya ya fara kwatanta wani dabba wanda ya bayyana a cikin wahayinsa.
An yi maganan zance mara daɗi kamar ƙugin diragon. AT: "ya yi magana da tsawa kamar yanda diragon na magana"
"kowane mutum a duniya"
AT: "wanda ya ke da rauni mai kamar na ajali da ya warke"
"mugun rauni." Wannan irin ciwo ne da ya isa ya sa shi ya mutu.
"Dabban daga duniya ya yi"
AT: "Allah ya yarda wa dabban daga duniya"
A nan kalmar "numfashi" na wakilcin rai. AT: "ba da rai wa siffar dabban"
Wannan siffar dabba na farko ne da an ambata.
"kashe kowane mutum da ya ƙi yin sujada ga dabba na farko"
"Dabban daga duniya ya kuma tilasta kowa"
"Mutane na iya saya ko sayad da abubuwa idan su na da alama na dabban ne kawai." Ana iya bayyana umurni da dabba wanda yake daga duniya ya bayar. AT: "Ya umurta cewa mutane na iya saya ko sayad da abubuwa idan su na da alamar dabban ne kawai"
Wannan alama ce da ya nuna cewa mutumin da ya karba shi ne na yi wa dabban sujada.
"Ana bukatar hikima" ko "ya kamata ku yi wayo game da wannan"
Ana iya juya kalmar "hikima" da "fahimta." AT: "Idan wani ya iya fahimtan abubuwa"
"ya gane abin da lambar dabban ke nufin" ko "ya fahimci abin da lambar dabban ke nufin"
AT: 1) lambar ya na wakilcin mutum ɗaya ko 2) lambar ya na wakilcin dukkan 'yan Adam.
1Sai na duba na ga Dan Ragon yana tsaye a kan Dutsen Sihiyona. Tare da shi akwai mutum dubu dari da arba'in da hudu wadanda aka rubuta sunansa da sunan Ubansa a goshinsu. 2Na ji wata murya daga sama mai kara kamar kogin ruwa mai gudu da kuma aradu mai kara. Muryar da na ji ta yi kama da masu molo suna kada molonsu.3Suka raira sabuwar waka a gaban kursiyin da kuma gaban rayayyun halittun nan hudu, da kuma dattawan. Ba mai iya koyon wakar nan sai dai mutum 144, 000 nan wadanda aka fanso daga duniya. 4Wadannan sune wadanda basu kazantar da kansu da mata ba, gama sun kebe kansu da tsarki daga halin jima'i. Wadannan ne ke bin Dan Ragon duk inda ya tafi. Aka fanso su daga cikin mutane domin su zama nunan fari domin Allah da Dan Ragon. 5Ba a iske karya a bakinsu ba; ba su da aibi.6Na ga wani mala'ika na firiya a tsakiyar sararin sama, wanda yake da madawwamin sako na labari mai dadi domin a sanar da ita ga mazaunan duniya - ga kowacce al'umma, da kabila, da harshe, da kuma jama'a. 7Yayi kira da babbar murya, "Ku ji tsoron Allah, ku daukaka shi. Gama sa'arsa ta hukunci ta yi. Yi masa sujada, shi wanda ya yi sama da kasa, da teku, da kuma mabulbular ruwa."8Sai wani malai'ka, malaika na biyu, ya biyo yana cewa, "Ta fadi, Babila mai girma ta fadi, wadda ta rinjayi dukan al'ummai su sha ruwan inabin fasikancinta."9Wani mala'ika - na uku - ya biyo su da murya mai karfi yana cewa, "Duk wanda ya yi sujada ga dabban da kuma siffarsa, ya karbi alama a goshinsa ko a hannunsa, 10shi ma zai sha daga ruwan inabin fushin Allah, ruwan inabi da aka zuba tsantsa cikin kokon fushinsa. Wanda ya sha shi za a azabtar da shi da wuta, da farar wuta, a gaban tsarkakan mala'ikun Allah da kuma Dan Ragon.11Hayaki daga azabarsu yana tashi sama har abada abadin, kuma ba su da hutu dare ko rana - wadannan masu sujada ga dabban da siffarsa da kuma dukan wadanda suka karbi alamar sunansa. 12Wannan shine kira domin hakurin jimrewa na wadanda ke da tsarki, wadanda suke biyayya ga dokokin Allah da bangaskiya cikin Yesu."13Na ji murya daga sama cewa, "Rubuta wannan: Masu albarka ne matattu da suka mutu cikin Ubangiji." Ruhu yace, 'I' domin sun huta daga wahalarsu, gama ayyukansu na biye da su."14Na duba sai ga farin gajimare. Zaune a kan gajimaren akwai wani kamar Dan Mutum. Yana da kambin zinariya a kansa da lauje mai kaifi a hannunsa. 15Sai wani malaika ya fito daga haikalin, ya yi kira da murya mai karfi ga wanda ke zaune kan gajimare: "Dauki laujenka ka fara girbi, domin lokacin girbin duniya ya yi." 16Sai wanda ke zaune a kan gajimaren ya wurga laujensa bisa kan duniya, aka kuma girbe duniya.17Wani mala'ika ya fito daga haikali a sama, shi ma yana da kakkaifan lauje. 18Sai wani mala'ika ya fito daga bagadin kona turare, wanda yake da iko kan wutar. Ya yi kira da murya mai karfi ga wanda yake rike da kakkaifan lauje, "Ka dauki kakkaifan laujenka ka tattara nonnan innabi daga itacen inabin na duniya, gama inabin ya nuna."19Mala'ikan ya jefa laujensa duniya ya tattara girbin inabin duniya. Ya zuba shi a cikin babbar taskar wurin matsar ruwan inabi na fushin Allah. 20Aka tattake wurin matsar inabin a bayan birni, jini ya yi ta gudu daga wurin matsar inabin, ya kai kamar tsawon linzami a bakin doki, har mil dari biyu.
Yahaya ya fara kwatanta ɗayan sashin wahayinsa. Akwai masubi dubu ɗari da arba'in da hudu a tsaye a gaban Ragon.
Kalmar "Ni" ya na nufin Yahaya.
"Rago" karamin tunkiya ne. An yi amfani da shi a nan domin kwatancin Almasihu. Dubi yanda kun juya wannan a cikin 5: 6.
"dubu ɗari da arba'in da hudu." Dubi yanda kun juya wannan a cikin 7:4.
AT: "wanda Ragon da Ubansa sun rubuto sunayensu a goshinsu"
Wannan muhimmin laƙabi ne wa Allah wadda ya na kwatanta dangantaka tsakanin Allah da Yesu.
"ƙara daga sama"
"mutane 144,000 su ka raira sabuwar waƙa." Wannan ya bayyana irin ƙaran da Yahaya ya ji. AT: "Ƙaran nan sabuwar waƙa ne da suka raira"
"rayayyen mutum" ko "abu mai rai." Dubi yanda kun juya "rayayyun halittu" a cikin 4:6
Wannan ya na nufin dattawa ashirin da hudu a kewaye da kursiyin. Dubi yanda kun juya "dattawa" a cikin 4:4.
AT: 1) "basu taɓa yin fasikanci da mace ba" ko 2) "basu taɓa yin jima'i da mace ba." Yin abun ƙazanta da mace na iya zama alama ne na bautar gumakai.
AT: 1) "basu yi jima'i da macen da ba matar su ba" ko kuma 2) " basu san mace ba."
An yi maganar aikata abin da Ɗan Ragon na yi kamar bin shi. AT: "su na yin duk abin da Ɗan Ragon na yi" ko "su na biyayya da Ɗan Ragon"
"Nunan fari" na nufin farkon bayaswa da za a yi wa Allah a bikin girbi. AT: "aka saya daga cikin sauran mutane kamar biki na musamman na ceto"
"Bakinsu" na nufin abin da sun faɗa. AT: "Basu taba yin ƙarya ba a lokacin da suke magana"
Wannan ya na nufin cewa mutane daga kowane harshe su na a haɗe. Dubi yadda kun fasara wannan irin tsarin sunaye a cikin 5:9.
A nan "sa'a" na wakilcin lokacin da an zaɓa don wani abu, kuma "zuwan" sa'a magana ne na lokacin da an zaɓa. Ana iya bayyana maganar "hukunci." AT: "yanzu ne lokacin da Allah ya zaɓa don hukunci" ko "yanzu ne lokacin da Allah zai hukunta mutane"
Mala'ika ya yi maganar hallakar Babila kamar ta faɗi. AT: "Babila mai girma ta faɗi"
"Babila babban gari" ko "muhimmin garin Babila." Mai yiwuwa wannan alama ce na garin Roma, wadda ke da girma, arziki, da kuma zunubi.
An yi maganar Babila kamar mutum ne, a maimakon gari da ke cike da mutane.
Wannan alama ne na kasancewa a cikin fasikancinta. AT: "zama da fasikanci kamar ita" ko "bugu kamar ta na cikin zunubin zina"
An yi maganar Babila kamar karuwa ce wanda ta sa mutane yin zunubi tare da ita. Wannan na iya zama da ma'ana biyu: fasikanci a zahiri ko kuma bautar alolin ƙarya.
"da ƙarfi"
Shan ruwan inabin fushin Allah alama ce ta hukunci daga Allah. AT: "zai kuma sha daga ruwan inabin dake wakilcin fushin Allah"
AT: "da Allah ya zuba da cikakken ƙarfi"
Wannan kokon, wanda yake a madadin alama ne, ya riƙe ruwan inabi wanda ke wakilcin fushin Allah.
"azabarsu" ya na nufin wutan da ya na azabtar da su. AT: "Hayaƙi daga wutan da ya na azabtar da su"
"babu sauƙi" ko "azaban ba ya tsayawa"
An yi amfani da waɗannan sashi biyu don a bayyana dukka lokaci. AT: "abada abadin"
"Dole ne tsarkaka mutanen Allah su yi jimriyan haƙuri da amincewa." Dubi yanda kun juya irin wannan jumla a cikin 13:10.
"waɗanda suka mutu"
"waɗanda suka mutu suke kuma haɗe da Ubangiji." Wannan na iya nufin mutane da makiyansu suka kashe su. AT: "waɗanda sun mutu domin su na a haɗe da Ubangiji"
wuya da azaba
An yi maganar waɗannan ayyuka kamar su na da rai kuma su na iya bin waɗanda sun aikata su. AT: 1) "waɗansu za su san kyawawan ayyukan da waɗannan mutanen suka yi" ko kuma 2) "Allah zai albarkace su don ayyukansu"
Wannan magana ya na kwatanta mutum, wani da ya yi kama da mutum. Dubi yanda kun juya wannan a cikin 1:13.
Wannan kamar reshen zaitun ko ganyen laurel ne, da an yi shi da zinariya. Ana ba da misalai da rawani da an yi daga ganye wanda ake ba wa masu nasara a wasan guje-guje don su sa a kawunansu.
kayan aiki ne da yake a lanƙwashe wanda ake yin amfani da shi don yankar ciyawa, hatsi da itacen inabi
"fito daga haikalin sama"
An yi maganar kasancewa a lokacin kamar ya zo.
AT: "ya girbe duniyan"
A nan "iko a kan" na nufin alhakin kula da wuta.
Wannan na nufin abu ɗaya ne.
" babbar taskar wurin matsa ruwan inabi inda Allah zai nuna fushinsa"
"kamar tsawon linzami a bakin doki"
dabara ne da an yi shi daga siririn fata wadda yake kewaye kan doki kuma a na amfani da shi don bi da doki
"stadia dubu ɗaya da ɗari shida" ko kuma "stadia ɗari goma sha shida." "filin wasanni" mita 185 ne. Wannan na iya zama kamar "kilomita 300" ko "mil 200" a awun na zamani.
1Sai na ga wata alama cikin sama, babba mai ban mamaki: Akwai mala'iku bakwai rike da annobai bakwai, wadanda sune annobai na karshe domin da su ne fushin Allah zai cika.2Na ga wani abin da da ya bayyana mai kama da tekun gilashi mai haske garwaye da wuta. Tsaye a gefen tekun sune wadanda suka ci nasara a kan dabban da siffarsa, da kuma lambar da ke wakiltar sunansa. Suna rike da molayen da Allah ya ba su.3Suna rera wakar Musa, bawan Allah, da wakar Dan Rago: "Ayyukan ka manya ne da ban mamaki, Ubangiji Allah, Mai iko duka. Adalci da gaskiya hanyoyinka ne, Sarkin al'ummai. 4Wanene ba zai ji tsoron ka ba, Ubangiji, ya kuma daukaka sunanka? Domin kai kadai ne mai tsarki. Dukan al'ummai za su zo su yi sujada a gabanka domin an bayyana ayyukan ka na adalci."5Bayan wadannan abubuwa na duba, kuma aka bude haikalin alfarwar shaida a cikin sama. 6Daga wuri mafi tsarki mala'iku bakwai masu rike da annobai bakwai suka zo. Suna sanye da tufafi masu tsabta, da lallausar linin mai haske, suna kuma da damarar zinariya a kirjinsu.7Daya daga cikin rayyayun halitu hudu ya ba mala'iku bakwai tasoshin zinariya bakwai cike da fushin Allah wanda yake raye har abada abadin. 8Haikalin ya cika da hayaki daga daukakar Allah da kuma ikonsa. Ba wanda ya iya shigarsa har sai da annoban nan bakwai na mala'ikun nan bakwai suka cika.
Wannan aya ya taƙaita abinda zai faru a ciki 15:16-16:21.
Waɗannan kalmomi suna da ma'ana kusan iri ɗaya kuma ana amfani da su don nanaci. AT: "wani abu da ya na ba ni mamaki sosai"
"mala'iku bakwai da su na da ikon aika annobai bakwai a duniya"
"kuma bayan su, ba za a sake wani annoba ba"
AT: "domin waɗannan annobai ne za su cika fushin Allah"
Ana iya bayyana yadda ya na nan kamar gilashi ko teku. Ma'anoni masu yiwuwa suna kamar haka 1) an yi maganar teku kamar gilashi. AT: "tekun da ya yi sumul kamar gilashi" ko 2) gilashi idan an yi maganar sa kamar teku ne. Dubi yadda an juya wannan a cikin 4:6. AT: "gilashi da an baza kamar teku"
Ana iya bayyana yanda suka ci nasara a kan lambar. AT: "waɗanda suka ci nasara a kan dabban da siffarsa ta wurin rashin bauta masu"
Ana iya sa wa a bayyane yanda sun ci nasara a kan lamban. AT: "a kan lamba da na wakilcin sunansa ta wurin rashin sa alama da wannan lambar"
Wannan na nufin lamba da an kwatanta a cikin 13:18.
"Waɗanda sun ci nasara a kan dabban su na rera waƙa"
An yi amfani da wannan tambaya domin a nuna mamakinsu a kan ɗaukaka da girman Ubangiji. Ana iya bayyana shi kamar magana mai shauki. AT: "Ubangiji, kowa zai ji tsoronka ya kuma ɗaukaka sunanka!"
"sunanka" na nufin Allah. AT: "ɗaukaka ka"
AT: "ka sa kowa ya san game da ayyukan adalcinka"
Mala'iku bakwai masu rike da annobai bakwai sun fito daga tsarkakken wuri. An riga an yi maganarsu a cikin 15:1.
Ana ganin waɗannan mala'iku rike da annobai bakwai domin a cikin 15: 7 an ba su tasoshi bakwai a cike da fushin Allah.
kaya mai kyau, da kuma tsada da ana yinsa daga abu mai siffar ganye.
Damara wani kaya mai ado ne wanda a na sa wa a jiki.
"rayayyen mutum" ko "abu mai rai." Dubi yanda kun juya "rayayyun halittu" a cikin 4:6
Ana iya bayyana kamanin ruwan inabin a cikin tasoshin. A nan kalmar "fushi" ya na nufin hukunci. Ruwan inabi alama ne na hukunci. AT: "tasoshin zinariya bakwai cike da ruwan inabi wadda ya na wakilcin fushin Allah"
"sai da mala'ikun nan bakwai su ka gama turo da annoban nan bakwai a duniya"
1Na ji babban murya na kira daga cikin haikali tana ce wa malai'iku bakwai, "Ku je ku zuba tasoshi bakwai na fushin Allah a kan duniya."2Mala'ika na fari ya je ya zuba tasarsa a kan duniya; munanan gyambuna masu zafi suka fito wa mutane wadanda suke da alamar dabbar, wadanda suka bauta wa siffarsa.3Mala'ika na biyu ya zuba tasarsa cikin teku. Ya zama jini, kamar jinin wanda ya mutu, kuma kowane abu mai rai da ke cikin tekun ya mutu.'4Malaika na uku ya zuba tasarsa a cikin rafuffuka da mabulbulan ruwa, sai suka zama jini. 5Na ji mala'ikan ruwaye ya ce, "Kai mai adalci ne - wanda ya ke yanzu wanda yake kuma a da, Mai Tsarkin nan, domin ka shari'anta wadannan abubuwa. 6Domin sun zubar da jinin masu ba da gaskiya da annabawa, ka basu jini su sha; shine abinda da ya dace da su. 7Na ji bagadi ya amsa, "I, Ubangiji Allah Mai iko duka, shari'un ka gaskiya ne da adalci."8Mala'ika na hudu ya zuba tasarsa a kan rana, kuma aka ba shi izini ya kone jama'a da wuta. 9Suka kone da zafi mai tsanani, kuma suka sabi sunan Allah, wanda ke da iko akan annobai. Ba su tuba ba ko su daukaka shi.10Sai malaika na biyar ya zuba tasarsa a kan kursiyin dabban, sai duhu ya rufe mulkinsa. Suka cicciji harsunansu saboda zafi. 11Suka yi sabon Allah na sama domin zafi da gyambunansu, suka kuma ki su tuba daga abin da suka yi.12Mala'ika na shida ya zuba tasarsa cikin babban rafi, Yufiretis. Ruwansa ya bushe domin a shirya hanya da sarakuna za su zo daga gabas. 13Na ga kazamun ruhohi uku suna kama da kwadin da ke fitowa daga bakin diragon, da makaryacin annabi. 14Gama su ruhohin aljanu ne masu aikata alamun ban mamaki. Sun fita za su wurin sarakunan dukan duniya domin su tattaro su wuri daya saboda yaki a babbar ranar Allah Mai iko duka.15("Duba! Ina zuwa kamar barawo! Mai albarka ne wanda ke zaune a fadake, wanda ke sanye da tufafinsa domin ba zai fita tsirara a ga tsiraicin sa ba.") 16Aka kawo su tare a wurin da ake kira Armagiddon da Ibraniyanci.17Mala'ika na bakwai ya zuba tasarsa cikin iska. Sa'annan babbar murya ta fito daga cikin haikali da kuma kursiyin, cewa, "An gama!" 18Aka yi walkiya, da kararraki masu tsanani, da aradu da babbar girgizar kasa - girgizar da ta fi kowacce da aka taba yi tun da 'yan adam suke a duniya, girgizar da girma ta ke. 19Babban birnin ya rabu kashi uku, kuma biranen al'ummai suka fadi. Sai Allah ya tuna da Babila mai girma, sai ya ba wancan birnin koko cike da ruwan innabi wanda aka yi daga fushinsa mai tsanani.20Kowanne tsibiri ya bace, sai ba a kara ganin duwatsun ba. 21Manyan duwatsun kankara, masu nauyin talanti, suka fado daga sama kan mutane. Suka zagi Allah domin annobar kankarar saboda annobar ta yi tsanani.
Yahaya ya cigaba da bayyana sashin wahayi game da mala'iku bakwai da annobai bakwai. Annobai bakwan ne tasoshi bakwai na fushin Allah.
Kalmar "Ni" ya na nufin Yahaya.
Ana iya bayyana siffar ruwan inabi a cikin tasoshin. Kalmar "fushi" a nan na nufin hukunci. Ruwan inabi alama ce ta hukunci. Dubi yanda kun juya jumla makamanci haka a cikin 15:7. AT: "tasoshi cike da ruwan inabi da ke wakilcin fushin Allah"
Kalmar "tasa" ya na nufin abin da ke cikinsa. AT: "zubo ruwan inabi daga tasarsa" ko "zuba fushin Allah daga tasarsa"
"ciwo masu zafi." Waɗannan na iya zama harbi ne daga cututuka ko lahani da bai riga ya warke ba.
Wannan alama ce da ya nuna cewa mutumin da ya karɓa ya na bauta wa dabban ne. Dubi yanda kun juya wannan a cikin 13:17.
Wannan ya na nufin dukka rafin ruwan gishiri da kuma babban teku.
Wannan ya na nufin dukka ruwa mai kyau.
AT: 1) Wannan na nufin mala'ika na uku wanda shi ne mai zuba fushin Allah a rafuffuka da mabulbulan ruwa ko 2) wannan wani mala'ika ne wanda ke lura da dukka ruwayen.
"Kai" ya na nufin Allah ne.
"Allah wanda yake, wanda yake kuma." Dubi yanda kun juya jumla makamanci haka a cikin 1:4.
A nan "zubar da jinin" na nufin kisa. AT: "sun kashe tsarkaka mutanen Allah da annabawa"
Allah zai sa mugayen mutanen su sha ruwayen da ya juya zuwa jini.
Mai yiwuwa kalmar "bagadi" a nan na nufin wani a bagadi. "Ni ji wani a bagadin ya amsa"
Yahaya ya yi maganar rana kamar mutum ne. AT: "aka kuma sa rana ya kone mutanen sosai"
AT: "tsananin zafin ya kone su sosai"
Sunan Allah a nan ya na wakilcin Allah. AT: "sun saɓa wa Allah"
Wannan jumla ya tuna wa masu karatu abin da sun riga sun sani game da Allah. Ya na taimako a wurin bayyana dalilin da mutane suke saɓa wa Allah. "Allah domin ya na da iko a kan waɗannan annobai"
Wannan ya na nufin iko sa akan waɗannan annobai da ke kan mutane, kuma da ikon hana annoban.
Wannan wurin ne da dabban ya na mulki. Ya na iya nufin hedkwatar ƙasarsa.
An yi maganar "duhu" a nan kamar wani abu ne mai kama da bargo. AT: "Ya zama duhu a duk mulkinsa" ko "dukka mulkinsa ya zama duhu"
Wannan ya na nufin mutane a cikin mulkin dabban.
AT: "Yufiretis. Ruwansa ya bushe" ko "Yufiretis, ya kuma sa ruwansa ya bushe"
Kwaɗo karamin dabba ne da na zama kusa da ruwa. Yahudawa sun ɗauke su a matsayin dabbobin mara tsarki.
Wannan babban, halitta ne mai rarrafe mai kuma ban tsoro, kamar kadangare. Alamar masifa dabala'i ne ga mutanen Yahudawa. An nuna diragon a cikin aya 9 a matsayin "Shaidan da kuma Ibilis." Dubi yanda an fasara wannan a cikin 12:3.
A aya 15, an je hutu daga ainahin labarin wahayin Yahaya. Waɗannan kalmomi ne da Yesu ya faɗa. Labarin ya cigaba a cikin aya 16.
Wannan ya na nuna cewa ba ya cikin sashin wahayin. Sai dai, wannan wani abu ne da Ubangiji Yesu ya faɗa. Ana iya bayyana wa da kyau cewa Ubangiji Yesu ya ce, kamar na cikin UDB.
Yesu zai zo a lokacin da ba wanda ke zato, kamar yadda ɓarawo na zuwa a lokacin da ba a zata ba. Dubi yanda kun juya jumla makamanci haka a 3:3.
An yi maganar yin rayuwa mai kyau kamar sanya tufafi. AT: "yin abin da ya kamata, kamar sanya tufafinsa"
Kalmar "su" a nan na nufin waɗansu mutane.
"ruhoyin aljanu su ka kawo sarakuna da sojojinsu tare"
AT: "wurin da mutane ke kira"
Wannan sunan wuri ne.
Wannan ya na nufin wani da na zaune a kan kursiyin ko wanin da ya na tsaye kusa da kursiyin ya yi magana da karfi. Ba a gane wanda na magana ba.
Ku yi amfani da yanda harshenku ke kwatanta yadda walƙiya yake a duk lokacin da ya bayyana. Dubi yanda kun juya wannan a cikin 4:5.
Waɗannan babban ƙara ne da aradu na yi. ku yi amfani da yanda harshenku ke kwatanta ƙaran aradu. Dubi yanda kun juya wannan a cikin 4:5.
AT: "Girgizan kasan ta raba babban birnin"
"Sai Allah ya tuna" ko "Sai Allah ya yi tunanin" ko "Sai Allah ya fara maida hankali a kan." Wannan ba ya nufin cewa Allah ya tuna wani abu da ya manta.
Ruwan inabi alama ce ta fushinsa. Sa mutane su sha, alama ce ta hukunta su. AT: "ya sa mutanen garin su sha ruwan inabi da ke wakilcin fushinsa"
Rashin iya ganin duwatsu magana ne wanda ke bayyana zancen cewa babu duwatsu. AT: "babu wasu duwatsu
Za ku iya sa wannan a awu na zamani. AT: "kilo 34"
1Daya daga cikin mala'ikun nan bakwai wanda ke rike da tasoshi bakwai ya zo ya ce mani, "Zo, zan nuna maka hukuncin babbar karuwarnan da ke zaune a kan ruwaye masu yawa. 2Da ita ce sarakunan duniya suka yi fasikanci. Da ruwan inabinta na fasikanci marar dacewa ta sa mazaunan duniya suka bugu."3Sai mala'ikan ya dauke ni cikin Ruhu ya tafi da ni jeji, sai na ga mace zaune bisa jan dabba cike da sunayen sabo. Dabbar tana da kawuna bakwai da kahonni goma. 4Matar kuwa tana sanye da tufafi na shunayya da kuma jar garura, ta kuma ci ado da kayan zinariya da duwatsu masu tamani da lu'u-lu'ai. Tana rike da kokon zinariya a hannunta cike da abubuwan kyama da na kazantar fasikancinta marar dacewa. 5Bisa goshinta an rubuta wani suna mai boyayyar ma'ana: "Babila mai girma, uwar karuwai da na kazamtattun abubuwan duniya."6Sai na ga matar a buge da jinin masu ba da gaskiya da kuma jinin wadanda aka kashe su domin Yesu. Da na gan ta, na yi mamaki kwarai da gaske. 7Amma mala'ikan ya ce mani, "Don me kake mamaki? Zan bayyana maka ma'anar matar da kuma na dabbar da ke dauke da ita, dabban nan da ke da kawuna bakwai da kahonni goma.8Dabban da ka gani da, yanzu ba ta, amma ta na kusan hawowa daga rami marar iyaka. Sa'annan za ta je hallaka. Wadanda ke zaune a duniya, wadanda ba a rubuta sunayensu cikin littafin rai ba tun kafuwar duniya - za su yi mamaki idan suka ga dabbar da da ta kasance, ba ta nan yanzu, amma ta kusa zuwa.9Wannan al'amari na bukatar hikima. Kawunnan bakwai, tuddai ne bakwai da macen ke zaune a kai. 10Su kuma sarakuna ne bakwai. Sarakuna biyar sun fadi, daya na nan, amma dayan bai zo ba tukuna; sa'anda ya zo zai kasance na dan lokaci kadan.11Dabban da ya kasance a da, amma yanzu ba shi, shi ma sarki ne na takwas; amma shi daya ne cikin sarakunan nan bakwai, kuma zai tafi hallaka.12Kahonnin nan goma da ka gani sarakuna goma ne wadanda ba a nada su ba tukuna, amma za su karbi iko kamar na sarakai na sa'a daya tare da dabban. 13Ra'ayinsu daya ne, za su ba da sarautarsu da ikon su ga dabban. 14Za su yi yaki da Dan Rago. Dan Ragon zai ci nasara a kansu domin shi Ubangijin iyayengiji ne da Sarkin sarakuna - kuma tare da shi sune kirayayyun, zababbun, amintattun."15Mala'ikan ya ce mani, "Ruwayen da ka gani, inda karuwar ke zaune, jama'a ce, da taro masu dumbin yawa, da al'ummai da harsuna.16Kahonnin nan goma da ka gani - su da dabban za su ki karuwar. Za su washe ta su tsiranceta, za su lankwame namanta, za su kone ta gaba daya da wuta. 17Gama Allah ya sa a zukantansu su yi nufinsa ta wurin amincewarsa, su sadaukar da ikonsu na yin mulki ga dabban har sai maganar Allah ta cika.18Matar da ka gani ita ce babban birnin nan da ke mulki bisa sarakunan duniya."
Yahaya ya fara bayyana sashin wahayinsa game da babbar karuwan.
Ana iya bayyana kalmar "hukunci." AT: "yadda Allah zai hukunta babbar karuwarnan"
"babbar karuwan nan da kowa ya sani." Ta na wakilcin wani birni mai zunubi.
Idan ku na so, za ku iya amfani da takamaiman kalma na irin ruwan. AT: "a kan rafuna dayawa"
Ruwan inabin ya na wakilcin fasikanci. AT: "Mutanen duniya sun bugu ta wurin shan ruwan inabinta,
Wannan na iya samun ma'ana biyu: fasikanci a tsakanin mutane da kuma bautar alolin ƙarya.
Wurin ya canja daga kasancewar Yahaya a sama zuwa kasancewa sa a jeji.
farin dutsen wuya. Ana samun su a cikin kwasfan wani ƙaramin dabba da na zama a cikin teku.
AT: "Wani ya rubuta suna a goshinta"
Idan ana so a bayyana cewa sunan na nufin macen ne, ana iya sa wa a jumla. AT: "Ni ne Babila, mai iko"
"ta bugu domin ta riga ta sha jinin ... ta kuma sha jinin"
"masubi waɗanda sun mutu saboda sun gaya wa waɗansu game da Yesu"
mamaki
Mala'ikan ya yi amfani da wannan tambaya domin ya tsawatawa Yahaya a hankali. AT: "Kada ka yi mamaki!"
Wani siririn rami ne mai tsananin zurfin. AT: 1) ramin wanda ba shi da ƙarshe; ya cigaba da yin ƙasa har abada ko 2) ramin ya na da zurfi sosai kamar ba shi da ƙarshe. Dubi yanda kun juya wannan a 9:1.
Ana iya juya kalmar "hallaka" da kalmar aikatau AT: "Sa'an nan za a hallaka shi" ko "Sa'annan Allah zai hallaka shi"
An yi maganar tabbacin abin da zai faru a gaba kamar dabban zai tafi wurin.
AT: "waɗanda Allah bai rubuta sunayensu ba"
Mala'ikan ya yi maganar halittar duniya da Allah ya yi kamar ya kafa tushen duniya kamar yanda wani na kafa tushen gini. AT: "kafin Allah ya halicci duniya"
Mala'ikan ya cigaba da magana. Ya bayyana ma'anar kawuna bakwai na dabban da matan ta ke kai.
Ana iya bayyana "hankali" da "hikima" tare da "tunani" da "dabara." Ana iya bayyana dalilin da ake bukatar hankali mai hikima. AT: "Ana bukatar hankali mai hikima domin a iya fahimtar wannan" ko Ya kamata ka yi tunani da dabara don ka iya fahimtar wannan"
"Wannan ya sa dole ne a sami"
A nan "ne" ya na nufin "wakilci."
Mala'ika ya yi maganar mutuwa kamar faɗiwa ne. AT: "Sarakuna biyar sun mutu"
"ɗaya sarki yanzu" ko "wani sarki na da rai yanzu"
An yi maganar rashin kasancewa kamar rashin zuwo. AT: "wani bai riga ya zama sarki ba, lokacin da zai zama sarki"
Mala'ikan ya yi maganar wani da ya cigaba da zama sarki kamar ya na kasance a wani wuri. AT: "zai iya zama sarki na ɗan loƙaci kadan"
AT: "1) dabban ya yi mulki sau biyu: na farko shi ne ɗaya daga cikin sarakuna bakwai, sai kuma sarki na takwas ko 2) dabban na ƙungiyar sarakuna bakwai ne domin ya na nan kamarsu.
An yi maganar tabbacin abin da zai faru a gaba kamar dabban zai tafi wurin. AT: " "Sa'an nan za a hallaka shi" ko "haƙiƙa Allah zai hallaka shi"
Idan harshenku ba ya raba rana zuwa sa'a ashirin da huɗu, za ku iya amfani da yanayin magana da aka saba yi. AT: "na ɗan lokaci" ko "na ɗan karamin sashin rana"
"Duka waɗannan su na tunanin abu ɗaya" ko "Duka waɗannan sun yarda su yi abu iri ɗaya"
"Rago" karamin tunkiya ne. An yi amfani da alamar a nan don a bayyana Almasihu. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 5:6.
Wannan na nufin taron mutane. Ana iya bayyana kalmomin "kira" da "zabi" a cikin siffar aiki. AT: "kirayayyun, zababbu, amintattun" ko "waɗanda Allah ya kira ya kuma zaɓa, waɗanda sun amince da shi"
A nan "ne" na matsayin "wakilci."
Idan ku na so, za ku iya yin amfani da takamamman kalma na irin ruwan. Dubi yanda kun juya "ruwaye dayawa" a cikin 17:1. AT: "rafuffuka"
babban taron mutane
Wannan ya na nufin mutane da su na da harshe ɗaya. Dubi yadda aka juya wannan a cikin 10:11.
"sace komai da ta ke da shi a kuma bar ta babu komai"
An yi maganar lankwame ta dukka kamar cin dukkan namanta. "za su hallaka ta dukka"
Za su yarda su ba da ƙarfinsu ga dabban, amma ba zai zama cewa su na so su yi biyayya da Allah ba. AT: "Gama Allah ya sa a zukantansu su yarda su bayar ... sai maganar Allah ta cika, kuma ta yin haka, za su yi nufin Allah"
A nan "zuciya" na nufin sha'awa. An yi maganar sa su su yi wani abu kamar sa wa a zuciyarsu su yi shi. AT: "Allah ya sa su su so"
"ikon sarauta"
AT: "sai Allah ya cika abin da ya ce zai faru"
A nan "ne" na matsayin "wakilci."
A lokacin da aka ce birnin na mulki, ana nufin cewa shugaban birnin ya na mulki. AT: "
1Bayan wadannan abubuwa sai na ga wani mala'ika yana saukowa daga sama. Yana da babban iko sosai, duniya kuwa ta haskaka da daukakarsa. 2Ya yi kira da kakkarfar murya cewa, "Ta fadi, Babila mai girma ta fadi! Ta zama mazaunin aljannu, da matattarar kowanne kazamin ruhu da kuma mazaunin kowanne kazami da kyamataccen tsuntsu. 3Gama dukan al'ummai sun sha ruwan innabin fasikancinta. Sarakunan duniya sun aikata fasikanci da ita. Attajiran duniya sun arzuta da ikon rayuwar annashuwarta."4Sai na ji wata murya daga sama ta ce, "Ku fito daga cikinta, mutanena, domin kada kuyi zunubi irin na ta, domin kuma kada bala'inta ya auko maku. 5Zunubanta sun taru sun yi tsayi har sama. Allah kuma ya tuna da miyagun ayyukanta. 6Ku saka mata gwargwadon yadda ta saka wa wadansu, ku biya ta ninki biyu na abin da ta yi; a cikin kokon da ta dama, ku dama mata ninki biyu.7Kamar yadda ta daukaka kanta ta yi ta annashuwa, ku wahalsheta da azaba da bakin ciki haka. Domin ta ce a zuciyarta, 'Ina zaune kamar sarauniya; ni ba gwauruwa ba ce, kuma ba zan taba yin makoki ba,' 8Saboda haka a rana daya bala'inta zai auko mata; mutuwa, makoki da kuma yunwa. Wuta za ta kona ta kurmus, domin Ubangiji Allah mai iko ne, kuma shine mai hukuntata."9Sarakunan duniya da suka yi fasikanci, har suka baude tare da ita, za su yi kuka da kururuwa domin ta sa'adda suka ga hayakin kunarta. 10Za su tsaya can nesa suna tsoron azabarta, suna cewa, "Kaito, kaiton babban birni, Babila, birni mai iko! Domin cikin sa'a guda hukuncinta ya zo."11Manyan 'yan kasuwan duniya za su yi kuka da bakin ciki dominta, da shike ba wanda ke sayan kayanta kuma - 12kayan zinariya, azurfa, da duwatsun alfarma, da lu'u-lu'u, da lilin mai laushi, da hajja mai ruwan jar garura, da siliki, da jar alharini da itacen kamshi iri iri, da kayan da aka sassaka da itace mai tsada, da na tagulla, da na bakin karfe, da na dutse mai sheki, 13da kirfa, da kayan yaji, da turaren wuta, da mur da lubban, da ruwan innabi, da mai, da garin alkama, da alkama, da shanu, da tumaki, da dawakai, da kekunan doki, da bayi, da rayukan 'yan adam.14Amfanin da kika kwallafa rai da duk karfinki sun fice daga gareki. Duk annashuwarki da darajarki sun bace, ba za a kara samunsu ba kuma.15Manyan 'yan kasuwa na wadannan kaya da suka azurta ta wurinta, za su tsaya can nesa da ita, sabili da tsoron azabarta, kuka da kururuwar bakin ciki. 16Za su ce, "Kaito, kaito ga babban birni da take sanye da lilin mai laushi da tufafi masu jar garura da kuma jan alharini, da ta ci ado da kayan zinariya, da duwatsu masu daraja da lu'u-lu'u! 17A cikin sa'a guda duk dukiyan nan ta lallace. Kowanne matukin jirgin ruwa, da fasinjoji, da masu tuki da duk wadanda suke samun biyan bukatun rayuwarsu daga ruwa, suka tsaya can nesa.18Suka yi kuka sa'anda suka ga hayakin kunarta. Suka ce, "Wanne birni ne ya yi kama da babban birnin?" 19Suka watsa kura a kawunansu, suka yi kuka da karfi, da kururuwa da bakin ciki, "Kaito, kaiton babban birnin nan inda duk masu jiragen ruwa suka azurta daga dukiyarta. Domin a sa'a guda an hallakar da ita." 20"Ku yi murna a kanta, sama, ku masu ba da gaskiya, manzanni, da annabawa, domin Allah ya kawo hukuncinku a kanta!"21Wani kakkarfan mala'ika ya dauki wani dutse mai kama da dutsen nika, ya jefa shi cikin teku yana cewa, "Ta wannan hanya, Babila, babban birnin, za a jefar da ita kasa da karfi, ba za a kara ganinsa ba. 22Muryar masu kidar molaye, mawaka, masu busa sarewa, da na masu busa algaita, ba za a kara ji a cikinta ba. Babu wani mai kowanne irin sana'a da za a samu a cikinta. Ba za a kara jin karar nika a cikinta ba.23Hasken fitila ba za ya kara haskakawa a cikin ki ba. Ba za a kara jin muryoyin ango da na amarya a cikinki ba, domin attajiranki sune 'ya'yan masu mulki a duniya, kuma ta wurin sihirinki kika yaudari al'ummai. 24A cikinta aka sami jinin annabawa da na masu ba da gaskiya, da jinin duk wadanda aka kashe a duniya."
Wani mala'ika ya sauƙo daga sama ya kuma yi magana. Wannan mala'ikan dabam ne da wanda yake a aya da ta wuce, wanda ya yi magana game da karuwa da kuma dabban.
Kalmar "ita" na nufin birnin Babila, wadda aka yi maganar ta kamar karuwace.
Mala'ikan ya yi maganar halakar Babila kamar ta faɗi. Dubi yanda kun juya wannan a cikin 14:8.
"kyamataccen tsuntsu"
Al'ummai na nufin mutanen waɗannan al'ummai. AT: "mutanen dukkan al'ummai"
Wannan alama ne na shiga cikin aikata fasikancinta. AT: "sun zama masu fasikanci kamar ita" ko " sun bugu kamar ita a cikin zunubin fasikancinta"
An yi maganar Babila kamar karuwace wanda ta sa waɗansu mutane yin zunubi tare da ita. Wannan na iya zama da ma'ana biyu: fasikanci a zahiri da kuma bautar allolin karya.
Attajiri mutum ne mai sayar da abubuwa.
"domin ta na kashe kuɗi dayawa akan fasikanci"
Kalmar "murya" ta na nufin mai magana, wadda mai yiwuwa Yesu ne ko Uban. AT: "wani dabam"
Muryar ta yi maganar zunuban Babila kamar abubuwa ne da na iya zama taro. AT: "zunuban ta sun yi yawa, su na nan kamar taro da sun kai sama"
"ya yi tunanin" ko "ya fara maida hankali a kan." Wannan ba ya nufin cewa Allah ya tuna wani abu da ya manta. Dubi yadda kun juya "tunawa" a 16: 19.
Muryar ta yi maganar hukunci kamar biya ce. AT: "hukunta ta kamar yanda ta hukunta waɗansu"
Muryar ta yi maganar hukunci kamar biya ce. AT: "hukunta ta so biyu fiye da"
Muryan ya yi maganar sa waɗansu su sha wuya kamar shirya ruwan inabi mai ƙarfi don su sha. AT: "shirya mata ruwan inabi na wuya da ke da ƙarfi ninki biyu kamar yanda ta yi wa waɗansu" ko "sa ta sha wuya so biyu fiye da yanda ta sa waɗansu su sha wuya"
AT: "shirya so biyu" ko 2) "sa shi ya yi ƙarfi so biyu"
"mutanen Babila sun ɗaukaka kansu"
A nan "zuciya" na nufin hankali da tunanin mutum. AT: "Domin ta ce wa kanta"
Ta na nuna cewa ita mai mulki ce, da ikonta.
Ta na nufin cewa ba za ta taɓa dogara da waɗansu mutane ba.
An yi maganar yin makoki kamar ganin makoki. AT: "Ba zan taɓa yin makoki ba"
An yi maganar kasancewa a gaba kamar zuwa.
An yi maganar konewa da wuta kamar wutar ya cinye ta. AT: "Wuta zai kone ta gaba ɗaya"
"yi zunubin lalata sun kuma yi abin da sun so kamar yanda mutanen Babila su ka yi"
Ana iya juya "azaba" a matsayin aikatau AT: "jin tsoro cewa za a azabtar da su kamar yanda Babila ta ke" ko "jin tsoro cewa Allah zai azabtar da su kamar yanda ya azabtar da Babila"
An nanata wannan don jaddadawa.
An yi maganar kasancewa yanzu kamar ya riga ya zo.
"yi makoki don mutanen Babila"
"duwatsu masu tsada dayawa." Dubi yadda kun juya wannan a cikin 17:4.
kaya mai tsada da an yi daga wani irin tsiro. Dubi yadda kun juya "linin" a cikin 15:6.
hajja mai ruwan jar galura ƙyalle ne mai jan kala da ke da tsada. Siliki ƙyalle ne mai laushi, da karfi da a ka yi shi daga kirtani.
"kowane kayayyaki da an yi shi daga haure"
farin kyakkyawan abu mai karfi da mutane ke samu daga haure ko hakorin katon dabba kamar giwa. AT: "haure" ko "hakorin dabba mai amfani"
dutse mai kyau da ake amfani da shi a gini
abin da ke da kamshi mai daɗi kuma ana samun sa daga bayan wani irin itace
wani abu ne da ana amfani da shi don ya ƙara daɗi ko kamshi mai daɗi a mai
Sun yi magana game da abubuwa masu kyau kamar 'ya'yan itace ko amfanin gona ne. AT: "Abubuwa masu kyau"
"so dayawa sosai"
Rashin samuwa na wakilcin rashin kasancewa. AT: "ɓace; ba za ku taɓa samun su kuma ba"
Ana iya sake bayyana "tsoro" da "azaba." AT: "domin za su ji tsoron azabar da Allah zai yi masu kamar yanda ya yi mata" ko kuma "domin za su ji tsoron jin wahala kamar yanda ta na shan wahala"
Wannan ne abin da attajiran za su yi. AT: "kuma su yi kuka da kururuwar baƙin ciki"
Gaba ɗaya a cikin wannan aya, an yi maganar Babila kamar mace ce. Attajirai sun yi maganar Babila kamar tana sanye da lilin mai laushi domin mutanen ta suna sanye da lilin mai laushi. AT: "babbar birni, wanda yake kamar mace da take sanye da lilin mai laushi" ko kuma "babbar birni, wanda matayensu suna sanye da lilin mai laushi"
AT: "da tana sanye da lili mai laushi"
AT: "yi adon kanta da zinariya" ko kuma "yi adon kansu da zinariya" ko "sa zinariya"
"dutse mai tsada"
farin dutsen wuya mai tsada. Ana samun su daga ciki kwasfar wani karamin dabba da na zama a cikin teku. Dubi yanda an juya wannan a cikin 17:4.
Jumlar "daga teku" ya na nufin abin da su ke yi akan tekun. AT: "wadda na tafiya a kan teku don bukatun rayuwarsu" ko kuma "wadda na tafiya a kan teku zuwa wurare dabam dabam domin sayar da abubuwa"
Wannan tambaya ya na nuna wa mutane muhimmincin birnin Babila. AT: "Babu wani birni da na nan kamar babban birnin, Babila!"
Ana iya bayyana kalmar "hukunci" cikin aikatau. AT: "Allah ya riga ya hukunta ta domin ku" ko kuma "Allah ya hukunta ta domin mugayen abubuwa da ta yi maku"
babban mulmulallen dutse da ake nika hatsi
Allah zai halakar da birnin gaba ɗaya. AT: "Allah zai jefar da birnin Babila da ƙarfi, babban birni, kuma ba zai sake kasancewa ba"
"babu wani da zai sake ganinta kuma." Rashin ƙara ganinta a nan na nufin cewa ba za ta sake kasancewa kuma ba"
AT: "Babu wani a birninki da zai ƙara kuma jin ƙarar da masu kiɗar molaye, mawaƙa, masu busa sarewa, da na masu busa algaita ke yi"
Mala'ikan ya na magana kamar Babila ta na jinshi a wurin. AT: "a cikin Babila"
"babu wani da zai sake jin su a cikinki." Rashin samuwa a wurin na nufin cewa ba za a same su a wurin ba. AT: "ba za su kasance a birnin ki kuma ba"
Rashin samuwa a wurin na nufin cewa ba za a same su a wurin ba. AT: "Babu wani mai sana'a na kowanne iri da za a samu a cikinki"
Rashin jin ƙaran wani abu na nufin cewa babu wani da zai yi wannan ƙaran. AT: "Babu wani da zai yi niƙa a cikinki"
AT: "Babu wani da zai sake ji a Babila muryoyin murna na amarya da na ango "
Rashin ji a nan na nufin cewa ba za su kasance a wurin ba. AT: "ba za su kasance a birninki ba"
Mala'ikan ya yi maganar mutane masu muhimmanci da iko kamar sun zama 'ya'yan sarki. AT: "attajiranki suna kamar 'ya'yan sarki a duniya" ko "attajiranki sune mutane masu muhimminci a cikin duniya"
AT: "kika ruɗi mutanen duniya da sihirinki"
Samun jini a wurin ya na nufn cewa mutanen sun yi laifin kashen mutane. AT: "Babila ta na da laifin kashen annabawa da masubi da kuma dukkan sauran mutanen duniya da an kashe su"
1Bayan wadannan abubuwa na ji wata karar da ta yi kamar muryar mutane masu yawa a sama suna cewa, "Halleluya. Ceto, daukaka da iko sun tabbata ga Allahnmu. 2Hukunce - hukuncensa gaskiya ne da adalci, domin ya hukunta babbar karuwan nan wadda ta kazamtar da duniya da fasikancinta. Ya dauki fansar jinin bayinsa, wadda ita da kanta ta zubar."3Suka yi magana a karo na biyu: "Halleluya! Hayaki na tasowa daga wurinta har abada abadin." 4Dattawan nan ashirin da hudu da rayayyun halittun nan hudu, suka fadi suka yi wa Allah sujada shi da yake zaune a kan kursiyin. Suna cewa, "Amin. Halleluya!"5Sai wata murya ta fito daga kursiyin tana cewa, "Ku yabi Allahnmu, dukanku bayinsa, ku da kuke tsoronsa, da duk marasa iko da masu iko."6Sai na ji murya kamar na kasaitaccen taron mutane, kamar rurin kogi na ruwaye masu yawa, kuma kamar tsawar aradu, cewa, "Halleluya! Gama Ubangiji yana mulki, Allah mai iko duka.7Bari mu yi murna, mu yi farinciki matuka mu kuma ba shi daukaka domin bikin auren Dan Ragon ya zo, amaryarsa kuma ta shirya kanta. 8An yardar mata ta sa kaya masu haske da tsabta na lilin mai laushi" (domin lilin mai laushi shine ayyukan adalci na tsarkaka).9Mala'ika ya ce mani, "Rubuta wannan: Masu albarka ne wadanda aka gayyace su zuwa bikin auren Dan Ragon." Ya kuma ce mani, "Wadannan kalmomin Allah na gaskiya ne." 10Na fadi a gaban kafafunsa domin in yi masa sujada, amma ya ce mani, "Kada ka yi haka! Ni ma abokin bauta ne tare da kai da 'yan'uwanka wadanda ke rike da shaida game da Yesu. Yi wa Allah sujada, domin shaida game da Yesu shine ruhun annabci."11Sai na ga sama a bude, na kuma duba sai ga wani farin doki. Mahayinsa ana kiransa amintacce da gaskiya. Yana shari'a da adalci yana yaki. 12Idanunsa kamar harshen wuta suke, a kansa akwai kambuna da yawa. Yana da suna a rubuce a jikinsa wanda ba wani da ya sani sai dai shi da kansa. 13Yana sanye da riga da aka tsoma a cikin jini, kuma ana kiran sunansa Kalmar Allah.14Rundunonin sama suna biye da shi a kan fararen dawakai, suna sanye da lilin mai laushi, fari mai tsabta. 15Daga cikin bakinsa takobi mai kaifi na fitowa, da ita yake sarar al'ummai, zai kuma mulke su da sandar karfe. Yana tattake wurin matsar ruwan inabi da matsananciyar fushin Allah Mai iko duka. 16Yana da suna a rubuce a rigarsa da cinyarsa: "Sarkin sarakuna da Ubangijin iyayengiji."17Na ga mala'ika tsaye a rana. Yayi kira da murya mai karfi ga dukan tsuntsaye da ke firiya a sama. 18"Ku zo, ku tattaru saboda babban bukin Allah. Ku zo ku ci naman sarakuna, da naman sarakunan yaki, da naman manyan mutane, da naman dawakai, da na mahayansu, da naman dukan mutane, yantattu da bayi, marasa iko da masu iko."19Na ga dabban da sarakunan duniya da rundunoninsu. Suna tattaruwa domin su yi yaki da wanda ke bisa doki da rundunarsa. 20Aka kama dabban tare da makaryatan annabawa da suka yi ayyukan al'ajibai a gabansa. Da wadannan alamu ya yaudari wadanda suka karbi alamar dabbar da wadanda suka yi wa siffarta sujada. Aka jefa dukansu biyu da rai cikin tafkin farar wuta mai ci.21Sauran aka karkashe su da takobin da ke fitowa daga bakin mahayin dokin. Dukan tsuntsaye suka ci gawarwakinsu.
Wannan sashin na gaba ne a wahayin Yahaya. A nan ya kwatanta farin ciki a sama akan faɗiwar babbar karuwan, wadda ita ce birnin Babila.
A nan "na" na nufin Yahaya.
Wannan kalma na nufin "Yabi Allah" ko "Bari mu yabi Allah."
A nan, Yahaya ya na nufin birnin Babila wanda mugayen mutanenta suke mulki a kan dukkan mutanen duniya kuma suna sa su su bauta wa allolin ƙarya. Ya na maganar mugayen mutanen Babila kamar su babbar karuwace.
A nan "duniya" na nufin mazauna. AT: "wadda ta kazamtar da mutanen duniya"
A nan "jini" na wakilcin kisa. AT: "yin kisar bayinsa"
Wannan na nufin Babila. An yi amfani da "kanta" domin ƙarin bayani.
A nan "su" na nufin taron mutane a sama.
Kalmar "ita" ya na nufin birnin Babila, wadda a na maganarsa kamar karuwace. Hayakin daga wutar da ke halaka birnin. AT: "Hayaki na tasowa daga birnin"
"Dattawa ashirin da huɗu." Dubi yanda kun juya wannan a 4: 4.
"rayayyun halittu huɗu" ko "rayayyun abubuwan nan huɗu" Dubi yanda kun juya wannan a 4:6
AT: "wadda ya zauna a kan kursiyin"
A nan Yahaya na maganar "murya" kamar mutum ne. AT: "wani ya yi magana daga kursiyin"
A nan "mu" na nufin mai magana da dukka bayin Allah.
A nan "tsoro" ba ya nufin jin tsoron Allah, amma a girmama shi. AT: "dukkan ku da ku na girmama shi"
Mai magana ya yi amfani da waɗannan kalmomi don ya na nufin dukka mutanen Allah.
Yahaya na maganar abin da ya na ji kamar ƙara ne da aka yi daga babban taron mutane, babbar ruwa mai gudu, da kuma babbar aradu.
"Domin Ubangiji"
Muryan taron da aka yi magana a baya.
A nan "mu" na nufin dukka bayin Allah.
"ba Allah ɗaukaka" ko "girmama Allah"
A nan Yahaya na maganar haduwan Yesu tare da mutanensa har abada kamar bikin aure.
Wannan ɗan rago ne. A nan na nufin Almasihu. Dubi yanda kun juya wannan a cikin 5:6.
An yi maganar kasancewa yanzu kamar ya riga ya zo.
Yahaya ya yi maganar mutanen Allah kamar sun zama amarya da ta yi shirin aurenta.
A nan "ta" na nufin mutanen Allah. Yahaya ya na maganar ayyukan adalcin mutanen Allah kamar sun zama kaya mai haske da tsabta da amarya na sa wa a ranar aurenta. AT: "Allah ya bar ta ta sa kayan haske da tsabta na lilin mai laushi"
AT: "mutanen da Allah ya gayyata"
A nan mala'ikan ya yi maganar haɗuwar Yesu tare da mutanensa har abada kamar bikin aure ne.
Wannan ya na nufin cewa Yahaya ya kwanta a ƙasa ya kuma miƙa kansa don girmama ko biyaya. Waɗannan muhimman ayyuka ne a sashin sujada, don nuna biyaya ko bauta. Dubi rubutu a cikin 19:3.
Kalmar "'yan'uwa" anan na nufin dukkan masubi, maza da mata.
A nan "riƙe" na matsayin gaskatawa ko sanarwa. AT: "waɗanda ke faɗan gaskiya game da Yesu"
A nan "ruhun annabci" ya na nufin Ruhu mai Tsarki na Allah. AT: "don Ruhun Allah ne na ba mutane ikon faɗan gaskiya game da Yesu"
An yi amfani da wannan magana don a nuna farkon sabon wani wahayi. Dubi yadda kun juya wannan magana a cikin 11:19 da 15:5.
Yesu ne mahayin.
A nan "adalci" ya na nufin abin da ke daidai. AT: "Ya na shar'anta dukkan mutane, ya na kuma yin yaƙi bisa abin da ke daidai"
Yahaya ya yi maganar idanun mahayin kamar sun haskaka kamar harshen wuta.
AT: "Wani ya rubuta suna a kanshi"
"a kanshi, kuma shi kaɗai ne ya san ma'anar sunan nan"
AT: "jini ya rufe rigarsa"
Ku na iya bayyana wannan a cikin siffar aiki. "Kalmar Allah" a nan na nufin Yesu Almasihu. AT: "ana kiran sunansa Sakon Allah" ko kuma "sunansa kuma Kalmar Allah ne"
Ruwan takobin ya na tsabga daga bakinsa. Takobin da kansa ba ya motsi. Dubi yanda kun juya irin wannan jumla a cikin 1:16.
"halaka al'ummai" ko "kawo al'ummai a ƙarkashin ikonsa"
Yahaya ya yi maganar ikon mahayin kamar ya na mulki da sandar karfe. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 12:5.
Yahaya ya yi maganar hallaka maƙiyan mahayin kamar su inabi ne da mutum ya ke takawa a cikin inda ake matse ruwan inabi. A nan "fushi" ya na nufin hukuncin Allah a kan mugayen mutane. AT: "Ya take makiyansa bisa hukuncin Allah, kamar yadda mutum ke taka inabi a wurin matse shi."
AT: "Wani ya rubuto suna a rigarsa da cinyarsa:"
A nan "rana" na nufin hasken rana. AT: "Sai na ga mala'ika a tsaye a cikin hasken rana"
Mala'ikan ya na nufin dukka mutane ne da ya yi amfani da waɗannan akasin kalmomi tare.
AT: "mahayin farin dokin ya kama dabban da kuma annabin ƙarya"
Wannan alama ne da ke nuna cewa mutumin da ya karɓi alamar ya bauta wa dabban. Dubi yanda kun juya wannan a cikin 13:17.
AT: "Allah ya jefa dabban da annabin ƙarya da rai"
"tafkin wuta da ke konewa da farar wuta" ko "wuri cike da wuta da ke konewa da farar wuta"
AT: "Mahayin dokin ne ya ƙashe sauran sojojin dabban da takobi da ya fito daga bakinsa"
Ruwan takobin ya na tsabga daga bakinsa. Takobin da kansa ba ya motsi. Dubi yanda kun juya irin wannan jumla a cikin 1:16.
1Sai na ga mala'ika na saukowa daga sama. Yana da makullin rami marar iyaka, yana kuma da babar sarka a hannunsa. 2Sai ya dauki tsohon macijin, wanda shine iblis, ko shaidan, ya daure shi shekaru dubu. 3Ya jefa shi cikin rami marar iyaka, ya rufe shi ya kuma sa hatimi a bisansa. Hakan ya faru ne domin kada ya kara yaudarar al'ummai har sai bayan shekaru dubu. Bayan wannan, dole a sake shi na dan lokaci.4Sa'annan na ga kursiyoyi. Wadanda ke zaune a bisansu sune wadanda aka ba ikon hukunci. Na kuma ga rayukan wadanda aka fille wa kai saboda shaidar Yesu da maganar Allah. Ba su yi wa dabban sujada ba ko siffarsa, suka ki su karbi alamar a goshinsu ko a hannu. Sun sake rayuwa, suka yi mulki tare da Kristi shekaru dubu.5Sauran matattun basu sake dawowa da rai ba har sai da shekaru dubu din suka cika. Wannan shine tashin matattu na fari. 6Mai albarka ne mai tsarki ne kuma wanda yake da rabo cikin tashin matattu na fari! Mutuwa ta biyu ba ta da iko akan wadannan. Za su zama firistocin Allah da na Almasihu za su kuma yi mulki tare da shi shekaru dubu.7Sa'adda shekaru dubu suka zo ga karshe, za a saki shaidan daga kurkukunsa. 8Za ya fito domin ya yaudari al'ummai da ke kursuyoyi hudu na duniya, Gog da Magog ya tattara su domin yaki. Yawan su zai zama kamar yashin teku.9Suka bazu a fuskar duniya suka kuma kewaye sansanin masu ba da gaskiya, kaunataccen birni. Amma wuta ta sauko daga sama ta lankwame su. 10Shaidan, wanda ya yaudare su, aka jefa shi cikin korama ta farin wuta mai ci, inda aka jefa dabban da makaryacin annabin. Za su sha azaba dare da rana har abada abadin.11Sai na ga babban kursiyi da wanda ke zaune a kansa. Duniya da sama suka guje wa fuskarsa, amma babu wurin da za su tafi. 12Na ga matattu manya da kanana- suna tsaye gaban kursiyin, aka bude litattafai. Sai aka bude wani littafi - Littafin rai. Aka yi wa matattu shari'a bisa ga abinda aka rubuta cikin litattafan, gwargwadon ayyukansu.13Teku ta ba da matattun dake cikinta. Mutuwa da hades suka ba da matattun da ke cikinsu, aka yi masu shari'a gwargwadon abin da suka yi. 14Aka jefa mutuwa da hades cikin tafkin wuta. Wannan shine mutuwa ta biyu - tafkin wuta. 15Duk wanda ba a sami sunansa a rubuce cikin littafin rai ba, aka jefar da shi cikin tafkin wuta.
Yahaya ya fara kwatanta wahayin mala'ika da ke jefa Ibilis a cikin rami mara iyaka.
A nan "na" na nufin Yahaya.
Wannan rami ne mai tsananin zurfi. AT: 1) ramin bashi da ƙarshe; ya cigaba da tafiya ƙasa har abada ko 2) ramin na da zurfin da na nan kamar bashi da ƙarshe. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 9: 1.
Wannan babban, halitta ne mai rarrafe mai kuma ban tsoro kamar kadangare. Alamar masifa da bala'i ne ga mutanen Yahudawa.
Mala'ikar ya hatimci ramin don ya hana kowa buɗewa. AT: "hatimce shi don ya hana kowa buɗewa"
A nan "alummai" na nufin mutanen duniya. AT: "yaudarar taron mutane"
" shekaru dubu ɗaya"
AT: "Allah zai umurci mala'ikar ya sake shi"
AT: "waɗanda Allah ya ba su ikon hukunci"
AT: "waɗanda waɗansu ne sun yanke kawunansu"
"domin sun faɗi gaskiya game da Yesu da kuma game da maganar Allah"
Waɗannan na nufin saƙo daga Allah. AT: "don abin da sun koyar game da nassi"
" Sun sake rayuwa"
"Dukka sauran matattun mutane"
"karshen shekaru dubu ɗaya"
A nan Yahaya ya kwatanta "mutuwa" kamar mutum ne mai iko. AT: "Waɗannan mutanen ba za su ga mutuwa ta biyu ba"
"Mutuwa ta biyu." An kwatanta wannan kamar hukunci na har abada a cikin tafkin wuta a 20:14 da kuma 21:8. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 2: 11. AT: "mutuwa na ƙarshe a cikin tafkin wuta"
AT: "Allah zai saki shaiɗan daga kurkukunsa"
Wannan karin magana ne da na nufin "dukka yankin duniya." Dubi yadda kun juya wannan a cikin 7: 1.
Waɗannan sunaye ne da annabi Ezekiel ya yi amfani don ya wakilci kasashe masu nisa.
Wannan ya na nanata tsananin yawan lambar rundunar sojojin Shaiɗan.
"Sojojin Shaiɗan suka tafi"
Wannan na nufin Urushalima.
Yahaya ya yi maganar wuta a nan kamar na da rai. AT: "Allah ya aiko wuta daga sama don ta kone su dukka"
AT: "Allah ya jefa Ibilis, wanda ya yaudare su, cikin" ko "Mala'ikar Allah ya jefa Ibilis, wanda ya yaudare su, cikin"
"tafkin wuta da ke konewa da farin wuta" ko kuma "wuri cike da wuta da na konewa da farin wuta." Dubi yadda kun juya wannan a cikin 19: 20.
AT: "inda ya kuma jefa dabban da kuma maƙaryacin annabin"
AT: "Allah zai azabtar da su"
Yahaya ya yi kwatancin sama da duniya kamar mutane ne da suke ƙoƙarin gudu daga hukuncin Allah. Wannan ya na nufin cewa Allah ya hallakar da tsohon sama da kuma duniya gaba ɗaya.
Yahaya ya haɗi waɗannan kalmomi masu akasin ma'ana don ya nuna cewa ya na nufin dukkan matattun mutane.
AT: "wani ya bude litattafai"
AT: "Allah ya hukunta mutanen da sun mutu, waɗanda suke kuma raye yanzu"
AT: "bisa abin da ya rubuto"
A nan Yahaya ya yi maganar teku, matattu, da kuma Hades kamar rayyayun mutane ne.
AT: "Allah ya jefa Mutuwa da Hades" ko "Mala'ikar Allah ya jefa Mutuwa da Hades"
A nan "Hades" magana ne da na wakilcin wurin da marasa bi su ke zuwa a lokacin da sun mutu, don su jira hukuncin Allah.
AT: "Idan mala'ikan Allah bai sami sunan mutum ba"
AT: "mala'ikan ya jefa shi cikin tafkin wuta" ko "mala'ikan ya jefa shi cikin wuta da ke ƙonewa har abada"
1Sai na ga sabuwar sama da sabuwar duniya, domin sama ta fari da duniya ta fari sun shude, ba kuma teku. 2Na ga birni mai tsarki, sabuwar Urushalima, wadda ta sauko kasa daga sama wurin Allah, shiryayya kamar amaryar da aka yi wa ado domin mijinta.3Na ji babbar murya daga kursiyinta na cewa, "Duba! Mazaunin Allah yana tare da 'yan adam, zai zauna tare da su. Za su zama mutanensa, Allah kuma da kansa zai kasance tare da su ya kuma zama Allahnsu. 4Zai share dukan hawaye daga idanunsu, kuma babu sauran mutuwa, ko bakinciki, ko kuka, ko azaba. Abubuwan da sun shude.5Shi wanda yake zaune a kan kursiyin ya ce, "Duba! Na maida kome ya zama sabo." Ya ce, "Ka rubuta wannan domin wadannan kalmomi amintattu ne da gaskiya". 6Ya ce mani, "Wadannan abubuwan an gama! Ni ne Alpha da Omega, farko da karshe. Ga mai jin kishi, zan bashi kyauta daga mabulbular ruwan rai.7Wanda ya ci nasara, zai gaji wadannan abubuwa, ni kuma zan zama Allahnsa, shi kuma ya zama da na. 8Amma ga matsorata, da marasa bangaskiya, da masu kazanta, da masu kisan kai, da fasikai, da masu sihiri, da masu bautar gumaka, da dukan makaryata, mazaunin su zai kasance cikin tafki mai ci da farar wuta. Mutuwa ta biyu kenan."9Daya daga cikin mala'ikun bakwai ya zo wurina, wanda yake dauke da tasoshi bakwai cike da annobai bakwai na karshe, yace, "Zo nan. Zan nuna maka amarya, matar Dan Rago". 10Sai ya dauke ni cikin Ruhu zuwa wani babban dutse mai tsawo ya nuna mani birni mai-tsarki, Urushalima, tana saukowa daga cikin sama daga wurin Allah.11Urushalima tana da daukakar Allah, shekinta yana kama da dutse mai tamani, sai kace dutsen yasfa, garau kamar karau. 12Tana da babban garu mai tsawo, da kofofi goma sha biyu, da mala'iku goma sha biyu a kofofin. Akan kofofin an rubuta sunayen kabilu sha biyu na 'ya'yan Isra'ila. 13A gabas akwai kofofi uku, a arewa kofofi uku, a kudu kofofi uku, da kuma yamma kofofi uku.14Garun birnin yana da harsashin gini goma sha biyu, a bisansu akwai sunaye goma sha biyu na manzanni goma sha biyu na Dan Rago. 15Shi wanda yayi magana dani yana da sandan awo na zinariya domin ya auna birnin, da kofofinsa, da garunsa.16Birnin; da tsawonsa da fadinsa iri daya ne. Ya gwada birnin da sandar awo, mil dubu sha biyu a tsaye (fadinsa, da tsawonsa, da tsayinsa duka daya ne) 17Ya kuma gwada garunsa, kamu 144, bisa ga gwajin 'yan adam (wanda shine ma'aunin mala'ika).18An gina garun da Yasfa birnin kuma da sahihiyar zinariya, mai kama da madubi mai kyalli. 19An kawata harsashin garun da kowanne irin dutse mai tamani. Na fari yasfa, na biyu saffir, na uku agat, na hudu emerald, 20na biyar Onis, na shida sardiyus, na bakwai kirisolat, na takwas beril, na tara tofaz, na goma kirisofaras, na sha daya yakinta, na sha biyu kuma ametis.21Kofofi goma sha biyu lu'u-lu'ai ne goma sha biyu; kowacce daya a cikin kofofin daga lu'u-lu'u daya aka yi shi. Titunan birnin kuwa zinariya ce sahihiya, sai kace madubi garau. 22Ban ga haikali a cikin birnin ba, gama Ubangiji Allah Mai iko duka da Dan Ragon su ne haikalinsa.23Birnin ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi gama daukakar Allah ta haskaka shi, kuma fitilarsa Dan Rago ne. 24Al'ummai za su yi tafiya cikin hasken birnin. Sarakunan duniya kuma za su kawo daukakarsu cikinsa. 25Kofofinsu kuma ba za a rufe su da rana ba, babu dare kuma a can.26Za su kawo daukaka da darajar al'ummai a cikinsa, 27babu wani abu mai kazanta da zai taba shiga cikinsa. Ko wanda yake aikata abin kunya da karya, sai wadanda an rubuta sunayensu a cikin littafin rai na Dan Rago kadai.
Yahaya ya fara kwatanta wahayinsa na sabon Urushalima.
A nan "na" na nufin Yahaya.
Wannan na kwatanta sabon Urushalima da amaryar da ta shirya kanta da kyau domin angon ta.
Kalmar "murya" na nufin wanda ke magana. AT: "wani ya yi magana da ƙarfi daga kursiyin da cewa"
Kalmar "duba" a nan yana sa mu mu saurare bayani mai ban mamaki da ke biye.
Waɗannan jumloli biyu na nufin abu ɗaya ne kuma ya na nanata cewa haƙiƙa, Allah zai, yi rayuwa tare da mutane.
Hawaye a nan na wakilcin baƙin ciki. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 7:17. AT: "Allah zai share baƙin cikinsu, kamar share hawaye" ko "Allah zai sa su kada su yi baƙin ciki kuma"
A nan "kalmomi" ya na nufin sakon da sun yi. AT: "wannan sakon amintattu ne da gaskiya"
Waɗannan jumloli biyu atakaice na nufin abu ɗaya ne kuma ya na nanata kasancewar Allah na matuƙa.
Waɗannan baƙaƙe ne na farko da ƙarshe na haruffar Greek. Ga ma'anoni masu yiwuwa 1) "wanda ya fara dukkan komai da wanda ya gama komai" ko kuma 2) "wanda ya ke rayuwa koda yaushe da kuma wanda zai yi rayuwa kullum." Idan masu karatun ba za su gane waɗannan ba, za ku iya amfani da baƙaƙe na farko da ƙarshe na harshenku. Dubi yanda kun juya wannan a cikin 1:18. AT: "A da Z" ko "na farko da ƙarshe"
AT: 1) "wanda ya fara dukkan komai ne zai sa dukka komai ya ƙare" ko 2) "wanda ya kasance kafin dukkan komai da kuma wanda zai kasance bayan dukkan komai."
Allah ya yi maganar begen mutum na rai na madawami kamar kishi kuma na mutumin da ke karɓan rai madawami kamar ya na shan ruwa mai ba da rai.
Wanda ya ke zaune a kan kursiyin ya cigaba da yi wa Yahaya magana.
"waɗanda suke tsoron yin abin da ke daidai"
"waɗanda su ke yin mugun abubu"
tafkin wuta da ke konewa da farin wuta" ko kuma "wuri cike da wuta da ke konewa da farin wuta." Dubi yadda kun juya wannan a cikin 19: 20.
"mutuwa ta biyu." An kwatanta wannan kamar hukunci na har abada a cikin tafkin wuta a 21:8. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 2:11. AT: "mutuwa na ƙarshe a cikin tafkin wuta"
Mala'ikan ya yi maganar Urushalima kamar mace ne da ta yi kusa ta auri mijinta, Ragon. Urushalima na nufin waɗanda sun gaskata, waɗanda za su zauna a ciki.
Wannan karamin tunkiya ne. Alama ne anan da ke nufin Almasihu. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 5: 6.
Wrin nuna wahayin ya canja sa'ad da aka ɗauki Yahaya zuwa babbar dutse inda zai iya ganin birnin Urushalima. Dubi yadda kun juya wannan jumla a cikin 17: 3.
Wannan ya na nufin "Urushalima mai zuwa daga sama" da ya kwatanta a aya da ya wuce kuma ba Urushalima da aka sani ba.
Waɗannan jumloli biyun na nufin abu ɗaya. Na biyun na nanata hasken Urushalima ta wurin ambatar abu mai tamani.
"garau sosai"
Wannan dutse ne mai daraja. Mai yiwuwa yasfa ya yi haske kamar gilas ko ƙarau. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 4:3.
" kofofi goma sha biyu"
AT: "wani ya rubuto"
Wannan na nufin Yesu. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 5:6.
"mil dubu ɗaya da ɗari huɗu." Za ku iya juya wannan zuwa awu na zamani. AT: "mita dubu biyu da ɗari biyu"
"kamu dari ɗaya da arba'in da huɗu." Za ku iya juya wannan zuwa awu na zamani. AT: "mita sittin da shida"
AT: "Wani ya gina garun da yasfa da kuma birnin da sahihiyar zinariya"
Zinariyan ya yi haske da har an yi maganar sa kamar gilas.
AT: "Wani ya kawata harsashin garun"
Waɗannan duwatsu ne masu daraja. Mai yiwuwa yasfa ya yi haske kamar gilas ko ƙarau, kuma mai yiwuwa sardiyus ja ne. Emerald kore ne. Dubi yadda kun juya waɗannan a cikin 4:3.
Waɗannan dukka duwatsu masu daraja ne.
kyakkyawan farin dutsen wuya mai kuma daraja. Ana samun su daga cikin kwasfan wani irin ƙaramin dabba da ke zama a cikin teku. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 17:4.
AT: "wani ya yi kowacce ƙofa daga lu'u-lu'u ɗaya"
Zinariyan ta yi sarai sosai har an yi maganarsa kamar ya zama gilas. Dubi yadda kun juya jumla irin wannan a cikin 21:18.
Haikalin ya wakilci gaban Allah. Wannan ya na nufin cewa sabon Urushalima ba ya neman haikali domin Allah da Ragon za su zauna a wurin.
An yi maganar ɗaukakar Yesu, Ragon, a nan kamar fitilace da na ba da haske a birnin.
"Al'ummai" na nufin mutane. "Tafiya" a nan na nufin rayuwa. AT: "Mutane daga dukka Al'umma dabam-dabam za su rayu"
AT: "Babu wanda zai rufe ƙofofin"
"Sarakunan duniya za su kawo"
AT: "abu mai tsabta ne kadai zai shiga, kuma babu wani"
AT: "amma sai waɗanda Ragon ya rubuta sunayensu kaɗai a cikin littafinsa na rai"
1Sai mala'ika ya nuna mani kogin ruwan rai, ruwa mai tsabta. Yana fitowa daga cikin kursiyin Allah da na Dan-Rago 2ta tsakiyar titin birnin. A kowanne gefen kogin akwai itacen rai, mai ba da 'ya'ya iri goma sha biyu, kowanne wata. Ganyayen itacen kuma domin warkar da al'ummai ne.3Babu sauran la'ana nan gaba. Kursiyin Allah da na Dan Rago za su kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa bauta. 4Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu. 5Babu sauran dare; ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba gama Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su yi mulki har abada abadin.6Mala'ika ya ce mani, "Wadannan kalmomi amintattu ne da gaskiya. Ubangiji, Allah na ruhohin annabawa, ya aiki mala'ikansa ya nuna wa bayinsa abin da lallai zai faru ba da dadewa ba". 7"Duba! Ina zuwa ba da dadewa ba! Mai albarka ne wanda ya yi biyayya da kalmomin littafin nan."8Ni, Yahaya, nine na ji na kuma ga wadannan abubuwa. Sa'adda na ji na gan su, sai na fadi gaban kafaffun mala'ikan da ya nuna mani wadannan abubuwa domin in yi masa sujada. 9Ya ce mani, "Kada ka yi haka! Ni abokin bauta ne tare da kai, tare da 'yan'uwanka annabawa, da wadanda ke biyayya da kalmomin littafin nan. Yi sujada ga Allah!"10Ya ce mani, "Kada ka rufe kalmomin anabcin littafin nan, gama lokaci ya kusa. 11Wanda yake mara adalci, bari ya cigaba da yin rashin adalci. Wanda yake mai kazanta bari ya cigaba da kazantar da kansa. Wanda yake mai adalci bari ya cigaba da yin adalci. Wanda yake mai-tsarki, bari yaci gaba da tsarki."12"Duba! Ina zuwa ba da dadewa ba. Sakamakona na tare da ni, zan saka wa kowa gwargwadon aikin da ya yi. 13Nine Alpha da Omega, farko da karshe, mafarin abu da karshensa.14Masu albarka ne wadanda suka wanke rigunansu domin su sami izini su ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta kofofinsa. 15A waje akwai karnuka, masu sihiri, masu bautar gumaka, fasikai, masu kisan kai, da duk wanda yake kaunar aikata rashin gaskiya.16Ni, Yesu na aiko mala'ikana ya shaida maku wadannan abubuwa saboda ikilisiyoyi. Nine tushe da zuriyar Dauda, tauraron asubahi mai-haske."17Ruhu da Amarya suka ce, "Zo!" Bari wanda ya ji ya ce, "Zo!" Kowanne mai jin kishi, da kowanne mai bukatar ta, bari ya sami ruwan rai kyauta.18Ina shaida wa duk mai jin kalmomin anabcin wannan littafi: Idan wani ya kara a kansu, Allah zai kara masa annoban da ke rubuce a cikin littafin. 19Idan wani ya rage daga kalmomin wannan littafin anabci, Allah zai rage rabonsa daga cikin itacen rai daga cikin birni mai-tsarki, wadanda aka rubuta cikin wannan littafi.20Shi wanda ya shaida wadannan abubuwa ya ce, "I! Ina zuwa ba da dadewa ba." Amin! Zo, Ubangiji Yesu! 21Alherin Ubangiji Yesu ya kasance tare da kowanne dayanku. Amin.
Yahaya ya cigaba da kwatanta sabon Urushalima kamar yadda mala'ikan ya nuna masa.
Anan "ni" na nufin Yahaya.
"rafin da ke gudu da ruwan bada rai"
An yi maganar rai madawami kamar an tanada shi ta wurin ruwa mai bada rai. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 21:6.
Wannan ƙaramin tunkiya ne. Alama ne a nan da ke nufin Almasihu. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 5: 6.
A nan "al'ummai" na nufin mutane da su ke zama a cikin kowane al'umma. AT: "mutanen dukka al'ummai"
AT: 1) "Ba za a sami wani da Allah zai la'hanta ba" ko 2) "Ba za a sami wani a wurin da na ƙarƙashin la'anar Allah ba"
Ma'anoni masu yiwuwa na "sa" 1) "Duk kalmomin na nufin Allah Uba, ko 2) Duk kalmomin na nufin Allah da Ragon, wanda na mulki tare.
Wannan ƙarin magana ne, da na nufin kasancewa a gaban Allah. AT: "Za su kasance a gaban Allah"
Wannan ne mafarin ƙarshen wahayin Yahaya. Mala'ikan ya na magana da Yahaya a aya 6. A aya 7, Yesu na magana kamar yanda aka bayyana a UDB.
A nan "kalmomi" na nufin sakon da sun yi. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 21:5. AT: "Wannan kalmomi amintattu ne da gaskiya"
Ma'anoni masu yiwuwa 1) kalmar "ruhohi" na nufin tunanin annabawa kuma ya na nuna cewa Allah ya sa su. AT: "Allah da ya sa annabawan" ko 1) kalmar "ruhohi" na nufin Ruhu Mai Tsarki da ya sa annabawan. AT: "Allah da ya ba da Ruhunsa ga annabawan"
A nan Yesu ya fara magana. Kalmar "Duba" na jan hankali ne a kan abinda na biye.
Ana nufin ya na zuwa domin ya yi hukunci. Dubi yadda kuka juya wannan a cikin 3:11. AT: "Ina zuwa in yi hukunci ba da daɗewa ba!"
Wannan na nufin cewa Yahaya ya ƙwanta a ƙasa ya kuma miƙe a kansa don girmamawa ko biyyaya. Wannan muhimmin abu ne a sujada, don nuna biyyaya da bauta. Dubi yadda kun juya irin wannan jumla a cikin 19:10.
Liƙe littafi, rufe littafi ne da wani abu da zai hana wani ya iya karanta abin da ke ciki sai ya yage liƙen. Mala'ika ya na gaya wa Yahaya cewa kada ya ajiye saƙon a ɓoye. AT: "Kada ka ɓoye ... wannan littafin"
A nan "kalmomi" na nufin saƙon da sun yi. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 22:7. AT: "Wannan saƙon anabcin wannan littafi"
Waɗannan jumloli na nufin abu ɗaya ne kuma su na nanata cewa Yesu ya na raye kuma zai kasance a dukkan lokaci.
Waɗannan baƙaƙe ne na farko da ƙarshe na haruffar Greek. Ga ma'anoni masu yiwuwa 1) "wanda ya fara dukka komai da wanda ya gama komai" ko kuma 2) "wanda ya ke rayuwa koda yaushe da kuma wanda zai yi rayuwa kullum." Idan masu karatun ba za su gane waɗannan ba, za ku iya amfani da baƙaƙe na farko da ƙarshe na harshensu. Dubi yanda kun juya wannan a cikin 1:18. AT: "A da Z" ko "na farko da ƙarshe"
Wannan ya na nufin kassancewar Yesu har abada. Dubi yadda kun juya wannan a cikin 1:17.
AT: 1) "wanda ya fara dukkan komai da wanda zai sa dukkan komai su ƙare" ko 2) "wanda ya kasance kafin dukkan komai da kuma wanda zai kasance bayan dukkan komai."
An yi maganar zaman adalci kamar wanke riguna. Dubi yadda kun juya jumla irin wannan a cikin 7:14. AT: "waɗanda su na da adalci, kamar sun wanke rigunansu"
Wannan na nufin cewa su na wajen garin ne kuma ba a yarda su shiga ba.
Kare a wannan al'ada dabba ne mai ƙazanta da ana kuma raina wa. A nan kalmar "karnuka" na ƙasƙantarwa ne kuma na nufin mugayen mutane.
Kalmomin nan "tushe" da "zuriya" na nufin abu ɗaya ne. Yesu ya yi maganar zama "zuriya" kamar ya zama "tushe" ne da ya fito daga Dauda. Kalmomin na nanata cewa Yesu ɗan iyalin Dauda ne.
Yesu ya yi maganar kansa kamar shi ne hasken tauraro da na bayyana a wani lokaci da asubahi kuma ya na nuna cewa gari ya yi kusan wayewa. Dubi yadda kun juya "tauraron asubahi" a cikin 2:28.
An yi maganar masubi kamar sun zama amaryan da za a ɗaura mata aure da angonta, Yesu.
Ma'anoni masu yiwuwa 1) wannan gayyata ne ga mutane don su zo su sha ruwan rai. AT: "Zo ku sha!" ko 2) wannan roƙo ne na ladabi don Yesu ya dawo. AT: "Zo!"
An yi maganar begen mutum don rai madawami kamar ƙishi ne da kuma mutum mai karɓan rai madawami kamar ya na shan ruwa mai ba da rai ne.
A nan "Ina" na nufin Yahaya.
Wannan gargaɗi ne mai ƙarfi na kada a canja komai game da wannan annabci.
AT: "waɗanda na rubuta game da su a cikin wannan littafi"
"Yesu, wanda ya shaida"
"kowanne ɗayanku"